Showing 39001 words to 42000 words out of 73204 words
mutuwarta ta biyota. Cikin mamaki nace "Mimah lafiya? Ke da wa?".
Kafin ta amsa, an sake turo kofar dakin dai an shigo, muka maida hankalinmu ga kofar gabadayanmu. Anty Sarah ta fado dakin, tana karewa dakin kallo, da alamu Mimah ta biyo.
Sai data karewa dakin kallo tsaf, sannan ta jiyo tana amsa mana gaisuwar da muke mata, ta kara da, "Mimah bata shigo nan bane?".
Muka kalli juna ni da Janan, ni ce na fara cewa "a'ah, bamu ganta ba". Daga haka ta juya ta bar dakin. Tana bada baya muka hade kawuna ni da Janan muka kwashe da dariya, tace "baki da kirki wallahi, mutum da diyarshi?".
Nayi dariya nace "kika san ko laifi tayi zata bata kashi? Sannan yarinyar nan tana bukatar fresh air da hasken rana, na tabbata rabonta da waje tunda aka dawo da ita daga makaranta jiya", na maida hankalina wajen inda Mimah ta boye, "Mimah fito, ta tafi".
Ba musu ta fito daga bayan labulen, da gudunta tazo ta haye kan cinyata, na shafa kanta ina murmushi, "meye na gudowa daga gida, laifi kika wa Mommy hala?".
Ta girgiza kai tana dariya, "naa, naki zuwa ta min wanka ne wai zamu raka daddy unguwa, ni kuma Uncle nake so, yace zai kaini wajen granny".
Muka yi dariyar yadda take maganar ni da Jan, na kamo kumatunta ina ja cikin wasa, "uhhhh Mimah, soooo adorable. Amma yi hakuri ki tafi kafin Mommy tayi fushi, ki bari idan kun dawo daga unguwar, sai Uncle din yazo ya kai ki".
Yadda ta dago da sauri, idanuwanta manya, farare tas cike da murna yasa naji zuciyata tayi rashin dadi akan turbar da zan dorata tunda nasan ba lallai hakan ta faru ba, tace "da gaske?".
Na daga mata kai da sauri, "hmm, ni da Janan ma zamu biyo ku muje tare". Tayi tsalle daga jikina ta dire cike da murna, "yay!!".
Gabadaya ni da Janan muka saki dariya, nace "to maza ki tafi kafin ta sake dawowa nan, ki kawo mana tsaraba fa". Ta fita daga dakin da gudu, ni da Janan muka bita da kallo muna murmushi har ta fita, sannan muka cigaba da tsifar da muke yi.
*
Washegari tun da safe, ina jin ko karfe tara bata yi ba, muna kwance muna barcinmu, muka jiyo ana ihun murna daga falo, hakan ya tashe mu babu shiri duk muka tashi zaune muna sosa idanu.
Su Haleemo ne suke ihun 'oyoyo, Mommynmu!', a raina na girgiza kai cike da mamaki. Zuwan suruka gidan surukai tun da safiyar Allah Ta'ala? Ban taba jin haka ba.
Janan ta fara shiga ta wanke baki da fuskarta ta fito, nima na bi bayanta. Bayan mun dan fito more presentable, muka fita falon. Babu kowa, amma muna jin tashin hayaniyarsu daga can dakin Raheemah da yake kusa dana Yaya.
Janan ta ja ni muka leka muka gaidata. Daga ganinta kasan kaga mahaifiyarsu, saboda kama da suke yi da ita gabadayansu, kamar tayi kaki ta tofar. Kallo daya zaka mata kasan cewa ka ga wayayyiyar mace, wadda duniya ta bude mata ido, wayewar kan har tayi yawa. Tun daga kan daurin dankwalin da tayi na yan duniya, da shigar da tayi, hakan yasa na daina mamakin irin shigar dasu Salama suke yi idan zasu fita, daga gani babu tambaya kasan gani suka yi ana yi. Duk da kasancewarta fara, har ma da 'ya'yan nata, amma daga ganin farinta kasan cewa an kara dana kanti.
Ta amsa mana gaisuwarmu tana yatsina kamar taga kashi, tuni naji matar ta fita daga raina. Tun ma kafin a sallamemu, muka sallami kanmu don bamu ga fuskar zama ba a wajen. Muka dafa abinda zamu dafa muka koma daki abinmu.
Yinin ranar nan cur, haka suka wuni a gidannan suna hayaniya da iface-iface kamar kananun yara. Da rana suka zage suka shiga kicin, kada ku sha mamaki idan kuka ji nace muku har uwar, suka dafa abinci, aka soya nama, su kaji, drinks. Muna daki aka kira mu aka ce muje mu ci abinci, muka fita. Ganinsu gabadaya a zaune suna cin abincin yasa muma muka dosana muka zauna, muka zuba namu muna ci, hankalinmu yana kan talabijin da take ta faman aiki.
Mu muka tattara kan kayan muka je muka wanke, suna rarrashe a tsakiyar carpet din dakin suna hira. Ba wai kuma normal hira ba, a'ah, hira ta gulma da abubuwan da basu dace ba. Su ambaci wannan matar, su kwashe mata albarka ita da iyalanta, su kira waccan, itama dai su mata nasu kalar yankar kaunar.
Bayan la'asar aka sayo musu tsire suka baje a tsakiyar falo suna ci, bayan nan suka kure gidan da kidan Ladi mai Kidan Kwarya, suka sha casun su kamar su kadai ne a duniyar.
Tunda garin ya waye bamu ga giccin Yaya a gidan ba, amma naji dadin haka. I mean, ta yaya zai kalli surukar shi tana irin wadannan abubuwan? Bana tunanin zai kara kallonta da mutunci. Sai dai again, ban sani ko hakan ta saba faruwa dama can ba.
Sai yamma likis sannan ta fito da shirin tafiya, dan siririn gyalenta a kafada kamar wata budurwa. Lokacin muna kicin muna dafa abincin dare, suka shigo kicin din. Da yake kicin dinsu hade yake da store, suka shige ciki. Babu kunya babu tsoron Allah suka dinga jidar mata kaya, kifin gwangwani, naman gwangwani, madarar gwangwani, kai tulin kaya kamar wani provision store ne suka shiga. Sai da suka cika mata leda shake da kaya, sannan ta bar gidan.
Kai kawai nake girgizawa, ina gyadawa cike da tsananin mamaki daya daure min jijiyoyin da suke sarrafa magana a jikina. Nayi tur da wannan rayuwa, ko wa ya fada musu rayuwar auren hauka ce, kuma abin wasa ce? Da har uwa zata dinga zuwa gidan diyarta, tayi bushashar da taga dama, ta kwashi kaya ba tare da izinin mai shi ba ta kara gaba kamar wani abin wasa? Ita daya kamata ta musu gyara, idan taga sun dauko hanya irin wannan ta tsawatar musu, amma ita ce take dora su akan wannan hanyar? Lallai suna bukatar gyara kwarai a cikin lamarinsu.
#F.W.A
[17/03 9:37 PM] Jiddah Lawal: 🌟 *⋆☆A ZATO NA...!☆⋆* 🌟
*⋆©Jeedderh Lawals⋆*
*☆⋆11⋆☆*
Kafin yinin ranar Lahdin nan ya kare, gabadaya naji na gama takura da zama a gidan. Na riga na saba da hayaniyar hostel, can hayaniya ce mai cike da nishadi, ko ta tsakanin roommates, classmates, ko abokai. Na riga na saba da rashin shirun can, duk lokacin da naga damar fita, zan dauki hijabi ne in fita kawai, ba kamar gidan Yaya ba. Nan da kofar gida sai ka nemi izini kamar wata matar aure, hayaniya kuma daga ta zage-zage sai ta gulmace-gulmace, don haka ji na nake yi kamar wata fursuna.
Zuwa ranar laraba da Baba ya turo min kudin registration dina, ji na dinga yi kamar wadda take yawo a sararin samaniya don murna. Dungurungum na ki shiga aji na tafi banki na biya kudin makaranta. Aka bani rasiti na tafi ofishin hall admin dake cikin hostel din yanmata na asibitin koyarwa na Shika na kai mata. Bayan ta dudduba files da sauransu dai, tayi assuring dina zuwa ranar Juma'ah zasu bani dakin saboda sai sun bincika wanda bai cika ba. Nayi mata godiya tare da mata sallama, aji daya na samu ranar, daga haka muka wuce gida.
Washegari ranar Alhamis data kasance ranar public holiday, bamu tashi daga barci da wuri ba, muna ta warware gajiyar da muka kwasa cikin wannan satin don lectures dinmu sun fara yin zafi yanzu.
Can da rana, Janan ta fita zata raka wata kawarta da take can cikin unguwar bakin titi. Ina zaune a falo, su Haleemo, Raheemah da Adi na zaune suma suna kallo, aikin da suka saba yi kenan. Yayin da nake wasa da wayata. Babu wanda yake magana a cikinmu sai su da suke hirarsu jifa-jifa. Abinda yake takura ni kenan. Na tsani zama kusa da mutanen da ba zamu yi hira dasu ba, meye amfanin zama a waje dayan to idan ba za ayi hira ba?.
Aka fara kwada sallama daga can waje, duk muka kalli kofar muna jiran a shigo, duk cikinsu babu wanda yayi kokarin tashi. Na mike na fita wajen, ina bude kofar na ci karo da Ummah tsaye. Nayi tsalle na fada jikinta, tayi yar dariyarta mai cike da haiba ta dora hannunta a bayana tana shafawa.
Cikin tsananin murnar ganinta nake gaidata, ta amsa fuskarta na bayyana murmushi sosai. Tace "Na'ilah, idonki kenan ko?".
Na sadda kaina kasa a kunyace, rabon da inje Kaduna har na manta, sai dai a waya kawai muke gaisawa, to yanzun ma a wayar mun kwana biyu, nace "Ummah kiyi hakuri don Allah, kin san al'amuran makaranta ne suka yi yawa wallahi".
Tace "ba wani nan, ke dai kawai kice zumuncinki yayi karanci ne!".
Na fara girgiza mata kai da sauri, "Allah da gaske fa Umma...", sai lokacin na tuna a kofar falo fa muke tsaye. Da sauri na matsa gefe daga cikin falon ina cewa, "Ummah shigo don Allah".
Ta shigo ciki tare da cire takalminta, fararen kafafunta da suka sha lalle jawur gwanin sha'awa suka bayyana. Muna shirin wucewa, Janan ta fado falon. Tana ganin wadda take gabanta ta tsaya cak, "Ummah na?". Sai kuma tayi tsalle ta dafe ta, na matsa gefe ina kallonsu cikin burgewa.
Hannunta ta kama ta fara ja kamar wata karamar yarinya, ni kuma na bi bayansu. A falo babu kowa haka muka tarar dashi kamar ba yanzu-yanzu na bar mutane suna kallo ba. Ga kuma talabijin din tana aikin yi. Gabadayanmu sai da muka dan dakata, sannan Janan ta wa Ummah jagora zuwa dakinta. Ummah tace "ni fa ba zama zanyi ba, yanzun nan zan koma Kaduna direba yana jirana a waje".
Ta turo baki cikin shagwaba, "amma dai kin tsaya ko ruwa ne ki sha ko? Sannan ku gaisa da mutanen gidan".
Ummah tace "suna nan ne? Naji gidan shiru".
Tace "ina zasu je? Yanzun nan da suke kallo anan falo fa, kila sun gaji da zaman ne suka koma daki". Ummah ta lalubi kujerar roba daya da take dakin ta zauna akai, Janan ta fita da sauri zata dauko mata ruwa. Gefen katifa na zauna, Ummah tana tambayata karatu da kuma yanayin damina daya fara shigowa, nace lafiya lau.
Babu jimawa Janan ta dawo dakin hannunta dauke da gorar ruwa mai sanyi, Ummah tana sha ko rabi bata yi ba ta mike tsaye, muma duk muka mike.
Janan tana turo baki ta kamo hannunta ta rike, "yanzu Ummah na maimakon ki jira sai yamma tayi sannan ki tafi?".
Umma tayi dariya tana rungumota jikinta, "Janan kenan, nasan idan kika ji na shigo Zaria ban leko nan ba ba zaki taba bari in samu lafiya bane shi yasa yanzun ma nazo".
Ta kara turo baki, "ni ai dama nasan kin daina so na yanzu shi yasa!".
Ni da Ummah duk muka dara, tace "yanzu idan na daina sonki wa zan so Janan??". Bata amsa ba sai baki data kara turowa.
A kofar dakin Raheemah muka tsaya, Janan ta tura kofar, amma gam, a kulle. Tasa hannu ta dan kwankwasa, nan ma shiru, babu ko alamun motsin mutane. Da ace ba kofar fita daya bace a gidan, duk inda zaka je dole sai kabi ta babbar kofar falo, da sai ince ko ta wata hanyar suka bi suka fita daga gidan. Amma suna zaune fa a falon tazo, daga zuwa bude mata kofa ta shigo har sun bace kamar masu tafiya akan iska? Shin hakan yana nufin da gangan suka buya kenan??.
Ummah ta kallemu tana dan murmushinta na manya, duk da haka zaka karanci damuwa da rashin jin dadi a cikin idanunta. Tace "da alamu ko barci suke yi, kada ku tashe su. Bari kawai in tafi, watarana idan na dawo in Allah ya yarda sai mu gaisa din".
Janan ta daga baki zata yi magana, nayi saurin girgiza mata kai alamun kada tace komi, nasan ce mata zata yi bai ci ace sunyi barci ba yanzu, hakan kuma shi zai ba Ummah damar sanin da gangan suka shige daki suka rufe mata kofa duk da dai ina zargin da kyar idan bata harbo jirgin ba. Janan ta kama bakinta ta datse, muka saka Ummah a tsakiya muka fita.
Sashen Yaya Jameel ta tsaya, nan kuma sai da muka kwashe kwararan mintuna uku muna buga kofa, har mun fara tunanin kila basa gidan ko kuma barcin rana suke yi, mun fara tunanin mu juya kawai, sannan muka ji alamun ana taba kofar alamun za'a bude. Anty Sarah ta bude kofar tare da dan fitowa waje, alamun bata da niyar barin wanda yake buga mata kofar ya shiga ciki.
Sai dai tana ganin Ummah, ta fara fara'a da nan-nan da ita, "su Ummah ne? Ku shigo daga ciki mana! Sannu da zuwa Ummah, sannu, ya hanya?...", ta fara jera mata sannu har ta zauna akan kujera. Ko zama bata yi ba ta fada kicin dinsu da sauri.
Ni da Janan kam falon kawai muke bi da kallo, da alama ta canza kayan daki akan wadanda muka sani da. Wannan wasu irin saitin royal kujeru ne purple da gold, gaskiya sunyi kyau ba karya. Ga kamshi da sanyi mai ni'ima da yake tashi, irin mai warware gajiyar nan. Dama can Anty Sarah ba daga nan ba indai ta fannin tsabta ne, babu na biyunta.
Ta fito daga kicin din hannu niki-niki da tarin kayan motsa baki akan wani katon tray, ta ajiye a gaban Ummah ta hau zuzzuba mata. Sai bayan data zuba mata komi sannan ta zauna a kasa a gefenta tana gaidata cike da girmamawa, Ummahn ta amsa.
Tace "ai kuwa yanzu suka fita shi da Mimah".
Ummah tace "ehh, na hadu dasu a babban gida (main house dinsu), Hajiya babba ce bata ji dadi ba kwana biyu dama shine nazo na dubata kuma sai nace bari in biyo a gaisa, kwana biyu".
Anty Sarah ta sadda kanta kasa tana dan murmushi, "wallahi kuwa Ummah, muna ta cewa zamu leka ku, bamu samu dama bane". Daga ji kasan ta fada ne kawai, amma duk da haka dai tafi wadda ta rufe kofar dakinta ma gabadaya.
Ummah tace "dama haka ne, bari mu wuce mu". Tace "Ummahn tun yanzu? Ba zaki bari mu sauke abinci ba, yanzu aka dora".
Ummah tace "Allah ya amfana, amma nagode". Ta mike, da sauri Anty Sarah ta koma kicin din, sai gata ta dawo da leda a hannunta, ta juye duk snacks din data kai a ciki, ta mikawa Janan. Daga nan muka mata sallama, ta biyo bayanmu har bakin kofa, ta wa Ummah Allah ya tsare hanya, ta maida kofarta ta gamtse. Ni da Janan duk kai muka jinjina kawai, muka takewa Ummah sawu har inda direban daya kawota yake jiranta.
Janan ta bude mata gidan baya ta shiga, ta dora mata ledar wajen Anty Sarah akan cinyarta.
Kafin direba ya ja motar su tafi ta kalleni, "yata Na'ilah, yakamata ki daure watarana ki zo mana weekend mana?".
Na yi murmushi a dan kunyace, "in Allah ya yarda Ummah, zamu zo".
Ta gyada kai, "to madallah, a maida hankali kan karatu dai. Allah yayi muku albarka". Duk muka amsa da 'ameen'. Direban yaja suka tafi. Sai da Ahmad maigadi ya maida kofar ya rufe bayan sun fita daga gidan sannan muka juya. Har muka shiga cikin falon babu wanda ya furta uffan a cikinmu.
Muna shiga falon muka ci karo da Adi da Raheemah a zaune abinsu, suna kallo. Wato da gaske dai suna sane suka gudu daki? Haushin abin ya cika ni, naji kamar in rufe su da duka su duka. Duk da ba ni suka wa abin ba, amma zafin da naji sai naji kamar ni ce naje gidan Yaya, matarshi ta rufe kofar dakinta don kada mu gaisa.
Duk da yadda naso danne zuciyata, hakan bai hana tsakin da nake ta dannewa ya fito ba. Daidai lokacin da zamu wuce su.
Adi ta wani tashi a fusace ta rike kugu, "ke malama waye kike ja wa tsaki a cikin dakin nan? Kin ga sa'an ki anan?".
Na tafi zan zagayeta ni da Janan, tayi saurin kamo wuyan hijabina ta janyo ni, na dawo muna fuskantar juna ni da ita ido da ido, tayi kasa-kasa da nata idanun cikin masifa, "wato yarinyar nan naga alamun wuyanki yayi kauri da yawa irin zama a gidan mutane yayi miki dadin nan. Ke har kin isa in dinga miki magana ki maida ni yar iska?".
Na kalli tsakiyar idanunta, ina kara nuna mata nima ba kirkin nan gare ni ba fa, nace "ai banyi zaton dani kike ba ganin cewa ni din ba yar iska bace. Maganar kiba kuwa da kike cewa nayi, gwanda ni ina girmama wadanda nayi kibar ta dalilinsu, ke kuma me kike yi?".
Ta fara hura hanci, dama gasu tubarkallah kamar kofofin wando, tana daga murya, "kan abu ta kazar abun nan!! (ta kawo zagi ta narka). Lallai yarinya kin daukowa kanki ruwan dafa kanki!. Ni zaki daga wannan tsantsaman bakin naki ki zaga kamar wata sa'ar wasanki? To wallahi na rantse da Allah yau ko ni ko ke a gidannan, sai naga wanda ya daure miki gindi!!".
Wani abin ban dariya shine, gabadayanta bata wuce sa'ar mu ba, abinda nafi tunani kenan tunda ko a tsayi ma na fita. Na kyalkyale da dariya, ina watsa mata wani kallon kaskanci tun daga sama har kasa, duk iskancinta sai data rusuna. Ina shirin maida mata amsa daidai da ita, Janan tayi saurin kama hannuna taja ni.
Adi ta fara ihu, "idan ba tsoro ba ki tsaya mana ki gani?! Wallahi da sai na nada miki na jaki, yadda ko uwar data kawo ki duniya ba zata gane ki ba!!".
Janan dai ta samu ta ja ni daki, ta maida kofar dakin ta rufe, amma duk da haka bamu fasa jiyo zage-zagen da Adi take yi ba, har Salama data fito itama ta sanya baki itama tana nata kalar zagin da gori. Wai anzo musu gida an zaune, an ki tafiya saboda sanyin AC da