Showing 57001 words to 60000 words out of 73204 words
nayi da dubu dai-daya har guda goma, wai inji Yaya inyi sayayyar azumi. Abin ya bani mamaki matuka, na karba nayi godiya. Da yake ma hannuna da kudi, cikin wannan satin wata karamar kwangila da Yaya yayi ta fito, cikin kudin da aka samu ne nima ya dan tsakuro min. Na hada su waje guda na ajiye ban tasar musu haikan ba, nasan a hankali a hankali idan na tattala zasu dade min.
Tunda Yaya Bilal yayi tafiyar nan, kusan kullum anan wajena Janan take shan ruwa. Wasu lokutan ma sai mun gama sallar tarawihi sannan take tafiya gida, idan kuma Allah ya taimaketa Is'haq ya shigo ta nan wajajen, sai ya dauketa su tafi.
Kasancewar ba wani dogon hutu zamu yi ba, yasa na yanke shawarar bin Janan Kaduna kawai inyi sallata acan. Don haka na lallaba Maryam ta karban min kayan sallar da aka bani, atamfa da leshi da takalmi kala daya, ta bayar ta motar haya aka kawo min na kai wajen dinki. Tun dai ana saura kwana biyar muyi tafiyar na kira Baba na fada mishi, yace babu laifi.
Shi dama Yaya da yake ya riga yasan Janan, itama wasu lokutan idan muka samu hutu gajere muna zuwa Gashua da ita. Sannan idan Allah yasa yayo ta wajen Zaria ya biyo mu gaisa, suna haduwa da ita. Ya santa sosai har su Ummahn, saboda haka koda na fada mishi acan zanyi sallah cewa yayi hakan ma yafi, tunda yafi kusa. Shima dubu biyar ya turo min wai in samu karamar atamfa in saya in dinka, na mishi godiya sosai kuwa.
Ranar da muka dauki azumi na ashirin da takwas, ranar muka wuce Kaduna. Sallah ta rage kwana biyu ko daya kenan. Itama Ummah a daren ranar zata dawo, yayin da Yaya Bilal kuma sai washegari.
#F.W.A
[26/03 8:03 AM] Jiddah Lawal: 🌟 *⋆☆A ZATO NA...!☆⋆* 🌟
*⋆©Jeedderh Lawals⋆*
*☆⋆19⋆☆*
Ranar sallah muka sha kwalliyarmu, da safe muka bi yaran gidan muka je idi. Jiya da dare bamu kwanta da wuri ba saboda hidimar abincin sallah. Mun yi miyar taushe, aka soya nama, kaji, har da su snacks. Da safe da zamu tafi idi muka bar yan aiki suna soya masa ta farar shinkafa. Don haka muna dawowa aka fara rabon abinci, gida-gida.
Ummah mace ce mai mutane sosai, saboda haka yinin ranar mutane ne yara da manya, yan gida ko yan unguwa, suna ta shigi da fici kamar wata hidimar biki ko suna.
Gidansu Janan babban gidane, Alhaji Salisu Makarfi mahaifinsu Janan babban mutum ne kuma dan dangi, tsohon soja ne amma yanzu yayi ritaya. Kafin ya auri Ummah yana da mata wadda ta mutu ta bar manyan 'ya'ya maza har su hudu, bayan sunyi aure da Ummah kuma ta haifi Janan, daga baya ne ya sake aurar Usaina babar su Harira da suke kira Yaya. Mutum ne shi na mutane, ya kuma rike zumunci sosai, shi yasa iyalanshi suka taso cike da zumunci da kauna ta yan uwantaka, idan kaje gidan baka banbance dan gida dana waje, baka banbance dan daki da dan daki. Yawancin diyan yan uwanshi a gidan suka girma har suka riski lokacin aure wasu kuma tare da nashi diyan suka yi makaranta wanda shi yake biya musu kudin makarantar. Shi yasa kullum baka raba gidan da mutane.
Samarin gidan da suka taso a gidan, ko bayan da suka yi aure, wasu lokutan idan kaje gidan zaka gansu ko a kofar gida, ko kuma a cikin gidan karkashin daya daga cikin bishiyoyin gidan suna hutawa ko suna hira. Da yake babban gidane, akwai part daban da aka ware wanda mazan gidan suke amfani dashi.
Yau ma haka gidan ya wuni, jama'a ta ko'ina musamman yara jikoki.
Muna dakin Ummah da yammacin ranar, yawanci duk kowa ma a dakinta yake. Ummar yara ma suke ce mata, yayin da suke kiran mahaifinsu Baban yara.
Nayi kwalliya cikin leshin da Baba ya bani, Janan kuma atamfa ta saka. Mu kusan biyar ne a dakin, Ni, Janan, Harira da Firdausi diyan Yaya sai wata Umaimah matar Yayansu Haneef. Danta Shamsu yana kan cinyata yana wasa da motar roba ina taya shi, hirarsu suke yi cikin raha, ni kam rabin hankalina yana ga hirar da suke yi, rabi kuma yana kan tunani akan Muhammad. Yace min zasu shiga can cikin wani kauye a Benin field work tun cikin azumi, yace ba lallai mu dinga samun damar yin waya dashi ba, amma fa yana min text kullum. Nayi tunanin zasu samu su fito daga kauyen tunda yau sallah, amma shiru kake ji. Yau ko albarkacin text din nashi ma ban gani ba. Tun safe nake zuba ido akan wayata, da naji tayi kara sai in zabura in wawureta a tunanina shine, sai inga wani ne daban. Wani lokacin har tsaki nake saki a kule.
Na tura mishi text amma shiru ba reply, idan kuma na kira wayarshi sai inji a kashe. Jikina ya fara sanyi. Nayi kewar mutumin nan, ina kan kewarshi. Sati biyu da muka yi bamu waya dashi, ji nake kamar shekaru biyu ne. Ban san cewa nayi mugun sabo dashi ba sai a wannan lokacin.
Janan ta tabo ni, nayi sauri na kalleta, ban san lokacin da Shamsu ya sauka daga jikina ba, sai yanzu na kula da cewa yana hannun mahaifiyarshi yanzu. Ta kalleni cikin nuna damuwa, da baki ta min alamar tambayar "lafiyarki lau kuwa?".
Nayi saurin girgiza mata kai, alamun babu komi. Nayi kokarin saka bakina cikin hirar da suke yi akan samarin su Harira muna ta kwasar dariya, amma fa lokaci zuwa lokaci idanuna su kan sauka akan wayata cikin fata.
Ummah ta shigo dakin da sauri, su Yaya Hafiz sune manyan mazan gidan. Shine na farko, suna ce mishi Babba saboda sunan mahaifin Baban Yara gareshi, sai Yaya Auwal, Yaya Haneef da Yaya Kabeer. Janan itace take bi musu, sai Harira, Firdausi da kuma auta Faisal, kanin Janan ne. Shekarunshi sha daya yanzu. Yaje gidan Yaya Hafiz hutunshi na sallah Abuja shi yasa bamu hadu dashi ba.
Karamar walima ce suke hadawa, a lokaci irin wannan, duk suna taruwa a gidan duk da kasancewar suna garuruwa mabanbanta wajen aikinsu duk cikinsu Yaya Haneef ne kadai yake zaune a Kaduna. Ina ga saboda kara karfafa zumuncinsu ne. Ummah ce akan hidimar hada musu abincin da zasu ci, shi yasa tun dazu ta kasa zaune tsaye ita da Yaya, mu kanmu tare damu aka yi aikin abincin da rana, sai bayan mun gama ne sannan muka yi wanka muka shirya.
Tace "wai dama kuna nan a zaune kuka barmu da aiki? Ku taso maza-maza aje a shirya wajen can, har sun fara zuwa".
Firdausi tace "Ummah ai kece da kin daukar shawara wallahi, sai da Yaya Babba yace za'a dauko wadanda zasu kula da hidimar nan, kika ce a'ah, sai anjima kuma kizo kina ta jajen ciwon kafa da baya!". Su Janan suka kwashe da dariya, nayi dan murmushi ina girgiza kai.
Ummah ma dariyar tayi, ta wa Firdausi dakuwa, "karbi nan ja'irar yarinya kawai. Da karfina da lafiyata sai in ki hidimtawa diyana? Idan suka dauko yan aiki ni ina zaune, to meye amfanina kenan?".
Harira tace "ki huta mana Ummah, muma kinga da yanzu ai bamu tashi daga zaman nan ba!".
Ummah tace "wai zaku taso ko kuma sai na zo na tada ku?". Babu shiri muka tashi gabadayanmu, muka bar Umaimah a falon.
Can bayan gidan inda aka ware musu kicin dinsu na gargajiya muka wuce tunda acan ake aikin. Akwai makeken kicin daya sha kayan zamani na yayi, amma ya zama na kwalliya kawai. Saboda basu cika amfani dashi ba, idan kaga matan gidan a ciki sai dai idan karamin abu ya kaisu, dafa ruwan zafi ko kuma wani abu dai. Yaran gidan ne ma suke amfani dashi.
Tuni an riga an zuzzuba komi a cikin abinda ya dace, saboda haka muka fara daukar kayan tare da wasu daga cikin yan aikin zuwa sashen maza. Babban falo ne sosai daya saitin manyan kujeru, dinning room shima babba, sai kuma dakuna. A dinning room din muka shirya komi, wasu daga cikinsu suna falo suna hira, wasu kuma suna waje yayin da wasu suke can kofar gida.
Muka shirya komi da zasu bukata, hatta da cokali, drinks da ruwan sha sai da muka ajiye komi sannan muka bar wajen.
A cikin yan hirar falon muka hango Yaya Bilal da Yaya Jameel a zaune, suna ta hirar sports da Yaya Auwal. Yawan zuwa yasa suka saba da yan gidan musamman mazan kasan zumunci irin na maza, shi yasa in ka gansu kamar yan uwa.
Zamu wuce Yaya Jameel ya kira Janan, mu kuma muka yi gaba. Can ta biyo bayanmu da kudin barka da sallah wai inji shi. Yau kam barka da sallah da muka samu daga yan gidan, da baki masu zuwa gidan Allah kadai yasan iyakarta. Ban taba zuwa sallah gidan ba sai wannan karon, shi yasa abubuwan duk suke zuwa min a mamakance.
Daga nan makotan su Ummah muka wuce, kannen Al-Mustafa suka zo muka hadu dasu ana ta cafta da kashe flashes din hotuna, kamar kada yinin ranar ya kare. Bamu samu kanmu ba sai da dare.
Muna falon Yaya da dare, hayaniyar gidan ta ragu kowa ya tafi gida, wasu kuma sun nemi makwanci. An gyara ko'ina ya fito fes, yana ta kamshi.
Janan ta ritsa ni da tambaya akan abinda yake damuna, nace mata babu komi.
Tace "wai karamar yarinya kike son maida ni ne? Tun da safe fa a haka kike, kina da wanda zaki gayawa matsalar ki ne bayan ni?". Ina shirin bata amsa da wata babu komi din, Firdausi ta shigo falo hannu dauke da babban tray da aka hada fruit salad a ciki. Dama shi muke jira, don haka duk muka sauka kasan carpet din dakin muka zauna.
Shiru babu wanda yayi magana tunda muka fara ci, sai talabijin da take ta faman aiki kawai duk da ba kallon ba muke yi. Firdausi ce ta fara sako hirar, cikin alamun gulma tace "ni fa nayi zaton Anty Ameerah zata tsaya ne anan, ko kuma tazo yau".
Da yake ta Kaduna suka sauka, sai da suka fara biyowa ta nan a jiyan. Gabadayanmu munyi zaton anan zasu zauna, har Ummah ta fara maganar azo a gyara musu daki, sai kuma suka ce wucewa zasu yi, amma shi Yayan zai dawo yau. Babu wanda ya tambayesu dalili.
Janan tace "lallai ma, wasa kuke yi da Anty Ameerah wallahi. Jiyan ma ganin idon Yaya ne yasa tazo, da ita kadai ce wallahi ko yace tazo ba zata zo ba".
Firdausi tace "amma dai kinsan tafi Anty Raheemah ko? Na tabbata ko tare suke da Yaya ba lallai tazo nan ba".
Harira tace "kinsan ai tunda Ummah ta hana aurensu da Yaya Bilal daga farko, take kulle da ita. Amma ni nafi son ta akan Anty Ameerah wallahi, bata da kirki ko kadan!".
Janan ta gyada kai cikin amincewa, yayin da Firdausi ta jefa mata harara, da yake shekara daya ce a tsakaninsu, kusan kansu tsaya, zasu iya yin sa'a da Maryam. Tace "Lallai ma baki san kirki ba, ke ni fa da mutum ya dinga gwada min mutunci saboda ganin ido, gwanda muyi ta zuba rashin mutunci dashi nasan dama can ba so na yake yi ba!". Kafin kace me! Muhawarar ta koma kan wanda aka fi so tsakanin matan Yayan. Nan da nan falon ya rikice da hayaniya. Ni kam ina gefe, ina zuba musu dariya idan wata ta fadi abin ban dariya.
Yaya ta shigo falon, muka yi tsit muna kallonta. Tace "idan kuka kuskura daya daga cikin Yayanku yaji wannan magana sai ya bata muku rai. Ina ruwanku da rayuwarsu? Ba tasu bace ba? Kuma kuji da taku mana!". Ta shige dakin barcinta.
Muka bita da kallo har ta shige, hirar dai ba'a daina ba, dorawa aka yi daga inda aka tsaya sai dai wannan karon cikin yin kasa-kasa da murya.
Firdausi ce mai cewa "ni wallahi wani lokacin har tausayi yake bani, kamata yayi ace zuwa yanzu ya samu yayi settling a waje daya, da matanshi da 'ya'yanshi. Amma ace kullum yana hanyar Abuja, Kaduna da Zaria? Baya gajiya ne wai?". Duk maganar da suke yi sai lokacin na gyada kai cikin nuna amincewa, ni kaina ina mishi wannan tunani. Sai dai a ganina, hakan duk shi yaso. Kasan cewa matan nan a karkashinka suke, to meye na zama kana rara-gefe akan tituna kamar wani mara galihu? A ganina idan ya nuna musu karfin ikonshi na mijin da yake aurensu, a sukwane zasu bishi.
Harira tace "ni kaina wallahi ina tausaya mishi, ko meye mafita a rayuwar aurenshi?".
Janan tace "aure kawai ya kamata yayi. Ya samu wata rikakkiya da tasan sirrin rayuwa ya aura". Suka fara gyada kai da sauri.
Kofar da aka turo aka shigo yasa muka maida kanmu can. Yaya Bilal da Yaya Jameel suka fado falon, jin mu kake yi munyi kus, kamar ruwa yaci mu. Har suka zauna akan kujerun falon. Yaya Jameel ya kallemu cikin murmushi, "gulmar me ake yi ne?".
Da sauri muka hau girgiza kai, Firdausi tace "laa, babu komi Yaya. Kawai hira ce muke yi!". Yaya Jameel ya kwashe da dariya.
Cikin yayun biyu, shine mai fara'a da faram-faram, yafi Yaya Bilal sakin fuska nesa ba kusa ba. A sauran halayya ma suna da banbancinsu, duk da ko a kamanni ma suna da banbanci. Shi Yaya Jameel yafi kama da Ummah da Janan, daka gansu shi da Janan kasan kaga yan'uwa. Shi kuwa Yaya Bilal ina tunanin ko mahaifinsu ya dauko, saboda kamanninsu da Ummah ba wai wani can bane. Sai dai kawai abubuwan da ba'a rasa ba, wanda haduwar jini yake haddasawa.
Duk muka gaida su cikin girmamawa suka amsa. Yaya Bilal ne yace "ina Yaya?".
Firdausi ta tashi taje ta kirata, tare suka fito da ita, ta samu kujera dan nesa dasu kadan ta zauna. Suka dan zame daga kujerar suka gaida ta, ta amsa cikin fara'a, bayan sun gaisa suka ce mata wucewa Zaria zasu yi yanzu, tace "ba zaku hakura ku kwana ba ku kuwa? Dare ya fara yi, karfe tara fa!".
Yaya Jameel yace "ai babu komi Yaya, in shaa Allah zamu isa lafiya, nan ne da Zaria fa".
Tace "to shikenan ai, Allah ya tsare ya kuma kiyaye hanya. Ubangiji Allah ya albarkaci rayuwa data iyali". Duk suka amsa cike da jin dadi, suka mata sallama suka bar falon muma muna musu Allah kiyaye.
Suna tafiya muma duk muka tashi. Dakin mata muka wuce muka yi shirin kwanciya. Kananan kadajen kwatako guda uku ne a dakin, sai spare din katifa, ita nake shimfidawa ina kwanciya akai. Ni kam ina kwanciya na rufa da bargo har ka a kaina, ina jinsu har lokacin suna tafka mahawararsu naki motsi. Damuwar cikina na ma ta ishe ni. Shirun Muhammad ya tsorata ni, ko dai shima irin na Umar zai min??!.
*
Kwana biyu hidindimun sallah sun riga sun wuce, amma banda gidan su Janan. Har yau wannan gida a cike da iyali yake yini. Yau Assabar, kwana biyar da gama sallah kenan, gobe kuma muke shirin komawa Zaria. Har yau shiru babu labarin Muhammad, nayi text har na rasa abinda zan rubuta tunda wayar bata shiga, ina cikin damuwa. Wani laifi na mishi dana cancanci wannan hukunci haka?
Yau tare muka wuni da iyalan Yaya Hafiz, sai yau suka zo tasu barka da sallah din. Matarshi mace ce mai mutunci da sanin yakamata, haka ma 'ya'yansu masu shiga rai.
Da yamma da kanta ta saka mu a mota dasu Harira muka shiga kasuwa tayi musu sayayyar komawa makaranta. A makarantar yanmata ta kwana ta FGGC Munjibir suke. Muma sai gamu mun shigo cikin sayayyar. Muna dawowa suka mana sallama suka tafi.
Washegari muma muka yi sallama da su Ummah, suma su Firdausi da safe aka tafi aka kaisu tasu makarantar. Mun fito daga dakin Baban Yara, mutum mai tsananin mutunci da kirki, yana ta mana addu'o'i da fatan alkhairi, muka samu su Ummah a falo. Tuni an fitar mana da kayanmu waje, nan muka musu sallama, har waje suka raka mu suma. Direban da zai kaimu yana tsaye a jikin motar gidan, yana ganin fitowarmu ya shiga ya tayar. Muka sake sallama dasu Ummah muka shige motar, direba ya ja muka fita daga gidan muka dau hanyar Zaria.
#F.W.A
[26/03 8:56 PM] Jiddah Lawal: 🌟 *⋆☆A ZATO NA...!☆⋆* 🌟
*⋆©Jeedderh Lawals⋆*
*☆⋆20⋆☆*
Tun da asubahi naji wayata tana kara babu kakkautawa, washegarin ranar da muka dawo kenan wadda ta kama litinin. Ko a cikin nisan duniyar mafarki, nasan kalar ringtone din, na kuma san ko waye mai kiran tun ma kafin in duba. Saboda haka duk da a cikin magagin barci nake, ban kasa rarumar wayata ba na latsa tare da kaita saitin kunnena na fara watsowa Muhammad tambayoyin da suka jima suna susar bangon zuciyata:
"Muhammad! Lafiya dai ko? Kayi rashin lafiya ne? Accident kuka yi a hanyarku ta dawowa daga Benin? Ko kuma wayarka aka sace maka ko ta lalace? Kayi welcome back ne? Ko kuma ka fara mantawa da ni ne?... Muhammad?!". Na saurara da tambayoyin da nake jera mishi sakamakon jin shiru da nayi ta daya bangaren da yake.
Sai daya ji na saurara sannan naji ya saki murmushi mai sauti, yace "naji dadi da kika damu dani har haka baby na... Sannan na farko babu abinda ya sameni, waya ta bata lalace ba, sannan lafiyata kalau kamar dai yadda kike ji na!".
Na hade fuska tamkar ina gabanshi, "shine kuma sati biyu cur ka dauke min wuta babu wani bayani. Kana ganin jerin texts din dana dinga turo maka a cikin wadannan kwanakin kuwa?".
Yayi shiru kamar ba zai yi magana ba, can kuma yace "kiyi hakuri, ina da dalili!".
Duk wani haushi da takaicin dana dinga tarawa ina makalewa a cikin