Showing 33001 words to 36000 words out of 73204 words

Chapter 12 - A ZATO NA

30 Oct 2024

1768

kuma? Kuskure ne nasan dana riga na tafka shi, amma ina neman afuwarki don Allah. Wallahi ban san abinda ya hau kaina ba, ok, na sani. Gajen hakuri ne irin nawa, amma wallahi na gane kuskurena, ba zan kara ba, don Allah ki bani dama Na'ilah, na miki alkawarin hakan ba zata sake faruwa ba".
Naji zuciyata ta fara yin sanyi da jin hakan, nace "how sure are you? Ta yaya zaka tabbatar da cewa nan gaba ba zaka sake tare ni a cikin mota, trying to touch me inappropriate ba?".

Ya hau girgiza kai da sauri, "I assure you hakan ba zata sake faruwa ba, na miki alkawarin ba zan kara taba ki ba tare da izinin ki ba har auren mu!".
Nace "idan kuma hakan ya sake faruwa fa?".
Yayi shiru yana kallona, nace "magana daya ce Umar, idan abu makamancin haka ya sake faruwa, we are over! Dama kasan hakan ta taba faruwa, yazo ya sake faruwa yanzu, to babu na uku. Idan kuma muka rabu, mun rabu kenan, ka yarda?".
Ya gyada kai, "it's not as if zan sake maimaitawa, but yeah, na yarda. Fushin ki ba abu bane da zan yi marmarin sake gani ba koda wasa. Yanzu dai kin yafe min?".
Nayi jim ina tunani, na yafe mishi? Ya riga yayi convincing dina, kuma yayi alkawarin hakan ba zata kara faruwa ba, saboda haka meye aibun yafe mishi a ciki? Don haka na gyada kaina, ya saki murmushi a tausashe wanda ya sanya ni sakin murmushin nima, "oh thank God! Wallahi baki ji yadda na damu ba, God, I miss you wallahi".
Nayi murmushi kawai, yayin da naji wani sanyi yana kwaranya a cikin raina. Ban sani ba, na yafe mishi din da nayi ne, ko kuma na dawowa gareni da yayi bane. Kafin in sake daga baki inyi magana, muka ji kiran sallah, ya kalleni yana murmushi, "bari in wuce masallaci to, zan kira ki zuwa anjima".
Na gyada mishi kai tare da shigewa gida.

Bayan mun ci abincin dare a dakin Janan, ta zauna a gefen katifa suna waya da Al-Mustapha saurayinta, ni kuma na shiga whatsapp chatting. Sakon mutumin nan na dazu shine abinda na fara gani, ni na ma manta dashi.
Amsar tambayar dazu dana mishi da safe ce ya turo min, "kamar yadda na fada miki, na san ki farin sani. Kuma ina matukar kula da lamuran wadanda suke very special a gareni, don haka ba wani abin mamaki bane".

Na maida mishi da amsar 'haba? Ta yaya aka yi na zama very special a gare ka?'.
Babu jimawa sai ga reply ya shigo, 'oh, you are very very special in fact! Idan nace zan miki bayani zamu jima a haka, to cut it short, ina jin ki a cikin raina fiye da yadda kike tsammani'.
Haka kawai na tsinci kaina da darawa. Wani abu game da mutumin is very fascinating, yet so familiar. A karo na kusan biyar tunda muka fara chatting dashi yanzu, da naji a jikina duk yadda za ayi mutumin nan ya sanni fiye da sani na, kuma nima ko yaya ne na san shi. Sai dai duk hakan bai dameni ba, yadda naji hira dashi ta dauke min hankali, shine abinda ya bani mamaki ya kuma daure min kai a lokaci guda. It's a first.

Mintunanmu talatin kacal muna hira ta hanyar musayar rubutattun kalmomi, sai gani kwance rigingine a tsakiyar daki, ina kallon fankar dakin dake juyawa, waya a hannu ina ta faman rubutu, yayin da lokaci zuwa lokaci sautin dariya zai fito daga baki na, walau na sani ko ban sani ba. Hakan ya kan sa Jan, da har lokacin tana kan waya, zata juyo ta kalleni cikin alamun tambaya, amma bata tambayeni ba.

Zuwa lokacin da yayi min sallama akan wani aiki da zai tafi yayi, ba ni kaina ba, hatta zuciyata da gangar jikina naji sun aminta da mutumin. Wanda hakan a karan kanshi ma abin tambaya ne, na farko ban san mutumin ba, babu abinda na sani dangane dashi sai sunanshi, yana aiki da wani kamfani da yake sarrafa takardu, shikenan. Dana tambayeshi yana da mata? Sai yace ba ga ki nan ba? Hakan yasa naji sautin bugun zuciyata kamar zai tsaga tsakiyar kirjina zuciyar ta fito.
Tsakanina da Allah ban so muka yi sallama dashi ba, na tabbata idan zamu kwana muna chatting dashi ba zan taba damuwa ba a cikin raina, kai a takaice ma zan so hakan ba kadan ba. Muka yi musayar sai da safe, ya tafi bayan ya turo min 'sleep tight!', ya Allah, ban taba jin dadin ganin kalmomin nan daga kowa ba a rayuwata sai a yau din nan.
Yana sauka naji gabadaya chatting din ya fita daga raina, don haka nima na sauka.
Na lalubo jakata na ciro littafai daga ciki na fara karatu da bibiyar practicals din da muka yi yau.

Sai wajen karfe goma Jan ta gama tata hirar da Almunta, (yadda take kiranshi). Ta juyo ta kalleni tana murmushin tsokana, "fadan masoya hutu, wato saboda kun shirya shine kike wannan glowing?".
Nayi murmushi kafin na jefa mata harara, "ni kada ki min sharri wallahi".
Tace "wani sharri? Ga abu nan a fuskarki, kin kuwa ga yadda kike ta zuba murmushi sanda kuke chatting dinnan? Har wani dariya kike yi, irin soyayya tayi dadi dinnan!".

Na danyi frowning ina kallonta, a hankali nace "ba da Umar nayi chatting ba dazu".
Ta hangame baki cikin mamaki, "wasa kike yi ko? I mean, idan ba Umar ba, waye to? Yanzu da kika fadi haka sai na tuna Umar baya dogon chatting, wanene muka samu??". Ta karasa fada tana daga min gira cikin alamun tsokana.
Na jefeta da littafin hannuna, ta cafe tana dariya, "fada min mana!".
Na mike ina tattara kayan dana baza a wajen na maida su cikin jaka. Bandaki na fada kai tsaye na barta tana ihun, "ko shekara zaki yi a ciki sai kin fito kin fada min wanene yarinya!". Dariya kawai na saki mai sauti. Nasan kafin in fito ta manta da zancen.

Har mun kashe wutar daki bayan mun kwanta, Janan ta kira sunana, na amsa a dan gajiye da kuma barci daya fara cin idanuwana, tace "wai me ya hada ki da Umar ne da?".
Nayi sighing a hankali, "abinda ya faru ya riga ya faru Jan, mun riga mun shirya dashi, that's all that matters. Tone-tonen abinda ya riga ya faru, babu abinda zai mana, don haka ki manta da maganar".
Tace "of course sugar, baki da matsala dani".
Kaunarta naji tana kara ratsa zuciyata, fahimtarta da goyon bayanta a kullum suna kara sa inji ta can cikin zuciya da ruhina. A hankali nace "nagode Jan".
Ina jin sautin murmushin data saki cikin duhun dakin, "sai da safe Na'ilah!".
Nima na maida mata martanin murmushin duk da nasan ba lallai ta gani ba, nace "sai da safe Jan!". Na juya barin damana, tare da rufe idanuna.

Daren ranar mafarkai nayi masu yawa, da yawa daga cikinsu sun kunshi wani mutum da yake ta nanata kalmar, "ke ce Matata!," kamar waka.



-Afuwan, in shaa Allah gobe zan turo mai yawa, wannan dinma aradun Allah da kyar hannuna da idanuna suka bada hadin kai nayi typing dinsa. Thank you all.








#F.W.A



[17/03 9:34 PM] Jiddah Lawal: 🌟 *⋆☆A ZATO NA...!☆⋆* 🌟


*⋆©Jeedderh Lawals⋆*




*☆⋆14⋆☆*





Halin dana sameta a ciki ya sanyayar min da jiki, gabadayanta ta fita daga hayyacinta don ma sun ce wai a hakan ma tayi dama. Yayan da Anty Sarah kadai na tarar a asibitin, a cewarsu wai Raheemah bata jima da barin asibitin ba. Na zauna a gefen gadon tare da shafa gefen fuskarta cike da tausayi, har ta dan fada, gashi yanayin numfashinta bai gama daidaituwa ba har yanzu.
Muna zaune a hakan har rana tayi, Yaya yake ta shiga da fita daga ofishin likita zuwa inda aka kwantar da ita din. An samu tayi barci, bayan anyi mata allura har aka samu numfashinta ya daidaita.

Da lokacin tafiya masallaci yayi, Yaya ya tafi akan cewa zai turo Raheemah tazo ta zauna damu, sai dai har aka fito daga masallacin, har muma muka yi tamu sallar bamu ga alamunta.
Lokacin daya dawo ina kan sallaya a zaune, Anty Sarah kuma tana zaune akan farar kujera tana jan carbi, ya ajiye ledar take away a gefen gadon, yace "ga abinci kuci, likitan yace zamu iya tafiya gida da ita idan ta tashi".
Anty Sarah tace ta koshi, nima nace na koshi da yake cikina a cike yake.

Karan text daya shigo wayata ne yasa na maida hankalina ga wayar, na duba naga daga Muhammad ne. "Hey baby!", abinda ya turo kenan. Na kara maimaita text din cikin mamakin kalmomin, motsin da Jan ta fara yi ne yasa na wancakalar da wayar gefe na nufeta da sauri. Yaya ya taimaka mata ta zauna akan gadon, gabadayanmu sannu muke jera mata tana amsawa a hankali.

Yaya ya dauko madarar ruwa ya fasa tare da mika mata, ta amsa ta sha kamar rabi ta maida mishi sauran, yace "har kin koshi?", ta gyada mishi kai.
Anty Sarah tace "dama ba lallai ta iya cin abinci yanzu ba".
Yaya ya umarcemu da mu hada kan kayanmu, ya miko gyalen Janan na yafa mata. Da taimakona ta sauko daga kan gadon, ina tallabe da ita a jikina muka fita daga asibitin zuwa wajen da Yaya yayi parking din motarshi. Ya bude mana gidan baya duk muka shige ciki. Bayan ya gama clearing din komi a asibitin, yazo ya shiga motar ya tayar muka tafi.

Yaya Bilal ya kashe motar a ainihin inda suke ajiye motocinsu, farko-farkon shiga gidan, daga nan tafiya ce zaka yi kadan daga bangaren damar ka da zata sadaka da wani zagayayyen karamin garden, grass carpet ne shimfide a wajen, wajen yana da fadi sai kuma bishiyoyin mangwaro, gwaiba, gwanda, ayaba, da sauran kayan marmari dai. Daga gefen garden dinne aka shimfida doguwar hanya da interlocks, kanana masu kyau, itace zata sadaka zuwa bangaren Yaya Bilal. Wadda kuma tayi barin hagu itace zata sada ka da bangaren su Anty Sarah.

Kan Janan yana kan kafadata, wani barcin ne yake kokarin daukarta. A hankali na tasheta, muka fito daga motar. Anty Sarah ta mana fatan Allah sauwake, ta wuce sashenta muna mata godiya. Rabin jikin Janan yana jikina, na tallabota muka wuce saboda har yanzu jikinta babu karfi sosai. Yaya Bilal yana binmu a baya hannu rike da makullin motarshi da kuma ledar take away din da yayi.

Gabadaya mutanen gidan suna falo, wannan karon a zaune suke kawai suna hira sabanin kallo da suka saba yi a yawancin lokuta. Raheemah ce ta fara ankara da shigarmu falon, ta mike tana zuba sannu da zuwa cikin alamun borin kunya, kannenta suma suka mike, "ah.., har kun dawo ashe? Yanzu muke cewa mu tashi mu koma fa! Sannunku, ya jikin?".
Muka amsa musu ciki-ciki, Yaya ya umarce ni da in taimaka mata Janan zuwa dakinta, don haka na gewaye su muka wuce zuwa dakinta. Bansan Yayan yana bayanmu ba sai dana ji karan sake bude kofa bayan na maida na rufe.
Na kwantar da ita akan katifarta, na ja abin rufa na rufa mata daga kafafunta zuwa rabin jikinta, tuni barci yayi awon gaba da ita. Yaya ya miko min ledar hannunshi, yace "ki samu ki zauna kici abinci haka nan, ki zauna ki huta kema".

Na karbi ledar, kaina a kasa, wata irin kunyarshi naji ta lullube ni wanda na rasa dalilin hakan. Nace "to, nagode, Allah ya amfana".
Ya girgiza kai a hankali, wani irin kallo a cikin kwayar idanuwanshi da suka sanya naji jikina ya dauki wata irin kyarma, ikon Allah! Ko dai bani da lafiya ne nima?! Yace "ni ne da godiya Na'ilah! You've no idea how grateful I am right now!".

Subhanallah!! Me ke shirin faruwa da ni ne? Jin fitar sunana daga bakinshi ya haifar min da jin wani irin abu a cikin raina, shin ko mai yasa hakan? Hakan bai taba faruwa dani ba! Sannan muryar Yaya Bilal, yau naji tana min kama da wata murya hallau, matsalar na kasa tunawa ko a ina ne na ji muryar.
Ban san lokacin daya juya ya bar dakin ba, sai karar rufe kofa naji.
Na bude ledar na fito da take away din ciki, guda biyu ne da lemukan fanta suma guda biyu, don haka na dauki daya na ajiye, dayan kuma na barsu a cikin ledar na fita domin in mikawa Anty Sarah nata.

A falo Yaya Bilal ne a tsaye kikam, kamar wani tsohon soja. Su kuma suna lafe akan kujeru kamar wadanda aka kama sun nannagawa sarki garinsu karya. Daga yanayin fuskar shi da take a cune da yadda bakinshi yake kumfa, zaka san cewa fada yake musu, fada kuma bana wasa ba. Tunda nake dashi ban taba ganin fadan shi ba sai yau. Janan tana yawan cewa Yaya Bilal yana da fada, duk da cewa baka sanin fadanshi sai ka mugun tabo shi sannan, to da alamun yau dai an tabo shi.

Ni dai na kada kai na fita. Yau kofar gidan na Anty Sarah a bude take, abin mamaki, na tura kofar na shiga. Tana kicin. Yanayin gidanta da ka shiga kicin zaka fara tararwa, sai falo da kuma bedrooms. Ta dago ta kalleni lokacin dana shiga, nace "kofar a bude take, shi yasa na shigo kai tsaye".
Tace "babu komi, ina tsammanin Mimah ne yanzu shi yasa, ya aka yi?".
Na mika mata ledar hannuna, "dama abincin da Yaya ya kai ne na kawo miki".
Murmushi naga tayi wanda ya bani mamaki, tace "da kin barshi wallahi kun ci, kin ga abinci ma nake shirin dorawa yanzu".
Nace "a'ah wallahi, ai guda biyu ne ya kawo".
Tace "to shikenan, na gode. Ya Janan din?". Nace "ta koma barci", daga haka na juya na fita daga gidan.

Har na koma can, Yaya fada yake yi, "... In fada muku gaskiya ba zan dauki wannan cin mutuncin ba! An fada muku ita yar aiki ce? Ko kuma bata san ciwon kanta ba? Waye bai san tana da asthma ba, da zaku barta tayi aikin da zai tado mata shi?!". Ya dire maganar yana sauke numfashi cikin bacin rai.

Raheemah ce ta samu ta iya magana duk cikinsu, "kayi hakuri, hakan ba zata kara faruwa ba. Ita ce tace zata yi ai...".

Tun ma kafin ta karasa ya katseta, "ke kuma saboda rashin hankali sai kuka barta ko? Na fa san abinnan ba tun yau yake faruwa ba, ina sane, iyaka gudun ruwanku ne kawai nake so in gani. Wallahi Tallahi, kunji rantsuwar da nayi, ba zan yi kaffara ba! Idan makamancin haka ya sake faruwa, gabadayanku sai kun bar min gidana. Kuma daga yau, duk wadda take son yin girki, ta shiga ta girka abinda zata ci ban yi mata iyaka da komi na gidannan ba, amma kun gama cin abincin Janan. Ba zata kara muku girki ba, haka ko tsinke ta tsince a gidannan da sunan shara ko gyara Allah zamanku a gidan nan ya kare! Kun dai ji na fada muku!!". Ya wuce dakinshi fuuuu! Kamar kububuwa tare da maida kofar dakin ya gamtso kamar tashin duniya. Mu kuwa duk muka bi bayanshi da kallo baki a dage.

Maimakon hakan ya dan zame musu darasi, su dan saduda koda na dan lokaci ne, inaa. Tunzura su ma yayi.
Adi ce ta fara jan tsaki, "mtswww, aikin banza! Yo mun taba matseta muka ce dole sai ta mana girki ko aiki? Kashi zamu bata idan bata mana aikin bane? Har da za'a zauna ana zagin mutane akan wata banzar bazara, gidan banza dana wofi! An fada musu mu bamu da gidan iyaye ne da za'a zo ana zaginmu ana mana gori?".

Salama ta cafe maganar, "ke ma dai kya fada. Aikin banza dana wofi, da dai ace bamu da gidan uba ne da sai muji haushi, to mun gode Allah muna da gidan uba, kuma ba a inda ba'a son zamanmu muke zaune ba! An fada mishi mu mabaratan abinci ne??".

Raheemah kuma tana ta kokarin sanya su suyi shiru a dan tsorace, "don Allah kuyi shiru mana!", ko kuma tace "don Allah kuyi a hankali kada ya jiyo ku ya sake fitowa!". Na girgiza kai kawai, wato shi dai mai rai ba'a taba iya mishi. Allah ya kyauta.
Na barsu anan na koma daki. Har yanzu Janan barci take yi. Na duba cikin kayanta na ciro doguwar rigar leshi mara nauyi, na dauki kayan na shiga bandaki na sanya na fito, na sake zama a gabanta.

Har bayan sallar la'asar bata tashi ba, bayan nayi sallah na zauna naci abincin da Yaya ya kawo mana, na maida sauran na rufe dana koshi. Ina nan a zaune naji karan buga kofa, na tashi na bude. Ga mamakina Anty Sarah ce a tsaye da kwando a hannunta, na mata sannu tare da bata hanya ta shiga cikin dakin. Tace "har yanzu bata tashi ba?".
Nace "wallahi har yanzu, kila an hada mata da allurar barci ne". Ta gyada kai idanunta akan Janan din, "Allah ya bata lafiya". Nace "ameen".

Ta min nuni da kwandon data ajiye, tace "ga wannan idan ta tashi sai taci, ba yawa".
Nace "Allah ya saka da alkhairi". Ta amsa tare da tashi ta fita, na bi bayanta na maida kofar dakin zan rufe. Su Raheemah suna falon a zaune har yanzu, ta wuce ta gabansu. Ina tunanin basu cika shiri dasu ba, kila ma hakan ce ta goge mu, ko kuwa wani abu daban? Naga kwana biyu kamar ta dan sassauto.

Sai wajen karfe biyar sannan ta farka, jikinta ya dan yi karfi ba kamar dazu ba. Na taimaka mata zuwa bandaki tayi wanka da ruwa mai dumi. Bayan ta fito na zuba mata abinda Anty Sarah ta kawo, wani irin abu ne tayi da kifi ban ma san sunanshi ba, kamar ta soya kifin, kamar kuma dahuwar ruwa ce, ga veggies da abin yasha sai tashin kamshi yake yi kuwa. Na zuba mata ta samu ta dan ci, tayi sallar azuhur da la'asar

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login