Showing 42001 words to 45000 words out of 73204 words

Chapter 15 - A ZATO NA

30 Oct 2024

1779

naman kaza, ni abin ya ma so ya bani dariya.
Na tsaya a tsakiyar dakin ina ajiye ajiyar zuciya daya bayan daya da sauri-sauri. Ta kalleni, "haba Na'ilah! Sau nawa nake fada miki ki daina biyewa wadannan mutanen? Kin san cewa ba ajinki bane ki zauna kuna sa'insa dasu ba ko?".
Na harareta cike da fushi, "wai sai ki dinga magana kamar baki wajen lokacin da take sauke min kwandon zagi da dibar albarka!".

Tace "ko ma menene dai, rashin tankawar yafi tankawar dai. Meye alfanun musayar kalamai, meye a cikin hakan?".
Na watsa hannuwa sama frustrated, "koma dai menene. Allah ne ya rufa mata asiri bata kai ga daga hannunta a kaina ba, da wallahi sai na baje shegiya yau a gidannan!!".
Janan ta girgiza kai kawai, ta fada bandaki tana furta "Allah ya shiryeki ke kam!". Nace "ameen", cike da izgilanci.

Sai dana huce sannan na zauna a gefen katifa. Sakon text din mysterious daya shigo wayata a lokacin ne ya kara sauko da zuciyata kasa sosai. Na hau karanta sakon ina kara maimaitawa kamar mai harda, daga karshen sakon nashi ya rubuta *'talk to you soon babe!',*
Shin hakan yana nufin mun kusa yin waya dashi? Nayi tsalle na sake dira akan katifa ina dan ihun murna, Janan da fitowarta daga bandaki kenan ta kalleni baki a dage, "ke kuma lafiyarki lau kuwa? Yanzu-yanzu kina fushi, yanzu kuma kina ihun murna again?".
Na harareta cike da wasa, fuskata na dauke da murmushi.


Washegari Juma'ah, muka shiga asibiti. Muna fita ajin karfe goma na yiwa ofishin hall admin tsinke. Nan ta bani lambar daki da teller, sai dana fara zuwa bank na biya kudin sannan na sake dawowa wajenta nayi clearance. Dakin mu uku ne, ka'ida mutane biyu ne a kowane daki, amma kasancewar wannan karon muna da yawa shi yasa suka maida shi uku per room. Ni duk bayanan da take yi ba jinta nake yi ba, ban damu ko mu hudu ko biyar zamu zauna ba, bukatata kawai in samu dakin.
Tana miko min makullin dakin, na karba na mata godiya na bar ofis din.
Dakin na fara zuwa na gani, wadanda suke zaune a dakin basa nan lokacin. Na sanya key na bude dakin, na kare mishi kallo sannan na maida dakin na rufe na koma class.

Lokacin period ta biyu ya ma kusa cika, don haka na samu wasu seats da aka tanada a gaban classes na zauna ina jiran su fito. Kafin su fito na ciro wayata na turawa Yaya text din abinda ya faru. Babu jimawa ya turo min da sakon taya murna da tambayar yaushe zan koma cikin hostel din gabadaya? Nace mishi sai ranar Lahdi, nasan duk abinda zanyi Janan ba zata bari in koma gobe asabar ba.
Ina nan har suka fito, na tari Janan a hanya muka dauki hanyar barin asibitin kasancewar mun gama da ranar. A hanyar nake fada mata yadda muka yi da hall admin da kuma ranar da zan koma hostel din. Daga ganin yadda ta turo baki nasan bata yi na'am da maganar ba, don haka na canza maganar kawai zuwa wata.

Yau ma kamar yawancin ranaku, gidan babu kowa muka same shi. Muka tura kofar dakin Janan muka shiga, kayan jikinmu muka fara ragewa muka dauro alwala muka zo muka tada sallah.

Da yamma wajen karfe hudu da rabi muna tsakiyar falo a kwance muna kallon 'Baaghi' a tashar Zee World. Meat pie din da Anty Sarah ta miko mana ne daga dawowarmu muke ci da lemun fanta na pineapple a kusa damu.
Gardama muke akan tsakanin jarumi Tiger Shroff da Hrithik Roshan wa yafi wani iya rawa?.

"ina fada miki Hrithik shine oga, ni gani nake duk duniya babu kamar shi ma. Kin san dai idan fannin rawa ne, babu wanda zai iya gwada mishi ko wanene kuwa, kada ma ayi zancen physique, halitta, kyawu, and his eyes! Ya Allah, how I love his eyes!!". Na fada dreamily ina kara zooming hoton shi dake cikin wayata ina kara nuna mata idanunshi da suka fito sosai a daukar da aka mishi.

Janan ta kada idanu sama, "nasan da haka, amma ki duba, Hrithik ya fara tsufa yanzu, Tiger shine jarumi mai tasowa yanzu, sannan idan halitta ce, shima fa Tiger ba baya bane, ga iya lankwasa jiki da acting".

Na mike zaune sosai, sautin muryata ya fara yin sama, "ni fa komi zaki ce, babu abinda zai canza min tunanina, Hrithik ne nawa. Sannan wa yace miki Hrithik ya tsufa? As in kin kuwa ga yadda yarintar shi take kara fitowa yanzu?".
Ta daga baki kenan zata musa, sai ga sautin, "idan kun gama musun naku, zaku iya taimaka min da wadannan kayan?".

Da sauri muka daga kai zuwa inda muka ji sautin maganar. Yaya Bilal ne tsaye a tsakiyar falon ya nade hannu a kirji. Sanye yake da suits ash color, ya sanya tie baki mai ratsin ash color akan white linen shirt din daya sa a kasan suit din. Cikin yan sakannin dana yi ina kare mishi kallo, naji ina raya 'wannan shine ainihin misalin wanda yarintar shi take kara fita kullum', a cikin zuciyata.
Da sauri duk muka tashi muna mishi sannu da zuwa. Ya amsa mana yana dan murmushi, "wato maimakon ku zauna kuna debate ko quiz akan karatu, sai ku zauna kuna gardama akan mazajen mutane ko? In anyi magana kuma sai ku ce duk duniya kun fi kowa yin karatu ko?".

Janan tace "wallahi Yaya ba haka bane, yanzun ma hira ce kawai, arashi ne aka yi kai kuma kazo a daidai lokacin".
Yace "whatever, kuzo ku taya ni dauko kaya a waje". Ya juya ya fita, muma muka bi bayanshi. Doguwar riga baka kirar kasar Saudiya ce a jikina, dama gyalenta yana kan kujera don haka na dauke shi na dora shi a saman kaina.
Kayane zube a kofar falon, kayan miya ne, vegetables, su doya da irish potato. Ahmad yake ta daukosu daga cikin mota yana ajiyewa a kofar falo, bakin kofar falon nan ne iyakar da Yaya ya musu. Ba'a barinsu su wuce nan.
Muka fara daukar kayan zuwa kicin sai da muka gama gabadaya. Yaya ya zauna akan kujera a falo yana cire takalmin kafarshi, Na dauko ruwa mai dan sanyi a cikin firjin na dora akan karamin tray na roba da cup, na kai gabanshi na ajiye.
Janan ce ta tsiyaya ruwan ta mika mishi ya karba yana furta "thank you".

Sai daya kusa shanye ruwan gorar gabadaya, ya ajiye kofin ya koma jikin kujerar ya jingina. Ya cewa Janan "gabadaya kayan can ku raba su uku, kashi daya ku mika gidan Jameel, dayan ku zuba su a cikin wani abun za'a kaiwa Ameerah, sauran ku ajiye su na nan ne". Muka ce "to".
Yace "ina Raheemah ne?", muka kalli juna ni da Janan, itace tace "bata nan!".
Ya karkata kanshi gefe daya kamar cikin mamaki, yace "ina taje?". A lokaci daya muka ce "bamu sani ba!".
Yayi shiru kamar cikin tunani kafin ya girgiza kanshi a hankali, ya tashi tsaye, "shikenan, kuje". Muka wuce kicin abinmu.

Muna gama aikin daya sanya mu, muka dora girkin dare. Sai gab da magriba sannan suka dawo gidan. Raheemah ce ta leko kicin din, muka mata sannu da zuwa, ko amsawa bata yi ba ta fara jero mana tambayar "yaushe baby ya dawo? Ya tambayi inda nake?".
Janan ce ta amsa mata, ni kam juyawa nayi ina juya miyar da muke yi, tace "tun dazu dai, kuma ya tambayeki muka ce kin fita".

Taja wani dan siririn tsaki ta juya ta fita, muna jiyota ita da Adi a falo tana tambayarta me zata ce mishi idan ya tambayeta inda taje? Adin tana cewa "meye na wani rikicewa don ya dawo baki nan? Kawai ki fuske ki ce mishi wajen Momcy kika je mana!".
Raheemah din tayi ajiyar zuciya, "baki san abinda muke ciki bane kwanannan, a saman ruwa muke dashi wallahi!".
Adin taja tsaki tana cewa "sai kiyi kuma, na tabbata ko tambayarki ma ba zai yi ba". Daga haka suka shige daki.


*


Washegari na hade kan kayana tsaf waje guda, nayi wanki da guga da sauransu. Ranar Lahdi Yaya ya bada mota da yamma, Is'haq direban gidan wanda yake musu aikace-aikace ya kaimu hostel ni da Janan. Sai ranar muka hadu da roommates dina, daya musulma ce yaren Ibira, sunanta Murjanatu, dayar kuma Esther Christian ce. Janan ta taya ni hade kan kayana waje guda muka shirya su, daga nan ta min sallama ta tafi. Na rakata har waje ta hau bus ta tafi, sannan nima na juya na koma hostel.








#F.W.A
[17/03 9:38 PM] Jiddah Lawal: 🌟 *⋆☆A ZATO NA...!☆⋆* 🌟


*⋆©Jeedderh Lawals⋆*




*☆⋆12⋆☆*





"Ok, spill the beans, me yake faruwa dake ne?".
Janan ta tambayeni. Fitowarmu daga labour ward kenan da yammacin ranar Laraba, mun tsaya a wani karamin gidan cin abinci dake nan mini market din asibitin. Na fasa lemun Dudu na jefa abin zuka a ciki ina kallonta cike da alamun tambaya, "ban gane ba, me yake faruwa dani?".
Tace "na fahimci tun shekaranjiya kamar jikinki a sanyaye yake, wani lokacin ana miki magana amma ba kya ji, ko kinji sai in ga kamar ba kya wajen saboda kinyi nisa a cikin tunani. Wani abu yana damunki ne? Ko kuma baki da lafiya ne? Kin gaji da zaman hostel dinne?".

Nayi murmushi jin tambayarta ta karshe, na girgiza mata kai, "ko daya, kawai dai...", ta dago kanta da sauri tana kallona cikin sauraren jin mai zan ce.
Na kawo ajiyar zuciya na sauke tare da girgiza kai, "na kasa fahimta ne ni kaina wallahi, kwana biyun nan sai in ga kamar Umar yana min kauce-kauce, amma ban tabbatar ba".
Ta kalleni a nutse bayan ta taune egg roll din data kai baki ta hadiye, ta kora da lemun la Casera. Tace "me yasa kika ce haka? Ko kuma ince me kika gani?".

Nace "na farko kusan sati daya kenan rabon da in kira Umar ya daga, daga farko ya fara biyo baya, ya cikani da maganganu marasa kan gado akan wai aiki ne yayi yawa, to yanzu yau kwana uku kenan rabon daya daga kirana ko kuma ya kirani ma. Sannan baya maido min da replying din message idan na mishi. Ke duk chats dinshi babu inda ban bishi na mishi magana ba, amma a banza, na fara damuwa".
Tace "haba, kada ki wahalar da kanki a banza mana, kamar yadda yace, zata iya yiwuwa aiki ne ya sako shi a gaba!".
Nace "shine kuma zai kasa daga wayata balle messages dina? Gaskiya sai dai wani abu daban, amma ba wannan ba. Ko lokacin da suka yi posting dinsu, abubuwa ai sun fi haka tsanani, amma a hakan yake samun lokaci ya amsa kirana har ma yazo ya ganni, balle yanzu".
Ta gyada kai, "haka ne kuma. Amma ki kara bashi lokaci dai, baki san abinda yake faruwa dashi ba, zata iya yiwuwa wani abun ne daban".
"to shikenan!". Na fada ina karasa juye sauran lemun daya rage a bakina, na jefa robar cikin kwandon ajiye shara na kalli Jan data gama jefa nata itama, nace "muje muyi sallah a hostel ko? Karfe hudu yanzu zata yi, kuma kinsan hudu da rabi ya kamata mu koma".

Duk muka mike muna daukar jikkunanmu, muka dauki hanyar hostel. Hostel dinsu yana da nisa da ainihin cikin asibitin, tafiyar kusan mintuna goma sha biyar ce. Muna isa alwala kawai muka yi, muka yi sallah, muka koma ward din da aka kaimu wannan satin.
Muna zaune a reception, Janan tana rubuce-rubuce, ni kuma ina gyara wasu files. Karan shigowar kira a wayata ya katse mu, abu na farko daya fara fado min rai kawai shine Umar. Na rarumo wayar da sauri, a raina ina raya kalar dibar albarkar da zan mishi. Sai dai duk wasu alwasai na sai suka koma can bayan zuciyata, sakamakon ganin mai kiran ba Umar bane, Maryam ce.

Na dan matsa can gefe kadan saboda hayaniyar mutane na daga kiran, maimakon muryar Maryam sai naji ta Aliyu. Babu kunya wai gaisheni yake yi, "Yaya Na'ilah ina yini?".
Mamaki ya kama ni, tunda na dawo babu wanda ya neme ni a gidan, daga iyayen har 'ya'yan. Kiran Aliyu a yanzu yana nufin abu daya ne,
Na daure na amsa da "lafiya lau Aliyu, ya kuke?". Ya amsa da lafiya lau, tare da fara kame-kamen tambayar ya karatu na da sauransu dai. Daga karshe dai ya dire a ainihin dalilin da yasa yayi kiran daga farko.

"Kati zaki turo min, subscription dina ya kusa yayi expire!". Wani lokaci sai in dinga mamakin ko ajiye ni yayi a matsayin personal bank account dinshi, da zai dinga cirar kudi a duk lokacin da yaga dama?
Sai dai Allah bai halicceni da riko ba, sannan bana rikon mutum inyi amfani da hakan idan yana bukatar abu a wajena in wulakanta shi. Bugu da kari ina son 'yan'uwana, ina kuma iyaka bakin kokarina wajen ganin na kyautata musu, na hidimta musu, matukar ina dashi ina musu iyaka bakin kokarina. Ba yabon kai ba, ina hana kaina ko cikina in ciyar da nasu cikin ko wata bukata tasu.
Su sun san da haka, ina zaton shi yasa suke amfani da wannan damar suna taka ni yadda suke so.

Nace mishi "har katin nawa kake so kuma?".
Yace "na dubu daya da dari biyar ma ya isa".
Na girgiza kai, ni kaina wannan watan ban yi subscribtion ba, kodayake Allah ne yasa Janan ta mana ni da ita. Nace "zan turo maka zuwa anjima, yanzu muna cikin ward sai mun fita".
Yace "babu damuwa, Maryam ma na bidar katin dari biyar". Babu ko godiya ko karin bayani, ya maidawa Maryam wayarta sai itace ta min godiya sosai. Daga nan muka kashe wayar.

Saboda haka muna fita daga ward din da misalin karfe shida na yamma, na tsaya a kasan ginin na sayi kati na tura musu. Zan yiwa Janan rakiya kamar yadda na saba yi mata, tace "yau dai an hutar dake, ga Almu na can yazo daukata".
Na kalleta ina daga mata gira cikin tsokana, "shi yasa tun dazu baki yaki rufuwa, masoyin usul yazo gida!".
Janan ta kai min duka a hannu tana yar dariya, "ni bana son sharri irin naki fa!".

A haka muka karasa jikin motar Almun Jan, silver Matrix 56 ce, daga ganinta ko dai sabuwar yayi ce ko kuma sabuwa ce dal, yadda take ta sheki da walwali. Yana ganinmu yayi kasa da gilashin motar yana murmushin shi da kullum baya barin kan fuskarshi.
Al-Mustafa kyakkyawan namiji ne, fari, dogo, mai dan jiki. Yana da kirki, haka gabadayan yan'uwanshi suke, wadanda muka sani kenan. Mazauna garin Kaduna, a takaice ma a unguwar NDC unguwar kaji, unguwar su Ummah ainihin gidansu yake. Yayi degree dinshi anan Jami'ar Kongo, yanzu haka lauya ne mai zaman kanshi anan Kaduna din. Soyayyarsu da Janan ta samo asaline tun daga zamanin da take sakandire, suka kulla soyayyarsu mai tsafta, gashi har yanzu suna tare, kuma ana son juna. Ba shi kadai ba, hatta da yawancin yan gidansu sun sanni, na sansu saboda yawan zuwa Kaduna da nake yi, kuma muna yawan zuwa can gidan ko kuma su kannenshi su zo mana. Daga ganinsu kuma Janan ba zata samu matsalar zama dasu ba, saboda suna da kirki da sanin yakamata.

Na gaishe shi a nutse, har ya hada da yar tsokanar daya saba min idan muka hadu, muna ta dariya. Daga karshe dai Janan ta shiga gaban motarshi ya tasheta yana kallona, "to Na'ilar Janan di ta, in shaa Allah a yau dinnan zan wuce Kaduna, sai dai in ce sai Allah yayi mana dawowa kuma".
Na gyada kai ina dan murmushi, "haka ne, to Allah ya tsare hanya. A gaida mutanen gida".
Yayi murmushi, "in ce musu me? Wadda ta guje su shekara da shekaru babu waiwaye tana gaida su?". Ya fada cike da tsokana.
Nayi dariya sosai, "ni wannan korafe-korafe naku dai, in Allah ya yarda hutunmu na gaba zan samu inje Kadunar nan dai, ko kwana biyu ne in muku hakanan".
Yace "inaa, ai rike ki zamu yi sai kin karas da hutunki sannan zamu sake ki".
Na girgiza kai ina murmushi, nace "to ai shikenan, yadda kuka ce haka za ayi. Ku gaida gida". Na musu sallama na wuce don nasan idan na tsaya zamu iya kaiwa har magariba anan muna hira, abin kamar a jinin shi yake, idan kuna hira dashi sam baka sanin lokaci yayi, kafin ka ankara sai dai kaji ka kwashe awanni dashi kuna hira. Ko kuwa yanayin aikinsa ne?.

Har na karasa hostel ban ji daga Maryam ko Aliyu ba, hakan yana nufin katinan sun shiga kenan. Idan naji kiran waya ko please call me bayan na tura kati, hakan yana nufin nayi kuskuren lamba kenan, dana tura kuma zan ji su dif, sai kuma bukatar hakan ta sake tasowa. Maryam ce ma ke kokarin kira lokaci zuwa lokaci haka nan a gaisa.

Akan katifa dana nade ta da zanin gado yellow mai dauke da kwalliyar Malam buda min littafi da wasu kyawawan furanni na zube, da uniform dina da komi har takalmin toms baki da yake kafata. Dakin babu kowa, da alamu basu dawo ba ko kuma sun shiga makotan dakunanmu. Yau ba karamar gajiya muka nada ba, yadda majinyata suka dinga karakaina a ward din da aka tura mu yasa bamu samu mun zauna ba ko da wasa. Na lumshe idanuna a hankali, ina jin gajiyar jikina na neman rinjayata barci ya daukeni. Da sauri na tashi zaune.
Kayan jikina na hau cirewa, na rataye su a jikin kusa dake jikin bango, na daura zanin atamfa tare da dora wata T-shirt baka akai, hula na dora akaina na fita tare da kulle dakin. Can kasa na sauka, da yake a sama muke. Sai dana tsaya a tap na debi ruwa, na daura alwala sannan na ciccibi bokitin ruwana na koma sama.

Murjanatu na tarar a dakin, na mata sannu kawai. Ita kadai take hadamu da ita tunda nazo dakin, wani irin girman kai ne da ita, tunda ta ganta da wata akwalar 406 data

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login