Showing 30001 words to 33000 words out of 73204 words

Chapter 11 - A ZATO NA

30 Oct 2024

1773

ihun neman taimako? Tambayoyin suka yiwa zuciyata yawa. Ban san lokacin da gwiwoyina suka saki ba, na zube akan gwiwata a wajen. Allah kadai yasan iya lokacin dana dauka a wajen, ban ma san a wani hali nake ciki ba. Kai ban ma san ina hawaye ba sai da naji lema da alamun gishirin hawaye akan lebena sannan na ankara. Sai kuma vibrating din da wayata take tayi babu kakkautawa. Na daga na ga sunan Umar yana rawa a jiki, tsaki na ja nayi declining, yana katsewa wani kiran ya sake shigowa. Wayar na dauka gabadayanta na kashe.

Na mike na kakkabe jikina tare da share hawayena. Sai dana tabbatar da na dawo cikin nutsuwata sannan na wuce cikin gida. Su duka suna falon suna kallo banda Janan, na musu sannu na wuce ba tare dana jira naji sun amsa min ko basu amsa ba.

Janan tana tsaye a tsakiyar daki da waya a kunnenta, ina shiga ta sauke wayar, "yanzu fa nake kiran wayarki, sai kuma naji ta kashe".
Na kalli wayar kafin na kalleta, "kashe ta nayi".
Ina tunanin bata kula da yanayin da nake ciki ba sai a lokacin, da sauri ta matso wajena, fuskarta dauke da alamun damuwa, "lafiyarki lau? Me ya faru??".
Na girgiza mata kai, "babu komi fa!".
Ban jira amsarta ba na yaye gyalena na rataye na shige bandaki. Alwala na dauro na fito.

Janan ta bini da kallo har na shimfida abin sallah, bata ce komi ba. Har na gama shafa'i da wutiri, na fara shirin saka kayan barci. Tasan ko ta dameni ma babu abinda zan iya gaya mata, sai ma karin bacin rai da hakan zai haifar min, don haka taja bakinta tayi shiru, tasan duk lokacin dana sauka don kaina, zan fada mata. Babu boye-boye a tsakanina da ita.
Instead sai tace "idan kin gama kafin mu kwanta, ki zo in danyi briefing dinki akan abubuwan da muka yi wannan satin".
Kai kawai na iya gyada mata. Dana gama shiryawan, naje gefenta na zauna, ta dauko littafinta ta bude ta fara min bayani.
Zuwa lokacin da muka gama, na dan fara saukowa daga fushin, haka ma zafin zuciyata ya dan lafa, amma duk da haka abin yana makale a cikin raina.
Kai har lokacin dana kai ga kwantar da jikina akan katifar Janan da niyar inyi barci, abin yana makale a cikin raina. Nasan cewa shi da fita har abada.















*☆⋆08⋆☆*





Da azumi muka tashi washegari, bayan munyi sahur, wanda ni ruwa kawai na iya sha, muka yi nafiloli har aka kira sallah, muka yi.
Janan ta tashi zata fita bayan gari ya fara yin haske kadan, lokacin na gama azkar dina kenan. Na dubeta cike da alamun tambaya, tace "breakfast zan je in hada, kiyi wanka kafin in fito".
A zato na ko haka dokar gidan take, don haka naga bai kamata in barsu suyi aikin su kadai ba. Na tashi na saka karamar hijabi akan kayan barcina, duk da ba masu fitar da jiki bane, kuma Janan tace Yaya a gidan Anty Ameerah ya kwana, still ba zan dauki chances ba. Sai dai ina zuwa kitchen din nayi turus, ganin Janan ita kadai a tsakiyar madaidaicin kicin dinsu tana kokarin dora tukunya akan gas. Na shiga ina karewa kicin din kallo, "ina sauran?".

Da sauri ta juyo ta kalli inda nake, ina tunanin bata tsammaneni a wajen ba shi yasa taji abin unexpected, "su wa fa?". Ta tambaya lokacin da take kokarin zuba mai a cikin tukunyar.
Na kada idanuwa, "ina nufin sauran wadanda kuke zaune a gidan dasu, ba zasu fito kuyi aikin tare bane?".
Ta danyi murmushi cikin girgiza kai, "ni kadai nake aikin dama can!".

Na zaro ido, "say what??!". Ta kwashe da dariya, na harareta, "wannan ba abin dariya bane Jan, this is serious! Ta ya za ace gardawan banza suna kwance sun saki baki da hanci suna barci, ke kuma zaki dage ki girka musu abinci? Wow! Ko da kike cewa suna sakar miki aikin gida, ban yi zaton har da wannan ba ai".
Tayi yar dariyarta a sanyaye, "ni ban ga abin daga jijiyar wuya a cikin wannan lamari ba. Na riga na saba ne, har ya zame min jiki wallahi. Sannan yawanci kafin Yaya ya wuce Abuja yana biyowa ta nan yayi karin safe, shi yasa nake tashi in hada, sai kuma abin ya zame min jiki."

Duk bayanan da take yi sai lokacin ta dago ta kalleni, ganin yadda nake kallonta kamar wata tababbiya yasa ta sake sakin wata dariyar, "da gaske ba wani abu bane, ni wallahi ban damu ba. Besides, su suke yin abincinsu da rana, wanda sai na ga dama nake ci".
Nace "ai shikenan, me zan taya ki dashi ne?".
Ta jefo min peeler, na cafe, tace "fara da dankalin can mu gani".
Na fara fereye dankalin yayin da taci gaba da soya kayan miya da tayi grating.

Cikin dan lokaci kankani na gama firar, muna yi muna hira jifa-jifa, duk da dai shiru yafi yawa. Na kunna stove tare da dora frying pan da mai a ciki, yana yin zafi na fara zuba dankalin da na yanka a tsaitsaye, bayan na zuba maggi da dan gishiri, wata dabarar soya chips da Fatsu ta koya min.

Muna gamawa ta dauko kula da flask, ta zubawa Yaya nashi da kunun gyada, fari tas dashi yana ta kamshi, ta kai falo ta ajiye.
Muna cikin maida kayayyakin da muka yi amfani dashi bayan mun wanke, muka jiyo karan bude gate. Janan ta leka ta tagar kicin din da take fuskantar gate, ta jiyo ta kalleni "Yaya ne!".
Na ajiye frying pan a inda yake na juya ina kallonta, "bari in shiga wanka kawai, bakwai ta kusa yi", kai kawai ta gyada min saboda hankalinta yana kan sauran kunun gyadar da take juyewa a cikin wani babban silver flask. Na fita daga kicin din.

Ina shiga daki na hada kayan da zan bukata na fada toilet. Bandakinta babba ne, yana da fadin shi daidai misali da kuma kayan amfani na zamani. Nayi amfani da sabulunta na 'Vix' mai kamshin sandalwood nayi wanka. Ban tsaya bata lokaci ba don nasan bamu da cikakken lokaci.
Ina gama wankan nayi amfani da karamin towel na kafe jikina. A cikin bandakin na zura doguwar rigar material ruwan kasa mai laushi, kafin na fita.

Janan tana gefen katifarta daure da towel, waya a hannu, da alamun jirana take yi. Ta daga kai ta kalleni lokacin da taji na maida kofar bandakin na rufe.
"wai fada kuka yi ne ke da Umar?".
Naji wata irin faduwar gaba lokacin da naji ta ambaci sunanshi. Tunda na tashi da safe nake ta gujewa tunaninshi a cikin raina. Na hana kaina sakat, da naji sunanshi ko fuskarshi na shirin fado min a cikin raina sai inyi saurin sako wani abun daban.
Na daka fuska ina zama akan kujerar dake gaban dressing mirror dinta, "me kika gani?".

Cike da tuhuma tace, "ban sanar dake bane kawai, amma tun jiya da dare yake kiran wayata da turo texts, sai daina dagawa nayi. Yanzu ma tun dazu yake kira, yace in baki hakuri".
Nayi kwafa kawai ban amsa mata ba, ta tashi tsaye tazo ta dafa kafadata, "ki daure ki daga kiranshi don Allah, baki san abinda yake son ya fada miki ba. Nayi zaton kun wuce matakin irin wannan fadan ke dashi?".
Na harareta ta cikin madubin, "bamu wuce ba, kuma ma in Allah ya yarda wannan shine karo na karshe da zamu yi fada dashi, we are done Jan!".

Fuskarta bata nuna komi ba, babu mamaki, farinciki ko akasinsa, sai kai kawai data gyada, tace "bari inyi wankan nima, amma ki dai daure ki bude wayarki, ko ba don shi ba saboda mutane masu nemanki. Yaya Mudan ma ya kirani lokacin da kina wanka, shima dai ya nemi wayarki a kashe".
Sai lokacin naji nayi murmushi, nace "wato har yanzu dai Mudan dinnan yana nan ko? Kinsan Yaya ya tsani sunan nan".
Tayi dariya, "ramawa kura aniyarta kenan!". Daga haka ta shige bandaki. Nayi dariya kawai naci gaba da shirina.

Zuwa lokacin dana gama hada komi da zan bukata, Janan ta fito daga wanka itama ta fara shiri. Da wayarta nayi amfani na kira Yaya, yana jin ni ce ya fara zuba min korafin ina na shiga? Excuse din dana bashi shine 'wayar ce babu caji tun jiya'.
Yace "su Malam ne nima suka dameni da kira tun safiyar yau, wai suna ta kiran wayarki su ji in kin sauka lafiya kuma a kashe, shine hankalinsu ya tashi!".

Ni gabadaya na ma manta ban kira su ba a jiyan. Na manta yadda suke ne, musamman idan zanyi tafiya, hankalinsu baya kwanciya sai sunji muryata na tabbatar musu da saukata lafiya sannan.
Nace "afuwan, ka basu hakuri don Allah. Wallahi mantawa nayi ban kira su ba, idan nayi caji zuwa anjima zan kira su".
Yace "to shikenan, Antynki tana gaishe ki", daga nan inda yake ina jiyo sautin muryarta tana kiran sunana, nayi murmushi nace "a gaishe ta itama, sai anjima". Na kashe wayar tare da ajiyeta a gefena.

Ina zaune har Janan ta gama shirinta, ta dauki jaka tana zuba jotters da handouts dake tsakiyar dakin a yashe inda muka barsu jiya da muka gama karatu. Na mike nima ina kara gyara kayan jikina. Muna gamawa muka fita daga dakin, ina kallo tasa key ta rufe dakin ta maida key din cikin jakarta.
Har yanzu falon babu kowa, gabadaya gidan ma shiru kake ji kamar babu masu rai.
Sai da muka fita daga gidan muka dauki hanyar da zata sada mu da babban titi inda zamu hau bus, tace "Yaya sauri yake yi, shi yasa bai tsaya kun gaisa ba, ya bar sakon gaisuwa dai".
Nayi murmushi, "babu damuwa, idan ya dawo zamu gaisa ai in da rabo".

Ta zage zip din bayan jakarta ta ciro dubu biyar, sababbi kar ta miko min, na amsa ina kallonta fuskata cike da alamun tambaya, nace "me zanyi dasu?".
Ta daga kafada, "Yaya yace a baki!".
Na zaro ido, "what?...," a lokaci daya kuma ina mika mata kudin, "A'ah, gaskiya ba zan amsa ba, this is way too much!".
Ta harareni, "sai ki bari in yazo ki maida mishi da hannunki. Kafin kuma ki fara wani tunani, wannan ba wani abu bane. Kamar kudin albashi ne daya saba bamu gabadayanmu har su Haleemo, saboda hidimar makaranta da sauransu, kin gane?".

Na karkata hankalina gabadaya na maida kanta, "duk sati yake baku 5k, kawai saboda hidimar makaranta?".
Ta gyada kai tana kallona, irin ba wani big deal bane a wajenta.
Nayi yar dariya, "Woah, dole a makale a gida aki tafiya, kuma dole ace kwadayi nazo yi ba wani abu ba. Maganar gaskiya though, ba zan iya amsar kudin nan ba gaskiya, kiyi hakuri ki amsa".

Ta fara huro hanci alamun na fara bata haushi, "sai kiyi kuma tunda kin saba, ni na gaya miki sako aka bani na baki, in kinga dama kada kiyi amfani dasu, ki jira har sai Yaya ya dawo sai ki maida mishi ki gani idan amsa zai yi!".
Na dan dakata da tafiyar da nake yi, "meye abin fushi kuma anan Jan?".
Tace "ke din ce ai idan ba gani kika yi ana miki wuta ba, baki cika fahimtar abu ba".
Nace "to naji, na karba, kuma na gode, Allah ya saka da alkahiri".
Ta harareni cikin wasa, "abinda yakamata ki ce tun dazu kenan, ba ki tsaya neman magana ba!".
Nayi dariya kawai jin abinda tace. Muka cigaba da takawa har muka fita bakin titi. Shatar keke-napep kawai muka yi saboda lokaci daya fara kurewa.

Allah ya taimaka muka isa akan lokaci. Kasancewar duk practicals ne muka yi, kuma abubuwa basu fara yin nisa ba, yasa bamu jima ba muka taho gida. Karfe biyu ma bata karasa ba muka dawo.
Wannan karon ma napep muka hau. Muna sauka, wata hadaddiyar Range Rover tana shiga gidan. Muka bita a baya muma muka shiga gidan. Ganin ta gangara can bangaren Yaya Jameel, yasa na kalli Janan, "Anty Sarah ta sake mota kenan?".
Tace "da alama, ko kuma ta gidansu ce. Tunda ko yau da safe motar bata nan".

Wadda muke maganar a kanta ta bude gidan gaba ta fito. Matar Yaya Jameel ce. Saratu da muke kira, ko ince ake kira da Sarah, cikakkiyar yar gayu ce, wadda tasan fashion, kodayake kamar akan abinda naji ance tayi karatu kenan, ko kuma dai wani abu mai kama da hakan. Daga yanayin yadda take shigarta, takunta da gudanar da al'amuran rayuwarta, zaka tabbatar da cewa wayayyiyar mace ce, wadda ilimin boko ya ratsa ta. Gidansu gabadayansu yan boko ne. Kai ita kanta a kasar Germany naji ance taje ta hado degree dinta. Matsalarta daya, rashin shiga mutane. Zaku iya kwashe sati cikakke baku hadu da junanku ba, ni da yake dama ba zuwa gidan nake yi sosai ba, zan iya cewa na kwashe watanni fiye da biyar ban ganta ba.

Muka karasa wajen da take, daidai lokacin da diyarsu mai kimanin shekaru biyar, Ruqayyah wadda suke kira Mimah, ta fito daga daya gefen mai zaman banza dauke da jakarta da lunch box.
A lokaci daya muka gaidata ni da Janan, ta amsa tana kama hannun Mimah da take kokarin isowa gareme, jininmu ya hadu da ita sosai. Halin mahaifiyarta na shiga part dinta ta rufe ta kuma hanata fitowa yasa bamu haduwa da ita sosai, sai lokaci zuwa lokaci.
Tana gamawa amsawa ta latsa key tasa motarta a lock, taja hannun diyarta suka tafi.

Duk da haka sai da Mimah ta juyo tana daga mana hannu, mu duka muka daga mata hannun muna murmushi har suka shige part dinsu, ta rufo. Ni da Janan muka kalli juna muka sake yin murmushi, kafin muma muka shige nasu part din.

Adi, da Haleemo suna kicin lokacin da muka shiga, Raheemah kuma tana zaune tana sana'ar kallo, ban san ina Salama ta shiga ba tunda bamu ganta ba. Mu dai muka musu sannu, muka shige daki ba tare da mun damu da kallon banza da aka bimu dashi ba.

Bayan la'asar muka fita waje ni da Janan muka sayo fruits a bakin titi. Muka zo muka hada fruits salad da kayan shan ruwa. Muna cikin soya yam balls, Salama ta shigo kicin din. Babu wanda ta yiwa ko sannu a cikinmu, ta dauki plate kawai sai ganin tana zuba yam balls din a plate din muka yi. Ta debi iya wanda zata dauka, ta fita daga kicin din. Duk kallo muka bita dashi har ta fita. Maimakon abin ya bani haushi, sai ya ma bani dariya. Na girgiza kai kawai, a zuciyata ina furta 'Allah ya kyauta!'.

Sai bayan mun sha ruwa sannan na kunna wayata. Messages, missed calls, voice mails, messages din whatsapp da voice notes babu iyaka daga Umar, duk abu daya yake tambaya, 'don Allah in daga wayata', na harari wayar tawa kamar shine a gabana, in daga wayata in ce mishi me?!











*☆⋆09⋆☆*





Har washegari Umar bai daina kiran wayata ba, nima kuma ban daga ba. Zuwa lokacin missed calls dinshi sun fi a kirga.
Da safe ina browsing din wasu procedures a wayata lokacin da nake jiran Jan ta fito daga wanka, don na rigata shiryawa. Wata bakuwar lamba ta min sallama ta whatsapp. Daga farko nayi zaton ko Umar ne, sai dana bi ta cikin description dinshi sannan naga kwata-kwata komi nashi bai yi shige da na Umar ba. Na farko dai Umar daya zauna ya zubo miki layi biyu a rubuce, ya gwammace kuyi awa biyu akan waya kuna hira. Shi yasa yanzun haka voice notes dinshi ne suka cika min waya.
Kamar wanda yake jira, ina amsawa ana maido da amsar ya nake? Fatan na tashi lafiya?.
Nace lafiya lau, ko wanene yake magana?
Sai aka turo, 'ba lallai ki sanni ba gaskiya, amma ni na sanki farin sani. Ba tun yau ba nake ta so in miki magana, sai yau Allah ya yarda. Sunana Muhammad'.

Na rubuta, 'to Malam Muhammad ko zaka iya sanar dani inda ka sanni? Don bana tunanin nasan wani Muhammad anan inda nake'.
Yace 'in shaa Allah zaki sanni nan ba da jimawa ba, na miki wannan alkawarin. Magana ta gaskiya yanzu bana gari shi yasa, amma da zarar na shigo zan zo in same ki, nasan lokacin kuna shika'.

Na daga gira cikin mamaki, ta alama mutumin nan ya sanni fiye da yadda nayi tsammani. Nace 'ta yaya aka yi kasan haka?', ina tura mishi amsar Jan tana fitowa daga bandaki, na kashe datar na sauka daga kan WhatsApp din ina kallonta. Zama tayi ta gama shirinta a nutse. Tana gamawa muka ci pancake da muka yi da ruwan shayi, da muka gama muka dauki sauran da muka yi muka kai kicin muka wuce.


*

Yau sai yamma likis muka dawo daga asibitin. Da yake yau a bakin titi muka sauka, akan kafafunmu muka gangaro zuwa gidan Yaya.
A kofar gidan, Umar ne tsaye ya jingina da motar shi. Na danyi turus da ganinshi, gabana yana faduwa, kafin na dake muka cigaba da tafiya.
Da sauri ya tari gabanmu, "Na'ilah, sweetie, don Allah ki dakata, don Allah ki saurareni, wallahi na tuba, don Allah....".

Jan ta kalleni, yadda na hade fuska kamar naga wani dan aiken mutuwata, yasa ta fara raba idanu tsakanina da Umar. Yaci gaba da zuba magiya yayin da na zagaya ta gefenshi na tunkari kofar gidan gadan-gadan. Janan ta riko hannuna, na juya ina kallonta, tace "meye haka Na'ilah? Ban san ki da wulakanta mutane ba sam".
Nace "kiyi shiru Janan, baki san abinda ya faru ba, don haka kada kiyi kokarin shiga cikin wannan fadan".
Umar yayi tsulum da bakinshi, "don Allah ki saurareni Sweetie, please...".

Na kare mishi kallo, duk da kokarin dannewa da nake yi, da nuna kamar ban damu ba, amma nayi kewar shi. Kwana daya da yini daya kacal, amma nayi kewarshi.
Na kalli Jan data tsaya tana kallonmu, nace "ki wuce abinki kawai, zan shigo in same ki". Babu musu ta shige cikin gidan ta barmu a tsaye.
Na harde hannu a kirji ina kallonshi, "me? Yanzu kuma mai kake bukata ne? Kana so mu kebe wani waje ne ko kuma ka kama mana daki ne a hotel?".

Ya dafe kai, "Subhanallah, haba Na'ilah me ya kawo wannan maganar

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login