Showing 27001 words to 30000 words out of 73204 words
ya hanya?".
Na dan saki tight murmushi, gajiyar dana kwaso tana kara lullubeni, nace "lafiya kalau, sannunku". Na gaishe su gabadaya, a lokaci daya. Duk suka amsa min, na wuce cikin gidan.
Duk cikin kannen Anty Raheemah, har ma ita Rahimar, Haleemo ta fi su sanyin hali, shiru-shiru, da kuma rashin rawar kai. Shi yasa tamu tafi zuwa daya da ita. Har wani lokacin idan naje gidan mu kan dan hiranta da ita. Salama kam, tsabar tsiwarta da rashin mutunci yasa ranar farko da muka fara haduwa da ita muka kusa yin baram-baram. Bata da kirki ko kadan, zata iya tsaga tsakiyar idanun mutum, ko ma wanene shi ta yanka mishi rashin mutunci ta kara gaba. To kada kuma Adi taji labari, ita ta damesu ta shanye.
Ni dai fatana daya, in samu in gama dan zaman da zanyi dasu lafiya ba tare da wani rikici ba. Shi yasa na taho da kudiri, kuma da burin kai zuciyata nesa, kauda kai daga lamarinsu koda zasu taka ni ne, da kuma maida komi ba komi ba. A takaice dai, naci damarar ba banza ajiyarsu.
Ina bi ta kofar gidan, maigadin gidan, Ahmad. Dan matashine, kuma buzu, ya fito daga dan dakinshi da sauri yana min oyoyo. Murmushi nayi a gajiye na amsa, ya karbi akwatin hannuna da jakar ya biyo ni a baya har sashen Yaya Bilal din.
Na buga kofar falon gidan, jin alamun kofar a bude take yasa na tura kofar na shiga bayan na cire takalmina anan dan corridor din da suka tanada musamman saboda ajiye takalma.
Ahmad ya ajiye min kayana na sake dauka na shiga babban falon nasu bakina dauke da sallama. Raheemah da kawarta Adi na zaune suna kallo, gefensu gwangwanayen lemuka ne da plates wanda nake tunanin suka gama cin abinci daga ciki.
Babu wadda Allah ya bata ikon amsa min sallamar da nayi, sai kallo da dukansu suka fara bi na dashi, dani da kayan hannuna. Duk kokarin da nayi, sai da naji zuciyata ta fara rawa. Wani bangare mai rauni na zuciyata ya fara raya min over and over, zuwana nan gidan was a bad idea. Yana kara gaya min dalilai da dama, masu nuni da cewa gaskiya yake fada min.
Bisa wadannan dalilai dama wasu, yasa naji na fara tantamar anya ba zan juya inda na fito ba kuwa? Musamman tunda Janan bata riga ta san da zuwa na ba, zan iya ce mata wani uziri ne ya taso na gaggawa da yasa na koma gida, ko rashin lafiya, ko...!
Daidai lokacin da kofar dakin Janan din ya bude, ta fito daga ciki. Muna hada ido da ita, ta saki murmushin daya haskake mata fuska baki daya. Ban san dalili ba, naji wani kwarin gwiwa ya shige ni, wani over confidence dana rasa daga inda yake. Da sassarfarta ta karaso wajena, bata yi wata-wata ba, ta janyo ni ta rungume.
Sai data gama murnar ganina sannan ta sake ni, ta ja baya tana kare min kallo tun daga sama har kasa. "ke hutun nan dadi ya miki sosai fa da alama... Taho muje daga ciki dai, kiyi sallah ki huta!".
Ta kama akwatin hannuna ta fara ja. A hankali na maida kallona ga su Rahima da har lokacin, idanunsu na kanmu kurr. Yadda suka yi yasa na fara tunanin anya sun san da zuwan bakuwar da zata zaune musu a gida na yan kwanaki kuwa? Nayi kokari na danne uneasiness din da naji a jikina, ko ma dai menene, tsakanina da Allah bana son wani abu yaje ya zo, a dinga cewa ta dalilina hakan ya faru.
Don haka na dage tun karfina na kakalo murmushin da ni kaina nasan cewa sun san na yake ne, gajiyar da nayi ta kara worsening abin. Nace "Anty Rahima, Adi, sannunku da gida!".
Adi ta amsa da 'lafiya lau', yayin da Rahimar ta dauke kanta daga gareni ta maida kan Janan.
Cewa tayi wai, "wannan fa?".
Nayi kwafa a boye, wani 'wannan fa!' sai kace wata shara ko kayan wanki, yadda kasan bata taba ganina ba.
Janan da bata kula da rainin wayon da tambayar tazo dashi ba, ko kuwa ta fahimta fuskewa kawai tayi? Cikin murmushi tace "Anty kawata ce fa, Na'ilah. Yaya ya fada miki zata zauna damu kafin ta samu wajen zama a cikin hostel".
Antyn ta sake waiwayowa ta kalleni, fuska a murtuke, bakinta a tsuke, wanda ba karamin kokari nayi wajen danne dariyar data kamo ni ba sanadiyar ganin expression dinnan ba. Tace "zama damu ko ke?".
Janan din ta danyi turus! Kafin ta sake yin murmushi ta cigaba da jan akwatin zuwa dakinta tana furta "muje". Ban kara waiwayarsu ba na bi bayanta.
Sai dai ko daga inda nake, ina iya jiyo sautin muryarta da maganganun da take yi da dan karfi, obviously yadda zamu jiyota sosai, "shima 'Baby' da dan banzan kwashe-kwashe. Kawai babu dangin iya balle na Baba ka wani kwaso mana yarinyar da baka sani ba, ka ajiye mana a gida. Ko da wanne yake so mutane su ji? Da wannan yar rainin wayon kanwar tashi ko kuwa da wata bare kuma?", tayi shiru tare da yin kwafa, "wai wani kafin ta samu daki! Ko kuma kwadayi ba!!. A dai zo a zauna din, aga idan wata tsiya za'a b'anb'ara daga jikinmu....".
Sauran maganar ta mutu lokacin da muka shige dakin Janan muka maida kofar muka rufe.
Janan ta dubeni fuskarta cike da damuwa, "don Allah kiyi hakuri da abinda tace!".
Na daga kafada cikin nuna alamun rashin damuwa, duk da cewa kawai don kada ta damu ne na fadi hakan, amma fa maganar kwadayin nan ta taba raina sosai, nace "menene abin jin haushi a maganganunta? Babu komi wallahi. Bari inyi sallah".
Tace "to", a lokaci daya kuma tana fita daga dakin. Ni kuma na fada bandakinta.
Ina gama sallah, ta hau turo min plates da bowls na abubuwa. Na kallesu ina kwashewa da dariya, nace "baiwar Allah ina kike so in kai wadannan abubuwan? Ba dai cikina ba ko?".
Itama tayi dariyar, "na san ki da rashin son cin abinci idan zaki yi tafiya, na tabbata rabonki da abinci tun karin safe".
Nayi shiru ban amsa ba saboda haka ne, shima karin safen da nayi shayi ne kawai, babu abinda na hada dashi. Daga shi sai maltina din wajen Umar. Hakan ya tuna min da ledar daya hado ni da ita.
Na tashi na nade abin sallar, na koma gefenta na zauna bayan na dauko ledar. Lemuka ne kala-kala was ciki, wasu juices wasu kuma fruit juices sai su tarkacen doughnuts da cupcakes. Tare muka ci abincin da ita muka gama, bayan mun gama ta fita da kwanukan abincin, yayin da na ciro wayata daga cikin jaka na hau kiran yan gida ina sanar dasu na sauka lafiya.
Wajen karfe takwas saura bayan mun gama yin sallah, Umar ya kira ni ya sanar dani yana kofar gida. Na dauki gyalena dana rataye a jikin hanger ina kokarin yafawa, ko hoda ban kara ba balle janbaki. Ni kwata-kwata bana ganin amfanin yin wannan kwalliyar ta dare idan za'a fita hira, koda yake dama ta yaya za ayi in gani tunda dama can kwalliyar ba damuna tayi ba?.
Janan dake kwance ruf-da-ciki akan katifarta tana chatting ta kalleni lokacin da nake shirin fita, tace "kada dai ki wuce karfe tara da rabi, idan kuma ya shigo daga ciki, ku koma daga waje duk da nasan cewa ba lallai Ahmad ya bude mishi gate ba, sai dai idan baya nan".
Nayi yar dariya ina kallonta, "kada dai kice min kuna da curfew a gidannan?!".
Tace "Yaya ne yasa wallahi. Samarin su Salama suke shiga da fita babu kakkautawa a gidannan, ko ina kuma shigo dasu suke yi har cikin falon nan, shine ya kafa wannan doka".
Na gyada kai, "yayi kokari gaskiya, da haka ake yi a wasu wajajen ai da an samu zaman lafiya kuwa". Tayi yar dariya, "kin ci sa'a ma Yayan baya nan, da sai kin amsa tambayoyi daga wajenshi kamar kina rubuta jarabawar jamb kafin ki fita yanzu".
Na kama baki cike da mamaki, gefe daya kuma ina jinjina kokarin Yayan, a ganina hakan da yayi hanya ce mafi sauki ta sanin halin da kannenshi da samarinsu suke ciki. Na dai mata sallama na fita.
A kofar gate muka yi clashing da Haleemo ita kuma zata shigo, ta ja da baya tana daga waje alamun ta bani waje in fara fita, na danyi murmushi appreciatingly na raba ta gefenta na fita. Ta kalli gefen gidan inda Umar yayi parking din motarshi, tace "saurayinki ne ya dawo?".
Mamakin tambayar ta kama ni, amma sai na fuske nayi yar dariya kawai ina gyada mata kai, tace "kinyi sa'a abinki ke kam!". Ta shige gida, na bita da kallo baki a bude slightly, ko meye hadinta da zancen soyayyata, sa'a ko rashinta? Na daga kafada tare da tsallakawa daya gefen.
Da kanshi ya bude min murfin motar, na shiga ciki bakina dauke da sallama. Barin murfin motar nayi a bude, ban maida shi na rufe ba. Ya amsa min sallamar, scowling, na kula baya son hakan ko kadan, ya sha fadin hakan ma ba sau daya ba sau biyu ba. Kunnen uwar shegu kawai nake yi dashi.
Mun fara hira dashi game da makarantarmu da wajen aikinshi. Ya fada min anyi posting dinshi zuwa Kaduna, satin sama zai shirya ya tafi. Na mishi addu'ar Allah ya taimaka. Daga nan hirar ta koma ta masoya, ya fara amayo kalmomin soyayya. Jinsu kawai nake yi suna shiga suna fita cikin kunnena. Ban sani ba, ko akwai ranar da zanji wani yace yana so na, in yarda da hakan? Inji zuciyata ta mamaye da haske da farinciki sanadiyar jin haka? Nayi nisa cikin tunanina, totally zoned out. Wani abu daya zame min jiki da zarar naji mutum ya fara amayo kalmomin nan, ban san lokacin da hakan take faruwa ba, kawai sai dai in tsince ni nayi nisa a duniyar tunani, I couldn't help it.
Umar ya murza yatsunshi biyu a fuskata, sautin da suka yi ne yasa na dawo daga tunanin dana shiga. Na kalleshi sosai, kallona yake yi, nace "me kace?".
Fuskarshi ta nuna alamun damuwa da kulawa, yace "Sweetie, ban san sau nawa kike so in fada miki cewa bana jin dadin abinnan da kike yi ba. Sau tari sai in ganki kinyi nisa cikin tunani, hakan yana kona min rai. Don Allah ki fada min, idan wata damuwa ce take damunki, ki fada min inyi miki maganinta!".
Na girgiza kai, ina mishi murmushi a sanyaye, "babu abinda yake damuna Umar, kaima kasan cewa da da akwai zan fada maka ne".
Ya juya kai, "abinda kike cewa kenan kullum, babu canji. Har zuwa yaushe ne don Allah? Sai inga kamar baki jin dadin kasancewa da nine".
Na kalleshi cike da mamaki, "meya sa ka yin wannan tunanin? Ni fa na fada maka babu abinda yake damuna, idan akwai zan fada maka wallahi, kaima ka sani".
Ya rausayar da kai, "to ai shikenan sweetie, yadda kika ce". Shiru ya ratsa wajen, kafin naga ya bude dashboard ya ciro wani kwali. Yanayin tsayin kwalin yasa nayi zargin waya ce a ciki.
Ya miko min, bakinshi dauke da murmushi kamar zai tsaga bakin. Yace "dazu na ganta a shago, sabuwar shigowa ce, ban yi tunanin kowa ba sai ke lokacin dana ganta".
Na sanya hannu na karba tare da budewa, sabuwar wayar Samsung ce sai sheki take yi. Duk da bai fada min kudin wayar ba, nasan ba karamin kudi zata yi ba.
Cikin alamun tambaya nace "amma me yasa? Ina da waya, ka tuna?".
Murmushin fuskarshi ya bace, "na sani mana, shi yasa ma na sai miki. Na kula da taki ta ma fara fading fa, kai gabadaya ma ta tsufa".
Na kai yatsa daya na shafo saman hancina, wani abu da nake yi unconsciously idan magana bata karbu a wajena ba, ko kuma idan maganganun mutum were so bored. Niyyata in tambayeshi sai me don wayata ta fara tsufa? Naga dai ina amfani da ita lafiya lau, kamar dai yadda sauran masu latest wayoyi suke yi. Sannan wayata lafiyayyiya ce, bata bani wata matsala balle yace saboda matsalar ta ne.
Sai dai nayi shiru kawai, nasan cewa idan na daga baki nayi magana hakan zai kaimu ga yin sa'in'sa, hakan kuma ba dadi zai mana ba. Don haka nace mishi "to nagode kwarai, Allah ya amfana. Amma zaka amshi tsohuwar tawa wayar ne ko?".
Yayi wani irin murmushi, idanunshi na karade fuskata da kallo, "ko kadan sweetie na, amma zaki iya bani dan kiss, a matsayin tukuici na".
Na daga kai na kalli tsakiyar idanunshi, babu alamun wasa ko kadan, alamunshi sun nuna da gaske yake. Duk da haka, sai na maida abin wasa, nayi yar dariya kawai, "dadina da kai ka cika ban dariya wallahi Umar... Bari in koma daga cikin gida don lokacin da aka dibar min ya kusa cika!"..
Ban jira ya bani amsa ba, na yunkura da niyar fita daga motar. Kawai ji nayi murfin motar ya koma ya rufe, tare da wani karamin kara alamun an sa motar a lock. Na kai hannu da niyar bude motar, sai dai naji gam, kamar yadda nayi zato ya rufe ni.
Na juya ina kallonshi, fuskata a dinke tsam babu alamun wasa balle yayi tunanin kawo min maganar shirme, nace "meye haka? Bude min kofa in fita don Allah".
Ya gyara zamanshi sosai, "a'ah, magana zamu yi dake sosai. Na kula duk lokacin dana fara furta miki abinda yake cikin raina, sai ki banzatar da maganar ki maidata wasa, an fada miki ni dan wasan kwaikwayon ban dariya ne? Ni fa in fada miki gaskiya na gaji haka nan Na'ilah! Na gaji! You are officially my girlfriend!! Yakamata ace zuwa yanzu mun wuce kan wannan maganar, ba tun yau ba yakamata ace wannan maganar a tsakaninmu ta wuce, ace mun wuce wannan matakin. Nima fa mutum ne. Nima ina so ace ina taba ki, ace zuwa yanzu jikinki ya riga ya saba da nawa, amma kullum sai ma kara janye jikinki da kike yi daga nawa, to na gaji, yau sai dai ayi ta ta kare tsakanina dake!!".
Tsananin mamakinshi ya dankarar dani a zaune, na kasa motsi. Bakina nake motsawa ina so inyi magana, in maida mishi martani ko yaya ne, amma kamar ansa zare da allura an dinke min shi, na kasa buda shi.
Ganin haka yasa ya cigaba da magana babu kakkautawa, "meye bana miki? Meye bana baki?? Idan ma abinda nake miki ne bai isarki, kema kinsan ai ba sai kin zauna kina wani shan kwana ba, ki fito ki fada min mana ki ga idan ban baki ba yanzu take! Meye na roki ki min? It's just a kiss fa! Meye a cikinshi?".
Sai lokacin naji bakina ya motsa, saboda tsananin bacin ran da maganganunshi suka haifar min yasa naji jikina yana wani irin rawa, nace "sau nawa kake so mu yi wannan maganar da kai? Jikina ba jikim banza bane da zan sakar maka shi kawai saboda kana yi min hidima. Na fada maka ina bukatar abubuwan da kake yi min ne? Na taba daga baki na tambayi wani abu a wajenka? Ko kuma na taba furta maka ina bukatar irin rayuwar da kake son yi? Kawai saboda kai kana ganin irin wannan rayuwar itace wayewa, ni a ganina ba hakan bane. Ba zan taba yin rayuwar zubda mutunci ba, ba zan taba zubar da mutunci da kimata ta ya mace ba akan mata'ul hayat, abubuwan da zasu kare cikin dan kankanin lokaci, saboda haka ka bude min kofa in fita!".
Cikin saurin magana da bacin rai nake maganganun, nasan da kyar ne idan ya fahimci duk abinda na fada.
Ya sauke ajiyar zuciya, "come on Na'ilah! Ni fa ban ce ki bani kanki ko wani abu ba, kawai kananun abubuwa nan da can ne fa, what's the harm in it? At least ki dan dinga appreciating dina mana!".
Na galla mishi harara, "kai a wajenka ba komi bane, saboda shaidan ya riga ya rufe maka idanu, amma ni a wajena it's a big deal. Kada ka manta, mun taba yin wannan maganar da kai, na fada maka idan kasan wani abu kake bukata daga wajena yafi mana sauki mu yanke alakarmu, don babu abinda zan iya maka. Ba zaka taba taking advantage dina ba Umar, ba zaka taba yin amfani da kayan banza ka yaudare ni ba wallahi, in Allah ya yarda nafi karfin haka. Don haka ka bude min kofa in fita tun muna shaidar juna ni da kai wallahi. Kuma ga wayar ka nan, bana so, kai bana so in kara ganinka ma!!".
Na hau kici-kicin bude kofa da sauri kamar wadda ta fita daga cikin hayyacinta. Ina ji yana kiran sunana amma nayi banza dashi. Ban tantance ba naji saukar hannunshi yana dafe min hannu, banyi wata-wata ba na wancakalar da hannun nashi can gefe. Bai daddara ba dai ya sake dafa kafadata, wannan karon dana kama hannunshi, twisting nayi da karfina duk da nasan ba lallai yaji zafin hakan ba, duba da yanayin aikinshi.
Cikin tsananin bacin rai da tunda muke dashi bai taba ganin kwatankwacinsa ba, daga murya da tsawa nace "kada ka sake taba ni!! Kada ka sake kuskuren taba ni!! Kuma wallahi ka cuce ni da kayi tunanin zaka iya saya na da kyale-kyalin banza, in shaa Allahu sai Allah ya saka min. Ka bude min kofa nace!!".
Tsananin ihun da nayi ni kaina ya bani mamaki balle shi. Ina jin hakan ne yasa bai ma san lokacin da hannunshi ya danna madannar ba, ina jin na taba murfin ya bude, na fita daga motar da sauri. Ko sakan biyu ba ayi ba naji shima ya fito, ya hau auna min kira. Babu ko waiwaye, na shige gida da sauri.
Jikina rawa yake, hannu, kafa, baki, kai, komi nawa rawa yake yi. A daidai parking space dinsu na tsaya, na dafa wani pole ina haki kamar wadda tasha tseren rai da rayuwa. Kodayake kusan hakan ne.
Tunanina daya a lokacin, da ace yaki bude kofar fa? Me zai faru da yaki bude kofar? Me zai faru idan bai daina taba ni ba? Me zai faru idan wajen da muke babu mutanen da zasu ji ihuna idan ina