Showing 21001 words to 24000 words out of 115646 words

Chapter 8 - Shahaab Complete Hausa Novel

12 Oct 2024

9586

kaidin Dan yankan kaine, tayaya zaka dauki kudi haka a fili kawai kabawa yarinya Bayan kace bata sanka ba?aikuwa kana bata wannan kudin yanzu nema zatace tabbas kaidin abun atuhumeka ne, Kayi hakuri ka dauki ko dubu biyar ne kabata, ahankali ahankali zata saba dakai harka bata kudaden masu yawa, Amma bade lokacin farko ba, tunda Naga kanaso ka taimaka mata ai nasan ganin ta kake kamar 'yarka, shiyasa kake tausayin ta, Amma Kuma yanada kyau koda abota zakayi da'ita to kasan halaiyarta kafin kufara, yakamata kasamu Mai sonka da abota ta tsakani da Allah bawai don kudinka ba "

Cikin damuwa yace
"Ramadan tayaya zan'iya mata kyautan dubu biyar? Kamar Almajira? Banason qarya, bazan zo daga baya tasan koni waye qarshe tamin rashin kunya ba, Gara infada mata gaskiyar koni waye, sannan inji dalilin dazaisa tacemin matsayaci, idan taqi fada Kuma sainasa ankama ta na zaneta dakyau yanda zata Dena rashin kunya"

Ramadan da jikinsa yayi yayi Sanyi akan maganganun Shahaab saiya tafi duniyar tunani, tabbas Shahaab yanason wannan yarinyar koma wacece,to da alama akwai abinda yahadasu har tayi masa rashin kunya, Wanda 6acin ran hakan yasa yakasa gane sonta yake.
bazai iyu yanaji yana Gani yabarshi yasake aure irinna munirat ba, Gara yafara gwada yarinyar yaga hankalin ta, to Amma shi Shahaab yadage baison qarya, ahankali yasaki ajiyar zuciya yace "zaka iya Abokina, mu gwada hakan"

Badon yasoba haka ya yarda da shawarar Ramadan akan zai 6oye mata koshi waye yaje mata Ahaka, Amma da yayi niyyar yaje ya fuskance ta, yafada mata shine Mahmud Wakili ba Shahaab ba, kamar yanda yafada mata ranar, sannan Kuma yasa tafada masa dalilin ta na zaginsa, Kuma yabata kudin takar6a Dan dolenta (tofa😲)


******

Da daddare inusa yazo, yaturo wani yaro Akira masa Aisha, gaba dayansu suna zaune atsakar gida, Yaron yayi sallama yace "Wai Ana Kiran Aisha inji Inusa me Kanti"

Hajja tace "hmm Kaikuwa yaro daga Kai har Inusa me katin Baku iya sakaya suna bane? Aisha haka gatsau ko dadin ji babu? To daga yau karna qaraji,jekace masa gatanan zuwa"

Yaron ya amsa da "to" sannan yafita

Aisha kuwa tanajin Kiran ranta ya6aci, saboda shirin tafiya sallar Ashan take yi, batason yin fashi kullum Sai taje, Kuma hakan baya hanata anjima ma karfe daya da rabi na dare tasake komawa sallar tahajjud,Amma yarasa yaushe zaizo Sai yanzu? To kode shi baya zuwa tarawih din?

Hajja tace "ba kiranki ake bane me sunan qawa?"

Tashi tayi tad'auki hijabin Sai turo dan qaramin bakinta take gaba, tana saka takalmi Hajja tace "zoki dauki dan ruwan Sanyi a fridge kitafi masa dashi, idan kinje Kuma kifada masa karya sake cemiki Aisha, uwarki da ubanki ma me sunan qawar Hajja suke cewa, danhaka karya sake cemiki Aisha, qawata tanada daraja ba sa'ar uwarsa bace" (😅🤭)

Itade Aisha batace komai ba tad'auki ruwan tafice, da sallama ta qarasa suka gaisa, tace masa "Inusa ga ruwan Sanyi inji Hajja"

Murmushi yayi yace "Haba Aisha, Inusa Kuma? Kuma kowa yana cewa Inusa kema Inusan zakice?"

Tace "Tome zance?"

"a a, Yunus zakice, ai awajanki sunan na daban ne"

Zuciyar ta daya tace "Nima to kadena cemin Aisha, sunan qawar Hajja gareni, Kuma su Abba ma basa fadar sunan saboda irin sunan Hajja ne"

"ikon Allah, to Amma Aisha arasa sunan wadda za'a saka miki Sai sunan qawar kakarki?"

Tace "Um Haka Hajja taso, Kuma Nima duk abinda Hajja takeso to inaso, saboda inason kakata, itama tana sona"

Murmushi yayi yace "Alhamdulillah kice Nima kinasona Kenan, tunda ai Dama kafin nazo saida akamin iso awajan Hajjan, yaushe zata fara kunun Ayar tane?akwai wani sikari (Suger) Dana dade da ajiye matashi, zan kawo miki shi saiki bata, tunda kince kina qaunar Hajja, nikuma kenake so, kinga Nima dole ne naso abinda kike so "

Ahankali tace" A a mungode Amma ka barshi "

"to ai kinji abinda yake had'ani dake, aini ne nayi niyyar baki,idan kikaqi kar6a ba zanji dadi ba, yanzu de Dama zuwa nayi naganki, ko zanji Sanyi araina, nasan zakije sallah, Bari nabarki haka Naga munyi kusan minti talatin, ga wannan naki ne, ki Kai a dinka miki da sallah, kudin dinkin yana ciki "yafadi haka yana bata wata baqar leda

Girgiza Kai tayi tace"a a nagode Amma ka barshi"

Tace "meyasa? Kode kin Rena?"

Kanta ta Girgiza masa, yace "to kar6i"

Hannu biyu tasa ta kar6a sannan tayi masa godia, yace "to yimin murmushi mana"

Kunya ce ta kamata, tasa hannu biyu tarufe fuskarta, cikin sauri ta wuce gida

Tana zuwa tabawa Hajja ledar , ta wuce ta dauki buta tayi alwala, Tai shirin tafiya masallaci

Hajja ta bud'e ledar atamfa ta bayyana, da kudi nera dubu biyu, atamfar irin ledar Nan ce me sauqin kudi (labona)
Hajja tasaki guda tace "Alhamdulillah, jikata tayi goshi, Hadiza, mamuda kunga abin Arziqin daya kawo mata, harda dubu biyu, tashi daya, yabata kudin albashin ta na wata guda"

Abba yace "Allah yasaka masa da alkhairi"

Ummah tace "ya kyauta, Allah yasa ayi damu, ai inusa bashida laifi, yana ganin girman manya duk inda yaganni saiya tsugunna yake gaisheni"


******

Yaso ace yanzu haka yana jigawa, yanaso yasake Sakata acikin Idonsa yaji dalilin dayasa take zaginsa, to Ramadan ya hanashi tafiya yace yabari su shirya sutafi tare.
Shikuma Ramadan dalilin dayasa yayi haka yanaso ne sutafi tare dashi danya dinga cusa masa ra'ayin yarinyar ahankali, harga Allah so yake Shahaab yayi aure ko Shima zai samu magaji

Mama ta kallashi, tunda ya dawo daga wajan aiki take lura dashi acikin tunani yake, kuma yakasa tashi yaje yayi wanka yacire wannan suit din ta jikinsa, hannu bibbiyu yayi tagumi yana kallo, Amma hankalin sa ba akan kallon yake ba,sau uku tana sauya Tasha Amma tana lura dashi ko motsi ba yayi Idonsa yana waje daya

Ahankali tace "Shahaab"

Cikin damuwa yajuyo ya kalleta yace "na'am mama"

Tace "har yanzu baka nemomin mekula Dani ba, koka manta ne?"

Maimakon yabata amsa saiya miqe tsaye, cikin damuwa yace "mama abubuwa sunmin yawa, kisa a duba miki kawai"

Daga yanayin yanda yake magana kad'ai zaisa kagane yana cikin matsananciyar damuwa
Ahankali tasake cewa "Shahaab"

Yajuyo yace "na'am"

"zonan"
Abinda tace dashi kenan, babu musu ya dawo gabanta zai zauna aqasan kafet din, cikin sauri tataroshi, ya dawo kan kujera, ahankali tajashi jikinta ta rungume shi, wata irin ajiyar zuciya yasauke, yasake qanqameta, sumar Kansa ta dinga shafa masa, ahankali har wani bacci me dadi ya dauke shi

Jin yasaki jikinsa yana bacci yasa tata6e baki, cikin zuciyar ta tace "banga amfanin munirat ba, mijinki yana cikin damuwa Amma ko ajikinki, yanzu haka damuwar akan office dinsu ne, tariga tasan inde akan wannan aikin nasu ne to baya kula da cikinsa ma kamar yanda yake kula da wannan office din"

Kusan awarsa d'aya yana bacci, mama da Hankalinta yakoma kan kallo can qasa-qasa taji Shahaab yana cewa " 'yar qarama...., 'yar qarama...."

Mamaki yakama mama, batasan lokacin data Kai dubanta gareshi ba, cikin zuciyar ta take cewa "wacece Kuma 'yar qarama?"






SHAHAAB littafin kudi ne,naira 300 ne kacal 👌🏻yar'uwa siyan nagari maida kudi gida, ki biya naira 300 ki karanta abinki Hankali kwance


Zaki tura 300 ta wannan account din


0164549488
Amina muhammad
GTbank

Zaki tura shedar biya ta wannan number 08033300034













Amnah El Yaqoub✍🏻
[10/09, 22:14] +234 803 697 8511: 🌸SHAHAAB🌸
(Romance)


Writing By Amnah El Yaqoub

Dedicated to Aisha's Name

Like my Page On Facebook👇🏻

https://www.facebook.com/amnahel




15&16



Kallan sa tasake yi, itade tasan cewa Shahaab baya kula mata, yanda yad'auki son duniya ya d'orawa munirat batajin wannan 'yar qaramar dayake fad'a da mace yake, takai shekara da shekaru tana fad'a masa yanemo yarinya ya aura, Amma har Zuwa yanzu saide yace mata shida munirat Sai Allah, tarasa Yaya zatayi dashi, shiyasa ta tattara shi ta watsa.
Ta6e bakinta tayi tad'auki remote tasake sauya Tasha

Sai yanzu ne yayi wani juyi, yaci gaba da baccinsa, yad'ad'e yana baccin sa me dad'i cikeda mafarkin Aisha, sannan ahankali yabud'e Idonsa,mama ta Kalle shi tace "katashi?"

Cikin shagwa6a yace "um"

Tace "to sannu da mafarki, d'agamin cinyata"

Gabansa ne yayi wata irin faduwa "karde mafarkin Dayayi yanzu mama tajishi" shiru yayi yakasa cewa komai, yasan cewa Saitayi masa tatas saboda yanda yaqi jinin a had'ashi da wata yarinyar, Amma yau gashi shine da mafarkin wata qanqanuwar yarinya, haushin Kansa ne ya kamashi, to Shima miye na mafarkin Nata? Daga kwanciya bacci, cikin baccin ma bazata barshi ya sarara ba?

Mama tace "karufawa kanka Asiri Shahaab, kar aikin ku yasaka ka koma qaramin mahaukaci, toma 'yar qaramar me kake kira?"

Cikin qaramar murya kamar baison magana yace "no mama kawai mafarki ne, akwai wata yar qaramar flower ne dana dad'e Ina nema" (🤭)

"toshi fure har wani muhimmanci ne dashi dakuke neman sa yanzu? Wasa kakeji dashi, kaga tashi kaje kayi wanka,babu abinda munirat take Sai riqe waya, saika sata ta duba ma furen"

Hamdala yayi cikin ransa ganin bata ganoshi ba,daga mata Kai yayi sannan yatashi yatafi

Yana tafiya tad'auki wayarta tasa wata mata akano ta bincika mata yarinya wadda zata dinga kula da ita, Amma anan arewa takeson yarinyar, saboda ta gwada na kudu dayawa Amma babu abun Arziqi

Matar kuwa cikin ladabi ta amsa mata, sannan sukai sallama


******

Yau jummai ce tazo musu gidan tunda sanyin safiya, dukansu kuwa suna gida babu Wanda yafita, Abba ma yana kwance yana jin taskar labarai a redion Aisha.

Bayan sun gaisa ta nemi waje ta zauna sannan tace "Hajja A'i gulma ajali inba'ayi ba amutu, wani zance ne nazo muku dashi keda mamuda Da Hadiza, Amma kafin Nan kunada Dan magi kubani? Saboda yau dafaduka zanyi"

Hajja tace "bamudashi jummai, fad'amin meyafaru?"

Jummai Tace "Ina wannan bawan Allah mejin tausayi da jinqan al'uma? To dazu dazu yayata Datake kano tamin magana tace itama maqociyarta ce wata Mai kudi, tace Dan Allah ayi mata ciki yar aiki, zata turawa wata Hajiya datake zaune a Abuja yarinyar, to Amma hajiyar Abujan ance tanada mugun kudi sosai, Dan da yan kudu take dauka aiki Kuma kasancewar anga tana bada kudi kamar ruwa, Sai mutane suka fara asiri, kowa so yake dansa yaje yayi aiki a gidanta "

Hajja tace" ikon Allah na kwance yafadi..., to ita kwa wannan wanne irin kudi ne da'ita haka kamar yayi?wacece? "

Jummai tace"ai hajiyar Kanon tace wadda take neman yar aikin Mahaifiyar shugaban EFCC ce wannan Yaron de MAHMUD WAKILI, Wanda yamana Rabon kayan Azumi, Amma fa Ana bala'i sosai idan mutum zaiyi aiki a gidan, sannan Kuma akwai kudi sosai,Kuma ance matar tanada izzah sosai, saide Kuma duk masu aikin gidan ma kadai, suna cikin kulawa saboda akwai tsaro a gidan na sojoji da yan sanda, sannan masu aikin ma inde a gidan suke to sun riga sunyi kudi, sainake ganin ko Zaku tura mesunan qawarki, tunda zataci Tasha, ta dinga aiko muku da kudade Kuma"

Hajja tayi ajiyar zuciya tace"ai jummai kin 6ata zance tunda kikace Ana bala'i sosai idan mutum zaiyi aiki a gidan, menene abun bala'i a neman aiki duk dade itama mesunan qawartawa yar bala'i ce?"(🤭🤣)

Jummai ta kalli Abba da Ummah tace"mamuda bakace komai ba, Hadiza kiyi magana mana"

Ummah tace "nikam duk abinda Hajja tace ai ya zauna, Hajja ai itace komai na mesunan qawarta, nikam ai kawai haifarta nayi"


Abba yace"gaskiya hakane Kam, saboda haka iya jummai da anyi hakuri da maganar aikin Nan, tunda de yanzu gashi inusa yafuto Kuma naga alama da gaske yake, to kawai babu damuwa zan hadata aure dashi, Nima Hankali na zaifi kwanciya, koba hakaba Hajja?"

ya qarasa maganar yajuya yana Kallan Hajja

Hajja tace"Gaskiya hakane Kam, idan takwarar ta taji Natura ta wata uwa duniya Abuja ma nasan bazata yafeni ba, Nasan halin Aysha Yakubu sagagi, cewa zatayi inrasa wazan tura aiki Sai takwarar ta? Nasan halin abata tsaf zata aikata, danhaka jummai ayi hakuri da wannan batu, me sunan qawa kawai zamu hadata da inusa"

Jummai tace "to shikkenan Hajja, Amma Dan kunqi ne, nikam naso Aisha taje komuma wataran maje Abujan mu dandani Arziqi"

Haka tadinga mita harta fice daga gidan, Sai Alokacin Aisha tasaki wata irin ajiyar zuciya, saboda harga Allah batajin zata Iya yiwa uwar wani bauta, itama Tata uwar tana buqatar kulawar ta, haka kawai saita tsallake mahaifiyar ta da Hajja tatafi tana yiwa wata mata aiki? Matar ma uwar mutumin daba birgeta yake ba, mutumin da taqi jinin taji sunansa, mutumin da saboda shi tadena jin redionta kwata kwata, bazai iyu ba

(tofa🥺)


******


Yau makara sukai a sahur, saura minti shida Akira sallah Sannan suka tashi, Ahankali Aisha ta bude idonta, taga babu Wanda yatashi sahur, Kuma wani lokacin bacci yana cikin dad'i za'a tasheta ace lokacin sahur yayi, Amma yau Kuma taga ta danyi baccin sosai, hannunta ta miqa tad'auki wayar Hajja, tana ganin lokaci tazaro idonta, durowa tayi daga gadon tace "Hajja....kunyi sahur ne nice Baku tasheni ba?"

Hajja tace "innalillahi wa inna ilaihirraji'un....ankira sallah ko?"

Aisha tace "A a, ankusa de, waidama babu Wanda yatashi kenan?"

Cikin sauri tafita taje tatashi Ummah da jabir, tasake tashin Abba, ai kowa a gurguje yatashi, Aisha yau babu batun brush, kawai bakinta ta kuskure tadauko musu kular dasuka zuba taliya aciki, da Ummah, da Hajja, da Aisha, da Jabir, gaba dayansu kowa hannu yasaka yafara ci, babu batun zubawa kowa, Abba yayi murmushi yaga yanda suka hade Kai kowa tura abincin yake, Ummah ta Kalle shi tace "kaidama ba sahur kake ba, duba mana saura minti nawa Akira sallah?"

Agogonsa ya kalla yace "saura minti biyu"

Cikin sauri suka qarasa cin abincin, ruwa kuwa kowa tashi yayi yake nema yanasha, kowa sauri yake inbakayi ban waje....

Suna gama shan ruwa kuwa aka kira sallah, Sai Alokacin Hajja tayi magana (😂)
"Oni Aishatu... Da yanzu yau munyi shige, wannan azumin na Bana Inkayi sahur ma Yaya aka qare bare Kuma bakayi ba"

Jabir ya kalleta yace "Hajja keda kikace sahur ba damunki yayi ba?"

"Kai da Allah Ina nufin Alokacin danake Aysha Sulaiman Bompai kenan, yanzu kuwa Hajja A'i nake"

Dariya Aisha tasaki tace "Hajja nifa jinake kun tasheni naqi tashi ne, shine kukai abunku kuka rabu Dani, ashe duka gidan yau makara mukayi"

Hajja tace "aini Gara hakan ma,nasan da yanzu kina Nan kina d'ora abincin a harshanki"

Cikin shagwa6a tace "kaii Hajja, aike nabiyo, kece kike cin abinci kamar bakya so"

Hajja tace "wa?.... Lalle yau na yarda bakisan wacece takwararki ba, ai Aysha Yakubu sagagi, idan tanacin abinci ke kyace yar sarki ce, Aysha inda ace me kudi ce ita bansan wanne irin mulki zatayi ba, Ada canma damuna boarding school dinmu ta Goron dutse idan aka zomin visiting mukaje muka kar6i abincin da aka kawomin, wato idan muka koma daki tafara cin abincin Nan saiki dauka yar wani gwamnan ce, saboda Aysha Yakubu sagagi akwai yanga, gashi batada 6oye 6oye, saide kaji haushin ta, Amma tana fadar gaskiya komin dacinta "

Jabir yasako musu baki cikin firar tasu yace"to Hajja ita qawar Taki ba'a zuwa mata visiting dinne ita? "

Tace"Ana zuwa mata mana, Yan gidansu suna zuwa, idan sukazo tare muke zuwa, kawai de Alokacin ne tafi yimin rakiya gaskiya, saboda kaga a wancen lokacin iyayena sunada kudi, ita Kuma nata iyayen basuda qarfi sosai, to saiya kasance Ana zuwamin visiting din sosai, da Azumi kullum Sai ankawo min abinci daga gida, Kuma idan natashi komawa makaranta Bayan motar Sai ancika min shi taf da Kaya, harnaje nadawo Bana iya cin wani abun, direban dayake kaini makaranta idan ya saukeni har dauke min wasu kayan yake yanamin wayo yana cewa ai wannan ma ba lalle kici ba, nikuma babu wayo, Sai ince eh, to haka mukai karatun mu babu abinda yake rabani da'ita, mutane dayawa suna tunanin ma gidanmu daya, saboda Bama fada, koda munyi fada to a ranar zamu shirya, ita babu rufi, idan na 6ata mata rai fadamin take, nikuma da masifa, inhauta da fada, anan de Sai mutane sun shiga tsakani sun raba mu, Amma kabamu awa uku, saide kaga mun shirya, ko ban kulata ba, to ita Kam saita kulani, tundaga Nan da mutane suka gane halin mu, ko sunga suna fadan saisu qyalemu saboda sunsan zamu shirya"


Aisha tace"to Hajja bakida photon tane kinuna mana? "

Tace"inada shi mana, yana cikin adaka ta aqasan gado na, zan nuna miki takwararki, har saurayinta na makaranta ma duk inada photon sa, Shima zan nuna miki "

Cikin sauri Aisha tace"au Hajja har soyaiya kuke a makaranta? "

Hajja tace" emana, kafin muyi candy kowacce tanada saurayi, mudinga rubuta wasiqa muna aika musu, suma suna aiko mana, Bayan munyi candy ne Kuma muka rabu da samarin kowa tafara tunanin aure, ni muka dawo jigawa, ita Kuma suna kano "

Jin ankira sallar asuba yasa firar tasu ta tsaya, Abba yatafi masallaci, sukuma kowa yafara kokarin daura Alwala.


******


Yau saura kwana uku sallah, tunda sassafe yatashi yayi wanka, yadauko suit takai Kala biyar, duk wadda yad'aga saiya ga batayi ba, daga qarshe yasaka wata ruwan toka wadda ta qarfi fatar jikinsa

Yayi mutuqar kyau shi Kansa daya kalli Kansa a mirror yasan yayi kyau, murmushi yayi yad'auki turarensa yafara feshi dashi ajikinsa
Munirat data shigo Dakin saita zubawa sarautar Allah ido tana kallo

Cikin mamaki tace "my Dear yanaga ka zubar da kayaiyaki akan gado, lafiya?"

Batare daya kalleta ba yace "naza6i Wanda zan saka ne"

"to yanzu duk wannan daka zubar akan gadon basu Maka ba? Dubafa kagani harda suit din Dana siyoma a Cairo"

Yatsina fuska yayi sannan ya kalleta yace "wannan naza6a"

Hannu tasa a qirjinta ta hardesu, sannan ta fuskance shi sosai tace "zakaje wajan Mr President ne?"

Gabansa ne yafadi, Sai alokacin yadago Kansa ya kalleta "no, zamuje jigawa nida Ramadan,ganin aikin gidan marayun Nan"

Wata wawuyar ajiyar zuciya tasaki sannan tace "Alhamdulillah....na yi tunanin wajan wata zakaje wallahi, yanda kake zuba kwalliyar Nan ai sai kasa jinina yahau, nasan inde kafita saiwata ta kallemin Kai, Amma tunda qauye zakaje, nasan banda damuwa,nasan Babu wadda tayi daidai da kalar mijina a wannan baqauyen Garin, babu ita, ba Kuma za'a yitaba"

Kansa ya girgiza yace"hakane"

Bakinsa yad'ora akan goshinta yasakar mata kiss, sannan yafice daga d'akin cikin sauri

Kai tsaye wajan mama yatafi, ganin ta yayi tana matsa qafafunta da kanta, cikin sauri ya qaraso ya tsugunna yaci gaba da matsa mata qafa fun, Kallan sa tayi tace "masha Allah,Dan mama yau Kuma Sai Ina? Ko qasar zaka Bari Amma baka sanar Dani ba?"

Murmushi yayi, dimples dinsa suka futo, yace "Wai nayi kyau ne mama?"

Tace "sosai ma kuwa, kamar Ango"

Murmushi yayi tare dayin qasa da Kansa, yad'ora hannunsa akan sumar Kansa ya Dan Sosa qeyarsa, sannan yace "haka munirat ma tace Wai nayi kyau, babu inda zanje mama, jigawa kawai nakeson zuwa saboda ganin

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login