Showing 45001 words to 48000 words out of 115646 words

Chapter 16 - Shahaab Complete Hausa Novel

12 Oct 2024

9622

Yanzu mamuda da gaske kake ashe,? Yanzu rabani zakayi da me sunan qawa,?to babu inda yarinyar Nan zataje "

Cikin nutsuwa yace" Hajja, tafiyar ta shine yafi alkhairi, zamanta anan bansan wacce irin magana zata Dauko min ba"
yana fadar haka yashige Dakin Hajja yakamo hannun Aisha suka futo, kuka take tana Kiran Hajja, Hajja ta kama hannunta ta riqe itama tana kuka, daqyar Abba ya fizgeta suka fita waje, wata yar qaramar mota ce a kofar gidan, cikin motar yasaka ta, sannan jummai tashiga, shikuma yarufe musu motar, yasunkuyo da Kansa ta window yace "idan kunje kano, Akira hajiyar a tambayeta aji koda tasamu yar aikin to asake tura mata Aishan ko bude get ne ta dinga yi musu, zamanta acan din Hankali na zaifi kwanciya, nasan babu ita babu haduwa da wannan Yaron dayake hure mata kunne"

Aisha tana jinsa saide ko d'ago kanta batayi ta kalleshi ba, kanta na cikin qafafunta tana kuka.

Jummai tace "karka damu mamuda, nasan ma za'a dace insha Allah, bazan dawo gida Bama Sai an tabbatar min sunje Abujan lafiya, kayi mata addu'ah"

Cikin sanyin jiki yayi murmushin qarfin Hali, tareda barin jikin motar yana juyawa gida, shi Kansa bazai so yarsa mace qwaya daya jal tayi nesa dashi ba, Sai dole, yana tare da'ita gida daya bai ta6a sanin akwai Wanda yake zuwa yana Kiran yarsa ba, zancen ma yawuce kofar gida agaban jama'ah saide a mota, Allah ne kadai yasan abinda zai faru inba Allah ne yakiyaye ba, juyawa yayi ya kalli motar yayinda suka fara tafiya, cikin ransa yana Binta da kyakkyawar addu'ah, Idonsa nakan motar har suka yi Nisa yadena hangosu.








Da alama Jummai ta shirya yin futo na futo tsakanin ta da Hajja😎😎

to, takwara tatafi wajan takwararta🙄, rashin kunya tatafi wajan masifa da iko🥹🥹

Wannan shi ake kira, angudu ba'a tsiraba 💁🏻‍♀️mahaifi yatura 'yarsa inda yake gudu 😇

Menene zai kasance Idan Shahaab ya dawo yaga Aisha acikin gidansa?🤔

Yaya makomar qaryaiyakin daya dinga shuka mata?🤔





(SHAHAAB littafin kudi ne, idan kika karanta min batareda kin biya ba, nabarki keda mahaliccinki,nera 300 Ne kacal bansaka kudi me yawa ba


0164549488
Amina muhammad
GTbank

My number
08033300034

Mutara zuwa gobe 🙏🏻

Amnah El Yaqoub✍🏻
Salam Alaikum,masu fitar min da littafi nagode, masu karanta wa batareda sisinsu ba nabarku kuda ALLAH,nide ban yafe muku ba, bazan yafe ba Kuma har abada, nabarku da futowar rana da faduwarta.

Masu cewa indinga yin posting biyu a rana kuyi haquri gaskiya bazan iyaba, Alokacin danace zan dinga yin posting biyu a rana, nayi tunanin yin VIP group 500, shine nace zan dinga yin posting biyu, to yanzu 300 dinma wasu suna cewa ta musu tsada,shiyasa nafasa yin VIP din, maganar posting biyu ta rushe, duk page guda daya, Ina bata awa hudu ne akansa, awa uku typing, awa daya editing, tayaya zan dinga bata awa takwas a rana inyi page guda biyu? Ayyukan gidan Ina zan kaisu? Masu min magana ta private inyi Yaya dasu? Masu kirana inyi Yaya dasu? Gaskiya kuyi haquri, kullum zamu dinga posting daya, idan Allah yasa nasamu lokaci zakuga posting biyu, idan bansamu ba zakuga daya, duk lokacin dakuka ga guda daya please 🙏🏻kuce Allah yayi masa Albarka Faqad👌🏻.


Page 22


Ganin tafiya de tazama dole yasa tabawa kanta haquri tayi shiru har Allah yakaisu kano lafiya, Bayan sun huta sun d'anci abinci Hajiya Amina tace "baba jummai ai nayi zaton kunfasa kawo yarinyar ma, itama Kuma Hajiyan bata sake kirana akan maganar ba, Amma gaskiya Ina tunanin tariga tasamu ma, Bari de inkirata inji Yaya ake ciki"

Addu'ah Aisha take a ranta Allah yasa tariga tasamu din, ba komai ne yasa take kukan barin gida ba Sai rabuwa da Hajja dakuma tunanin yanda Shahaab zai dawo yaji labarin bata Garin.

Jin Hajiya Amina tana magana awaya yasa tamaida Hankalinta kanta, Bayan sun gaisa cikin ladabi Hajiya Amina tace "Hajiya Mama Dama akan maganar me kula dakene, nace gashi ansamu wata yarinya idan har yanzu baki samu ba"

Daga can 6angaren mama tayi magana, Sai Hajiya Amina tace "a a wallahi yarinya ce qarama baki ganta ba, Kuma babu qazanta a tareda ita, ke kanki Sai hankalin yarinyar ya birgeki, babu wani datti tsaf take, babu Wanda zaice yar aiki ce"

Mama ce tasake magana, Sai Hajiya Amina tasake cewa "to.... To shikkenan, saisun zo d'in, babu komai wallahi Nima nagode"

Aisha tanajin haka ta Lumshe idon ta, shikkenan tafaru ta qare.

Kallan su tayi tace "to Alhamdulillah tace ba'a samu ba, Aisha saiki huta yau, gobe zansa driver daga Nan yatafi dake, zai Kaiki har can insha Allah"

Jummai tace"to yanzu Amina Yaya batun kudin aikin ta?saboda idan nakoma inshaida wa mahaifinta yanda mukai dake "

Murmushi tayi tace"idan taje gidan Hajiya Mama zata fad'a mata yanda zata dinga biyanta, Nima tace zata turomin wani abu ta account dina, Baba jummai Aida kinsan gidan da Aisha zata tafi da bakiyi min maganar kudin aikinta ba, saboda duk Wanda suke aiki a gidan suna samun alkhairi sosai, bare Kuma Nata aikin special ne, bawani aikin wahala zata dinga yiba,"
Tajuya ta kalli Aisha sannan tace"Aisha idan kikaje babu ruwanki da harkar kowa kinji ko? Mahmud yanason mamansa, zai iya yin komai saboda wannan tsohuwar matar, bayason abinda zai 6ata ranta, Kuma zai iya 6atawa da kowa saboda ita"

Iya jummai tace "yawwa to ai Gara kifada mata tun yanzu kinga idan taje gidan shikkenan tahuta da bincike akan halaiyar 'Yan gidan, menene ma zai had'ata da wannan matar bare har ta 6ata mata rai?"

Hajiya Amina tace "inde ta kiyaye tsakaninta da mama to ai batada wata matsalar komai, saboda a yanda naji shine, Mahmud din yana son matarsa sosai, amma duk soyaiyar dayake mata inde ta 6atawa mama rai to sa6ani take samu dashi"

Tunda suka fara magana Aisha bata saka musu baki ba Sai yanzu, ahankali tace "yanada mata?"

Murmushi Hajiya Amina tayi tace "haba Aisha, Babban mutum kamar Mahmud Wakili ai dole ya ajiye iyali, Amma ke ai ba 6angaren matarsa zakije ba, kefa kina wajan Hajiya mama, duk ayyukan da zakiyi to abinda ya shafi mama ne"

"wanne irin aiki ne?" tasake tambaya

Hajiya Amina tace "Zaki dinga kula da'ita, zaki dinga riqe hannunta kudinga Dan tattaki a gidan saboda ciwon qafafunta, zaki dinga matsa mata qafafunta, idan angama abinci Zaki zubo mata ki kawo mata, zaki dinga yimata hira saboda karki Barta cikin tunani"

Aisha ta Jinjina kanta tayi shiru, irin wannan hidima haka saikace basarakiya?(🤔)
Iya jummai tace"saboda Allah yanzu wannan har aiki ne?ai wannan bazaka kirashi aiki ba tunda kince matar ta manyanta wannan aikin ai idan ka taimaka mata kaima zaka samu Lada,tobakada aikin fari bare na baqi kawai zama fa zakayi tareda ita,"
Tajuya ta kalli Aisha tace"me sunan Hajja,kisa aranki saboda Allah Zaki mata komai, sannan ki kalleta kamar Hajjanki, insha Allah sakamakon ki yana wajan ubangiji"
Haka suka dinga zancen gidan har dare, kasancewar akwai kayan kallo a gidan Sai Aisha tad'an saki ranta tana kallo,lokaci zuwa lokaci Hajja da Ummah suna Fado mata Arai.

******

Hajja ta kalli Ummah da Abba tace"yanzu mamuda abinda ka aikata kayi daidai kenan? Yarka guda daya jal 'ya mace ka dauketa ka rabamu da'ita? Mamuda kodan yanda na shaqu da mesunan qawa ashe bazaka Gani ba?bansan cewa bakada mutunci ba Sai yau, Ina kuka yarinyar Nan tana kuka haka ka rabani da'ita, ai shikkenan babu komai, yau ka nunamin kafini iko akan AISHA"
Tana qarasa fadar haka ta Fashe da Kuka, cikin sauri Ummah ta kalleta jin sunan AISHA data fada Kai tsaye, abinda bazaka ta6aji Hajja tafada ba, ahankali tace"Hajja kiyi hakuri, abinda yasa bansaka baki ba akan maganar yarinyar Nan, Hajja ke kanki sheda ce munbawa Aisha tarbiya, kema kin bata, Aisha tana da Hankali, Barta de da rashin kunya wani lokacin, Amma abun mamaki da tsoro shine yanda ta'iya kallon idon mahaifin ta tace ita Shahaab take so, yana Dukan ta Amma yarinyar Nan haka take sake fada ita Shahaab take so, Sai abun Nata yabani tsoro, lokacin da akazo da maganar inusa ko musu batayi da mu ba, Amma zuwan wannan yaro Shahaab cikin rayuwar ta gaba daya ya sauya mana tunanin Aisha, yanzu dasuke shiga mota suna zance bamu San yaushe take zuwa wajan sa ba, inda ciki nema haka zaiyi amfani da qananun shekarun ta yayi mata, Amma Kuma saida tatafi nake jin kamar mun aikata kuskare, Ina tsoron kar Yaron Nan Shahaab yabita can Abujan suci gaba da abinda suke" tana fadar haka tafara share hawaye

Hajja datake kuka tace"kul Hadiza, banaso na qara ji kince mesunan qawa zata aikata wannan mummunan aikin, inde halin takwararta ta'iyo babu abinda zata aikata, kuskure de ubanta gashinan yariga yayi, duk abinda yabiyo baya, saiya kuka da Kansa"
Tana fadar haka, ta share Hawayen idonta tatashi tashige dakinta tanajin kamar zataga Aisha tana game a wayarta.
Ajiyar zuciya Abba ya sauke yana sake gaskata wa zuciyar sa cewa dade ace yabar Aisha anan, Gara tatafi Abujan yafi masa kwanciyar Hankali, ko banza idan Yaron yazo yagaji da zuwa zai haqura yabar masa yarsa

******

Washe gari karfe Goma nasafe suka tafi, jummai bata tafi ba saida taga tashin su Aisha sannan itama tafara haramar tafiya gida.

Sai Bayan la'asar suka Isa Abuja, Aisha tun tana bacci tana farkawa harta daina,bata ta6a tafiya me Nisa irin wannan ba, Sai abun yazame mata Sabo, tunda suka shigo cikin Garin kuwa tabaza ido tana kallo, sunyi tafiya me Nisa sosai acikin Garin sannan suka qaraso wani tanfatsetsen gida, baki bude take ganin tsaruwar gidan, yanayin unguwar babu hayaniya, Babban titin daya kawoka har bakin get din gidan ta kalla babu wasu mutane dasuke zama awaje kamar yanda akeyi a garinsu, Lema ce a kwance akoi'na alamun ruwa aka gama yimusu, Sai yanayin Garin yasake yin kyau, bata gama mamaki ba taga sojoji sun bude musu get din gidan, saida direban ya basu wani I'd card suka Gani sannan suka barsu suka shiga, batasan dalili ba haka Nan ta tsinci kanta da faduwar gaba har Sai tafara karanta "hasbunallahu wani'imal wakeel" acikin ranta.


Motar su tana tsayawa aharabar gidan taga sojoji ta ko'ina suna shawagi, Sai yanzu tasake ganin kyan gidan, tashin Hankali ne ya wanzu akan fuskar ta, yanzu wannan gidan mutane ne suke rayuwa aciki gida kamar aljannar duniya?
Sai yanzu ne tasake tabbatar wa Mahmud Wakili ba qaramin mutum bane, duk yanda ake bata labarinsa ashe yawuce haka, wannan shi ake kira jinka yafi ganinka.

Direban ne yafuto yabude mata motar yace "futo muje" yanda yabata girma harda su bude mata mota yasa Shahaab yafado mata Arai, duk yanda yake da kyau dakuma shekaru bude mata mota yake kamar itace shugabar sa, kawar da tunanin tayi daga cikin ranta suka qarasa cikin part din Hajiya Mama.


Tsaruwar falon Nata ne yasa Aisha tasake daga kanta ta kalli falon sosai, batace komai ba face Jinjina kanta datayi, wata mata ce zaune acikin daya daga cikin kujerun falon ta dora kafarta daya Kan daya,banana ce a hannunta tana karya kamar bata son ci, hankalin ta nakan abinda ake yi a TV.

duk da daga nesa ta hangeta saita ga batafi Hajja shekaru da tsufa ba, daya daga cikin masu aikinta dake tsaye abakin kofar itace tace dasu "sannunku da zuwa, ku qaraso"

Direban ne ya amsa da "yawwa" sannan tayi musu jagora zuwa wajan mama, qasa ta tsugunna tayi wa mama magana sannan ta juya zuwa kitchen

Cikin farinciki mama ta juyo ta Kalle su tace "sannunku da zuwa,mutanan kano ne?"

Aisha batayi magana ba Sai kallon matar take, haka kawai taji matar ta kwanta a ranta,kwata kwata a shekaru batafi Hajja ba, saide kana ganin ta kaga hutu da jin dadi daram ajikinta, tayi tunanin zata yi musu kallon wulaqanci a yanda ake bada labarin izzarta.

Zama sukai har suna hada baki wajan gaida ta, cikin murmushi tace"sannunku da zuwa," ta maida kallonta ga Aisha tace"yar kyakykyawa kece Mai aikin?"

Cikin sauri Aisha ta kalleta sannan tayi qasa da kanta, cikin ladabi tace "eh nice MAMA"

Jin yanda ta kirata da mama Sai hakan yayi mata dad'i, duk yanda akai yarinyar tanada nutsuwa, cikin jin dadi tace "masha Allah, kema daga kano kike?"

Kanta aqasa tace "A a Jigawa"

Gaban mama ne yafadi,jin sunan Garin yasa ta tuna da qawarta Aysha Sulaiman Bompai, Sai taji a ranta koda batada ra'ayin yarinyar to dole zata sake riqeta saboda tafuto daga jihar da qawarta tayi aure, dalilin Garin dole zata dauketa, cikin murmushi tace "menene sunanki?"

"AISHA" tafadi hakan kanta tsaye.
Mama tace "masha Allah,kice tsohuwa ce"

Murmushi su Aisha sukayi, Adede lokacin Mai aikin takawo musu abun motsa baki, mama tace "kikai masa Dakin baki saiki dawo kitafi da Aisha"

Cikin ladabi tace "to mama"

Tashi Direban yayi yabi Bayan me aikin, Bayan sun tafi mama tasake kallon Aisha tace "Aisha kisaki jikinki kinji? Maganar gaskiya Ada maiyi min hidima nace akawo min, to Amma kasancewar kinfuto daga jihar datake da dumbun tarihi awajena, saina ji bazan iya sakaki aiki ba, idan babu damuwa zan dauke ki kamar jikata, Nan gidanku ne, kidaukeni kamar mahaifiyar ki, ni banida matsala inde anyi min abinda nakeso, abu daya nakeso kikula dashi shine banaso idan Dana yazo inda nake Inga wani mahaluqi awajena, inde Mahmud yana tare Dani inaso inganni nida shi mu biyu"

Cikin ladabi Aisha tace"insha Allah zan kiyaye mama"

Mama tace"kinada account ne Wanda za'a dinga tura miki kudin aikinki aciki?"

Cikin mamaki tace "kibarshi mama, ba saboda kudi Abbana yaturo ni aiki ba saidon laifi Dana aikata masa Kuma yake hukuntani ta wannan Fannin, koba Dan haka Bama Ina ganinkine kamar Hajja ta, saboda haka zan yi miki komai tsakani na da Allah Kuma saboda Allah"

Cikin mamaki mama ta kalleta, awannna zamanin har za'a samu yarinya wadda abun duniya bai rufe mata ido ba kamar wannan yarinyar? Jitayi yarinyar tasake birgeta, tun farko irinta taso Allah yabawa Mahmud dinta,Amma Allah baiyi ba.

murmushi tayi tace"Aisha ai ba'awa iyaye laifi, biyaiya ake musu sosai, yanda Mahmud yake kyautata min yakemin biyaiya inda yaji cewa kinyi wa iyayenki laifi har suke hukuntaki toda saiya zaneki"(😄)

Murmushi Aisha tayi tafara wasa da yatsun hannunta, (nikam nace me zanewa ai shine maqasudin me laifi mama 😂)

Adede lokacin yar aikin tadawo, mama ta kalli Aisha tace"za'a bude miki account Sai Adinga saka miki kudinki aciki, wannan haqqin ki ne, bazan tauye miki haqqi ba, tashi kuje zata nuna miki d'akin ki, kiyi wanka kici abinci kihuta, zuwa gobe"
Tajuya ta kalli Mai aikinta tace"Mansura baquwa ta ce wannan, takawo min ziyara ne daga jigawa, a kaita daki na musamman"
Cikin ladabi mansura ta amsawa mama, itama Aisha tayi wa mama godia tana tunani fal ranta, wacce irin mata ce wannan? Ita datazo aiki meyasa ta 6oyewa yar aikinta tace ita din ziyara ta kawo mata? To menene na jihar Jigawan tayi mata dahar take ganin qimarta saboda kawai tace daga jigawa take? Haka ta dinga yiwa kanta tambaya har suka bar wajan maman.

Acikin falon maman Dakin yake daga can Gefe, tsaruwar Dakin ne yasa Aisha ta shagala da kallon komai, daki saikace baza'a mutu ba, akwai komai na more rayuwa aciki, nuna mata komai tayi, sannan ta juya ta fita domin kawo mata abinci, tana fita Aisha ta zauna jagwab akan gadon Dakin, cikin zuciyar ta tace"duk wannan daular gidan saboda wannan tsohuwar? Aikuwa yanda na'iya zama da Hajja Toda kowama zan zauna"


Har dare tana daki bata sake gigin futowa falon ba, tunda taji mama tayi mata kashedi akan idan danta yana Nan tana buqatar kebewa, saita rufawa kanta asiri tayi zamanta adaki, bata fatan ace ma ta ganshi, menene ma hadinta dawani danta bare har zaizo tazo tasasu agaba?

Haka ta dinga tunani, daga qarshe Takoma tunanin gida, gashi de tana cikin gida har gida, Amma Kuma tana tunanin su Hajja, Sai yau taji taqaicin rashin waya, da yanzu kiransu zatayi taji muryar su, ko Hajja tayi kunun Aya yau? Haka ta dinga tunani har bacci ya dauketa Bayan tayi sallolin dake kanta

Washe gari tunda tayi sallar asuba bata koma bacci ba, kitchen tashiga tana taya masu aikin yin wasu ayyukan, anan suka Dan saba da'ita ganin tanada budadden baki har suka sake wayar mata da kai akan yanayin gidan,yanda tasake dasu sosai ta basu mamaki, saboda Hajiya Mama bata ta6a yin baquwa wadda tashiga ransu kamar Aisha ba, gashi ita ba yar aiki ba Amma tashiga cikin su kamar wasu yan'uwanta, basu gama aikin ba Sai karfe bakwai da rabi, sukam kowa daki Takoma, tunda sungama aikinsu, saide idan mutanan gidan sungama bacci sun futo shine zasuzo su zuba musu, Aisha Kam bata koma ba, afalo ta zauna tana kallo har mama tafuto, less ne ajikinta wuyanta da hannunta d'aukeda sarqa da zoben gold,kana ganin ta kasan kudi, hutu, Dajin dadi ya zauna mata, cikin sauri Aisha ta gaishe ta, sannan tace "akawo miki abincin yanzu?"

Mama tayi murmushi tace"nace kisaki jikinki tsohuwa, kidinga yin abunda yadace kawai basai kin tambayeni ba, saide idan kinyi idan Bana buqata zan sanar miki"

Aisha tayi murmushi jin sunan da mama ta kirata tace "to insha Allah" sannan tanufi dinning tafara zuba mata abincin.

Abincin takawo mata, maimakon ta zauna aqasan kujera, saita zauna akan kujera kusa da mama(😳🤭)

Mama ta kalleta cikin mamaki, saboda ba'a ta6a yimata hakan ba, koda yaushe masu mutanan gidan girmamata suke, kafin tagama tunanin Aisha ta debo abincin a spoon tace "mama bude bakinki dakaina zan baki abincin"

Wani irin shock ne yakama mama,lokaci daya Mahmud yafado mata Arai, inda ace tayi masa aure da wuri, da yanzu tanada Jika kamar wannan yarinyar, inama yanda halayen yarinyar yake, haka halin munirat yake? Da menene zaisa ta dinga Yiwa Shahaab maganar qarin aure? Murmushi tayi tace "Aisha Anya kuwa baki ta6a aiki awani gida ba kafin Nan?"

Cikin sauri tace"a a mama,banta6a yiba,inajin ki araina ne kamar kakata Hajja, kiyi hakuri Bana daukar ki a matsayin uwar gidana, Ina daukar ki ne a matsayin kakata Hajja, inda Hajja ce take matsayin ki, Tozan iya goyata ma, saboda Hajja tana sona"

Murmushi mama tayi, tarasa meyasa yarinyar ta kwanta mata fiyeda sauran Wanda take dauka aiki, ganin ta take kamar jikar ta, wani lokacin Kuma Sai halaiyarta ta dinga birgeta taji Dama ace Mahmud da'ita yafara haduwa, babu musu ta bude mata bakin, ahankali cikin kulawa Aisha tafara bata abincin, harta kammala munirat bata

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login