Showing 1 words to 3000 words out of 61919 words

Chapter 1 - RUMANA BOOK COMPLETE BY MAMAN KHADY

22 Aug 2025

253

Ruma[4/2, 11:15 AM] Re@l💍 K@usy🌹: 💞💞💞 *RUMANA* 💞💞💞


Na


*MAMAN KHADY*🙇🏻‍♀
(Mk)


*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡
(Home of expert and perfect writer's)




Page 2




Bayan kwanaki biyu da misalin karfe biyar na yammacin ranar alhamis Alhaji Aminu ya dira a kofar gidan abokin nashi zuciyarshi cike da d'okin kawo mishi wani albishir da yayi. Wayarshi yasaka ya kira alhaji Yusuf d'in tare da gaya mishi cewar gashinan a k'ofar gida yana jiransa.


Wata farar jallabiya ya saka sannan ya fito hannunshi rike da k'aramar wayarshi wacce ita ce yafi amfani da ita akan sauran wayoyinshi.


"Alhaji kacika matsala wallahi kashiga tunda kasan ina ciki shine sai ka wani toge a nan kace min gakanan waje, toh na ganka ai zo mu shiga daga ciki.'' Tare suka jera harda wani mutum wanda tare suka zo da alhaji Aminun.


"Yauwa dama zanda zai kula da Haidar ne kamin wani lokaci aka samu kaga namijine sannan kasan dole d'awainiyar Haidar sai dai namiji maiji da karfi, gashi nan sunansa Mudi d'an maigadin gidana ne ya amince zai kula da Haidar tsakanin shi da Allah amman fa na wani d'an lokaci domin yana zuwa nijar wajan mahaifiyarshi.'' Numfasawa Alhaji Yusuf d'in yayi kafin yace.


"Toh alhamdulillah nagode sosai Allah yabar zumunci tsakanin mu, amman kayi mishi bayanin halin da haidar d'in yake ciki ko?''


"Eh nai mishi ya kuma fahimta sai dai muyi mishi fatan Allah ya bashi juriya.''


"Eh hakan yayi toh muje in nuna masa d'akin nashi, aikin naka zai kasance bashi abinci ne da wanka sai gyara mishi jiki idan ya b'ata. Kuma zakai aikin ne idan bana nan amma idan ina nan to zan amsheka saika huta kaima, amman dan Allah karike min amana idan ka cutar da Haidar lallai Allah yana ganinka kuma da sannu zai saka mishi, ban yadda cikin matana wata ta kawo masa abu tace kabashi ba kaji ko?''


"Naji alhaji kuma insha Allahu zan kiyaye.'' Cewar Mudi.


"Toh alhamdulillahi duk karshen wata zan baka dubu d'ari ammafa idan naga yanda kake yin aikin naka idan yayi min.''

Wata sufa Mudi yayi a gaban alhajin tsabar jin dad'i da farin ciki, godiya yake yi kamar bakin shi zai yage. Tare suka shiga d'akin Haidar d'in yana rakabe can wajan labulen toilet ya takure kanshi kamar wani maraya, kanshi a k'asa yana ta faman murzar yatsunshi kamar wanda aka yiwa dole.


"Ah Abban Haidar wai dama yana nutsuwa irin haka?'' Cewar alhaji Aminu.


"Eh yana yi wani lokacin ko kuma kaji yana ta sambatu babu kai balle k'afafu, wani lokacin yaita kuka wani lokacin kuma yaita bige-bige amma idan yai wannan nutsuwar sai kaga inama ace haka lalurar take wallahi wani lokacin sai naga kamar ya warke ni bige-bigen da yake yine kawai bana so domin wani lokacin kana gani duk sai ya jiwa jikinshi ciwo.''


Mudi dake tsaye bayan su yana jin duk abinda suke cewa tuni ya shagala da kallon kayataccen d'akin wai wannan ne dakin mahaukaci lallai dukiya na inda take, amma shi aganin shi wannan lalura ai maganin gargajiya ya dace ai mishi bawai na asibiti ba. Nan dai sukabar Mudi suka fice.


****


BAYAN sati daya Mudi yana matukar k'ok'ari wajan ganin ya taimakawa Haidar domin har addu'a yake tofa mishi yana bashi yana sha ba tare da sanin alhajin ba, kuma sosai yake ganin cigaba amma wani idan abun ya tashi sai kaga kamar ya k'arasa haukacewa gaba d'aya.

Cikin d'akin Haidar babu wani abu me sunan makami domin hatta gado babu shi cikin d'akin sai dai k'atuwar katifa kayan sawarshi kuwa like suke a bango.


Sosai Mudi yake k'ok'ari wajan kula dashi, da kanshi yak emai wanka kuma ya gyarashi kai shi har gyaran fuska yake mishi da hammata da gabanshi idan yana bacci shi yasa nan da nan Haidar d'in ya kuma kyau sosai duk ya canza.


Satin alhaji Yusuf uku da tafiyar da yayi zuwa k'asar China, sosai yai farin ciki da yaga yanda yaron shi ya koma, sai dai aranar ya tadda Mudi da rauni agoshinsa wai wajan yima Haidar d'in wanka ne ya had'ashi da bango dan yaki bashi sabulu yaci.


Naira dubu d'ari cif ya bawa mudi tare da tsara ba na kayan sawa da sauran bukatu, ai kuwa sai da yaji kamar zai mishi sujjada tsabar godiya.


Da dare....


Mudi na kwance gefen Haidar bayan alhaji yai musu sallama ya tafi wajan iyalin shi jiyai Haidar d'in yana lalubarshi tare da sakin nunfarfashi kamar dai wanda yake cikin matsananciyar sha'awa.

Da mamaki Mudi ya kunna hasken d'akin ya kura mishi ido yana kallon juye-juyen da yake yi ga abun nashi ya wani cika gaban wandon shi. Wasu irin hawaye ne suka shiga zubowa Mudi tsabar tausayin da yaji yana neman rufe shi.

''Allah ya kawo maka sauki Haidar, Allah ya kawo maka iyakar wannan lalura da kake ciki, duk wanda yai maka wannan abun Allah ya maida mishi da aniyar shi inda lafiyarka lau ai da yanzu kana nan da iyalinka amma yanzu babu wacce zata yadda ta rabeka wallahi, Allah yabi maka hakkinka.'' Addu'a yai ta tofa mishi har saida yaji saukar numfashinsa alamar yai barci.


Da safe...


''Alhaji an tashi lafiya ya gajiyar tafiya?''


"Lafiya lau Mudi ya mai jikin ya kuka kwana?''


''Alhamdulillah alhaji, amma jiya dai gaskiya ya kwana babu dad'i domin inaganin sha'awarshi bata samu nak'asa ba dan ni dai naga jiya ta tashi kuma da kyar ya samu bacci.'' D'an murmurshi alhajin yayi yace.


''Eh hakane Mudi tana tashi wani lokacin to kaga babu yanda zanyi dashi musamman a halin da yake ciki yanzu babu wanda zai yadda ya bada d'iyar shi ta auri mai irin larurar Haidar, amma kwannan zanje gida can bakori insha Allah zan kuma cigitawa idan Allah yasa an samu saina aura mishi.''


"To to Allah ya zab'a masa ta gari kuma mafi alkhairi, shi kuma Allah ya bashi lafiya.''


*****


Asalin su Rumana, malam Habu shine mahaifin Rumana d'an garin maska ne ta jahar katsina kagabada, a nan aka haife shi kuma a nan ya taso yana sana'ar sai da itace matar shi subanta Habiba itace kuma mahaifiyar Rumana itama 'yar nan cikin garin ce tare take zaune da surukanta kasancewar sam malam habu bashi da ikon siyen gida balle ya saka matarshi a ciki.

Iyayen malam habu sam basa kaunar Habiba ba kuma dan komai ba sai dan mahaifinta ya kasance babban malami wai kadda su saki jiki ashanye musu yaro duk da cewa matsalar tafi yawa daga wajan ita mahaifiyar malam habu d'in. Daga baya ne sai ya dawo cikin garin funtuwa ya fara sai da kayan gwanjo kuma alhamdulillah sana'ar ya farata cikin nasara.

A lokacin da ya maido da Habiba funtuwa sai da akai d'an k'aramin yaki da mahaifiyarshi musamman daya kasance har lokacin ita Habiban bata haihu ba, tunda har an fara yi mata kiran ita juya ce bata haihuwa.


Malam habu irin mutanan nan ne masu tsananin hakuri da kauda kai haka itama matarshi Habiha sam basu da hayaniya. Allah ya basu haihuwar Rumana kusan lokacin da basu zata ba domin sai da cikin yai wata hud'u cikin na biyar sannan suka farga akai ta taya su murna sosai fiye da tunani kowa. Cikin iko na Allah suka raine shi Allah ya basu Rumana mahaifinta yasa mata sunan sabida yana kaunar sunan sosai Ummu Rumana sai dai tuni Rumana ya bita.

Tataso cikin kula sosai ta uwa data uba sannan kakanni domin idan sukaje maska kowa nan nan yakeyi da ita, Basu kuma samun haihuwaba kuma hakan be zama damuwa ba a gare su.

Akwai tarin ilmi mai yawa awajan Rumana kasan cewar makarantar kud'i ya sakata islamiyya da boko sabida ta samu ingantaccen ilmi, sannan yana ganin basu da yara da yawa balle dawainiyar su tai mishi yawa.

Sannan kullum dare mahaifiyarta takan d'ora mata karatun addini amatsayinta na d'iyar babban malami tare da addu'o'i musamman wad'anda suka danganci na neman tsari tare da karya lagon makiya.


Shekararta goma dai-dai, wani mummunan al'amarin ya faru domin wuta ce takama d'akin da iyayenta suke kwance har sai da ta cinye su tas! dalilin maganin sauro da aka kunna. Mutane suka cika gurin masu temako amma babu wani abu da yayi saura balle ataimaka musu kasancewar Rumana na tsakar gida. itama kuka take yi irin kukan nan mai tsananin azaba da tashin hankali.


Kowa yaji wannan mutuwa musamman wad'anda suka mu'amalanci malam Habu da matarshi Habiba, sannan kuma iyaye wad'anda suka kusa zaucewa sabida jin mutuwar.


Rikon Rumana sai ya koma hannun kakaninta na wajan uba dake nan madai, sun kula da ita da dad'i babu dad'i ana tare har Allah yasa tayi shekara uku a nan gurin su, daga baya sai yayar babanta wacce ke aure a bakori ta amshi rikonta sabida ita Allah bai tab'a bata haihuwa ba amma mijinta yana da yara har guda biyar duk mata kuma sunyi aure, ya tab'a auran wata matar sai dai daga baya ta rasu,.

Gwaggo Suwaiba irin matan nan ne masu tsananin ganin kyashin tsiya sam bata iya gani ta kauda kai ga uwa uba zalinci babu ruwanta amaimakon tunda ita bata haihu ba tasamu ta kula dani amatsayi na na d'iyar kaninta kuma uwa d'aya uba d'aya amma ina kullum wulak'ancin yau daban na gobe daban kai yanda ma malam d'in yake jin tausayina kuma yake kula dani saika d'aukama shine d'an uwan nawa bawai ita ba.

Inda Allah ya taimakeni sam bata hanani neman ilmi na ba kuma dai-dai bakin gwargwado tana min sutura sai dai akwaita da masifa da jaraba dan sam bata da hakuri.

Tun ina da shekara goma sha biyar nai saukar alkur'ani daga baya ne na fara hadda wadda alhamdulillah ina da sani sosai musamman ta b'angaren addini har larabci na iya sannan har yanzu duk karatun da Ummana tayi min yana nan akaina kuma kullum ina musu addu'a suma.

Malam sule shine mijin gwaggo Suwaiba amma ina ce mata inna sabida duk haka 'ya'yan malam d'in suke kiranta, sannan shi kuma malam d'in na kan kirashi da baba kamar yadda naji ana kiran shi.

Yana sona sosai yana kuladani sannan duk abinda ya shige min duhu yana k'ok'arin haska minshi domin shima yana da ilmi sosai kayan miya yake sai dawa a nan cikin kasuwar bakori.

Ayanzu inada shekara goma sha takwas da wata hudu, ni d'in bawai fara bace amma kuma baza akirani da bak'a ba ina da fata mai kyau sosai, fuskata doguwa ina da dogon hanci da idanu masu kyau kuma madai-daita wanda mutane da yawa sukan yaba su, bani da irin tsawon nan amma kuma ban kasance gajera ba, kirar jikina ta fita sosai alhamdulillah da baiwar da Allah yayi min, na gama secondary d'ina tun watanni uku da suka wuce sai dai har yanzu ban daina zuwa makarantar islamiyya ba kasan cewar ilmi zurfi ne dashi musamman na addini da kullum baka gajiya da neman sa.

Inna da kanta take korar duk wani wanda ya nuna yana sona sabida tsabar kwad'ayin ta tuni ta daina zuwa dani maska sabida ana mata fad'an taki barina nayi aure. Ita kuma tace duk masu sona basu yi mata ba sabida tsabar kwad'ayi irin nata.

Hidimar inna da duk wahalar da take bani sam ba ta cika damuna ba domin idan nai wani tunanin sai naga ai itama tana kuladani kuma dan ta isa dani ne shi yasa amma shi baba yana nuna sam baya so domin kusan kullum sai ya tuna mata da illar cutar da maraya.

Kubiyoni......
















*MAMAN KHADY*🙇🏻‍♀
[4/2, 11:15 AM] Re@l💍 K@usy🌹: 💞💞💞 *RUMANA* 💞💞💞


Na


*MAMAN KHADY*🙇🏻‍♀
(Mk)


*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡
(Home of expert and perfect writer's)




Page 3






Ina kwance tunanin da nake yi wanda yai nisa naji saukar dundu a bayana, a zabure na mike ina neman kallabina ina cewa.


''Inna banji kina kirana ba wallahi.''


''Dallah kyaleni ina aiken da nayi miki gidan su Dije?'' Idanuna harsun kawo ruwa sabida tsoro baki na rawa nace.


''Wallahi mantawa nayi inna lokacin da naje bata nan sai dai su Dijen.''

"Amma shine dan Iskanci kikai min shiru bakije kin sanar min ba? Toh saiki tashi muje ki wanke kayan can kafin lokacin islamiyyar ku tayi kuma kice ke islamiyya zakije.''


Binta nayi da kallo kai inna ko ta maidani sai kace injin wanki kullum sai nayi wanki ko basu taru ba, koda yake ai nakoyi tsafta wajanta tursasawar ai.


Sai wajan uku na gama wankin a gaggauce nayi wanka tare da alwalar la'asar sannan na shige d'akina wanda babu komai sai wani k'aramin gadon bono da jakar kayana a gefe, ko kayan kwalliya na azo agani bani dasu koda yake koban yi kwalliyar bama akan yaba kyauna, dan kallo d'aya zai wadatar da kai akan cewa lallai ni d'in mai tarbiyya ce domin haka Allah ya halicceni kalar tafiya ta ma kawai mai matukar d'aukar hankali ce.


"Kai Ruma wai da wucewa zaki yi?'' Cewar Dije.

"Yo da jiranki zanyi ke da kullum saikin makara kike jin dad'i, shi yasa zan wuce na barki kawai.''


"Toh Allah ya kamaki wai ya maganar taron da makaranta ta shirya ne? Nifa tunda naji ance wad'anda suka gama hadda za'a yaye naji raina baya so dan idan an yayemu sai a kaimu gidan wa?'' Dariya nayi har kumatuna suka lob'a sannan nace mata.


''Ni wallahi matsalata dake garaje, yo ina kuwa zasu kaimu, amman dai ina tunanin zamu fara tallafawa sauran malaman ne kota b'angaren kula da yara ne tunda kinga ana ta samun dalibai amma ba malamai da yawa sannan kinga duk girman makarantar nan mune manya tunda mune na farkon wad'anda zasu yaye.''

"Eh haka ne na gane.''


Cewar Dije lokacin da muka shiga cikin makarantar. Kusan duk karin bayani akai mana akan abubuwan da zamu gabatar ranar asabar domin ranar ne za'a yi gagarumin taron da aka jima ana shiryawa.

"Ke Rumana kinsan cewa kece shugaban d'aliban makarantar nan, sannan karatunki yana fita ta yanda ake so sabida haka ki shirya duk wasu addu'a da za'a yi domin kece wacce zaki bud'e taro da addu'ar. Sannan zaki yi karatu kuma zaki mana fashin baki akan wasu hadisai wanda za'a aiko miki dasu gobe ko kuma yau ki wuce dasu gida dan ki sake dubawa."


Malam tijjani yai maganar idanunshi kur akaina wanda hakan ne ya tilasta min sunkuyar da kaina kasa.


Agajiye muka koma gida ga jikina yai wani irin mugun sanyi musamman da naji ana fad'in irin manyan mutanen da aka gayyata kuma wai nice mai bud'e taro na san ma kila jikina rawa zai tayi sabida farga ba.


Innan na samu da maganar duk yadda muka yi da malaman tayi farin ciki sosai a wannan lokacin sannan ta k'arasa maganar da fad'in.


''Allah yasa kafin a tashi kisami miji a wajan na nunawa sa'a, Kinga anjima da daddare aka ce aje a anso d'in kin ki, toh amma ki bari sai da safe ki amso sannan ki yanko yadin hijabin da zaki saka, takalmin kuma gashi can Allah ya bada sa'a, amma sai kin daure idan ba haka ba kunya da idanun mutane baza su barki kiyi abin kirki ba wallahi.''

Oh yau wace rana inna namin magana cikin sanyin rai bada tsawa ba....


*****


Bige-bigen da ake yi a cikin d'akin sai kai tunanin wasu mutane ne masu yawa cikinsa amma ina shi kadai ne cikin d'akin amma tuni ya can zama d'akin fasali sabida tashin ciwon shi. Mudi ne ya shigo da sauri yana nanata kalmar.


''Subhanillahi Haidar wannan lalura taka Allah yai mana maganinta.'' Alhajin ya fita nemowa a waya ya sanar dashi halin da ake ciki ya kira likita wanda dole sai da aka mishi allura sannan suka samu sa'ida.


Sai yamma lik'is sannan alhajin ya shigo garin kasan cewar dama yana garin abuja yaje gano wani kamfaninshi. Kai tsaye d'akin Haidar d'in ya shiga nan ya tarar dashi kwance yana bacci, yayin da Mudi ke zaune a gefenshi yana gyangyad'i.


Ganin kamar Haidar d'in ya rame a yau ya kuma tashin hankalinshi tare da hanashi nutsuwa ya fara tambayar Mudi.


"Kai Mudi.!'' Cewar alhajin yana taba kafad'ar Mudin.


"Na'am alhaji barka da sauka.''

"Yauwa wai cewa nayi ya naga Haidar ya fad'a ko akwai wata damuwa ne?''


"Babu damuwar komai alhaji amma jiya ciwon ya bigeshi sosai yauma hakan, dan kaga nan wannan kululun da yai min wallahi had'ani da bango yayi, ni sai naga kamar ma ciwon neman yin gaba yake yi.''


"To Allah ya kyauta daman ranar asabar zanje bakori insha Allah kome muka yi da yayana zan sanar maka ya gayyaceni wani taron yaye dalibai da zamu yi shawarar yanda za'ayi tunda dama nine naki yadda ayi mishi na gargajiya.''


"To shikenan alhaji hakan shine dai-dai gaskiya domin yaron nan yana cikin wani hali wallahi gashi yana da karfin sha'awa sosai, in ta taso mishi har hawaye nake yi sabida nasan babu dad'i gashi besan yanda zai yi ba.''


******


Ranar asabar kamar yadda aketa jira tare da tsara yanda taron zai tafi daidai tazo, sun shirya komai kuma alhamdulillah komai yayi yanda ake so. Gaba d'ayanmu wad'anda za'a yaye mu sha takwas ne maza takwas sai matan mu goma, muna cikin ankon wata dalleliyar shadda me ruwan sararin samaniya tare da farin hijab da farin takalmi.

Mazan ma shaddar irin tamu ce sai farin takalmi da farar hula, Hakika munyi kyau munkuma bada kala tun a wannan lokaci manyan mutane suka fara yabama tsarin da muka yi.


Munsami halartar manyan mutane wa indama bamu zata ba sannan iyayen mu da dangin mu kowa burinshi ace ga nashi shima ya samu wannan d'aukakar.


''Ki daure Rumana dan Allah kadda ki badamu a wajan nan, kiduba kiga yanda manyan mutane suka zo gurin nan kadda ki kalli fuskar kowa kedai kawai kiyi abinda ke gabanki bana san wannan rawar da jikinki keyi ki dake sosai kilama daganan ki wuce saudiyya insha Allahu.''

Malam Aminu kenan shine

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login