Showing 78001 words to 81000 words out of 127530 words
ya qarasa asibitin. Kuka sosai ya sameta
tanayi idanunta jajur. A rude yake tambayarta
abinda ya sameta. Bata tanka ba. Yace, to ga
gasasshen kifi na siyo miki, nasan zaki ci. Ya duba
cikin kular da yaya ta dafo mata abinci kafin su
wuce, ashe faten wake ne da kifi, amma bata ci ba.
Ya dawo ya zauna bakin gadon. “Kar dai duk yau
bakici abinci ba? Ta kalleshi idanunta jajur, “yau na
yarda banida kowa, muryarta tana rawa irin na
wanda ya gaji da kuka. Yace me akayi miki khadija da
bana nan? Fadamin. Kuma karki sake cewa, bakida
kowa. Gaki da ni, ga yaya Amina, muma da mu biyu
ne, amma ynxun kinga mun qara mun zama mu
uku. Mun tafi da tunanin ki. Ya warwaro tissue ya
soma share mata hawayen. Sannan ya dauko kifin ya
soma bata a baki sala-sala tare da jajjagaggen kayan
miya. Taci sosai, sannan ya debo ruwa ya kawo mata,
ya taimaka mata ta wanke hannu da kuma baki.
Sannan yace khadija tunda ynxu kina iya zama zaki
iya yin sallah. Ta 6ata rai. Yace wai meyasa duk
lokacin da nayi miki zancen sallah, sai ki 6ata rai?
Tace to yaya zan iyayin sallah a haka? Yace, zaki iya
mana. Shi addinin musulunci sauqi ne dashi, ya nuna
mana yadda zakayi ibada matsawar kana cikin
hankalinka. Ita kuwa sallah sbd muhimmancinta, ko
a filin yaqi anayin ta. Tace, ni ynxun dai ka barni
barci zanyi. Ya ce, kinada yaqinin daga varcinnan zaki
farka?
Tayi shiru, yace bakida yaqinin cewa, zaki farka,
kuma zaki iya farkawa ki ganki a kabari. Tace, oh
Allah na, don Allah kabar zantukannan. Yace assha!
Assha! Ina tsoron kar zuciyarki ta kamu da mugun
ciwo, wanda batason ko kadan taji an ambaci Allah
ko manzonsa, ko wani abu na addini. In hakane
kuwa lallai kin daura qawance da shaidan, kuma yaci
galaba akanki. “Don Allah ka barni mana! Ga
mamakinsa, sai yaga ta soma kuka, shiru yayi, ransa
6ace. Lallai akwai matsala babba, akan zancen addini
mimi ke kuka. A fili yace “akwai aiki!.
Hajiya Nana tace, Nafisa in har zaki fitar da kudi
gurin shawo kan yaronnan, ba zai zama matsala ba.
Nafisa tace, haba Nana kamar baki sanni ba, in ta
samu kan yaronnan koni sai na qara haskawa a idon
babansu bare ita. Kin sani ban tausayin kudi a gurin
kashewa, ynxun dai fada min me za’a yi? Hajiya Nana
tace, tsabar katan qamshi za’a hada masu fizgar
hankali. Sai yabi ta ko ba don Allah ba. Ba sai ta shafa
wani man bilicin ba. Tashi muje gidan Hajiya Hauwa.
Naje naga kayan, daga kaduna aka turo mata su jiya,
lokacin ina gidan nata. Dandano ta bani na shafa,
amma Alhaji, yadda kk san ya zauce. Surutai kuwa
daya dinga zubowa, wane yayi kaza, wacce ma tayi
kaza. Momy Nafisa ta sheqe da dariya. “kai Nana!
Allah ya shiryeki.
Tace, kin zata qarya ne? Zomuje in mun dawo kidan
ta6a ki gani. Momy tace, ni mijina da bashi da lfy,
yaushe zan sake zauta shi. Har suka kai gidan Hajiya
Hauwa, Hajiya Nana tana bawa momy Nafisa labarin
kyawun kayan. Da ido kurum momy nafisa ta kalli
kayan, ta gamsu da batun Hajiya Hauwa. Ta basu
kayan, inda daganan suka nufi gidan Na’ima. Cikin
sauri ta bude falon lokacin da taji qaran alarm.
Domin tana tsoron kar ta sake yin laifi. Rungume
momy tayi tana kuka.
Kayanta ta soma hadawa bayan sun zauna a bakin
gadon Na’imar. Tana fadin momy qafata qafarki. Ba
zan sake zama a gidannan ba. Hajiya Nana tace, “ke
da Allah natsu! Na’ima ta tsaya tana share hawaye
don tasan Hajiya Nana bata daukar raini, tace zonan
ki zauna in karanta miki. Nan ta soma shiryo abinda
suka zo dashi, tace kin zauna kinata faman wasu
koke-koke. Duk matar da kk ganta gidan auren ta,
karki tsaya tona irin qalubalen da take fuskanta, ko
kuma wanda ta fuskanta a baya. Mu kanmu nan da
kk gani munsha gwagwarmaya kafin mu kafu a cikin
gidajenmu.
Ta ciro mata wata kwalba, wannan ki lura dashi da
kyau, don duk yafisu tsada kuma ya fisu aiki. Natsu
sosai kiji yadda zakiyi amfani da ko wanne. Nan suka
karanta mata, tare da bata shawarar yadda zata
shanye duk wani wulaqncin da zai mata. Momy tace,
kar in sake jin batun tafiya a bakinki, du-du-du,
yaushe akayi auren da zakice kin gaji. Salon kija
mana dariyar ‘yan baqin ciki. Da ma gashi jikin
dadynku yaqi, ki jure kawai, kuma kiyi aiki da abinda
aka fada miki. Nan dai suka dan kwantar mata da
hankali, suka fita, suka tafi.
Sha biyu da kusan minti arba’in na dare lokacin ne
Abokan Abbas suka sauke shi a gida a buge. Daga
bugun qofar falon, zaka san baya cikin hayyacinsa.
Na’ima, wadda ta soma barci sbd gajiya da tayi da
jiranshi, ta miqe a tsorace ta nufi qofar inda yaketa
kiranta. “Na’ima in na shigo sai na ci miki mutunci.
Ba zaki budemin qofar ba? Tana budewa yabi ta da
kallo tun daga qasa zuwa sama. ‘yar mitsilar rigar
varci ce a jikinta mai shara-shara. Yana kai idanunsa
fuskarta, sai yaga ta rikide masa ta koma mimi.
Cikin wata kidima ya rungume Na’ima a zaton ta
abubuwan da tayi amfani dasu ne suka fizgeshi.
Amma shi mayensa da yake ciki shine ya suranta
mashi haka. Sai kurum taji yana cewa, Mimi kin
dawo gurina ko? Dama nasan zaki dawo gareni.
Samansa sukayi yanata ririta ta, tare da nuna
qaunarsa tamkar zai cinyeta. Na’ima tana kukan
takaicin yana tare da ita, amma yana ambatar sunan
mimi, har lokacin da yayi buqatarsa da ita ya fadi
gefe, yana sheqa varcinsa.
Hajiya Nana tace, Nafisa in har zaki fitar da kudi
gurin shawo kan yaronnan, ba zai zama matsala ba.
Nafisa tace, haba Nana kamar baki sanni ba, in ta
samu kan yaronnan koni sai na qara haskawa a idon
babansu bare ita. Kin sani ban tausayin kudi a gurin
kashewa, ynxun dai fada min me za’a yi? Hajiya Nana
tace, tsabar katan qamshi za’a hada masu fizgar
hankali. Sai yabi ta ko ba don Allah ba.
Ba sai ta shafa wani man bilicin ba. Tashi muje gidan
Hajiya Hauwa. Naje naga kayan, daga kaduna aka
turo mata su jiya, lokacin ina gidan nata. Dandano ta
bani na shafa, amma Alhaji, yadda kk san ya zauce.
Surutai kuwa daya dinga zubowa, wane yayi kaza,
wacce ma tayi kaza. Momy Nafisa ta sheqe da dariya.
“kai Nana! Allah ya shiryeki. Tace, kin zata qarya ne?
Zomuje in mun dawo kidan ta6a ki gani. Momy tace,
ni mijina da bashi da lfy, yaushe zan sake zauta shi.
Har suka kai gidan Hajiya Hauwa, Hajiya Nana tana
bawa momy Nafisa labarin kyawun kayan. Da ido
kurum momy nafisa ta kalli kayan, ta gamsu da
batun Hajiya Hauwa. Ta basu kayan, inda daganan
suka nufi gidan Na’ima.
Cikin sauri ta bude falon lokacin da taji qaran alarm.
Domin tana tsoron kar ta sake yin laifi. Rungume
momy tayi tana kuka. Kayanta ta soma hadawa
bayan sun zauna a bakin gadon Na’imar. Tana fadin
momy qafata qafarki. Ba zan sake zama a gidannan
ba. Hajiya Nana tace, “ke da Allah natsu! Na’ima ta
tsaya tana share hawaye don tasan Hajiya Nana bata
daukar raini, tace zonan ki zauna in karanta miki.Nan
ta soma shiryo abinda suka zo dashi, tace kin zauna
kinata faman wasu koke-koke. Duk matar da kk
ganta gidan auren ta, karki tsaya tona irin qalubalen
da take fuskanta, ko kuma wanda ta fuskanta a baya.
Mu kanmu nan da kk gani munsha gwagwarmaya
kafin mu kafu a cikin gidajenmu.
Ta ciro mata wata kwalba, wannan ki lura dashi da
kyau, don duk yafisu tsada kuma ya fisu aiki. Natsu
sosai kiji yadda zakiyi amfani da ko wanne. Nan suka
karanta mata, tare da bata shawarar yadda zata
shanye duk wani wulaqncin da zai mata. Momy tace,
kar in sake jin batun tafiya a bakinki, du-du-du,
yaushe akayi auren da zakice kin gaji. Salon kija
mana dariyar ‘yan baqin ciki. Da ma gashi jikin
dadynku yaqi, ki jure kawai, kuma kiyi aiki da abinda
aka fada miki. Nan dai suka dan kwantar mata da
hankali, suka fita, suka tafi.
Sha biyu da kusan minti arba’in na dare lokacin ne
Abokan Abbas suka sauke shi a gida a buge. Daga
bugun qofar falon, zaka san baya cikin hayyacinsa.
Na’ima, wadda ta soma barci sbd gajiya da tayi da
jiranshi, ta miqe a tsorace ta nufi qofar inda yaketa
kiranta. “Na’ima in na shigo sai na ci miki mutunci.
Ba zaki budemin qofar ba? Tana budewa yabi ta da
kallo tun daga qasa zuwa sama. ‘yar mitsilar rigar
varci ce a jikinta mai shara-shara. Yana kai idanunsa
fuskarta, sai yaga ta rikide masa ta koma mimi.
Cikin wata kidima ya rungume Na’ima a zaton ta
abubuwan da tayi amfani dasu ne suka fizgeshi.
Amma shi mayensa da yake ciki shine ya suranta
mashi haka. Sai kurum taji yana cewa, Mimi kin
dawo gurina ko? Dama nasan zaki dawo gareni.
Samansa sukayi yanata ririta ta, tare da nuna
qaunarsa tamkar zai cinyeta. Na’ima tana kukan
takaicin yana tare da ita, amma yana ambatar sunan
mimi, har lokacin da yayi buqatarsa da ita ya fadi
gefe, yana sheqa varcinsa, amma yana ambatar
sunan mimi, har lokacin da yayi buqatarsa da ita ya
fadi gefe, yana sheqa varcinsa.
Na’ima tayi kuka, iya kuka cikin daren kafin varci yayi
gaba da ita. Qarfe takwas ya farka. Halin daya ganshi
ciki ya sashi kallon gefensa. Na’ima ya gani kwance
cikin irin yanayin daya samu kansa. Ya soma tunanin
da yaushe har tazo masa daki akai hakan? Ya dai iya
tuno jiya sun samu matsala da Jennifer. Yarinyar
daya kawo ta Abuja da kansa ya kama mata gida tana
zamansa, ynxun kuma sai ta dinga munafuntarsa.
Jiya yaje mata zuwan bazata sai ya sameta ta kawo
wani gidan. Yayi mata magana tana fada masa cewa,
itafa ba matarsa bace bare ya dinga yi mata dokoki.
Yayi mata duka kafin ya baro gurin ta ya nufi club
dinsu inda suke hadewa da abokansa suna shayeshayensu. Ya fada musu halin da yake ciki, nan suka
bashi shawarar cewa, yasha mayensa ya manta da
ita, ya daina zuwa ta gani in akwai wanda zai mata
kwatankwacin abinda yake mata. Sha yayi sosai, don
bai ta6a sha irin haka ba. Ko iyayensa basu san yana
sha ba, domin baya sha da yawa.
Ya kasa komai don haka suka kawoshi gida. Tuna
hakan yasa shi gane cewa, maye ne ya suranta masa
Na’ima a matsayin Mimi. Tsaki yaja sannan yasa
hannu ya daddaka mata duka. Firgigit ta farka tana
kallonsa, fuskarsa daure. Yace, tashi ki fita! Tace
dama kai ka kawoni bani nazo ba. Ta soma kuka,
yace ban tambayeki wani dogon zance ba. Nace dai
ki fita. Na’ima ta saka rigar varcinta ta fita da kuka. Ya
jima shiru yana takaicin faruwar hakan Tsakanin su,
don bai tsara zaiyi hakan da ita ba. Amma sai ya
miqe ya nufi bandakinsa.
Na’ima ma bayan tayi wanka da sallah, ta koma ta
zauna tanata tunanin yadda mijinta yake mutuwar
son mimi. Kai ita da ta sani, da bata kawo kanta gurin
son maso wani ba. Can ta miqe ta nufi kicin, yauma
da kanta ta girka abinda zataci kifi ta gasa, irin gashin
da Mimi kansa ayi mata. Na’ima ta dan iya girki,
domin ko a gidansu tana shiga kicin gurin masu yi
musu girki jefi-jefi.
Ta gasa bread dinta, zata fito shi kuma zai shigo kicin
din, ya kalli tiren hannunta, “bani kiyi wani! Bata
musa ba, ta miqa masa don tanason su riqa ‘yar
hulda ko yaya. Ta koma ta hado wani abin karin.
Bayan ta karya ne ta shiga turare gidan da turarukan
da aka kawo mata. “Yayi qamshi. Ya fada, duk da ba
cikin walwala yayi maganar ba. Taji dadi, kuma taji
mamaki. Don haka bayan fitarsa, sai ta dauko sauran
abubuwan ta kama amfani dasu.
A waya Abbas ya kira Usman, yana bashi labarin
abinda ya faru a jiya. Usman yace, kai sakarai me
nace maka? Ai na fada maka kawai ka more
quruciyar Yarinyar kace a’a, to ynxun don ja nuna
ma Jennifer kurenta kawai, ka share ta kaci
amarcinka. Abbas yace, banason Yarinyar tayi
tunanin cewa, ina sonta ne. Usman yace, ai ba wai
zaka sakar mata fuska bane sosai. Ka gane? Abbas
yace, shikenan zan kwatanta. Tun daga ranar Na’ima
tadan samu sauqin mijinta. Zai sata ta dafa masa
abinci, kuma zai kirata shimfidarsa. Amma ba wata
soyayya, ko kulawa, ko hira ko sakin fuska.
Abin da ta lura amfaninta kenan tayi masa girki,
sannan yayi buqatarsa. Wani dare ya kirata a waya
taje samansa. Ta sameshi a falo tace gani. Yace ki
shiga mana. Kin tsayamin akai, sai kace wani sa’anki.
Ranta ya sosu, tace, wai kai kana bani mamaki. Kana
nema a gurina amma kayi ta dauremin fuska, kana
fadamin abinda kk so. Yace kar ki kawomin raini. Ki
wuce muje. Tace, ni varci nakeji, ta juya. Nan take ya
kamota, saida ya mammareta, sannan yayi abinda
yake so anan falon, ya kuma koreta zuwa dakinta.
Zahiri baya sonta, amma abubuwan da take sha, da
wanda take qamsasa jikinta suke fizgarsa gareta. Irin
Rayuwar da Na’ima ke ciki kenan. Gashi danginsa sun
tsane ta, musamman uwarsa wadda tace, Na’ima ta
bada ita a gaban Qawayen ta. Zainabu kuwa
tana can gidansu, saiga Alhaji ya diro da la’asar
sakaliya. Yayi sallama dz innar su Zainabu. Yau kam
fuska daure ta fita, da nufin bala’i tare da ita. Sai dai
shima tana kallon sa tasan cewa da hakan yazo,
kuma in ba sa’a bama shi ya dama ta ya shanye.
Kafin tayi magana ya riga ta.
Nazo daukar Zainabu ne. Ta lailayo ashar ta maka,
sannan tace, Zainabu ba zata koma ba, sai ya sauke
dubu ashirin da hudu na asibiti. Yace, tunda dai
banyi muku qorafin cikina da kuka zubar ba, to ku
bani matata kawai mu tafi. Inna tace, au tanan ka
biyo? To ai inason ka sani, tuni muka samu labarin
baka son haihuwa, bare kayi wata barazanar banza.
Ba zata koma ko ina ba, sai ka canke kudin mutane.
Yace, haka kk ce? To kuwa ku shirya cin wani bashin
don zaku amsa sammaci, kotu zamu shiga.
Ya ciro wayarsa, iroro dake gefe yace, Alhaji ai sai ka
kira lauyannan naka tukun, domin duk wanda baisan
mutunci ba, gara ayi masa abinda yafi sani. Wato
rashin mutuncin ba. Inna tace, ku kira alqali, ba
lauya ba. Kai kuma dan kanzagi makwadaici kabi a
sannu. Kaje ka nemi sana’a ba maula ba. Iroro yace,
ai indai wannan ne sunanmu daya dake, wato ‘yan
maula. Kwadayinki kuwa ya ninka nawa. Tunda kk
miqa ‘yarki ga wanda bashi ta za6a ba. Alhaji yace, ko
ba haka bama Iroro, ai baka kaita roqo ba, kullum
dan aike yana hanya. Tace, kodai me zaku fada, ku
fada.
Lokacin ne layin ya shiga wanda yake nema. Alhaji
yace, yauwa Barista audu kaji ko? Daga can suka ji
murya tace, eh ina jinka Alhaji lawal. Iroro yace,
Yauwa Alhaji ai gara kasashi a speaker taji. Alhaji
game da zancen da mukayi ne na matata. Ynxun
haka ina gidan uwarta ta hanani matata, don haka
zanzo mu shigar da qara. Daga can sukaji muryar
barista yace, qarar kisan kai zamu shigar, tunda basu
da mutunci. Ina ga ko dan gidan da suka mallaka, sai
sun daida ba tare da kuma sun kare kansu ba. Don
haka kar ka damu. Alhaji yace, shikenan nagode. Ya
kalli inna yayi murmushin mugunta, sai mun hadu a
kotu. Iroro ya sheqe da dariya. Dana sani tanata
bibiyarki. Har sun juya tace, Alhaji ya tsaya. Sannan
ya waiwayo.
Lafiya? Tace, bari in turo ta ku tafi. Kudin mutane
dana aro kuma idan nayi maka Allah ya isa fa? Tare
suka sheqe da dariya, Iroro da Alhaji. Iroro yace,
shegiya wuya! Alhaji yace, inna ai dama Allah
ishasshe ne. Cikin jin haushi, inna tace, ni ba innarka
bace don na tabbata ni kaina ka girmeni. Ta juya
cikin takaici, suna tayi mata dariya. Zainabu tana
kuka, tana komai, ta fito tabi Alhaji, tabar innarta
cikin takaici. Wani qarin abin haushi a lokacin suna
isa gida, saida yayi buqatarsa ya fita, ya barta tana
kuka.
Kishiyoyin suka shigo sunayi mata sannu tare da bata
haqurin rashin zuwansu. Ko kawo mata abinci sunce
Alhaji ne ya hana. Haka Zainabu taci gaba da
Rayuwar gidan Alhaji mai cike da matsi da takura,
gami da wahala, duk ta qara kodewa, ta fige ta lalace.
Kuma ya hana innarta zuwa, kamar yadda itama
yace ta daina zuwa gidansu. Innar Zainabu tasha
kuka tare da takaici da kuma da na sanin hada
Zainabu da Alhaji lawal.
Alhaji bashir ya dauki wayarsa ya soma neman layin
Abba. A ringing na biyu Abba ya dauka, ya kara a
kunne yana fadin dad ina kwana? Bayan sun gaisa
Alhajin yace, inason kazo yau ka tafi dani katsina.
Abba yace, amma lfy dai ko dad? Alhaji yace, lfy lau,
inason ganin mahaifiyarku ne, gashi har ynxun bana
jin dadin jikina. Abba yace, shikenan daddy, sai nazo.
Qarfe biyu Abba ya sauka garin Abuja. Tuni daddy ya
turo direba yana jiransa. Suka nufi maitama. Momy
Nafisa batasan da batun ba, saidai taga Abba. Ya
gaisheta tare da tambayar jikin daddyn, tace da
sauqi. Lokacin data shiga don sanarda Alhajin zuwan
Abba, sai yace ta hada masa wasu kayansa na ciki da
kuma wasu takardunsa. Tace, ina zaka Alhaji? Yace
katsina, nine nace wa Abba yazo ya tafi dani. Tace, ba
zaka bari kadan qara samun sauqi ba? Yace, karki
damu, can ma zanci gaba da ganin likita.
Shida daidai suka sauka a filin jirgin sama. Sun samu
direba na jiransu, domin kafin su taso daga Abuja,
Alhaji yasa Abba ya kira direban hajiya sauda,
batasan da zuwan Alhajin ba tana zaune a falo tana
ba Zainab magani, don yau kwananta uku babu lfy,
kullum suna hanyar asibiti. Sai kurum taji Sallamar
su. Bata zaci Alhaji bane, don muryar Abba irin ta
Alhajin ce. Saida taji yaran suna Oyoyo daddy. Da
sauri dago tace, sannu da zuwa Alhaji. Ta miqe cikin
sauri bayan ta kwantar da Zainab, tace, Alhaji baka
sanar dani cewa kana tafe ba. Yace karki damu tu
tunda mun iso lfy. Sun gaisa da Abba sannan ya nufi
gidansa.
Hajiya kuwa ta dauki jakarsa kuma ya bita zuwa daki.
Sannan ta dawo kusa dashi. Ya kamata kayi wanka
ko? Ya kalleta, zan yi wankannan kuwa? Barci nakeji
kuma inajin sanyi, sai inga kamar in nayi wankannan
zazza6i zai iya rufeni. Ta cire masa riga, sai singileti.
Ya kwanta akan gado, ta zauna bakin gadon. Kasha
magungunan ka kuwa? Yace, nasha, sai dai akwai na
ynxun qarfe shida, amma sai zan kwanta sannan zan
sha. Tace, a’a nidai kasha ynxun, yana da kyau kabi
dokar likita.
Ynxun tashi zakayi in taimaka maka kayi wanka,
kasha magani kayi sallah don kaga magriba ta kusa.
Ya tsura mata ido, “sauda nayi miki laifi ko? Ta kama
hannunsa, ni baka min laifi ba, to muje kayi? Yace, to
sauda muje. Kafin yayi sallah har ta shiga kicin da
kanta tayi masa tuwon alkama miyar alayyaho. Yana
zaune kan sallayarsa yana istigfari. Can qasan
zuciyarsa kuwa tunanin mimi takeyi.
Zuwa ynxun ya gama tabbatar ma kansa cewa, son
da yake wa mimi ya zarta tunaninsa, kuma ba zai
ta6a son wani cikin ‘ya’yansa kamarta ba. Amma dole
ya jure sbd ya samu ya ida nufinsa don ta samu
canjin rayuwa. Wasu hawaye suka soma zubo masa.
Sam baiji Sallamar Hajiya sauda ba, har saida ta dafa
shi, sannan ta tsugunna tare da aje abincin dake
hannunta dayan. Duk da saurin da yayi ya share
hawayen sa, saida tace “na shiga ukuna! Alhaji kukan
me kkyi? Cikin sarqaqqiyar murya yace, ba kuka
nake ba. Sauda ta zauna dirshan akan sallayar, cikin
tashin hankali tace, haba Alhaji. Shekarunmu nawa
ban ta6a ganin hawayen ka ba sai yau.
Dole akwai wani babban al’amari. Ta kama
hannunsa. “Na roqeka karka 6oyemin komai.
Idanunta suka cika da hawaye yadan matsa
hannunta, “sauda karki tada hankalinki ba wani abu
bane. Sannan inason don Allah ki yafe min nasan
cewa, na