Showing 15001 words to 18000 words out of 94417 words

Chapter 6 - Garkuwa Book 2

11 Oct 2024

3627

ɗan kwalinta.

Turarenta mai ƙamshi ta fesa.
Kana ta ninke kayan data ciren.
Da sauri Hibba da yanzu ta shigo ta amshisu tace.
"Yauwa bari in kai a wonkesu agoge kadama su tarun miki."
"To". tace, kana ta maida marfin jakarta ta rufe.
Safiyyah na fitowa ta kimtsa itama nan suka zauna suna hira har dai aka kira sallan magriba.
Bayan anyi magriba anyi ishane.
Duk suka fito babban falon.
Sai Umaymah dake can cikin ƙawayenta da matan abokan Abbansu HAROON.

ita kuwa Aunty Hafsat ta Tara zuriyarsu kab sunata hira.

Suna tsara tafiyarsu da za'ayi gobe jumma'a da hantsi, zuwa Leddi julɓe.
Da yamma ayi kamu jibi a asabar ɗaura aure da hantsi sannan su dawo da amarya da daren ranar kuwa ayi walimar washe gari Lahadi kuma ranar wuni ce ayi fansan ido da yamma, da dare kuma ayi shagalin mother's day.
Duk yadda sukaso ayi bidi'a da yawa, Sheykh ya karya musu logo daya samu Ibrahim da Abbansu Haroon da kawunshi Baban Aunty Juwairiyya dasu Ibrahim da amarya Jannart ɗin.
Ya dai tsara yadda yaga dama a bikin.
Haroon kamar ya rinka ihu.
In ya kufula sai Sheykh ya koma gefe yana kallonsa yana taɓe mishi baki.

Shi da Ibrahim dama su sunce sai jibi zasuje asabar zasu sammaka da tawagarsu zuwa ɗaurin aure da ɗaukan amarya.

Washe gari ranar Jumma'a da hantsi jirginsu Safiyya, Hibba, Aysha, Azeema, Aunty Kubra, da wasu ƙawayen Umaymah da ƙannen baban Haroon jirgisun ya isa birnin Jalaluddin.

Sheykh kuwa shi tunda sukazo idonshi ma bai sake ganin Aysha, duk da tana ɗan faɗo mishi a rai lokaci zuwa lokaci sai dai baya bin ta kanta.

Dan hidimomin sun sha kansu.

Suna isa masarautar Jalaluddin.
Kai tsaye suka wuce Side ɗin kakarsu.
Sitti kenan wacce taketa dakon zuwansu dan ganin Aysha matar jikanta mafi soyuwa a ranta.

Suna Shuga babban falonta Safiyya ta fara kiranta.
"Sitti! Sitti!! Sittin Jadda ko dai kina can wurin tsohon zumanki ne".
Dariya tayi ganin Sitti ta fito da sauri.
hannu ta buɗe wa Aysha irin dai al'adar su ta larabawa.
Cike daso tace.
"Iye masha ALLAH Jazlaan ya samu kekyawar mace mai nagarta".
A kunyace fuska ɗauke da murmushi Aysha ta isa jikinta.
Ruggume ta tayi tare da cewa.
"Sannu da zuwa masarautar julɓe, jikata".

Cikin sakin jiki da ita Aysha tace.
"Yauwa Sitti na sameku lfy?".
Alhamdulillah tace.
Tana kallon tsohuwar da kyau tana gani wasu kamannin Ummey a fuskarta.
Jansu tayi har cikin Bedroom ɗin ta.
Duk jikokinta ne.

Safiyya ce ta zaro wayarta ta kira Aunty Rahama tace mata sun isofa.

Aunty Rahma kuwa dake tsuma Jannart da kayan gyara na al'farma Juwairiyya da Jazrah da Saddiƙa na gefenta.
Da sauri tace.
"Gani nan zuwa yanzu kuwa, Safiyya".

Tana katse kiran tace.
"Muje Side ɗin Sittiina.
Su Safiyyah sun iso."

A tare suka miƙa suka nufi ƙofar Sitti.

Tafiyar a kwai yar tazara tsakaninsu.


A can Side ɗin Sitti kuwa, Bayan sun zauna Sitti tasa hadimanta sun kawo musu abin ci dana sha.
Sunaci suna hira.

Ita kuwa Aysha Ishma ƴar Aunty Rahma dake bacci kan gadon Sitti ta zubawa ido.
Duk da bata ganin fuskar yarinyar gaba ɗaya amman ta hango wani irin masifeffen kama da takeyi mata da Junainah.
Shiyasa gaba ɗaya hankalinta na kan yarinyar.

Hibba ce ta ɗan kalleta tare da cewa.
"Aunty Aysha kici mana, kin tsaya kallon Ishma".
da sauri ta ɗan rusuna ta fara cin Couscous da miyar hanta da Sitti tayi musu da kanta.

Suna shigowa Aunty Rahma ta tsaya tana kallonsu cikin sakin fuska tace.
"To yau duk kamar takuma ta zama ɗaya ina surkar tawa".
Sitti ce ta kalleta cikin son yar autar tata tace.
"Gata nan a gabanki".
Ta ƙarashe mgnar tana nuna mata Aysha dake zaune tana fuskantar gado.
Ɗan juyowa Aysha tayi da murmushi a fuskarta.
Da sauri ta juyo gaba ɗayanta tana kallon Aunty Rahma cike da mamakin tsananin kamarta da Ummeynta, hatta muryarsu iri ɗaya.

Da sauri tayi ƙasa da kanta, jin ta zauna kusa da ita.
Cike da Muryar mamaki tace.
"Aunty Rahama ina kwana".
"Lfy lau Alhamdulillah my surka ya ɗana, Jazlaan".
"Alhamdulillah yana lfy". tace fuska a sake tare da alamun kunya da kuma al'hinin abin da take gani da ji na kamanceceniyar fuska da murya.
Sitti ce tayi dariya tare da cewa.
"Tab lallai kuwa da yana kusa da kinsha tsuka, kin san baya son kina ce masa ɗanki dan yace ya fiki".
Safiyya ce tace.
"Tab ai Hamma Jabeer baya son ace ta fishi, sai yace.
"Dan wata biyun ne wani abun".

Dariya dai sukayi ita kam Aysha.
Ta shiga ruɗani kamannin.
Ƴarinyar da aka kira da Ishma da Junainah sun bata mamaki, sai kuma ga kamannin da yafi bata tsoro ma yanzu kam ko murya da dariyar Ummey nata irin na Aunty Rahma ne.
Ya ilahi ya mujibadda'awati".
Ta faɗa cikin ranta.
Lokacin da Ishma ta taso zaune daga baccin da takeyi, har kamar zata faɗi.
Da sauri tasa hannu ta tare yar yarinyar da bazata gaza shekara biyar ba.
Da sauri ƴarinyar ta manna kanta a jikinta tare da cewa.
"Mommy zansha ruwa".
Da sauri ta sunkuyo kan yarinyar hannunta tasa ta dafa goshinta, cikin sanyi tace.
"To ga ruwan buɗe baki". Ta ƙareshe mgnar tare da ɗaukan bottle water mai ɗan sanyi dai-dai misali, tana buɗe marfinshi.
Juyowa Ishma tayi jin baƙuwar murya.

Cikin sauri ta kalli Azeema tare da cewa.
"Laa Aunty Azeema kalli Aunty Ayshan Hamma Jabeer tazo".
Tayi mgnar da alamun tasan Aysha a hoto.

Murmushi tayi tare da sa mata bakin gorar ruwan a baki.
Cikin mussuke ido ta buɗe baki ta fara shan ruwan.
Aunty Rahma kuwa, kallon Aysha take cike da ƙauna.
Aunty Juwairiyya ce ta ɗan kalli Aysha cikin yanayin da bazaka gane manufarshi ba tace.
"Sannuku da zuwa yau kam gaki a masarautarmu tushenmu, gaki ga Sitti kakarmu data haifi babana ta kuma haifi Mamansu Sheykh da Ya Jafar dasu Jamil jininmu ɗaya".
Ta ƙareshe mgnar cikin nuna kusanci da dangatakar dasu Sheykh na jinine.
Kai Aysha ta ɗan juyo ta kalleta,
murmushin gefen baki tayi,
dan ta gane manufar Aunty Juwairiyya tana nuna mata cewa su jini ɗaya ne, itace bare a tsakaninsu.
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
"Eh yau kam gani ga Sitti ga Aunty Rahma".
Ta ƙareshe mgnar tana wata mgnar a zuciyarta.
"Uhumm Aunty Juwairiyya kenan, ai dama saida ɗan gari akanci gari da yaƙi, kina matsayin yar uwarsu kuma kike cutar dasu, in da zasu sani da bazasu aminta da keba".
Muryar Ishma ce ta katse mata mgnar zuci da takeyi.
"Aunty Aysha ina Hamma Jabeer".
Kanta ta ɗan shafa tare da cewa.
"Yana Tsinako".
Da sauri tace.
"To shi bazai zo bane?".
Gyara zamanta tayi tare da cewa.
"Zai zo".
"Yaushe?". Ta kuma tambayarta a gajarce.
murmushi ta ɗan yi tare da cewa.
"In Sha Allah gobe zasu zo".
Allah ya kaimu ta tafaɗa tana wasa da jelan gashin Aysha dake bisa kafaɗarta.


Aunty Rahma ce ta ɗan harareta tare da cewa.
"Maza tashi a jikinta ki barta ta huta".
da sauri ta ɗan zame ta sauƙa ita kuwa.
Aysha kai ta ɗan karya tare da cewa.
"Aunty Rahma barta".
Safiyya ce tace.
"Ahyya baki san Ishma bane da shegen surutu da son jiki".
dariya sukayi ganin yadda Ishma ta zumbura baki.
Sitti ce ta miƙe tsaye tare da kallon jikokin nata da yar autar tata, tace.
"Toh maza ku tashi muyi sallan azahar, in mun idar ku isa wurin Jadda ku gaisa."
Kusan a tare suka mimmiƙe, Aunty Rahma ce ta kamo hannun Ishma tare da cewa.
"Jadda ya fita, ai ɗazu ya kirani yace in masa abincin dare, wai ya ɗan fita zai kai dare kafin ya dawo".
Dariya Sitti tayi tare da cewa.
"Uhumm kai Jadda wato ki masa abincin dare. In kun koma kuwa naga wa zai ce ta dafa mishi".
Safiyya ce tace.
"Oh zai ci girgikin yar autarsa".
Ita dai Ramatu murmushi tayi tare da cewa.
Aysha Juwairiyya Jazrah Safiyya mu tafi ɗakina".
To sukace kana suka bita a baya.
Har zasu fitane Sitti tace.
"A a Aysha dawo nan, ke kam baƙuwa tace ga masauƙinki".
Murmushi Aysha tayi kana ta juyo ta dawo sabida tafi gamsuwa da zama kusa da Sitti akan a tsakiyar Juwairiyya da Jazrah dake mata wani irin mayataccen kallo.


Haka dai sukayi sallan azahar,
kana suka fara shirin kamu.
Wanda tuni ango Haroon da tawagar abokanshi sun iso.

Anayin Sallan la'asar suka fara.

Sai gab da magriba suka tashi.
Ranar kusan kwanan zaunen sukayi anata hirar yan uwantaka.
Yayinda Aysha bata gajiya da jin muryar Aunty Ramatu da kallon fuskarta da fuskar Ishma.

Basu samu sun isa wurin Jadda ba.
Sun bari a akan sai gobe da safe in Allah ya kai rai.


A can Tsinako kuwa, gaba ɗaya al'ummar masarautar Tsinako da baƙi abokan Abbansu Haroon dana kakansu Sarki.
Da kuma baƙi na nesa dana kusa duk an kwana cikin shirin, tafiya ɗaurin auren.
Masu tafiya a jirgi ƙarfe tara jirginsu zai tashi.
Masu tafiya a motoci kuma sammako zasuyi.
Sabida sha ɗaya na safe za'a ɗaura auren.



Haka kuwa akayi washe gari da safe masarautar Jalaluddin, ta fara amsar baƙi tako wani saƙo na ƙasar Nigeria.


Fadar masarautar dama farfajiyar ta cika tayi tab da baƙi da ƴan gari, tako ina halarta mutane keyi.

Karfe sha ɗaya dai-dai na safe taron al'ummar musulmi suka shaida ɗaurin auren Haroon da Jannart.

Bayan an ɗan wawwatse mutane duk sun kama hanyar komawa inda suka fito.
Sai Abokan ango da zasu ɗauki ƙawayen Amarya da wasu yan uwa.
Dan amarya dasu Aunty Juwairiyya da Jazrah da Aunty Rahma Ishma da ƙannen mamansu Jannart duk sun tafi a jirgi, da ango.
Safiyyah da Aysha da Azeema da Hibba ne kaɗai suka rage.
Dan Safiyyah ce ta hana Aysha tafiya dasu Auntyr Rahma tace, ita tare zasu tafi.
Haka kuma Sitti ma tace haka yasa koda suke ribibin tafiya ita tana bacci a ɗakin Sitti bisa gadon mulkinta, dan kwanan da sukayi ba bacci yasa duk suna cike da bacci.

Ibrahim da Sheykh kuwa sune suka tsaya da wasu abokan Haroon biyu, sai sunga duk mai buƙatar zuwa ta tafi.


Ƙarfe sha biyu dai-dai Sheykh Jabeer da Ibrahim da Munnir da Mansur abokan Haroon Suka shigo babban falon Sitti.

A nan suka samu Jalal da ya Jafar da Ammar ƙanin Aunty Juwairiyya da Ibrahim wanda shine yayan Jannart.

Sai kuma Goggo Mairo ƙanwar Jadda da kuma sauran yaran Jadda wanda kishiyoyin Sitti suka haifa.

Safiyyah na ganin shigowarsu ta miƙe ta nufi Dinning area fridge ta buɗe ta haɗo musu ya'yan itatuwa masu sanyi, ta gyara kana ta kawo musu.

Bayan sun gaggaisa ne,
Ibrahim ya ɗan kalleta tare da cewa.
"Kun gama shiryawa ko?".
Kai ta gyaɗa mishi al'amar eh.
Sai ta kuma kalli Sheykh dake miƙawa Ya Jafar nonon inabi yana kuma ce mata.
"Sitti fa?".
jujjuya kai tayi cikin falon ta kalli gabas da yamma kudu da arewa.
Gane wai neman inda Sitti takene yasa Goggo Mairo cewa.
"Bata nan ai ta fita".
ɗan miƙewa tsaye tayi tare da cewa.
"Ikon Allah kuma fa da muna nan tare da ita. To ina tayi".
Aunty Salima wacce take itace Babba a yaran Jadda ne tace.
"Nima fa ita nake jira".
Jalal ne ya ɗan kurɓi ruwan sanyi tare da cewa.
"To ko tayi ciki ne".

"Ba mamaki". Goggo Mairo tace.

Cikin nitsuwa Sheykh ya miƙe tsaye, kekyawar al'kyabbar jikinshi ya ɗan buɗa tare da gyara zamanta jikinshi.
Corridor'n da zai sadashi da special Side ɗin Sitti ya nufa, a nitse.

A can bedroom ɗin Sitti kuwa.
Aysha ce tsaye gaban dreesing mirror bayan ta gama ado da kolliyar ta.
Wani dandatsetsen Shadda lace ne mai masifar kyau da taushi tare da sheƙi ne a jikinta, ɗinkin Doguwar rigace.
Ta zauna ɗas a jikinta gwanin burgewa da ban sha'awa.

Kalan kayan sun taimaka kwarai wurin burgewa, dark red wine mai masifar kyau, sai ratsin zare Royal blue mai azabar kyau da sheƙi da aka zubashi suffar zanen ɗawisu.

Turare ta feshe jikinta dashi,
kana ta maida kolbar sannan ta dawo gaban dreesing mirror kujerar ta jawo ta zauna.
Kasan cewar dreesing mirror babbane mai tudu hakama kujerar.
hannu tasa ta fara tsaɓule ribon ɗin da ta tubke himilin gashinta dashi.


A nitse ya iso bakin ƙofar Bedroom ɗin Sitti.
hannunshi yasa ya tura ƙofar,
ɗan wani guntun tsaki yaja tare da sa guiwar yatsunshi biyu ya ɗan ƙonƙosa kofar sau uku.
Kana ya ɗan tsaya gefe.

A hankali ta juyo kanta ta ɗan kalli bakin ƙofar,
har kamar bazata tashi ba.
Sai kuma ta tuna ta rufe ƙofar lokacin da Safiyya ta shigo ta tasheta kan ta tashi ta shirya su tafi.
To da zata shiga wonka ne ta rufe ƙofar dan tana jin kunya kada ta fito tana shiryawa wasu su shigo su sameta.

A hankali ta miƙa tare da juyawa ta nufi ƙofar tana ƙoƙarin warware ɗan kwalinta.

Isowarta bakin ƙofar yayi dai-dai da lokacin ɗaya kuma ɗan buga ƙofar.
Hakan yasa bata gama warware ɗan kwalinba tasa hannu ta buɗe ƙofar dan a zatonta Sitti ce ko Safiyyah.

Tana buɗe ƙofar sai ta ɗan koma da baya, haka yasa bata ganshi ba.
Bai ganta ba.

Kutsa kanshi yayi cikin ɗakin tare da sallama a bakinshi.
kana yasa hannunshi ya maida ƙofar.
Kasan cewar dreesing mirror yana fuskantar ƙofar shigowan ne, yasa. Mutun zai iya ganin abinda ke bayansa muddin yana kallon cikin madubin.

Kanshi a sunkuye da alamu wayarshi yake ɗan lallatsawa.

Haka yasa hankalinshi baya kan madubi.

Ita kuwa Aysha, wani irin sassanyan numfashi ta sauƙe a hankali jin daddaɗan ƙamshin turaren jikinshi.

A hankali ta zubawa bayanshi idanu tun daga kan dudduniyar farar kekyawar ƙafarshi, har zuwa kan tattausan suman dake kwance lib a ƙeyanshi.
Kasan cewar da yasa hiramin yau yayi irin siririn sakun nanne ya tattare gefe da gefen hiramin.

Taku uku yayi ana huɗu ya tsaya cak, ba tare da ya ɗago kanshi ba ko ya juyoba, yace.
"Wannan kallon fa?".
Cikin tsananin mamaki da tsoron al'amarin Sheykh tayi saurin yin ƙasa da kanta.

Shi kuwa Sheykh a hankali ya ɗago kanshi, ya dire idanunshi kan faffaɗan mafubin daya hasko mishi ita ras a ciki.

Shigarta surarta yanayin tsayuwarta da yadda take wasa da yatsun hannunta da kuma sumanta dake zube a kafaɗunta sunyi masifar jirkita mishi jiki da jini da kwanya.

Tabbas jikinshi ne ya sanar mishi ana kallonshi.
Shiyasa yace.
"Wannan kallon fa?".
A zatonshi ma Aunty Rahma ce, ko Sitti dan yasan sun iya tsura mishi ido duk da sun san baya son kallo a rayuwarsa.

Ita kuwa Aysha, Koda tayi ƙasa da kanta digadigin sawunshi ta zubawa ido.

Shi kuwa Sheykh a hankali yaja wani nannauyan numfashi ya sauƙe a hankali.

A hankali ya ɗan juyo fuskarshi ya haɗe tare da cewa.
"Ke da izinin waye kika baro Tsinako kika zo nan?".

A hankali ta ɗan ɗago kanta, kana ta ɗan turo baki,
sannan ta gyara tsuyawarta, tare da cewa.
"Cemin akayi in zo".
Ta ƙareshe mgnar da yin taku biyu zuwa na uku da nufin zata koma gaban dreesing mirror ta ƙarisa shirinta.

Tana isowa gab dashi, da nufin zata wuce da sauri ta rumtse idanunta.
jin ya...




Littafin GARKUWA na kuɗine Special Group 1k a mako biyi huɗu ake gama Part one da two. Normal group Kuma 300 a mako takwas za'a gama Part one da two. Idan kina buƙatar special Group kimin TRANSFER ɗin 1k ta asusuna na Jaiz bank 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. Sai kiyi screenshort na shaidar biyanki ki turo min ta wannan number da nakeyin whatsApp da ita 09097853276. In kuma Normal group kikeso na ɗari ukun, shima kiyi min TRANSFER ta ASUSUNA na Jaiz din in baki da halin turowa ta banki to ki sayi katin Mtn na ɗari uku ki copy numbers ɗin ki turo min ta WhatsApp 09097853276. BANA SON VTU KADA KIYI MIN TRANSFER'N DIN KATI BANA SO.


By
*GARKUWAR FULANI*
3/23/21, 5:06 PM - ": Yasa ƙafarshi ya ɗan taɗe mata ƙafa.
Da sauri ta rumtse idanunta tare dasa hannunta ta kamo nashi ta riƙe gam.
Haka yasa bata ida faɗuwar da ta kusa yiba.

Shi kuwa Sheykh fuskarshi ya tsuke tare da sa hannunshi ɗaya ya ɓamɓare hannunta dake ƙamƙame da nashi, kana ya ɗan ture ta.
Da sauri ta kuma riƙo hannunshi jin tayi gefe zata faɗi.
Wani irin ɗan ihun tsoro tasa, jin ta tafi shi kuma ya biyota,
da sauri ta rumtse idanunta jira kawai takeyi taji kanta ya raɗu da ƙasa, sabida tsoro yasa tama mance ta gefen gado take.
Jin ta faɗa kan tattausan katifar gadon Sittine yasa tayi wani irin dogon ajiyan zuciya.
Sai kuma ta buɗe idonta da sauri jin ya faɗo jikinta.
Da sauri ta kuma maida idon ta rufe ganin yadda sukeda kusanci.
Fuskarshi na kan fuskarta, hancinshi na gogan mata gemunshi na bisa haɓarta, goshinsa na kan nata, hakan yasa data buɗe idon nata sukayi kiciɓis da nashi idanun masu kwarjini.
Cikin jan numfashin tace.
"Wayyo Allah na nauyi ƙirjina zai fashe,
Babba da kai zaka fasamin ƙirji".
Ido ya zubawa lips ɗinta yana ganin yadda take motsasu, sai sheƙi sukeyi.
Haka nan yaji yana kusanto da bakinshi ga nata,
da sauri kuma ya maida kanshi tsakankanin wuyanta da kafaɗarta, ya cusa hancinshi cikin tattausan suman kanta da ya baje a kafaɗun nata,
wani irin sassanyan numfashi ya zuƙa tare da ƙamshin gashin kanta da jikinta,
wani irin Yar-yar yaji tsikar jikinshi na zubawa suna miƙewa tsaye.
hannunshi ya cusa tsakanin bayanta da katifar, ya ruggumeta gam-gam a jikinshi.

Shiru tayi tana jin yadda yaketa sunsunar wuyanta yana ƙara matseta tare dasa harshensa yana ɗan lasar fatan wuyan nata.
Tattausan sajenshi na gogar haɓarta, haka yasa tsikar jikinta zubawa.

A hankali ta buɗe idonta ta zubasu kan sajen nashi dake kwance lib-lib tamkar ciyawar dake samun yabanyar safe da yamma.
sai sheƙi yakeyi da ƙamshi,
da sauri ta ɗan maƙe kafaɗarta jin yadda ya manna hancinsa da bakinshi ya manna mata wani irin sihirtaccen kiss mai masifar ratsa jiki da zuciya.
Sosai take jin nauyinshi sabida duk jikinshi ya sake gaba ɗaya nauyinshi ya sakarmata.
Haka yasa tasa tattausan tafin hannunta ta tallabe gefe da gefen fuskarshi cikin jan numfashin tace.
"Ƙirjina kayi nauyi na tuba sauƙa".

Ƙara matseta yayi a jikinshi kana ya maida bakinshi cikin kunnenta cikin dafeffiyar murya yace.
"Waya ce ki jawoni jikin naki?
Kuma da izinin waya kika baro Tsinako kika zo nan?".
Cikin fidda nishi tace.
"Ni ba jawoka nayiba na riƙeka ne dan kar in faɗi.
Zuwa nan kuma ai Umaymah ce tace inzo".
ƙara manna ƙirjinshi da nata yayi sannan yace.
"Na'am wato Umaymah ce Allah yace kada ki fita in ba izinin ta?".
Cikin cinna ɗan bakinta sama tace.
"To ba Mamanka bace".
kanshi ya maido ya haɗe fuskarshi da tata, on expected taji yasa bakinshi kan nata.
Lips ɗin ta na ƙasa ya kama da fararen haƙoranshi na gaba ya ɗan ciza ka ɗan.
da sauri tayi zillo tare da buɗe bakinta zatayi ihu, hakan ya bashi damar lalumar tattausan harshenta yayi mata wani irin masifeffen tsotsa mai gigitarwa.

Ta kasa gane a zahirine ko a mafarki, wani irin kiss yake mata mai masifar ratsa jiki da zuciya.
Tana gaza nazari ko tunanin gane Sheykh wanne iriyar halittace

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login