Showing 39001 words to 42000 words out of 94417 words
tafi.
Ummi kuwa da Jamil suka zauna a falo.
Ita kuwa Aysha bedroom ɗinta ta, shiga.
Bathroom ta shige sabida, wani shegen fitinenne fitsarin da takeji.
Bisa toilet ɗin ta zauna tare da lumshe idanunta, sabida jin daɗin juye nauyin mararta da takeyi.
Bayan ta gamane, tayi amfani ruwan ɗumi.
Sai kuma ta kwabe dan zafin da takeji tace bari ta ɗan watsa ruwan sanyi lumshe idonta tayi lokacin da ruwan sanyin ya sauƙo jikinta, kana dai-dai lokacin ta tuno mafarkin da tayi da safiyar yau, da sauri ta rumtse idanunta gam sabida a fili take ganin yadda Sheykh yayi ta murzata a mafarkin da kuma irin kukan da tayi sabida azabar da ya azabar da ita da sauri ta ware idon da kyau sabida sai takega kamar zai shigo yanzune ya ritsa da ita haka yasa taci gaba da wonkon da sauri-sauri.
Cikin tsananin isa da izza da tsaurin ido, take taku har zuwa tsakiyar falon kana hadimanta na Binta a baya.
Tsakiyar falon ta tsaya tare da watsawa Ummi da Jamil ido dogon tsaki taja tare da cewa.
"Ina yake ɗan masu fiffigen!?".
Da sauri Jamil ya miƙa tsaye tare da watsa mata wani irin mugun kallo mai cike da tsana yace.
"Baya buƙatar ganin irinku da ko sallama baku iyaba".
Cikin tsawa da ɗaga murya tace.
"Rufe min baki ƙaramin kwaro, ka bari inyi da shi jan wuyan naku".
Da sauri Sheykh ya miƙe tsaye jiyo muryar Gimbiya Saudatu a tsakiyar falonshi.
Affan ma miƙewa yayi da sauri kana yabi bayan Sheykh daya nufi falon da sassarfa.
Yana fitowa Gimbiya Saudatu ta gyara tsayuwarta tare da buɗe al'kyabbar jikinta kana tace.
"Yauwa al'huda-huda sarkin karatu.
Zo nan zo ka gayawa wannan ɗan tayin ƙanin naka cewa.
Duk lalacin mutun ya iya sallama amman banda tsuntsaye su sai dai su gani anayi, gwarama tsuntsun da ba zunibi ne ya maidashi tsuntsuwar ba dama haka Allah ya halicc...".
Cikin wani irin tsananin tafasan zuciya da tuƙuki da ciwo a rai.
Sheykh yayi mata wani razanenne tsawan da saida tayi tsalle ta koma baya kaɗan.
Tsawar daya danna matane yasa Aysha fito da sauri tana mai gyara ɗaurin ɗan kwalin doguwar abayar da tasa yanzu.
Cikin rawan jiki yake taku har gabanta.
Ummi da Affan da Jamil kansu jikinsu kerma yakeyi.
Jalal dake Side ɗin su ma yajiyo sautin muryarsa hakane yasa ya nufo falon da sauri.
Cikin azabar fushi ya nunata da ƴar yatsarshi manuniya murya na rawa yace.
"Duk tsuntsuwar da kika gani Allah yasan da zamanta, ki kuma sanni wannan tsuntsuwar ta fiki daraja har gaban Allah".
Cikin jajir cewa da ƙarfin hali ta ɗan ja da baya tare da cewa.
"Eh lallai kam ta fini har gaban Allah mana tunda girman zunubanta da jafa'inta yasa Allah ya nuna mana ikonsa da aya a kanta ya sauya mata halitta daga mutun zuwa tsu..".
Wani irin zabura Ummi, Affan, Jamil, da hadiman Gimbiya Saudatu
Sukayi sabida wani irin azabebben ihu da ta kurma da karfi sabida wasu irin gigitattun tagwayen maruka da Sheykh ya yarfa mata da hannunshi.
Wanda sukayi nasarar tafiya da jinta da ganinta.
Kanta ya sake nufa da azama alamun zai tabketa da iyakar iyawarsa
Cikin rawan jiki Ummi tace.
"Sheykh kayi haƙuri barta kasan hannunka".
Ina wani marin ya kuma yarfa mata wanda saida taji wani fitsari ya tsarto mata.
Ihun data kurma yayi dai-dai da kife kanta da tayi da jikin kujera.
Cikin wani irin azama da sauri haɗi da kiɗima Aysha tayi sauri ta nufi gaban Sheykh sabida ganin baya cikin hayyacina.
Affan da Jamil da sukayi nufin riƙeshi ne ya yarfawa maruka wanda yasa suka ja da baya.
Cikin azama tasha gabanshi tare dasa hannunta ta riƙo hannunshi da ya ɗago zai mari Gimbiya Saudatu, cikin azaban fushi ya juyo ya kalleta da rinannun idanunshi.
Da sauri ta kuma ƙara riƙe hannunshi tare da matsoshi kana murya na rawa tace.
"Yan Sheykh! Kayi haƙuri".
Fusge hannunshi yayi da ƙarfi ya nufi kan Gimbiya Saudatu domin idonshi ya rufe rib baya ji baya gani kamar yadda itama Gimbiya Saudatu idonta da kunnenta suka dena aiki kana fitsari ke tsiyayo mata.
Da sauri Aysha ta kuma shan gabansa, kawai sai ta faɗa jikinshi ta ruggumeshi gam-gam a jikinta,
cikin rauni take cewa.
"Yah Sheykh ka bari, kada ka kulata Please Yah Sheykhhhh kada ka sake barin hannunka mai daraja da kullum yake cikin taɓa al'ƙur'ani mai girma ya taɓa fuskarta kada ka bari fuskarta ta samu darajar da hannunka zai taɓata.
Kar-kar haka jikinshi ke rawa da tsuma tamkar mazari, yana mai jiyo amon sautin muryar Aeech cikin kunnuwansu.
Ita kuwa Aysha a hankali tasa tafin hannunta ta tallabe gefe da gefen fuskarshi ta karkatoshi gareta, cikin sanyi da tattausan lafazi tace.
"Mai hankali keyin mgn ya dami mutane ba, majanuniya irinta ba. Bata da ma dafa, ita fa bushiyace mai baya kamar allurai, Please kada idonka ya sauƙa a kanta".
Ta ƙare mgnar tana jan hannun sa na dama tana ja ta nufi Side ɗinsa.
Cike da mamaki Ummi, Affan, Jalal, Jamil, Hadiman Gimbiya Saudatu suka bisu da ido ganin ya bita a baya, tuni ta sarrafa fushinsa.
Ita kuwa Gimbiya Saudatu har yanzu lalube takeyi wanda yasa Affan da Jamil murmusawa dan sai tafi kyau da makanta.
Ita kuwa Aysha Kai tsaye har bedroom nashi ta wuce riƙe da hannunshi suna shiga ta faɗa jikinshi.
Wani irin rumtse idanunshi yayi da azaban ƙarfi tare da ruggumeta tsam a j...!
Littafin GARKUWA na kuɗine Special Group 1k Normal group 300 zaku turo ta asusuna na Jaiz bank 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. Sai kiyi screenshort na shaidar biyanki ki turo min ta whatsapp 09097853276.
Bana son VTU in kinyima ni ba ruwana. In ya kama dole ma baki da damar tura kuɗin ta Account ɗina to katin mtn zaki saya ki copy numbers ɗin ki turo min ta whatsapp 09097853276.
Gareku *Murmushi group* ngd da halaccin ku, zumuncin kenan.
By
*GARKUWAR FULANI*
3/23/21, 5:06 PM - ": A jikinshi, ya matseta da ƙarfi, sabida tsananin fushin da yake ciki da tafasar da zuciyarsa keyi, ji yakeyi tamkar ya matseta ya medata cikin jikinshi kanta ya danni zuciyarsa ko zaiji sassaucin.
Ƙuna da ƙuncin da kalaman da Gimbiya Saudatu ke jifarshi dashi da mahaifiyasa dasu.
Haƙiƙa ita kaɗaice mutun da ta samu nasarar gano abinda ke ta'azzara fushinsa har ya kasa control ɗin kanshi ta tunzurashi.
Wani irin wahaltaccen numfashi Aysha ta fesar a hankali sabida jin wani fitinenne rugguma da yayi mata tamkar zai gamesu ya cure jikinsu wuri ɗaya.
Gaba ɗaya jikinshi rawa da kerma yakeyi tamkar mazari.
Cikin fizgo numfashin ta kwantar da kanta bisa ƙirjinshi dai-dai kan ƙahon zuciyarsa,
Kana tasa hannun ta saƙalo wuyanshi, ta ware yatsunta manya tana yin sama da ƙasa dasu a kan tattausan sajensa
Cikin sanyi tare da muryar kwantar da hankali tace.
"Indai har ikon Allah kan iya yaye duhun dare da hasken rana ya meye gurbindun.
To tabbas yaye baƙin ciki i zuwa farin ciki a zuciyar bawansa al'amarine mai sauƙin gaske.
Abin sani kawai shine su mumanai girman jarrabawa ko ƙalubalen rayuwa baya sasu fidda tsammanin samun rahamar ubangijin taliƙai."
Murza kanta ta kumayi bisa ƙirjinsa sabida tanajin wuya da zafin ruggumar da ya mata cike da fushi.
Cikin sassanyan murya tace.
"A shawarce kayi ƙoƙarin jagorantar zuciyarka, kayi baya da lamuran kowa ka ruggumi naka.
Sabida kana zagaye da Magauta makusanta yau da gobe ita ce zata ganar da kai abubuwa da yawa, ka fuskanci magautanka ka dena dukan dungu."
Mutsu-mutsu ta farayi a jikinshi sabida kalamanta na ratsashi kuma suna sashi zafafa ruggumar da yayi mata. Koda yake hakan baya rasa nasaba da hautsunewar kwanyarsa a kan kalamanta.
Cikin ɗan buɗa murya taci gaba da cewa.
"Kafin ka yarda da mutane to ka rinƙa morar Kekkyawar ƙwaƙwalwarka mai tarin basira da nazartarsu, ka dena yarda da mutun a bisa fuskarshi ta zahiriya.
Kafin ka buɗe musu zuciyarka ba basu kekkyawan mazauni na mutane masu amana.
Da yawan mutane dake da kaifin basira da iya tsara zance, har su sanyaya zuciyar mutun su sa mishi yardarsu a ransa.
Da idan zaka shiga zukatansu zaka samu dafin guban dake zuƙatansu yafi na baƙin kumurci.
Yah Sheykh kada ka damu da sauyin ɗan Adam tunda dama shi halittace mai rauni kan rikon amana da halaccin.
Har kullum ka jingina da kanka, duk wanda ya nuna zai zamto tsanine a gareka, koma yake ganin shine tsaninka, nuna mishi tun kafin zuwasa gareka.
A tsaye kake da ƙafafunka.
Ta hakane zai san ƙaucewarsa bata nufin faɗuwarka."
Ɗan tsagaitawa tayi ta ɗago kanta, ta kalleshi sabida jin yadda tattausan gemunshi ke shafa goshinta.
Lip ɗinshi na ƙasa ya taune tare da girgiza gemun.
Ya kuma rumtse idanunshi sai dai yanzu ya ɗan fara sassauta ruggumar da yayi mata.
A hankali taci gaba da cewa.
"Gimbiya Saudatu fa, ba belbela bace, Yah Sheykh ka nazarci kalamai na, ita bushiyace ko ince kunkuru.
Zanfi son ka ɗauki zancenta dana mai taɓun hankali a ma'auni ɗaya.
Ni dai ban san menene tsakaninku ba, sabida bani da damar sanin komai naka, da ace na sani da ni zanji da ita, sai dai batun gsky ka dena yankewa littafi hukunci a bisa bongon bayanshi, ka buɗe littafi ka nazarceshi shafi zuwa shafi kafin ka yanke wa littafin hukunci".
A hankali ya buɗe idanunshi.
Ya zuba matasu, tabbas yaji wani abu ya ɗarsun masa a zuciya, da zai samu yanzu duk suturan jikinta zai kekketashi ko zaiji sassaucin abinda yakeji.
A hankali ya saketa.
Kana ya zauna a bakin gado,
Kanshi ya dafe da hannunsa duka biyu.
Still har yanzu jikinshi kerma yakeyi.
Ita kuwa Aysha juyawa tayi da sauri ta nufi falon, da nufin ta ɗauko mishi ruwan sanyi yasha ko zaiji sassaucin abinda yakeji a ransa.
Ba ruwa Fridge ɗin nasa.
Hakane yasa kai tsaye ta wuce babban falon.
A can falon kuwa Affan da Jamil, sai dariya sukeyi ganin yadda har yanzu Gimbiya Saudatu taketa lalube a inda ta faɗi kasa dirsham.
Tuni fuskarta ta haye ta kumbura tayi sintim.
Hakama bakinta.
A hankali ta fara bude idanunta, sai ta kuma rufesu.
Ummi ce tayi murmushi mai cike da jin daɗin marukan da Sheykh ya yayyarfa mata.
Cikin dakiya ta kalli hadiman Gimbiya Saudatu dake gefe suna murmushi suma tace.
"Ku matso kuyi mata jagora".
Da sauri Gimbiya Saudatu ta gyara zamanta tare da buɗe jajayen idanun nata, cikin masifewar murya tace.
"Ke tafi daga nan Jakadiya mara galihu".
Da sauri suka juyo suka kalli inda Aysha ke tsaye wacce ta nuna Gimbiya Saudatu hanyar fita tare da cewa.
"Ki ɓace min daga nan, sabida mijina bazai juri jin ihun haukanki ba".
Wani mugun kallo ta watsawa Aysha da jajayen idanunta kana tace.
"To fitsarerriyar ƙauye, mai gaggawar tsiri da cewa miji Baba, waya kasa dake bare ki zari babban kashi".
Jalal ne ya ƙaraso cikin falon, sabida yana son yaga matakin da Aysha zata ɗauka tunda ta iya fesa Hajia Mamansu ma rashin kunya.
Ummi, Jamil, Affan, suma gyara zama sukayi.
Ya Jafar da yanzu ya shigo ma gefen Jalal ya zaune.
Ita kuwa Aysha cikin isa da ƙasaita ta iso gaban Gimbiya Saudatu kujerar dake gabantan ta zauna a kai wacce kujerar zaman Sheykh ne. Kai ta jinjina tare da cewa.
"Ƙauye tushen kowa! Duk wanda bashi da ƙauye to bashi da asali kenan, shin baki san cewa da ƙauye akanyi birni ba.
Shin ke kinma san me ƙalmar ƙauye take nufi kuwa?".
Ƙafarta ɗaya ta ɗaura kan ɗaya, kana taci gaba da cewa.
"Da fari Makka itace babban birni sabida Annabi Sallallahu alaihi Wasallama yana cikinta.
Da yayi hijira ya koma madina kuwa sa madina ta zama babban birni mai cike da salama sabida addinin da kanshi ya koma can.
In kin gane me ƙalmar ƙauye take nufi garin da babu addini ba ilimi garinda kafurai suke, shine ƙauye, domin duk inda hasken addini yake da ilimin da masana ilimin to sun zarta ace musu ƙauyawa, domin kalmar ƙauyawa tana nufin jahilai, niko nan da kike ganina gidanmu tushene na tsanƙaya yara da dattawa.
Dan haka janye kalmarki ta fitsarerriyar ƙauye, gorinki bai samu muhalliba."
Tsaki taja tare da cewa.
"Baki san cewa kunne ya girmi kaka ba ko? To inma baki saniba Ni nan Aysha ina sane da labarin ƙuruciyarki da rashin kunyar da fitsarar da kikayi da taraddadin da kika sawa iyayenki na alamun lalacewa, dan haka kece fitsarerriyar. Kana kuma in kin mance in tuna miki ƙauyenmu ya zarta asalin naku ƙauyen girma da daraja ko dai kin mance inane asalin ƙauyenku.
In kin mance in tuna miki, ita kanta masarautar Joɗa kafin a auroki cikinta zata amsa kiran suna ƙauyen da hausawan ke nufi.
Yau da gobe shike sauya komi da kowa.
Ni nan da kike gani da mgnarki data ɗaurerre a turu basu da maraba."
Cikin masifa Gimbiya Saudatu tace.
"Sai dai in kece mahaukaciyar".
Dariya tayi tare da cewa.
"A a akan bola nake".
Miƙewa tsaye Gimbiya Saudatu tayi tare da fara gyara al'kyabbar jikinta, tare da cewa.
"Zanyi mgninku zaku gane kurenku".
Taɓe baki Aysha tayi.
Ita kuwa juyawa tayi ta, fice hadimanta na biye da ita a baya.
Dariya sosai Ya Jafar yayi wacce saida ta basu mamaki.
Sheykh kuwa da tun ɗazu ya fito bayan yayi al'wala ganin azahar tayi,
Tsayuwa yayi yana jin yadda Aysha keyi da Gimbiya Saudatu.
Ita kuwa Gimbiya Saudatu ganinshi ne yasa ta miƙe maza ta fice.
Miƙewa Aysha tayi da sauri jin muryar sa yana cewa.
"Ku tashi kuje kuyi al'wala lokacin salla yayi".
Juyowa tayi ta zuba mishi ido.
Tabbas daga jin muryarsa da yanayin fuskarsa zai iya nunawa mutun cewa har yanzu a zuciye yake.
Kallonta yayi a fizge kana yaja idonshi yayi gaba su Affan na biye dashi a baya.
Murmushi Ummi tayi tare da cewa.
"Dai-dai kenan yau dai Sheykh ya sawa Gimbiya Saudatu tsoron zuwa nan ta baje kolin rashin kunyar ta."
Juyowa tayi ta kalli Ummi tare da cewa.
"Uhummm Ummi an dukan tenki akefa aka bar jaki a ɗaure"
Cikin sauri Ummi tace.
"Kamar yaya?".
Kai ta jinjina kana tace.
"Muje muyi salla, Ummi".
To tace tana mai son nazartan kalaman Aysha.
Bayan sunyi salla ne suka fito falon.
Suna zama Sheykh Jabeer ya shigo.
Affan, Jalal, Jamil, Ya Jafar. Na biye dashi a baya.
Su duk Dinning table suka nufa.
Ummi na biye dasu a baya.
Abinci ta fara zuzzuba musu.
Shi kuwa Sheykh tuni ya wuce Side ɗinsa.
Ita kuwa Aysha waya takeyi da Aminiyarta Rafi'a.
Gyara zamanta tayi tare da cewa.
"Rafi'a naji kamar an nememu a makaranta ko?".
Ɗan gajeren tsaki Rafi'a taja tare da cewa.
"Haka dai akayi ta cewa, to amman zancen Babu tushe, ance ƙaryane, gwamnatin ma bata nemi malaman ta zauna dasu ba."
Ɗan murmushi tayi tare da cewa.
"Alhamdulillah aini wannan yajin aikin da aka shiga yamin rana, kinga da wannan tsarkafeffen auren da aka liƙamin da ya sani a tsaka ba fita.
To amman yanzu kinga duk muna a tare, zan kuma dage inyiwa Umaymah batun karatun nawa, kafin a nememu, in tayiwa Yah Sheykh mgna dai nasan zai barni."
Tsaki Rafi'a ta kumayi tare da cewa.
"Hegiya Aysha wato ke murna kikayi".
Dariya tai kana tace.
"Sosai ma kuwa". Kauda zancen Rafi'a tayi da cewa.
"Yauwa su Ummey sun dawo kuwa? Ɗan na kwana biyu banyi mgn da suba."
Jingina kanta tayi da jikin kujera kana ta fesar da numfashi a hankali tace.
"Uhummm basu dawoba, Rafi'a bani da kowa nawa a kusa dani, tunda nazo gidan nan ban sake ganin Ummey naba gwara Bappa na da Ya Al'ameen sunzo da bani da lfy, ina kewar Junainah, ina kewarsu Yah Giɗi in na tunosu hankalina na tashi ina masifar kewa da son ganin Dedde na".
Cikin tausayawa Rafi'a tace.
"Ba komai Aysha kiyi ta musu addu'a in sha Allah zasu baiyana kuma Allah zai karesu.
Su Ummey kuwa kwanaki da mukayi mgna da Junnu tace min wai sun kusa dawowa".
Cikin sanyi tace.
"Wasa sukewa Junnu, sabida ta matsa wai ita zata zo wurina kuma ita ko a gidansu Junaidu zata zauna".
Dariya Rafi'a tayi tare da cewa.
"Uhmm su Junainah manya wato ita fa da gaske har ranta take son Junaidun fa".
"Sosai ma kuwa".
Aysha ta faɗa tana kallon Ummi dasu Affan da suka miƙe tsaye alamun sun gama cin abinci.
"Yauwa ga Umma wai tayi kewarki kwana biyu baku gaisaba".
Rafi'a ta faɗa tana miƙawa Ummanta wayar.
Amsa Umma tayi tare da cewa.
"Aysha ya gida ya kwana biyu".
Cikin jin daɗi tace.
"Lfy lau Alhamdulillah Umma yasu Jamila".
"Lfy lau suna gaidaki".
Tace.
Kana ta miƙawa Rafi'a wayar tare da cewa.
"Tashi kije kinyi baƙo".
To tace kana ta katse kiran sannan ta fita.
Ita kuwa Aysha juyowa tayi ta kalli Ummi dake miƙa mata wayarta tare da cewa.
"Amshi Umaymah ke son mgna da Sheykh ta kira wayarsa baya ɗagawa ke kuma ta kiraki taji kina waya."
Amsa tayi da sauri kana ta kara a kunne tare da cewa.
"Assalamu alaikum, Umaymah ina wuni".
Umaymah dake kwance kan gado Mamma na gefenta,
Murmushi tayi tare da cewa.
"Lfy lau Alhamdulillah Aysha, ya gajiyar hanya?".
"Alhamdulillah Umaymah inasu Hibba da Safiyyah".
"Suna lfy, suna can Side ɗin Jannart".
Ayyah tace, ita kuwa Umaymah gyara kwanciyarta tayi tare da cewa.
"Yauwa Aysha Kaiwa Jazlaan waya".
Da sauri ta miƙe tare da cewa.
"To Umaymah bari in Kai mishi".
Corridor'n ta shige, tana tafiya tana gaisawa da Mamma data amshi wayar.
A hankali ta kutsa kanta cikin falon shiru, babu kowa sai hasken wuta daya karaɗe falon.
Ƙofar bedroom ta nufa, tare da kallon wayar da taji kiran ya katse.
A hankali tasa hannun ta tura ƙofar Bedroom ɗin tare da sallama a saman lips ɗin ta.
A hankali ta meda ƙofar ta rufe,
kana ta ɗan tsaya tana kallon yadda ya kunna wutan ɗakin gaba ɗaya hasken ya cika ko ina.
Can ta hangoshi konce bisa gadonshi,
ya kwanta a kife, kana babu riga ko singilet babu a jikinshi.
Dagashi sai gajeren wondon, wanda yazo mishi har guiwarsa.
Roban ya zagaye ƙugunshi ya manne gam.
A hankali ta fara yin taku, tana matsowa, kusa da gadon.
Shiru ta ganshi kwance lib.
Ya kwantar da kanshi bisa pillow'nshi yana kallon gefe jikin gini.
Cikin nitsuwa ta ƙaraso gabanshi, ido ta zurawa Kekkyawar farar fatar bayanshi, da take tamkar ta Balarabe.
Sumar ƙeyanshi ta kalla, ido ta lumshe tare da ɗan sunkuyowa, bakinta ya kusanta da kunnenshi, a hankali ta buɗe baki tare da cewa.
"Yah Sheykh!".
Idonshi ya kuma lumshe da kyau, jin sautin zazzaƙar muryarta cikin kunnensa.
Tun shigowarta idonsa biyu, dan ya gaza samun bacci, yaso ace ya sauyawa Gimbiya Saudatu kamanni ta yadda har abada bazata sake tsayuwa a gabanshi ta ƙalubalanci ƙaddarar mahaifiyarshi ta kalmar sakaiyar zunibinta ne ba.
Ƙara manna kanshi da pillow'nshi yayi, jin alamun ta hau kan gadon.
Ita kuwa Aysha a hankali ta rarrafo ta matso gareshi.
Sunkuyowa tayi ta leƙa fuskarsa,
tare da