Showing 30001 words to 33000 words out of 94417 words
mata. Yana lumshe idonsa.
A hankali ta mirgina zata matsa, sai kuma ta ɗan tsaya jin tama isa bakin gado, daga ita sai katanga, juyowa tayi ta fuskanci katangar ta kwanta tayi shiru.
Shi kuwa Sheykh shima shirun yayi, yana dogon nazari kan al'amarin Jahan da yake girmama kullum a wurinta, ya lura yau saura kiris ta suma.
Numfashi ya ɗan fesar a sanyaye kana ya juyo da kyau ya fuskanceta, sannan ya matsota ya manna bayanta da ƙorjinsa.
Da sauri ta buɗe idonta tare da buɗe baki zatayi mgna sai kuma tayi shiru jin ya sunkuyo kanta kanta sosai daga koncen, kanta ya ɗaga kana ya ture pillow'n da kanta yake kai, sannan miƙar da hannunshi a wurin,
kanta ya kwantar bisa damtsen hannunshi da ya miƙar, kana ya juyota rigingine, ƙafarshi ya ɗan ɗaura gefen cinyarta kaɗan,
kana yaja cinyarta yasa tsakankanin cinyoyinshi.
a hankali ya fesar da numfashi kana murya can ƙasa yace.
"Shike nan baki da iska.
Kiyi haƙuri, Umaymah kawai na gayawa fa."
Cikin wani irin masifeffen sanyi da jin daɗin kulawarshi gareta a hankali tace.
"Toh, amman Yah Sheykh da gaske inada iska ne wai".
Kanta ya shafa kana yasa bakinshi ya sumbaci goshinta cikin son kawar da tambayar tata yace.
"Me Jahan ɗinkin yake miki in yazo wurinki? Yana mgna ne? In yanayi me yake ce miki?".
Baki ta tura tare da cewa.
"Ni dai ba Jahan ɗina bane".
hannunshi yasa a hankali ya fara janye dogowar rigar jikinta yanayi sama dashi kana yace.
"To na ji, me yake miki?".
Cikin takaici tace.
"Ba kanaga kamar wai al'januna bane sai kake ɗaukar abin wasa to wata rana sai yamin ciki ai da ƙarfi".
Cikin sauri ya rumtse idonshi da ƙarfi tare da yin sama da rigar sosai kana a hankali yace.
"Na yarda ai baki da al'janani.
To amman ta yaya zai miki ciki".
Juyowa tayi ta fuskanceshi da kyau kanta na damtsen hannunshi, tattausan gemunshi na taɓa goshinta, cikin muryar da tafi kama data tsoro da raɗa tace.
"Duk fa lokacin da ya zo na ganshi sai yayi kissing lips ɗina.
Ɗazu kuma harfa kwance min igiyoyin wuyan rigata yayi, gasuba har yanzu ban ɗauresu ba".
Cikin hikima ya zare hannunta ɗaya cikin rigar kana ya zare ɗayanma sannan yace.
"To sai kuma yayi me daya kunce igiyoyin?".
ya ƙareshe mgnar yana ajiye rigar tata bisa inda ya ajiye al'kyabbar shi.
Kana ya zare jallabiyar jikinshi, ya ajeta, sannan ya matso gareta tare da jawo musu blanket yace.
"Uhumm".
Cikin tsurawa inda yake ido tace.
"Harda sa hannunshi cikin rigata, kuma yana mammatse min ƙirj.."
Da sauri ya lumshe idanunshi tare da jawota jikinshi ya matseta gam har saida tayi ƙara sabida matsar tayi ƙarfi, shi kuwa Sheykh gaba ɗaya jikinshi tsuma yakeyi ya gama gamsuwa Shatu Mar'atussaliha ce.
Ya yarda ita bata da wanda ta yarda dashi a Masarautar Joɗa sama dashi bata ɓoye mishi komai, ya kuma gamsu da son kiyaye lfyarsa da takeyi.
Cikin wata iriyar fitinenneyar murya mafi daburcewa yace.
"Bana son ji, kuma kodama al'janin nakine, zanyi mgninshi da izinin Allah, bashi da hurimi da mallakin Muhammad, shi kaɗai yake mallakar abunsa, kuma ko gani nai wani bazai yiba in sha Allah a mutum dai babu mahaluƙin da zai min kutse a gidana ma bare a kan iyalina."
Ita dai ba jinshi sosai takeyi ba, sabida wasu abubuwan da yakeyi mata sun zarta abinda Jahan ya aikata mata.
Dib, dib, dib, haka zuciyarta keyi lokacin da taji ya haɗe lips ɗinshi da nata, kana tattausan tafin hannunshi na yawo a cikin dukkanin sasan jikinta.
Gaba ɗaya sai tsoro ya rufeta, a hankali taketa jujjuya kai alamun a a.
A hankali ya rabe lips nasu, cikin sanyi tace.
"Ya Sheykh bacci nakeji".
Uhummm yace kana ya gyara musu kwanciyar.
A can ƙasar Cameroon kuwa.
Ba'ana ne zaune gaban wani ƙasurƙumin bokanshi mai ƙara buɗa mishi ido, da koya mishi siddabaru iri-iri.
Wani ƙaton kaskone a gabansu.
Cikin muryar da babu daɗin amo boka Dumba ya cewa Ba'ana.
"Leƙa ka gani, gacan ajiyarka tana kwance tana bacci lfy lau babu wani mahluƙin namiji da zai iya taɓa koda farcenta ne bai mutuba, bare har ya shafeta ko ya kai ga taɓa wani sashin sirri na jikinta bare a kai ga ya kusanceta".
Tuni Ba'ana ya leƙa kanshi yana ƙarewa fuskar Aysha kallo, cikin jan dogon numfashi yace.
"Boka Dumba to shi wannan haskenfa da yake kwance kusa da ita menene shi kuma wane haskene ya zagaye ɗakin da fuskarta?".
Cikin yin cacuɓe-cacuɓenshi yace.
"Wannan haskene dake wanzu da izinin ubangiji haskene dake kare wanda ke kusa da ita sam bamu da tsumi ko dabarar ganin komai a kanshi, sabida shi mutum ne da bakinshi baya bushewa da ambaton Allah kana baya rabuwa da al'wala a jikinshi.
Ita kanta in dai tana kusa dashi ainun jikinta ya taɓa nashi to bazamu ga komai a kanta ba, batun kusanta ne dai tabbas babu mahaluƙin da zai kusanceta ya rayu, domin madadin ɗanɗanon ni'imomin da ko wacce mace take dashi, in namiji ya sadu da ita, to ita dafin kuna da macijiya ne ni'imarta zata shigeshi a sashi mai tsada a jikinshi kan gari ya waye zai mace ya bar duniya".
Wata iriyar muguwar dariya suka kece da ita kamar zasu fasa kogon da suke ciki, boka Dumba ne yaci gaba da cewa.
"Kai dai ka gama aiyu kan ka hankalinka kwance, shi wannan da yayi sanadin faɗinka gasar Shaɗi har yasa kabar ƙasarku, tuni munsa ajalinshi a jikin matar da yakega matarsa ce, kaga koda baka tare da Shatu zata tayaka yaƙi ba tare da ta sani bama".
Cikin jin daɗi da baƙar mugunta Ba'ana yace.
"Dole ma ya mutu, sai dai babarsa ta haifi wani hegen bafullatani mai jajayen kunnuwa".
Daga nan sukaci gaba da hirarsu da tanadin hana fulanin ƙasar Nigeria da Cameroon zaman lfy.
A nan Ɓadamaya kuwa, cikin Masarautar Joɗa, a wannan lokaci na tsakiyar dare.
Suka fito cikin masarautar suka nufi gidan boka Tsitaka, garin yayi duhu yayi dim sai azabar zafi da ake tsulawa zafi irin na tsakiyar damuna irin wanda in an kwana biyu ba'ayi ruwan samaba, bisa alamu hadari ke diddigowa daga ƙasa shiyasa garin yayi dim babu alamun iska.
Suna shiga Boka Tsitaka ya kwashe da dariya tare da cewa.
"Lbri mara daɗin gashi can konce da matarsa bisa gado ɗaya, sai dai kun san ɗan naku ba'a iya ganin sirrinshi, ko matar tashi bana gani sai wani haske daya rufesu.
Kuma yana gab da ɗirkawa ƴar fulani ciki hegen yaro dan yanada ƙoyayen haihuwa da ƙenƙesa".
Cikin tashin hankali ɗayan yace.
"Kusantar mata harda haihuwa, anya kuwa bazan sa a dandatse min wannan yaron ba, shin wai shi wanne irin mutum ne da baya jin sihiri da tuggu da makirci".
Ɗayan ne yace.
"Ai kuwa koda ya haihu yarane dai bazasu rayuba".
Dariyar mugunta Boka Tsitaka yayi tare da cewa.
"Ku dai kun iya kawo aiki kun kuma iya faɗin mugunta sai dai tabbas akwai wani wanda yake gefenku, da yake aikata musu fiye da shirinku, kullum in kun tuna yimasa wani abun kafinma kuyi abun zakuga fiye da hakan ya faru tun shekarun baya.
To bare kuma yanzu an sake samun wani taƙadirin ma yasa mishi ido".
Dariyar jin daɗi sukayi kana sukaci gaba da muhawarar mugunta.
Washe gari azahar Gimbiya Aminatu ce zaune gefen Lamiɗo da ya kira Sheykh suna gaisawa, tare da cewa.
"Muhammadu Akwai babban uzurin dake buƙatar ka dawo gobe".
Gyara zamanshi yayi tare da kallon Aysha dake gefenshi ita da Hibba da Jalal da sune suka kawo musu abinci a hotel ɗin da suke. Maida kanshi yayi ya jingina da kujera kana ya lumshe idonshi tare da cewa.
"Eh dama gobe zamu taho, amman sai dare jirginmu zai tashi.
Su Ya Hisham da Affan kuwa sunce sammako zasuyi wai tafiyar mota zasuyi".
Cikin sauƙe numfashin Lamiɗo yace.
"To Allah ya kaimu ya kuma dawo daku lfy, itafa Juwairiyya sai yaushe zata dawo".
Kanshi ya ɗan mirgina kana yace.
"Zan dai taho da Ya Jafar da Jalal, in bata gama uzurorinta ba, sai ta koma masarautar Jadda ta dawo daga baya."
Cikin gamsuwa da hakan Lamiɗo yace.
"To hakan yayi Allah ya kawoku lfy".
Amin Amin yace kana ya katse kiran.
Jalal ne da Hibba suka miƙa tare da cewa.
"Mu zamu tafi."
Bai kulasu ba, Jalal ne ya ɗan matsoshi tare da cewa.
"Umaymah tace ka kai mata Ɗiyarta taga ya ta kwana da jikin".
Kai ya gyaɗa alamar to.
kana Hibba ta kalleta tare da cewa.
"Aunty Aysha sai kin dawo, Allah ya ƙara sauƙin".
Amin tace tana gyara zamanta tare da jawo ƴar jakar kayan da Hibba ta kawo mata. Wai na anko ɗin fansan idon da za'ayi.
Su kuma nan suka fita.
Suna fita, ya miƙe ya rufe ƙofar, kana ya dawo ya hau kan gado ya kwanta.
Da ido ta bishi tare da cewa.
"Yah Sheykh gado kuma to yaushe zamu tafi ko inbi su Hibba kawai ne?".
Lumshe idonshi yayi alamun bacci zaiyi, a hankali tace.
"Dole ne kullum sai kayi baccin tsakanin azahar da la'asar ɗin nan". Kanshi ya gyaɗa mata alamar eh.
kana ya juya mata baya.
Dole itama ɗin ta hau ta kwanta, tana konciya ya jawota jikinshi nan take sukayi bacci.
Ƙarfe uku da minti arba'in da biyar ya farka, da sauri ya zareta daga jikinshi kana ya shiga bathroom, wonka yayi fes kana yayi al'wala ya fito.
zaune ya sameta bakin gado.
"Tashi kiyi wonka mu tafi tunda ke bakya cikin masuyin salla".
Cikin sanyi tace.
"Ah ina cikin masuyin salla mana".
Kai ya gyaɗa yana zura tattausan al'kyabbar shi. Yace.
"Eh amman ni dai tun jiya banga kinyi salla ba".
Cikin rashin fahimtar wayon da yake mata tace.
"In Sha Allah gobe dai da safe ai zan fara".
Murmushi yayi tare da cewa.
"To tashi kiyi wonka kafin inyi sallan".
To tace kana ta miƙe ta shiga Bathroom da ƴar jakar kayanta.
Shi kuwa ya kabbarta sallan la'asar.
A cikin bathroom ɗin ta canza kayanta bayan ta kimtsa jikinta.
Kana ta ninke wanda ta cire ta saka a ciki ta feshe jikinta da turarenta mai sanyin ƙamshi, sannan ta fito.
Zaune ta sameshi bisa sallayar yasa System ɗinshi a gaba ya maida hankalinshi kab kanta. Bisa alamun wani abu mai tarin mahimmanci yakeyi.
Dan gaba ɗaya yatsun hannunshi aiki sukeyi sai kwayar idanunshi da yake jujjuyawa kan screen ɗin na'ura. Yanayi kuma yana motsa lips ɗinshi alamun still kuma tasbihi yakeyi bincikar number da ake tura masa text a rufe yakeyi yadda zai samu ya buɗe layin yabi diddiginshi.
A hankali ta kalleshi da kyau, kana ta kalli kayanshi da ya cire ɗauka tayi ta ninninkesu ninkewa mai kyau, tasa a ƴar jakar ta zuge zip ta rufe.
Sannan ta koma gefenshi can ta zauna bayanshi.
Cikin sanyi tace.
"Ni dai banga wayata ba".
Bai kulata ba, domin aikin da yakeyi ya tunzura mishi nitsuwa.
Cikin sanyi tace.
"Ayyah to dan Allah. Sammin wayarka in yi kira".
Tura mata wayarshi dake gefenshi yayi sabida ya samu ta rabu dashi dan tana raba mishi hankali".
Ɗaukar wayar tayi sai kuma taga akwai security code a jiki.
Matsoshi tayi da mamaki dan tasan akwai woyoyin shi biyu data taɓa riƙewa basa da security, jujjuya yar wayar tayi ganin yar micilace kuma harda liƙa mata matakan tsaro, taɓe baki tayi tare da cewa.
"Me code ɗin buɗe shi".
"Mamey". Yace mata ba tare da ya kalleta ba.
jujjuya yar mitsitsiyar wayar tayi a tafin hannunta, contacts ta danna da nufin ta ɗan duba ko da number sai ta samu nanma a garƙame yake.
Ikon Allah tace a hankali kana ta danna. Phone na ma kirib yake, cike da mamaki tace.
"Wayarfa tako ina ansa mata kan tsaro".
Da sauri ya juyo ya kalli wayar da ke hannunta. Hannunshi yasa ya amshi wayar da sauri tare da zurata a al'jihunsa kana ya yasa kan yatsunshi ya ɗan bugi goshinsa tare da kwaɓe fuska kana ya kalleta cike da alamun damuwa yace.
"Kai Alhamdulillah, Allah na gode maka daka jarabceni da wannan fitinenneyar yarinya Aish mata, kinzo kin tasani gaba da surutu, kuma kina gani aiki nakeyi, ko so kike na ki rikitamin tunani ne".
Kanta ta langoɓar tare da kwaɓe fuska tace.
"A a, Ni kawai wayata zan kira".
Cikin zubawa lips ɗinta ido yace.
"Ba kin barta a motaba".
Da sauri tace.
"Laah hakafa ni na manta ma".
Kanshi ya gyaɗa kana ya gyara zamanshi ya fuskanci System ɗin nasa.
Gefenshi ta ɗan kalla tare da cewa.
"Yah Sheykh!".
Shiru bai amsa ba yaci gaba da aikinshi.
a hankali ta kuma cewa.
"Yah Sheykh!!".
Bai amsaba bai kalleta ba.
A karo na huɗu ta kuma kiranshi.
"Yah Sheykhhhh". Ta ƙarashe kiran murya can ƙasa da alamun bacci ya fara kamata, a hankali ya ɗan juyo kwayar idanunshi ya kalli inda take.
Cikin lumshe ido tace.
"Mu tafi mana, za'ayi fansan ido da bamu jeba".
Kanshi ya gyaɗa alamun to, daga nan ya meda kai yaci gaba da aiki.
A can gida kuwa, tuni anyi fansan idon amarya da ango gaba ɗaya an gama komi da komai.
Har an fara shirya farfajiyar Side ɗin Umaymah wanda anan za'ayi shagalin mother's day ɗin.
An gyara wurin an kimtsa an shirya komai yadda ya kamata.
Ƙarfe biyar dai-dai duk an gama shirya amarya cikin shiga ta al'farma, hakama ango Haroon ɗan ayi.
Aunty Rahma kuwa tasa mabusan masarauta da makaɗa yan kakaki da tambura da al'gaita duk sun shiryawa shagalin tunda abu na jinin sarauta ai dole a gwada iyawar.
Safiyyah ce ta shigo bedroom ɗin Umaymah inda ta wuce zugan ƙawayen ta duk suna falo cikin kwalliyar ƙasaitattun mata, matsowa kusa da Umaymah tayi tare da cewa.
"Umaymah Aysha fa har yanzu fa Hamma Jabeer bai kawota ba,".
Cikin sauri Aunty Juwairiyya tace.
"Dan Allah Umaymah kirashi ya kawota Mamma tace su Haroon ma bazasu fitoba sai sun iso".
Murmushi ta ɗan yi tare da cewa.
"Uhummm Jazlaan fa ba son waɗannan abubuwan yake ba. Bana son tirsasa masa yin abinda baya so ku kuma kun dage, ala dole tunda bikinsa ba shiri ba'a zoba yanzu sai kunyi shagalin".
Ummi ce ta ɗanyi murmushi tare da cewa.
"To bari ni in kirashi".
Cikin sauri Umaymah tace.
"Yauwa yama fi min".
Ita kuwa Ummi wayarta ta kara a kunne bayan ta danna mishi kira.
Bugu biyu ana uku taji ya katse kiran.
Jim kaɗan kuwa sai ga kiranshi.
Bayan sun gaisane sai kuma ta ɗan yi shiru.
Jin hakane ya sashi cewa.
"Na'am Ummi meke faruwa ne?".
Cikin tausasa murya tace.
"Eh dama duk an gama shirine ku kaɗai ake jira".
Kanshi ya ɗan juyo ya kalli Haroon dake ta murmushi kana a hankali yace.
"Ummi ai mun dawo, yanzu muka shigo, bata iso wurinku bane?".
Da sauri Ummi ta juyo ta kalli bakin ƙofar jin muryar, Aysha tana sallama.
"Yauwa gata ta iso". Ta faɗa mishi tare da katse kiran".
Safiyyah ce tayi sauri kamo hannun Aysha tare da cewa.
"Yauwa zo muje ɗakin Hibba ki shirya".
Murmushi tayi tare da cewa.
"Safiyyah barni mu gaisa dasu Umaymah mana".
Murmushi Mamma da yanzu ta shigo tayi tare da cewa.
"Uhumm Safiyyah kuwa da gaggawa".
Cikin ladab da biyayya ta rusuna ta gaidasu kana, Safiyyah ta jata suka tafi ɗakin Hibba.
A can Side ɗin dasu Haroon suke kuwa, Ibrahim ne ya ɗauko wasu tattausan kaya masu masifar kyau da taushi, yadin Getzner ne mai ɗan karen kyau kalar pink guava mai masifar kyau, riga da wonɗone da babbar riga gariya an watsawa mats aiki da surfani mint green color irin mai sheƙin nan, sai baƙin hula mai ɗan karen kyau shima da ratsin mint green da fari,
amsa yayi tare da kallon Haroon da Ibrahim ɗin sosai kayan sukayi masifar musu kyau, kanshi ya ɗan juya ya kalli takalman da Ibrahim ke nuna mishi baƙaƙene irin masu sheƙin fatar nanne.
Fita sukayi, dan bashi wuri yasa kayan.
Sosai kayan sukayi masifar amsar fatar jikinshi da surarshi ya fito ras balaraben asali. Komai.
Hular ta zauna ras a kanshi, gefe da gefen kan nashi duk tattausan sumanshi ya ɗan fito, Especially ƙeyarshi da sumar ta kwanta lib kana farar fatarshi tayi ras ciki sajenshi da girarshi komai tubar kalla masha ALLAH.
A hankali ya taƙo ya fito falo.
Nan take su Haroon Suka miƙe, kasan cewar duk abokansu sun tafi sun watse tunda bikin maza ya ƙare, sai su uku suka rage sai kuma su Ya Hisham, Affan, Jamil, Jalal, Azeez, Sadiq, imran, Kabir, Kamal, Sulaiman, da dai sauran ƴan uwa da wasu makusanta.
Haka suka fito a tare,
Tuni harabar wurin ta cika tayi maƙil manyan matane tako ina matan sarakuna da manyan yan kasuwa da siyasa, aminan Umaymah da matan abokon Abbansu Haroon, sabida ranar tasuce ko wacce tasan Umaymah da Jazlaan ɗin ta sun san soyayyarsa a ranta fiye data Haroon ce sun kuwa san biyayyarsa gareta.
Shiru wurin babu hayaniya, hakane yasa Sheykh bai damuba dan baiga abun kiɗe-kiɗen da ya tsana ba.
Kuma gashi babu wasu taron maza, duk ƙannenshi ne.
Sai kuma iyayenshi, duk da har ga Allah har ransa baiso wannan tsarin ba sai dai bisa dole Umaymah'nshi da Abba Hajia Mama da Ummi suka tirsasashi.
Kuma suma basu san Aunty Rahma ta tsara kayan kiɗa da bushe-bushen sarewa da al'gaitanba.
"To ma in banda su Umaymah ya za'ayi ayi abu salam".
inji Aunty Rahma da take tare da mabusan. Hibba ce ta ɗan kalleta tare da cewa.
"Ai kuwa Hamma Jabeer zaiyi faɗa".
Dariya tayi tare da cewa.
"Me ruwana".
Sai kuma ta juyo ta kallesu tare da cewa.
"Kuna ganin amaren sun fito ku fara buga tambura da kakaki ayi bikin gidajen sarakuna haka Salam".
Ai kuwa bata ida rufe baki ba.
Aunty Juwairiyya ta buɗe ƙofar babban falon Umaymah ta fito ita da Jazrah.
Jannart na bayanta Aysha na bayanta.
Sai kuma Safiyyah ta biyosu.
Wani irin murmushi da gyaɗa kai Aunty Rahma tayi lokacin da taji an saki sautin tamburan.
"Uhum yauwa haka mana asan ana biki kam".
Ta ƙarashe mgnar tana tahowo kusa dasu Umaymah cike da mamaki suke kallonta ita kuwa tana musu murmushi Yar autar Sitti kenan.
A hankali Aysha ta lumshe idonta sabida wani irin yam da taji tsikar jikinta na badawa.
Hannun Safiyyah dake riƙe da nata ta ɗan juya itama ta riƙe.
A hankali sukaci gaba da taku cikin irin wasu masifaffun kaya masu masifar kyau, irin dai kayyakin nan da yan gayu ke sawa mai shara-sharan tattausan yadin cikin pink guava ne, kana net ɗin saman kuwa mint green ne. Anyi ɗinkunan dogayen riguna masu kyau cib cib da jikinsu.
Sai wasu takalma masu ɗan karen tsini kalar azurfa da yar karamar fosa sai a goggoronsu shina kolon takalman. Sosai sukayi kyau,
A hankali suke shigowa cikin taron ana mc ɗin yana mai bin waƙar da ya saki ta.
"Ku-martsa-ku-martsa ga amarya ta iso".
Wani irin murmushi mai cike da jin daɗi Umaymah tayi kana ta kalli Hajia Mama dake gefenta tace.
"Kinga surkanki masha Allah".
Uhummmm tace tare da kaɗa ƙafarta.
Sheykh kuwa wani irin rumtse idanunshi yayi lokacin da yaji an saki kuɗin badujalan injishi da faɗin.
Tsayawa yayi cak ba tare da ya ƙara koda