Showing 12001 words to 15000 words out of 73969 words
layin yafara cika da mutanensu Amma sai 'yan anguwa dasuka fara halartowa
shidai dattiya kallon kowa yakeyi zuciyarsa ba dadi ga cikin gida ma Nadiya jikinta sai rawa yakeyi sbd tashin hankalin data samu kanta aciki ga zazzabi tanaji ga Rashin sukunin da zuciyarta ke ciki.
Lokacinda yafito cikin sky-blue din shaddarsa 'yar ciki da babbar riga ga hularsa Yana daura agogo yafito daki daidai fitowarta daga daki zataje Kiran iya talatu cak ta tsaya tareda juyowa ahankali daidai ya kallo gefen Suka hada ido.
Wasu irin hawaye ne Suka ciko idanuwanta sanin daga yau idan ta auri Bello bazata sake rayuwa a inda yakeba.
Dauke Kai yayi Yana sake hade fuska ya fito waje.
Wani irin annuri da haiba ke fita a fuskarsa sbd tsananin kyawun da yayi tamkar shine angon musamman izzarsa dake qara masa burgewa da kyau.
Nufosa JJ yayi cikin tsananin farin ciki ya miqa masa hannu sukai musabaha batareda ya saki hannunsa ba yace"
ALEEYU HAIDAR Ina cikin farin cikin ganin kana taredani a yau ranar aurena Rana mafi farin ciki agareni Saidai Ina roqon wani Abu daga gareka.
Wani irin murmushi yayi Yana basarwa yakalli JJ din ganin yanda yayi wani iri sai habarsa ta dakesa atake yaji tsananin qaunar JJ din nasake shigarsa Dan kuwa shikadai yasan irin son dayakewa JJ Wanda yasa yake danne ciwon dayakeji a qirjinsa ganin JJ na farin ciki da auren.
Cikin kulawa yace"
Kafadamin abinda kakeso agurina zan baka kodan tarihin wannan Rana agareni.
Murmushi JJ yayi yace"
_*NADIA*_ nakeson tasamu dukkanin farin ciki da walwala tareda kulawa da qauna data rasa tun rasuwar umma,
Kallonsa yayi tareda dauke Kai Yana zame hannunsa daga nasa fuska a daure yace"
Wannan duk zaka Bata bayan aur.....
Bai qarasaba ya juya zai wuce
JJ yace"
Nayi Mata alqawarin nema Mata lafiyarta matuqar Ina raye da lafiyata,
Saidai bansaniba kozan iya,
Roqona anan shine Ina roqonka da a duk lokacinda na gaza cika wannan alqawarin to cikaminshi koda inanan ko banan.....
Juyowa zakin yayi Saidai kafin yayi magana ya hango kb tafe cikin mutane ya rufe fuskarsa Yana boye wani Abu cikin riga.
Janye JJ yayi da sauri zai tare kb din Saidai jj na juyowa yaga sharbebiyar wuqarda ke hannun kb wadda asalinta bakin lace ne da Ida kamar tafiyar maciji idan aka sokeka da ita yanada wuya ta fito Bata yanko hanjinkaba shiyasa ba'a tsallaketa.
Kb na daga wuqar JJ ya tare atake ta shige cikinsa gaba dayanta kafin kb ya fizgota da qarfi yanda zatafi yimasa illa.
Wani irin numfashin wahala JJ yasaki tareda zubewa qasa kb na ganin hakan ya gudu musamman da Babu Wanda ya Ankara da abinda ke faruwa
Zaki zabura yayi ya damqo hannun kb JJ yayi saurin riqe nasa a wahalce yace"
Ina buqatar kusa Dan Allah.
Cikin karaji yacewasu nano subi kb su kamosa karsu Bari ya gudu.
Atake guri ya kaure da hayaniya sbd ganin abinda ya faru jini gabaki daya ya Bata farar shaddar jikin JJ har qasa.
Wani irin runguma Zaki yamasa Yana cewa"
JJ Dan Allah karka rufe idonka zamuje asibiti zaka warke yanxu muxo a daura maka aure,
Karka manta Kaine kuzarina da ganina,
Kaine magajina,
Karka rufe idonka Dan Allah JJ......
Cikin tsananin karaji yace akawo masa mota.
Hankali tashe da ganin jininda ke zuba Suka sakashi mota a gigice Zaki ke tuqin hannunsa daya na damqe dana JJ da tuni idanuwansa Suka rufe.
Duk yanda su dattiya ke cikin 6acin Rai hankalinsu yatashi matuqa da abinda yafarun Dan kuwa tabbas kowa yasan JJ shine abunda Zaki yafi so,shine komai na Zaki.
Zancen na shiga kunnen Nadiya ta sulale qasa tana tsiyayo hawaye da idanuwanta dasuka gama kumbura dayin jajir.
Suma sauran mutan gidan sun firgita sosai da jin zancen musamman da aketa cewa JJ yariga ai yarasu.
A asibiti kuwa suna zuwa 'yan sandan da ale dikko yaturo musu suna isa nan aka karbesa a gagauce akai cikin theatre dashi.
Kasa zama Zaki yayi tareda yamutsa sumarsa yanajin zuciyarsa kaman tana qonewa sbd tsananin tashin hankali da baqin cikin dayake ciki.
Su nano tuni Suka iso asibitin sbd dai kb ya gudu Amma dai aisunsan bazai guje musu ba idan hankali ya kwanta.
Sosai suke cikin tsananin tashin hankali da fargabar abinda zai faru,
Asibiti kuwa atake kowa yasan yau su sarki na asibitin Dan kuwa tuni kowa ya dauko makansa.
Minti goma Sha hudu da shiga dashiga dashi likitoci biyu Suka fito fuskarsu ba dadi Kai tsaye 'dayan yace"
Sai hakuri Allah yamasa rasuwa..
Akaro na farko arayuwarsa da hawaye Suka sauko idanuwansa yayi baya tareda zubewa a kujera Yana dafe kansa dazai tsage sbd wani irin sarawa da jijiyoyin kan sukeyi.
Su Nanu kuwa tuni duk Suka saki makamansu kowanne na sunkuyar dakai cikeda baqin cikin rasa 'dan uwansu,aminsu mai qaunar dukkaninsu.
Sosai Dr aminu da Dr faruk Suka tausayawa halinda Zaki yashiga musamman dasuka lura kansa yake ruqewa sunsan illar dake cikin hakan sukai saurin sa nurses maza su kamosa ashigo ciki dashi Yana buqatar kwanta suyi masa allurar minti goma.
Miqewa yayi da kansa yashiga kodan yaga gawar JJ 'dinsa Saidai suna shiga yaga gawar JJ din rufe har Kai da qafa
Atake yaji zuciyarsa na neman tarwatsewa itama ya isa bakin gadon yayi shiru Yana tuno maganganunsu na qarshe.
Ya dade Yana kallon gawar kafin ya juyo baiko tsaya sauraron Kiran da Dr kemasa amasa allura ba yafito atake yaransa Suka Mara masa baya musamman dasukaga fuskarnan ba rahama ko daya.
Cikin motarsu Suka figeta sai qofar gida lokacin Sha biyu saura minti ashirin gashi mutane na nesa basusan da abinda ke faruwaba tuni aka sake cike gurin taf da 'yan zuwa daurin aure.
Dan kuwa tuni akayi shimfidu anata gaishe gaishen barka da zuwa.
Suna sauka Kai tsaye gurin kawun ya nufa shima yana ganinsa yayiwa idi ido nan aka fara shelar za'a daura auren.
Take kowa ya zazzauna aka fara.
Yana isowa ganin mutane da yawa yasa yazo har kusada kawun ya zauna Kai tsaye yace"
Zanyi magana dakai kar a daura sbd JJ ya....
Cikin nutsuwa kawu yace"
Kabari agama daura auren muyi magana yanxudai ka nutsu auren 'yatane bana son matsala.
Miqewa yayi yabar gurin ya hargitse kansa yake.
Cikin nutsuwa dattiya ya fitarda dubu goma a miqawa liman yace"
Ga sadakin 'dana nan.
Karba akayi aka miqawa mal idi dashine yayi waliyin Nadiya.
Yakai mota zai shiga subar gurin yaji ana cewa"
*_AN DAURA AUREN ALIYU HAIDAR DA NADIYA DATTIYA AKAN SADAKI NAIRA DUBU GOMA LAQADAN BA AJALAN BA ALLAH YASA WANNAN AURE SAI MUTUWA_*
Aminnnnnn jama'a Suka karba anata miqawa dattiya hannu ana tayasa murna nan guri ya kaure da hayaniyar Taya murna.
#MAMUH*_BURI DAYA Yana cikin Zafafa2020 na siyarwane ba free ba idan baki biyaba ki nemi wainnan numbers din kibiya ki karanta cikin amincin allah._*
07067124863
08030811300
*_Mamuhgee12_*
Kasa shiga motar yayi hakama yakasa juyowa
Zuciyarsa nason qin gasgata abinda kunnuwansa Suka jiyo masa musamman yanda numfashi ke sauri gurin fita.
Dukkanin yaransa kuwa wuta Suka dauke Basu nuna farin cikinsuba daya wanxu cikin zukatansu sbd jimami da radadi dasuke ciki na Rashin dayan jigonsu JJ.
Ahankali ya juyo bayan ya rintse idanuwansa ya bude atake Suka qara kadawa Suka rikide.
Kallon kawun yayi daketa miqawa mutane hannu Yana yaqen dole Dan kuwa shima ayau din zuciyarsa dif take da damuwar wannan aure Saidai baida yanda zaiyi Dan kuwa wani bangaren auren Zaki ga nadiyarsa shine mafita Dan kuwa idan tana matsayin matarsa Babu shegen da zaiyi Gigi ko gangancin ko yiwa inda take mugun kallo,
Saidai ta bangaren rayuwar aure yasan Zaki bazai taba kulada Nadia ba musamman ganin yanda yafi hukuntata akan kowa.
Hada ido sukayi sukayiwa juna kallon cikin ido kowanne zuciyarsa cikeda damuwa da tsananin bacin Rai Saidai hakanan ya juya yafada mota sukabar gurin Dan zuwa dauko gawar JJ azo ayi Mata sallah.
Suna barin gurin aka fara watsewa sbd wasu da dama basusan da rasuwar JJ ba.
Acikin gida kuwa lokacinda dahiru yashigo bayan daurin aure shine yafara shigowa ya nufi dakin iya talatu dake 'dan cikeda mutane anata hayaniyar biki ya miqa Mata goro da dabinon daurin auren yana cewa"
Ga goron nan ki ajiye har baban yashigo andaura aure da yardar Allah Saidai abin mamakin baba baya qarewa mu munxo da sanin Bello ne mijin saigashi mukaji baba agurin yacewa liman da Zaki za'a daura auren.
Saurin kamo goron daya kusa zubewa iya talatu tayi tana kallon dahiru tace"
Zaki fa kace????
Eh, Allah yabasu haquri da juna shine fatar kawai tunda andaura.
Numfashi iya talatu tasaki tana sake zare 'yan fici ficin idanuwanta cikeda mamakin dattiya da Rashin sanin abin fada kawai tace"
To Allah ya sanyaya zuciyar Zaki mudai da wannan danyen hukuncin na babanku.
Kallon zainab dake tsaye gefenta tana waya da wasu qawayenta datakewa kwatancen gidan tace"
Auren nan kinji da Zaki aka daura.
Wani zaro ido tayi cikeda mamaki da son qin gasgata zancen tace"
Yaya Zaki yanxu shine mijin Nadiya????
Kwarai kuwa cewar dattiya daya shigo gidan.
Aikuwa nan aka dauki guda ana Allah ya sanya albarka.
Zainab kuwa daki tayi da sauri Dan fesawa Nadiya zancen.
Qare Mata kallo tayi daga bakin qofar tana kwatanta irin dacewarda zasuyi da ace zasuyi zaman aure kamar na kowane maaurata Saidai tasan Yaya Zaki Kam ko kallo Nadia bazata ishesaba duk da wasu lokutan tanayi musu kallon masoya duk da irin tazarar halaye da banbanci dake bayyane a tsakaninsu.
Qarasowa tayi cikin dakin ta zauna kan katifar dake dakin tareda aje wayarta tana daukar Hoda tafara shafawa fuskarta da Bata rabo da kwalliya koyaushe hankali kwance race"
Andaura aure dai yau kukan auren Bello yaqare Saidai na Yaya Zaki....
'dago jajayen idanuwanta tayi takalli zainab din ahankali batareda hawayen cikin idonta sun gangaroba sbd kokawar da zuciyarta keyi gurin auna zancen kafin ta yarda dashi a zuciyarta.
Aje hodar zainab tayi tareda kallonta tace"
Baki yarda bane ko me?kike min kallon qurulla...
Sallamar dattiya tasasu kallon qofar dakin atare,
Zainab ta miqe tareda daukar wayarta da gyalenta ta fice Dan tarbo baqinta.
Cikin sanyin jiki data fara ganin mahaifin nata dashi akaro na farko rayuwarta taga yashigo ya tsaya akanta zuciyarsa ba wani dadi yakalleta tayi qasa da Kai hawayenta na sake saukowa sbd yanayinsa kawai ya tabbatar matada zancen da zainab tafada gskia ne da Yaya Zaki aka daura Mata aure.
Cikin sanyin murya yafara cewa"
Nadiya Allah yayi yau nasauke nauyinki dayake kaina amatsayin mahaifinki Dan kuwa na 'daura Miki aure ayau din da Zaki Wanda shi na zabar Miki amatsayina na mahaifinki Dan haka Babu wani Jan dogon bayani Saidai Ina Miki adduar Allah yasa hakan shine alkhairin rayuwarki duk da nasan Babu abinda Zaki tsinta acikin auren zakin.
Qaramin kuka Mai ban tausayi ta fashe dashi Babu sauti Yana ji yajuya ya fice Yana jin wani qululun baqin ciki da takaicin zakin.
Sosai tayi kuka Wanda sai yanxu take jin gwarama auren bellon tunda shi Yana sonta yanxu wannan auren wace irin rayuwa baban ke tunanin zatayi da mutuminda ko kallon inda take bayayi da daraja bare ma matsayin Mata.
Cikin yan biki kuwa Babu Wanda ya damu da wannan juyi da akayi hidimarsu sukeyi hankali kwance saidaima rasuwar JJ ce dake 'dan rage musu armashin abun duk da dai shiru har yamma tasomayi su zakin Basu dawo da gawar JJ dinba bare ayi jana'iza.
Har guraren magriba Babu labarin dawowarsu bare ayi jana'iza tuni aka gama yinin bikin aka watse ba maganar Kai amarya tunda gida daya suke ataqaice ma Babu gurin kaita.
Ahaka gida ya watse aka barsu sukadai yan gidan Dan ko dangin mahaifiyarta da maraicen Suka tattara Suka tafiyarsu ko Dan ganin angon nata ba irin Wanda zasu tsaya suyiwa nasihar riqe 'yar marainiyar 'yarsu bane Dan kuwa su kansu ranar dasuka fara zuwa sukaga bataliyar makamai da yaransa a qofar gidan a tsorace sukeda gidan har Suka tashi tafiya musamman yanxu dasukaji shugaban bataliyar shine mijin yarsu.
***
Lokacinda Suka koma asibiti Sun Jima suna neman likitanda case din yake hannunsa gashi yashiga theater Dole Suka jira yafito sbd asibitin ta dikko Dilla ce dokace ba'a bayarda gawa sai likitan daya karbeka yazo yasaka hannu kunsaka sai abaku gawar.
Sai kusan yamma Dr jimoh yafito zuwa lokacin ran Zaki yafara baci Amma sbd yanason mutunta gawar JJ bazaiso yin kowane irin Abu na ta'addanci ba akan gawarsa sai angama komai akwai Wainda zaiyi settling scores dasu.
Atare Suka nufi dakinda gawar take bayan ansaka hannu da komi.
Tura qofar dakin sukayi Dr jimoh yayi saurin qarasowa ciki Yana kallon gadon ganin baiga gawar ba.
Kallon nurses dinda ke bayansa yayi suma Suka kallesa da tsoro da mamaki...
Wani irin kallo zaki yayiwa likitan Yana jiran qarin bayanin inda gawar JJ take Dan zuwa lokacin yagama zuciya zai iya tada asibitin kowama ya mutu ahuta.
Zare coat din saman kayansa Dr jimoh yayi Yana taba gadon murya na rawa yace"
Nurse Ahmad go and call all the nurses on duty and Dr ib Idris now.
Jiki na Bari kuwa yafice ko gani dukkaninsu basayi sosai sbd carriers dinsu ce zatayi rawa tunda maganar Rashin ganin gawa akeyi anan.
Cikin qanqanin lokaci hankalin asibitin yatashi sbd dai duk iya bincikensu anyi gawar JJ dai ta Bata Saidai abinda yafi daure musu Kai da mamaki duk security sun tabbatarda Babu gawar da'aka fita da ita Saidai Idan gawar na cikin asibitin a boye kokuwa sai kuwa idan gawar ce tafita da kanta.
Wannan zancen shiya qara hasalta zuciyar Zaki atake yaransa Suka tsare dukkanin qofofin asibitin Babu shiga Babu fita
Nan hankula Suka tashi Dan kuwa Dole hukuma tashigo ciki sbd ganin irin illar da za'ayiwa Wainda basujiba Basu ganiba.
Alee dikko dake zaune cikin lafiyayyen palonsa riqeda tumbler yanashan Champaign hannunsa riqeda wayarsa da AM DILLA wato dansa yakirasa yafada masa halinda ake ciki gashi zancen na neman shiga hannun media Wanda zai iya lalata sunan asibiti bama ita kadaiba zai iya taba asibitocinsa da kamfunan maganinsa Wanda bazai iya daukar hakanba Dole something has to be done.
Zeel dilla dake shigowa palon tareda am cikin wata irin Isa da iko tareda wani irin mulki ta qaraso kujerar gefensa ta zauna cikin kwanciyar hankali tadauki remote tana cewa"
Karka Bata ranka tun yanxu sbd ainihin tension din nazuwa matuqar baka kawarda Zaki a duniyarba gabaki daya.
Miqewa yayi tareda zuba hannayensa a aljihu ransa na qara baci sbd da ace wani ne yau yayi wannan abin ko haka baza'a kawoba baibi gawar dayake nemanba,
Amma Zaki na neman caza masa Kai Wanda yake kawarda hakan Dan kawai Yana buqatar zakin Saidai wannan karon Dole zai dauki mataki duk da Yana tunanin abinda zai faru ranarda Zaki zai gano abinda yake Shirin masa
Amma Dole za'ayi hakan Dan kuwa Babu wata Rai dabaya iya kawarwa akan dukiyarsa daya Tara da abubuwa da yawa matuqar yanada damar iyawa.
Juyowa yayi yakalli am dake faman amsa waya Yana bawa security orders na duk yanda za'ayi ayi kar abari media su fitarda abin nan.
Sake kallon am din yayi Kai tsaye yace"
Kaje asibitin da kanka asan yanda za'ayi ayi a nunawa Zaki cewar JJ bai mutuba ya gudu ne......
Cikin wani irin yanayi zeel ta kallesa tana cewa"
Wat???
Kana tunanin Zaki daqiqi ne kamar qaton danka dake gabanka...
Hade fuska am yayi tareda juyowa zai katseta ta 'daga masa hannu tana cigaba da cewa"
Kana tareda shine Amma kamar idanuwanka sunkasa ganin meyene a a tattaredashi,
Wannan zancen idan ma kayisa kana bude qofofin yaqine dashi Dan kuwa kafi kowa sanin waye JJ agurin Zaki.
Cikin fushi da bacin Rai ya katseta da cewa,
Stop giving me lectures akan yaronda na haifa nesa.,idan kinada wani option akan hakan ne just tell us and stop wasting my time bayan kinsan the power of media.
Miqewa tayi tana kallon cikin idonsa tace"
JJ na hannuna Kuma Yana cikin asibitin and he's alive bai mutuba...
Cikeda baqin ciki dayafi mamakinsa yawa yake kallonta duk da yasan wani lokacin zeel tamafisa sanin hanyoyin Rashin Imani Saidai bayason abinda zai taba sunansa koyayane sbd shine kadai yasan irin abubuwan dayayi kafin yayi sunan.
#MAMUH.*_BURI DAYA na kudine idan ba ki biyaba nemi wainnan numbers din kibiya ki karanta cikin aminci_*
*07067124863*
*08030811300*
*_Mamuhgee13_*
Rintse idanuwansa yayi ya bude cikin wani irin zafi yace"
Kinfi kowa sanin abinda nake iyayi da Wanda zan iya yiwa kowa akan harkar dukiya,meyasa kikeson batamin ayyuka so da dama?
mezakiyi da JJ dakika sa akace ya rasu???
Wat are you planning this time zeell?
Yafada cikin daga murya da bacin rai,
Wat Eva u're planning karki sake ki batamin aiki sbd Zaki is one of the precious abunda bana Wasa dashi Dan kuwa Ina hango wa kaina taskokin nasara da ikon mulki dazanyi amfani dashi nasamu so be very very careful with me.
Daukar wayarsa yayi tareda juyowa ya kalli am dake cikin takaicin abinda ke faruwa Rai bace yace"
Nasan kasan inda takai JJ kuyi gaggawar kashesa ku maida gawar inda take tunda anriga ance ya mutu
Bazan dauki ganganci irin nakuba.
Ficewa palon yayi zuwa samansa Yana sake jin haushin abinda zeel din tayi duk da dai yasan tanada dalilin yin hakan Amma Koma meyene dalilin bayason rasa Zaki yanxu batareda yasamu cimma burikansa akansaba.
Acikin daren am yakira wasu yaransa dake boyayyen gurinda Babu Wanda yasani cikin asibitin yace su shaqawa JJ din phamialiasinon shida 'dayan likita dinda yatayasu aikin sace JJ din su mutu su jefarda gawarsu ko Ina suka samu ciki asibitin su gudu.
Hakan kuwa akayi suna shaqa masa Basu tsaya duba koya mutum ba Suka Shaqawa dr shima atake ya mutu Suka fito tareda cinnawa gurin wuta suka tafiyarsu Saidai suna fitowa yaran Zaki sunga fitarsu Suka bisu nan Suka gudu dayake da baqar mota suke atake suka guje musu.
Ahankali wutar tafara yin yawa hartanayi sama nan aka lurada gobara a dayan bangaren asibitin da ba'a zuwa sbd ko gamasa ba'ayiba.
Atake aka fara Kiran fire Bridget sbd ganin wutar naci sosai.
Koda su nano Suka dawo Suka sanarda Zaki take yagane gawar JJ ce agurin nan hankalinsa yatashi Suka fara kashe wutar yanajin kamar yashiga ciki ya fiddo gawar JJ.
Qurmus wutar ta cinye gurin ba'a samu ciro gawar JJ ba sai asuba inda gawar ta cinye ba'a ganesa gabaki daya ya canxa.
Gawa 'daya Suka gani Suka tabbatar JJ ne kawai kenan aciki suka kunna wutar.
Sabon kukan baqin ciki na zuci Zaki yayi zuciyarsa na daukar radadin Rashin JJ,
Kallon qonanniyar gawar JJ yayi ya rintse idanuwansa dasukai jajir yanajin zafin zuciya Dan kuwa ya tabbatarda wannan kisar wulaqanci ce akayiwa JJ Dan kuwa Dole akwai abinda ke boye tunda aka dauko gawar aka kawo nan aka qona.
Ido jajir yadago yakalli su nanu murya can qasan maqoshi yace"
Ku shigoda mota asa gawar muje da safen nan zamuyi jana'izarsa
Asibitin kuwa duk securitynsu da ma'aikatan dake cikinta ku sauya musu kamanni.
Dan kuwa suka Suka rufe ido Suka hau duka