Showing 6001 words to 9000 words out of 42966 words

Chapter 3 - AUREN FANSA COMPLETE NOVEL

23 Aug 2025

503

koma parlor, Laila ke bata har ta
kammala sannan aka bata ruwa.
A tare suka girka abincin rana inda Laila tayi ma
Zarah wanka, sannan suka dafa fried rice da
papered chicken sai had'ad'en salad. Wuraren
uku da kwata Laila tayi sallama da Bilki ta tafi
gida.
Sai wurin biyar saura sannan Bilki tayi ma
Meenah wanka ta bata abincin rana.
Kamar kullum bayan Alhaji ya dawo gida yayi
wanka yaci abinci, suka zauna palor suna 'yar
fira kafin a kira sallar magrib. Kasancewar
Meenah batasan dawowar Baban nata ba, tana
can d'aki tana wasa. Sai data fito, aiko tana
ganin shi ta rugo da d'an gudunta ta zo kusa da
shi tana fad'in
"Dada!"
Cike da jin dad'i Alhaji yace
"D'iyar Dada ashe ana ciki, zo nan."
Tana zuwa ya d'auke ta ya zaunar kan cinyarsa
yana mata surutu tana dariya. Can kuma sai
tace
"Dada kaga Maama ta bije ni d'azu."
Ya ware idanu
"Me kikayi wa Maama ta bige ki?"
Tayi shiru tana kallonsa can tace
"Bakomai."
Bilki ta taso tana dariya tace
"Kai yaro ma dai daban ne, d'azu ne fa na shiga
wanka nazo na iske ta tana zubar da madara,
shine fa nace mata kar ta k'ara. Alhaji yayi
dariya
"Ah ah Meenah a daina 6arna ba kyau kinji ko?
Idan Maama tace a daina a daina kinji?"
Ta gyad'a kai. Sai kuma yace
"Bilki ya naga Meenah ta rame ne ko bata son
cin abinci?"
Tayi dariya tace
"Ay Alhaji inda kasan yadda nake da fama da
yarinyar nan akan taci abinci ko? Sai kayi
mamaki sam batason ci na rasa dalili."
Yace
"To kuma ya baki sanar dani ba? Muka sani ko
wani abin ke damunta? Kinsan yaro tunda ba
fad'a zatayi ba."
Tace
"To k'ila dai."
Ya juyo da dubansa ga Meenah
"Haba Meenan Dada, meyasa baki cin abinci?"
Nan ma shiru. Yayi murmushi
"Zaki sha ice cream?"
Nan take da washe baki tana murna. Shima yaji
dad'i yace
"Yauwa to bari idan na fita yanzu kafin na dawo
gida zan siyo maki harda biscuit ma."
Saukar da ita yayi daga cinyarsa yace
"Bilki bari na wuce masallaci lokacin sallah yayi
sai na dawo."
Tace
"A dawo lafiya."
Sai da ya fita ta bishi da harara dashi da
Meenah dake tsaye a tsorace gaban Bilki.
Tana huci tace
"Gaskiya abinnan ya fara isa ta, sai wani nan
nan yake da yarinyar nan amma naga ba
ruwanshi ma da Zarah, lallai Alhaji ka haifi d'iya
a cikinka amma ka nuna son d'iyar wata? To da
sake mts."
Daga nan ta shige d'aki, Meenah na tsaye tana
zare idanu.
Haka kuwa akayi Alhaji da zai dawo sai da ya
tsaya ya siya ma Meenah ice cream da biscuit
sai ya k'aro mata kayan lashe lashe na yara.
Zarah kuwa wani d'an abin wasa ne na yara ya
siya mata tunda yasan bata isa shan wad'annan
kayan ba.
Yana dawowa Meenah ta tare shi tana murna,
ya bata ice cream d'inta nan ta zauna ta shanye
tas sannan ya bata biscuit d'inta ta tafi d'aki.
Abin wasan yara ya bama Zarah dake hannunsa
yana mata wasa. Ita kuwa sai dariya takeyi.
Bilki na zaune kusa dasu tana wasa da Zarah.
Can Alhaji yace
"Ina Meenah tayi ne?"
Tayi tsaki a ranta tace
"Yanzu ta tafi d'aki ay ta ga k'wad'ayi kuma
tunda bazata ci abinci ba."
Tashi yayi yana fad'in
"Ina zuwa."
Ta6e baki tayi tana mai jin haushin Meenah.
Yana shiga d'aki ya ishe Meenah kwance k'asa
da biscuit a hannunta bacci ya kwashe ta.
Murmushi yayi ya d'auko ta ya d'ora ta kan
gado, ya gyara mata kwanciya sannan ya kashe
fitilar ya fito.
Koda ya fito Bilki bata nuna komai ba, Zarah ta
k'ar6a tayi d'aki da ita don yi mata wanka.
BAYAN KWANA BIYU
Bilki ta fito wanka da safe kiran Laila ya shigo,
tana d'auka Laila tafara magana
"Kash Hajiya Bilki yanzu naji labarin iyalen Alhaji
Adam sun koma Abuja gaba d'aya."
Da sauri Bilki tace
"Haba dai? To yanzu ya kenan?"
"Bansani ba nima, plan d'inmu ya rushe don
gidansa na Abuja akwai tsaro sosai, ko ina sojoji
ne a gidan."
Bilki tace
"Gaskiya akwai had'ari mu ce zamuyi wani motsi
yanzu. Amma ki bari tukunna a sake shawara."
"To shikenan." Laila tace tare da katse kiran.
Nan tayi ta sak'a da warwara ta rasa mafita.
***
Haka rayuwar ta cigaba da gudana har akayi
shekara d'aya amma har yau sun rasa wata
mafita.
A lokacin kuma Meenah ta shekara biyu harda
rabi Alhaji ya fara shirye shiryen saka ta
makaranta da kuma islamiyya. Don ya fuskanci
zata iya da wuri don a yadda ya fahimce ta, ta
iya saurin d'aukar abu da kuma maganarta ta
fito ga surutu ba abinda bata fad'i.
Sheyasa ma yanzu Bilki ta rage takura mata don
muddin Alhaji ya dawo zata kwashe komai ta
fad'a masa. Tana gudun kar tun baya tunanin
komai har ya fara zarginta...



AUREN FANSA 09
✨⭐✨⭐✨⭐✨⭐✨
⭐🌹🌹🌹⭐🌹🌹🌹⭐
🌹⭐✨⭐🌹⭐✨⭐🌹
🌹✨⭐✨⭐✨⭐✨🌹
✨🌹✨⭐🌞⭐✨🌹✨
⭐✨🌹✨⭐✨🌹✨⭐
✨⭐✨🌹✨🌹✨⭐✨
⭐✨⭐✨🌹✨⭐✨🌟
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
AUREN FANSA!!!
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
🌹Na🌹
🌹MARYAM S BELLO🌹
(MSB)
🌟🌹Pure Moment Of Life Writers🌟🌹
🌹09 🌹
http://MaryamSBello.blogspot.com
Haka kuwa akayi washe gari da safe Hamza da
Bilki suka fita don saka Meenah a makaranta.
Gobarau Academy itace makarantar da suka
nufa, da zuwansu da komai basu wuce minti
talatin ba aka kammala komai aka saka ta Pre
nursery, duba da shekarunta kuma a k'a'idar
makarantar idan yaro bai kai shekara 3 ba to
baza'a saka shi nursery ba daman. Daman 'yan
pre nursery ba'a saka musu uniform.
A ranar aka barta makaranta kuma ko kuka
batayi ba da su Hamza zasu tafi don ta samu
abin wasa sai dad'i takeji.
K'arfe 12 suke tashi don haka dole Bilki ke
d'auko ta don Hamza na wurin aiki lokacin, ba
yadda ta iya haka nan take hak'ura tana d'auko
ta d'in.
Haka rayuwar ta cigaba da gudana cikin hukunci
da hikimar ubangiji, Meenah har ta shiga
nursery. Meenah Allah ya bata k'walwa komai
aka koya mata ta iya sai dai idan ba'a koya
mata ba, kuma idan ta dawo gida ta dinga yi
kenan ko gajiya batayi.
Ba'a saka Zarah makaranta ba sai da Meenah ta
shiga nursery 2 a lokacin ita kuma Zarah tana da
shekara 3 a duniya yayinda Meenah keda hud'u.
Ranar wata juma'a akayi ma su Meenah hutu
suna zuwa gida Meenah ta fara neman babanta
don nuna mai report card nata, sai
dai rashin sa'a yayi tafiya zuwa Lagos a safiyar
ranar, tayi ta kuka tana kiran ita Baba.
Bilki tana tsaki ta ansa report card nata dana
Zarah tana dubawa, abin takaici a wurinta wai
Meenah na d'aya tayi ita kuwa Zarah na ashirin
tayi cikin su ashirin da shidda. Bilki kamar tayi
kuka don takaici. Wato Meenah dai tafi d'iyarta
k'ok'ari kenan?
"Gaskiya da sake!" Ta kalli Meenah tace mata
"Ke! Zo nan!" Meenah tayi tsaye idanunta k'wal
hawaye a duniya tana tsoron Bilki, fizgo ta tayi
da k'arfi.
"Ke dan ubanki sai da kika yi na d'aya wannan
karon ma? Kin manta bugun da nayi maki last
term kenan? Salon kija babanta ya dawo ya
zane Zarah ko? Ke ga mai k'ok'ari ko? Shegiya
mai kama da mage! Wuce ki bani wuri!" Da gudu
Meenah tayi d'aki tana kuka sosai, jawo Zarah
tayi ta rungume tace.
"Don Allah d'iyar Baba ki dage kifi waccan
yarinyar k'ok'ari kinji?" Zarah ta gyad'a kai.
Da rana ta zuba ma Zarah abinci ta shiga
wanka, Meenah na zuwa Zarah tace.
"Zo muci." Ba musu ta zauna suka fara cin
abincin tare.
Ba'a jima ba Bilki ta fito wanka tana lek'owa
taga Meenah nacin abin da d'iyarta abinda ta
tsana! Da tsawa tace
"Ke!" A firgice Meenah ta tashi tana kyarma,
Bilki ta k'ara daka mata tsawa.
"Bana hana ki cin abinci tare da Zarah ba?
Shegiya wuce ki tafi d'aki." Tayi d'aki da gudu a
tsorace. Zarah ta aje cokalin hannunta tace
"Bazan ci ba nima sai da Meenah." Daman Bilki
tasan abinda zatace kenan, tsaki taja tace
"To sai dai kar kici wallahi amma bazakici tare
da Meenah ba, kinji na fad'a miki!"
Aikuwa aje cokalin tayi tana fushi sosai ta bar
parlon. Tsaki Bilki ta k'ara yi tana k'ara jin
haushin Meenah...
***
Sauri yakeyi ya dawo gida don nuna ma iyayensa
result nasa na shedar kammala jss3 nasa. Driver
na yin parking ya fito da gudu yana murna
shigarsa keda wuya ya taradda abinda ya d'aga
masa hankali, ya kuma gigita shi a lokaci guda,
take zuciyarsa ta fara bugawa da sauri a
yayinda k'walwarsa ta tsaya cak! ta bar aiki
lokaci d'aya!!!
Iyayensa ne kwance jina jina, a yayinda wasu
mutane kusan su bakwai ke tsaye cikin
bak'ak'en kaya hartta fuskokinsu an rufe da
black mask!
Tsaye yayi ya kasa tantance a wace duniyar
yake, take kuma ya fashe da kuka yana fad'in.
"Su waye ku? Mey...asa ku...ka kashe min
iyaye?"
Direwa yayi k'asa yana kuka yana jijjiga iyayen
nasa a yayinda yake kiran Anisah! Mutumin yayi
dariya yace.
"Ka bar kuka yaro, sun tafi inda ba'a dawowa
kaima kuma yanzu zaka bisu!" Yakece da dariya
sannan ya saita bindigar daodai saitin k'irjinsa
ya harba.
A gigice ya farka duk da Ac d'in da ke aiki amma
hakan bai hana sa yin sharkaf da zufa ba. Ta6a
jikinsa ya soma yi amma baiga jini ba, ajiyar
zuciya ya sauke ya shiga yin addu'a don ba
k'aramin tsoro yaji ba.
"Wane wane irin mafarki ne haka..... ?"
Ya fad'a yana mai k'ara tunawa da mafarkin da
yayi. Zumbur! Kuma ya mik'e ya fice da gudu
don duba lafiyar iyayensa don gani yake kamar
da gaske ne....!

AUREN FANSA 10
✨⭐✨⭐✨⭐✨⭐✨
⭐🌹🌹🌹⭐🌹🌹🌹⭐
🌹⭐✨⭐🌹⭐✨⭐🌹
🌹✨⭐✨⭐✨⭐✨🌹
✨🌹✨⭐🌞⭐✨🌹✨
⭐✨🌹✨⭐✨🌹✨⭐
✨⭐✨🌹✨🌹✨⭐✨
⭐✨⭐✨🌹✨⭐✨🌟
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
AUREN FANSA!!!
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
🌹Na🌹
🌹MARYAM S BELLO🌹
(MSB)
🌟🌹Pure Moment Of Life Writers🌟🌹
🌹10 🌹
http://MaryamSBello.blogspot.com
"Mummy...! Mu.." A firgice suka farka daga
bacci, da mamaki suka ce
"Waye?" Kasancewar d'akin gauraye yake da
duhu fitila a kashe take, Daddy ya kai hannunsa
ya kunna bedside lamp yana kallon Faruk dake
tsaye, da sauri Faruk ya rungume mahaifiyar
tasa yace.
"Alhamdulillah! Ashe duk lafiyarku lau, wallahi
naji tsoro."
Mummy tayi murmushi don tasan ya k'ara yin
mafarki. Tace
"Faruk nasha fad'a maka mafarki ba gaskiya
bane ka daina d'aga hankalinka akan mafarki,
nasha fad'a maka bakaji."
Faruk yace
"Nasani Mummy amma meyasa a duk lokacin da
nayi mummunan mafarki sai naji gabana ya
fad'i, sannan na kasa samun nutsuwa, gani nake
kamar wani abu na shirin faruwa da mu!"
Daddy yace
"Haba Faruk! Ka zamo mai tawwakali mana, an
fad'a maka mafarki ba gaskiya bane haba! Tashi
kaje ka kwanta."
Sum sum ya tashi ya fice, Daddy ya kalli
Reemah yace.
"Wai shin kuwa yaron nan na addu'a a duk
lokacin da zai kwanta bacci?"
Reemah tace
"Yana yi, kullum sai na je na tabbatar da sai
sunyi addu'a kafin su kwanta su duka."
Daddy ya numfasa yace
"To Allah ya kyauta amma sai ya k'ara dagewa
da addu'a sosai."
Reemah tace
"Insha Allah."
***
BAYAN WATA D'AYA
Zaune yake yana karatu wayarsa ta fara k'ara,
ganin sunan Daddynsa yasa yayi saurin
d'agawa.
"Hello kaine Faruk?"
Yace
"Eh nine lafiya ina mai wayar nan?"
"Sai dai kayi hak'uri mai wayar nan ya rasu
dashi da matarsa!"
"What? Innalillahi wa'inna ilahir raj'un!"
"Ya Faruk!"
A firgice ya farka ganin Anisha tsaye gabansa
tana kakkarwa, yasa yace
"Ke lafiya menene?"
Ta fashe da kuka.
"Mummy! Ya Faruk Daddy da Mummy babu."
Yace
"Kamar ya? Ina suke?"
Tace
"Wasu mutane na nan sun zagaye Mummy da
Daddy..."
Kafin ta k'arasa ya mik'e da gudu ya fita."
Zuwansa keda wuya ya taradda abinda ya d'aga
masa hankali lokaci guda kuma ya gigice ya
shiga rud'ani! Murza idanunsa ya fara yi don
yayi tunanin wannna karon ma mafarki yakeyi,
la6ewa ya shiga yi a bakin k'ofa yana sauraren
mutanen da ke tsaye. Kusan su hud'u majiya
k'arfi.
"Hello Hajiya Laila Sunusi! Aikin da kika samu fa
an kammala abu biyu ya rage. Na farko bamuga
yaransu guda biyu da kika lissafa mana ba! Na
biyu takardun gidannan da sauran mahimman
takardun da kika ce a baki."
"Yes Ma! Ok Ma! Insha Allah na miki alk'awarin
cika miki dukkan aikin da kika
samu da ke da aminiyarki ya sunan ta ma?
Haha yes Bilkisu Ringim! Ok..."
Kamo hannun Anisah yayi yana kuka d'akinsa ya
fad'a ya kwashi wasu takardu nasa dashi dana
Anisah na makarantarsa da abubuwan da yake
buk'ata ya jefa jikka suka fito da sauri sukayi
hanyar fita. Anisah na kuka shima yana kuka
suka fito gate, gaba d'aya masu gadinsu basu
nan, security sunfi goma amma yanzu bai ga
kowa ba. Adaidaita ya samu suka wuce wata
police station, yana zuwa ya fad'a masa dukkan
abinda ya gani ya kuma ji sannan yace suzo su
ceci iyayensa kafin su mutu.
Ba 6ata lokaci suka nufo gidan sai dai da
zuwansu abin mamaki ba komai gidan asali ma
gidan a rufe yake da kwad'o sai dai gawar
iyayensa, nan akayi examining d'insu aka
tabbatar da basuda rai, take Faruk ya rasa a
wace duniyar yake, kansa yayi dip, hawaye kuwa
kamar an bud'e pampo. Sambatu kawai yakeyi
yana fad'in.
"Daman nasha yin mafarki an kashe mana iyaye!
Nace abin kamar zai faru amma ba wanda ya
kula ni..."
Duk police d'in da yayi yunk'urin tab'asa da
niyyar rarrashi turesu yakeyi suna fad'uwa k'asa,
gaba d'aya kamar ya zauce. Yama k'i nutsuwa
asan ina danginsa suke a sanar masu de abinda
ya faru. Gaba d'aya gidan ba mota ko d'aya,
motocin mahaifinsa sunfi kala takwas amma
yanzu ko d'aya babu.
Nan kuma kan Faruk ya fara juyawa kafin ya
ankara ya fad'i k'asa tim!
AUREN FANSA 11
✨⭐✨⭐✨⭐✨⭐✨
⭐🌹🌹🌹⭐🌹🌹🌹⭐
🌹⭐✨⭐🌹⭐✨⭐🌹
🌹✨⭐✨⭐✨⭐✨🌹
✨🌹✨⭐🌞⭐✨🌹✨
⭐✨🌹✨⭐✨🌹✨⭐
✨⭐✨🌹✨🌹✨⭐✨
⭐✨⭐✨🌹✨⭐✨🌟
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
AUREN FANSA!!!
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
🌹Na🌹
🌹MARYAM S BELLO🌹
(MSB)
🌟🌹Pure Moment Of Life Writers🌟🌹
🌹11 🌹
http://MaryamSBello.blogspot.com
A hankali ya bud'e idanunsa bakinsa d'auke da
salati, sai kuma ya fara kiran
"Mummy! Daddy! Wai da gaske ne an kashe su?
Ina Anisah? Wallahi duk wanda ya kashe min
iyaye sai na rama masu koma waye..."
"Alhamdulillah kunga ya farka ma ashe! Sannu
ya jikin?"
Kallon likitan yakeyi kafin kuma ya fashe da kuka
sosai. Da k'yar aka rarrashe shi, sannan likitan
ya zauna kusa da gadon da yake kwance tare da
dafa sa.
"Faruk, hak'uri zakayi iyayenka sun riga sun
rasu, kukanka bazai ta6a maido su ba, yanzu
addu'arka ita kad'ai suke buk'ata, kayi hak'uri
kaganni nan na maka alk'awari k'wato maka
'yancika a gurin azzaluman da suka aikata maka
wannan mummunan aikin, kar ka d'aga
hankalinka kaji ko?"
Ya share hawayensa
"Nasani doctor, iyayena basa buk'atar kukana
amma kuma ya zama dole nayi kuka, ba wanda
zai gane abinda nakeji a zuciyata abin yana min
ciwo, zuciyata tana min zafi, iyayena sune komai
na, banida kowa a garinnan sai su, don haka
dole nayi kuka saboda na rasa komai na rayuwa,
na rasa iyayena, sannan na rasa gidanmu da
dukiyar mahaifina..."
Kuka yaci k'arfinsa. Doctor ya numfasa
"Faruk kaganni sunana Dictor Ishaq Aliyu, ni d'an
garinnan ne, daga yau na maka alk'awarin
taimaka maka har sai ka samu ingantacciyar
rayuwa da kai da k'anwarka, inada mata d'aya
da yara hud'u, maza na guda biyu sai mata biyu,
kar ka damu bazakayi maraici ba Indai kana tare
dani don haka ka bar kuka ka share
hawayenka."
Faruk ya kalleshi da mamaki yace
"Da gaske doctor? Zaka taimaka min duk da
baka san koni waye ba?"
Likitan ya gyad'a kai
"Zan taimaka maka kuma zan taya ki fighting
battle d'innan har sai kayi nasara, yanzu kaga
kwananka hud'a a nan asibitin, kana buk'atar
muje gida ka huta."
Faruk yace
"Nagode doctor! Nagode Allah ya saka da
alkhairi! Ya k'ara budi."
Likitan yayi murmushin jin dad'i yace
"Amin Faruk mu tafi ko?"
Yace
"Eh, amma ina Anisah?"
Likita yayi murmushi.
"Gata can office d'ina tana bacci muje mu d'auke
ta sai mu wuce."
Ba'a d'auki lokaci ba suka iso gidan Doctor
Ishaq, gida ne tangameme na gani na fad'a da
ke Maitama, lallai shima doctor Ishaq
mahashuk'in mai kud'i ne.
Shi ya jagorance su har cikin gidan, suna shiga
wata mata dattijuwa ta fito da murmushi a
saman fuskanta.
"Sannu da zuwa Alhaji."
Ta fad'a tana k'ok'arin amsar jakarsa dake
rataye a kafad'arsa.
"Yauwa sannu da gida Malama Rukayya."
Tayi murmushi. "Ahh bak'i mukayi kenan,
sannunku da zuwa ku shigo mana."
Suka shiga suka zazzauna kan kujera.
Alhaji ya fara magana, ga yara nan, ki shiga
dasu ciki suyi wanka ki basu abinci akwai
maganar da zamuyi da ke bayan nan."
Tace
"To Alhaji."
Ta tashi sannan su Faruk suka bi bayanta. Wani
d'aki suka nufa daga gani na yaranta ne mazan,
tace ma Faruk ya shiga yayi wanka, sannan ta
fiddo masa kayan da zai saka. Hannun Anisah
taja, ta mata wanka ta saka mata kaya masu
kyau.
Kan dinning taja su ta zuba masu abinci suka ci
sosai sannan suka wuce parlor inda Alhajin ke
zaune da alama abinci ya gama ci.
Bayan sun zauna Alhajin ya fara magana.
"Ina su Yazeed?"
Tace
"Suna can waje suna buga ball."
Yace
"Jeki kirawo man su gaba d'ayansu."
Da girmamawa ta amsa ta fice.
Can sai gata yaran na biye da ita a baya.
"Dada welcome." Suka fad'a gaba d'aya.
Yace
"Thanks, ku zauna." Duk suka zauna, nan kuma
suka hau kallon su Faruk. Alhaji ya numfasa ya
fara magana.
"Hajiya kinga wad'annan yaran guda biyu?"
Tace
"Eh nagansu."
Yace
"Yauwa, wannan shine Faruk sai ga k'anwarsa
nan Anisah, shine yaron da nake kula dashi a
asibiti bayan rasuwar iyayensa."
Tace
"Allah sarki sune yaran kenan? Allah ya jik'ansu
da rahama."
Yace "Amin, so nake mu cigaba da rik'esu a
matsayin iyayensu, na farko kinga marayu ne
gasu yara k'anana, na biyu duk wanda ya
taimaki wani Allah zai taimake shi. Yara ne
kuma marayu, basuda kowa sai Allah, shine na
ga dacewa in d'auko su in rik'e don samun lada,
ko ya kika ce?"
Ta numfasa.
"Haka ne Alhaji, wallahi wannan ba wani abu
bane, insha Allah zan rik'e su a matsayin uwa a
garesu, Allah ya bamu ikon rik'e amana."
Yace
"Amin, Faruk wad'annan k'annenka ne gasu nan,
kaga wannan shine babba mai suna Yazeed,
shekarsa sha biyar sai mai bi masa Hauwa'u ana
kiranta Jidda shekararta Sha hud'u, sai k'aninta
Nabeel shi yakeda da sha biyu sai auta gata nan
Yusra ita keda shidda, don haka kuna jina
wannan 'yan uwanku ne ban yarda wani ya nuna
musu wariya ba a cikinku, kuna jina?"
Suka ce
"To Dada."
Alhaji yayi murmushi
"Faruk ga kannenka nan sai kuje kuyi wasa ko?"
Faruk yayi murmushi inda gaba d'aya suka mik'e
suka fice.
Alhaji ya ce
"Allah ya bamu ikon rik'e su amana, ya tona
asirin azzaulumai."
Tace
"Amin ya Allah Alhaji, yaran sun bani tausayi
wallahi, Allah ya bi musu hakk'insu."
Yace
"Amin amin, anjima zanje inyi magana da
manyan lauyoyin da na sani, asan me za'ayi a
kai."
Tace
"Hakan yayi daidai, yanzu makarantarsu fa?"
Yace
"Makarantarsu ba matsala bace na d'auki
nauyin karatunsu, yanzu ayi k'ok'ari a saka su
makarantarsu Yazeed."
Tace
"Haka yayi daidai, Allah ya k'ara bud'i."
Yace
"Amin Amin, bari inje in d'an kwanta kafin
anjima zan koma asibiti."
Tare suka mik'e ya fice tabi bayansa.

(MSB)
🌟🌹Pure Moment Of Life Writers🌟🌹
🌹12 🌹
http://MaryamSBello.blogspot.com
***
Washe gari aka saka su makaranta. Yanzu
abubuwan sun ma Faruk sauk'i tunda yanzu
gidan da suke basuda matsala, daidai
gwargwado suna samun kulawa sosai, sai dai
har yau hoton gawar iyayensa ya kasa 6ace
masa kai, ko rufe ido yayi sai ya gansu ya kuma
ga mutanen da suka kashe su, sannan sunayen
da aka ambata har yanzu ya kasa mantawa
hasali ma ya samu diary nasa ya rubuta
sunanayen nasu.
Ya samu shak'uwa mai k'arfi tsakaninsa da su
Yazeed komai a tare sukeyi su uku abin sha'awa
sun had'e kansu. Duk inda kaga d'aya to zakaga
d'ayan. Haka ma Anisah da Yusra sun zama
k'awaye, ita Jidda ta girmesu don haka sai dai
sama sama suke shiri, daga gaisuwa sai kuma
cin abinci ke had'a su. Duk da k'arancin
shekarun Anisah ta fuskanci Jidda nada wuyar
sha'ani sannan miskila ce ta k'arshe, sai dai
akwai kuma kirki halayen nata dai gasu nan a
baibai, mutum ce mai wuyar fassara, sheyasa ta
lura yaran gidan basu shiga harkarta, don haka
itama sai tayi baya baya kad'an.
Har yau Anisah ta kasa gane iyayensu sun mutu
har abada bazasu dawo ba, don kusan kullum
sai ta tambaya. Meyasa suka dawo nan da
zama, ina Daddy da Mummy? Yaushe zasu
dawo? Haka take tasa Faruk gaba da ire iren
wad'annan tambayoyin har idan ya rasa amsa
sai tasa masa kuka, dole sai dai yace sunyi
tafiya mai nisa kuma zasu dad'e basu dawo ba.
To tun wata rana da abin ya fara isarsa ya daka
mata tsawa yace tayi hak'uri Mummy da Daddy
basu dawowa, da farko ta tsorata amma da
Faruk ya zauna yayi mata bayani sai kuma ta
fahima, ya kuma d'ora da cewa ta dinga yi musu
addu'a kullum, aikuwa tun daga ranar bata k'ara
tambayarsu ba haka ma da ta motsa sai tayi
musu addu'a.
***
BAYAN WANI LOKACI...
Zaune suke kan dinning suna breakfast gaba
d'ayansu, Dada ne ya aje cokalin hannunsa ya
soma magana.
"Wai ina Faruk ne?"
Hajiya Rukayya da suke kira da Mama tace
"Inaga yana ciki kamar wanka ya fito."
Sanye yake cikin bak'in wando wulik pencil
trowser sai ya d'ora ash shirt marar hannu, tun
daga k'afafuwansa ya isa ka gane cewa
kyakkyawan mutum ne, don kuwa

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login