Showing 42001 words to 42966 words out of 42966 words
dad'e yana
shayar da ita zuma kafin kuma suyi bacci mai
dad'i.
Washe gari ya fara shirin tafiya, kafin ya tafi sai
da ya nemo mata wata mata dattijuwa da zata
zauna da ita har ya dawo, haka suna ji suna
gani sukayi bankwana har airport ta kaishi, sai
data ga tashin jirginsu sannan ta dawo zuciyarta
na k'una ta rasa meke mata dad'i.
Haka ta kwana tunaninsa har ciwon kai ya
sauko mata wanda kafin safe zazza6i mai zafi
ya rufe ta, sai da tayi ta shan magaunguna
sannan ta samu taji sauk'i.
Shi kuwa gogan naka yana sauka masaukinsa
dama ya siya sabon sim, yana sawa ya kirata,
bugu biyu ta d'auka.
"Hello."
"Baby ya nake jin muryarki can k'asa ko jikin
ne?"
Ta lumshe idanu tace
"Eh to zazza6i ne yake d'an damuna amma da
sauk'i."
Ya rude ya shiga mata tambayoyi.
"Kinsha magani? Yanzu meke miki ciwo? Ya kike
ji yanzu?"
Tayi murmushi
"Wallahi yanzu kam bana jin komai sai kasala,
so ya hanya? Ya kuma gajiya?"
Yace
"Alhamdulillah, gani nan na sauka masaukina
yanzu zanyi wanka sai na kwanta na huta."
Tace
"Ai gara kayi bacci kam, sannu."
Yace
"Yauwa baby, kema sannu."
Sun dad'e suna fira kafin suyi sallama, kowane
yana jin kewar d'an uwansa.
Meenah ta cigaba da karatunta cikin kwanciyar
hankali, kullum cikin missing Faruk takeyi sai dai
kullum suna mak'ale a waya suna fira basa
gajiya da junansu.
Sun cigaba da zumuncinsu itada Zarah kusan
kullum suna ziyartar juna, haka ma Anisah wacce
ke fama da tsohon ciki itama tana k'ok'ari wajen
ganin tana zumunci dasu Meenah.
****
BAYAN WATA BAKWAI
Meenah na zaune a parlor tana cin guava kamar
a mafarki taji horn, ta yunk'ura da k'yar ta lek'a
ta window ganin motar haya ya sanya ta fara
mamakin ko waye?
Bata gama mamaki ba sai data ga ana fiffido da
akwatina daga boot, gabanta ya fad'i batayi
tsammanin ganinsa yanzu ba, yayi wani kyau
yayi k'iba sai k'yallin hutu yakeyi. Ga k'asumbar
nan tasha gyara sai walk'iya takeyi.
Ta lalla6a ta fito bakin k'ofa daidai nan ya
k'araso yana murmushi, take ya ware
hannuwansa duka biyun alamun ta iso gareshi.
Ta dafe cikinta daya turo gaba tare da sunkuyar
da kanta k'asa, yayi murmushi tare da takowa
daf da ita sannan ya rungume abarsa tsam tsam
kamar za'a k'wace masa ita don ma tulelen
cikinta ya hana shi ya rik'e ta sosai.
Ya sumbace ta a goshi yana dubanta yace
"Wow! Baby cikinnan fa yayi miki kyau sosai."
Ya k'arasa yana kashe mata ido d'aya, tayi
murmushi, ta zum6uro baki cikin shagwa6a tace
"Shine zaka taho ban sani ba?"
Yayi dariya
"I'm sorry baby, just wanted to surprise you
daman."
Hannunta ya rik'o suka k'arasa ciki, ta taimaka
masa ya rage kayan jikinsa yana ta zolayarta
wai yanzu ta zama k'atuwa ko tafiya da k'yar
takeyi, ita dai sai dariya takeyi. Bayan ya huta
kuma ya shiga bubbud'e akwatina yana fiddo
mata tsarabarta, kaya ne mak'il akwati guda na
kayan baby wanda babu abinda babu a ciki, kaya
masu kyau da tsada, sai akwati guda nata
wanda ya k'unshi leshi, atamfa da su kayan
bacci da kayan kwalliya da sauransu, tayi murna
tayi ta masa godiya ba adadi.
A ranar dukkansu sunyi kwanan farin ciki da
kuma kewar juna.
Washe gari sai ga Jidda itama ta warke ras,
tazo neman gafara kuma duk sun yafe mata,
tace ta samu mijin aure, sun taya ta murna da
fatan alkhairi inda har Faruk yayi mata
alk'awarin bata tasa gudumuwar.
A kwana a tashi ba wuya wurin Allah yau Allah
ya sauki Meenah da misalin k'arfe biyu na dare,
Faruk yana tare da ita har ta haifi santalelen
d'anta k'ato mai k'oshin lafiya, bayan an gyare
shi tas aka mik'a ma Faruk shi sai kallonsa
yakeyi cike da sha'awa, ya sumbati kumatun
Meenah yace
"Wane suna zamu sa masa?"
Tayi murmushi tace
"Duk sunan da kaga ya dace dashi ka sa masa."
Yayi masa hud'uba da sunan mahaifinsa wato
Adam amma za'a ringa kiransa da Khalifa.
Ranar suna anyi taron suna lafiya kuma ya
k'ayatar mai jego tayi fes da ita tana sanye cikin
wani golden lace sai k'yalli takeyi kamar wata
amarya.
Mai jego da d'anta sun cigaba da samu kulawa
sosai a wurin Faruk, ga yalwatar arzik'i
musamman da akayi masa k'arin girma kud'i
sun zauna masa sosai, hakan yasa Meenah ta
bashi shawarar ya gina masallaci ya kuma ringa
bada tallafi a gidan marayu, ba k'aramin dad'i
shawarar nan tayi masa ba, yayi tasa mata
albarka yana jin dad'i.
A haka har sukayi arba'in inda ta cigaba da
karatunta a lokacin ne kuma ita Zarah ta haifi
d'iyarta mace sun sha suna babyn taci sunan
mahaifiyar Nabeel wato Sadiya, za'a ringa ce
mata Nasreen.
A yanzu su Meenah har sun kammala karatunsu
suna jiran result.
****
Zaune take tana shayar da Khalifah Faruk ya fito
daga d'aki da alama bacci ya tashi, yana zuwa
ya rank'wafo yana sumbatar kanta, yace
"Zo muje na baki wani abu."
Ta mak'ale kafad'a alamun a'a tace
"Nak'i wayon, nasan dalilin da yasa ka kirani."
Yayi murmushi yace
"A'a fa result d'inki zan nuna miki."
Da sauri ta aje Khalifah ta mik'e tsaye tana
murmushi tace
"Da gaske? Mu je nagani."
Ya wuce tabi bayansa suna shiga yasa ma k'ofar
key yana dariya k'asa k'asa, tace
"La daman wayau zakayi min ko? Ni gaskiya ka
bud'e min na fita."
Yace
"Nak'i, ga key d'in zoki k'wata."
Ta nufo sa ta fara k'ok'arin k'wace key d'in
aikuwa ya damk'e ta yace
"Wana kama?"
Ta fara kukan shagwa6a tana fad'in.
"Wayyo my soul, mun bar Khalifah shi kada'ai a
parlor fa kar yayi kuka."
Yace
"To tsaya mu nema masa k'anwa sai ki tafi."
Tace
"Nidai a'a."
Yace
"Aiko baki isa ba."
Ya fara k'ok'arin zage mata zip da k'yar tayi
nasarar k'wace kanta tana ta faman dariya sosai
sannan ta d'auki pillow ta jefe shi da shi har
yanzu bata bar dariya ba. Nufo ta yayi ya chafke
ta yace
"Zan baki punishment, kina jifan mijinki."
Kafin tayi magana ya had'a bakinsa na nata....
ALHAMDULILLAH!!!
Alhamdulillah da Allah ya nuna min farkon book
d'innan da k'arshensa lafiya! Darasin dake ciki
Allah ya bamu ikon d'auka, kuskuren da ke ciki
Allah ya ka yafe mana.
Godiya ta musamman ga dukkanin masoya na
da wanda na sani da wanda bansani ba kusani a
duk inda kuke ina k'aunarku.
Fatan alkhairi ga duk wani mai karanta novel
d'ina, Allah ya bar zumunci Amin.
Daga k'arshe ina mai bak'in ðŸ˜ðŸ˜cikin sanar da
masoya na cewar zan dakatar da rubuta ðŸ˜ðŸ˜ðŸ˜novel
zuwa wani lokaci bisa wasu dalilai wanda basai
na fad'e su ba da fatan masoya na zasuyi min
uzuri zasu kuma fahimce ni, nagode da k'aunar
da kuke nuna mun nima kusani ina k'aunar ku a
duk inda kuke.😘