Showing 30001 words to 33000 words out of 42966 words
suka
shaida auren Jidda da Faruk sai Zarah da
Khaleel.
Dad'i Meenah takeji Zarah kusa da su za'a kawo
ta, bayan an gama aka zarce 'yar walima da
Faruk ya had'a masu.
****
Tana zaune kan gado taji ana maganar an
d'aura aure, haba kanta ya k'ara girma ji take
kamar a mafarki, mutumin da take ganin shine
class d'inta yau ta malleke shi a matsayin miji,
wani murmushi tayi tare da lumshe idanu, Luby
ta daka mata duka a baya tace
"Banza keda wa kike murmushi ke kad'ai?"
Ta dube ta tace
"Ina tunani gami da yin mamaki wai yau nice na
zama matar ya Faruk ya zama mallakina fa
kenan?"
Luby tace
"Ke ni ba wannan ba, kinsan mutumin nan yana
da mata, kuma kinsan yadda yake k'aunar ta
kawai suddabarunki ne yake aiki, baki gudun
maganin ya bar aiki mu shiga uku mu lalace? Ke
nifa na fara ji miki tsoro kar ya wulak'anta ki,
sannan yasan babu, baki gudun labari yasha
banbam?"
Ras ras! Gabanta ya yanke ya fad'i tace
"Haka ne fa, ko da yake ay kin min tanadi mai
kyau kar kiji komai."
Luby tace
"Keni sheyasa nake son auren yaro wanda
baisan dawon garin ba, amma masu mata ay
sun san komai."
Haka aka cigaba da shagalin biki, jikin Jidda yayi
mugun sanyi saboda gudun abinda zaije ya
dawo tsakaninta da angonta.
K'arfe tara da rabi motoci suka soma layi a
k'ofar gidan su amarya, bayan fad'a da nasihohi
daga Mama da Dada har Faruk sai da yasha
fad'a sosai da nasiha.
Uwar gida kan gida Meenah tana zaune a
d'akinta ta ci ado tsayawa fad'ar kwalliyarta ma
6ata baki ne. Gud'a ta matan da suka rako
amarya itace ta fara yo sallama, Meenah ta
danne kishinta sosai ta k'ak'alo murmushin dole,
amarya tana rik'e a hannun wata mata.
Kansu tsaye d'akin amarya suka nufa, 'yan kawo
amarya, k'ofa ce kawai zatayi linking d'inka
zuwa d'ayan 6angaren na sashen Jidda.
Masu kawo amarya suka shiga zagaye gidan don
kashe kwarkwartar ido. Suka gama kallon komai
sukayi niyyar tafiya gida.
Washe gari akayi walima k'arfe biyar na yamma
Hajiya Lami ta rik'o hannun Jidda ta nufi parlon
Meenah, sukayi sallama Meenah ta amsa. Hajiya
Lami ta ce
"To ga amarya nan don Allah ku had'a kanku ku
zauna lafiya, yanzu an bar haukan kishin nan
zaman lafiya shi kowa ke buk'ata.
Tayi murmushi
"To Allah ya taya mu rik'o."
Suka tashi suka maida amarya d'akinta bayan
iyayen sun kama gabansu, d'akin ya rage daga
amarya sai 'yan matanta wad'anda ke zaman
jiran ango.
Luby tace
"Kar fa kiganta kamar mutuniyar kirki ki raga
mata, idan tace miki kul ki ce mata cas cas!
Kinji na fad'a miki."
Nan sukayi ta zuga ta har akayi isha'i.
K'arfe takwas, tara, goma, shiru ba ango ba
alamunshi, har dai sha d'aya ta wuce
Luby tace
"Nidai zan tafi gida na gaji da jiran ango."
Haka suka tarkata suka tafi, Sai dai ta dinga
binsu da ido don batada bakin magana da kuma
tana son jin dalilin rashin zuwan ango duk da
tanadin da tayi masa, haushi kamar zai kashe
ta.
"Kar dai yana wurin waccan tsinanniyar?"
Gabanta ya fad'i, ta hau sak'e sak'e, tayi ta
kiransa yana rejecting, daga k'arshe ya tura
mata sak'o kamar haka:
"Kiyi hak'uri ki bar kirana yau bazan shigo
wurinki ba."
Ta rud'e ta gigice gashi maganin idan aka wuce
yau shikenan ya kare!
Ta hau salati tana cigaba da kiransa amma ina
sai ma ta kira taji ta a kashe.
Safa da marwa takeyi daga k'ofa zuwa gado,
tana tunainin mafita a gareta, don akwai had'ari
muddin ango baizo gareta ba a daren yau ba!
AUREN FANSA 36
✨⭐✨⭐✨⭐✨⭐✨
⭐🌹🌹🌹⭐🌹🌹🌹⭐
🌹⭐✨⭐🌹⭐✨⭐🌹
🌹✨⭐✨⭐✨⭐✨🌹
✨🌹✨⭐🌞⭐✨🌹✨
⭐✨🌹✨⭐✨🌹✨⭐
✨⭐✨🌹✨🌹✨⭐✨
⭐✨⭐✨🌹✨⭐✨🌟
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
AUREN FANSA!!!
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
🌹Na🌹
🌹MARYAM S BELLO🌹
(MSB)
PURE MOMENT OF LIFE WRITERS
_We don't just entertain and educate, we touch
the heart of readers_
P.M.L
🌹35 🌹
http://MaryamSBello.blogspot.com
Washe gari aka kai lefen Zarah akwati bakwai da
kit, yayinda aka kai ma Jidda akwati takwas da
kit.
An fara gudanar da shagalin biki a wadace, sai
dai matsalar Jidda d'aya da ta masa maganar
kud'i sai sunyi fad'a, sannan idan har suna tare
yana nuna mata so da k'auna marar iyaka
amma da zarar sun rabu shikenan ko kiranta
baiyi sai dai ita ta kirasa. Hankalinta ya fara
tashi haka kuma ta soma tunanin ko maganin ya
fara dena aiki ne?
Ranar da akeyin event d'in Jidda anyi kwalliya ta
gogaggun 'yan matan nan, ta had'u har ta gaji
duk da ba wani kyau gareta na azo a gani ba.
'Yan matanta kansu da ka kallesu kaga
gagaggun 'yan mata masu ji da kansu, Luby best
friend d'in amarya ita nata ashobin ya banbanta
da na sauran ya kuma fi tsada da kyau.
Suma kuwa su Zarah na can suna shan tasu
hidimar, da yake bazasuyi abubuwa da yawa ba,
kuma bikin nasu yafi tsari da kyau.
K'arfe biyar da rabi Faruk ya iso ya kira wayar
Jidda, can sai ga ta fito itada k'awayenta su da
yawa kamar wata tawaga.
Bayan sun iso aka fara gabatar da events cike
da kwanciyar hankalin, Luby ita ta fara bud'e
wurin da rawa yadda kasan ba kowa wurin haka
take tik'ar rawa ba ko kunya.
An gayyato amarya da ango don taka rawa, shi
kam ango kunya ta hana shi rawa sosai ba, ita
kuwa amarya bako kunya sai wani rausaya
takeyi kamar ba amarya ba. Faruk sai yanzu
yake k'ara gane halin Jidda, bai ta6a tunanin
haka take ba. Sai yanzu ya fara tunanin aurensu
shida Meenah komai cikin tsari haka akayi shi.
K'arfe sha d'aya aka tashi taron, ya ajiye Jidda
gida shima ya nufi nasa gidan.
Washe gari ya tashi yana ta hidimar d'aurin
aure. K'arfe biyu daidai dubban mutane suka
shaida auren Jidda da Faruk sai Zarah da
Khaleel.
Dad'i Meenah takeji Zarah kusa da su za'a kawo
ta, bayan an gama aka zarce 'yar walima da
Faruk ya had'a masu.
****
Tana zaune kan gado taji ana maganar an
d'aura aure, haba kanta ya k'ara girma ji take
kamar a mafarki, mutumin da take ganin shine
class d'inta yau ta malleke shi a matsayin miji,
wani murmushi tayi tare da lumshe idanu, Luby
ta daka mata duka a baya tace
"Banza keda wa kike murmushi ke kad'ai?"
Ta dube ta tace
"Ina tunani gami da yin mamaki wai yau nice na
zama matar ya Faruk ya zama mallakina fa
kenan?"
Luby tace
"Ke ni ba wannan ba, kinsan mutumin nan yana
da mata, kuma kinsan yadda yake k'aunar ta
kawai suddabarunki ne yake aiki, baki gudun
maganin ya bar aiki mu shiga uku mu lalace? Ke
nifa na fara ji miki tsoro kar ya wulak'anta ki,
sannan yasan babu, baki gudun labari yasha
banbam?"
Ras ras! Gabanta ya yanke ya fad'i tace
"Haka ne fa, ko da yake ay kin min tanadi mai
kyau kar kiji komai."
Luby tace
"Keni sheyasa nake son auren yaro wanda
baisan dawon garin ba, amma masu mata ay
sun san komai."
Haka aka cigaba da shagalin biki, jikin Jidda yayi
mugun sanyi saboda gudun abinda zaije ya
dawo tsakaninta da angonta.
K'arfe tara da rabi motoci suka soma layi a
k'ofar gidan su amarya, bayan fad'a da nasihohi
daga Mama da Dada har Faruk sai da yasha
fad'a sosai da nasiha.
Uwar gida kan gida Meenah tana zaune a
d'akinta ta ci ado tsayawa fad'ar kwalliyarta ma
6ata baki ne. Gud'a ta matan da suka rako
amarya itace ta fara yo sallama, Meenah ta
danne kishinta sosai ta k'ak'alo murmushin dole,
amarya tana rik'e a hannun wata mata.
Kansu tsaye d'akin amarya suka nufa, 'yan kawo
amarya, k'ofa ce kawai zatayi linking d'inka
zuwa d'ayan 6angaren na sashen Jidda.
Masu kawo amarya suka shiga zagaye gidan don
kashe kwarkwartar ido. Suka gama kallon komai
sukayi niyyar tafiya gida.
Washe gari akayi walima k'arfe biyar na yamma
Hajiya Lami ta rik'o hannun Jidda ta nufi parlon
Meenah, sukayi sallama Meenah ta amsa. Hajiya
Lami ta ce
"To ga amarya nan don Allah ku had'a kanku ku
zauna lafiya, yanzu an bar haukan kishin nan
zaman lafiya shi kowa ke buk'ata.
Tayi murmushi
"To Allah ya taya mu rik'o."
Suka tashi suka maida amarya d'akinta bayan
iyayen sun kama gabansu, d'akin ya rage daga
amarya sai 'yan matanta wad'anda ke zaman
jiran ango.
Luby tace
"Kar fa kiganta kamar mutuniyar kirki ki raga
mata, idan tace miki kul ki ce mata cas cas!
Kinji na fad'a miki."
Nan sukayi ta zuga ta har akayi isha'i.
K'arfe takwas, tara, goma, shiru ba ango ba
alamunshi, har dai sha d'aya ta wuce
Luby tace
"Nidai zan tafi gida na gaji da jiran ango."
Haka suka tarkata suka tafi, Sai dai ta dinga
binsu da ido don batada bakin magana da kuma
tana son jin dalilin rashin zuwan ango duk da
tanadin da tayi masa, haushi kamar zai kashe
ta.
"Kar dai yana wurin waccan tsinanniyar?"
Gabanta ya fad'i, ta hau sak'e sak'e, tayi ta
kiransa yana rejecting, daga k'arshe ya tura
mata sak'o kamar haka:
"Kiyi hak'uri ki bar kirana yau bazan shigo
wurinki ba."
Ta rud'e ta gigice gashi maganin idan aka wuce
yau shikenan ya kare!
Ta hau salati tana cigaba da kiransa amma ina
sai ma ta kira taji ta a kashe.
Safa da marwa takeyi daga k'ofa zuwa gado,
tana tunainin mafita a gareta, don akwai had'ari
muddin ango baizo gareta ba a daren yau ba!
Maryam Saidu at 06:16
AUREN FANSA 37
✨⭐✨⭐✨⭐✨⭐✨
⭐🌹🌹🌹⭐🌹🌹🌹⭐
🌹⭐✨⭐🌹⭐✨⭐🌹
🌹✨⭐✨⭐✨⭐✨🌹
✨🌹✨⭐🌞⭐✨🌹✨
⭐✨🌹✨⭐✨🌹✨⭐
✨⭐✨🌹✨🌹✨⭐✨
⭐✨⭐✨🌹✨⭐✨🌟
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
AUREN FANSA!!!
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
🌹Na🌹
🌹MARYAM S BELLO🌹
(MSB)
PURE MOMENT OF LIFE WRITERS
_We don't just entertain and educate, we touch
the heart of readers_
P.M.L
🌹37 🌹
http://MaryamSBello.blogspot.com
A zuciye ta shige ko gabanta bata gani sosai,
tana shiga suka d'ago suka dube ta sai sukayi
ido hud'u da Faruk, wani tsananta ya sake dira a
zuciyansa ga wani zafi yana ji a k'irjinsa, yanzu
a yadda yakeji baya jin son wata 'ya mace a
duniya in ba Meenah ba, ya kalli inda Jiddar ke
tsaye da rik'ak'en k'ugu tana kad'a jiki kamar
wata mazari. Wayancewa yayi ya jefo mata
tambayar rainin hankali
"Jidda ya gida?"
Ta yamutsa fuska gami da yin fari da ido tace
"Lafiya."
Yayi murmushi kad'an yace
"Kina son wani abu ne? As you can see I am
busy here."
Tambayar ta bata haushi sosai ta kuma 6ata
mata rai ainun, ta dube shi tace
"Inada buk'atarka ko ka manta matsayinka
gareni?"
Yace
"A'a ina sane, kije zanzo muyi maganar."
Ta cika tayi fam tace
"Babu inda zanje, wai shin ya Faruk wane irin
aure mukayi? Na k'iyayya ko na soyayya?"
Yace
"Bafa haka bane, nace ki dai je zanzo, idan kuma
kina da buk'atar wani abu ki fad'a min."
Tayi shiru tana tunani, ta dubi Meenah da ke
tsaye kamar abin bai dame ta ba, sai tayi
mamakinta sosai, ta d'auka Meenah macece mai
sauk'in kai har ma tayi tunanin zatasa baki a
cikin maganar ko don ta taimaka mata, to me
hakan ke nufi?
Kawai sai Jidda ta fita da gudu daga d'akin tana
dana sanin zuwan da tayi da kuma zubar da
class d'inta da take da shi a gaban kishiya da
kuma mijin da bai damu da ita ba. Sai dai ta
k'udiri gana ma Meenah wuta, har sai ta gane
matsayinta a gidan, a shirye take don ganin
hakan ta faru kuma sai ta fi kowa farin cikin
ganin hawayenta!
Washe gari da safe Meenah na kitchen tana
had'a kalacin safe Jidda na la6e tana jiran ta
gama don ta san abinda ta shirya mata!
Sai da Meenah ta kammala abincinta soyen
dankali ne da sauce d'in k'wai, ta zuba ma
Faruk nasa a plate da na kowa sai ta koma
d'akinsa don sanar masa ya fito ya ci abinci.
Tana ganin ta shige sai ta fito cikin sand'a ta
bud'e abincin Faruk ta zazzaga ma sauce d'in
uban yaji sannan ta zazzaga ma dankalin gishiri
mai yawa. Tafiya taji ya sanya ta koma d'akinta
a guje tana dariyar mugunta don yau zatayi
kallon fad'an da Faruk zaiyi ma Meenah. Sai
murna takeyi.
Meenah ta shigo d'akinta ta kalle ta tace
"Ki fito kici abinci ko."
Tayi 'yar dariya tace
"Yanzu kuwa."
Da d'an tsalle tsalle ta fito daga d'akin sannan
kuma ta nutsu tabi bayan Meenah.
Kowa ya nutsu kan dinning zasu fara cin abinci,
Faruk ne zai fara cin abinci har ya fara d'ebo
dankalin kawai kwatsam Meenah ta lura da
d'igen d'igen yaji a gefen plate d'insa sannan ga
abincin ya chanza kala ya zama jawur, take ta
fara tunanin yadda akayi hakan ta faru, sai ta
kai dubanta ga Jidda yanayinta kad'ai ya isa ya
tabbatar ba wanda ya aikatan hakan sai ita.
Cikin dabara ta kwa6ar da lemon da ke cikin cup
a gaban faruk, hakan ya dakatar da shi daga cin
abincin da zaiyi wanda saura k'iris ya kai
bakinsa.
"Subhanalillah garin yaya hakan ta faru?"
Meenah ta mik'e da sauri tana cewa
"Kayi hak'uri wallahi ban lura ba, bari na goge."
Cikin dabara ta janye abincin Faruk ta matsar
kusa da abincin Jidda ta shiga kitchen ta d'auko
tsumma ta soma gogewa, ta faki idon Jidda ta
sauya abincin dana Faruk sai ta tura na Jidda a
gaban Faruk da sauri.
Bayan ta gama ta dawo ta zauna tace
"Sorry please, kaci abincin mana."
Yace
"Ay da kin bari sai da aka gama kika goge."
Tace
"Hakan yayi ay kaga yanzu sai aci abincin cikin
kwanciyar hankali."
Ya d'ebi abincin ya kai bakinsa, Jidda nata
kallonsa tana dariyar mugunta sai dai me? Bata
ga komai ba sa6anin abinda tayi tsammani, ta
shiga rud'ani, ta kalli plate d'inta sai taga na
Faruk ne aka chanza mata, ta kai dubanta ga
Meenah taga tana mata kallon irin ya kika ga
nayi k'ok'ari ko?
Meenah ta k'ura mata ido tana murmushi, Faruk
ya d'ago ya dubi Jidda yace
"Ya naga bakya cin abincin ne? Kici mana yayi
dad'i."
Meenah tayi murmushin mugunta tace
"Eh kici abinci Jidda, yayi dad'i sosai."
Ta fad'i haka har yanzu bata bar murmushin ba,
ba yadda ta iya haka ta d'ebo ta kai spoon a
bakinta, take taji wani irin yaji da gishiri ya
had'an mata, ta dinga taunawa da k'yar tana
hawaye tana gogewa don kar a gane.
Faruk ya kammala cin abincinsa ya mik'e yana
fad'in
"Zan tafi aiki, sai na dawo."
Meenah tayi murmushi tace
"Sai ka dawo, amma bari na gyara maka zaman
rigarka."
Yayi murmushi yace
"To."
Ta gyara masa sannan ta fita raka sa bakin
mota, suna fita Jidda tayi toilet da gudu tana
faman tari da kakarin amai, sai da ta d'auki
lokaci mai tsawo tana wanke bakinta sannan ta
fito tana faman goge bakinta da har yanzu bai
bar mata yaji ba.
Kaci6us tayi da Meenah a bakin k'ofa ta hard'e
hannayenta duka biyun tana murmushi. Ganinta
yasa ta d'an dafa ta tace
"Meyafaru?"
Jidda ta kwa6e mata hannu cike da masifa tace
"Muguwa! Azzaluma kawai."
Dariya ta su6uce mata tace
"Muguntar me nayi? Sannan kuma zalunci me
nayi?"
Jidda ta dalla mata harara sannan tace
"Wallahi kin bani mamaki Meenah, nayi tunanin
ke macece mai sauk'in kai ashe ba haka bane?
Ashe haka kike?"
Meenah ta dawo tana fuskantarta ido cikin ido
da hannayenta a hard'e sannan tace
"K'warai ina da sauk'in kai idan aka bini ta
sauk'in kai, sannan kuma ina da wuyar sha'ani
idan aka bini bata lalama ba, Jidda kar kiyi
tunanin kina ganina kamar bansan abinda nakeyi
ba, to da hankalina sannan kallonki nake tar!
Nasan ke wacece sannan nasan wane irin zama
ya kawo ki, a dah nayi niyyar muyi zaman lafiya
dake, amma tunda na gano sirrinki da kuma
k'udirinki na son rabani da Faruk na sake taku.
Wallahi baki isa ba, kinyi kad'an kice zaki rabani
da Faruk, nasani ta yadda kika k'waci
soyayyarsa ta k'arfi da kuma ta magani, anma
kisani duk abinda aka d'ora shi ba bisa tirba ta
gaskiya ba to labari ne."
Jidda ta daka mata tsawa
"Ke Meenah! Yafa isheki haka, shiru shiru fa ba
tsoro bane gudun magana ne, kar ki nemi ki
fad'a min magana yadda kikeso fa."
Meenah tace
"Ni ba fad'a zanyi da ke ba, amma kisani zan
fad'a zan kuma k'ara fad'a ke baki isa ki rabani
da Faruk ba, saboda yana yi min true love ne
babu boka babu malami, soyayyarmu had'in
Allah ce, kuma banga ta yadda zaki raba abinda
Allah ya had'a ba, duk naji conversation d'inku
keda k'awarki sannan a shirye nake nayi fighting
back don ganin baki rabani da Faruk ba."
Jidda tace
"Haka kika ce?"
Meenah tace
"Haka nace."
Jidda tace
"Shikenan mu zuba, niko bama Faruk ba har
gidannan sai na raba ki dashi, ta yadda idan kika
fita har abada bazaki dawo ba."
Meenah tace
"In kin dama ki rabani da duniyar nan gaba
d'aya bama gidan ba, sannan kisani babu abinda
kika isa kiyi min sai abinda Allah yayi min,
sannan ina so ki sani k'arya fure take bata
'ya'ya!"
Jidda tace
"Zaki gani."
Meenah tace
"Zanga alkhairi."
Daga haka ta sa kai ta fice zuwa d'akinta, inda
ta bar Jidda tsaye kamar gunki in banda cizon
yatsa babu abinda takeyi, gaba d'aya idanunta
sun sauya daga fari zuwa ja, cikin sanyin jiki ta
koma d'akinta tana mai mamakin Meenah da
kuma maganganun data fad'a mata a yau.
BELLO
‹ › Home
View web version
Saturday, 26 August 2017
Maryam Saidu at 06:17
AUREN FANSA 38
✨⭐✨⭐✨⭐✨⭐✨
⭐🌹🌹🌹⭐🌹🌹🌹⭐
🌹⭐✨⭐🌹⭐✨⭐🌹
🌹✨⭐✨⭐✨⭐✨🌹
✨🌹✨⭐🌞⭐✨🌹✨
⭐✨🌹✨⭐✨🌹✨⭐
✨⭐✨🌹✨🌹✨⭐✨
⭐✨⭐✨🌹✨⭐✨🌟
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
AUREN FANSA!!!
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
🌹Na🌹
🌹MARYAM S BELLO🌹
(MSB)
PURE MOMENT OF LIFE WRITERS
_We don't just entertain and educate, we touch
the heart of readers_
P.M.L
🌹38 🌹
http://MaryamSBello.blogspot.com
Daddare bayan sallar maghrib Faruk ya kirawo
su a babban parlor yana son magana dasu.
Bayan sun iso ya fara magana kamar haka.
"Abinda yasa na tara ku a nan shine, na farko
ina so ku sani shi aure ba abin wasa bane,
sannan ban k'ara aurennan da wata manufa ba
sai alkhairi, kamar yadda kuka sani ana yi wa ko
mace kwana biyu ko uku, don haka na ware
kwanaki biyu zan rik'a yi wa ko wacenku, ranar
girkinki ya zagayo zaki kar6i girki, saboda
Meenah ba baiwa bace da zata rik'ayi maki girki
sai dai kici. Sannan banison raba abinci, idan
girkin d'aya ne to zata dafa ma duka gidan
abinci, da fatan kun fahimta?"
Meenah tace
"Mun fahimta."
Yace
"Yauwa daman shine maganar."
Jidda ta k'ule meye na ci mata mutunci a gaban
Meenah?
***
Da safe Faruk na d'aki yana shirinsa zai fita aiki
Jidda ta shigo sai faman zum6uren baki takeyi,
ya kalle ta ya kawar da kansa tare da cigaba da
abinda yakeyi, ta matso kusa dashi tace
"Ya Faruk ina son magana da kai."
Ba tare da ya kalleta ba yace
"Ina jinki."
Kai tsaye tace
"Mota nakeso ka siya min."
Ya dakata daga abinda yakeyi ya juyo yana
kallonta cike da mamaki yace
"Mota fa kika ce? Anya kina da hankali kuwa?"
Tace
"Da hankalina ai itama d'ayar matar taka tana
hawa mota, ni bana hawa, don haka ance kayi
adalci a tsakaninmu nima sai ka bani mota."
Yayi ajiyar zuciya yana fad'in
"Jidda, Jidda, a gaskiya rigimarki ta fara isata,
idan kina maganar mota dana bawa Meenah ina
kikaga tana zuwa inba makaranta ba? Ke kuwa
ba zuwa makaranta kike ba saboda bakici Jamb
ba koba haka ba? Don haka tunda bakya zuwa
makaranta ni ba motar da zan baki, da dai kina
zuwa ne wannan is understandable sai na d'auki
d'aya daga cikin motocina na baki kema kina
zuwa makaranta, don haka kar na k'ara jin
wannna maganar a bakinki ma."
Ta juyo cike da masifa tace
"Ni gaskiya baka kyauta min ba, kawai don nace
ka bani mota sai ka min gori? Ni gaskiya ka
bani mota tam."
Yace
"Bazan bada ba zo ki k'wata, ko ita Meenah ba
rok'a na tayi ba ni naga dacewar hakan na bata,
don haka kema idan naga ya dace na baki zan
baki."
Ta fara jijjiga jiki tana masifa
"Kawai don nace a bani mota shine mene? Naga
dai motocinnan kana da su to meye don ka bani
d'aya?"
Yayi tsaki yace
"Ke kinga tashi ki fita ki bani wuri, mota kuma
zo ki k'wata sai muga ta tsiya, sakaryar banza
wadda batasan ciwon kanta ba, kullum ke kenan
rigima daga kice wannan sai kice wannan? Haka
kikaga 'yar uwarki nayi ne? Haba!"
Tashi tayi ta fita tana wannan cika tana batsewa
ita a dole an 6ata mata rai, shi kuma Faruk tsaki
kawai yakeyi har ya kammala shirinsa.
Haka ta koma d'akinta zuciyarta na rad'ad'i ta
dubi agogo k'arfe bakwai da minti hud'u
7:04am, Faruk mamaki yake bata kafin suyi aure
kamar zai maida ta cikinsa, amma sunayin aure
komai ya chanza mata, gashi bata son sanar da
Luby halin da take ciki gudun kar ta mata dariya
sheyasa ma ta bar abin a ranta.
BAYAN KWANA BIYU
Bayan kwana biyu kuma ta samu Faruk ya lafa
mata tunda har yana kwana d'akinta kuma yana
kulata, don haka sai ta fara jijji da kanta a
gaban Meenah, wai ita nan ta fara samo kansa.
Meenah ta kira Faruk a waya ta tambayesa
zataje gida kuma