Showing 33001 words to 36000 words out of 42966 words
ya barta, don haka ta shirya
tsab direba zai aje ta, don yau ma Zarah zataje
gida itama, ta fito parlor nan ta iske Jidda nata
faman shan kankana duk ta 6ata wurin, Jidda
badai k'azanta ba.
Jidda ta d'ago ta dube ta a shek'e ta ta6e baki
sannan tace
"Fita zakiyi ne?"
Meenah tace
"Gida zanje."
Jidda ta bushe da dariya sannan ta dubi Meenah
tace
"Haba Malama ke dai fad'i gaskiya, ashe duk
k'aryar banza ce kikace kissa tafi magani, tunda
gashi zaki fita neman maganin kema? Sai dai kin
makaro don kinga yanzu Faruk ya k'ara dawowa
hannuna kuma, kuma kisani na riga nayi miki
nisa sannan a sannu zan tantance miki da
magani da kissa wane yafi tasiri, kuma yanzu
kika soma ganin chanji don nayi alk'awarin sai
kin bar gidannan kika k'aryata ni, to muje dai
zuwa, don haka kema kinbi sahu ay sai mu goga
ni da ke."
Meenah tayi murmushin da ya k'ara bayyanar da
kyawunta tace
"Ko shakka babu ni na fad'a miki kissa tafi
magani tasiri kuma zaki gani, babu boka babu
Malami, nayi alk'awarin nuna miki tasirin da
kissa take da shi, ki fara k'irga daga yanzu na
baki kwana bakwai kima fara lissafi tun daga
yanzu, sannan banga ta yadda kina k'azanta
zaki iya zama da miji lafiya ba ko wannan kad'ai
ya isheki, ni na tafi sai na dawo."
Tasa kai ta bar gidan, Jidda ta sake bushewa da
dariya tana wani huro chewing-gum d'in da ke
bakinta tayi k'wai tace
"Da sannu dai zan ci ubanki sai kin gwammace
kid'a da karatu."
****
Gaba d'aya Meenah ta dage da addu'a ba dare
ba rana, sannan ga extra kula tana masa da
kuma kaucewa duk wata hanya da zata sa su
samu sa6ani, lalla6a sa takeyi kamar k'wai,
shiyasa ma take ganin chanji sosai.
Yau da rana abinda yake so tayi masa wato
waina da miya, ta masa zo6o mai dad'i da
kunun aya tayi masa tasani sarai yafison
abubuwan gargajiya akan tarkacennan. Yana
cikin cin abincin ne Jidda ta shigo ta wani kashe
d'ankwalin ture kaga tsiya tana taunar chewing-
gum, da sauri ta janye plate d'in tana ma Jidda
wani irin kallo. Tace
"Baby ban yarda da abincinnan ba, ka daina ci
kazo na had'a maka wani."
Meenah ta mik'e tace
"Sai dai ki jira zuwan ranarki."
Faruk yace
"Kinga Jidda don Allah ki wuce ki bamu wuri
banason tashin hankali."
Cike da mamaki ta kalle shi tana kad'e kai tace
"A gaskiya bazakaci abinnan ba, saboda sam
ban aminta dashi ba."
AUREN FANSA 39
✨⭐✨⭐✨⭐✨⭐✨
⭐🌹🌹🌹⭐🌹🌹🌹⭐
🌹⭐✨⭐🌹⭐✨⭐🌹
🌹✨⭐✨⭐✨⭐✨🌹
✨🌹✨⭐🌞⭐✨🌹✨
⭐✨🌹✨⭐✨🌹✨⭐
✨⭐✨🌹✨🌹✨⭐✨
⭐✨⭐✨🌹✨⭐✨🌟
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
AUREN FANSA!!!
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
🌹Na🌹
🌹MARYAM S BELLO🌹
(MSB)
PURE MOMENT OF LIFE WRITERS
_We don't just entertain and educate, we touch
the heart of readers_
P.M.L
🌹39 🌹
http://MaryamSBello.blogspot.com
Meenah ta dube shi tace
"My soul bai isheka ba abincin ko?"
Ya gyad'a mata kai, ta mik'o masa hannu ya sa
nasa cikin nata tace
"Zo muje na had'a maka wanda yafi wannan,
babu mamaki k'ila tana son cin wannan ne."
Baiyi gardama ba yabi bayanta suka nufi
sashenta, tana tsaye da plate a hannunta suka
fice, galala take kallonsu har suka fice, babu
shakka Meenah ta yi gaba a halin yanzu ta barta
baya, dole ne ma ta d'auki mataki akan haka.
Ta fito daga sashen cin abinci (dinning) ta nufi
sashenta.
Zaune take abin duniya ya ishe ta, ta sak'a
wannan ta warware, daga k'arshe ta mik'e ta
fito daga d'akin tana cizon hannu. Shiru babu
motsin kowa, da alama suna cikin d'akin Faruk,
haushi ya turnik'e ta kamar zata fashe.
***
Dawowarsa kenan daga gidan, rashin ganin
Meenah bata tarosa ba ya tabbatar tana
makaranta don tace masa yau zatayi test har
biyu.
Yana shigowa yaci karo da Jidda daga bakin
k'ofa sai faman washe baki takeyi.
"Sannu." Tace dashi tana taunar chewing-gum,
yayi tsaki yace
"Yauwa." Ya sa kai zuwa d'akinsa yana Allah
wadaran da mace marar tarbiyya.
Yana zaune bakin gado yana cire safarsa ta
shigo sai wani cika take tana batsewa. Zama
tayi gefensa tace
"Ya Faruk magana nazo muyi."
Yace
"Yanzu Jidda daga dawowata sai ki tare ni da
wata magana kuma, ay kya bari in huta dai ko."
Tace
"Nidai ka bari na fad'a maka."
Ya dakata yace
"Ina jinki."
Tace
"Ay dai kace kai baka tauye hakkin iyalanka ko?"
Yace
"Haka ne."
Tace
"Yauwa, to tunda baka tauye hakkin iyalanka so
nake ka barni na tafi Dubai, na karanta Fashion
and Design."
Ya karkato yana dubanta yace
"Da igiyar wa?"
Tace
"Da igayarka mana."
Yace
"Kinga Malama banson zancen banza, ta yaya
kina matar aure kawai don rashin hankali sai ki
tafi wata uwa duniya da sunan karatu, ke bari
ma kiji ni ba irin mazan nan bane da mata ke
juya su yadda suka ga dama ba, don haka
wallahi sai na sa6a maki kika k'ara yi min zance
makamancin wannan."
Cike da shagwa6e tace
"Haba don Allah ya Faruk, wai ni meyasa kake
min haka ne? Saboda Allah ita Meenah ay ka
barta tana karatu sai ni zaka hana ni."
Yace
"Ita Meenah ba kina ganin cikin garinnan take
ba? Yau ga zancen banza zancen wofi, ke nafa
gaji da rigimarki haba! Mutum kullum da abinda
zaice daga wannan sai wannan to wallahi na
gaji."
Kawai ya tashi ya bar mata d'akin.
Ita kuwa sai tasa kuka tana ta magana ita
kad'ai.
****
Ranar wata Juma'a Luby tazo gidan, nan suka
baje suna fira. Jidda ta dubi Luby tace
"Luby gaskiyar magana nayi dana sanin wannan
aure, banida tantama alhakin Meenah ne ke
bibiyata, ke tunda nazo gidannan ban ta6a
tsintar farin ciki ba daidai da rana d'aya ba,
nikam na gaji wallahi auren ma ya fita raina,
mutumin nan sai shegen kulle baya bani abinda
nakeso, ga abin takaici wai Meenah yanzu tayi
min in mata batada tsoro ko kad'an, ke wallahi
aurennan na gama shi sai ya sake ni."
Zumbur Luby ta mik'e tana salati tace
"Yanzu Jidda abubuwa nata faruwa shine
bansani ba? Baki iya fad'a min? Sai da abubuwa
suka jagule miki suka fi k'arfinki shine zaki
sanar da ni yanzu ko?"
Jidda tace
"Kiyi hak'uri Luby wallahi na d'auka zan shawo
kan abin ne."
Luby tace
"Aiko sai mun d'auki fansar abinda tayi miki,
bata isa ba, wacece ita? Ke kin bani kunya kinfa
girme ta, amma kin zauna tana juya ki."
Jidda tace
"A'a Luby ke kinsani sarai mu da magani mukayi
aiki, ita fa? Ay ba d'aya bane ba ma."
Luby tace
"Shikenan, amma kar kiyi saurin karaya, aure
kuma yanzu kika soma shi, yo mekenan idan
kika tafi tun yanzu, ay ko baki warci wani abu
ba ni kya wabto mani, kuma ke ina son da kike
masa? Ko dama k'aryar banza ce?"
Jidda tace
"Luby don bakisan irin wahalar da nake sha ba,
babu fa yadda muka iya saboda matarsa tayi
mana zarra."
Luby tace
"Wallahi k'arya takeyi! Kedai ba kina amfani da
kwallin da turaren ba?"
Jidda tace
"Wallahi ina yi, kedai Luby munzo inda aka kere
mu."
Luby tace
"Yanzu akwai wani abu a wurinki?"
Jidda ta girgiza kai
"Babu komai sai tarin wahala da takaici."
Luby tace
"To zan san matakin da zan d'auka, zan dawo
anjima ko gobe."
Washe gari da sassafe ta dawo, ta d'auki Jidda
amma sai da suka shirga ma Faruk k'arya
sannan ya barsu da k'yar, shima akan kar su
dad'e.
Suna tafe a mota Luby tace
"Kar ki damu k'awata, zan kai ki inda za'a share
miki hawaye."
Jidda tace
"Ina kenan?"
Luby tace
"Me kike ci na baka na zuba, kedai ki tsaya ki
gani."
Luby ta koro ma Barmuje bayani, yayi 'yan
tsubbace tsubbacensa zuwa can yace da Luby
"An 6ata aiki ay, saboda tun farko sai dana
fad'a miki kar ya wuce daren farko baiyi tarayya
da ita ba, amma ina bakuji ba, sannan kuma sai
da ya fara yin tarayya da uwar gidanki akanki,
don haka aikinki bazai ta6a yin tasiri ba! A
yanzu komai ya wargaje saboda uwar gidanki
tana da rik'o da addini sosai, a gaskiya kafin
wani abu ya kamata da wuya. Ina tunanin kawar
da ita ne kawai zai baki damar mallakar mijinki
don haka sai kisan abinyi."
Suka kalli juna itada Luby tace
"To yanzu meye abinyi?"
Barmuje yace
"Akwai maganin da zan baki, zaki zuba mata a
wani abun sha, kamar koko, fura da sauransu,
wannan abin da kike gani guba ce data sha ita
da duniyar nan sai dai a lahira."
Luby tace
"Akwai wata hoda da ka bani jiya, inaga kamar
zata fi yi mata amfani."
Yace
"Tabbas! Zaifi sauk'i sai dai zan k'ara
gargad'inki da kada ki kuskura ki shak'i hodar
nan don idan kika shak'a.... hahaha to kema
zaki bak'unci lahira, idan kuma baki mutu ba...
haha! To zaki wahala a nan duniyar sai kin
zamo abin tausayi."
Luby tace
"Zata kiyaye ma."
Da haka suka baro dajin da Barmuje yake, suka
dawo gida.
Luby tace
"Yanzu dai ga maganin nan, kuma kinji gargad'in
Barmuje wallahi kibi a sannu."
Jidda tace
"Haba kar ki damu komai zai tafi yadda akeso."
Luby tace
"In ta mutu ki sanar dani, zan had'a mana grand
party."
Jidda tace
"Ay dole ne ma wannan."
Suka k'yalk'yale da dariya gami da tafawa.
Daga haka sukayi bankwana Luby tayi gida cike
da murna.
****
Meenah na kwance a d'aki tana baccin rana inda
Jidda ta lalla6o da hodar a hannunta, Jidda ta
huro mata hodar tayo baya da sauri, sai dai
mey? Memako Meenah taji wani abu sai ma ita
Jiddar ta kurma uban ihu sakamakon jikinta dake
mata rad'ad'i. Meenah ta farka tana salati
sannan ta fito da sauri ganin meke faruwa.
Jidda ce a tsakar parlor tana kurma ihu tana
soshe soshe, Meenah tayo kanta tana tambayar
lafiya? Ture ta Jidda tayi, sannan tayi d'akinta
da gudu ta fad'a toilet tayi wanka da ruwa masu
sanyi sosai. Sai dai babu wani sauk'i data
samu. Ta kasa zaune ta kasa tsaye, kuka kawai
takeyi, ga sam ta hana Meenah ta ta6a ta, sai
surutai takeyi marassa kan gado.
Hijabinta ta saka ta fito parlor a lokacin Meenah
na sallah d'akinta, aiko da sauri ta fito ta tafi
gidansu.
Mama na d'aki tana sallah ta shigo tana kuka,
sai tirje tirje takeyi, bayan Mama ta sallame ta
juyo tace
"Ke lafiya..."
Bata k'arasa magana ba Mama taja baya cike da
tsoron ganin fuskar Jidda kamar ba tata ba,
Mama ta fito da gudu tana salati tana fad'in
"Wacece ke?"
Jidda na biye da ita tana dariya tana cewa
"Ni ce, nice naje wurin boka nida Luby muka
anso magani zamu kashe Meenah."
Mama tasa salati tana fad'in
"Jidda. Meya kaiki? Mekika zama? Innalillahi wa
inna ilahir raj'iun! Jidda."
Jidda tasa dariya, sai ta susa kai, ta susa jiki
tana zum6uro baki tace
"Wai laifina ne? Kaji man Mama, nifa kawai
d'ora ni akayi akan turbar nabi kuma."
Ana haka Dada ya dawo, shima cike mamaki
yake tambayar lafiya. Mama ta kwashe komai ta
fad'a masa abinda Jidda ke cewa.
Dada yace
"Da alama fa kamar hauka takeyi ko?"
Mama tace
"Nima shi nagani."
Suka sa salati, Dada yace
"Duniya budurwar wawa Jidda, Allah ya shiryeki,
Hajiya kamo ta ki kai ta d'aki ki rufe kafin mu
san abinyi."
Tace
"To."
Ta kamo Jidda, tana tirjewa da k'yar suke tafiya,
Jidda taci kwalar Mama tana dariya tace
"Ina zaki kaini? Iye?"
Mama tace
"Muje d'aki ki kwanta."
Jidda tasa dariya, can kuma tasa kuka, can tasa
dariya, sai kuma tasa kuka, ta jawo hancin
Mama ta matse tace
"Daman haka boka yake? Laifin duk na Luby ne
saboda ita ta kaini tun farko, saboda ban ta6a
zuwa ba ay ko?"
Mama tana kuka tace
"Eh muje."
Mama ta sha wahala don da k'yar ta kai ta d'aki
ta rufe, sai dai taji ana bubbuga k'ofar ana ihu,
can taji dariya, can taji surutai, can kuma taji
ana cewa
"Boka, boka, Barmuje sunansa."
Mama tayi tsaye tana kuka, tace
"Innalillahi wa inna ilaihir raji'un, Jidda kinga
halin da kika jefa kanki ko? Kinzo kiyi wa wata
asiri ya dawo kanki, duniya ina zaki damu? Ka
haifi d'a amma baka haifi halinsa ba. Allah ka
shirya shine kawai abinda zan ce miki Jidda,
Allah kuma ya yaye miki."
Dada ya kira Faruk ya sanar masa yazo yana
nemansa yanzu yanzu.
Ba'a d'auki lokaci ba ya iso, Baba ya kwashe
komai ya fad'a masa, Baba ya d'ora da cewa
"Ina so idan ta warke ka sallame ta, baka
buk'atar cigaba da zama da ita, tunda har kamar
Jidda tasan tayi kisa ay kaga zama da irinsu ba
amfani.
Faruk yace
"Allah ya kyauta, Allah kuma ya bata lafiya."
Baba yace
"Amin."
Faruk yace
"Bari na dubo ta, daga nan sai na nemi asibitin
da za'a kaita."
Baba yace
"To kabi a hankali, don jikin ba dad'i."
A hankali ya tura k'ofar d'akin tana zaune
dirshen a k'asa tana kwa6a sabulu da toothpaste
cikin wata roba, ya kalle ta duk ta shafa ma
kanta, ya zauna a bakin gado yana kallonta cike
da tausayi, wannan wace irin rayuwa ce? Wai
Jidda tasan taje wurin boka? Ya kalli Dada dake
tsaye a bakin k'ofa sannan ya maida dubansa ga
Jidda da ke shafa sabulun a jikinta.
Ya gama kallonta yayi mata adduo'i sannan ya
tashi ya fita.
Ba'a d'auki lokaci mai tsawo ba ya je ya nemo
asibitin da za'a kaita, daga nan aka kwasheta da
da k'yar daga gidan. Faruk ya sanar ma sauran
'yan uwanta suma sunyi jimami sosai, daga
k'arshe sukayi mata fatan shiriya da samun
lafiya.
***
AUREN FANSA 40
✨⭐✨⭐✨⭐✨⭐✨
⭐🌹🌹🌹⭐🌹🌹🌹⭐
🌹⭐✨⭐🌹⭐✨⭐🌹
🌹✨⭐✨⭐✨⭐✨🌹
✨🌹✨⭐🌞⭐✨🌹✨
⭐✨🌹✨⭐✨🌹✨⭐
✨⭐✨🌹✨🌹✨⭐✨
⭐✨⭐✨🌹✨⭐✨🌟
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
AUREN FANSA!!!
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
🌹Na🌹
🌹MARYAM S BELLO🌹
(MSB)
PURE MOMENT OF LIFE WRITERS
_We don't just entertain and educate, we touch
the heart of readers_
P.M.L
🌹40🌹
http://MaryamSBello.blogspot.com
Ya shigo gidan a lokacin da ya tarar da Meenah
a bakin k'ofa, tana sanye da brown and cream
atamfa d'inkin riga skirt, tayi kyau sosai, da
sauri ta taro sa ya k'ura mata idanu yace
"My baby ya akayi ne?"
Yaushe rabon da taji sunan nan a bakinsa har
ma ta manta, tayi murmushi tace
"Jidda ce tun d'azu banganta ba, ko da saninka
ta fita?"
Ya kwashe labarin komai ya fad'a mata, tace
"Ikon Allah kenan, amma Jidda bata yi wa kanta
adalci ba, amma sai inga duk bai kai na saki ba
my soul."
Ya kamo ta suka dawo parlor suka zauna yana
kallonta sosai yace
"Rabuwa da Jidda shine mafi alkhairi a garemu
my baby, saboda a gaskiya bazan iya cigaba da
zama da ita a matsayin matata ba, besides ba'a
son raina na aure ta ba."
Ta dube shi cike da mamaki tace
"Bangane ba my soul."
Yace
"Wato akwai wata rana na fito zan tafi aiki sai
naji Jidda na magana da mahaifiyarta tana ce
mata ita ba wanda takeso sai ni, a nan naji
Mama na ta rarrashinta akan tayi hak'uri tunda
ni ba sonta nakeyi ba, tun daga wannan lokacin
sai na karaya nake ganin kamar ban kyauta ba,
abin yana ta damuna sosai, a ganina abinda
kawai zanyi na faranta ransu shine na bijiro da
maganar auren Jidda, a tunanina sun mani
komai a rayuwa bai kamata d'iyarsu tana sona
nak'i ta ba."
Meenah ta kamo hannunsa tana murmushi tace
"A gaskiya kayi tunani mai kyau kuma ka kyauta,
sai dai daman tun farko kayi min bayani da sai
nafi fahimtarka my soul."
Yace
"Naso yin hakan my baby, amma a lokacin sai
na rasa dalilin da yasa na kasa fad'a miki
gaskiya, kuma wallahi bansan yadda akayi ba
sai dai naji ance wai matata ce, abin zai baki
mamaki is like bansan abinda nakeyi ba, kuma a
lokacin Jidda tayi amfani da magani wajen jawo
hankalina gareta, nidai kawai idan ta warke zan
sallame ta, taje can ta nemi wani daidai da ita."
Tace
"Bazan iya saka yin abinda baka so ba, duk
abinda kaga yafi dacewa kayi ni kuma zan baka
goyon baya d'ari bisa d'ari my soul."
Ya kamota ya rungume a k'irjinsa gami da
lumshe idanu yace
"Sheyasa nake sonki my baby."
Tace
"Nima haka, yanzu muje kayi wanka kaci abinci
ko, na dafa maka abinda kafi so."
Cike da jin dad'i yace
"Allah my baby?"
Tace
"Wallahi kuwa."
Yace
"Shikenan muje, don yau ma kece zakiyi min
wanka da kanki."
Ta tashi tana fari da ido tace
"Muje."
Ta wuce yabi bayanta.
****
Yana zaune a office d'insa aiki yasha gabansa
wayarsa ta fara ringing, ganin Hajir ya sanya ya
dakata ya d'auka.
"Hello Hajir."
Tace
"Hello Sir ina wuni?"
Yace
"Lafiya lau, ya dai?"
Tace
"Aikinka na kammala komai Sir, yanzu ya
za'ayi?"
Cike da jin dad'i yace
"Da gaske kin had'a komai da komai?"
Tace
"Yes Sir komai ya kammala."
Yace
"Wow Weldon Hajir, a gaskiya nayi matuk'ar
farin cikin jin haka, yanzu abinda za'ayi, ki
shirya zuwa gobe zan shigo gidan, dana kiraki
sai ki fita daga shigar Atika ki koma Inspector
Hajir d'inki. Sauran bayanin zan kiraki. Yanzu
wani d'an bincike nakeyi akan wad'anda suka
turo domin kashe iyayena, nama kammala don
har na tura a kamo yaran, don muna
buk'atarsu."
Tace
"Yayi haka sir, sai Allah ya kaimu goben."
Yace
"Amin, thank you."
Daga haka sukayi sallama, Faruk yayi
murmushin jin dad'i sosai.
****
Kiran farko na sallar asuba a kunnensa akayi,
domin ba bacci yake ba, saboda tsabar farin
cikin kalar matar da Allah ya bashi, shi kwata
kwata bai k'ara tabbatarwa ba sai yau,
tambayar kansa yakeyi anya kuwa akwai wanda
ya kai shi sa'a?
Ya lalubi bed side lamp sannan ya dube ta tana
bacci, numfashinta yana fita a natse.
Kyakkyawar fuskarta nata annuri, yayi ta kallonta
baya ko kyaftawa har sai da idanunsa suka
kawo ruwa sannan ya dawo hankalinsa, ya
sunkuyo a hankali ya manna mata light kiss a
goshinta, ya numfasa, Allah kad'ai yasan tarin
son da yake mata. Da k'yar ya lalla6a ya sauka
daga gadon ya shiga toilet yayi wanka ya fito da
alwalarsa, ya shimfid'a sallaya yayi nafilfili har
alfijir ya fito, sannan ya nufi masallaci.
Yanda ya barta haka ya dawo ya same ta, yayi
tsaye a gaban gadon rungume da hannayensa
yana kallonta.
"Wai lallai baby an gaji."
Ya zauna gefenta ya tallabo kanta sannan yace
"Meenah... Meenah..."
Ta bud'e ido a hankali tabi shi da kallo har idon
ya washe gaba d'aya. Yace
"Ki tashi kiyi sallah, ko gajiyar ce ta hana ki
tashi?"
Ta runtse ido tana k'ok'arin tashi, yayi
murmushi kawai ya d'aga ta cak sai toilet, ya
tarba ruwa masu d'umi ya saka ta ciki, ita kuwa
idonta har yanzu a lumshe yake, yana tsaye yace
"Haba ragguwa sai kace first time dai."
Tayi murmushi kurum, daga haka ya fita ya bata
wuri don ta kimtsa.
Tsawon minti 20 tafito, ya matso yana dariya.
"Ragguwa kawai ni tuni naje masallaci na
dawo."
Ta wuce shi tayi shirin sallarta tana jin wani irin
nishad'i marar misaltuwa. Kwanciyarsa yayi, ta
gama sallarta tayi adduo'inta gami da mik'a
godiyarta ga Allah da ya karkato mata da
hankalin mijinta gareta tana fatan su dauwwama
haka har k'arshen rayuwarsu. Sai kuma ta tuna
Jidda ko a wane hali take yanzu? Ta dad'e tana
mata addu'ar samu sauk'i, tana gamawa sai
kawai ta maida kanta bisa sallayar tana lazumi.
Ya d'ago yana dubanta yace
"Ya zaki kwanta a nan?"
Tace
"Haka nan."
Yace
"To kodai?"
Ta k'udundune fuskarta da hijabi ta k'yale shi,
cicci6o kanta yayi ya d'ora bisa jikinsa yace
"Tashi mu koma kan gado."
Tayi shiru tana kallon kyakkyawar fuskarsa, yace
"Allah yayi miki albarka my baby."
Taji dad'i sosai ta amsa da
"Amin my soul."
Ya cigaba da fad'a mata dad'd'an kalamai masu
rikita lissafi, ganin haka yasa na tashi na baro
d'akin, sai dai fatan Allah ya kawo k'azantar
d'aki..
AUREN FANSA 41
✨⭐✨⭐✨⭐✨⭐✨
⭐🌹🌹🌹⭐🌹🌹🌹⭐
🌹⭐✨⭐🌹⭐✨⭐🌹
🌹✨⭐✨⭐✨⭐✨🌹
✨🌹✨⭐🌞⭐✨🌹✨
⭐✨🌹✨⭐✨🌹✨⭐
✨⭐✨🌹✨🌹✨⭐✨
⭐✨⭐✨🌹✨⭐✨🌟
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
AUREN FANSA!!!
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
🌹Na🌹
🌹MARYAM S BELLO🌹
(MSB)
PURE MOMENT OF LIFE WRITERS
_We don't just entertain and educate, we touch
the heart of readers_
P.M.L
🌹41 🌹
http://MaryamSBello.blogspot.com
A hankali ta bud'e idonta juyi d'aya tayi ta
hango shi bakin wardrobe da alama wanka ya
fito yana shirin fita, duba agogo tayi k'arfe
8:30am, zumbur ta mik'e tana mamakin abinda
ya haddasa masa makara yau, zaune ta mik'e
tana kallonsa yana k'ok'arin d'aura agogo a
hannunsa, ta sauko daga gadon ta kamo
hannunsa tana cigaba da sa masa.
"Yau ka makara my soul."
Jin yayi shiru ya sanya ta d'ago tana dubansa
da mamaki, damuwa ta gani k'arara bayyane a
fuskarsa wanda idanuwansa ma sun nuna hakan.
"Meyake damunka my soul?"
Yace
"Babu komai, kije kiyi wanka yau tare zamu fita,
sannan ki sanar da Zarah ta tamabayi mijinta ya
bata izini zamu fita tare da ita."
Tayi shiru tana tunani can kuma tace
"Lafiya?"
Yace
"Koma me kenan zaki gani nan da lokaci kad'an,
kedai kawai ki kirata ki sanar da ita."
Tace "To." Sannan ta wuce tana tunanin
dalilinsa nace mata haka.
Tayi wanka ta sanya bak'ar after dress, tea
kawai suka sha inda a waje sukayi kaci6us da
Zarah inda take shaida musu da mijinta zasu tafi
yace zai kaita, haka ma Anisah tazo a daidai
sadda zasu shiga mota, itama ta shaida musu
mijinta zai kaita, nan kuma kowa ya fara shirin
tafiya.
A mota babu wanda yayi magana ko wane da
tunanin da yakeyi, ta kai dubanta ga Faruk da
alama ya zurfafa cikin tunanin, ta ta6o sa tace
"My soul wai meke faruwa haka ne? Sannan duk
ina zamuje da su Anisah?"
Ya karkato kad'an ya kalle ta sannan ya maida
kansa ga