Showing 39001 words to 42000 words out of 42966 words

Chapter 14 - AUREN FANSA COMPLETE NOVEL

23 Aug 2025

1539

tabbas Faruk baka kyauta ba a wani
6angaren, amma kuma ina so ke Aminatu kiyi
hak'uri na tabbata yanzu Faruku yana sonki
bada wasa ba, kuma tunda ya fito fili ya fad'a
miki bai kamata kuma ki juya masa baya ba.
Don haka ina so kiyi hak'uri ki d'auki k'addara,
kuma komai na duniya mai wucewa ne, ki rik'e
mijinki kiyi masa biyayya don shine gatanki
duniya da lahira."
Meenah tace
"Nagode Baba, amma ni gaskiya bazan koma
gidansa ba, ya sauwak'e mini kawai."
Ba Faruk kad'ai ba hartta Baba sai da ya razana
da jin kalaman Meenah, Faruk sunkuyar da
kansa kawai yayi yana jin tashin hankalin da bai
ta6a ji ba.
Baba yana kallon Meenah yace
"Aminatu, kalamanki basuyi min dad'i ba, don
banyi zaton kamar ki mai ilimi da aiki da shi zai
furtawa mijinki haka ba, amma ina so ki sani
saboda gaba duk wani 6acin rai in zaizo miki to
kisan irin kalaman da zaki furta. Mijinki dai
mijinki ne. Sannan zancen ya sake ki ma bai
taso ba, idan ma ya taso sai kiyi tunani wa
kuma zaki aura? Maza majoritin mu halinmu a
rufe yake, kafin kuma ki gane halin sai kin zauna
da mutum.
Aminatu duk rintsi kiyi hak'uri ki zaunawa
aurenki, kedai ki cigaba da add'ua, duk wani
hargirsi idan ya taso a tsakaninku kok'ari zakiyi
wajen ganin kun zauna kun warware
matsalarku."
Ya gyara zamansa ya d'an yo gaba daga
jinginar da yayi, yayi ajiyar zuciya ya cigaba
"Kin bani kunya Meenah, ban ta6a tsammanin
haka daga gareki ba, ni kome Faruk yayi na yafe
masa, don haka kiyi k'ok'ari ki yafe masa kema.
Ki tashi ki fara shirin komawa d'akinki, Allah yayi
maku albarka ya kwa6e muku duk wata fitina."
Ya kai dubansa ga Faruk yace
"Allah ya jik'an iyayenka ya gafarta masu, ga
matarka nan sai a kiyaye gaba, ka kula da ita da
kuma kanka, kasan dai matsayinta yanzu, don
haka ka rik'e ta amana Allah yayi maku
albarka."
Yace
"Amin Baba, na gane kuskure na kuma insha
Allah hakan bazata sake faruwa ba, nagode
sosai insha Allah zan kula da Meenah, zan kuma
rik'e ta bisa amana da gaskiya."
Cike da farin ciki Baba yace
"Amin, zan shiga daga ciki na d'an kwanta."
Sukayi sallama ya fice.
Zarah ita da mijinta su sukayi mata rakiya har
gidanta da misalin k'arfe biyar da rabi na
yamma, suna nan har akayi sallar isha'i bayan
sunci abinci suka fara shirin tafiya, Zarah ta
k'ara yi mata fad'a sannan ta bita da nasiha,
sukayi sallama dasu suka shige gida suma.
Bayan ta shigo ta maida k'ofar ta rufe, yana nan
tsaye bakin k'ofa yana faman murmushi, ta
kauda fuskarta tace
"Ya dai?"
Yace
"Bacci nakeji my baby, amma inaso na fara yin
wanka kuma ke nakeso kiyi min da kanki, kinsan
na gaji da yawa rabona da bacci mai dad'i har
na manta."
Ta so ce masa bazatayi ba amma tuno da
nasihar Baba ya sanya bata musa ba ta bishi da
"To."
Ta kunna masa ruwan zafi da taimakonta ya
watsa, ta taimaka masa ya shafa cream mai
k'amshi shi kuwa duk wani motsinta akan
idonsa yake. Ta kammala ta tafi tayi wanka ta
fito sanye da kayan baccinta masu kyau da
kuma firgita tunani, sai zuba k'amshi take ya cije
lips d'insa na k'asa yace
"My baby, kullum k'ara chanza min kikeyi,
yanzun ma sai naga kinfi ko yaushe yin kyau."
Duk da taji dad'in kalaman nasa haka bai hanata
turbune fuska ba tana cigaba da linke kayansa
da ya cire yanzu.
Yayi murmushi ya mik'e ya jawo ta ta fad'o bisa
k'irjinsa yana kallonta cike da so da k'auna
marar misaltuwa, ita kuwa k'ok'arin k'wace
kanta ta shiga yi wanda ta kasa saboda irin
rik'on da yayi mata....
AUREN FANSA 45
✨⭐✨⭐✨⭐✨⭐✨
⭐🌹🌹🌹⭐🌹🌹🌹⭐
🌹⭐✨⭐🌹⭐✨⭐🌹
🌹✨⭐✨⭐✨⭐✨🌹
✨🌹✨⭐🌞⭐✨🌹✨
⭐✨🌹✨⭐✨🌹✨⭐
✨⭐✨🌹✨🌹✨⭐✨
⭐✨⭐✨🌹✨⭐✨🌟
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
AUREN FANSA!!!
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
🌹Na🌹
🌹MARYAM S BELLO🌹
(MSB)
PURE MOMENT OF LIFE WRITERS
_We don't just entertain and educate, we touch
the heart of readers_
P.M.L
# *WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
# *IG PML WRITERS
# *https://www.facebook.com/PML_-Writers-
FANS-459256761123035
# *http://maryamsbello.blogspot.com
_wannan sune safikan mu da zakuna ziyarta dan
neman nvl d'in mu. Fatan mu Allah ya baku ikon
zuwa Ameen_❣️
🌹45 🌹
Ya d'an yi tsai yana dubanta, ta kawar da
fuskarta gefe, yace
"My baby, ki tausaya min ki kula ni, idan har
kika za6i ki guje ni to wallahi rayuwata tana
cikin matsala, nayi laifi tabbas kuma na gane
kuskure na har ma na bada hak'uri, to meyasa
bazaki yafe min ba? Allah ma muna masa laifi
ya yafe mana bare mu mutane? Wallahi ina
k'aunar ki, da zaki bani dama da na nuna maki
hakan Meenah..."
Shirun dai ta kuma yi, yace
"To in bazaki yi magana ba, kiyi hak'uri ki saki
ranki, kin hak'ura?"
Ya shafi fuskarta yana mai juyo da ita, take tayi
k'asa da k'wayar idonta.
"Kinji ni baby? Ki tuna matsayina a gareki, na
baki hak'uri kiji tausayina don Allah Meenah. Da
me zanji? Kina fushi dani kink'i hak'ura, ke
kad'ai fa guda nakeda a halin yanzu, ina zansa
kaina Meenah? Please please! Tuba nake, na
tuba bazan k'ara ba, kar6i wannan takardar ki
gani abin farin cikin da ya same mu."
Ya zura mata takardun cikin hannunta, ta kalla
shek'ek'e ba tare da ta karanta ba ta mik'a
masa yace
"Yanzu har kin duba baby?"
Ta gyad'a masa kai, yace
"To me kika gani?"
Tace
"Oho!" Kalmar data ambata a ciki kenan ashe ta
fito fili, yayi murmushi yace
"Daman wannan takardar k'arin ilimi ne aka tura
ni na tsawon shekara biyu wanda zanyi shi a
k'asar ingila, shine nake neman shawararki
saboda karatunki."
Har ranta taji dad'in alherin da ya same shi
wanda ta tabbata yaga hakan a fuskarta
Sai kawai ta ce masa
"Na taya ka murna, sai dai duk yadda ka tsara
yayi min."
Yayi murmushi yace
"Alhamdulillah naji dad'i, sai dai inaga kamar
zamanki a nan don ki k'arasa karatun naki yafi,
amma zan rink'a waiwayanki, bawai natafi har
sai na kammal ba ne, a'a zan rink'a ziyartarki,
donma in banda ina son kiyi karatun da k'afata
k'afarki, yanzun ma idan kinfson mu tafi taren
sai mu ajiye shi gaba kya yi shi."
Ba tare da ta kalleshi ba tace
"Babu damuwa, kaje zan zauna."
Yayi murmushi yace
Ay da yake yanzu level 3 zaki shiga kinga dana
dawo kin kammala insha Allah, kinga dana dawo
sai mu baje soyayyarmu yadda ya kamata."
Tace
"Allah ya taimaka."
Haka yayi ta lalla6a ta kamar k'wai, sai wani
riritata yakeyi yana yi mata kalamai masu
tausasa zuciya har ya samu ta d'an sauko daga
dokin data hau har ma tana d'an kula sa.
Washe gari ne yayi shirin aikinsa, bayan ya
kimtsa ta raka shi bakin motarshi yace mata yau
da wuri zai dawo yaci abincin rana ta masa
amala da miyan ku6ewa d'anya, ta bishi da
"To." Da fatan dawowa lafiya.
Yana tafiya ta tashi tayi wanka ta kimtsa gidan
sannan ta hau mota tare da kud'in da ya bata ta
nufi kasuwa, ta siyo garin amala da k'ashin rago
da ku6ewa, tana dawowa ta fad'a kitchen ta fara
kacaniyar dafa abinci, k'arfe d'aya da rabi daidai
ta gama 1:30 pm, tana gamawa ta fad'a wanka
ta fito ta shirya cikin wata atamfa dark blue
d'inkin riga da skirt d'inkin ya zauna dabas a
jikinta.
Amma shiru ba alamunshi har wajen uku, ta
d'auko wayarta ta shiga neman layinsa nan ma
bai d'auka ba. "Oh God!" Ta fad'a tare da jefar
da wayar ta mik'e bisa doguwar kujera, sama
sama bacci ya ringa fisgarta tana k'in yi don
bata son baccin yazo.
Can wayarta ta fara ruri ta mik'e zumbur ta
d'auka yace
"Baby zan aiko a d'aukar min abincin nan don
meeting zamu shiga yanzun nan, idan nace sai
na dawo kafin na koma zan makara."
Tace
"Sai ka turo bakomai."
Ta mik'e ta had'a shi cikin basket, ta kira d'an
almajirinta Yusha'u tace
"Koda bacci zai d'auke ni idan wani yazo ka
d'auko basket bisa dinning ka mik'a masa."
Yace
"To Anty."
Ta koma tayi kwanciyarta. Itace bata tashi ba
sai k'arfe hud'u har da 'yan mintina, tashinta
yayi daidai da k'wank'wasa k'ofa, ta mik'e
zaune daga kwanciyar tana gyara d'aurin
d'ankwalinta, sannan ta mik'e tayi tattaki izuwa
bakin k'ofa gami da bud'ewa.
Wata budurwa ce sai dai ko ba'a fad'a mata ba
tasan yarinyar tana cikin matsala babba.
Ta bata izinin shigowa, ta koma kitchen ta had'o
mata kayan lashe lashe da tand'e tand'e, ta
koma ta zauna suka soma gaisawa a mutunce,
Meenah tace
"Baiwar Allah sai dai ban gane ki ba, sannan
meya faru da ke haka naga jikinki duk ciwo
haka?"
Maimakon budurwar tayi magana sai kawai ta
durk'usa har k'asa tare da fashewa da wani irin
kuka mai tsanani.
Meenah ta razana tana tambayar lafiya? Da
k'yar budurwar ta tsagaita daga kukan da takeyi
sannan ta fara magana cikin sanyin jiki.
"Mu talakawa ne tu6us, wanda har cin yau
yakan gagare mu, Allah yayi ma mahafina
rasuwa da jimawa, sai mahaifiyata, mahaifiyata
ita take fafutukar nema mana abinci da kuma
kud'in makaranta, ba irin aikin da batayi ba,
haka muka cigaba da rayuwa mahaifiyata itace
komai na, sai dai a kwana a tashi na had'u da
hatsabiban k'awaye wanda suke hure min kunne
har na biye musu na kai kaina a halaka!"
Ta share hawayenta ta cigaba.
"Nazo na fara fita lokacin dana ga dama na
dawo lokacin dana ga gama, tun mahaifiyata na
fad'an tana duka na har ta gaji ta bini da
addu'a, gashi bana jin maganarta, nabi na raina
ta ban d'auke ta a bakin komai ba, tasha yi min
kuka akan abubuwan da nake mata amma ni ko
a jikina, na had'u da samari 'yan k'arya suna
min wayau suna kaini hotel su bani kud'i, daga
nan idanuna suka ida bud'ewa gaba d'aya, bana
ji bana gani, sutura kuwa sai wadda na cire duk
akan idon mahaifiyata, har ta kai ta kowa
mahaifiyata bata iya fita unguwa, data fita za'a
fara nuna ta ana gulmarta.
Kwatsam wata rana sai na had'u da Jidda..."
Thursday, 14 September 2017
Maryam Saidu at 23:38
AUREN FANSA 46
✨⭐✨⭐✨⭐✨⭐✨
⭐🌹🌹🌹⭐🌹🌹🌹⭐
🌹⭐✨⭐🌹⭐✨⭐🌹
🌹✨⭐✨⭐✨⭐✨🌹
✨🌹✨⭐🌞⭐✨🌹✨
⭐✨🌹✨⭐✨🌹✨⭐
✨⭐✨🌹✨🌹✨⭐✨
⭐✨⭐✨🌹✨⭐✨🌟
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
AUREN FANSA!!!
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
🌹Na🌹
🌹MARYAM S BELLO🌹
(MSB)
PURE MOMENT OF LIFE WRITERS
_We don't just entertain and educate, we touch
the heart of readers_
P.M.L
# WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
# IG PML WRITERS
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-
FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com
_wannan sune safikan mu da zakuna ziyarta dan
neman nvl d'in mu. Fatan mu Allah ya baku ikon
zuwa Ameen_
🌹46🌹
Da mamaki Meenah tace
"Jidda kuma? Meye mahad'inki da ita?"
Budurwar tace
"Nasan zakiyi mamakin idan na sanar da ke ni
ba kowa bace face Lubabatu wacce aka fi sanin
da Luby..."
Meenah ta mik'e tsaye a razane tace
"Luby? Kece haka?"
Luby da kanta ke k'asa tace
"Eh nice! Nice Luby aminiyar Jidda, ki zauna Zan
k'arasa bayani na."
Ta k'i zama still tana kallonta da mamaki, Luby
ta sake d'agowa tace
"Ki zauna don Allah ba don ni ba."
A hankali ta koma ta zauna tace
"Ina jinki." Luby ta cigaba
"Kamar yadda na fad'a miki a baya cewar na
had'u da Jidda a wurin bikin wata 'yar
makarantar mu da akayi, duk da ba ajinmu d'aya
da Jidda ba amma a ranar muka k'ulle muka
zama best friends. Nice sanadin lalalacewar
Jidda, ni na d'ora ta bisa gur6attaciyar hanyar
ita kuma ta bi, a tare muka cigaba da harkar mu
ta bin maza da sauransu. Nidai yanzu ba komai
ya kawo ni ba illa nazo neman gafararki, ba don
ni ba don Allah ki yafe min, nayi kuskure amma
yanzu na gane kuskure na, ki gafarce ni..."
Meenah tace
"No kar ki damu ni banida rik'o, kuma na yafe
maku, Allah ya tsare gaba, sai dai garin yaya
kika ji wannan ciwon haka a hannu?"
Ta kai dubanta ga hannun dake nad'e da
bandage gaba d'aya tace
"Wannan a ranar muka samu sa'insa da
mahafiyata akan ina so na fita da misalin k'arfe
takwas na dare, a lokacin mahaifiyata ta tashi
tace ita sam bazan fita ba, niko na dage akan
sai na fita sai dai ayi wacce za'ayi, na fad'a
mata maganganun sannan nayo hanyar waje, sai
dai daidai bakin k'ofa mahaifiyata ta tako da
sassarfa tana fad'in, Lubabatu idan kika sa k'afa
kika fita ban yafe maki ba, daga haka kawai ta
juya ta koma gida, ni kuma kawai naja tsuka na
fice abina ba tare da na damu ba. A ranar hotel
muka kwana bayan mun gama abinda mukeyi
muka zarce club, muna can har asuba, sai da
gari ya fara haske sannan muka fito don
komawa gida. Sai dai me? Muna kan hanya nida
saurayin nan nawa muna jin kid'a muna rawa a
mota ba tare da mun ankare ba muka yi had'ari,
shi saurayin nawa take ya cika ni kuwa asibiti
aka wuce dani rai a hannun Allah, sai dana
kwana bakwai ban farfad'o ba, bayan na farfad'o
naji likita na cewa sai an yanke min hannu, nayi
kuka nayi kuka, nayi bak'in ciki, nayi nadama ba
kad'an ba. A ranar nayi Allah wadarai da son
abin duniya gami da bijire wa iyaye, nidai cewa
nayi ban yarda ba, daga nan akayi wa hannuwa
na hotuna (Scan) kusan kala uku, gashi banida
kowa dole ni likitan yake tunkara da maganar.
Yace min k'ashin hannun ya lalace da yawa, ya
ratattake k'ashin, wato sai an yanke su, ido waje
na zaro nace
"Duka hannuwa na?"
Yace
"Eh to, zai iya yiwuwa dukansu amma gaskiya
hannu d'aya yafi samun dameji wanda idan aka
d'auki lokaci zai iya ru6ewa, zamuyi iya
k'ok'arinmu muyi miki 'yan dabaru a shi d'ayan
hannun, idan Allah ya taimaka sai ya zauna.
Sannan abu na biyu wurin yin 'yan bincikenmu
mun gano kina d'auke da wannan cutar wato
cutar H.I.V AIDS."
Luby ta d'an dakata saboda kukan da yaci
k'arfinta, haka itama Meenah sai da tayi
hawayen, Luby ta cigaba.
"Wani abu naji ya sokeni a k'irji kamar an sara
mani mashi, kuka nakeyi tamkar raina zai fita,
gaba d'aya duniyar da abinda ke cikinta sun fitan
min a rai, likita ya zayyano min kud'in aiki wato
gaba d'aya miliyan biyu harda rabi, kaina ya
d'auki chaji sosai, nace su sallameni na tafi na
samo kud'in aikin sai na dawo. Suka sallame ni
nayi gidanmu, na tarar da mahaifiyata tana
ganina ta razana tana tambayar meyasame ni,
na koro mata bayani, tayi ta min fad'a tace ita
ba ruwanta dani don haka na tafi na nemo kud'in
da kaina daman na saba neman kud'i, ta koro ni
na fito ina kuka. Babu wadda ta fad'o min rai
kamar Jidda, nasan ko bata bani kud'i ba zata
taimakeni da shawara, sheyasa na taho nan."
Meenah ta kalli Luby kallo na k'urilla sannan
itama ta koro mata nata bayanin.
"A gaskiya Luby idan har kud'in aiki kike nema
sai dai kije ki nemi taimako kamar su gidan
radio, wurin manyan k'asa, sannan Jidda da kika
zo nema bazaki same ta ba, saboda Jidda dai ta
haukace."
A razane tace
"Ta haukace kuma?"
Meenah tace
"Eh ta haukace, a ranar da kuka je wurin boka
amso maganin da zaku sa min ta saka min ya
koma mata, tun daga wannan ranar ta fara
hauka tana tona muku asiri, yanzun ma zancen
da nake miki ana can ana hadaniyar fidda ta can
k'asar waje neman magani. Luby wato ita
daman duniya haka take, duk yadda ka d'auke ta
haka zata zo maka, tabbas kin tafka babban
kuskure a rayuwarki, waya ce miki iyaye abin
wasa ne? Musamman uwa, kin wulak'anta
uwarki ya za'ayi kiga daidai a rayuwarki? Kin bi
boka ya za'ayi kiga daidai a rayuwarki? Kinyi
zina ya za'ayi kiga daidai a rayuwarki? Shekara
da shekaru kina shayar da mahaifiyarki gubar
6acin rai, ke ba yarinya ba ak'alla zaki kai
shekaru ashirin da shidda yanzu a yadda nake
kallonki, yaci ace yanzu kina gidan mijinki kina
bautar Allah amma kin tsaya shashanci,
shekarunki sun kai ace kinyi hankali ki gane halin
da duniya ke ciki, abinda yafi miki kije ki rungumi
mahaifiyarki ki nemi gafara, ki mata biyyaya
sannan ki gyara rayuwarki tun kafin ki koma ga
mahaliccinmu. Ina so ki maida komai kamar
tafiyar ruwa ki kuma tari gaba, ki yarda da
kaddara mai kyau ko marar kyau, wallahi Allah
gafurur Raheem ne, kuma insha Allah nima zan
taimaka miki da wani abin, cikin gadon
mahaifina zan baki wani abu sai ki k'ara cikin
kud'in aikin da za'ayi miki."
Ta bud'e baki cike da mamaki sai kuma hawaye
suka fara wanke mata fuska.
"Meenah, nagode! Nagode Allah ya saka da
alkhairi, Allah ya k'ara bud'i, Allah ya jik'an
iyaye yayi mana gafara, bani da bakin da zan
gode maki, na bibiyeki da sharri ke kuma kin
saka min da alkhairi, haka rayuwa take daman
ko wannan ya ishemu ishara."
Meenah tayi murmushi
"Kar ki damu, bakomai wallahi ai yiwa kai ne,
wannan ba wani abu bane."
Tana kallo Meenah ta mik'e ta shiga d'aki, ba'a
jima ba ta dawo hannunta d'auke da paper, ta
zauna tana mik'a mata.
"Gashi."
Tasa hannunta mai d'an lafiyar ta kar6a tana
kuka, Meenah tace
"Yanzu shiga ta na kira Faruk, na masa bayani
shine yace na k'ara miki shima ya bayar." Luby
ta duba tace
"Har dubu d'ari uku? Kai nagode Allah ya k'ara
bud'i."
Meenah tace
"Wannan ba abu bane ba babu damuwa, Allah ya
k'ara tsare mana imaninmu, ya tsare mu daga
fad'awa halaka, Allah ka shirye mu ya ganar da
mu."
Luby tace "Amin ya Rabbi."
Luby bata tafi ba sai da Meenah ta bata abincin
rana tana mai k'ara mata fad'an ta nemi yafiyar
mahaifiyarta, a haka ta bar gidan tana mai
jinjina al'amarin.
BAYAN SATI BIYU
****
Ranar wata talata, tana zaune taji horn d'in
motarsa, ta mik'e cike da mamakin ganin ya
dawo da wuri, ta lalla6o ta fito don tun jiya bata
jin dad'i. Ta k'arasa wajensa sai fara'a yakeyi
yana mata murmushi itama tana tayasa duk da
batasan dalilin farin cikin nasa ba. Ta kar6o
jakarsa suka jero har parlor ta dire jakar ta
d'auko masa ruwan sanyi a fridge ta tsiyaya
masa ta bashi.
Bayan ta zauna tace
"Lafiya ka dawo da wuri yau?"
Ya kuma dubanta yace
"Lafiya lau, tafiyar nan ce ta taso wai jibi jibin
nan zamu tafi, kin tuna maganar da mukayi a
baya ko?"
Tace
"Eh na tuna."
Yace
"To itace yau abin ya ida tabbata."
Tace
"Masha Allah, yanzu jibi zaka tafi?"
Yace
"Insha Allah."
Tace
"Zaku dad'e kenan?"
Yace
"Da shekara biyu zamuyi amma yanzu insha
Allah bazai wuce shekara d'aya ba mun juyo,
kuma in mun dawo zamu iya samun chanjin aiki
da kuma k'arin girma. Yanzu ma so nake naje
na shaida masu Dada maganar kuma ke nakeso
ki raka ni."
Ta d'an yamutsa fuska tace
"To amma fa ni bana ma jin dad'i."
Ya zaro idanu yana k'are mata kallo, yace
"Kodai abin arzik'in ne ya samu?"
Tace
"Me kenan?"
Yaja hancinta yace
"Kinfini sani, amma banga ta zama ba tashi
zakiyi mu tafi asibiti a auna ki don a tabbatar."
Kafin ma tayi magana ya zura mata hijabinta
pink color tare da jawo hannunta suka nufi
mota.
Ba k'aramar murna Faruk yayi ba da yaji daga
bakin likita cewar ciki ne da ita har na kusan
wata biyu, tun da suka shiga mota yake washe
hak'ora kamar gonar auduga.
‹ › Home
View web version
Thursday, 14 September 2017
Maryam Saidu at 23:39
AUREN FANSA 47/END
✨⭐✨⭐✨⭐✨⭐✨
⭐🌹🌹🌹⭐🌹🌹🌹⭐
🌹⭐✨⭐🌹⭐✨⭐🌹
🌹✨⭐✨⭐✨⭐✨🌹
✨🌹✨⭐🌞⭐✨🌹✨
⭐✨🌹✨⭐✨🌹✨⭐
✨⭐✨🌹✨🌹✨⭐✨
⭐✨⭐✨🌹✨⭐✨🌟
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
AUREN FANSA!!!
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
🌹Na🌹
🌹MARYAM S BELLO🌹
(MSB)
PURE MOMENT OF LIFE WRITERS
_We don't just entertain and educate, we touch
the heart of readers_
P.M.L
# WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
# IG PML WRITERS
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-
FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com
_wannan sune safikan mu da zakuna ziyarta dan
neman nvl d'in mu. Fatan mu Allah ya baku ikon
zuwa Ameen_
🌹47 🌹🔚
A ranar sukaje wajen Dada, ya dad'e yana sa
masa albarka tare da fatan dacewa, sannan ya
ce lallai lallai sai ya bashi takardar Jidda don
data warke ya mik'a mata, yasan dole zata koyi
hankali. Haka Faruk ya rubuta ya mik'a ma
Dada, haka ma Mama tayi masa fatan dacewa
da sanya albarka. Daga nan suka wuce gidansu
Meenah ya shaida ma Baba, Baba ya bishi da
doguwar addu'a ya sanya masa albarka.
Sai dai tun ana gobe zai tafi hankalinsa ya tashi
bai ta6a tunanin daidai da kwana d'aya zaiyi
nesa da Meenah ba gashi har za'a shafe watanni
bai ganta ba, yana shigowa d'aki a lokacin tana
kwance kan gado ya zauna gefenta yace
"A gaskiya Meenah bazan iya tafiya na barki ba,
kawai kiyi hak'uri ki shirya mu tafi tare." Ta juyo
tana dubansa tace
"Nidai jeka ka barni, ina nan gida Nigeria bazan
iya binka ba a yadda nake jina d'innan."
Ya tur6une fuska ya shiga zayyano mata
matsalar da zai shiga idan bata bishi ba, har da
cewa tayi differing semester d'in mana idan suka
dawo sai ta gyara. Da k'yar ta lalla6a sa yayi
hak'uri ya barta, amma idanunshi sun kad'a
sunyi ja, haka itama ta wuni tana kuka har bacci
yayi awon gaba da ita. A daren ranar Meenah
taga tarairaiya kamar wata k'wai, ya

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login