Showing 27001 words to 30000 words out of 42966 words

Chapter 10 - AUREN FANSA COMPLETE NOVEL

23 Aug 2025

490

hannunta! Lallai indai
kuwa hakane komai zaizo mata da sauk'i tunda
har ya kamu da wuri haka. A fili kuwa
murmushi tayi tace
"To yadda za'ayi ka samu Dada da maganar don
maganar tana hannun manya, amma tambayar
amsar ka itace, eh na yarda kuma na shirya
aurenka ya Faruk."
Yayi murmushi
"Kina so na kenan?"
Ta gyad'a kai cike da farin ciki, yayi murmushi
yace
"To ba matsala ay, kuma gaskiya bana son aja
lokaci mai tsawo, in zan samu ne ma nan da sati
biyu yayi min, amma da yake zanyi gyaran inda
zaki zauna ana iya sashi nan da wata d'aya."
Tace
"To duk yadda kace ni yayi min."
Da zai tafi ya fiddo kud'i masu tsoka ya bata,
yace
"Kya sa kati da wannan, sai munyi waya."
Ta kar6a tace
"Nagode."
Sukayi bankwana ta shige d'aki, tana zuwa ta
kira Luby, ta kwashe labarin komai ta fad'a
mata, ta sanar mata ya bata kud'i masu tsoka.
Luby tayi shewa
"Duniya sabuwa, kinga a nan kenan kin harbi
tsuntsu d'aya da igiya biyu."
Jidda tayi dariya tace
"A gaskiya nagode Luby bansan ya zanyi ba idan
baki ba, kin taimaka min sosai."
Luby ta k'yalk'yale da dariya tace
"Somin ta6i ne ay, ya Faruk sai ya raina kansa,
sai ya dawo kamar zai maki sujjada"
Jidda taji dad'i tace
"Nagode 'yar uwa sai munyi magana gobe."
Sukayi sallama ta kwanta rigingine tana tunanin
ranar da zata mallaki Faruk a matsayin mijinta.
Koda ya koma gida bai iske Meenah a parlor ba,
kuma sai yaji bai wani damu ba, d'akinsa ya
wuce kansa tsaye yayi wanka ya kimtsa cikin
kayan bacci ya hau gado ya kwanta, sam ya
kasa bacci sai tunanin Jidda da ya addabe shi,
wayarsa ya d'auko ya kira ta amma har ta
tsinke ba'a d'auka ba, ya sake kira a karo na
biyu nan ma sai da ta kusa tsinkewa ta d'auka.
"Hello ya Faruk..."
Ya lumshe idanu kafin ya bud'e, sannan yaja
ajiyar zuciya yace
"Kar dai har kinyi bacci na tashe ki?"
Tayi murmushi
"Eh na fara sama sama dai, da fatan ka koma
gida lafiya?"
Yace
"Lafiya lau, gani nan ma har nayi shirin bacci."
Ta mik'e da sauri daga kwance da take tace
"La ya Faruk kuma shine ka kira ni? Idan
amaryarka ta farka taga kana waya dani fa?"
Yayi murmushi
"Kar ki damu bazata farka ba, besides tama san
da maganarmu so kar ki damu."
Tayi wani shu'umin murmushi tace
"To shikenan ya Faruk sai da safe."
Ya 6ata rai
"Kar dai har mun gama firar?"
Tace
"Eh."
Yace
"Gashi ban gaji da jin muryarki ba."
Tayi dariya
"La ya Faruk, nima haka, amma bacci nakeji
yanzu.
Yace
"To shikenan sai da safe."
Tace
"Allah ya kaimu love you."
K'itt! Ta kashe bata jira ya bata amsa ba. Ya
sagale wayar a kunnensa ya kasa cirewa. Haka
ya kwanta da tunaninta har garin Allah ya waye.
Kallo d'aya zakayi mata ka tabbatar da tana
cikin matsananciyar damuwa, banda idanunta da
suka rikid'e suka koma ja alamar rashin bacci da
kuma kukan da tayi a daren jiya.
Sanye take da wani navy-blue atamfa d'inkin
riga da skirt sai wani yalolon gyale data gyala a
saman kanta. Kwata kwata yau batada kumari
haka take jinta wani iri tunda ta tashi batada
walwala.
Tsaye take a kitchen tana faman had'a masa
kalaci mai rai da lafiya. Sai da ta kammala
komai ta jera saman dinning sai ta koma ta
kimtsa kitchen d'in.
Tana tsakar yi ne taji alamun tafiya, hakan ya
dakatar da ita gami da fitowa daga kitchen d'in.
Sanye yake da uniform d'in aikinsa wato komai
in black tun daga sama har k'asa, ta k'ara
dubansa a karo na biyu gami da yin murmushi.
Maimakon ya maida mata murtani sai ya fara
k'ok'arin gyara zaman belt d'in wandonsa.
Hakan ba k'aramin k'ona ranta yayi ba gami da
bata mamaki tsantsa.
Ta daure tare da had'iye 6acin ranta ta k'araso
inda yake tsaye tace
"Ina kwana?"
Bai motsa ba ya amsa
"Lafiya."
Ta dai daure tace
"Naga kana shirin fita baka karya ba."
Sai a sannan ya d'ago yana dubanta amma
fuskarsa babu annuri ko kad'an kamar wanda
aka aiko ma da sak'on mutuwa. Yace
"Azumi nakeyi."
Tace
"To... wane iri naga yau ba Monday ba kuma ba
Thursday ba?"
Ya k'ule da tambayarta sai ya kalle ta kad'an
yace
"Dole sai wannan ranakun Allah ya halasta
azumi? Mutum yana iya yi ko yaushe don samun
lada."
Ta k'ak'alo murmushi tace
"Haka ne kam, Allah ya bada lada."
Yace
"Amin, ni zan wuce sai dare zan dawo yau."
Tace
"To a ina zaka sha ruwa?"
Yace
"Zan siya abinci, don yau aikin da ke gabana da
yawa da k'yar zan samu dawowa wannan
lokacin yau."
Tace
"To."
Har yayi hanyar waje sai kuma ya dakata tare
da karkatowa kad'an yace
"Gobe za'a fara gyaran gida, za'a k'ara fasa
d'aki da parlor da kitchen daga can baya."
Bata tanka ba don ta gane inda maganar ta
dosa, shi kuwa gogan daga haka kawai sai yasa
kai ya fice don shi ko ganinta bai son yi yau,
Jidda kawai yake tunani.
Yana fita ta fashe da kuka mai tsanani don ko
maganar auren da ya tarkato bata d'aga mata
hankali irin yau da taga yadda ya chanza mata.
***
Yana office yana shirin fita don an kirasa wai
akwai wani kisa da akayi a wani gida, zasu je
bincike. Yana tsakar tattara mahimman
abubuwan da zai buk'ata aka shigo da sallama.
Ya amsa tare da bada izinin shigowa, sai dai a
yadda ya tsaya yana kallonta cike da mamakin
sauyawar da tayi kamar ba Hajir ba, gaba d'aya
ta zama bak'auya sak!
Sanye take da wani tsanwar atamfa ta k'ok'e
sosai, d'inkin k'auyawa riga da skirt, sai
d'ankwalin daban, fuskarta harda d'ige d'igen
kwalliya. Hakan ba k'aramin dariya ta basa ba.
Sai da yayi mai isarsa sannan ya dakata yana
kallonta yana tafa hannu.
"Bravo! Lallai kinyi k'okari Hajir, aww na manta
Atika ashe. Aikinki yayi kyau, are you ready?"
Tace
"Yes sir."
Yace
"Good, d'auko kayanki inada wani aikin da
zamuje muyi yanzu, amma ina iya kaiki gidana
da zarar na dawo sai mu kaiki gidan da zaki
zauna."
Tace
"Haka ma yayi sir."
Kayanta ta d'auko dake cikin ghana most go
tabi bayansa.
Da sallama suka shiga, tana zaune a parlor tana
karatun wani novel, ganin Faruk ya shigo yasa
ta dakata gami da amsa sallamar tasa. Tare
suka shigo da Hajir, bayan sun zauna Faruk ya
soma magana.
"Meenah wannan 'yar aikin da kika ce a samo
miki ce, sunanta Atika, yanzu ina sauri zan koma
aiki, so zan barta nan sai na dawo sai mu kaita
ko?"
Taji dad'i sosai suka gaisa da Hajir a mutunce
sannan tace masa.
"Ay naji kace yau zakayi dare a wurin aiki, why
not ka bari na kaita da kaina ko ya ka gani?"
Ya mak'e kafad'a alamun oho yace
"Hakane tunda kin iya mota ki d'auki d'aya daga
cikin nawa sai ki kaita, ni zan koma."
Ta masa a dawo lafiya ya fice. Meenah ta kalli
Hajir tace
"Don Allah ki tashi daga k'asa ki koma kan
kujera."
Hajir ta koma kan kujera tana ta faman
murmushi. Meenah tayi murmushi tace
"Ko kefa, bari na k'arasa abincin rana kici sai na
kaiki ko?"
Hajir tace
"To nagode."
Meenah tayi murmushi ta mik'e ta shiga kitchen.
BELLO
‹ › Home
View web version
Monday, 7 August 2017
Maryam Saidu at 08:23
AUREN FANSA 33
✨⭐✨⭐✨⭐✨⭐✨
⭐🌹🌹🌹⭐🌹🌹🌹⭐
🌹⭐✨⭐🌹⭐✨⭐🌹
🌹✨⭐✨⭐✨⭐✨🌹
✨🌹✨⭐🌞⭐✨🌹✨
⭐✨🌹✨⭐✨🌹✨⭐
✨⭐✨🌹✨🌹✨⭐✨
⭐✨⭐✨🌹✨⭐✨🌟
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
AUREN FANSA!!!
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
🌹Na🌹
🌹MARYAM S BELLO🌹
(MSB)
PURE MOMENT OF LIFE WRITERS
_We don't just entertain and educate, we touch
the heart of readers_
P.M.L
Kuyi sorry Fans muna fama da matsalar rashin
wuta🤗
🌹33 🌹
http://MaryamSBello.blogspot.com
Bayan ta kammala abincin suka ci sai ta zarce
zuwa gida don kai ta, Bilki bata zargi komai ba
sai ma murnar samun mai taya ta aiki dama
Zarah keyi to zata fara zuwa makaranta ga
bikinta da za'a sanya.
Nan aka gabatar mata da ayyukan da zata rik'a
yi tun daga su shara, wanki, wanke-wanke, girki
da sauransu.
Kafin ta tafi sai da shiga wurin Baba da ke
zaune parlor yana kallon news, ganin Meenah ta
shigo ya sanya yayi murmushi, ya bita da kallon
k'urilla a lokacin da take zama kan carpet.
"Baba ina wuni?"
Ya gyara zamansa yana kallonta yace
"Lafiya lau Amina, ya gida ya kuma mai gidan
naki?"
Tace
"Duk lafiya lau Baba yana wurin aiki."
Yace
"Madallah, naji zancen zai k'ara aure hakane?"
Ta had'iye miyau mai d'aci tace
"Hakane Baba."
Yace
"Kinsan komai muk'addari ne daga Allah Amina,
kar ki d'aga hankalinki ki jure, ki zamo mace mai
hak'uri da biyayya kinji? Allah ya za6a maku
mafi alkhairi, ya bada zaman lafiya."
Tace
"Amin Baba nagode, daman zan wuce gida
yanzu."
Yace
"To ki gaida mijin naki, da fatan baki buk'atar
wani abu?"
Tace
"A'a Baba."
Yace
"Kuma zaku tafi jami'ah, ku kula sosai, karatu
kukaje yi shi zakuyi Allah ya taimaka."
Tace
"Insha Allah Baba, amin."
Sukayi sallama ta tafi gida.
K'arfe goma saura ya shigo gidan, tana zaune
tana karatun alk'ur'ani, daga bakin k'ofa yaja ya
tsaya yana sauraron muryarta tana karanta
suratul Mujadala, yayi tsaye shi bai shigo ba
haka ma shi bai fita ba, take kuma ya tsinci
kansa cikin nutsuwa don karatun yana masa
dad'i.
Sai data kai aya sannan ya shigo, ganinshi ya
sanya tayi saurin mik'ewa ta isa garesa gami da
amsar brief case d'insa, tayi murmushin da bai
kai zuci ba tace
"Sannu da zuwa."
"Yawwa." Kawai yace ya wuce zuwa ciki, ranta
ya sosu ta dai daure ta bishi ciki a lokacin data
shiga taji alamun watsa ruwa. Sai kawai ta fito
ta zauna parlor tana kallo abinta.
Shiru bai fito ba har kusan sha d'aya ta wuce,
ga ita kuma tana kunyar binshi d'aki yanzu kada
ya fassara ta, sai kawai ta mik'e ta tattara
abincin tasa fridge ta wuce d'akinta.
Gaba d'aya ta kasa bacci sai uban tunani, ko a
mafarki akace mata Faruk zai mata haka bazata
yarda ba. Ganin hakan bashi ne mafita ba ya
zama tilas ta kai kukanta ga Allah don shine zai
share mata, toilet ta fad'a ta d'auro alwalla ta
fara sallah tana kai kukanta ga Allah.
Tana wurin har akayi sallar asuba, hakan yasa
tana gama sallah kanta ya fara yi mata
barazanar ciwo, ta lalla6a ta kwanta ba'a d'au
lokaci ba bacci yayi awon gaba da ita.
Cikin baccin ne taji kamar ana ta 6arar da
abubuwa, a gigice ta farka tana salati, duba
lokaci tayi k'arfe 11:41am lallai tasha bacci.
Hijabinta ta d'auko ta sauko daga gadon, tana
lek'owa taga mutane maza suna ta aiki a gidan,
gabanta ya yanke ya fad'i, maganar Faruk ta
dawo mata a cikin kanta.
"Gobe za'a fara gyaran gida, za'a k'ara fasa
d'aki da parlor da kitchen daga can baya."
Dafe kanta tayi da ke juya mata sannan ta fara
bin bango ji take kamar zuciyarta zata fad'o
k'asa.
Note ta gani a bisa drawer d'inta hannunta na
kyarma ta d'auko ta warware ta ta soma
karantawa...
"Na tafi office, kamar jiya yau ma azumi nakeyi
kar ki wahalar da kanki yin wani girki sai dare
zan dawo, idan masu aikin nan sun gama da na
yau ki shiga d'akina ki d'auko 5k ki basu zan
kirasu na masu bayani."
Wani k'ululun bak'in ciki ne ya tokare mata
mak'oshi, ta daure tayi ta maza ta maida note
d'in ta ajiye a inda ta d'auka, ta rasa dalilinsa
na shan ruwa a waje, at least ko bai dawo da
wuri ba ay ya kamata ya ci abincin data girka
masa komai dare, amma ta lura kamar baya son
cin abincin ne gaba d'aya a nan.
Da k'yar ta sha ruwan tea ta koma d'aki ta
kwanta, k'arar aikin gidan ne ya ishe ta shi
yasanya ta kasa baccin kirki.
Allah ya taimake ta Zarah tazo zasuje
makaranta registration, tayi ta murna ta kirasa
don shaida masa amma bai d'aga ba sai kawai
ta aika masa da sak'o.
Cikin sa'a kuwa suka kammala komai suka
dawo gida, Zarah tsabar haushin gyaran inda
kishiyar yayarta zata zauna yasa ko gidan bata
iya shiga, daga waje sukayi bankwana ta tafi
gida.
Yanda ya umarce ta hakan tayi don kuwa k'arfe
shiddan yamma suka gama, ta shiga ta d'auko
masu kud'in ta basu suka tafi.
Haka kullum sai sun zo da safe su gama k'arfe
shidda, da yake ana sakin kud'i sai gashi ginin
har ya mik'a sosai.
A zamantakewar auren Meenah kuwa babu
abinda ya chanza gaba d'aya Faruk ya chanza
mata kamar bashi ba, bai damu da ita ba bare
cinta, shanta da kuma lafiyarta.
Abincinta ma baya ci ko tayi masa, tun yana
bata excuse har ya fara fitowa 6aro 6aro yana
ce mata bazai ci ba. Ga abu kad'an fad'a da
masifa, nan da nan sai ya hau fad'a ba dalili.
Nan kuwa yana can ya tare wurin Jidda, wani
lokacin can yake da anyi sallar isha'i har goman
dare. Kuma komai ta bashi ci yakeyi, gaba d'aya
ya sussuce ya rikice.
Hakan yasa aka sanya bikin sati uku masu
zuwa, don ya kusa kammala aikin gidansa saura
kad'an ya rage, haka aka tattara aka sanya bikin
aka had'a dana su Zarah da Nabeel.
Shi kuma ya cigaba da had'a lefe da kuma
akwati biyu na kayan fad'ar kishiya da zai kai
ma Meenah.
AUREN FANSA 34
✨⭐✨⭐✨⭐✨⭐✨
⭐🌹🌹🌹⭐🌹🌹🌹⭐
🌹⭐✨⭐🌹⭐✨⭐🌹
🌹✨⭐✨⭐✨⭐✨🌹
✨🌹✨⭐🌞⭐✨🌹✨
⭐✨🌹✨⭐✨🌹✨⭐
✨⭐✨🌹✨🌹✨⭐✨
⭐✨⭐✨🌹✨⭐✨🌟
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
AUREN FANSA!!!
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
🌹Na🌹
🌹MARYAM S BELLO🌹
(MSB)
PURE MOMENT OF LIFE WRITERS
_We don't just entertain and educate, we touch
the heart of readers_
P.M.L
🌹34 🌹
http://MaryamSBello.blogspot.com
Meenah kuwa duk wani abu bazata fasa yi masa
ba, har girki sai tayi koda kuwa bazaici ba, ga
tana k'ok'ari wajen ganin ta kai zuciyarta nesa
don gudun fitina, sauk'inta ma yanzu shiryen-
shiryen bikin Zarah ya fara kankama hakan yasa
ta rage yawan shiga damuwa, don kuwa tana
gida kuma bata cika dawowa ba sai yamma.
Karo na farko da ta fara shiga gidan Aneesha
tunda sukayi aure, bayan ta shirya cikin green
d'in material d'inkin doguwar riga sai ta gyala
gyale marar kauri sosai. Da sallama da shiga
gidan, Aneesah na kitchen tana fama da girki taji
sallama ta lek'o, murmushi tayi tace
"Bismillah shigo."
Bayan ta zauna Aneesah ta shiga kawo mata
lemo da kayan motsa baki, yau duk kunya ta
kama Aneesah ganin itace k'arama kuma ko sau
d'aya bata shiga gidan ba. Meenah tayi
murmushi tace
"Baki gane ni ba ko?"
Aneesah tace
"Nagane ki mana, matar ya Faruk ce nasanki."
Meenah tace
"Allah sarki ya gida?"
Tace
"Lafiya lau."
Shiru ya biyo ba, na 'yan mintina sai suka kafa
ma tv ido ana wani film. Meenah ta katse shirun
ta hanyar mik'a mata kati
"Daman Iv na kawo maki na bikin sister d'ina."
Aneesah tayi murmushi tace
"Allah sarki, Allah yasa alkhairi yasa munada
rabon gani."
Tace
"Amin ni zan koma."
Aneesah tace
"Haba tun yanzu? Na d'auka sai kin ci abinci
tukunna."
Meenah tace
"Kai haba, bamuda nisa ta yaya zan cinye ma
amarya girkin angonta?"
Aneesah tayi murmushi cike da kunya tace
"Kai a'a wallahi ba haka bane."
Meenah tayi dariya tace
"Kedai wasa nake miki, idan na dawo next time
zanci insha Allah."
Aneesah tace
"To ina zuwa."
Ta mik'e ta shiga ciki, can ta dawo hannunta
d'auke da leda tana murmushi tace
"To ga wannan."
Meenah tace
"La harda wahala haka?"
Aneesah tace
"Ba wata wahala wallahi."
Meenah tace
"To nagode ni zan tafi."
Aneesah tace
"Nima zan shigo, ay kina WhatsApp ko?"
Tace
"Eh inayi."
Aneesah tace
"Zamu rik'a gaisawa insha Allah, nagode sosai
wallahi."
Meenahtace
"Babu komai wallahi."
Sukayi bankwana ta tafi, tunda Meenah ta tafi
Aneesah ke raya kyawunta da kirkinta, sai taji
haushin kanta da meyasa bata ta6a shiga sun
gaisa ba, amma ta k'udiri a ranta zasu fara
zumunci daga yau.
****
Meenah sun soma lectures, yanzu damuwarta ta
ragu sosai, kuma tayi sa'a yana bata mota idan
zata tafi.
Ranar litinin da daddare sai ga Faruk ya shigo
da akwatina guda biyu, tunda Meenah ta ganshi
tasan na menene, don haka bata nuna
damuwarta ba ko kad'an, sai ma fatan alkhairi
da tayi masa.
Hakan ba k'aramin mamaki ta basa ba, kuma
sai ta bashi tausayi, nan ta bubbud'e akwatina
ta gani bayan ta gama ta tashi ta shiga ciki. Ya
dad'e zaune ranar farko da ya ji auren ya fita a
ranshi kuma.
Mik'ewa yayi cikin sanyin jiki ya bita ciki, tana
kwance a d'aki tayi ruf da ciki idanunta a
lumshe, hakan ya k'ara bayyanar da zara zaran
eye lashes nata. Ya dad'e tsaye yana kallonta
kafin ya tako a hankali yatsaya yana k'are mata
kallo. Sanye take da 'yar k'aramar vest pink
color sai tasa pink dogon wando, harta ribbon
d'in kanta pink ne, daga gani ba bacci take ba
amma kuma tak'i bud'e idanunta.
"Meenah..."
Ta bud'e idanunta a hankali ta sauke bisa
fuskarsa da yake kallonta kafin ta amsa da
"Na'am."
Sai kuma ya rasa abin cewa, ya sosa kai yace
"Dama zuwa nayi naji ko kina lafiya."
A ranta tace
"Sabon salo sai kace damuwa yayi da ni bare
kuma lafiyata."
A fili kuwa cewa tayi
"Lafiya lau."
Shi yadda take sharesa d'innan yaji ba dad'i,
yayi missing kula da shi da takeyi, amma yanzu
ko kallonsa bata son yi, magana ma da k'yar
take amsa masa. Da yanzu ta tambeyesa ko
yana buk'atar wani abu, amma yanzu ta daina.
"Ko kana buk'atar wani abu ne?"
Yayi sauri yace
"A'a, sai da safe."
Tace
"Allah ya kaimu."
Ta rufe idanunta alamun bacci, ya dad'e tsaye
yana kallonta kafin ya fita daga d'akin a
sanyaye.
Yana shiga d'akinsa ya iske miss calls ba iyaka
daga Jidda, kiranta yayi bugu d'aya ta d'auka.
"Haba my dear ina ka shiga inata kiranka?"
Yace
"Sorry na shiga wanka ne."
Yace
"Ok daman kud'in da zan siya anko ne na 'yan
mata baka bada ba..."
Yace
"Kud'in anko kuma?"
Tace
"Eh da kud'in k'unshi."
Yace
"To fah har nawa?"
Tace
"Gaba d'aya dubu 500 ne!"
Yace
"What? Dubu 500? Gaskiyar magana ko banida
su, bazan iya baki dubu 500 ba."
Tace
"Haba mana my dear, wai nan fa na maka
sauk'i."
Yace
"Dubu 100 zan baki, idan baki so good and fine."
Tace
"Wai wannan fad'an na menene daga
tambayarka kud'i?"
Yace
"Jiya jiya kika tambayeni dubu 200 na baki,
shekaranjiya dubi 50, yanzu kuma dubu 500, to
banida su."
"Don Allah kayi hak'uri ka bani, daga yau bazan
k'ara tambayarka wasu kud'in ba."
A fusace yace
"Ke kar ki raina min hankali fa! Na riga nace
bazan baki ba, don haka sai da safe."
K'it ya kashe wayar, cike da jin haushinta, gaba
d'aya haushinta yakeji. Yau ko baccin kirki ya
kasa, haka yasa ya mik'e ya lek'a d'akin
Meenah tana kwance tana bacci peacefully, ta
masa kyau sosai, sai dai dole ya koma d'akinsa
ya kwanta amma ina ya kasa bacci, sai gabansa
dake ta fad'uwa ya rasa dalili.
Washe gari sai ga 'yan jere, nan sukayi ta
hidimarsu ita kuma Meenah ko fitowa ma batayi
ba, tana d'aki tana jinsu suna ta aikin jerensu,
har dare suna nan basu gama ba, har washe
gari sai da suka dawo da safe suka k'arasa
wanda basu idasa ba.
Itama Meenah jeren Zarah suka tafi the next day,
hakan ba k'aramin dad'i yayi mata ba.
Biki nata matsowa yau saura kwana biyu a
d'aura aure....

AUREN FANSA 35
✨⭐✨⭐✨⭐✨⭐✨
⭐🌹🌹🌹⭐🌹🌹🌹⭐
🌹⭐✨⭐🌹⭐✨⭐🌹
🌹✨⭐✨⭐✨⭐✨🌹
✨🌹✨⭐🌞⭐✨🌹✨
⭐✨🌹✨⭐✨🌹✨⭐
✨⭐✨🌹✨🌹✨⭐✨
⭐✨⭐✨🌹✨⭐✨🌟
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
AUREN FANSA!!!
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
🌹Na🌹
🌹MARYAM S BELLO🌹
(MSB)
PURE MOMENT OF LIFE WRITERS
_We don't just entertain and educate, we touch
the heart of readers_
P.M.L
🌹35 🌹
http://MaryamSBello.blogspot.com
Washe gari aka kai lefen Zarah akwati bakwai da
kit, yayinda aka kai ma Jidda akwati takwas da
kit.
An fara gudanar da shagalin biki a wadace, sai
dai matsalar Jidda d'aya da ta masa maganar
kud'i sai sunyi fad'a, sannan idan har suna tare
yana nuna mata so da k'auna marar iyaka
amma da zarar sun rabu shikenan ko kiranta
baiyi sai dai ita ta kirasa. Hankalinta ya fara
tashi haka kuma ta soma tunanin ko maganin ya
fara dena aiki ne?
Ranar da akeyin event d'in Jidda anyi kwalliya ta
gogaggun 'yan matan nan, ta had'u har ta gaji
duk da ba wani kyau gareta na azo a gani ba.
'Yan matanta kansu da ka kallesu kaga
gagaggun 'yan mata masu ji da kansu, Luby best
friend d'in amarya ita nata ashobin ya banbanta
da na sauran ya kuma fi tsada da kyau.
Suma kuwa su Zarah na can suna shan tasu
hidimar, da yake bazasuyi abubuwa da yawa ba,
kuma bikin nasu yafi tsari da kyau.
K'arfe biyar da rabi Faruk ya iso ya kira wayar
Jidda, can sai ga ta fito itada k'awayenta su da
yawa kamar wata tawaga.
Bayan sun iso aka fara gabatar da events cike
da kwanciyar hankalin, Luby ita ta fara bud'e
wurin da rawa yadda kasan ba kowa wurin haka
take tik'ar rawa ba ko kunya.
An gayyato amarya da ango don taka rawa, shi
kam ango kunya ta hana shi rawa sosai ba, ita
kuwa amarya bako kunya sai wani rausaya
takeyi kamar ba amarya ba. Faruk sai yanzu
yake k'ara gane halin Jidda, bai ta6a tunanin
haka take ba. Sai yanzu ya fara tunanin aurensu
shida Meenah komai cikin tsari haka akayi shi.
K'arfe sha d'aya aka tashi taron, ya ajiye Jidda
gida shima ya nufi nasa gidan.
Washe gari ya tashi yana ta hidimar d'aurin
aure. K'arfe biyu daidai dubban mutane

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login