Showing 48001 words to 51000 words out of 94661 words

Chapter 17 - RAINON SOJA COMPLETE Hausa Novel

Unknown   

05 Oct 2024

45180

Ma'eesha na! Ta kira sunan ma'eesha da ta zuba mata lumsassun idanun ta kamin tace “ Na'ma Mami”.

Kin shirya Uncle Haidar ya ƙara Miki RAINON SOJA a karo na biyu?. Zai kula dake sosai ina da yarda dashi da amincewa da zai kula mun dake 💯 . Cike da Yarinta ta saki Murmushi tana gyaɗa kan ta tace da cewa “ Eh mami nasan Uncle zai kula dani sosai . Muje fara shirin tafiya 💃🏻 nidai kam sai da ɗan hawaye ya tsillo daga ido na😢 don na tausaya ma Ma'eesha a hannun Ali haidar a wannan karon ”.


Tana Rungume a jikin mami suka nufi bedroom din ta suna barin falon . Jidder taso hana wannan tafiyar amma kuma bata da yanda zatayi saboda Tafi son taga ta raba Mami da Ma'eesha kamin ta dawo ta ɓanɓareta ta da Haidar,amma ita har a yau so take taga Ta bude ido Ma'eesha ta bar cikin gidan .
**
7:00pm.
Zaune suke duka a falon Daddy kowa da Abin da yake yi. Ma'eesha na gani daga ƙasa inda Ƙafar Daddy yake tana rungume da yar teddy din ta Pink mai kyau tana murmushi alamun Daddy wani maganan yake faɗa mata . Ɗagowa tayi tana kallon Khalil da shima ita yake kallo . Sosai yake tsintar kansa cikin yanayin jin daɗi a duk lokacin da yaga murmushi a tare da Ma'eesha ”. Ya Khalil i will miss you ”. Ta furta tana kallon sa . Murmushi yayi yana danne abun dake taso mata kamin yace “ i will miss you too Ma'eesha na”...Da Sauri Ma'eesha ta miƙe tana nufar inda Khalil yake tare da rungume shi.... Rungume ta yayi yana murmushi tare da cewa "nan kusa zaki dawo ai . Wani irin zafi Aliyu................!





*Ban yarda ki karanta mun baki biyani ba . Wanda ya karanta shi da Allah . Masu ɓukatar regular group ₦500 vip group ₦1000 SPC payment ₦1500 via 6037312299 Mohammed A'isha keystone bank*
[1/13, 7:33 AM] +234 704 512 5150: *🕊️RAINON SOJA🕊️*
*Through the gate of love a valiant fearless heroical and Sympathetic Story.*
https://youtube.com/@mamanteddy4123?si=1cwxAAGsGEzYkelS
Subscribe to MAMAN TEDDY channel @youtube.
24.
Ya Khalil nifa ƙaramar yarinyace kai ne fa naji kana yi ma Anti Jidder faɗa kan karta fara soyayya! “Yesss”Na sani Ma'eesha, amma tawa soyayyar ba shiririta bane irin nasu . I really......A'a Ya Khalil Anty Maryam fa? Kwanan fa Za'a yi baikon ku . Muryar Ma'eesha ya kuma katse ta wanda har kyarma jikin ta ke yi . Ma'eesha!!! Ya kira sunan ta cikin wani irin Murya wanda bata taɓa jin sa da irin ta ba . Hummmm .... Furzar da Huci yayi kana yace “ Ma'eesha Ni SOJA ne , duk Abinda zai saka Soja ya gurfanar da kan sa da Gwiwowin sa ƙasa ba ƙaramin abu bane ba , babba ne , wanda girmanta ya kai Akira wannan abun da rayuwar sa . Ma'eesha idan na rasaki numfashi na zai dakata da Aiki . Ina nufin zan zaɓi mutuwa da Rayuwa ta😭”. Dam-dam-dammmm ƙirjin Ta ya buga da ƙarfi ....cikin Muryar matsanancin kuka ta furta “ Sorry Ya Khalil ina Sonka”. Wani irin baya Aliyu yayi da yake jikin ƙofan yana zame hannun sa a hankali duhu duhu na gilma ma idanun sa . Ji yayi jikin sa yayi Wani irin mugun sanyi sam babu ƙarfi a tare dashi bisa ga jin Furucin Ma'eesha na “ Ina Sonka!”. Zazzaƙar Muryar ta ne ya kuma katse shi tana faɗin “ Kar kayi tunanin bana sonka Ya Khalil kome kace nayi maka a shirye nake zan maka shi ”.

“ Cikin Sauri cike da jin Daɗi mara iyaka Khalil ya miƙe daga gurfanen da yake , Hannun sa biyu yasa yana tallabo kuncinta ta tare da saita idanun sa yana Ɗaurawa bisa nata. “Thankyou Ma'eesha , na gode!

Ya Khalil to Anty Maryam fa? Da.....shii ki manta da Wannan maganan zan Auri Maryam a wannan shekarar ke kuma zan cigaba da dakon soyayyar ki har ki girma ki kai lokacin da Daddy zai Aurar dake , A wannan lokacin zamuyi Aure mu gina Rayuwar mu cikin jin daɗi . Kece nake so ki haifa mun ƴaƴa masu kama dake ....ya ƙare maganan yana Ɗaga mata gira tare da Sakin mata murmushi kana ya cigaba da cewa “ Zan Auri Maryam ,amma ba zata haihu ba . Kece zan jira ki zo ki haifa mun masu Albarka ”.

Cike da Yarinta Ma'eesha ta gyaɗa masa kai tare da cewa “ Shikenan Ya Khalil zan yi barci yanzu ”. Alright sweat dream...ya furta yana kama ta tare da nufar Bed ɗin ta sai da ta kwanta sannan ya rufa mata bargo yana takawa tare da rage hasken fitilun Bedroom din yana nufar Ƙofar fita .

Jin takon sa yasa Ali Haidar Saurin barin wurin yana nufa falo .

A wannan dare a taƙaice sam Aliyu ya gaxa rintsawa , zuciyar sa na masa saƙa da Warwara . Inda ya kasa gasgata wani ɓangare ɗaya na Zuciyar sa . Sai dai kafewa da yayi akan cewa “ Khalil na son lalata Ma'eesha ne . Har ya fara tunanin ɗaukar mataki da fushin Zuciyar sa ,sai kuma yace “ A'a ba haka zan yi ba , Ni yanzu da zan tafi tare da ita , ganin ta sai yayi masu duka wuya .bare har ya kawo wani zancen shashanci mtsww .

**
7:35am.
Mami na hango gaban dressing mirror tana gyara gashin kan Ma'eesha da yake fidda Sanyayyar ƙamshi , ga tsawo da cika sunan ta kama mata shi ne wuri ɗaya amma Tudunshi har yayi yawa gashi ya sauko har gadon baya . Ka rantse da Allah Jinin mami ce itama wato fulani . Riga da Wando ne ta jikin ta ,irin suit masu kyau na mata . Sai mami ta ɗaura mata Hijab ƴar ƙarama wanda bai ƙare sauka kafaɗa ba ”. Turare take sa mata tana murmushi tare da cewa “ Yau sai na Lagos . Yessss Mami😄 Ma'eesha tayi maganan tana Wangale mata baki cike da fara'a kaman mai jin daɗin tafiyar ,nan kuwa dole ne yasa ta murmushin . Gyara mata fuska tayi cikin simple make Up Babu Hayaniya. I love my daughter .....Ina sonki Nima Mami ”. Hannu Mami tasa tana rungume Ma'eesha tare da cewa “ ki kula sosai kinji Eaasha na?”............!

**
Dinning room
Tun da Aliyu da Khalil suka zauna babu abin da suke yi ma juna face auna ma juna kallon banza . Duk da shi Khalil na kai Zuciyar sa nesa . Sannan duk abin da suke yi babu wanda ya gane daga gare su .

Keeee Da Allah kici a hankali ....kaman Ƴar matsiyata wanda suka fito da ga fari? . Muryar jidder ya katse su inda take doka mawa ma'eesha Tsawa cikin Faɗa da hantara . A hankali Ma'eesha ta janye Fork ɗin da take cin Irish tana Ajewa a gyefe....inda cikin Faɗa Mami ta katse jidder da cewa “ Akan ki take ne? Masifaffiyar banza kawai , Ai sauri take kada Ali ya fara Mata nashi sababin.....ku kiyaye ni duka ”.


Gummm Jidder tayi tana cigaba da Kai Cuscus bakin ta , ranta a ɓace don bata son tayi ma Ma'eesha faɗa Mami ko Daddy su katse ta .

Muryar General Saleh ne ta katse su inda yake furta “ Kici a hankali Ma'eesha ba zaki bishi ba sai kin ƙoshi kinyi nakkkk sannan .

Gyaɗa masa kai tayi kana ya cigaba da cewa “ Kai kuma Ali ina so nan da 1 mount to 2 mount kafin bikin Khalil ka fidda wacce kake so ka Aura yanda muna gama nashi sai naka . Saboda dukan ku kun isa aje iyali kuna da Abunyi da ƙarfin ku haka da Arziƙin ku ka fahimce ni?.

Shiru Haidar yayi na yan sakanni don a yanzu shi babu lissafin aure a rayuwar sa , a cewar sa Abin da ake yi ma Auren yana Samun na bati a banza a waje . Kuɗin sa nayi masa komai don haka baya sha'awar aure a yanzu .

Aliyu da kai nake yi .....Muryar Daddy ya katse shi inda cikin sauri Aliyu ya furta “ Okay Daddy inshallah kamin lokacin ma , Abun da yasa har yanzu kuka ji shiru saboda Ni ina so na Auri SOJA ce . Ma'ana matar da zan Aura ta kasace SOJA kama na ” .

SOJA...!!!!

Duka suka haɗa baki wurin furta kalmar ciki har da Daddy da abun bai masa ba sam . Ita kuwa Mami buɗan bakin ta cewa tayi “ wow that's very good, Hakan yayi sosai Haidar Nima zan so ganin hakan . Ai hadin yayi ko Janar? . Ta ƙare Maganan tana duban inda Daddy yake ya saki baki yana kallon ta .

Kamin Daddy yayi magana ne Khalil ya amshe da cewa “ No Mami Sam baiyi ba . Ni fa babu Abin da na tsana irin naga mace wai SOJA abun ba burgewa sam .


Hahahaha!
Wani irin dariya Aliyu yasa wanda duka sai da suka tsaya suna binsa da kallo . Kana ya tsagaita yana kallon Khalil tare da cewa “ I found the solution, Ma'eesha taho mu wuce ”.

Cikin Sauri Ma'eesha ta miƙe tana ma su Mami waving tare da furta “ Dad Byebye! Mami anti jidder sai na dawo ”. Banza jidder tayi mata a haka ita dai ta wuce Daddy suna biyo bayan su har farfajiyar gidan sai da suka fice daga gidan ne sannan suka koma ciki ” .

Kaduna ya ɗau hanyar nufa inda tun shigar ta tayi shiru ta koma kamar marainiya .

Aammm Ma'eesha me kike son ki karanta nan gaba? .

Muryar Aliyu ya katse ta inda cikin sauri ta kalli inda yake , amma sam idanun sa baya ma akan ta . Cikin sakin fara'a irin nata ta furta “ I want to be a nurse ”. Ba tare da ya kalle ta ba idanun sa na kan hanya cikin bada umarni ya furta “ Ba zakiyi ba , SOJA zaki zama🙀 wannan tafiyar da zamuyi za'a fara baki horon atisayen zama soja........................!



*Don girman Allah kar ki karanta indai baki biya Ni ba . Gama su buƙatar wannan littafin regular group suna biyan ₦500 Vip group ₦1000 SPC payment ₦1500 via 6037312299 mohammed Aisha keystone bank ko katin MTN ta Wannan number 08081202932.©Maman-teddy..... YouTube channel@MAMAN TEDDY.* *https://youtube.com/@mamanteddy4123?si=1cwxAAGsGEzYkelS*
[1/13, 7:33 AM] +234 704 512 5150: *🕊️RAINON SOJA🕊️*
*Through the gate of love a valiant fearless heroical and Sympathetic Story*


https://youtube.com/@mamanteddy4123?si=1cwxAAGsGEzYkelS
Subscribe to my channel@maman teddy.


26.
*Don Allah kar ki karanta wannan labarin indai baki biya kuɗin sa ba . Ga masu buƙatar payment na littafin Rainon soja ga yanda tsarin yake.... Regular group₦500 Vip group₦1000 SPC payment₦1500 via 6037312299 Mohammed A'isha keystone bank ko katin MTN ta Wannan number 08081202932*


Taƙaici ne ya kama Ma'eesha sai kawai ta cigaba da rera kukan ta don shi zaifi mata Daɗi a yanzu....Tun da babu mafita a tsakanin ta da Haidar abun da yaso ya kuma ga dama shine yake yi , idan yayi niyyar Abu babu wanda ya isa yasa shi ko ya hana shi . Hasbunallahu wani'imal wakeel . Shine kalmar data Furta a zuciyar ta . Jikin ta har ɓari yake yi na tsaban shiga tension . A Zuciyar ta cewa take “ Yanzu shikenan mafarki na ya wargaje kenan na zaman Nurse . Yanzu bani ba wani Aikin Asibiti sai aikin shiga Daji ? , Kai Uncle a cikin rayuwata matsala ne . Kallon sa tayi nan taga hankalin sa ƙwance hannun sa ɗaya na Driving ɗaya kuma na bisa Gyefen Kuncinsa yana Shafa Sajen fuskar sa da ya ƙwanta luffff .... Ji Ma'eesha take tamkar ta kame sajen ta fizga da ƙarfi don a yanzu tafi son taga ɓacin Ransa fiye da Annurin sa , tun da shima Baya son ganin farin cikin ta . Komawa tayi tana kwantar da kanta bisa Kujerar da take bisa kai , tare da kallon gyefen hanya tana lumshe sexy eyes ɗin ta . Tun daga nan babu wanda ya ƙara furta kalma ɗaya sai dai kowannen su da Abin da yake saƙawa a Zuciyar sa a haka har suka isa NDA . Inda a yanzu Da yawa Abokanan sa suke nan da Aiki don sun zama manya . Wasu kuma suna wasu garuruwan na daban . Don shima a gobe yake so su wuce Lagos .

**
Kaiwa da dawowa Hajiya Falmata ta keyi , tana cigaba da Bama ma'aikatan nata umarni . Wani irin Ɗauri tayi shi ya turo gaba ta wani kinkimashi irin na hamshaƙan Hajiyoyin nan marasa kirki Ɗaurin No Respect🤨.

“Oya kuyi maxa a fita dashi , a kwashe Kaman Buhu 100 haka Ina tunanin zasu isa ”. Ta furta zancen tana basu umarnin kwashe Buhuhunan Shinkafa ta Alhajin su . Sudai su Hajiya Turai da Hajiya Atika suna daga Sama suna Ƙallon ikon Allah, kowacce tana part ɗin ta ne , amma idanun su duka na kan inda Ake fitar da Buhunhunan shinkafan nan. Kowaccen su ji take a ranta inama ace itace ta samu irin wannan iko haka ?.

Wani irin tsaki Hajiya Atika tayi kana tace “ Rabi wai Anya kina ganin Aikin Bokan nan yana yi kuwa? Naga har yanzu banda iko irin na Hajiya Falmata ne a cikin gidan nan! Yo kina tsammanin idan da nice na fitar da Wannan Shinkafar zan kwana cikin gidan nan lafiya? Ai da sai dai na kwana a garin Kano ba dai nan ba .

Humm...Rabi ta sauke Numfashi na munafurci da ƙara famfo kana tace “ Ƙwarai kuwa Hajiya shi kuwa Aikin sa keyi tamkar yankar wuƙa , ta ƙare maganan tana fiƙi fiƙi da ido kamar na Ƙaramar kifi ”. A Zuciyar ta kuwa cewa take “ A'a ina ai ba zan yi sakacin da zaki daina aikana Wurin Aruguntsu ba . Saboda nima ina samun nawa ...yanda nake babu miji idan naje muna ɗan jefa zuciya nishadi , don ko aikin ki da yake yi sai ya neme Ni sannan , shi ba kudi yake so ba , Yaji daɗin mace kawai . Kudi kuma nike riƙewa.

To yanzu ya kike gani za'a yi ? Nifa SO nake a haɗa mawa Falmata Masifar da Ayau sai tayi kwanan gidan su ....Don wannan izzar nata da mulkin nata ya fara isa ta haka nan . A'a Ina magana kuma kinyi shiru ??. Hajiya Atika tayi maganan tana kallon Rabi cike da nuna damuwarta .

Allah yaƙarama Hajiya Lafiya tuba nake ”.

Hummm ....jan numfashi Atika tayi tana saukewa kana tace “ Me kika gani? Ya kuma za'a yi yanzu ?”. Ai yanzu Hajiya Zan gudu na isa gurin Aruguntsu amma kin san idan Aikin yanzu yanzu kike so sai an bashi masu kauri .

Wani irin dariyar jin daɗi Hajiya Atika tayi kana tace “ Ai wannan ba matsala bane indai za'a cika Aiki ....! Maza muje ki amsa sai ki wuce . To Hajiya Da girman kujeran ki . An buga Dole a bariki kece ta gaban Gaban Kowa indai a fadan Alhaji ne . Kan Hajiya Atika ne ya kara girma Wani irin cika wuya take yi cike da jin daɗi kana tace “ Kai Rabi wannan kirari haka ”. To ai gaskiya ne Hajiya kin san daga kuma ƙinta sai ɓata ”.

Muje yanzu a kai ma Aruguntsu bana son yau Falmata tayi kwanan sukuni .

**
Kaduna
11:00am.
Tun da suka isa direct Ɓangaren ƴan termer 1 ya nufi da ita . Wani babban fili Ma'eesha ta gani wanda duk abin ka babu karshen ta ,don idan kayi gudu gudu sai dai ka ganka a irin dajikan nan . A can bayan wurin kwanan Ɗaliban Sojan yake nan ne kuma wurin atisayen su.

Kallon Ɗaliban Sojan take yi maza dai sun fi yawa ,don mata bai fi biyu ta gani ba kuma ba Musulmai bane.

“Uncle What I'm I going to do here? , Kalli fa ka gani Wai Soja ka kawo Ni nayi ko girki kace zan rinƙa maka ? . Ta ƙare maganan tana narke masa tare da shirin saka masa kuka 😭 tana yi tare da kallon wani irin murɗaɗɗen Soja da yake ta Aikin Atisayen Motsa jiki da gudu .



Muryar Haidar ne ya katse ta cikin dakewa na ba wasa ya furta “Wanne kika yi choosing? ”. Da Sauri Ma'eesha ta furta “ Mai girkin ka zan zama ”.

Weldone Sir”. Muryar sojojin da sai a yanzu suka farga da isowan canonel Aliyu haidar suna darawa tare da ƙamewa. Gyaɗa masu kai yayi cike da bada umarni cikin ɗaga murya irin na Sojoji ya furta “ Su cigaba da Atisayen su , nan take kowa ya koma bakin aikin sa”.

Kallon Henry yayi kana ya kalli Ma'eesha yana furta “ maza jeki kuyi tseren gudu tare 🥺 Idanun Ma'eesha ne suka juya . Wanda sam ta kasa motsi don ita fa kalallaɓa ce , Wannan wacce irin rayuwa ce , Wallahi nasan ko da nake ƙarama ba ƙaramin wahalar Sa nasha ba .

Cewa nayi kiyi gudu dashi fa? Ya furta kalmar cikin doka Tsawa , wanda jiki na rawa Ma'eesha ta matsa ga Henry...........🤣🤣🤣tirƙashi Jama'a ya kuke ganin Ma'eesha da Wannan rangajejen halittar? Meye mahangarku bisa ga Abun da Haidar yake yi ma Ma'eesha , yana cikin So ne ko kuma ƙiyayya😌🥹. Meye ra'ayin ku bisa ga soyayyar Khalil da Ma'eesha .? Sannan waye ne asalin Alhajin Yes da No🤣 wato mijin su Hajiya Falmata?.

*Don Allah kar ki karanta mun wannan labarin indai baki biya ba . Regular group ₦500 Vip group ₦1000 SPC payment ₦1500 via 6037312299 Mohammed A'isha keystone bank ko katin MTN ta Wannan 08081202932#mamanteddy.*
[1/13, 7:33 AM] +234 704 512 5150: *🕊️RAINON SOJA🕊️*
*Through the gate of love a valiant fearless heroical and Sympathetic Story*

https://youtube.com/@mamanteddy4123?si=1cwxAAGsGEzYkelS
Subscribe to my channel@maman teddy.

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login