Showing 18001 words to 21000 words out of 79238 words

Chapter 7 - UBANA NE KO KISHIYATA

trying your no for a long period of time bana samun ka,har Na zo Na hakura,

Ayya wlhy Habeeb line ina ne ya samu matsala Na canza sabo,sai kuma nayi losing contact in ka,how have you been,wai me ma ya kawo ka Bauchi,

Dariya doc Habeeb ya sanya sannan ya ce see you ai kai zan wa wannan tambayan domin Bauchi kam ai garin mu ne,and wlhy a nan Na samu aiki,so ka ga am working here kai fa me kake yi a Bauchi,

Hmmm bari kawai Habeeb ni ba Na manta ba Ashe kai Dan Bauchi ne wlhy transfer aka mun daga 44 xuwa nan hospital in jiya shigowa ta ma,

Ayya toh ubangiji ya sa da abunda ya tare,where is madam ko ka bar ta a can masaukin ka,am very sure yanzu kam kuna da babies ko,

Jin abunda ya fadi ne ya sanya annurin fuskan Doc Nameer daukewa cak,lura da hakan ne ya sanya Habeeb cewa am sorry friend ko Na fadi abunda be dace bane,

Aa sam baka fadi abunda be dace ba ya daure ya ce,sannan ya kara da Alhamdulillah we are blessed with a little beautiful daughter, saidai unfortunately Noor ta koma ga me sama gurin haihuwar angel,

Allahu Akbar am so sorry for your lost friend,Habeeb ya ce yana girgiza kai,domin ba karamin mamakin mutuwar Tata yayi ba,and ya tausaya wa Nameer in domin shi kanshi sheda ne da irin kaunar da ke tsakanin Nameer da Margayiya,

Ubangiji ya mata rahma ya jikan ta sannan ya raya bayan ta,Ameen ya Allah Habeeb thank u so much,

Haba babu komai Mr handsome, so ina angel in take,wlhy Na baro ta Kaduna a gurin mama jiya da zan taho,

Allah sarki Allah ya raya ta bisa sunnah sannan yayi mata Albarka ya kuma baka mata ta kwarai Wanda za ta maye maka gurbin noor ta kuma rike Haanaan da amana,murmushi kawai Nameer yayi domin shi yana ji a jikin shi har ya koma ga Allahn sa bare kuma Kara soyayya ba balle har a kai ga batun aure,

A fili kuwa cewa yayi me hali baya fasa halin shi Habeeb har yanzu dai surutun Na nan,na biye ka sai mu kwana kana mun zuba,

Dariya Habeeb in yayi sannan yace ga ka kai kuma miskili ba baka kaunar surutu ko kadan saisa Sam bara ka iya zaman gida Na ba ashe domin daga ni har Madam da little boy in mu surutu gare mu,

Wait Habeeb wai kana nufin kayi aure,dariya ya dan yi sannan yace getting to 2 years ke nan da aure Na har Allah ya kawo karuwa mun samu baby boy,

Kai Masha Allah ubangiji ya raya shi da imani Allah ya kade fitina a zaman ku,ameen ya Allah doc Nameer ashe dai za mu Kara haduwa ikon Allah sai gashi guri daya za mu Na aiki,kai it was so nice seeing you again,

Smile Nameer yayi yace it was nice seeing too,ni dai yanzu nuna mun office in senior Doc in da ke gurin nan nayi reporting don Na samu mu fara aikin da kake murna an hada mu guri daya,

Dariya Habeeb yayi sannan yace bara ka gane bane,wlhy,Nameer haduwa da Wanda ka sani tun before dadi gare shi,mu je in gwada ma office in shi,sunan shi doctor Bashir sai kayi a hankali don mutumin Dan banza ne,

Kai kawai Nameer ya girgiza domin in dai surutu ne da gulma Habeeb to ya iya shi kamar wata mace,

Har bakin office in doctor Bashir Ubaidullah ya rako shi sannan yace da shi in kun gama da shi ma hadu a new office in ka ko nawa,da ki kawai ya amsa shi sannan yayi knocking in kofar bakin shi dauke da sallama,

A zaune ya tarar da Doc Bashir bayan yace da shi ya shigo,seat ya nuna mishi alamun ya zauan,bayan ya zauna in ne,yake tambayan shi daga ina,

Nan Nameer yayi masa bayani kan daga kaduna aka mishi transfer nan,

Saida ya kare masa kallo sannan yace ina takardun naka,

Akan table ya aje masa,sannan Bashir ya shiga dubawa a gadarance,ganin komai ya cika ne ya sanya shi dagowa yace well doc Nameer Abdallah Na ga takardun ka,komai normal ka koma gida daga gobe za ka fara aiki,

Da mamaki Nameer ke kallon shi why zai ce ya koma sai gobe ya dawo bayan shi ya dauka ya zai fara aiki,sai sa ma yayi sammakon sassafe,

Yana kokarin magana ne ya ji an bango kofan,a zuciye Bashir yace wannan wani irin Jaki ne haka zai bugowa mutum kofar office, ganin Nurse Kareematu ce tsaye tana watsa mishi kallon banza domin ta ji me ya ce wato ni ce jakar shine kalman da ta furta tana hararan shi,

Dariya ya dan yi sannan yace dadi Na da ke saurin fushi wallahi ai ban San ke bane,tsaki ta ja sannan tace wai ka je kayi baki,

Da mamaki ya maimaita kallman baki kuma ni kuma suka ce suna nema,

Ji wani tambayan iskanci Bashir in ba kai suke nema ba meyasa zan zo Na fada ma,SEN da wani matashi,

Jin sunan da ta ambata ya sanya da sauri Mike wa sannan yace haba Kareema why baki fada mun since ba kika sa zan bata masa lokaci ya kare yana gyara zaman lap coat in shi,

Nameer ya kalla sannan yace I got important issues a gaba Na so see u tomorrow kawai,ah Doc kace sabuwar hannu muka yi,Kareematu tace tana me bin shi da wani irin mayen kallo,

Jin abunda ta fadi ne ya sanya Nameer mikewa tare da watsa mata wani irin wulakantattcen kallo sannan ya bar office in,cike da mamakin wani SEN ne ya zo cikin asibitin nasu,

Doctor Bashir kuwa yanda kuka san zai yi wa SEN sujjada tsaban dukawa yana gaida shi,fuska sake SEN ya amsa shi tare da tambayan ya aiki,domin ba karamin murna yayi ba da jiya ya kira shi a waya ya sanar da shi plan in su Na ta working out,

Afzaal ya gaida wanda ya amsa shi cike da isa da gadara kamar Dan sarki,sannan suka nufi Isolated room inda aka killace Nadeeya,

Tun daga waje suke jiyo ihu da dariyar ta da alamun surutu take da kanta take irin wannan mugun dariyan,

Saida ya rubuta pin code in sannan kofar ta bude suka samu suka shiga kofar ta rufe,

A dantamalin kasan tiles suka same ta tayi zaman yan daukan karatu gashin kanta ya sauko sun rufe mata har fuska,Wanda su take irgawa wai don ta ga yawan,su sai ta kai quarter in counting in Sai ta manta shine abun yake bata dariya,

Da ido Afzaal yake bin ta da kallo domin ya kasa yarda wai Nadeeya ce wannan zaune a kasa hakan nan da sunan tayi hauka,

Kusa da ita SEN ya zo tare da taba shoulder in ta yana fadin princes look who is here to see you,

Juyowa tayi a razane don Jin an yi mata magana saidai Sam bata gane me yace ba,karaf idanun ta suka sauka a kan fuskan Afzaal,

Wata iriyan ihu ta sanya me mugun Kara Wanda saida kusan rabi yan cikin clinic in saida suka ji a ciki kuwa har da Nameer Wanda ke Dan zagawa don ganin ya tsarin gurin yake kafin zuwa gobe ya fara aiki,

Kamar Wanda aka tsikara ta mike da sauri har tana harde kafa tana kusan faduwa,flower vase in jikin gadon ta ta dauka kafin kowa yayi auni ta kwada wa Afzaal a goshi Wanda nan ya fashe kalban kuma ta yanka mishi fatan goshi nan take jini ya balle masa,

Wata iriyan Kara ya sake sakamakon azaban zafin da yake ji da kuma yanda jini ke zuba masa yake yi,baki bude Doc da Sen ke bin ta da kallo domin tunda ta fara haukan nata bata taba duka Ko attempting in ji wa kowa ciwo ba in ba kanta ba,

Kafin sukai ga mamakin ya sake su tayi wata super in Albarka tare da fitowa akan Afzaal Wanda saida ya kai kasa,

Wuyan rigan shi ta cukumo Wanda ya baci da jini,idanun ta Na fidda hawaye tana ihu ta hau cizon shi tana Marin shi ta ko ta ina a fuskan shi,

Ihu yake domin ba karya ba karamin azaba yake sha ba,domin in ta kama fatan yanda ka san ta samu fatan rago ko kaza yanda take ja ga shi zafin Marukan nata yake ji har cikin brain in shi,

Ihu yake yana fadi Daddy help me pls zata kashe ni,ina Nadeeya bata ma San yana yi ba duka take mishi ta ko ta ina kamar Wanda Allah ya aiko ta,tana kuma kan ihu tana surutan da ni kai Na ban San me take fadi ba,

Ganin tana kokarin kashe shi da duka ne ya sanya doc Bashir danna wani red button Wanda yayi alarming in nurses su taho da sauri akwai matsala,

Ai ko cikin sauri sai ga su Sister Kareematu da kyar aka samu aka banbare ta daga kan Afzaal tana ihu tana cizon nurses in tana fadin su bar ta sai ta kashe wannan dan iskan mara tsoron Allah,a bar ta ta ga bayan shi,domin barin irin wannan mugayen shi da Sen a doran kasa masifa ne domin Jinin su ya Riga da ya halatta,shine irin ihun kukan da take yi,da kyar da sidin goshi aka tsikara mata aluran bacci tare da kwantar da ita,tare da sanya mata chain a hands inta,ganin tayi bacci ne ya sanya Doctor Bashir cewa Kareematu ta ja Afzaal a je a gyara masa ciwuwukan shi,in an gama ya same su a office in shi,

Hannun SEN ya ja tare da fitowa da shi daga dakin har suka iso office in shi jikin SEN a mace yake da abunda Nadeeya ta aika ta,

Zaunar da shi Bashir yayi tare da ibo mishi ruwa me sanyi a cup daga dispenser ya mika wa SEN,yallabai ga ruwa ka samu ka sha,

Kofan SEN ya buge cike da tsantsan bacin rai Wanda yayi sanadiyar tarwatsewan cup in,

In sha ruwan me Bashir ruwan uwar ka kake son Na sha ya kare tare da wanke fuskan doctor Bashir da Mari,(Sen irin mutanan nan ne da Sam basu Iya controlling anger in su ba,in ran su ya baci in ba duka suka yi ba basa Jin anger in zai fita ko in ce irin masu saurin hannun nan ne),

Da hannu biyu Bashir ya dafe kumatun shi domin ba karya Marin ya shige shi,

Cikin zafin rai SEN yace Amman wlhy Bashir ban taba ganin Dan iska da ya raina mun wayo ba irin ka,Dan uban ka kace da ni Nadeeya tayi hauka ita kanta bata san waye ita ba balle ta san su waye a kan ta ya kare yana tsare shi da ido,

Ba karamin baci ran Doc yayi ba Amman haka ya daure yace ranka ya Dade kayi hakuri,wai hakurin uwar me zan yi kana nufin 50 mil in da ka karba a banza ne ko me?

Aa sam SEN ba haka bane, wlhy Na rantse ma da girman Allah a halin da ake cikin nan Nadeeya is not in her normal senses, tabbas ta yi nisa a hauka sabida injections In da nake bata,

In har ta haukace a taya ta gane Afzaal har tayi attacking in shi tana neman kashe shi,za ka fada mun gaskia ko sai Na sa an daure mun kai domin wlhy babu Wanda ya isa ya ci kudi Na ya kwana lfy Dan uban shi ba a yi shi ba,

Zufan goshin shi Doc ya goge yana Jin radadi a kan kumatun shi har yanzu kafin yace,

Ranka ya Dade maganar gaskia wlhy Nadeeya ta samu tabin kwakwalwa a yanzu haka,saidai one thing da nayi observing shine,har yanzu zuciyar ta ta kasa manta abunda kayi mata Wanda kila yana da hadi da wannan yaro da kuka zo tare,domin tun da muke da ita ko yatsan wani bata taba kamawa ba,

Tayu mun tsayar da aikin brain in ta mun kuma sanya shi kamuwa da tabuwa sabida aluran da muke bata amman abubuwan da ke heart in ta fa,ranka ya Dade daga gani akwai abunda kuka mata kai da Azaal Wanda ta kasa manta shi har yayi motsa ciwon nata har tayi attacking in ta,

Dan numfashi ya ja sannan yace sir zan iya sanin miye kuka mata da zafi har haka duk da tana cikin hauka ta kasa mantawa,domin ga dukkan alamu yarinyar nan zalintar ta kuka yi,

Baki a bude SEN ke bin bashir da kallo kafin can yace,lalle Bashir ka mance da waye kake magana,yanzu don asaraa a zuriar ku ta kare ni ne zaka kalli tsaban idona kace Na zalunci yarinya ta Na sanar da kai me muka mata,Dan uban ka har kayi girman da za ka fada mun wannan maganar banzan,ya kare tare da nufo kanshi,Wanda tsoro ya cika basir dam domin har fitsari ya fara digawa a wandon Shi, don ya ga alamun bugun bura uba SEN zai yi masa a cikin office in nan,

Afzaal ne yayi saurin riko shi Wanda shigiwan shi ke nan saman kan shi dauke da bandeji,

Take it easy dad kar ka ji masa ciwo,sake ni son Dan bura uba ni wannan matsiyacin ke fada min maganar da ya zo masa,Dan uwar shi dan Kabiru ya kawo shi ya ci arziki,saisa ni Sam ban so nan din ba Amman Kabiru ya nace,ka sake ni in samu in fasa wa Dan iska baki,

Gam Afzaal ya rike shi yana daddy pls try to control ur anger mu samu solution domin Na ga anya Nadeeya tayi hauka kuwa,I can see so much hate in da take mun daga cikin idanun ta,

A gaban SEN doc Bashir ya zube yana me rogon SEN afuwa kan ya yafe masa yayi kuskure,da kyar aka samu SEN ya hakura bayan ya kafa wa Doc last warning kan ya tsaya iya inda aka aje shi,

Duk shiru suka yi kowa Na tunanin ta ina ne mafita domin kan SEN gabadaya ya kulle gani yake da daga inda aka haukatar da Nadeeya matsalan shi ta kare,zagi da cin mutuncin da take masa zai kare,Amman me abun da tayi yau din nan ba karamin dada tsorata shi tayi ba ,although an ce tayi haukan but abun Na ranta wanda wat if wataran ta fada a inda be dace ba fa shike nan ta tona mishi asiri fa,kai ina bare yu ba shine abunda ya fada yana me girgiza Kansa,

I got an idea shine abunda doc ya fadi,go on dad yace da shi,cike da farinciki kila treatment zai canza mata,

Dan shiru yayi don be san yanda SEN zai karbi idea in nashi ba

Hmmm ranka ya Dade duba da nayi Nadeeya barazana ce a cikin rayuwan ka why not kawai a kau da ita,wat I mean hers is why not a kashe Nadeeya kawai ka ga shike nan hankalin kowa zai kwanta,

Ai ko be kai ga rufe baki ba ya ji saukan yatsu tassss a fuskan shi,wannan karan saida ya saki Kara sabida azaba,

Both daddy maganar Doc Na kan hanya duk abunda zai baka ciwon kai kashe wannan abun shine zaman lfyn ka since ai Na fada maka ka bari a kashe ta kawai ko ma samu mu huta Afzaal ya kare yana turo baki,

Tassss ya ji saukan Mari a fuskan shi Wanda cike da mamaki ke kallon Daddyn,

Ku Ashe mutanan banza ne mutanan wofi ban sani ba,wai Nadeeya muke maganar a kashe ka,kai Afzal ka mance Na fadin maka Nadeeya ita ce rayuwa ta,ko nesa da ni baran bari ta je ba balle ace ta bar duniyar,

Dole Nadeeya ta zama a raye,and wlhy wannan ya zamo Na karshe da za ku Kara yin irin wannan tunanin ko kuma wlhy ku kare rayuwar ku a cikin prison, wawaye Wanda basu da amfanin komai, shike nan ni da kai Na Na san mafitar da zan dauka,wuce mu tafi yace da Afzaal yana fita daga office in,

Idanu taf da hawaye Bashir ya bi bayan SEN da shi Allah ya isa na,mutum yayi ta Marin ka kamar uban ka,ya San yana son yar tashi ya kawo ta nan in haukatar masa da ita,sannan yanzu ya zo yana ta faman marin mutane, akan me,(ni ko nace son duniyar ka ai duk me kwadayi yana tare da wulakanci, kadan ma ka gani),

**************Doctor Nameer

Sister don Allah ihun Ms nake ji ne hka,and daga ina ihun ke fita haka,ya tambayi wata nurse da ta zo wucewa,

Hmm kila kai bako ne a hospital in nan,daga IR ne ihun nan ke fitowa,

Kallon rashin fahimta yayi mata sannan yace pls miye IR kuma,Dan dariya tayi sannan tace Isolated room, mamaki ne ya kama shi shi sannan yace kar ki ce Na fiye tambaya waye a IR in,

Baki ta Dan taba sannan tace eh wlhy Na ji dai an ce wai Yar gidan SEN ce a cikin dakin Nadeeya Audu Waziri,ta kare tare da barin gurin,

Wani irin mamaki ne da al'ajabi ne suka Kama Doc Nameer, domin shi wlhy tun Randa suka yi hira da Mujaheed ga me da case in su be kuma matsa wa kan shi sai ya San abunda ke wakana,domin shi duk daukan abun yake akan acting ne don ya samu sympathy in mutane,a haka ya fito ya shige motar shi don komawa masaukin sa,zuciyar shi cike da tarin tambayoyi kan me ya kawo Nadeeyan gidan mahaukata......


A cigaba da sharing ana commenting ina yi muku son so fisabillilah🙏🏻❤️
[6/21, 8:37 PM] My Best Best ❤️: 😭😔UBANA NE KO KISHIYA TA💔💔

WRITTEN AND STORY
BY
NERNAH MARYAM
(MARTEY BEE)

........

My what's app group link

https://chat.whatsapp.com/JYJvskgTzZICC4ksRfiMlK

In har kin San bara ki Na comment ba toh don Allah kar ma ki shigo,domin ko kin shiga zan fidda ki,haka zalika maza ma kar su shigo group in nan,domin group in mata ne zallah🙏🏻,

Ga masu son a tallata musu hajojin su contact me via:

08100046388

........
Page eleven & twelve

************

Odogwu Na shiga uku na lallace asiri Na ya dab da tonuwa a bai nan duniya,ka taimake ni in baka rufa min asiri ba ban San yanda zan yi ba,duniya za su yi mun tofin Allah tsine, komai da Na mallaka zai kare,sanin kan ka ne bani da burin da ya wuce na samu kujeran takaran gwamma na jahar Bauchi,SEN ya kare cike da kuka zufa duk ya wanke mishi fuskan shi

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login