Showing 3001 words to 6000 words out of 79238 words

Chapter 2 - UBANA NE KO KISHIYATA

yace don Allah RILWANU stop all this is not that necessary ta ho mu shiga ka samu ka sha ko ruwan sanyi ne,

Bayi da option sai bin bayan Alhaji salis in Wanda ke matsayin Aminin shi kuma mataimakin shi domin shi ya tsayar as deputy governor in shi,ko ba don komai ba ya ci ya jiga makoshin Na shi don ba karamin bushewa yayi ba,

A tangameman parlor in shi da ya gaji da tsaruwa suka ya da zango,fridge ya bude tare da dauko bottle water me sanyi ya zuba masa a glass cup tare da mika masa have a sip yace da shi calmly,

Ba musu Sen ya karbi cup in ruwan tare da nufan bakin shi sa cup in Sai kuma ya tsaya kallon Salis yayi yace Salis wat will happen in har shegun yan jaridun nan sun yi recording scene in da princess ta gama yi,

Numfashi Salis ya ja tare da zama kusa da shi yace kai I don't think za suyi shooting because gaba dayan mu are shocked am sure harda su ina za su samu daman dauka, Allah sa ba Wanda ya dauka domin in har an dauka yadawa za suyi a duniya and muddum aka yada shike nan makauta sun samu nasara akan mu,

Da yardar Allah bare ma faru that way ba just be faithful my friend,dan shiru suka yi duka kafin yace yanzu ina ita princess in,

Cup in hand in shi ya aje tare da furzar da iska yace an mata alauran bacci,

Gyara zama salis yayi sannan yace wai ni kam me ke damun NADIYA ne lfyan ta kuwa ni dai sani Na da ita bata da wata cuta da ya shafi brain inta balle nace shine ya tashi mata,

Ajiyar zuciya SEN ya sauke sannan yace wlhy Salis karan shigowar waya ce ta katse mishi abun da yayi niyan fada,tare da zaro wayar tasa daga aljihu,

Ganin Wanda ke kiran sa saida gaban shi ya fadi ba kowa bane illa shugaban party in su,Na shiga uku shine kalman da ya fadi be ma San ya fada ba,dafa shoulders in shi Salis yayi yace ka dauka komai zai tafi daidai,

Dauka yayi jiki ba kwari,gaishe shi yayi inda yayi sauran tsayar da shi ta hanyar cewa SEN RILWANU shin ka shiga social media kuwa yau,idanu ya runtse yana fatan ba dai video in abunda NADIYA tayi masa ke trending ba,

Cikin sarkewaan murya yace aa ranka ya Dade ban shiga ba wa niiii abuunnn ne ya faruuuu ya fada da kyar,

Lalle RILWANU au baka ma San me ke faruwa ba ko to gaba daya kafofin sadarwa Na duniya kama daga kan Twitter Facebook YouTube Instagram video in ka ne kawai yake trending wani irin shirme ne haka ace a dauki yarinya ka tana maka zagin tsamen nama a gaban media Inalilahi,Anya ba muyi zaben tumin dare ba kuwa za ka jawo bacin sunan party in mu daman can kai ba mutumin kirki bane wai,

Cikin tashin hankali yace yallabai kar ka ce haka wlhy tallahi nima yanda kake cike da mamaki haka nake Sam ba haka princess take ba duk Wanda ya sanni yasan akwai kyakkyawan soyayya da kauna tare da shakuwa tsani na da tilon yarinya ta,wannan definitely sa hannun magauta ne an ga nasara da daukaka Na tattare da ni,but don Allah sir kayi hakuri a kuma bai wa yan party hakuri in sha Allah I got this I can control it duk me nema Na da sharri Na fi karfin shi,

Hmm shike nan gaskia try your best ka wanke kanka domin wlhy banda maganar ka babu abunda ake yi a media kowa da irin abunda yake fadi son ranshi ka ga kuma kujeran gwamma ba karamin kujera bane,

Hakuri ya bashi tare da bashi assurance zai kawo karshen matsalan gobe in sha Allah,suka yi sallama tare da kashe wayan,

Wata irin wawan jifa yayi da wayar ta bugi bango nan take kuwa ta tarwatse,cikin ihu yace damn it meyasa haka zai faru da ni why za a yi using NADIYA ta domin bata mun siyasa ta why my baby ,rike shi Salisu yayi yace calm down in sha Allah za muyi coming over this,

Shiru yayi yana ta Dan nazari kusan Na mintuna sannan ya mike yace Salisu thank u so much you can take za ka iya tafiya,kace da Kabiru ina son ganin shi in ka fita,okay Ranka ya Dade a huta lfy Allah ya kyauta Na gama yace tare da barin parlor in cike da mamakin me ke damun Nadiyar har haka,

A hanyar fita daga gidan ya hadu da Kabirun sanar da shi yayi ya je part in Senator yana son ganin shi,da toh ya amsa suka yi saying good bye in su don shi Salisu gida zai koma,

Shi ko Kabiru kai tsaye part in Senator ya nufa inda ya tarar da shi ya kasa zaune ya kasa tsaye,

Dafa shi yayi yace SEN take it easy sanin kan ka ne dai over thinking baya solving problems, cikin murya me rauni yace Kabiru ya kake son nayi dazun nan shugaba party ya kira ni har yana ce mun sun yi Dana sanin tsaida ni zaa iya kwace ma kujera na a tsaida wani,

Calm down ba wanda ya isa ya kwace ma kujera yan gari ai suna bayan ka,wani irin baya Kabiru bayan an samu Dan iskan da ya yada video in nan yanzu haka shike trending a duniya,

Whattttttt Kabiru yace yana zaro idanu shegu tsiyan yan jarida ke nan munafurci Amman ba komai we got this in control zauna ka ji yanda za aka yi,

Nan ko SEN ya zauna shima Kabirun zama yayi suka shiga tattaunawa game da yanda za a yi,sai ga SEN har yana dariya suna tafawa da Kabirun ganin sun kawo karshen matsalan nan,Kabiru be bar gidan SEN ba sai dab Magriba akan gobe yana so ya kara gayyato masa yan jaridun zai Kara tattaunawa da su a haka suka rabu ya tafi gidan shi akan sai zuwa goben,

Around 10 Na dare

Senator RILWANU ne zaune a bakin gadon da NADIYA ke kwance kallo daya za ka mata ka gano baccin wahala kawai take yi,hannun ta Na cikin nashi ya tsurawa fuskan ta ido yanda take sauke numfashi a hankali, idanu ya damke da karfi tuno irin munanan kalmomin da ta jefe shi da su dazu da safe,


Hawayen idanun sa ya goge da hannun daya Allah ya isa miki princess ita an cuce ni wlhy dake an ga ba yanda aka iya da ni shine aka biyo kan abunbda Na fi kauna duk rayuwa ta,shiru ya dan yi tare da shafa kanta don't worry my love you will get well in no time,am so sorry baby but I have to do this I got no option ki yafe ni princess ita ya kare yana hawaye tare da daukan wayan shi tare da danna wata lamba,


Ringing uku aka dauka cike da girmamawa doctor Bashir Ubaidullah ya gaida Senator,amsawa yayi yace yauwa Doc kana jina make sure gobe karfe 11 Na safe ku iso gida Na ku tafi da ita domin haukan da ta mana yau ta baki ma bare iya fadan shi ba ya kare yana breaking down into tears...........


Kar amanta ana sharing sabida da Allah

Gama su son a tallata musu hajar su za su iya mun magana ta wannan no in

08100046388.
😭😔UBANA NE KO KISHIYA NA💔💔

WRITTEN AND STORY
BY
NERNAH MARYAM
.........

My what's app group

https://chat.whatsapp.com/JYJvskgTzZICC4ksRfiMlK

Don Allah duk wanda ta san bara tana yin comment ba to don Allah kar tayi joining, sannan wannan group in Na mata ne zallah banda maza don Allah🙏🏻,

Ga ma su son a tallata musu hajojin su, za su iya mun magana ta wannan no:
08100046388

.............
Page three

*************

Karfe goma daidai doctor Bashir ya iso cikin gidan SEN shida workers in shi a cikin motan daukan marasa lafiya wato (Ambulance),

A zaune suke a parlor in SEN daga ganin alamun su tattaunawa suke me matukar mahimmanci,

Doctor ne ya dago tare da kallon SEN yace ranka ya Dade ban ki ta taka ba saidai ina Jin tsoron abunda ke iya zuwa ya zo,

Look Bashir we do trust u ne ya sanya har muka damka amanar princess a hannun ka so pls don't let us down,Kabiru ya fadi yana kallon cikin idanun doctor,

In sha Allah Alhaji I will not let you down yanda kuka ce hakan za a yi,cike da alhini Sen yace I still can't believe this wai Nadeeya Rilwanu audu waziri ce tayi hauka ya salam,don Allah doc do take care of my princess for me I don't mind spending ko nawa ne ni dai all I want shine ta dawo normal ya kare kamar zai yi kuka,

Patting bayan shi Kabiru ke yi yana haba my friend be a man mana Na san da ciwo sosai ko dan kasancewar ta ya daya tilo a gurin ka ammman we are doing this for her own good,so allow the doctors to do their job pls,

Numfashi ya sauke sannan yace yeah haka ne you gat some point ne dai all am saying here is Bashir ka kula mun da princess kar a samu wata matsala make sure duk abubuwan da Kabiru ya sanar maka ka gane ko,

Da sauri Ubaidullah yace yeah sir Na gane in sha Allah bara a samu ko wani matsala ba ai mun sha dealing da cases in da ya fi Na princess ma in no time za ka ga ta samu lfy,

Nan take Kabiru ya ciro wayan shi tare da masa transfer in mil 5,debit alert ya nuna masa sannan yace ga shi for a start mu dai fatan mu komai ya tafi daidai and ta samu lfy make sure a siya mata duk abunda take so extra kula nake so ku bata,

Nan take ya washe baki tare da zaro idanu Jin huge amount in da aka ambata hakan ma wai for a start wow harka da gidan gwamnati akwai samu ya fadi a can kasan ranshi,while a fili kuma godia yake ta zuba wa tare da Kara jaddada musu kan cewa babu wata matsalan da za a samu daga Gare shi his daughter will be safe and sound,

Mikewa SEN yayi yace okay in dai haka ne ai no need of wasting time mu je ku tafi da ita kawai,

............... Nadeeyah

Ba yanda Falmata bata yi da Nadeeya ba kan ta tashi daga kwanciyan kukan nan da take yi tayi wanka ta sauya kaya ko itama ta ji dadin jikin ta domin Sen ya aiko ace da ita ta sanya Nadeeyan wanka za a tafi da ita,tayi kuka sosai tare da tofin Allah tsine ga duk me sa hannu a samun rashin lfyn Nadeeyan,

Kallon ta Nadeeya tayi da red eyes in ta tace wai Inna Falmata ke ma kallon mara lfy kike mun,wai me yasa kun kasa gane wancan mugun mutumin azzalumi ne,I thought in duk duniya sun kasa fahimta ta ke za ki fahimce ni duba da irin shakuwar da ke tsakanin mu,ta kare tana kuka don Allah Inna Falmata kar ki bari a kai ni ko ina tunda ke ma kin ce baki San yanda za a kai ni ba ni fa lafiya ta lau ta kare tana share hawaye,

Ita din ma Inna Falmata hawayen take yi tana Allah ya baki lafiya uwar daki Na tabbas an cuce mu an zalunce mu,in ba haka ace duk irin shakuwa da soyayyar dake tsakanin ki da Ranka ya Dade ace ki masa irin wannan diban Albarkan??,

Jin knocking in kofar da aka yi ne ya sanya ta mike wa da sauri Nadeeya ta riko ta tana rokon ta don Allah kar ta bar ta,jiki a sanyaye tace yi hakuri uwar daki Na ina zuwa da sauri ta bar gurin don ta cigaba da zama kuka za suyi ta yi,hakika ciwon nan Nadeeya ke yi amman har cikin Jinin jikin ta take Jin zafi da radadi,

Bude kofar tayi ganin SEN ne da kanshi ya sa ta zube tana gaida shi ko amsa wa be yi ba yace ya Falmata ta shirya don za su tafi ne,aa ranka ya Dade tun safe nake binta tayi wanka amman Sam taki yi ko tashi taki balle tayi wankan sai kuka da sumbatu kawai take yi marasa dadin ji,

Goshin shi ya shafo sannan yace kai Nadeeya ina ba dai taurin kai ba,daman can ya balle yanzu ya hadu da lalura,matsa baran shiga da kaina,

A hankali ya shiga cikin dakin zuciyar shi Na bugawa domin daga jiya zuwa yau yar ta shi tsoro ta koma bashi,

A kwance ya same ta ta kifa fuskan ta a cikin hannuwan ta yana jiyo sheshekan kukan ta,

Zuciyar shi a karye ya zauna bakin gadon tare da dafo kafadunta da hannun shi,yace Nadeeyan Daddyn ta,

Da sauri ta buge hannun nashi tare da Saurin Mike wa ido cikin ido ta kalle shi tace kar ka kuma taba ni da wannan kazaman hannayen naka mara tsoron Allah,

Baki a bude yake kallon ta yace princess yau ni kike kiran hannaye na masu datti ,hannun da ya Raine ki ya koya miki tafiya ya ciyar da ke ya wanke ki,haba Nadeeya ta,

Cikin tsawa tace I beg u in the name of Allah to drop this act ai wlhy an yi walkiya Allah ya tona ma asiri zan so duniya su San kai wani irin mutum ne wlhy ka sanya fuskan mutunci kana yaudara da zalumtar bayin Allah,in sha Allah Allah bare bar ka ba yanda ka tarwatsa mun rayuwa kai ma,dakatar da ita yayi saurin yi domin ji da yayi zuciyar sa Na kokarin bugawa,ya isa haka ko ma miye za ki ce baran ga laifin ki ba domin ba a cikin hankalin ki kike ba Allah ya isa an cuce ni,Allah ya baki lafiya my baby girl am so sorry I have to do this ni ma ba don raina ya so ba ya kare a raunane tare da cewa doctor you can come in,

Nan ko doc Bashir da wasu murdaddu majiya karfin mataye sanye da uniform su biyar suka shigo dakin,

Go get her shine abunda Bashir yace da Matan,

Jin haka ya sanya Nadeeya birkicewa ta dauko bed side lamp in ta ta rike tana rantsuwa akan duk Wanda ya taba ta sai ta kashe shi ita she is not mad,juyar da kai SEN yayi cause his heart bare iya daukan hakan ba,

Tsayawa cak suka yi matan suna kallon ta,tsayawa kallon ta za kuyi ko za ku dauko ta kun taba ganin mahaukacin da ya amsa kan cewa shi mahaukaci ne?dallah kuyi sauri kar ku bata mana time,

Nan fa aka shiga kokuwa inda Nadeeya Sam taki yarda su kama ta banda ihun neman ceto da kwala wa Inna Falmata kira babu abunda take yi,a garin haka har ta fasawa biyu goshi,ganin tana bata musu lokaci ne ya sanya doc bashir tsikara mata Alluran kashe jiki,in da a take ta kwalla ihu tare da zubewa a kan gadon,

Nan take jikin ta ya mutu in da ba wasting time suka dauko ta tare da fitowa da ita daga dakin,

Duk Wanda ke gidan saida ya zubda hawayen tausayin hajiya Nadeeya kar Inna Falmata ta samu labari tana ji tana gani aka sanya ta a bayan Ambulance,

Kusa da ita SEN ya zo tare da mata kiss a goshi sannan yace am so sorry my love,in sha Allah za ki samu sauki zan Na zuwa duba ki take care of your self for me I love you so much,ya kare yana hawaye

Ji take wata wutan tsanan shi Na Kara ruruwa a ranta tabbas da da akwai wuka a gefen ta sai ta luma masa,

Doctor make sure to take care of my daughter ita kadai Gare ni ina matukar kaunar ta,in sha Allah kar ka samu damuwa Alhaji shine kalman doctor Na karshe kafin ya shiga mota,

Ina ji ina gani aka rufe ni tare da Jan motan aka bar gidan mahaifina da ni,ban San ina yace su kai ni ba kila ma kashe ni za ayi halan yau ne Jan numfashi na Na karshe a duniya, tabbas da da yanda zan yi da Na gudu Na tafi wata nahiyar daban Na fara sabon rayuwa ta yanda babu Wanda ya sanni Amman kash ni tawa kaddaran da haka ta zo mun,

Fitan su yayi daidai da isowan yan jaridun,Wanda cike da mamaki suke bin motan ambulance in da kallo zukatan su fal da tambayoyi,

Kai tsaye Sa'eed ya wuce da su confrence Hall in SEN yanda suka yi taro jiya zaman su da be fi da 5 mints ba sai ga SEN ya shigo da makarraban sa,

Sai da suka zauna yan press suka mika gaisuwa sannan SEN ya mike da kanshi,

Gyaran murya yayi daga kallon yanayin sa kasan ranshi a tsantsan bace yake domin babu ko dikon faraa a fuskan shi, idanun shi sun yi jawur alamun ya sha kuka har ya gaji,

Kamar kullum da sunan Allah ya bude taron sannan ya fara magana kamar haka,

Hakika nin gaskia ina kara gode wa Allah da ya bani adon rai da lafiya har nake tsaye a gaban ku,nasan daga ku har aluman gari gaba daya kun zaku ku ji kundin labarin game da abunda ya faru jiya a gida Na,Wanda ko a tarihi ban taba Jin makamancin hakan ba har wasu Na tantaman Anya wannan yarinyar sa ce ko wasu suce Anya wannan asalin uban ta ne,

Numfashi ya sauke sannan yace tabbas Nadeeya yarinya ta ce ita ce ya daya tilo Wanda Allah ya mallaka mun Wanda nake son ta fiye da rayuwa ta,

Tabbas mulki daukaka arziki suna da shahara duk Na Allah ne,shi ke azurta bawan sa a sanda ya so kuma ya talauta shi sanda ya so,shi ke bada mulki kuma shi ke hanawa,

Soyayya da daukaka ta da kuma farin jini Na duk daga Allah ne,ni Na yarda da hakan,

Sannan duk Wanda ya sanni ya San ni mutumin arziki ne ba wai yabon kai Na nake ba,Amman an sani ina da kyakyawan muamala tsakanin Na da mutane

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login