Showing 48001 words to 51000 words out of 79238 words

Chapter 17 - UBANA NE KO KISHIYATA

zaunannan mazaunan ta,murna fal cikin ta wannan Shi Ake Kira farin dare,daga ganin kyakkyawan alhajin nan me kama da larabawa (dake shuwa ne),naira gare Shi,irin su kuma ba sanin zafin kudin suka yi ba,da haka suka shige ya karbi makullin daki ta bi bayan Shi zuciyar ta fal za ta cafki Yan kudade ta mance da Amanar auran da ke Kan ta Wanda za ta ci ta mance uwa ce ita akwai Amanar Yara Akan ta,ta mance kimar ta na ya mace idanun ta sun rufe,bata son mutun ba bata san daga ina yake ba miye intentions in shi ta mika kai buri ya hau,

(Ubangiji Ka tsare mana Imani mutunci da lafiyar mu,Allah Ka Raba mu da son abun duniya ya Allah Ka kare mu daga San zuciya,masu hali irin na Kareematu Allah ubangiji ya shirya Ku in masu shiryuwa ne Ku),

**********Doc Nameer

A hankali ya dauko ta bayan yayi parking har lokacin bacci take yi,Kai tsaye dakin baccin sa ya wuce da ita tare da shimfide ta akan gado,

Zama yayi tare da zuba Mata idanu,Yana me tunanin da be je ya ji me su Bashir ke shirya wa ba fa,kila da iyanzu wani zancen Ake daban,

Tabbas be taba ganin mugun mutun me son abun duniya irin Bashir ba,kana likita a hada Baki da Kai a yi kokarin kisan Kai,

Shi kuma Afzaal sam brain in Shi ya kasa yarda wai Shi mijin Nadeeya ne,wai daman tana da aure,toh me tayi mishi da zafi da zai biya don a kashe ta,

Wai shin ma ina Mahaifiyar ta take,and a yanda ya ji mahaifin ta na kaunan ta Yana ina har sirikin Shi ke son kashe mishi yarinya,

Kwata kwata brain in Shi ya kulle ya kasa sanin amsoshin tambayoyin da yake da su game da ita,

Ganin tunanin be da amfani ya Sanya Shi Mike wa,sai kuma zuciyar Shi ta tambaye Shi,wait Nameer da Ka dauko ta Ka kawo ta gidan ka wat about her family,

Numfashi ya sauke,maganar gaskia Shi be san wanda zai yarda da Shi kuma,haka kawai ya ke Jin yarinyar tana cikin danger,and haka kawai yake jin bazai iya yarda da kowa ba kuma,

Wat of her Father zuciyar Shi ta kuma tambayan Shi, actually har Shi ban yarda da shi ba for Allah knows why,domin ya Dade Yana tunanan nan akan Shi,why be tsaya kai da fata gurin samun lafiyar Nadeeyar ba,beside tun Randa ya ga injections in da Bashir ke Dura wa Nadeeya jikin Shi yayi sanyi game da lamuran Sen,toh daman can da lafiyar ta ya Sanya aka kawo ta gidan mahaukata,ko kuwa ta Dan yi haukan kadan shine Bashir ke dada birkita Mata brain, wannan duk tambayoyin ke ringing a head in Shi,

Tsaki ya ja tare da dafe goshi,har ga Allah be san ko daidai yayi ko laifi ba da ya dauke ta daga hospital in nan,shi dai kawai ya bi shawarar zuciyar Shi ne,domin tunda ya ji su Bashir na Shirin kashe ta ya kasa zaune balle tsaye,karshe ya yanke shawarar yi wa Bashir aluran bacci ya dauke ita Nadeeyar,

Wat if wani ya gan ka shine wani tambayan da zuciyar ta Shi ta masa,Nameer kasan aka gane kama Ka za ayi da laifin kidnapping,tunda daukan ta kayi ba tare da yardar ta ba,

Mikewa yayi tare da sauke ajiyar zuciya ya san tabbas haka ne toh Amman Shi a ganin Shi taimakon ta yayi,ganin in ya zauna tunani ne kawai zai cika masa kai ya Sanya Shi juyawa don shiga toilet ya watsa ruwa ko ya ji sanyi a jikin Shi da zuciyar sa,

Jallabiya ya dauka tare da quranin Shi da laptop in Shi ya ja Mata bargo bayan ya rage Mata sanyin AC in dakin sannan ya fito tare da rufe kofar,a palor ya Aje kayan tare da fadawa dayan dakin nan yayi wanka ya shirya sannan ya zo ya tada nafila,ya Dade Yana adduo'i ,kafin ya shafa ya shiga karatun Alqurani me girma,Saida ya ji ya fara jin bacci sannan ya aje ya kwana,a nan Kan kujera,

Bacci yayi hankalin sa kwance babu wani tsoro ko fargaba a ranshi,ji yake Yana daidai da kowa a cikin asibitin like he is ready wa koma miye zai faru,abunda ya sani dai shine be bayar da Nadeeya har sai Allah yayi ta warke,

Ba Shi ya farka ba sai asuba,Saida ya leka ya ga tana lafiya sannan yayi alola ya tada sallah,a nan kan sallayan ya maida bacci kafin alarm in Shi ta tada Shi,


Around 7:00 ya ji ana buga masa kofa Wanda karar bugun ne ya farkar da Shi da sallati a bakin Shi,ya mike yana me karanto adduar tashi daga bacci,wayar Shi ya dauka tare da ganin time,

Ya salam Ashe bacci Nayi sosai,time ya tafi,be ma yi wanka ba break balle Shirin zuwa aiki,Jin ana cigaba da buga gate in ne ya sanya Shi mikewa Yana me mamakin Waye haka zai zo mishi gida da sassafiyar Allah.....

Ayi mun afuwa na so ya fi haka wlhy Allah be yi baπŸ₯Ή,

Ina yi wa kowa fatan Alkhairi da kuma fatan ayi shagalin sallah lafiya.
[6/21, 8:37 PM] My Best Best ❀️: πŸ˜­πŸ˜”UBANA NE KO KISHIYA TA πŸ’”πŸ’”

WRITTEN AND STORY
BY
NERNAH MARYAM
(MARTEYBEE)

........

My group link

https://chat.whatsapp.com/JYJvskgTzZICC4ksRfiMlK

In har kin san ba sharhi da karanta book ina ne zai Shigo da ke ba toh don Allah yi Zaman ki ba sai kin yi joining ba,haka zalika Maza stay away from my group domin wannan group na Mata ne xallah ko Ka shiga Zan hidda kaπŸ™πŸ»,

Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via:

08100046388

..........
Page twenty- three

************

A kwance ya samu doc Bashir ana yi mashi Karin ruwa kallo daya zaka masa ya Baka tausayi,inda ya kuma duhu har Ramar dole yayi na lokaci daya,doc Jameel ke gefan Shi Yana me bashi Baki Kan ya dau komai a sannu za a gan ta in sha Allah domin daga fargawar Shi zuwa yanzu ya Suma ya Kai sau 8🀣🀣Ni ko nace madallah AI daman kwadayi aka ce mabudin wahala,

Da sallama doc Nameer ya Shigo inda doc Jameel ya amsa sallaman tare da Mika mishi hannu Yana fadin doc sai yanzu,

Hannun shima ya Mika suka yi musabaha sannan yace wlhy fa doc yau makara nayi,Ayya ai daman jiki da jini dole wataran a gaji, hope kana lfy,

Kujera ya ja ya zauna sannan yace Alhamdulilah wlhy ya aikin, Alhamdulilah fa,toh madallah,

Da kallon tsana ya bi doc Bashir ganin yanda ya ficiccike daga jiya da dare zuwa yau sai abun ya so bashi dariya,Amman sai ya daure yace,

Doc Bashir Ashe abunda ya faru ke nan,wlhy yanzu shigowa ta nake Jin wannan munannan labarin garin yaya haka ta faru,

Da kyar ya iya Bude idanu ya kalli Nameer in sai ya yi shaar da Shi,nan take tausayin kanshi ya kama Shi sai kwalla ya kuma kallan doc Jameel ya ga sai danna waya yake abun Shi,kuka ce ta kwufce masa,yayi danasanin Sanya kanshi a matsala kila da be bi son zuciya ba da shima Yana rayuwar Shi cikin Jin dadi da annashuwa,yanzu da wani yare zai sanar da Sen Kan cewa an sace yarinyar sa,ai ba ma zai kama zancan ba,

Doc kayi shiru yana maka magana,Jameel yace Yana mikewa,

Ajiyar zuciya me nauyi ya sauke sannan yace wlhy Nameer ni Kai na ban san garin ya haka ta faru ba,abunda Zan iya tunawa dai na shiga in duba ta ci abinci ko as da daddare sannan na bata maganin dare ganin Kareematu bata nan,shine wani makiyin Annabin Wanda babu Allah a zuciyar Shi ya soka mun alura suka dauke ta,

Subhanallahi toh garin ya su Waye su Ka san su ko Ka ga yawan su,a garin ya ma suka shiga dakin na ga da pin a jiki,

Wani zufa ne ya kuma karyo mashi domin tabbas babu Wanda zai yarda ba Shi ya sace Nadeeya ba tunda duk asibitin babu Wanda ya san pin in sai Shi kadai da Kareematu,ita kuma throughout jiya bata nan,ya Zama dole Shi za a tuhuma,na shiga uku shine abunda yace tare da matso kwalla,

Nameer dariya ce fal cikin Shi, farinciki kamar ya mutu,ba karamin dadin ganin Bashir a cikin tashin hankali yayi ba,AI daman duk wanda ya hau motar kwadayi tashan wulakanci yake sauka,

Cikin sanyin murya yace wlhy Doc Bani na sace yarinyar nan ba,

Goshi Nameer ya shafa sannan yace in har mu mun yarda da Kai doctor mahaifin ta da sauran alumma fa,kasan ko kwana dubu za Ka yi kana fada wa duniya Baka da hannu batan yarinyar nan babu me yarda domin wannan magana ce ma da hankali ba zai dauka ba,yarinyar nan hannun Ka take hasalima babu Wanda kake Bari ya zo ko kusa da ita,daga Kai sai Kareematu ke Kula da ita,to kuwa Ka ga duk wani alamomin zargi suna Kan Ka ne da ita,don haka Ka kara tunani da kyau,

Kuka Bashir yake yi hawaye biyu biyu Yana matukar tausayin kanshi,wallahi tallahi doc Ku yarda da ni na rantse ban san komai game da batan yarinyar nan ba,na san ni kadai da Kareematu muka san pin in shiga dakin ta Amman wlhy ni babu inda na dauke ta na Kai ta,kila aljanu ne suka sace ta tunda yarinyar ma ba iya motsi take da jikin ta ba,tunda na ji an ce aljanu na iya dauke mutaneπŸ˜‚πŸ˜‚,

Dariya ne ya so kama doc Nameer Jin furucin Bashir,tabbas ya yarda doc Bashir na da matukar tsoro,Amman madallahn sa ai tunda junin Shi son zuciya da duniya ne,

Hmmm ni duk ba ma haka na,Ka dai san bare yu yarinyar Sen ta bata baida masaniya ko,ko Ka sanar masa ne,

Da sauri Bashir ya mike cike da kidima yace don girman Allah na roge Ka Nameer Kar Wanda ya sanar da mahaifin yarinyar nan,na rantse da girman Allah wlhy kashe ni zai yi har lahira,

AA Doc wannan Sam ba shawara me kyau bane,ya za a yi yar sa a nema a rasa bayan ya damka Amanar ta a hannun Ka sannan ace Kar a Bari ya sani,AI hakan be yi ba ko da dabbar gidan Shi kake kiwo ya bace dole ya sani balle Dan mutun,don haka Ka kwantar da hankalin ka a sanar masa kila ya san inda take tunda yana da connection,don haka ina so Ka Bani no sa in Kira in sanar masa halin da Ake ciki,

Aa Nameer Ka duba girman Allah da soyayyar da kake wa mahaifan Ka,Kar ka Kira Sen wlhy baka san Waye shi na rantse da Allah ba karamin so yake wa Nadeeya ba,in har ya ji babu ita toh wlhy rayuwa ta ta zo karshe,

Dariya Nameer yayi sanann yace Ka san da haka kake kokarin kashe ta a cikin ranshi while a fili kuma cewa yayi duk dai boye boyen nan babu inda zai Kai ka,abune ya riga da ya faru ba za mu iya canzawa ba,sannan Shirun amfanin me zai yi ba gwara a sanar masa ba let him do his worst in har za a same ta,AI lafiyar ta da halin da take ciki yanzu ne abun dubawa,so be a man babu abunda ya Isa ya maka abunda Allah be ma ba,so Ka kwantar da hankalin ka ka bani no in sa,

Aa Nameer don girman Allah Ka bari mu gani zuwa gobe in ba a ganta ba a sanar mashi wlhy tallahi Baka san Sen ba na rantse da Allah bare taba raga mun ba ya kare yana kuka,

Doc ke nan kana ganin za a same ta ne,Nadeeya fa bata cikin asibitin nan don da tana nan da an ganta tun tun,Ka dai Bari a sanar in,

Na roke ka Nameer Ka rufa mun asiri don kaunar Ka da Manzon Allah,zan shiga in fita in sha Allah za a samo ta,akwai wani malami da ke kan tudu naji Yana bada taimako Zan je ya bincika mun inda yarinyar nan take,

Nameer can't hold it Saida yayi dariya,kafin ya rike bakin Shi,sannan ya mike yace toh shike nan as you wish baran sanar masa ba Allah ya Baka lafiya, ubangiji kuma ya sa a ganta din,da ameen Doc Bashir ya amsa Shi tare da cewa Jameel ya cire masa drip in nan don Allah ya samu ya mike ya tafi gurin malamin,


*************Sen Rilwanu

Kwance yake kan tafkeken gadon Shi yana baccin Rana,domin ba karamin gajiya ce a jikin Shi kasancewar jiya ya dawo daga kasar waje,

Knocking in da Ake tayi ne ya sanya Shi jan tsaki tare da mikewa ran Shi bacci wani dan iskan ke son katse mishi baccin ranar sa,

Rai a bace ya Bude kofar Saa'eed ya gani fuskan Shi cike da tashin hankali,

Kai Dan uban Ka ban ce da Kai Kar uban da ya tashe ni ba,ina son yin bacci ya kare tare da wanke fuskan Shi da Mari,

Kumatu ya dafe sannan ya zube a kasa tare da cewa ranka ya Dade kayi hakuri hankali na ne a tashe ya sanya na kasa hakuri Saida na tashe Ka,

Harara ya maka masa sannan yace uban miye ya daga maka hankali beside ina ruwana da tashin hankalin naka,don Rashin kunya za Ka daga ni bacci wai kana cikin tashin hankali tashin hankali uwar me ya kare cike da Ihu,

Kayi hakuri yallabe, yanzu ne na ga wani posting Yana ta yawo wai an nemi karamar hajiya an Rasa,

Da mamaki Sen ke kallon Sa"eed kafin yace kamar ya wacece wata karamar hajiya (domin sam hankalin Shi be bashi wai akan Nadeeya Ake magana ba),

Shiru Sa"eed yayi Yana me jin tsoron sanar mishi ganin be gane me yake nufi ba,

Ba magana nake maka ba Dan uban Ka kayi mun shiru ya kare a harzuke kamar zai rufe Shi da duka,

Cikin sanyin murya yace Sen daman yanzu na gani Yana ta yawo wai an nemi Princess Nadeeya Sama da kasa an Rasa a cikin asibitin mahaukata,AI da Jin wannan zance wani irin jiri ne ya Debi Sen yayi baya yuuuuu,a tsorace Saa"eed ya mike yana yallabe kafin ya Kai ga taro Shi ina har ya kai kasa sai karan faduwar wa Tiiim kake ji........


Kuyi hakuri da ji na shiru jiya wlhy mara lafiya gare ni ina jinya,Ku Sanya ta cikin adduo'in Ku don Allah,

Na san na yau babu yawa ayi mun uzuri in sha Allah na samu dama Zan Kara page daya zuwa dare in kuma ban samu ba a yi mun afuwa sai zuwa Monday in sha Allah,

Na gode sosai da kulawa da kaunar Ku gare ni Allah saka wa kowa da khairan,

Ina yi wa kowa fatan Alkhairi.
[6/21, 8:37 PM] My Best Best ❀️: πŸ˜­πŸ˜” UBANA NE KO KISHIYA TA πŸ’”πŸ’”


WRITTEN AND STORY
BY
NERNAH MARYAM
(MARTEYBEE)

.....

My what's app group link

https://chat.whatsapp.com/FKZuWu1yj7VJ9L6izLqLhA

In har kin San ba karanta book ina da comment bane zai kawo ki toh Don Allah kiyi Zaman ki ba sai kin Shigo ba,Maza should stay away from my group domin wannan group in Mata ne zallah πŸ™πŸ»,

Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via:

08100046388

............
Page twenty- four

************

A matukar rude Saa'eed yayi Kan Sen Yana kuka yana yallabai Ka tashi don Allah domin Shi dauka ma yayi zuciyar sa ce ta buga ya mutu,

Daman ya sani muddum Sen ya samu labarin nan toh zuciyar Shi bara ta iya dauka ba ya Sanya yake ta Jin tsoron sanar masa tun daga lokacin da ya ga abun na trending a social media(kun Riga kun san zamanin da muke ciki yanzu kafin ki Isa gidan ki ma in kika yi wanni abun sai ki ga ya watsu duniya,wani kamar jiran Ka ake wannin baka ma sanin an dauka Yana da kyau mu kasance masu aikata alkhairi sannan masu guje wa riya.da kuma sabon Allah domin wannan social media in saidai godiar Allah kawai,Allah yafe mana sannan ya cigaba da rufa mana asiri duniya da lahira),

Ganin Sen Baya mosti ne ya sanya Shi a tsorace ya dauko waya Yana kuka ya shiga kiran layin Alh Kabeeru,

Kira biyu kuwa ya dauka,cikin rudewa Saa"eed yace yallabai akwai matsala,Sen ne tun dazu ya Fadi na yayyafa mishi ruwa har yanzu be motsa ba ina tsoron ko dai mutuwa yayi,

A zabure Kabiru ya mike tare da fadin what Saa"eed Ka ko san me kake Fadi kuwa miya samu Sen in,ko da yake ba lokacin bayani bane yanzu gani tahowa daga haka ya kashe wayan,

A hanzarce ya mike tare da zira babbar rigan shi sannan ya dauko makullin motar Shi,tsaban rudewa mancewa yayi ma wai Yana da wani driver,

Kai tsaye gidan family doctor in Shi ya nufa lucky him ya same Shi Yana nan a gida so da sauri ya ce da Shi ya fito su tafi,grabbing kayan aikin Shi yayi a box sannan ya fito ba bata time suka nufo gidan Sen,

A daki suka same Shi kwance be numfashi Saa"eed da sauran workers in gidan na tsaye bisa kanshi sai kuka suke suna ya tashi,

Tsawa Kabiru ya daka musu sannan yace kowa ya fice daga dakin ya koma bakin aikin Shi while Saa"eed ya Jira Shi a parlor,sim sim haka kowa ya fice, Doc bismillah check on him ko Yana Raye,

Da haka Doc ya shiga baiwa Sen taimakon gaggawa inda ya tabbatar wa Kabiru da Yana raye dogon Suma ce kawai yayi sabida wata yar firgici da ya samu,kuma muddum hakan ta cigaba da faruwa watarana kumbura zuciyar Shi za ta yi ta fashe Allah ya kyauta,Saida ya ga Doc ya dawo da daidaituwar numfashin Aminin nashi sannan ya fito domin ganawa da Saa"eed ya ji menene ya razana Shi har ta Kai Shi ga suma,

A tsaye ya tarar da Saa"eed yayi tagumi daga gani Yana cikin damuwa,

Kujera ya nema ya zauna sannan yace ya Ka Saa"eed da sauri ya nufe Shi tare da zubewa a kasa nan gurin kafafun Shi,domin ya san halin Alh Kabiru Sarai da saurin fushi da kuma saurin hannu,

Miye ke faruwa da Amini na

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login