Showing 1 words to 3000 words out of 29481 words
[7/5, 10:51 PM] INDO CE..: *💖💖💖RINTSIN SO💖💖💖*
(Wa nake SO???)
*Shafi na 1*
Alƙalamin
*INDO CE..*
ELEGANT ONLINE WRITER'S
*Bismillahirrahmanirrahim*
(my Fans😂😂 mabiyan littafin 💖💖SIHIRIN ƘAUNA💖💖, Dan Allah kuyi min uzuri kuyi min afuwa sannan ku gafarce ni🙏🏻 nasan zaku so jin ya zata kaya tsakanin Yaaye da Annur da kuma Minoji da Yaa-ya, sai gashi lamarin Allah ya gifto, na ajiye SIHIRIN ƘAUNA na ɗora RINTSIN SO inkiya (WA NAKE SO) Shima labarin soyayya ne me sarƙaƙiya, ina fatan zakuyi min kyakkyawar Fahimta sannan ku cigaba da bibiyata a cikin wannan SALON me taken RINTSIN SO dan jin meke ƙunshe a cikin wannan littafin wanda har ya samu nasarar sani nayi abunda ban taɓayi ba, wato ajiye wani littafi da nafara rubutawa na ɗora wani, ban taɓayi ba tinda nafara rubutu sai akan wannan, kuyi haƙuri ku cigaba da bi na💞💞 INA SONKU KAMAR YADDA KUKE SO NA💖)
[26/5/ 2022. Kamar yadda nafarashi lafiya ina rokon ALLAH yabani ikon gamashi lafiya]
"Anti Aisha kiyo gudu kiran ze tsinke"
Yaron yafaɗa cikin ɗaga murya.
gudun tayi ta ƙaraso ɗakin ta karɓi wayar tana kallonta dan ganin wanda yake kiran, wani dogon tsaki ta zuƙa kafin tace, "aikin banza aikin wofi wannan kiran ba wani me ma'ana bane amma kake min wannan mugun kiran shashasha kawai, daga yau se yau idan KHAALIF MOH.. yaƙara kirana ka gaya min ma sai na dauje maka baki bare ma kana yimin ihun nan aka, da na zame na faɗi Fa? kaga ni na cutu shi kuma bashi da asara"
Yaron ya turo baki, ƙasa ƙasa yana cewa "shine ma yana fama da girkeken kai ko me zaki masa ma oho"
Zaram tayi dan kuwa ya sosa mata inda ke mata ƙaiƙayi cikin sauri tace, "wallahi kuwa kaifa kasan me ze min, ina jiran kira me muhimmanci shine ze wani kira ni, da yasan baƙin cikin da nakeji idan ya kirani wani lokacin da be fara kirana ba"
shi dai Sayyid abun dariya yabashi dan haka ya dara sosai, daga baya faɗan ya koma kanshi da gudu ya fice yana dariya dan gudun kar ta lode shi .
da sallama ya shigo gidan, fuska a haɗe ta amsa ƙasa ƙasa,
Cikin fara'a yace, "ƙanwata barka da yamma"
Kallonsa tayi ta kauda kai kafin tace, "naga kiranka ɗazu lokacin ina aiki ne"
Ya murmusa gami da cewa, "shikenan dama ba komai bane, ina Mama?"
Haka kawai ta saki murmushin da bata shiryawa zuwansa ba sannan tace, "tana ɗakinta"
Kasancewar ba'a rabashi da fara'a yasa be dena washe baki ba sai ma ƙara buɗe haƙora da yayi dan kuwa murmushinta ko bakai niyya ba idan tayi maka shi sai naka murmushin ya kwance indai ka cika namiji"
Khaalif Mohammad kenan.
juyawa tayi tana wani tattausan murmushi harda lumshe ido, dai-dai lokacin aka ƙara yin sallama, lokaci ɗaya annurin fuskarta ya ɗauke ta koma kadaran kadahan ba yabo ba fallasa, ko kallonsa batayi ba ta cigaba da abunda takeyi, da ido ya bita yana murmushi.
A fizge tace, "Ina wuni"
"Ya amsa da lafiya lau yagidan?"
"Lafiya"
Kawai tace daga haka yayi gaba itama ta cigaba da aikinta.
Saifu kenan.
har Khaalif ya fita ya kuma dawowa cikin yanayinsa na sanyi yace, "ƙanwata temaka ki zuba min abinci dan Allah"
Wata shegiyar harara ta zuba masa sama da ƙasa sannan tace, "banida lokacin hakan aiki nake"
sai da ya haɗiye wani ƙululu sannan yace, "shikenan"
Yayi waje ta rakashi da harara sannan ta kora masa tsaki.
runtse idonsa yayi da ƙarfin gaske yanajin wani mugun ɗaci yana turnuƙo masa, ya cije gefen leɓensa yana girgiza kai har wani lokaci sannan ya furzar da huci, a hankali ya furta "kina Azabtar dani Ayeeshahh!!!"
A cikin gida kuwa Sayid ta kalla tace, "kaji fa wannan ɗan rainin hankalin wai na zuba masa abinci, naƙi zuba masa ɗin, banida asara idan ya kwana da yunwa, yana Faman jan jiki kamar maciji"
Mama ce ta ƙwala mata kira ta amsa tareda nufar inda take cikin sauri.
Mama tace, "meyesa bakida Kunya ne Aisha?? ke kowa ma baki raga masa ba?"
keɓe fuska tayi tana cewa, "ni bana son iyayin tsiya ne Mama, kuma ai zan bayar a kai masa Dama dan banaso yaje yai ta ƙunci a banza"
Mama tace, "Allah ya shirye ki Aisha halinki akwai gyara amma da ba haka kuke da Khaakif Muhammad ba"
Shiru ta ɗanyi kafin tace, "ko me nayi masa shine ya jawa kansa, sai dai har yanzu wani lokacin sai naji duk duniya tausayinsa nakeji"
Mama ta taɓe baki tace, "to Allah ya shirya ku kuwa"
Ta amsa da amin tana dariya.
Har tayi shirin kwanciya taji wayarta tana ruri ɗauka tayi ganin kiran Saifu ne harda murmushinta, ta Kara a kunne ba tareda tayi magana ba.
Cikin lumana yayi mata sallama ta amsa sannan ya cigaba da cewa, "kina lafiya My Baby?"
Ɗan taɓe baki tayi sannan tace, "lafiya Lau"
Yace, "har kinyi bacci ne? fatan dai ban takura miki ba"
Ta murmusa tareda sauke ajiyar zuciya tace , "tayaya kuwa zaka takura min bayan koda yaushe begen ka nake"
Murmushi me sauti yayi yace, "kyakkyawata kenan naji daɗi, nasan bakyason takurawa ne bari na barki kiyi bacci ko? sai da safe"
Ta amsa da, "Allah ya tashemu lafiya.
Da haka sukai sallama ta gyara kwanciyarta tana murmushi har cikin ranta tanajin farin ciki, take zancen aurensu ya dawo mata yanda ƴan uwa da abokan arziki suke lissafawa kuma suke ɗokin bikin nasu wasu ma sukance baze wuce watanni biyar ba, ita dai jinsu kawai take dan kuwa ba'a sa rana ba an dai kawo kuɗi, kuma bataji ana zancen sa ranar ba ma bare ta tabbatar"
Yau kwana biyu kenan Aisha bata saka Khaalif Mohammad a idanunta ba haka kawai duk sai ta shiga damuwa.
Mama tana zaune ta lallaɓo ta raɓe a kusa da ita, cikin sanyi tace, "Umma ta, ina ɗanki yayi ne?"
Mama tace, "meye kuma abun tambayata? Meke faruwa?"
Cike da damuwa tace, " Mama Khaalif fa baya nan ne kawai babu komai tambaya dai kawai nayi dan kwana biyu ban ganshi ba"
Tace, "oho shirmen banza idan ya dawo ma banda rashin kunya me zaki bashi?"
Ƙasa tayi da kai dan kuwa batada ta cewa haka ta tashi jiki ba ƙwari saɓalo saɓalo tayi ɗaki.
Khaalif yana zaune kusa da Yayansa ABU suna hira Khaalif yace, "Bro wai in tambaye ka"
ABU Yace, "Ina jinka ƙani na, Allah yasa dai ba zancen aure zakai min ba, dan na lura ka girma da yawa har kana neman zama Muzuru"
yayi maganar cike da zolaya.
Dariya sosai Khaalif Mohammad yayi kafin yace, "Bro kai ko bakayi aure ba dan tsaurin ido ni sai na ɗebo zancen aure?, ba yanzu ba tukunna dan ni banida ma wata a ƙasa, kawai inason tambayarka ne akan baka zuwa gidan mu, kodai akwai wani laifin da sukayi maka har kayi fushi?"
Shiru yayi yana ɗan tunani kafin yace, "Khaalif se yanzu wannan ya faɗo cikin tunaninka?, ba komai babu wani abunda za'a yimin a gidan ku wanda ya wuce alkairi, kai tsaye ma dai zan iya cewa babu wani ƙwaƙƙwaran dalili"
Cikin ransa kuwa yana tunanin dalilin nasa, tabbas ba kowa bane dalili face ƙanwar tasu wadda Khaalif yake tutiyar ƙanwarsa ce, tabbas itace sila a duk lokacin da ya ɗora idonsa a kanta yakanji kamar kar ya sauke, idan yaje gidan ji yake kamar ya ɗauke ta ya tawo da ita gidansu, Tin tana yarinya indai ya ganta haka Zuciya zatai ta raya masa abubuwa da dama, dan gudun ɓacin rana yasa ya ƙauracewa gidan da duk abunda ze haɗashi da ita, sai dai a koda yaushe be fasa tunaninta ba yana sane da ita sarai kawai jiran ranar da ze bayyana gareta yake..
Marai-rai-cewa Khaalif yayi yace, "haba Bro shiyasa fa duk ƙanne na basu sanka ba gaskiya ya kamata kaje, idan akace waye yasan Abu yayan Khaalif dan abun kaico har Ayeeshah cewa take bata san ka ba"
.
Murmushi yayi yace, "zata sanni indai Eeeshu ce kabari kawai Zanzo muku ka faɗawa Mama ta shirya ɗanta da baya zumunci ze zo"
Sosai Khaalif Mohammad yayi farin ciki dan kuwa yana so yaga ɗan uwan nasa a gidan.
Kwana biyar yayi sannan ya dawo, lokacin tini Aisha tafara koma danja da an taɓota sai masifa haka kawai batasan meke damunta ba, randa ya dawo kuwa dan farin ciki kasa dena murmushi tayi, sai dai ko da wasa bata bari ya gane tsantsar farin cikin da take ba.
jikinsa duk yayi sanyi damuwa da ƙunci suka ƙara kafa sansani a cikin zuciyarsa, lallai yanzu ya tabbatar Ayeeshan sa tayi masa nisa, ya kasa gane wane laifin ya aikata mata da ta zaɓi hukuntashi ta wannan hanyar, yau gashi an wayi gari bata damu da ganinsa ba har yayi kwanaki a wani gurin amma ko a wasa bata nuna tasan ma ya dawo ba bare yaga farin cikinta.
*INDO CE..*
[7/5, 10:51 PM] INDO CE..: *💖💖💖RINTSIN SO💖💖💖*
(Wa nake SO???)
*Shafi na 2*
Aƙalamin
*INDO CE..*
ELEGANT ONLINE WRITER'S
*Bismillahirrahmanirrahim*
Haka ya kwana cikin tunaninta sai juye juye kawai yake baccin ya gaza yimasa daɗi.
Washegari
yana Shigowa yayi karo da ita, lallausan Murmushi tayi gami da cewa,"yaushe ka dawo?"
Shima murmushin yayi yace, "jiya"
Tace, "inace ma bazaka dawo ba, to sannu da dawowa"
Murmushi me ciwo yayi kafin yace, "ya zame min tamkar wajibi ne dawowa gidanku Ayeeshah dan ni maraya ne banida uwa banida uba, uhm, to ya za'ayi dama ai ɗan riƙo sai haƙuri, haka nan zan dawo dolena har zuwa lokacin da Allah ya ƙa'ide min"
Murmushin gefen baki tayi tace, "haƙƙun zancen ka yana kan hanya sai dai kai ka bauɗe, meye naka na wannan zancen? ka fiye neman fitina Khaalif Mohh... ka fita idona in rufe banason haɗin faɗa, yanzu da Mama tana kusa ko zan shiga kogin rantsuwa bazata yarda ba wani abun nayi maka ba, dan haka ka tarkata kayi gaba, ni gaba ɗaya ka ɓatan rai"
Cikin sanyi yace, "kiyi haƙuri dan Allah ba'a son raina na faɗa ba kinsan wani zubin baki ba'ai masa shamaki, banso ranki ya ɓaci ba ƙanwati, kiyi haƙuri dan Allah"
Ƙasa tayi da kai tana murmushi kafin ta ɗago murya ƙasa ƙasa tace, "nayi kewarka Mohammad"
Murmushin sa ne yaƙara faɗaɗa, har cikin rai yaji daɗin maganar sai dai baze iya gazgata gaskiyarta ba, kamar bazeyi magana ba sai kuma yace, " da gaske?"
Taɓe baki tayi tace, "banda lokacin ɓatawa, ina fatan ka fahimta"
Ya jinjina kai tareda cewa, " na fahimta"
Haka lokaci yake tafiya rayuwa tana cuɗawa, tsakanin Khaalif da Ayeeshan sa, wataran suyi faɗa wata suyi daɗi, ita da Saifu kuwa kullum soyayya suke sha ba kama hannun yaro.
Yau tinda ya tashi yake farin ciki dan kuwa ɗan uwansa yace masa ze zo ranar,
Ta lura da yadda yake murna amma da yake ba damuwa tayi da abunda ya dameshi ba yasa bata bi ta kansa ba.
Sai kusan yamma yazo, Khaalif Mohammad sai rawar jiki yake, tana dawowa ta shiga ɗakinta da nufin sutale kayan jikinta sukai ido huɗu dashi, ko ba'a faɗa ba tasan duk inda taje tazo wannan jinin Khaalif Mohammad ne dan haka ba sai tayi tambaya ba.
Da sauri tayi baya tana zaro ido tareda cewa, "Auzubillah, meyesa basu gayamin ba na shigo sangam sangam haka? laifin Khaalif Moh.. ne ba wani ba, mutum idan akace ƙwaƙwalwar kifi gareshi sai dai addu'a"
Muryar ABU ce ta dawo da ita hayyacin ta, "A I INDO"
Saurin shiga ɗakin tayi tace, "ba haka ba Aisha zalla ba wani kwalo kwalo"
kafin yayi magana Mama tace, "to arasai, shima bazaki raga masa ba? duk ba sunanki bane? daga dawowa zaki fara tijara ko gaisawa bakuyi ba?, memakon kifara tambaya daga ina ya fito dan kuwa ni kaina ban ganeshi ba"
Ta ƙarasa maganar tana dariya.
ɗan rissinawa tayi tace, "ina wuni?"
Ya amsa da "lafiya lau ya karatu?"
Tace, "Alhamdulillah"
Yace, "Eeeshu kin sanni kuwa?"
Tana dariya tace, "ta sanadin Khaalif Mohammad dan kuwa kana kama dashi, kuma naji labarin cewar yana da yaya hakanne ma yasa da na ganka ban gudu ba"
Dariya sosai yayi yace, "lallai ne wai da gaske muna kama kenan?"
Kafin tayi magana Mama tace, "ke do Allah maza kizo ki kawo masa abun taɓawa"
Gaba Maman tayi ita kuma tanabinta a baya, duk ta harhaɗa mata a tire sannan ta ɗakko, da sallama ta shigo ɗakin ya amsa cikin sakin fuska, dire masa tayi tana cewa, "gashi nan saura kayi mana fulatanci"
Yayi dariya kafin yace, "zauna ki tayani"
Keɓe baki tayi tace, "nifa yanzu na dawo yana da kyau naje na huta"
Yace, "Eeeshu ban zata zaki manta ni ba kuma ban zata zaki gane ni da wuri haka ba"
Murmusawa kawai tayi kanta a ƙasa, sai a lokacin taji gaba ɗaya yayi mata kwarjini ko motsin kirki takasayi.
Cigaba yayi da cewa, "lallai ƙanwata ta girma kice na fara shirye shirye"
Ko ɗagowa tayi ta kalleshi batai ba sai murmushin da batasan usulin sa ba da takeyi.
Shigowar Khaalif ce ta katse masa hanzari sai da ya amsa sallamar tasa sannan yace, "ƙanina kaga yadda A i ta girma?"
.
Khaalif yace, to ya zamuyi Bro haka ake haifar yara ƙannen mu sai su zo su girme mu dan ko yanzu Ayeeesha tamin tazara"
ABU be ɗauki maganar a komai ba sai maganar da sukeyi, ita kuwa Ayeeshah haka kawai taji maganar tasa tafi mata kama da harshen damo, ABU yace, "Eeeshu kije ki huta naga kamar kin gaji"
Tace, "to Allah dai ya shiryi wanda basa zumunci, sai anjima"
yana dariya yace, "zo nan Eeeshu da wa kike?"
Dawowa tayi tana murmushi kanta a ƙasa tace, "da wanda basa ziyara nake"
Yace, "ohh ai bana cikin su, shiyasa naso tawowa da aboki na JOSE nasan shima ba lallai kinsan shi ba, dan nasan halin kayana ba zumuncin yake ba shima"
Tunani ta ɗanyi kafin tace, "ohh Jose dai ƙanin Khalil? to ai shi ya fika zumuncin ma, nasanshi dan muma muna zuwa gidan su kaɗan kaɗan ba da yawa ba, be fi sau biyu naje ba"
Dariya yayi yace, "lallai Jose ya ciri tuta, kice ya fini zumunci gaskiya nima zan dage"
Tace, "gwara dai, amma fa bana magana da Jose ɗin kawai daga gaisuwa shikenan"
yace, "subhana to Allah ya shiryaku kuwa, shi Jose miskilanci...
Khaalif ya katse shi da cewa, "ƙanwata kuma girman kai"
Kallon sama da ƙasa tayi masa bata tanka masa ba ta maida hankali kan ABU tace, "karkaji wani ya faɗa fa ka yarda ni banida girman kai ko kaɗan, ni an ɓata min rai ma sai anjima"
Daga haka ta fice ta basu guri.
Sosai jikin Khaalif Mohammad yayi sanyi, duk wani farin cikin da yake ya gushe, ya rasa meyesa Ayeeshah take masa haka.
ABU ya lura da canjin yanayin Khaalif haka kawai yaji gabansa ya yanke ya faɗi, ido ya zuba masa yayin da shi kuma kansa yake ƙasa yana tunanin ta,
Duk yadda ABU yaso karantar wani abu daga Khaalif yakasa dan haka ya canja musu hira.
tuƙa motar yake amma tunanin sa da hankalinsa nutsuwar sa duk basa gareshi suna ga Eeeshu tabbas idan yayi kwance kwance za'ayi masa kwance kwance dan haka yake jin gwara ya bayyyanawa Eeeshu irin soyayyar da ya daɗe yana tanadar mata tin bata san kanta ba.
haka ya koma gida cike da tunane tunane da sallama ya shiga gidan Umma ta amsa tanabbinsa da ido, ya gaishe ta ta amsa a ciki ciki, bayan ta gama ƙare masa kallo tace, "ina kuma kaje?, ana ta neman ka amma an rasa ka"
cike da rashin kulawa yace, "gidan yayar mahaifiyata naje dan itama tana da haƙƙi a kaina"
.
A hasale tace, "ni zaka gayawa wani haƙƙi lallai ABU wuyanka ya isa yanka"
Murmusawa yayi yace, "ba haka bane Umma yana da kyau ne ziyarta, kyautatawa dangin ka ɓangare biyun nan dangi mahaifi da na mahaifiya koyarwa ce ta addinin mu muslinci duka sun rataya a wuyanka, da dai banyi ba amma yanzu zan fara"
Daga haka yayi waje be tsaya sauraron abunda zata faɗa ba.
Baki buɗe ta raka bayan sa da ido.......
*INDO CE..*
[7/5, 10:51 PM] INDO CE..: *💖💖💖RINTSIN SO💖💖💖*
(Wa nake SO???)
*Shafi na 3*
Aƙalamin
*INDO CE..*
ELEGANT ONLINE WRITER'S
*Bismillahirrahmanirrahim*
(yau fa mura nakeyi taimin mugun kamu😥😥 sai dai kuyi haƙuri da abunda kuka samu😞 ban sani ba ma ko zan iya read more 1😂INA GAISUWA GAREKU🙏🏻😊)
Har sai da ya ɓacewa ganinta sannan ta jinjina kai tace, "lallai ABU ka cika ai, har ni yaron nan ze gayawa magana?? dan yana ganin ya girma? hehe!! ta yaro kyau take bata ƙarko, zaka gane a hannu na ka taso ni na raine ka"
ABU ganin tana neman ɗora masa hawan