Showing 69001 words to 72000 words out of 141906 words

Chapter 24 - Ta Fita Zakka Part 2

10 Oct 2024

4150

Jakar data Hada kayan nata Hajiya ta karba ta farayin gaba itama ta shirya Tsab da ita,Hajiya na gaba tana Binta abaya har falon Mallam suka gaisa ya kara mata Nasiha sai ga Idi ya Dawo Hajiya ta mike tace zasu tafi mallam yace"Ko in kira Sa"idu ne su yi sallama..?
Hajiya tayi shuru kafin tace"kyalesa kawai ai na Fadamai jiya..
Mallam bai kara mgana ba shi ya rakosu har bakin mota sai ga Hajiya Nasara ta fito domin ita ke da Turakan mallam jiya ganin Hajiya da Amina yasa tace ko anguwa zasu je Hajiya tace eh ba Dadewa zasu yi ba mallam dai na gefe bai ce komai ba domin yayi alkwarin bazai ma Hajiya kaladan kan abunda ta Tsara ba ya yarda da ita fiye da duka matansa bazata taba aikata ba Daidai ba.
Agaban idon Hajiya Nasara da Mallam Suka fita Daga gidan idi ke jan su a Motar mallam din prado baka suka Dauki Hanyar Abuja Amina na ta sharan kwallah???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~? Hajiya na kallonta batace komai ba Domin bazata hanata ta koka ba.
Su hajiya basu yi nisa ba,Aba ya fito zai Tafi gidan gona mallam ke Fadamai su hajiya sun tafi yayi mata Fatan Dawowa lafiya bai Dade ba gaiswawa kawai sukayi da Mallam ya shiga Motarsa ya tafi bayan tafiyarsa sai ga mamanmu ta shigo gaida Amina da Haj.Nasara ta fara Cin karo ita ke shaida mata Hajiya sun fita da Amina mamanmu bata Damu ba aranta tace agayas ayasha ta gaida ayyah..!
Shashen Anty Amarya ta shiga ta Duba Sakina sannan suka kule Daki suna Kulle kullensu da suka saba mamanmu ke fadama Anty Amarya Abunda Aba ya fadamata Hajiya ta Sanar dashi kan Amina da Tafiyar tasu yau.
Anty Amarya ta tabe baki Tana Fadin"Ko shiyasa Daga jiya zuwa yau take wani Shan kamshi..ko Sakina ta Daina lekota su gaisa. !
Mamanmu tace"Yau she kuwa..?
Tana chan tana shirin kaita inda Zata kwace miji..!.
Anty Amarya tace"Aikin banza ne wannan..Ai Danmallan din yana Tafe nan da wata Biyu in ya Dauki Sakina suka koma ai sai naga karyan koyon kula da miji..!
Wai ina ma Zata kaita..?
Mamanmu tace"Oho ni dai yace min Gidan Da'ya Daga Cikin yaran mu..!
Anty Amarya tace"Ni ba ma wannan ne agabana ba Dayyaba..Mallam nake jira ya Kirani so nake ayi ma Sakina mganin abunda uwani tayi mata Datake bari in aka gama da wannan bangaran mganinta bamai matsala bane..!
Mamanmu tace"Ai Allah dai ya Tsine ma Uwani..!
Anty Amarya tace"Amin matsiyaci ce..Ta gaban anuna ma jarida. !
Nan suka Cigaba da Tattauna yadda zasu Taru suyi mganin Uwani hankali kwance in sun gama da matsalan Sakina suna ganin Amina bata gabansu.Suna ganin ita karamar alhaki ce bata isa ba yanzu.
Abunda basu sani ba wanda bai isan ba Allah yafi nuna isarsa akansa sannan alokacin da Uwani ta Dauke musu hankali Dan Zaki zai girma sannan Tsammanin abunda basu tsammani ba zai faru..!.

*****

Abuja..!

Misalin karfe Shadaya na rana suka isa gidan Aisha Dake maitama Abuja Kwatsam sai dai ta ga Hajiya abun Farincikin ma harda da Amina Aisha ta kasa Boye Murnanta ta Daka Tsalle ta Rumgume Hajiya sannan ta rumgume Amina Hajiya ta kalleta tana Fadin"Ki mata a hankali bata jin Dadi..!
Sai alokacin Aisha ta Lura da yadda Amina tayi kiba Sannan Fuskarta ta Kumbura,haka ta jasu falonta Cikin murna tana da yar aiki wata yar matashiya ita ta cika gabansu da Kayan Taba ka Lashe,Amina sai Bin Gidan ya Aisha take da kallo mai kyau dashi.
Aisha ta rasa ina Zata saka su Hajiya Saboda Murna Hajiya ta kalleta tana Fadin"Aisha to ki Zauna mana..!.
Ta Zauna gefen Amina tana Fadin"Hajiya murna ce..Ga ki ga Amina.
Hajiya ta yi mirmishi kafin tace"Yanzu dai ba wannan ba. ki sama ma Idi waje yaci abinci ya Huta kafin mu tafi..!
Da azama ta mike tana amsa ma Hajiya yar aikinta mai suna Saude ta ma mgana taa shiga da Idi Dakin Baki na waje tazo takaimai ruwa da abinci.
Tana Dawowa tace ma Hajiya"Hajiya Zaku gaisa da yakaka kakar Usman. !
Hajiya tace"Zan shiga mu gaisa Aisha kada ki damu..!
Aisha ta koma ta Zauna kusa da Amina tana Fadin"Aminene ikon Allah Amaryan ya Danmallam ya naga kin yi Shuru ne bakya mgana..!
Nice fa ya Aisha..?
Ko bakin ya mutu ne basu Hamida..?
Amina tayi Mirmishi ta gaisheta ta amsa tana Fadin"Amina kinyi Kiba Lokacin Bikin su Abida kina lange Langenki fa..!
Hajiya tace"Na sanar Dake bata da Lafiya ne Dalilin zuwana ma kenan..!
Aisha tace"Eh usman ya Fadamin sunyi mgana da mallam..Dama Amina ce Zata Zauna damu Hajiya..?
Hajiya sai da ta gama shan ruwa sannan Ta gyada mata kai Aisha ta Zaro ido kafin tace"Hajiya ba ta tare gidan ya Danmallam ba..?
Ko ansamu wata matsala ne .?
Hajiya ta mike tana Fadin"Mu je Ciki mu yi mgana..Amina kici wani abu kafin mu gama. !
Ta daga ma Hajiya kai Aisha na gaba Hajiya na bayanta har bedroom dinta Gefen gado suka Zauna Aisha Duk ta Tsorata fatanta kada ace auran ne ya Lalace.
Hajiya ta kalleta tana Fadin"Kada ki damu ba wata matsala bane..Auran su na nan sannan da sanin shi Danmallam din da Mallam kanshi na kawota wajenki. !
Sai alokacin Aisha ta ji sanyi Tace"Hajiya har gabana ya fadi na Zata ko wani abu ne ya samu auran nasu..!
Hajiya tace"Ko Daya..Sai dai matakin dana Dauka duk saboda Kara Karfafa auran su ne Aisha..Ina mai Sanar Dake Amina na Dauke da Cikin yayanku har tsawon wata Hudu da kwanaki. !
Aisha ta zaro ido kafin tace"Ciki Hajiya..Aminar..?
Kai ta gyada mata tana fadin"Kwarai kuwa baki ga alama ba ko..?
Aisha ta washe baki tana Fadin"Bangani ba Hajiya sai kibar Data kara..Alhamdulillah na taya ya Danmallam Murna daman ga Sakina na ta samun bari Allah yasa na Amina ya Zauna ta sauka lafiya..!
Hajiya ta amsa da Ameen kafin ta Kira Sunan Aisha ta amsa mata Cikin bada Hankalinta ganin yanayin Hajiyar.
Hajiya tace"Aisha na yarda Dake kaf Cikin ya"yana shiyasa na Zabi Amina ta Zauna agidanki ki kula da ita ta Reni Cikinta na wani Lokaci Sannan na zabe ki saboda baki da Surutu achan gida dagani sa mallam sai Danmallam muka san da Amina nada Ciki sai ke yanzu sabida haka ina so ya Zama sirri Tsakanina Dake..Ban so wani yaji labarin Cikin jikinta ballatana labarin tana wajenki Shima ba wanda ya sani Harta ko da Sa"idu da su hanne basu san komai ba.ki kama Bakin ki koda tambayarki akayi kice baki sani ba Dani kadai zamu Dinga mgana in wani abu ya taso kina jina..?

Aisha ta gyada kai Cikin mamaki Hajiya ta Cigaba da Fadin"Nasan Zaki yi mamakin meyasa nayi hakan..!?
To ina da Dalilina ammh ba yanzu zaku sani ba sai nan gaba..Fatana ki kula da ita don Allah da abunda ke Cikinta sannan ki koyamata Girke girke da Sauran Kissa na mata Amina haka tataso Sakaka ba wani abunda ta iya Kinsan Tana da abokan zama dole sai ta kara wayewa kan wasu abubuwan..!
Aisha tace"Insha Allahu Hajiya Zan yi Duk yadda kikace Sannan zan rike Amina kamar yadda Zan rike Hanne .!
Hajiya taji Dadi ta Dinga saka mata albarka sannan tace tatashi ta Rakata Dakin kakar mijin nata su gaisa.
Tare da Amina Hajiya tace suka shiga Dakin da Yakaka take Zaune Yar Dattijuwa kamar zata girme ma hajiya hutu ne da jin dadi suka boye girmanta ta amshe su da Fara"a tana Fadin bata son zuwansu ba,da ta fita sun gaisa Tana nan tunda ta idar da sallar walha bata matsa ba..Hajiya tace bakomai suka gaisa sai kallon Amina take yi Hajiya ta mata Bayanin kanwa take wajen Aisha tana da Ciki zata dan Zauna na wani Lokaci Tare dasu ta karishe da Fadin"Hajiya don Allah a kula..Daga Aishar har Aminan yara ne suna karkashin kulawarki Hajiya ga Amana nan..!
Yakaka na kallon Amina tace"Insha Allahu Hajiya..Na karba zan kuma kula da ita..Allah Sarki gata yarinya karama Allah ya bata..To Allah ya Rabasu lafiya..!
Su Hajiya suka amsa da Ameen Amina ta gaisheta ta amsa Cikin Sakewa tana da Sakin Fuska ga Fara"a nan da nan Hira ta barke tsakaninsu da Hajiya Har Aisha taja Amina suka fita ta nuna mata Dakin dake kusa da na yakaka nan takai mata kayanta Tace nan zata Zauna Daki ne babba mai katifa a kasa sai Cafet da Tiolet aciki Dakin ya Hadu sosai.
Nan Aisha ta bar Amina ta shiga wanka ta fito Cikin Farinciki zata Zauna da Amina sannan gefe Daya tana Tunanin yadda zata inganta Rayuwar Aminene jidali ZUWA Aminene mai aji da Haiba.
Taya Saude tayi suka yima su Hajiya girki ta Dibarma Idi da megadi ta Dibar ma Amina ta mika mata na Hajiya kuma da yakaka Saude ta mika musu Dakinsu.
Aisha tare da Amina sukaci abinci tana yi tana janta da Hira Farar shinkafa ce da wake mai miya Amina kadan taci sai Amai Aisha ta Tsausayama Amina ganin yadda ta wahala wajen amai sannan gata da karancin Shekaru Allah ya bata wannan kyautar ita da tana son Cikin ammh har yau ko bari bata taba yi ba Allah bai kawo ba. !
Ita ta Wanke inda tayi aman a Cikin Tiolet ta kamo Aminar suka tafi tana Tambayanta me zataci tace Tea shi ta Hado mata ta samu ta sha ya Tsaya Daganan Aisha ta barta ta koma Dakin Yakaka ta iske su Hajiya sai Hirar garinsu Bama suke da yakaka nan Hajiya ke fadamata ai su ma sun a zauna a bama su yakaka asalinsu yan Maiduguri ne a bama da labari ya yi Labari Hajiya ta san har gidan su yakaka anan bama kafin yan Boko Haram su Tarwatsa su kowa yayi ta kansa..
Daman ai Yakaka ba ruwanta akwai Hira tare suka ci abinci da Hajiya tayi Sallarta anan wajen Uku saura tayi Shirin Tafiya suka rabu da Yakaka Cikin Aminci kafin su tafi Hajiya ta Damka ma Amima wayar nan da Jafar ya taba kawo mata.
Ta bata ta Sanar da ita Tuntuni mijinta ya aiko da ita sai dai a wanchan Lokacin bata bata ita bane Saboda wasu Dalilai ammh yanzu gata nan zata Fadama Danmallam Saboda ya rika kira yana jin Lafiyarta Sannan tama Aisha bayanin Da Amina Zata Zana jarabawa ammh Dalilin haka yasa zata fasa sai wani Lokacin in ta Haihu.
Amina sai da taga Hajiya Zata tafin da gaske sannan ta riketa tana ta kuka Hajiya tana llashinta tace zasu yi mgana ta waya tana ji tana gani Hajiya ta tafi ta barta sai kuka Aisha ce ta Zauna ta na bata baki Saukinta Daya ma akwai ya Aishar duk da ba kamar su hanne ba ammh da Sauki akwai wanda ka sani a kusa Dakai....
Sai da tayi sallar La"sar barci ya Dauketa Yakaka kuma na jin ance Amina ta kwanta tace maza Aisha ta Tasheta ba kyau barcin yammah Sannan gata da Ciki Dole ta tasheta ita yakakan tazo Dakin Aminan ta Zauna da ita tana janta da Hira ai Tun Amina bata Saki ba har ta Saki jikinta Saboda Yakaka akwai ban Dariya da barkwanci haka ta Dage tana bama Amina labarin Lokacin suna bama farkon hareharen yan Boko haram yadda suka ringa Gudun ceton ransu sai ga Amina na Dariya harda kyatatawa Aisha taji Dadi sosai domin yakaka uwace kamar Hajiya yadda take Daukanta kamar yarta Shiyasa ta matsa sai da Usman ya Daukota daga kaduna wajen kaninsa ya dawo da ita wajensu tasan Amina Zataji Dadin ZaMa da ita sannan zata Dauki darasin wasu abubuwan..!

Hajiya sai Dare ta Kira tace sun isa lafiya har sukayi mgana da Amina ta bata Labarin yadda su hanne suka Dinga kuka ta Fada musu Ta kaita wani waje bazata Dawo ba yanzu Amina itama taji kamar tayi kuka Hajiya ta kara Lallashinta da Fadin kada ta saka Damuwa har ya shafi abunda ke Cikinta To in batayi hakuri ba ya Zatayi..?
Ai hakuri ya Zama Dole tunda haka Allah yayi da ita daga wannan sai wannan..!






*Janafty*
[10/19, 6:19 PM] +234 810 431 4972: *TFZB2018*

*Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yada'ashi..Pay N500 via Jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan lambar 09069067488*

Tun daga ranar Danmallam bai taba kwana batare daya Kira Amina ya lallasheta ba ganin da gaske fa abun na cinta aranta Fatansa Allah yasa kada Damuwar ta haifarma da abunda ke cikin wata matsala sannan bayaso ta fadama kowa abunda ta Fadamai mganar tana Bukatar Bincike da Lura sannan ba kowa bane zai iya Daukan mgar har ya Fahimceta sannan yayi tunanin mafita Shiyasa yake kokarin kiran Aminar yana amfani da Hikimarsa wajen kara Lallashinta da bata Baki.
Wani Lokacin yafi Kiranta in yaje Wajen aiki ko in ya bar gida Zashi masallacin Madina ammh in yana Gida baya Kiranta Daga ita har Sakinar saboda Gudun matsala Ga Sarood kamar ta goyasa haka take ji Dashi bazai so yayi abunda zai ci mata Fuska ba shiyasa yake kiyaye wasu abubuwan sannan nauyi ne akansa ya kwatanta adalci Tsakanin mtansa.
Abunda Amina ta Fadamai na nan aransa kamar ya Tuntubi Hajiya da mganar sai kuma ya fasa yana Tunanin ta ina Zai fara duk da fa yana da Zargin Hajiya tasan wani abu Shiyasa ta Boye Amina da Cikin Dake jikinta,Mallam ma kamar Zai mai mgana sai kuma yaga ai bai da wata Sheda itama Aminar ji tayi bata Nadi murya ba Tunkarar wani da wannan mganar ma a yanzu bai taso ba,Sannan abu ne na Kashe rai duk da daman kowa yasan Mutuwa ta Allah ce sai dai mutum ya Zama Sanadinta.
Bangaran Sakina kuma ai ya Dade da Fahimtar mganar Amina Hakane kodaga yadda bata taba mai mganar Amina ba Ranar Dayake so? ji ta? Bakinta suna waya sai Rigima take mai kan yaushe zai zo ya Dauketa..?
Ita ta gaji da Zama agarin nan baya nan sannan ta yi bari tana son maida Cikinta,Mirmishi kawai yayi kenan mganar Amina ta fito su Burinsu kawai Sakina ta Samu Ciki ta Haihu..?
Saboda ya jarabata yasa yace mata Bata taba Tambaynsa ina Amina ba..?
Sai Sakina tayi Tsaki kafin tace"To ni ina Ruwana..Tunda ta bar min gidan mijina ban damu ba..Ba"an ce hajiya takai ta wani waje ba..?
Yana jinta ammh Daganan bai kara mata mganar Amina ba Itama Sakinan bata Damu ba,ita kamar ma Dadi Take ji tunda ta bar mata gidanta ai taje koma ina ne bata Damu ba Allah ya raka taki gona..!
Allah duk ya shafe musu Tunanin Mezai sa rana Tsaka a Dauke Amina Daga Gumel..?
Duk basu yi wannan Tunanin ba Idonsu ya Rufe da nasu Cikar Burin dukkansu.

******

Usman mijin Aisha ya Dawo washegari suka kai Amina asibiti shi da Aisha speacialist? Hop suka kaita Inda Aisha ke zuwa in Bukatar Hakan tataso,anyi mata Scan cikin Amina Har ya shiga wata na Biyar sannan jininta yana sama kadan Saboda Tana saka Damuwa sannan kuma Sugar masu Ciki na son kamata ammh ita da Abunda ke Cikinta suna Cikin koshin Lafiyan an bata mganin karin jini su Vitamin c da sauransu sai kuma? na cin abinci tunda Aisha Tayi Korafin batacin abinci Likitan yace Normal ne indai tana cin abunda Cikin yake so ba wata Damuwa...!
Ya sanar dasu zata fara zuwa awo Duk bayan Sati Hudu sannan in yayi? shiga wata shidda za"a sake mata wani Scan din
Basu Dade a asibitin ba suka Dawo Gida suka ijiye Amina suka kara Fita kasuwa suka shiga Aisha ta Zabo ma Amina Dogayen Riguna guda Biyar da Wanduna plazo sai ruguna masu yalwar wadanda zasu mata Saboda ta kara kiba kaya wanda tazo dasu sun mata kadan sannan nata bazasu wadaceta ba.
Data kawo ma Amina taji Dadi sosai kamar ta goya ya Aisha tana Daga rigunan adakin Yakaka take fadin"Yakaka kalli Rigar nan bata miki kyau ba .?
Tana zaune saman Cafet tana Gogan goranta tace"Sosai ma ai sai ma kin sakata Ajikin ki takwarata ai mu duk kayan da muka saka sai ya karbemu..!
Ya Aisha na Dariya ta Fice tana Fadin"Ki fito kiyi ma Darling godiya yana Falo..!
Amina in Aisha ta Kira mijinta Da Darling mamaki take bata,agida shuru shuru kamar bazata aikata ba kamar ma batasan komai ba.
Kwashe kayan tayi ta maida a leda ta Saka Hijabinta ta fita falo ta Durkusa tama Usman godiya ya amsa mata yana Fadin"Bakomai Matar yayanmu..Kin dai ji abunda Likita yace ko..?
Ta gyada mai kai kanta na kasa tana jin kunya ya cigaba da Fadin"To sai ki yaye in kina Bukatar wani abu ga Sweety nan ga kuma Yakaka Dukkansu They are Their for u..!
Kanta na kasa ta amsamai Lokaci Daya damai godiya kafin tatashi ta koma Dakin yakaka tana Santin kayanta ta gwada wannan ta gwada wannan tana nuna ma yakaka ita kuma tana yabonta Amina ta gwada wata Riga Mai yalwa ta juya ta Sake juyawa kafin tace"Sai yanzu najini Daidai...Ammh wacce ya Aisha ta bani jan nan tamin kadan fa yakaka..!
Yakaka tace"To Daman ai irin wannan ne Daidai dake..Daga gani ba wani Girman Ciki Zaki yi duk a kiba Zai tsaya .!
Amina ta bata rai kafin tace"Wai sai nama kara Kiba yanxu..?
Yakaka na cin soyayyan gyadan da su Aisha suka siyomata a kasuwa tace"Af ai sai kin ninka kibanki na yanzu..
Ai sai Amina ta Zauna akasa ta Fashe da kuka Yakaka ta saki baki tana kallonta Kafin ta tabe baki tana Fadin"Yarinyar nan kin samu waje..Ki bari Balaraban Madina yazo sai ki mai wannan shagwabar..!
Amina Ta tura baki Batayi mgana ba Yakaka tayi Dariya kafin tace"Tsoro kike ji kada su kwace shi..?
Amina tace"Tab..Allah ya Tsareni ni bana tsoron su har ita gajeran ma..!
Yakaka tayi Dariya kafin tace"yauwa haka nake son naji Tsoro ai ba namu bane..kada ki Damu kina Haihuwa Zaki Dawo silandiyan dinki..!
Amina ta washe baki Tana Fadin"Da Gaske kike yakaka..?
Yakaka tace"sosai ma ai mu ko da kiban mu muka je mune agaba bazamu taba komawa baya ba. !
Amina ta amsa da wlh kuwa Daganan ta warware suka Cigaba hirarsu Daman kukan Aminar na Tabara ne da jidalinta.

Hajiya suna waya da Amina ta wayar Amina Tunda Aisha ta Tura mata lambar Aminar koda yaushe sukayi mgana sai Amina tace ina su hanne abasu su gaisa sai Hajiya tace ba yanzu ba ko Aba bata yarda ta Kira ba sai Mallam kawai ta Turo mata Lambarsa ta Kirasa suka gaaisa ya Dinga

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login