Showing 33001 words to 36000 words out of 141906 words

Chapter 12 - Ta Fita Zakka Part 2

10 Oct 2024

4179

ce mai soya kwai wajen Rabin Kires suka soya yazo yayi musu yawa ga Tea nan suka Ragesa cikin su ya cika Hanne tace"Ko zamu kaima megadi ne..?
Hamida tace"Ke ina ruwanki ga matar gida batace ba..!
Amina data gama shan mganinta ta koma ta kwanta saman Cafet Cikinta ya Cika tace"Uban matar gidan ce Ina ga da wannan gajerar matar yayan Hanne kike mgana itace mai gidan..!
Dariya sukayi kafin Hanne tace"Kema me gidan ce wlh..Gashi Dalilin ki har mun Dankwali arziki ko ba Haka ba Hamida..!
Ta Daga mata kai suna Dariya har da ta tafawa Amina tayi karamin Tsaki kafin tace"Yan iska kawai..!
Sukace sun ji ba bakomai karshenta saman Dining suka maida suka rufe amjima zai musu amfani.
Amina Daganan barci ya kwasheta su koma sai suka tashi Hamida ta gyara Dakin da suka kwana da Kitchen Hanne ta gyara Falo suka goge shi Tas sun nemi burner nasa Turaran wuta basu gani ba sai suka kunna na Tsinke Gidan ya Dau kamshi Sai da suka gama Amina tatashi ganin aikin da sukayi ne yasa tayi mika tana Fadin"Dadina da Kawayena akwai aiki kamar Dawakai..!
Baki suka saki suna kallonta Hamida tce"Zaki ga Dawakai nan da jibi in muka tafi in kika fara yi da kanki..!
Amina tamarairaice kafin tace"wai ku nan da gaske tafiyar zaku yi..?
Hanne tace"Wlh Hajiya tace Ranar Lahadi idi zai zo ya Daukemu..!
Amina tace"Tare dani kenan domin kafar ku kafata..!
Suka Sheke da Dariya kafin Hanne tace"Wa ?ai kin zo kenan yarinya har Abada..!
Hararansu tayi ta tashi ta shige Dakin nan ta gansa tas har da Tiolet Hamida ta wanke shi Tas kwanciya tayi kan gado tana kara jin Dadin ganin su Hanne Tare da ita.
Su kuma basu kwanta ba Wanka sukayi Hanne ta farayi sannan Hamida da suka ma Amina mgana bayan sun Daketa tatashi Tana masifa Hanne tace"Ki tashi kiyi wanka malama sai ki kwanta..!
Amina ta koma ta kwanta tana fadin"Jiya nayi wanka..Wlh ni yau bazan yi ba haba kamar wata
kwado..!
Basu yi mamaki ba Saboda susan Amina bata shiri da wanka Hamida tace"Amina da fa da yanzu ba Daya bane..Ke yanzu matar aure fa kazanta bana ki bane..!
Ko kallonsu batayi ba Hanne tace"Ita ta sani..kishiyoyi dai har Biyu gareki kuma Duka yan gayu ne sannan ya Danmallam bai shiri da kazanta..!
Hamida tace"Kuma bazamu ji Dadi ya raina mana ita ba ko kishiyoyinta su ran mata ba..!
Amina ta Dago kanta kafin tace"Da ku da Kishiyoyin duk naci ubanku na Zauna Lafiya..!
Hamida ta kalli Hanne suka Hada ido suna kunshe Dariyansu tana ganinsu tayi banza dasu daman Hanne da Hamida akwai gulma sun kware wajen munafunci.
Haka Amina ta wuni batayi wanka ba sun gaji da mata mgana sun kyaleta da Rana basu yi girki ba sauran kwan daya rage suka ci suka kuma kara soya samosa suka ci suka hada da maltina da Daddare kuma suka Tarun ma Dambun mana suka ci suka kwanta Washegari Hamida da Hanne Dakyar suka ga Safe suka kwana Murdawan Ciki da Zawo Amina Daman akwai Lafiyan ciki bakomai ke bata mata Ciki ba.
Haka ta Dinga musu Dariya Hamida tace"Hanne Amina wlh muguwace tasan cikinta ita lafiyansa kalau ba sai tace kada mu ci da yawa ba..!
Hanne daman nada ulcer tana Mai da Numfashi tace"Ni sam na manta inda Ulcer ma..!
Amina me zatayi ban Dariya Cikin Dariya tace"Hajiya ni tace ku kawo ma abu ammh Saboda maita ku sai an ci komai daku kadan kuka gani..ma..!
Haka ta wuni yi musu Dariya Ranar ban da Tea basu iya cin komai ba sai da Daddare da suka ji sauki Zawon ya Tsaya da ciwon ciki sannan suka Dafa Doya sukayi miyar kwai suka ci suka kwanta.
Washegari ma barcin su suka sha sai sha Biyu suka tashi suka karya da Sauran Doyan jiya suka gyara gidan Amina na zaune tana kallonsu An samu Amina tayi wanka jiya ammh yau kam tace bazatayi ba ta gaji sudai sukayi suka Sauya kaya Daganan aka Fara Tunanin me za"a Dafa.
Amina tace Hamida tayi musu wainar Fulawar datake yi agida mai Dadi Tunda ga Yajin da Hajiya ta kawo mata .
Nan da nan suka yarda da mganar Amina suka Dunguma zuwa kitchen suna neman Faluwa sun sha mamaki Fulawa buhu Guda ko kwata ba"a taba ba Nan suka Diba suka kwaba suka saka kwai ma"ishi suka yanka albasa Hanne tayi Gireting din kayan miya da suka gani Cikin Freezer harda nama wanda Amina tace soya shi za su yi Hanne tace sai dai Ferfesu basu da lafiyan ciki..Amina na Dariya tace"A soya yafi Dadi..!
Hanne tace"Muguwa muguntarki ta kare miki Amina..!
Sai Dariya Amina ke kyatatawa har tana Hawaye.

********

Mamanmu na kitchen tana soya kifin da Aba yaba Jafar ya kawo Dazu wayarta Dake tsakar gida kan Tabarma ta Dau kara alamun kira Gidan ba kowa sai ita kadai Hamida suna gidan Amima jawaad kuma sun tafi Hadda.
Burin Mamanmu ya cika ita kadai ke juyi a gidan Sa"idu sai abunda tace akeyi sai kuma an nemi Shawaranta.
Fitowa tayi da Sauri bayan ta juya kifin Dake kan gas kada kafin ta Dawo ya Kone.
Tana Daukan wayanta taga Madina ke kiranta sai da gabanta ya fadi Bata rai tayi afili ta Furta"Har Abada madina baza ta barni na Huta ba
Haba wannan kawwazzaba dame tayi kama mtswww..!
Ta ja wani Dogon Tsaki kafin ta Daidaita kanta ta Daga kiran tana Fadin"Buhun Sikari baki Farin banza ba..!
Dagachan bangaran Anty Amarya ta Katseta da Fadin"Ba bu abunda zaki Fadamin Ya sanyayamin rai Dayyaba..Ki ma yimin shuru kawai..!
Mamanmu ta marairaice kafin tace"Me kuma ya faru..?
Allah yasa ba kwabarmu ce zatayi Ruwa ba..!
Anty amarya tace"Kwabata dai Zatayi Ruwa Dayyaba...aike kin samu abunda kike so shiyasa kika maidani Wata Shashasha ko nema na baki yi Dayyaba Tunda na gama Taimaka miki kin samu Sa"idu a Hannunki ni kuma kin kasa taimakamin nawa Burin ya cika ko..?
Ni ban raba Maallam da Sa'idu ba sannan ta bangaran Sakina har yau ba wani mgana mai Dadi..!

Mamanmu ta Harari wayar kafin tace cikin karyewan murya"Haba Madina meyasa kin cika gaggwa ne..?
Kin Tsaya na gayamiki irin kokarin da ni ke nan ina yi miki akan abubuwa su Daidaita kuma da kike Fadin na Samu Sa"idu ai ban ga samunsa ba Domin har yanzu akwai rina akaga Hajiya da mallam sun sha gabana..mganar Sakina kuma ai mun gama mgana kince zaki sa ka mallam yasa turama danmallam son ko ya tafi sai ya Dawo ya Dauketa sannan mu na Fatan Zata samu ciki kuma zai zauna Zata Haifesa da yardan Allah mganar Shegiyar yarinyar nan kuma Amina sai dai su mallam su gaji su Raba bazai Taba wani amfani ba..!

Sai alokacin Anty Amarya taji ta dan Sauka Cikin Saukan Numfashi tace"Dayyaba ni Hankalina yaki kwanciya gani nake yi abubuwa duk suna ta lalacemin Tsarina duk ya lalace..Umar din ya tafi ni Kawai Burina ya Dawo ya Dauki Sakina su koma,in har ya tafi mallam yace ba lalle ya dawo nan kusa ba kinga mallam da Hajiya haka zasu gaji da ganinta ahaka su raba auren daman wanchan balarabiya Hoto ce itama in ta gaji zata kara gaba ne..
Mamanmu tace"Sosai ma ina amfani Zama da miji Hotiho ba wani amfani ina mai Tabbatar miki bazata zauna ba..Ki kwantar da Hankalinki Saura Kiris burinmu ya cika kada ki manta Sakina ba Juya bace tana samun cikin yana Barewa ne..!
Anty amarya tace"Dayyaba shine abun Damuwata ko an samu cikin baya Zama na fara Tunanin akwai wani a kasa..!
Mamanmu tace"Ko..?
Kanar na menene..?
Anty amarya tace"Ciki wajen sau Hudu da an sanu sai ya lalace anya Dayyaba..?
Mamanmu tace"To kin sa malam ya Duba mana kuwa..?
Tace"Eh ya Duba yace bai ga komai ba..Ammh ni haka kurum nake ji akwai wani wanda muke Tufka Daga Gefe yana mara warwara ko shakka bana yi.. kinsan daman ya taba Fadamin acikin matan mallam akwai wacce itama bata zauna ba..bai dai Fadamin sunan kowa ba.
Mamanmu tace"to wa kike Zargi..?
Anty Amarya tace"Cikin matan mallam ne dai..Ko Haj.Nasara ko Hj.Uwani..Akwai wacce acikin su bata so mu cimma namu burin..!

Mamanmu ta zaro ido kafin tace"in ma sune to saboda mene..?
Anty amarya tace"Saboda cikar Burinta itama..Kamar yadda muke son mu cimma namu Burin..!
Mamanmu tace"Tabdijam akwai kura Tsugunno bata kare mana ba..!
Ni fa basu nake zargi ba ina Tunanin ko dai Hajiya ce bata so Sakina ta Haihu..?
Anty amarya tace"Ba Hajiya bace..Bata yar da za"ayi ta hana Sakina Haihu wa kada ki fa manta Umar D'a???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?nta ne..zata fi kowa son ganin kwansa a duniya..!
Mamanmu ta jinjina kai kafin tace"Kuma fa hakane..!
Ni ban ma taba kawo wannan Tunanin ba sai da kika Fada na gane zai iya Faruwa..!
Anty amarya tace"Ai ki bar mugu..Bai da kama Dayyaba..Da mugu nada kama da Tuni Sa"idu da ya"yansa basu baki Dukkan yarda ba..Da mugu nada kama da Yaya bata taba Sakin miki Ragamar ya"yanta ba har Abada..!
Mamanmu ta bata rai kafin tace"Bangane ba..?
Ki sa min jaye mugaye zaki ce..!
Anty amarya tayi wata Dariya kafin tace"Ban kai ki mugunta ba Dayyaba. ina mai kara gayamiki ban kai ki ba..Domin ko ni sanda kika zomin da Fuskarki ta Dayyaba domin mu Hada Hannu na Girgiza ballatana Sa"idu da ya"yanku..?
Ina mai Tabbatar miki kiji Dadinki yanzu ammh in alalan geren mu ya tashi yin Ruwa da Tsami wlh naki sai yafi Nawa Tsamewa..!
Mamanmu tace"Da izinin lahi bazan ga haka ba..Ni Dayyaba Nasara na sani ba Faduwa ba Madina..!

Dariya tasake yi kafin tace"Muna fatan haka yanzu ba wannan ba yaushe zamu hadu..?
Ya kamata mu sauya Tsarin mu sannan mu san ta yadda zamu gano wanda ke kokarin batamana aiki..!
Mamanmu tace"Ina so mu hadu bana samun Lokaci ne gida ba kowa sai ni kadai..Hamida bata nan tana gidan Amina..!
Anty Amarya ta Zaro ido kafin tace"Wata Aminar..?
Mamanmu ta tabe baki tana fadin"Wacce kika sani mana..Bakisan suna gidan Amina ita da Hanne ba Tun Ranar alhamis da yammah Hajiya ta turasu..!
Anty Amarya ta mike Daga Zaunen Datake gefen gadonta tana fadin"Kan burauba..Bansani ba..Naji dai jiya Sa"adatun na fadin bata ganinsu a Hadda ban maida mganar mai ma"ana ba shiyasa ban bincika ba..Na Shigesu Dayyaba Sakinarma tun aranar da Umar ya koma tana Dutse..!

Mamanmu tayi shewa kafin tace"Au to..Aiko tayi wauta suna chan ta bar musu gidan suna Yadda suka ga Dama..!
Anty Amarya bata jira cewar Mamanmu ba ta yanke kiran ta bar Mamanmu da Hararan waya Lokaci Daya ta Ijiyeta nan kan Tabarma ta koma Kitchen tana fadin"Kawai kin zo kin Tsaidani kan mganar banza..Badai nawa Burin ya cika ba..Ban Damu ba..In dai ni na samu abunda nake so Uban kowa kada ya samu..!
Bana kaunar Amina ta Dawomin gidan nan zata lalatamin Tsarina Yadda tatafi tatafi kenan har Abada Shegiyar yarinya mai kama da Uwarta..!
Haka tayi ta manganganu ita kadai.tana ciga da suyan kifinta Duniya tayi mata Dadi.

Anty Amarya kuwa Lambar Sakina ta Kira sai da kusa katsewa ta Daga ko Sallamanta bata amsa ba ta fara Fadin"To shashassha..kina nan kwance ga Amina chan da su Hamida suna yadda suka ga dama da gidanki. !
Sakina na kwance ne sai da ta mike tana Fadin"Bangane ba.?
Nan Anty ta shaida mata abunda mamanmu ta fadamata Sakina tace"Kuturun uba.... to ubansu zasu ci na kulle ko"ina har Kitchen fa..!
Anty Amarya kamar ta Zageta haka taji cikin Tsawa tace"Dayake ke kadai ke da key din gidan ba..?
Karki manta Uwarsa ma na dashi kuma na tabbata sun tafi dashi ki cigaba da zama agidan da nayi Burin ki Rayu ke kadai tun ba"a je ko"ina ba yana neman ya zama ba naki ba..!
Daga haka ta Datse kiran tana Faman Huci Dagachan Dutse kuwa Sakina ta Diro Daga kan gado ta Fada wanka sai yanzu ta Dawo Cikin Hayyacinta.
Allah ya taimaketa akwai wani yayanta zai taho kano shi ya Daukota har Gumel har kofar gidanta ya ijiyeta sannan ya wuce alokacin Shida na yammah har tayi san da ta abuga get din megadi yazo ya Bude mata bata Tsaya amsa sannu da zuwansa ba taja akwatinta ta nufi Cikin Falon.

Amina da Hanne suna Zaune Saman Cafet hamida na Saman kujera suna Hira sannan ga filets nan da suka gama cin wainar Fulawarsu nan da Ferfesun naman rago da sukayi ga Kofuna ga abun maltinan da suka gama sha Falon dai kaf ba Kintsi? Saboda? tunda suka gama suka koma gefe suna Hira sun ma manta yau zasu koma gida Tsabar yadda Rayuwa tayi musu Dadi gaddamace ta Sarke Tsakanin Hanne da Amina kan lokacin Bikin su ya Abida Amina na Fadin yadda Hanne ta manne ma Sa"adatu saboda yar"uwatance ita kuma Hanne tana kokarin nuna ma Amina Daga su har Sa"adatu duk Dayane hamida kuwa bata sako bakinta ba sanin Halin gaddaman Amina ko bata da gaskiya bata saki. kwata kwata basu san Sakina ta Shigo ba ashe ta Dade Tsaye taba Bin Falon gidanta da kallo yadda ya zama.
Ranta in yayi Dubu ya baci akwatin Hannunta ta saki ji kake garam lokaci Daya ta Rike kugu tana fadin"Kutumar Uban chan Falo na ne ya koma kamar gidan abinci?
Lalle yau zaku gane baku da wayau duk sai naci Ubanku daga ku har kazamar data jawo ku..!
Ta karishe fada tana Cire gyalenta ta Ci Darama dashi Tana jifan su Amina da wani matsiyancin kallo wadanda sai alokacin suka san da wanzuwarta afalon Hamida da Hanne ne suka Tsorata Amina kuwa ko ajikinta itama kallon rainin ta maida ma Sakina kafin ta tabe baki ta kauda kai.
Hanne ce da Hamifa suka mike da Sauri Jikinsu na rawa Hanne na faman Fadin"Sannu da zuwa Anty Sakina..!
Ita kuma Hamida ta fara Tattara filets din tana fadin"Kuyi hakuri yanzu zamu share mu gyara ko"ina..!
Sakina ta kariso Falon tana Hararansu Lokaci Daya tana fadin"Dilla kumin shuru..uban wa ya baku izinin zuwarmin gida batare da sanina ba.?
Hannu hamida tabi da kallo kafin tace"Kan uba har kitchen dina ma kuka Bude kuka shiga kuna min kazanta..?
Yau zan ga wanda zai Rabamu daku acikin gidan nan..!

Amina mamaki kamata yayi ganin yadda Hamida da Hanne suke bata Hakuri jikinsu na rawa sai Faman Zaginsu take yi ranta ya baci ta Dauka tayi sanyi ashe batayi ba batasan Sadda ta Mike ba sai jin muryanta sukayi tana fadin"Dillah ku daina bata Hakuri..Kun zo din ai ba gidan Uban kowa bane nan..Gidan mijina ne kamar yadda yake gidan mijinta sannan kada ta manta nan din gidan yayanku ne ko sama da kasa Zata Hade shi din jininku ne wata fa..?Yar karo ce..Saboda haka ku saki jikin ku ku Wala ba wacce ta isa ta Daga muku Hannu ina gidan nan wlh..!
Ta karishe Fada itama tana Hararan Sakinar da manyan idanuwanta.
Hamida da Hanne suna ta kyafta ma Amina ido bata bi ta kansu ba Sakina ta nuna kanta tana fadin"Wai dani kike..?
Amina ta karkace baki tace"Ban kira suna ba..Ammh in kin Tsargu ba ruwana..!
Sakina taji ranta ya kara baci Tayi kukan kura tayi kan Amina tana Fadin"Yau sai naci Ubanki acikin gidan nan.!
Su Hamida suka shiga Tsakani suna bata Hakuri Hanne sai ta Fara kuka tana fadin"kiyi hakuri yanzu zamu gyara ko"ina Hanida ko ba"a zo Daukan mu ba yanzu zamu tafi..!
Amina datayi ke Tsaye Cikin mamakin ko Sakina Dukanta zatayi tayi Shewa kafin tace"Wlh badai ubana ba..kin gama Zagin Ubana na kyaleki..!
Sakina tace"Sai nawa Uban ko..?
Amina ta Tura dankwali Gaban goshi kafin tace"To nidai ban ce ba..Ko banza nasan Darajan tsohon wasu..!
Sakina ta Harzuka haka take Zagin Amina har tana fadin"Badai ke yar iska bace ko...?
Bari? zan kira? habibin Wlh bazan iya Zama Da kazama irin ki acikin gidana ba. !
Amina tace"Gidanki ko gidanmu..?
Malama ki kara Min jaye..!
Mu uku keda wannan gidan Dake da ni Amina da yar balarabiya baki da kuma yadda zaki yi..!
Ran sakina ya baci tana mamakin yadda yarinya karama ta zauna tana Fada mata mgana Hamida da Hanne na Faman bata Hakuri suna fadin zasu tafi.
Amina ta kallesu tace"kudai wlh bazanye ne..To uwarki ce ita..kun zauna kuna ta wani bata Hakuri tana Kara Zagin ku..bazaku gyaran ba tayi abunda zatayi..!
Hanne tace"A"a Amina mu muka bata bari mu gyara mu zo mu tafi..!
Amina tace"In kun tafi Allah tsinan naga mai fita agidan nan..!
Ta fada tana wani juya ido kafin taja Tsaki Sakina taji kamar tayi Bindiga ta koma ta Dauko akwatina Kamar Kububuwa ta wuce ta Bude Dakinta ta Shiga tana Tunanin yadda zata yi Biji Biji da Amina Umar ya ja mata raini wajen wannan yarinyar.
Tana shigewa ta banko kofa Amina tayi Tsaki ta koma ta zauna hakanan taji Ranta na kuma kamar tayi Bindiga haka take kada kafa tana Girgiza jikinta Hamida da Hanne suka Bita da kallo basu tankata ba Azaton su Jidalin Amina ya ragu ashe karuwa yayi basu sani ba hamida ta tatattara komai Takai kitchen ta Hada wanke wanke Hanne kuma ta Fara gyaran Falon Amina na Zaune tana kada kafa Ranta na mata wani Zafi kamar ana Hura mata wuta ita kanta Hanne bata taba ganin Amina tayi irin wannan ba,Shiyasa bata tankata ba itama batace mata komai ba..!












*Janafty*
[10/19, 6:19 PM] +234 810 431 4972: *TFZB2010*

*Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yad'ashi..Pay N500 via jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan Lambar 09069067488*

*Bayan kwana biyu..!*
_Area:Prince Naif ibn Abdulaziz Road,Aljami"a P.O Box 170,Madina Saudi Arabia_

Shigowarsa kenan Cikin kayataccen Office dinsa mai girma da Fadi yana Hawa na Hudu ne a bangaran ofishin Malaman makaranta ta Madina bangaran Shashin Qur'an and islamic Studies babban Shashi ne mai Dimbin Tarihi a cikin babbar Jami"ar ta Musulunci Dake madina.
Littafan hannunsa ya zube bisa Babban Tuburin dake cikin Ofishin kafin ya samu waje ya zauna Hular kansa ya cire Lokaci daya yana shafa Sumar kansa data fara Tohowa.!

Gajiya ce ajikinsa domin yau tun Safe ya bar gida yana da ajin karfe takwas na Safe zuwa goma sannan bayanan ya shiga na goma zuwa sha biyu daganan kuma suna da meeting da zasu yi na malaman shashin Dayake koyarwa gabadaya
Sakamakon yau Alhamis ya tashi da azumin Lada kamar yadda ya saba so yake ya tashi ya isa babban masallacin Cikin makaranta yayi karatun Qur"ani kafin lokacin Sallah yayi ammh ya kasa tashi kasala Tare da Gajiya sun Taru sun lullubesa.
Kansa ya kwantar kan kujeran Dayake zaune idanuwansa suna lumshe kamar mai jin barci nan kuwa ba barci yake ji ba Tsabar Tunanin abunda ya faru tsakaninsa da Sarood jiya da Daddare ne ya

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login