Showing 60001 words to 63000 words out of 141906 words

Chapter 21 - Ta Fita Zakka Part 2

10 Oct 2024

4145

irinta su Marliya da ma wasu Boyayyin wadanda Allah bai bayyanasu ba Domin ta tsorata Ta kasa ma yarda da kowa gani take Tunda Uwani ta Cutar da ita to wanda batayi Tunani ba shima zai iya Cutar da ita kafin Su farga da Cikin Amina ya kamata tayi wani abu a matsayinta na Uwa yau dai ta cire kawaici da kunya da nuna ikonta in takamar su boka da mallan ita ta rike Allah sannan bawa bai isa yayi ma Mutum abunda Allah bai masa ba.
Zata kare Amina da abunda ke Cikinta Har sai ya bayyana Lokacin da Danzaki ya girma basu isa su ga karshensa ba Umaru zai haihu Tabbas zai ga kwansa Daga Tsatso mai Daraja Tsatson Sa"idu da Hadiza ta sani addu"arta ne Allah ya amsa ta Dade tana Fatan Ganin Zuru"a mai yawa ta bangaran Umar da Amina tun kafin mallam ya Hada wannan auran Burin haka ke ranta.
Zata nuna musu ba su isa ba..Allah ya Fisu sannan suna Raye za"ayi komai Da yardan Allah sun fara ganin Rashin Nasara har abada acikin Rayuwarsu sannan burikansu bazasu taba Cika ba..!
Tsam ta mike Amina ta leka taga ta Samu barci kafin ta kada kai ta Shiga Dakinta wayarta ta Sake Dauka ta Kira Dannallam har alokacin yana Cikin Daki bai fito farimcikin abunda Hajiya ta Fadamai ya kasa sakinsa Tsammamin abunda baka Taba Tsammani ba wajen wanda bakayi Tsammani ba..!
Sarood na falo tana ta samu barci ya lekata ya gani shiyasa ya Dawo Daki ya Zauna kawai yana ta Tasbihi da yima Allah kirari Lokaci Daya soyayyar abunda ke Cikin Amina ya shiga ransa shiga ran da ko Sakina in ta Samu Ciki bai taba jiba Fata yake da Addu"am Allah ya bar masa wannan Ciki shi kadai yake tunanin Haihuwar Amina Zai faranta ran mallam da Hajiya da Baba Sa"idu fiye da Tunaninsa alokacin Kirjinsa ke Budewa Da sunan Amina da dukkan abunda ya Faru Tsakaninsu sai ga wani Kira Daga Hajiya gabansa ya fadi ya rika Allah Allah yasa ba cewa Zatayi wasa take mai sai da ta gama Ringing sannan yabi bayan kiran.
Sai a wannan karon ne Hajiya ta bari suka gaisa Cikin Yanayinta na rashin Dadi tace"Ina fatan mganar da na Fadamaka baka Fadama kowa ba ko..?
Kai tsaye ya amsa mata da Eh Hajiya ta gyara Zama tana fadin"To ka min alfarman bazaka fadama kowa ba Ciki kuwa har da matanka da Sa'idu da abokinka Aliyu ko yan"uwanka ban amince ka Sanar da kowa Amina dana Ciki ba .!
Cikin mamaki yace"Hajiya har da mallam..?
Hajiya tace"Ni zan sanar dashi Dakaina wannan..Ta bangaranka ka bar mganar nan asirri Umar..Ban yarda da kowa ba za"a iya Cutar da Abunda ke Cikin Amina nayi alkawarin da sunan Allah zan bata kariya saboda haka kayi shuru da bakinka ..!
Cikin gamsuwa yace"Na Fahimta Hajiya..Allah ya saka da alheri..!
Hajiya ta amsa da Ameen ta Cigaba da Fadin"Sannan zan Dauke Amina Daga idon mutane..Saboda wasu Dalilaina bana son bayan ni dakai da mallam wani yasan da mganar Cikinta da kuma inda zan kaita ajiya har zuwa Lokacin da Cikinta zai isa Haihuwa..!
Cikin mamaki yace"Hajiya ina kenan..?
Kai Tsaye tace"Abuja zan kaita Wajen Aisha..Chan zata Zauna na wani Lokaci kafin abubuwa su Daidaita..!
Danmallam mamaki ya cikasa sai dai baya yima iyayensa gaddama yace"Shikenan Hajiya kiyi duk abunda ya kamata..!
Ta jinjina kai kafin tace"Kada ka Damu zuwa Lokacin duk zaku san Dalilina na hakan sannan zan bata Wayar nan a hannunta in ta koma chan ku cigaba da mgana ta waya..!
Cikin girmamawa ya amsa mata kafin Cikin wani yanayi yace"Tana Lafiya ko..?
Hajiya tayi Mirmishi kafin tace"Lafiya kalau..jiya ne ta kwana da Zazzabi shine yau mukaje asibiti likita ya auna jininta sai ga Ciki kaji abun Allah ko..?ko ni Da nike Tare da ita Allah bai bani ikon gano hakan ba..Shiyasa na yarda akwai abunda Allah ya Boye kan cikin nan na Amina..Umaru ka Dage da addu"a don Allah azkar safe da yammah da Karatun Qur"ani na yarda Bawa bai isa yayima Mutum abunda Allah bai mai ba addau"armu gareku bazata taba Faduwa kasa banza ba duk Salolinka kada ka manta da Rokar ma Amina Tsarewar Allah da ita da Abunda ke Cikinta kaji ko..?
Sai duk jikinsa yayi sanyi da kalaman Hajiya duk da tana yawan fada musu su dage da Addu"a ammh na yau na Dabam ne Cikin Sanyinsa ya amsa mata ta Dinga sakamai albarka kafin suyi sallama tace Zata kirasa in sun yi mgana da mallam zuwa gobe take son ta kai Amina Abujar bazata ba ta Lokaci ba.
Bayan ta gama mgana da Danmallam Nazir ta kira suka gaisa shima abunda tace ma Danmallam tacemai shima sai yaji wani iri Hajiya kamar tana barin Wasiya suna gama waya ya Kira Danmmallam a chan madina yana Tambayansa ko sun yi waya da Hajiya yace eh sai yake tambayansa ko ta yimai nasiha da rokom ya Dage da addu"a yace eh sai nazir ya fara Tambayansa ko Hajiya bata da lafiya ne ya Tabbatar mai da lafiyanta kalau sun Dade suna tattaunawa kafin su rabu kan Shi Nazir din ranar Lahadi zai zo yaga Hajiya ya koma saboda Hajiya is d Best mother in d word.
Bashi ba ko Hidiya na Fadin bata ga Uwa kamar Hajiya ba mai kirki mai kawaici sai ta kirata sau goma su gaisa bata kira dan data Haifa ba Tunda suke da Hajiya sai dai ta Bisu da addu"a bata taba Saka ido kan samun su ba bata taba tambayansu wani abu ba sai dai su Dauka su bata ta amsa tana godiya tana saka albarka ita da Mallam samun a iyaye is a Bleesing basu taba Dogara ga abun hannun ya"yansu ba sai dai su bisu da saka albarka da addu"an nasara.

Hajiya kuma suna gama mgana da Nazir ta shiga wanka Saboda tana sauri suka Fita asibiti bata Tsaya yi ba tana fitowa taga wayarta na Haske tana Dubawa taga Mallan ke kiranta ta Dauka sukayi mgana yace mata ya Dawo tace mai gatanan zuwa Daman shi take jira,Mai ta shafa ta shirya Cikin wani sabon less din da Mijin Aisha ya Dinkamata suka aiko mata dashi har da mallam ma sun dinkamai shadda ganin Dattakon Mijin Aisha da kuma sanyin Aishan yasa ta Zabi ta kai mata Amina ta Zauna awajenta tasan zata kula da ita sannan kuma ba wanda zai san tana wajenta indai ba ita Hajiyan ta Fadama wani abu ita kuma tayi alkwarin bama Amina da abunda ke Cikin kariya da ikon Allah..!
Kitchen din Shashenta ta shiga ta Dora ma Maallam Ruwwn Tea dinsa Datake dafamai na Sassaken mganungun Musulunci mganin sanyi ne sai da ya tafasa ta Juyemai a Fulas Ta Dauka da kofi saman wani katon Faranti ta fita zuwa Kitchen din Tsakar gida suka gaisa da su Lami taga Doya suka soya sai Miyar albasa da sukayi ta Diban ma mallam din ta Nufi Shashenta ahanya ta Hadu da Anty Amarya ta Dawo daga wajen mallam din Fuska kozai kozai kamar wacce tatashi Daga jinya sama sama Hajiyar ta Tsaya suka gaisa ta wuce Anty Amarya ita kanta sai da ta Bita da kallon mamaki ganin yanayin Hajiya na yau din da bata taba gani ba ,ko Sakina bata tambaya ba akwanakin nan kuwa ko bata shiga ba in suka Hadu sai ta tambayi Jikin Sakinar sai ta Danganta hakan da abunda ya Faru Jiya Uwani ai tatashi Wasa da ita yanzu ma mallam taje kara bama Hakuri har ya Sallameta bata samu wani kyakyawan kallo Daga garesa ba.
Ta bi shawaran Dayyaba ta kira mallaminsu ta gayamai yayi mata mganin Uwa sannan ta sanar dashi ya Dakatar da Barin Cikin da Sakina take yi yace zai kirata nan da kwana uku ta Saurareshi,so take kafin Lokacin ta Samu mallam ya kalleta da kallon yafiya da kauna sai abun da yazo mata da Sauki ammh kalli fa mallam ko son ganinta bayayi ai Uwani ta gama Cutar da ita..!

Hajiya koda ta shiga Falon mallam yana zaune yana nazarin Wani Littafin labarci ya amsa mata sallamanta ta shigo ta ijiye farantim Hannunta ta Zauna gefensa suka gaisa
Ya tambayeta jikinn Amina tace da Sauki ya karya Tukunnah sai suyi mgana Littafin hannunsa ya ijinye ya Sauka kasa ya Tankwashe kafa ta Zubamai ya fara ci Hajiya na gefe tana kara Nazarin shawaran data yanke tana fatan Allah yasa mallam ya yarda da Tsarinta kada ya matsa sai yaji Dalili duk da awajensa ya"yansa suka Dauko Rashin son jim abunda ba"a so su ji ba
Suma haka suke basu da yawan Tafiya ballatana Bin kwakkwafi.
Sai da ya gama sannan ta tattara komai ta matsar gefe ita ko yunwar bata ji Cikinta ya Cushe da yanayin Data ke Ciki shima mallam din kallonta yake yi Cikin wani yanayi yace"Zainabu Fuskarki ta bayyana Damuwa..?
Me yake Faruwa ne..?
Hajiya ta Sauke Numfashi kafin ta mike tana fadin"Mganace dani mallam mu shiga ciki..!
Yayi mamakin jin tace su shiga Ciki bai mata musu ba ya tashi yabi bayanta zuwa Cikin kuryan Dakinsa abunda ya basa mamaki suna shiga ta Sakayo kofa shidai yana binta da kallo ta Dawo ta Zauna agabansa asaman Katuwar Dardumar Dake Dakin.
Cikin ajiyar rai tace"Mallam Munje asibiti likita ya Dibi Jinin Amina an aunata kuma yaga Ciki wanda yakai kimamin Wata Hudu da kwana goma ajikinta..!
Mallam sai yayi mata kyar yana kallonta na tsawon Lokaci kafin kawai ya saki kabbara..!
"Allahu akbar..!
"Allahu akbar..!
"Allahu akbar..!
Sai da ya maimaita sau uku sannan Cikin Tsantsan Farinciki yace"Kin gani ko Hajiya..?
Allah shi kadai yasan Lamarin Daya Boye kam Mamana da Umaru ...Kai wannan labarin Farinciki ne Hajiya Masha Allah ina mamar tawa fata Dai Likitan yace ba wata matsala ko..?
Hajiya tace"Ba wata matsala..!
Mallam na jinjina kai Cikin Farinciki yace"madallah..Allah ya inganta Allah ya Bata lafiya ya zaunar dashi Allah yasa ta Sauke lafiya..!
Hajiya ta amsa da Ameen Mallam yaga yanayin ta wani a sanyaye yasa yace"Hajiya naga bakya murna ne..?
Ko da wata matsala ne..?
Sannan ya kamata a Fadama mijinta..!
Hajiya tace"Na fadamai..!
Cikin mamaki yace"kin fadamai fa kikace..!?
Ta gyada kanta kafin tace"Eh mallam..Kuma na rokesa bayan ni da kai da shi ko Sa"idu bazai ji labarin Cikin nan na Amina ba mallam..!
Mallam ya kalleta yana fadin"Bangane ba.?
Hajiya ta gyara Zama tana fadin"Ina da Dalilina mallam..Bana son cikin nan na Amina ya fallasa..Daga ni sai kai sai Danmallam shima don yakamata ya sani ne tunda shine Uban cikin..Mallam kamin wannan alfarman cikin matanka ba wacce Zata sani ko Sa"idu kada yasani mallam Don Allah..!
Mallam yayi shuru kafin yace"Duk naji Toh ammh meyasa kika ce haka..?
Miye Dalilinki..?
Hajiya tace"Zaka ji Dalilina ammh ba yanzu ba sai nan gaba Dalilin nawa zai bayyana kansa..
Mallam yayi shuru kafin yace"To sai yaushe Sa"idu zai sani..?
Balaraba fa..?bai kamata ta sani ba makafin uwa take ga mamana fa..?
Hajiya taji har Balaraban yanzu bata da yarda da ita ba yasa ta girgiza kai kafin tace"ya kamata ta sani..ammh a wannan gabar itama bai kamata ba mallam..Nidai kayi hakuri akwai Lokacin da zan fada maka Dalilaina nayin haka sannan zasu sani in lokacin su sani yayi..!
Mallan ya tari numfashinta da Fadin"Yaushe kenan..?
Hajiya ta kallesa Cikin ido kafin tace"Kafin abunda ke Cikinta ya Fito Duniya..!
Ya kalleta yana mamakinta meyasa Hajiya tace haka sai kuma yaga bazai iya Ture alfarmanta ba.
Yasa ya jinjinamata kai kafin yace"Shikenan..!
Hajiya tace"Ba shikenan ba..Alkawarin zakamim ba wanda zai ji sannan kuma ina so na Fada maka zan Dauke Amina Daga gidan nan zan kaita inda zata yi Renon Cikinta har Zuwa Lokacin da zai bayyana kansa shima bayan ni da kai da Danmallam ba wanda zai san inda Amina take..!
Mallam ya fara Tunanin da wani abu Cikin mamaki yace"Ina zaki kaita..!?
Kai Tsaye tace"Gidan Aisha Abuja..!
Mallam yace"Aishan ce zata iya kula da mai Ciki..?
Nawa take ko itama ta Haihun ne bansani ba..?
Hajiya tace"Ko Daya bansani ba ko tana da Ciki ammh ina da Dalilina na kaita Chan din ni na Haifi Aishan nasan Halinta Zata kula da Amina Sosai kuma ba ita kadai bace agidan yanzu akwai kakar megidanta da tadawo gidan da zama kaga kenan zata Tayata kula da Amina da abunda ke Cikinta..!
Mallam ya kalli Hajiya ya kara kallonta kafin yace"Duk me ya kawo wannan..!?
Sannan in tatafi karatunta fa kin san fa sun kusa fara jarabawar da kika matsa na Biya mata ita da yan"uwanta sannan mijinta ya kusa zuwa ya Dauketa kamar yadda kika basa Umarni..!
Hajiya tace"yanzu ba lokacin karatu bane..Ta Haifi abunda ke Cikinta Lafiya sai komai ya Biyo baya mallam..!
Zai yi mgana ta Riko hannayensa tana Fadin"Don Allah mallam.!
Idonta sai ya ciko da kwallah gani take in tayi wani Sakaci Amina Zata Shiga wani Hali..ganin haka yasa ya Jinjina ma Hajiya kai kafin yace"Naji na amince mijinta fa..?
Kinsan bazaki Dauke matarsa bai sani ba ko..?
Sannan ita Aishar ai ba ita keda kanta ba An nemi izinin mijin nata..?
Hajiya tace"Danmallam bai da matsala na Fadamai ya amince Megidan Aisha kuma Usman kai ne zaka kirasa kai mai mgana nasan ma bazai ce konai ba ni kuma zan kira Aishar na Fadamata komai zuwa gobe nake so mu tafi..Kada ka manta mallam iya ni dakai da Danmallam ko Sa"idu kar ya sani ballatana Sauran yaran don Allah..!
Mallam bai da tacewa illah gyada kai kafin yace"Shikenan nayi alkawari..Zan kira Usman din muyi mgana..Allah yasa hakan shi yafi Zama alheri bazan ja da mganarki ba Domin baki taba aikata wani abu Sabanin Tarbiyan gidana ba na baki Dama ki kula da Mamana da abunda ke Cikinta Allah ya raba su lafiya..!
Cikin jin Dadi Hajiya ta amsa da Ameen Ameen sannan ta mike tana Fadin"Nagode mallam..Ka taya mamarka da addu'ar Allah ya Tsareta ita da abunda ke Cikinta ya rabata da Sharrin mugum mutum da aljan..!
Wannan karon bai boye mamakinsa ba sai da yace"Hajiya kodai wani abu ya Faru ne..?
Da Sauri ta girgizamai kai kafin tace"Ko Daya..Kasan duniyar ne ta lalace..Ba kowa ke zaune dakai don Allah ba..Sannan ba kowa ke son ganin cigabanka ba. !
Daga haka ta Bude Dakin ta fice ya Bita da kalli yana kara nazarinta aransa yana Tunanin me ya faru..!?
Hajiya bata Cika irin wannan mganar ba.?
Tabbas wani abu ya faru sai dai bazai matsa mata sai yaji ba yasan ta bata aikata wani abu bata da Dalili mai karfi shiyaasa zai bata goyon baya insha Allahi zai kuma taya Amina da addu"a kamar yadda tace Duk da bai taba gazawa da mata addu"an shirya da Daidaituwa Tsakaninta da Umaru ba..!





*Bakina yayi kadan wajen nuna godiyata ga masoyana..Nagode kwarai da gaske ina ganin Addu"o'in ku gareni Yadda kukemin Fatan Alheri nima ina bin ku dashi Godiya ta musamman ga Masoyan da suka siya wannan Littafin Allah ya rubanya muku da Alheri Allahu ya bar zumunci Ameen..*





*Janafty*
[10/19, 6:19 PM] +234 810 431 4972: *TFZB2017*

*Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yad'ashi..Pay N500 via jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan Lambar 09069067488*

_A WEEK LATER._

Bayan Sati Daya da Tafiyar Amina Abuja acikin Satin Dayan data yi a garin Abuja karo na farko tun da take ta fita garin gumel taje wani waje da sunan Zama na wani dan lokaci.
Alokacin da Hajiya ta mata mganar zuwanta Abuja ta shiga Damuwa,Da kuma Tunanin zatayi zaman kadaici ba hanne ba Hamida sannan inda bata Saba ba sai gashi kuma Cikin kwanaki da zuwanta Abuja ta Saki jikinta sosai da garin Musamman ma da Yakaka data kasance mai kirki da Dattako Sannan Aisha ma na iya Bakin kokarinta sosai akan Amina abaya Amina tasan ya Aisha bata da Hayaniya sosai da yawan mgana ammh yanzu haka zata zauna tayi ta jan ta da hira suna tuna irin Rashin ji da su kayi ita dasu hanne Tana bama Yakaka Labari itama Dayake sunan Amina gareta ake ce mata Yakaka tace ai masu suna Amina haka suke yarintarsu an sha kwallo sannan haka suke basu Daukan raini su taru da Amina su yita yabon masu sunansu Nan da nan Amina ta Saki jikinta Dakin Yakaka ma take kwana yanzu Saboda bata son kwana ita kadai yakaka tace ta dawo Dakinta su Zauna tare itama ta samu abokin zama.
Haka kuwa akayi sai da ya Aisha taga Amina ta kwashe kayanta takai Dakin Yakaka suna Zamansu lafiya batayi mgana ba saboda ko bakomai yakaka Zata kula da ita sannan ga Ciki ajikinta tana Bukatar wani a kusa da ita.
Usman mijinta ya Dawo ya ga Amina har sun gaisa saboda yasanta abakin ya Aisha lokacin tana amarya in kewar gida ya isheta sai ta Zauna ta rika basa labarin kannenta Amina da Hamida da Hanne sannan yasan mganar auranta da ya Danmallam din Tunda sukan yi mgana da shi Lokaci bayan Lokaci haka Itama Aminar tasan Usman sun taba ganinsa Sanda yazo wajen ya Aisha kafin auran sannan sun gansa ranar Daurin auran shiyasa dukkansu basu Tarbi juna abaki ba..
Achan gumel kuwa Hanne da Hamida sun gaji da tambayar Hajiya ina takai Amina..! Sun kyaleta saboda bata gayamusu sai dai tace Amina na nan Dawowa insha Allahu sun Damu Matuka,Ammh kuma Dole suka hakura sai dai kana ganinsu kasan sun rage walwala Sannan a makaranta ko an tambayi Amina cewa suke yi tayi tafiya,Hamida har mamanmu tama mgana ko tasan inda Hajiya takai Amina..?
Mamanmu tace bata sani ba tadai san Hajiya tace ma Aba bata wuce Tsakanin gidajen yaran gidan nan ko na gidan mallam ba,ita duk a Tsammaninta bata wuce Tsakanin gidan Jawahir ko Jalela ba tafi ma Tunanin Jalela saboda tayi mgana da yan Gusai kuma bataji Labarin Zuwan Amina ko Hajiya abakinsu ba ita bama wannan ne agabanta ba shiyasa bata Damu da tasan Inda take ba,Saboda kada azargeta da rashin kula da Jawad yasa ta jawosa ajiki ganin yana neman yaki Zama wajenta ya koma wajen Hajiya Hamida kuma ganin ba Amina sai ta Dawo kwana agidansu tana kula da kanta da jawaad tunda Daman Amina ta bar mata Amanarsa to shima ganinta yasa bai Damu ba Duk da shima ya gaji da tambayar ina ya Amina..?
Sai dai Hamida tace mai tayi tafiya ammh ta kusa Dawowa..
Sun kusa fara jarabawar Fita nan da Sati uku hanne da Hamida suna Zaton Amina Zata dawo kafin su fara jarabawa Tunda Hajiya bata sanar dasu komai ba.
Sakina ta koma

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login