Showing 30001 words to 33000 words out of 40828 words
Mahmud tayi ya sakar mata murmushi
IKLAS na shigowa bada dadewa ba yaron Mahmud ya shigo da zaliha
Ai abida na ganin zaliha hakalin ta ya tashi
Tashi IKLAS tayi zatayi magana kwai sai taji muryar Abida
Tace"na ansa laifi na na kashe nuratu da zainab"
Kallonta alkali yayi ya tambaye ta sau uku tace"eh ta aikaita laifinta"
Nan dai alkali yayi gyran murya yace"Abida nasir ta amsa lai fin kissa wato kashe nuratu da zainab bisa wanan dalili wanan kotu ma adalci ta Yankewa Abida nasir hukunci kisa ta hanyar rataya"
Kukar nadama ta fashe dashi dai-dai nan RAYHAN da abdul suka shigo shigo
Nan police suka tafi da Abida
Da gudu RAYHAN ya zo ya rungumeta itama rungume shi tayi domin dama anga zamar kotu
Abokin Mahmud ne ya karaso dashi kusa dasu
Kallonsu IKLAS tayi tace"ina minal?"
Abdul yace wata minal?"
Shima RAYHAN kallonta yayi nan dai kwashe komai ta sanar da su cikin tashin hankali Abdul yace"ina ne wajen?"
Mahmud yace"bari a sanar da yan sanda"
Kafin suyi.magana Abdul ya tafi ya barsu da gudu RAYHAN ya bishi itama IKLAS da Islam binsu sukayi Wanda da k'yar take tafiya
Mahmud shi kad'ai aka barshi dan ya aiki yaronshi wake
Har da zaliha ta fara tafiya sai ta juyo ta kalleshi dawowa tayi ta taimaka me suka fito
'Bangaren Mugu ko kiranshi aka yi aka sanar dashi an yanke wa Abida hukuncin kisa ta hanya rataya
Yace"what?ta ya haka ta faru?"
Police d'in yace"ai barrister IKLAS ta zo kotu kuma abida da kanta ta ansa laifinta"
Yace"ban gane ta zo kotu"
Tashi yayi yaje d'akin da suka boye IKLAS dan tun safe bai ba leka ba"
Yana shiga yaga minal zaune,karasawa yayi ya d'aga mata fuska ganin fuskar minal yace"nasan wanan aikin babsy ne"
Fita yayi ya kalli babsy cikin rashin gaskiya babsy yace"oga ya dai?"
Ba tare da yayi magana ba ya halbe shi a kafa yace" ni zaka yaudara gashi sanadiyar ka an kashe mun masoyiya"
Kallonshi tayi yace"ku kuna gidan nan dasu a ciki"
Suka ce"toh oga"
Bude gas suka yi suna fita suka sa ashana,nan take gidan ya fara konewa
Abdul ne yana tuki kamar zai tashi sama dan shi bai jira yan sanda ba
Su IKLAS ne a police station RAYHAN yace"he gida ki jira mu kinga baki da lafiya ko"
Tace"ni bazan iya ba muje tare sanadiyata minal ke cikin wanan halin"
Ba dan ya so ba yace"toh muje"mota d'aya suka shiga da Islam,yan sanda kuma nabin su a baya"
Suna isa suka tarar da Abdul zaune a kasa idanun shi sun yi jajur,ga gidan ya kone kurumus
IKLAS ta fashe da kuka tace"wallahi nan ne gidan Allah yasa basu kasheta ba"
A fusace Abdul yace"ba abinda ya sameta"
Yan sands suka ce"......
Maman
Noorul
Hudahββ
Luv u my fans
Pls share
[3/18, 00:43] Hubeey Kn 2: ππππ
IKLAS
ππππ
By maman noorul
Hudah
πGORGEOUS WRITERS FORUMπ
πG.W.F.π
Home of gorgeous,interllingent,and expert writers,we are the best among the rest.
π
Ώ7β£3β£&7β£4β£
Bismillahir Rahmani Rahim
Yanda suka CE"bari mu kira fire service a kashe wutan"ba tare da b'ata lokaci ba sai ga fire service sun iso
Bayan sun kashe wuta,suka shiga cikin gidan da kone kurmus
Shigarsu da minti ashiri sai gashi sun fito da gawa
IKLAS na ganin gawa saki wani mugun kara dan duk a zaton ta minal ne
Tace"shikenan sun kashe minal"
A zabure Abdul ya tashi yace"ke kiwa mutane shiru minal bata mutu ba"
Kafin fire service suyi magana IKLAS ta dafe ciki tana ihu,jinine ya fara bin kafarta
Cikin tashin hankali RAYHAN ya saki Abdaul dan dama ya rike tun kan fire service sun zo,dan cewa yayi shiga zaiyi shima wutan ya kashe
Zuwa yayi ya rike ta yace"wiffy menene?"
Tace"cikina,mutuwa zanyi ka taimake ni"da Sauri ya sakata mota ya zaga ya zauna,ko ta kan Islam bai bi ba dake faman cewa"yaya jira ni"
Direct asibiti ya kaita,da sauri Dr suka fara aikin su sai dai cikin ya riga ya zube
Kallon Abdul police sukayi d'aya daga cikin su yace" mun duba ko ina bamu gan gawarta ba sai na wanan"
Islam ta fashe da kuka tace"kila ta kone kena kurumu........"maganan ta makale ne sakamakon mari da Abdul yayi mata
Yace"wallahi in kika kuskura kika kara cewa minal ta mutu sai na hallaka ki"
Cikin b'acin rai ya shiga mota ya ja kamar zai tashi sama yana tuki yana magana yana cewa"minal meyasa kika yi mun haka?miyasa baki nimi shawarata ba?please ki dawo ko masifa ne kiyi mun ki taimaki rayuwata bazan iya rayuwa babu ke ba"
Parking yayi a gefen titi ya samu gefen titi ya zauna gindi wani bishiya'
RAYHAN ne gaban Dr yace"Dr ya ake ciki ne yanzu?"
Dr yace"jikin da sauki sai dai tayi b'ari cikin ya zube sakamako wani abu da ta ji ko gani ya firgita ta kuma tana zama da yunwa kamar kuma bata samun barcin kirki"
RAYHAN a ranshi yace"dama tana da ciki ne?no wonder"a fili kuma yace"eh dr hakane"
Cikin damuwa yace"Dr zan iya ganin ta?"
Yace"eh amma kar a tashe ta"
Yana fitowa ya kira ummi da mamy ya fad'a musu halin da ake ciki
Shiga d'akin yayi ya ganta kwance kamar mai barci hawaye nabin kunne ta
Zuwa yayi ya kwanta kusa da ita ya shafa cikin ta
Tana jin shi kusa da ita ga kuma hanun shi a cikin ta ai sai ta saki kuka mai cin rai
Juyo da ita yayi suna fuskarta juna sai dai idon ta rufe
Yace"wiffy bude idon ki kalle ni" babu musu ta bude
Yace"meyasa kike kuka?kina so nima nayi ne?" Girgiza kanta yayi alamun a'a
Yace"kema ki san bani da wuyan kuka,iam too emotional balle nagan ki kina kuka zuciyata zafi take yi"
Kuka ta fashe da shi yace"ya salam,toh menene"
Cikin kuka tace"baby mun ya tafi ya barmu"
Rungumeta yayi yace"karki damu wiffy Allah zai bamu wani,Allah bai nufi zaizo duniya ba,da kin samu wani zan baki wani kema kinsan bana wasa"ai batasan sanda dariya ya subuce mata ba
Kashe mata ido yayi yace"da kin farfado zan fara aiki"
Kallonshi tayi ta kara fashewa da kuka tace"ina minal ta mutu ko"
Yace"a'aba a tabbatar ba dan babu alamun gawanta a nan,yanzu ma zan je in same abdul "
Suna cikin magana ummi ta turo kofa da sauri ya mike ganin mamy tare da ita
Bayan sun gaisa yayi wa mamy ya jiki ummi tace"yariyar nan ta cuce mu,yanzu ya magana minal"
Yace"yanzu wurin Abdul zan je kuma yan sanda sunyi nasara kama mugu da yaranshi"
Yana fita ya kira Abdul yace"ina kake"jin shiru ya sake cewa hello"karshe ma Abdul ya sinke kiran
Sultan ne zaune a asibitin bye-bye pass yace"bari in kira Abdul"
Kiran Abdul yayi yace"hello!hello kana jina"
Abdul yace"uhrmmm"
Sultan yace"Abdul ka fad'awa kawayen amare ba zan samu zuwa yau ba ina asibiti da nake zuwa naga wata gefen titi a sume shine na taimaka mata yanzu ina asibiti amma da ta farfado zan shigo"
Jin shiru yasa yace"hello kana jina?"
Yace"eh"
Sultan yace"tana ji murya ka haka?"
Abdul yace"ba a ga minal ba"
Sultan yace"ban gane ba"nan ya kwashe komai ya fad'a mashi
Sultan yace"toh ko ta mutu ne"
Abdul yace"no ina ji a jiki na minal na raye"
Kallon minal dake kwance a gadon asibiti sultan yayi a ransh yace"ko dai ita ne?bari ta farfado in tambayeta"
Abu kamar wasa anyi kwana uku ba gan minal,cikin kwana uku nan Abdul ya rame yayi baki,umma minal ko kullum cikin kuka
IKLAS ko tashiga tashin hankali sosai,Mahmud yace"laifi nane dana bari ta je dan yanzu sun bala'in shakuwa da zaliha
Yau likita ya sallami IKLAS a asibiti suka dawo gida
'Bangaren sultan ko misallin karfe 4:pm tana zaune a kujera minal ta farka
Tana farkawa tace.....
Maman
Noorul
Hudahββ
Luv u my fans
Pls share
[3/18, 00:43] Hubeey Kn 2: ππππ
IKLAS
ππππ
By maman noorul
Hudah
πGORGEOUS WRITERS FORUMπ
πG.W.Fπ
Home of gorgeous,interllingent,and expert writers,we are the best among the rest.
π
Ώ7β£5β£&7β£6β£
Bismillahi Rahmanir Rahim
Minal na farfadowa ta fara kallon wuri,sultan ma kallonta yake
Tace"ina nike?"
Yace"a gefen titi na gan ki a sume,na kawo ki asibiti yau kwanan ki uku"
Zaro ido tayi a hankali ta fara tuna komai da ya faru
Yace"bari in kira likita"
Likita na zuwa ya duba ta allura yayi mata ya fita
Kallonta sultan yayi yace"ki kira gida a san halin da kike ciki"
Tace"ba waya hanun na"
Yace"kin san noba wani a kanki?"
Tace"eh"waya ya ciro yace"kira inji"
Nan ta fara kiran noban Abdul,yana dialling ya ga sunan Abdul ya fito kallonta yayi
Yace"minal ko?"
Cikin mamaki tace"eh ya akayi kasan suna na ne?"
Yace"ai ni cousin brother Abdul ne bikin Ku ma zani na gan ki,nine Wanda kawaye ke jira"
Tace"sultan ko"
Cigaba yayi da kiran Abdul amma yaki d'agawa
Abdul da ke kwance ba lafiya ya duba wayar yana ganin sunan sultan yace"wanan sarkin surutu,zai dame ni"
Sultan yace"bai d'aga ba"
Tace"toh kira wanan,kiran noba ummata tayi sai dai shima har ya katse bata d'auka ba"
Yace"shima ba a d'aga ba"
Na IKLAS ta bashi amma noban be je ba"
Tace"please kira wanan na karshen inba sai in hakura"
Islam dake zaune kusa da IKLAS tun dawowan su daga hospital IKLAS ke kuka tana kiran sunan minal Islam itama zaliha kuka takeyi tana cewa"laifi nane"
Islam zatayi magana wayarta yayi kara tana d'agawa sultan yayi ajiyar zuciya
Tace"hello!"jire wayar yayi a kunne ya kalla ya kuma maidaw
Yace"hello"itako Islam sanda ta dafe kirjin ta dan wani bugu zuciyarta ya farayi da Sauri
Mikawa minal wayar yayi dan haka kawai yaji baya da kuzarin magana da ita
Minal tace"hello"Islam na jin muryarta ta mike tsaye tace"minal dama kina raye?"
IKLAS na jin an kira sunan minal ta kwace wayar batayi magana ba ta saki kuka
Minal tace"meya same ki sunyi miki wani abune"
IKLAS tace"please karki kara tafiya ki barni nayi kewar ki,Abdul kamar zaiyi hauka yanzu ma fushi yake da kowa"
Minal ma hawayen takeyi tace"ku zo ku d'auke ni ina asibiti"
Da sauri IKLAS ta saka hijabi Islam tace"ina zaki ke da baki da lafiya"
Kafin tayi magana RAYHAN ya sauko yace"meke faruwa ne?kuma ina zaki?"
Tace"minal ta kira wai tana asibiti"
Yace"alhamdullilah bari inki kira Abdul mu had'u a asibiti"
Sanda ya kira Abdul sau biyu bai d'auka ba a a na ukun ya d'aga
Yace"kai baban soyyaya ai sai ka tashi muje mu d'auko minal a asibiti daga yau zaman takaba ya kare"
Da sauri Abdul ya mike yace"da gaske an ganta?"
Yace"eh yanzu ta kira Islam wai sun kira ka baka d'aga ba"wani uban yayi,Wanda RAYHAN ya cire wayar a kunna yace"kar a fasa mun kunne"
Kiran ummi Abdul yayi ya gaya mata an gan minal
Cikin murna tace"toh sai kun dawo"kicin ta shiga ta fara had'a abincin mai lafiya dan ba karya tana ji da minal kasancewar ita kad'ai ta Haifa
Lokaci d'aya suka isa asibiti RAYHAN yace"har ka iso"
Abdul yace"ba dole ba"
Suna shiga IKLAS ta ruga da gudu ta rungume minal
Abun mamaki ina sanmani ganin Abdul yana farin ciki sai na gan ya tamke fuska kamar Wanda bai tab'a dariya ba"
RAYHAN ko gaisawa yayi da sultan
Islam ko ta rakube a gefe d ya dan wani irin kallo da sultan keyi mata
Abdul na karasowa kusa da minal ya..........
Maman
Noorul
Hudahββ
Luv u my fans
Pls share
[3/18, 00:43] Hubeey Kn 2: ππππ
IKLAS
ππππ
By maman noorul
Hudah
πGORGEOUS WRITERS FORUMπ
πG.W.F.π
Home of gorgeous,interllingent,and expert writer,we are the best among the rest.
π
Ώ7β£7β£&7β£8β£
Bismillahir Ramanir Rahim
Yana karasowa ya sinka mata lafiyyayen mari,rike wurin tayi tana hawaye
Yace"me kike tunani?bakiyi tunanin halin da zan shiga ba ko umma ki,ki san irin tashin hankalin dana shiga"
Cikin kuka da zafin marin da yayi mata tace"yi hakuri naga babu lokaci ne kuma ina tausayin IKLAS dan na lura a lokacin tana da ciki shiyasa"
Yace"ni na hanaki taimako ta ne?amma miyasa baki sanar dani ba?da ansan abinyi,da a ce sunyi miki wani abu fa"
RAYHAN yace"gaskiya ne da kin fad'a mana dan da wani abu ya same ki wallahi bazan iya yafewa kai na ba"
Haranrar shi tayi tace"wa zan fad'awa kai,kai da ka zama hoto kullum cikin kuka kamar mace sai wani cewa kake matata ki dawo gareni na tuba shine kake cewa in fad'a ma"
Dariya kowa yayi shima Abdul bai san lokacin da dariya ya sub'uce me ba
RAYHAN ya susa keya kallonshi IKLAS tayi tace"gaskiya minal baki da mutunci yanzu mijina kike yiwa siya"
Minal tace"ai gaskiya na fad'a"
RAYHAN yace"oho dai ai ki sha mari"
Kallon Abdul tayi ta harare shi,zama yayi kusa da ita yace"ba inda ke miki ciwo ko?"share shi tayi
IKLAS tace"ya akayi kika fita a gidan?"
Tace"bayan mugu ya bar d'akin da suka ajiye ni dan a lokacin ya gane bake bane yana fita na kwance kaina dan dama babsy bai d'aure ni da kyau ba ina gamawa na fara niman hanyar guduwa wajen window naje kawai sai naji kara bindiga da sauri na fara girgiza karafuna jikin window,gajiya nayi na zauna ina zaune na hango wani karfe da sauri na buga shi karfen yayi gefe na hau window na yi tsalle fad'owa nayi kai na ya bugi dutse, ina fita a gidan na gan su mugu sun shiga mota ga warin gas ya cike ko ina b'oyewa nayi suna tafiya na fara gudu sai dai banyi nisa ba na gan gidan ya buga kamar tashin bomb,gudu na dingayi a daji da k'yar na iso titi tun a lokacin ban kara sanin kai na ba"
Abdul yace"sorry dear"
IKLAS ko kara rungumeta tayi tana hawaye
Minal tace"ya baby na?"
IKLAS tace"ai baby sai dai wani"
Minal tace"ban gane ba"
Tace"cikin ya b'ere ai lokacin da na gan gidan na konewa"
Tace"Allah sarki ina raye ai"
Tace"eh ai Abdul kad'ai ya yarda baki mutu ba dan har haukacewa tayi"
Kallonshi minal tayi ta hararre shi susa kai yayi yace"ai ina taji a jikina kina raye dan ko wanan hararran ne ayi tamun kafin in kashe bakin nan mai siwa siya"
RAYHAN yace"karki damu kwana nan zamu samu wani baby"
Sultan ne yayi gyran murya yace"sai soye kuke toh nima ai nayi mata"
Abdul ya zaro ido yace" waye
Yace"gata nan"ya nuna Islam da hanun"sai a sanan RAYHAN ya tuna da ita a wurin yace" ke bar nan"fita tayi sultan yace"gaskiya bana son haka"
Kallon Abdul minal tayi tace"toh ai sai kaje wajen likita ka anso mana sallama ko"
Yace"toh umma"
Sultan ya kalleshi a ranshi yace"lallai ta raina shi, babu mace da zan sakarws fuska har ta raina ni haka"
Abdul na dawowa yace"tashi muje an sallame ki"
Suna fitowa suka tarar da Islam a mota tana jiran su
Kallonta sultan yayi ya basar"
Suna isa gidan umma minal umma ta rungume minal,minal na kokarin yi mata bayani umma tace"bana son inji komai dan nasan IKLAS zata iya yi miki abin da ya fi haka"
Abinci ta basu white rice dan minal na mutuwan sonshi
Minal tace"umma ina Abba na"
Umma tace"ai yana nan tafe ina fad'a me yace gashinan zuwa ya ga princess d'inshi ya je station ne ko sun samu labarin ki "
Suna cikin cin abinci sai ga zaliha ta shigo da sallama
IKLAS tace"zauna mu ci abinci"
Tace "ni da Mahmud ne yana waje"
Minal tace" toh ta yaya ya so"
Zaliha tace"driver
Shi ya kawo mu"
IKLAS tace"ke barta kawai kullum fa Mahmud na gidan su Islam ko gidan mu ta zo sai yace "zasu zo su d'auke ta kamar ba gurgu ba soyyaya ake sha"
Minal tace"kin ma tuna min akwai wani likita mai zuwa asibitin mu kowani karshen wata shi specialist ne a irin matsalan Mahmud amma a Egypt yake,muje inyi me magana"
Zaliha tace " Allah yasa ya yarda dan da kayi me irin wanan magana sai yace"ba zai je ba wanan lalurar ita ce kaddarar shi"
Minal tace"muje dai"
Suna fita suka gan shi zaune mota
Bayan sun gaisa da minal tace"Mahmud wata shawara na kawo please kar ka ce a'a"
Yace"ina ji"
Tace"wani likita ne nayiwa maganan condition d'inka shine yace a kawo file d'ika"
Tun da Mahmud yaji likita ya canza fuska
Tace "please Mahmud kayi tunanin maganata you are still young please"
Yace"OK zanyi tunani"
Zaliha tace" baby please ka yarda"
Yace"na yarda amma sai bayan auren mu saboda mu tafi tare"
Tace"ba matsala ai"
Minal dai murmushi tayi ta shige ciki"
IKLAS na zaune a palourn umma tana ganin minal tashigo tace"ya akayi ne ya yarda ne?"
Tace"ya yarda amma said bayan auren su"
IKLAS zatayi magana wayar ta yayi kara tace......
Maman
Noorul
Hudahββ
Luv u my fans
Pls share
[3/18, 00:43] Hubeey Kn 2: ππππ
IKLAS
ππππ
By maman noorul
Hudah
πGORGEOUS WRITERS FORUMπ
πG.W.F.π
Home of gorgeous,interllingent,and expert writers,we are the best among the rest.
π
Ώ8β£1β£&8β£2β£
Bismillahir Ramanir Rahim
Yace"ai naji"
A ranta tace"ikon Allah"
Sanda ya gama ja mata aji yace"muje ko"
Tace"ok"
Palour ummi ta kaita shi suka gaisa
Bayan sun gaisa ummi ta shige ciki
Islam tace"muje guest palour ko garden?"
Da k'yar ya bude baki yace"garden"
Tace"ok "
Suna fita hanyan garden suka nan suka tarar da zaliha da Mahmud gaisawa tayi da mahmud,mahmud ya mika mai hanun suka gaisa
Mahmud yace"nice choice"dariya tayi shiko sultan ya had'e rai a ranshi yace"meyasa take dariya dashi?"
Zama sukayi nisa dasu tace"bari inkawo maka drinks tashi tayi bayan minti biyar ta dawo da drinks da snack a hanya zaliha tace"hmmm wanan gayen akwai miskilanci"
Murmushi tayi,tana zuwa ta siyaye me a cup
Tace"gashi"
Ya karba zama tayi
Babu wanda yayi magana shiko danna wayarshi yake ta faman yi
Bayan awa d'aya da rabe tace"kana jina?"
Shareta yayi a ranshi yace"wato bazata ce tana sona ba kenan"
Can anjima tace"ina tafi ne in ba magana"
A fusace ya juyo yace"nina ce ki tafi ne bana son raini"shiru tayi
Sakawa wayar yayi a aljihu yace"miye sunan ki?"
Tace"Islam"wow yace a zuciyar shi
Yace"sunana sultan,zan turo magabata na a saida maganan auren mu"a ranshi addu'a yake yi Allah yasa ta amince da shi
Shiru tayi na wasu mintina
Cikin tashin hankali shirun datayi ya dak'e
Yace"no zaki iya fad'i ra ayi ki in bamiki ba sai in hakura"
Tace"na amince"
Yace"toh kiyi ta saka hijabi kuma bana so kiyi ta dariya da ko wani namiji"
Tace"toh"
9:50 dai dai ya bar gidan
'Bangaren RAYHAN fushi yake yi da IKLAS ko tayi me magana baya amsawa
Tace"toh miye na