Showing 15001 words to 18000 words out of 35734 words
wurin Juni ke banda ci babu abinda kika iya. Tilly ta hadiye naman da ke bakinta da kyar kin dai sanni tun farkon haduwarmu ina da son abinci musamman idan akwai nama. Rosie ta bata fuska to naji mayya amshi ki karanta wannan. Dafe kirji Tilly tayi me zan gani haka? Aure zaiyi, ai wallahi uban kuturu yayi kadan. Ni fa banda kudinsa shima kansa ina so. Wata takardar Rosie ta mika mata tace to wanan kuma fa. Ci...ci...ci me? Mun shiga uku Rosie ya akayi kika bari ciki ya shige. Rosie ta dakatar da ita tsaya kiji ai cikin nan shine license dinki for now. Ke dai ki saurare ni da kyau kinsan tunda muke bamu taba yin babban kamu irin haka ba dole mu rike wuta.
****************
Nafisa da Hamida sai shirye shirye suke dan uwansu zaiyi aure. Kashe kudi suke kamar babu talauci a nigeria har sai da mommy tayi magana. An hada lefe na gani na fada a cikin gidan daga baya Senator ya yi musu gine mai kyau babu abinda bai saka ba yace a nan zasu zauna har sai yaga kamun ludayin zaman nasu don bai gama yarda da dan nasa ba.
A kano ma su maman Hafsi suna nasu shirin duk da sun san Senator Rufai da iyalinsa ba tsaransu bane amma dai suna gudun gori ace sikau suka kai yarsu.
Ranar karbar lefe tazo dai dai da sati daya kafin biki Hafsi bata sake ganin Junaid ba shima bai neme ta ba don yasan ta kusa shiga hannunsa wannan yatsine yatsinen da take masa dole ta ajiye a gefe.
Batul Mamman💖
TUN KAFIN AURE💐 21
Yan uwa da abokan arziki sun cika gidan. Yan ganin kwal uwar daka ma suna nan zaune suga irin abinda zaa kawo wa Hafsi.
Akwatuna ne ake ta shigowa dasu gidan har goma sha takwas. Hajiyan Dangi ita ce tayi jagora ta nuna musu kayan. Akwati set biyu guda sha biyu na amarya ne komai na ciki me tsada ne harda set din gwal uku. Sai daya na baffa, na Mama, na 'yan uwanta sai kuma wanda zaa bawa yan uwa da abokan arziki. Dukkansu shake suke da kaya. Ga kudin dinki dubu dari biyu. Wai a haka ma don kada su zake da yawa ne. Ranar bakunan mata sunyi magana har sun gaji kowa da abinda take fada. Mama dai dubu hamsin baffa ya bata na tukwici shima don su fita kunya ne. Wata yayarsa ta kira ta fadawa tare da dora nata dubu goma. Yayar da yake tana da dan rufin asiri ta kawo talatin itama Hadiza ta kawo goma suka cike dari. Hajiyan dangi mace mai kwarjini da kamala tace ko kwandala ba zasu karba ba yar da aka basu ma sun gode. Suna fita aka hau bude buden akwatuna ana kallon yadda ake wasa da kudi a kasar mu.
*******************
Hafsi tasha gyaran jiki sai sheki take ga lalle wanda mai lallen ma Hamida ce ta turo ta har gidansu. Ummati tace Allah Yasa kuyi zaman lafiya naga kamar basu da raina mutane. Haka akayi kamu a wani makeken filin senator wuri ya dauki mutane. Idan kaga Hafsi kamar wata yar tsana saboda mai kwalliyar ma tafiyayya ce. Tayi kyau har ta gaji. Su ummati ma da kannenta baa barsu a baya ba. Itama Batul Mamman sai wani shishshige musu take taga kudi.
Ranar dinner wasu kaya da mama ta kure basira ta dinka Hafsi ta saka. Ummati tana zuge mata zip din rigar Hamida ta shigo da wata riga da skirt na lace ne ko material gashi nan dai abin mai daukar ido golden brown. Tunda aka fara biki ta likewa su ummati sun zama kamar kawaye. Kayan hade suke da takalma da head and veil. Hafsi ta bata rai ni fa wanan zan saka mama ce ta dinka min. Hamida ta marairaice haba matar yaya anko yake son kuyi da kansa ya bayar aka dinka miki. Suka shiga ban baki ita da Ummati amma sam Hafsi taki yarda har zancen yakai kunnen mama. Nan tayi musu sulhu gobe idan zaa kaiki sai kisa nawan zan ga mai hanaki amma yau dai ki saka na angonki. Maman ummati tayi dariya to yar shagwabar Mama gobe dai zanzo da bokitin share hawaye.
Taro yayi taro wuri ya cika da mutanen da suka amsa sunansu a naija. Yan mata anyi dinkunan rashin mutumci suna tafiya kamar sanduna babu lullubi. Matan aure sai hura hanci wai kar a raina su. A mota aka tsayar da hafsi har Junaid ya iso. Ko da ya fito da shaddarsa golden brown bata gane shi ba. Duk da yasa hula ta kula yayi aski, ya gyara fuska gaba daya ya canja. Shima kallonta kawai yake har ya karaso. A kunnenta ya rada mata ni kada ki cinye ne da kallo, it has been three weeks, kin kara kyau kema. Cak ta tsaya saboda yadda yayi kusa da ita. Ana fara musu alamar su shigo cikin hall din taji yana kokarin kama mata hannu. Kokarin fizgewa tayi shi kuwa ya matse hannun ga zobba a hannun har ta fara jin zafi. A hankali tace kaci bashi wallahi. Ya sassauta rikon suka shiga.
Dinner tayi kyau kuma ko liki baayi ba wannan kuma dokar Hajiyan dangi ce. Tilly da aminiyarta Rosie ma sun sami shiga a wurin daukar hoto Junaid ya gansu. Tsoro ne ya kamashi ya hau adduar kada tayi masa wani haukan a wurin don bai ma tsaya tunanin yadda suka sami katin shiga ba. Bayan sun dau hoto ta bashi wani envelop congrats Juni boy. Hafsi ta dan kalle ta Tilly tace amarya mun dai rigaki lasar zumar muna fata tayi miki dadi yadda....junaid ne ya katse ta get out...ba musu ta kama kawarta suka fita don idanunsa sunyi jazur tasan halinsa sarai. Babu wanda ya kula sai Hafsi kowa na shaanisa.
Dreba ne a gaba sai Ummati baya kuma Junaid da Hafsi don ya nace shi zai mayar da ita gida. Tayi kokarin daurewa ta kasa can kasa kasa tace wace wannan matar ne. Dama ransa ya gama baci gashi yana son dena shaye shaye babu ko taba a aljihunsa ya harareta idan zaki bude baki kiyi magana ki bude sai wani kasa kasa kike da murya kamar wata mumina. Ummati ta juyu don taji me yace...zare mata ido yayi ke bana son gulma me kike kallo. Ba shiri ta juyar da kanta. Tooooh wannan ne mijin da Hafsi zata zauna dashi. Hafsi dai shiru tayi tana kallon fuskarsa. Sai tayi da gaske akan wannan mutumin. Abu daya ta sani dai da yana cikin farin ciki kafin yaga wannan matar. Babu ko sallama suna zuwa gida suka fita yace da dreba yaja motar su tafi.
Daki ya shiga hankalinsa a tashe yana tarrabin abinda ke cikin takardar da Tilly ta bashi.
Juni boy
Nasan kana cikin farin cikin auren da zakayi gobe nima ina taya ka murna. Sai dai ina me tabbatar maka gobe zanzo Abuja a tawagar amarya. Ga wedding gift nan.
Luv Tilly
Bude daya takardar yayi gumi ya karyo masa ganin reult ne dake tabbatar da Tilly na da ciki har wata uku.
Batul Mamman💖
TUN KAFIN AURE💐 22
Ko kayan jikinsa bai canja ba ya fita zuwa hotel din da abokinsa Imran yayi masauki. A waje ya tsaya yayi masa waya. Sai a karo na uku ya dauka ya sanar dashi yana wurin parking ya fito.
Suna hada ido Imi yace yace ya mutumin you sounded worried fa. Me ya faru ne? Envelop din Junaid ya mika masa. Imi ya rinka dariya bayan ya karanta harda hawaye a idonsa. Can ya daki kafadar junaid...haba mutumina kada ka bada ni mana. Yanzu har akwai wata chick da zata ce kayi mata ciki ka yarda? Matan nan fa sun fi mu tsoron faruwar hakan tunda su ke da wahala. Wani abin kawai take so. Fuskar Junaid babu sauran kwanciyar hankali uhm uhm Imi aure fa zanyi kuma Allah Ya sani ina son yarinyar ina kuma son gyara rayuwata. Kaima Allah Ya baka tagari. Kayya yaro gigin soyayya ke dibanka bari romon ya kare zaka neme ni ne. Bayan ina kallo dazu amaryar taka ta murguda maka baki. Kansa ya shafa yana dariya da irin tsokanar fada ne yaga tana kulashi shiyasa yake mata haka a fili yace Kai kam kamar ana kada maka gangar shaidanu..ya ina cewa zan shiryu kana min mugun baki. To yi hakuri na Hafsa Imi ya fada yana dariya...yanzu dai ka manta da wannan yarinyar kada ma ka sata a rai. Idan ta sake nemanka kaci ubanta da kyau wallahi zata kyaleka. Kada ma ka fara bata kudi don sai tayi blackmailing dinka. Nan suka yi ta shawara sai wurin ukun dare Junaid ya koma gida.
******************
Bacci sam yaki zuwa idanun Hafsi sai tunani take kala kala. Wannan Junaid din dabiunsa na bata tsoro( wai ma don ya rage!) Gashi haka hankalinta bai kwanta da matar da ta bashi envelop ba. Maganar Tilly duk ta tsaya mata a rai wai sun rigata lasar zumar.....ehew abin kyankyami ma zancen ta fada a fili tana yamutsa fuska. Anya ba yan is...sai tayi shiru zargi babu kyau don haka mafitar ta daya shine ta mike ta dauro alwala ta tayar da sallah. Haka tayi ta nafila har asuba tana addua sannan ta yi bacci.
Sai wuraren goma na safe ta farka. Shima Hadiza ce ta tasheta da dundu...to kasa ana shirin fita daurin aure kina kwance kina bacci hankali kwance. Mutssika idanu tayi ta mike...ina ummati ta tafi Yaya? Debo miki ruwan zafi kiyi wanka. Kinsan dai baffa yace karfe biyu zaa bar kano so kiyi da jiki kafin a dawo daga daurin aure. Ta kalli agogon wayarta...Allah sarki nan da mintuna arbain da bakwai kin zama matar aure. Cikinta taji yace kulululu da gaske abin yazo. Kuka tasa wa Hadiza inama basuyi wadannan hotunan ba tun kafin aure da yanzu Saif ta aura. Ummati ta ajiye bokitin hannunta ki gode Allah baa daura dashi ba don yadda aka ce Junaid yayi bayan yaga hotonki da kila a gidan auren zai biyo ki ko ma ya kashe auren. Hadiza tace kyale ta ummati ai tasan wani baya auren matar da ba tasa ba.
Kayan da mama ta dinka da aka hanata sawa daren jiya su tasa ai kuwa tayi kyau sosai. Katon mayafi ta yafa ga kamshi ko ta ina.
Taro yayi taro don manyan mutane na kusa da nesa sunzo bikin dan manya. Junaid yasha cream shadda harda babbar riga da brown din takalmi da hula maroka suna ta sanaar su. Daga karshe dai Liman ya daura auren Junaid Rufai Bukar da Hafsa Aminu Garba.
Mijin Hadiza ne ya bugu ya sanar da ita an daura auren kan sadaki dubu dari gida ya cika da guda da hayaniya. Wata 'yar makarantarsu tace gaskiya Hafsa Aminu kinyi saa muma Allah Yasa mu a danshinku. Yan Amin kuwa suka amsa.
Ansha koke koke lokacin dasu Hajiyan dangi suka zo daukar amarya. Mama kasa daurewa tayi ta kulle kanta a daki. Baffa ma yana mata nasiha yana sharar kwalla. Bai taba tunanin zata yi auren nesa ba, aure ma irin na gidan Senator Rufai Bukar. Motoci har wajen layinsu Hafsi. Cikin motocin kuwa harda wadda Rosie da Tilly suka dauko haya suka bi ayarin kai amarya. Don karfin hali har mutane uku suka dauka aka dauki hanyar abuja.
Batul Mamman💖
TUN KAFIN AURE💐 24
Dakata Imi zanyi maganinta da kaina. Cheque ya bata na dubu dari biyu. Idan na sake ganinki duk abinda ya faru dake ki kuka da kanki. Suna jan mota ta fita ta tari taxi don yau Rosie bata biyo ta ba saboda laulayi daya fara damunta. Murna take sosai don wannan cheque din sabon makami ne a gareta.
Daki aka bawa Hafsi da kawarta sauran yan biki suna wani masaukin. Nafisa ta tafi da yayarta Hadiza gidanta ita kuwa Hamida ta nace tare zasu kwana da amarya kafin washegari a kaita side dinta.
******************
Wani sabon kukan Hafsi da Ummati suka dasa lokacin da aka fito rakasu bakin motocin da zasu mayar dasu kano. Yanzu haka zata zauna da mutanen da bata gama sanin halinsu ba. Ga uban gayyar wato Junaid ko doriyarsa bata sake ji ba tun a wurin dinner. Kamar yasan tunaninsa take sai gashi ya fito da kananan kaya a jikinsa. Yau ma yayi kyau tunda kayan ba oversize bane. Har kasa ya durkusa ya gaishe da gwaggwaninta dasu Maman Ummati. Hadiza ta rungumota tana ta bata baki akan ta dena kuka haka. Kyaleta Hadiza na gulma ne fa kuna tafiya zata sake. Harararsa tayi yace ai gara ki nuna musu halin da kike min. Hajiyan dangi ta kama hannun Hafsi rabu dasu zan miki maganinsu. Anisa ta Amira ma sunyi nasu kukan da alkawarin zuwa idan anyi hutu. Haka dai suka rabu abin tausayi ana janye Hafsi daga jikin Ummati.
Bayan duk sun tafi aka dawo falo. Hajiya da mommy suka yi musu nasihohi da fatan alkhairi. Nafisa da Hamida suna gefen amarya suna kula da masu dada share wurin kafin su kaita. Sai da aka gama fadan Junaid yace to Allah Ya saka da alkhairi amma yaushe zaku bani matata? Mommy ta cire takalminta ta jefa masa to tsohon mara kunya ai gara ka nuna hali. Ya dafe kai Hajiyan dangi tana duba masa...yauwa Hajiya duba ki gani ko kan ya fashe. Hafsi kuwa dariya tayi har sauti ya fito yace kinci bashi Hafsi Hafsi. Nan suka zauna ana ta raha sai kawai suka ji sallama.
Mata ne biyu sunsha hijab daya sai kuka take dayar tana bata hakuri. Dif Junaid yayi ya dena dariyar da yake saboda ya gane mai muryar. Zuciyarsa ke bugun uku uku yaji yawon bakinsa ya kafe. Itama Hafsi ta gane yarinyar ko baa fada ba tasan akwai matsala don ta kula da yadda ya kidime da ganinsu. A fusace ya kallesu ubanwa yace ku shigo har nan? Wai ma waye ya baku izinin shigowa.
Mommy da Hajiya cikin rashin fahimta suke kallonsa. Junaid kana hauka ne zaka ga baki kayi musu irin wannan tarbar? Rosie ta kiyi hakuri Talatu an gama cutarki shine zaa ci mutumcinki saboda baki da galihu. Mommy tace ku zauna muji abinda ya kawo ku. Tilly harda fyace majina ai yafi kowa sanin dalilin zuwanmu. Idanun Junaid kamar an bada masa yaji yayi kanta yana sirfa mata zagi.
Kana tabata zansa a kulleka mara mutumci kawai. Daga kai yayi suka hada ido da Senator Rufai. Alhaji wai me ke faruwa ne? Yace ku zauna muyi magana. Su Rosie aka wani rakube a kasan carfet ita da Tilly. A bakin gate na gansu suna fada da security yarinyar can ya nuna Tilly tana ta kuka. Ganin haka na tsaya aka kirasu tayi min bayani. Cheque ya dauko daga aljihunsa ta mikawa Mommy. Kingani kudin daya bata jiya wai taje a zubar mata da ciki. Kinga goshinta inda ya fashe lokacin da yake dukanta ta fadi. Kamar anyi masa wanka da ruwan zafi haka yake ji. Me tilly ke nema ne a tare dashi? Kokari yake su hada ido da Hafsi ita kuwa idonta na kasa tana kuka a hankali. Salati su Hajiya suka hau yi tace lalacewar taka har ta kai ka bada kudin yin kisa. Kuka ne ya kwace musu ita da Mommy. Junaid yana ta basu hakuri. Hafsi ta mike zata shige daki don taga zancen kamar ba nata bane. Dawo dawo ai gara kada a munafunce ki Hafsa. Senator ne ya kirata ta dawo ba musu. Ya maida kallonsa ga Junaid. Ka san yarinyar nan? Eh na santa amma wallahi ban dake ta ba. Rufa min baki shashasha. Kullum yadda zaka zubar min da mutumci yake nema. Ko tsoron mutuwa baka yi.
Ke ya daka ma Tilly tsawa ta dago a firgice garin yaya kika amince masa. Ta kara jan majina ta fara bada labari. Ni ina sayar da kati ne kusa da wani club da suke zuwa a gidan wannan yayartawa nake da zama shine ya biyoni wai yana sona. Rannan rannan sai kuka....Rosie tace kudin kati yace taje ta karba shine yayi mata fyade. To ganin cewa danka ne bamu daga zancen ba.
Wallahi Álhaji karya suke duk karuwai ne....bakinsa yaji Hajiya ta make. Rufa mana baki. Rosie ta cigaba to da mun hakura sai kuma ga ciki shine muka neme shi kawai jiya sai yazo har gida ya bata cheque ita kuma ta karba don taga bana nan.
Hafsi tayi saurin daga kai tace ba kece kika zo wurin dinner ba kuwa daren jiya? Junaid yace yauwa Alhaji wallahi kaga itama zata min sheda wurin dinner ta biyoni ba raping dinta nayi ba. Mommu tace Hafsa kada ma ki fara kare masa don bakisan waye Junaid ba. Duk abinda akace yayi zan yarda. Allah wadaran iskanci yau mahaifiyarsa ma taki yarda dashi.
Senato Rufai ya kalli dansa cikin bacin rai yace ka taba ganinta? Eh ya amsa masa. Muamala ta shiga tsakaninku? Shiru ya kasa magana. Ya daka masa tsawa kai kurma ne. Hawayen da yake boyewa ya sauko yace eh. Innalillihi wa inna ilaihi rajiun. Koda ba auren so suka yi ba amma ace mijinka yana neman mata akwai ciwo. Hafsi duk auren ya kara fice mata a kai. Senator yace to ke zaa kaiki asibiti a sake miki gwaji idan ya tabbata da gaske yayi wa Junaid wani mugun kallo zamu jira ta haihu a aura maka ita. Mikewa yayi a fusace su Hajiya suka bi bayansa.
Batul Mamman
TUN KAFIN AURE💐23
Tunda suka hau hanya basu tsaya ba sai a garin Abuja. Motar da Baffa ya hado da kayan da yayi wa 'yarsa ita ce ta karshe cikin jerin motocin.
Duk girman gidan ba duka motocin bane suka sami shiga ba saboda yawansu. Shima gidan cike yake da mutane gashi basu iso da wuri ba. Dakin mommy su Hamida suka kai Hafsi. Ita dai kanta a kasa taki dagowa ta kallesu. Mommy cike da murna tace nasan kun gaji ga magriba ta kawo kai a kai su masauki suyi wanka aci abinci sai su shirya akwai wata dinner din karfe takwas. Hafsi ta kankame hannun ummati sai Nafisa tace mommy wanan fa aminiyarta ce tare zasu zauna kafin anjima ta dan kanne ido ai sai kamarsu ta Junaid ta kara fitowa Hafsi tayi saurin dauke