Showing 291001 words to 294000 words out of 356830 words
Kansu Marigayi Alhaji Labaran kachia. Tundagafa wannan lokacin saina tsananta bincike da kwakwalwa dakuma tannin aiki, bisa taimakon sir Isa, mun baza yara cikinsu Tanderu batare da sunsaniba, kullum kuma cikin bin diddigin motsinsu suke. Kwatsam sai Tanderu ya rasu sanadin had'in mota, babu jimawa shima Alhaji Labaran khacia ALLAH yamasa rasuwa sanadin rashin lafiya. daga nan saina d'an dakatama gaba d'aya da wani bincike Na koma gefa Na zuba musu ido kawai.
Saida Na d'auki kusan shekaru biyu ban sake wani yunk'uriba sai kwatsam muka wayi gari mijin Yayata Haneefa yayi had'arin Mota, saidai kuma a ranar ne aka turomin massage daya nuna accident d'in nashi akwai saka hannu a ciki, dayake bai rasuba a lokacin sai a asibiti bayan awanni uku da kaisa, Alhaji shehu Darma abokinsa ne Na kut da k'ut sannan d'an uwansa, Dan haka yana tare damu a wajen, saina matsanta akan tambayarsa kozai fad'amin akan miya faru dashi kafin had'arin? Bai iya cemin komaiba sai murmushin k'arfin hali da yayi yana kallon Alhaji shehu har numfashinsa ya k'are, wannan kallo ya tsayamin a rai sosai, Dan nagaza mantawa dashi, abinda Yakuma k'arfafa min zargin Alhaji shehu shine Aunty Mimi Na fita daga takaba sai Yace yanason aurenta, nine Na hana, nama tattarata gaba d'aya itada y'ay'anta Na maidasu india, dukda dangin mahaifin yaran sunso d'aukarsu suma. Dama can lokaci-lokaci Alhaji shehu yakanbi mijin Aunty Mimi suje duba Abie, dan haka ko bayan rasuwarsa bai daina zuwaba, abinda na fara fahimta shine Samha d'iyar marigayi tana tsoron Alhaji shehu, amma shi yana tsananin nuna mata kulawa dayin kaffa-kaffa da ita a gaban mutane. Wannan ma yasa na kuma saka ido a kansa, abinda Na fara karo dashi shine Alhaji shehu yana tursasa Samha ta hanyar mata barazana akan ta d'akko masa wasu sirrikana”. Galadima ya murmusa cikin takaici yana gyara tsayuwa da goge fuskarsa da handkerchief. Yaciga da fad'in,
“Tunda Na fahimci hakan saina jata a jikina, nakuma dinga ajiye mata dukkan abinda yasaka ta d'akko, itako data gani saita tura masa saboda tsoron barazanar da yake mata. Suma sauran Na cigaba da bibiyarsu suda ayyukansu, so banida matsala da sauran mugayen halayyarsu, nidai kawai wadda ta had'amu nakeson Sani, Dan Na gano sun gana da mahaifina ana gobe abinda ya sameshi zai sameshi, kuma yafito daga d'akin tattaunawar ransa a 6ace. Batanci da akaimin a shekara d'aya data wuce cikin jaridar manuniya shine mafarin yalwatur haske a matsalolina, dukda Na fahimci ankai tsawon shekaru ana bibiyar dukkan al'amurana, kuma inhar Nazo k'asarnan kullum cikin bibiyata ake, domin rufe bakin mak'iyana Na auri wadda sukaso sakawa a matsalar dabatajiba bata ganiba, wadda a yanzu Alhmdllh itace uwar y'ay'ana, nasan hakan ya girgizasu a lokacin kwarai da gaske, adalilin zama da ita nama fahimci abinda ban fahimtaba da farko, Dan da Duk zargina ko da itane aka had'a kai wajen Neman 6atamin suna, amma sainaga dukba haka baneba, ya mai shari'a Alhaji Auwal Fharuk sai shine surikina mahaifin matata, kuma anyi yink'urin kasheshi watanni kusan 7 da suka shige, saidai ALLAH ya k'addara yanada sauran kwanaki a gaba, bisa dalilin yun k'urin kisansa ne kuma Na fara karo da alak'ar case d'in mahaifina dashi, hakan kuma tafaru bisa sanadin matata, data dinga zak'ulomin wasu masu alak'a da mahaifinta kuma Na jikinsu tanderu, irinsu Mamman k'afur, Alhaji Halluru, saikuma daga baya ga SD, wato Alhaji shehu Darma, Wanda shine aka saka yake bibiyar Alhaji Auwal Fharuk yana masa barazana, satar yarana da akayi a ranar sunansu ta kawo bayyanar aminina d'an uwana cikin case d'in mahaifina daban ta6a tunanin kasantuwarsa a cikiba, wato Harun d'an gidan waziri, shine wazirin mahaifina shine kuma wazirin Sarki Na yanzu, ina cikin rud'anin Hakan saikuma ga Alhaji Rabilu ya bayyana a gareni shida Badi d'a ga mai dokuna a masarautarmu, Wanda tun ina k'arami Na sanshi, amma daga baya ya 6ata 6at. Bayanan wad'annan bayin ALLAH da bincikena Na had'a suka tabbatar min da zargina akan wad'annan mutanen, nasan abune mai wahalar gaske samunsu cikin sauk'i da fahimtata da duniya zatayi akan zargin danake musu, shiyyasa naza6i yin Garkuwa da yaransu bisa tursasasu tilas sufad'i abinda ke ransu da Wanda suka aikata. Dukkan Wanda ya shigo cikin labarin nan nawa akwaishi a wajennan, mijin yayatane kawai bayada rai sai mahaifan Badi, dakuma wasu daga cikinsu da sukabar duniya, Dan haka ina rok'on wannan kotu data nemo dukkan Wanda Na ambata domin jin ta bakinsa”.
Alk'ali ai yama kasa magana, sai kad'a kai kawai yake mamaki da al'ajabi Na cinsa, yayinda kotu tayi tsit kowa yana k'ullawa da kwancewa da tausayin Galadima, irinsu Alhaji Halluru kam ai cikine ya d'uri ruwa, sunsan dai tasu tagama k'arewa kam, Dan yau ranar bankad'a Ce da walle-walle.
Alk'ali yad'anyi rubuce-rubucensa sannan ya buk'aci ganin Badi da Alhaji Rabilu, Galadima kuma yaje ya zauna.
Alhaji Rabilu da Badi sun bayyana a gaban kotu, hakan ya kuma hargitsa hanjin cikin Waziri, yana mamakin dama Badi bai mutuba? Amma su hak'ilu sukazo sukace ya mutu a wancan lokacin, dan agabansu mai besfa ya kad'eshi, innalillahi ya shiga ambata a zuciyarsa, sai zufa ke jik'eshi, sauk'insa ma akwai malun-malun da rawani a jikinsa, Abba Hayatudden kallonsa kawai yake da tsantsar tsana da mamakinsa.
Duk yanda Badi da Alhaji Rabilu sukaima Galadima bayani haka suka maimaita a gaban kotu, wasu harda hawayen tausayinsu suke matsewa, Alk'ali yace, a kawo Alhaji Auwal Fharuk Dan Badi yaga idan shine yabama camera.
An kawo Abba, Wanda Alhmdllh jikinsa yayi sauk'i sosai, saidai abinda ba'a rasaba Na k'arfi, kallo d'aya Badi yayma Abba ya ganeshi Dan bai canja masaba sai canjin girma irinnan shekaru, hakama Abba ya gane Badi sarai Dan shima d'in bai canja masanba, aiko suka rungume juna kowa yana hawaye, Abba yana fad'in “Bawan ALLAH Dama baka mutuba a waccan ranar?”.
Shima Badi cikin kuka yace, “ban mutuba, sai daga baya ne Na farfad'o a wajen”.
Alk'ali ya ankarar dasu cewa a kotu suke, kotu kuma Na buk'ar jin bayani daga bakin Abba, ta Yaya Camera ta dawo hannunsa?.
Abba ya dai-daita tsayuwarsa sannan ya gabatar da kansa ga kotu, ya d'ora da fad'in “shekaru 22 kenan da suka shud'e wannan camera take a hannuna ranka ya dad'e, nakuma sametane ta hanyar kad'e wannan bawan ALLAH danayi da abin hawana a wancan lokacin, saboda ya shigo hanya yana matsanancin gudun dabansan mafariba sai yanzu danaji a ya fad'a a gaban kotu. bayan na bigeshi numfashinsa Na Nuna alamar bankwana da gangar jikinsa ya d'auki wannan camera yabani acikin akwati da sunan amana, yakuma ambatamin sunan wad'anda zanba kamar yanda yafad'a, daganan numfashinsa ya tsaya cak da aiki, ina cikin k'ok'arin taimakonsa saiga wasu mutane da gudu da makamai sun dosoni, tsoro naji, Dan inada tabbacin shima sune suka biyoshi, saboda son isar da amanar daya bani inaji ina gani badan nasoba Na tsallakesa Na gudu, Dan nasandai zasu iya kwatar abinda yabani d'in. tunda camera d'in nan ta dawo hannuna ban sake barci mai dad'iba, kullum burina da tunanina tayaya zan Isar da amanarta Na huta, tsawon shekaru ban ta6a fuskantar wani k'alubale akanta ba, Dan ko iyalina babu Wanda yasan da zamanta a hannuna, matata tasha tambayata idan taganni cikin damuwa amma banta6a fad'a mataba, kwatsam cikin laluben Wanda zan bamawa sai Marigayi Alhaji Abdul-hakeem Uba tsohon Governor d'inmu ya fad'omin, Dan ganin yana auren d'iyar tsohon Sarki wadda tana d'aya daga cikin wad'anda akace nabamawa, to lallai anan Alhaji shehu SD yasan Camera Na hannuna, Dan tabbas yaji zancen da mukayi da Alhaji Abdul-hakeem d'in ta hanyar la6ewa, aranar da mukayi zan bama Alhaji Abdul-hakeem camera ya damk'ata ga matarsa sai aka samu akasi wani aiki ya tasomin Na manta ban fito da camera ba, amma mun had'u da shi marigayi Alhaji Abdul-hakeem Na bashi hak'uri da sanar masa uzirina, shikuma SD a tunaninsu nabama Alhaji Abdul-Hakeem wannan camera, shine suka hari rayuwarsa da nufin kar6a kafin ya kaima matarsa, inaga daga baya da suka fahimci babu Camera d'in a hannunsa shine suka juyo kaina. Sunta matsama rayuwata da barazana iri-iri, kiran waya da sauransu, duk number da suka kirani da ita gobe bada ita zasu kirani ba, hakkane ya sakani ware sim card guda kawai dansu, babu Wanda ya sanni dashi, sai matata Dana saka number cikin wayarta batare da itama tasan hakanba, nayi hakanne saboda watarana koda ALLAH yabasu nasarar kasheni d'in. A lokacin da akaima yarana 6atanci da Galadima lallai hankalina ya tashi matuk'a, amma daga baya danayi nazari saina gano maybe su SD ne suka aikata hakan domin 6atamin suna, hukuncin ALLAH kuma saigashi mai martaba Sarki jalaludden da mai martaba Sarki Abdul-fatah sunzo nemawa d'ansu Galadima auren yarinyata da abin yafaru akanta, dukda a 6adda kama sukazomin ni sarai Na ganesu, amma ko y'an uwana ban sanarmawaba, abinda yabani k'arfin gwiwar aurar musu da yarinyata shine Isar da amanar hannuna cikin sauk'i, saikuma aminin mahaifina Baba mai kanwa yace nabasu, Dan shine kawai yasan da zaman Camera a hannuna, shima bani Na sanar masaba, bankuma San a ina yajiba. A randa za'akai y'ata gidan mijinta a ranar Na saka wannan camera da takarda cikin wani kwali Na sakashi a kayanta batare da tasaniba, bansaniba kota gani? Dan cikin gifts d'inta data samu a hannun abokan mijinta ranar dinner d'in auranta Na sakashi, nabama d'an uwantane Abdul-Hameed babban d'ana yabata batare da shima ya san minene a ciki ba. Hikimata anan idan tagani tabama mijinta batare da kace Na ceba. SD bashikad'ai ke bibiyar rayuwata ba, Dan akwai masu sakashi yazomin da farashin kud'i masu tsoka akan camera d'in amma nayi kunnen uwar shegu dasu, hakanne yasakasu k'ok'arin salwantar da rayuwata wai tunda Na hanasu camera, nasan sunajin tsorone saboda Na kusantu da Galadima a lokacin, zan kuma iya bashi camera d'in, saidai abinda basu ma saniba tuni Camera d'in tabar hannuna. Alhaji Halluru abokinane Dan school mate d'inane, ada babu wata alak'a mai k'arfin tsakanina dashi, amma daga baya sai yayta Jana a jikinsa, ban fahimci manufarsaba dagashi har Alhaji Mamman, Dan da zuciya d'aya ni nake zaune dasu. Sai wannan karon da suka tabbatarmin da zulwa jahainin fuskarsu, sannan suka tursasa y'ay'ana biyu Dana d'auka nabama y'ay'ana Alhaji Halluru aure saboda yarda wai su d'akko musu camera a d'akina kosu kashesu dani dakuma iyayensu mata, sun razanasu da cewar sun dasa bomb a gidana, agabana duk suka sanar musu a waya. Abinda yasa ban damuba nasan k'arya suke, sannan Camera d'inma bata gidan, duk k'ok'arin lalatama Galadima sirrika da sukayi agabana sukayishi, amma ALLAH baibasu nasaraba, jin asirinsu zai Toni ta hanyar Garkuwa da y'ay'ansu da Galadima yayi shine suka shak'amin abinda ban saniba, daganan ban kuma Sanin ina kaina yakeba sai a asibiti yamai shari'a”.
Wannan bayanima Na Abba ya girgiza zukata sosai. Dan har alk'ali kasa motsawa yayi, saidai yaja kusan mintuna biyu sannan ya sauke ajiyar zuciya mai k'arfi. Ya buk'aci a kawo masa camera nanda awa 2 kacal. Anbar lokacin a matsayin hutun kotu.
Babu Wanda yaso matsawa konan da can, kowa burinsa dai camera ta iso aga mita k'unsa.
Galadima ya kira Munaya, yace ta shirya ga Sarkin motanan zasuzo da Nuren su kaita masarauta ta duba cikin gifts d'inta Na Aure data samu Abba yace camera Na ciki.
Dayake a labarai an nuna takuma gani, sai kuka dama takeyi da mamakin miyasama bata duba gifts d'in auren nataba tun wancan lokacin? Koda yake bata dad'eba a Nigeria suka wuce India, itakam a dukkan zaman da suka d'an tayi idan sun dawo bata sake bi takan gifts d'inba, to kawai tace masa ya yanke wayar, Dan yanzu babban burinsa kawai a tabbatar camera d'in tana wajen nata.
Tana gama shiryawa sarkin mota yazo da Nuren dakuma police, bata d'auka yaro ko d'ayaba tafito suka tafi masarauta.
Sun iske masarautar tsit, tamkar anyi sharar mutane, kowa Na sashensa abinda ke faruwa yama zukatansu murus, hannu kawai take iya d'agama hadiman sashen nasu dake gaisheta, basu damuba, dansunsan tana cikin wani yanayine.
Sashen nasu yayi y'ar k'ura, saboda kwana uku babu kowa a ciki, Munaya kanta tsaye bedroom d'inta ta shige kawai, ta bud'e wardrobe nata tashiga fiddo gifts d'in aurenta data tara gefe, tareda Na haihuwar su Abdurraheem. d'ai-d'ai taita farkesu, idan taga bashi bane ko bud'awa batayi take jefawa saman gado, tasha wahala matuk'a kafin ta gano akwatin da idonta ya ta6a tozali dashi a d'akin Abba itada Munubiya, rungume akwatin tayi ta fashe da kuka maiban tausayi, ana haka kiran Galadima ya shigo wayarta, share hawayenta tayi ta d'aga.
A d'arare yace, “kin hanshi?”.
Cikin dariya da kuka ta amsa masa da eh ta gansa, shima murmusawa yayi, yace, “maza Ku tahoto, mintuna 46 suka rage a lokacin da alk'ali ya bada, sonake kawai a kammala shari'arnan a yau”.
Munaya ta amsa da “to gamunan.................✍🏻
“insha ALLAH gobe idan ALLAH ya kaimu, koma mike cikin camera d'in dai zamu gani, nima Na k'osa nagani a wuce wajen😬🤦🏻♀”.
ALLAH ya gafartama iyayenmu😭👏🏻
BOOK 3 👉🏻1⃣9⃣
.................Su Munaya sunyo nisa da tafiya danja ta tsaidasu, kamar daga sama suka fara jin harbi, y'an tsirarun mutane dake bisa titin suka fara guduwa, dan titin wajen baicika yawan mutaneba, kasancewar wajen tamkar sabuwar anguwane kuma gefen gari kad'an, itace hanya mai sauk'i da zata iya kaisu da wuri shiyyasa suka biyo.....
Batakai k'arshen tunanintaba taji wani azababben zafi a damtsen hannunta, ko kad'an bataji k'arar wannan harbinba (dam inhar harbi zai shiga jikin mutum aishi bazaiji k'arar bindiga ba) kallon inda akayo Harbin Munaya tayi, glass d'in ya huda ga wani garjejen k'ato yayo wajen motar, a kid'ime ta kalli sarkin mota da hankalinsa shima yake a tashe, sai zufa yake yana waige-waigen ganin yanda police d'in suka fita sunason basu kariya.
Cikin k'arfin hali Munaya race, “Sarkin mota, ka kar6i Camera d'in nan ka hanzarta kaita kotu, ya tabbatar min lokacin buk'atarta tayi, karka sanar masa komai harsai shari'arnan ta kammala dan ALALH, inason burinsa yacika koda ace zan rasa raina a yau, please karka damu sarkin mota jeka, maza jeka kar Mara imaninnan ya k'ara so.
Badan sarkin mota yasoba ya kar6a ya fice da sauri cikin dabara, saboda Munaya tabashi tausayi, ga harbi ta samu, amma bata kanta takeba ta cikar burin mijinta takeyi.
Fitar sarkin mota tayo dai-dai da isowar garjejen k'atonan, ya bud'e murfin motar yana fisgo Munaya waje, fad'owa tayi kanta ya bugu da kwalta sai jini kawai, tuni numfashinta yafara fita da k'yar, dishi-dishi take hango wani Na dukan Nuren da bakin bindiga yana k'ok'arin kare kansa da kiran sunanta yana mik'o hannu, amma ina, sun riga sunci k'arfinsa, idanunta suka lumshe a hankali, yayinda wasu hawaye masu zafi suka gangara ta gefen kumatun data fad'in, fuskarta d'auke da murmushin k'arfin hali.
Nuren daketa kwala mata kira a rikice yana mik'o hannu, dukda dukansa da ake, ya zube a k'asa yana fashewa da kuka maiban tausayi da ambatar “please Munaya karki tafi kibarmin d'an uwa, ke wani yankin farin cikinsace mai matuk'ar girma ple......
Shima baikai k'arshenba ya sulale k'asa saboda dukansa da sukayi a kai.
Wani dake bincika camera d'in a motar ya juyo a fusace yana fad'in “babu camera d'in fa boss”.
A rud'e Boss d'in dake tsaye gaban Munaya ya taka hannunta da mugun takalminsa yayo wajen, ko motsi kuwa batayiba alamar ruhinta yabar gangar jikinta.
Ture yaron nasa yayi yafara lalube da kansa, hankalinsa yakai gaban motar. yace, “Ina driver!!? ”.
Yanda yay maganar a rikice ya saka yaran rikicewa suka hau waige-waige, sarkin mota dayay nisa a gudu yana jiyo ihun ogan, saiya k'ara k'aimi.
Wani yace, “gashi can zai gudu da camera d'in ”.
Tuni suka rufoma sarkin mota baya a guje, shima yacigaba da gudu iya k'arfinsa. Cikin amincin ALLAH saiga wani mai mashin tamkar an jehoshi, ya tsaya yana fad'in “maza hau muje”.
Sarkin mota ya haye, mashind'in nabarin wajen suna k'arasowa, Dutsuna suka d'auka suka dinga jifansu sarkin mota suna binsu da gudu, amma ALLAH bai basu nasaraba. Hardai ubangijin sammai ya kaisu court lafiya.
Sai lokacin Na lura Ashe Ahmad ne yaron Alhaji Bana, ya kalli sarkin mota yana fad'in “Maza kakai, yanzu haka ita kawai ake jira, kasa nutsuwa a ranka kar boss ya fahimta balle yakasa nutsuwa a shari'ar shima, yanzu haka suma police zasuje su taimakesu, muma can zamu tafi da sauran y'an uwana”.
Kai sarkin mota ya jinjina, ya k'arasa gaban k'ofar kotu yay knocking yana share hawaye da tausayin Galadima. Anzo an bud'e masa aka shiga dashi, dama camera d'in kawai ake jira.
A can kuwa suma saiga Police an k'aro, wad'anda suke tare dasu Munaya su 6 ne kawai dama, gashi bawani isassun kayan aikine dasuba, bindugun hannunsu babu mai bullet, sun daki d'aya yasuma, d'aya kuma yasamu ya sulale domin kira yasanarma ogansu abinda ke faruwa, yayinda biyu suka gudu, biyune kawai a wajen, sukuma sunyi musu yawa y'an ta'addan.
Isowar police d'in ta saka wasu a cikinsu yunk'urin guduwa, saidai ina, ALLAH yakan