Showing 306001 words to 309000 words out of 356830 words
garama idan tea ne, shima sai an had'a da lallashi, babu abinda ke addabar ransa irin damuwar Munaya da yaransa, sukansu duksun rame, danma suna samun tsantsar kulawane ta kowanne fanni.
Papi yazo ya dubasu, hakama su mom da iyayen su Nuren d'in da y'an uwansa, mai martaba ma da daddare yazo cikin 6adda kama ya dubasu.
Mama Fulani ma kullum saitazo, a matan Sarki gimbiya Zulfah Ce kawai batazoba, Dan kunyama ta hanata walwala gaba d'aya a masarautar, Mai martaba kuwa ya hanata hanyar ganinsa gaba d'aya itada y'ay'anta, sai matawalle kawai daya nuna damuwa akan abinda kakansu da mahaifiyarsu suka bada gudunmawa wajen aikatawa wan mahaifinsa, sanan yay ALLAH wadai akan son zuciyarsu, koda yaushe yana tare da Galadima da Muftahu a asibitin, da wata buk'ata ta taso kafin Galadima yayi shi yayita.
A koda yaushe Momma cikin kira take taji yaya jikinsu Munaya, koda wasa ba'a sanarma Abie komaiba, Dan ana ganin cigaba da haske game da jikinsa sosai, ba'a fatan wani abinda zai maido da hannun agogo baya game da ciwon nasa.
Addu'oi kam sosai aka duk'ufa yinsu game da Munaya, wadda har yanzu Galadima ne kawai keda alhakin shiga ya dubata, shima sau d'aya a rana kawai, yau dai duk ake saka ran farkowarta, Dan an dakata damata dukkan wata allura dake sakata barci, saidai kuma har dare babu wani bayani.
Zasu tayar da hankalinsu doctor yace suyi hak'uri, maybe zuwa dare ko safiyar gobe ta farka d'in, danba a sume takeba, barcine kawai da sune suka sakata ta hanyar mata allurar.
Badan hankalin nasu ya kwantaba sukai shirun, har lokacin barinsu asibitin yayi babu wani bayani game da farkawar tata.
Washe gari.
Duk dai yanda akaso farkawar Munaya a ranar sai a washe garine ALLAH ya amince da hakan, Alhmdllh anci nasarar farkawar tata yanda ake buk'ata, saidai ciwukan jikinta a halin yanzu.
Saida doctors suka gama dukkan kai kawonsu naganin komai ya ida daidaita sannan aka bama Galadima damar shiga.
Tamkar mai sand'a haka ya shiga d'akin, tana kwance amma idonta biyu, sai dai a lumshe suke, an kuma cire mata bandejin da aka zagaye mata fuska, sai kad'an aka bari inda ciwon yake.
Durk'usawa yay a gaban gadon, ya kamo hannunta Na haggu dakeda lafiya ya saka nashi ciki, a hankali ta bud'e idanunta saboda jin tattausan hannunsa cikin nata, ga k'amshin turarensa daya mamaye d'akin Wanda ya tabbatar mata da shid'inne, tana shak'a a hankali.
Idonta ta saka cikin nasa, kowanne yakasa koda kwakwkwaran motsi tsawon mintuna 2, a hankali Galadima ya bud'e baki tamkar mai rad'a ko gudun wani ya jisu yace, “Munaayaa I love you, I really love you, I love you more and more my Heartbeat..”
Lumshe idanu Munaya tayi, wasu hawaye suka gangaro daga cikin idanu zuwa gefen kunnuwanta, zuciyarta sai wani irin bugawa take da sauri-sauri, ta kuma damk'e hannunsa cikin nata tana maijin tsigar jikinta Na tashi, jininta sai yamutsawa yake a kowanne 6angare. Kuma bud'e idon tayi a kansa, suka sakarma juna lallausan murmushi ga hawaye Na zuba a idonta har yanzu, shima kwalla sun tarar masa a cikin ido sun saka idon wani k'yalli Na musamman daya kuma sakama munaya wata kasala da tsantsar k'aunarsa, ya lumshe idanunsa alamar tabbatar da abinda ya fad'a mata har cikin ransane ba iya fatar bakiba.
Itama hawayen ta kuma matsowa, ta bud'e baki da k'yar tana cigaba da kwararo hawaye. Tace, “i love you too yalla6ai, I love you so much...”. ‘takai k'arshen maganar wani kukan Na kwace mata.
Hannunta dake rik'e cikin nasa ya sumbata yanamai jin farin ciki, yace, “ki kasance dani Munaya, ki kasance dani har k'arshen rayuwata, ke Katanga tace, haskena ce, farinciki nace, duniyata ce, duk duniya kece mace ta farko bayan mahaifiyata da y'ar uwata danakema so Na musamman, please karki barni uwar y'ay'ana, karki gujeni komai rintsi, nima namiki alk'awarin kasantuwar mu tare har k'arshen numfashi, ki rayu dani, ki mutu dani bugun zuciyata, kamar yanda nima burina kenan a gareki tsawon lokaci”.
Lallai yau daba'a halin ciwo takeba har rawa sai tayi, Wanda bata ta6a tsammani ko tunanin zaisotaba shine yake furta wad'annan dad'ad'an kalamin agareta, shine yake rok'onta ta kasance dashi har k'arshen rayuwarsa?, shine yake kiranta katangarsa?, harskensa, bugun zuciyarsa? Koda a yau tabar duniya ta ribantu da nasarorin masu yawan da wahalar k'ididdiga wajen lissafi.
Galadima dake share mata hawaye da hannayensa ya duk'a ya manna mata kiss a goshi da saman la66a.
Ta kuma bud'e idonta da suke jajur akansa, murmushi suka kuma sakarma juna, ya girgiza mata kansa alamar tabar kukan, idanunta ta lumshe alamar amsawa.
Shikam ya tsura mata idanu ko k'yaftawa bayayi, y'ar ramar da tayi saiya k'ara mata k'yau da k'uruciya, ya shafa k'ananun kitson dake kanta ta kuma bud'e ido tana kallonsa.
Cikin d'age gira d'aya yace, “baki tambayi ina yaraba?”.
Lallausan murmushi ta kuma sakar masa, ta kwanto hannunsa dake sark'e da nata saitin bakinta ta sumbata, sannan ta d'orasa a saman k'irjinta.
Tausayinta ya kamashi sosai, domin jikinta akwai zafi har yanzu, ga abincinsu sunyi matuk'ar cika, Wanda zazza6in nata yanada nasaba da rashinsu gareta, dukda akwai Na zafin ciwo.
Hakan da tayi shima saiya fahimci mitake nufi, kuma duk'owa yay ya sumbaci goshinta, zaiyi magana doctor ya shigo.
Shiru Galadima yay ya juyo yana kallonsa, itama Munaya daga kwancen take kallon doctor ta k'asan ido.
Doctor dake gulma da zuciyarsa yana fad'in lallai ya yarda, duk sarautar Sarki a gaban matarsa bawane, matarce ke zama sarauniya..... (Ga naku Matan kwarai sarakin duniya👍🏻👌🏻😜)
Galadima ya katse tunaninsa ta hanyar buga yatsunsa biyu suka bada sautin d'as-d'as.
Doctor ya dawo hayyacinsa a kunyace. Yace, “sorry ranka ya dad'e, dama Nurse zata goge mata jikine da kuma gasa mata, Dan tasamu sauk'in nauyin da yay mata”.
Murmusawa Galadima yay, ya zare hannunsa daga cikin Na Munaya yana mik'ewa tsaye, hannayensa ya hard'e a k'irji yana kallon doctor da fad'in “Doctor da raina zan bar wasu ganarmin sirrina? Ku kawo kayan buk'ata kawai”.
Doctor daya fahimci Inda zancen Galadima ya nufa saiya murmusa yana cewa “Afuwan ranka ya dad'e”.
Hannu kawai Galadima ya d'aga masa, ya juyo suka had'a ido da Munaya ya d'aga mata gira da cizar lips d'insa.
Baki ta tunzuro masa tana yamutse fuska.
Ya d'aga kafad'a da ta6e baki alamar bashida matsala🤷🏿♂🤣.
Nurses biyu suka shigo da dukkan abinda ake buk'ata, Galadima Na tsaye ko kallon inda suke baiyiba, idonsa nakan matarsa k'yam, sukam sai satar kallonsa sukeyi, suka ajiye suna fad'in “Gashi Ranka ya dad'e”.
hannu kawai ya d'aga musu amma ko tari baiyiba.
Fita saukai cikin takaici, dan sunso yayi musu magana koda sau d'aya ne.
Takawa yay a hankali jikin k'ofar ya Mirza key, sannan ya dawo yana cire link d'in hannun rigar farar shaddarsa da tattarewa zuwa sama.
Suka had'a ido da Munaya tai azamar janyewa cike da kunya.
Murmushin gefen baki yayi yana zama bakin gadon kusa da k'ugumta.
Bottoms d'in jikin green d'in rigar asibitin yafara cirewa a hankali, itadai kunya ta hanata bud'e ido, gashi ya tsareta da idanu, Dan tanajin yanda idanunsa ke yawo cikin jininta, salon daya koma wajen cire bottoms d'in ya sakata dafe hannunsa da hannun haggunta, ta bud'e ido tana kwa6e fuska.
Gira ya d'aga mata, da wani mata salo da kwayar ido.
Babu shiri ta maida idonta ta rufe ruf, tsigar jikinta Na tashi.
A haka dai aka gama cire rigar, yaja bedsheet d'in da ake lullu6a mata a k'afafu ya rufa mata a jiki, sannan ya kuma gyara hannun rigarsa yana tsoma madaidaicin towel d'in cikin ruwan d'umin dake a boket, ya matsa dukda akwai d'an zafi ruwan haka yafara danna mata jiki dashi.
Tanajin zafi, amma kuma tanajin dad'in d'umin ruwan sosai, k'in yarda tayi su had'a ido har aka gama, ya d'auki wani d'an kwalba da mai ke ciki tamkar zaitun, karantawa yay yaga amfaninsa sannan ya zuba a tafin hannunsa yana murzawa, kumajin tattausan hannunsa daya had'u da sul6in mai tayi a k'afafunta, tad'an kuma bud'e ido tana kallonsa. Ganin ba ita yake kalloba saita shagala da kallonsa, babban mutum mai daraja jinin mulki yau shine ke mata hidima irin haka, itako badan kar ace tayi alfahari ba da cika baki da yawa da tace ta more fiye da kowacce mace (🙄nidai fa bandani, reader's Ku kun yarda harda Ku🤷🏻♀)?.
Sosai tafara jin dad'in tausar, Dan da salon nutsuwa yake mata, tuni tafara lumshe idanu, hardai barcin yaci galaba a kanta. Sai dai saukar numfashinta yaji a hankali.
Ya kalleta yana murmushi da lumshe idanu, bai bartaba saida ya tabbatar barcin yayi nisa, cikin dabara ya canja mata rigar da suka sakko a kayan domin canji. Ya duk'o ya sumbaci goshinta da bakinta yanajan bedsheets d'in sosai ya kuma lullu6a mata.
Kayan ya maida gefe, ya koma saman kujerar dake gefem gadon ya zauna ya zuba mata idanu, kai kace yaune ya fara ganinta, ya dad'e a haka kafin ya d'auka wayarsa yana dannawa.
A haka Nurses d'in suka masa Knocking, izinin shigowa yabasu, amma sai suka murd'a k'ofar a rufe.
K'aramin tsaki yaja yana muk'ewa, shi yama manta ya rufe. Bud'ewa yay yadawo ya zauna yana d'ora k'afa d'aga kan d'aya da kuma d'aure fuska.
Tuni Nurses d'in suka shiga hankalinsu, cikin risinawa d'aya tamasa bayanin zasu canjama Munaya bandejin jikinta ne.
Batareda ya kallesuba yace, “kuyi a hankali, Dan barci takeyi, idan kuma kunsan zata iya farkawa kubarsa saita tashi ”.
Kallon juna suka, kowacce tad'an ta6e baki, d'ayar tace, “insha ALLAHU bazata tashiba ranka ya dad'e”.
Nanma Kansa kawai ya jinjina musu yacigaba da latsa wayarsa.
Haka sukai wannan aiki a gabansa Dan yak'i fita, data motsa ya zuba musu uwar harara mai rikita hanjin ciki.
Dolensu suka bita a sannu har suka samu kammalawa lafiya, kowacce ta fice a tsorace.............✍🏻
ALLAH ya gafartama iyayenmu😭👏🏻
♦RAINA KAMA...!!♦
(Kaga gayya)
Bilyn Abdull ce🤙🏻
BOOK 3 👉🏻2⃣3⃣
.................Mud'in mun kasance wasu yankin ahali daga wannan masarauta, sai dai nasan al'ada da ak'idar masarautar ta jima da shafemu daga kasantuwar tsatsonta.
Iftila'in al'ada Nak'in kar6ar d'iya mace a matsayin y'ar farko ga Sarki mai mulki shine silar barin iyayenmu damu kanmu, sarakuna da yawa sun shud'e labarinsu ya shafe tamkar yanda Na Sarki Madou Amadi yazama shud'ad'd'e” inna ta share hawayenta, sannan tacigaba da fad'in, “Lokacin da mahaifinmu yake bisa karagar Mulki da k'arfin iko sai ALLAH ya azurtashi da haihuwa ta a matsayin d'iyarsa ta fari. Haihuwata ta girgiza k'arfin mulkinsa matuk'a, Dan Al'adar masarautar shine tilas d'an Sarki Na farko ya kasance d'a namiji, acewarsu d'iya mace rusa masarauta takeyi da tsiyatata, dan ita bata mulki, kamar yanda ake korar duk wani Sarki da matarsa ta haifi y'a mace a haihuwar farko ga mahaifinmu sai bai yuwuba, saboda k'arfin iko da ALLAH ya bashi, anbuga-anbuga yak'i sauka, danshi burinsa ya canja wannan al'adar masarautar, har ALLAH yasa Na cika shekaru 7 a duniya. A tsakaninnan bayyana harmutsi da hayaniyar da taita faruwa 6ata lokacine, Dan mahaifinmu Sam yak'i sauka daga Matsin da suke masa. cikin amincin ALLAH sai kuma ga cikin Rabi'a babu zato, har wannan lokacin babu wani kwanciyar hankali a masarauta, saidai bayyanuwar cikinta yasa akace za'a dakata aga mizata haifa, idan d'a namijine shikenan. Saidai kash, daga lokacinda Rabi'a ta canyara kukan isowa duniya sai masarauta tayi tsitt, Dan kuwa dai kowa yaji macece. Dandanan fa aka tada Sabin bore akan dolenefa sarki ya ajiye a wannan karon, amma mahaifinmu saiya k'i a wannan karonma, danshi burinsa ya canja wannan mummunar al'adar kowa ya fahimci itama d'iya mace tanada tata darajar fa, kufa namijin bai fitaba, domin itama ALLAH ya haliccetane danta bauta masa tamkar namijin, dukansu kuma idan sunk'ibin ALLAH wuta zai sasu, idan sun bishi Aljanna zai kaisu, amma Sam sai suka bijirema dukkan tunatarwarsa, masuma goya masa baya suma sai suka daina, watan Rabi'a 1 kacal a duniya akai mana korar kare daga wannan masarauta dama yankin baki d'ayansa, muna kuka muda mahaifinmu haka muka tafi, mukabar ahalinmu, yankinmu , al'ummarmu. Saboda mummunanr Ak'ida, saidai kuma babu inda muka Sani, Dan haka iyayenmu suka yada zango awani k'aramin k'auye dagacan bakin gari, anan muka rayu tsawon wasu shekaru dahar nakai girman zama minzalin budurwa, itama Rabi'a ta girma, rana tsaka saiga tawagar masarauta wai ankai mata bayanin mahaifinmu baibar wannan yankiba, halan akwai abinda yake shiryawa? Dan bazai yuwu ayi sarki biyu cikin nahiya d'aya ba, sarkin ma da aka d'ora bayan korarmu shima matarsa mace ta haifa, tuni sun korashi, Na yanzunma kuma hakance ta faru, dalilin korarsane ma sukaji labarin mahaifinmu yana a wannan waje tare damu. Korar cin zarafi da akai mana a wannan lokacin tamafi Na farko, Dan alokacin munada wayo muma, munsan zafi munsan d'aci, a wannan karon bama Nahiyarmu ba, k'asar gaba d'aya muka bari, tafiya ta tsawon wattani da yada zango ce takaimu Nigeria, a wahalce a jigace, inda muka samu mafaka a tashar da suke lodin motocin da suke zuwa kasuwanni, makonmu uku a wajen, Dan bamu rasa abincin dazamu ciba iftila'in rayuwa da k'addara ta fad'amin, Wanda muka wayi gari da rashin mai taimakonmu sai wani bawan ALLAH (Malam fharuku kakansu Munaya😅)”
Inna taci gaba da bada labarin k'yautatawar dasu Innaro sukai musu, har mutuwar iyayensu da aurenta da Abba, Dana mama Rabi'a, da zuri'ar da suka samu harda jikoki, ko kad'an bata fad'i muzanwa ko cin fuska da Innaro taita musuba sai alkairin mijinta da y'ay'anta.
Nanfa kowa ya shiga matse hawayen tausaya musu, hardamu, Dan munji abinda koda wasa bamu ta6a saniba balle tunanin kasantuwarsa, Dama iyayenmu jinin sarautane mai girma irin haka? Amma kullum suka kasance cikin shanye k'ask'anci da gorin talauci Dana ahali, lallai wannan banzar al'ada batada wani abin birgewa.
Shikansa sarkin saidai yay hawayen tausayinsu inna, Yakuma buk'aci su matso garesa, hakama tsohuwarnan rungumesu tayi tana kuka.
Innaro dai anyi zugudim tana kallon ikon ALLAH, Wanda ya girma ya d'aukaka, kunya da d'unbin nadamar Dana Sani sun dabaibayeta tagaza koda kwakwkwaran motsi balle d'aga ido ta kalli su inna, yanzu nan dukkan cin kashi dacin zarafin dataitama su Ai'sha musammanma ita shine zata lullu6e bak'in mugun halinta ta wanketa da alkairin mijinta Dana y'ay'anta? Wace irin k'yak'yk'awar zuciyace da wannan baiwa haka?.
Munsha kukan tausayin su innarmu, sannan munyi murna matuk'a da tarbar da akai musu damu kanmu, Su Abdurraheem dasu Aiyaan, da Aryaan, Ahmad, dake k'anan duk an janyesu, kowa yana d'aukarsu cikeda tsantsar so da k'auna. Saida akad'an lafa sannan Sarki yay bayani cikin nutsuwa da dattako.
“Lale marhabin agareku y'an uwana, kun kafa tarihin da tilasne a yaba muku, Dan babu wasu da suka sake waiwayen wannan masarauta bayan korar da akaimusu, sun tafi ba'a kuma jin labarinsuba ko inda suke. Bak'aramin durk'usar da wannan masarauta waccan Mummunar Al'ada tayiba, mun rasa ahalinmu masu d'inbin yawa, masarauta dake cikeda dangi yau takoma sai tsirarune a cikinta, kunganmu nan dudu iyakarmu kenan muka rage, wasu sarautunma sai hannun jama'ar gari da bayi ta koma, saboda babu masu rik'ewar, haihuwa itace yad'o, mukuma mun nisanta kanmu da wannan yad'on, masarautar nan ta dad'e tana korar ahalinta saboda haihuwar y'ay'a mata, ALLAH kuma yayta jarabtarmu da samunsu a matsayin y'ay'a, bayan shud'ewar marigayi Sarki Madou Amadi sarakuna kusan 20 sun shud'e a dalilin hakan, bamusan duniyar da sukeba, saida mahaifina yahau ya tsaida wannan al'adar gaba d'ayanta, saboda ganin wataran lallai sai kowa dake cikin ahalinmu ya k'are inhar wannan al'adar tacigaba da wakana, muna baku hak'uri, muna kuma Baku hak'uri, a yanzu wannan masarautar ba ita bace waccan da kukasani, mace Nada daraja sosai a yanzu, tanada kima da k'arfin fad'a aji, muna fata bazaku sake nisantarmu ba, zakuzo mu had'a k'arfi da k'arfe wajen kuma samun yad'uwar wannan masarauta ”.
Innarmu da mama Rabi'a Na hawaye suka amsa masa da insha ALLAH.
Zayyana muku farincikin daya cigaba da gudana 6ata lokacine, mun shige cikin dangin mahaifanmu munata warkajami, kulawa ake bamu ta musamman da birgewa, aranar aka canja mana masauki Na musamman dayafi wancan k'awatuwa da komai,