Showing 9001 words to 12000 words out of 17277 words

Chapter 4 - Kwai Cikin Kaya Complete Hausa Novel

12 Oct 2024

2365

ita kunyarsu ma taji sosai, domin dai kallon iyayenta take musu, gashi yanzu ta aure musu miji harda rabon ɗa tsakani, ta baza ido taga ƙawayenta su Atika sun shigo amma sai taji tsitt, bayan kuma ance dukansu sukazo, dama bata saka ran ganin su Yaya Naseer da sauransu ba, tunda su mazane.
Bayan suna kowa ya kama gabansa, Maryam ta cigaba da rainon ɗanta Abdul-Aziz da kulawa da mijinta.

Rayuwa ta shuɗa, dan har maryam ta yaye Abdul-aziz, gashi yana tafiyarsa ko ina ga surutu ko akku ta shafa masa lafiya, yaron akwai wayo na haƙiƙa, gashi kullum yana cikin yara idonsa na sake buɗewa.
A hankali duk wasu wahalhalu da yaran ƙauyen keyi Maryam bata hana Abdul-Aziz shigaba, kiwon dabbobin babansa ma shine ya koma bin yara daji yi, ko yabi zugar yara yo ciyawa, shine zuwa gona shuka ko kwaso amfani da kaka, yana girma wahalhalu na sake hawa kansa, gashi yanata zuwa makaranta anan cikin ƙauyen, dan da farko Alhaji Yusif yayi niyyar maida Abdul-Aziz birni ya samu ilimi tamkar ƴan uwansa amma sai Maryam ta hana, cikin hikima ta nuna masa ta fison Abdul ya tashi cikin wahalhalu irinna ƙauyen, hakan zai taimakawa rayuwarsa ta gobe harma wani ya amfani jibinsa. Badan ya soba ya barsa, itako ta cigaba da sakashi duk abinda ya dace, lokacin da Abdull yakai shekara goma sha biyar tsaf zai ja maka kunyar gona sama da ashirin a nome, faskare wannan yinsa yake, ragamar kiwon dabbobin gidan kam ya koma hannunsa baki ɗaya, duk safiya da an fito sallar asubahi yana makarantar allo, zuwa takwas suke tashi sai yazo yay shirin makarantar boko ya tafi, yana tasowa abinci kawai yakeci ya ɗebo ruwa ya zuzzuba a gidan ya ɓalle dabbobin gidan ya tafi jeji kiwo, bazai dawoba sai gab da magriba, da yayi wanka zaije sallah shi da babansa idan yana gari, idan yana birni wajen sauran matansa zaije shi kaɗai, baya dawowa sai tara da rabi, dan ana gama sallar isha'i yake wucewa makarantar allo again.
Sai rayuwar Abdul-Aziz tazam sam babu hutu, har wasu na ganin maryam ta cika tsauri aka sa, gashi shi kaɗai ALLAH ya azurtata da samu, tun bayan haihuwarsa bata sake koda ɓari ba, baza'a ce bata damuba kam, amma ta danne ta cigaba da harkokinta hankali kwance, tasan dai haihuwa ta ALLAH ce, kuma shine ke badawa ga wanda yaso a lokacin da yaso, guda ɗayanma ta godama ALLAH, fatanta ALLAH ya rayasa ya zama amfananne ga al'ummar musulmai da addinin musulinci.
Rayuwa haka ta cigaba da shillawa, Abdul-Aziz shine autan gidansu, dan suma matansa na birni babu wadda ta sake haihuwa, abinda zai birgeka shine zuwa wannan lokacin kuma duk sun saki jiki da maryam, komai ya wuce, yaransu kan ɗanje hutu wani lokacin wajenta, itama Abdul kanje wajensu dukda dai baya jimawa sabida ya saba da ayyukansa anan ƙauye, acewarsa canko sai dai aita yawon banza da barci da kallo bayan anci an ƙoshi, shiko sam bazai iya rayuwar lalaci ba.
Sauran ƴan uwansa sukan masa kallon mahaukacin da baisan ciwon kansa ba, shiko ko a kwalar rigarsa, har zuciyarsa yake faɗar abinda ke ransa ne.
Yayunsa mata kusan duk sunyi aure, mazanne dai babu wanda ya yunƙuro har yanzu, dukda kuwa a cikinsu akwai waɗanda suka isa auren.
Lokacin da Abdul ya kammala secondary ne wasu a cikin yayunsa sukai aure, shiko Alhaji Yusif yay masa zancen dawowa birni dole saboda cigaba da karatu, sam bayason dawowar, idan ta shine abarsa yayta harkar nomansa da kiwo yafi birgesa, secondary ɗinma da yaya ya gamata, gashi yanzu ne mahaifinsu yafi bukatarsa saboda kulawa da harkokinsa na kiwo da noma, dan ƙarfinsa ya fara karewa girma ya fara kamashi, gashi sauran yayyen Abdul babu mai son zuwa ƙauyenma bare su taimaka masa, su kawai boko suka saka gaba da burin samun daula ta birgewa suci duniyarsu da allura, kasancewar mahaifinsu manomi makiyayi ma takaici yake basu, a ganinsu ajinsu ya wuce ubansu ya ƙare a harkar noma da kiwo, bayan kuma da itace duk suka samu tallafin karatun nasu.
Sosai Abdull ke lallaɓa babansa akan baison zuwa makaranta, amma sam yaƙi saurarensa, yace dolene shima ya fita haƙƙinsa akan karatu tamkar sauran ƴan uwansa.
Babu yanda Abdul ya iya dole yay biyayya, amma koda yatashi karatun sai ya karanci fanin kiwo da noma, dan aganinsa yafi fahimtarnan ɗin.
Ƴan uwansa dariya abun yayta basu, dan aganinsa abunfa na haukar Abdull ya fara wuce makaɗi da rawa, yaro kamar tsatson ƴan rawar banjo. Sam baya kula zancensu, abinda yasa a gaba yakeyi, ga ƙwarin gwiwa yana sake samu da ga mahaifiyarsa da babansa.

Kammala karatun Abdull babu jimawa ALLAH ya ɗauke Alhaji Yusif a duniya, wannan mutuwa ta girgiza dukkan ahalinsa musamman maryam da Abdull, abin ya taɓasu masuƙa, ansha ruguntsumi da tashin hankali har komai ya lafa zukata suka dawo hankalinsu bayan haƙuri da dangana da ya riskesu bisa rahamar UBANGIJI.
Ranar da akai addu'ar arba'in a ranar aka ɗakko zancen raba gado, babu wanda yay jayayya wajen amincewa akai rabo, ita dai maryam bata da abin faɗa, dan ɗaya tilo ne gareta, ita babban tashin hankakinta ma ta yadda zata bar ƙauyen, dan tasan tilas zamanta ya ƙare kenan, gashi ta saba da kowa da komai na yankin.
Ilai kuwa hakance ta faru, dan a yanda rabon gadon yazoma sai da gidan sukayi, dukda Abdul yace abasa zai saya da ɗan kuɗinsa kakarsa ta wajen uwa mahaifiyar maryam sukace zasu cika masa kuɗin, amma tsabar mugunta aka hanasu saya, maryam da ta lura zamansune ba'a sonyi saita lallaɓa Abdull akan yayi hakuri yabar zancen, duk inda ALLAH ya sake ƙaddara zamansu suyi haƙuri su karɓa kawai.
Da wannan nasihar taci ƙarfinsa yayi biyayya, angama raba gado tsaf, ɗan filin gonar da Abdull ya samu ma bawata mai yawa bace, dan haka yay zuciya ya saida tasa, cikin yayyun nasa da aka haɗasu ya saye suna masa dariya akan ya gama wahala amma ya tashi babu tsuntsu babu tarko.
Abdul ma yanada haƙuri, amma lallai akwai zuciyar masifa idan aka kai haƙurinsa tunga, wannan kalmomi da aka jefesa da sune suka bashi ƙwarin gwiwar mikewa da ƙafafunsa ya shiga fafutukar neman na kansa, yayinda maryam ta koma gidansu ta cigaba da rayuwarta, dukda kuwa ana takura mata da batun tayi aure tunda bata wuce yinsa ba.

Abdul ya zage damtse wajen neman halalinsa, ya manta ma da wasu takardun kwalin shaidar gama karatu, kai gaba ɗaya yama manta kansa matsayin ɗan boko, dukda kuwa ga yayyensa sunaci da biro cikin sauƙi, 100% kuma shima ya goyi bayan mahaifiyarsa akan tayi aure, dan shine mutuncinta.
Maryam bata musaba tai aure anan ma cikin anguwar kusa da gidansu, ta auri wani bawan ALLAH da matarsa ta rasu ta bar masa ƴaƴa har huɗu duk mata.
Mama maryam mace ce da ta san kanta, ta kuma yarda ɗa na kowane, dan haka ta rungumi yaran a jikinta tamkar nata, ta kuma tsaya tsayin daka akan tarbiyyarsu musamman babbar da ta zama budurwa. Wannan dalilinne ya jefa ƙaunarta mai tsanani a zukatan yaran da mahaifinsu, harma da danginsa da na mahaifiyarsu. Shima sai ya sake jan Abdull a jikinsa tamkar shine ya haifesa, ya kuma sake nuna masa hanyoyin neman na kai masu sauƙi, dan shi ɗan kasuwane.

A cikin amincewar UBANGIJI sai ƙauna mai ƙarfi ta shiga tsakanin Bilkisu ɗiyar mijin mama maryam da Abdul-Azez, duk da babu burin aure kusa a ransa sai gashi ta canja masa dukkan tunani da tsarinsa, ya rikice ya fara kafa manufofinsa a gareta, koda mahaifinta ya fahimta sai yayta murna, dan shikam dama halayyar Abdul na matuƙar birgesa, hakama mama maryam taji daɗi sosai, ga yaran akwai tarbiyya dama, sannan gasu ainahin ƙyawawa abin son kowa.
Abdul sam bai ɗakko maganar auren bilkisu ba sai da yasamu ɗan abin dogara wajen riƙeta, dan shima dai kudin farko da ALLAH ya albarkacesa dasu a kasuwa saiya koma ƙauyensu ya sai gona ya tsunduma harkar noma tamkar mahaifinsa, ga kuma ɗan kasuwanci yanayi na sai da dabbobi da abincinsu anan cikin binni, ganin yanada abinda zai riƙeta gwargwadon iko sai kawai aka saka biki, haya ya kama na ɗakuna biyu a wani gida, su biyune kawai suke haya a gidan, dan haka komai sai ya zam musu da sauƙi, dan matan nasu duk masu hankaline, babu mai rawar kai aciki.
A Ɓangaren ƴan uwansa kuwa kowanne yana fantamawa rayuwa, dan mafi yawansu duk da biro sukeci, matan kam ba laifi suna auren masu hali, arziƙin ƴan uwansa bai taɓa kwaɗarsa ba balle ya zame masa abin rikewa wajen yimusu hassada, harkar gabansa yake da iya gwargwadon abinda ALLAH ya hore masa, bai dogara su bashiba, bai kuma zauna damuwa da sunfishi ba. Suko kullum cikin kallonsa mafi ƙasƙanci a cikinsu sukeyi, suna ganin ya tashi a ƙauye, sun fishi karatun boko, sun fishi komai na rayuwa, ko tarkacen kwancen kayansu ko wani abu suka tashi saisu bashi, shiko ya amsa cikin murna da girmamawa, bai taɓaji a ransa dan ƙaskanci sukai masa ba, yasa a ransa da yarda sun fisa ɗin da gaske.

ALLAH mai alkairi, harkar nomansa nata bunƙasa, hakama sana'ar saida dabbobi da abincinsu, har lokacin bilkisu bata taɓa koda ɓatan wata ba, sai da suka shekara huɗu da aure ALLAH ya bata ciki, zo kaga murna wajen Mama Maryam da shi kansa uban gayyar da ƴan uwan bilkisu, ciki na kai wata baƙwai haihuwa tazo mata, aiko tasha wahala kafin ta haifi bakwaini biyu tagwaye, ɗaya ma baizo da raiba.
Sun karɓa hannu biyu kuma sunyi murna da jin tausayin kansu na rasa ɗayan, sai dai kuma hukuncin ALLAH shima ɗayan bai kai labariba ya koma.
Tun da ga nan Bilkisu bata ma sake samun cikiba tsawon lokaci.

*Komai na da sanadi*.

Wannan magana haka take, dan kuwa sanadin dam da akajema ƙauyen su Abdul ne ya zamar masa wani gagarumin alkairi, gonarsa ta kasance ɗaya da ga cikin gonakin da dam ɗin zai cinye, hakan yasa aka biyasu makudan kuɗaɗe gwamnati ta saya, shi kuma Abdul yana da ilimi, sai yazama shine ya tsayama jama'ar ƙauyen da duk abinda ya shafa har sai da aka biyasa haƙƙinsa, ya kuma basu shawarwarin su sake sayen wasu gonakin dan ga damar yin noman rani ya sake samuwa, ɗari bisa ɗari suka amince da shawararsa da ga manyansu har matasansu.
Turawan da sukazo wannan aiki sai al'amuran Abdul-aziz suka matukar birgesu, hakan yasa suka jashi jikinsu ya zama abokin hirarsu duk da kuwa ba ko yausheba, dan shima yanada harkokinsa da yakeyi.
Turawan ba cikin ƙauyen suke kwana ba, zuwa yamma suke tashi su koma cikin birni inda suke da masauki, hakan yasa suka sake jan ra'ayin Abdull har yasan mazauninsu, suma kuma sukasan nasa.
Kafin kace mi shaƙuwa ta shiga tsakaninsu sosai, halayensa na neman nakai da dattako na sake birgesu, gashi dai ba wani babba ba can amma akwai halayyar manya, kafin su kammala aikin ƙaton dam ɗinnan da ko Abdul baisan iyakarsa ba shakuwarsu ta wuce misali, dan har bilkisu ya kaimasu suka gaisa, sannan wani lokacin yakan sakata tayi abinci ya kai misu, acewarsu suna koyon cin abincin arewacin Najeriya.
Bayan kammala aikin nasune sukai haramar komawa, dukansu sun fuskanci halin kewa na tsantsar sabo, sai kowanne ya tsinci kansa a damuwa, lokacin da zasu tafi suka damƙa gidansu kacokan ga Abdull ƙyautar ALLAH, dama saya sukai dansu zauna harsu gama aikinsu, ganin sun kammala kuma sai suka bashi da zasu tafi, rasama mizai faɗa musu yayi dan susan yaji daɗi, dan gidane mai azabar ƙyau da tsari, kowa yasan dai yanda turawa suka amince da gyaran muhalli, to shima wannan ya ɗauki tsari na musamman, gashi a anguwar manyan mutane.
Duk sai da ya ɗauki ƴan uwansa ya kaisu suka sanya albarka da matan babansa, hakama dangin mahaifinsa dake ƙauye, mota biyu suka ciko sukazo suka tayasa murna. Sannan ya maida iyalansa can, harda mama maryam yaso amma mijinta da ita kanta suka ƙi, aganinsu yaya zasuje suyima ƴaƴansu zaune dukda dai gidan babbane. Dole Abdul ya haƙura amma ya ɗauke ƙannen Bilkisu biyu da suka rage ya maida gabansu, dan ɗaya a cikinsu itama tayi aure.
Shekara ɗaya kacal da faruwar hakan saiga turawannan sun dawo Najeriya, ashe zuwa sukai tafiya da Abdull, dan su dai yamusu har ƙasan zuciya, bayan ɗan kace nace da aka samu akan tafiyar tasa dai da ga karshe ALLAH ya amince su mama maryam suka barshi ya bi turawannan, sai dai yabar matarsa a nan gida Nageriya.
Wannan tafiya itace ta sake canja komai da ga rayuwar Abdul-Aziz Yusif Tafida, cikin ƙankanin lokaci ya bunƙasa, dan kuwa acan ƙasar turawannan ashe sun jashine akan harkar noma da kiwo irin nasu, suka sake wayar masa da kai, shima ya sake wayar musu da kai akan nasa sanin da ALLAH yay masa, dama su kunsan komansu da tsari, tamkar kamfani nasu yake, sai suka dirasa matsayin babba mai kula da komai, a duk bayan wata uku yake zuwa gida Nageriya yay wata guda ya koma can ƙasar, sannan anan Najeriya ma ya kafa jijiyoyi musamman a ƙauyensu, dan kuwa ya tallafa ma matasan ƙauyen da magidanta akan noman da kiwo, harma ya kwashi wasu acikin matasan suma sunacan turai ɗin tare dashi.

Rayuwa ta matukar sauyawa, duniya ta bama Abdul-Aziz babban filin fantamawa a cikinta, abin birgewa kuma yana amfani da damarsa sosai wajen gina kowansa, tamkar ƴan uwansa da abaya suke ganin sun fisa yanzu ya zamar musu runfa, dan kuwa dukkan dukiyarsa da ke Najeriya su ya ɗaura akanta, dukkan sirrinsa sun sanshi, duk abinda kaga bai sanar musuba to lallai sai dai sirrin da ya shafi matarsa ko mahaifiyarsa, wannan kam da ga shi sai su sai ALLAH, har zuwa yanzu kuma basu haihuba, kuma bai taɓa yunƙurin sake aure ba, hakama babu wanda yace masa ya sake auren ko za'a dace. Yana son matarsa sosai, dan haka bai taɓa nuna mata ya damu da rashin samun ƴayansu ba dukda yana kwaɗayin son ganin tsatsonsa a duniya.
Ba a cikin ahalinsa kawai yake taimako ba, hatta da mutanen gari ta kowanne fanni amfanuwa suke da tagomashin arziƙinsa, ya zama bango abin jinginar kowa, sannan runfa mai lulluɓe zafin rana ga kowa, dukda hakan kuma bai isa zama mai ƙyautata zukatan kowa ba, dan ko UBANGIJI daya hakicci ɗan adam baya iya masa............✍🏻



_Please mu haɗu page ɗin gobe idan ALLAH ya kaimu dan jin yanda zata kaya_.😉








*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭👏🏻_*I think you'd like this story: "ƘWAI cikin ƘAYA!!" by BilynAbdull on Wattpad https://my.w.tt/tRmHPDmnJ5


*_Typing📲_*





*_🧺ƘWAI_* _cikin_ *_ƘAYA!!_*🧺


*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*


*_SADAUKARWA:_*
_Aunty Fareeda Gachi_
_Aunty Rahma A-Majeed_


*_Wattpad_*:- _BilynAbdull😉_

*______________________________________*
*_BOOK ONE_*
_Shafi na biyar_
*______________________________________*


...........A yanda Abdul-Aziz ke bautama al'umma da hidimarsa, sai ka ɗauka bai ma san ciwon dukiyarsa ba, kokuma a banza ya sameta ba da guminsa ya taraba. Abubuwa yake na bajinta ko tunanin kuɗin zasu iya ƙarewa bayayi, kafin kace kwabo sunansa ya zauna ɗam abakin mutane, ko yaro ƙarami ka ambatama sunan Alhaji Abdul-aziz tafida da gudu zai amsa maka harma yay maka sharhi gwargwadon fahimtarsa.

Rayuwa ta ci gaba da shurawa, yayinda wasu da ga cikin jama'a suka fara kafa dandalin kiranye ga Alhaji Abdul-aziz zuwa ga siyasa. Duk da yana jinsu, kuma yana ganinsu, sai ya maida kansa makaho kuma kurma akan batun, dan shi sam siyasa bata cikin tsarin tafiyarsa ko burinsa.
A na cikin wannan yanayinne ya fara ginin wasu katafaren gidajen gona guda biyu, amma a jihohi mabanbanta. Sai wani katafaren family house da zai haɗa dikkan ahalinsa waje guda, kuma kowa da ɓangarensa babu ruwanka da shiga sabgar gidan ɗan uwanka, Wannan aikinne ya kauda hankalinsa ga nacin jama'a na son ganinsa cikin siyasa.
Lamarin kuɗi sai mai su, kafin kace wani abu gidajen gona sun kammala, hakama gidansu, matasa da yawa harma da magidanta sun samu aikinyi a ciki, abubuwan alkairi harsun fara fitowa ta gidan, sannan suma sun koma sabon gidansu shi da duk sauran ƴan uwansa da iyalansu, mama

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login