Showing 9001 words to 12000 words out of 13059 words
wannan littafin.
Nan fa
MAALIKUS-SAIF yanuna shi sam baiyarda ba saidai ta tafi tare dashi, dole kuwa
hakan tayi tatafi tare dashi amman kafin haka saida ta bashi wani bakin ruwa na tsafi
tace ya watsa qa jikinsa, watsarshi keda wuya yaga ilahirin jikinsa ya zama baki
kamar yadda fatar 'yan garin suke, Bokanya AKILA ta bashi jakarta ta bokanci ya
rike, tana tafe yana binta a baya har suka fito daga cikin gidan.
Fitowarsu keda wuya
suka tadda bokayen nan dake qarqashin Bokanya AKILA a bakin gidanta suna jiranta
tana qarasawa inda suke suka dunguma sai dakin bauta,
koda suka kusa shiga sai
MAALIKUS-SAIF ya qarasa kusa da Bokanya AKILA ya miqa mata jakarta, ita
kuma cikin rada ta qara jadda mashi kan cewa kada ya kuskura yayi yunqurin daukar
littafin nan ya amsa mata da to amman badan ya yarda da shawararta ba.
Koda Bokanya AKILA ta isa cikin dakin bautar sai gaba daya mutanen dake dakin
bautar sukayi wa littafin sujjada bayan Sarki KAMARUNU ya fito dashi daga
maboyarsa ya dorashi bisa wani taburi, ganin sunyi sujjada ga wannan littafin yasa
MAALIKUS-SAIF ya taho a hankali cikin sanda, yazo inda littafin nan yake ya miqa
hannu da niyyar ya dauko shi sai kawai yaga littafin ya fado qasa tim! Ya fara
zagayeshi.
Jin qarar fadowarshi yasa Bokanya AKILA; Sarki KAMARUNU da
sauran jama'ar dake wannan dakin bautar suka dago daga sujjadar da suka yi, aiko
sukayi ido biyu da MAALIKUS-SAIF, nan fa suka hau dukansa baji ba gani,
MAALIKUS-SAIF shima ya hau dukansu,
kasancewarsu suna da matukar yawa sai
wani daga cikin.dakarun ya zagayo ta bayan MAALIKUS-SAIF ya sammaceshi ya
bugesa a tsakiyar kai, nan take MAALIKUS-SAIF ya baje a kasa baiko shura ba,
koda ganin haka sai Sarki KAMARUNU yayi godiya ga wannan littafi sannan ya
umarci wasu dakarunsa dasu je su jefa MAALIKUS-SAIF cikin wata tsohuwar rijiya
dake a bayan gari.
Bayan sun dauki gawar sun jefata a wannan rijiyar ne suka dawo
suka sanar da Sarki KAMARUNU. Sannan Sarki KAMARUNU yace da jama'a aci
gaba da shagalin biki.
Ita kuwa Bokanya AKILA koda taga an kashe MAALIKUS-
SAIF sai hankalita yayi mugun tashi kasancewar tasan irin son da yarta "DAMATU
takewa MAALIKUS-SAIF saboda haka ta sulale ta koma gida ba tare da sanin
kowaba.
Koda tafada wa DAMATU abinda ya faru a dakin bauta, kuka °DAMATU
ta dinga yi da qyar Bokanya AKILA ta shawo kanta.
******
Alamarin MAALIKUS-SAIF kuwa ashe ba mutuwa yayi ba lokacin da aka
MALIKUSSAIFI DAN ZIYAZZANUN
littafi na daya 1
part 8
post by Shuraih 99%
.
dokeshi a tsakiyar ka suma yayi, yana cikin wannan hali na suma wata aljana ta
bayyana tsulim! A cikin wannan rijiyar koda ta daga hannunta sama sai wani ruwa ya
dinga fita daga wannan hannu yana jiqa fuskar MAALIKUS-SAIF, jim kadan sai
MAALIKUS-SAIF ya farfado daga suman dayayi, nan fa ya fara tariyo abinda ya
faru dashi a dakin bauta,
bai gama tunanin dayake ba yaji anyi sama dashi anfito
dashi daga wannan rijiyar.
Anan MAALIKUS-SAIF yayi godiya ga Allah madaukakin Sarki daya kubitar
dashi daga cikin wannan rijiyar, to bayan ya gode ma Allah, sai ya tambayi wannan
mutumin daya fito dashi yace kai kuwa wane ne kai? Mutumin ya dubi MAALIKUS-
SAIF yace ni ba Namiji bane ni mace ce, kuma aljana, na kasance diyace a gurin
Sarki fararen aljanu mai suna ABAYARU ni suna na AKISA, nan da nan ta juye ta
koma budurwa.
Kuma nazo nan ne domin wani taimako da zakayı mani.
MAALIKUS-SAIF ya dubeta yace wane taimako kikace zan maki? Aljana AKISAA
tace ya Dan uwana akwai wani bakin aljani mai suna MUTTADI'U.
Shi wannan
aljani kafiri ne mukuma musulmai ne, mun samu musuluncin mune a wajen wani
bawan Allah mai suna Shehu Abdussalam. Wata rana wannan bakin aljani mai suna
MUTTADrU ya sauka a Garinmu yace yazo ziyara, duk da karfin mulkin mahaifina
amman yana tsanananin tsoron wannan bakin aljanin, saboda haka mahaifina ya
saukeshi suka zauna afada suna fira.
Can nazo wucewa da bakin aljanin nan ya
dubeni sai yace yana sona, saboda tsananin tsoronsa da mahaifina yake sai yace masa
ya bashi ni, ni kuma banason sa, saboda ba musulmi bane, hankalina sai ya tashi, nayi
iya tunanina naga babu mai iya kubutar dani daga wannan bala'i da nake ciki, sai na
yanke shawarar na tafi wajen wannan bawan Allah Shehu Abdussalam wanda ke
garinmu, na fada masa halin da nake ciki na nemi ya taimaka mani.
Da Shehun yaji
haka sai yace Ai duk duniyar nan babu mai iya kubutar dake daga hannun wannan
bakin aljanin sai wani mutum kuma Dan uwane gareki mai suna MAALIKUS-SAIF
Dan ZIYAZINUN.
Sai na tambayeshi inda zan sameka sai ya ce mani Inkoma wajen
babata zata gaya mani inda kake. Dana koma Gida sai na tambayi uwata shine take
bani labarin cewa ai yanzu wasu aljanu daga kasar KAIMARA suke bata labarin
cewa gashi can a jefashi a cikin wata rijiya, maza jeki ki kubutar dashi to shine
kaganni nazo to kaji abinda nakeso ka tainmakeni ka kubutar dani daga wannan baqin
aljanin.
Da MAALIKUS-SAIF ya gama jin wannan batu daga bakin AKISA sai ya shafa
bulalarsa yaji tananan, sai yace in sha Allahu zan kubutar dake daga hannun wannan
bakin aljanin.
To amma kuma naji kina cewa ni Dan uwanki ne, ya akayi ni ina
mutum ke kina aljana har na zama Dan uwanki?.
AKISA tace uwata ta sanar dani cewa ai kaima danta ne domin tare ta shayar dani
da kai nono lokacin muna jarirai.
MAALIKUS-SAIF yace to ya sunan babar taki?
AKISA tace DASUKATU. Koda MAALIKUS-SAIF yaji wannan suna sai yace na
yarda ke yar uwata ce, to yanzu saikiyi maza ki kaini wajen wannan uwa tamu.
Kafin ya rufe bakinsa sai ga DASUKATU ta dira dif! a gabansa yana ganin haka
ya rungumeta, yana ce Mata mai yasa kika rabani da ku shekaru da dama.
DASUKATU tace ya Dana munyi maka haka ne domin zamanka a wajenmu bazai
yiwuba saboda dabi'un mu da naku na mutane sun banbanta, shiyasa ya zama mana
dole muka mayar dakai ga mutane yan uwarka, yanzu maza ka hanzarta domin
kubutar da yar uwarka. Da gama wannan magana sai tayi masu sallana ta tafi.
MAALIKUS-SAIF ya kalli AKISA yace To yanzu sai ki daukeni ki kaini wajen
wannan aljani.
AKISA ta dauki MAALIKUS-SAIF ta tashi dashi izuwa qololuwar
sama tayita tafiya dashi, can sai AKISA ta tsaya da tafiya ta sakko kan wani dutse, ta
nuna masa wani tsauni ta ce Kaga wancan tsaunin to akansa gidan wannan aljanin
yake.
MAALIKUS-SAIF yace "To shiken an tsaya anan ni na shiga na fito", yakama
hanya, daya isa gindin tsaunin nan yai zagaye ya rasa inda zai kama ya hau, yana
cikin haka sai yaji ana kiran sunan sa daga saman tsaunin nan, ya daga kansa sai yaga
wasu yan mata ne suke dago masa hannu suna kiran sunan sa.
Sai suka zuro masa
igiya ya kama, suka jashi harkan tsaunin nan.
Da MAALIKUS-SAIF ya hau kan dutsen nan sai yaga yawan yan matan nan yakai
su Arba'in,kuma dukkansu yan matane kyawawa, sai daya daga cikin su wadda
kamar itace shugabarsu mai suna NAHIDA tace ai jiya a cikin baccina naga Annabi
HALLIRU
laihissasatu Wassalam, yace inbada Gaskiya akan addinin Annabi
Tbrahim Alaihissasatu wassalam, ya musuluntar dani Sannan ya fada mani cewa yau
akwai wani mutum mai suna MAALIKUS-SAIF zai zo ya kubutar damu, ya kuma
fada mani cewa ni ina daya daga cikin matayen da zaka Aura, shine na fito ina baiwa
wadannan yan uwa nawa labari sai muka leko muka ganka.
MAALIKUS-SAIF ya tambayi yan matan nan ku kuma me ya kawoku nan?
NAHIDA tace ai mu duk nan daka ganmu yayan Sarakuna ne, ganinmu da kayi anan
wannan aljanı shiya kwasomu ya kawomu nan, dama shi dab1arsa shine duk inda
yaga yar Sarki kyakkyawa to sai ya daukota ya kawota nan, ahaka duk ya taramu
anan.
Da MAALIKUS-SAIF yaji wannan bayani sai ya tuna lokacin dashi wannan aljani
yaje zai dauke SHAMATU ya sare masa hannu daya, suna cikin haka sai suka ji wani
rugugi da hayaqi ya tunkaro su, sai matan nan suka ce wa MAALIKUS-SAIF ya
gudu ya nemi wajen buya domin ga aljanin nan ya dawo.
MAALIKUS-SAIF ya ce
Ku barni dashi babu inda zani, yan matan nan suka shige cikin wani daki suka bareshi
tsaye a waje.
Jim kadan sai ga aljanin nan ya bayyana, koda yaga MAALIKUS-SAIF
sai yace yauwa daman kaine ka taba sare mani hannu yau gashi kazo har gidana, kaga
sai na rama na kasheka nima.
Koda gama fadin haka sai aljanin nan ya miko hannu d nufin ya kama
MAALIKUS-SAIF. Cikin zafin nanma MAALIKUS-SAIF yayi wuf! Ya zaro bulalar
sa ya tsula wa aljanin nan. Nan take aljani ya kama da wuta yana kururuwa yana ihu
yana ya kasheni! Ya kasheni...! Cikin lokaci kankani aljanin nan ya qone kurmus,
ya baje kamar turbaya.
Da yan matan nan sukaga haka sai suka fito a guje suna murna, shi kuma ya yi
kiran AKISA ta taho ta shigo wajen. Koda taga ya kashe wannan aljanin sai tace Ya
Dan Uwana na gode wa Allah, na gode maka daka kubutar dani daga sharrin wannan
aljanin, ni kuma babu abinda zanyi na saka maka illa kawai na rika maka hidima.
MAALIKUS-SAIF ya umarci AKISA da ta dauki yan matan nan duk ta mayar dasu
kasashensu kuma idan ta mayar dasu ta sanar da iyayensu cewa shine ya kubutar
dasu.
Nan da nan AKISA ta rika daukar yan matan nan tana mayar dasu qasashensu,
sannan tayi bayanin kamar yadda MAALIKUS-SAIF ya fada mata, da haka har ta
kwashesu kaf ya rage saura NAHIDA kadai.
MALIKUSSAIFI DAN ZIYAZZANUN
littafi na daya 1
part 9
post by Shuraih 99%
.
AKISA tazo zata dauketa amman sai taqi. MAALIKUS-SAIF yace Ki tsaya mana
ta daukeki ta mayar dake wajen iyayenki.
Sai tace "Ai ni tunda Annabi HALLIRU ya
fada mani cewa ina daya daga cikin matan da zaka aura to ba inda zani ina tare da kai
duk inda zaka kuwa".
Da MAALIKUS-SAIF yaji wannan magana ta NAHIDA sai ya
tambayeta yace "Ke mutumiyar wace qasa ce'?" ta amsa mashi da cewa "Ita
mutumiyar birnin Sin ce, kuma ubana shiyake mulkin wannan kasa". MAALIKUS-
SAIF ya amsa da cewa "Naji kuma zan Aureki to ammanfa ki sani bazan aureki ba
har saina auri SHAMATU DA 'DAMATU tukunan.
Saboda haka yanzu ki koma
qasar ku". Tayi nacim duniyar nan amman yaqi, koda ganin yaqi yarda sai tayi masa
wata addua tace "To tunda kaki insha Allahu duk lokacin da zaka shiga garinmu,
dagakai sai wando zaka shiga". Shikuma sai yace "Ni kuma insha Allahu lokacin
kina a makance zan shiga, bazaki ganni a tube ba" Dukkansu kuwa sa aka amsa
masu adduarsu.
MAALIKUS-SAIF ya umarci AKISA data dauketa ta mayar da ita kasarsu.
AKISA ta kaita ta dawo da AKISA ta dawo sai tace da MAALIKUS-SAIF to ya Dan
Uwana in kanaso zan kaika birane bakwai mafiya kyau a Duniya?MAALIKUS-SAIF
yace "Eh inaso ki kaini nayi kallo, amman kafin nan inaso ki kaini wajen Shehun nan
na garinku nayi masa ziyara.
AKISA ta daukeshi suka tafi. Da zuwansu, sai
MAALIKUS-SAIF yaga wata hasumiya. AKISA tayi sallama sai sukaji daga ciki an
amsa masu da cewa Barka dai MAALIKUS-SAIF Dan ZIYAZINUN.
Suna tsaye sai
wani Tsoho ya fito. MAALIKUS-SAIF ya tambayi AKISA yace Shikuma wannan
Tsohon wanene shi? AKISA tace "Ai shine Shehu Abdussalam din da nake baka
labari". Suka yi musabiha shida MAALIKUS-SAIF yajashi ya shiga kogon dashi
yana fada wa MAALIKUS-SAIF wasu nauoi da sigogi na zikirin Allah.
Bayan sun
kammala ne Shehun yace ka zauna ka kwana anna ni gobe zan mutu, bayan na mutu
kayi mani wanka ka daga kasan shirmfida ta zakaga likkafani sai ka lillibeni dashi.
Sannan sai ka fita waje kofar hasumiyar nan kayi kira sallah, zakaga mutane ta sama
da qasa sunata zuwa kar kayiwa kowa magana, kuyi zana' ida tare da mutanen nan
bayan kun gama, zakaga ba kowa a cikin mutanen nan.
Sai kaima ka binneni ka kama
gabanka. Haka kuwa akayi gari na wayewa Shehun nan ya cika. MAALIKUS-SAIF
yayi jana'idar yadda Shehun nan ya fada masa.
AKISA tazo tace Ya Dan Uwana idan ka shirya to zan kaika birno na farko,
MAALIKUS-SAIF yace Na shirya. AKISA ta daukeshi suka samu Kamar sa'a daya
a suma suna tafiya, sai suka isa ganuwar wani birni AKISA ta sauka tace "To dan
uwana gamu a qofar birni na farko, yanzu sai ka shiga ka fito ni bani da ikon shiga
wannan birnin, domin akwai kafi wanda zai iya koneni idan har nayi kuskuren shiga.
MAALIKUS-SAIF ya kama hanya ya shiga cikin wannan birni na farko. Da shirsa
sai yaga nmanyan gine gine masu matukar kyau, sannan da Abubuwa masu balain
kyau, yaita yawo yana kallo. Can sai ya iso wani fili yaga wasu mutane sunata fada.
Koda suka ganshi sai duk sukayo kashi, daya daga cikin su yace "Yakai wannan
baqon sai ka raba mana rikicin dake tsakanin mu.
MAALIKUS-SAIF yace Wane
rikici zan raba maku? babban yace nida Dan Uwana mahaifinmu ya kasance shine
baban malami a wannan birni, sunansa Malam AFLADIN, ya mutu ya barmana
gadon wata hula, wadda ita wannan hula ta tasance indai ka sakata to mutum ko aljan
babu mai ganin ka.
To shine muketa rigima akan ko wannenmu yanason ace shine ya
gaji wannan hula, dama kafin kazo mun yanke shawarar duk wanda yazo ya samemu
to shi zai Yanke hukunci a garemu, sai kuma gashi kazo, to muna so yanzu ka raba
mana wannan rigima tamu.
Da MAALIKUS-SAIF yaji haka sai yace "To zan
rabamaku wannan rikici, ku bani kwari da baka zan harba ta duk wanda a cikinku ya
fara dauko ta, ya kawo mani ita nan to wannan hular tazama tashi.
Wadannan yan uwa biyu suka amince da abinda ya fada, suka bashi kwari da baka
gami da hular ya rike a hannunsa.
MAALIKUS-SAIF ya harba kibiya duk mutanen
suka saki dawakansu suka bazam neman kibiya, suka barshi a tsaye da hula a hannun
sa, can bayan wani lokaci sai MAALIKUS-SAIF ya hango daya daga cikin mutanen
nan ya dawo a sukwane, kafin ya karaso sai MAALIKUS-SAIF ya raya a zuciya sa
cewa To niko in gwada wannan hular in gani in gaskiya suka fada mani akan wannan
hular, sai MAALIKUS-SAIF ya saka Wannan hular.
Koda mutumin ya qaraso wajen
sai ya rinka kwada kira yana yakai wannan alkali namu ina kashiga gani na dawo da
kibiyar, yayita diri diri.
Koda MAALIKUS-SAIF yaga mutumin baya ganinsa sai
yace a zuciyarsa "To lallai na yarda da lamarin wannan hula idan kasa mutum baya
iya ganinka, yanzu saura na gwadata akan aljani nagani, can sai ya tuna ai AKISA
aljanace bari yaje ya gwadata akanta.
MAALIKUS-SAIF yai tafiyarsa yabar wannan mutumin yanata diri-dirin neman
sa, daya fito ne ya iske AKISA tana tsaye tana jiransa yazo gabanta ya tsaya amman
duk bata ganshi ba, saiya kira sunan ta *Ya 'yar uwanta AKISA". AKISA tayi wani
turus! "Tace kana ina ne Dan Uwana, kardai ace kasamo hular nan ta Malam
AFLADIN? MAALIKUS-SAIF yace kina ganina?
"Tace A'a bana ganin ka kana
inane?" Koda MAALIKUS-SAIF yaji haka sai ya godema Allah daya bashi ikon
mallakar wannan hula, Sannan ya cire hular da hanninsa sai AKISA ta ganshi a
gabanta, ya kwashe labari kaf game da yanda akayi ya mallaki wannan hula ya fada
wa AKISA.
"Ai manyan sarakuna da dama na samu labarin sun rasa rayukansu akan
neman wannan hula, amman kai gashi ka sameta a sama" AKISA take bashi labari,
taci gaba da cewa MAALIKUS-SAIF to yanzu saika shirya na tafi dakai izuwa birni
na biyu.
MAALIKUS-SAIF yace to yanzu karbi hulata ki ajiye mani, tana karba yace
da ita to muje na shirya.
MAALIKUS-SAIF da AKISA suka kama hanyar birni na biyu nan ma dai AKISA
ta saukeshi a kofar shiga gari yai mata sallama ya tinkari kofar shiga garin, da shigar
MAALIKUS-SAIF garin sai jama' ar garin sukayiwo kansa suna ga bako! Ga
bako...!Suka taso masa zasu kamashi sai rigima ta barke a tsakaninsu suna dukanshi
shima yana dukansu, ahaka hardai sukaci karfinsa suka kamashi suka kaishi wajen
Sarkin su.
Shi Sarkin wannan gari sunan sa Sarki DUHANI, ita wannan qasa suna da
wani zobe wanda duk wanda ya mallaki wannan zoben to shine zai zama Sarkin
wannan gari, saboda shi wannan zoben shi suke bauta mawa, sannan idan aka nuna
mutum da wannan zoben sai kanshi ya guntule y fadi qasa, a wannan lokaci Sarki
DUHAN shiya mallaki wannan zoben, saboda haka ya zama Sarki.
Sarki DUHAN ya
dubi MAALIKUS-SAIF yace "Kai ko mai ya kawoka qasata?" MAALIKUS-SAIF
yace "Nazo ziyara ne da kuma yawon bude idanu." Da Sarki haka sai yace Shine
kuma kazo ka fara fada da mutanena harka kashe mani wasu daga ciki.
Sarki yayi
umarni ga wani babban bawansa da ya tafi da MAALIKUS-SAIF gida yayita gana
masa azaba har sai gobe da safe a dawo bakin kogin dake gaban gidan Sarki a fito
dashi a kasheshi. BULAKI ya kama MAALIKUS-SAIF ya tafi dashi ya kaishi cikin
wani daki yayita azabtar dashi har dare ya raba sannan ya koma dakinsa ya kwanta.
MALIKUSSAIFI DAN ZIYAZZANUN
littafi na daya 1
part 10
post by Shuraih 99%
.
Can bayan wani lokaci, MAALIKUS-SAIF yana a daure sai yaga BULAKI ya
shigo dakin ya fadi gabansa yace ka gafarceni ya Sarkin Sarakuna MAALIKUS-
SAIF Dan ZIYAZINUN ka gafarceni.
Koda MAALIKUS-SAIF yaga haka sai yace
"Ya ya haka kainefa kayita azabtar dani dazu kuma yanzu kazo mani da wannan
maganar."
BULAKI ya nisa yace "Ai yanzu cikin baccina naga Annabi HALLIRU ya
musuluntar dani kuma yace dole na kubutar dakai.
Nan da nan BULAKI ya kwance
MAALIKUS-SAIF, ya kawo masa abinci yaci ya koshi sannan ya kawo masa ruwan
sha, sannan ya kara jadda musuluncinsa a gaban MAALIKUS-SAIF.
A wannan dare BULAKI yabi duk mutanen gidan ya musuntar dasu sai wata baiwa
kwaya daya data ki musulunta, akayi akayi amman taki. Nan BULAKI ya kamata ya
daure yace "Gobe Zan je ya jefata ruwa a mainakonka." MAALIKUS-SAIF yace
"Tunda kai yanzu musulmine Zan canja maka suna daga yau ka koma Abdussamad."
Gari na wayewa Abdussalam ya fito da wannan kuyangar lullube dan ayi tunanin
MAALIKUS-SAIF ne, yazo da ita bakin kogi ya tsaya. Jim kadan sai Sarki ya leqo ta
taga, yai Umarni da Abdussamad daya kashe MAALIKUS-SAIF shi a tunaninsa
kenan amman baisan ba MAALIKUS-SAIF bane.
Bayan Abdussamad ya kashe
wannan kuyanga mai taurin kai. Sai Sarki yayi nuni da hannunsa daya jefa gawar
cikin ruwa. Abdussamad ya jefa gawar cikin ruwa ya koma gidansa.
A lokacin da
Sarki yayi nuni da hannunsa da a jefa gawar cikin ruwa bai saniba ashe a wannan
lokaci zobensa ya subuto ya fada cikin ruwan.
Zoben na fadawa cikin ruwa sai wani
kifi ya hadiyeshi a tinaninsa abinci ne.
Da isar Abdussamad gida sai yace da MAALIKUS-SAIF "Mai kake da sha'awa
yanzu na kawo maka?" **Yace kifi nakeso naci yau domin naji ina marmarinsa.
Abdussamad yace Kash! Sai dai babu sauran kifi a gidan nan amman bari na fita nayi
fatsa na kamo maka.
Da MAALIKUS-SAIF yaji haka Sai yace kaga kuwa nima ina
da sha' awar fatsa bari mu tafi tare. Abdussamad ya yarda da hakan suka tafi wannan
kogin da suka jefa wannan kuyangar, can suna fatsa sai suka kamo wani katon kifi
ganin kifin yana da girma sai suka hakura suka taho dashi kadai gida.
Abdussamad ya
yanka cikin kifin a dafa, koda ya kwaso kayan cikin