Showing 6001 words to 9000 words out of 23399 words

Chapter 3 - Darajar Yayana Part 1

20 Nov 2024

3038

zan kara
lokaci ba sai dai in ajalina bai zo ba.Da kyar bacci
ya daukeni, lokacin iya tayi nisa da bacci.Shima
Aliyu tun da ya koma dakin shi fa ya kasa ko
zama, lallai dole ne ya nemi mata, sai dai
matsalar shi ta ina zai fara?Bai taba yin budurwa
ba, bai taba soyayya ba, shi kuma yana ganin
kamar raini zai ja masa in yaje kofar gidan su
yarinya.Amma bari gari ya waye yaje wajen
usman amininshi.Kafin ya wuce masallaci sai da
ya fara lekowa dakin mu ni da iya duk muna
sallah, sanan ya wuce,dan Allah ya kawo mata
sauki a cikin daren daga masallaci gidan Usman
ya wuce, ta wya ya kira shi cewa gashi a kofar
gida,Usman ya ce, lafiya?Aliyu ya ce, lafiya ba lau
ba, fito kaji.Da sauri usman ya bude gida ya fito,
sama sama suka gaisa.Usman ya ce, aboki lafiya?
Aliyu ya ce ina fa lfy, jiya tsohuwa ba lafiya, ta
fara bar mun wasiya, sannan tayita jaddada min
burinta kawai nan duniyar shine inyi aure.Usman
yace aboki ba ita kadai ba, ni kaina buri na
kenan, to tunda kaga tsohuwa ta tsananta gara
kayi ko kwa rabu lafiya.Aliyu ya ce, ai baka sani
ba, tunani na yanzu ina zanje nemo mata?Na
rantse maka banda budurwa...


Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100



DARAJAR YAYANA1-02
Posted by ANaM Dorayi on 08:55 PM, 09-Mar-16
Under: DARAJAR 'YA'YANA
___________________NA
___________HALIMA K/MASHI
Usman yayi yar dariya sanan ya ce, ni da zakaji
shawarata wanan sadiya ta gidanku?Aliyu yace,
ah haba?Usman yace, naga yanda ake yabon
hankalin yarinyar, ko a gida tana da matsalane?
Aliyu ya ce, sam ko a gida bata da matsala
gaskiya, amma ban taba jin koda alamar sonta
ba, to wanan yarinyar ma ina ganin ta tsaida
wanda take so, in ma ba ta tsayar ba sai inga ta
yi mun yarinya.Shekarunta sha bakwai fa yanzu
in ban cika ma ba, usman ya ce, dai dai.Nafi son
wacce ta shiga makarantar gaba da scondary a
kalla ta mallaki hankalinta, ta san yadda zata kula
dani sai nine zan koma in kula da ita.Usman ya
ce, ba yaran yanzu ba, tunda kaga bata yiba in
kaga wata da tayi maka ko a unguwarku ko a
kafatanin unguwar mu'azu ka fada min yanxu
anjima sai muje, kaga yanxu sai kaje wa iya da
kwarin gwiwa.Aliyu yayi shiru yana tunani can ya
ce, aboki kasan Allah?Nifa ba wai ina kallon mata
bane, na layinmu ma ban sansuba balle na
unguwa.Usman ya ce, to aboki ka tsaya a Sadiyar
mai hankalice,Sadiya tayi.Aliyu yace inda ta kaicin
yake sai kuma in kirata ince ina sonta?Usman ya
ce in baka iyawa bi ta sama mana ka samu iya
ka fada mata kana son Sadiya, nasan zatayi
murna.Aliyu ya ce, aboki daina cewa ina sonta,
zadai ayi aure amma ba wai ina sonta ba, Aliyu
yace kuma ba zanyi karya ba tunda banji cewa
ina sonta ba,har Aliyu yaxo gida tunani yake anya
kuwa zai amince cewa yana son auren sadiya?
Lokacin da ya shigo dai dai na bare magani na
mikawa iya, ta afa tare da kora ruwa, ya tsaya ya
rike kugu yana kallon mu, tunaninshi a wanan
lokacin lallai babu wanda ya dace ya auri irina,
bisa hujjarshi tacewa ba zai sami matsala ba
wace take tsakanin iya da matan yayanshi ba.Iya
tana kuka cewa cikinsu matar yaya Sulaimance
kawai ta san darajarta, kuma tabbas hakane
domin sai suyi wata uku basu zo sun gaida ta
ba.Ita ba wai tana kwadayin abin hannunsu ba
ne, a a ko ba komai taga yan jikokinta yayi,
amma Sadiya bata da uwar da ta wuce iya.Dan
haka yana nan ko baya nan zata zamo a
karkashin kulawarshi, burinshi yaga ya daukewa
iya duk wani matsalarta, su kuma yayinshi suji da
iyalinsu.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Tunaninsa ya katse lokacin da iya ta ce, gadanga
ka shigo ne?Yayi firgigit, na shigo iya.Na gaida shi
na fita, shima a ranar bai iya yi mata zancen ba,
karshe ma tunani yayi ya samu yaya sulaiman
suyi shawara.Haka kuma bayan sallar isha'i ya
nufi gidan yayan nasa bayan sun gaisa sai ya
sanar dashi abinda ke tafe dashi.Yaya sulaiman
yaji dadin zancen da Aliyu yazo dashi, sanan yace
sai ka samu yarinyar ku daidaita, Aliyu ya ce, ina
ga ba sai na sameta ba, indai iya ta amince shi
kenan.Yaya Sulaiman ya ce, iya ba zata ki ba,
yarinyar ce abinji, in ta ce bata sonka fa?Aliyu ya
ce, ai nima ba wai ina sonta bane, dacewar
auren kurum nake dubawa, shi yasa.Ya Sulaiman
ya ce, shirme kenan, to kai in kaje wajen iyar ce
mata zakayi ba sonta kake ba?Aliyu yayi
murmushi ce mata kurum zanyi ina so na auri
Sadiya, Sulaiman ya ce, Allah yayi mana zabi na
alkairi.Ka bari zanje gurin iyar, duk yanda mukayi
zakaji.Aliyu ya ce to.Yayi godiya yayi masa
sallama ya tafi..Sulaiman ya sami iya cike da
karfin gwiwa, ganinshi babu wanda zaikai iya
murna kai yasan har goron albishir zata
bashi.Amma ga mamakinshi yana gama labarta
mata dalilin xuwansa sai yaga tayi kicin kicinda
fuska ta ce kaine kaga sun dace ka bashishawara
koko shine ya sameka da zancen?Yace, a a dazu
ya zo mun da zancen sai kuma naga dacewar
haka.Ta ce, to ka koma ka fada mashi ban
amince ba, kace mashi ya nemo matarshi can
itama ta nemo nata mijin.Jikin Sulaiman yayi
sanyi ya sake tausasa murya ya ce, iya ban san
dalilinki ba, kokuma akwai abinda kika hango
wanda ba na Alkairi ba?Ta ce, na farko dai kasan
halin gadanga, zuciya ce dashi ga saurin fushi, ga
miskilanci tsiya, ga shegen jin kai.Sanan na sha ji
ko in ce ya sha fada min cewa shi yar jami'a yake
son aura.Niko tawa ko secondary din bata gama
ba.Sulaiman ya ce, iya in kin duba tunda shi din
ya ce ta mashi ai ina ganin ba za a sami wata
matsala ba.Fir iya ta ki zancen, duk ta inda
sulaiman ya bullo sai iya tabi ta wata hanyar,
haka nan yaya sulaiman ya hakura ya fita rai
babu dadi.Aliyu ya sunkuyar da kai yana
sauraron sakonshi a gurin yaya sulaiman, sam bai
zaci jin haka ba, amma sai ya ce, ba komai Allah
yasa haka shine mafi alkairi, na shi ganin ba zai
damu ba, tunda dama ba wai yana sonta
bane.Sai dai kuma yanda ya tsammaci abun yafi
haka, samun kanshi yayi da shiga damuwa, ko ba
ya son yarinyar hakika ya tsananta dason
aurenta.Ya samu iya da kan shi wata safiya yaxo
gaida ta bayan yayi shirin fita cikin dakin sa.Ya
ce, iya me yasa ba zaki bani auren sadiyaba? Ta
lissafo mashi dalilinta kamar yanda ta lissafawa
yaya Sulaiman takuma fada masayaje ya nemo
mata can.Ranshi ya baci amma bai nuna ba, sai
dai cikin sanyin murya ya ce, to shikenan iya na
hakura, amma ba zan taba xuwa ko ina neman
aure ba saboda ina da munmunan halayen da
ban can canta a bani mataba,tace, ni ban ce
ba,ya ce to iya tunda ba a bani a gida ba in naje
nema a wani gida suka bani na cutar dasu tunda
ba su san hali na ba,yana kai aya ya mike tare
da cewa, sai na dawo.Ita kuma lafuzan nashi
suka hanata magana.Ita zahiri ba wai bata son
auren ya Aliyu da sadiya bane, na farko ta san
halinsa, sanan tana tsoron ta tursasa min.Kullun
Aliyu sai yayiwa iya naci amma taki ko ta ga zai
dauko zancen sai ta hade fuska.Wata safiya ina
kwance kangado ina fama da matsananciyar
ciwon mara, dama mun rabu da yin waina tunda
iya tayi rashin lafiya.Ya Aliyu ya ce, a daina yin
wainar duk wata nake wanan ciwon marar.Yaya
Aliyu ne ya shigo gaida iya, bayan sun gaisa ta
ce, har ka shirya fita kenan?Ya ce mata eh, akwai
wani case a hannunsane yana son ya kammala
dashi kafin fitowar(AC) ta ce, to Allah ya taimaka,
a can zaka karya?Ya ce, eh.Sanan yayi shiru ta
ce, da magana ne?Ta sani in har yayi haka to da
magana a bakin sa, ko da yake ta san zancen na
sa daya ne, bai wuce na sadiya ba.Kuma tana
son Sadiyar ta ji ma kunnenta in ta amince
ruwanta don haka ta ce yaya autana?Yace iya dai
maganar Sadiya, Allah iya ba maganar yabon kai
ba, ina da kamalar da za'a bani mata, ya ko ta
gidan waye 'yar taki ai ba kyau tafini ba,ya fada
cikin sigar wasa, ta ce,duk da haka ba zan baka
ba, kai ita fa tarigata fidda mijinta.Yace dan Allah
iya ki fada mata kinji?Ta ce, au, nice ma zan fada
mata?Lallai ba ma son auran nata kake ba.Ya ce,
ni iya in na fada mata sai naga tamkar zata
rainani ne.Iya ta ce, kun ji girman kan ba?Don
Allah kayi hakuri nifa ka tayar dani,ba zan yarda
ba.Aliyu da ya gaji ya fita.Tun daga lokacin da
naji ya Aliyu ya ambaci sunana na mike zumbur
hankalina atashe,ni Sadiya yaya Aliyu yake nufi
ko wata?Kai in ko nice na more, dan gaskiya yaya
ba irin mijin da zance bana so bane, tab!Wanan
shine tsintar dami akala.A a iya kada kyi min
bakin ciki, ina jin fitarshina fito da sauri ina
kallon iya, ko zata ce wani abu, amma sai ta
shareni, na ta nufintadaga yanda na dauki
al'amarin tunda ta tabbatar naji.Ko daga irin
fitowar da nayi, ganin iya ba zatayi magana ba
sai na ce iya ta dubeni, wai ya Aliyu wa yake so?
Ta tabe baki dan Allah rabu da shi, wai ke, na
dafa kirji da karfi na furta da gaske?Ta ce, zan
maki karya ne?Na ce to iya shine zaki ce mashi
ina da wanda nake so?tace, au.Sharri nayi maki
kenan?Ina ce ke naji kina cewa kin tsaida Idris?
Na ce, ai ban fada mashi ba.Ta ce, meye nufinki
yanzu?Kina so ki ce min kina son Gadanga?Nayi
shiru tare da hade fuska, mamaki ya cikata, ta
ce, Sadiya dama can kina son Gadangan ne?Na
ce, nifa ban ce ina sonshi ba, amma ke meye
dalilin da kika ca baki yarda ba?Iya ta shiga tafa
hannu tana salati.Kin tirke nine lallai sai kinji?To
ba wani dalili bane sai na kare mutuncinki,
gadanga yana da zuciya, gadanga yana da fushi,
sanan ga miskilanci,ina tsoron ki shiga matsala,
gaki karamar yarinya, shi kuma shekaru sun dan
soma ja.Da sauri na ce iya in dai dan wanan ne
na yarda kinji?Ta ce, wai me ya burgekine a dan
sanda duk jikinki ya hau bari?
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Na ce, to iya gaskiya ya Aliyu ba irin mutumin da
za a ce ba a so bane .Ta ce, ni dai na ce a a ban
yarda ba.Na mike cikin fushi na fita tsakar gida,
da kallo iya ta bini, matuka ta ji mamaki
musanman ta sanni bani da rawar kai.Ni kuma
kicin na shiga na zauna banyi aune ba sai kurum
naga hawaye suna zuba a ido na, ni kaina har
naji mamakin kaina.To da bai ce yana sona ba
fa?Ranar haka na yini har dare, kusan mutum
uku suka aiko kirana naki fita, iya duk tana lura
dani tana kallona ranar bai dawo gida ba sai sha
biyun dare, sanan tunda a subahi ya fita.Yau
sam na kasa sukuni, iya sai kallona takeyi tana
salla, can bayan ta idar ta ce sadiya!Nayi shiru, ta
ce, nasan kina jina ta shi kawaiki tashi, na tashi
zaune ta ce, sadiya ina ganin baki gane nufina ba
game da zancenkike da gadanga shi yasa har kike
fushi dani.Gadanga bahogon mutum ne, ni na
haifeshi na sanshi tun yana dan karamin shi,
gadanga bashi da dadin lamari, amma in kinji
Allah ya baki sa'a.Sai dai ina so ki sani in da
wanda zaiyi farin cikin aurenki da gadanga to ya
biyo baya na,sai dai duk da haka ba zan kasa
fada maki gaskiya ba.Shawarar da zan baki kuma
ki rage rawar kai in ya fahimci kina doki kimarki
ta zube.A zaton iya zan hakura amma sai taji na
ce, in sha Allahu ba zan sami matsala ba.Ta tsura
mini ido haka kika ce?
Nayi shiru ta ce shi kenan, to da sharadi ba zuwa
kawo kara.Da sauri na ce, to,da kallo tayi ta bina
ni dai na tashi na koma makwancina ina
murna.Na zaci da safe zata neme shi ne ta fada
mashi ayi sai kurum ta share, ko da dai ya fita
da wuri, wasa wasa sam taki zancen inaji lokaci
da yawa da ya dauko zancen zata ce don Allah ya
rabu da ita.Sai dai abinda ke bani mamaki,
kullum yanda yaya Aliyu bai can za min yanda
yakemin ba , amma nakanyi uziri cewa kila sai
iya ta amince sanan za mu soma yin tadi.Cikin
haka ne har aka dauki tsawon lokaci muka shiga
shirin zana jarabawa (SSCE) duk na kori samari na
babu wani mai zuwa tunda na fada musu na
tsaida miji.Shikam ya Aliyu bai san na sani ba,
kullum ya zo gurin iya sai yayi mata nacin shi fa
yana nan yana jira ita kuma takan ce mishi kar
ya dame ta, ba ya ce ya fi son yar jami'a ba?Ya
je ya nema.Ni kuma in ya tafi wani sa'in in ce iya
don Allah ba kince kin hakura ba, tunda na
yarda?Sai ta ce min sakarya, dubi fa ko kallo baki
isheshi ba, amma duk kin tsamgwami kanki don
fitina, ni dan kare mutuncinki nake kin abin nan.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Usman abokinsa yaji shiru batun maganar Aliyu
da sadiya, sai ya zo gurinshi musanman don
zancen , dama ya kirashi a waya yaji cewa yana
nan.Bayan sun gaisa usman ya ce, aboki wai
haryanxu ban sake jin batunka da yarinyar nan
sadiya ba, in mun hadu baka yimin zancen ba, ni
kuma ban tambaye ka ba.Aliyu ya gyara zama
yayi sanan ya lumshe ido don haushi ya ce,
kabari kawai abokina, haushin maganar nake ji,
shiyasa ban taba yi maka zance ba.Ya miko
hannu ya dafa gyiwar usman abokina ban taba
samun abinda ya bani matsala ba kamar
maganar yarinyar, ni abin haushi duk lokacin da
nayi kudirin hakura dazancen sai na kasa.Kullum
adu'a ta Allah ya yaye min ita daga raina, amma
abin ya faskara.Ko son yarinyar ne ya kamani?
Usman yayi murmushi lallai sonta kake yi, Allah
yasa ita ma ta soka hakan.Aliyu yace ina ruwana
da ita?Iyace kurum damuwata, in da ta amince
shi kenan, amma baiwar Allah nan wai zan cuci
yarinyar ita ba zata bani yarinya karama
ba.Ranar harda cewa na tsufa.Usman yace zanje
in sameta aboki, kada kadamu.Aliyu ya ce, ko
kaje matarnan ba zata yarda ba, na dai fada
mata ni na hakura da yin auren.
.Usman yayi ta dariya tare da zolayar Aliyu da
cewa, aboki ka dai shiga da yawa, to da ka ajiye
duk wani girman kai ka dinga kiran yarinya hira
in taga haka zata fi yarda cewa da gaske kake
yi.Aliyu ya ce ka yarda ni ba zan taba iya kiran
yarinyar ba, ko ba Sadiya ba, kuma sanin kanka
ne ban taba ba, so bansan ta ina zan fara ba.Ba
ta ita fa nake ba, in iya ta yarda tayi hakuri ta
aureni dan da cewa auren sai kuma ya ja tsaki
kada ma ta hakura.Tama ji dadin zancen ta samu
miji irina, Usman ya ce, yabon kai?Aliyu yayi
dariya aboki ka fadi gaskiya, ni da ita wa yafi
kyau?Bai jira amsa ba ya ci gaba na farko dai
kaga ita fari ne kurum ya ceceta..... Usman ya
katsishi au, wai dama haryanzu akwai
mummuna?Ni dai yanzu na daina ganin
mummunaai tunda naga alamun kai ya waye, ba
a zama da kazanta, Aliyu ya ce, haka ne, amma
wani wan wani ne a kyau.Usman ya ce, duk da
ka fi ta kyau dai ita zuciyarka ta zaba, zanyi
maka kokari, zanje in samu iya.Aliyu yace tunda
ka dage jeka din, duk yanda kukayi zamuji.
Kamar yanda Usman ya alkawarta yazo ya samu
iya wajen la'asar ina yi mana tuwo, itakuma tana
zaune a kofar dakinta.Na gaida shi sannan na
dauko masa tabarma ya zauna, na kawo masa
ruwa sanan naje na ci gaba da aiki na.Daga inda
nike ina jiyosu suka gaisa sanan ya fara yi mata
zancen da ya kawoshi.Iya dama akan batun
abokina ne da yar uwarsa sadiya, iya dukkan su
naki ne, a ganina wanan abin farinciki ne.Iya ta
tsuke fuska,Usman ina ganin kimarka, zaifi kyau
ka bar zancen nan bana jin cewa zan
amince.Usman yayi shiru yana tunanin yanda zai
bullo mata.Can ya ce, to shi kenan, amma na so
ki amince domin yana cikin wani hali na son
yarinyar nan, nasan halinshi kin san halinshi,baya
daga cikin mutane ma su magana biyu.Yayi mun
rantsuwar ba zai taba aure ba in ba Sadiya ba,
duk duniya ita yake so.Zaman shi haka nasan
yana damunki.Ta ce in duk duniya Sadiya yake so
ita Sadiyar ya tambayeta ta ce tana sonshi? Nifa
ba zanyiwa yata auren dole ba, don in faranta
masa.Daga inda nake a kicin na da ga hannu ko
nace ya tsa tamkar mai bada amsa a cikin
ajinmakaranta, sanan na kwalawa iya kira!!Ta
kalleni tare da yi mun da kuwa, shi dai baisan
dalilin dakuwar ba, tunda ya bani baya, ita kila
ya zaci laifin nayi mata.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Usman ya fahimci nufin iya, shi yasa ya ce mata
Aliyu ya dinga kiran yarinyar suna fira.Ya dubi
iya, to in sha Allahu za mu tuntubi yarinyar, idan
bata amince ba shike nan.Yana fita ya dauko
waya ya kira Aliyu, bugu uku ya dauka. Usman ya
ce, Aboki da farko fara bani goron albishir.Cikin
sauri Aliyu ya ce kada dai ka ce mun
tasaurareka? Usman ya ce, in sha Allahu munyi
nasara Aliyu ya ce shi kenan sai na xo aboki,
gidanka zan sauka kaitsaye daga office yanxu ina
kan wani aiki.Suna cin abinci a falonsu Usman
yana koro mashi bayani duk yanda sukayi a
karshe yace yanzu kaga tana nufin ta yarda sai
dai amma tana so ka kira yarinyar ka nemi
amincewar ta.Aliyu ya tsirawa Usman ido, sanan
ya ce, ai wanan shine mai wahalar, gaskiya a boki
ba zan iya kiranta ba.Usman ya ce, tsoronta kake
jine?Raini ne bana so, yanxu dai kai kaje ka
sameta kuyi magana.Usman ya ce, nima ke nan
zan yi maka yakin neman sonta?Aliyu ya ce, duk
yanda ka ce amma ni in na kira tafa ba ra'ayinta
zanjira ba, umurni xan bata.Usman ya ce, shi
kenan ka bari xanje.Bayan sallar isha'i muna
zaune ni da iya muna cin abinci tare kamar
yanda muka saba, yaya usman yayi sallama shi
da matarshi Anty Abida da yaran shi guda
biyu,tsam na mike daga cin tuwon ina yi musu
sannu da zuwa, suka zauna na kawo musu abinci
da ruwa, sukace yanxu suka tashi daga kan cin
abinci.Na koma tsakar gida bayan na dauki
yarinya wato Ummulkhairi, yarinyar tana da wayo
yar mai kyau taji kitso, na ce Ummulkhairi kina
makaranta? ta ce eh mana, kuma Abban mu yake
kaini har ma da Abulkhairi, nace, iye, to koya
mun karatu.Ta ce, na islamiya ko na boko?Na ce,
a a islamiya dai.Ta gyara zamanta a cinyata ta ce,
in miki sunayen Allah kyawawa?Na ce, eh,ta fara
kenan babanta ya fito, ya kallemu karatu kuke yi?
Na ce, eh, tana koya mun ne.Yayi dan murmushi
ya ce ummu jeki wajen umman ki, ki ce mata ta
jira ni ina zuwa.Ta na shiga daki ya ce, kanwata
zo mana.Na mike na bishi zuwa kofar gida,
nasake gaisheshi nayi , bayan mun tsaya ya
ce,Sadiya nasan ba zakiji mamakin kiran da nayi
maki ba ko?Na ce ba wani mamaki, kila zaka
aikeni ne.
Yyace bahakabane na kiraki ne dan in sanardake
wani abun alkairi, ko da yake ban san yanda zaki
amshi abun ba.Na gane zan cen ya Aliyu, ya
duba duk cikin matan da ke garin nan yaga babu
wadda tayi masa sai ke, tamkar bai san zancen
ba na furta da karfi so!!!Usman ya ce ba wani
abun mamaki bane, dami ne kika tsinta a kala.A
raina na ce lallai

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login