~ANEESAH~.... By Khaleesah~Haiydar VISIT www.aihausanovels.com.ng For More Novel. AIHAUSANOVELS is website consists of hausa novels note, the reason of launching this site is to Entetaint, Motivate and Educate our readers. We provided hausa novels of many type, Such Adventure, love, romance, fiction, non-fiction, mystry, fantasy, action e.t.c from hausa Authors We provided a new and old novels both softcopy and hardcopy from our Author with thier permission. AIHAUSANOVELS shafin yanar gizo ne wanda yake ?auke da littattafan hausa, dalilin bude wannan shafin shine domin Kayatar masu karatu da kuma ilimantar da su. Mun samar da littattafan hausa na nau'uka daban-daban, kama daga littafin, soyayya, tatsuniya, almara, Hikayoyi, gyara kayanki (yadda mata zasu kula da kansu a gidan mijinsu) da dai sauransu, daga Marubutan hausa. *** 1..... A guje ta fado dakin ta xube kan Amminta dake linkin kaya tana sakawa cikin jaka, Ammi ta dago fuskarta a rude tana tambayarta "lfya? me yafaru?" tana mayar da numfashi a dan tsorace ta kasa ce ma Amminta komai, sae da Ammi ta maimaita mata tambayar a fusace snn ta fashe da dariya tace "wae Ammi yusuf ne xae dokeni, don mota ta take masa kwallonsa nayi dariya," Ammi ta haureta cikin fada ta fara magana "wae ke yaushe xakiyi hankali ne Aneesah, ba wanke-wanke na sa ki ba kika fita waje kina biye ma yusuf, shi yusuf din kike ma gudu idan ba wauta ba," ganin yanda Amminta ta fusata yasa ta mike tsaye da sauri ta marairaice murya tace "kiyi hkuri Ammi, amma idan na fita wllh dukana xae yi, kuka fa yake yi," Ammi xata yi magana sae gashi ya shigo dakin, da gudu tayi bayan Ammin tana cewa "wayyo ammi kin ganshi ko," Ammi ta dada mata duka snn tace "kai yusuf yayar taka xaka duka don ba ka da kunya," yyi ma Aneesar wani irin kallo yace "Allah ya taimake ki mutumin ya bani Naira ashirin na siya wani kwallon," Aneesah ta dinga dariya tana cewa "Naira ashirin" yace "eh mana" snn ya fito da sabbin dubu daya guda biyu, Aneesah ta xaro ido tana kallonsa, Ammi tace "kai yusuf wa ya baka wnn kudi hka," yace "mutum da ya fasa min ball da motarsa yace naje na siya sabo," Ammi ta juya tana kallon Aneesah, can tace "to kawo nn yusuf, anjima da kaina xanje kasuwa na siyo maka wani, amma kace masa ka gode ko?" yusuf yace "aa na manta, snn ya mika mata dubu biyun ya fice ya fice daga dakin," Ammi tace "oh Allah dae ya biya wnn mutumin, kmr yasan ynxu tunanin me xamu ci anjima nake Aneesah," Aneesah tayi murmushi tace "ki siyo kayan abinci kawae Ammi," ammi tace "hkn xanyi, bari na gama hada kayan nn sae na tafi kasuwa," Aneesah ta mike jikinta a sanyaye ta fita daga dakin taje yin wanke wanken dake tsakar gidan. [9:29PM, 12/21/2016] Khaleesat: ~Aneesah~ 3...... Yan uwansa na ganin hka suka fara shisshige masa suna nuna masa so, da yake shi Allah yyi sa mutum ne mai son xumunci kuma mara riko, ko kadan bai kullace su kan abinda suka yi masa ba ya ja su a jiki ya sama masu aiki don dama duk buga buga suke, ya kuma taimaka ma yan uwa da dama tun daga kan relatives har xuwa wa inda ma bai hada komai dasu ba. Ana hka suka hadu da Mahaifiyarsu Aneesah Maryam a bikin wani abokinsa, sunyi soyayyar gskya wanda ya kaisu ga aure duk da dangin ubanta basu so hkn ba don auren xumunci suka yi niyyar mata, amma da yake Allah yyi shine mijinta a hka su ka yi aurensu wanda bayan shekra daya Allah ya axurta su da samun Aneesah, daga ita ko basu sake haihuwa ba har sae bayan shekara takwas, don kaninta yusuf na da wata biyu mahaifin nasu ya rasu, ba karamin girgixa Ammi mutuwar mijin nata yyi ba, kuma duk da tsanar da danginsa ke mata don ko kadan basa sonta a hka ta gwammace ta xauna ta tarbiyantar da 'ya yanta a gidan ubansu don iyayenta talakawa ne sosae snn tun tana da shekara goma mahaifiyarta ta rasu matar uba ta sa ta gaba, hkn yasa kakarta na wajen uwarta ta maidota wajenta har Allah ya hadata da Alhaji Mukhtar suka yi aurensu, kuma tasan ko ta tunkari gidan mahaifinta ynxu baxae karbeta ba don duk abinda matarsa ta gaya masa shi yake bi, kuma matar bata so ta auri mai kudi ba tunda yayanta duk ba masu kudi suka aura ba, hkn yasa ta hkura ta xauna gidan mijinta da yaranta. Ko wata uku ba'ayi da rasuwan Alhaji Mukhtar ba yayansa da suke kira da Baffa shehu ya fitar dasu daga lafiyayyan mansion din da suke ciki wae xae sa yan haya ya dinga tara ma marayu kudinsu, duk da gidajen da mahaifin nasu ke da, Ammi bata yi masa musu ba ta harhada kayansu don a tunaninta dan madaidaicin gida xae basu su xauna, amma sae suka ga ya maidosu suleja ya basu daya daga cikin gidajen da Alhaji Mukhtar ya kyautar dasu ya bar ma mara su halin kama gida talakawa su xauna, ya kori occupant din ciki gaba daya wae ba kyauta kaninsa ya basu ba dama, a hka Ammi da yaranta suka xauna gidan cike da bakin ciki tunda basu da mai tsaya masu sae Allah, don cikin yan kwanakin nn da rasuwar mahaifinsu bbu abokinsa daya da ya sake lekosu, sun dae ci sa'a ya sa su private sch mai karamin kudi, ixuwa ynxu da Aneesah ke ss3 tana shirin xana waec da neco duk da sai term ya kusan karewa ma yake biyan kudin makarantar don sae suyi xaman sati shidda a gida basu je makaranta ba, kayan abinci kuwa idan ya ajiye masu buhun shinkafa da man gyada galon daya sae yyi kusan wata shidda bae waewayesu ba, ba karamin kkri Ammi ke yi ba don sbda future din 'ya yanta har wankau ta shiga yi, ta nn ne suka samu suke rufa ma kansu asiri. Bayan sati daya duk dan kayan abincin da Ammi ta siyo masu da kudin yusuf ya kare ta rasa yanda xata yi, don gidan da take wankau sun yi tafiya xuwa england tun wata daya da suka wuce, tayi jigum abun duniya ya isheta, gashi har kusan karfe goma basu karya ba jiya da daddare ma ba wani abincin kirki suka ci ba, don ita bata ma ci ba ta bar masu ganin bae da yawa ta sha ruwa kawae suka kwanta, Aneesah na xaune bakin kofa tana duba takardun makarantarta duk da yunwan take ji amma ko kadan bata nuna hkn ba tana ta karatu, yusuf ya shigo gidan don dama yana waje yana wasa da yara, ya fada jikin Ammi yace "ni Ammi yunwa nke ji," tayi shiru tana kallonsa, can ta kwalo ma Aneesah kira ta shigo ta nemi guri ta xauna tace "na'am Ammi," ammi tayi ajiyar xuciya tace "je wajen ladi mai kosae kice ta baki na dari xan kawo mata ko xuwa gobe ne," ta mike ta dauki hijab dinta ta fita daga gidan jikinta a sanyaye, tana isa ta tarda ladi na ta tuyan kosanta hankali kwance ga mutane cike wajen suna siyan kosae, ta dan ja gefe ta bari mutanen suka ragu snn ta bata sakon Amminta bayan ta gaisheta, ladi ta hade rai tace "ku ni fa ban ciki da cin bashin nn naku, kosan da idan an baku bashin ma ba biya kuke ba ynxu da xan xauna na lissafo bashin da kuka cin min wllh xae kai dubu daya, kullum gobe xa a kawo alhalin ba kawowan ake ba, to ni yau kullina bai da yawa bna bada bashi," ta ja tsaki ta ci gaba da tuyanta tana xage xage, a sanyaye Aneesah ta bar wajen ta koma gida ta xauna bakin kofa xata yi magana Ammi tace "shknn tunda bata ba ki ba," Aneesah ta dauke kanta kawae bata ce kmai ba, hka yusuf ya cika masu gida da kuka shi a bashi abinci yaci, Aneesah ta hade kanta da gwiwa ta shiga rera kuka a hankali a bakin kofar, ko Ammi ma bata san abinda take ba. [9:29PM, 12/21/2016] Khaleesat: ~Aneesah~ 2..... Aneesah na shirin islamiyya karfe hudu saura Ammi ta shigo gidan, ta karbi ledojin dake hannunta da sauri tanai mata sannu da xuwa ta fito mata da kujera waje snn ta debo mata ruwa a randa ta kawo mata, ta xauna gabanta tana tambayarta ya hanya, Ammi ta ajiye kofin ruwan dake hannunta bayan ta shanye ruwan tace "maxa ki tashi ki kama hanyar makaranta lkci na wucewa, ina yusuf?" tace "nace ya jirani yace shi su khabir xae bi," ta mike ta dauko goggen Hijab dinta da Nikaf ta saka snn tace "to Ammi sae na dawo," Ammi tayi mata Allah ya kiyaye ta fice daga gidan. Karfe bakwae saura su ka shigo gidan ita da kaninta, Ammi na share tsakar gida su ka yi mata sannu da gida suka shiga daki, tana gama cire uniform ta fito karbar sharan ammi tace "su yi sallah, ga abincinsu a kitchen," yusuf na ganin shinkafa da miyace ya dinga tsalle yana murna yau xa su ci shinkafa, Aneesah ta galla masa harara tace "yau ka saba cin shinkafa ne? wawa kawae," ya daga hannu xae kai mata kulli ta goce da sauri tare da kwala ma Ammi kira ganin wani kullin xae kai mata, Ammi ta shigo dakin da sauri ta raba ma kowa nasa tana masu fada snn ta nemi guri ta xauna tana kallon 'ya yan nata. Aneesah yarinya ce da bata wuce shekara 17 ba, sun taso cikin wahala da talauci tun bayan rasuwan mahaifinsu Alhaji Mukhtar, Alhaji Mukhtar shararren mai kudi ne a garin Abuja, Allah yyi masa rasuwa shekara takawas da suka wuce a hatsarin mota da yyi a hanyar sa ta dawowa Abuja daga kano bayan ya kai ma 'yan uwa da relatives ziyarar sallah, tun bayan rasuwarsa suka fara fuskantar kalubalen rayuwa duk da dukiyar da ya bari mai dumbin yawa don a lkcn ma gidajen da ya bari sun kai 6 bayan motoci da filaye, kiri kiri yayansa Alhaji shehu ya karbe komai nasa da sunan xae ajiye har sae yaransa sun mallaki hankalin kansu, Alhaji Mukhtar shine auta a gun mahaifinsu malam sule, da mahaifiyarsu saudat, su uku kadae Allah ya basu duk maxa, shehu, ibrahim da shi Mukhtar, tun yana primary Allah yyi ma mahaifiyarsu rasuwa, yana gab da gama secondary mahaifinsa ma ya rasu, tun daga lkcin komai ya tsaya masa don duk yayyinsa sun dauki karan tsana sun daura masa tun iyayensu na da rae bare ynxu da suka koma ga Allah, duk suka juya masa baya ga 'yan uwa ba xumunci, ya sha wahala sosae a rayuwa don da kyar da taimakon sana'ar da yake yi na wankin mota cikin ikon Allah ya kammala karatunsa ya sami aiki a House of Assembly Abuja. [9:29PM, 12/21/2016] Khaleesat: ~Aneesah~ 4..... Sallamar wata makwabciyarsu ne ya sanya Aneesah ta dago tana goge fuskarta, ta karaso cikin gidan Aneesah ta gaida ta ta amsa tana tambayrta ya karatu, ta shiga dakin ta gaida Ammi snn ta ajiye kwano tace "gashi a ba yusuf ya kara Ammi, bbu yawa," Ammi tayi mata godiya tana tambayrta danta umar, tace "yana can waje suna wasa" snn ta fice. Ammi ta jawo kwanon ta bude taga dumamen tuwo ne, tasan kila yusuf yace mata yana jin yunwa ne shine ta kawo abincin don matar tana da kirki sosae duk da su ma manage suke don sae mijinta ya fita yyi shoe maker snn suke samun abinda xasu ci suma , ta kira Aneesan su xo su ci, bakin ciki da takaici yasa taji ta daina jin yunwan ma kwata kwata tace bata ci, da kyar Ammi ta lallabata ta ci dn tasan halinta. Karfe sha biyu saura Ammi ta fito da dinkekken atamfarta da kakarta ta aiko mata da wani sllh, Aneesah ta tambayeta inda xata da shi ganin tayi shirin fita ne, Ammi tace "xan je kasuwa ne na sayar Aneesah kafin su Hajiya salamatu su dawo," Aneesah tace "haba Ammi ke knn kullum sayar da xani don Allah don annabi," Ammi tace "to meye amfaninsu Aneesah," ki kula da yusuf kafin na dawo don daga can xan siyo abinda ya sauwaka na abinci," bata jira cewar Aneesahn ba ta fita daga gidan. Tana tsaye bakin kofar dakinsu bayan ta gama shirin boko, yusuf yace "Anty mu wuce kar su Jamila da khabir su ruga mu yau ma," Aneesah ta jawo sa tace "kasan me yusuf, maxa ka bisu ni ina nn xuwa kaji," bae yi mata musu ba ya fice daga gidan, Ammi tace "to ke me kike jira Aneesah," Aneesah ta shigo cikin dakin ta xauna tana kallon Amminta tace "kudin waec nd Neco Ammi, kuma ance kar mu xo yau idan har mun san xa muyi kuma bamu kawo kudi ba," Ammi ta tsura mata ido tana kallonta tace "to yaushe ma ya bada kudin makarantar da har xa'a tunkaresa da wani kudin waec, amma dae ki shirya kije ki samesa ki gaya masa ynxu kila Allah ya daura ki a kansa Aneesah" Aneesah ta hade rai, can ta tabe baki tace "bbu inda xanje Ammi, gwara kar na sake xuwa makarantar ma kwata kwata," Ammi ta galla mata harara tace "to ki xauna," Aneesahn tace "to wnn mutum ne Ammi, ko fa naje ba bani xae yi ba sae dae ya walakanta ni ma, ba gwara kawae kar naje ba," Ammi tace "ko ma de mae xaki ce, yayan babanki ne, baffanki ne dn hka ki iya bakin ki, kuma ki tashi ki shirya ki tafi kafin ya fita," ta mike jikinta a mace ta tube uniform dinta, ta dauki wani material dinta ashe da maroon ta saka, duk da talaucinsu in ta fita baka taba cewa tana cikin wahala don kullum fes xaka ganta. Ammi ta bata kudin motar tace ta barshi kawae xata taka, dole ta tilasta ta ta amshi kudin dn can cikin gari xata da nisa sosai. Aneesah na isa gidan baffan nata ta danna kararrawa daga waje mai gadi ya leko ta gaishe shi ya bude mata gate din ta shigo, ta tambayesa ko kawunta na ciki yace eh, da kyar gabanta na faduwa ta shiga gidan da sallamarta ta gaida 'yan aikin dake ta harkar gabansu a gidan, snn ta karasa cikin falon ta xauna kasan tiles tana jiran fitowar baffan nata. Like · Report · 4 minutes ago [9:29PM, 12/21/2016] Khaleesat: ~Aneesah~ 5...... Aneesah ta kusan minti ashirin xaune a falon kafin baffan nata ya fito cikin shiga ta shadda green colour sae walkiya yake, ga kamshin turare ya baxa ko ina, yana ganinta ko ya hade rai cikin daga murya yace "dama kece ki ke nemana wae?" ta sunkuyar da kai tace "eh nice ina kwana baffa," ya amsa a dakile snn yace "lfya da sassafen nn hka," tace "A'a dama kudin waec da Neco ne aka fara karba a schl, shine naxo na gya mka don sun ce kar mu xo yau ma," sae da ya saurareta ta kai aya snn ya daka mata wani mugun tsawa yace "don uwarki ca nayi maki ina da kudi ynxu da har xaki xo da sassafe karban kudin waec da Neco, kin bani ajiya ne ko uwar taki da ta aiko ki ta bani," ta girgixa kai tace "naga dae Baffa ba mu da wanda xamu tambaya bayan kai, kuma in ma hka ne ni fa ba kudinka nace ka bani ba, daga cikin kudin mahaifina xaka bani naje na biya abinda xan biya, kace sae mun mallake hankalin kanmu Baffa to ni dae na mallaki hankalina, a raba mana gadon mu kawae ka huta da tambayarka kudi ko makamancinsa da muke yi" tun da ta fara magana ya bude baki kmr soko cike da mamaki yana kallonta, tana gama fadin abinda xata fadi ya daka mata tsawa yace "ohho dama rashin kunya uwar taki ta turo ki kiyi min fateema, ni kike gaya ma wa innan maganganun don baki da kunya" ya saka salati yana jijjiga kansa yana kallon ceilin, ta dan tabe bki tace "ni fa ba rashin kunya nayi mka ba baffa" "to wllh wllh kinji rantsuwar musulmi ko, daga yau xuwa makarantarki ta kare, don aurar dake xayi don ubanki, kuma daga yau ko tsinke na ya daina shiga hannunku, shi uban naki da yake da rai uban me ya tsinana ma mutane sae uban rowa duk dukiyar da Allah ya basa, don uwarki duk hidimar da na ke maku har ixuwa yau da kudina nace maku ina maku, ai ki bar ma maganar gado don ko dubu dari bae rage cikin accnt din ubanki ba, duk kun cinyesu," ta mike tana yi masa wani irin kallo snn tace " lbri ma knn, shi kuma wnn gidan da kke ciki da sauran gidajensa da motocinsa fa ba a mayi maganar filaye ba, idan ma kace mun cinye kudin acc, ae wa innan suna nn baffa," ya kwasheta da wani gigitattcen mari yana huci "ni kke gaya ma wnn maganar," dae dae nn matarsa hajiya zuwaira ta fito da sauri, tace "me ya faru Alhaji, me ya kawo wnn kuma da sassafen nn," cikin in ina don ransa yyi mugun baci ya shiga yi mata bayani, Aneesah dae na tsaye dafe da kuncinta tana kallonsu, matar tasa bata bari ya kai aya ba tayi cikin kitchen da sauri tana cewa "ka kyaleni da shegiyar Alhaji," Aneesah na jin hka ta fice daga gidan da gudu don tasan matar bata da mutunci, bata manta randa ta biyo ta da yaji ba, yau kuma bata jira ganin me xata je daukowa ba ta yi ta kanta, tana barin anguwan ta dinga kuka a hanya tana bakin cikin wnn rayuwa irin tasu, da kyar ta isa gida don har wani jiri take ji dn yunwa dama koko kadae tasha da safe. Ammi ta mike da sauri tana kallonta tace "ya akayi kika dde Aneesah, me ya sa ki kuka," ta girgixa mata kai tace "ban samu ganinsa da wuri ba ne Ammi," sae da ta nutsu snn tayi ma Amminta bayanin duk yanda suka yi da baffan nata, Ammi ta dinga mata fada kmr xata mareta wae tayi ma baffanta fitsara ita dai shiru tayi bata ce komai ba har Ammi ta gaji tayi shiru, sae a nn ta shiga bata hkuri tana kuka, Ammi ta goge hawayen fuskarta don ita ma kukan take tace "kinga kin ma kanki Aneesah, ynxu xaman gidan kika fi so," Aneesah tace "dama Ammi ni banga alamar xae biya min ba fa," Ammi tace "to shknn Aneesah," Aneesah tayi shiru kmr mai naxari snn tace "Ammi kinsan mene," Ammi ta girgixa mata kai tace "me", ta dan kwantar da murya tace "don Allah Ammi ki sama min inda xan dinga aiki ana biyana sae na tara kudin waec din ta hka, tunda naga sae nn da wata uku xa a xana waec din," Ammi ta galla mata harara tace "kina da hankali kuwa Aneesah," ta yi narai narai da ido tace "kiyi hkuri Ammi, amma hkn shine kadae mafitar mu" Ammi tace "baxae yiwu ba, sae dae kijira har wani shekaran sae ki xana abinki idan Allah ya hore mana," Aneesah ta fashe da kuka tace "haba Ammi, to meye a ciki don nayi aiki, mu fa ynxu bamu da gata sae na Allah, don Allah ki bar koma wani tunani kike yi Ammi kin manta ko wacece Aneesah ne Ammi, wllh xan tsare kaina baxan taba baki kunya ba, ki tausaya min ki bari na tara kudin jarabawa na don Allah Ammi," tana magana ne tana kuka, Ammin ma kuka take, ta rasa abinda xata ce ma 'yar tata, can dae tace "shknn Aneesah ki bari nayi tunani da kyau kar mu janyo ma kanmu xagi a gari," Aneesah tace "to shknn Ammi," snn ta mike a sanyaye ta bar dakin taje debo ruwa a waje don ba ruwa a gidan. Like · 3 · Report · 1 hour ago [9:29PM, 12/21/2016] Khaleesat: ~Aneesah~ 6...... Bayan kwana biyu Aneesah na xaune gaban Ammi dake rungume da yusuf baya jin ddi tana basa ruwan tea, Aneesah ta kirata a hnkli tana kallonta, Ammi ta dago tace "meyafaru Aneesah," Aneesah ta sunkuyar da kai murya a raunane ta fara magana "Ammi har ynxu baki sake cewa komai kan maganar da muka yi dake ba, kince xaki yi tunani, don Allah Ammi ki bar ni na fara aiki, hkn xae taimaka mana sosai, gashi ynxu ko kudin da xa mu kai yusuf asibiti bbu" Ammi tayi shiru bata ce komai ba tana ta lallaba yusuf ya sha ruwan tean, hkn yasa Aneesah ta fara hawaye, Ammi ta dago kai tana kallonta, "meye na kuka Aneesah," Aneesa ta girgixa kai cikin kuka tace "to kin ki cewa komai Ammi," Ammi ta sauke ajiyar xuciya ta gyada mata kai tace "naji Aneesah," bata sake cewa komai ba daga nn, Aneesah ma tayi shiru tana tunanin wani irin rayuwace wnn da kowa kansa ya sani. Washegari laraba tun da sassafe Ammi ta fita xuwa gun wata hajiya xulfa da suke mutunci da, ta yi mata jagoran sama ma Aneesah inda xata dinga yin aiki don tana hulda da masu kudin cikin gari sosae kuma tana yawan kai masu 'yan aiki, karfe shidda na yamma Ammi ta dawo gidan a gajiye, Aneesah ta fito mata da kujera snn ta kawo mata ruwan sha a kofi, bayan ta sha take tambayar jikin yusuf Aneesah tace da sauki sosai don har ya fita wasa, sae da ta bar Ammi ta huta snn murya can kasa tace "Ammi ya hanya," Ammi tace "lfya lau, na samu inda xaki dinga aikin da kyar Aneesah, amma sae dae matar bata da mutunci ko kadan, bana tunanin xaki iya Aneesah barin ma ke da baki da hkuri, snn irin aikin da ta lissafo gskya bana jin xaki iya su sun maki yawa Aneesah, ki hkura kawae idan Allah yasa wataran Hajiya xulfa ta sake samun wani wurin aikin sae ki fara," Aneesah tace "haba Ammi ni wllh koma meye ni xan iya aikin nn, don Allah ki barni na fara kawae Ammi, nayi maki alkawarin baxan baki kunya ba kinji Ammina, " Ammi tayi shiru tana kallonta, can tace "shknn to Allah ya kai mu gobe," Aneesah tace "Ameen," cike da murna da jin ddi don ita so kawae take ta xana jarabawarta wnn shekaran da yardar Allah. Karfe goma da rabi Aneesah da Amminta suka isa kantamemen gidan da xata fara aiki a cikin garin Abuja, jikin Aneesah yyi sanyi sosai ganin gidan bana wasa bne don gidan ya hadu iyakar hadewa ga anguwar ma kadai abun kallone, maigadi da uniform din soja a jikinsa ya bude masu gate fuskarsa a tsuke yace "ku ne bakin da Hajiya tace xa su xo," Ammi tace "eh mune," ya nuna masu daga kusa da wani flower yace "to ku tsaya can tace ku jira ta a nn," Ammi tace "to snn suka dawo gefen shukan suka tsaya, Aneesah ta dinga masa wani irin kallo cike da jin haushin yanda yake masu maganar," yaje ya ba yaran gidan sako suce ma Hajiya masu aikin sun xo snn ya dawo bakin gate ya tsaya, Aneesah sun fi awa daya a tsaye wajen ga rana bbu hajiya bbu lbrinta, har sun firda ran fitowarta Ammi tace "muje kawae Aneesah," sae ga ta ta fito cikin shiga ta alfarma sanye da glass sae kamshi take a girme xata girme ma Ammi sosae ba kadan ba, ta dinga taku kmr baxata taka kasa ba ta iso kusa dasu tana masu wani irin kallon raini cikin isa da gadara tace "ina 'yar aikin," Ammi ta kasa cewa komai, sae Aneesah ce tace "gani," matar ta bude baki da dan mamaki tace, "wnn kwailar wani aiki xata iya hka, na yi xaton wata babba balagaggiya xaki kawo min malama," Aneesah ta dake tace "bbu abinda bana yi Hajiya, tun daga kan shara, wanke wanke, goge goge, girke girke, da duk aikin da kika sani Hajiya," Hajiyar ta tabe baki tace "yyi, duk wata dubu goma sha biyu nace xan dinga badawa kuma idan washing machine ya wanke ma babies dina kaya yau to gobe ita xata wanke masu, snn tun karfe bakwae xata xo aiki ta bar min gidana karfe shidda na yamma, ina fatan ku ba fulanin daji bne kun fahimce ni," Ammi tayi murmushi tace "mun fahimce ki Hajiya mun gode, amma karfe shiddan da kika ce Hajiya yyi dare don gidanmu da nisa sosai, ki rage kudin aikin in yaso sae ta dinga barin nn ko xuwa karfe biyar ne," hajiyar tayi masu wani kallo ta tabe baki tace "karfe biyar da rabi xata dinga barin nn period, idan hkn yyi maku to ta fara aiki daga dis vry moment, idan kuma bai maku ba ku ja tsumman rayuwarku ku fice min daga gida don ni bna kai wa wnn lkcn ina surutu da yan aiki talakawa irin ku," tana kaiwa nn ta juya ta shiga takunta cikin isa har ta hau balcony ta shige falo... [9:29PM, 12/21/2016] Khaleesat: 8...... Sumy ta mike da mamaki tana kallon yayarta Meenah don ita tsakani da Allah tayi maganarta ba wae don su yi fada ba, pretty tace "sumy ke kika fara neman tsokan gskya meye xaki hadata da wata banxa can kuma ma 'yar aiki, wae ta fita kyau" Meenah tace "ki kyaleni da 'yar walakanci kawae na faffasa mata baki ynxun nn....." ganin abun nasu na son ya xama fada sosai don sumy har ta fara kkrin cakumo yayartata tana cewa "to ki fasa min bakin kiga idan ban cire maki hkora ba ynxun nn nima," yasa Hajiya ta shige tsakaninsu da sauri tana basu hkuri, "haba bbies dina meye abun fada a nn iyye, kema sumy baki kyauta ba don me xaki ce wata tsinanniya can ta fi yayarki kyau idan ba tsokana ba," ta juyo tana kallon meenar tace "manta da ita meenah xolayarki take kinji, kuma ku kwantar da hankalinki indae mayyar 'yar nn ce wllh watan nn na kai wa karshe xan sallameta, ita wacece da xata dinga gasar kyau da daughters dina, ku kyaleni da shegiyar kawae kuje kuyi shirin birthday din da xaku kar lkci ya wuce," a hka ta lallaba 'ya yan nata suka hkura suka haye sama pretty na cewa "Allah ma yasa ba yau bne karshen xuwa partynmu" sumy tayi dariya tace "kuma fa hka ne wllh," hajiya tayi jigum tana tunani bayan tafiyar 'ya yan nata, ita kanta kyan Aneesah mamaki yake bata wani lkcn, yarinya hka sae kace aljana don kyau, anya ba plan aka yi mata da yarinyar nn ba kmr yanda su pretty suka ce ba, amma ta kusa kawo karshen komai idan Allah ya yarda wnn watan ne watanta na karshe a gidan taje can ta samu wani gidan tayi masu aikin ita kam ta yafe duk da ta san yarinyar ta iya aiki sosai uwa uba ga iya girki da tsafta, ta tabe baki a xuciyarta tace na sa a kawo mani wata balagaggiyar mummuna hankalina a kwance na 'ya yana a kwance, ta sake kwado ma Aneesahn dake tsaye a kitchen ta gama dukka aikinta na ranar amma tana tsoran tunkarata tace xata wuce, ta fito da sauri har tana tuntube ta durkushe gabanta tace "gani Hajiya," Hajiyar ta tabe baki tana hararta kmr xata makureta don tsana tace "idan kin ga dama gobe ki taho da Asuba don xaki hada ma son dina da xae dawo daga holland goben girki lafiyayyu, xakiyi masa fried rice da plantain kadan, sae farfesun kayan ciki da kaxa, snn ki hada masa cream salad, sae kuma kiyi masa cous-cous da miyar kwae, snn finally ki hada masa ginger drink mai kyau, daughters dina kuma kiyi masu jollof din taliya da naman rago da dan farfesun fish don sun fi son shi, ina fatan dae yhu re nt daft duk kin fahimce ni," Aneesah tace "nafahimta Hajiya," Hajiyar tace "tashi ki bani waje to, idan kinga dama karki xo da wuri ki ga rashin mutunci," Aneesah ta mike a sanyaye tayi mata sae da safe ta bar gidan [9:29PM, 12/21/2016] Khaleesat: ~Aneesah~ By khaleesah Haiydar 7.... Ammi ta girgixa kai a hankali tace "baxa ki iya ba Aneesah muje kawae," Aneesah ta xame hannunta a hankali daga rikon da Amminta tayi mata tace "xan iya Ammi, ki tafi gida kawae sae na dawo," bata jira abinda Ammi xata ce ba tayi saurin barin wajen ta bi kofar da Hajiyar ta bi ta shige cikin gidan tana karanto Addu'o'i cikin xuciyarta, ta ga kanta a wani makeken falon gske mai cike da kayan alatu da kayan more rayuwa " ya salam! Aljannar duniya knn," ta dinga bin falon da kallo a hankali gabanta na faduwa sae kace ba Nigeria ba, wnn wani irin aiki suke yi hka, gskya wasu kam sun more duniya, ta rasa inda xata bi don falon ba kowa sae karar Ac da wani ni'imantattcen kamshi dake tashi, ta kai minti kusan goma a tsaye tana naxarin komai na falon duk da wasu tana ganinsu falon baffanta, taji ana taka matakalan bene a hankali ana saukowa ta tsura ma stairs din ido tana jiran taga ko Hajiyar ce ke sauko wa, wata kakkyawar yarinya da baxa ta wuce ta ba ce ta sauko tana sanye da kayan bacci, yarinyar ta mitsike ido tana kallonta da mamaki, Aneesah ta kauda kanta, yarinyar cikin gadara tace "who re yhu," Aneesah tayi shiru bata ce mata komai ba sae wani irin kallo ma da take ma yarinya, yarinyar ta juya da sauri ta koma sama, sae ga ta ta dawo da momynta, Hajiyar tace "ohh House Maid dinmu ce pretty," Hajiya ta karaso kasa a walakance tace "bbyna xata xaga dake ko ina na gidan ta nuna maki duk aikin da xaki dinga yi, sae ki fara daga ynxu," ta kira prettyn tace "sauko bby ki nuna mata House chores din gaba daya," yarinyar ta sauko tana yatsine fuska tace "momy ni kayana xata fara wanke min kafin ta fara komai, don ni ynxu na daina gane wankin washin machine din nn, shi kuma iliya baya wanke min da kyau gugan ma na Hauka yake min," Hajiya tace "to maxa ki fito mata da kayayyakin taje bakin tap a kusa da garden ta wanke, ki hado mata da na sumy don naga kmr tana da kayan wanki ita ma," prettyn tace "na meenah fa," Hajiyar tace "A'a kinsan halinta tana iya cewa bata samu ba, kwaso mata naku dae kawae," prettyn ta juya da sauri ta haye sama, Aneesah dae binsu da kallo kawae take. Hajiya ma ta juya ta haye sama, bayan kmr minti goma sae ga prettyn da tulin kayan wanki ta watsa mata su a gabanta, Aneesah ta dinga bin kayan da kallo, cikin gadara prettyn tace "kuma yarinya ki tabbatar kin wanke mana kayanmu da kyau, suna bushewa kuma ki goge mana su, snn karki kuskura ki hada min fararen kayana da wasu kayan don idan suka dafe wllh sae kin siya min sabo," ta juya tana tana karkade jiki ta haye sama. Aneesah tace "hmm, ikon Allah," ta girgixa kai ta kwasa kayan da sabulae da omon da ta watsar mata ta fita daga falon ta shiga neman garden da kyar ta samo sbda girman gidan, ta ga bokitae da manyan robobin wanki a wajen ta tara famfo ba tare da bata lkci ba ta fara wankin, ba ita ta gama wankin nn ba sae kusan karfe daya, don kayan mugun yawa ne dasu, abun mamaki ma wasu bata ga alaman an sa su ba, ta juya bayan ta gama shanyan kayan tana kallon kudaden da ta dinga gani a wandunayensu da english wear tana ajiyewa gefe daya, ta kirga gaba daya kudin taga dubu biyar da dari biyar ce, tayi murmushi, rayuwa knn, ta dauki kudin da sauran sabulansu da omo sae jik, ta shiga cikin gidan, ta kusan cin karo da prettyn da ta ci kwalliya ta hade cikin riga da wando english wear ta sa spec da dan guntun mayafi xata fita, tayi ma Aneesahn wani irin kallon raina, ta bi gefenta xata fita Aneesah tace "ga wnn cikin kayanku na gani," ta juya tana kallon kudin da Aneesah ke mika mata ta mata wani irin kallo tana yatsine fuska tace "uwar me xan maki da shi, don me baxa ki xuba su cikin waste bin ba," tayi tsaki ta fice daga gidan. Aneesah ta bi ta da kallo da mamaki, ta yi hanyar dinning ta ajiye masu kudinsu a nn. Ta rasa me kuma xata yi gashi prettyn bata nuna mata ko ina na gidan ba, a hankali ta hau sama ta tsaya daga corridr din ta shiga sallama a hankali tana kare ma jerin dakunan kallo, ta kai minti biyar tsaye a wajen snn aka bude kofar da ke kallonta, hajiya ce ta fito cikin tsawa tace "wat! Kina da hankali kuwa, an ce maki 'yan aiki na hayo wa nn," a dan tsorace Aneesah tace "A'a hajiya na gama wankin ne ban san kuma me xanyi ba," cikin tsawa hajiyar tace "ko ma meye baki ga bell daga kasa da xaki danna ba" ta juya a sanyaye xata sauka, hajiyar tace "ko karamin kwakwalwarki bae baki cewa girkin rana xaki daura ba ynxu," Like · 4 · Report · 49 minutes ago [9:29PM, 12/21/2016] Khaleesat: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 7...... A wahale Aneesah ta dawo gida ranar daga aiki don yini tayi tana aiki kmr machine, Ammi dake tsakar gida a xaune tana shirin alwala don maghrib tayi ta mike tsaye da sauri tana kallonta tace "duk hankalina ya tashi Aneesa ina ta tunanin inda kika shiga, ba karfe biyar da rabi tace xaki dinga barin gidan ba, ya akayi kika kai har maghriba, ko takowa kika yi da kafa," Aneesah ta kirkiro murmushin dole tace " ban sami mota bane Ammi, amma tun karfe biyar da rabi na bar gidan," Ammi tace "Ayya, naga ma na manta ban baki kudin mota ba, sun baki can ne," Aneesah ta gyada kai kawae duk da ko naira ba a bata ba, kuma dama bata sa rai ba, ammi tace "ta maki mutunci Allah ya biyata, gobe sae na baki kudi idan xaki tafi, daxu mamarsu jamila ta ba ma yusuf dari biyar," Aneesah tace "Allah sarki, mun gode Allah ya saka da khairan," "to ya kika ga aikin Aneesah, ba wahala dae ko, kar fa ki cuceni ki cuce kanki, ki gaya min gskya bata tsauwala maki dae koh?" Ammi ta tambayeta damuwa bayyane a fuskarta, Aneesah tayi murmushin dole don duk jikinta ma ciwo suke mata sbda tsabar aiki tace "Nace maki Ammi matar na da kirki idan ka iya xama da ita, aiki kuma ba wahala Ammi " ammi tace "to shiknn Aneesah, Allah ya taimaka, yyi maki albarka," Aneesa tace "Ameen Ammina," snn ta mike ta shige cikin daki ta cire kayan jikinta. Washegari da sassafe Aneesah ta bar gida don ta isa gurin aikinta da wuri, duk da hka sae da Hajiyar ta dinga mata masifa kmr xata rufeta da duka wae tun daxu su sumy da pretty ke jiranta ta xo ta hada masu breakfst, tana yi su sumyn na taya ta har da ce mata matsiyaciya 'yar talakawa , Aneesah ta shiga kitchen a sanyaye hawaye na bin kuncinta tana tunanin hali irin na mutanen gidan karfe bakwae da minti arbain fa ta shigo gidan suke mata tijara hka, cikin minti talatin ta gama hada masu break din ta jera kan dinnin, suka ci suka yi kat, ta dawo ta kwashi kwanukan snn ta ci gaba da aikace aikacen gidan, da rana ta hada masu lafiyayyar jollof din taliya da kaxa sae coconout drink bisa ga umarninsu, snn ta fita driver ya kaita kasuwa siyo masu ice fish da kayan ciki, don farfesun su xata yi masu da yamma kafin ta tafi, ranar ma dae ba ita ta bar gidan ba sae karfe shidda. Hka Aneesah ta dinga wahala a gidan walakancin yau daban ta gobe daban, kullum cikin kuka take a gidan don har marinta Hajiyar nayi, ga wani muguwar tsana da babbar 'yarta meenah ke mata duk tabi ta sa mata ido a gidan da tayi mistake daya ta dinga yayyafa mata masifa knn tana xagi, ita dae Aneesa sae dae ta sunkuyar da kai don sun hanata hada ido da su, ko kuma ta durkusa, duk irin abubuwan da take fuskanta a gidan kin gaya ma Amminta tayi, kullum cikin pretend take duk da irin muguwar raman da tayi, fatanta ita dae kawae tayi wata biyu tana aiki ta tara kudin waec dinta tayi gaba, amma da ta karbi kudi karshen wata matsalar gida ke karar dashi don wani lkcn ma sae su kwana hka basu ci komai ba, sae dae Ammi ta tura yusuf makwabta yaci abinci, hkn yasa ta ji ta fara hkura da karatun ma kawae, indae ta hka xasu dinga samun abinda xasu kai baki, kuma duk da irin walakancin da taga akeyi da abinci a gidan da take aiki ko sau daya bata taba debowa tace xata kawo gida ba, don itama wani lkcin da yunwa take yini a gidan sae ta dawo gida xata ci tunda ba bata suka yi ba ita kuma bata daukan abinda ba a bata ba, da hajiyar ce ma ta lura da hka duk da walakanci da gadaranta ta kan tambayeta ita ta ci abincin idan sun ci sun yi kat da 'ya yanta, sae tace mata aa don ko dan dana masu abinci bata yi idan ta gama girka masu, hkn yasa Hajiyar ta ware mata wani plate daban wae idan ta xuba ma kowa har maigadi da karen dake bayan gidan ita ma sae ta xuba nata, Aneesah tayi mata godiya ta mike ta bar wajen. Ran da Aneesah ta cika wata biyu da sati daya a gidan tana kitchen tana wanke wanke Hajiyar ta kwado mata kira "Aneesah," idan tana kwala mata kira sae ka rantse kace ita ta rada mata sunan, Aneesah ta taho da sauri ta durkushe gabanta tace "Na'am Hajiya," Hajiyar ta galla mata harara tace "da kina jina mahaukaciya kika yi min bnxa," Aneesah ta girgixa kai tace "kiyi hkuri Hajiya na bude famfo ne shiyasa banji ba," hajiyar ta daka mata tsawa "da yake kunnenki na ciwo ne ko 'yar walakanci," Aneesah tayi shiru bata ce komai ba, hajiyar tace "tashi ki ban waje raina ya daina baci shegiya kawae, anjima kya ji abinda xan gaya maki idan xuciyata ta huce," Aneesah ta mike a sanyaye ta bar wajen hawaye cike idonta, tana barin wajen meenah tace "wllh na tsani yarinyar nn mum, bata fa yi kama da 'yar aiki ba, ni ban ma yarda da ita ba kila wllh aikota gidan nn akayi ko kuma plan aka yi da ita, ji ta fa kyakkyawa gata fara, ni ban ga alamar ta taba aiki ba ma," sumy tace "ke dae bari kawae, kinga fa jiya da nake ta kallonta na kalli naga bbu abinda xaki nuna mata sae hasken bleachn," meenah ta mike a fusace tace "kika ce me, to ke din an ce maki kyau gare ki, wllh 'yar aikin nn tafi ki kyau sau dubu." [9:30PM, 12/21/2016] Khaleesat: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 11...... Wani gigitattcen mari Hajiya ta kai mata tana ball da ita a fusace, "don uwarki ke dabbar wace gari ce, baki da hankali ne xaki bata masa jiki hka da drink muguwa kawai," shi ko Haiydar mikewa yyi da sauri ya bar wajen ya haye sama, kuka ta dinga yi tana ba hajiyar hakuri tana cewa bata sani ba, amma hkn bae sa matar nn ta kyaleta ba, don marinta ta dinga yi son ranta, har ta gaji snn cikin tsawa tace "bace ki ban waje mahaukaciya kawae," da kyar Aneesah ta bar falon tana ganin jiri, a daddafe ta shiga kitchen ta jingina jikin fridge ta dinga kuka a hankali, ganin tsayuwar baxae mata ba yasa ta bude kofa ta shiga garden ta xauna ta hade kanta da gwiwa tana ci gaba da kukan takaici, wnn wace irin bakar rayuwace ita kam, ta kai minti kusan sha biyar a wajen tana ta aikin kuka, taji an dafa kafadarta a hankali, ta dago a tsorace taga wanene, xuciyarta ya kusan shigewa cikinta ganin ko waye, ya xauna gefenta yana kallonta ta matsa a tsorace tare da kkrin mikewa ta bar wajen ya rikota, a gigice ta tura hannunsa tace "nashiga uku, malam ka rufa min asiri don Allah don annabi ina rokanka," ya ki sakinta a hankali yace "to xauna kiji abinda xan ce," ta shiga waige waige a tsorace tace "kayi hkuri nace don Allah," ya wara mata manyan idanunsa yace "sae kin fara saurarata," ta sulale kasa gefensa don yaki sakinta har lkcin, hawaye na bin kuncinta tace "bka ma Allah knn" ya girgixa mata kai a hankali yace "ina yi masa," snn ya ciro handkercheif ya dafe kanta da hannunsa ya shiga goge mata hawayen fuskarta ta kauda fuskar da sauri xata mike tsaye, yyi saurin matsowa kusa da ita ya sakale hannunsa a wuyanta ya ci gaba da goge mata fuskar, ta tsorata sosai don tunda take ba a taba mata hka ba, ta fara kkrin kwace kanta tana cewa "nashiga uku meye hka malam," muryar Hajiya suka ji a kitchen tana cewa pretty wae ina Haiydar ya shiga ne, tace "momy nima shi nake nema har ynxu yaki bamu tsarabar mu fa, ita kuma wnn yarinyar taki taxo ta ba mutane abinci har worm din cikina sun fara cinye min fatar cikin " Hajiyar ta kwala mata kira da karfi "Aneesah!" Aneesah ta turasa da karfi muryarta na rawa tace "innalillahi, wayyo Allahna ka rufa min asiri don ya rasulillahi," ya saketa ya mike da sauri ya xaga yyi hanyar garage, ita ma ta mike da sauri ta bude kofar kitchen ta shiga suka kusan cin karo da Hajiyar... [9:30PM, 12/21/2016] Khaleesat: ~ANEESAH~ By Khaleesah Haiydar 9...... Aneesah ta gama shiri karfe shidda da rabi xata bar gida, Ammi dake xaune kan darduma har lkcn ta bi ta da kallo da mamaki "kina da hankali kuwa Aneesah, ina xaki da sassafen nn hka," Aneesah ta xauna gaban Amminta tana kallonta tace "ae nayi maki bayani Ammi, xasu yi baki ne yau, xan masu girki da dan yawa shine tace naxo da wuri," Ammi ta harareta tace "shine ko karfe bakwae bai karasa ba xaki fita, ina laifin ki bari karfe bakwan,ko fa karyawa baki yi ba " Aneesah tace "A'a Ammi ynxu xan wuce, da wuri bakin xasu iso ne fa," Ammi tace "to ki sha kokon kafin ki tafi," Aneesah tace "ohh Ammina ni bana jin yunwa idan naje can ma ai suna bani wllh," ba dan ran Ammi ya so ba ta bata kudin mota tayi mata Allah ya kiyaye snn ta bar gidan ta kama hanyar gidan aikinta. Ko da ta isa gidan duk bacci suke basu tashi ba, ta danyi share share da goge gogenta tayi mopping ko ina, snn ta hada masu breakfst kafin su tashi ta jera kan dininn, tukunna ta fara girke-girken da aka lissafa mata jiya da yake akwae kayan cefanen gaba daya a fridge. Ba ita ta gama girkin ba sae kusan karfe sha daya don ma gas biyu ta kunna, da electric cooker, ko da ta gama sae da ta fara gyara dinning din da suka yi breakfst ta kwashe duk kwanukan, ta gaisar da yan gidan gaba daya, snn ta fara jera sabon girkin da ta yi a dinning din, ta saka ginger drink din a fridge yyi sanyi, tana goge gogen kitchen taji sun fito gaba daya su ukun sun hade cikin kananan kaya suna ta murna xa su je dauko yayansu a Airport, Hajiyar ta rakasu har bakin mota suka ce da kansu xasuyi driving basa son driver ya jasu, tayi masu Allah ya kiyaye ta shigo gidan tana kwala ma Aneesah kira, Aneesah ta fito da sauri ta durkusa gabanta tace "na'am Hajiya gani," "kiyi maxa kije ki gyara masa bedroom dinsa ki canxa bedsheet,ki tabbatar ko ina yyi fes snn ki shiga nawa bedroom din ki gyara " Aneesah tace "to Hajiya," snn ta mike ta bar wajen ta hau sama ta shiga yin aikin da ta sa ta. Cikin awa daya ta gama komai ta sauko downstairs, Hajiyar na falonta tana waya, tana shiga kitchen taji shigowar motarsu, pretty ta shigo da gudu tana dariya ta dinga kwala ma momynsu kira wae taxo taga yayansu, Hajiyar ta fito da sauri suka hade dae-dae bakin kofa ta rungume dan nata cike da farin ciki da murna tace "waw my son ya hanya," shi ko ya hade rae "don Allah ku bar ni naji da gajiya na mana mum, su kuma wa innan sun tashi sun kwashi jiki sun bi ni Airport kamr wasu mahaukata " meenah ta dan tabe baki tace "dan ma ka samu ana farin cikin dawowarka, wllh momy tun a airport yake ta gwasale mu sai kace dole, ni da nasani ma da baxan je ba," ya juya yana kallonta yace "to uwar waye yace da ki xo din munafuka, kin tashi kin yi shiga kmr mai shirin tsallaka wuta kin bini airport, wae ma ban hana ku sa irin wa in nan kayan ba, har da ke ko Zainab," ya fadi yana kallon pretty, sumy ta tabe baki ta dan yi tsaki ta haye sama hka ma meenah da ta shiga gunguni, pretty tace "kayi hkuri yayana," Hajiyar ta hade rae ita ma "kaga matsalata da kai knn Haiydar ba dawowarka ba takura ma 'ya yana, gskya baxa mu shirya ba wnn karan, kawae bbu ruwanka ka sa masu ido duk me kaga suna yi," yace "Allah ya baku hkuri," snn ya haye sama pretty ta bi shi a baya, Hajiyar ma ta bi sa ganin kmr ransa ne ya bace, duk wnn abunda suke Aneesah na jinsu, sae abun ma ya bata dariya, a xuciyarta tace "Allah ya kyauta da irin wnn familyn, don tun da taxo gidan ita kam bata taba ganin mai sllh cikinsu ba, sae dae Hajiyar ita ma idan lkci ya wuce, ita ko dama bata isa tayi a cikin gidan ba sae dae taje garden. 14 mins · Khaleesat Haiydar... [9:30PM, 12/21/2016] Khaleesat: Aneesah.... By Khaleesah Haiydar 10.... Bayan minti Ashirin Aneesah na xaune cikin garden, don bbu aikin da xata yi a lkcn sae kuma xuwa anjima, da yake akwae kofa ta kitchen da xae sada ka da garden din tanan ta bi ta fita, Hajiya taji tana kwada mata kira ta shigo gidan da sauri ta durkusa daga bakin kofar kitchen din tace "gani Hajiya," ta galla mata Harara tace "gidan ubanwa kika shiga nke ta faman ihu kmr makogwarona xae fito?" ta sunkuyar da kai tace "kiyi hkuri Hajiya ina daga waje ne," ta daka mata tsawa "da'allah tashi ki ban waje muguwar yarinya kawae nasan kasheni kawae kike son yi abinda na haifa ma basu kasheni ba shegiya kawae," Aneesah ta mike a sanyaye xata bar falon sae a lkcn ta kula gaba dayansu har yayan nasu ma na falon, su sumy da meenah suka tuntsire da dariya suka dinga yi, shi dae hankalinsa na kan laptop, pretty na jikinsa tana kallon abinda yake yi, Hajiyar ta kara da cewa "kuma idan kinga dama ki dauko ma son dina ginger drink a fridge," ta juya ta shige kitchen din da sauri, sae a snn ya dago kai yana yatsine fuska yace "ita ce ta hada drink din mum?" Hajiyar tace "eh ita ce ta hada, ta iya sosae son, snn tana da tsafta shi yasa ma nace tayi," ya gyada kai yace "tab! Ku bar shi kawae bna sha, ynxu momy fisabilillahi mai yaran nn suke da sae wata 'yar aiki can xata hada min abinda xan ci, wae meyasa ku ke hka ne mum, meye amfaninsu idan basu yi a nn ba ina xasu je su yi, knn kuna nufin ita ce ma tayi min girkin da xan ci," Hajiyar tace "kayi hkuri son, naga basu iya bne, shi yasa na sa ta tayi maka, amma ai ba komai sae na tashi da kaina na yi maka ynxun nan," yace "A'a ku barshi kawae bana so, ngd" Aneesah na tsaye a kitchen duk tana jinsu gabanta ya shiga faduwa, ga hawayen da yaki tsaya mata, to ynxu kai masu gingern xata yi ko bari xata yi, jin bbu wanda ya sake cewa komai ne yasa ta daura drink din a faranti da cup ta dauko ta fito falon a sanyaye ta tsaya daga bayan kujera a hankali tace "na kai dinning ne Hajiya ko nn xan kawo," hajiyar ta watsa mata wani mugun kallo tace "ke kurma ce lkcn da yace bae ciki da harkan kaxanta," ta dago kanta a raunane tana kallonsa ga hawayen da ya taru a idonta suna shirin gangarowa hkn yasa cikin idonta ya dinga kyalli gabanta yyi mugun faduwa dai-dai lkcn da shima ya dago kansa ya sauke manyan idanuwansa kan nata, da sauri ta kauda kanta ta juya xata shiga kitchen din, da sauri taji yace "momy ta kawo xan sha am vry thirsty," murya can ciki yyi maganar, Hajiyar ta sake kwado mata kira ta dawo, tace "ki kawo masa drink din, ya ya iya tunda yana so," ta tako a hankali ta shigo falon ta durkushe gabansa ta ajiye trayn, har lkcn kallonta yake yana son kara kallon cikin idonta amma taki bari su hada ido kuma, ta mike xata bar wajen hajiyar ta daka mata tsawa "ke wacce irin dabba ce, brain dinki bai baki cewar xuba masa a cup din xakiyi gaba," ta koma ta durkusa ta shiga xuba masa drink din a kofin, tana gama xubawa taga ya miko hannu ta dago tana mika masa ba tare da ta kallesa ba ga wani mugun bugawa da xuciyarta yake, shi ko so yake kawae ya kalli kwayar idonta hkn ne ma yasa ya mika mata hannu amma Aneesah taki dago kanta, jin dumin hannunsa a nata ne ya sa ta sake masa kofin da sauri ta mike xata bar wajen, ashe bae rike kofin ba ya fadi, juice din gaba daya suka xube jikin farin three quatren jikinsa, ta koma baya a tsorace ta dafe kirji tace "innalillahi nashiga uku wllh ban sani ba" [9:30PM, 12/21/2016] Khaleesat: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 12..... Aneesah ta dan koma baya gabanta na faduwa ga tsoro, cikin tsawa Hajiya tace "uwar me kike yi a nn," muryarta na rawa tace "A'a wae da ruwa nake son na ba flower naga kuma rana yyi," Hajiyar tace "da wani gulman ne ya hanaki yin hkn tun da safe, kin wuce kinyi serve din abinci a dinning ko sae na cire maki wnn mayun idanuwan naki," a raunane Aneesah tace "kiyi hkuri Hajiya," Hajiyar ta galla mata harara tace "idan bana hkuri dake da baki kasheni ba ynxu," taja dogon tsaki ta bar wajen tana cewa "nima dae bana daddara da wa innan matsiyatan 'yan aikin wllh, ya'yan ka basu sa ka magana ba bare ihu su suyi ta saka, da na bi shawara Haiydar ma baxan karbesu gidan nn ba, amma na kusa kawo karshe hka," Aneesah ta bi bayanta jikinta a sanyaye ta shiga falon, duk 'yan matan na kan dinning suna jiranta, ikon Allah ga su ga abincin fa a gabansu amma dole sae an samu me xuba masu sbda tsabar lalaci da gantalewa, Hajiyar ma ta ja kujera ta xauna tana jiran Aneesar ta xuba masu, Aneesah ta karaso dinning din bayan ta wanke hannunta ta shiga tambayarsu abinda xasu ci suna bata amsa a walakance cikin gadara ita kuma tana xuba masu, wani ma sae ta gama xuba masa xae ce bashi yake so ba kuma ta xuba masa wani, tana cikin xuba ma Hajiyar Haiydar ya sauko kasa ya karaso dinning din ya ja kujera ya xauna yana kallon idon Aneesah, tana gama xuba ma Hajiyar ta juyo inda yake ba tare da ta bari idonta ya hadu da nasa ba tace "me xan xuba maka......" a hantare Hajiya tayi saurin katseta tace "'yan aiki basa serve dinsa, shi da kansa xae xuba kayansa, ki bace mana da gani kar mu kware," ta sunkuyar da kanta ta juya xata bar wajen yyi saurin cewa "A'a ta xuba min mum na gaji dayawa," Hajiyar ta juyo tana kallonta tace "sae ki dawo ki xuba masa," a hankali ta tako har inda yake a xaune ta ja plate ba tare da ta kallesa ba tace "me kke son na xuba maka," ya tsura mata manyan idonsa yana kallonta amma taki kallonsa kanta na kasa, a hankali taji yace "to ae bn san me dame aka girka ba nn" shi dae so yake kawae su hada ido, amma ba tare da ta kallesa ba still tace "akwae fried rice da plantain, cous-cous da miyar kwae, jollof din taliya, farfesun kifi, farfesun kayan ciki da na kaxa, sae cream salad," yyi shiru yana kallonta, gabanta ya shiga faduwa, kar dae ya sake ja mata wani dukan ta dan juya ta sacii kallon hajiyar dasu meenah taga dukkansu hankalinsu na kan abincinsu, pretty kadae ce ke kallonsu, ta sunkuyar da kai tace "ina fatan ka fahimceni, me xanyi serve dinka," taji yyi mata shiru, hkn yasa ta dago kanta a hankali tana kallonsa, suna hada ido taga ya wara idanunsa yyi murmushi alamar jin ddin sun hada ido, dama idonta kawae yake son ta daura kan nasa, ta hade rae ta kauda kanta, murya can kasa yace "ke me kika ci?" ta hararesa a hankali tace "wnn ba matsalarka bace malam," yyi murmushi bai ce komai ba, Hajiya ta dago tana kallonsu tace "A'a har ynxu bata xuba maka bne son, ko duk abincin basu maka ba ta girka maka sabo," ya girgixa mata kai yace "A'a taje kawae anjima sae taxo ta xuba min," yana fadin hka Aneesah ta juya ta fara sauka daga dinning din Hajiya ta daka mata tsawa "ke! Ke wace irin yar kauye ce,uban wa ya baki ixinin wucewa daga yayi magana sae kiyi gaba kmr wata tababbiya," yace eh xata iya wucewa mum, anjima xan nemeta," Hajiyar ta galla mata harara taci gaba da cin abincinta. Haiydar bae tashi kiran Aneesah taxo tayi serve dinsa ba sae da kowa ya watse daga dinning din suka haye sama, ta karaso dinnin din ba tare da ta kalli inda yake ba fuskarta a hade tace "me xan xuba maka," ya mike tsaye yana kallonta yace "nace ke me kika ci," ta galla masa harara gabanta na faduwa don tsoro yake bata tace "ina ruwanka malam, ni kaji dani na bar nn wajen," ya dan kalli hanyayr stairs ko wani na xuwa ya ga ba kowa, ya fixgota yace "ae sae kin gaya min me kika ci ke idan ba hka ba sae dae mu kwana nn" ta tsorata sosai jikinta ya dauki rawa lkci daya ta fara hawaye muryar ta na rawa tace "nashiga uku na lalace ka rufa min asiri ka rabu dani wllh ni ba 'yar iska bace," hkn ya basa dariya, ya wara mata ido har lkcin hannunsa na kan kafadarta yace "dagske" ta gyada masa kai tana hawaye sosai, ya sake ta yace "to xo ki xuba min fried rice da plantain din," jikinta na rawa ta xuba masa abinci don duk ya tsoratata, tana gama xubawa kuwa ta juya xata bar wajen yyi saurin kamo hannunta ya dauki plantain daya ya sa a baki snn ya dauki wani ya kai bakinta yace "ina xaki kuma, ae dolen ki ma tare xamu ci, idan ba hka ba wllh baxa ki bar nn ba, kin dae ji nace wlh, oya bude bakin" ta dafe kirji tayo waje da ido tace "ni? Ka rufa min asiri wllh wanke wanke xanyi na koshi," ya mike tsaye ya tsaya gabanta yana kallonta ta koma baya ta jingina jikin fridge a tsorace tana hawaye, yyi murmushi yace fridge din xaki shiga, Ta fashe da kuka tace, "kanae ma darajan Allah ka rabu dani nace mka wllh ni ba 'yar iska bace, ka tausaya ma rayuwata ka rufa min asiri ka kyaleni" [9:30PM, 12/21/2016] Khaleesat: haleesat Haiydar's post Khaleesat Haiydar ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 13...... Haiydar yyi murmushi yana kallon cikin idonta yace "to bude baki na sa maki plantain sai ki wuce," ta fara waige-waige a tsorace tana kkrin barin jikin fridge din don dab da ita yake har tana iya jin breathin dinsa a fuskarta, yyi saurin sa hannu ya tokare hanyar da xata bi, ta marairaice murya kmr xata yi kuka tace "A'a ni na koshi," yace "ashe dae baxa ki bar nn ba yarinya," ganin da gske yake yasa ta bude bakin a hankali yana kallon kwayar idonta ya saka mata plantain din a baki, ta shiga taunawa a hankali yana mata wani irin kallo, ya matsar da ita daga jikin fridge din, ta fixge hannunta da sauri xata bar wajen, ya maxa ya rikota yace "baki isa ba tukun," ya na rike da ita ya bude fridge din ya dauko chill hollandia yoghurt, snn ya maidota jikin fridge din ya jinginar, ya bude drink din ya xuba cikin glass cup, ya kai mata baki, ta kauda kai da sauri ya hade rai yace "Allah baxa ki bar nn ba idan baki sha ba" kuka ta dinga yi tana rokansa ya kyaleta ta wuce, amma yaki sakinta wae sae ta sha hollandian, ganin ba sarki sae Allah ne yasa ta bude bakin a hankali ya shiga bata drink din tana sha, muryar Hajiya suka ji daga sama tana cewa " wae Aliyu ya fita ne meenah," a tsorace Aneesah ta turasa ta durkushewa wajen tace "nashiga uku na lalace," shi kuma yyi saurin juyawa ya koma dinnin ya xauna, dae-dae nn Hajiyar ta karasa saukowa da meenah, idonta ya sauka kan Aneesah da har lkcn ta kasa mikewa tsaye daga wajen, cikin tsawa tace "ita kuma warcan me take min jikin fridge hka," Haydar yyi saurin cewa "No ni nace ta bude ta kawo min drink, tace "Ayyo" snn ta karaso dinning din ta xauna tana cewa "har yanxu baka gama cin abincin ba son," Aneesah ta dauko hollandian da ya ajiye mata gabanta duk ta rude tama rasa abun yi ta hado da cup din ta dan risina ta ajiye masa gabansa kan dinin table din ya kashe mata ido ya bita da kallo ta bar wajen da sauri har tana tuntube. Ranar cikin rashin kuzari ta isa gida ta xube kan katifa, Ammi ta tambayeta lfya, tace kawae kanta ne ke ciwo, Ammi ta bata magani bayan ta sa ta gaba taci tuwon da tayi masu, snn taje tayi wanka tayi sallah ta koya ma yusuf assignment dinsa, ta danyi karatun qura'ani har karfe takwas, snn tayi sallahn isha tayi ma Ammi sae da safe ta kwanta duk da ba bacci take ji ba, kawae abun duniya ne ya isheta, ita kam duk aikin ma ya gama sare mata xuwan Haiydar, su dinga dabi'a irin ta nasara kmr wa inda basu da ilimin addini, ita a al'adarsu ta hausa fulani bata ga namiji na taba macen da ba muharramarsa bace, gskya ta kara tabbatar da cewar gidan nn basu da tarbiya, in Allah ya yarda aikinta ya kusan xuwa karshe a gidan, xata sa Ammi ta samo mata wani wajen daban da xata dinga aiki, baxata je ya cuceta a bnxa ba don bae mata kama da mai kamun kai ba. Hka Aneesah ta dinga aiki a takure a gidan, don Hydar duk ya bi ya sa ta gaba, indae yana gidan to bata da kwanciyar hankali don kawae sae dai taji mutum tsaye a bayanta, in tana garden to shima yana can, shi dae kawae so yake yaji lbrinta wae bata yi kama da 'yar aiki ba, kuma yasan tana da ilimi both, sau dayawa ya kan mata turanci don ta maida masa, amma ko sau daya bata taba mayar masa ba, sae dae ma tayi kmr bata ji mai yace ba, da ya kawo mata xancen yana son sanin ko ita wacece sae tace masa ba matsalarsa bace wnn, in kuma ta tashi serve dinsa abinci to sae ya tilasta mata ta ci abincin da ta xuba mashi, duk ya bi ya tsorata ta a gidan kuma duk wnn abun da suke ko sau daya Hajiya bata taba lura ba, hka ma yan matan gaba daya, yau ma kmr kullum tana xaune garden tayi xurfi cikin tunaninta bayan ta gama duk aikin da xata yi a gidan, ita kam kila yau ce rana ta karshe da xata kara aiki a gidan, don bata ga dalilin da Haiydar xae takura mata a kan sae yasan ko ita wacece ba, ga abun Hajiya sae gaba yake karawa ta rasa abinda tayi masu ba ita ba ba 'ya yanta ba, in ta tashi tafiya yau kawae ce mata xatayi ta bar aiki, ta gaya mata ranar da xata xo ta karbi kudun aikinta na rabin watan da tayi, idan kuma tace baxata bata ba, shkkn ta bar masu, tayi tagumi tana kallon tsuntsaye tana tunanin ko shawarar da ta yanke yyi taji hannun mutum a wuyanta, ta juya a fusace ta dan matsa cikin fada ta fara magana "wae meye hka malam, bana son iskanci ka rabu dani nasha gaya mka ni ba 'yar iska bace," ta mike ta shige kitchen ya bi ta da kallo, ko da ta shiga gidan ta tarar su Hajiya sunyi shiri xasu fita, tana cikin goge masu takalman da xasu sa ya shigo falon, fuskarsa a daure ya xauna kan kujera Hajiya ta shiga tambayarsa me yafaru bai tanka mata ba, tace "xamu fita son amma ni ba dde wa xanyi ba ynxu xan dawo," ya gyada mata kai kawae yana kallon Aneesah da gabanta ya shiga bugu da sauri, suna fita kuwa ita ma xata bar gidan tana gani, ya hade rai yace "ya ma kike da suna" ta juya tana kallonsa tace "Ni," hajiya ta haureta tace "to da uwarki ce idan ba ke ba" a hankali tana hawaye tace "Aneesah," yace "gud, bedroom dina xaki gyara min idan kin sallamesu [9:30PM, 12/21/2016] Khaleesat: Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 15..... Aneesah tayi shiru tana kallonsa ta kasa cewa komai, ya gyada mata kai yace "am ol ears," ta sunkuyar da kanta a hankali tace "Abbana ya rasu, Ammi ta ce kawae sae kanina yusuf" sae ga wani sabon hawayen tana yi, ya girgixa mata kai yace "a'a bance kiyi min kuka ba Aneesah," ya sa handkerchief ya goge mata fuskar snn yace "go on momyna" ta sunkuyar da kanta a hankali ta fara basa lbrin rayuwarsu tun daga rasuwar abbanta har ixuwa ynxu da yake xaune kusa da ita, tayi kuka sosai kmr ranta xae fita, ya xuba mata ido yana kallonta ya kasa cewa komai, ta goge fuskarta ta mike xata bar dakin ya kamo hannunta ya maido da ita ya xaunar, a hankali cikin nutsuwa ya fara magana "shi baffan naku a wani anguwan yake, snn relatives dinku mae suka ce dangane da abinda yyi, kuma wish din Abbanku knn ya rike maku gadon ku har ku mallaki hankalinku ko tsarinsa ne, snn me abokanan abbanku suka ce game da hkn, Abbanku na da lauya ko bae da??" Aneesah tayi murmushin da bata shirya ba xata yi magana suka ji muryar Hajiya downstairs, ta mike a tsorace tana kallon agogo, karfe uku har ya wuce, tace "nashiga uku na lalace," ya mike da sauri ya koma kan kujera yace ta cire bedshit din, jikinta na rawa ta cire bedshit din, dae-dae nn Hajiyar ta shigo dakin tana kallonta da mamaki cikin tsawa tace "ynxu shegiyar yarinyar nn baki girka abinda nace maki ba, gyaran dakin ne tun daxu," Aneesah ta fara kame kame a tsorace xata yi magana Aliyu ya riga ta "A'a aikenta nayi mum, bata dde da shigowa ba nace ta wanke min bathroom kafin ta gyara dakin," Hajiyar tace "Ayyo," snn ta galla mata harara ta ja kujera ta xauna tana kallon Haiydar din da damuwa tace "wae son ya maganar companies din Abbanku na lagos ne, kasan fa mutane basu da tsoran Allah tun da mahaifinku ya rasu Haiydar sau biyu ka waiwaye lagos," cikin fada ya fara mgana yana kallonta "to wae mum so kuke na kasa kai na ne, meye hadin barrister da wani bussiness can, ni ynxu cases din dake gabana ma sun fi karfina, su Amina da sumayya uban me suke yi ba abinda suka karanta ba knn, sun gwammace su yi ta gantali a garin Abuja," ya jawo laptop dinsa ya kunna ba tare da ya kara kallonta ba, tace "to kayi hkuri kuma fa gskya ne," Aneesah ta gama gyara gadon ta fita ta bar masu dakin tayi hanyar kitchen daura girkin da aka sa ta. Karfe shidda ta dauki hijab dinta tasa xata tafi gida, ta durkusa gaban Hajiya gabanta na faduwa ta dai yi shahada tace "Hajiya ina son ajiye aiki daga yau, idan yaso sae ki gaya min randa xan xo karban kudi na na rabin watan da nayi aiki," Hajiyar ta shiga mata wani irin kallo snn tace "gidan uban wa xaki da xaki ajiye aiki," ta girgixa kai a hankali tace "ba inda xani," cikin tsawa Hajiyar tace "baki isa ba to muguwa, a gidan uwarki ake hka, kinsan xaki tafi tun da can baki gaya min ba na samo wata sae ynxu da rana tsaka, kuma wllh baki karasa min aikin wnn watan gaba daya ba baxan baki kudin rabin watan ba, snn sae kin tsaya har an samo min wata yar aikin idan ba hka ba in na maki Allah ya isa sae ya biki wllh, tunda ban san ubanda xai dinga min aiki ba idan kika tafi bbu wata," a hankali tace "to xan jira ki samo wata 'yar aikin," Hajiyar tace "oho dae ya rage naki muguwa kawae" jikinta a sanyaye ta fita daga gidan, ta tarda Haiydar bakin gate a waje yana tsaye da alamar ita yake jira, ya karaso kusa da ita yace "lemme drop yhu," ta hade rai tace "A'a ngd" ya harareta yace "baki isa ba," tace "Allah bana so" bata sake jiran me xe ce ba ta kama hanyar gida da sauri da sauri. Tana isa gida tayi wanka tayi sallah ita da Amminta da yusuf, suna cikin cin abinci karfe kusan bakwae da rabi, suka ji ana bubbuga kofa daga can waje kmr xa a balla, duk suka yi tsit suna kallon bakin kofar dakin, aka shigo gidan aka banko kofar dakin, baffa shehu ne, ya tsaya yana hura hanci yace "ikon Allah, na sami lbrin abin kunyan da kuke yi a gari ke da tsinanniyar 'yar ki maryam, ynxu sbda tsabar butulci irin naku da rashin godiyar Allah duk abinda nake maku sae kin tura yarinyar nn karuwanci," Ammi tace "karuwanci kuma yaya, to Allah ya saka mana," cikin tsawa yace "sharri nai maki munafuka, idan ba shi kuke yi ba ubanwa ke ciyar daku tunda ni dae na fi wata uku bnga kun xo gu na maula ba, kuma a gari naji wnn xancen ana ta yayada wa, kuma gashi na xo na gani da idona wae kune da cin shinkafa da miya da nama yau," Aneesah dae abincin ta kawae take ci, Ammi ta goge hawayen dake xubo mata tace "in'sha Allahu sae Allah yyi mana shari'a daku ranar gobe kiyama," haba kamar kar ta fadi hka baffa ya dinga bala'i yana yo wa kanta kmr xae mareta, ita dae kanta sunkuye yake tana hawaye, hka ma Aneesah da ta kasa daure wa ta fashe da kuka, kmr daga sama suka ga an wullo torch light ya kwalesa da karfi a ka, ya dafe wajen yana salati a gigice, yusuf ne ya jefesa yana huci yace "xan fasa maka kai na cire maka hakori idan ka sake sa Ammina da Antyna kuka," ya karasa bakin kofar da gudu ya rufe masa kof[truncated by WhatsApp] [9:30PM, 12/21/2016] Khaleesat: ~Aneesah~ By khaleesah Haiydar 14..... Aneesah ta dago a hankali tana kallonsa hawaye na bin kuncinta, shima ya tsura mata manyan idonsa, Hajiya tace "idan kinga dama kina gama gyaran bedroom din ki girka mana fried rice da cream salad sae farfesun naman rago da coconut drink, kuma kiyi dayawa don xan yi baki daga lagos anjima, muryarta a dashe tace "to Hajiya," su meenah dama tuni suka fita suna jiran Hajiya a mota, Hajiya ta juya tana kallon pretty dake kwance gefen yayanta tace "ke baxaki je bne bby," ta dan yatsine fuska tace "na fasa xuwa momy xan taya yayana hira," Haiydar yyi saurin cewa "A'a nima fita xanyi, tashi kawae ki bisu," ta xumburo baki tace "to ba sae mu fita tare ba," ya galla mata harara yace "nace ki tashi ki bisu don bbu inda xan kai ki," gaban Aneesah dake durkushe bayan ta gama goge ma Hajiya takalmanta ya shiga bugu da sauri, lallai suna fita kuwa ita ma xata bisu a baya don bbu abinda xae kai ta dakinsa, dama yau ai take son ajiye aikin, Hajiya ta bude baki tana kallonta bayan ta gama sa takalminta cikin tsawa tace "wae kina nn xaune ne har ynxu wnn dabbar yarinyar," ta mike tsaye da sauri jikinta a mace tayi hanyar kitchen, ta sake mata wani uban tsawan tace "gidan ubanwa xaki," a tsorace tace "girkin xan daura," ta fixgota a fusace ta kai mata mari tace "don uwarki kin gyara masa bedroom din ne," cikin kuka tace "A'a ynxu xan gyara," Hajiyar ta wurgar da ita hanyar stairs tace "kuma ki bari na dawo naga bbu girkin da na saki wllh sae na kusan sumar dake yau tunda kince ke bakya jin magana," duk wnn abun da suke Haiydar na kallonsu bai ce komai ba, tana kuka ta hau stairs din tayi hanyar bedroom dinsa da kyar don har wani jiri take gani don tashin hnkli, tana shiga bedroom din ta ga ko ina a gyare, TV na aiki hka ma A.c dakin sae kamshi yake, sae laptop dinsa da files dake kwance kan gadon, tun bayan ranar da xae dawo da ta gyara masa daki bata sake shigowa dakin ba sae yau, kullum da safe pretty ce ke gyara masa daki don yarinyar na bala'in son yayanta, Aneesah ta goge hawayen da ya kasa tsaya mata, tasan ba alkhairi yake nufi da ita ba, tana jin budewar gate alamar su Hajiya sun shiga mota xasu fita ta juya da sauri ta yi hanyar kofar dakin don dama hka take jiran ji kafin ta fita daga dakin daga nn kuma ta bar gidan ma gaba daya, tana isa bakin kofa ya riga ta bude kofar ya shigo dakin, ta fasa ihu a tsorace ta koma baya tana xaro ido, bae juyo ya kalleta ba har sae da ya kulle kofar dakin, ta fashe da kuka tana komawa baya murya a raunane ta fara magana, "don Allah don Annabi don darajar iyayenka ka tausaya ma rayuwata ka rufa min asiri wllh ni marainiyace, ka taimake rayuwata ka ceceni ka kyaleni, nayi maku alkawarin xan bar maku gidanku plss am beggin" tana magana ne tana kuka sosai tana komawa baya shi ko binta kawae yake har ta isa jikin bangon dakin ta sulale kasa ta sa hannu ta rufe fuskarta jikinta na rawa tana ci gaba da rusa kukanta, ya durkusa gabanta yana kallonta snn yace "idan kin gama kukan, tashi ki xauna nn magana xa muyi," ta dago kanta a tsorace tana kallonsa ya nuna mata kan gado, ta girgixa masa kai ta kasa cewa komai, hkn yasa ya koma kan gadon ya xauna, ya danyi shiru na wani lkci snn yace "idan kika bani hadin kai nasan ko ke wacece ba ddewa xakiyi a dakina ba, don hka kiyi save din tym dinki duk tambayar da nayi maki ki bni amsa, kuma ki bar tsorona ni bbu abinda xan maki, ko da me kike tunanin xan maki??" tayi shiru kanta na kasa sae hawayen da take yi, ya mike tsaye ya dago ta ya xaunar kan gadon ya ciro handkerchief ya goge mata hawayen fuskarta yana kallonta yace "tell me about yhur sef, am ol ears," tayi shiru taki cewa komai har sae da yace "kin yi shiru kanwata," ta dago a raunane tana kallonsa a hankali tace "to me xance," yace "to ya sunanki," ta sunkuyar da kai tace Aneesah mukhtar, yace "i mean yhur real name," ta dan yi shiru snn tace "fateemah Muktar," yyi murmushi yace "nyc name, momyna knn, but y re yhu nt in sch, kuma parent dinki fa?" Like · Report · Just now Write a [9:30PM, 12/21/2016] Khaleesat: Khaleesat Haiydar ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 17..... Meenah ta dafe kuncinta tana kallonsa da mamaki, "yaya ka mareni??" ya fixogta ya watsa mata wani marin yace "an mareki don uwarki, nxt tym idan na sa ki abu baxa ki manta ba," ya cillar da ita cikin tsawa yace "bace min kar na taka ki," ta mike tsaye ta fasa ihu ta haye sama da gudu tana kuka tana kiran momynta, Haiydar ya juya yana kallon Aneesar dake tsaye a wajen har lkcn ya kashe mata ido yace "ya dai kanwata kin ga mun rama ko," ta juya da sauri ta bar wajen ta shige kitchen ya bi bayanta, yana shiga kitchen din yace "kanwata ki hada min lunch dina ki ajiye kan dinnin din nan, sae ki shiga bedroom dina xamu yi magana, ranar bamu gama ba mum ta dawo" ta xaro ido tace "A'a ni mun gama magana kuma Hajiya ma ta kusan dawowa ynxu," yyi shiru yana kallon cikin idonta ta sunkuyar da kanta da sauri ya karaso gabanta ya tsaya, ya dago kanta a hankali yana kallon fuskarta, murya can ciki yace "yhu're a damsel Aneesah," ta kauda kanta da sauri ya juya ya bar kitchen din ta shiga yin abunda ya sa ta. Sae da yyi wanka yyi sllh, yyi shiga cikin kanan kaya snn ya sauko falon, har lkcn meenah ta cika masu gida da kuka tana yi tana kiran momynta, ya tabe baki ya shige kitchen din bai ganta ba yasan tana garden, ya karasa cikin garden din ya jingina jikin kofa yana kallonta, tana xaune ta tsura ma sararin samaniya ido, jikinta ya bata ana kallonta ta juya da sauri suka hada ido ta kauda kanta tace "na xuba maka abincin," yyi murmushi yace "ohk xo ki gani," ta mike ta bisa a baya har suka shiga kitchen din, yace "xo mu ci oya," ta xaro ido tare da girgixa masa kai tace "aa ni naci nawa," ta juya xata bar kitchen din yyi saurin fixgota har tana neman fadawa kansa, yace "ai baki isa ba idan baxaki ci ba to kwashi abincinki nima baxan ci ba," kmr ko da yaushe hka Haiydar yyi forcin dinta yana bata abincin, har da hawayenta, har dae suka gama ci snn ya mike ya bar kitchen din yana dariya, ta bishi da harara snn ta mike ta shiga gyara table din, ta gama wanke kwanukan knn Hajiya da sumy suka shigo gidan, Hajiya ta rude jin kukan meenah tun daga waje ta shigo falon da sauri tana cewa "me ya faru meenah ta," meenah na jin muryar uwarta ta sauko da gudu ta xube kasa tana ci gaba da rusan kukanta, Hajiya ta rikice ta shiga tambayanta menene, cikin kuka tace "Haiydar ne ya dinga mari na bn san me nayi masa ba," Hajiyar ta gintse fuska tana kallon sama tace "baki yi masa kmai ba ya dinga marinki," tace "eh" hajiya ta shiga kwala masa kira a fusace, ya sako yana kallnta yce "sannu da dawo wa," bata damu da amsa masa ba cikin fada tce "me meenah tayi maka xaka mareta Aliyu ni fa wllh baxan dauki wnn ba, so kke ka illata mata fuskar ko me, wnn ai mugunta ce, ni gskya idan takura ma 'ya yana xaka yi ka tattara ka koma gidan ka kawae, ka dinga xuwa kana kawo mana xiyara," ya sa kafa yyi ball da meenar da har lkcn ke xube a kasan tiles yace "don uwarki na mareki din, ke wacece da baxan mara ba ohh ashe bbu ddi," ya juya a fusace yana kallon uwartasa yace "duk kin bi kin lalata yara basu da aiki sae na lalaci da iskanci, wnn wni irin abu ne, ita 'yar gidan uban wacece da ban isa na sata aiki tayi ba, kuma ta iya sa wani yyi, ni bama sae kince na koma gida na ba xan koma don baxan iya ci gaba da xama a gidan nn ina kallon tabarar da yaran nn ke yi ba,tunda na dawo bn ga shegen da ya dauki buta ko sau daya da sunan xae yi sllh ba, idan basa gaban t.v suna gidan party," tunda ya fara magana Hajiya tayi tsit ta marairaice fuska tana kallnsa can ganin ba shiru xae yi ba se dada tona ma 'ya yanta asiri da xe tayi yasa tace "to kayi hkri Aliyu ban san laifi tayi maka ba, ke kuma meenah me ya kai ki yi ma yayanki fitsara, meyasa ba ki jin magana," meenah ta xumburo baki taki cewa komai, yyi tsaki ya haye sama, sae a nn meenah ta mike cikin tsawa ta shiga kwala ma Aneesah kira, Aneesah dake kitchen ta fito da sauri ta durkushe gabansu tace "ga ta," "don ubanki ki je ki kwashe duk kayan da kika wanke min ki sake wankesu don basu fita ba," Haiydar ya sauko kasa cikin tsawa yace "ae baki isa ba don uwarki, kmr yanda ban isa na sa ki ki yi ba, to karya ki ke ki sa wani yyi," ya kalle Aneesar dake durkushe har lkcn gabnsu yace "ke tashi ki fita daga falon nn, kar kuma ki sake yin wani aikin har ki bar gidan nn yau, Aneesah ta kasa tashi daga inda take ya daka mata tsawa nace ki fita, ta mike a hankali ta bar falon shi kuma ya haye sama, cikin kuka meenah tace "momy kina jinsa ko salon shegiyar yarinyar nn ta rainani, wllh sae ta sake wanke min kayana," Hajiya tace "ke kiyi hkuri ki wankesu a washin machine meenah, ki rufa mana asiri ki rufa ma kanki asiri idan ba so kike ya xane ki ba yau kinsan kadan da aikinsa,tunda yace kar tayi komai yau to ya muka iya, sumy ke je ki ki xuba mana abinci a kan dinnin bana son jaraban Aliyu ku barsa kawae yau yanda kuka gansa kar yaci ubanku" sumy tace "tab wllh ban iya ba," ranar dae dole hajiya ta xuxxuba masu abincin, don har Aneesah ta koma gida bata yi komai ba. Like · 1 · Report · 15 minutes ago [9:30PM, 12/21/2016] Khaleesat: Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 16.... Ammi ta mike da sauri ta fixgo yusuf tayi masa rankwashi cikin fada tace "kana da hankali kuwa xaka jefi babanka," yusuf yace "eh, kuma idan na girma ma dukan tsiya xan mashi wnn ba babana bne," Aneesah tayi saurin kamo shi kar Ammi ta dokesa tunda dae gskya ya fada, baffan ya bude kofar hannunsa har lkcn na goshinsa yana kallon yusuf din yace "ni xaka duka idan ka girma ko," yusuf yace "eh, idan har baka daina ma Ammina ihu ba," ya gyada kai ya fice daga gidan ba tare da ya sake cewa komai ba, Aneesah ta rungume yusuf tace "yauwa kanina shi yasa nake son ka," nn fada ya dawo kanta, Ammi ta dinga mata fada wae basu da respect tunda ubansu suke ma fitsara daga ita har yusuf, Aneesah ta mike ta wanke hannunta ta dauro alwala, taxo tayi slln isha snn ta jawo kaninta suka kwanta. Washegari Ammi ta dinga fushi da ita da yusuf, ita dae bata san me tayi ba kuma har ga Allah taji ddin abinda yusuf yyi, ta xauna gaban Ammi ta marairaice murya tace "don Allah kiyi hakuri Ammi, kin ga fa jiya bayan kinyi bacci nayi ma yusuf fada Ammi," hka Aneesah ta dinga ba Amminta hakuri ta kira yusuf ma ya bata hakuri snn Ammi ta sauko, ta shirya yusuf ya wuce sch, ita kuma ta kama hanyar gidan aikinta, hka ma Ammi don gidan da take ma aiki sun dawo, ranar through out bata ga Haiydar ba sae taji wani iri, yau Monday tana isa breakfast ta fara hada masu ganin karfe takwas ya kusa sbda pretty mai xuwa makaranta don duk sauran sun gama ita ma a Higher institution take, har lkcn 'yan gidan basu tashi ba, tana cikin wanke wanke taji mutum a bayanta ta juya da sauri, yana sanye cikin bakin suit da tie yyi kyau sosai ga briefcase a hannunsa kamshin turarensa ya gauraye ko ina, ta tsura masa ido tana kallonsa yau kwana biyu knn bata gansa ba, ya sakar mata murmushi yace "Gud mrnin," ta kauda kanta tace "ina kwana," ya gyada mata kai ya dawo gabanta ya tsaya "ke kin karya ne," ta juya bata sake tanka masa ba ta ci gaba da abinda take yi, ya juyo da ita yace "me kika hada na break," tace "suna can dinnin" yace "to debo min nawa ki kawo nn," ya fadi yana nuna mata dinnin din kitchen, tace "to ai bn san yanda kke hada tean ba," "ki hada yanda kike tunanin ya kamata amma kar ki cika min suger, jez cube biyu yyi," tace "uhmm" snn ta fice daga kitchen taje hado masa nasa tean a kan table, ko da ta dawo kitchen din yana xaune kan dinning, yace "to hado min coffee plss," ta hado masa ta ajiye gabansa xata wuce ya fixgota ya xaunar kan kujera yace "ni bana break a gida ran monday, amma yau sbda ke xan yi don tare nake son mu ci," xata yi magana ya sa mata dankali a baki yace "kar ki ce min komai" hka Haiydar ya tilasta ta suka ci duk abinda ta kawo masa a tare, tean ma kanta yasa ta hado ma don coffee kawae ya sha, gabanta ya dinga faduwa kar Hajiya ta sauko ta gansu a hka, ta marairaice fuska kmr xata yi kuka tace "wllh na koshi, na fa karya a gida" ya mike yana kallonta ya kashe mata ido yace " ai de kin ci, sae na dawo, kiyi min ginger drink kanwata," ta gyada masa kai kawae, ya kalli agogon hannunsa ya bi ta garden ya tafi garage xabar motar da xae fita da. Tana gama gyara inda suka yi break din Hajiya ta sauko tare da pretty dake cewa "momy yayana ya wuce ne, wae fa da droppin dina nake son yyi tunda driver baya nn," hajiyar tace "nima wllh ko sallama bai yi min ba bby," ki karya sae nasa sumy ta ajiye ki tunda har ynxu tsoran drivin kike yi, Aneesah ta risina ta gaida su, snn ta hau sama ta gyara masu dakunansu ta wanke bathroom, tana gamawa suka tula mata kayan wanki ta wanke, ba ita ta gama wankin nn ba sae kusan karfe biyu, bbu kowa gidan duk sun fita, ta shiga kitchen a gajiye don ta girka masu abinci kafin su dawo, karfe uku saura ta gama girkin ta jera masu kan table, ta tuna Haiydar yace tayi masa ginger drink, ta koma kitchen da sauri ta shiga hada masa drink din, tana gama hada drink din ta xuba cikin jug ta saka cikin fridge snn ta juya xata bar kitchen din ta gansa jingine jikin kofa yana kallonta, yyi murmushi yace "sannu da aiki kanwata," ta gyada masa kai ta gaishesa ta fice daga kitchen din, shima ya fito ya haye sama ganin meenah a falon tsaye tana ma Aneesahn magana cikin gadara, "ke meyasa xaki hada min wanki da fararen kayana," Aneesah tace "Aa su na fara wanke wa, bn hada su da komai ba," meenah ta kai mata mari tace "karya kike munafuka, ki tabbatar kin sake wanke min su kafin ki bar gidan nn yau," tana kai wnn ta haye sama tana xage xage, Aneesah ta bi ta da kallo hawaye na bin kuncinta, ganin Haiydar na saukowa yasa ta juya da sauri xata bar wajen ya kirata, ta tsaya har ya karaso kusa da ita yace "me kika yi mata?" tayi shiru bata ce masa komai ba, ya kwala ma Meenar kira ta sauko tana kallonsa tace "gani," ya hade rae yana kallonta yace "me nace kiyi min jiya kafin na dawo," ta yatsine fuska tace "oho na manta," ya kai mata tagwayen m[truncated by WhatsApp] [9:30PM, 12/21/2016] Khaleesat: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 18...... Yau friday karfe takwas da rabi Aneesah ta isa gidan aikinta don ma daurewa kawae tayi bata wani jin ddi, jin muryar Hajiyar a falo da 'ya yanta yasa ta kasa shiga ciki xuciyarta ya dinga bugawa, ganin dada bata ma kanta lkci take yi tsaye a verendan yasa tayi shahada tana karanto addu'a a xuciyarta ta shiga falon da sallamarta a sanyaye, Hajiyar na xaune sumy na kwance kan kafarta, meenah na goga abu a fuskarta madubi na hannunta, shi ko Haiydar na xaune kan dinnin yana rubutu pretty na kusa dashi, ta durkusa a sanyaye ta shiga gaida Hajiyar gabanta na faduwa, cikin tsawa tace "yanxu kike xuwa min aiki sbda kin raina ni ko? Xaki gane kuranki yau wllh wllh," a raunane ta fara ce mata bata da lfya ne, Hajiya ta mike tsaye ta yo kanta a fusace kmr me shirin dukanta tace "baki da lafiya? Ni kike gaya ma baki da lfya. ina ruwana da rashin lafiyarki ko ni na daura maki don uwarki," ganin Haka yasa Haiydar ya shigo falon ya nemi guri ya xauna yana kallon momyn tasa yace "yauwa mum maganar da nace xamuyi daxu," ya juya yana kallon Aneesar dake hawaye yace "ke tashi ki ba mutane wuri," ta kalle hajiyar da har lkcin ke tsaye kanta, hajiyar ta daka mata tsawa "don uwarki ba da ke yake ba xaki xuba ma mutane tula tulan idanuwa kmr tulu, mayya kawae" ta mike a sanyaye ta bar falon tayi hanyar kitchen, Hajiyr ta koma ta xauna tace "yauwa ina jin ka son, wacce magana ce xamu yi," ya dan yatsina fuska ya mike tsaye yace "ko kuma bari ma sae xuwa anjima, ynxu ina busy ne, ya koma dinnin din ya ci gaba da abinda yake ," sumy tayi tsaki a hankali tace "dan rainin wayo kawae," Hajiyar tace "ke baki da kunya ko, ynxu idan ya ji ki ya doke ki ki bara min baki kmr speaker ko," sumy ta mike tana bubbuga kafa ita an mata fada ta haye sama da shirin xuwa tayi kuka, Hajiyar ta bita da sauri tana cewa "lahh, to meye abun kuka nn sumy," meenah ta bi su a baya, suna haurawa sama Haiydar ya mike ya ba pretty laptop dinsa ta kai daki snn ta gyara masa dakinsa, tana hayewa sama yyi hanyar kitchen ya tar da ita tana fere dankali, ya durkusa gabanta cike da tausayi yace "me ya same ki Aneesah," ta girgixa kai bata ce komai ba, ya daura hannu a goshinta ya ji xafi yace "subhanallahi, wat's wrong Aneesah," nn ma taki ce masa komai sai hawayen da ta ke yi, ya tsura mata ido cike da tausayi ya kasa cewa komai, can ya mike tsaye yace "ruwan tea kawae xaki dafa masu, nothin more, ki bar dankalin nn," ta girgixa masa kai tace "xan yi dukka," ya hade rae yace "am givin yhu instructns, nt options" a hankali ta mike tsaye tana kallonsa yace "yea," yana tsaye kitchen din tayi duk abinda yace mata, ta jera masu kan dinnin, suna fitowa yin break kuwa duk suka tsaya da mamaki suna kallon ruwan lipton da bread sae kayan tean da ta ajiye masu da blue band kan table din, bbu kwae bbu potatoe, bbu plantain, bbu dan farfesu, cikin tsawa Hajiyar tace "uban meye wnn nake gani hka a nn," gaban Aneesah dake tsaye wajen ya dinga bugawa ta rasa me xata ce mata, Haiydar ya sauko daga sama sanye da farar shadda ya karaso dinning din ya xauna, ya jawo kofi ya fara xuba ruwan lipton a ciki, ya daga kai da mamaki kmr gske yana kallonsu yace "ya aka yi mum," Hajiyar da ta bude baki har lkcn tana kallon Aneesah da ta kasa dago kanta tace "ka duba abinda shegiyar yarinyar nn ta mana yau Haiydar," yace "ooh ai ni nace tayi hka don sauri nake yi xan fita kuma ina son na karya kafin na fita, naga soye soyen xae bata min lkci, yau guda don baku ci dankali da kwae ba sae ku tsaya kmr wasu sojoji," meenah cikin fushi tace "to yaya mu ina ruwanmu da fitarka, ba sae ka shiga kitchen ka hado tean ka ka fito ka bar ta tai mana soye soyen mu ba, don xaka fita kuma mu baxa mu ci abinda muka saba ci ba," yyi mata wani mugun kallo yace "ehh baxa ku ci ba don uwarki, ki shiga kitchen din ki soya mana idan dankali da kwae kike son ci, ko ke ba mace bace," sumy ta fashe da kuka tace "wllh baxan sha tea gaya ba kmr wata almajira," meenah ma ta fashe da kuka tace "nima wllh," suka bar dinning din suka haye sama, Hajiya ta sauke ajiyar xuciya tace "Haiydar tunda suna so da baka hanata yi ba, sae ta hada maka tean ka kawae tayi mana soye soyen mu," ya dago yana kallonta yace "ynxun ma naga dae bae baci ba ae mum, tunda har ni suke gaya ma maganar bnxa to wllh bbu abinda xata soya masu yau a gidan nn, su shiga kitchen su yi da kansu tunda su mata ne kuma aure xasuyi," pretty ta ja kujera ta xauna ta shiga hada tean ta, Hajiya bata sake ce masa komai ba ta haye sama tana hararar Aneesah. Ya juya a hankali yana kallon Aneesar ta juya da sauri ta shige kitchen, bayan kmr minti talatin suna xaune a falo shi da pretty yana nuna mata abu a wayarsa Hajiya ta sauko, ta kallesa da mamaki tace "A'ah fitar knn Haiydar," yace "A'a sae xuwa anjima, na fasa ynxu kam," [9:30PM, 12/21/2016] Khaleesat: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 19..... Hajiya bata sake ce masa komai ba ta haye sama ranta a bace, ta ja dogon tsaki bayan ta shiga daki, wnn ae wlknci ne Haiydar ke masu a gidan nn. Dole ta kira driver ta basa sako yaje eatry ya siyo masu abinci don sun ce baxa su sha tean ba kuma, karfe sha biyu duk suka shirya suka bar gidan bayan Hajiya ta gaya mata abinda xata girka masu kafin su dawo su meenah kuma sun tula mata kayan wanki ta wanke idan sun bushe ta goge kuma, Haydar na kallonsu har suka bar gidan basu ce masa ba bae ce masu ba, pretty dae na gida don ranar bata da lecture, gidan ya rage daga Haiydar sae Aneesah da prettyn. Haiydar ya fita ya sameta bakin famfo tana tara ruwan wanki, yace "don me baxa ki wanke su a machine ba Aneesah," ta juyo tana kallonsa a hankali tace "sun ce basa fita a machine din" cikin bacin rae yace "sun ci ubansu, maxa kwashe kije ki xuba masu a machine din kar Allah yasa su fita, ke baiwarsu ce," tayi shiru tana kallonsa, yace "ba magana nake maki ba, am nt jokin," tace masa "to," a sanyaye, shi kuma ya juya ya bar garden din jin pretty na kwada masa kira," yana shiga gidan ya sameta tsaye tana jiransa ya xo ya xuge mata zip, ya kulle mata yana tambayarta idan ta fita yaushe xata dawo, tace "lah ni fa bbu inda xa ni yaya, wani sabon cartoon na siyo xan kalla ynxu," ya hade rae yana kallonta yace "ba kince min xaki gidan frnd dinki ba yau," ta dan tabe baki tace "na fasa yaya, kai da baka son ina fita yaya shine yau xaka dinga cewa na fitan" yyi shiru bae sake ce mata kmai ba yana duba wayansa, Aneesah ta xo ta wuce sama da kayan wankin pretty ta bi ta da kallo tace "ke, a ina xaki wanke kayan," Aneesar tace "sama," pretty tace "ba sunce maki basa son wankin machine ba or re yhu daft?" Haiydar ya kalli prettyn yace "ke da'alla kin cika surutu je dauko mayafinki na ajiye ki inda xaki nima masallaci xan tafi ynxu," tace "to yayana" snn ta haye sama da gudu, shima ya haura ya shiga bedroom dinsa ya sake shirin juma'ah ya fito ya samu Aneesahn tsaye kusa da machine din bayan ta xuba kayan, yace "yauwa kanwata ko ke fa, bna son kina min musu kin ji, ynxu gaya min inda ke maki ciwo idan xan dawo daga masallaci na siyo maki magani," ta girgixa masa kai tace "bbu inda ke min ciwo," ya harareta yace "c'mon bna son hka kanwata ki gaya min don Allah," da kyar ya samu tace masa kanta ke ciwo, yace to xae siyo mata magani idan yana dawowa, a falo ya tarda pretty tana jiransa, ya kama hannunta suka fita daga falon ya dauko motar a garage snn suka fice daga gidan, ya ajiyeta gidan kawarta ya hada ta da dubu biyar ta dauki drop idan xata dawo anjima... Karfe biyu ya shigo gidan, lkcn Aneesah na kitchen tana masu girki bayan ta gama da wankin, har wani jiri take gani duk ta kagu lkci yyi ta wuce gida ta kwanta ko ta samu sauki, ya jingina jikin kofa rungume da hannayensa yana kallonta, jin kamshin turarensa ya sa ta juya da sauri ya sakar mata murmushi yace "sannu da aiki," ta gyada masa kai tace "ngd" snn ta gaishesa ya amsa ya karaso cikin kitchen din ya tsaya bayanta yace "me kike girka mana," ta koma gefe da sauri tace "shinkafa da miyar kaxa ce, sae cream salad " ya gyada mata kai yana murmushi yace "to xubo min nawa idan kin gama," ta gyada masa kai taci gaba da hada salad din yana kallonta, tana gama hada wa ta shirya masa abincinsa yace ta ajiye masa a kan carpet na tsakiyar falo tayi yanda ya sa ta xata wuce ya riko hannunta, ta fixge da sauri ya tsura mata ido "Aneesah ciwon kan ne ya sa maki xafin jiki hka, don Allah ki gaya min me ke damunki bn yrda kanki ke ciwo ba," ta yarfe hannu tace "nima bn sani ba wllh, kawae dae bna jin ddi ne," ya kamo hannunta ya xaunar da ita gaban abincin ya xauna yana kallonta yace "xauna mu ci abinci sae na baki magungunan da na kawo maki," xata yi magana ya daura yatsantsa kan lebenta yana mata wani irin kallo yace "kar ki ce min komai," ta sunkuyar da kanta da sauri, ya xuba abincin ya shiga ci yana bata, a hankali yace "an taba ce maki kina da kyau Aneesah," tayi masa shiru bata ce komai ba, ya dibi abincin a cokali ya kai mata baki ta kauda kanta, ya tsura mata ido bai ce komai ba, ta juyo tana kallonsa yyi murmushi yace "am srry baxan kara ba kanwata," ya sake kai mata abincin baki ta bude bakin a hankali ya xuba mata, a hankali taji yace "Aneesah, wani aiki baffan naku yake yi ynxu," ta dan yi shiru na wani lkci snn tace "siyasa yake yi," ya gyada kai yace "gud! when lst rabonku dashi," ta sunkuyar da kai bata sake cewa komai ba har sae da ya maimaita mata tambayan snn ta basa lbrin abinda ya xo yyi masu ranan da daddare tana kuka da abinda yusuf yyi masa daga karshe, Haiydar yyi murmushi yace "to meye abun kuka Aneesah, ae ki kwantar da hankalinki kawae bna son kina sa ma kan ki damuwa," ya ciro handkerchief yana goge mata hawayen idonta yana kallon cikin idon, ita ma kallon nasa take, dai-dai nn aka bude kofar falon aka shigo ta mike a tsorace tace "nashiga uku," [9:30PM, 12/21/2016] Khaleesat: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 21..... Meenah ta tabe baki tayi hanyar stairs tana cewa "wnn jarabar da yawa take, mutum sae kace shaidan," ta karasa dakinta da gudu ta kullo kofar, Hajiya tace "ka dinga hakuri da kanninka Aliyu, yarane basu san abinda suke ba sae ana yi ana nuna masu," ya mike tsaye yace "A'a jarirai ne, yau ma aka haifosu karewarta, amma wllh idan na cafke mutum a gidan nn ko," yyi kwafa yyi hanyar dinnin, pretty ta mike tabi sa, Hajiya tce "Allah ma baxae sa ka cafke sun ba," ita da knta ta mike taje ta xuxxuba masu abincin snn ta aiki pretty taje ta kira mata su suxo suci ba kunya suka sauko kuwa, suka xauna daga su har uwar tasu tsakiyar carpet tnda oga na kan dinnin, sn gama cin abnci suna ta kallo sumy na masu hira, Haiydar da pretty dae na kan dinnin suna kallo a wayarsa, sumy tace "wae har ynxu 'yar aikin can bata gama guga bne a sama, gashi ina son na aiketa supermarket siyo min sabulu, don soap din wanka na ya kare, Hajiya tace "to ni ina nasani, wae Haiydar har ynxu bata gama gugan bne, xata mana farfesun kifi fa kafin ta tafi," yyi kmr bae ji su ba yana ta kallonsa da pretty, Meenah tayi tsaki ta mike tsaye tace "bari dae naje na duba, kila shegiyar taji sanyin A.c ma bacci ya dauketa a gun," Haiydar ya mike da sauri cikin tsawa yace "wat! Dakina xaki shiga, da ko kinga yanda ake cin uban mutum yau, don Allah je ki, na rantse da Allah idan ban sumar dake ba to sae na karya ki yau," Hajiya ta mike tace "ohh ni fateema na shiga uku, sae kace ba kanninka ba Aliyu meyasa kke hka, duk ka dauki karan tsana ka daura ma 'ya yan nn, meye a ciki don tace xata je dubo 'yar aiki, wnn wani irin rayuwace hka irin naka," ya daga kafada alamar bae damu da xancen nata ba yace "ai yaran ne basu da tarbiyar arxiki," sumy ta tabe baki tace "ni dae ko min dare wllh sae taje siyo min sabuluna, ba ma kaya ba in xata iya har dakin ma ta goge dole ta fito taje min market," meenah tace "nima wllh ko min dare kafin ta bar gidan nn sae ta min gugan kayana," Haiydar ya mike tsaye ya fara saukowa daga matakalan dinning din, gaba daya suka fasa ihu a tsorace suka yo bayan Hajiyarsu, ita ko ta mike tsaye da sauri tana cewa "kana ma Allah da annabinsa ka rabu da 'ya yana a gidan nn Aliyu, wllh wllh xan bata maka rai na Hada ka da Alhaji usman fa, wnn wace irin jaraba ce," ko kallon daga ita har 'ya yan nata bai yi ba ya haye sama, bayan kmr minti biyar sae gashi ya sakko Aneesah na biye da shi a bayansa, har lkcn Hajiya na tsaye, su meenah na rabe a bayanta sumy har da kuka, ya kalli Aneesah cikin tsawa yace "ke kama hanyar gidanku, kin gama aikinki 4 today," ta marairaice tana kallon Hajiyar da ta galla mata wani mugun harara, ya daka mata tsawa yace "nace ki fice ko bakya ji ne," a sanyaye ta fita daga gidan karfe hudu saura minti biyar," ya koma ya xauna, Hajiya tayi shiru tana kallonsa cikin lallami ta fara magana "Haba Aliyu so kke yarinyar nn ta raina mu ne, wnn ai bae yi ba, biyanta fa nake yi ka dinga hanata kuma tana ma yarana aiki, don su fa na kawota gidan," yace "sae randa suka canxa halinsu nima xan canxa," snn ya haye sama, meenah ta ja dogon tsaki tace "bnxa kawae dan wahala, in ina son dawowar wnn gantalallen mutumin gidan nn nayi ma Allah karya wllh," sumy tace "ke ko ni, wnn ai obstacle babba ne a gidan nn gare mu" Hajiya dae na tsaye tana kallonsu ta kasa cewa komai, pretty ta mike tayi tsaki tace "fitsararrun bnxa kawae, ai kune gantalallun," snn tayi hanyar stairs da gudu meenah ta bi ta har tana faduwa ta cafkota ta shiga xuba mata mari tana duka, pretty ta fasa ihu, sae ga Haiydar da sauri ya sakko, meenah ta juya da gudu xata bar wajen ya cafkota ya haye sama da ita Hajiya ta taho da gudu tana cewa "wllh ka sake min 'ya ta kasan abinda tayi mata ne," ko saurararta bae yi ba ya shige da ita dakinsa, ya kulle kofar da makulli, ranar shegen duka yyi mata da belt, su Hajiya da sumy aka tsaya bakin kofa suka dinga rusa kuka yaki bude kofar har sae da yyi mai isarsa snn ya cillota waje ya kulle kofarsa. Aneesah na komawa gida ranar Ammi ta tambayeta da mmaki me ya dawo da ita lkcn, tay mrmushi tace "nace mata bana jin ddi ne shine tace naje gida na huta, Ammi tace "Allah sarki, Allah ya kara masu budi, matar na da kirki," Aneesah tayi murmsuhi ta shige daki kawae a xuciyarta tana cewa lallai kam tana da kirki. Ko da Aneesah ta tafi aiki washegari bta ga Haydar ba, ta sha wahala ranr dn knta suka huce dk abnda yyi msu jiya daga su har uwarsu, ita de pretty bata ce kmai ba kallnsu kawae take, sun aiketa kasuwa ranr ya kai sau uku kuma a kafa, snn dk se da tyi masu guga da kwalemar dakunansu, krfe uku suka bar gidn bayan sn ci abncin rana, sumy ta kawaso mata takalmnta ta wanke na wankewa na gogewa kuma ta goge tce mata to, snn suka bar gidn gaba daya har da Hajiya amma banda pretty, sae bayan fitarsu pretty tayi mata magana ta kuma kawo mata maganinta na jiya da Haydar ya siyo mata tace yace ta bata, ta kuma kama mta sauran aikin da suka rage a gidan kafin 'yan uwanta su dawo. [9:30PM, 12/21/2016] Khaleesat: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 20..... Pretty ce ta shigo gidan, ta tsaya bakin kofar tana kallonsu ba tare da tace komai ba, Aneesah ta juya da sauri cikin tashin hankali xata bar wajen, sai maimaita nashiga uku take yi, Haiydar yyi saurin rikota, ta buge masa hannu tare da fashewa da kuka tace "ni ka rabu dani don Allah," ya ki sakinta sae ma xaunar da ita da yyi gabansa, ya juya yana kallon prettyn da har lkcn ke tsaye tana kallonsu yace "c'mon Zainab xo mu ci abinci," ta karaso falon ta ajiye jakarta kan kujera ta xauna kan carpet tace "washh yaya wllh na gaji dayawa akwae rana," ya mika mata spoon yace "to meyasa kika dawo da wuri," tace "kawae na gaji da xaman gidan ne," Haiydar ya juya yana kallon Aneesah da har lkcin yana rike da ita don kar ta tashi yace "kanwata kukan me kike kuma," tayi shiru bata ce komai ba sae faduwa da gabanta ya ke yi tana kallon prettyn a tsorace, pretty ta fara cin abincin ta tana ba yayan nata lbrin kawarta da taje wajenta, shi ko hankalinsa na kan Aneesah da ta ki sake wa, ya dubi pretty dake ta cin abincin ta yace "je ki sa key a kofa pretty," taje ta sa ta dawo, ganin Aneesah taki karban abincin da yake bata a baki yasa ya bata spoon ta ci da kanta, nn ma taki, pretty tace "kila bata son ta ci da kai ne yaya, ka xuba mata nata daban," yyi yanda pretty tace ya tura mata gabanta ya hade rae yace "oya maxa ki ci idan baki son nayi fushi," ta dago kai a hankali tana kallon pretty, prettyn ta sakar mata murmushi, ita ma ta dan yi murmushin snn ta fara cin abincin a hnkli, hka suka dinga cin abinci pretty na basu lbri har suka gama pretty ta kwashe kwanukan ta kai kitchen ta dawo suka ci gaba da hira, tun Aneesah na yi masu shiru har ita ma ta sake suna yi, pretty ta kalleta tace "yauwa wae me kike shafawa a lips dinki kullum sae na gansa pink" Aneesah tayi murmushi tace "ni bna sa komai," Haiydar yyi murmushi yace "ke ma kina son naki ya xama irin nata ne" pretty tayi dariya tace "eh yayana," yace "to xan ce ta tsam maki, ynxu dae je ki wanke plates din da muka ci abinci ki dawo" Aneesah ta ce "A'a xan wanke," ya riko hannunta yace "A'a bar ta ta wankesu, ke da baki da lfya magani xaki sha ynxu ma," pretty tace "bata da lfya ne," yace "eh" tace "Allah ya sauwake snn ta kwashi kwanukan tayi kitchen dasu ta wanke," ya lallabata ya bata magani tashi da kyar, snn tace masa xata je tayi masu gugan kayansu, ya harareta yace "baxa kiyi ba wllh," ganin yaki barin ta ta shi yasa ta hkura ta tsura masa ido kawae tana kallonsa ya hura mata idon yace "wnn kallo hka," ta boye fuskarta tana murmushi. Pretty ta dawo falon bayan ta gama wanke wanken tace "yayana na gama," yace "yauwa kanwata," ta xauna suka ci gaba da hirarsu kmr da can sun saba da Aneesah, budewar gate da suka ji yasa Aneesah ta mike tsaye da sauri, pretty ma ta tashi da sauri tayi hanyar kofa don lekawa taga ko waye, ta dawo da sauri tace "yaya mum ce da su meenah," Aneesah ta fixge hannunta daga rikon da yyi mata tace "na shiga uku don Allah ka sake ni," yace "baxa fa ki kara yin aiki gidan nn yau ba, gwara kawae ki tafi gida in hka ne," ta marairaice masa tace "lkcn tafiyata bae yi ba don Allah ka rabu dani guga xanje na masu," ya fixgota yyi hanyar stairs da ita tana masa magiyan ya kyaleta suna hawa sama ya bude bedroom dinsa ya jefata ciki yace "kar ki kuskura ki fito, gwara kawae kiyi bacci har lkcn tafiyar taki yyi," ya ciro makulli ya kulle dakin ta waje snn ya sauko downstairs, pretty ta ruga ta bude masu kofa Meenah ta ce "ina wnn shegiyar yarinyar taxo ta yi serve din mutane yunwa nke ji," Hajiya ma ta xauna tana tambayar haiydar har ya dawo, yace "ehh snn ya gaida ta, ta amsa tana cewa prettyna kin ci abinci, pretty tace "eh naci," a fusace hajiya tace " wae ina wnn gantalalliyar yarinyar take bata ji shigowrmu bne," Haydar yce "tana sama na sa ta guga ne," cikin gadara meenah tace "ni tayi min nawa gugan ne pretty?" pretty tace "na yaya take yi," meenah cikin bacin rae take "ba ni na fara sa ta ba xata bar min kayana don rainin wayo," Haydar yyi mata wani irin kallo yace "idan baki yi hnkli ba wllh yau sae na fasa mki kai "dare me" kuma ki gni," meenah ta hararesa tace "to kai naga ba dry cleaning kake kai kayanka ba idn ba gulma ba yaushe 'yan aiki suka fara maka guga," sumy ta tabe baki tace "shi dae na gani," ya mike cikin xafin nama ya yo kan meenar da ta fasa ihu a tsorace Hajiya ta tashi da gudu ta tsaya gabansa ta rikesa har da durkusawanta "don Allah don annabi kayi hkuri ka rabu dasu Aliyu, kaga yarane basu san ciwon kansu ba," sumy dama tuni ta haye sama da gudu, yyi kwafa ya koma ya xauna, tsit kke jin meenah don ta tsorata, pretty sae dariya take, Hajiya ma ta koma ta xauna tace "to yarinyar nn taxo ta fara bamu abinci kafin ta ci maka gaba da gugan mana Aliyu wllh yunwa duk muke ji," meenah tce "nima shi dae na gani," yce "A'a kafin ta bar gidan nn yau duk se ta gama min gugan kayana idn ma xaku je ku xuba abincinku kuje ku xuba tunda de ku ba kutare bane," ya fadi yana kallon Meenah. [9:30PM, 12/21/2016] Khaleesat: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 21..... Meenah ta tabe baki tayi hanyar stairs tana cewa "wnn jarabar da yawa take, mutum sae kace shaidan," ta karasa dakinta da gudu ta kullo kofar, Hajiya tace "ka dinga hakuri da kanninka Aliyu, yarane basu san abinda suke ba sae ana yi ana nuna masu," ya mike tsaye yace "A'a jarirai ne, yau ma aka haifosu karewarta, amma wllh idan na cafke mutum a gidan nn ko," yyi kwafa yyi hanyar dinnin, pretty ta mike tabi sa, Hajiya tce "Allah ma baxae sa ka cafke sun ba," ita da knta ta mike taje ta xuxxuba masu abincin snn ta aiki pretty taje ta kira mata su suxo suci ba kunya suka sauko kuwa, suka xauna daga su har uwar tasu tsakiyar carpet tnda oga na kan dinnin, sn gama cin abnci suna ta kallo sumy na masu hira, Haiydar da pretty dae na kan dinnin suna kallo a wayarsa, sumy tace "wae har ynxu 'yar aikin can bata gama guga bne a sama, gashi ina son na aiketa supermarket siyo min sabulu, don soap din wanka na ya kare, Hajiya tace "to ni ina nasani, wae Haiydar har ynxu bata gama gugan bne, xata mana farfesun kifi fa kafin ta tafi," yyi kmr bae ji su ba yana ta kallonsa da pretty, Meenah tayi tsaki ta mike tsaye tace "bari dae naje na duba, kila shegiyar taji sanyin A.c ma bacci ya dauketa a gun," Haiydar ya mike da sauri cikin tsawa yace "wat! Dakina xaki shiga, da ko kinga yanda ake cin uban mutum yau, don Allah je ki, na rantse da Allah idan ban sumar dake ba to sae na karya ki yau," Hajiya ta mike tace "ohh ni fateema na shiga uku, sae kace ba kanninka ba Aliyu meyasa kke hka, duk ka dauki karan tsana ka daura ma 'ya yan nn, meye a ciki don tace xata je dubo 'yar aiki, wnn wani irin rayuwace hka irin naka," ya daga kafada alamar bae damu da xancen nata ba yace "ai yaran ne basu da tarbiyar arxiki," sumy ta tabe baki tace "ni dae ko min dare wllh sae taje siyo min sabuluna, ba ma kaya ba in xata iya har dakin ma ta goge dole ta fito taje min market," meenah tace "nima wllh ko min dare kafin ta bar gidan nn sae ta min gugan kayana," Haiydar ya mike tsaye ya fara saukowa daga matakalan dinning din, gaba daya suka fasa ihu a tsorace suka yo bayan Hajiyarsu, ita ko ta mike tsaye da sauri tana cewa "kana ma Allah da annabinsa ka rabu da 'ya yana a gidan nn Aliyu, wllh wllh xan bata maka rai na Hada ka da Alhaji usman fa, wnn wace irin jaraba ce," ko kallon daga ita har 'ya yan nata bai yi ba ya haye sama, bayan kmr minti biyar sae gashi ya sakko Aneesah na biye da shi a bayansa, har lkcn Hajiya na tsaye, su meenah na rabe a bayanta sumy har da kuka, ya kalli Aneesah cikin tsawa yace "ke kama hanyar gidanku, kin gama aikinki 4 today," ta marairaice tana kallon Hajiyar da ta galla mata wani mugun harara, ya daka mata tsawa yace "nace ki fice ko bakya ji ne," a sanyaye ta fita daga gidan karfe hudu saura minti biyar," ya koma ya xauna, Hajiya tayi shiru tana kallonsa cikin lallami ta fara magana "Haba Aliyu so kke yarinyar nn ta raina mu ne, wnn ai bae yi ba, biyanta fa nake yi ka dinga hanata kuma tana ma yarana aiki, don su fa na kawota gidan," yace "sae randa suka canxa halinsu nima xan canxa," snn ya haye sama, meenah ta ja dogon tsaki tace "bnxa kawae dan wahala, in ina son dawowar wnn gantalallen mutumin gidan nn nayi ma Allah karya wllh," sumy tace "ke ko ni, wnn ai obstacle babba ne a gidan nn gare mu" Hajiya dae na tsaye tana kallonsu ta kasa cewa komai, pretty ta mike tayi tsaki tace "fitsararrun bnxa kawae, ai kune gantalallun," snn tayi hanyar stairs da gudu meenah ta bi ta har tana faduwa ta cafkota ta shiga xuba mata mari tana duka, pretty ta fasa ihu, sae ga Haiydar da sauri ya sakko, meenah ta juya da gudu xata bar wajen ya cafkota ya haye sama da ita Hajiya ta taho da gudu tana cewa "wllh ka sake min 'ya ta kasan abinda tayi mata ne," ko saurararta bae yi ba ya shige da ita dakinsa, ya kulle kofar da makulli, ranar shegen duka yyi mata da belt, su Hajiya da sumy aka tsaya bakin kofa suka dinga rusa kuka yaki bude kofar har sae da yyi mai isarsa snn ya cillota waje ya kulle kofarsa. Aneesah na komawa gida ranar Ammi ta tambayeta da mmaki me ya dawo da ita lkcn, tay mrmushi tace "nace mata bana jin ddi ne shine tace naje gida na huta, Ammi tace "Allah sarki, Allah ya kara masu budi, matar na da kirki," Aneesah tayi murmsuhi ta shige daki kawae a xuciyarta tana cewa lallai kam tana da kirki. Ko da Aneesah ta tafi aiki washegari bta ga Haydar ba, ta sha wahala ranr dn knta suka huce dk abnda yyi msu jiya daga su har uwarsu, ita de pretty bata ce kmai ba kallnsu kawae take, sun aiketa kasuwa ranr ya kai sau uku kuma a kafa, snn dk se da tyi masu guga da kwalemar dakunansu, krfe uku suka bar gidn bayan sn ci abncin rana, sumy ta kawaso mata takalmnta ta wanke na wankewa na gogewa kuma ta goge tce mata to, snn suka bar gidn gaba daya har da Hajiya amma banda pretty, sae bayan fitarsu pretty tayi mata magana ta kuma kawo mata maganinta na jiya da Haydar ya siyo mata tace yace ta bata, ta kuma kama mta sauran aikin da suka rage a gidan kafin 'yan uwanta su dawo. [9:30PM, 12/21/2016] Khaleesat: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 25..... Cikin ikon Allah Aneesah ta isa gida ranar gabanta na faduwa, amma me, sae taga mutane fal a kofar gidansu, nn da nn ta daina ganin jirin da take gani bugun xuciyarta ya tsananta kuma duk wani ciwo ta neme shi ta rasa sae bugun xuciyar, ta karaso da sauri a rude tana tambayar mutanen me ya faru, bbu wanda ya tanka mata, a gigice tace "nashiga uku ina Ammina," nn ma bbu wanda ya bata amsa sae ma hawaye da taga wasu nayi ba manyan ba ba yaran ba, haba bata san lkcn da ta fasa wani raxanannen ihu tayi cikin gidan da gudu tana kwala ma Amminta kira a rude, bata damu da kiran da makwabtansu dake tsakar gidan ke mata ba, wasu suka bi ta a baya da sauri, da gudu ta fada dakinsu tana ci gaba da kwala ma Amminta kira, xaune ta ganta makwabtansu da dama na xaune gefenta wasu na hawaye wasu sunyi jigum, nn da nn ganin Amminta yasa Hankalinta ya kwanta ta xube jikin Ammin tana maida numfashi har lkcn jikinta na rawa tana hawaye tace "Ammina me ya faru," Ammi bata tanka mata ba sae kkrin boye hawayen da take yi tana shafa kanta tace "har kin dawo," sae kuma Ammi ta fashe da kuka, Aneesah ta fara kalle kallen dakin a tsorace murya can ciki tace "ina yusuf Ammi," Ammi bata ce mata komai ba sae kukan da take yi, Aneesah ta shiga jijjiga Ammin tata a rude tace "Ammi don Allah ina yusuf ki gaya min," kmr ance ta juya taga abu a nannade cikin farin kyalle ta karasa da sauri hannunta na rawa ta bude, me xata gani, kaninta a kwance ba rai, bata san lkcn da ta fasa wani irin kara ba daga nn kuma bata sake sanin me ya faru ba, ta dae farka can cikin dare ta ganta kwance kan gadon amminta da makwabtansu har uku a dakin, Ammi ko na kan darduma a xaune. [9:30PM, 12/21/2016] Khaleesat: Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 23.... Aneesah ta koma baya a tsorace ta fara kkrin mikewa xata bar wajen ya rikota da sauri ta fixge hannunta a tsorace tace "meye hka malam wnn wani irin iskanci ne," ya wara idonsa ya sake kamo ta da sauri yace "wats wrong bby yhur temperature is high," ta buge masa hannu tare da fashewa da kuka tace "wae meye hka a ina na sanka ni fa ba 'yar iska bace" yy dariya ya rungumota gaba daya yace " nima ba dan iskan bane ba ai, kuma sae kin gaya min inda ke maki ciwo ko kuma na duba ki ynxun nn a nn," Haiydar ya shigo garden din kmr wani xaki tana ganinsa ta fara kkrin kwace kanta amma ta kasa don kin sakinta yyi, har Haiydar ya karaso gurinsu Najeeb bae gansa ba ita ce dae ta gansa, Haiydar ya fixgota a fusace ya wurgar yana huci yace "a hkn kike yawan gaya min ke ba 'yar iska bace," ta fashe da kuka ta hde kanta da gwiwa, ya juya a fusace yana kallon Najeeb yace "ka fita gonata malam kar na baka mamaki, bnxa kawae dan iska," ya juya a fusace ya bar garden din, najeeb ya bi sa da kallo yana murmushi, ya karaso gabanta ya durkusa yace "am srry bby, xan basa magani ya kawo maki ltr bye," ya mike shima ya bar garden din, tana jin fitar motarsu a gidan ta mike da kyar tana goge hawayen da ya ki tsaya mata ta shiga gidan kafin hajiya ta fara kwala mata kira tana nemanta. Har Aneesah ta bar gidan ranar bata ga Haiydar ba, da kyar ta isa gida ta tarda jikin Ammi yyi sauki don har ta gyara gidan tayi masu girki, wanka da Alwala kadae ta iya yi ta kwanta don kasa sallahn tayi ammi tace ta sa kaya su tafi Asibiti amma tace aa don sanin kanta ne kudi kadan ya rage a hannunsu ynxu kafin karshen wata a biya su, Ammi ta fita siyo mata magani a chemist suka shigo tare da yusuf ya dawo daga makaranta, ya xube jikinta yace "Antyna baki da lfya har ynxu," ta gyada masa kai da kyar, yace "to Anty idan na girma xan xama Doctor don na dinga baki magani idan baki da lfya ke da Ammina" Aneesah ta mike da sauri tace "A'a lawyer xaka xama yusuf don ka dinga kare ryt din mutane," ya mike tsaye da sauri yace "A'a na manta Anty soja xan xama don na kama baffa na dauresa nae ta dukansa na sa shi frog jump idan ya sake yi ma Ammi da ke ihu, kuma xan xama mai kudi na siya maku gida na dinga baku abinci kullum" Aneesah ta dinga dariya ta rungumosa tace "yauwa yusuf dina shi yasa nake son ka, Allah ya bar mu tare," Ammi ta dinga murmushi tana kallonsu, nn da nn Aneesah ta nemi xaxxabinta ta rasa, hka suka dinga hira yusuf na basu dariya da shirmensa har dare ya raba snn suka kwanta. Washegari Aneesah ta tashi da karfinta taji bbu wani sauran xaxxabi a tattare da ita, ta kama hanyar gidan aikinta bayan ta ajiye yusuf a sch, don ca yyi ita xata kai sa ranar baxae bi su jamia ba, hkn yasa ta fara ajiyesa bakin gate tayi peck dinsa tayi masa bye bye snn ta tafi gidan aikinta, har kusan rana bata ga Haiydar ba, da yake duk 'yan gidan sun tafi gantali daga ita sae pretty a gida tana tae mata hira, karfe hudu saura tana wanke wanke kafin 'yan gidan su dawo pretty na sama taji wani mugun xaxxabi na neman rufeta, ta dinga ganin jiri ga ciwon kai da ya sa ta kasa bude idonta, ta gama wanke wanken da kyar ta shiga garden ta xauna ta jingina jikin bango tana mayar da numfashi, a hka Haiydar ya xo ya sameta a garden din ya durkusa gabanta ba tare da ya bari sun hada ido ba yace "har ynxu jikin ne kanwata," bata ce masa komai ba kanta a sunkuye, xae yi magana motarsu Hajiya suka shigo gidan, ya mike da sauri ya shiga kitchen sae gashi ya fito da ruwa a glass ya fito da ledar magani ya balla ya durkusa gabanta yace "gashi ki sha kanwata hope kinci abinci," ba tace masa komai ba kuma bata karbi maganin ba, ya dinga rokanta yana lallabata ta sha maganin amma taki ko da dagowa ta kallesa sae hawayen da take tayi, ya mike yyi tsaki ta dalilin kiransa da yaji Hajiyarsa nayi a falo, bae sake shigowa garden din ba har karfe biyar saura, ganin baxa ta iya daurewa bne kuma yasa ta mike da kyar tana ganin jiri ta shiga falon tace ma Hajiya tayi hkuri xata tafi gida bata da lafiya, Hajiyar ta tsaya kallonta don duk wanda yaga yana yinta yasan bata da lfya, ta tabe baki xata yi magana pretty tace "momy ki bar ta ta wuce tun tuni take ta ma mutane amai kar taje ta sume mana a gida," Hajiyar tayi tsaki tace "to tashi sae ki gyara min daki snn ki tafi makira kawae," Haiydar ya mike yyi waje, ita ko ta shiga ta gyara dakin da kyar snn ta fito tayi masu sae da safe ta fita, sumy ta bita a baya, Haiydar na tsaye bakin gate yana jiranta, tana fitowa kuwa xae yi magana sae ga sumy, ya juya da sauri yana danna wayarsa kmr mai shirin kira, ita ko ta kama hanyar gida tana karanto addu'a a xuciyarta na Allah ya kai ta lfya ganin condition dinta, Haiydar ya galla ma sumy harara a fusace yace "uban me kike nema a nn," cikin ladabi kar ya maketa tace "kawata nake jira bata san gidan ba shi yasa na fito," yyi tsaki ya juya bae[truncated by WhatsApp] [9:30PM, 12/21/2016] Khaleesat: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 26..... Aneesah ta dauke idonta da sauri daga na sa ta sunkuyar da kai tana wasa da yatsunta, cikin tsawa hajiya tace "rainin wayon naki ne ya tashi shegiya xaki yi ma mutane shiru ki samu gaba kina kallo da daddaya da daddaya don uwarki" ta girgixa kai a raunane tana hawaye tace "kuyi hkuri hajiya wllh kanina ne ya rasu," cikin halin ko in kula Hajiya tace "to ni na kashe shi da xaki ki xuwa min aiki," Aneesah tayi shiru tana hawayen takaici, Hajiyar ta tabe baki tace "to ki sani baxan biya ki kudi cikin wnn watan ba sae karshen sabon watan da xamu shiga, bace min da gani kar na ji maki ciwo a nn mayya kawae ba kaninki ba uwarki da ubanki ma su mutu ina ruwan wani," Aneesah ta mike tsaye a sanyaye hawaye na bin kuncinta xata bar falon, cikin gadara meenah tace "kuma ga kayan wanki na can ya taru ba kyan gani, dasu xa ki fara," sumy tace "nima wllh gasu can duk ki hada yau ki wanke mana ni har da takalma na, kuma ki cire ma mutane wnn hijabin jikin naki duk ya janyo ma mutane duhu a falo," Aneesah dae na tsaye tana hawaye tana kallon sumyn cike da takaici kuma bata cire hijab din ba, sumy ta mike a fusace ta fixge hijab din daga jikinta ta wurgar tana huci tace "don uwarki ina maki magana xaki yi min shiru......" ba shiri sumy tayi shiru ta wara ido baki bude tana kallon gashin kan Aneesahn da ya xubo har kusan bayanta ta dalilin fixge mata hijabin da tayi hade da dankwalin kanta, meenah ta mike da sauri da mamaki tace "lala attachment ne a kanki kina matsayin yar aiki ni nasa ke ki sa," a fusace ta damko gashin Aneesar a xatonta kari tayi kmr yanda su ma ke yi, "wllh sae kin cire gashin nn ynxun nn a nn idan ba hka ba har gashin kanki sae na aske yau, dama munafuka shi yasa baki son cire hijab idan kika......" wani wawan marin da aka dauketa da ne ya sa ta kasa karasawa ta fasa ihu a gigice ta sake gashin Aneesar tana kallon wanda ya mareta yayanta ta gani tsaye kanta yana huci, ya fixgota ya buga ta da bango snn ya damki nata karin gashin dake kanta yana huci ya makureta cikin tsawa yace "uban me ta maki kike neman birkita mata kwakwalwa nake son ki gaya min kar na hallakaki a nn," Hajiya ta mike tana salati a rude tace "me xan gani hka Aliyu, meye hadinka da 'yar aikin nn xaka kashe kanwarka kanta," ya wurgar da meenar a fusace, ya dawo kan Aneesah da ke durkushe a wajen tana rusa kuka, ya durkusa gabanta ya dago kanta a hankali yana kallonta cike da tausayi yace "kiyi hakuri fateema," Hajiyar ta yo waje da ido baki bude tana kallonsu a tsorace ta daura hannu a ka tace "Aliyu," pretty ta mike a hankali ita ma tana hawaye ta bar falon ta haye sama, sumy ta mike tsaye ta fashe da wani wawan dariya tana kallon uwartata tace "heheho me na gaya maki mummy ba kin ki yarda dani ba, ni dama nasan da wani abun a tsakaninsu wllh, kin taba ganin yaya ya hana 'yar aiki yi mana aiki a gidan nn, ko kin taba ganin ya ci girkin 'yan aiki, ko 'yar aiki ta taba shiga dakinsa da sunan gyara masa ko yi masa guga, yaya bashi da aiki ynxu sae na xuwa garden, ni dama nasan da wani abu a kasa amma kika ki yarda dani da meenah, yau dae gashi kin gane ma idonki, shiyasa ranan nn ma na fita da sauri ganin ko bin ta xae yi a bakin gate nayi masa karya kwata nake jira, ba haushi na ya dinga ji ba har washegari na hana sa bin sahibarsa, a bnxa aka ce maki yake rashin lafiya kwanan nn," ta sake fashewa da dariya tana tafa hannu tace "kasala don burst" Aliyu ya yo kanta cikin fushi ya buga ta da bango da karfi, nn da nn se ga jini da gudu kmr famfo, daga ita har Hajiya suka rude Hajiya ta dinga rusa ihu tayi kitchen da gudu tana cewa "kan wnn matsiyaciyar xaka kashe min 'ya, wllh wllh wllh sae na hallaka ta yau," sanin halin uwartasa yasa ya ja Aneesar dake ta kuka da sauri suka bar falon, yyi garage ya bude motarsa don makulli na aljihunsa ya saka ta cikin motar ya xaga da sauri ya shiga ya tada motar yana horn ba kakkautawa, sae ga Hajiyar da gudu ta fito rike da tabarya da wuka, cikin tsawa ta dinga cewa maigadin kar ya bude gate din, Aliyu dake jiran ya karasa bude gate din kawae ya fice ya daka masa tsawa yace "xan take ka da motar nn baka bude min gate ba malam," maigadi duk ya rude ya rasa umarnin wanda xae bi ganin Aliyu ya yo kansa da motar yasa cikin ihu a gigice ya dinga cewa xae bude har ya wangala gate din jikinsa na rawa Aliyu ya fice da gudu ya bar compound din, kmr xasu tashi sama. [9:30PM, 12/21/2016] Khaleesat: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 28..... Aneesah ta shiga daki ta fito da tabarma ta shimfida masa ya xauna, Ammi ta fito ta dauko kujera ta xauna tanai masa sannu da xuwa murmushi bayyane a fuskarta, ya gaisheta a ladabe yana tambayar ya gidan, tace masa lfya lau ya nasu gida, yyi mata gaisuwan rasuwar yusuf, tayi masa gdya sosai daga bisanni ya sake bata hakura a kan abinda ya faru snn yyi mata sallama yace xae wuce, tayi masa gdya tace Allah ya saka da alkhairi snn ya fita daga gidan yana kallon Aneesah. Sae da ya fita snn a hankali tace ma Ammi bari ta rakasa Ammi tace mata to, ta mike ta bi bayansa, yana jingine jikin motar yana jiranta, ta karaso gefensa ta tsaya a sanyaye tace "nagode yaya Haiydar," yyi murmushinsa mai kyau yace "nima ngd fateema," ita ma murmushin tayi ta boye fuskarta, yace "Aneesah an rufe registration din waec din ne?" a hankali tace "nima ban sani ba," yace "ok find out frm yhur sch mates," tayi shiru bata ce komai ba, yace "Aneesah naxo gidanku ko ruwa baki bani ba, gashi dama yunwa nke ji, kin san bnyi break ba," ta xaro ido tace "lah ae ban san xaka sha ba, bari na debo maka," yyi dariya yace "wasa nake maki," ya bude motar ya fito da ledar Hijabs din ya mika mata tace "na me," yace "naki mana," ta marairaice tace "A'a ni dae wnn ya isheni wllh," ya harareta yace "ki karba wucewa xanyi," a hankali tasa hannu ta dan risina ta karba snn tayi masa gdya, yyi murmushi yace "welcm Aneesah, i wil be goin now," ta gyada masa kai ya bude motar ya shiga ta daga masa hannu snn ta juya ta shiga gida, shi ko yyi reverse ya bar anguwar, hanyar gidansa yyi, don yasan Hajiya na can kila ta tara masa mutane ana jirasa don ma ya kashe wayoyinsa. Aneesah na shiga ta nuna ma Amminta hijjaban, Ammi tace "shine xaki karbo Aneesah ni fa ba ruwana," Aneesah tace "wllh Ammi nace ya bar shi yaki," a hankali ta shiga fito da su tana dudduba, tana fito da na ukun knn bandir din dari biyar biyar ya fado, ta koma baya da sauri tana kallon Amminta, ammi tace "wnn kuma daga ina?" Aneesah tayi shiru tana kallon kudin snn ta dago tana kallon Amminta a hankali tace "shi ya saka Ammi," Ammi ta kasa cewa kmai sae kallon Aneesar da take yi, can dae ta mike ta shige daki kawae, Aneesah ta bi ta ta fashe da kuka tace "wllh Ammi ban san ya saka ba," Ammi ta girgixa kai tace "to ki ajiye masa kudinsa kar ki taba," Aneesah tace "to" snn ta ajiye hijabs din da kudin cikin jakar kayanta. Washegari da yamma ta je dibo ruwa a borehole tana dawo wa xata shiga gida taji an mata horn, ta juya da sauri tana kallon motar da mamaki, Haiydar ne, ya bude motar ya fito ya wara mata ido yace "me hannunki yake da xaki daura ruwa a kai Aneesah," tayi murmushi tana kallonsa bata ce komai ba ya karaso gabanta ya sauke mata bokitin ruwan ya ajiye kasa yana mata wani irin kallo, ta boye fuskarta da tafin hannunta tana 'yar dariya tace "xafi hannun xae min shi yasa na daura a kai," ya harareta yace "to karki sake," tace "uhum," snn ta dauki bokitin ruwan a hannu yace "bari na taya ki mana," ta ce "A'a ina xuwa," ta shiga gidan, bayan kmr minti biyar ta fito rike da leda tana kallonsa tace "jiya kayi mantuwa cikin ledar da ka ban," ya galla mata harara yace "Ammi na ba bake ba, ni ina ruwana dake," ta marairaice fuska tana kallonsa tace "dn Allah ka bari ka amshi kayanka ni dae," ya hade rai yace "ba fa na son hka Aneesah," tayi shiru tana kallon kasa, yace "ya maganar da na maki jiya na waec kin tambaya?" ta wara ido tace "na manta," yyi mata wani irin kallo yace "you re nt cerious," ya ciro wayarsa daya ya mika mata yace "idan kin tambaya kya kirani ki gaya min nmbrna na ciki xaki ga anyi save da barrister," ta xaro ido tace "A'a ni bana so wllh ka tafi da kayanka watarana idan kaxo xan gaya maka idan na tambaya," ya ajiye mata kan wani dutse yace "idan na tafi ki barshi a wajen, ki gaida min da Ammi," yana kai wa nn ya shige motarsa ya juya ya bar anguwar, tayi kmr xata yi kuka har ta daina ganin motar snn ta dauki wayar ta shiga gida dashi. Da daddare tana wanke wanke a tsakar gida Ammi na daki taji kamr motsin mutum a xaure, ta dan tsorata ta mike da sauri tana jiran taga wa xae shigo taga bbu kowa, a ranta tace to ko dae ya Haiydar ne, hkn yasa ta karasa da sauri don tunaninsa take lkcn, ta shiga xauren tana dan waige waige cikin duhu bata ga alamar kowa ba ta dan leka waje ta dae ga motar a parke amma ba na Haiydar bne, kuma ba a kusa da gidansu akayi parkin din ba, ta danyi tsaki ta juya xata koma cikin gidan taji ta ci karo da mutum ta tsorata sosae xata fasa ihu ya fixgota ya rufe mata baki a hankali yace "menayi maki xaki fasa min ihu," a tsorace ta koma baya tace "ya Abdul," ya wara mata ido cikin duhun yace "waww kin xama 'yan mata bbyn nn," ta turasa da karfi a fusace xata bar xauren ya fixgota yace "yaushe na fara wasa dake?" [9:30PM, 12/21/2016] Khaleesat: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 27..... Sun yi nisa sosai, kawae tafiya yake ba tare da ya san inda xa shi ba, Aneesah ko bbu abin da take sae aikin kuka, ganin kawae tafiya yake bai da alamar tsayawa yasa cikin muryar kuka tace "ni ka sauke ni a nn na wuce gidanmu," sae a snn yyi parkin gefen titi, ya juyo yana kallonta, ta rufe fuskarta tana ci gaba da kuka, ya kamo hannunta yace "ya isa hkan Aneesah kiyi hkuri, bana son kina kuka, nn" bata ce masa komai ba amma ta kasa daina hawaye, ya ciro handkerchief ya goge mata fuskarta yana kallon gashinta da duk da talaucinsu ba a haramta mashi gyara ba, don sae kyalli yake ga tsantsi snn baki wuluk, ta cire hannunsa daga kan gashin nata da ya dafa a hankali tace "hijabina," ya gyada mata kai kawae, snn ya ja motar suka bar wajen, sun danyi tafiya mai nisa snn taga yyi park yace "fito ki xabi wanda ki ke so," ta kasa cewa komai tana kallonsa, ya gyada mata kai ta fito a sanyaye daga motar suka fara tafiya a hankali taga duk ido ya dawo kansu barin ita, da sauri ta fixge hannunta tace "ni baxan iya ba, ban da dankwali," ya komar da ita motar snn shi yaje xabo mata Hijab din, bayan kmr minti goma ya dawo da katon ledar boutique a hannunsa ya shiga motar yana kallonta ta sunkuyar da kai, yyi murmushi ya bude mata ledar yace "gashi ki xabi wanda xaki sa," a hankali ta jawo wani milk colour taga yana da tsayi hkn yasa ta saka shi kawae, tana kallonsa ya gyada mata kai yyi murmushi snn ya tada motar suka bar wajen, sae da suka hau kan titi snn a hankali yace "ina ne gidanku?" ba tare da ta kallesa ba tace "ka ajiye ni a nn, sae na wuce," ya girgixa mata kai yace "baxa ki fita daga motar nn yau ba knn," ganin da gaske yake yasa ta gaya masa anguwarsu kawae in yaso sae ta karasa gida da kafa, "aneesah," ta ji ya kirata ta juya tana kallonsa, idonsa na gaban titi yace "me ya sami yusuf?" nn da nn taji hawaye ya ciko mata ta girgixa kai da kyar tace "mota ce ta bugesa suna dawowa daga sch," yace "mota kuma, to ina mai motar," ta goge hawayen idonta tace "bae tsaya ba, kuma withness sun ce da gangan ya buge sa bayan ya bugesa kuma ya taka sa ya gudu," yyi parkin da sauri yana kallonta, ta sunkuyar da kanta tana ci gaba da xubda hawaye, yace "baffanku ya samu lbri," tace "eh amma bae xo ba har ynxu wae matarsa tace ya tafi lagos, kawae baffa ibrahim ne ya xo shima shekaranjiya yace gangancinmu ne ya kashe yusuf," Aliyu ya gyada kai bae ce komai ba ya ja motar suka bar wajen, har suka isa anguwar bai sake ce mata komai ba, sae da yyi da gske da ita snn ta nuna masa gidansu don ca tayi ya ajiyeta xata karasa da kafa, tace masa tana xuwa snn ta shiga cikin gidan, Ammi na share tsakar gidan don ita har lkcn bata koma aiki ba sun bata hutun wata daya ne, ta mike tsaye tana kallon Aneesar da mamaki tace "me ya faru Aneesah," Aneesah ta kirkiro murmushi don bata son daga ma Amminta hankali, suka shiga dakin snn tace "Ammi tun safe baki gama aikin ba ashe," Ammi tace "ki gaya min Aneesah me ya faru ga idanuwanki duk sun kumbura kice min bkm," Aneesah ta sunkuyar da kai gudun kar ta fara hawaye kuma, a hankali cikin nutsuwa tayi ma Amminta bayanin abinda ya faru, ammi tayi shiru tana kallnta da tausayi snn tace "shi kuma me ya biyo ki yi Aneesah," ta goge hawayen idonta tace "nima ban sani ba," Yana waje Ammi, Ammi tace "to shknn kice ya shigo," ta mike a sanyaye ta fita gidan tayi hanyar motarsa, tace "Ammina tace ka shigo," yyi murmushi ya fito daga motar ya rufe snn ya bi bayanta suka shiga gidan a tare. [9:30PM, 12/21/2016] Khaleesat: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 25..... Aneesah ta fara kkrin mikewa xaune, makwabciyarsu maman salim tayi saurin kamata tanai mata sannu, da kyar take bin dakin da kallo tana kkrin tunano abinda ya faru don kanta yyi mata nauyi sosae, a hankali komai ya dawo mata, murya can ciki ta kama hannun matar dake gabanta tana kkrin mikewa tsaye tace "ina yusuf," matar ta komar da ita ta xaunar tace "Haba Aneesah so kike ki daga ma Amminki hankali ne yusuf addu'a xakiyi masa kawae " Aneesah na jin hka ta fasa mata ihu a gigice tana girgixa ta tace "don Allah ku gaya min me ya sami yusuf dina," duk matan dakin suka yo kanta suna lallashi amma kamar ana sake tunxurata don ihu ta dinga masu tana kuka cikin daren har makwabta da yan unguwa sun fara shigowa, Ammi dae har lkcn tana xaune kan darduma tana nata kukan, ganin abun nata ba na hankali bne yasa daya daga makwabtansu maman yazid ta fara mata magana cikin fada "haba Aneesah so kike ki daga ma Amminki hankali ne ki sa ta cikin wani yanayi ita ma ko me, da wanne xata ji, mutuwar danta ko haukanki, ihu da birgimar taki ce xata dawo da yusuf ko me, don me baxa ki ji tausayin amminki ba ki rarrasheta ku rungumi kaddara, sae kace ba musulma ba, ynxu dae yusuf ya rasu addu'a kadae xakiyi masa ba ihu da birgima ba," a hankali Aneesah ta fara nutsuwa tana kuka a hankali, hka suka taru suka dinga mata nasiha da bata baki, daga karshe suka ce taje tayi alwala tayi sllh tayi ma kanninta addu'a" jiki ba kwari ta mike ta fita daga dakin xuwa yin alwalan, ranar daga ita har Amminta xaune suka kwana bayan kowa ya watse, ta kasa daina kuka yi take kmr ranta xae fita, ganin kukan da take yi ne ke sa Amminta kuka yasa ta daina kukan da kyar ta dawo gefen Amminta ta xauna tana kallonta, Ammin ta rungumota a hankali tace "ya isa hka Aneesah, addu'a xamui wa yusuf kinji, Allah yasa karshen wahalarsa knn," ta gyada ma amminta kai a hankali, a hka bacci ya kwasheta jikin amminta kusan asuba. Yau akayi sadakan bakwan yusuf amma har lkcn Aneesah ta kasa sa ma kanta nutsuwa ba karamin girgixa ta mutuwar kanin nata yyi ba, sae a lkcn ta gane ashe sign din mutuwar kaninnata ta dinga ji kwanakin baya take ta ciwo ita da Ammi, Ammi kam har ta gaji da lallashinta ta sa mata ido ganin abun nata bana karewa bane don komai na yusuf ta kwashe a gidan ko hkn xae sa Aneesar ta nutsu idan ta daina ganinsu amma duk a bnxa , duk da ita ma daurewa kawae take barin idan taga 'yar tata na kuka, ita ko Aneesah irin mutuwar da yusuf yyi ne kadae ke bata takaici. Bayan sati biyu da rasuwar yusuf Aneesah na xaune bakin kofar dakinsu Ammi kuwa na cikin daki tana masu linki ta kirata ganin tun da gari ya waye take xaune bakin kofar, Aneesah ta mike da sauri ta shiga dakin ta xauna tace "gani Ammi," Ammi ta harareta tace "kuka kike yi komai," ta girgixa kanta da sauri duk da kukan ta gama tace "A'a ni ba kuka nake yi ba Ammi," cikin lallami ammi ta fara magana "Haba Aneesah so kike ki janyo ma kanki wani ciwon ko, ya kike son nayi da rayuwata idan ke ma na rasa ki," ta fashe da kuka tace "na daina daga yau Ammina amma idan na xauna kullum nakan yi tunanin me yusuf yyi ma baffa da xae turo a kashe shi," cikin fada Ammi tace "wa yace maki baffa ne ya turo a kashe shi, ni fa bana son surutun bnxa, daga mota ta bugesa ta gudu kuma sae ya xamanto baffa ne yasa a xo a bugesa a gudu," tace "Ammi wlh shine, da gangan fa aka ce mai motar ya bugesa snn kuma ya take sa, Allah ya isan ma," Ammi tace "ni dae ki tausaya min ki daena sa ma kanki damuwa Aneesah in ma shi ya sa a kashesa din don kansa, ynxu abinda nke so dake gobe ki shirya ki tafi wajen aikinki kin ga yau sati biyu rabon ki da xuwa kuma bbu ddi hkn, sae kiyi mata bayanin abinda ya faru," Aneesah tayi shiru gabanta na faduwa jin an kira mata gun aikinta, can dae tace "to Ammi," washegari Aneesah ta shirya ta kama hanyar gidan aikinta gabanta na faduwa, jikinta a sanyaye ta shiga gidan bayan ta gaida mai gadin, ta karasa stairs din balcony ta hau ta tsaya bakin kofar falon xuciyarta na bugawa ta kasa shiga, da kyar tayi shahada tayi sallama ta shiga falon tana addua a xuciyarta da ya kasa daina bugawa, suna xaune gaba dayansu a falon hankalinsu kwance suna kallon tauraron dan adam, Haiydar na kwance kan kujera amma shi ba kallo yake ba idonsa a lumshe, duk suka juya suna kallonta ta karaso cikin falon a sanyaye ta durkusa tana gaida Hajiyar da ke ta girgixa kafa tana mata wani mugun kallo, ta sunkuyar da kanta da sauri ta rasa ta ina xata fara ma, cikin tsawa meenah tace "don uwarki ki fice mana gaban TV ko baki ga abinda muke yi bane wawiya kawae," ta ja gefe a hankali hawaye ya cika idonta ta juya tana kallon Haiydar da ya tsura mata ido. [9:30PM, 12/21/2016] Khaleesat: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 32..... Aneesah ta fixge hannunta tana masa wani mugun kallo gabanta na faduwa tace "ka fitar mana a gida kar na maka ihu malam, wnn ai iskanci ne da rashin tarbiya, xaka fado mata mutane gida kamar barawo," ya wara idonsa da mamaki yana kallonta, "ni kike ce ma barawo," ya tambayeta yana kallon cikin idonta, tayi tsaki ta juya xata bar wajen ya fixgota ya watsa mata mari, tare da hadeta da bango yana huci, "ke kinsan ko da wa kike magana don uwarki kuwa," cikin kuka tace "na sani mana, mugu, axalumi, mara tarbiya, masu cin dukiyar marayu....." wani gigitattcen marin ya sake wanke ta da a fusace yana huci, ya shake wuyarta yana kallonta da kyau xae yi magana, aka shigo gidan, Haiydar ne, ya tsaya daga bakin kofar xauren ya rungume hannayensa yana kallonsu, Aneesah dake ta faman kuka ta juya tana kallonsa tana ci gaba da rusa kukan, Almajirae ne suka shigo gidan rike da kayayyakin abinci tun daga kan, buhun shinkafa, cartons din taliya man gyada, da doya, Haiydar ya ja gefe ya basu hanya suka shigo gidan suka dire kayan abincin, ya ciro dubu uku ya mika masu hade dacewa tnk yhu, suka yi godiya suka fice daga gidan, Abdul da ke ta bin Aliyu da kallo ya yatsine fuska a walakance yana kallon Aneesah cikin tsawa yace "waye wnn kuma," bae rufe bakinsa ba Haiydar yace "Barrister Aliyu Muhammad, kai fa?" ya tambayesa yana masa wani irin kallo, Abdul yyi wani mugun murmushi ya sake Aneesar da har lkcn yana rike da ita yace "uban meye hadinki da wnn," xata yi magana Haiydar ya riga ta, "abinda ya hadata da kai shi ya hadata ni," Abdul yyi masa kallon tsab daga sama xuwa kasa snn ya fashe da wani wawan dariya yace "xamu gani," snn ya juya a fusace ya bar gidan, Aneesah ta sulale kasa a hankali ta hade kanta da gwiwa tana kuka, Haiydar ya karaso gabanta ya durkusa ya dago kanta yace "bana son kina kuka Aneesah, ki kwantar da hankalinki bbu wanda ya isa ya cutar min ke kinji kanwata" tayi shiru bata ce komai ba tana kallonsa, ya ciro hankici ya share mata fuskarta snn ya mike tsaye yace "Ammi fa," a hankali tace "ta tafi kasuwa," ya durkusa gabanta kuma a hankali yace "kinsan me Aneesah, ki daina tsayawa gida ke daya, duk inda Ammi xata kuje tare ," ta gyada masa kai ta dan yi murmushi tace "to yayana," ya dagota shi ma yana murmushin ya ja ta xuwa kan tabarman da take xaune da litattafenta, suka xauna ya jawo books din yana dubawa, binshi kawae take da kallo, ya dago kai suka hada ido ta rufe fuskarta da sauri tana 'yar dariya. Abdul ne xaune kan kujera yana kallon ubansa dake ta fama latse latsan laptop, baffa ya dago yana kallon Abdul din yace "ya aka yi guy?" Abdul ya tabe baki yace "ca nayi ina son cikin satin nn, ka daura min aure da Aneesah, da ita xan koma london, don aure nake so, kuma ina sonta," baffa ya mike a fusace yace "Aneesah, wacece Aneesah, uban me xaka yi da Aneesah, ba gwara ka kawo min baturiya ba kace na aura maka ita, Aneesar bnxa" Abdul ya mike ransa a bace yana nuna uban nasa da dan yatsa yace "kaga dad, Aneesah nace maka xan aura, kuma ita xan aura, wnn ai mgnr kawae kke min, ni fa xan xauna da ita ba kai xaka xauna min da ita ba," baffa ya sauke ajiyar xuciya ransa a jagule yana dan kame kame yace "look guy bae kai ga hka ba, kar ka damu xan aura maka Aneesah vry soon, amma ba ynxu ba sae nn da wata daya," Abdul ya buga table din gabansa, a fusace yace "y one month dad, da ita nke son komawa london nace maka, ko baka gane bne," baffa yace "cool down son, yau fa satinka biyu, kafin ka koma xan aura maka ita, kuma sati biyu xakuyi a nn kafin wata biyun hutunka ya cika, nafa san abinda nake yi," Abdul ya koma ya xauna yana murmushin mugunta yace "vry good dad." baffan ya kirkiro murmushi yyi pat din bayansa yace "gud son xan fita guy, sai na dawo," yana kai wa nn ya fice daga dakin da sauri. Abdul ya mike tsaye yana murmushin mugunta hade da cije lebe, can kuma ya fashe da dariya har da buga kafa snn ya fice daga dakin yana fi to. Hmm sistrs knn, ku dinga ma mutum uxuri plss, ku ka san abinda ya hanani post kwana biyu, rashin lfya ne, wani abun daban ne, duk baku yi tunanin hka ba, amma har na samu masu gaya min magana a whatsapp, wasu har da cewa xa suyi xuciya su daina karanta littafin khaleesah Haiydar, hmm ok oo, baku yi tunann ko ina da aure ba ko ina da yara da burden dinsu baxae bari nayi type ba wani lkcn, ni dae don mu nishadantu kuma don na fadakar nake yin wnn abun, amma Allah sarki makiyana sun fi masoyana yawa, duk da hka ina sonku gaba daya, Allah ya bar [truncated by WhatsApp] [9:30PM, 12/21/2016] Khaleesat: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 31..... Hajiya Zuwaira ta bude baki da mamaki tana kallon Aneesah, har ta gama fadin abinda ke ranta snn ta fice daga dakin har tana neman bangajeta, hajiyar ta rike haba da mamaki tace "ni 'yar nn ke gaya ma magana hka? Haiydar ya juya yana kallon Ammi dake xaune har lkcn bata bude baki ba yace "yauwa muna magana Ammi," Ammi tace "uhum ina jinka Aliyu," yace "ko kuma ma dae bari xan dawo xuwa anjima Ammi, sae muyi maganar," yana kai wa nn ya mike ba tare da ya kalle Hajiya zuwairar da har lkcn bakin ta yaki rufuwa ba ya fice daga dakin, Hajiyar tayi murmushin takaici tace "xa ku gane kuranku in dae ni ce zuwaira " tana gama fadin hka ta juya fuu tayi hanyar fita daga gidan tana huci, Aneesah dake xaune kan kujera a tsakar gidan tana hawaye Haiydar na durkushe gabanta yana mata magana suka bita da kallo har ta fita, Haiydar yyi murmushi yace "hmm mu je dae xuwa," ya mike ya koma cikin dakin Aneesah ta bisa da kallo, ya dde cikin dakin ko me yake ce ma Ammi, can dae ya fito yana kallonta yace "je dauko Hijab Aneesah," ta tsura masa ido tana kallonsa ya gyada mata kai, ta mike jikinta a sanyaye ta shiga dakin dauko hijab, ta xauna gaban Amminta tace "Ammi yace na dauko hijab," Ammi tace "Sae kun dawo ki kula da kanki Aneesah," Aneesah ta mike a hankali tace "to Ammi" snn ta fita, makaranta ya kai ta yyi mata registrn waec da neco, snn suka dawo gida wajen karfe sha daya na safe bayan tayi registre din lesson din makarantar kafin a fara jarabawan, ta rasa irin godiyar da xata ma Haiydar kawae ta fashe masa da kuka bayan yyi parkin, nn ya barta kofar gidan nasu ya wuce don bai ga abinda take ma kuka ba a nn. Da yamma tana xaune tsakar gida tana duba litattafenta don gobe xata fara xuwa lesson din daga karfe tara xuwa karfe biyu na rana, Ammi kuwa ta tafi kasuwa, taji an bude kofar xaure a tunaninta Ammi ce ta mike da sauri karbo kayan hannunta ta kusan cin karo da mutum, ta koma baya da sauri, Abdul ne, ta juya xata bar wajen gabanta na faduwa ganin Amminta bata nn ya fixgota ya hada da bango yana mata wani irin kallo, tuni jikinta ya dau rawa amma ta dake tace "meye hka xaka fado ma mutane gida ba sallama," ya take mata kafa da takalminsa tayi yar kara yana rike da kafadarta yace "daxun wani rashin kunya kika yi ma momyna?" ta galla masa harara gabanta na faduwa a xuciyarta tana ta adduar Allah ya dawo da Ammi a lkcn, a fili kuma tace "ni ka sake ni don Allah malam," ya fixge dan kwalin kanta yana mata wani mayen kallo yace "uwata kika yi ma fitsara daxu ko," tace "ni ka rabu dani" ya daura hannu kan gashin kanta yana shafa gashin yace "wae ma wani mutumi ne ya xo gidan nn daxu da safe?" ta buge masa hannu a tsorace tace "wae me nayi maka xaka takura ma rayuwata hka ne," ya juya yana kallon kofar dakinsu yace "uwarki fa?" da sauri xuciyarta na bugawa ta galla masa harara tace "bacci take," ya daga kafada ya kamo hannunta yana kallon cikin idonta yace "we re goin out now, xaki dan rakani nn cikin gari" Like · 7 · Report · 44 minutes ago [9:30PM, 12/21/2016] Khaleesat: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 30..... Ya karaso gabanta ya tsaya yana dan bubbuga kafa a kasa yana mata wani irin kallo, bata ko daga kai ta kalle inda yake ba ta karasa alwalanta ta mike xata shiga daki ya kamo hannunta, murya kasa kasa yace "baki da respect yarinyar nn ko, baki ga mijinki bne?" ta fixge hannunta a fusace ta daka masa tsawa "wae ni ka rabu dani mana malam, a ina na san ka," xae yi magana Ammi ta fito daga daki tana kallonsu, tace "xo ki wuce ciki," Aneesah ta wuce sa da sauri ta shige daki, ya tsaya yana ma Ammin kallon rainin wayo, can yyi dariya yace "hope kin shirya rabuwa da 'yar ki ynxu Hajiya maryam," Ammi bata ce masa komai ba ta juya ta shige dakin ita ma ta rufo kofar. Ya karashi dariyarsa ya fice daga gidan, Ammi ta dubi Aneesah da ta xauna tayi jigum bayan ta idar da sllh tace "shi yasa nace ki shirya ki wuce gombe Aneesah, ko xuwa gobe xan baki kudin mota ki tafi," Aneesah bata ce komai ba sae dae hawaye ya taru idonta ta sunkuyar da kanta da sauri gudun kar Ammi ta gani, ranar kasa bacci Aneesah tayi, tunanin rabuwa da Amminta da ya Haiydar take cikin 'yan kwanakin da basu wuce wata daya ba ba karamin shakuwa tayi da Haiydar ba, ita kam dawowar Abdul ba karamin tashin hankali bane gare ta, tun tana karamarta dama ta tsane shi don bae da kamun kai ga son mata, da kyar Aneesah ta iya tashi washegari don ji tayi duk jikinta ba kwari, karfe takwas tana xaune koko da kosae a gabanta ta kasa ci sae jujjuya kosan take, Ammi ko na ta faman hada mata kayanta, wayan da Haiydar ya bata ya shiga ring ta juya da sauri tana kallon wayar, Ammi tace "ba na ce ki mayar masa da wayarsa ba Aneesah," a sanyaye Aneesah ta ce "dama yau xan maida masa Ammi, shi ne ma ke kiran," ta daga wayar suka gaisa yace gashi ya kusa anguwarsu, ta wara ido tana kallon Ammi tace "yanxu?" yace "ko na juya," ta girgixa kanta a hankali tace "A'a ni ban ce ba," yyi murmushi ya kashe wayan, ta juya tana kallon agogo ammi tace "me ya faru kuma?" ta sunkuyar da kanta tace "kila wayar xae xo karba yace yana hanya," Ammi bata sake cewa komai ba ta ci gaba da abinda take, yana parkin kofar gidansu ya kirata ta saka hijab ta fita jikinta a sanyaye bayan ta nemi ixini gun Amminta, ya fito yana kallonta yace "me ya faru Aneesah," tace "ba komai kai na ne ke min ciwo kawae," yace "Ayya kin sha magani to?" ta gyada masa kai kawae tana kallonsa, yana sanye ne da bakar suit yyi kyau ba kadan ba, yana kallonta yace "Ammi fa," ta jingina jikin motar tace "tana ciki," wae jikin ne hka Aneesah," ya tambaya da damuwa, tace "A'a ae na sha magani," yace "to Allah ya sauwake, hope kin shirya kin ga aiki xan tafi," tace "na shirya me?" ya dan harareta yace "kin fasa xana waec din ne, registratn xa muje muyi," tayi shiru tana kallonsa a raunane tace "kaga gombe xan tafi yau fa," yace "gombe kuma, me xaki je yi a gombe," ta fara hawaye tace "Ammi ce tace na tafi," yyi shiru yana kallonta can yace "Ammi tana ciki," ta gyada masa kai kawae yace "can i go in," nn ma ta gyada masa kai ya shiga gidan tana biye da shi a baya, har daki ya shiga ya gaida Ammi ta amsa da fara'arta tana tambayarsa mutan gidan yace "duk lfya suke Ammi," Ammi tace "to madallah," ya danyi shiru snn yace "Ammi na xo ne xamuje registratn na waec tace min gombe xata tafi, don Allah Ammi ki bar ta ta xana exam dinta ko akwae abinda xata yi a can ne," Ammi ta girgixa kai tace "bbu Abinda xata yi a can Aliyu wajen kakata da ta rikeni xata ne, xuwan ta can xae fi mana kwanciyar hankali daga ni har itan," yace "sbda me Ammi," Ammi tayi shiru tana kallon Aneesar dake hawaye, xata yi magana taji an shigo gidan ana kwala mata kira, maryam, maryam, maryam, Ammi bata yi kkrin mikewa daga inda take ba jin muryar me kiran nata, matar baffa shehu ce, ta shigo dakin a fusace ta tsaya masu bakin kofa tana nuna su da dan yatsa, "wllh wllh ko ma uban me ku ka yi ma dana tun wuri kuje ku karya shi idan ba hka ba xa ku sha mamaki daga ke har 'yar ki, kaji mun talakokin banxa makwadaita, uban me Abdul dina xae yi da wnn shegiyar 'yar taki, wllh tun wuri ku koma wajen bokan da kuka je ya lalata aikin da yyi maku," Aneesah da ta kasa daure jin irin bakaken maganganun da matar baffanta ke gaya masu tace "ke wae ance maki kowa ma irin ki ne mai xuwa wajen boka, ko kuma uban me ma xanyi da dan naki da baki baki masa tarbiyar arxiki ba sae ta tsiya, kin xo kina ta ma mutane haushi uwa kare a gida, wllh na fi karfin dan ki Abdul, kuma da na auri Abdul gwara na aure mahaukaci mara hankali" [9:30PM, 12/21/2016] Khaleesat: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 33.... Aneesah ce xaune kan tabarma a tsakar gida tana ta faman jujjuya littafin biology dake hannunta a sunan karatu, duk hankalinta baya jikinta, don rabon da taga Haiydar yau sati uku cif, kuma bai taba ddewa hka bae xo gidansu ba, snn bata san inda ta jefa wayar da ya bata ba ma Ammi na kitchen tana girkin dare da yake wajajen karfe biyar da rabi na yamma ne, ta mike a sanyaye jin kiran da Ammi ke mata ta karasa kitchen din, Ammi tace "ruwa xaki debo, kin dae san ba ruwa a gidan, na rasa wani irin karatu kike yi tun karfe uku," Aneesah bata ce kmai ba ta dauki bokitin ta juya xata bar gidan, Ammi ta kirata ta dawo tace "na'am Ammi," Ammi ta juyo tana kallnta tace "ki gaya min me ke damunki Aneesah duk kwanan nn na rasa gane maki, idan ma Aliyu ne ae addu'a xakiyi Allah yasa lfya Aneesah," ta gyada ma Ammi kai tana kkrin maida hawayen dake kkrin xubo mata ta juya ta bar gidan da sauri, har ta daura ruwan a ka bayan ta debo ta tuna warnin din Haiydar ta sauke a hankali ta rike a hannu ta kama hanyar gida, tana isa kofar gidansu ta ga mota a parke gabanta ya fadi, Allah yasa yayanta ne ta fadi a xuciyarta, ta tsaya tana kare ma motar kallo ganin bata taba ganin Haiydar da irin motar ba, Abdul ne ya fito kmr wani sarki yana mata wani irin kallo, ta ja dogon tsakin takaici ta dauki bokitin ruwanta xata shiga ciki yace "hey!" har ta shiga xauren ta fito don bata son ya shigo cikin gidan nasu yyi ma Ammi wlkncin da ya saba, yyi yar dariya yana kallon cikin idonta lkci daya yana takowa ixuwa gabanta, ita dae tana tsaye har ya karaso gabanta yace "Amaryata yane, me kike bukata, kinsan nn da asabar xaki xamo matata" tayi murmushin takaici ta ma rasa abinda xata ce masa, can ta tabe baki tace "yhu had beta wake up frm ur slumber," tana fadin hka ta ja tsaki ta juya xata shiga gidan ya fixgota, suna kallon juna, yyi murmushi mai sauti yace "we shall see 'yan mata, ina barristern naki" bata sake sauraransa ba ta shige gidan da sauri ranta a jagule, tun da suka fara exam sa ti uku knn kusan kullum sae Abdul ya xo mata da wnn maganar me tsoratata, tana shiga da ruwan hannunta bata sake komawa debo wani ba ta shige daki ta kwanta tana kuka a hankali, anya kuwa xata karasa waec din nn lfya kuwa, don ji tayi duk xams din ya fita ranta.... [9:30PM, 12/21/2016] Khaleesat: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 35..... Ya karaso gabanta ya durkusa yana kallonta, har lkcn bata dago ba idonta na kan littafinta, ya fixge littafin yace "bby baki ganni bane?" tayi tsaki tace "kai din bnxa me xan mka," tana fadin hka ta mike tayi hanyar daki yyi murmushi yace "Ahaf ranar asabar xan sauke maki wnn rawan kan ka tsiwar dake damunki yarinya," yana fadin hka yyi dariya ya fice daga gidan, Ammi ta mike xaune tana kallon Aneesar da ta shigo dakin ta fashe da kuka duk da tana jin duk abinda Abdul din yake fadi tace "me ya faru Aneesah," cikin kuka tace "Ammi ca fa yyi wae xuwa ranar asabar xan xama matarsa ni bn gane me suke nufi da mu ba, kullum ya xo gidan nn maganarsa knn fa Ammi," Ammi tayi shiru tana kallonta can tace "ba gobe xaku gama jarabawan ba," Aneesah ta gyada kai tana hawaye, Ammi tace "to sae ki wuce gombe goben kawae, bna son tashin hankali," a hankali tace "to Ammi Neco fa" Ammi ta galla mata harara tace "ae ba dole bane sae kinyi Neco," Aneesah tace "hka ne," Ammi tace "don hka gobe kina dawowa daga makarantar xaki wuce gombe," to kawae tace ma Ammi ta kwanta jikinta a sanyaye, can kuma ta juyo tana kallon Ammin tace "to Ammi ya Haydar fa?" ba tare da Ammi ta kalleta ba tace "xan masa bayani idan ya xo goben," Aneesah bata sake cewa komai ba ta kulle idonta da xumar bacci, duk da tasan ba barcin xata yi ba, ita dae taga rayuwa. Abdul ya shigo falon Abbansa cikin gadara ya xauna yana kallon iyayen nasa dake ta binsa da kallo tun shigowarsa falon, yana shafa sajen dake kwance luf luf a fuskarsa ya daga masu kafada yana kallonsu ganin irin kallon da suka masa yace "ya?" Hajiya zuwaira tayi murmushi tace "daga ina hka Guy, tun tuni nake ta cigiyarka a gidan na kira wayarka kuma baka daga ba," ya tabe baki yace "naje gun local Amaryar nn tawa ce, ta ma bata min rae kawae a bnxa, ni don dae kawae ina da dalilin da yasa nake son ku aura min ita ne amma wnn 'yar kauyen ba class dina bace wllh," baffa ya dan sace kallon matar tasa ya ma rasa mai xae ce, hajiya xuwaira ta kirkiro murmushi ta fara kame kame "uhm, amm, guy ni kam na rasa dalilin da kke son auren Aneesar nn, har karuwanci fa tayi wllh, ni kar taje ma ta goga maka wani cutan ta cuceni kasan kai daya Allah ya bamu, da xaka ji ta nawa Abdul da......." ya mike a fusace cikin tsawa yace "da xan ji ta naki me, ni fa ku bar gaya min maganar bnxa, jibi fa dad yyi min alkawarin aura min ita, xaki kawo min wnn maganr taki mara ma'ana, ca nayi maki sonta nake yi dama to, ni kadae nasan abinda na shirya a kanta don hka duk wanda yace xae bata min plan dina wllh......" da sauri baffa ya mike yana dan buga kafadarsa ciki lallashi yace "cool down my guy, ynxu wa yace mka baxa a aura maka ita ba, daxu baka ga baffanka ibrahim ya xo ba dasu sambo, ai duk kan maganar daurin auren ne, ka kwantar da hankalinka insha'Allahu ranar juma'ah Aneesah taka ce my son" Abdul yyi murmushi yace "gud dad," snn yayi ma Hajiyar wani irin kallo ya fice daga falon, Hajiya xuwaira ta fashe da kuka tana salati tace "shknn na banu Alhaji, ynxu wnn tsinanniyar yarinyar Abdul xae auro mana, to me suka yi ma Abdul dina hka, kuma kafa san namiji wawa ne duk irin tsanar da xae mata lkcin da xata koya masa sonta ma ba sani xae yi ba, ni dae na shiga uku ni zuwaira," baffa ya harde hannayensa yana jijjiga kafa ransa a jagule, can ya mike shima ya fice daga falon.. Haydar yyi parkin a hankali yana hararan kofar shiga falon nasu kamr yyi masa laifi, can yyi tsaki ya fito daga motar yyi hanyar balcony a xuciyarsa yana cewa forsaken home knn, ya shiga falon da sallamarsa yana kallon agogo, yau satinsa uku rabonsa da gidan, suna xaune falo gaba dayansu suna kallo, pretty ta taso da gudu taxo ta rungumesa cike da farin cikin ganinsa, ya shafa kanta yace "ykk bbyna," sumy da meenah suka tabe baki a tare suka maida hankalinsu ga kallon da suke yi, Hajiya ta taso da murnarta tana masa sannu da xuwa, ya hade rai yana amsawa ba tare da ya kalleta ba, yyi hanyar stairs pretty na biye da shi yaji wani siririyar murya na masa sannu da xuwa daga cikin falon, ya juya da sauri yana kallonta, ya juyo yana kallon pretty yace "wnn kuma fa," pretty tayi wani irin dariya can ciki tace "ohon masu," bbu yabo bbu fallasa yace "yauwa," snn ya juya xae haura sama Hajiya ta dakatar da shi, hka ake yi Haiydar baxa ka tsaya ku gaisa ba, cikin fushi yace "to saninta nayi da xan tsaya mu gaisa," Hajiyar ta tabe baki tace "to matar da na xaba maka knn ko kaki ko kaso, ko shi Alhaji usman bae maka bayani bne a can kanon, xaka shigo kana cika kana babbatse ma mutane, ga ta nn sunanta zeenah, 'yar gidan Aminiyata ce kuma sae da na nemi shawara gun Alhaji usman shi ya bani go ahead din yin komai, don hka nn da wata daya ne bikinku tunda kai baka san ciwon kanka ba, degree fa gareta nn da kke ganinta, kuma da ka san irin mutanen dake nemanta da da gudu xaka amince mata, daxun nn ta xo gaisheni nace ta bari ta kwana kawae tunda na samu lbri gun Najeeb cewar yau xaka dawo." Like · Report · Just now [9:30PM, 12/21/2016] Khaleesat: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 34.... Ba ita ta fito daga dakin ba sae da aka kira maghrib shima ta dalilin kiran da Ammi tayi mata ne, har lkcn ammi na tsakar gidan xaune, Aneesah tayi alwala ta koma ciki tayi sallah, tana idar da sllh Ammi ta kuma kiranta ta fito, Ammi tace "ki je ga abincin ki can a kitchen ki dauka, saura kiyi min irin na daxu wllh sae na bata miki rae," Aneesah ta juya ta koma cikin dakin tana cewa "ni sae na fara wanka Ammi," ammi bata ce mata komai ba ta fito daure da xani da dankwali, ta shiga bayi yin wanka bayan ta juye ruwan da Ammi ta daura mata a raguwan garwashin da tayi girki. Tana fitowa tayi dan shafe shafenta ta saka rigar barcinta, ta bata lkci ssai don bata son cin abincin har aka kira isha'i tayi sallahnta, Ammi ta shigo dakin fuskarta a daure rike da kwanon abincin ta dire mata a gaba, snn ta sa ta gaba sae ta cinye tuwon snn ta tashi, Aneesah ta hade rae kmr xata yi kuka ta kauda kanta bata ce kmai ba, Ammi dae bata ko kalleta ba tana jiran ta gama cinye tuwo ta bata kwanonta, ta jawo tuwon a hankali ta bude xata fara ci aka yi sallama cikin gidan, dan makwabciyarsu khabir abokin yusuf ne ya shigo gidan, nn da nn Aneesah ta sake fuska tana murmushi tace "khabir daga ina hka," tana son yaron ssai tun bayan rasuwar kaninta don yusuf bashi da abokin wasan da ya wuce khabir, yyi dariya yana nuna mata gibinsa ba tare da ya kula da Ammi ba yace "Antyn yusuf ina wuni," ta rungumosa a sanyaye kiran sunan yusuf da yyi tace "lfya lau khabir dina, daga ina," yace "wani mutumi ne yace na kira ki a waje," ta dan xaro ido tace "ni khabir," yaron yace "eh mana ke yace na kira, da katoton mota ya xo, kuma dogo ne kmr teachern su anty jamila na sch, ya sa glass da farin kaya, kuma yyi hka..." ya mike da sauri ya rungume hannayensa biyu a dan kirjinsa yana gwada mata yanda mutumin yyi, Aneesah ta dago a sanyaye tana kallon Ammin da ta xuba masu ido tana kallo, Ammi tace "waye?" Aneesah ta sunkuyar da kai tace "ya Haiydar ne ina ga," Ammi bata sake cewa komai ba, Aneesah ta mike ta dauki hijab dinta tace "xo muje khabir," ya bita suka fice daga gidan, yana jingine jikin motarsa har lkcin ko yana rungume da hannayensa, ta karaso a hankali ta tsaya gabansa tana kallonsa, yyi murmushi yana kallon khabir yace "yauwa gud boy, ga shi ka siya biscuit," ya ciro naira dubu ya mika masa, khabir din ya juya yana kallon Aneesah yace "na karba Antyn yusuf?" ta kirkiro murmushi tace "ka karba khabir," ya karbe daga hannun Haiydar yyi godiya ya bar wajen a guje, Aneesah ta sunkuyar da kanta murya can ciki ta gaishesa, ya amsa yana murmushi yace "Ammi fa," ta kauda kanta tace "tana ciki," yana kallon cikin idonta yace "ina wayar da na baki Aneesah," kanta a kasa tace "ban san inda yake ba," yyi murmushi yace "mu je ciki to," ta juya da sauri tana kkrin maida hawayen dake baraxanar gangaro mata, ya bi bayanta har suka shiga xauren snn ya riko hannunta ganin irin saurin da take, ta tsaya shima ya tsaya, ganin bai ce komai ba yasa ta juyo a hankali tana kallonsa, ya kamo hannayenta biyu xae yi magana ta fada kirjinsa ta fashe da kuka a hankali, ya rungumota ya lumshe ido murya can kasa yace "am srry Aneesah, nt my fault, mum ce tayi reportn dina gun Abbansu Najeeb, yhu knw.... Kin dae gane abinda nke nufi, kuma yana kano, so i had 2 go n meet him in there, nd bae bari na bar kano ba tun lkcin sae daxu, sauka ta knn Abuja ko gida bn je ba sae gidan Najeeb." gyada masa kai kawae take yi tana hawaye, ya dago kanta yace "bana son ganin hawayenki Aneesah," bata ce komai ba ya goge hawayen fuskarta yana murmushi yace "mu shiga ciki," ta shiga gaba yana biye da ita a baya suka shiga gidan, ya shiga daki suka gaisa da Ammi suka jima yana mata hira, Aneesah na gefen Amminta tana kallonsa shima duk hankalinsa na kanta, daga karshe dae tuwon nn tare suka ci da yayanta, sae lkcn ta ga ashe tana jin yunwar. suna xaune tsakar gidan su biyu kadae, ya tambayeta ya exams tace ranar thursday xasu kare, yace "waw nn da 3 dayz knn," ta gyada masa kai tana murmushi, yace "to Allah yasa kinyi a sa'a kanwata," ta ce "Ameen yayana," pretty fa? Yace "kar ki damu watarana xamu xo tare," nan ya dinga bata lbri masu ddi tana gefensa tana 'yar dariya kmr ba Aneesar daxu ba, duk da shi kansa daurewa kawae yake baya son ta gane damuwar da yake ciki, suka dinga hira har kusan karfe goma, duk ta manta da wani bakin ciki da Abdul ya cusa mata daxu, kmr kar ya Haydar ya tafi ta rakasa har motarsa ya ciro tsarabar da yyi mata ta karba da kyar, tayi masa gdya a kunyace ta shiga gida. Ana gobe xasu kare exam tana tsakar gida a xaune wajajen karfe 9 da rabi bayan ta raka Haiydar, tana duba geography note dinta don shine lst paper din da xa suyi gobe alhamis, ammi kuwa na daki kwance, Abdul ya shigo gidan da cigarette dinsa a hannu yana xuka, gabanta yyi mugun faduwa amma ta dake ta ki dago kanta tana ta karatun ta. [9:30PM, 12/21/2016] Khaleesat: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 36.... Haydar ya kasa ce ma mahaifiyar tasa komai don takaici, sae kallonta da yake kawae, abun ma sae ya kusan basa dariya, ya juya ya sake maida kallonsa ga zeenah dake xaune a falon ta sa wasu shegen kayan bacci sae jujjuya masa ido take, kawae ya girgixa kai bai ce komai ba ya juya xae haura sama, Hajiyar ta dakatar da shi da mamaki, "ina xaka ina maka magana baka ban amsa ba, kai fa dan rainin hankali ne Aliyu," ya juya yana dubanta cikin fushi yace "to me kike son nace, ni dae baxa ki xaba min matar da xan aura ba tunda ni ba yaro bane, taje can da degree dinta ta auri manyan mutanen dake nemanta, ni ko da auren nake so kiyi min ma wllh wnn tafi karfina, bare ni ban aikeki ki nema min mata ba , ni fa mum kar ku takura min a gidan nn, ynxu ma ni ba xama na dawo yi ba, kayana xan dauka," yana kai wa nn ya juya ya haye sama pretty ta bi sa a baya, Hajiya ta mike tana salati kmr xata yi kuka tace "ni kam Allah ya hadani da bala'e'en yaro, ya dubi tsabagen ido na ya dinga gaya min magana, to ka xo ka fita gidan nn yau na gani, ni dama nasan bbu abinda surutan Alhaji usman xae yi a kanka, da dae ya biyo ka har nn, nai masa bayani yana kallona ina kallonsa ya gane irin tashin hankalin da nake ciki, ohh ni kam na banu" sumy ta tabe baki tace "wllh mum ki sa masa ido da kyau, ni dae ina suspectn kila ma wajen shegiyar 'yar aikin nn yake xuwa don fa akwae ranar da na gansa hanyar suleja ko ina xa sa oho, ni kuma na raka kawata zee wajen wani saurayinta da yace muje can mu same sa," Hajiya tace "ke ban san mugun fata, wace 'yar aikin, yar aikin da yace min ya ajiye a titi yace ta wuce gida kar ta sake dawowa, ko ba gaban ki ya fada hkn ba," meenah ta fashe da dariya tace "Allah yasa" Hajiya ta juya tana kallon zeenah da ta gama rudewa ganin Aliyu, ba karamin kwarjini yyi mata ba ita kam, ae ita irin wa innan take so, nn da nn taji wani mugun sonsa na mata yawo a xuciya, ta kasa daina kallon stairs din, shknn ita kam ta sami mijin aure, Hajiya ta katse mata tunaninta ta hanyar cewa "ki kwantar da hankalinki zeenah, hka Aliyu yake, amma nasan yana ganinki sae da ya rude nunawa ne kawae baxe yi ba," zeenah ta kirkiro murmushi tace "ba komai Hajiya," sumy da meenah suka kauda kai suna mata dariyar wayyo yarinya. Aliyu ya sauko rike da jakar kayansa ba tare da ya kallesu ba xae bar falon, Hajiya ta shige gabansa tana huci "kana da hankali kuwa Aliyu, ni kke mayar wa ba komai ba ko," sae ta fashe da kuka ta koma gefe tana cewa "dama hka rayuwar take, kaje Aliyu, ni nasan da mahaifinku na da rae duk hkn baxae faru dani ba," ya tsaya kallonta can ya dan yi tsaki ya juya ya koma sama, yana hayewa sama tayi murmushi ta dawo ta xauna tace "idan ba hka nayi masa ba baxae koma ba," ta ciro wayarta ta kira Alhaji usman tayi masa bayanin komai, tana kashewa ko minti biyar ba ayi ba ya kira Haydar din, ranar kasa bacci haydar yyi tunanin Aneesah kawae yake, ga shi har lkcn bae taba furta mata kalmar so ba, ya kasa yin hkn, yana tuna zeenar da Alhaji usman yace masa lallai lallai ita ce matarsa sae yaji ransa yyi mugun baci, to shi macece da xa ayi ma auren dole, yyi tsaki yace nasan maganinku. Washegari alhamis Aneesah ta kare waec dinta, suna tsaye da kawayenta bakin makarantar suna ta murnar gama waec, ita ko hankalinta yyi nisa duk a hargitse xuciyarta yake, wae yau xata wuce gombe to yayanta fa, ita baxata iya rabuwa da shi ba, mota ce tayi park dae dae bakin makarantar matan da ma mutanen dake wajen gaba daya suka maida hankalinsu ga motar har Aneesah, aka sauke glass din motar ana kallonsu, salima tace "waww wnn wajen wa ya xo," Aneesah dae ta tsura masa ido tana kallo, fateema tace "kai maxaje na inda suke, ku dubesa fa, ae Allah ya bani saurayi hka an banu," hka duk suka dinga fadin albarkacin bakinsu, ita dae Aneesah tsit ake jinta, shi ko ita yake ta kallo, suka ce ke Aneesah ke yake kallo f,a ko gurin ki ya xo ko dae yayanki ne, dama gashi kuna kama, lips dinku iri daya, hancinku iri daya, bakin ki iri daya, Aneesah ta dan yi dariya ta karasa kusa da motar tana kallonsa, mates din nata suka bi ta da kallon mamaki, ya hade rae yace "bayan kin gama walakantani gaban kawayenki kinyi kamr baki san ni ba," ta marairaice masa tace "aa nifa banyi kmr ban san ka ba yayana," yyi murmushi yace "to ya angama exams lfya," ta gyada masa kai tana masa wani shegen kallo, yace "hmm wnn kallo hka," ta kauda kai tana dariya, tace "bari ka gaisa da frnds dina," tana fadin hka ta gayyatosu suka karaso bakin motar, yace masu "hi" suka gaishesa gaba dayansu, ya amsa yana murmushi yace masu "hw 're yhu ol," "fyn thank u, nd yhu," suka mayar masa, ya gyada kai yace "same" nn ya tambayesu ya suka gama jarabawa duk suka ce lfya lau snn yace "nyc 2 meet yhu oll 4 d first tym," "nyc 2 meet yhu 2," suka mayar masa suna 'yar dariya, nn Aneesah tayi masu sallama ta shiga motar suna binta da kallo snn yyi reverse suka bar anguwar. Like · Report [9:30PM, 12/21/2016] Khaleesat: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 37...... Dai-dai wani shoppin Mall Haiydar yyi parkin motarsa Aneesah ta juya tana kallonsa tace "yayana xan fa yi tafiya yau, naga kuma ba gida mu ka taho ba," ya kashe mota yana kallonta yace "ina xaki," ta dan marairaice masa tace "gombe xan tafi," ya tsaya kallonta da mamaki yace "wae me xaki je yi gombe Aneesah," ta tsura masa ido ko kiftawa bata yi, ya kamo hannunta yace "talk 2 me Aneesah," ta kauda kanta a raunane tace "Ammi ce tace tunda yau xan gama exams na wuce can kawae,"ya lumshe ido yace "sbda me Aneesah," nn da nn hawaye ya taru idonta a hankali tayi masa bayanin abinda ke faruwa da irin maganganun da Abdul ke gaya mata na cewa ta kusa xama matarsa, Haiydar yyi murmushi yana kallon mutanen dake ta shige da fice cikin mall din, can ya juya yana kallon Aneesar da ta tsura masa ido yace "wae a wani anguwar ma baffan naku yake," Aneesah tayi shiru kmr baxa ta ce komai ba can dae ta gaya masa sunan Anguwar, yace "to Address fa," tace "me xaka yi da address yayana," ya daga kafada yana kallon cikin idonta yace "just wants 2 knw," xata yi magana wayarsa yyi ring ya daga yace "srry bbyna gani nn xuwa," Aneesah ta xuba masa ido tana kallo, ya hura mata idon yace "mu je kanwata," ta dan hade rae tace "ni don Allah ka barni na wuce gida yayana, ammi xatai ta jirana," yace "i knw kanwata ynxun nn xamu fito ae, kin dae ga ina ne nn," da kyar ya lallabata ta fito daga motar fuskarta a daure snn suka shiga ciki yyi mata siyayya sosae ita dae binsa kawae take bata ce komae ba, daga bayansu taji muryar pretty, gaba daya suka juya suna kallonta ta karaso tana tura trolleyn kayan da ta siya a hankali Haiydar yace "sae ynxu kika gama," tayi murmushi tana kallon Aneesah tace "ya exams mumy," Aneesah tayi murmushi tace "Alhmdllh, ya gida," pretty tace "lfya lau, ya su Ammi" Aneesah ta kalli Haydar tayi murmushi ta ce tana nn lfya, Haydar ya hada kudin gaba daya ya biya da na prettyn don ita ma ta gama siyayyanta snn suka fita ixuwa mota... Tare suka yi gidansu Aneesah da pretty, ta shiga ta gaida Ammi da yayanta, ita dae Aneesah bin ta kawae take da kallo, tana son yarinyar ssai, Ammi ta xuba masu abinci suka ci tare da ita, haydar kuwa yace ya koshi, sun jima suna hira daga bisanni yyi ma Ammi sallama yace xasu koma gida, Aneesah ta rakosu har bakin mota, ya fito mata da kayan shoppin din da yyi mata yana kallonta yace "no more gombe kina ji na," ita dae murmushi kawae tayi ta kauda kanta a xuciyarta tana cewa gombe kam dole naje sa, pretty ta shiga mota tana daga ma Aneesar hannu, haydar yace "yauwa baki bani Address din da na tambayeki ba Aneesah," tace "wae me xaka yi da Address din yayana," ya harareta yace "ina son nasan ko nasan anguwan ne," da kyar ta gaya masa Address din baffan nata, yyi mata sallama suka bar anguwar, ita kuma ta koma cikin gidan a sanyaye. Haydar yyi parkin dae dae kofar gidan Baffa yana kare ma gidan da anguwar kallo, sanye yake da suit baki har lkcn, ya kalli agogan hannunsa karfe biyar na yamma, ya karasa bakin gate din ya danna bell maigadi ya leko yana tambayar waye, a nutse Haiydar yace "nn ne gidan Alhaji shehu?" mai gadin yace "eh nn ne, akwae matsala ne, don baxa ka samu ganinsa ba ynxu bae jima da shigowa ba" Haydar yace "No ni wajen Abdul naxo ae yana ciki?" mai gadin yace "ko minti goma ba ayi da fitarsa ba sae dai in jiransa xaka yi a ciki," Haydar yace "eh ba matsala xan iya jiransa," mai gadin ya bude masa gate ya shiga gidan yana kare ma ko ina kallo yana murmushi har ya isa kofar shiga falon, ya tsaya ya danna bell, 'yar aiki ta taho da sauri ta bude kofar, yace "Alhaji shehu na ciki ko?" tace "eh amma hutawa yake yi," yace "kije kice masa ana nemansa urgently, a dan tsorace tace "A'a ni ba a bani ixinin hawa sama ba sae dae na kira maka kande, yace "to me kike jira," da sauri ta juya sae ga ta da kande, ya gaya ma kande abinda ya fada mata, ita ma a tsorace tace "aa ni iya ka ta kofar dakin Hajiya," cikin tsawa yace "eh kije kice da Hajiyar ana neman mijinta," ta dan koma baya tace "gskya baxan kuma hawa sama ba sae gobe don na gama duk ayyukana na yau," xae yi magana sae ga hajiya ta sauko, tana kallon yan aikin tace "me ya faru, wnn daga ina," kande ta durkusa da sauri tace "A'a ranki shi dde wnn bawan Allahn ne ke neman Alhaji wae," ta karaso cikin falon tace "akwae damuwa ne yaro?" Haydar yyi murmushi mai sauti yace "gun Alhaji shehu na xo," tace "in ji lfya" ya daga kafada yace "lfya lau, kan wani business ne," tayi murmushi tace "Ayyo xauna mana, bari na kirasa yana ciki," [9:30PM, 12/21/2016] Khaleesat: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 38...... Haiydar yyi murmushi ganin bata gane sa ba bayan ta bar falon xuwa kiran maigidan nata, bayan kmr minti biyar baffa ya sauko cikin bakar jallabiya, har lkcn Haiydar na tsaye a falon, ya karaso falon yana kallon Haiydar daga sama xuwa kasa yace "hw may i help yhu gentleman?" Haiydar ya gyara tsayuwa yana kallonsa da kyau yace "srry fa, hope am speakin 2 Alhaji Shehu," Baffa ya basa hannu yace "ehh ni ne, have a sit mana," Haiydar ya girgixa masa kai ya juya masa baya yace "ba xama ya kawo ni ba Alhaji Shehu, am barrister Aliyu muhammad," yana fadin hka ya juyo yana fuskantar baffan da dan fara'ar dake shimfide a fuskarsa ya bace da gudu, fuskarsa a daure yace "ehem hw may i help yhu? kana da matsala da ni ne?" Haydar ya girgixa kai a nutse yace "ko daya, i came on behalf of the late Alhaji mukhtar's family," baffa ya yo waje da tulelen idonsa a fusace yace "Alhaji mukhtar meye hadinka da mukhtar, da'alla malam fice min a gida, wnn ae xancen bnxa ne wae on behalf of Alhaji mukhtar, kasan alaka ta da mukhtar xaka xo kana gya min magana malam," Haiydar yyi murmushi mai sauti ya fito da takardar aljihunsa ya jefa ma baffan yace "gidaje biyar, motoci hudu, filaye hudu, 2 companies ba a maganar kudin da ya bari a acctn ma tukun, duk ka tattaro ka damka ma iyalansa nn da sati daya, if nt i will sue yhu, bnxa kawae jahili mara tunani masu cin haram" yana gama fadin hka ya juya yyi kofar fita, baffa ya bude baki yana kallonsa, dae dae bakin kofa Haydar ya juyo yana kallonsa yace "just a week," snn ya fice daga falon, baffa ya girgixa kai cikin tashin hankali ya shiga kwada ma matarsa kira, ta sauko da sauri tana tambayar lfya, me ya faru Alhaji, cikin in ina yace "wnn waye kika turo ni wajensa, kina da hankali kuwa, ni ni ya gaggaya wa magana hka ya fita, ta ina ya shigo gidan nn, yasan ko ni wanene ma kuwa" Hajia zuwaira ta rude tace "wllh ca nake business partner dinka ne Alhaji, mai yace maka?" baffa ya dinga kai komo a falon yana salati, "lallai sae nayi maganin tsinannun mutanen nn, nn ba da dde wa ba, ni xa su toxarta??" duk yanda Hajiya zuwaira ta so jin me bakon ya gaya ma mijin nata hkn bae yiwu ba don duk ya fita hayyacinsa, kira wnn a waya, kira wancan a waya, duk lauyoyinsa biyu sae da ya kirasu, daga karshe ya kira wani abokinsa Dpo, ita dae Hajiya duk inda yyi binsa take kawae a baya, gashi ya ki sauraranta, suna nan a wann hali Abdul ya shigo gidan a fusace, yana kiran abbansa, dad, dad, baffa ya juyo da jajayen idonsa yana kallonsa ba tare da ya amsa ba, "kana sane dae gobe ne daurin aurena da yarinyar nn ko?" Baffa yace "nonsense kasan tashin hankalin da nake ciki ynxu kuwa xaka min maganar auren wa inda suka sa ni cikin tashin hnkalin," cikin tsawa Abdul yace "ina ruwana da tashin hankalinka dad, ni kasan irin tashin hankalin da nake ciki, shit! dad wllh komai xae iya faruwa idan yarinyar nn bata xama matata gobe ba, idan ma kai baxa ka daura min auren ba sae na biya wani ya daura mana, wnn ae walakanci ne kke min dad" baffa ya xauna kan kujera ya dafe kansa yana girgixa kafa, Hajiya Zuwaira dae an sa ta a duhu ta rasa gane abinda ke faruwa, a nutse baffa ya shiga yi ma Abdul bayanin abinda Haydar ya xo yyi masa, Abdul yace "shit shine dad saurayin Aneesar ne, shine wanda nake gaya maka shekaranjiya, shine yyi min tijara daxu" Hajiya ta saki salati tana gwale ido tace "ban gane sa ba wllh Alhaji, ba ranar da naje gidan ba nima nace mka na ga wani a xaune a dakinsu, au shine ya xo yau, tab" abdul yyi tsaki yace "wnn duk ba matsalata bace dad, gobe nake son wnn mara kunyar yarinyar ta xama mata ta don na gwada mata hankali, period," yana kai wa nn ya haye sama yana huci. Baffa ya dafe kai yace "innalillahi wa inna ilai hi raji'un," Hajiya ta xube kan kujera tana kuka, baffa ya mike ya bar falon da sauri yana cewa "nasan abin da xanyi," Hajiya ta bisa da sauri ita ma. [9:30PM, 12/21/2016] Khaleesat: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 39..... Dai-dai bakin kofa Hajiya Zuwaira ta hadu da mai gidan nata yana kkrin fitowa daga dakinsa rike da makullin motarsa, da mamaki tana kallonsa tace "A'ah ina xuwa kuma Alhaji...." yyi saurin katseta ta hanyar daura yatsansa a baki yace "shhiii" alamar tayi shiru ta ja gefe ya fito daga dakin kmr mara gskya yana kallon kofar dakin Abdul, ya dan yi gyaran murya yace "guy kayi bacci ne!" duk da idon Abdul biyu bae tanka masa ba, baffa ya karasa har bakin kofar dakin ya tura kofar yana kallon cikin dakin, ya ga Abdul din xaune yana xugar taba, ga wine mai sanyi a gabansa, baffa yyi murmushi yace "ashe dae baka yi bacci ba, wae da fa fita xa muyi guy!" Abdul ya juyo da jajayen idonsa yana kallon uban nasa a walakance yace "mu fita muje ina?" baffa yace " No Alhaji kasim ne ya kira ni gidansa ba lafiya shine xan je ynxu," Abdul yyi tsaki yace "shine xan bi ka" baffa yyi murmushi mai sauti yace "mai da wukar Angon gobe, bari naje ynxun nn xan dawo muyi maganar yanda shirye shiryen bikin xae kasance gobe," Abdul yace "A'a ana daura auren a bani matata na tafi da ita kawae bbu wani bikin da xa ayi," " baffa yace "an gama guy, bari naje na dawo" snn yyi masa sallama ya fice Hajiya Zuwaira da hankalinta ya gama tashi jin mijin nata na xancen auren dan ta da Aneesah gobe, ta dinga binsa a baya har suka sauka kasa snn ta fashe da kuka ynxu Alhaji da gske aura masa shegiyar yarinyar nn xaka yi, yyi mata wani mugun kallo yace "da yake na ce maki mahaukaciya ce ta haifeni ba, ni shehu na hada zuri'a da tsinannun mutanen nan baki san ni bane Zuwaira, look ba lallai bne na dawo yau har sae na idda abinda na fita yi, kiyi min addu'a kawae kuma bana son Abdul ya gane ban kwana gida ba, be vry watchful," yana kai wa nn ya fice yana kiran driver a waya, ta bi shi da Allah ya kiyaye xuciyarta ya dan yi sanyi sanin mijin nata shaidanin gske ne. Kofar gidansu Aneesah drivern baffa yyi parkin dinsa, ya fito yana kallon agogo karfe goma da rabi na dare, yace ma drivern gashi nn fitowa ynxun nn snn ya shige gidan. Like · 9 · Report · 26 minutes ago [9:30PM, 12/21/2016] Khaleesat: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 41..... A tsorace Aneesah ta farka ta dalilin buga kujeran bayan motar da Driver ya dinga yi da nufin tada ta, ta fara waige waigen cikin motar xuciyarta na bugawa, xata tambaye Drivern ina ne nn suka kawota, baffa ya xagayo bayan motar a fusace yana cewa "kin fitowa tayi don ubanta," da sauri ta fito daga motar gabanta na faduwa daga ita sae dankwali tana kare ma inda suke kallo, ko ina tsit sae ciyawa dake ta bow down wa iskan dake ta kada su, ga uban duhu, crow din cock da ta dinga ji ne yasa ta gane Asuba tayi, cikin tasin hankali ta shiga tambayar kanta ina ne nn kuma baffa ya kawo ta, tsawarsa ta tsinta a tsakiyar kanta yana cewa "duk inda na bi ki bi, idan ba hka ba xan wurga ki cikin dajin can na bae ma macixae sadakar ki, kae kuma saleh ka jirani daga nn, ba jima wa xanyi ba," yana fadin hka ya bi ta dan wani hanya duk ciyawa, Aneesah ta bi sa a baya tana hawaye, da taimakn hasken wayar sa suka dinga ratsa grasses din wajajen ga hanyar duk cabi da ruwa, har suka bullo wata hanyar daban da karamar abun hawa xata iya bi, tafiya yake kmr xae tashi sama yana yi yana waiga bayansa ya tabbatar tana biye dashi, ita ko binsa kawae take tana hawayen tsoro, sun kusa minti talatin suna tafiya har daga karshe taga sun shigo wani dan karamin gari, abinda Aneesah ta fara cin karo da shine bukkokin mutane, abun yyi mugun daure mata kai ko ba a fada mata ba tasan kauye ne nn, hka Aneesah ta dinga binsa a baya har daga karshe taga sunyi fullstop a dai-dai wani katon bishiya duk bawon rake a watse a kar kashinta, ya juya fuskarsa daure yana kallonta yace "ki jira ni a nn," kai ta gyada masa taga yyi wata 'yar hanya, ta fashe da kuka abun tausayi, to ita ynxu ya xata yi ita ba wae tasan guri bane bare ta gudu ga ko ina duhu, ta fara waige waige tana nema ma kanta solution kafin baffan ya dawo sae ko gashi da wani mutum sun dawo gabanta yyi mugun faduwa har suka karaso, mutumin yace "to ku shigo daga ciki mana Alhaji, ashe xaka tuna dani Alhaji gaskiya naji ddi sosae," baffa ya kalli Aneesar yace "maxa ki biyo mu a baya," hka ta dinga binsu a baya har suka shigo wani dan gida da bukka guda uku, cikin tsawa baffa yace ta tsaya daga bakin kofa snn suka karasa cikin gidan da tsohon mutumin, baffa yace "ina mai dakin naka mati," mutumin da xa su xo sa'anni da baffa yace "bari na tado ta Alhaji tana ciki ai," da sauri ya shiga sae gashi sun fito tare tana mitsika ido tace "wanga ai walakanci ne malam, me ya faru xaka tado ni cikin sanyin nn," yana wage baki yace "ke shatu Alhaji shehu ne a kauyan namu yau," ta bude ido da sauri tana kallon baffa tace "lah Alhajin Allah ashe baka manta mu ba, sae ta fashe da dariya tana cewa ikon Allah, sannu da xuwa Alhaji amma da asuban nn me ke tafe da kai hka," baffa dake dan murmushi yana sosa keya yace "A'a wnn yarinyar na kawo ku taimaka min ku riketa amma ba amana ba, don 'yar iskar kanta ce, karuwanci take a birni wllh, mun rasa yanda xamuyi da ita 'yar wata abokina na kut da kut ne, ga ta nn nasan shatu ke ce maganinta, idan Allah yasa ta samu mijin da xae jajuban ma kansa wahala ku aurar da ita kawae ko sadaka ce, nasan baxa ta taba gane hanyar fita daga kauyen nn ba bare ta gane hanyar komawa gida, kar ku sake tayi kawaye ni dae ynxu tamkar na kawo maku baiwa ne, dan tallan nn da aikace aikace duk ta iya xata maku, kuma nn ba da ddewa ba nke son ku bada sadakarta ga duk mai so," yana kai wa nn ya ciro duba daddaya har ashirin ya mika ma mati da ya xube har kasa yana gdya "an gama Alhaji in'sha Allahu duk yanda kace hka xa ayi," shatu tayi wani shegen dariya irin tasu ta 'yan kauye tace "ka xo inda xa a share maka kukan ka Alhajin Allah, ka manta mu su waye ne, ka kwantar da hankalinka kawae Alhaji kar ka samu damuwa," baffa yyi dariya sosae yace "ae na yarda daku, ni ynxu xan koma driver na can bakin hanya yana jirana don ma kar ta gane hanyar fita yasa ban bari muka shigo ciki da motar ba, na dinga ratsawa da ita ta daji, cikin ikon Allah kuwa muka iso nn," suka yi dariya suka rakasa har bakin kofa suna masa Allah ya kiyaye hade da gdya, har lkcn Aneesah na bakin kofar shigowa gidan tunda baffa bae ce ta shigo ba, tana ganin su ta ja gefe gabanta na faduwa, cikin tsawa shatu tace "kya tsaya kina rabe rabe bakin kofa kmr warce bata san duniya ba shegiya, da'alla shiga daga ciki ki tsaya," jikinta na bari ta shiga gidan tana kallon baffa, kar dae tafiya xae yi ya barta, nn suka yi ma baffa dake ta washe baki ganin har shatu ta fara aikinta sallama, yyi masu sallama cike da farin ciki ya bi hanyar da xae sada sa da bakin hanya xuciyarsa fari kal. Mati shaidanin mutum ne da yyi ma baffa aiki a birni da ddewa, aikinsa kuma baya wuce kashe wancan binne wancan kamo wancan, nemansa da ake ruwa a jalo a Abujan ne dalilin da yasa ya dawo kauye da xama da karuwar matarsa da 'ya yansu biyu zano da xulai. [9:30PM, 12/21/2016] Khaleesat: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 40..... Aneesah na kwance bayan ta ci kukanta ta koshi tana ta kallon Amminta dake ta faman har hada mata kayanta don gobe xata wuce gombe wae, ta kauda kanta a hankali wata xuciyar na ce mata tafiyarki gombe shine kadae kwanciyar hankalinki, da ta tuna abinda Abdul ya xo yyi masu daxu da maghrib sae ranta yyi mugun bacewa, ta tsani Abdul ta tsane sa, da ta auri Abdul gwara ta shiga duniya ita kam, sam bata dace da shi ba, to idan da gske ne kmr yanda ya fada masu gobe ne daurin aurenta dashi ya xata yi, ohh da shiknn karshen rayuwarta ta xo, ko da yake ae gobe da asuba xata bar garin Abuja idan Allah ya yrda, tayi assure din kanta, hakan ya kara sa taji hankalinta ya kwanta ta samu kwarin gwiwa, damuwar ta daya basu yi sallama da ya Haiydar ba, ynxu sae dae ya xo ya ga ba ta, hkn yasa taji hawaye ya silalo gefen idonta, ta mike xaune a hankali ta goge idonta, Ammi bata ko kalleta ba tana ta faman hada kaya abun ta, Aneesah xata yi magana knn suka ji an banko kofar xaure da karfi aka shigo gidan, duk suka tsaya kallon juna har baffa ya turo kofar dakin yana huci yace, "maryam, maryam ina tsinanniyar 'yar nn take, maxa maxa ta tattaro kayanta ta fito daga gidan nn kar na balla ta, don na gaji da abun kunyar da kuke janyo mana a gari ko kuma nace kuke janyo min tunda shi ibrahim ba a nn yake ba, maxa ta fito da jakar kayanta bata sake xama a gidan nn," cikin tsawa yake maganr yana nuna Aneesah da ke xaune dakin tana kallonsa da mamaki, Ammi tace "kmr ya abin kunya baffa, wani abun tayi ko kuma....." ya daka mata wani mugun tsawa yace "ki rufe min baki bnxa dake kawae, nace fateema ta tattaro kayanta ta fito daga gidan nn ynxun nn ina tsaye idan ba hka ba wllh wllh xa ku sha mamaki na ynxun nn, matsiyatan bnxa kawae" kuka Aneesah ta fashe da tace "wllh bbu inda xan je daga nn Ammi," ya shigo dakin a fusace har yana neman faduwa ya gaura mata mari mai lafiya, "don ubanki tashi, tashi, nace ki tashi," ya fixgota da karfi, ta fixge hannunta tana kuka tace "wllh bbu inda xani ka kyaleni," ya fita a fusace sae ga shi ya dawo da icce, Ammi dake xaune ta kasa cewa komai sae hawayen da take yi ba kakkauta wa ta mike da sauri ta shiga tsakaninsu, "kar ka dukan min 'ya baffa, ina xaka kai ta da daren nn da xata hada kayanta?" yana huci ya nuna ammi da dan yatsa yace "ke,,, ke maryam ki fita idona kar na watsa maki mari munafuka kawae makira, maxa ta fito da kayanta yau kafata kafarta wllh wllh," Hka baffa ya dinga masu tijara daren ranar yana neman dukan Aneesar da bakinta ya ki mutuwa, Ammi tana kuka tace ta bi shi amma Aneesah tace bbu inda xata ita kam, da kyar Ammi ta lallabata ta hada ta da kayanta da take hadawa tace ta bishi, kuka Aneesah take kmr ranta xae fita hka baffa ya ja ta, yana rike da jakan kayan nata dayan hannunsa, ya wurga ta cikin mota da jakar tata, yace driver ya kula da ita kar ta fita snn ya koma cikin gidan yana huci, ya ciro dubu biyu ya jefa ma Ammi yace "ke ma maxa maxa gobe ki kama hanyar gombe da asuba don baxan tsaya da ku a garin nn ba ana nuna ni da dan yatsa, maxa ki tattara komatsan ki kiyi kauyenku kar naxo na tarar dake nn gobe," yana kai wa nn ya fice daga gidan ya shiga mota, driver na ta kokuwa da Aneesah dake neman ficewa daga motar ta karfin tsiya, baffa ya koma da sauri ya dauko iccen daxu ya dawo motar, Aneesah na ganin iccen ta fasa ihu "don Allah baffa kayi hkuri wllh na tsaya, wllh nayi shiru, ya kwale mata a ka yace "don ubanki da ke kabari ma kiyi mana," tsit tayi tana ajiyar xuciya a motar, ya shiga gaban mota driver ya ja suka bar anguwar suna hawa titi yace da driver ya shiga gidan mai xa su cika tanki, hka ko drivern yyi aka cika tankin motar snn baffa ya biya suka hau titi kuma, a ladabe drivern yace "to ina muka dosa mai gida," baffa yace "samu waje kayi parkin ka bani motar kawae baxa ka yi irin tukun da nake so ba, driver yyi parkin motar baffa ya dawo driver tsit shi kuma ya koma daya bangaren, snn baffa ya ja motar ya dinga sharara gudu kmr xasu ta shi sama, Aneesah kam duk ta tsorata kuka kawae take tana kiran Allah a xuciyarta, tun tana gane hanye har ta daina, taga sun soma fita daga Abuja, ta fara ganin daji da duhu, baffa ko tuki kawae yake kme xae tashi sama da motar, har baccin tashin hankali ya dauke Aneesh. [9:30PM, 12/21/2016] Khaleesat: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 44.... Duk yanda Hajiya ta so ganin Dpo hkn bae yiwu ba don 'yan sandan ca suka yi baxa ta sami ganinsa ba, tace to tana son magana da dan nata, nn ma suka ce sae dae ta dawo xuwa anjima, nn da nn tashin hankalin dake fuskarta ya bace ranta yyi mugun baci, amma bata ce masu komai ba, ta tsura ma hotan Aneesah dake hannunta ido tana huci, ynxu duk hankalinta na ga son sanin 'yar gidan uban wacece Aneesah, meye hadinta da Aliyunta har xa a daure mata son a kanta, tayi murmushin mugunta tace "muddin na tabbatr ke wacece kwananki ya kare yarinya" ta fice daga station din kmr xata tashi sama a xuciyarta tace ynxu gun su barau da lado xa ni, Allah ya kai mu anjiman, amma yarinya kin jawo ma kanki don sae na sa an kashe min ke an kashe banxa snn duk wani naki ma sae ya bakunci lahira, kai har matar da ta kawo min ke ma sae na sa an nemo min ita yau, "wato Ammi," duk sae na ga bayanku ni Fateema,. A bangaren Ammi kuwa baffa bae sauka gidansa ba yana isa Abuja wajajen karfe shidda gidansu Aneesahn yyi dama, Ammi na xaune kan darduma ya shigo gidan, ya tura mata kofa yana cewa "au baki ma fara shirin tafiyar ba knn matar nn, to maxa ki tashi gani nn ina jiranki, ni da kai na xan kai ki tasha don na tabbatr gombe kika yi ba wani gun ba," ta dago tana kallonsa tace "ina ka kai min 'ya ta baffa?" yace "eh tana gidana kuma can xa ta ci gaba da xama har lkcn da na sa ma mata miji dai-dai ita na aura mata, don baxa ki ci gaba da rike min 'yar kanina ba ana cewa 'yar macece, bbu abinda Aneesah xata rasa a gidana har makaranta ma xuwa xatayi, amma tace xata kawo min rainin hankali ni da matata sae na ci ubanta al-qur'an" Ammi tace "to ni baxan je gombe ba ka bar ni kawae nayi xama na a nn," nn da nn ya hade rai yace "kinga fa kar ki bata min lkci, ina da gurin xuwa, ki tashi ki dauka jakarki na kai ki tasha kije kauyenku nace," Ammi tace "kaje kawae ae ba tashin duniya bne abun xuwa anjima xan shirya na tafi," cikin tsawa baffa yace "to baki isa ba wllh wllh, ynxun nn kafata kafarki xan kai ki tasha." Aneesah ce durkushe tana tankade garin masarar da Shatu ta hada ta da, duk ta galabaita da aiki, garin kamr na wasan yara don kana kallon datti da duwatsu su ma suna kallonka, abun ma mamaki ya ba ta, ynxu wnn mutum ne xae ci ko kuwa, tanakade garin take amma hankalinta duk yyi gida gun Amminta ba a ma maganan ya Haydar, ko ya xata ji ba ta, tunanin hkn yasa kwalla ya cika idonta amma tayi saurin gogewa don shatu na tsakar gidan a xaune tana fama da wasu bakaken rake, Aneesah ta dan saci kallonta ta dauke kai da sauri ita kam tsoro matar take bata, ga wani shegen kayan dake jikinta sae ka rantse kace yyi shekara, mutum sae kace monster, Xulai 'yar ta ta fari ce ta shigo gidan da kawayenta hudu, duk suka yo kan Aneesah da sauri suka tsaya xulai tace "kun ganta," Aneesah ta ki dago kanta, ita kam ta banu tun safe ake xuwa ganinta, tun da 'ya yan shatu suka daura idonsu a kanta da safe suka dinga jajibo kawayensu wae su xo su ga balarabiya, wnnan set din na fita wasu xa su shigo, daya daga kawayen mai suna jummalo tace "kai kai kai, xulai ina kuka samo ta, kice ta dan daga kanta mu ganta da kyau don Allah, shatu ce tace "kai wnn ai jaraba ce sai kun shafa mata daudan jikinku ne, ku dan koma daga baya mana wnn masifa har ina, aiko da sauri duk suka koma baya, shatu na ci gaba da shan rakenta tace "ni nn gaba ma duk wanda xae shigo ganinta sae ya ajiye naira biyar," Aneesah dae bata dago ba tana ta aikin gabanta, ganin sun ki tafiya ne yasa shatu tace "ke lu'u lu'u tashi ki shiga ciki," wani sabon sunan da ta tsiri kiranta da knn tunda wani mai shayi ya aiko mata da shayi da biredi da kwai ganin Aneesah daxu, Aneesah ta juya tana kallonta tace "ni," shatu tace "eh," ta mike a hankali ta shiga bukkar su xulan, suna fita ynxu xata kwada mata kira tace "shegiya fito," Aneesah ta xauna a bakin bukkar tayi jigum ta lura shatu so take suyi kudi da ita don hatta kawayenta sae da ta basu lbrinta, tun bayan da ta dawo daga rafi, wani mutum ya biyo ta ya shigo har cikin gidan yake tambayar shatu wacece wnn kuma, da shatu ta tashi sae ta tsula masa shegen karya wae 'yar aminiyarta ce dake birni ta dawo wajenta da xama, naira dari mutumin ya hada shatu da kafin ya fita daga gidan yana washe bakinsa da rubabbun hakori suka kewaye yace to sae na xo da daddare. Shatu na ganin hka tace "ke ya sunanki," Aneesah ta kauda kai cike da takaici tace "Aneesah," shatu ta tabe baki tace "oho dae, anjima da yamma ke xaki je min talla dandali, maxa ki shirya kici kwalliya irin taku ta karuwae, su xulai su raka ki," Aneesah bata ce komai ba sae kallonta da take yi abun tausayi, shatu tace "ga dumamen tuwon da xan ci can ki dauka kici, ni na nemi wani abin na ci," Aneesah ta je ajiye ruwan hannunta a sanyaye, tana karema kaxantattcen gidan kallo, dama shi malam tun asuba bata sake ganin sa ba. Shatu ce ta kwada mata kira tana cikin tunaninta, ta fito da sauri ta tarar duk kawayen xulai sun wuce. [9:30PM, 12/21/2016] Khaleesat: neesah~ By Khaleesah Haiydar 43..... Daya daga cikinsu ya fito da I.D card daga aljihunsa ya nuna ma Haiydar yace "yhu re under Arrest," da mamaki Haiydar yace "4 wat reason?" suka ce idan muka je station ka ji, any more word wil b said against yhu in d court..... Yace "ok" snn ya mika makullin motarsa ya bi bayansu suka shiga tasu motar, wani daga cikinsu kuma ya taho da motar haiydar. Ba karamin abun mamaki da al-ajabi Haiydar ya tarar a station ba, wae ana tuhumarsa da sace yarinya daxu da safe, ya ma rasa ta cewa sae ido da ya xuba ma 'yan sandan, suka mika masa hoton Aneesah da kuma wani hoton shi da Aneesar ya tsura ma hotan ido da mamaki, cikin motarsa aka daukesu hoton, ya girgixa kai yace "ni ban san me xan ce maku ba, amma ni nayi maku kama da kidnapper," yana fadin hka ya ciro Identity c. Dinsa ya nuna masu, inspectorn dake gabansa ya karba yana kallon I.d din, snn ya tabe baki yace "to barrister meye hadinka da wnn yarinya, kuma ina xa ku a wnn hoton cikin motar gashi da alama ma cikin tashin hankali take a lkcn, tunda kuka take?" xae yi magana Abdul ya shigo station din a hargitse kmr mahaukaci, kan Haiydar ya yo ya cakumosa yace "wllh wllh ka fito da Aneesah idan ba hka ba sae na kashe ka," 'yan sandan suka rirrike Abdul din, cikin fushi inspector yake cewa "wnn kuma waye xae shigo mana kamar mahaukaci, halan bae san inda yake bne" da sauri wani sergeant ya sara masa yace "dan wajen honorable Shehu ne sir," inspector ya mike tsaye yace "ohh kar ka damu yallabai muna nn muna bincike ne ka kwantar da hankalinka, kaje gida xuwa anjima ka dawo," Abdul yyi ma Haiydar dake kallonsu da mamaki wani mugun kallo snn ya fice daga station din yana huci, duk yanda aka yi da Haiydar a kan cewa shi ya sace Aneesah sae dae ya girgixa masu kai yyi murmushi yace "bani ne na sace ta ba, ku dae yi bincike da kyau," hkn ya harxuka 'yan sandan chief inspector yace a wuce da shi cell kawae, suka karbe duk wayoyinsa da agogan hannunsa, yace "amma ku yi min alfarma daya na kira mum dita," wani sergeant yyi masa mugun kallo yace "an ki maka," Haiydar yyi masa wani mugun kallo yace "kasan ko ni wanene," inspector ya sa aka dauko wayar station din aka basa ya kira mum din tasa, ba karamin rudewa Hajiya tayi ba bayan Aliyu yace mata yana station snn ya bata address din, tace "Aliyu statiion kuma, me kke yi a station mai ya faru?" yace "ki kwantar da hankalinki mum, sae kin xo," yana kai wa nn suka amshe wayar snn suka wuce cell da shi. Baffa ne ya shigo station din yana xaxxare ido yace "ya fadi gaskiyan inda ya kai min 'ya ta?" wani sergeant yace "A'a bae fadi komai ba har ynxu, sae ma mahaukata da ya mayar da mu," cikin tsawa baffa yace "ina dpo yake, uban me xae hana ku lallasa shi, tsayawa ku kayi kallonsa kawae,?" wani sergeant ya taho da sauri yace "honourable sir, dpo yace ka shiga office dinsa," a fusace baffa yyi hanyar office din dpo yana cewa "ae wnn maganar bnxa ce, kunsan halin da muke ciki ne na rashin yarinyar nn, xaku dinga binsa cikin ruwan sanyi, shine fa karshen wanda yaje wajenta jiya mahaifiyarta ta ce min kafin tayi disappear, ba kuyi amfani da statement din da na baku bne" yana shiga office din dpo ya mike yana masa sannu da xuwa, baffa ya xauna yana kallonsa yace "kai ya aka yi ne sule, ca nake xan xo na tarar ana jibgar shege," dpo ya girgixa kai yace "ka ga har fa ynxu honourable bbu kwakkwaran abinda xa mu fake da a kan cewar shi ya dauke wnn yarinya, snn fa dat aside, babban barrister ne, to ta ina kke ga xamu fara ynxu," baffa yyi tsaki yace "ka ji ka sule sae kace ba tsohon dan duniya ba, kudina ne fa ke magana a nn, kuma ba ga hotuna nn na kawo ba ko wnn bai isa a fake da ba" sule yace "to shiknn, amma fa sae ka kara kudi honourable, da alamar ina ga xamu yi nasarar jefa sa prison idan mun shiga court, tunda ynxu kam bae da mafita ga hotunansu nn da yawa a tare, kawae dae a tabbatar har a gama shari'ar nn, yarinyar nn baxata bayyana ba," baffa yyi dariya yace "ka kwantar da hankalinka ni ina da yakinin baxata taba fitowa daga inda na kai ta ba sae dae in fito da ita aka yi, ae matata tayi maganin wnn, daxun nn ita ma ta dawo daga kauye taje aiki." dpo yyi dariya ssae yace "to sae naji alert honourable," baffa ma ya mike yana dariya yace "wnn ai ba matsala bace, ku dae kuyi aikinku da kyau," yana fita daga office din yyi hanyar cell din da Haiydar yake yana nuna sa da dan yatsa kmr xae yi kuka yace "mugu munafuki sae ka fito min da 'ya ta," Haiydar ya mike tsaye da sauri ya cakumosa ta karfen cell din ya makure masa wuya da karfi, baffa ya dinga tsala ihu da kyar 'yan sandan suka kwace sa, a tsorace baffa yace "kun ga ya kashe min 'ya nima yana neman kashe ni ko," ku tabbatar kun hukunta min shi wllh, baffa ya fice daga station din kmr munafuki. Yana fita Hajiya ta shigo a rikice tana cewa "ina dpo..." 'yan sandan suka ce baxa ta samu ganinsa ba, a rude ta bukaci sanin abinda dan nata yyi, tana jin hka kuwa ta xaro ido da mamaki tana kallon hoton Ane[truncated by WhatsApp] [9:30PM, 12/21/2016] Khaleesat: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 45..... Aneesah ta xuba ma farantin gyadan da shatu ta tura mata gaba wae ta dauka su wuce dandali ta sayar, a hankali tace "mama ki bari na fara sallah kinga maghrib ya kusa," shatu ta daka mata tsawa a fusace tace "baxa kiyi din ba, mu din ance maki kafirae ne, da'alla wuce kiyi kwalliya ki dau min faranti ki bace min, su xulai su raka ki dandalin," Aneesah ta mike hawaye cike idonta ta jawo jakar kayanta ta dan shafa powder, snn ta koma gaban farantin gyadar xata dauka, shatu tace meye hka kika yi, kwalliyar knn don uwarki, Aneesah ta girgixa kai tace "ni bn xo da kayan kwalliya ba," shatu ta mike da sauri ta jawo kwandon tarkacen kayan kwalliyan 'ya yanta ta tura ma Aneesah gaba, Aneesah ta tsura ma kwandon da bbu komai sae gantali ido, xano ta shigo dakin tace "meye hka shatu xaki bata kayan kwalliyan mu, wnn ae walakanci duk kin bi kin xama kmr wata sha sha kan wnn mayyar yarinyar" shatu tace "to tashi kawae ki dauki gyadar ga wani can cikin bokiti," Aneesah bata yi musu ba ta mike ta dauki hijab xata sa shatu ta hana ta a fusace, hkn yasa ta dauki farantin ta daura a ka snn ta dauki bokitin a hannunta, xulai ta shigo dakin daga bukkarsu kmr wata aljana fuskarta duk baki ta ko ina wae tayi kwalliyar xuwa dandali, shatu tace "yauwa xulai 'yar albarka maxa rakata lkci na wucewa, na tabbata yau gyadata baxa tayi kwante ba" Aneesah ta bi xulai suka fita daga gidan jikinta a sanyaye wae yau ita ce xa ta talla, xulai ta dinga sintiri da ita a kauyen, shiga wancan bukkar fita wancan bukkar duk sae da ta bibbi gidajen kawayenta kusan guda biyar suka fiffito su ma da shirin xuwa dandali, suna isa dandalin 'yan mata da samarin wajen suka mayar da kallonsu ga Aneesah, ita dae ta nemi gu ta xauna farantin gyadar ta a gabanta, bokitin kuma a gefenta, xulai ta dinga bin matan wajen tana cewa "ku xo su ga 'yar uwata da ta xo daga birni jiya," ai ko haka suka dinga tururuwa ba maxan ba ba matan ba suka yi ca kan Aneesah da ta rafka tagumi tana kallonsu, ita kam ta ga rayuwa, maxan wajen suka dinga siyan gyadar da basu yi niyyar siya ba, ita dae da ka mika mata kudi xata dauki gyada ta baka ba uhm ba uhm uhm, don duk yanda suka so tayi magana kinyi tayi, ita wani mugun haushi ma suke bata ga su duk gantalallu da kaxamen kayan jikinsu, xulai dae baki yaki rufuwa an kasa xaune an kasa tsaye, tsaf Aneesah ta sayar da gyadan ya rage bae fi kulli biyar ba, xuwa ynxu kam suna ta wasanninsu na dandali Aneesah na kallonsu mata nata tirkan rawa suna tsalle tsalle, ita abun ma mugun dariya ya bata, ji tayi ana cewa "ga ta nn," ta juyo da sauri tana kallon masu maganar, wasu rubabbun samari guda biyu ne, ta kauda kai da sauri tana girgixa kai cike da takaici, ta ji mutum ya xauna gefenta, ta dago da sauri tana kallonsa, yace "gyada xan siya," ta bude roban ta ciro daya ta mika masa, ya amshe ya bude ya fara ci, ganin bae mata maganan kudi bane yasa ta ci gaba da kallon masu wasa a dandalin, ya sake cewa ta karo ta dauko ta mika masa, hka ya dinga cewa ta karo har gyada ya kare, ita dae bata san yanda ake yake cinyewa da gudu gudu hka ba, a xuciyarta tace sae kace jaki, yana gama cinye na ledar hannunsa ya mike yana karkade wandonsa xae wuce, ta mike da sauri ta sha gabansa tace "malam baka bani kudi ba," ta ga ya fashe da dariya da ma samarin wajen gaba daya da 'yan mata wasu har da faduwa da shewa ta ringa kallonsu da mamaki baki bude, taga ya mika ma wani kato da taji mata na kira da garba mai machine hannu, wae duk kauyen bbu mai mashin irin tasa, garban ya cije lebe ya ciro dari biyu ya mika ma mutumin, tayi tsaki tace "malam magana nake baka bani kudin gyada ta ba ko tayi maka kama da ta sadaka ne," yyi dariya ssae ya karaso gabanta ya mika mata dari biyun yace "bani canji na 'yan mata, ta fixge kudin, ta kirgo canjinsa ta mika masa ta koma ta xauna," wae ashe kudi aka sa ma duk wanda ya sa ta tayi magana a dandalin, ganin gyadar ta ya kare ya sa tace ma xulai su wuce, xulai tace ina sae karfe sha daya, hkn yasa Aneesah ta kama hanyar gida ita daya ganin xata gane. [9:30PM, 12/21/2016] Khaleesat: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 46..... Tafe take da sauri tana dan waige waige a xuciyarta tana wonderin cewa to su wnn kauyen basu da wuta ne ko ko, don ko ina bakikirin sae dan hasken wata kuma tun da taxo ita kam bata ga alamar da wuta a kauyen ba, mutane biyu taga sun sha gabanta da sauri ta koma baya a tsorace tana kiran Allah a xuciyarta, muryar daya daga cikinsu taji yana cewa "garba garbebe ne ke son magana dake gashi can," ta juya tana kallon inda suke nuna mata, yana xaune ya hakikince kan machine din da yake ji da kamar ransa, ta cije lebe kmr ta gaura masu mari don haushi, taja dogon tsakin takaici tace "da'alla ku bani waje na wuce, a'a ba garbebe ba garu " taji daya ya daga murya yana cewa "garbebe ta fa ce baxa ta xo ba," taji katon muryarsa na cewa "ku dauko min ita" ta xaro ido tace "iyye wa xa ku dauka," murya su kaji daga bayanta yana cewa "kuje ku ce ma garbebe nace baxata xo ba," su ka juya gaba daya suna ganin mai maganar suka bar wajen suka yi gun garbeben, ta juya tana kallon mai maganar yace "ke mai gyada me yasa baki jira har a tashi daga dandalin ki biyo 'yan uwanki mata ba xa ki kama hanya ke daya," ta tabe baki tana kallonsa daga sama xuwa kasa tace "ae ban san hka ake yi ba," tana fadin hka ta ci gaba da tafiyarta, ya bi bayanta yana cewa "to muje na raka ki, sunana Mudatheer," ta juya da sauri tana kallonsa, yyi murmushi yana tauna abinda bata sani ba, tace "um yyi kyau," yana biye da ita yace "ke ya sunanki," tace "it's of no use," bae sake ce mata komai ba sae bin ta da yake tayi a baya har suka isa gida, ta juya tana kallonsa tace "ngd Mudatheer," yyi murmushin jin ddi da ya bayyana fararen hakoransa yace "to nima ngd," sae abun ya bata dariya, a xuciyarta tace "for d 1st tym na samu mai hankali da fararen hakora a kauyen nn, sae dae dressin din ne sae a slow," mutumin daxu ne na dandali. Ta shige gidan bayan tayi masa sallama, tsaye ta ga shatu bakin kofa tana huci, ta kasa karasawa har sae da shatu tace baxa ki karaso ba dn ubanki, Aneesah ta karasa gabanta na faduwa shatu tace "don ubanki shi garbeben ne kika walakanta a hanya," Aneesah tace "A'a ni....." mari shatu ta wanke ta da ta tura ta da karfi tace "maxa ki bi sa ki nemo sa ki ji abinda xae ce maki," Aneesah na kuka ta fice daga gidan ta rasa inda xata tafiya kawae take tana kuka, ta dan yi nisa ssae ta ga mudatheer xaune a kan wani benci da wasu yara biyu yana shan rake, yana ganinta ya mike tsaye da sauri yace "A'a 'yar birni ina xuwa kuma," bata ce masa komai ba ta tsaya tana kallonsa ya karaso gabanta ya tsaya yana ci gaba da shan rakensa yace "ko manta gidan naku kika yi, wae ma meye hadinki da su xulai ne" Haiydar ne xaune ya dafe kansa, Hajiya ta sa sa gaba a rude tana mako masa tambayoyi, ganin yaki bata amsan ko daya ne yasa tace "wae wlknci ne wnn Aliyu ko me, ka min magana mana nasan inda muka dosa," ya dago kai da kyar yana kallonta yace "me kike son sani mum, ta matso kusa dashi a hankali tace "ka gaya min tsakaninka da Allah Aliyu meye hadinka da Aneesah?" [9:30PM, 12/21/2016] Khaleesat: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 47..... Haiydar ya tsura wa mum din tasa ido bai ce komai ba har sae da ta sake maimaita tambayar a kage snn ya kauda kansa yace "son ta nake," Hajiya ta dafe kai a rude tace "so Aliyu, nashiga uku na lalace ni fateema, ita Aneesar," ba tare da ya kalleta ba yace "ehh," ta dan matso kusa dashi a tsorace, a hankali tace "kai ka dauketa da gsken knn," ya girgixa kai yana kallonta yace "ba ni na dauketa ba, baffanta ne for sure," Hajiya ta xaro ido tace "ni dae na shiga uku, to hoton da ku ka yi a tare a mota tana kuka fa?" yyi murmushi xae yi magana aminin mahaifinsa Alhaji usman ya bullo inda suke wani dan sanda na biye da shi a baya, da sauri kafin su karaso Hajiya tace "to abinda nake so da kai ynxu kar ka taba nuna ma kowa kana sonta ne, kai ka nuna ma kai baka taba saninta ba son, ka bar komai a hannu na kawae na san yanda xanyi, xa su ci ubansu kuma belin da suka ki bayarwa sae sun bayar," Haiydar yyi murmsuhi kawae yana kallonta, Alhaji usman ya karaso wajen yana kallon Haiydar da tuhuma yace "Ali ya aka yi hka, garin yaya meye hadinka da wnn yarinya Aliyu na san wnn sharri ne aka maka Ali?" dan sandan dake tsaye wajen yace "minti takwas ya rage cikin mintunan da muka baku," yana kai wa nn ya bar wajen. Abdul ne tsaye kan mahaifinsa dake magana da dpo a waya, baffa na gama wayan ya juya cikin jimami yana kallon Abdul yace "ka kwantar da hankalinka guy idan Allah ya yrda xa a ga Aneesah," cikin tsawa Abdul yace "nonsense, kullum surutan bnxan da kke min knn xa a ganta amma gashi yau har sati daya bbu yarinyar nn bbu lbrinta," baffa yace "ohh God ya kke son nayi guy, kaga kullum sintirin station nake, nn da kwana biyar kuma xa a shiga kotu, ko belinsa fa ban yrda an bayar ba, ka kwantar da hankalinka duk inda ya kai Aneesah xae fito da ita," Hajiya xuwaira dake xaune ta xabga tagumi kmr gske, tace "ni duk na rasa ta cewa Alhaji, ynxu wa yasan halin da yarinyar nn take ciki, amma wnn anyi tsinannan yaro" Abdul yyi tsaki yace "to ita ma uwartata sace ta aka yi knn don bata gidan" baffa yace "no, ni na sa ta ta tafiya gombe washegarin ranar da abun ya faru, ko daxu na kirata nace ta kwantar da hankalinta an kusan ganin Aneesah, ko so kke na bar ta nn ita ma ayi awon gaba da ita, ace gangancina ne, Allah kadae yasan me suka yi masa ya dauke Aneesar,duk kwadayinsu ne ya jawo masu wnn abun " hajiya xuwaira tace "kuma fa haka ne wllh, amma kadaina cewa hka Alhaji dan adam baya wuce fadawa kaddara" Abdul ya tabe baki yace "duk wnn ku ta shafa ni dae kawae a fito min da Aneesah na aura," yana kai wa nn ya fice daga falon fuuu. Baffa yyi dariya kasa kasa yace "yaro man kaxa," Hajiya xuwaira ma dake dariyar tace "ae ni Alhaji ina alfaharin da na same ka a matsayin miji, kayi a rayuwa wllh," yyi dariya yace "kinga ina maka wnn tsinannan a kurkuku shi ma Abdul kama gabansa xae yi ya koma kan harkokinsa can london, kinga shi knn magana ta mutu, ita kuma tsinanniyar matar can tana gombe ta sake baki kan 'yar ta na gidana," suka yi dariya ssae Hajiya xuwaira na koda mijin nata tana wasa masa kai. Aneesah na tafe suna hira da karime da ta kulla kawance da xasu rafi debo ruwa, karime tace "har yau dae kin ki shigowa gidanmu ki gaida babata Aneesah," Aneesah tayi murmushi tace "ki bari anjima da yamma idan xamu sake komawa debo ruwa sae naje gaidata," karime ta tafe hannun jin ddi tace "yauwa kawata mai kyau," mudatheer su ka gani yana tafe yana shan rake, Aneesah ta bi sa da kallo har ya wuce su ganin bae masu magana bane yasa tace "kai dae baka gajiya da shan rake," ya juya yana kallonta yyi dariya yace xaki sha ne? Ta tabe baki ta girgixa kai tace "kayi ta shan kayanka," yace "me yasa jiya nake maki magana kika yi bnxa da ni," Aneesah tace "ohh shiyasa kayi kmr baka gan ni ba knn ynxu," yyi dariya yace "eh mana, sae mun hadu a dandali anjima sauri nake ynxu" yana fadin hka yyi gaba, Aneesah ta bisa da kallo tana girgixa kai, karime ta sauke ajiyar xuciya tace "Aneesah ina bala'in son mudasir din nn kmr xan kashe kai na amma shi bae ma san ina yi ba, kuma bani kadae ba duk matan kauyen nn rububinsa suke, duk baya kulasu sae ke da ko sati biyu ba ki cika a kauyen ba, dubi fa yanda yake fira dake yake raka ki duk inda xaki snn yake hana su garbebe da tasiu kawo maki raini" Aneesah tayi dariya tace "kar ki damu xan gaya masa" karime ta xare ido tace "ke ki rufa min asiri don Allah, ba ruwana tsoro nake ji," a hka suka isa rafin Aneesah na ta dariya, cike suka tar da rafin da 'yan mata sun xo deban ruwa da yake da safe ne, Aneesah ta tsaya har mutane ukun da suka tarar gabansu suka gama deban ruwa snn ta tsoma tulunta cikin rafin, da karfi taji an fixgota, ta juya da sauri, tana juyawa ta ga Abu ce da kawayenta uku, tun da suka lura da shirin da Aneesah ke yi da mudatheer a kauyen dama suka tsaneta suka sa ta gaba. [9:30PM, 12/21/2016] Khaleesat: 2:43pm Sep 27 ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 50..... Aneesah ce xaune karkashin wata bishiyar mangwaro da tulunta cike da ruwa don daga rafi take, gefenta kuwa mudatheer ne da ke ta harbin tsuntsaye da catapault yana shan mangwaro, kallonsa kawae take ba tare da ya san ma tana yi ba, can ta mike tsaye tana kkrin daukar tulun ruwanta tace "kaga sae Anjima," ya juyo da sauri yana kallonta yace "au yi hkuri mantawa nayi ashe kina nn har ynxu," ta galla masa harara tace "lallai ma mudassir ka kirani kuma kace ka manta ka bar ni xaune kmr wata sha sha baka san ana jirana a gida ba," yace "yi hkuri dama tambaya kawae nake son maki," ta dawo ta xauna tace "to ina jinka," ya juya yana ci gaba da harbin tsuntsayen yace "wae da gske ne jiya kin ma Abu duka a rafi?" Aneesah tace "koh?" yace "eh mana, ashe dae ke din jaruma tunda har kika iya nakada ma katuwar nn duka" ta tabe baki ta mike tsaye tace "to yyi kyau, shknn tambayar dama ta gulmace" yyi dariya yace "to yi hkuri xo muyi magana 'yar birni," ta dawo ta xauna da sauri tace "ehem yauwa dama ina son nayi maka tambaya mudatheer," yace "ina jinki," tace "dama ina son sanin ina ne hanyar gidanku a nn kauyen ni ban san hanyar gidanku ba," yana kallonta yace "xa ki je ne?" xata yi magana wani abokinsa mudi ya kwala masa kira daga nisa "mudassiru," ya mike da sauri yana amsa kiran abokin nasa yace "gani nn xuwa," da sauri Aneesah tace "A'a baka bani amsa na ba mudassir xaka wuce kuma," ya juya ya kalleta yace "it's of no use 'yar birni," yana fadin hka ya juya da sauri ya bar wajen yyi gun mudi dake jiransa. Ta bisa da kallon mamaki baki bude har suka bace mata, lah yana jin turanci, abinda ta fadi knn a xuciyarta ta mike tsaye har lkcn tana mamaki ta dauki ruwanta ta bar wajen. Yau ita ce ranar da aka shigar da karar Haydar cout, kotun ya samu halartar jama'ah da dama masu son jin yanda xa a kare don lbrin ya baxu ko ina a Abuja ta dalilin Alhaji shehu don babban dan siyasa ne, gidan redio, tashoshin tv da sauransu duk xancen ake yi, kowa dae ya baxa kunnuwa ana son jin hukuncin da xa ayi ma Haydar da ya sace 'yar honourable shehu wae, wasu suce kasheta yyi wasu kuma su ce saida ta yyi dae, duk yanda barrister umar ya so kare Haydar bisa xargin nn da ake masa na sace Aneesah hkn bae yiwu ba don xafi kawae Haydar ya tara masa a kotu ya rikita masa kwakwalwa duk yanda ya so Haydar ya basa hadin kai kin basa yyi, tsaf bbu karya ya xayyane ma kotu abinda ke tsakaninsa da Aneesah har ixuwa ranar da aka ce ta bace sabanin yanda mahaifiyarsa tace xae yi, bbu abinda ya daga ma Hajiyar tasa hankali irin wnn, don daga ita har barrister umar ca suka yi masa ya nuna bae san Aneesah ba ma kwata kwata, amma Haydar bae yi hka ba, iyakar gskyansa ya fada ma alkali har hoton su da aka nuna masa bae karyata ba yace su ne kuma kuka take yi lkcn amma bae san wanda ya dauki hoton ba, Alhaji usman duk ya rikice sae xufa yake bae yi tunanin Haydar xae yi hka ba bayan ga yanda suka tsara masa, baffa da matarsa kuwa kmr su xuba ruwa a kasa su sha a lkcn dan murna amma basu nuna ba don Hajiya xuwairar sae matsar kwalla take wata munafukar kawarta na lallashinta kmr gske, baffa ko sae jijjiga kafa yake cike da jimami yana girgixa kai, Haiydar kam ca yyi Allah kadai ne shaidarsa da mahaifiyar yarinyar nn amma kuma bae ganta a nn ba, nn da nn baffa ya rude, Alkali ya bukaci da a fito da mahaifiyar yarinyar lawyern da baffa ya kawo yyi saurin cewa ae tana can gadon asibiti rae a hannun Allah don ba karamin girgixa ta batar 'yar ta kwaya daya yyi ba, dole Alkali yyi adjourn din case din har xuwa nn da sati uku, Haydar kuwa daga nn prison xa a wuce da shi, kuma a tabbatar mahaifiyar yarinya xata bayyana cikin kotu ranar da xa a sake xama, lawyern baffa yyi saurin amsawa alkali ya kama gabansa don ita ce kara ta karshe a tym din, Hajiya bata nuna ko alaman tashin hankali ba bayan an fita da Haydar din, sae ma murmushin mugunta da tayi ta fice daga kotun pretty na biye da ita a baya tana kuka, su sumy dama ca suka yi bbu inda xa su, a bakin motar Hajiya ta daka ma pretty tsawa tace "da'alla ki rufe min baki munafukar bnxa kawae, Amina nayi nayi dake ki gaya min inda gidansu yarinyar nn yake kin ki, nace ki gaya min ko kinsan wani abu game da ita nn ma kin ki, kuma nasan karya ne ace yanda ku ke da Aliyu baya maki xancen shegiyar yarinyar nn," pretty bata tanka ma uwartata ba ta shiga mota tana ci gaba da kuka, baffa ne ya karaso gaban motar yana kallon hajiyar yace "munafukan bnxa kawae mugaye, ae asirin mugu macucin danki ya kusa tonuwa, in Allah ya yarda sae ya fito min da 'ya ta," Hajiya tayi wani irin dariya tana kallon baffan tace "mu xuba da ku, wllh wllh sae nayi maku abinda har ku bar duniya baxa ku taba mantawa ba kai da iyalan gidanka, ita kuma tsinanniyar 'yar taka sae nasa tayi da ta sanin sanin da na," tana kai wa nn ta shige mota ta tada masa kura ta bar wajen a guje, baffa yyi dariya ssae yace " to fa, ashe dae ita ma ba[truncated by WhatsApp] [9:30PM, 12/21/2016] Khaleesat: Khaleesat Haiydar‎Khaleesat Haiydar Novels 7 hrs · ~Aneesah~ By khaleesah Haiydar 49..... Shatu ta juya da sauri tana kallon Aneesah da ta kasa gaskata kanta cewa shatu ce ke kare ta yau, shatu tace "ke Aneesah duk shegen da ya taka ki a kauyen nn ki karyasa ni na sa ki, shiga muje ciki, idan ba tsiya ba duk an bi an takura ma 'ya ta a garin nn don bakin ciki, ae ma kadan tayi mata wllh, don ma bata kwashe mata hakora ba ta karkata mata baki" kyauta na huci a fusace tace "Ae kuwa yau bbu abinda xae hanani rama ma Abulo abinda karuwar yar nn tayi mata kan uban nn, wllh sae na rama ma 'ya ta" shatu tayi dariya da shewa tace "wllh kika sake ce mata karuwa sae na watsa maki garwashin wuta don tsohon barawon ubanki, akwae karuwar da ta wuce 'yar ki Abulo me fita gari a kauyen nn, kaji min mara kunyar mata" kyauta ta karaso tsakar gidan da gudu ta yo kan Aneesah Abulo na biye da ita a baya tana cewa "wlh yau sae mun kashe ki," shatu na ganin hka tayi hanyar murhun dake ci da icce ta kwaso itacen ta yo kansu da gudu tana cewa "dan bantan ubanku ku taba ta,", ba shiri suka fice daga gidan kmr mahaukata Abulo na ihu, shatu ta tsaye bakin kofa tana huci tace "da kun tsaya tsinannun ku ka ga yanda xan maku kaca kaca da wutan nn shegu matalauta kawae, barayi," Aneesah ta rakube jikin bango xuciyarta na ci gaba da bugu, shatu ta dawo cikin gidan har lkcin tana huci tana kallon Aneesah tace "kin min dai dai wllh, ae ni da kin gaya min tun farko dambe kika tsaya yi a rafi uban me xae kai ni taba ki, daga yau duk wanda ya taka ki a kauyen nn ki nutse sa cikin rafi ma karewarta ni na sa ki," Aneesah dae gyada mata kai kawae take a tsorace, tana kai wa nn ta shige daki sae ga ta ta fito da rub, ta mika ma Aneesah, tace "maxa ki shafa wnn a jikin ki," kai kawae Aneesah ta gyada mata nan ma, Zano ta tabe baki ta bar tsakar gidan, xulai kuwa tace "kinyi min dai dai Aneesah ae da cikin rafin ma kika jefata don na tsani Abulon nn," Aneesah dae bata ce mata komai ba sae kallonta da take, shatu ta kwalo mata kira ta xo ta dama kunu ruwan kan murhu ya tafasa, ta amsa da sauri ta shiga bukkar yin abinda ta sa ta. Haiydar yyi shiru yana kallon lawyern da Alhaji usman ya turo masa a matsayin lawyern da xae tsaya masa, lawyern dake ta jefo masa tambayoyi yaki amsa ko daya yace "Haba Aliyu sae kace ba barrister kmr baka san yanda ake tafiyar da case ba, pls ka bani hadin kai na karbi duk information din da ya kamata ka ga jibi xa a shiga kotu" Haiydar ya daga kafada yace "ni nace maku bna bukatan ko wani lawyer ya tsaya min, nima lawyern kai na ne," a fusace barrister umar yace "a ina ka taba jin anyi hka Aliyu, wnn ae haukane, ni don Allah ka amsa min tambayoyina na bar nn kafin lkcin da aka bamu ya cik," Aliyu yace "kaga what i only want yhu 2 have in mind is dat ba ni na dauke Aneesah ba, period. Kuma koma uban waye ya dauketa xae fito da ita, xae gane yyi da brrstr Aliyu," lawyern ya tabe baki ya mike yace "to yyi kyau, kana kullen xaka sa ya fito da Aneesar, idan ka ga dama jibi kayi compose din kanka, idan ko kaje kayi fuck up a court, dats ur cup of coffee kai ma kasan yhu will b goin straight 2 jail," yana kai wa nn yyi gaba, Aliyu yyi murmushi yana kare ma inda yake kallo ya gyada kai yace "ae gwara nayi ta xama a jail din da wnn takaicin," Baffa ne xaune a dakin Abdul dake ta faman smokin cigarette, duk ya cika dakin da hayaki, baffa yace "look son wajen ka fa na xo ka kashe wnn abun mana," a fusace Abdul ya mike tsaye kmr xae make uban nasa yace "me xan maka da ka xo wajena din," baffa yace "cool down son bnce xaka min wani abu ba," Abdul yyi tsaki ya koma ya xauna, baffa ya nisa yace "abinda nake so da kai shine ka koma bakin aikinka kafin lkcn da Aneesah xata......" cikin tsawa Abdul yace "kace me? Na koma london ba tare da wnn yarinyar ba, ina! Impossible baxae yiwu ba, ae in kaga na bar garin nn bbu wnn yarinyar to ba ni bne," yana kai wa nn ya jefar da guntun taban hannunsa kan tiles din dakin yace "nonsense, duk yanda xaku yi ku nemo yarinyar nn ku bani na tafi da ita inda xa ni na koya mata hankali da iya magana" ya fice daga dakin ya bar baffa da ya bisa da kallo ya kasa rufe bakinsa. Baffa yyi murmushi bayan ya fita yace "yaro yaro, yaro man kaxa, amma xaka ci ubanka," yana fadin hka ya mike har lkcin yana murmushi ya fice daga dakin. [9:30PM, 12/21/2016] Khaleesat: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 48...., Aneesah tace "meye hka xa ki fixgo ni hka Abu?" a fusace Abun tace "an fixgo ki din, baki ga mun riga ki ba xaki wani shige gabanmu," Aneesah ta tsaya da mamaki tana kallonta don ita bata ga kowa bayan 'yan matan nn biyu ba, karime tace "kai Abulo wllh bamu tarar da ku a nn ba," daya daga kawayen Abu ta watsa ma karime wani mugun harara irin ta 'yan kauye tace "xan nakada maki mugun duka idan baki kama kanki ba, yar shisshigi," Aneesah ta fixge rigarta daga rikon da Abu tayi mata tace "da'alla sake ni malama," mari Abu ta kai mata, Aneesah ta bude baki da mamaki tace "kika mareni?" Abu na huci tace "an mara din shegiya," Aneesah bata san lkcn da ta fixgota ta kai ta kasa ba ta shiga narka kamr an aikota, kawayen abu suka ruga a guje suka bar rafin, karime sae ihu take tana tsalle tana cewa "wayyoo Aneesah ki rabu da ita mu gudu babarta muguwa ce wllh," Aneesah bata ma san karime na yi ba, dukanta kawae take don tun ba yau ba Abu ke shiga gonarta a kauyen kawae kyaleta take yi, duk 'yan mtan rafin suka kasa raba fadan har sae da Aneesah ta gaji don kanta ta kyaleta ta deba ruwanta ta bar rafin, karime ta bi ta da gudu, suka bar Abu tana ta kwala ihu kmr xata tsaga rafin, ko da Aneesah ta isa gida bata gaya ma shatu abinda ya faru ba, shatu dake tsakar gidan xaune ta cika fam tana jiran aneesar da ta fi kusan minti talatin a rafi, Aneesah na shigowa gidan shatu ta dauki iccen da ta ajiye gefenta ta biyota a guje Aneesah ta durkushe wajen ta fasa ihu a tsorace tana kiran Amminta, sae da ta nakadeta iya son ranta snn ta kyaleta tana huci tace "don ubanki gobe idan na aike ki rafi baxa ki shanya ni a tsakar gida ba ga 'ya yana ko karyawa basu yi ba, xano ta fito tana huci tace "duk ba ke kika bata ta ba shatu, ta ga kullum nn nn kike da ita don ana shigowa gida ana hada ki da naira hamsin a sunan ana sonta, alhalin gamu nn bbu mai xuwa wajen mu ynxu, shatu xata yi magana kyauta mahaifiyar Abulo ta shigo gidan a fusace tana huci "shatu shatu shatu, fito ki ga abinda karuwar 'yar wajen ki tayi ma Abu na," shatu ta juya da sauri tana kallon abu da baki ya kumbura fuska duk jini tace " ikon Allah meye hka nke gani sae kace warce ta fado daga bishiya," kyauta na huci tace "bishiya?? tsinanniyar 'yar can ce tayi mata hka," shatu ta juya tana kallon Aneesah da jikinta ya dau bari tana hawaye, tace "me tayi maki ke?" Aneesah na hawaye a tsorace tace "mama ita ce ta fara neman tsokanata" shatu ta juya tana kallon kyauta tace "to kin dae ji," kyauta ta yo waje da ido tace "me?? Kmr ya naji," shatu tace "ca tayi Abulo ce ta fara tsokanarta ko ke kurma ce, don hka sae ki ja ma abulo kunne ta fita harkarta don Aneesah salaha ce ni nasan bbu ruwanta, kar watarana ta je tayi mata wnda ya fi wnn don nasan Abulo akwae aukin tsokana" kyauta ta saki shewan rashin mutunci tace "kan uban nn, ae yau wllh sae na rama ma 'ya ta," shatu ta cire tsumman dankwalin kanta ta daura kugu tace "kika taba min 'ya yau na nakada maki uban duka wllh wllh," [9:37PM, 12/21/2016] Khaleesat: [12/8, 21:11] ‪+234 803 751 8717‬: Khaleesat Haiydar ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 51..... Aneesah tayi shiru tana sauraran shatu da ta sa ta gaba wae xata yi mata magana a cikin bukkarta, shatu tace "kina dae jina ko?" Aneesah tace "eh mama ina ji," shatu tayi kasa da murya tace "ae dae kinsan malam tanko na nn kauyen?" Aneesah ta girgixa kai tace "A'a ban san shi ba?" shatu ta harareta tace "shi uban garbeben ne baki sani ba?" Aneesah ta dan yarfe hannu tace "ina dae jin lbrinsa mama," shatu tace "yauwa, kin dae san duk kauyen nn bbu mai kudinsa ko, kuma shanayensa ma sun fi ashirin da biyar kin sani, snn da siminti aka gina masa gidansa dake kusa da kasuwan 'yan gwari, 'ya yansa maxa da mata suna can wnn kauyen dake gaba da namu suna karatu wae a firamari, kin dae san bae ma cika xama a kauye ba sae lkci lkci don a can birni yake aiki amma duk matansa uku suna nn kauyen," Aneesah dae kai kawae take gyada mata gabanta na faduwa, shatu tayi murmushi tace "yauwa Aneesah, shi fa, wllh jiya malam ya xo ya sameni wae yace son ki yake da aure, da kin san yanda matan kauyen nn ke rububinsa ko Aneesah," shatu tayi kwafa ta cija dan yatsa tace "kar ki bani kunya Aneesah, mu ba mara da kunya, kinga dae ina da 'ya ya mata amma ban maki bakin cikin auren tanko ba don nasan duk karuwa xamuyi ko ba komai, don hka nake sonki bani hadin kai, wllh dubu daya jiya ya ba malam da kaji biyu," Aneesah ta kasa cewa komai don tashin hankali, ta shiga uku wnn tsohon namamajon da taji karime ke cewa xa a hada ta da? Da kyar ta gyada kai ganin shatu jiran cewarta take tace "to mama naji duk abinda kike so shi nke so," shatu tayi murmushi har sae da jajayen hakoranta suka bayyana snn tace "yauwa lu'u lu'u 'yar Albarka shi yasa nake son ki, amma fa karki ki kula su garbebe da su hudu da mai shayi, duk abinda suka ba ki ki karba ae basu san da xancen ba, amma gskya wnn mudassirun ki rabu dashi don na tsanesa wllh, gashi ko kwandala baya baki na gani," Aneesah dae to kawae take ta ce mata kanta a kasa, tana kkrin mayar da hawayen dake neman xubo mata, shatu tace "yauwa Aneesah maxa tashi ki je ga can guntun kaxan jiya ki dauka ki ci ki yi min wanke wanke ki gyara min gida ki debo ruwa ki ajiye, ni ynxu xan je saro gyada ne, tunda su gantalallun yaran nn ban san inda suka yi ba, tana kaiwa nn ta saba bakin gyalenta ta fita daga bukkar tana cewa sae na dawo, kuka kam har da na tashin hankli Aneesah tayi shi ranar, ohh ko wani Hali Amminta ke ciki ma ynxu, ko ina yaya Haydar dinta gashi ana shirin mata aure da tsoho, da kyar ta iya yin duk aikin da shatu ta sa ta kafin ta dawo don duk jikinta yyi sanyi. Da yamma tana gantalin nemo itacen girki a kauyen suka hadu da mudassir da lado, lado na ganinta yace "gidan malam mati basa taba siyan itacen naira goma, sae dae su tsinta a daji," bata ko kallesu ba ta wuce su don dama basa shiri da lado tunda ya nuna yana sonta tayi shun dinsa, mudatheer ya bita yace "'yar birni ba gaisuwa," ta juya tana kallonsa taga lado yyi gaba abinsa, hkn yasa ta xauna karkashin wata bishiya mudassir ma ya xauna, yace "shatu ta dokeki ne halan," ta tabe baki bata ce masa komai ba tana harhada icenta, sae da ta gama snn ta juyo tana kallonsa tace "wae don ina son sanin gidanku shine xaka wani ce min it's of no use ko [12/8, 21:11] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 53..... Yau ma kmr kullum Aneesah ta fita neman itacen girkin yamma ta hadu da Mudatheer, ta karaso karkashin bishiyar da yake ta xauna tana kallonsa tace "to baka fa gaya min gidan wa kke ba a nn kauyen" ya dago yana kallonta yace "ina yini?" tayi dariya tace "au na manta ina yini?" bae ce komai ba sae murmushin da yyi, snn yace "gidansu sanusi da lado nake ai kin sansu?" tace "lah wa inan kaxaman masu xaman kashe wando sae ji da kan karya, ko gona bnga suna xuwa ba" mudatheer yyi dariya yace "xasu maki duka kuwa idan suka ji ki" ta hararesa tace "tunda 'yar su ce ni ba, wae in tambayeka meysa su garbebe ke jin tsoranka toh?" nn ma yyi dariya yace "sbda mun taba gwada karfi dasu na raunata su gaba daya, daga nn suka gane ni wanene, kuma na samu kwanciyar hankali daga lkcn a kauyen." Aneesah ta dinga dariya har da buga kafa, yyi murmushi yace "yau ma sae shatu ta biyo ki koh, wae ma meye hadinki da mugayen mutanen nn marasu hali?" Aneesah tayi shiru bata ce komai ba, can ta mike tace "ni xan je neman woods na girki bye bye," ya mike da sauri yace "to bara na rakaki inda xaki samu woods da yawa," tace "to muje," ya shiga gaba tana biye da shi a baya. Da daddaren ranan tana dandali tana sayar da gyada wata 'yar makwabciyarsu shafa ta xo da gudu kiranta, wae shatu tace ta maxa ta dawo gida ko bata sayar da gyadan duka ba, Aneesah tayi ma kawarta karime dake saida xobo sallama snn ta dauki bokitin gyadar ta ta bar dandalin don abokinta mudatheer ma bae xo ba, tana isa gida taga wata tsohuwar mota da ta gama shan wahalar duniya tana neman freedom a fake a kofar gida, ta bi ta gefen motar ta shiga gidan, shatu ta gani xaune kan 'yar kujera, kan tabarma kuwa wani tsoho ne dake ta washe baki, gaban Aneesah yyi mugun faduwa ta dake ta karaso dan tsakar gidan da sallamarta snn ta shige bukkarsu, shatu na wagale baki tace "sannu da dawowa lu'u lu'u, in kin ajiye bokin ki fito ga malam tanko ku gaisa," Aneesah tayi kmr bata ji ta ba ta sulale kasa a hankali cike da tausayin kanta taji kmr ta fasa ihu, shatu ce ta shigo dakin da kanta tana ganin Aneesah a wnn hali ta hade rai, tace "ke ni fa ban son iskanci da rainin hankali, kina ji ina kiranki xaki yi bnxa dani ga bawan Allah can ya xo tun daxu yana jiranki, an gaya maki yana xuwa gun 'yan mata ne da sunan xance, wllh sae dae su suje gidansa su same shi, don mun samu ya tuko santaleliyar motarsa har nn shine xaki masa walakanci, maxa shafa jan baki da hoda ki fito yana jiranki," Aneesah ta mike tsaye da kyar tana kkrin mayar da hawayen da ya cika idonta, shatu na kallonta tayi duk yanda ta ce mata, snn ta sa ta yafa wani dan guntun mayafi, xata fita shatu ta jawo ta da sauri, ta marairaice fuska kmr xata yi kuka tace "ki tausaya min Aneesah idan muka rasa wnn daman mun shiga uku hka xamu ta tsaya wa a talauce har mu mutu, don Allah ki ba sa hadin kai, duk me yace maki kiyi, kinga ko sati biyu baxa a yi ba xa a daura auren ku, idan ma baki son xama wnn kauyen ne sbda 'yan sa ido kawae sae ki koma kauyen dake gaba da wnn yana da gida a can aka ce wae, ki rufa min asiri kar ki sa a mana dariya don ixuwa ynxu lbri ya gama baxuwa wae malam tanko na birni xae aure Aneesah, kar ki bani kunya don Allah," tunda shatu ta fara xancen ta kan Aneesah a kasa yake tana kukan xuci, har shatu ta sallameta tace maxa taje yana jiranta, ta fita jikinta a sanyaye ashe har ya fita kofar gida yana jiranta, tana karaso wa kuwa ya washe hakora yana murmushi yace "yauwa 'yan mata sannu da fitowa," ita dae bata ce kmai ba ta tsaya kanta a kasa, yace "to mu shiga cikin mota muyi hiran mana amaryata," ta dago cike da tsana tana kallonsa tace "A'a nn ma ya isa," yace "haba amaryata ae yawa ne a gan mu tsaye kmr yara a nn, ke dae shiga kawae,"ya bude motar yana kallonta, Aneesah tayi murmushin takaice tace "ni fa baxan shiga wnn motar ba malam," ya tsaya kallonta na kusan minti biyar snn ya bude motarsa ya shige ya ja ta yyi gaba, ta tabe baki a xuciyarta tace Alhmdllh ta shiga gida abinta, shatu na tsaye a bukkarta sae kai komo take ta kasa xaune ta kasa tsaye, Aneesah na shigowa ta riko hannayenta da sauri har wani bari jikinta yake tace "har ya tafi, nawa ya baki," Aneesah ta dan koma baya tace "wae fa mama sae na shiga motar da kila ko fitila ma bbu, ni ko nace masa baxan shiga ba shine ya wuce," shatu ta xaro kwala kwalan idonta ta daura hannu a ka ta kwala ihu tace "shiknn ta ja mana, Na shiga uku ni shatu don ubanki koransa kika yi sbda kin isa?? Na banu na lalace," Aneesah ta tsorata sosae da yanayin da shatu ta shiga, ta dinga komawa baya, cikin tsawa shatu tace "xo nn don ubanki shegiya mugu," [12/8, 21:11] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 54..... Aneesah ta fasa ihu ta durkushe wajen ganin shatu ta yo kanta, duka kam ta sha shi ranar don shatu komawa tayi kmr wata mahaukaciya, daga karshe ta saba gyale wae xata bi sa gida ta ba shi hkuri duk a rude take, Aneesah dae na durkushe tsakar dakin tana kuka, har shatu ta fita ta dawo kmr an hankadota cikin fushi tace "kuma maxa ki dauki bokitin gyadata ki koma dandali ki tabbatar kin sayar min gaba daya idan ko ba hka ba kar ki kuskura ki dawo min gida, shegiya kawae mugu 'yar bakin ciki," tana kai wa nn ta fice. Aneesah ta kife kanta a kasa tana kuka mai ban tausayi Amminta kawae take tunawa, da kyar ta lallaba ta mike ta dauki bokitin gyadar ta fita daga gidan, a hanya suka hadu da mudatheer ya kirata da kmr baxa ta je ba, har tayi gaba ta dawo, yace "shatu ta doke ki knn," tayi shiru bata ce komai ba tana goge hawayen fuskarta, ya nuna mata benchi ta xauna, bata yi musu ba ta xauna, yace "dandali xaki" ta gyada masa kai, yace "meyasa tun tuni baki je ba sae ynxu, gashi har kusan ten, ae an kusa tashi ma," bata ce masa kmai ba, yyi murmushi yace "me kika yi ta doke ki?" xata yi magana ta fashe da kuka, yyi shiru yana kallonta har tayi mai isar ta, snn ya sake tambayarta me tayi, ta kwashe duk abinda ya faru ta gaya masa, yyi dariya xae yi magana, ta mike a fusace xata bar wajen ya riko hannunta da sauri yace "Haba 'yar birni ni malam tanko ne ya ban dariya," tayi tsaki ta dawo ta xauna, yace "to wae baki gaya min hadinki da su shatu ba har ynxu" tayi shiru, yace "yau ma baxa ki gaya min ba knn" tace "sbda me kke son sani?" yace "i just want 2 knw a bit about yhu, kinga i may b leavin in 3dayz tym" ta wara ido tace "wucewa xaka yi?" yace "yes, na gama abinda ya kawo ni," Aneesah tayi shiru duk sai ta ji ba ddi, xata yi magana sae ga Zano da kawayenta sun dawo daga dandali, tana ganinta ta mike da sauri gabanta na faduwa tace "na shiga uku mudatheer xata gaya ma mama, kuma ban ma gama saida gyadar ba, ya ce nawa ne gaba daya, tace "dari uku ne ina ga," ya ciro dari biyar ya mika mata tace "aa ni ka rike kudin ka kawae," ya harareta yace "xaki koma ki kara shan wani dukan kuwa," ta karba tana kallonsa, tace "to gyadar fa?" ya ce "ki koma gida da shi, sae kice su garba ne suka baki kudin xata ji ddi tunda mayyar kudi ce," Aneesah tace "to bbu canji," yace "eh ki kai mata hka," tayi masa gdya ta mike jikinta a sanyaye ta kama hanyar gida, tana tunanin shawarar da karime ta bata ranan bayan ta bata lbrinta tun daga farko har ixuwa ranar da baffa ya kawota kauyen, karime tace ta gudu kawae amma ta kasa gudu wa daga kauyen kuma ta rasa dalili, kwata kwata bata sha'awar barin kauyen ita kam ta rasa meyasa, don wani lkcn ko tunanin gida bata son yi, a hka ta isa gida gabanta na faduwa a xuciyarta tana cewa "Allah yasa Zano bata gaya ma shatu ta gan ta da mudatheer ba, amma sae ta samu ma bata karaso gida ba, shatu na ganin dari biyar ta rikice ta dinga sa ma Aneesah Albarka ba tare da damu da inda ta samo ba ma. Washegarin ranar sae ga malam tanko ya xo da daddare, shatu ta lallabata ta fita, bata yi masa musu ba ta shiga rubabbiyar motar tasa, sae washe hakora yake yace "amaryata muje gun sule mai suya in dan siya maki nama," ta girgixa kai tace "bana ci," yyi dariya snn yace "to muje in xaga dake kauyen ko ya kika ga," gabanta ya dinga faduwa ga tsoran shatu, ba tare da ta sake wani tunani ba tace "toh," yyi murmushi yace "yauwa Amaryata, snn ya tada motar, ya ja ta," shatu na leke ta katanga, tana ganin hka ta sauke ajiyar xuciya ta daga hannu sama tace Alhmdllh bata tona min asiri ba, 'yar albarka. [12/8, 21:11] ‪+234 803 751 8717‬: Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 55..... Aneesah dae bata tanka ma malam tanko dake ta sharara mata surutu a motar ba, hasalima kauda kanta tayi tana kallon glass din motar, ita duk kyankyamin motar ma ta isheta, yace "Haba amaryata ya hka ina ta magana kin min shiru," nn ma bata tanka sa ba, har suka isa gun sule mai nama, ya siya naman dari da hamsin ya bi ta shagon lado ya siya pure water leda biyu snn ya dawo ya shiga motar rike da naman da ruwan ya mika ma Aneesah yana washe rubabbun hakoransa, tayi kmr bata san yana mika mata ba, ya ajiye gefenta yace "sannu amaryata," ko kallnsa bata yi ba har ya ja motar suka bar wajen, taga yyi parkin wajajen gonannakin mutane, ko ina duhu sae dan hasken wata, ya kamo hannunta yace "amaryata ci nama," ta fixge hannunta gabanta na faduwa tace "meye hka?" ya dan hade rae yace "nama nace kici," a fusace tace "ban ci, ka ci kayanka nace mka yunwa nke ji ne" tana fadin hka ya fixge dan mayafin dake kanta yace "ke kar fa ki kawo min raini, kin san ko ni wanene," ta fara kkrin bude motar xata fita ya fixgota yace "ina xaki," ta hankadesa da sauri tace "to motar ta ubana ne da baxan fita ba," yace "ae baki isa ba yarinya sae kin biya min bukatata yau, cikin kwanaki uku na kashe maku fiye da dubu daya, hakosu nace ina yi a rami" ta yo waje da ido a tsorace ta fara kkrin bude motar ya rikota yana kkrin yaga rigar jikinta tace "nashiga uku, meye hka, malam ka rabu dani ni ba 'yar iska bace," yace "ae nima din ba dan iskan bne, kudina da kuka ci xan amsa ta nn," bae ko damu da haukan da take yi ba ya matse ta yana kiciniyar cire mata kayan jikinta, ta fasa ihu, amma bbu mai jinta dan gurin kmr daji yake, ta wanka masa wani lafiyayyan mari tare da basa wani naushi a ido da karfinta, ba shiri ya saketa bayan ya saki 'yar karar axaba, hannunta na rawa ta shiga bude motar ya budu xata fita ya fixgota ta yakushi fuskarsa ta fice a guje, ko dankwali bbu a kanta, gudu kawae take a tsorace tana bin hanyoyin da ta san xae sada ta da gida, garbebe da lado ta hadu da a wani corner suna ta tuntsirar dariya suna lbrin irin bata wata yarinya hajjo da suka yi jiya da daddare, tana ganinsu ta juya da sauri ta canxa hanya, ji tayi lado na cewa kae garu ga 'yar birnin nn ita ce, suka ko bita a guje, ita ma gudun take kmr xata tashi sama, cikin ciyawa ta labe jikinta na rawa har suka wuce ta da gudu, gabanta ya dinga faduwa ga tsoran kar maciji ya sareta a wajen, ta kai kusan minti goma a cikin ciyawar gudun kar ta yi gaba su hadu kuma, daga karshe wata hanyar ta canxa kuma, ta dinga gudu tana waige waige tana kuka kide kide ta dinga ji daga nesa alamar ta kusa dandali, ta tuna mudatheer yace ta xo dandali xae nuna mata abu, bata bi ta dandalin ma ba don bata san ko sun yi can ba ta sake canxa hanya tana dan tafiya da sauri da sauri tana waige waige, ji tayi ta ci karo da wani katon dutse ta fasa ihu tayi kasa xata fadi taji an yi saurin rikota su ka fadi a tare duk da bata wani buge ba dan kan wanda ya kamota ta fada sae da ta fashe da kuka, taga ya ciro wayarsa da sauri yana kkrin haska fuskarta yace "Goddam Yhu baki kalln gabanki ne kina..." yana haska fuskarta da wayarsa taji ya dan koma baya da sauri yyi tsit, ita ma shirun tayi tana ta kallon fuskar dake gaban screen din wayar, ganin ya ki daina haska ta ne yasa ta fixge wayar daga hannunsa ta shiga haska fuskarsa ita ma, wani kyakkyawan handsome guy idonta yyi tozali da, ta tsura ma manyan fararen idanunsa nata idon, ta saukar da kallonta kan pink lips dinsa dake ta kyalli, wayyo ya Haydar dinta exactly, fixge wayar yyi daga hannunta ita ma, ya tura ta ya mike tsaye yace "kina tafiya kmr wata mara saiti dubi yanda kika min da jikina," bata ce komae ba ta fara tafiya a sanyaye ya fixgota yace "cnt yhu thank me, da na barki da kin fasa kai yarinya," ta fixge hannunta ya sake fixgota ya ja ta suka xauna kan dakalin da yake a xaune, yace "amma fa ke kyakkyawa ce, wait ko ma dae kece mudatheer yace na xo na gani a wancan gurin haukan naku?" ya fadi hkn yana nuna mata dandali, tace "lah kasan Mudatheer ne?" ya gyada mata kai yace "yea sch son dina ne muna sec sch, nn yake service ae, amma gobe xai gama shine yace na xo naga yanda kauye yake tunda ina garin," ke kuma naga baki yi kalan 'yan kauye ba, hw come kike kauye, ko dae hutu kika xo kema, ya sunanki, me ma yake sa ki gudu da daren nn, baki tsoro baki dauki fitila ba Aneesah tace "kai wnn irin tambaya hka sae kace dan jarida," yyi dariya da ya bayyana dimples dinsa, ta tsura masa ido tana kallo, Haydar kawae take tuna wa, ya daura hannu a kanta ya wara idonsa yace "ya dae" ta buge masa hannu tace "meye hka," yace "ohh sowie bby," ta tabe baki a xuciyarta tace "wnn dae dan iska ne dama yyi kama da su," ta mike xata bar wajen ya fixgota har tana faduwa kansa yace "ke baki gaya min sunanki ba," tace "A'a meye haka malam," yace "sae kin gaya min sunanki xaki bar nn," d[truncated by WhatsApp] [12/8, 21:11] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 57..... Kamar daga sama Aneesah taji abu ya buge ta da karfi, daga nn kuma bata sake sanin abinda ya faru ba, karime da su xulai suka fasa ihu ganin abinda ya faru suna cewa "wayyo shiknn ya kashe mana Aneesar mu," mai motar ya fito daga motar da sauri yace "subhanallahi," ya durkushe gabanta ya dago ta, su karime duk suka xagaye shi suna koke koken Aneesah ta mutu, ya tura xulai dake daf da kansa tana rusa ihu a fusace yace "ke da'alla ja can uban wa yace maki ta mutu," xulai ta koma baya da sauri tana yarfe hannu tace "wayyo ashe bata mutu ba karime," daukar Aneesah yyi ya saka cikin motar ya dawo xae shiga driver sit, karime ta bisa da gudu xulai da yayarta Xano na biye da ita a baya, karime ta rike motar tace "kai ina xaka kai mana 'yar uwarmu?" xulai ta fara kkrin bude motar a rude wae xata ciro Aneesah, ita kuma xano ta yi kauye da gudu neman taimako wae wani xae sace Aneesah a motarsa, shi ko ya fixge xulai daga jikin motarsa ya jefar snn ya bude motar ya shige, suka dinga ihu suna bubbuga motar da karfi, bae ko damu da hka ba ya tada motarsa ya ja ta ya bar wajen a fusace kuma da gudu don har yana neman buge karime. Shatu ta saki salati ta fito kofar gida a guje bayan lbrin abinda ya faru ya risketa tana cewa "wayyo shknn na shiga uku ni indo, ku ka ce me? Ya tafi da ita ina?" xulai dake ta rusa kuka tace "a motarsa ya tafi da ita," nn da nn lbri ya baxu kauyen wani mai mota ya kade Aneesah ya tafi da ita kuma a motarsa, mutane suka dinga fiffitowa da daddaya da daddaya aka taru kofar gidan shatu da ta xama kmr mahaukaciya wae an sace mata 'ya kuka har da majina faca faca, karime da mamarta ma na tsaye wajen ana ta jajanta abun sae kuka karime take yi, xano ta raka samarin kauyen xuwa gun da abun ya faru aka bi bayan motar amma aka rasa inda mota tayi, sae kusan maghrib kowa ya watse ya koma gidansa, aka bar shatu da 'ya yanta suna ta kuka, banda Xano da tace "to wae shatu sae kace uwarki ta bata ko 'yar da kika haifa a cikinki, tunda ba a ganta ba ba shiknn ba" tayi tsaki ta jawo kayan kwalliyanta xata yi shirin dandali, shatu ta sharbe majina tace "don ubanki da kin san abunda muka rasa ynxu da baxa ki ce komai ba," Malam mati ya shigo gidan da buhu a hannunsa, rabon sa da gidan yau kwana biyar knn don bae cika xama kauyen ba, yana shiga Bukkar shatu yace "ke shatu me nake ji a gari wae yarinyar nn mae mota ya gudu da ita, ina ya kai ta, kin manta jan kunnen da Alhaji ya mana, masifa kike son ja mana" shatu tace "to ba aikensu nayi ba malam," yace "to shi mai motan daga ina yake kuma ina xa sa?" xulai tace "bakaken kaya ya saka gaba daya har takalmi da tabarau, kuma mu bamu san inda xa shi ba" Xano tace "kila ma dan yankan kai ne," shatu tace " lah! kuma fa wllh hka ne ya motar tasa yake?" xulai tace "katuwa ce motar ita ma bakakirin kmr kayan jikinsa," malam yace "shknn ae barka ma da ya tsaya a kanta," xano tace "shi dae na gani malam amma tun tuni shatu ta bi ta cika ma mutane kunne da kuka da sharban majina, sae kace uwarta aka sace," shatu ta sauke ajiyar xuciya tace "to idan shehu ya xo kauyen nn me xamu ce masa malam," mati yyi mata kalln bnxa yace "ba sae mu ce mun aurar da ita, a can wani kauye ba, kuma ba na ce maki ko sati biyu ba ayi ba da ya kira ni ta wayar Buba ba, yace idan ta addabemu mu kasheta kawai mu huta da jaraba, da na kawo maki xancen ba ca kika yi aa ba kina da babban shiri a kanta," shatu tace "hka ne malam to tanko fa, ynxu shknn munyi hasara knn?" yace "to ya xa ayi, ni dae daga yau bna sn na sake jin batun yarinyar nn a gidan nn, tunda ta bata ta bata, idan shehu ya xo iya ka nace masa ma an kasheta kawae," shatu ta mike tsaye tana gyara tsumman xaninta tace "to shknn, amma ni dae ba hka na so ba wllh, ga shi ynxu shknn mun rasa tanko, tunda dae bae ce yana son su xulai ba," A hankali Aneesah ta bude idonta ta tsura ma agogon dake manne a bangon dakin da take, karfe sha daya ta gani, ta shiga bin dakin da kallo kmr mai son tunano abu bbu tantama ta gane asibiti take, ta mike xaune a hankali tana kallon hannunta dake manne da alluran drip, taji an bude kofa, ta daga kanta da sauri tana kallon mai shigowa, ya tsakar mata murmushinsa mai kyau ya karaso gefenta ya xauna yace "bby kin tashi," kallonsa kawae take yi da mamaki, ya daura hannu kan goshinta ta cire hannun a hankali tace "ka mayar da ni gidanmu," ya harareta yace "kina under treatment xan mayar dake gidan naku?" tayi kmr xata yi kuka tace "xa ayi ta nemana fa don Allah ka mai da ni gida, ina mudatheer?" yace "oho! kuma naki mayar dake gidan karfe sha dayan daren xan mai dake gida," tayi shiru tana kallon agogo, yace "ynxu dae me xaki ci," ta daure fuska tace "ba komai," yace "gud, bari na kira maki Dr," yana fadin hka ya fice daga ward din ta bisa da kallo. 2 mins · Khaleesat Haiydar... [12/8, 21:11] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 56..... Ya wara dara daran idonsa yace "waw sweet name Aneesah," Aneesah tace "to ka sake ni ai na gaya maka sunan nawa," ya xaunar da ita yace "No Aneesah tsaya mu dan yi hira, don Allah" xata yi magana ya daura yatsunsa biyu kan lips dinta yace "shhiii," tayi shiru tana kallonsa yyi murmushi yace "kina da kyau Aneesah," ta kauda kanta nn ma bata ce komai ba, ya kamo hannunta yace "hu2 kika xo yi nn Bby?" ta fixge hannunta tace "wae meye hka kke taba ni ne na sanka ne," ya kashe mata ido yana lasan lebensa yace "ni sunana Mujaheed Yusuf," tace "to naji," amma ka bar ni na koma gida, ya harareta yace "not until u tel me y u were running," ta dan marairaice fuska tace "wllh wasu mutane ne ke bi na," ya mike da sauri yace "su wa? A ina suke, me kika yi masu, xo ki nuna min inda suke," yana fadin hka xae fara tafiya ta riko hannunsa tana dariya tace "to me xaka masu?" yyi mata wani irin kallo yace "nuna min su kawae ki ga abinda xan masu," tana dariya tace "ae bn san inda suka bi ba," ya dawo ya xauna yace "da sun biyo ki har nn wllh da na cire masu hakoran bakunansu gaba daya," Aneesah tace "uhmm naga alama" Nan Mujaheed ya dinga mata surutu kmr da can sun taba sanin juna, ita ko ta biye masa sae dariya take yi, ana fara fitowa daga dandali ta mike da sauri tace "kaga ni xan wuce gida kar yayyina su gan ni a nn," xae yi magana ta hangosu xulai ta juya da sauri ta fara gudu ta bar wajen, yace "shit ban san wacece ita ba," mudatheer ne ya karaso gurin yana kallon Mujaheed yace "kana nn har ynxu ashe big bro, da ka shigo da ka ji ddi, amma sae dae 'yar birnin bata xo ba yau" Mujaheed ya dan daga kafada yace "na ganta, ko ba Aneesah ba," mudatheer yace "waw ita fa, a ina ka ganta?" Mujaheed yace "she's such a beauty, ynxun nn ta bar nn wae kar yayyinta su ganta, da gske nn aka haifeta" Mudatheer yyi dariya yace "A'a ko wata uku bata cika ba a nn," Mujaheed yace "ni kam na xo kauye a sa'a don na samu mata, kaga xuwa nan ya kamani duk sati knn" Mudatheer yyi dariya ssae yace "gskya ne, ka ga ni xan tafi kai kuma ynxu kke xuwa, amma fa sae dae gidan da take a nn ba gidan mutunci bne don mutanen gidan kowa ya san su da halinsu a kauyen nn," Mujaheed yyi tsaki yace "dont tel me dat, ina ruwana da halinsu, as far as ba su suka haifeta ba its none of my bzz," mudatheer yyi dariya suka bar wajen yana cewa "kaga ina ta damunka kaxo kauye kana ja min aji ashe alkhairi xaka xo ka tarar a nn," mujaheed yace "yaushe xaka tafi," "gobe da safe," mudatheer ya ba shi amsa, Mujaheed yace "xan samu ganinta da safe kafin mu tafi don Abuja nake son wucewa direct," Mudatheer yace "yes of course amma idan kaje rafi," Mujaheed yace "ehh sae naje to meye a ciki?" Mudatheer yace "to xaka kwana nn ne ko fita xaka yi," Mujaheed yace muje motata ma tana nan ae, ba karamin tashin Hankali Aneesah ta tarar a gidan ranan ba daga shatu don kasheta ne kadae bata yi ba, kuma wae washegarin ranar a gun tanko xata kwana ko taki ko ta so tunda dae shi xae aureta wae, kuka kam ta yi shi har kusan asuba, Da safe ta je debo ruwa a rafi duk jikinta a mace ga yawan faduwar gaban da take yi ta hadu da su Mudatheer suna jiranta karkashin wata bishiya, tayi mamakin ganinsu a tare amma tayi kmr bata gansu ba tayi gaba mudatheer ya kirata da sauri taki juyowa, ya mike ya bi ta yana cewa "Aneesah yau fa xan tafi shine kike min wlknci?" ta juyo da sauri tace "da gske?" yace "ehh," ta ce "to baxa ka sake dawowa ba," ya juya yana kallon Mujaheed da ya kasa daina kallonta yace "yayana xae dinga kawo maki visit ae," ta kalli Mujaheed ya kashe mata ido, ta galla masa harara tace "bana son visit din," Mudatheer yyi dariya yace "yayana ne fa," bata tanka sa ba tayi gaba duk jikinta a sanyaye ynxu Mudatheer wuce wa xae yi ya bar ta, da rana Mudatheer ya bar kauyen duk da ya so ganin Aneesah amma bae samu ganinta ba, Mujaheed ya kai sa har tashan da xae hau mota a motarsa shi da ya kamata daga can ya kama Hanyar Abuja yace ina ae sae ya dawo yyi sallama da Aneesah. Aneesah dasu xulai da karime na dawowa daga kauyen dake kusa da nasu sunje saro ma shatu gyada, suna tafe suna hira banda Aneesah da tayi nisa a tunaninta, oh ita ynxu hka rayuwarta xae kasance a gantale knn, tana tuna abinda shatu tace mata jiya da daddare wae gidan tanko xata kwana sae taji wani hawaye na xubo mata, xulai taji tana cewa "lah ga abokan Aneesah xuwa," Aneesah ta dago kai da sauri ta ga shanaye ke tahowa ta inda suke, a rayuwarta tana bala'in tsoransu ba kadan ba, duka suka tuntsire da dariya, ita ko ta hade rae xata canxa hanya xulai ta rikota tace "ae baki isa ba sae kun gaisa yau," ihu Aneesah ta dinga yi tana dukanta ta sake ta amma taki, sae dariya suke yi, karime ce kadae ta hade rae tace "meye hka xulai ku kyaleta mana," ganin sun ki sakinta ne kuma ga abun da take tsoro sun kusa inda take yasa ta fixge hannunta daga rikon da suka yi mata a guje ta afka dan titin motar dake wajen, suna ihu suna ga mota ga mota, amma ina bata ma san suna yi ba. [12/8, 21:11] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 59..... Mujaheed ya gyara xama yana kallonta yace "ina jinki" ta dago kai tana kallonsa hawaye kwance fuskarta tace "shknn," yace "karya kike," ta girgixa kai tana ci gaba da xubda hawaye tace "Allah gskyata knn nake gaya maka, baffa na ne ya kawo ni kauyen nn," Mujaheed yace "waye dan nasa da baya son ya aure ki?" ta dan yi shiru snn tace "su suna da kudi mu kuma talakawa ne shi yasa baya san dan sa ya aureni," Mujaheed yace "gud, to me ya hana mahaifiyar ki biyo ki nn?" A sanyaye Aneesah tace "bata san inda ya kai ni ba ai," Mujaheed yace "ku nawa ne a gurinta?" Aneesah tace "ni kadae ce, kanina ya rasu kwanaki, dama mu biyu ne," Mujaheed ya girgixa kai yace "Allah sarki, Allah yasa ya huta," Aneesah tace "Ameen," "to shi baffan naki ya ku ke da shi?" ya tambayeta yana kallon idonta, Aneesah ta sunkuyar da kai tace "yayan Abbana ne," mujaheed ya gyada kai yace "yaushe mahaifin naki ya rasu, kuma meye aikinsa kafin ya rasu" Aneesah ta galla masa harara tayi tsaki tace "ni don Allah ka kyaleni hka ka mayar da ni gida, komai ne xan gaya maka, kuma mai hakan xae kara ka da" Mujaheed yace "tab, ba gida kike son koma wa ba knn yarinya," Aneesah ta fashe da kuka tana kallonsa tace "don Allah kayi hkuri, nasan ana ta nemana a gida ynxu " ya dan kwantar da murya yace "kiyi hkuri, kina ban amsa ta xan mayar da ke gida," Aneesah ta goge hawayen fuskarta snn ta gaya masa lkcn da abbanta ya rasu da aikin da yake yi kafin ya rasu, Mujaheed yyi shiru yana kallonta snn yace "to bae bar maku komai bne, ko ko sun kare ne," Aneesah ta gyada masa kai tace "ehh," yace "ok ynxu baki son xuwa gun ummarki knn, kin fi son xama da mutanen nn su cuceki su yi maki auren dole?" Aneesah tayi shiru tana hawaye, yace "talk 2 me mana," cikin kuka tace "ina son xuwa gun Ammina," Mujaheed yace "to kin amince na kai ki gun Ammin ta ki ynxu?" Aneesah ta tsura masa ido har lkcn tana kuka, Mujaheed ya kamo hannayenta yace "dnt wrry kanwata, xan kai ki gun Ammin ki idan kika yarda da ni, baxan bari ki sake komawa kauyen can ba, am takin yhu home Aneesah trust me, nima ina da kanni kaman ki ," Aneesah ta fixge hannunta tana kuka ssai tace "su mama xasu yi ta nemana kuma," a fusace Mujaheed yace "ita kuma mahaifiyarki bata nemanki aka ce maki ko, sakayyar da xaki yi mata knn, kinsan halin da take ciki ynxu na rashin ki, ke daya fa kika rage mata, gujeta kike son yi ko ko uban me ya hada ki da 'yan kauyen nn marasu imani, consider yhur dear mum Aneesah, kar ki yi mata hka baki san halin da take ciki ba ynxu," kuka ssae Aneesah take ta kasa cewa komai, ya tsura mata ido bae hanata kukan ba sae da ta dan yi shiru snn yace "kin amince ynxu xaki gun Amminki?" a hankali ta gyada masa kai hawaye na xuba a idonta, yace "Gud Aneesah, ina xuwa" yana fadin hka ya mike ya fita daga dakin xuwa office din likita, Aneesah ta fashe da kuka tace "ni baxan iya bin ka ba nasan su mama na can suna nemana," tana fadin hka ta mike tsaye ta gyara daurin dankwalinta ko takalmi bbu a kafarta tayi gun kofa ta bude a hankali ta fita snn ta fara neman hanyar da xata bi ta fita daga asibitin, duk a rikice take duk inda ta bi ward ne, har daga karshe ta bi wata mata dake goye da yaronta suka iso har bakin kofar fita harabar asibiti, da sauri ta isa gate xata fita ta ci karo da nurse din da tayi mata allura jiya da daddare, nurse din tace "ke ina xaki, an sallameku ne," Aneesah ta fashe da kuka a rude tace "ehh," nurse din ta riko hannunta tace "ban yarda ba, ina mutumin da ya kawo ki," dae dae nn Mujaheed da likita da nurses har biyu suka fito haraban asibitin, Mujaheed ya jingina jikin bishiya yana kallonta, kuka kawae take ta kasa daga kai ta kallesa, ya karaso gabanta ya kama hannunta yyi ma nurses din da Dr. gdya snn yyi hanyar motarsa dake haraban asibitin ya bude baya ya sa ta shiga, snn ya xaga ya shiga ya tuka motar suka fice daga asibiti. [12/8, 21:11] ‪+234 803 751 8717‬: Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 58..... A tare Mujaheed ya shigo dakin da likita, likitan ya karaso kusa da Aneesah yace "yan mata hope bbu inda yake maki ciwo ko?" ta gyada masa kai kawae, mujaheed ya harareta yace "ke dae ki fadi gskya," ita ma ta galla masa hararan bata ce komai ba, likitan yyi dariya yace "to a dae tabbatar ta ci abinci, anjima nurse xata xo bata allura," yyi masu sallama ya fita, Mujaheed ya juya yana kalln Aneesah yace "bbyna me xaki ci?" da mamaki tace "waye kuma bbynka?" ya kashe mata ido yace "ke mana," sae abun ma ya kusa bata dariya amma bata ce kmai ba, ya hada mata tea ya xauna kusa da ita yace "bude bakin na ba ki, bbu xafi," ta hararesa ta dan matsa tace "wae meye hka ni ka mai da ni gidanmu," yace "to tashi ki tafi," ta fara kkrin cire alluran hannunta ya rike ta da sauri yace "ke kina da hankali kuwa?" ya kwantar da ita yana kallnta yace "kwanta ki huta dear, kiyi hkuri gobe xa a sallame mu sae na mai da ke gida," hkn da ta ji ne yasa hankalinta ya kwanta tayi shiru, ya ajiye mata tea a kan table din dake kusa da gadon da take yace "to kiyi hkuri ki tashi ki sha tea kanwata," yana gama fadin hka ya kma kujera ya xauna yana danna wayarsa, ta mike xaune a hankali ta dauki tean ta fara sha har ta manta rabon da ta sha tea, ta sha rabi ta ajiye ta koma ta kwanta daga nn bacci ya dauketa, Nurse ta shigo tayi mata alluranta ta fita. Can kusan karfe daya Aneesah ta farka, Mujaheed na xaune har lkcn amma wnn karan waya yake, ya juya yana kallnta yace "xaki yi fitsari ne kanwata?" ta hade rae tace "nace maka?" ya taso ya xauna gefenta yace "Allah ya baki hkuri," ita dae bata ce masa kmai ba, ya tsura mata ido, tace "lafiya?" ya kashe mata ido yace "Allah kina da kyau," takaici ya sa ta kasa ce masa kmai wnn dae da ganinsa dan iska ne, ta fadi a xuciyarta, yace "wont yhu thank me," bata ko kallesa ba bare ta tanka masa yace "kin san me, Allah baki gaya min ke wacece ba baxan maida ke kauye ba, don Mudatheer yace kin ki gaya masa hadinki da mutanen da kike tare da a kauyen," Aneesah ta xaro ido tace "ina ruwanka da ko ni wacece ni dae ka maidani gidanmu malam," yace "tab ashe dae baxa ki koma gidan naku ba, don gudu ma xanyi dake don ki sani," ta marairaice fuska kmr xata yi kuka tace "don Allah kayi hkuri," ya daure fuska yace "tohm nayi," oya tel me about yhur sef kuma bn da karya, don Mudatheer ya gaya min halin da kike ciki a village din nn," tace "to me hkn xae kara ka da," yyi dariya yace "abubuwa da yawa kuwa, haba kanwata ni fa yayanki ne," Aneesah ta tabe baki tace "ni dae bacci nke ji ma," yyi murmushi yace "to kwanta," tayi kwanciyarta ta juya masa baya. Washegari da safe, Mujaheed ya siyo mata breakfst ta ci kadan, ya ci sauran, ita dae duk hankalinta yyi kauye kar ma ta koma shatu tayi mata duka shi yasa take Allah Allah ya maida ta da wuri, karfe tara ya xauna gabanta yace "oya ina jinki kanwata gari ya waye," ta fixge hannunta tace "kai malam ni ka rabu dani," yace "tab, wllh baki gaya min ko ke wacece ba baxan mai da ke gidan naku ba," tayi shiru tana kallnsa jikinta a sanyaye, da ta dau ma kanta alkawarin karime ce mutum ta karshe da xata san ko ita wacece, ga shi Mujaheed ya takurata sae ya sani, alhalin ko mudassir da suka shaku da ma bata gaya masa ba, hawaye ya cika idonta tuno rayuwarta da tayi, Mujaheed yyi murmushi, don yasan akwae abu a kasa dama, yace "ina jinki" xata yi magana wayarsa tayi ring ya daga, ta tsura ma kyakkyawan fuskarsa ido tana kallon lebbansa dake kyalli, bayan sun gaisa taji yace "in'sha Allah Mum yau xan shigo Abujan... No ki kyaleni da dan iska mara hankali, ya ci ubansa da son yarinyar, yarinyar bnxa, wae ma shi uban yarinyar wanene a Abuja?" Aneesah dae kallon Mujaheed kawae take yanda yake yi sae abun ma ya bata dariya, taga yyi dariya yace "ki kwantar da hankalinki mum duk xasu cicci ubansu ina nn shigowa," yana kai wa nn ya kashe wayar yace "aikin bnxa kawae, ya ci uwarsa daga shi har shegiyar yarinyar, yarinyar bnxa" Aneesah tayi murmushi tace "xagi dae ba kyau," yace "ohh nayi xagi koh? Ni ban ma sani ba, wllh Aminina ne ke cikin matsala a Abuja, tare muka taso muka yi karatu da shi a holland, ynxu hka yana prison ana xarginsa da sace wata bnxa wae, shi da yake da big big babes a holland, ni fa shiyasa bbu ruwana da matan abujan nn dan 'yan iska ne, ynxu ma mum dinsa ce ta kirani, Allah kadae yasan idan ba plan bne wnn aka masa," Aneesah tace "Allah sarki, amma kar kayi saurin goya bayansa kila da gsken shi ya dauketa" Mujaheed yace "koma shi ya dauketa yyi min dae dae kuma xanje na karesa a kotu, don uwarta ba kwadayin abun duniya ya kaita soyayya da shi ba,kinsan ko waye shi kuwa," yyi kwafa yace "ki bari kawae ke dae," bck 2 bzz ina jinki" ta dan yi shiru snn a hankali tace "Ni marainiya ce, baffa na ne ya kawo ni nn ya ajiye don kada dansa ya aureni, bn san kowa a kauyen ba, ya raba ni mamata ya kawo ni gun mugayen mutanen nn da ban sani ba ya tafi ya bar ni" tana kai wa nn[truncated by WhatsApp] [12/8, 21:11] ‪+234 803 751 8717‬: Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 60.... Sae da suka kai dae dae titin da xae yi lead dinka xuwa kauyen snn Mujaheed ya juyo yana kallon Aneesah da har lkcn ke kuka yace "ae xaki gane gidan naku daga nn ko?" Aneesah ta kasa cewa komai sae kukan da take, yace "ohk, to sauka ki tafi, xan juya daga nn ne," cikin kuka Aneesah tace "to Ammina fa?" ya daga kafada yace "oho" ta hade kanta da gwiwa tana kuka, bae sake ce mata komai ba illa wayarsa da yake ta dannawa, ganin har kusan minti sha biyar bata ce komai ba kuma bata bude motar ta fita ba, yasa ya tada motar yyi driving dinta suka bar wajen, ta dago kai da sauri tana kallonsa tace "ka tsaya na sauka," yyi kmr bae ji taba, ya dinga sharara gudu da motarsa, kuka ta dinga yi da ihu tana bubbuga motar wae ya bude mata ta sauka, tafiyarsa kawae yake bae tanka ta ba, har sae da suka shigo kaduna, snn ya juya yana kallonta yace "idan na kai ki gun Ammin ta ki, ki gudo ki dawo nn," bata ce masa komai ba sae dae a hankali take kukan ynxu tana kallonsa, daga karshe bacci ya dauketa ma. Ko da ta farka sun kusa shiga Abuja, yana kallonta ta madubi yace "me xaki ci kanwata nasan kina jin yunwa?" ta girgixa masa kai tace "ba komai," sae ynxu taji tana mugun son ganin Amminta, kewar ta ya isheta, amma a kauye da ta fara tunanin amminta ciwon kai xae sa ta daina, ynxu Allah Allah kawae take ta ganta a gida kusa da Amminta, har haushin kanta ta dinga ji kan abun da tayi daxu. Karfe uku saura suka shigo Abuja, sae a lkcn tayi masa magana ganin hanyar da ya dauka tace "ba fa nn bane hanyar gidanmu yaya," ya ce "kin san me kanwata, ki bari da daddare na kai ki, bna son kowa yasan kina Abuja ynxu," ta marairaice kmr xata yi kuka tace "dn Allah nayi missin din Ammita ka kaini gida kawae na ganta bbu wanda xae san na dawo," ya girgixa kai yace "No sae anjima xan kai ki kanwata," har tayi shiru sae kuma tace "to ynxu ina xaka kai ni?" a tsorace tayi tambayar, yace "gida xa mu," cikin tashin hankali tace "gida kuma, gidan wa?" suna shiga traffic ya juyo yana kallonta yace "gidanmu," ta fashe da kuka tace "A'a ni ba ruwana wllh, ka kai ni gun Ammina kawae," yace "haba kanwata baki yrda da ni bne, wllh xan kai ki gida amma da daddare sbda tsaro," a hka ya dinga kwantar mata da hankali yana lallabata har ta hkura, basu suka isa gidansu Mujaheed ba sae kusan hudu sbda traffic, Aneesah ta dinga bin anguwan da kallo, a xuciyarta tace kudi na inda yake, yyi horn a wani kantamemen gida mai kyan gske, mai gadi ya bude gate da sauri har yana neman faduwa, ya ja motar ya shiga haraban gidan dake kewaye da shuke shuke masu kyau, bayan mai gadi ya gaishesa da yi masa sannu da xuwa, a garage yyi parkin, snn ya juyo yana kallonta xae yi magana ta riga sa tace "to yayana su mommy baxa su yi magana ba," ya kwantar da murya yace "kin san me Aneesah?" ta girgixa masa kai tace "A'a," yace "gidanmu ne nn, amma su mommy suna Malaysia," bata bari ya karasa ba ta katse sa da sauri "to waye a gidan ynxu," yace "ba kowa," ta fashe da kuka tace "wllh ba ruwana shine xaka kawo ni gidan da ba kowa, ni ka kai ni gun Ammina kawae," ya harareta a fusace yace "baki yarda dani ba knn? Idan kina tunanin xan cuceki ne sae ki xauna da matar mai gadin don yana da mata, har lkcn da xan kai ki gidan," yana fadin hka ya bude mota ya fito yyi hanyar shiga gidan, ita ma ta fito jikinta a sanyaye tana kare ma gidan kallo, juyawa yyi ya ga tana biye da shi a baya, ya jirata har ta iso gunsa snn ya ci gaba da tafiya, ya ciro makulli a aljihunsa ya bude kofar shiga gidan ya shiga da sallama ita ma tayi sallamar ta shiga katon falon dake cike da kayan alatu na more rayuwa, ta tsaya a bakin kofa tana bin falon da kallo, shi ko har lkcn yana tsaye bayanta yana jira ta karasa ciki ya kullo kofar, ta juya da sauri tana kallonsa a dan tsorace tace "kulle kofar xaka yi?" ya ma rasa me xae ce mata don haushi, kawae ya hangame kofar gaba daya yyi gaba abinsa ya haura sama, ta karaso cikin falon a hankali ta dan xauna bakin kujera, ta kai minti ashirin xaune a falon bata ga Mujaheed ba har ta fara bacci ya dan bugi kujeran da take kai, ta mike tsaye a tsorace tana kallonsa, jallabiya milk colour ce jikinsa, da ganinsa kasan wanka yyi, kamshin turarensa ya baibaye ko ina ta dauke idonta daga kallon da take ma kyakkyawan fuskarsa, yace "xo ki ga," a dan tsorace ta bisa sama gabanta na faduwa, taga ya bude wani daki ya shiga, ta ki karasawa ta tsaya bakin kofar bae damu da hkn ba yace ni xan tafi masallaci, ki tabbatar kin yi wanka snn kiyi sallah bathrom na cikin dakin, yana kai wa nn ya fito ta ja gefe da sauri ya tabe baki yyi gaba, sae da taji tashin motarsa snn ta shiga dakin, tana bin ko ina da kallo daga gani dakin kanwarsa ce, ta kalli kayan da ya ajiye mata kan gado, snn ta bude kofar bathroom din ta shiga tana kar[truncated by WhatsApp] [12/8, 21:11] ‪+234 803 751 8717‬: Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 61...... Aneesah na fitowa daga wanka ta sa kayan da Mujaheed ya fito mata da, ta dauki hijab din dake kan gadon ta saka, snn tayi salla kan darduman da ya shimfida mata a dakin, tana idar wa tayi jigum tana kare ma hadadden dakin kallo, ynxu kawae so take ta ganta kusa da Amminta, Allah Allah take karfe shidda yyi Mujaheed ya kai ta gida, tana cikin tunane tunanen nn taji yyi sallama, ta gyara Hijab din jikinta da sauri tana kallon kofar dakin, ganin bae shigo ba har lkcn yasa ta amsa sallamarsa, sae a snn ya turo kofar dakin a hankali ya shigo, ya karaso gabanta ya durkusa, ta dan koma baya da sauri, ya ajiye ledan Hannunsa yace "ga abinci nn ki ci," yana gama fadin hka ya mike ya bar dakin, sae da ya kullo kofar snn ta bude ledan, abincin eatry ne da kaxa sae lemun kwali, ta dan ci abincin kadan ta mike ta dauko glass cup ta debi lemun ta sha snn ta tura ledan abincin. Karfe shidda nayi Aneesah ta mike da sauri ta harhada kayan da ta cire ta dauka ta bude kofar dakin a hankali ta fara saukowa daga stairs din har ta iso falon, yana xaune sanye da 3qtre da farar singlet yana danna laptop, ta juya da sauri kmr warce xata koma sama, ya mike tsaye yace "ya dae kanwata," ba tare da ta juyo ba tace "kace da Maghrib xaka kai ni gidanmu ai," yyi murmushi yace "hka ake Maghrib kanwata?" ta fashe da kuka tace "wllh gidanmu nake so na wuce yayana," bae ce mata komai ba sae kallonta da yake, ganin shirun yyi yawa ne yasa ta juyo a hankali tana kallonsa, suna hada ido ta juya da sauri tana kuka a hankali, yyi murmushi yace "to xo ki xauna na sa kaya sae mu wuce," ta juyo ba tare da ta bari sun hada ido ba ta rabe ta nemi gu ta xauna a takure kan kujeran falon, shi ko ya haura sama, ko minti goma ba a yi ba ya fito sanye da kananan kaya hannunsa rike da makullin motarsa yace "to muje kanwata," ta mike da sauri ta bi bayansa rike da kayanta a hannu, ya juya yana kallonta yace "a hannu xaki rike kayan?" ta gyada masa kai yyi murmushi suka isa garage ya bude mata mota ta shiga shima ya shiga mai gadi ya bude gate ya ja motar suka fita daga gidan, Hka ta dinga yi masa kwatancan anguwarsu har suka iso layinsu, Mujaheed yace "ina da wani aboki a layin nn da, amma ya tashi ynxu" Aneesah da farin ciki ya isheta ga ta ga unguwarsu tace "haba dae da gske?" yace "eh wllh na taba xuwa nn sau daya kafin ya tashi," Aneesah tace "Allah sarki, a nn xaka yi park," ta nuna masa kofar gidansu, yyi parkin din snn suka fito daga motar, tayi kofar shiga gidansu da sauri yace "kanwata jirani mana," ta dawo cike da doki tace "to yayana," a tare suka shiga gidan, Aneesah ta karasa bakin kofar dakinsu da sauri tana cewa "Ammina, Ammina" amma shiru, ta tura kofar dakin da sauri taga duhu, ta fara kalle kallen tsakar gidan bata ga alamar da mutum cikin gidan ba, bata san lkcn da ta fashe da kuka a rude ba, Mujaheed ya karaso kusa da ita da sauri yace "me ya faru kanwata," cikin kuka tace "Ammina bata ciki?" ya kunna fitilar wayarsa da yake gari ya fara duhu yana haska dakin, ko ina baja baja, ga hotuna ta ko ina a dakin, kuka sosae Aneesah ke yi a bakin kofar dakin, Mujaheed yyi sallama ya shiga dakin ta bi sa a baya, bbu alaman mutum na rayuwa a dakin a ynxu dae don ko ina yyi kura, ya juya yana kallon Aneesah yace "haba kanwata, ki kwantar da hankalinki Amminki na nn bbu inda ta je," bata ce masa komai ba sae dae har lkcn bata fasa kukan da take ba, ya durkusa yana kallon hotunan dake watse a dakin, ya dauki hoton yusuf yana kallo yace "ina kuwa na taba ganin yaron nn, he looks familiar" Aneesah ta durkushe gabansa da sauri tace "ka taba ganinsa ne," Mujaheed ya sosa kai yace "yea ina ga kmr hka," can yace "yes na taba ganinsa ranar da nace maki na xo anguwan nn gun frnd dina," Aneesah na murmushi tace "don Allah, a ina ka gansa toh?" Mujaheed yace "ball dinsa na taka da motata ranan," Aneesah tayi shiru a sanyaye tana kallon Mujaheed, Mujaheed yyi murmushi yace "he ix a vry brave boy, tun kan na fito yyi knck din min kofar motata, ina fitowa kuwa yace sabuwa xaka siya min ko gyaramin wnn xaka yi," Mujaheed yyi dariya ssae yace "kai yaban dariya ranan, don mamaki ma kasa ce masa komai nayi" yana ganin hka yace "to idan bnda kudi na tafi, amma watarana na kawo masa ball dinsa," Mujaheed yyi murmushi yana kallon Aneesah da hawaye ya cika idonta yace "dubu biyu ke hannuna ranan, na dauka na basa yyi min gdya ya shiga gida abokanansa na ta dariya, a vry brave boy" can Mujaheed yyi shiru daga surutun da yake yace "hope ba sh[truncated by WhatsApp] [12/8, 21:11] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 63..... Budewar kofar da Mujaheed yyi ne yasa ta mike xaune da sauri ya karaso cikin dakin yace "kin yi sallah kanwata," ta gyada masa kai yace "Gud, sauko ki ci abinci to," ta girgixa masa kai tace "na koshi," ya harareta yace "c'mon, ko naxo na daga ki ne," da sauri ta tashi tsaye tana kallonsa, ya juya ya fita yace "ina jiranki," sae da ta daina jin takunsa a stairs snn ita ma ta fito daga dakin ta sauko falo, yana xaune kan dinnin yana cin apple, ta xauna a falo yace "ki taho mana kanwata," "A'a ni nn xan xauna," ta fadi hkn ba tare da ta kallesa ba, yace "Allah idan kika bari na tashi dauko ki xanyi, ni fa bna son kina min hka," ta hararesa bata ce komai ba, ya mike tsaye, da sauri ta tashi tsaye ita ma tace "wayyo don Allah kayi hkuri xan xo," tayi hanyar dinnin din ya ja mata kujerar ta xauna, snn ya tura mata kulan abinci gabanta, shinkafa ce da miya sae farfesun kaza da lemo, yace "gidan matar abokina naje na karbo maki, naga fried rice din daxu baki ci ba, kin saba da tuwon masara da miyar kuka a kauye koh?" murmushi kawae tayi bata ce kmai ba, da kansa ya dibar mata abincin a plate ya tura mata gabanta yace "maxa ki ci," bata yi musu ba ta dauki spoon tayi bismillah ta fara cin abincin, kallonta kawae yake yana tauna apple a hankali, ta dago kanta yyi saurin kauda kansa yana tace "kai baxa ka ci bane," yana kallonta yace "ae baki ce na ci ba," tayi murmushi ta ci gaba da cin abincinta, yace "ohh baxa ki ce na ci ba," ba tare da ta kallesa ba tace "ka ci mana," yace "to xuba min," tace "abinci nake ci," yyi murmushi yace "to yyi kyau bari na xuba da kaina," ita dae bata ce masa komai ba, ya xuba abincin shima ya fara ci, ta ci rabi ta tura sauran yace "ya dae, bae maki ddi ba ko?" tace "A'a na koshi ne," xae yi magana wayarsa tayi ring, ya dauka yana kallon mai kira, yyi murmushi yace Hajiya knn, Aneesah ta tsura masa ido, ya daga kiran taji yace "an yini lfya mum, eh ina Abuja daxun nn na shigo wllh... A'a ba sae kin xo ba ina gama cin abinci xan taho ynxu dama, ok bata mu gaisa, Hello 'yan matan yayanta ykk," Aneesah tayi murmushi ganin yanda yyi maganan, shi ko dariya yyi yace "to srry bby sae na xo," snn ya katse kiran ya ajiye, ya kalli Aneesah da ta kasa daina kallonsa har lkcn yyi mata far da ido yace "ya dae," kunya ya kamata ta sunkuyar da kanta bata ce komai ba, yyi murmushi yace " je ki shirya xa mu fita kanwata," ta hade rae tace "ina xa mu?" yace "gidansu wnn frnd din nawa da nake baki lbri, mum dinsa ce ta kirani ynxu," Aneesah tace "bbu inda xa ni," yace "sbda me kanwata, so kike na bar ki ke daya a gida," tace "ehh" yace "hmm sbda me baki sn xuwa ki gaya min kanwata," "don kar su yi wani tunanin daban," ta fadi ba tare da ta kallesa ba, yyi dariya yace "bbu ruwansu da hkn bby, they live a vry free life," ganin tayi shiru ne yasa yace "oya je ki shirya, ki bude wardrobe ko wani kaya yyi suit dinki ki dauka ki sa, nima shiryawa xan je nayi" ta mike tsaye tace "ni fa bbu inda xanje, ka je ka dawo," ta bar dinning din ta haye sama, ya bita da kallo yyi murmushi yace "perfect!" snn ya haura sama shi ma, yana gama shirinsa ya fito, yyi sallama ya shiga dakin da take, yace "idan kwanciya xaki yi ga bed, bana son kina kwantawa a kasa," yace "na kunna maki tv ne?" ta girgixa masa kai yace "to kina karanta Novel ne?" ta juya tana kallonsa tace "wani iri?" ya jingina jikin kofa ya rungume hannayensa yana mata wani irin kallo yace "na turanci mana, love nd romance," ta kauda kanta da sauri tace "A'a bna karantawa," yace "amma daxu na ga Novels a dakin ku ae," ba tare da ta kallesa ba tace "ba nawa bne," ya juya ya fita tayi tsaki a xuciyarta tace "wnn dae gantalalle ne," a tunanin ta wucewa yyi sae ga shi ya dawo da Novels har kusan uku ya ajiye gabanta yace "nyc Novels amma fa akwae romance....." a fusace tace "kai wae ni nace maka ina karantawa ne, ni ka tafi da kayanka," ya daga kafada yace "just 2 while away ur tym, ni na tafi bye, me xan siyo maki," ta galla masa harara tace "ba kmai," yyi dariya yace "to, idan lkcn sllh yyi kiyi," yana kai wa nn ya fice daga dakin, ita tsoro ma yake bata wllh, sae da taji fitar motarsa snn ta mike ta kulle kofar dakin da makulli[truncated by WhatsApp] [12/8, 21:11] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 62..... Aneesah ta fashe da kuka tace " uhm shine," Mujaheed ya wara ido yace "innalillahi wa inna'ilaihi raji'un," me ya samesa?" ta kasa ba sa amsa sae kukan da take yi har da shessheka, ya dago kanta yace "ya isa Aneesah Allah ya sa ya hutu, kar ki sake kuka, Addu'a xa kiyi masa," kai kawae ta gyada masa, ya dago ta yace "ina kike tunanin ammi xata tafi ynxu?" ta girgixa kai tana hawaye tace "nima bn sani ba," ya ciro handkerchief ya goge mata fuskarta yace "wani neighbour ne kuka fi close da a anguwan nn muje mu ji ko sun san inda Ammi tayi," a hankali Aneesah tace "Anty Amina ce," ya kamo hannunta yace "to xo mu je gun ta," suka fita daga gidan ta nuna masa gidan matar, Aneesah ce ta fara shiga da sallama Amina na xaune tsakar gida tana alwala, ta amsa sallamar tana cewa "wanene," Aneesah tace "ni ce maman mubarak," sororo ta tsaya kallon Aneesah baki bude, Aneesah ta yi murmushin dole tana gaisheta, matar ta rike haba tace "anshiga uku ke Aneesah daga ina hka?" Aneesah bata ce komai ba sae murmushin karfin halin da take, Aminar ta ja ta da sauri suka shiga daki tace "ikon Allah Aneesah ina kika shiga, daga ina hka" Aneesah tace "maman mubarack Ammina fa?" Matar ta girgixa kai cike da jimami tace "ae Ammi rabona da ita yau kusan wata uku Aneesah ban san inda tayi ba wllh, tun bayan sallaman da ta xo tayi min gashi ita ba waya ba, na kira su kaka a can gombe sun ce bata je ba, amma kuma suna waya ko ta yaya oho," Aneesah ta shiga xubda hawaye ba kakkautawa maman mubarack tace "ynxu me ya kawo ki nn Aneesah rayuwarki na cikin hatsari wllh kullum a kalla mutane fiye da biyar sae sun xo anguwan nn don ke, tsinannan baffanku ma duk kusan bayan sati yana xuwa kila don ya xo ya ga ko Ammi ta dawo ne ya sake korata oho, don ca tayi min shi yace ta tafi, wllh nemanki ake ruwa a jallo ban san me ke faruwa ba har kudi aka ce xa a bama duk wanda yasan inda kike ko ya gano inda kike a anguwan nn kuma mugayen mutane ne da alama, ynxu ke da waye, daga ina kike kuma?" kuka ssae Aneesah take tace "ni da bako ne maman mubarack," tace yana ina shi kuma a ina kika san sa, ko wnn ne mai xuwa gun ki, dama baffanki ba gidansa ya kai ki ba, Aneesah tace "yana waje," matar tace "to ya shigo mana, Aneesah bana son ki kara ko da minti goma ne a anguwan nn kar yan iskan layin nn su gan ki mu shiga uku," ynxu dae maxa je ki ce bakon ya shigo," Aneesah ta fita gabanta na faduwa suka shigo tare da Mujaheed ya gaisheta ta amsa da fara'a snn ta fara masa bayanin abinda ake ciki ynxu, Mujaheed ya fara jero mata tambayoyinsa na gado taki amsa ko daya tace ita dae ba ruwanta kawae ya tafi da Aneesah kar su sake dawo wa anguwan, Aneesah na kuka Amina ta hadata da nikaf ta saka, ta rakosu har mota suka shiga, Mujaheed ya bata kudi mai yawa ta karba da kyar snn suka bar anguwar har lkcn Aneesah na kuka kmr ranta xae fita, cikn kuka tace "ina xaka kai ni yayana," bae tanka ta ba har suka isa gida ya shiga yyi parkn snn ya juyo yana kallonta a nutse ya fara magana "ki yarda dani Aneesah ba xan taba cutar ki ba, ki daukeni a matsayin yayanki da kuka fito ciki daya, idan ma baxa ki iya tsayawa tare da ni a gida daya ba ni xan bar maki gidan snn na maki alkawarin xan nemo maki amminki, Aneesah me yasa baki gaya min gskyan cewar baffan ku ne ya rike dukiyarku ya hana ku ba, wllh wllh ni Mujaheed sae na sa mutumin nn ya gane kuransa, xan sa ayi masa abunda har ya mutu baxae manta ba kuma baxae sake sha'awar cin abinda ba nasa ba, snn ko tsinkenku baxan bari a hannunsa ba" yana gama fadin hka ya fito ya bude mata mota ita ma ta fito a sanyaye, yana gaba tana binsa a baya har suka shiga cikin falon, ta xauna kan kujera duk jikinta a mace shi kuma ya haye sama. Ba a jima ba ya sauko yace "xan tafi masallaci, ke ma kije kiyi sallah," to kawae tace masa ya fita daga gidan, ita kuma ta hau sama ta shiga dakin da ya gwada mata daxu. Tana idar da sallah ta sake wanka, tayi kwanciyarta kan carpet din dakin abun duniya ya isheta. [12/8, 21:11] ‪+234 803 751 8717‬: Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 64..... Karfe takwas Mujaheed ya shiga da motarsa gidansu Haiydar, ya nemi gu yyi parkin ya fito, ya daga ma mai gadin dake gaishesa ba kakkautawa hannu kawae ya shiga falon gidan da sallamarsa, Hajiyar na xaune tana cin tufar dake gabanta a kan dan table, pretty na kwance kan kujera tana kallo, tana ganin Mujaheed ta mike da sauri ta rungumesa tana cewa "yayana oyoyo," yyi dariya ya daga ta sama yace "kai garin yaya kika yi nauyi hka bbyna," ta galla masa harara tace "ni ba nauyin da nayi yaya, karfinka dae ne ya ragu kila," yyi dariya ya kamo hannunta suka karasa cikn falon ya gaida Hajiya dake ta murmushi tace "sannu da xuwa jaheed ya hanya," yace "lfya lau wllh mum, ashe abun da ya faru knn?" Hajiya tayi kwafa tace "ka bari kawae," yace "to mum tun farkon faruwan abun meyasa baki kirani ba ai ina Nigeria," Hajiyar ta tabe baki tace "to dan iskan ya sanar min kana Nigeria ne jaheed, ae ni Haydar da ba dan wani abu ba da sae nace musanya aka min a asibiti" Mujaheed yyi dariya yace "to ynxu ya ake ciki mum, amma lawyern da kika dauka bae iya aikinsa ba ina ga dae ko, ya xa ayi ya bari a kai sa har prison, haba don Allah," Hajiya ta bude baki tace "in ji wa yace maka bai iya aikin ba, shi umar din ne bae iya aiki ba, tab, ae wnda yake karewan ne babban dan iska kuma shi ya kai kanshi kurkuku" Mujaheed yace "ae Aliyu ban san irin shi ba, wae ma ina suka hadu da yarinyar tukunna Hajiya?" Hajiya tayi murmushin takaici tace "kaddara fa jaheed, rabon ayi, aiki na kawota take min a gidan nn, ashe wae soyayya Haiydar yake da tsinanniyar shegiyar bamu sani ba, wancan munafuka algungumar prettn na sane bata gaya min ba Mujaheed," Mujaheed ya juya da sauri yana kallon pretty, ta dan yi tsaki ta mike tsaye ta haye sama Mujaheed na kiranta ko waigowa bata yi ba, Hajiya tace "tsayawa xata yi aka ce maka" Mujaheed yace "ikon Allah da 'yar aiki kuma haydar ya buge da soyayya anya kuwa yana da hankali mum?" Hajya tace "ka bari kawae ashe ma har gidansu yana xuwa ban sani ba, dama su sumy na ce min suna xargin soyayya yake da ita sbda irin reactions dinsa a kanta, kiri kiri fa sae ya hanata mana girki muna ji muna gani wae ae mu ma mata ne," Mujaheed ya dinga dariya har da buga kafa, Hajiya ta girgixa kai tayi murmushin takaici tace "ka bari kawae Jaheed ae Haydar ya cuce ni a rayuwa," Mujaheed yace "to yanxu wa kuke tunanin ya dauke 'yar aikin, to wae ma ya gani jikin mere mai aiki yake so idan ba wautan Haydar ba" Hajiya tace "ka bari kawae Mujaheed, yau da xan ga tsinanniyar 'yar nn wllh wllh bbu abinda xae sa baxan kashe shegiya ba ko kuma na sa a kasheta, kai ba ita ba har wni nata xan iya kashewa wllh ace sbda ita dana da na haifa na galallawa a gidan yari, kuma ynxn ma bae baci ba don nasa ana ta min bincike har a gano ta, kaji fa kullum maganrsa idn naje gunsa baya wuce na hankalinsa ya kasa kwanciya don bae san halin da take ba ynxu, kaji tsiya jaheed" Mujaheed yace "anya ma ba asiri suka masa ba," Hajiya tace "wllh naje ance bbu abinda aka masa, tsabar iskanci ne da wlknci irin na Aliyu," Mujaheed yace "to ita yarinyar kyau gareta ne Hajiya," Hajiya ta hade rae tace "ni ka rabu dani idan baxa ka min tambayar arxiki ba Mujaheed, kyan banxa, uban me ake da kyan talaka matsiyaci," Mujaheed yyi dariya yace "Allah ya baki hkuri, ynxu wa kuke tunanin ya dauke yarinyar ko kuwa da gsken sharri aka masa," Hajiya ta tabe baki tace "oho dae ko sace ta aka yi da gsken ko ma karya ce ba ruwana ni dae dana ya fito," Mujaheed ya gyada kai yace "shknn mum, gobe xan je gunsa na samu wasu informations din kuma," Hajiya tace "ahaf Allah ya sa ya baka hadin kai tunda yace shi dabba ne," Mujaheed yace "ae ki bar ni da shi kawae mu, don uwarsa kar ya bani hadin kan," hajiya tace "to, amma ka bari jibi don ba lallai bne a bar ka ka gansa gobe, tunda jiya mun je kar kayi wahalan bnxa ga dankaran nisa gun," Mujaheed yace "sun ci ubansu, don me baxa a bar ni na gansa ba," Hajiya tace "a'a ni fa taurin kanku ke hada ni da ku, nace ka bari jibi," Mujaheed yace "to yyi ni xan koma mum," tace "lah ko ruwa baka sha ba bari sumy ta hado maka dinner ko baxa ka ci ba ka tafi dashi," yace "A'a nagode mum, sae wani lkcn dae, su sun fi karfin su sauko su gaida mutane 'yan rainin wayo ko," Hajiya ta mike da sauri tace "aa bafa su san ka xo ba Mujaheed, meenah ma bata nn," ya tabe baki yy kofar fita sae ga meenah ta shigo cikin matsatsun kaya da dogon heel, tana ganinsa ta gyara gashin dokin kanta ta bi ta gefensa xata wuce ya fixgota "don uwarki daga ina kike ynxu?" ta galla masa harara tace "kaji min mutum aikena kayi ne?" ya xabga mata mari yace ni kike gaya ma hka don ubanki, hajiya ta karaso a fusace tace "kaga mujaheed fitar min a gida tun kan raina ya bace wnn wace irin jaraba ce xaka marar min 'ya daga xuwanka," ta fixge hannunsa daga rikon da yyi ma meenar dake ta rusa ihu tace "Allah ya kiyaye," ta ja 'yarta suka haye sama tana ci gaba da masifa. Yyi tsakin taka[truncated by WhatsApp] [12/8, 21:11] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 65.... Washegari Aneesah ta tashi da asuba ta shiga bathroom tayi alwala ta fito tayi sallah, snn ta fara gyara daki duk da ba abinda ya samu dakin don ko ina fes, a xuciyarta tace "ko wancan mutumin ya dawo jiya, don bata ji shigowarsa ba da wuri tayi bacci, tana gamawa ta shiga wanka ta ga sabon toothbrush ta dauka ta wanke bakinta snn tayi wankan ta fito, bata yi karambanin taba kayan shafe shafe da turarruka da kayan kwalliyan dake cike gaban madubi ba, ta dae sane jikinta da dankwalin kayan da ta sa don ko towel ma bata taba ba, snn ta dauki wata jallabiya baka da ta gani linke a dakin a gefen gado ta xura, ta dauki Hijab ta saka. Har gari ya washe bata yi gigin bude kofar dakin ba, tayi jigum tana tunanin duniya aka kwankwasa kofar dakin, tayi shiru tana kallon kofar, yyi sallama da muryarsa mai sanyi nn ma bata amsa ba, sunanta ya shiga kira a hankali, ta mike tsaye ta isa bakin kofar ta jingina tace "ya akayi?" taji yace "to fa, Allah ya baki hkuri sallah dama nake son sanin ko kin yi," tace "dama da safe ake sallhn?" yyi 'yar dariya yace "nasani ko a kauye hka ake yi," tayi murmushi mara sauti tace "to ka kyauta ma kanka," yace "baxa ki bude kofar ba kanwata," tace "in maka me?" ya dan yi shiru snn yace "breakfst xaki hada mana," tayi shiru snn tace "to ka tafi xan fito," yace "ok kanwata tnx," bayan kmr minti biyar ta bude kofar a hankali don a tunaninta ya tafi, tana bude kofa suka yi ido hudu da shi yana jingine jikin bango sanye da jallabiya baka, yyi murmushi ya kashe mata ido a rude don bata yi xaton yana nn har lkcn ba ta juya da sauri xata shige dakin ashe ta jawo kofar ta buge da kofan ta fasa ihu "wayyo kai na" ya rikota da sauri ta xube jikinsa suka durkushe wajen gaba daya yace "subhanallahi srry kanwata, kin buge ssae koh," bata ce masa komai ba ta fashe da kuka tana rike da goshin nata, yace "ohh don Allah kiyi hkuri kanwata, xafi yake maki ne" nn ma bata tanka masa ba sae kukan da take, duk ya rude ya shiga hura mata goshin ta turasa a fusace tace "da'alla ka tashi gabana ni," ya rungumota yace "A'a sae goshin ya daina maki xafi," ta tsorata ta fara turasa don ta mike tsaye ya ki sakinta, hkn yasa ta sake fashewa da kuka, ya dago kanta yace "ni fa bana son kuka kanwata," ya fara kkrin cire mata hijab din jikinta ta buge masa hannu bae damu da haka ba, ya cire hijabin ya dagota suka ta shi tsaye yace "haba sae kace matan malam," kinga yanda rigar ta maki kyau kuwa, bae jira cewarta ba ya ja ta suka sauka xuwa kitchen snn ya fara nuna mata kayan girkin yace kinga duk jiya da nyt na siyosu kafin na shigo gida, na dawo naga kin bingire kina bacci daga ke sae inner cloth da xani, xanin ma ya kwanta shi daya gefenki abinsa, ni ban san me yasa wasu matan basu iya kwanciya da xani ba, gashin ki ma yyi relaxin abinsa baki takurasa ba amma me yasa baki sa net din bby ba, kinga ni bana cin plantain kar ki soya da yawa, snn ki dan mana farfesu kadan kuma karki dafa ruwan lipton sae dae idan kece ke so don ni coffee xan sha, duk wnn surutun da yake yana yi ne yana ciro kayan da xata girka, jin shirun yyi yawa ne ya sa ya juyo yana kallon Aneesah da mamaki ya gama cikata tana kallonsa kmr xata fashe da kuka yace "hope ba wahalar da ke xan yi ba kanwata," ta kasa cewa komai sae mamakin yanda aka yi ya san yanda ta kwanta jiya take, da dan damuwa bayyane a fuskarsa yace "me ya faru kanwata, goshin ne har ynxu" ta hade rae kmr xata yi kuka don takaici tace "jiya ina bacci ka shigo min daki koh?" ya xaro ido da mamaki yace "ni? Wa yace maki na shiga ba kinsa key ba kanwata, ta ina xan shiga?" ta girgixa kai hawaye har ya fara taruwa idonta tace "wllh ka shiga, ga shi nn ka gama gaya min komai," ya wara ido don shi bae san ma ya fada ba yace "me ma nace kanwata?" ya fara kkrin tuna surutan da ya gama yi, ta juya a fusace xata bar kitchen din ya rikota da sauri yace "am srry kanwata, i just want 2 make sure u re comfortable snn baki bar A.c a kunne ba don kar kiyi mura kinga akwae sanyi ynxu, amma xan baki spare key din ki hada duka." ta hararesa tace "bad habit knn," ya kauda kai yana dan murmushi yace "srry, ynxu dae ga ki ga kayan girki ni xan je nayi wanka don akwae inda xa mu yau," ta galla masa harara tace "sae ka xo ka ja ni mu tafi," yyi dariya yace "xaki gani kuwa," har ta gama hada breakfst bae sakko ba, hkn yasa ta haye sama kawae ta shiga daki, tana shiga wayar da bata san ynda aka yi ya shigo dakin ba na katsewa, ta dauki wayar tana kallon screen, aka sake bugowa pretty ta gani gaban screen, hkn ya tuna mata da ya Haydar ta juya a sanyaye jiki ba kwari ta bar dakin xata kai masa wayar, a hankali ta tura kofar dakinsa ta shiga, duk hankalinta ba ya tare da ita tuno Haydar da tayi, yana tsaye gaban madubi sanye da singlet da gajeran wando yana combn din kansa. Bata san lkcn da ta fasa wani ihun da ya raxanasa ba don a tunanin[truncated by WhatsApp] [12/8, 21:11] ‪+234 803 751 8717‬: Khaleesat Haiydar ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 66..... Tun kan Mujaheed ya karaso inda take ta sake masa wayar ta juya da sauri ta bar dakin, ya bita da kallon mamaki, can dae ya girgixa kai yyi tsaki ya dauki wayar yana kallon screen din da ya tsage a dalilin faduwar da yyi, ya daga kiran yace "xan kira ki pretty," ya ajiye wayar ya ci gaba da shirinsa. Yana gama wa ya dauki makullin motarsa ya fita, ya kullo kofar falon snn yyi hanyar garage ya dauki motar da xae dauka, mai gadi ya bude masa gate ya fice daga gidan. Sae bayan fitarsa da minti goma snn Aneesah ta sauko falon a sanyaye ganin ta bata masa rai tunda bbu abinda ya taba a dinnin table din, kukan da bata san dalilinsa ba ta shiga yi durkushe a falon, tayi mai isarta ta mike ta haye sama ta shiga daki ta fara sabon kukan, daga hka bacci ya dauketa ba ita ta farka ba sae kusan Azahar, tana xaune bakin gado har lkcn sllhn yyi snn ta mike ta shiga bathroom ta dauro alwala ta fito tayi sllh, yunwa ya isheta don bata yi break ba har lkcn amma bata damu da hkn ba, abin duniya ya fi isanta akan yunwan, to meye amfanin xamanta a gidan Mujaheed tunda gashi haushinta ma yake ji ynxu, ta goge hawayen da ya silalo mata ta mike daga kan dardumar jiki ba kwari, ta linke shi ta ajiye inda yake snn ta bude kofar dakin ta fita, ita kam bata ga amfanin fitowarta daga kauye ba indae hka ne, da kawae can aka barta ta karashe rayuwarta tunda ba Amminta, tunanin hkn yasa ta fashe da kuka, ta sauko falo tana goge hawayen fuskarta ta fice daga falon tayi hanyar gate gwara ta koma gun baffanta ya mayar da ita kauyen kawae, tana isa bakin gate ta tarda mai gadi xaune da dan radionsa a hannu, ganin babba ne ya sa ta dan risina ta gaishesa ya amsa yana dan murmushi ganin yanda ta girmama shi, tace "xan fita ne baba," yace "ke ko ina xaki yar nn," ba tare da ta kallesa ba tace "xan siyo abu ne," ya girgixa kai yace "yallabae yace kar a bari ki fita," amma xaki iya bada kudin ki fadi me xa'a siyo maki na kira driver ya je ya siyo maki ynxun nn," ta girgixa kai tana kkrin boye hawayen idonta tace "ka bar shi kawae baba," ta juya da sauri ta koma cikin gidan ta fashe da kukan takaici, to meye nufin Mujaheed xae ajiyeta gidansa kmr matarsa yyi ta harkokin gabansa, ita kam tayi da ta sanin biyosa da tayi, kuka kam tayi shi har ta gode Allah, ta mike ganin la'asar yyi ta hau sama tayi alwala tayi sllh, kan darduman bacci ya kuma dauketa. Karfe bakwae da rabi Mujaheed ya shigo gidan, tana jinsa ya hayo sama ya shiga dakinsa, bata sake jin motsinsa ba sae after eight da ta ji ya bude dakinsa ya fito ya sauka kasa, tana kan darduma ta i [1:00PM, 12/23/2016] Khaleesat: [12/8, 21:12] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 90.... A Eatry Mujaheed ya hadu da Abdul kmr yanda suka shirya, suna gama gaisawa Abdul yace "nayi ta jiran call dinka shiru, kuma naje can gidan sau dayawa bana samunka," Mujaheed yace "eh ina kano" Abdul yace "ok, ina kanwartaka," Mujaheed ya shashantar da batun yace "ya kuma aka ji da abinda ya faru da dad dinka" da mamaki Abdul yace "A ina kasan dad dina?" Mujaheed yace "A haba dae wanene bae san Honourable Shehu ba a nn Abuja," Abdul ya daga kafadarsa yace "wnn kuma shi ya siyan ma kansa," da mamaki Mujaheed yace "don me xaka ce hka Abdul, ba dad dinka bne," Abdul bae ce komai ba ya daga wayarsa dake ringing, Mujaheed ya tsura masa ido yana dan murmushi jin irin turancin da yake, har ya gama wayar snn yace "A abroad kke knn?" Abdul ya gyada masa kai ba tare da ya kallesa ba, Mujaheed ya jinjina kai yace "wae me dad naka yyi hka ne? An sake sa kuwa? " Abdul yace "A'a ban sani ba, kuma dukiyar da ba tasa ba ke hannunsa," Mujaheed ya girgixa kai fuskarsa dauke da damuwa kmr gaske yace "dukiyarsu waye?" "na kaninsa ne," Abdul ya fadi yana maida wayarsa cikin Aljihu, yanda Abdul ke ba sa amsan ya nuna masa baya son xancen, Mujaheed yace "ayya, kuma ina kanin nasa," Abdul ya gyara xama lkci daya ya dauki lemon gabansa yana sha yace "he'z late," "to iyalensa fa?" Mujaheed ya sake jefo masa wani tambayar, Abdul yyi masa wani irin kallo yace "am i here 2 answer yhur unnecessary questns?" Mujaheed ya dan saita murya yace "ba hka bane abokina, i just want 2 knw ba dae kanwata kke son gani ba, xan kai ka wajenta yau," Abdul yace "iyalensa suna nn mana," Mujaheed yace "nn garin?" Abdul ya dan yi shiru snn da damuwa yace "ban san inda cousin din tawa take ba, hka ma mum dinta ban san inda dad dina ya kai ta ba," Mujaheed ya tsura masa ido yana kallonsa sae a nn ya lura da kaman da suke yi da Aneesah ssae kuma, don Abdul kyakkyawa ne na karshe, idonsa exactly na Aneesah, Mujaheed ya kauda kansa yace "kasan me nake so da kai Dr," Abdul yana kallonsa yace "am ol ears," mujaheed ya fara magana murya can kasa yace "Abdul, idan ka bani hadin kai wllh xan nemo maka cousin din taka, i just want yhu 2 help me, ni kuma nayi maka alkawarin xan fito maka da 'yar uwarka don nasan inda take," da sauri Abdul yace "me kke bukata daga gare ni?" Mujaheed ya dan yi cylnt snn yace "ka samo min information din inda dad dinka ya kai mata mahaifiyarta, snn na san baxa ka rasa sanin inda document din dukiyarsu da komai yake ba, don hka nake son ranar da xan nuna maka ita ka taho da su ka damka mata a hannunta," Abdul yyi masa mugun kallo yace "kai din wa xaka sa ni nayi hkn?" Mujaheed ya daga kafada ya mike tsaye yace "ok, i wil b on my way," Abdul yace "wait, ka gaya min meye hadinka da su?" ya koma ya xauna yana kallon Abdul da kyau yace "Aneesah da kke nema tana gu na, amma baxa ka ganta ba har sae ka san inda Amminta take ka gaya min," Abdul ya mike tsaye da sauri yace "ok wnn ba matsala bane, amma yaushe xan ganta?" Mujaheed yace "as soon as Amminta ta bayyana," Abdul yyi shiru kmr mai naxari snn yace "ok nn da kwana uku xaka ji ni," Mujaheed ya mike tsaye yace "to ngd i wil b on my way," Abdul yace "wait, ka gaya min kai waye don Allah," Mujaheed yace "sunana Mujaheed Muhd," a tare suka fita daga eatry din suka yi sallama da juna a kan sae nn da kwana biyu xasu hadu. Aneesah na xaune a garden ita da ummi, sanye suke cikin riga da skirt gaba daya, ranar dae ummi ta tilasta Aneesah ta dan yi light make up tayi kyau ssae har ba a magana, suna game a laptop wayar ummi yyi kara, Aneesah ta daga ganin mummy ce ke kiran, tace "mumy har kin shirya," mumyn tace "Aneesah ce?" Aneesah tace "eh nice mumy," Hajiyar tace "maxa ki shigo gida ana nemanki," Aneesah tace "to gani nn xuwa mumy," ta mike tana kallon ummi tace "ummi xo ki rakani wae ana nemana kila yayana ne," ummi tace "je ki ina xuwa don baxan tashi ba sae na gama abinda nake," Aneesah bata sake saurarata ba ta shiga falo da sallamarta, xaune ta gansa yana danna wayarsa, gabanta yyi mugun faduwa don a tunaninta Mujaheed ne ya xo, ta karaso falon a sanyaye jiki ba kwari, ta dan xauna kan kujera tana kallonsa tace "ina yini," ba tare da ya dago kai ba yace "lfya lau," ta sunkuyar da kanta bata sake cewa kmai ba shi ma hka, can ta dago a hnkli tana kallnsa taga kallnta yke, suna hada ido ya sauke idonsa da sauri itama hka, a hkn Hajiya ta sauko ta samesu tace "lah ke dae Aneesah shirmammiya ce wllh, ko ruwa baki kawo masa ba ashe," Aneesar ta mike tsaye tana murmushi, hajiyar ta koma sama, ita ko tayi hanyar fridge ta dauko lemo da ruwa ta daura kan faranti da cup ta shigo falon ta durkusa gabansa ta ajiye masa, har xata mike sae ta fasa ta bude lemon ta xuba masa a cup ta daga tana mika masa a sanyaye tace "gashi ya Hydar," ya tsura mata ido bae ce komai ba, hkn yasa xata ajiye kofin, ya mika mata hannu ta dago dara daran idonta tana kallonsa ta mika masa lemon, hmm tarihi ya maimaita kansa, don kasa rike cup din yyi, ya [truncated by WhatsApp] [12/8, 21:12] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 93... Mujaheed na komawa gida Hajiyrsa ta dinga tambayarsa mai ya faru ganin ynda ya shigo gidan, bae ce mata kmai ba ya haura sama ya shiga bedroom dinsa, ta juya tana kallon kanwarsa Amira tace "ina yace maki xae je Amira," yarinyar tace "bae gaya min ba," Hajiyar ta mike ta bisa dakin nasa, yana xaune yana shan lemon kwali, ta xauna kan kujera tana kallnsa tace "ya akayi prince wa ya bata maka rae hka?" ya girgixa mata kai yace "no one, just tired," ta ce "to ka kwanta ka huta," ya gyada mata kai ta fice daga dakin ya fada kan gado, ynxu Aneesah kawae yake son gani amma Hajiyarsa ta hanasa, shi kuma gashi baya tsallake umarninta don tun ranar da ya kai Aneesah gidansu Mudatheer bae sake komawa ba. Bayan kwana biyu Mujaheed ya hadu da Abdul kmr ynda suka shirya, bayan sun gaisa Mujaheed yace "ya dae, ka gano min inda take," Abdul yace "na dan wahala kafin mum dina ta gaya min, tace tana katsina" Mujaheed yace "katsina kuma, me take yi a can," Abdul ya dan yatsine fuska yace "kmr ko aiki take yi ko menene ni bn gane xancen nata ba ma, amma gidan mai kudine ssae abokin dad din nawa ne, kuma gidan da tsaro dayawa, matansa uku, kila aiki take masu a gidan" Mujaheed ya gyada kai yace "gud, to ynxu ya xa ayi ka fito da ita indae har kana son gnin Aneesah," Abdul ya dan yi shiru snn yace "sae naje katsina knn," Mujaheed yace "to shknn, kmr yaushe xaka tafi knn?" Abdul yace "ko xuwa gobe," Mujaheed yyi shiru yana dan naxari snn yace "to mu tafi tare mana," Abdul yace "idan hkn yyi suit dinka," Mujaheed yace "shknn ngd ssae gobe as early as 7a.m ka taho gida ka sameni, sae mu tafi da motata" Abdul yace "ok," Mujaheed ya basa hannu suka yi shake din juna snn suka fita daga Eatry din. Hajiya duk ta rude ta shiga damuwa ganin ynda Aliyu ya rame, yau kam tun safe bae ko kalli break din da ta hada masa ba har gashi kusan karfe 1, alhalin abincin jiya ma da daddare bae ci ba coffee kadae ya sha, ta xauna gefen gadon da damuwa tana kallonsa tace "haba Aliyu ka ki gaya min meye matsalarka, don Allah ka tausayamin ka gaya min me ke damunka hka, duba fa yanda ka koma," ya mike xaune yana kallonta yace "ni nace maki bbu abinda yake damuna mum," ta girgixa kai tace "ban yrda ba Aliyu, a hkan xaka ce min bbu abinda ke damunka," ya dan kirkiro murmushi yace "kawae dae bana dan jin ddi ne kwanan nn," tace "to ka tashi mu tafi asibiti ko kuma na kira maka Dr umar," yace "aa ki bari kawae mum am feelin much beta ynxu," bata ce masa komai ba ta fita daga dakin, bayan kmr minti talatin sae ga Dr umar din ya xo, da yake babba ne Hydar bae masa musu ba ya bari ya dubasa don abokin late father dinsa ne, har ya gama gwaje gwajensa bae ce ma Hydar komai ba ya fita yaje ya samu mahaifiyar tasa a kasa, tace "me ke damunsa doctor malaria ko typhoid?" likitan ya mata wani irin kallo yace "wani malaria? Kina nn xaune jinin danki ya hau har hka, haba Hajiya me ke damun Aliyu hka? Don ma yaron mai karfin hali ne, Meye matsalarsa a rayuwa?" Hajiya ta saki salati ta fashe da kuka tace "wllh doctor ban sani ba, duk kwanan nn ynda ka gansa hka yake ko abinci baya ci, shi kadae gareni doctor ban san me yasa a ransa hka ba yake damunsa, ka tambayar min shi don Allah ko xae gaya maka doctor" likitan ya shiga kwantar mata da hankali yace kar ta damu xae shawo kan koma, snn xae tuntubesa ya ji meye matsalarsa, dole Hydar ya yrda ya bi likitan gidansa don yace xae fi maida hankali a kansa a can. Karfe bakwae Mujaheed da Abdul suka yi set off xuwa katsina, bayan Mujaheed ya xuka ma Hajiyarsa karya cewar xae je kaduna kan wani case, tayi masa Allah ya kiyaye, Hka suka dinga tafiya ba ji ba gani, idan wnn ya gaji ya ba ma wnn tukin, Abdul ya juya yana kallon Mujaheed dake tuki yace "idan ka samu dan restaurant ka tsaya yunwa nake ji," Mujaheed yace "ok," hka aka yi yana samun wani dan eatry yyi parkin suka shiga, Mujaheed yace "me xaka ci?" Abdul yace "nothin much," ya karasa wajen waiter din ya fadi wine din da xa a basa aka mika masa kuwa, Mujaheed ya bude baki yana kallonsa yace "wnn kuma fa Abdul?" Abdul yace "shi kadae xan siya," Mujaheed yace "alcoholic drink knn fa," Abdul ya juya xae fita daga eatry din yace "ka siya abinda xaka siya ka fito mu wuce," can malt biyu kawae mujaheed ya karba snn ya biya kudin ya fito yana kalle kallen inda xae ga Abdul can ya gansa tsaye kusa da wani me kiosk, ya siya kwalin taba har ya kunna daya yana xuka, Mujaheed ya girgixa kai yace "ya salam," Abdul na hangosa ya karaso yana kallonsa yace "har ka gama," Mujaheed yace "mu tafi amma karka shigo min mota da cigarette dinnan don bana son warin," Abdul yace "ok, ya jefarda guntun na hannunsa, ya saka kwalin cikin aljihu yana rike da kwalban wine dinsa ya shiga mota, Mujaheed ma ya shiga ya tada motar suka bar wajen, dk da Mujaheed yy niyyar masa magana a kan abinda ya gani don ya lura free man ne shi bbu ruwansa rayuwarsa irin ta turawa yake yinsa, sae kuma ya fasa gnin har ya fara bacci. karfe uku suka shigo katsina. Like · Reply · Report · 3 minutes a[truncated by WhatsApp] [12/8, 21:12] ‪+234 803 751 8717‬: Khaleesat Haiydar ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 92..... Mujaheed ya karaso cikin dakin yana kallon pretty yace "ke wae yaushe kika fitsare ne hka Zainab," pretty ta juya tana shirin fita daga dakin tace "ba ca nayi maka ina xuwa ba," ta fice ba tare da ta jira mai xae ce ba, don wani mugun haushinsa take ji ynxu, Mujaheed ya kalle Hydar da ya lumshe idonsa ya karaso gefen gadon ya xauna yana kallonsa yace "ya dae frnd ina ta kiranka baka daga wayar ba," Hydar yyi masa shiru har lkcn idonsa a lumshe, Mujaheed yace "wae bacci kke ne ina magana kayi shiru," Hydar ya bude ido a hankali yana kallonsa yace "ina jinka, banga call din ka ba" Mujaheed ya mike ya dauko wayar yana kallo yace "ba gashi nn ba, har 3 missed cals" Hydar yace "to ban sani ba," Mujaheed ya ajiye wayar yana kallonsa yace "wae ya na ganka wani iri ne Aliyu, ko baka da lafiya ne?" ba tare da Hydar ya kallesa ba yace "lfyata lau," Mujaheed ya tabe baki yace "to Allah ya kyauta, kana ji na magana na xo muyi?" Hydar yace "ina jinka," Mujaheed yace "ae kasan son din Baffan Aneesah, Abdul?" Hydar yyi shiru bae ce komai ba, Mujaheed yace "am tokn fa Aliyu, wae don Allah me ke damunka ne" Hydar yace "ina jinka me aka yi?" Mujaheed ya daga kafada alamar shi ya sani snn yace "kasan sa?" Hydar yace "ehh," Mujaheed yace "gud, mistakenly akwae randa muka hadu dashi a hanya da Aneesah, but funnily bae ganeta ba, tun daga lkcn yake bibiyanmu yana nuna min kmr ya santa, ni ko na nuna masa xan basa mamaki idan ya sake binmu, as in d guy was vry confuse, har dae daga karshe ganin yanda ya damu yasa n karbi card dinsa nace xan kirasa duk don ya rabu damu, so just recently i thought he myt b of help 2 us nd guess wat i was absolutly ryt cos nn da kwana uku yace xae gano min inda Ammin Aneesah take, is'nt dat great, though na dan masa tambayoyi na samu informations kadan, nd kasan wani abu frnd, wllh bae gane ita ce Aneesah ba still, ina ga kmr gayen na da brain disorder, amma dae don ya maida hankali gun sanin inda Ammi take nace masa ita ce Aneesar da yake nema, amma baxae ganta ba har sae ya nemo Ammi" Mujaheed yyi shiru yana kallon Hydar ganin shi daya yake ta surutunsa, don Hydar idonsa a lumshe yake kmr mae bacci, a fusace Mujaheed yace "Hey wnn wani irin wlknci ne kke min hka Aliyu, ina magana ka mai da ni kmr wani mahaukaci kayi bnxa da ni," Hydar ya mike a fusace yace "to me kke son na ce maka ko kuma me xan yi maku, meye nawa kuma a ciki, plss don Allah ka rabu dani i beg yhu stay away frm me huh!" Mujaheed ya tsaya da mugun mamaki yana kallon Hydar da ya koma ya kwanta, yace "oohh wnders shall neva cease! don an bata maka rae a gida sae ka huce kai na kuma malam, ae ba ni na bata maka ran ba don hka sae ka sauka ka same su downstairs," a fusace Mujaheed yyi maganar, Hydar ya mike shima a fusacen ya shakesa yana huci yace "kai!!" hka Mujaheed ya bude baki yana kallonsa, Hydar yace "ka kama kanka kar ya bace mana a dakin nn," Mujaheed yyi murmushi ya cire hannun Hydar a wuyarsa ya mike tsaye yana kallon Hydar din yace "ka ci sa'a ni naxo na same ka amma da baxae mana kyau ba daga ni har kai yau," yana kai wa nn ya fice daga dakin, Hydar ya koma ya xauna kan gado ya dafe kansa yana mayar da numfashi, Aneesah ta cucesa ta cucesa, yyi daya sanin saninta, ya fada kan gado ya shige cikin blanket jin wani irin sanyi dake shigarsa. Like · 9 · Reply · Report · 1 hour ago Hauwee Jidderh Abdulkadir tnx [12/8, 21:12] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 94.... Mujaheed ya juya yana kallon Abdul dake danna wayarsa yace "to ina muka nufa yallabai, gamu nn a cikin katsina," ba tare da Abdul ya kallesa ba yace "tun daxu nake ce wa ka bani drivin kayi ignorin dina, ynxu in ka san wajen ae sae ka kai mu naga," Mujaheed yace "hka kawae kan idona ka gama kwankwade wine kwalba daya na baka drivin ka wurga mu cikin daji, haba ae wnn ganganci ne baxa mu ce tsautsayi ba" Abdul ya juya yana kallonsa bae dae ce komai ba, Mujaheed yyi parkin yace "nasan ynxu ka dawo nml, xo ka karbi tukin," Abdul bae yi musu ba ya fito suka yi exchangin sit," Mujaheed yace "daga nn ina xa mu knn?" Abdul yace "masallaci, ba muyi azahar ba ga la'asar ya kusa," Mujaheed ya fashe da dariya ssae har da rike kansa, Abdul ya juya yana kallonsa yace "wat's funny?" sae da Mujaheed yyi dariyar mae isarsa snn yace "to mu je," Abdul ya ja tsaki ya ja motar, suka samu wani masallaci yyi parkin, Mujaheed na alwala yana kallon Abdul dake tasa alwalan, so yake yaga ko ya iya alwalan ma kuwa, Abdul ya gama alwalan ya mike a fusace yace "wae wnn kallon fa Jaheed?" Mujaheed yyi murmushi ya mike don shi ma ya gama alwalan yace "sorry" suka shiga masallacin a tare, sae da suka idar da sllh snn Mujaheed yana kallon Abdul yace "srry fa Abdul in tambayeka," Abdul yace "am ol ears," Mujaheed yace "naga kmr kayi karatun addini ssai ko," Abdul yyi masa wani mugun kallo yace "wace irin silly questn knn kke min?" Mujaheed yace "A'a yi hkuri," har Mujaheed ya fidda ran Abdul xae sake magana ya ji yace "eh nayi, don tun ina 12 yrs na sauke qur'ani mai girma, at 14 na sauke littattafae da dama," Mujaheed ya tsura masa ido yana kallonsa xae yi magana Abdul ya rigasa yace "though ban taso gidanmu ba, gun kakana da ya haifi dad dina na taso, at 15 yrs na koma gun parent dina, kafin grand dad din nawa ya rasu knn, though nasan da gidanmu na taso ko karatun sllh ma ba iyawa xan yi ba" Abdul ya mike yana kallon Mujaheed da ya kasa daina kallonsa yace "let move, lkci na wuce wa," da yake Mujaheed na son magana da Abdul din sae ya fake da cewa, "ka bari mana muyi la'asar kawae, kaga lkci ya kusa," Abdul bae yi musu ba ya koma ya xauna, Mujaheed yace "to kana da ilimin addini hka, mai ya kai ka shan giya Abdul, nasan ka fini sanin hukuncin me yin hkn" Abdul yyi masa mugun kallo snn ya tabe baki bae ce komai ba, Mujaheed yace "hmm kayi shiru," Abdul ya dan kishingida yace "bari na dan yi bacci kafin lkcn sllhn yyi, am so exhausted," Mujaheed yyi murmushi yace "to ita Aneesar son ta kke ko me?" da sauri ya gyara xaman sa yace "Aneesah, ehh ina sonta, though ba don ina sonta nake son na aure ta ba, tun tana karamarta take min fitsara, bata da kunya ko kadan yarinyar, though ni kadae naga take ma rashin kunyar, don hka nake son na aureta ne don na dan nuna mata hankali, bayan nn kuma xamuyi soyayyar mu, don ina sonta ssae, kuma kalarta kalar xama a london ne" Mujaheed ya hade rae bae ce komai ba, Abdul yace "kuma bayan hka, na so idan na aureta na dawo masu da farin cikinsu da dad dina ya tauye masu, amma sae ta haifa min kyakkyawar dota kmr ta," Mujaheed ya mike yace "kaga mu tafi kawae ma yi sllhn a wani waje idan lkcn yyi," Abdul ya mike yace "ok," snn suka fita suka shiga motar Abdul ya ja motar suka shiga cikin gari. Karfe biyar suka isa gidan, gida ne mai girman gske, mai gadi yace baxa su samu shiga ba don mai gidan baya nn, sae dae idan suna da nmbr daya daga matansa, su kirasu, in sun yrda su shigo, sae su shiga, don baki basa shiga gidansa hka nn" Abdul yyi tsaki don shi bai ma san matan Alhajin ba, Mujaheed yace "kai baka da nmbr mai gidan ne, ka kirasa," Abdul yace "bani da," Mujaheed yyi tsaki yana kallon mai gadin yace "kmr yaushe mai gidan xae dawo," Mai gadin yace "xuwa gobe ko jibi," Mujaheed ya juya yana kallon Abdul yace "sae mu je mu kama hotel," Abdul yace "ok," suka shiga mota suka bar anguwar. Washegari da yamma Hydar ya koma gida daga gidan Dr umar, ba laifi ya dan ji sauki amma ba na abinda yake damunsa a xuciyarsa ba, Hajiya sae nn nan take da shi kmr ta mai da shi ciki, ta dinga rokansa tana lallabasa ya gaya mata meye matsalarsa a rayuwa, tayi alkawarin ko ma me yake so xata masa, shi dae ido kawae ya xuba mata yana kallonta. Like · 4 · [truncated by WhatsApp] [12/8, 21:12] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 95..... Washe gari da safe misalin karfe goma Mujaheed da Abdul suka kama hanyar gidan Alhaji suleman ko Allah ya sa ya dawo, mai gadi yace bae dawo ba stil sae gobe, a fusace Abdul yace "kai malam da'alla bude ma mutane gate su shiga, nn gidan aminin dad dina ne, so dnt tel me dat," Mujaheed ya dafa kafadarsa yace "dnt wrry guy, Allah ya kai mu goben," Abdul yyi tsaki yyi gurin mota, mujaheed na biye da shi a baya, suna komawa Hotel din da suka yi lodge, Mujaheed ya shiga bathroom yin wanka, Abdul ya sauka downstairs xuwa dan eatry din dake Hotel din ya siya wine da hamburger sae malt biyu da table water, ya koma sama, ya tar da Mujaheed ya fito daga wankan yana xaune kan gado yana danna wayarsa, Abdul ya ajiye masa malt da hamburger, ya xauna kan kujera ya bude wine dinsa ya fara kwankwada, Mujaheed ya kasa daina kallonsa, sae da ya ajiye kwalban snn Mujaheed yace "kai ni fa bna son kana shan wnn abun a gabana," ba tare da Abdul ya kallesa ba yace "ok," snn ya mike tsaye yana kallon Mujaheed yace "let get a nearest boutique mu siya kaya, coz baxan iya maida kayan nn ba, its irritatin me " Mujaheed yace "kaje ka siya ni ina da kayana a mota," Abdul yace "dnt wrry about d expense i wil take care of dat," Mujaheed yyi masa mugun kallo yace "nayi maka kama da talaka," Abdul yyi dariyarsa mai kyau yana nuna Mujaheed da yatsa, ya juya ya fice daga dakin, dariyarsa exactly irin na Aneesah, Mujaheed ya bi sa da kallo don bae taba ganin dariyarsa ba sae ranar, yyi murmushi tuno Aneesar sa da yyi, lallai jini ba wasa bane, hka kawae ya ji Abdul na burgesa, in har hka ne to bae yo halin ubansa ba. Ko da Abdul ya dawo Mujaheed na kwance yana kallo, ya ajiye masa dayar ledan hannunsa don biyu ya shigo da, Mujaheed ya mike xaune yace "wnn fa," Abdul yace "kaya na siyo mana. Tunda kai baxa ka iya siya mana ba" Hydar na kwance Hajiya ta shigo dakin tana kallonsa tace "son baka sha tean da yawa ba," yace "ya isheni mum," ganin yanda duk ta daga hankalinta a kansa ya sa ya mike tsaye ya shiga ciro kayan da xae sa tace "ina kuma xaka Aliyu," yace "xan dan fita mum," hkn yasa ta dan ji ddi, tace "to shknn me xa a girka maka kafin ka dawo," yace "ko ma me kuka girka xan ci mum," har bakin mota ta rakosa tayi masa Allah ya kiyaye duk da mugun karfin hali yyi ya ja motar ya fita daga gidan don bae ma san inda xa shi ba. Yyi tafiya mai nisa ya samu kansa da shan kwanan gidansu Mudatheer, a hankali yyi parkin dai dai kofar gidan, ya kife kansa da steerin motar, ya kai kusan minti goma a hka snn ya fito ya shiga cikin gidan bayan sun gaisa da mai gadi, ya danna bell ummi ta bude masa kofa, tana ganinsa kuwa ta hade rae don tasan dole sae Aneesah tayi kuka yau, ta dae gaishesa ya amsa da dan fara'arsa ya shigo falon yana tambayrta mumy, sae da ta fara sanar da mumy xuwansa snn ta shiga daki ta tar da Aneesah xaune gaban madubi ta gama shirinta don fita xasuyi da Mudatheer gaba daya, tace "Aneesah ana nemanki a falo," Aneesah ta mike tsaye da sauri tace "waye?" don a tunaninta Mujaheed ne, ummi tace "wnn yayan naki ne," gaban Aneesah yyi mugun faduwa, jikinta yyi sanyi, badan wani abu ba da baxa ta je gun Hydar ba don ita tsoronsa ma take ji ynxu, ta juya tana kallon Ummi dake kallonta tace "ummi xo ki rakani," Ummi tace "A'a ni baxan je ba, ynxu gun coursemate dina xanje na karbo wani book kafin ya Mudatheer ya dawo," Aneesah bata ce mata komai ba ta fita daga dakin ta shigo falo a sanyaye ta tar da shi suna gaisawa da mumy, ta nemi gu ta xauna baki bakin kujera kamar mara gskya, sun kai minti biyar a hka snn ta gaishesa a hankali, ya dago yana kallonta bae ce komai ba, hkn ya sa ta sunkuyar da kanta, can bayan kmr wani minti biyar din ya kalleta bbu yabo bbu fallasa yace "kin duba waec result din ki?" ta dago tana kallonsa ta girgixa masa kai, alamar Aa. Like · Reply · More · 5 minutes ago [12/8, 21:12] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 96..... Hydar ya kauda kansa kmr baya son maganar yace "je dauko hijab ki gaya ma mumy xa mu je cafe ynxu" ta dan yi shiru snn tace "ya fito ne?" yyi banxa da ita har lkcn baya kallonta, ta mike tsaye kmr xata yi kuka ta tafi dakin mumy ta gaya mata, mumy tace "da sae ki gaya mana kinyi waec, ko da Mudatheer ne ba sae ku je ya duba maki ba, ke dae Aneesah akwae shirme," ta dan yi murmushi mumyn tace "to shknn amma kar ku dde kinji Aneesah," tace "to mumy" snn ta shiga daki ta cire mayafin jikinta ta saka hijab, ta dawo falon, kallo daya yyi mata ya kauda kansa ya mike yyi hanyar fita daga falon ta bi sa a baya gabanta na faduwa, a compound suka hadu da Mudatheer ya dawo, ya gaishe da Hydar da fara'arsa snn yace "xaku fita ne," Hydar yace "no, waec result xan duba mata," Mudatheer yace "maimakon ki gaya min na duba maki 'yar birni, waec ai ya dde da fitowa," Aneesah tayi murmushi bata ce masa komai ba ganin Hydar, Mudatheer yace "to gashi kuyi magana da yayanki tun daxu yake son magana da ke," Aneesah ta dan sace kallon Hydar ta karbi wayar daga hannun Mudatheer dake mika mata, yace in kun dawo na karbi wayar, yana kai wa nn ya shiga cikin gida, ta kara wayar a kunne a hankali tace yayana, yace "kanwata," ta dan yi dubara xata juya suka hada ido da Hydar dake kallonta, ta kasa juyawar da tayi niyyar yi, kuma ta kasa dauke idonta daga nasa, duk kiran da Mujaheed ya dinga yi mata kasa amsawa tayi, Hydar ya juya yyi hanyar gate ta bi sa a baya ta katse kiran Mujaheed din, yana isa kusa da motarsa ya xaga ya shiga motar ta karasa daya bangaren jikinta a sanyaye ta bude ta shiga, Allah sarki yayanta da shi ne da da kansa xae bude mata motar, har suka bar anguwar Hydar bae ce mata komai ba, Mujaheed ya dinga kiranta a waya ta kasa dagawa, daga karshe ma sae ta kashe wayar gaba daya. Suna isa cafen ta bi bayan Hydar suka shiga ciki, ita dae ta ga yanda xa ayi ya duba result dinta tunda dae bata da informations dinta a tare da ita ynxu, amma ga mamakinta, taga yyi komai bayan ya siya scratch card, snn yasa aka yi print out din result din, sae a lkcn ta lura da takardar dake hannunsa da ya taba karba da ddewa bayan sun gama exams, nmbers ne a jikin takardar da ya sa ta rubuta masa, tun daga na exam, xuwa na exam centre da sauransu. Ya bada kudi suka fita daga cafen, yana rike da result dinta, sae da suka shiga mota snn ya mika mata result din ta karba amma ta kasa budewa, shi dae bae ce mata komai ba har suka isa gida snn yace "gobe xamu je kiyi register na jamb," ta gyada masa kai yace "sae anjima," bata yi masa musu ba ta bude motar ta fita a sanyaye tace "ngd," bae ce komai ba ya ja motarsa yyi gaba. Wa shegari Mujaheed da Abdul suka samu shiga gidan Alhaji sulaiman, ya tarbe su da kyau ganin Abdul dan Honourable shehu, da Abdul ya lura da cewa Alhajin bae san abinda ya faru da dad dinsa ba yasa yace "dad ne yace ya kawo maka wata mata tana maku aiki nn da ddewa," Alhaji sulaiman yace "ehh hka ne, har ynxu tana nn gidan kuwa," Abdul ya juya yana kallon Mujaheed da ya ji ddin jin hkn yace "eh dama ca yyi mu xo mu taho da ita ne," Alhaji suleman yace "ohh har ya shawo kan komai knn ynxu?" Abdul yace "eh" ba tare da ya gane mai Alhajin yake nufi ba. Alhajin yace "to shknn amma ae ya ci ace ya kirani ya fara sanar min da xuwanku, ga shi duk kwanan nn bna samun layinkansa" Abdul yace "ehh ya dan fita waje ne, ynxu hka ma yana can kila gobe xae dawo gida," Alhaji suleman yace "to shknn," kmr yaushe xa ku tafi da matar? Abdul ya juya yana kallon Mujaheed da ya dan masa sign alamar yace yau, yace "aa ynxu xa mu koma tun shekaranjiya muke garin nn, aka ce baka nn, kuma sae kana nn ake shigowa gidan," ya gyada kai cikin gamsuwa yace "shknn bari na kira su hajiya na sanar masu," ya ciro waya ya kira matan nasa da daddaya da daddaya suka su dinga shigowa falon, ya sanar da su abinda ke tafe da su Abdul, 1st wife din tace "to amma ai da Hajiya zuwaira xata kira ni tayi min magana in hka ne," Abdul yace "dad bae ma sanar mata ba," 2nd wife din tace "to ynxu ta ina xa a fara neman wata mai aikin, gashi muna jin ddin aikinta a gidan nn," last wife din tace "to ai akwae masu aiki dayawa a gidan naga," 1st wife din ta watsa mata harara tace "amma ai duk ta fi su kwarewa," last wife din ta tabe baki tace "sae yau ku ka san da hka knn, duk da da kuke walakantata baku san tana aiki ba sae yau da ake shirin tafiya da ita ," Abdul ya mike hka ma Mujaheed kamr sun hada baki, yana kallon Alhajin yace "dad, xamu koma lkci na kurewa tana ina ne," yyi hakan ne don baya son asirinsu ya tonu su yi saurin barin katsina don matan na iya kiran mum dinsa. Alhajin ya kalli matan nasa, da yake shima dan duniya ne cikin tsawa ya ce "ku kira min ita mana kun min hake hake a falo kmr an dasa ku," suka mike kowa na fadin abinda ke xuciyarsa suka bar falon. [12/8, 21:12] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 97..... Hajiya salamatu matar Alhajin ta uku ta shigo falon Ammi na biye da ita a baya, tace "ga ta nn Alhaji," Ammi ta ja tunga daga bakin kofa ta tsaya kallon Abdul da mamaki, shi din ma kallonta yake, Alhaji suleman yana kallon Abdul yace "gata nn, kace ma Shehu ina expectn kiransa, shi hka ake yi" Abdul yace "ok xan gaya masa dad" Abdul ya kalle Mujaheed da ya kasa daina kallon Ammi don mugun kamar da suke da Aneesah kamr an tsaga kara, baka taba cewa ita ta haifi Aneesah don she look 2 young a ido, Abdul yace "mu tafi," Ammi ta dake ta hade rae tana kallonsa tace "mu tafi ina," Abdul ya kauda kansa yana dan murmushi ya juya yana kallon Mujaheed, Mujaheed ya dan fara kame kame kar Alhaji suleman ya gano su, yace "em, dama mumy, Aneesah ce bata da lafiya shine baffa yace mu xo mu taho da ke," nn da nn tashin hankali ya bayyana a fuskarta a sanyaye tace "Aneesah, me ya sameta, ita din ma kashe min ita xae yi ne," tana kai wa nn ta fara hawaye, Abdul yace "ke take son gani shi yasa aka ce mu xo mu taho da ke," yana fadin hka yyi gaba Mujaheed ya bi bayansa, Ammi ta bi bayansu har lkcn tana hawaye tana tunanin halin da 'yar ta ta ke ciki, kullum da Aneesah take kwana take tashi a ranta, barin in ta tuna bata gama mallakan hankalin kanta ba, kuma bata nuna mata abubuwa da dama na rayuwa ba. Tunda Ammi ta shigo gidan ranar ce rana ta farko da ta fito, har ta manta yanda anguwar yake ma, Mujaheed ya bude mata bayan mota, xata shiga taji an kirata da Anty, ta juya sanin me kiran nata, Faruuq ne dan Alhaji suleman din, shima baxae wuce su Abdul din ba, ya karaso yana kallonta yace "ina xaki Anty, su waye wnn," tayi murmushi tace "xan koma can Abuja ne faruuq," yace "me kuma xaki je yi a can Anty, ba gwara ki wuce gombe ba," tace "A'a Aneesah ce bata da lafiya wae," yace "ya salam, me ya sameta, tun yaushe take rashin lafiyar, ix it dat critical," Mujaheed yyi masa wani mugun kallo yace "kana bata mana lkci malam," ya juya yana kallon Mujaheed din yace "fuck yhu, nayi da kai ne" Ammi tace "kar ka damu faruuq sae naje na gani, nima ban sani ba," yace "to bari na bi ku Anty sae na dubata, quack doctors sunyi yawa a Abuja ynxu" a fusace Abdul yace "ah'ah!! Da'alla get out malam kana bata mana lkci, kai kama san hanyar Abujan ne" Ammi tace "kasan halin hajiyarka Faruuq kawae kar ka damu kayi xamanka kai da xaka koma aiki gobe," ya ciro wayarsa daya, ya mika mata yace "to shkkn Anty, ga waya ma dinga gaisawa kafin na shigo Abujan, don ina ga na daga tafiyar tawa, ki gaida min da Aneesar ssae, xanyi missn dinki mum " ta karbi wayar tai masa gdya da fara'arta, snn ta shiga motar, Abdul ya ja motar kmr mai shirin buge faruuq din, suka bar anguwar, Ammi tana kallonsa tace "ka kai ni tasha kawae na hau mota," Mujaheed yace "A'a momy ki bari mu tafi kawae," kiri kiri Ammi taki yarda ta bi su tace su kaita ta hau motar haya kawae, Mujaheed ya kalli Abdul yace "muje park kawae," Abdul bae yi musu ba suka tafi gun shiga mota, suka biya mata ticket, suka tsaya har motar ta tashi, snn suma suka shiga motarsu su ka kama hanya. Karfe shidda na yamma suka shigo Abuja, daga park din ma bbu yanda ba su yi da ita ta shiga mota su kai ta gida ba ta ki, duk da a lkcn basu ma san inda xa su kai ta ba, Ammi na kallon Mujaheed da yafi takura mata a kan ta shiga su kai ta gidan tace "kar ka damu samari, gida xan wuce daga nn, xuwa Anjima sae naje gidan baffan." hkn yasa suka bar ta ta hau tricycle, ta wuce gida, su kuma suka shiga cikin gari, Mujaheed yana kallon Abdul yace "ina xan ajiye ka guy" Abdul yyi masa mugun kallo yace "hw dare yhu? dat's nt our deal, ina Aneesar da kace xaka nuna min," Mujaheed ya dan yi shiru snn yace "ae sae ka bari mu fara hutawa ko yallabai" tare suka isa gidansu Mujaheed da Abdul din, a falo suka tar da Hajiya da autarta Amira, Amira ta rungume yayanta tayi masa oyoyo snn ta gaida Abdul dake kare ma gidan kallo kmr sabon shiga gun ganin hadadden gida, ya kalleta ya gyada mata kai kawae, snn ya gaishe da Hajiyar ta amsa da fara'arta, Amira tace yaya dady ya dawo fa, Mujaheed yace "da gske?" tace "Allah amma a lagos ya sauka gobe xo iso nn," Mujaheed ya kalli Abdul yace "mu tafi sama," Bae yi musu ba ya bi bayan Mujaheed din suka haura sama. [12/8, 21:12] ‪+234 803 751 8717‬: Khaleesat Haiydar ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 99..... Mujaheed yyi shiru yana kallon Abdul, Abdul yace "yes, ae ba xuwan kanka xa kayi ba, rakani xaka yi," Mujaheed yyi murmushi ya ciro wayarsa, yyi dailn nmbr Hydar, ya shiga kiransa, tun bayan abinda ya faru tsakaninsu har yau basu yi cmmncate ba, har ya fidda ran Hydar xae daga ya ga ya daga, ba tare da bata lkci ba yace "dama na kiraka na gaya maka ne, mum din Aneesah na gida ynxu, ko xaka je ka dauketa daga inda take ka kai ta gida," Abdul ya fixge wayar daga hannun Mujaheed din ya katse kiran yace "ni ka bani Address din gidan naje na dauketa na kai ta gida, kila hkn xae sa ta daina min abinda take min, ta dinga ganin mutunci na," Mujaheed ya tsaya kallonsa yana doubt dinsa a xuciya, can dae yace bari kawae muje, xan ma mum bayani nasan xata yafe min, ko minti biyar ba ayi ba Hydar ya kira Mujaheed, mujaheed ya daga hydar yace "ban gane xancenka ba," Mujaheed yace "no barshi ma kawae," yana gama fadin hka ya katse kiran, suna isa gidansu Mudatheer, Mujaheed ya kirasa yace "ga su nn a kofar gida Mudatheer yace su shiga daga ciki don shi baya gida, Mujaheed bae lura da motar Hydar dake parke a waje ba ya shiga gidan, Hydar dake xaune kan kujera karkashen wata 'yar bishiya yana jiran Aneesah don shima shigowarsa knn gidan ya bi su da kallon mamaki, su kam basu lura da shi ba ma, Aneesah da tunda mai gadi yace ana nemanta taji gabanta na faduwa don tasan Hydar ne ita kuma tsoransa take ji ynxu ta fito a sanyaye bayan ta nemi ixini gun Momy, tana fitowa daga falo suka yi ido huda da Mujaheed a tsakar compound yana taho wa, Abdul kuma na bayansa, ko lura da Abdul din ma bata yi ba, ta yo waje da ido cikin wani mugun farin ciki tace "yayana," Mujaheed ya wara mata ido shima da farin cikin yace "kanwata," ta taho da gudu, ya buda hannunsa ta fada jikinsa ta kankamesa, ya daura bakinsa kan goshinta, kmr xata yi kuka tace "yayana, ina ka tafi ka barni," cikin rada yace mata "abubuwa ne suka min yawa kanwata," sae a lkcn ta lura da Abdul ya dan koma baya a tsorace tana kallonsa, ta kauda kanta da sauri tana shirin barin wajen gabanta na faduwa, cak komai na ta ya tsaya ta dalilin ido hudun da suka yi da Hydar, tuni jikinta ya dau rawa, ta fixge hannunta daga rikon da Mujaheed yyi Mata da karfi ta sulale kasa wajen jin kafarta ya kasa daukarta, Mujaheed ya durkushe gabanta da mamaki yace "me ya faru kanwata," ta fashe da wani matsanancin kuka tana kallon Hydar da ya mike da kyar daga kan kujerar da yake, yyi hanyar fita daga gidan, Mujaheed ya bi sa da kallon mamaki shima, Aneesah ta mike tsaye da sauri ta bi bayan Hydar din, Mujaheed ya bi ta da kallo xuciyarsa na tafarfasa, har hydar ya bude motarsa xae shiga Aneesah ta karaso kusa da shi ta durkushe gabansa tana kuka ssae tace "wayyoo ya Hydar wllh ban san....." mari mai rai da lfya ya watsa mata snn ya fincikota ya jefar da ita daga gabansa ya shige motarsa ya wuce, kallon kallo Mujaheed da Abdul suka shiga yi a tsakar gidan, a nutse Abdul ya karaso kusa da shi yana masa wani irin kallon yace "dama son Aneesah kke, kake amfani da ni wajen cimma burinka," to bari kaji na gaya maka, baka isa ka aure Aneesah ba, Aneesah tawa ce ba ta kowa ba, Abdul na fadin hka ya juya xae fita daga gidan Mujaheed ya riko hannunsa yace "ka cire Aneesah a ranka, she ix mine" yana fadin hka ya cika sa yyi hanyar fita daga gidan shima. [12/8, 21:13] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 98..... Hydar ya juya yana kallon Aneesah bayan ya gama parkin a kofar gidansu Mudatheer, karo na farko yyi mata magana yana kallonta don tun da suka fita xuwa cafe yin registration din jamb a duk inda ya kama sae yyi mata magana baya kallon fuskarta yake maganar, ynxu kam kallonta yake ganin bata ma lura da sun iso gida ba, ko tunanin me take oho, tayi saurin sunkuyar da kanta da ta lura da kallonta yake, a nutse yace "me ke damun ki?" ta dago tana kallonsa hawaye cike a idonta, yyi mugun hade rae yace "ni bance ki min kuka ba, i only asked u a questn" tayi saurin goge idonta da tafin hannunta, yana kallonta a hankali yace "me ke damunki Aneesah," tayi shiru, shi ma hka, bayan kmr minti biyar yace "to fita, sae anjima," ta dago kai da sauri tana kallonsa a sanyaye tace "kayi hakuri," ya tsura mata ido snn yace "to me ya faru?" ta goge hawayen idonta tace "ni ban san me nayi maka ba ya Hydar...." sae kawae ta fashe da kuka, ya kauda kansa da sauri, ya bar ta tayi mai isarta snn yace "ki shiga gida dare yyi," bata yi masa musu ba ta bude motar har lkcn hawaye yaki tsaya mata tace "ngd" ya bi ta da kallo snn ya dafe kansa cike da takaici, haushi Aneesah take basa bae san meyasa ba, ganin xae tada xaxxabinsa ne ya sa ya ja motar ya bar anguwar. Duk jikin Aneesah a mace yake ranar, kawae ji tayi tana mugun son ganin Amminta hka kawae, duk da irin kular da momynsu mudatheer da dad dinsu ke mata, ta kasa bacci cikin dare tunanin Amminta ya isheta, to wae ina Amminta, ina ta shiga ta bar ta, meyasa ta kwantar da hankalinta 4 ol dis while ba Amminta, kuka kam ta yi shi har ta gaji ranar da daddare. Abdul kam a gidansu Mujaheed ya tare bayan dawowarsu daga katsina, don ko awa daya basu yi da isa gida ba Hajiyarsa ta kirasa kmr xata yi hauka bayan ta samu lbrn yaje ya dauko Ammi, daga matan Alhaji suleman, daga karshe bae bari ta kai aya ba yace mata, "2 hell wif yhu," ya kashe wayarsa ma gaba daya, Mujaheed yace "ya dae, kae da wa," yace "mumcy na ta samu lbrin na dauko mum din Aneesah," Mujaheed yace "to ynxu ya aka yi," Abdul yace "nothin," Mujaheed yace "xan maka bayanin komai Abdul don naga bbu ruwanka, yhu're vry calm," shi dai Abdul kallonsa kawae yake, cikin nutsuwa Mujaheed ya fara ma Abdul bayanin yanda abubuwa suka wakana, tun daga lkcn da ya dauko Aneesah daga kauye har xuwa gidansu mudatheer da ya kai ta, bbu abinda ya boye ma Abdul, Abdul yyi murmushi yana cije lebe yace "ku kuka daure min dad knn," Mujaheed ya daga kafada yana kallonsa, Abdul ya tabe baki yana kallon agogo yace almost tym 4 prayer. bayan sllhn maghrib Mujaheed yace su je can gidansu Aneesah kar Ammi taje gidan baffa, suka tafi kuwa, Mujaheed yyi mata bayani ita ma briefly, amma irin kallon da ta dinga masu yasa suka gane bata yarda da xancensu ba, Hkn yasa Mujaheed ya mike tsaye yace "to momy xa mu koma, goben xamu kawo Aneesar, jibi kuma akwae xama a kotu" bata tanka masu ba suka mata sllma, dama shi Abdul tun shigowarsu bae ce komai ba. washegari da Asuba, Abdul ya tashi Mujaheed sllh ganin yanda ya ke bacci kmr wani matatce alamar gajiya, tare suka tafi masallaci suka dawo, Mujaheed ya koma xae kwanta Abdul yace ya ba shi qur'ani, Mujaheed ya nuna masa inda yake, yyi kwanciyarsa. Karfe bakwae dai-dai Abdul ya da da masa duka, Mujaheed ya mike xaune da sauri yana kallon Abdul din yace "wat's wrong," Abdul yace "ni bana son naga namiji na bacci after 6 o clck, wnn ae ragwanci ne, kaga 2 b a doctor ma is a great thing in lyf, da wuya ka ga likita still on bed after six a.m," yana kai wa nn ya mike ya fada bathroom, Mujaheed ya ja dogon tsaki yace "to ni nayi maka kama da doctor ne, wnn ae wlknci ne," karfe takwas Amira ta kawo masu break sama, ta gaishe da yayanta, snn ta gaida Abdul dake bnta da kallo ya gyada mata kai, ta ajye masu ta fita, Abdul yace "kanwar nn taka bakauyiya ce wllh," Mujaheed na kallonsa ya tabe baki bai ce komai ba ya sauko ya shiga hada tea, Abdul yace "ni fa coffee nake sha, " dole Mujaheed ya sake kiran Amira ta kawo masa coffee. Bayan sun gama karyawa Mujaheed ya fito masa da kayansa ganin yaki mai da kayan jikinsa daga shi sae singlet da nicker, Abdul yace "bana sa kayan mutane, boutique xan tafi ynxu" Mujaheed bae tanka masa ba ya shige bathroom, ko da ya fito ya tarda Abdul sanye da kayan nasa yace "ashe dae kai karamin dan iska ne, ae da ca nake da singlet din xaka boutique," Abdul bae tanka masa ba yana ta kallon hotunan wayar Mujaheed din, ya mike yana nuna ma Mujaheed hotansa da Hydar yace "wnn shine Hydar din da kke fada min ko?" Mujaheed yace "yea," mujaheed na gama shiri suka sauka downstairs a tare, mumy tace ina xa ku, Mujaheed yace xamu dan fita ne, tayi masu Allah ya kiyaye, suka shiga mota Abdul ya ja ta. Sae da suka yi nisa snn Abdul yace "ina xamu?" Mujaheed yce waida inda Aneesah take xamu, amma mum ta hanani xuwa kuma ni bana tsallake umarninta," Abdul yyi tsaki yace "kai fa wani gara ne, ae ba kai xaka je ba kai ni kawae xaka yi, naga kanwata." [12/8, 21:13] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 100..... Mujaheed na fitowa kofar gidan ya tarda Aneesah durkushe kasa tana kuka, tana ganinsa ta mike tsaye tana share hawayenta, ya karaso gabanta yana mata wani mugun kallo yace "me yasa baki bi sa ba," ta girgixa masa kai tana kuka tace "yayana....." sae kuma maganar ya makale ta fashe da wani sabon kukan, Mujaheed ya girgixa kai ya daga mata hannu yace "kar ki gaya min komai, hold on 2 yhur crocodile tears, dama munafurta ta kika yi kika ce min Hydar baya son ki, don me kika min karya kikace bbu komai tsakaninki da Hydar, whereas masoyinki ne, why Aneesah?" kuka kawae take tana girgixa masa kai, ya kauda kansa ya hade tafikan hannunsa, can ya juya yana kallonta cikin tsawa yace "don me baki bi sa ba, nace don me baki bi sa ba, ae da kin bisa da kukan da kika tsaya kina ma mutane a nn, munafuka kawae" yana kai wa nn ya juya a fusace ya shige motarsa yyi gaba. Aneesah ta sulale kasa a hankali ta bi motar da kallo tana girgixa kanta, kukan ma wnn karan kasa yi tayi, wnn wace irin rayuwace, a hankali taji Abdul ya dafa kafadarta ta juya da sauri tana kallonsa sae a snn ta fashe da wani kuka mai ban tausayi, ya dago ta yana kallonta ya shiga share mata idonta yace "it's owkay Aneesah," bata ce masa komai ba ya dauko gyalenta ya mika mata ta karba hawaye na bin kuncinta, ya kama hannunta suka bar wajen, ita bata ma san binsa take ba suna tafiya, duk abun duniya ya isheta, har lkcn bata daina hawayen da take ba, sae da suka bar anguwar snn tayi saurin fixge hannunta ta shiga waige waigen inda suke tace "ina xa ka kaini?" yana kallonta yace "gurin babarki xan kai ki," ta girgixa masa kai tana kuka ssae tace "aa Ammina bata nn, ka barni na koma gida," ya kamo hannunta yace "kar ki damu Amminki na gida," ta juya da sauri tana kallonsa cikin muryar tausayi da rashin hope tace "da gske ya Abdul," ya gyada mata kai yace "eh, xan kai ki ki ganta ai," hkn yasa ta dinga binsa jiki ba kwari, suna ta tafiya a kafa, duk a rikice take don bata san ko Abdul gaskiya ya gaya mata ba, ita dae kawae ta ga Amminta, sunyi tafiya mai nisa, ta dan duka alamar gajiya, ya juya yana kallonta yace "me ya faru?" a sanyaye tana kallonsa tace "ruwa xan sha ya Abdul," yaji tausayinta ssae, ya dago ta yace "ba kudi hannuna Aneesah, bank nake dubawa ko xan samu mu cire kudi a Atm," ta gyada masa kai kawae, ya kama hannunta suka ci gaba da tafiyar, har daga karshe suka samu wani banki, ya ciri kudi a ATM tana gefensa a tsaye, sae da ya fara siya mata table water biyu snn, ya tsayar da taxi ya fadi anguwarsu Aneesar, hkn yasa taji mugun ddi, ta yrda ba cutar da ita Abdul xae yi ba, duk da a xuciyarta tana cewa wahalar bnxa kawae xasu je suyi, amma bata nuna masa sun je da Mujaheed Ammi bata nn ba, ko bakomai xata ga makwabciyarsu ta gaya mata ko suna communicate da Amminta, bayan minti talatin suka iso anguwar tasu, sae taji duk wani bakin cikinta ya yaye, hankalinta ya kwanta, Abdul ya nuna ma mai taxin inda xae tsaya dae dae kofar gidansu Aneesah. Like · Reply · More · 2 minutes ago [1:05PM, 12/23/2016] Khaleesat: [12/8, 21:07] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 101..... Abdul yyi kofar shiga gidan ganin Aneesah ta kasa shiga sae kallon gidan da take kmr bakonta, yana shiga xauren gidan ta bi sa a baya da sauri, yyi sallama ya shiga cikin tsakar gidan, tana biye da shi a baya kmr munafuka, cak ta tsaya ganin Amminta tana wanke tsakar gidan da ruwa, Ammi ta dago tana kallonsu, Aneesah bata san lkcn da ta fasa wani ihu tayi kan Amminta da gudu ta fada kanta ta fashe da kuka, suka xube kasa gaba daya Ammi ta dago kanta tana kallonta, Aneesah ta kankameta tana kuka mai tsuma xuciya, Ammi ta kasa ce mata komai, ita ma hawayen cike a idonta, Abdul dae na tsaye har lkcn kusa da su, sae da Aneesah tayi kukan mai isarta kmr ranta xae fita snn Ammi ta dago ta suka mike tsaye, ta ja ta suka shiga daki, muryarta na rawa tace "wayyo Ammina, ina kika tafi kika barni, meyasa kika tafi kika barni" Ammi ta share mata hawaye tace "gani Aneesah, ki daina kuka baxan sake barin ki ba," Aneesah ta dinga gyada mata kai tana jikinta, tana sauke ajiyar xuciya, can ta xauna da sauri tana kallon Amminta tace "Ammi ya Abdul yana waje," Ammi tayi shiru tana kallonta snn tace "ki ce ya shigo to," ta mike tsaye ta fita bata gansa ba, har kofar gida ta fita amma bata ga Abdul ba, ta dawo tana kallon Amminta da take ji kmr a mafarki take ganinta, ta xauna tace "Ammi ya tafi ban gansa ba," Ammi tace "Aliyu fa Aneesah?" Aneesah ta sunkuyar da kai wani sabon hawayen cike a idonta tace "nima ban sani ba Ammi," Ammi tace "to ina baffan naki," Aneesah tayi shiru tana kallon Amminta. Mujaheed na komawa gida Mudatheer ya kirasa, ya daga ko gaisawa basu yi ba Mudatheer yace "yah Jaheed kai ka dauki Aneesah ne," mujaheed dake kwance kan gado ya mike da sauri yace "ni? A'a ban dauketa ba me ya faru?" Mudatheer yace "tun daxu fa bata gida, momy tace tunda mai gadi yaxo yace ana sallama da ita ta fita bata sake shigowa gidan ba, kuma duk an duba ba aganta ba," Mujaheed ya mike tsaye ya katse kiran yace "innalillahi wa inna'ilaihi raji'un," Abdul, fa di da karfi snn ya figi makullin motarsa ya fita, yana fita titi ya kira nmbr Abdul din cikin tsawa yace "ina a kai Aneesah," Abdul yace "fuck yhu," ya katse kiran, Mujaheed ya kusa sake motar don tsabar rudewa, da sauri ya samu gu yyi parkin ya kira dayar nmbrsa, ya daga kuwa, Mujaheed yace "don ya rasullilahi ina ka kai Aneesah Abdul," Abdul yace "ka bani ajiyar Aneesah ne? Dnt disturb me malam," nn ma ya kashe wayar gaba daya, Mujaheed duk ya rikice ya shiga kiran Hydar, sae da yyi ring fiye da sau uku snn Hydar ya daga, bae damu da hkn ba da sauri yace "Hydar ka dauki Aneesah ne?" Hydar yace "yhu must b vry vry crazy," yana fadin hka yyi tsaki ya katse kiran, Mujaheed yace "ya salam, wats happenin" da sauri ya shiga kiransa da dayan layinsa nn ma sae da ya ga dama ya daga, Mujaheed yace "wllh wllh am nt jokin ba a ganta ba Hydar, ka tsaya ka saurareni plss," Hydar yace "kmr ya?" Mujaheed yace "ynxu Mudatheer ya kirani wae tun daxu bata gida," Hydar yyi shiru snn yace "to ina ta je?" Mujaheed yace "wllh nima ban sani ba," Hydar yace "kana ina ynxu?" Mujaheed yace "na fito gida ynxu," Hydar yace "gani nn xuwa," ko da Hydar ya iso Mujaheed na nn cikin mota yana ta try din nmbr Abdul, Hydar yace "wae meye hka kke gaya min, ba tare na barku ba" Mujaheed yace "nima na fita na barta da Abdul," Hydar ya shakesa a fusace yace "don me xaka barta da wnn mahaukacin," Mujaheed ya kasa cewa komai Hydar ya sake sa yana cewa "innalillahi wa inna'ilaihi raji'un" tare suka tafi gidansu Mudatheer din da Hydar, duk suka rude rashin ganin Aneesah, Ummi kuka momynta kuka, aka dinga kiran nmbr Abdul a kashe. Kowa dae yyi da kyau a rayuwa don kansa, ni banda abinda xance ma masu bi na da sharri, ana ganin baki na a social ntwrk. [12/8, 21:13] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 102.... Hydar yana kallon Mujaheed yace "ina kke tunanin xae kai ta?" Mujaheed ya girgixa kai cikin damuwa yace "wllh ban sani ba, gashi duk ya kashe wayoyinsa," Hydar ya dafe kansa yana kiran Allah a xuciyarsa, Mudatheer dake wajen a tsaye ya ma kasa cewa komai shima sae try din nmbr Abdul din yake, mujaheed yyi hanyar motarsa yace "ina xuwa" Hydar ya sha gabansa yace " ina kke tunanin xa ka? tun wuri lkci bae kure maka ba ka fito da Aneesah kar na baka mamaki, don nasan karya kke, karya kke, kai ka dauke Aneesah," Mujaheed yyi masa wani mugun kallo snn yyi kwafa yace "am on my own fa, kar ka tunxura Hydar, dont piss me off, baxae mana kyau daga ni har kai ba a nn," Hydar ya bugi kirjinsa yace "do yhur worst" Mudatheer ya shiga tsakaninsu yace "haba dis is nt a matter of quarrellin guyz, a bi komai a nutse xa a ga Aneesah idan Allah ya yrda," Mujaheed ya shige motarsa, yyi reverse, Hydar ma ya shiga tasa motar ya bi sa a baya, suka shiga tafiya, Hydar yyi mugun mamaki ganin Mujaheed ya sha kwanan anguwarsu Aneesah bayan tafiyar da suka yi mai nisa, ya na ta binsa har suka isa dai-dai kofar gidan snn duk suka fito daga mota, ko kallonsa Mujaheed bae yi ba ya shiga gidan, Hydar din na biye da shi a baya da mamaki, Aneesah na xaune tsakar gidan tana wanke wanke, Ammi ko na ta gyare gyare a daki wajen karfe biyar na yamma, wae yau ita ce ga ta ga Amminta a gidansu, Allah kadae yasan irin mugun farin cikin da take ji yau, wani lkcn sae ta ga kmr mafarki take xata farka, jin an shigo gidan ko sallama bbu yasa ta juya da sauri a dan tsorace tana kallon kofar soron, mikewa tayi da sauri ganin Hydar da Mujaheed, Mujaheed ya jingina jikin bango ya lumshe idonsa tare da sauke wani ajiyar xuciya, Hydar kam kasa daina kallonta yyi, ta juya a hankali tayi cikin dakinsu, Mujaheed ya bude idonsa yana kallonta, Ammi tace "kin gama ne Aneesah," ta girgixa ma Ammi kai a sanyaye tace "ya Hydar ne ya xo," Ammi tace "haba," ta gyada ma Ammi kai, Ammi tace "to ki ce ya shigo mana," ta girgixa mata kai tace "ba shi kadae bne," Ammi tace "to duk su shigo," ta mike ta fita tana kallonsu tace "wae ku shigo," Mujaheed ya juya yana kallon Hydar dake kallonta, da mamaki Hydar yace "Ammi na gidan nn ne?" kai kawae ta gyada masa yyi hanyar dakin, Mujaheed ya juya ya fice daga gidan. Hydar suka dinga hira da Ammi tana basa lbrin inda baffa ya kai ta bayan sun gama dogon gaisuwa, sae a snn ya shiga bata lbrin abinda baffan yyi masa shima, Ammi ta kasa cewa komai don tausayin hydar, ita ko Aneesah na tsakar gida a xaune don har lkcn ita bata ba ma Ammi lbrin irin abubuwan da ta fuskanta na rayuwa ba, Abdul ya shigo rike da ledojin eatry tana kallonsa har ya karaso gabanta snn tace "sannu da xuwa," ya gyada mata kai yace "Ammi fa," ta juya tana kallon daki alamar tana ciki, ya isa bakin kofar yyi sallama Ammi ta amsa, ya shiga, Hydar ya juya yana kallonsa, shi ko kallo daya yyi masa ya kauda kansa, ya ajiye ledan hannunsa yace "sae da safen mu," Ammi tace "to Allah ya kai mu mun gde Abdurrahman," ya gyada mata kai ya fita daga dakin, har lkcn Hydar bae daina kallonsa b [12/8, 21:13] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 103.... Hydar bae bar gidansu Aneesah ba sae kusan Maghrib, tana xaune har lkcn a tsakar gida amma wnn karan alwala take, bae ce mata komai ba ta bi sa da kallo har ya fita daga gidan snn ta mike a sanyaye ta shiga dakin, sae da ta idar da sllh snn Ammi ta kirata, ta juya tana kallon Ammin bayan ta amsa, Ammi tace "Aneesah dama abinda ya faru da ke knn, dama kauye baffanki ya kai ki, meyasa baki son gaya min irin abinda kika fuskanta Aneesah" Aneesah tayi shiru bata ce ma Ammi komai ba tana kallonta, Ammi ta girgixa kai hawaye cike idonta tace "Allah ya saka mana Aneesah, ba mu da abinda xamu ce da ya wuce hka" ta kamo hannunta a hankali tace "Aneesah ina fatan wahala bata sa kin yasar da mutuncinki da darajar ki a waje ba," Aneesah ta girgixa ma Amminta kai tana hawaye tace "A'a Ammi," Ammi tayi shiru tana kallonta, can kuma tace "to shi kuma wnn da suke tare da Abdul waye," Aneesah ta share hawayenta tace "ya Mujaheed sunansa, shi ya dauke ni daga kauye ya dawo dani Abuja, abokin ya Hydar din ne, yana da kirki Ammi," Ammi tana kallonta tace "da ya daukeki a kauyen ya dawo dake nn ina ya ajiye ki?" Aneesah tayi shiru tana kallon Ammi snn a hankali tace "gidansa," Ammi tace "gidansa? Kike me a gidansa?" Aneesah ta kasa cewa komai har sae da Ammi ta sake maimaita mata tambayar snn tace "Ammi ko ina nemana ake wae xa a kasheni ni bansan me nayi masu ba, harda Hajiyarsu ya Hydar ma, shine daga baya ya kaini gidan maman wani abokinsa nake tsayawa a can, suna da kirki gidan ssae Ammi," Ammi tace "kin kwana gidan nasa ne Aneesah kar kiyi min karya," da sauri ta girgixa ma Ammi kai tace "A'a" Ammi tace "to Allah ya taimakesa kmr yanda ya taimake ki," sallamar da suka ji daga bakin kofa yasa Aneesah ta mike da sauri tace "Ammi shine," Ammi na kallonta tace "to ya shigo," ta fita da sauri ta samesa tsaye, tace "wae ka shigo," ya bi ta a baya har suka shigo dakin, suka gaisa da Ammi da fara'arta tana tambayarsa ya gajiya, Ammi tace "a xubo maka abinci," Mujaheed na kallon Aneesah dake kallonsa yace "ehh Ammi a xubo," Aneesah ta mike ta kawo masa abincin ta ajiye gabansa ta koma ta xauna, hira suka dinga yi da Ammi yana cin abincin, sun yi hira ssae fiye da yanda suka yi da Hydar ma kmr da can sun saba da juna, Mujaheed bae bar gidan ba sae kusan karfe sha daya, Aneesah ta fita rakasa bae ce mata komai ba har suka iso bakin kofa snn ya juya yana kallonta bbu yabo bbu fallasa yace "ki koma gida," yana fadin hka ya fice daga gidan, ta juyo jikinta a sanyaye ta koma daki, Ammi tace "amma yana da kirki Aneesah, shima iyayensa a nn garin suke," Aneesah tace "aa yace min suna malaysia," duk surutun da Ammi ta dinga mata kan Mujaheed hankalinta baya gun, ta rasa dalilin da yasa suke mata hka, ganin Ammi na shirin kwanciya lura da tayi cewar 'yar ta ta ba jin yin hiran take ba, yasa Aneesah tace "kinsan me Ammi," Ammi na kallonta tace "sae kin fada," Aneesah ta dan yi shiru snn a sanyaye tace "shine fa wanda ya taba fasa ma Yusuf ball dinsa ya basa dubu biyu," Ammi ta tsura mata ido tana kallonta, Aneesah ta hau kan gado tana kallon Amminta tace "sae da safe Ammi," tayi kwanciyarta tare da lumshe ido. washegari tun da sassafe Abdul ya xo gidan, Aneesah na sharan tsakar gida ta mike tsaye tana kallonsa har ya karaso cikin gidan snn ta gaishesa, ya amsa ya tambayi Ammi fa, Aneesah ta nuna masa daki, ya gyada mata kai snn ya ciro wayarsa ya kira Mujaheed yace "hy ka taho gidansu Aneesah ynxu, just want 2 hand over d documents over 2 yhu" yana gama fadin hka yyi sallama ya shiga cikin dakin. Ko minti ashirin ba ayi ba Mujaheed ya taho, shima ya shiga dakin bayan sun gaisa da Ammi Abdul ya mika masa takardun hannunsa, Mujaheed na murmushi yace "no Abdul, sae anjima a kotu xaka fito da wnn," kan Abdul yace komai wayar mujaheed ya shiga ring da kmr baxae daga ba ganin Hydar ne sae kuma ya dan tabe baki ya daga, Mujaheed yace "what?" bayan ya gama jin abinda Hydar yace, ya mike tsaye da sauri yace "subhanallahi," Abdul na kallonsa yace "me ya faru?," hka ma Ammi. Gobe baxa ku samu post da wuri ba sisters, shi yasa na daure nayi wnn, muna da bikin sisterna hidimomi sun min yawa wllh, kawae ina managing kaina ne, kar kuma aji shiru wata 'yar albarkan tayi amfani da sunana tace sae bayan wata shidda xan karasa Aneesah, a fara wani sabon cece kuce kan Khaleesah, littafin da kila ma nn da kwana hudu idan na maida hankali xan karasa shi, masu amfani da sunana suna laka min sharri akan abinda ban ce ba kuma ban san anyi ba suji tsoron Allah su daina, ni ban masu komai ba, ban ma san su ba, su tausayamin su daina sawa ana criticizing dina. Kila daga Aneesah ma baxa a sake ji na ba bare a xageni. Allah ya bamu alkhairi. [12/8, 21:13] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 104.... Mujaheed ya maida wayar cikin aljihunsa fuskarsa bayyane da damuwa, Abdul yace "wae me ya faru?" Mujaheed yace "wae kanninsa ne suka yi hatsari a hanyarsu ta dawowa daga lokoja, ko uban me ya kai su lokoja oho," Ammi tace "ya xaka ce hka Mujaheed kai da xaka masu addu'ar Allah ya basu lfya," Mujaheed bae sake cewa komai ba, Abdul yace "dama yana da wasu kannin bayan wnn warce nake ganin hotonta a wayarka?" Mujaheed yace "kaninsa uku ai duk mata," Ammi tace "to Allah yasa da sauki," Mujaheed yace "Ameen, bari muje asibitin" Abdul ya mike suka fita daga dakin bayan sun mata sallama, a kofar gida suka tar da Aneesah ta dawo daga debo ruwa, kallo daya Mujaheed yyi mata ya dauke kai yace "baki da hankali kike daura ruwa a kai," bae saurari mai xata ce ba yyi gun motarsa Abdul na biye da shi a baya. Ko da suka isa hsptl din a reception suka tar da Hydar xaune, pretty na xaune gefensa ta kifa kai tana kuka, Mujaheed yace "ya dae frnd, hope its nt critical, su biyun gaba daya suka je lokojan? to wae ma me suka je yi a can Hydar," Hydar ya mike cikin fada yace "ka tambayeni Mujaheed? Ka tambayi uwarsu, Ae wllh tllh naga abun yafi karfina cire hannuna kawae xanyi, wnn ae bala'i ne da masifa, yara an sake su kmr wasu akuyoyi, basa can basa nn, ka shiga kaga ko xaka iya kallonsu Mujaheed," Mujaheed yace "innalillahi wa inna 'ilaihi raji'un," Abdul ya karasa ward din da ya lura suke, gnin ynda likitoci ke sintiri Mujaheed ya kasa binsa, ko minti biyar ba ayi ba ya fito ya xauna kan kujera yana girgixa kai, da ganinsa kasan bae ji ddin abinda ya gani ba, ya juya yana kallon Hydar yace "shawarar da xan baka kawae a fita da su waje, bbu abinda xa a iya masu a nn, ku fita dasu kawae," Hydar yace "abinda ya kai su can lokoja ya xo ya fita dasu wajen amma ni bbu ruwana," Mujaheed xae yi magana Hajiyarsa da kanwarsa suka shigo da wasu mata har uku, basu ko kallesu ba suka yi cikin ward din, da daddaya da daddaya suka dinga fitowa da kuka. [12/8, 21:13] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 106.... Da yamma Hydar ya shigo gidan, Ammi ta ba shi abincin da ta girka ya kai asibiti, Hydar yace "Ammi da ma kin bar ba kanki wahala don ban tsamman suna iya cin abincin ba ma, wahalar da suka dauko ma kansu yafi karfin su ci abinci, ina ga da daddare ma xasu tafi india. " Ammi tace "wae kai meyasa kke hka Hydar, yau ko ba kanninka bane baxa ka ji tausayinsu ba bare kanninka uwa daya uba daya, haba Hydar" yace "a'a Ammi ni bance baxan kai masu ba ai xan kai," Ammi tace "to bana son kana irin wnn maganganun, Allah ne ya kaddara masu hkn," Aneesah dae na xaune tana kallonsu don ko da ya shigo ma yi yyi kmr bae ganta ba, Ammi tace "baki iya gaisuwa bne ke," ta dan wayance tace "A'a naga kuna magana ne," ta juya tana kallon Hydar din tace "ina yini ya Hydar," yace "lfya lau," Hydar ya karbi basket din da Ammi ta ajiye masa yace "to xan tafi Ammi, Allah ya saka da alkhairi," Ammi tace "da yaushe xasu tafi yau?" Hydar yyi shiru yana dan tunanin snn yace "ina ga xuwa bayan maghrib jirginsu xae tashi," Ammi tace "ummanka xata bi su ne," Hydar yace "A'a yayarta ce xata bi su da kanwar dad dina sae mum din Mujaheed," Ammi tace "to Allah ya sauwake masu ya basu lfya," Hydar yace "Ameen Ammi," Ammi ta juya tana kallon Aneesah tace "tunda yau xasu tafi da Aneesah kin shirya kuje ki gaishesu," gaban Aneesah yyi mugun faduwa ta kasa cewa komai sae kallon Amminta da take, shi kansa Hydar sae da ya dan ji wani iri, amma yyi saurin cewa "to ta shirya mu tafi mana," Ammi ta kalleta tace "ki shirya kuje Aneesah," Aneesah ta gyada mata kai, Hydar yace "ina jiranki a mota" snn ya fita, ta mike a sanyaye ta dauki Hijab dinta milk colour har kasa ta sa, snn ta dan gyara fuskarta, Ammi tace "amma fa kar ku dde Aneesah kinji, naga yana da kirki ne shi yasa nace kije," Aneesah tace "to Ammi" snn ta saka takalminta ta fita taje ta samesa a mota. [12/8, 21:13] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By khaleesah Haiydar 105..... Aneesah da Amminta suka dawo gida jikinsu a sanyaye ranar daga kotu, Rayuwa knn dama watarana sae lbri, kuma Hkuri shine wadata, Abdul ne yyi drivin din a motar Hydar ya mayar da su gida, Hydar ko na xaune gefensa a gaba, Mujaheed dama daga kotu yana shiga motarsa yyi gaba, suna isa gida bayan Aneesah da Amminta sun shiga, Hydar ya juya yana kallon Abdul yace "kar ka damu frnd, nn da 'yan watanni sae mu sake tada case din, daga nn sae a samu dad dinka ya fito," Abdul yace "in shi ya fito sae wa ya shiga?" Hydar yyi murmushi yace "ba kowa idan Allah ya yrda" Abdul ya daga kafadarsa bae ce komai ba, Hydar ya fito shima ya fito suka shiga gidan, Abdul dae na xaune a tsakar gidan yana kallon Aneesah dake kkrin kunna wutan coal xata daura girki, yyi murmushi yace "na karshe kike yi hka ko me," ta juya tana kallonsa bata ce komai ba sae murmushin da tayi ta cigaba da abinda take, ita kam tausayi yake bata, ashe dama Abdul ba ruwansa hka, Hydar na daki xaune da Ammi, sae da ya bari ya gama jin batun Ammi dake masa magana a sanyaye snn yace "wnn ba matsala bane Ammi, nayi masa magana daxu a mota bae dae ce min komai ba, nace nn da 'yan watanni xa a sake dago case din," Ammi tace "amma ba ddewa xa ayi ba ko Hydar?" Hydar yace "sae nn da wata uku don yaji ya xaman prison yake, nxt tym baxae yi marmarin taba abinda ba nasa ba, ae dama rayuwar sae da had i knw" Ammi xa tayi magana ya riga ta da sauri don bae son jin abinda xata ce yace "to ynxu Ammi yaushe xa ku bar nan?" Ammi ta girgixa masa kai tace "A'a ni ina nn," Hydar yyi shiru snn yace "kar ki ce hka Ammi, muje ki xabi daga cikin gidajen da kike son ki xauna," Ammi tace "ni fa ina nn Hydar," bae sake ce mata komai ba, tace "kaje Asibiti kuwa yau," ya girgixa mata kai tace "sbda me Hydar? Wae me yasa kke hka ne Hydar?" yace "ae akwae mutane a asibitin, amma ynxu nake son tafiya dama," Ammi tace "to ka tashi ka tafi, kuma ka gaida mana su, Allah ya sauwake," yace "Ameen Ammi," snn ya mike yyi mata sallama ya fita, ya kalli Abdul da har lokacin ke kallon Aneesah tana ta aikinta yace "mu dan tafi Asibiti Abdul" Abdul ya mike yace "ni akwae wani allura ma da nake son ayi masu naga nn ko maganar alluran basa yi, amma tsada gare shi may b sae an fita da su," tare suka fita daga gidan Aneesah ta bisu da kallo, suna fita ko minti goma ba ayi ba Mujaheed ya shigo, ta juya tana kallonsa ta gaishesa murya can ciki, ko kallonta bae yi ba, kuma yyi kmr bae ji ta ba yyi sallama Ammi ta amsa ya shiga dakin, ya gaishe da Ammi ta amsa tana tambayarsa ya gajiya, yace "Ammi, wani gidan kike son a bude maku in ma da gyara ciki a yi sae ku koma," Ammi ta girgixa masa kai tace "A'a ina nn Mujaheed nn ma ya isheni," nn fa Mujaheed yace bae san xance ba dole sae sun bar wnn gida, Ammi tayi murmushi tace "to ka bari ba ynxu ba tukun, sae an sake baffansu," Mujaheed yyi shiru bae ce komai ba, bae kuma sake musu da ita ba yace xae tafi, tace "ka tsaya kaci abinci mana Aneesah ta kusan gama girki," ya dan kalli tsakar gidan snn yace "xan dawo Ammi," ya mike yyi mata sallama ya fita. Da yamma Hydar ya shigo gidan Ammi ta tambayesa ya jikin kannin nasa da babarsa, ya dae ce da sauki, Ammi tace "wae da tuwo nake girka masu ka kai masu," yace "to mun gde Ammi," karfe shidda ta gama hada Abincin ta basa ya kai masu, ya karba yyi gdya ya bar gidan, ranar da daddare Aneesah ta ci kuka jikin Amminta wae yau ga su ga dukiyar Abbansu a hannunsu, duk da a hkn ma ba duka ba, gidaje uku suka samu, sae motoci uku da filaye da dama, snn kudin dake accnt ma an basu kayansu, sae taji tausayin Abdul ganin ya dake bae nuna komai ba har aka yanke ma ubansa hukunci, duk da ta lura hkn ya girgixa sa. Washegari da safe Abdul din ya xo gidansu, ta hada masa breakfst a daki ta fita ta cigaba da abinda take yi don Ammi na makwabta, suna tsakar gidan su biyu a xaune tunda dae ba hira suka saba ba, sae dae ya kalleta ta kallesa Mujaheed ya shigo gidan, Aneesah ta mike tsaye tana kallonsa ta gaida shi, yana kallon Abdul yace "Ammi fa," Abdul yace "bata nn," Mujaheed yace "ok, xo muyi magana Abdul," Abdul ya mike ya bisa suka fita. Aneesah ta koma ta xauna a sanyaye kmr xata yi kuka, ita kam bata san me tayi masu ba duk basa amsa gaisuwarta, Abdul kadae ne ke amsawa. Maganar da Hydar yyi ma Abdul, shi Mujaheed yyi masa kan cewar xa a daga case nn da watanni. [12/8, 21:13] ‪+234 803 751 8717‬: Haiydar ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 107..... Aneesah ta fito ta same shi cikin mota yana jiranta, ta bude back sit ta shiga gabanta na faduwa don ita kam ynxu tsoron Hydar take, ga kuma Hajiyarsa da xata je ta tarar a asibiti, bae ce mata komai ba yyi reverse suka bar anguwar, sunyi tafiya mai nisa taga ya nemi gu yyi parkin bae ce mata komai ba ya bude motar ya fita ta bi sa da kallo taga ya shiga wani store, bayan kmr minti goma ya dawo rike da ledan Hollandia yorgurts da wasu lemun daban, ya shiga motar ya ajiye ledan kan sit din gaba snn ya ja motar suka bar wajen, ita dae kallonsa kawae take bae ce mata ba bata ce masa ba, suna isa wani guri da ake sayar da fruits nn ma yyi parkin ya fita, ya siya fruits kala kala ya dawo cikin motar snn suka kama hanyar asibitin, babban Asibiti ne ssae ya nemi guri yyi parkin a Haraban Asibitin ya fito, ita ma ta fito gabanta na mugun faduwa, yana tsaye har ta karaso gabansa ya mika mata ledojin hannunsa ta karba tana kallonsa, shi din ma kallonta yake, ta sunkuyar da kanta yyi gaba tana biye da shi a baya. Dai dai shiga reception ya juya ya ga ta tsaya taki karasowa, ta marairaice masa tace "tsoro nake ji ya Hydar," ya dan yi shiru snn yace "bana son na sake juyawa na gan ki a tsaye" yana fadin hka yyi gaba, ta shiga binsa a sanyaye har suka shiga ward din da Hajiya ke kwance don ita ma drip ake karamata, xuciyarta na bugawa ta tsaya daga bakin kofa ta kasa karasawa ta dalilin kallonta da taga Hajiya na yi, Hydar ya karasa ciki ya ja kujera ya xauna gefen gadon yana kallonta yace "ya jikin mum," Like · 3 · Re [12/8, 21:13] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 108...... Aneesah ta kasa karasawa ciki har sae da daya daga cikin matan dake xaune a dakin tace "shigo mana 'yan mata," da kyar ta iya karasawa cikin ward din gabanta na faduwa har lkcn Hajiyar bata fasa kallonta ba, Hydar ya ja mata kujera gefen gadon ta xauna, muryarta na rawa tace "ina yini mummy, ya jiki," Hajiya ta sauke ajiyar xuciya a sanyaye tace "lfya lau Aneesah, ya gida," Hawaye ya cika idon Aneesah ta kasa cewa komai, Hajiyar ta mike xaune tana kallon Aneesah tace "kinga yanda rayuwa tayi da ni da 'ya yana ko Aneesah, kila ma hakkin ki ne ke bibiyarmu" Aneesah ta fashe da kuka tana girgixa kai ta kasa cewa komai, Hawaye ya cika idon hajiyar tace "ki yafe mana Aneesah, ki yafe mana, bamu maki adalci ba a rayuwa," kuka ssae Aneesah take ta fada kan Hajiyar tace "ni baku yi min komai ba mummy, nima ku yafe min," haka suka dinga kuka abun tausayi, Hydar ya mike ya fice daga dakin, da kyar matan dakin suka lallashi Aneesah tayi shiru, Hajiya tace taje ta duba su sumayya da Amina, ta mike a sanyaye, wata mata ta rakata, a hanya suka hadu da pretty, tayi mata wani kallon bnxa kmr bata san daga inda ta fito ba, Aneesah ta gaisheta a sanyaye, pretty ta wuce abinta tare da ce mata sannu, Matar da ke tare da Aneesah kanta bata ji ddin abinda pretty tayi mata ba, Aneesah dae ta dinga binta jiki ba kwari har suka isa ward din gabanta ya shiga faduwa don bata san me xata je ta tarar ba, a tsorace ta bi matar suka shiga dakin, ai kam tayi da ta sanin shiga don kuka ta dinga yi ssae don abin kam sae du'ai, matar tace "ba kuka xakiyi ba, addu'a xa kiyi masu Allah ya basu lfya," kai kawae ta gyada ma matar snn suka koma can dakin da Hajiyar take, xaune taga Mujaheed gefen Hajiyar yana hada mata tea, yyi mugun mamakin ganin Aneesah, ya kasa daina kallonta. [12/8, 21:13] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 109..... Daga Hydar har Mujaheed tsayawa kallonta suka yi cikin wani yanayi da baxa a kira da mamaki ba, Mujaheed ya karaso gabanta a hankali yana kallonta a sanyaye yana gyada kai yace "shknn Aneesah, dama ni na taimake ki ne sbda Allah da kuma ina sonki, tunda kika yi wnn furucin xan nuna maki ban taimake don wani abu naku ba Aneesah, xan rabu dake, Allah ya bamu Alkhairi," yana kai wa nn ya juya ya bude motarsa, Aneesah ta matsa daga jikin motar a hankali hawaye na bin kuncinta, ta bi motar da kallo har ya bar anguwar, snn ta fashe da kuka tana kallon Hydar da ya juya ko tunanin me yake oho, ta ga ya juyo a hankali yana kallonta, idonsa ya kada yyi jajur, ta juya masa baya tana kuka ssae, a raunane taji ya fara magana "Aneesah kin ban mamaki, ke har xaki iya biyana abinda na maki," ya girgixa kai kmr xae yi hawaye muryarsa can kasa yace "na rabu dake Aneesah, dama badan wani abu naku na tsaya maku ba, nayi sbda Allah ne da kuma son da nake maki, kiyi hkuri na rabu dake na har abada Aneesah i promise yhu baxan sake shiga rayuwarku ba, neva, Allah ya sada mu da Alkhairinsa" Aneesah ta rasa ma me xata ce don tashin hankali kuka ssae take tana girgixa masa kai, hawayen da ta ga idonsa ya dada rikita ta, ya juya yyi hanyar motarsa, ta sulale wajen cikin tashin hankali, da kyar ta iya cewa "na shiga uku," tana kallo har Hydar ya bar anguwar, ta fashe da wani sabon kukan da ta sanin abun da tayi, da kyar ta iya mike tayi hanyar shiga gida tana ganin jiri, bata bari Ammi ta lura da kukan da take ba, tana shiga daki kwanciya kawae tayi, ranar tayi kukan da ta sanin abun da tayi da daddare, bacci ya kaurace mata duk taji bbu abinda ke mata dadi a duniyar, taji ta tsani kanta, sae kusan karfe uku ta samu bacci, da safe Ammi ta lura da yanda idonta ya kumbura tayi tayi da ita me ya sameta taki gaya ma Ammi tace kanta ne ke ciwo kawae, karfe sha daya su ummi da Momynta suka xo gidansu, Aneesah tayi farin cikin ganinsu ssae kuma tayi mamakin yanda akayi suka san gidansu, Ammi ta tare su da kyau don Aneesah ta bata lbrinsu, har Ammi na shirin xasu je gidan nasu xuwa nxt wk sae kuma ga su sun xo, momy na ta hira da Ammi bayan ta mata jajan Abinda ya faru, duk wnn hiran da ake Aneesah dakewa take kawae don xaxxabi take ji na neman rufeta, duk she is nt herself ta rasa abinda ke mata ddi a duniyar, kar ummi tace ta shareta yasa ta shiga tambayarta Mudatheer da mutanen da ta saba da xamanta gidansu, ummi tace "yana kano ae tun lst wkk," Aneesah ta dauko takarda da pen tace ummi ta rubuta mata Nmbrsa, sae kusan sha biyu Ammi da Aneesah suka rakasu bakin motarsu xasu koma gida, Ammi tace masu suna nn xuwa suma. Bayan tafiyar su ummi da kmr minti ashirin Faruuq ya shigo gidan, Aneesah ta kirkiro fara'a tana gaishesa ya amsa yana murmushi, tace "sae ynxu ya faruuq," yace "wllh kuwa ya shiga ya gaida Ammi a daki," Aneesah ta xauna ta rafka tagumi tayi jigum a tsakar gidan abun duniya ya isheta, tuna abinda ya faru jiya yasa hawaye ya shiga bin kuncinta, bata masu halacci ba, ta butulce masu, ta cuce kanta, kuka ssae take amma mara sauti, ta ga mutum durkushe gefenta yana kallonta, ta mike tsaye da sauri tana goge hawayenta tace "ya faruuq," ya girgixa mata kai yace "me ya faru Aneesah," tana goge fuskarta tace "bbu komai," ya harareta yace "karya kike yi, bana ce ki daukeni matsayin yayanki ba Aneesah, meye damuwarki ki gaya min, kar ki boye min ni yayanki ne kinji" wasu sababbin hawayen na bin kuncinta tace "bbu komai ya faruuq," yace "to bari naje na kira Ammi sae ki gaya mata ita," ta girgixa masa kai da sauri tace "A'a don Allah kayi hkuri," yace "to gaya min me ya sa ki kuka, tunda na shigo na lura kina cikin damuwa kanwata," tana goge fuskarta a sanyaye ta kasa cewa komai, yace "ki yarda dani Aneesah, ki gaya min damuwarki don Allah," a hankali tace "xan gaya maka to," ya shiga dakin da Ammi ta gyara masa don dakuna uku ne a gidan dama, ta bi sa a baya ta xauna kan kujera tana kallonsa yace "ina jinki kanwata," a sanyaye tace "lbrin mutane biyu xan baka yayana, sae ka gaya min wanda yafi cancanta a cikinsu ya xama mamallakin warce ke cikin lbrin nawa," ya hade rae yace "lbri nace maki nake son ji, matsalarki nace ki gaya min na sama maki solution kanwata," tace "ka fara saurarana yaya, wllh xaka ji damuwata idan na gama baka lbrin," yace "to ina jinki," a nutse ta shiga basa lbrin kanta ba tare da ta bari ya gane ba, tun daga farko har ixuwa lkcn da ta fara aiki gidansu Hydar, da irin taimakon da yyi mata, tun daga nn ya gane lbrinta take basa, ya dae yi shiru yana sauraranta, bbu abinda ta boye ma faruuq har xuwanta kauye da haduwarta da Mudatheer, snn Mujaheed, Faruuq ya tsura mata ido yana sauraran lbrin nata har ixuwa abinda ya faru jiya da daddare, bbu part din da ta boye masa, ta fashe da kuka tana kallon faruuq da ya lumshe idonsa ya kasa cewa komai, a hankali taji yace "Hydar ya cancanci xama mamallakin ki Aneesah," [12/8, 21:13] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 110.... A hankali Aneesah ta sulalo daga kan kujeran da take hawaye na bin kuncinta, Faruuq ya tsura mata ido snn yace "me yasa kika ce xaki biyasu abinda suka maki Aneesah, kinga alamar xaki iya biyan abinda suka maki, barin Hydar da ya xauna prison na watanni," kuka ssae take tana girgixa kai tace "ban san lkcn da nace masu hka ba ya Faruuq," faruuq yace "to ki kirasu ki basu hakuri," a sanyaye tace "ban da nmbrsu," yyi shiru yana kallonta snn yace "ki bani address dinsu duka, kafin na tafi yau xanje na samesu," ta gyada masa kai tana kallonsa, a takarda ta rubuta masa address dinsu gaba daya, snn ya mike yace "to ki share hawayenki kanwata kar ki daga ma Ammi hankali, sae na dawo" yana kai wa nn ya fice ta bi sa da kallo hawaye mai xafi na bin kuncinta, ta mike da kyar tana gyara fuskarta ta fita daga dakin xata je yin wanke wanke, throughout ranar Ammi ta kasa gane kan Aneesah duk ita ma ta daga hankalinta, ita dae Aneesah jiran dawowar ya faruuq kawae take, da yamma tana share tsakar gida taji an bude kofar gidan ta mike da sauri a tunaninta Faruuq ne, pretty ce ta shigo gidan kmr mahaukaciya wasu mata na biye da ita a baya, gaban Aneesah yyi mugun faduwa, pretty ta karaso kusa da ita da sauri ta rikota ta fashe da kuka tace "me kika yi ma yayana Aneesah, ki gaya min me kika yi ma yayana," ta sulale kasa ta daura hannu a ka tana kuka mai ban tausayi tace "don Allah ki gaya min me kika yi masa," Hajiyar Mujaheed ta karaso cikin gidan ita ma a rude tana kallon Aneesah tace "ke ce Aneesah ko," Aneesah ta kasa cewa komai don tashin hankali, a hankali ta sami kanta da sulale kasa ta fasa wani ihu a tsorace, hajiyar ta durkushe gabanta a rude ta rikota tace "don Allah ki rufa mana asiri," don a tunaninta suma Aneesah xata yi, Ammi da bata gidan ta shigo dai dai lkcn, ta karaso a dan tsorace tace "me ya faru," pretty na kuka ssae tace "don Allah mama ki bar ta ta bi mu asibiti, kar yayana ya mutu ita yake ta kira," daya daga cikin matan da suka shigo gidan ta dago Aneesah tayi waje da ita, Hajiya na biye da su da sauri, duk da ganinsu kasan suna cikin tashin hankali, Aneesah komawa tayi kmr statue duk ta kasa wani kwakkwaran tunani da kwakwalwarta, ta xama kmr wata mutum mutumi, hawayenta ma tamkar sun kafe take ga, Amai ta shiga kwararawa cikin motar ba gaira ba dalili, don har lkcn ita bata gama fahimtan abinda ke faruwa ba, matan suka riketa a rude wata na xuba mata ruwa, sae a snn maganganun pretty suka dinga dawo mata, daga nn kuma bata sake sanin abun da ya faru ba, don sulalewa jikin matar da ke rike da ita tayi sumammiya.duk suka rude a motar wasu har da kuka, pretty nata kam ba a magana, suna isa asibitin ita ma aka shiga da ita da sauri. Ko da ta bude idonta pretty ta gani xaune gefenta tana kuka, pretty ta kamo hannunta cikin kuka tace "don Allah kar ki sake rufe idonki Aneesah ki tausayama yayana," wata nurse ta shigo ta janye pretty daga kusa da Aneesah da ta xuba mata ido kmr wata mara hankali, nurse din tasa duk matan dake dakin suka fita, Aneesah dae binsu kawae take da kallo, nurse din ta fita ta ja kofar, bacci mai nauyi ya dauketa daga nn. [12/8, 21:13] ‪+234 803 751 8717‬: Khaleesat Haiydar ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 111..... A hankali Aneesah ta bude idonta ta shiga kare ma inda take kallo, daga karshe ta sauke idonta kan drip din dake hannunta, ta fara kkrin mikewa xaune, taji muryan mutum a gefenta, ta juya da sauri taga Abdul ne, yace "ya jikin kanwata" tayi shiru tana kallonsa, ya mike ya fita ya shigo da nurse ta cire mata drip snn tace a bata tea ta sha, Abdul ya fita ya shigo tare da mum din Mujaheed ta karaso kusa da Aneesah tace "sannu kinji Aneesah," Aneesah dae bata ce komai ba sae kallonta da take, ta hada mata tea ta shiga bata da kanta, kadan Aneesah ta sha ta kauda mata kai Hajiyar tace "ki sha mana Aneesah," Aneesah ta girgixa mata kai a karo na farko muryarta a shake tace "ya Hydar fa," Hajiyar tace "ki daure ki sha sae na kai ki gunsa bacci yake," da kyar ta shiga kurban tean har tayi rabi tace ta koshi, wata nurse ta shigo da magunguna mum din Mujaheed ta karba tace "xa mu iya dan fita da ita nurse," Nurse din tace "idan har bata ganin jiri xaku iya fita da ita amma kar kuyi nisa," Hajiya tace "A'a bama waje xamu ba, ward din dake sama xamu," nurse din tace "ok," tana kallon Aneesah tace "hope bbu inda ke maki ciwo ynxu," Aneesah ta gyada mata kai nurse din ta fita, Abdul yace "mum ku bar Hydar ya huta kar a tada shi," hajiya tace "aa baxa mu tashe sa ba dama, da ya ma aka samu yyi baccin," hajiyar ta taimaka ma Aneesah ta mike tsaye ta bata takalmi ta sa, snn suka fita daga dakin, dakin da Hajiyar ke kwance ta fara kai ta, hajiya duk ta rame ta xama wani iri ita ma a daxun ciwonta ya tashi bayan an aiko mata da rasuwar sumy a can india, snn ga Hydar da aka rasa me ya samesa lkci daya, don lkcn bai ma san da mutuwar kanwartasa ba bare ace shine, Aneesah ta shigo dakin a sanyaye tana kallon hajiyar da ta mike xaune da sauri ganinta, ita ma ruwan ake kara mata, Ammi ma na xaune dakin, cikin murya mai ban tausayi Hajiyar ta fara magana tana kuka, "don Allah Aneesah ki yafe mana, ki tausaya ma rayuwata ki amince ki aure Hydar, shi daya nake da bana son wani abu ya samesa Aneesah, ban gama dawowa hayyacina daga mutuwar Sumayya ba sae ga na Hydar, idan wani abu ya sami Hydar ban san ya rayuwata xata kasance ba," kuka ssae Hajiyar take, Aneesah ma kukan take, duk mutanen dake xaune dakin sae da jikinsu yyi sanyi, Ammi ko kasa dago kanta tayi, Hajiya ta juya a sanyaye tana kallon mum din Mujaheed tace "kun ki gaya min halin da Aliyu ke ciki," mum din Mujaheed tace "nace maki bacci yake yi Hajiya," tana fadin hka ta kama hannun Aneesah suka fita daga dakin, wani ward din daban suka shiga gabanta yyi mugun faduwa ganin Hydar kwance ana kara masa ruwa har leda biyu, faruuq na xaune dakin da wani frnd dinsa, pretty ma na xaune gefensa kmr xata shige jikinsa, duk ta xama wani iri itama abun tausayi, Aneesah ta karasa kusa da shi da sauri ta fada kan gadon tana kuka, faruuq ya janyeta da sauri yace "kar ki tada sa Aneesah," ta koma gefe tana kallonsa tana ci gaba da kukanta mai ban tausayi, Mum din Mujaheed ta kalli Najeeb tace "na samu Mujaheed a waya daxu Najeeb, wae ashe ya koma holland ne, kaji tsiya ko ubansa fa bae sanar ma wa ba bare ni," Najeeb yace "ikon Allah, to kin gaya masa rashin lafiyar Hydar din ne mum," Hajiyar tace "eh na gaya masa, yace gobe xae juyo, yana can duk ya daga hankalinsa shima yau ya kirani yafi sau ashirin " a sanyaye pretty tace "nima yana ta kirana," Najeeb yace "dama kice masa mu hadu a Egypt kawae, can xamu wuce da Hydar gobe," Hajiyar tace "egypt kuma Najeeb," Najeeb yace "wnn Abdul din ne yace hka, shima likita ne ssae, kuma daxu ma wani doctor ya kirani office ya gaya min hka," Hajiyar tace "to mu dae ga mu ga Allah, Allah dae ya basa lfya, ku ba Aneesar kujera ta xauna," Najeeb ya jawo mata kujera ta xauna da kyar, Hajiyar ta juya ta fita, ana kiran sllhn isha duk suka fita yin sllh dakin ya rage daga Aneesah sae pretty, wata mata ta leko tace pretty taje Hajiya na nemanta, ta fita daga dakin tana kallon Aneesah kmr me tsoron kar ta ma yayanta wani abun, bayan ta fita Aneesah ta mike ta karasa kusa da gadon a sanyaye ta dafa gadon tana kallonsa hawaye na bin kuncinta, a hankali ta shiga kiransa ganin bae amsa ba yasa ta fada kansa tana kuka ssae, ranar dae asibitin ta kwana don likitocin ca sukayi ta xauna ko da xae farka ya xamana tana kusa da shi kuma a kanta xae daura ido kafin kowa, dole Ammi ta wuce gida ta barta, cike da tausayin Hydar, Aneesah dae na gefensa a xaune jira kawae take taga ya bude ido amma yaki budewa, hkn yasa ta kasa samun nutsuwa hawaye yaki tsaya mata, ba ita ba kowa ma abinda yake jira knn har likitocin amma shiru. Like · 5 · Reply · Report · 27 minutes ago A'ishah Abubakar [12/8, 21:13] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 112..... Washegari friday aka fara shirin fitar da Hydar xuwa Egypt ganin har lkcin bae farka ba, bbu wanda hankalinsa yafi tashi irin Aneesah da mum dinsa, Aneesah na xaune gefensa ita dae gata nn, wani lkcn ma sae ayi ta mata magana bata san da ita ake ba, tamkar mai brain disorder ta koma, Hajiya ce ta shigo dakin don taga bbu abinda kwanciya xae mata dan ta na nn rai a hannun Allah, ta karaso cikin dakin a sanyaye tana kallon Aliyu, Aneesah ta mike xata bata kujera tace "yi xamanki Aneesah dama magana na xo muyi dake," Aneesah tayi shiru tana kallonta snn tace "to mumy ina jinki," Hajiya ta juya tana kallon Abdul dake xaune dakin, Aneesah ta gane me take nufi tace "kiyi maganarki mum, yayana ne," Hajiyar ta ja kujera ta xauna a raunane ta fara magana kmr mae shirin fashewa da kuka "Alfarma naxo nema gunki Aneesah, kuma nasan baxa ki hanani ba, Aneesah nasan Hydar na sonki ssae, ke dae ce ban san abinda ke xuciyarki ba, wnn rashin lfyar sbda ke yake yinta, kuma tun ba yau ba yake da hawan jini kuma ni kam nasan ta dalilinki ya samu hawan jini sbda yanda yake sonki, Aneesah ki tausaya mana don Allah don Annabi ki amince a daura maku aure da Hydar sae ki bi su can Egypt din har Allah ya basa lfya, kinga ni baxae yiwu na bi su ba, jiya sumayya ta rasu, kiyi hkuri ki taimake mu Aneesah hkn kadae ne xae dawo min da farincikin da na ko da ya warke ya ganki a matsayin matarsa" tana kai wa nn ta fara hawaye abun tausayi, gaban Aneesah ya shiga bugu da sauri da sauri ta kasa daga kai ta kalle Hajiyar sae hawayen da take ita ma, a xuciyarta tace wayace maki Hydar na sona ynxu, da knn amma ba ynxu ba, muryar Abdul taji yace "ki amince kanwata nasan Hydar na sonki ssae, kuma daga reactions dinsa jiya bbu tantama ta dalilinki hawan jininsa ya tashi, save lyf kanwata, dama Allah yyi shine mijinki" kuka ssae Aneesah take tana kallon Abdul, ya gyada mata kai alamar ta yrda da batun Hajiyar, hajiya sae hawaye take tana jiran cewar Aneesah, da kyar Aneesah ta iya ce mata "sae Ammina ta amince," ko minti biyar Hajiyar bata kara a asibitin ba ta sa aka kaita gun Ammi, Ammi ma ta kasa cewa komai jin batun da Hajiyar ta xo da shi, daga karshe da kyar ta samu na cewa tace to Hajiya ki bari muyi shawara da yan uwana da na ubanta, Hajiyar tace "ba komai 'yar uwa duk yanda kuka yi ina jiran bayani, kinsan kila yau xa a su fita, kuma ga abinda likitoci suka ce ya kasance tana kusa da shi xae far fado, shi yasa nake son ku taimaka nasan Hydar xae riketa amana, kuma son gskya yake mata" Ammi tace "xaki ji ni gobe Hajiya Allah dae ya bashi lfya," Hajiyar taji ddi ssae kmr an mata albishir da gidan Aljanna. Faruuq Ammi ta fara magana da kan batun da Hajiya ta xo da, yyi shiru na dan lkci snn yace "gskya yana sonta ssae Ammi ita fa ya dinga kira ko da muka isa asibiti jiya, sae dae ki fara tuntubarta kar a cuceta ita kuma, amma ya cancanci xama mijinta," faruuq yaje asibiti ya maido da Aneesh gida ranan, duk ta xama wani iri ta rame kamr ita ce mai ciwon, a nutse Ammi ta sa ta gaba ta shiga tambayarta ko tana son Hydar, ta fashe da kuka ssae tana girgixa ma Amminta kai, Ammi tace "kiyi min magana Aneesah kar ki ji komai" cikin kuka muryarta na rawa tace "to Ammi ya Mujaheed fa?" Ammi tayi shiru tana kallonta snn a hankali tace "shi kike so Aneesah?" Aneesah ta kife kanta kan gado tana kuka kmr ranta xae fita ta kasa ce ma Amminta komai, Ammi ta rasa me xata ce mata ita ma, duk iya yan da Ammi ta so jin ko Mujaheed din take so Aneesah kin cewa komai tayi sae kuka, dole Ammi ta kyaleta ta fita daga dakin, daga nn bacci ya dauketa. [12/8, 21:13] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 113..... Bayan sllhn Magrib Aneesah na kwance daki tayi jigum abun duniya ya isheta, Ammi ta shigo dakin tace "ki je wae ana nemanki a waje Aneesah," Aneesah ta mike xaune tana kallon Ammi a sanyaye tace "wa ke nemana Ammi," Ammi tace "wae abokin Hydar," Aneesah tayi shiru, Ammi tace "tashi ki je mana, kar dae ki dde ae faruuq ma na waje," Aneesah ta mike jikinta a sanyaye kmr mara lfya, ta dauki Hijab dinta ta sa ta fita daga gidan, yana tsaye jikin mota, sae dae ya juya baya, ta karaso kusa da shi da sauri tana kallonsa, muryarta na rawa kmr xata yi kuka tace "ya Mujaheed," ya juya da sauri ya sakar mata murmushi yace "ya akayi kika son ni ne," hawayen da ya cika idonta ya gangaro, ya girgixa mata kai yace "kuka kuma kanwata," ta kasa ce masa kmai sae kukan da take yi a hankali, ya kama hannunta suka samu wani dan dakali suka xauna snn yace "ni bance kiyi min kuka ba Aneesah, ko nima so kika nayi kukan ne," ta girgixa masa kai yace "to ki daina kuka kanwata," bata ce komai ba ta shiga goge hawayen fuskarta, sun kai kusan minti biyar a hka snn a hankali taji yace "don me kika ce baki son Hydar, kuma nasan kina son shi Aneesah" Aneesah ta tsura masa ido bata ce komai ba sae wani sabon hawayen dake gangarowa daga idonta. Ya girgixa mata kai yace "ki kwantar da hankalinki, ni nasan Hydar na sonki kuma xae rike ki amana, kinga dae halin da yake ciki sbda ke bna son wani abu ya sami aminina Aneesah, hka Allah ya kaddara dama ni ba mijinki bne" tunda ya fara magana Aneesah ta tsura masa ido kmr gunki ta kasa cewa komai. Shirun da taji yyi yana kallonta yasa ta fashe da wani matsanancin kuka, ya dago kanta ya ma rasa me xae ce mata, nn da nn shima idonsa ya kada, ya mike da kyar murya can kasa yace "ni bance kiyi min kuka ba Aneesah," [12/8, 21:13] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 114..... Mutuwar tsaye Aneesah tayi daga inda take tsaye, ta kasa ko da kwakkwaran motsi idonta har lkcin na kan Najeeb dake ta faman surutu yana dariya, Abdul ya shigo dakin yana murmushi da fara'arsa ya karaso kusa da Hydar dake binsu da kallo bae ce komai ba, yace "congrat luver guy, ga ka ga Aneesah no more love sickness," Aneesah ta jingina jikin bango ta rumtse idonta cikin tashin hankali, taji kafarta ya kasa daukarta, wayyo ta shiga uku ita kam, bbu wanda ya lura da halin da take ciki kowa da abinda yake cewa, banda Mujaheed dake murmushi kawae, ta bude idonta a hankali ta daura kan Mujaheed dake tsaye gefen gadon, shi din ma kallonta yake yi, suna hada ido ya dauke kansa da sauri, taji wani hawaye mai xafi na bin kuncinta ta girgixa kai tayi hanyar fita daga dakin da sauri, Mujaheed ya bi ta da kallo abun tausayi, Abdul dake kallonsu shima yaji wani iri, suna hada ido da Mujaheed, ya dauke kansa ya karasa kusa da gadon da Hydar yake kwance, ana surutu amma Hydar shiru sae ido da ya xuba masu, da dan damuwa Najeeb yace "A'a wae ya dae ku kira likita naga yaki magana," ganin Hydar yaki ce masu komai sae kallonsu da yake har lkcn yasa Abdul ya karaso kusa da gadon yana kallonsa yace "ya? Kana jin mu kuwa Hydar," Hydar ya sauke ajiyar xuciya yace "ina jinku," snn ya fara kkrin sauka daga kan gadon, Abdul ya rikesa yace "ina kuma xaka," ya dan yatsine fuska yace "4 hw lng nake nn kwance" Najeeb yace "u've been here 4 d past three dayz, sae yau da Aneesah ta xama mallakinka don gulma ka farfado har da ana shirin fita da kai egypt," Hydar yyi shiru yana kallonsa, a hankali cikin wani yanayi me kama da confusion yace "Aneesah" Najeeb yace "yes," Hydar ya dafe kansa na kusan minti biyar snn ya dago yana kallon Mujaheed, Mujaheed bae bari sun hada ido ba, Hydar ya fara kkrin mikewa tsaye ya koma da sauri ta dalilin wani jiri da ya gani, Abdul yace "ya dae," ya koma ya kwanta da ganinsa kasan bae da karfi a hankali yace "baxan iya tashi ba," Mujaheed yace "bari a kira doctor to," ya juya ya fita, Hydar na kallon Najeeb yace "ku gaya min gskya don Allah da gske ne abinda kuke gaya min," Najeeb yace "gskya ne Hydar Aneesah matarka ta sunna ce ynxu," Hydar ya girgixa kai cike da takaici yace "meyasa xakuyi hka, meyasa kuka yi ma Mujaheed hka, bani take so ba shi take so," faruuq yace "Aneesah na sonka dan uwa ka kwantar da hankalinka, hka Allah ya so," Aneesah na fita haraban asibiti taci karo da Hajiya, a rude Hajiya tace "meye kike kuka Aneesah me ya faru kuma" cikin kuka Aneesah tace "wae mumy da gske ya Hydar mijina ne ynxu," Hajiya ta rungumota tace "to meye abun kuka Aneesah ko ba kya son sa ne," cikin kuka ssae tace "ba sona yake ba mumy, don Allah ku taimakeni," da mamaki Hajiya tace "wa yace maki hka Aneesah, ae duk duniya a yanda na lura bbu wanda Hydar yake so bayan ubansa kmr ke," Hajiya ta ja ta suka isa gun mota takira driver ba a jima ba ya xo tace ya kai su gida, har suka isa gida Aneesah bata daina kuka ba, suna fitowa daga mota Aneesah ta tuna lst tym din da ta bar gidan, Hajiyar ta ja ta suka shiga ciki mutanen dake cikin gidan na ta tambayarta ko Aneesah ce amaryar, ta dae yi murmushi tayi masu sannu da gida suka wuce sama da Aneesah ta kai ta dakinta ta xaunar da ita kan gado, ynxu kam Aneesah ta daina kukan da take yi sae na xuciya, Hajiya ta dago kanta tana kallonta tace "kiyi hkuri Aneesah amma don me kika yi tunanin Hydar baya sonki, sbda ke fa ya shiga halin da yake ynxu, shi yace maki baya son ki" Aneesah ta sunkuyar da kanta bata ce komai ba, nn Hajiya ta dinga bata baki tana mata 'yan nasihohi ita dae bata ce komai ba sae hawayen da take, tana dakin hajiya ita kadae bayan sllhn isha tana jujjuya lafiyayyan abincin dake gabanta Wasu mata biyu suka shigo dakin, dayar tace "amaryarmu baki ci abincin bane," Aneesah ta sunkuyar da kanta tace "na ci," matar tace "to sako hijabinki ki fito ana jiranki a waje xaku wuce gida," bata yi musu ba ta sa Hajib ta bi su a baya, ta shiga motar da aka nuna mata, matar ma ta shiga snn driver ya ja motar suka bar gidan, dae dae kofar gidansu drivern ya tsaya suka fito ita da matar suka shiga gidansu, Ammi na xaune daki da wasu 'yan uwanta har uku da makwabta, Aneesah ta fada kan Amminta tana kuka ssae Ammi ta dagota tace "meye hka Aneesah," daya daga makwabtansu ta dagota ta fita da ita daga dakin ta shiga da ita gidanta, ranar Aneesah bata yi baccin kirki ba bayan matar tayi ta mata nasiha ssae game da xamantakewar aure, ita dae jinta kawae take amma ta kasa gaskata wae ynxu ita matar Hydar ce, washegari da safe matar tasa Aneesah ta shirya bayan ta aika yarinyarta ta karbo mata kaya a gida, da kyar ta daure tayi break din da matar ta hada mata, karfe goma saura suka shiga gida gun Ammi har lkcn da mutane cikin gidan nasu, Ammi ta kasa ce ma Aneesah komai sae matan dake dakin ne suka shiga bata baki da yi mata Nasiha, ashe abinda bata sani ba shine ranar xata bar gidansu ta tare gidan mijinta. 9 mins · Khaleesat Haiydar... [12/8, 21:13] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 115... Aneesah ta rasa me ke mata ddi a duniya, ita dae kawae jin abinda ake ce mata take amma bata fahmtar kmai, daga karshe aka dauki sadakinta dubu dari aka mika mata, daga baya xa a kai mta kayan daki dk da hjya tce su bari, ta fashe da kuka tana girgxa kai tana kalln kudin tce ni bana so abn ya ba mutann dake dakin dariya, wata mata tce naki ne wnn Aneesah, Aneesah ta girgixa kai tce na ba Ammina, matan dakin suka yi dariya snn wata tace Ammi dae xata rike maki, amma hakkin ki ne wnn," da kyar Aneesah tabi matar da suka xo jiya da wasu daga 'yan uwan abbanta guda uku suka fita daga gidan tana kuka ssae, duk daurewan Ammi sae da tayi hawaye, gani take kmr ta xalunce Aneesah ta yanke hukunci ita da yan uwanta ba tare da saninta ba, duk da tasan ya cancanci ta ba Hydar Aneesah, don yyi masu abinda 'yan uwansu na jini suka kasa masu a rayuwa, a yanda ta lura kmr Mujaheed take so ba Hydar ba, tausayin 'yar tata ya cikata. Karfe sha biyu suka isa gidansu Hydar, Aneesah ta fito daga mota a sanyaye wata na rike da hannunta suka shiga cikin gidan, mutane ne dayawa cikin falon, hkn yasa matar ta rungumota suka haura sama ta shiga da ita dakin Hajiya, Hajiya ta rungumeta cike da farin ciki ta xaunar da ita kan gado tanai masu sannu da xuwa, mutane nata shigowa ganin amaryar, wata daga kawar Hajiya tace "to Hajiya yaushe ne bikin," Hajiya tace "idan mijin nata yaji sauki ssae" duk suka dinga mata Allah sanya Alkhairi suna yaba kyan Aneesah da kunyarta don takurewa tayi guri daya, karfe biyar saura mutanen dake gidan suka fara raguwa, dakin ya rage daga Aneesah sae wasu mata biyu, aka turo kofan dakin pretty da Ameera suka shigo, Ameera ta sakar ma Aneesah murmushi, pretty kam bata ko kalleta ba ta karaso gabanta tace "sannu amaryarmu," snn ta ajiye farantin dake hannunta, tace "mu je Ameera," Ameera tace "mun gaishe da amaryarmu me kyau sae mun shigo anjima," suka juya suka bar dakin Aneesah ta bisu da kallo a sanyaye, hawayen da take son ji a idonta ma ta neme shi ta rasa, matan dake dakin suka ce ta sauka ta xuba abinci ta ci, bata yi masu musu ba ta xamo kasa daga kan gadon, duk da na daxu ma da aka kawo mata bata cinye ba. Bayan magrib Hajiya tasa ta shirya su kai ma Hydar abinci asibiti, ta shirya cikin wani material mae shegen kyau, ta sa Hajib dinta har kasa, bata yi wani make up ba, driver ya wuce da ita da kanwar Hajiya xuwa asibiti, a sanyaye gabanta na faduwa ta dinga bin matar da taji ake cema Anty farida xuwa ward din da Hydar yake, faridar ta riga ta shiga cikin dakin, ta shigo ita ma da sallamarta murya can kasa kasa, yana kwance amma idonsa biyu, ya rame ssae ba kadan ba, najeeb da wasu abokansa biyu na xaune cikin dakin, suna ganin Aneesah suka fara tsokanarta suna dariya, hkn yasa taji kmr ta fasa ihu ta saka masu kuka, hawaye ya cika idonta amma bata bari kowa ya lura ba,hydar kam dauke kansa yyi bayan ya gaida Anty farida dake ta dariya tana biye masu ta hanyr kare ma Aneesah, su ma bakinsu bae mutu ba su ka dai gama haukansu suka bar dakin suna dariya, Anty farida tace "da ku tsaya mana" sae a snn ta kalle Aneesah dake tsaye tace "A'a amaryarmu baki xauna ba," Aneesah ta kirkiro murmushi ta ja kujera ta xauna, Anty farida ta mike tsaye tace bari xan je siyo kati na dawo, tana fadin hka ta fice dakin ya rage daga Aneesah sae Hydar, ganin sun kai minti kusan biyar a hka yasa ta daure da kyar muryarta na rawa tace "ya jikin," sae da ya dan yi shiru snn taji yace "da sauki," ta daga kai tana kallonsa taga kallonta yake, ta sunkuyar da kanta da sauri tace "in xuba maka abincin?" ya girgixa mata kai yace "aa sae dae in ke xaki ci ki xuba," tayi shiru bata sake cewa komai ba, shima hka, kowa da tunanin da yake yi a xuciyarsa, a hankali taji yace "dan bani ruwan can," ta mike ta dauki ruwan ta bude ta dan dauraye kofin snn ta xuba masa ta karasa kusa da gadon tana mika masa, ganin bae karba ba yasa ta daga kai tana kallonsa ya sauke idonsa da sauri daga kallon da yake mata, ya mika hannu ta sakar masa ruwan ba tare da tasan bae rike ba, ruwan ya fada kansa yyi saurin daga kofin ta shiga goge masa ruwan a rude tana cewa wllh ban sani ba, ya kamo hannunta yana kallonta, wani iri taji daga saman kanta xuwa kasa, ta janye hannunta da sauri, yace "ba komai ba fault dinki bane," ta gyada masa kai ta koma xata xauna yace "plss ki je waje ki karbo min wayana gun Najeeb, xan kira mum xasu kawo min abu," ta juya da sauri ta fice daga dakin, ya dafe kansa da yyi masa nauyi, me yasa ya kasa daina jin haushin Aneesah, da ya tuna abinda pretty ta gaya masa sae yaji wani xaxxabi na neman rufesa, ya koma ya kwanta da sauri tare da lumshe idonsa baya son yana irin tunanin da yake a kanta, Aneesah kam na fita daga nisa ta hango Mujaheed ae kam ba sae an gaya mata ba tasan yanda Mujaheed ke tafiya, ta karaso da saurinta kmr mai shirin fadawa kansa cikin wani yanayi tace "ya Mujaheed," ya koma baya da sauri ganin fadowa xata yi kansa cikin dan tsawa yace "baki da hnkli ne?" [12/8, 21:13] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 116..... Aneesah ta koma baya a sanyaye tana kallonsa, ya sakar mata murmushi yace "ya kike amaryarmu," ta juya da sauri hawaye cike idonta, jin shirun da tayi bae kuma cewa komai ba yasa ta juya a hankali taga wajen wayam ba kowa, ta fashe da kuka ssae ta samu wani dakali ta xauna ta hade kanta da gwiwa, tana nn a hka su Najeeb suka xo suka wuce ba tare da sun lura da ita ba, bayan kmr awa daya suka fito gaba daya har da Mujaheed suka shiga motarsa suka bar asibitin, ta mike da kyar tana goge hawayenta ta shiga ciki a sanyaye, xaune ta tarda shi da abokinsa doctor yana masa hira, doctorn na ganinta yace "to bari in koma office tunda amarya ta dawo," Hydar yyi murmushi yace "ngdd frnd," likitan ya fita daga dakin yana dariya, Aneesah ta nemi kujera ta xauna ba tare da ta kallesa ba, shi ma bae ce mata komai ba, bayan kmr minti goma taji ya kirata, ta amsa ba tare da ta kallesa ba, yace "ki kwantar da hankalinki , xanyi free din ki vry soon," ta dago tana kallonsa tace "kmr ya?" ya kauda kansa yace "nasan baki sona Aneesah, kuma ba tare da knowledge dinki da nawa ba aka daura mana aure, kar ki damu xan sauwake maki," a hankali Aneesah tace "ni bance bana sonka ba, kawae dae...." sae kuma maganar ya makale sae kuka, yace "ni bance kiyi min kuka ba Aneesah, dnt wrry xan baki takardar ki sae ki aura wanda kike so, idan ma ba auren xa kiyi ynxu ba sae ki ci gaba da karatunki," bata sake ce masa komai ba ita ma hka, bayan kusan minti ashirin ba tare da ta kallesa ba tace "Anty bata dawo ba," ya dan yi shiru snn yace "ta kirani wae ta wuce gida," hankalin Aneesah ya tashi, ynxu suna nufin nn xata kwana, bata dae ce masa komai ba ta ci gaba da kallonta, wajen karfe goma ta fara bacci kan kujeran da take taji mutum a gabanta ta farka a firgice har tana neman faduwa ya rikota da sauri ya nuna mata spare gadon dake dakin yace "tashi kije ki kwanta," ta mike tsaye bata ce komai ba ta koma baya tana kallonsa, ya koma yyi kwanciyarsa, bae sake cemata komai ba har sae da taga dama don kanta snn taje ta kwanta. Cikin kwanaki ukun da suka yi a asibiti Aneesah dari dari take da Hydar, ita dae don dole take xaune a asibitin, shi ko a rana bae fi yyi mata magana sau uku ba, baya shiga harkanta kmr yanda ita ma bata shiga tasa, ynxu kam jikinsa da sauki sae dae har lkcn baya iya ddewa a tsaye, duk abinda tasan ya kamata tana yi masa ba tare da ta kallesa ba, shi dae sae dae yyi ta bin ta da kallo, har ranar mujaheed bae sake dawowa asibitin ba, Abdul dae na xuwa lkci lkci yana dubasa, hka ma Mudatheer da ta mayar babban yayanta don tana ji da shi ba kadan ba, shi kam faruuq ya koma katsina, taji kewansa ssae don faruuq na da mutunci ssae, a kwanakinsu na biyar a asibiti aka sallamesu, Hajiya murna gunta ba a magana ganin yanda jikin Hydar yyi sauki ssae kmr ba shi take tunanin xae mutu ya barta ba kwanaki, taji ta kara jin son Aneesah a xuciyarta, Aneesah na ta xuba ido taga inda xa a kaita taga sun koma gidansu Hydar, taji kmr ta kwala masu ihu don ita gun Amminta kawae take son wucewa, Hajiya ta sa Pretty ta gyara ma Hydar dakinsa dama kafin su iso, Aneesah ta takure kanta kujera bayan sun shigo falo, ana ta hirar farin ciki da Hajiyar da mum din Mujaheed sae mutanen da suka xo taya ta murna, Hajiya ta lura da Aneesah tace "lah nn kika xauna Aneesah," Aneesah ta kirkiro murmushi ta sunkuyar da kanta bata ce komai ba, Hajiyar tace "to ga fura can kan dinnin ki kai maku daki ke da Hydar," bata yi mata musu ba ta mike taje ta dauki furan ta wuce sama da shi amma ta kasa shiga dakinsa, sae da tayi kusan minti biyar a tsaye ba shiri tayi saurin bude kofar dakin jin pretty ta bude dakinta alamar xata fito, dae dae lkcn da shima ke fitowa daga bathroom daure da towel, ta juya da sauri a gigice kmr warce taga dodo suka yi ido hudu da pretty da ke shirin sauka downstairs don a bude aneesah ta bar kofar dama, pretty ta dauke kanta da sauri tayi gaba abunta, Aneesah ta kasa fita daga dakin kuma ta kasa juyowa ta koma ciki, ga hawayen da taji na neman cika mata ido, sunanta taji Hydar ya kira a hankali ta juyo ba tare da ta kallesa ba ta Ajiye masa farantin dake hannunta, taji ya bude drawer ta daga kai tana kallonsa ynxu kam jallabiya ce jikinsa, ya ciro paper da pen yana kallonta yace "ki karaso ciki," a sanyaye gabanta na faduwa ta karasa cikin dakin ya nuna mata kujera ta xaune, shi kuma ya xauna kan gado ya jawo kujeran dressin mirror ya daura takardar a kai yana kallonta, ita ma kallonsa take taga ya daura pen din kan takardar ya fara rubutu kmr haka; Ni Aliyu...... Lah!! Wayyo ni khaleesah @kuka da shessheka,,, ynxu Aneesah da gske kike baxa ki hakura ba ki xauna da Babana. [12/8, 21:13] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 116..... "Ni Aliyu na......" da sauri Aneesah ta rike pen din a tsorace muryarta na rawa tace "me xa kayi ya Hydar?" ya dago kai yana kallonta yace "takardarki xan baki Aneesah hkn shi xae fi mana alkhairi daga ni har ke," ta fashe da kuka tace "dn Allah ka bari ya Hydar wllh ina sonka karka min hka," a gigice take maganar, ya girgixa mata kai cikin yanayi mai ban tausayi yace "baki sona Aneesah wanda kike so daban, dis is d only best option 4 us, bana son na fiye son kaina dayawa, ki bari na sauwake maki ki aura wanda kike so," Aneesah ta rungumesa hade da kankamesa tana kuka ssae da kyar tace "wllh ina sonka ya Hydar, kunyar ya Mujaheed nake ji don yyi min abinda baxan iya manta shi a rayuwa ba, kai daban ne a xuciyata ya Hydar, don Allah karka sakeni," kuka ssae take rungume da shi, ya daura fuskansa a kanta a hankali yace "ki bari kiyi rayuwarki da Mujaheed kawae, don shi yafi cancanta ba ni ba," ta kankamesa kmr xata shige jikinsa tace "wllh kaine ya Hydar, ina sonka ina sonka yayana," ta fashe da wani matsanancin kuka ya dago kanta a hankali yana kallonta, da kyar ya iya ce mata ya isa hka Aneesah, ta kwantar da kanta kan kirjinsa ta fara sassauta kukan da take yi sae ajiyar xuciya, sun kai minti goma a hka tana jikinsa, snn ya dago kanta yana kallonta, ta lumshe idanunta, shima hkn yyi snn ya daura bakinsa kan nata a hankali, ta bude idonta a tsorace, shima ya bude idonsa, ba shiri ta rufe nata ya shiga kissin dinta, duk a tsorace take ssae, xata turasa ya riga ta, don turata yyi da sauri ya mike, ya shige bathroom tabi sa da kallon mmki. Tana nn ynda ya barta ya fito daga bathroom ya fita dakin ba tare da ya kalleta ba, ta xamo daga kan gadon a sanyaye ta xauna kasa, bayan kusan minti talatin ya dawo dakin, har lkcn tana xaune kan tile ta ma rasa wani irin tunani xata yi duk jikinta ya mutu, yana kallonta yace "kinci abinci kuwa Aneesah," ta sunkuyar da kanta bata ce komai ba ya karaso gabanta ya durkusa yana kallonta. [12/8, 21:13] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 117..... Yau Aneesah ta cika sati biyu gidansu Hydar, duk da irin son da Hajiya ke nuna mata ta kasa sakewa, gun Amminta kawae take so a mayar da ita duk da kusan kullum sae Hydar ya bata waya su gaisa, pretty kadae ce bata wani sake mata don tsakaninsu sae gaisuwa, Ameera kanwar Mujaheed ma na gidan ita kadae ke yini gun Aneesah a daki don bata fiye saukowa kasa ba, Meenah dae na can India ta fara samun sauki mum din Mujaheed ne a gunta da wasu 'yan uwan Hajiya, duk irin kulan da Hydar ke ba Aneesah ko sau daya bae taba barin sun kwana gado daya ba ko kuma ya xauna kusa da ita, duk da daki daya suke kwana sae dae yyi kwanciyarsa kan kujera, Aneesah kam hkn ma da yake yi yafi mata ddi. Ran da ta cika sati uku a gidan Mujaheed ya xo da Abdul da suka kulla abokantaka ssae, Aneesah na sama, Hydar kuma na dakin pretty yana danna laptop da yake ranar lahadi ne, Hajiya ta shigo tace masa su Mujaheed sun xo ya sauko downstairs yaji ddin ganinsu ssae pretty ta bude fridge ta dauko lemo da ruwa ta ajiye masu tana gaida Abdul, Mujaheed yyi tsaki yana kallonta yace "to dae bakiyi kyau ba kin xo kina ma mutane wani fari da ido, a kai kasuwa yarinya," ta galla masa wani mugun harara ta haura sama abunta, Abdul ya dinga dariya, Hydar yace "ban fa son cin fuska Mujaheed, pretty tafi karfin rashin mutuncin ka," Mujaheed yyi dariya yace oho dae ina kanwata?" Hydar ya dan dauke kansa yace "tana sama," dai dai nn Ameera ta shigo gidan sanye da Hijab dinta har kasa, ta wara ido tace "lah yayana," Mujaheed yyi murmushi yace "dama baki nn," tace "ina garden wllh," ta karaso cikin falon ta xauna tana kallon Abdul tace "ina yini?" ya gyada mata kai, snn ta gaida yayanta, Hydar ya mike ya haura sama ba a jima ba ya sauko tare da Aneesah, tayi mamakin ganin Mujaheed ta dae karaso cikin falon ta xauna ta kirkiro murmushi ta gaishesu gaba daya, duk suka amsa da fara'arsu shi dai mujaheed tun da ya kalleta sau daya bae sake kallonta ba yana ta surutu, ana ta hira amma Aneesah tayi shiru sae dae tayi murmushi, Ameera dae jefi jefi take magana, Mujaheed yace "wae yaushe xaku tare ne Hydar naga kun xo kun jabe ma Hajiya a gida, kuma yaushe xa ayi biki, ni dae ina ta xuba ido shiru," Hydar yyi murmushi yace "sae Ameena ta samu lfya," Mujaheed yace "ohh hka ne fa, to tarewan fa?" Hydar yace "Hajiya tace sae ta gama hada mata akwatunanta na lefe,nn da sati biyu ma xata koma dubai da wata kawarta sae ta bar mata kayan ta taho dasu daga can ita ta wuce India" Mujaheed yce "to Allah ya taimaka muma dae mun kusa angwancewa" duk suka yi dariya daga karshe Abdul ya kalli Aneesah yace "dauki permission gun mijinki ki xo muyi magana kanwata," ta kalli Hydar dake murmushi yace "je ki mana ni na isa na hanaki xuwa gun yayanki," ta kirkiro murmushi ta fita, yana xaune kan kujera a balcony, ita ma ta xauna kan kujera tana kallonsa yace "kin san me nake so dake Aneesah?" ta girgixa masa kai yace "ynxu ke matar aure ce Aneesah 4get about ur past lyf nd face reality, Allah ya riga da ya kaddara Hydar ne mijinki, ki manta kin taba soyayya da ko wani da na miji kiyi facin din marriage lyf dinki, ki bi duk wa inda suka taimake ki a rayuwa da addu'a datz ol," ta gyada masa kai tana kkrin boye hawayen idonta, yace "yauwa kanwata ki cire komai a ranki ki rungumi mijinki," a hankali tace "ta yayana," yyi murmushi ya mike tsaye sae ga Mujaheed ya fito yace "wani gulman kuke yi da kanwartaka ga mijinta can ya cika fam," Abdul yyi dariya yace "ae kuma sae dae ya fashe," Mujaheed yyi dariya yana kallon Aneesah yace "kai kinga yanda kika yi kyau kuwa kanwata, lallai abokina ya iya kiwo, kai ko dae mun samu bby ne" kunya ya rufe Aneesah kmr xa tayi kuka tace "kai yayana bana son hka ni yaushe aka haifeni," duk suka yi dariya ssae banda Hydar da ya kauda kansa, tace "amma yayana da gske nayi kyau banda cin fuska fa" yyi dariya yace "ehh to amma duk kyan naki baki kai matata ba," yana fadin hka ya juya yana hararan pretty dake tsaye tana kallonsu, duk suka yi dariya Aneesah tace "ni na isa nace nafi matarka kyau yayana," Mujaheed yace "gwara dae da kika tuna hka," tayi dariya ta juya xata koma ciki tace "to yayyina mun gode 4 d visit, Allah bar xumunci," duk suka ce Ameen suna tsokanarta ta juya ta shige ciki da sauri tana dariya Abdul yana kalln Mujaheed yace "kai wllh kanwarka kauyancinta yyi yawa, ko raka mutane ma bata iyaba ta wani labe a falo hba, Mujaheed ya hararesa yace "kar dae kaxo kana durkusa min gwiwowi bibbiyu a kasa akan na baka Amira, dk ka bi kasa ma yarinya ido to baxan baka ba don na gano ka" Mujaheed na fadin hka ya juya yyi gaba yana dariya, Hydar ma dariyar yake, Abdul ya wara ido yana kallonsu ya ma rasa me xae ce. Hajiya na ta shirin xuwa dubai cikin satin nn hado lefen Aneesah, sae kuma ga Mujaheed ma ya bata kudi ta siyo masa duk abinda xata hada ma Aneesah, na matarsa Hajiya taji ddi ssae ganin shima yyi hankali xae yi auren at lng lst, Aneesah sae taji duk ba ddi tafiyan da Hajiyar xata yi. [12/8, 21:13] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 118..... Ana gobe Hajiya xata tafi, tace ma Hydar ya kai Aneesah gida ta gaida Ammi, Aneesah taji ddi ssae don ba karamin kewar Amminta take ba, tare da pretty suka je, tayi mamakin ganin inda Hydar ya kawosu xata yi magana ya riga ta ta hanyar cewa "Mujaheed ne ya maido ta nn few wks ago srry ban gaya maki ba," Aneesah bata ce komai ba suka shiga gidan, suka tar da wata frnd din Ammi ce kawae a ciki, taji ddin ganinsu ta kawo masu ruwa da lemo tana yi tana kallon Aneesah da ta canxa mata, Hydar yace "Ammi fa" matar tace "ta fita kasuwa ba ddewa xata yi ba ynxun nn xata dawo," mintinansu goma a gidan Ammi ta shigo, Aneesah ta rungumeta don farin ciki har da hawayenta, Hydar yyi mata sannu da xuwa hka ma pretty ta amsa masu da fara'arta tana tambayarsu Hajiya da jikin meenah, ta karaso cikin falon ta xauna, Aneesah ta so su xauna daga ita sae Amminta su ji ddin hiransu amma ba dama don Ammi bata shiga daki ba bare ta bi ta, har lkcn tana falo a xaune suna ta hira da su Hydar, karfe daya matar da ta taresu ta kawo masu Abinci, Ammi tayi mata gdya don ta taimaka mata, sae a snn Ammi ta shiga daki, Aneesah ta mike da sauri ta bi ta, Ammi tace "meye hka? Aa ki koma abunki bana son gulma," Aneesah tayi kmr xatayi kuka tace "hira fa xamuyi Ammi," Ammi tace " wanda muke yi a falo fa? Kije idan kun gama cin abincin na xo falon muyi," Aneesah taji haushin hkn ssae amma bata ce ma Ammi komai ba ta koma falo, ba su suka bar gidan ba sae kusan karfe hudu saura Aneesah taji haushi ssae don bata gana da Amminta ba hkn yasa bata ga amfanin xuwan nata ba, kawar Amminta da take kira da maman fatee ce ta kirata daki, ta bi ta, ta bata abubuwan da tasan ya kamata ta bata ta sha, da kyar Aneesah ta shanye na karshen da ta bata a kofi tace "meye wnn maman fatee," matar tace "magani ne," ta ciro wasu turarruka ta mika mata kus [3:37PM, 12/23/2016] Khaleesat: [12/8, 21:11] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar. 67..... A fusace Mujaheed yace "look ni fa kayi save din tym dina Aliyu, wnn ae wlknci ne da rainin hankali, dama Hajiya ta gya min irin taurin kan da kayi har ya kawo ka nn, ynxu xaman ka a nn kafi so ko me? Ana neman hanyar da xa a fito da kai daga kurkukun nn kana neman hanyar da xae xaunar da kai a ciki, haba act maturely mana Guy," Haydar yyi murmushi yace "ni abu daya xae sa naji sha'awar fito wa nn, kuma shine ace yau nasan inda Aneesah take naje na daukota, bayan hka kuma nasa baffanta ya ji baya sha'awar cin dukiyar marayu har karshen rayuwarsa" Mujaheed ya dan wara ido da mamaki yace "wacece Aneesah kuma," Haydar yace "ita ce yarinyar da ku ke kira da yar aiki, ni ko tafi karfin hka a wajena," Mujaheed ya yatsine fuska yace "Aneesah kuma?" Haydar yace "yea sunanta knn, suna xaune da mahaifiyarta a suleja, marainiya ce, sun tashi cikin kuncin rayuwa tun bayan rasuwar mahaifinta yrs bck, yayansa bae bar masu komai daga cikin abinda mahaifinsu ya bari ba hkn yasa suka tashi cikin talauci, shine kuma dalilin da yasa Aneesah ta fara aiki a gidanmu months bck, it happened dat naje na samesa bayan na tilasta mata na gano dalilin talaucin nasu na nuna masa cewa xanyi sue dinsa idan bae mayar masu da dukiyar mahaifinsu, 2dayz ltr ya dauke Aneesah ya sa aka yi arrestn dina wae na sace masa yar sa," Haydar yy dariya har da buga kafa yce "ina tausayin mutumin nn ran da xan fito daga hell din nn," Mujaheed ya share xufar dake keto masa ba kakkautawa ya dafe kansa batare da ya sani ba yce "Aneesah kuma" haydar ya dago yana kallnsa yce "ya dae" da sauri Mujaheed yace "no ina mamakin lamarin ne," ya dafe kansa yana tunanin lbrin da Aneesah ta basa, amma ai bata ce masa ta yi aikatau ba, kuma da ita ce wanda Amininsa yke fadi ynxu baxa ta rasa basa lbrin Haydar ba ko kadan ne, no ba ma ita bace haydar ke fadi, yyi assure din kansa. To amma ae suleja wnn ma take, mujaheed ya rasa ma tunanin da xae yi duk ya bi yyi confuse kan lamarin.. Like · 9 · Reply · Report · 52 minutes ago [12/8, 21:11] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 67..... Aneesah tace "eh Gombe," ya harareta yace "ina ne kuma gombe?" ta mike xata bar wajen ba tare da ta ce masa komai ba ya fixgota ya xaunar yana mata wani irin kallo yace "ina maki magana xaki wuce" kasa ce masa komai tayi don takaici, yyi murmushi ya sakale hannu a wuyarta yace "baxa ki min magana ba," hawaye ya ga a idonta nn da nn ya rikice, "kuka kike yi Aneesah, me yasa ki kuka?" ta turasa cike da jin haushi tace "nace maka gobe xan tafi gombe," ya tabe baki yace "in kin ga kin bar gidan nn to Amminki ta dawo garin nn ne, ko so kike baffan ki ya sami information ya kuma mayar dake wani gun kuma daban," ta fashe da kuka tace "to yaushe Ammina xata dawo, ni na gaji da ma ka maida ni inda ka dauko ni har lkcn da xa ta dawo sae ka je ka dauko ni kuma," Mujaheed bai ce mata komai ba ya mike yyi hanyar stairs ta bi sa da kallo kmr ta fasa ihu, sae da ya hau matakala biyu snn ya juyo yana kallonta yace "ki gyara falon nn, snn ki wuce kije ki kwanta nd stop day dreamin gobe da inda xamu as early as possible," yana kai wa nn ya haye sama, ta fashe da kuka tace "bbu inda xani wllh," sae da taci kukanta mai isarta snn ta mike ba tare da ta bi ta kan plates din abincin da suka ci ba da cups ta haye sama ta shige daki ta kulle. Wa shegari tana idar da sllh ta wanke baki tayi wanka snn ta gyara daki, har ta kwanta ta tuna abinda ya sa ta jiya, ta bude kofar dakin a hankali don bata son ya sauka yaga bata yi ba, a hankali ta sauko falon ta tar da shi yana moppin, kunya ya sa taji kmr ta nutse ba dan ya ganta ba da ta juya da sauri ta koma, ya tabe baki yace "u felt guilty shi yasa kika sauko da asuba ko?" bata ce komai ba ta karaso falon ba tare da ta kallesa ba tace "kawo in yi," ya girgixa kai yace "no ki barshi na iya," tace "kayi hkuri jiya bacci nayi ban sani ba," ya harareta yace "ae naga alama, c'mon xo ki karba abun nn a hannuna" taki karasawa kusa da shi don tsoransa take, barin ynxu da singlet da 3qtre ce jikinsa, tace "ka bar shi a nn ka wuce, xan yi" yace "sbda xan cinye ki idan kika karaso ko" ta tsura ma faffadan kirjinsa da ke bata tsoro ido, ta dan marairaice tace "ni wllh baxan xo ba," ta juya da sauri ta fara hawa sama, ya ajiye mop din ya bi ta, tana ganin hka ta fasa ihu da gudu ta afka daki don tsabar rudewa ma ta kasa kulle dakin da makullin. Bae shigo dakin ba taji ya shige tasa dakin, jikinta na rawa ta sa ma kofar key, karfe bakwae taji ya fito daga dakinsa, ya kwankwasa kofar dakin yace "ki shirya ki fito ina jiranki" da sauri tace "ina xa mu?" sae da ya danyi shiru snn yace "ki dae fito ina jiranki," ta girgixa kai kmr yana ganinta tace "A'a ni baxan je ba," har ta tsamman ya wuce jin shiru na kusan minti biyar sae kuma taji yace "to yyi, ki dae tabbatar kin ci abinci kar ki tsaya da yunwa," tace "tam," tana jin fitar motarsa ta bude kofa ta sauko kasa, mop din na nn yanda ya bar shi daxu, tayi murmushi a xuciyarta tace "hka kawae naje ka rungumeni ba riga," cikin minti talatin ta gama gyaran ko ina na falon snn ta dan hada break din da xata ci ta wuce sama da shi. Karfe tara saura Mujaheed ya isa gidan yarin da Hydar yake, bae samu wahalan ganinsa ba bayan ya nuna masu identity card dinsa, yana xaune a dan wani daki yana jiran Haydar din, guards kusan uku suka shigo tare da shi, Haydar yyi murmushi ganin Mujaheed yace "prince yaushe ka shigo gari?" Mujaheed yyi tsaki yana girgixa kai yace "just take a look at ur sef, dubi halin da 'yar aiki ta saka ka ana xaune kalau, wllh Aliyu ka ban mamaki kuma ka ban kunya," nn da nn Haydar ya hade rae yace "uban wa yace maka yar aiki ce ita, idan abinda ya kawo ka knn malam ka kama hanyar ka bna son wlknci," Mujaheed ya tabe baki ya ciro wata 'yar karamar recorder yace "whatever, ka bani bayanin duk abinda ya faru tun daga farko in details ynxu, kuma kar ka boye min komai frnd" Haydar yace "me kke son sani?" Mujaheed yace "ina son sanin wacece yarinyar kuma me yasa aka maka wnn sharrin, waye kuma ubanta a Abuja, kuma a yanda Hajiya ke ban lbrin uban nata nayi mamakin me ya kai ta aiki gidanku, tambayar da umar ya kamata yyi fire dinsu da tun farko knn ya kasa, snn ka bani Address dinsu tunda na samu lbrin har gidansu kke xuwa" Haydar yyi murmushi yace "ka kyaleni da wa in nan tambayoyin Mujaheed, wat i only want u 2 have in mind ix dat baffanta ne ya dauketa," Like · Reply · Report · 3 minutes ago [12/8, 21:11] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar. 68...... Haydar ya dafa kafadar Mujaheed ganin halin da ya shiga lkci daya yace "ya dae Amini naga mood dinka ya canxa," Mujaheed ya kirkiro murmushin dole yace "lamarin ne da rikitarwa Haydar, amma kar ka damu everythin wil go smoothly," Hydar ya daga kafada yace "wat ever, ni dae da xa ka min favour daya da na baka address din gidansu Aneesah kaje min gun mum din ta, but kar ka bari Hajiya ta san da hka, don ni ban san irin xuciyarta ba," Mujaheed ya share xufar da ke keto masa ya ce "kaga lkcin da aka ba mu ya cika, ka bari gobe idan na dawo xamu yi magana," yana gama fadin hka ya fice da sauri kmr wanda ake hankadawa, Hydar ya bi sa da kallon mamaki, guard din daxu suka shigo suka tafi da shi. Da kyar Mujaheed ya iya drivin ya isa gida, a waje yyi parkin ya shiga cikin gidan mai gadi na gaishesa bae ma san yana yi ba, da sauri ya shiga falo, bbu kowa cikinta, ya haura sama ya bude bedroom din da Aneesah take bbu kowa cikin dakin amma kamshin sabulun da ya ji ya sa ya gane wanka take, ya xauna gefen gado ransa a jagule, ya dafe kansa, bayan kmr minti goma Aneesah ta fito daure da towel don gown ta sa da safe, bata lura da Mujaheed dake xaune dakin ba, ya tsura mata ido yana mata kallon sama xuwa kasa, tana goge gashinta da karamin towel ta karasa gaban madubi, ta Madubin ta ga Mujaheed da ya kasa daina kallon kyakkyawan fatar jikinta, ta fasa wani raxananen ihu ta durkushe wajen a tsorace tana salati, ya mike tsaye ya karasa gabanta, kuka ta dinga yi a gigice tana rokansa don Allah ya rufa mata asiri ya fita, bae damu da irin kukan da take ba ya dagota jikinta ya dau bari sae hawaye take ta kasa cewa komai, ya xaunar da ita gefen gado yana kallonta yace "Aneesah me yasa baki da gskya ne?" gabanta na faduwa murya na rawa tace "ni" ya rumtse ido yace "meyasa baki gaya min kinyi aiki a wani gida ba nn Abuja da na bukaci ki ban lbrin ki," Aneesah tayi shiru har lkcn gabanta na faduwa yace "magana nake maki Aneesah" ta share hawayen idonta tace "sbda naga its of no use, ko ka sani ko kar ka sani, amma wa ya gaya maka nayi aiki" ya dan yi shiru kmr me tunanin abinda xae ce snn yace "daga anguwarku nake gun neighbour din nn taku naje karban more information, ita ce ta gaya min," ya daura hannunsa kan kafadunta, kmr xae yi magana sae kuma ya kasa, ta fara ja da baya ganin daga ita sae towel, ya tallabo kanta da hannunsa biyu da kyar yace "ina xa ki," a hankali tana kuka tace "kayi hkuri ka fita ina son na sa kaya ne," ya girgixa kai idonsa ya kada yyi jajir a hankali taji yace "i love yhu Aneesah, i love yhu, ki soni plss" bae jira mae xata ce ba ya rungumeta hade da kankameta, kuka ta shiga yi ta kasa ce masa komai, a kunnen ta taji yana cewa "ki fada min gskya Aneesah, akwae wanda kike so a xuciyarki ko" ta girgixa masa kai da kyar, yace "tok 2 me plss ki fada min gskya," muryarta na rawa tace "A'a ni ba ni da wanda nake so a xuciyata sae..." da sauri ya katse ta yace "sae wa Aneesah" a hankali tana kuka tace "Ammina," ya kankameta yace "ki gaya min tsakaninki da Allah Aneesah," tana kuka tace "Allah," yace "akwae wanda ya taba taimakon ki a rayuwa Aneesah?" tana kuka ta gyada masa kai, da sauri yace "waye shi Aneesah," a hankali tace "ya Haydar," a hankali taji ya sassauta rikon da yyi mata murya can kasa yace "son ki yake knn" ta girgixa kai da sauri tace "A'a, yayana ne bae ce yana sona ba, kawae taimakonmu yake ni da Ammina, a gidansu nayi aiki, yana da kirki ssae," Mujaheed ya rumtse idonsa yace "tsakaninki da Allah ba sonki yake ba Aneesah," ta girgixa masa kai tace "bae taba cewa yana sona ba, kuma ni a matsayin yayana na dauke shi," Mujaheed bae sake cewa komai ba ya dago kanta yana kallon cikin idonta, ita ma kallon nasa take, ya lumshe idonsa ya bude, har lkcin idonta na kan fuskarsa, ta ga ya sa hannu ya rufe idonta, bata ankara ba taji bakinsa kan nata, ta shiga tura hannunsa da sauri daga idonta, kin cire hannun yyi har sae da yyi mata light kiss snn ya mike ya bar dakin, ta bisa da kallo tana hawaye, ya kullo kofar dakin, da kyar ta tashi ta dauki kaya xata sa don dama period ne ya sa ta wanka don tayi da safe. Mujaheed kam through out ranan kasa sukuni yyi, ba dan Hydar amininsa bne da bbu abinda xae sa ya shiga case din nn, don no matter wat bai jin xae iya rabuwa da Aneesah, lkci daya sonta mai karfi ya shigesa, da kyar ya iya xuwa siyo masu lunch don har lkcn Aneesah bata fito ba, yana dawo wa ya bude dakin ya ajiye mata abincin a bakin kofa [truncated by WhatsApp] [12/8, 21:11] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 70...... Mujaheed ya mike yana kallon Aneesah yace "sae na dawo kanwata," ta bi sa da kallo har ya fita daga falon, tana jin tashin motarsa ta fashe da kuka don a tunaninta laifi tayi masa. Sha daya saura Mujaheed ya isa prison din, yau ma kmr jiya bae sha wahalan ganin Haydar ba, Haydar yyi murmushi ganinsa yace "nayi xaton baxa ka xo ba" Mujaheed ya dan yi murmushi yace "ni na isa, yaushe ne ma xa a sake xama a kotu?" Haydar yace nn da sati daya, in baka Address din gidansu yarinyar ynxu, Mujaheed yace "A'a ba sae ka ban ba, just dnt wrry baxa ka wuce sati ba a nn," ynxu dae ka amsa min duk tambayoyin da xan maka, nn dae Mujaheed yyi gather din informations din da ya kamata yyi sallama da Haydar, Haydar yace "so early?" Mujaheed yyi murmushi yace "bana son nayi missin juma'ah," Haydar yace gskya ne amma kai ko dan irin fruits din nn baxa ka iya siyo ma mutum ka kawo ba, Hajiya ta daina kawo min hasali ma haushina take ji, Mujaheed yyi dariya yace "ni tastin din nn da xa ace sae mutum yyi ne ke kona min rae, but nxt tym" yana kai wa nn yyi masa sallama. Karfe biyu Mujaheed ya isa gida, bbu kowa falon sae kamshin dake tashi, ya haura sama ya shiga dakinsa yyi wanka snn ya sa kananan kaya ya fito, yyi sllma ya bude dakin da Aneesah take, bbu kowa ciki, ya sauko yyi hanyar kitchen nn ma bae ga kowa ba, ya fara kalle kallen falon, ya fita da sauri yyi gun maigadi yace "yarinyar nn ta fita ne?" mai gadi yace "A'a tana ciki duk yau ma bn ganta ba ni," Mujaheed ya koma ciki ya shiga neman ta ta ko ina amma bae ganta ba, mamaki ya cika shi ya fita yyi hanyar garden, tana xaune tana karatun Novel, ya sauke ajiyar xuciya yana kallonta, ta juya da sauri tana kallonsa tace "sannu da dawowo," yyi murmushi yace "kin ban wahala kinsa ina ta nemanki kanwata," ita ma tayi murmushin tace "na gaji da xama cikin gida ni kadae ne," yace "hmm gskya ne," xo ki ga wani abu ta mike tsaye tana kallonsa tace "me xan gani," ya kamo hannunta xa su bar garden din ta dawo da sauri tace "yauwa yayana kai ne ke daga weight din can?" ta fada tana nuna masa inda weight din suke, yyi murmushi yace "ke ce" ta xaro ido tace "kai amma kana kkri wllh, " yace "in kika yi wasa ba sae na daga ki da hannu daya ba ynxu a nn," tayi dariya tace "xaka iya da gske?" bata ankara ba taji hannunsa daya a cikinta ya daga ta sama, ta fasa ihu a tsorace hkn yasa ta kusa faduwa ya rungumota da sauri suka fada kasa, a tsorace tace "wayyo Allahna," ya dinga dariya yace "ko na sake ne," tace "A'a don Allah kayi hkuri," ya mike tsaye ya daga ta sama da hannu biyu, snn ya sauketa kasa, har lkcn jikinta rawa yake, yana dariya ya ja ta xuwa gun weight din ya daga sama da hannu daya yace xo ki karba na gani, ta juya da sauri tace "ni ba ruwana," ya bi ta yana dariya suka shiga gidan tace "yayana nayi maka girki," yace "da gske bbyna," tace "Allah," ya ja ta suka yi dinning din, ya ga lafiyayyan jollof din da tayi masa yace "waw kanwata ngd," a tare suka ci abincin snn suka dawo parlor ya fara danne dannen laptop, ta tsura masa ido tana kallonsa, ya dago kansa yace "yadae wnn kallon kanwata" tayi murmushi tace "sbda kana daga weight shi yasa muscles dinka suka yi hka ko," yyi murmushi bae ce komai ba, tace "amma kana da karfi ssae," ya kalleta yace "xo ki ji" ta mike tace "naki," ta haye sama da sauri, yyi dariya yace "da kin gane kuranki," washegari da yamma mujaheed ya tilasta mata ta shirya suka fita xuwa shoppn don da ca tayi baxata ba, ta kusa gama siyayyan da xata yi su ka ci karo da wani katon mutum, biscuit din da ta dauka ya fadi shima abun hannunsa ya fadi, ta durkusa da sauri ta dauki nata, snn ta daukar masa nasa ma ta mike tsaye ta mika masa yace "kiyi hkuri fa," tace "aa bkm," har ya juya ya sake juyowa da sauri yana kallonta, ta dauke kanta da sauri ta ci gaba da daukan abinda take, taji mutumin a hankali yace "bala," wani mutum ya karaso da sauri yace "ya dae" taga duk sun tsaya kallonta ido a xaxxare, ta tsorata ssae ta ja trolly din ta ta je ta sami mujaheed dake xaune yana duba newspaper, yana ganinta yace "ba dae har kin gama ba kanwata," ta gyda masa kai da sauri kmr munafuka tace "Allah na gama yayana," yace "aa dae kanwata ki dauki duk abinda kike so," kmr xata yi kuka tace "aa ni nace mka na gama," ya daga kafada ya ja trollyn xuwa inda xa su biya kudi. Aneesah ta dan waiga taga lekota suke, suna ganin ta juyo suka dauke kansu da sauri bala yace "kan uban nn, wllh ita ce sallau," ya fito da hotanta a aljihunsa yana nuna ma sallau, sallau yyi dariya yace "ba karamin farin ciki Hajiya xata yi ba yau miliyan biyar cash" Aneesah ko a tsorace tayi bayan Mujaheed yace "ya dae kanwata," ta girgixa masa kai kawai, ya gama biyan kudin aka xuba masu kayan a booth, ya bude mata mota ta shiga shi ma ya shiga suka bar wajen, biyosu Aneesah ta ga mutanen sunyi a motarsu, tayi mugun tsorata amma bata ce ma mujaheed dake ta mata surutu komai ba. Suna isa gida taga sun canxa hanya, hkn yas[truncated by WhatsApp] [12/8, 21:12] ‪+234 803 751 8717‬: Khaleesah Haiydar 69..... Karfe shidda saura Mujaheed ya shigo dakin, Aneesah na xaune gefen gado tana karanta daya daga novels din da ya bata, tana son karanta novel ssae, bata yi xaton ganinsa wnn lkcn ba, kuma can ciki yyi sallamar ya shigo dakin, don hka bata ji sallamar ba shigowarsa kawae ta gani, da sauri ta boye novel din bayanta, ya tsura mata ido yace "me kike boye wa?" da ganinta kasan bata da gskya tace "ni?" ya karaso cikin dakin tace "wayyo ni wllh kar ka matso kusa da ni" ya tsaya tsakiyar dakin yana kallonta yace "me kike boyewa," ta fara kame kame "ni, ni dae bbu abinda nake boyewa, Allah kar ka xo kusa dani xan maka ihu," ya harareta ya karasa gabanta, xata kwala ihu ya xauna gefenta da sauri ya rufe bakin, ya hango Novel din a bayanta ya dauka ya mike tsaye yana murmushi, kunya ya kamata tayi tsaki ta kauda kai, ya ajiye gefenta yace "ynxun ma baxa ki mana girki bne?" ganin tayi masa bnxa ne ya sa ya xauna kusa da ita yana kallonta, ta mike tsaye ba tare da ta kallesa ba tace "me xan girka?" yace "abinda ke ranki," bata ce komai ba ta fice daga dakin ya bi ta da kallo, tana isa kitchen ta fito da indomie da kwai, cikin minti sha biyar ta gama girkin ta fito, ta debi nata ta ci snn tayi hanyar daki, a stairs suka hadu yace "har kin yi me?" tace "na gama." yyi shiru yana kallonta, xata wucesa ya riko hannunta yace "to xo muje mu ci together," tace "na ci nawa," ya harareta tace "wlh kuwa," ya ja ta suka isa dinnin din ya bude plate din da ta rufe masa nasa ya xuba ma indomien ido, can yyi murmushi yace "kin yi kkri," amma ni bana cin indomie, tace "ayya," sae abun ya basa dariya jin yanda tayi maganan, yace "je dauko hijab din ki," tace "mu je ina?" ya girgixa kai yace "bna sn musu Aneesah ki dinga yin duk abinda nasa ki," ta sunkuyar da kanta, yace "maxa je dauko hijab din ki," ta juya ta bar falon, ta dawo sanye da hijab din," yana gaba tana biye da shi a baya, suka isa mota, ya bude mata ta shiga snn ya xaga ya shiga, suka bar gidan, eatry ya shiga ya siyo masu kaxa da drinks sae ice-cream da hamburger, tace "na waye wnn?" yace "ni da kanwata," tayi murmushi bata ce komai ba, yace "in xa ga dake ki ga Abuja kanwata?" ta gyada masa kai, yace "ko ke fa kanwata," hka ya dinga nuna mata wajajen da ta sani da wanda ma bata sani ba a Abuja har kusan karfe tara snn suka kama hanyar gida, tace "yaya bamu yi sllh ba," yace "na sani kanwata," ta hanyar gidansu Haydar ya bi da su da xa su koma gida don kawae ya ga reaction dinta, bin gidan ta dinga yi da kallo, yace "ya dae kanwata" ta sauke ajiyar xuciya tace "bkm," ya hade rae yace "bna son karya ki fada min gskya," a hankali tace "wancan gidan ne gidansu ya Haydar, ko yana nn ma" bae ce komai ba taga yyi parkin snn yace "to fita ki je gun sa" ta xaro ido tace "iyye" ya hade rae yace "eh mana," ta girgixa kai tace "ni bance xan je ba fa," gate din gidan suka ji an bude ta juya da sauri sae ga pretty ta fito, Mujaheed ya tada motarsa ya bar wajen da sauri, Aneesah ta kasa daina kallon pretty, har suka isa gida Mujaheed bae ce mata komai ba, ya shiga dakinsa, ita ma ta shiga daki jikinta a sanyaye, har kusan karfe sha daya bae nemeta ba bare ya bata abinda ya siyo masu, jikinta a sanyaye ta sauko downstairs yana xaune yana danna laptop ya dago kansa yana kallonta, ta kasa karaso wa cikin falon, can ta juya xata koma sama, ya kirata, ta juya hawaye ya cika idonta tana kallonsa, yace "come kanwata," ta karasa gabansa ya xaunar da ita yace "baki yi bacci ba," bata ce masa komai ba, ya rungumota a hankali yace "am srry kanwata, amma bana son kina min xancen wani namiji a gabana," ta gyada masa kai ya share hawayen idonta yana murmushi, a hka suka xauna tare a falon ita tana kallo shi ko hankalinsa na kan na'urar gabansa, karfe daya saura ya gama abinda xae yi, ya kalli Aneesah da tun sha biyu tayi bacci ya shiga tashinta, a hankali ta bude ido tana kallonsa, ya mike tsaye ya kamo hannunta yace "xo muje ki kwanta kanwata," binsa kawae take don bacci na idonta har lkcn, suka hau sama ya bude dakin da take suka shiga ya kwantar da ita ya ja mata bargo ya rada mata gudnyt a kunne, snn ya kashe A.cn dakin dn garin da sanyi, ya kashe wutar dakin ma ya fita ya ja mata kofa ya shiga nasa dakin. Washegari friday da yace ma Haydar xae xo sae ya tsinci kansa da kasa xuwa gun Aminin nasa, Aneesah tace "yayana ba kace xaka fita ba yau," ya juya yana kallonta ya kasa ce mata komai, ta ce "kun gama case din wnn abokin naka da kace min ya sace yarinya?" bae ce mata komai ba ya kauda kansa ya shiga danna wayarsa. Unlike · 3 · Reply · Report · 3 minutes ago [12/8, 21:12] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 71..... Mujaheed na gama parkin Aneesah ta bude motar xata shiga gida Mujaheed yace "show! Wa xae daukar maki load din naki kanwata," ba tare da ta juyo ba tace "ni na gaji, snn ta shige gida, yyi murmushi ya shiga fiffito da kayan yana shiga da su, mai gadi ya xo ya taimaka masa suka shiga da dukka kayan, a tsakiyar falo ya dire kayan snn ya haura sama ya bude kofar dakinta ya shiga, tana kwance ta kudundune cikin bargo har lkcn xuciyarta ya kasa nutsuwa, ya karaso kusa da ita da sauri ya xauna ya cire bargo yace "ya dae kanwata, me ya faru," a hankali tace "kai na ke ciwo," ya dagota ya daura hannu kan nata da damuwa yace "subhanallahi tun yaushe kanwata baki gaya min ba" ta girgixa masa kai bata ce komai ba, ya kwantar da ita kan faffadar kirjinsa yace "srry kanwata xo ki ci abinci ki sha magani," bata yi masa musu ba ya dagota suka bar dakin suka sauko downstairs ya hada mata tea ya bata ta sha snn ya dauko magani ya bata ta sha da kyar daga nn bacci ya dauketa a falon. Ba ita ta farka ba sae kusan karfe shidda yana xaune gefenta yana kallon American film, ta mike ta xauna, ya rikota yace "ya jikin kanwata," ta hararesa tace "baka kai kayan can daki ba," ya juya yana kallon kayan shoppn din da yyi mata baki bude yace "iyyee, ni ma xan kai maki daki ko" ta ce "eh mana," ya fixgota yana dariya yace "ke din nn ko kanwata, kan ya daina ciwo ynxu ko" ta gyada masa kai ya jawo ledan fruit yace "ga shi na sa a siyo maki," tayi murmushi tace "ngd yayana," ya gyada mata kai yana kallonta, ta mike taje kitchen ta dauko plate ta juye don anyi slice dinsu, snn ta fara sha, ta daga kai taga kallonta yake tace "xaka sha ne, ya gyada mata kai, tace "to bude bakin," ya bude ta dauki kankana kmr xata kai bakinsa ta saka nata bakin, ya xaro ido yana kallonta ta dinga dariya, tace "srry bude to na baka," tana daukan fruit din kuma tayi kmr xata kai bakinsa ta tura nata bakin ya fixgota ya daura goshinsa kan nata yace fito da shi, da sauri ta fito dashi, ya sa baki ya karbe kankanan hade da kiss dinta. A tare suka shanye fruit din snn yace taje tayi sllh shi xae wuce masallaci, ko da ya dawo tana wanke wanke a kitchen ya shiga kitchen din ya jingina jikin kofa yace "kanwata gobe ki shirya xa muje gun abokina..... " da sauri ta katse sa tace "wnn da ya sace yarinya," ya kauda kansa yace "bae sace yarinya ba sharri aka masa," tace "A'a ni ba ruwana tsoro nake ji bbu inda xani," yyi shiru yana kallonta ganin hka ne yasa ta marairaice tace "to yi hkuri yayana xan je," ya kirkiro mata murmushi ba tare da yace komai ba ya bar kitchen din, suna xaune a falo kusan karfe goma ya jinginar da ita jikinsa tana kallo shi ko yana dan rubuce rubuce kan centre table laptop kunne gabansa, ya juya yana kallon Aneesah yace "kanwata bacci kike ji, kije ki kwanta gobe da wuri xa mu fita," ta girgixa masa kai tace "ni ba bacci nake ji ba," bai sake cemata komai ba ya ci gaba da abinda yake, bayan kmr minti biyar ya sake juyo wa yaga idonta a lumshe ya shafi fuskarta a hankali yace "nace kije ki kwanta Aneesah," ta bude ido da sauri tace "ni nace maka ba bacci nake ba," ya gyada kai yyi kwafa yace "yarinya kika min bacci a nn, barin ki xanyi idan na gama abinda xanyi naje na kwanta," cikin muryar bacci tace "ko dae kai xaka yi baccin a nn na barka naje na kwanta," yyi murmushi bae sake ce mata komai ba sae dae har lkcn tana jingine jikinsa, ya waigo yaga tayi bacci yyi murmushi ya gama abinda xae yi ya kashe na'urar gabansa ya mike tsaye xae daga ta sama ta bude ido da sauri tace "wayyoo," yyi dariya yace "ae da sae dae kiji na dauke ki na kai ki daki," ta galla masa harara ta mike ta yi hanyar stairs, yace "ba sae da safe," ba tare da ta kallesa ba tace "eh" ta haye sama ta afka daki," yyi murmushi ya kashe kayan wutan falon ya wuce dakinsa shima, Aneesah na shiga daki ta shiga bathroom tayi wanka don bata yi ba, kusan minti ashirin tayi tana wankan, snn ta fito daure da towel, tana kkrin dauko kayan da xata sa taji taku a hankali a stairs, ta ci gaba da abinda take yi, bata ankaraba taji an bude kofar dakinta a hankali, ta juya da sauri xata shige bathroom don a tunaninta Mujaheed ne, taji ance "ke," ta juyo a tsorace jin bakon murya taga mai magana, mutanen daxu na supermarket ne, ta xaro ido a gigice xata fasa ihu daya ya nuna mata bindiga, a hnkli yace "kina bude baki ina harbe kanki yarinya," ta toshe bakinta jikinta ya dau rawa taji kafarta ya kasa daukarta ta sulale kasa a hankali hawaye na bin kuncinta, bala ya karaso kusa da ita ya tsugunna yana kalln jikinta yce "hadin kai kawae xaki bani," sallau yace "kai meye hka da'alla harbeta mu fice dgann hadin kan me" bala ya galla masa harara yce "in ga santaleliyar budurwa hka na kasheta ba tare da na....." yana fadin hka ya daura hannu kan cinyarta yana shafawa yana murmushi yace "ban san ki bar duniya a wahale 'yar budurwa, bna son kwarmato kawae ki bani hadin kai," cikin rada yake mata maganar, sallau yyi tsaki yace "ae sae kayi sauri mu bar nn ko" Like · 2 · [truncated by WhatsApp] [12/8, 21:12] ‪+234 803 751 8717‬: Khaleesah Haiydar 73..... Likitan yace "to ina kayan aikin da xan duba ta da?" Mujaheed ya hararesa yace "dole sae da kayan aiki kawae ka duba min ita malam," Aminu ya girgixa kai yana kare ma su bala dake kwance shememe a tsakar dakin kallo ya karasa kusa da Aneesah ya kara dubata snn yace "ka kwantar da hankalinka yallabae tsorata ce kawae tayi ba wani abu ba, basu taba ta ba ina ga, wae yan fashi ne wa in nan koko?" mujaheed yace "oho," snn ya ciro wayarsa ya kira wani abokinsa dan sanda yyi masa bayanin abinda ya faru, dayake dan sandan babba ne yace to gasu nn xuwa, ya katse wayar yana kallon Aminu yace "don Allah kaje gida ka dauka su stesthoscope da allurori ka farfado min da yarinyar nn Aminu," Aminu yyi dariya yace "asibiti ma gaba daya xan dauko," yana fadin hka ya fice daga dakin yace "ina xuwa," mujaheed ya bi bayansa yace "ni ban ma je na duba mai gadin nn ba," suna fita suka tura dakin mai gadi suka tarar da shi a kwance an xuba masa cocaine, da sauri Mujaheed ya kullo dakin kar shima ya shaka yace "Allah sarki," ya bubbude windows din dakin don warin ya fita snn ya koma ciki bayan fitar Aminu da kamr Minti sha biyar 'yan sanda suka shigo gidan, suka shiga yi ma Mujaheed tambayoyi yace "ni fa ban san ko suwa ye ba" nn dae yyi masu bayanin abinda ya shigo dakin ya tarar yyi defendin din kansa kuma, suka kwashe su bala da bindigoginsu suka saka cikin motarsu mujaheed yace ma su gobe xae xo station din snn suka wuce, suna barin gidan Aminu ya dawo, yyi mata allurori, snn ya taimaki Mujaheed suka gyara dakin, bayan kmr minti ashirin ya duba ta yace "kaga ynxu bacci take, at anytime xata iya farkawa ga magunguna nn ka bata idan ta tashi ni xan koma gida," Mujaheed yace "haba dae it's too late ka bari gobe mana," Aminu yace "aa bbu koma ae da mota nake," Mujaheed ya rakosa waje ya nuna masa mai gadi, shima yy masa alluran snn yace "ka bar kofar dakin a bude gobe xae dawo hayyacinsa shi kuma," Mujaheed yace "ok," snn ya rakasa ya shiga mota ya dawo ciki ya kulle gidan yana mamakin me ya hana mai gadi kulle gidan da wuri, bae san tun karfe tara su bala ke labe a anguwar ba, suna ganin mai gadi ya fito suka shaka masa cocaine suka shiga da shi dakinsa suka kulle, snn suka fita daga gidan suka rufo gate, sae daxun nn suka shigo. Mujaheed na komawa dakin ya yaye bargon da ya lullube Aneesah da ya tsura mata ido yana kallonta daga ita sae inner wears, tausayinta ya cikasa, ya rumtse ido rufeta ya koma gefen gado ya xauna ya dafe kansa, yana xaune wajen har kusan karfe daya ya ga tana motsi, ya juya da sauri yana kallonta a hankali ta bude ido tana kare ma dakin kallo, lkci daya ta fasa ihu, ya mike da sauri ya karasa gabanta ya riketa yace "menene kanwata" ta fashe da kuka tana kkrin mikewa xaune ya rikota yace "haba Aneesah nine fa yayanki," ta kankamesa tana kuka tace "na shiga uku yayana," ya rufe bakinta da sauri yace "sun maki wani abu ne kanwata," kuka kawae take kmr ranta xae fita bata ce masa kmai ba, hankalin Mujaheed ya tashi yace "haba kanwata kiyi min magana mana, sun maki wani abu ne," ta girgixa masa kai da kyar tana kuka tace "wae kasheni suka xo yi," ya rungumota da sauri yace "bbu wanda xae kashe min ke kanwata sae lkcn ki yyi, bana son ki sake wnn kukan" gyada masa kai kawae take tana hawaye yace "xaki sha tea na baki maganinki" ta girgixa masa kai da sauri tace "aa," yace "to ina ke maki ciwo ynxu kanwata," bata ce masa komai ba sae ajiyar xuciyar da take, ya sake tambayarta ta girgixa masa kai tace "ba ko ina," ya dago kanta yana kallonta yace "ki kwanta kinji kanwata," ta kankamesa ta fashe da kuka tace "wllh ni baxan kwana cikin dakin nn ba tsoro nake ji don Allah kar ka tafi ka barni," yace "haba kanwata, add'ua fa xaki yi ki kwanta, baxa su sake dawowa ba, nasa an tafi da su station," cikin kuka tace "wllh tsoro nake ji ka kaini gun Ammina," Mujaheed ya rasa me xae ce mata yyi shiru yana kallonta, a hankali tace "yayana kar ka tafi ka barni don Allah ina rokanka," yace "to naji, kiyi kwanciyarki a kan gado ni sae na kwanta a kasa," ta rikesa tace "A'a wucewa xaka yi ka barni yayana," a hankali yace "shekaranki nawa Aneesah," ta na goge hawayen fuskarta tace "16" ya mike tsaye ta rikosa da sauri tana kuka tace "wayyo yayana wucewa xaka yi," ya girgixa mata kai yace kaya xan dauko maki ki sa, ita ma ta mike da sauri ta bisa ya juya yana kallonta bae ce komai ba ya fito mata da wani gown mara nauyi ya mika mata tana rike da shi duk don kar ya fita ya barta ta sa rigan, ya koma kan gadon tana biye da shi a baya ya kwantar da ita ta riko hannunsa tana sabon kuka har wani rawa jikinta yake tace "wucewa xaka yi ka barni yayana?" ya girgixa mata kai ya kwanta ta daya side din yace "kiyi baccinki bbu inda xa ni kinga na kwanta," ta gyada masa kai ta matso kusa da shi a hankali ta kwanta tayi lamo a bayansa tana sauke ajiyar xuciya, ya juyo yana kallonta da kyar yace "kinga Aneesah idan baxa ki kwanta a can ba ni xan bar maki dakinki," Like · 5 · Reply · Report · 15 minutes ago Hauwee Abdulkadir [12/8, 21:12] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 74...... Aneesah ta girgixa masa kai da sauri tace "A'a kar ka tafi ka barni yayana," a hankali yace "to koma can," ta koma inda ya nuna mata tana hawaye ta kwanta, ya juya mata baya, Mujaheed ya kasa bacci, kuma bae sake juyawa ba bare ya kalli inda take, a hankali yaji ta birginowa kusa da shi tayi lamo a bayansa, ya rumtse idonsa bae dae ce mata komai ba, har bayan kusan minti talatin snn ya juyo a hankali yana kallonta ta takure kanta amma bacci take, ya mike xaune a hankali kar ta tashi, ya kusan minti biyar a xaunen daga bisani ya mike ya shige bathroom dae dae lkcn da agogon dakin ke struck din 2 o clck ya dauro alwala ya fito, ya dauki darduma ya shimfida ya fara sallah, ya kai kusan minti sha biyar yana sllh Aneesah ta farka a tsorace ta mike xaune da sauri cikin kuka tace "na shiga uku yayana ina kke," tayi shiru hankalinta ya kwanta ganinsa yana sllh, ta bar kan gadon ta dawo gefensa da sauri ta xauna, can dae ganin ba gama sllhn xae yi ba, ta tashi ta shiga bathroom ta wage kofar yanda xata dinga ganinsa da kyau tayi alwala ta fito ta dauki hijab dinta ta fara binsa sllhn ita ma, daga karshe gajiya tayi da binsa ta sallame ta kwanta kan darduman a bayansa nn da nn bacci ya kuma dauketa, ba shi ya idar da sllhn ba sae kusan karfe hudu, ya mike ya dauko bargo ya lulluba mata snn ya koma kan darduman ya xauna yana addu'a, daren ranar dae Mujaheed bae yi bacci ba asuba tayi xae tafi masallaci ya tuna kar Aneesah ta tashi ta dinga rusa mashi ihu a gida hkn yasa yyi sllhn a dakin, snn ya tasheta ita ma tayi sllh, har gari ya waye bata bar gefen Mujaheed dake duba wani littafi ba, can ya juyo yana kallonta yace "kin tashi lfya kanwata?" ta dan yi murmushi ta sunkuyar da kanta a hankali tace "ina kwana yayana," yyi murmushi ya gyada mata kai ya mike yace "kije kiyi wanka, nima shi xanje nayi, da wuri xamu fita yau don sae mun fara xuwa station," ta marairaice fuska tace "aa ni yaya kar ka tafi ka barni," yace "to je kiyi wankan ki fito ina jiranki, baxan tafi ba," ta mike jikinta a sanyaye ta shiga bathroom ya bi ta da kallo yana murmushi, bayan kmr second talatin ta budo kofar ta ga ko yana nn har lkcn, ta rufe da sauri ganin yana nn, shi ko yyi murmushi sae da ya ji ta bude tap snn ya bude kofar dakin a hankali ya fice, ko da ta fito bata gansa ba ta fashe da kuka ta fice daga dakin da sauri tayi hanyar dakinsa, ta jirasa xaune a dakin har ya fito, yana ganin ta yace "xan fa bata maki rae kanwata baki shirya ba xaki fito," muryar ta na rawa tace "tsoro nake ji," ya harareta yace "tsoron idonki ba," ya rakata ya tsaya daga bakin kofa ta sa kayan snn ta fito da sauri, tana xaune ya shirya a dakin, snn suka sauko falo tare, coffee kawae ya sha ita ko ya tilasta ta ta ci tea da bread snn suka bar gidan bayan Mujaheed ya duba mai gadi, a hanya ya kalleta yace "Aneesah su waye mutanen jiya," nn da nn hawaye ya cika idonta tace "nima ban sani ba, amma jiya na gansu a supermarket, kuma naga kmr suna biyo mu har muka kai gida snn suka canxa hanya," yyi parkin da sauri yace "wat, shine baki gaya min ba Aneesah," ta fashe da kuka tace "ni ban san da gske binmu suke ba ashe," mujaheed yace "to me suka ce maki?" a hankali tace "sunce aiko su akayi su kasheni," Mujaheed ya gyada kai yace xasu ci ubansu, snn ya ja motar suka bar wajen, kin shiga station Aneesah tayi tace xata jirasa a waje, ya shiga shi daya, bae fito daga station din ba sae kusan karfe tara, yace "srry kanwata kin gaji da jira ko," ta girgixa masa ka kawae yyi reverse suka kama hanyar gidan yari, bae ce mata komai ba ita ma bata tambayesa ya akayi ba, ko da suka isa ba su sami ganin haydar a lkcn ba, aka ce masu sae eleven, suna xaune suna jiran eleven din yyi Aneesah tace "yayana tsoro nake ji gabana sae faduwa yake ban san meyasa ba," ba tare da ya kalleta ba yace "kiyi ta addu'a," a hankali tace "yaushe xaka nemo min Ammina yayana," ya juya yana kallonta yace "vry soon," tace "yayana amma ba gidan nn xamu kwana ba yau ko?" yyi murmushi yace "eh" ba tare da ya kalleta ba, karfe sha daya aka basu ixinin shiga gun Hydar, Mujaheed ya juya yana kallonta a sanyaye murya can kasa yace "tashi muje kanwata," Aneesah ta xaro ido tace "aa ni baxan shiga ba yayana tsoransa nake ji, ba kace yarinya ya sace ba," Mujaheed yyi murmushi ya kamo hannunta yace "c'mon sharri aka masa abinda ma xae ga yarinyar ynxu," bae jira me xata ce ba ya ja ta tana nonnokewa kmr xa tayi kuka suka shiga inda Hydar yake. Hmm wae Khaleesah ta cika abinda ya saba ma al'adar Hausa fulani a lbrin Aneesah inji mutane, ohh hka nace maku baxan sa side effect din hkn ba ba, nifa na san abinda nake yi kuma idan ina sa batsa a lbrina tun a Inteesar xa ku gane hkn, in kun bi ni sannu a hnkli xaku ga yanda xa a kaya. I knw wat am doin. [12/8, 21:12] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 75..... Haydar ya dago kai yana kallonsu, har lkcn Aneesah na labe bayan Mujaheed wae ita tsoro take ji, Hydar ya hade rae yana kallon Mujaheed ganin ba shi kadae bne don a xatonsa daya daga gantalallun 'yan matansa ya taho masa da, Mujaheed ya kyaleta ya karaso kusa da Haydar ya xauna yana kallonsa, kasa karasa wa Aneesah tayi ganin Hydar bayan Mujaheed ya bar ta gun a tsaye, ji tayi kafarta ya kasa daukar ta ta durkushe wajen jikinta na rawa, hkn ne dalilin da ya sa Hydar dago kansa yana kallonta don har lkcn bae kalle da warce Mujaheed ya shigo ba, ya mike tsaye a hankali yana kallon Aneesah da mugun mamaki, Aneesah ta fashe da kuka tana kallon Mujaheed da ya tsiri danna waya tace "wayyo Allahna ya Hydar me kke yi a nn," Hydar ya juya yana kallon Mujaheed da alamar tambaya, amma ya kasa cewa komai, ba tare da Mujaheed ya kallesa ba yace "ita ce Aneesar da kke gaya min ko," Hydar ya koma ya xauna da kyar yana ci gaba da kallon Aneesah da mamaki yace "ina ka samo ta Mujaheed," Mujaheed ya juya yana kallon Aneesah dake kuka ssae tana kallon Hydar, bae ce komai ba ya ci gaba da danna wayarsa, Hydar ya karasa kusa da Aneesah ya durkushe gabanta yana kallonta, ta dago kai ita ma tana kallonsa, a hankali yace "Aneesah," ta girgixa masa kai ta fashe da wani sabon kukan ta fada kansa, ya dagota ya girgixa mata kai yace "No Aneesah," muryarta na rawa tace "ya Hydar me kke yi a nn dama kai ne yayana ke fada min," ya tsura mata ido yace "waye yayanki," ta juya tana kallon Mujaheed da har lkcn idonsa na kan waya bae ko kalle inda suke ba, Hydar ma ya juya yana kallonsa, mujaheed dae bae ce masu kmai ba, Hydar ya dawo da dubansa ga Aneesar yace "ina ya kai ki Aneesah?" ta goge hawayen fuskarta tace "wa?" yace "baffanki" ta dan yi shiru tana ci gaba da goge hawayen da yaki tsaya mata tace "can wani gari ya kai ni," Hydar yace "gun wa?" ta fashe da kuka tace "ban san su ba, can wani kauye ya kai ni a kaduna," Hydar yyi shiru snn yace "Ammi fa?" cikin kuka tace "ya Hydar ban ga Ammina ba amma yayana yace xae samo min ita," Hydar yace "gun wa kike ynxu?" tace "gun yayana," yace "waye yayanki," ta juya tana kallon Mujaheed, wnn karon dae Hydar bae kallesa ba, Hydar bae sake ce mata komai ba ya kauda kansa, ganin yyi shiru ne ya sa tace "ya Hydar ka gaya min wa ya kawo ka nn, me kayi?" ba tare da ya kalleta ba yace "ca akayi na sace ki," ta fashe da kuka tace "wa yace hka ya Hydar?" Hydar yace "baffanki," kuka ta shiga yi ssae, ya dagota ya sa hannu yana share mata hawayenta yace "kar ki damu Aneesah, in'sha Allah komai ya xo karshe ki kwantar da hankalinki," ta gyada masa kai kawae, ta juya bata sake ganin Mujaheed ba, ta tsayar da kukanta ta mike tsaye da sauri tace "ya Hydar ina yayana?" bae ce mata komai ba ya tsura mata ido, ta fara waige waigen neman Mujaheed, Hydar yace "ki duba sa a waje," ta fice da sauri ta gansa xaune daga waje, tace "yayana," ba tare da ya kalleta ba yace "kun gama?" ta gyada masa kai, ya mike ya shiga inda Hydar yake yace "sae mun hadu a kotu ran monday," Hydar yyi shiru yana kallonsa ganin ya juya xae wuce ne yasa yace "so early?? Bbu bayanin komai jaheed?" Mujaheed ya juyo yana kallonsa yace "bayanin me?" Hydar yyi shiru yana kallonsa can kuma yace "shknn Allah ya kiyaye hanya," har mujaheed ya juya xae wuce sae kuma ya fasa ya juyo ya dawo ciki yana kallon Hydar yace "kar ka damu Aliyu gobe xan dawo a kwae lbri, ynxu sauri nake wllh" yana gama fadin hka yyi murmushi yyi pat din shoulder dinsa yace "c yah," snn ya juya ya fita Hydar ya bi sa da kallo, Mujaheed ya kalli Aneesah dake tsaye daga bakin kofa a hankali yace "ki je kuyi sallama," tace "to ka jirani" ya gyada mata kai ta karasa kusa da Hydar a sanyaye tace "ya Hydar mun tafi," yyi shiru yana kallonta snn yace "ina xaku ynxu?" ta sunkuyar da kai tace "ni da yayana xamu wuce gida," ya dauke kansa yace "ok," Aneesah ta juya hawaye cike a idonta ta fita ta samu Mujaheed tsaye a waje ya jingina da bango idonsa rufe yana jiranta, tace "yayana," ya bude idon yana kallonta bae ce komai ba yyi gaba tana biye da shi a baya har suka fita ya bude mata mota ta shiga snn ya xaga ya shiga driver sit ya ja motar suka bar wajen. [12/8, 21:12] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 76..... Mujaheed na gama parkin Aneesah ta bude motar xata fita ya kirata a nutse, ta koma ta xauna tana kallonsa, yace "kinji ddin ganin Hydar yau ko?" ta sunkuyar da kai bata ce komai ba, ya kira sunanta ta dago a hankali tana kallonsa yace "magana nake maki" tace "yayana a ina ka san shi to" yace "ki amsa min tambayata," ta dan karyar da kai ta marairaice tace "ehh mana ssae ma," ya gyada kai yace "to yyi kyau," ya bude motar ya fito ya bar ta a ciki, ta bishi da kallo har ya shiga cikin gida snn ta fara kuka, tayi mai isarta ta fito ita ma ta shiga gidan a sanyaye, yana kwance falo ya lumshe idonsa, ta karaso falon kmr bata son taka tiles din dake shinfide a falon, ta isa gabansa ta sulale kasa tana kallonsa a hankali ta shiga kiransa "yayana," ya bude ido yana kallonta, ta sunkuyar da kai hawaye na xuba idonta, ya mike xaune yace "ya akayi," ta girgixa masa kai bata ce komai ba, yace "ko na sake maida ke gun Hydar din ne?" ta tsura masa ido tana kallonsa bata ce komai ba, ya mike tsaye yace "fine! Sae ki je ki harhada kayanki," yana kai wa nn ya juya ya bar wajen da sauri ya haura sama, ta fashe da wani sabon kukan ta kife kanta kan kujera. Baffa ne xaune hankalinsa kwance a falonsa yana kallon tashar bbc, Hajiya zuwaira na xaune gefensa tana waya, Abdul ya shigo falon da jakar kayansa ya xaune kan kujera yana kallonsu, shehu yace "ya dae guy na ganka da katuwar jaka hka?" ba tare da ya kalli mahaifin nasa ba yace "yau xan kama hanyar london ne dad," baffa ya dan sace kallon Hajiya da ta kauda kanta tana dan murmushi yace "a haba dae guy, har ka gama hutun," Abdul yace "ni nama rasa me ya xaunar da ni har ixuwa ynxu a Nigeria yau fa watana kusan biyar," Hajiya tace "ae shine son, kar ma kaje ka samu matsala gurin aiki," baffa yace "shknn son Allah ya kiyaye, kana bukatan wani abu ne?" Abdul ya mike ba tare da ya kallesa ba yace "ba komai," ya ja jakarsa ya fice daga falon, baffa yace "amma driver ne xae kai ka airport ko?" basu ji ya ce komai ba, Hajiya ta juya tana kallon baffa, tayi dariya tace "ya kaga aiki na Alhaji," cike da jin ddi yace "yana kyau matata, shi yasa nake bala'in san ki wllh," ta mike tana dariya tace "bari naje muyi sallama mai kyau da dana," karfe hudu Mujaheed ya sauko kasa tun bayan hawansa sama, har lkcin Aneesah na xaune inda ya barta, ya karaso cikin falon yana kallonta yace "kin gama hada kayan," ba ta kallesa ba kuma bata ce komai ba, ya xauna kan kujera yace "na fa gaya maki ki je ki hado kayanki na kai ki gun Hydar din ki xauna," ta tashi tsaye tana kallonsa tace "ae ba da kaya naxo gidan nn ba," tana fadin hka ta juya tayi hanyar fita daga falon, ya mike tsaye da sauri yace "ke ina xaki" bata ko juya ba bare ta tanka sa, ya fito shima da sauri yana kiranta, har ta kusa gate, mai gadi na sllh dakinsa don hka kawae ta bude gate din ta fice, tana fita ta saka gudu sanin Mujaheed xae biyota, ko da ya fito kofar gidan tayi nisa, yace "ya salam," ya koma ciki da sauri ya dauko makullin mota ya bude gate ya bita, ya rasa hanyar da ta bi don hanyoyin daban daban ne, Aneesah gudu kawae take tana kuka ba tare da ta san inda xata ba, ta isa titi xata tsallaka wani mai taxi ya tsaya yace "tafiya ne Hajiya," bata ce masa komai ba ta bude bayan taxi ta shige, ya ja taxin yana tambayarta ina xata, tace "can gaba," sae da yyi nisa don har sun fito babban titi snn tace "malam banda kudi fa?" ya juya yana kallonta snn yyi parkin yace "to fita," tace "to ngd," snn ta fito ya ja motarsa yyi gaba, ta fara kalle kalle ta rasa inda xata yi ta fashe da kuka, xata tsallaka titi kmr daga sama taji mota ya bugeta ta fasa ihu ta durkushe wajen don bata wani bugu ba amma ta tsorata, mutane suka taru gun suna mata masifa bata kallon inda xata wae, mai motar ma ya fito yana kallonta a fusace yace "ke wace irin mara hankali ce kina tafiya hankalinki na karkashin takalminki haka kurum ina xaman xamana ki ja min sittin," Aneesah ta dago da sauri jin muryar mae maganar, dae dae nn kuma Mujaheed ya shigo crowd din. [12/8, 21:12] ‪+234 803 751 8717‬: post Khaleesat Haiydar ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 77..... Abdul yyi tsit daga masifar da yake yi yana kallonta kmr mae son tuna Abu ya dafe kansa, can ya durkusa gabanta yana kallonta yace "sannu baki ji ciwo ba dae ko," ta mike da sauri tayi gefen Mujaheed da ya kasa ce mata komai sae kallonta da yake cikin bacin rae, ta kamo hannunsa a rude tana kuka tace "yayana mu tafi gida don Allah," ya fixge hannunsa yace "ki dae tafi inda xa ki" ta juya da sauri xata wuce ya fixgota a fusace yace "na ga alamar baki da hankali," Abdul yace "ka bi ta a hankali mana," Mujaheed bae ko kalli Abdul ba yyi hanyar motarsa da ita, ya bude bayan motar ya jefata ciki, snn ya xa ga ya shiga driver sit ya ja motar suka bar wajen, Abdul ya xaga ya shiga tasa motar ya bi su a baya, kuka kawae Aneesah take a bayan motar, duk a tsorace take ganin Abdul, Mujaheed bae ko kalleta ba bare yace mata komai, kamr ance ta juya taga Abdul biye da su a baya, ta fasa wani raxanannen ihu, Mujaheed ya taka burki da sauri ya juya yana kallonta da mamaki yace "ya salam wae kina da hankali kuwa Aneesah?" ta nuna masa baya a tsorace ya juya yana kallon motar Abdul da ya tsaya, mujaheed ya kalleta yace "meye wnn?" cikin kuka tace "bin mu yake," Mujaheed ya bude mota ya fito yana kallon motar Abdul, Abdul ya fito daga tasa motar Mujaheed ya karasa gunsa yace "malam kana da matsala da mu ne?" Abdul yace "A'a just want 2 make sure she's alryt don na bugeta ssae," Mujaheed yace "dnt bother xan kai ta asibit," Abdul yace "dama ka bari na dubata nima likita ne," xae fito da I.D card dinsa mujaheed yace "nace maka karka damu malam," Abdul ya daga kafada alamar ok, snn yace "kanwarka ce," ba tare da mujaheed ya kallesa ba ya juya xae koma motarsa yace "matata ce," Abdul yace "matarka? karya kke wnn bata yi kama da matar aure ba, ina tunanin ma kmr na taba saninta," Mujaheed ya dawo da sauri ya cakume Abdul yana huci yace "kai! Wllh xan iya kasheka a kan wnn yarinyar, ka kama hanyar ka kar kasa nayi maka dukan fitan hankali a nn," bae jira cewar Abdul din ba ya turasa da karfi yyi hanyar motarsa ya shiga yyi reverse ya fasa komawa gida duk da sun kusa gidan tunda a layinsu yake, bae damu da irin kukan da Aneesah take ba har sae da yyi nisa ssae snn yace "waye wnn mutumin Aneesah," cikin kuka tace "yayana ne," ya taka burki da sauri don bbu motoci a titin anguwar yana kallonta yace "yayanki kuma?" ta gyada masa kai tana ci gaba da kuka tace "dan baffana ne," Mujaheed yace "wat?" ya sanki ne?" ta gyada masa kai nn ma tace "shine wanda ke son aurena baffa ya dauke ni ya kai ni kauye," Mujaheed yace "innalllahi wa'inna ilaihi raji'un," ya ja motar suka bar wajen snn yace "to ya akayi bae gane ki ba?" ta goge fuskarta tace "nima ban sani ba," bae sake ce mata komai ba har suka isa wani gida, yyi horn mai gadi ya bude gate ya shiga yyi parkin ya fito ya bude mata mota tace "ina ne nn yayana?" yace "nn ma gidanmu ne," tace "me xamuyi a nn?" ya kauda kansa yace "ae ya riga da ya san anguwarmu hatsari ne babba idan muka ci gaba da xama a can, shi yasan me yasa yyi pretend kmr bae sanki ba, kuma nasan xae kai ma ubansa information," Aneesah ta gyada kai tana hawaye tace "haka ne," yyi hanyar shiga gidan tana biye da shi a baya. Abdul na shiga gida mahaifansa suka tsaya kallonsa da mamaki, na farko a tunaninsu kmr yanda yace masu xae je gun abokinsa yyi sallama da shi ya ajiye motarsa a can snn ya wuce tashar jirgin sama, na biyu kuma ya shigo masu a hargitse kmr mahaukaci, baffa ya mike da sauri yana kallonsa yace "ya akayi son, wa ya taba min kai," ya xube kan kujera ya dafe kansa yace "dad wata nagani kuma ina tunanin kmr na santa, dad duk nayi confuse," Hajiya tace "ikon Allah, to a ina ka santa Abdul?" Abdul ya yatsine fuskarsa kmr mai son tuna abu sae kuma yace "wllh na manta amma ni dae na santa," baffa yace "a ina ka ganta to?" Abdul yace "kawae shigo min titi tayi na dan bugeta amma bbu abinda ya sameta, sae yayanta ko mijinta ne ni dae ban sani ba ya xo xae tafi da ita," Baffa yyi dariya yace "guy knn, da ynxu ka isa airport ka bata lkcn ka a bnxa ka dawo kan maganar da bae da tushe," Abdul ya mike a fusace yace "maganar tawa ce bata da tushe, wllh na san yarinyar nn, kuma ni sae na nemota, ae nasan anguwar da take," yana kai wa nn ya juya fuu ya bar falon ya haura sama, Baffa ya juya yana kallon Hajiya da ta kasa rufe bakinta yace "anya Hajiyata wnn karon aikin ki yyi kyau kuwa," tace "haba Alhaji sae kace baka san ni bane, ae idan akwae abinda yafi kyau ma aikina yyi, ka barni da shi kawae, ni nasan wanene son dina," Mujaheed na xaune kan dinnin table ya dafe kansa, Aneesah na kitchen tana girkin da ya sa ta, duk case din Aneesah ya birkita masa kwakwalwa can station an gano cewa wata Hajiya ce ta tura su bala su kashe Aneesah duk da har lkcn ba a gano wacece ba don su bala sun ki fadi shi ko yasan Hajiyar Hydar ce, nn kuma ga dan baffanta ya gansu, dole yasan baffa xae samu information, kai rayuwar Aneesah na cikin hatsari. [12/8, 21:12] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 78..... Aneesah ta gama girkin da take yi a kitchen ta jera masa kan dinnin don har lkcn yana xaune gun sae dae wayarsa yake dannawa wnn karon don tunanin da yake na sa masa ciwon kai, xata wuce yace "ina xaki," bata kallesa ba kuma bata ce komai ba, ya mike ya karasa kusa da ita ya kamo hannunta suka koma kan dinin din ya xaunar da ita kujeran dake gefen wanda yake, snn ya shiga xuba mata shinkafa da miyar yace "kin gaji ko? Dana sani da cefanen da driver yyi da siyo mana kawae yyi a eatry," ita dai bata ce masa komai ba, ya juya yana kallonta, ta sunkuyar da kai da sauri, a hankali ya dago kanta yace "ki daena sama kanki damuwa Aneesah," hawaye ya ciko idonta ya sakala hannu a wuyarta yace "xa fa muyi fada kanwata bana son wnn unnecessary kukan naki, kullum baki da aiki sae na kuka, dnt wrry kanwata Hydar na fitowa xaki ga Amminki," a hankali tace "yayana yaushe xae fito?" Mujaheed yyi shiru kmr baxae ce mata komai ba sae kuma ya sauke ajiyar xuciya yace "ran monday," tace "yau thursday," ya gyada mata kai kawae snn ya shiga bata abinci tana karba a baki, tace "kai baxa ka ci ba?" yace "sae kanwata ta koshi," tayi murmushi ta dauki cokali tace "aa ni xan ci da kaina kai ka ci naka," ya tsura mata ido ta rufe fuskarta da sauri tana murmushi, shima yyi murmushin yace "to kanwata an gama," snn ya fara cin abincin, ganin ta daina ci ne ya sa yace "ya dae kanwata," tace "na koshi," yace "da gske," ta gyada masa kai ta dauki newspapern dake kan dinnin din tana dubawa, bae sake ce mata komai ba ya ci gaba da cin Abincinsa, wayarsa tayi ring ya dauka yana duba mai kiransa, ya daga yana murmushi yace "ya akayi son," yyi dariya yace "ba hka bane wllh, abubuwa ne suka sha min kai ga ta nn ku gaisa," Mujaheed ya mika ma Aneesah dake kallonsa wayar ta ki karba tace "wanene," yace "Mudatheer," ta karba da sauri tace "da gske," tana kara wa a kunne tace "uhm yau ka tuna dani Mudatheer," Mudatheer yyi dariya yace "'yar birni ashe kin koma birni," Aneesah tayi dariya tace "kaji da shi, ya gida ya aiki," yace "lfya 'yar birni," ganin yanda Aneesah ke ta fira tana dariya da Mudatheer ne yasa Mujaheed ya karbe wayarsa yace "xan kiraka ltr Mudatheer," snn ya kashe wayar, Aneesah ta hade rae tace "magana fa yake min yayana ka karbe," Mujaheed ya harareta bae ce komai ba ya mike ya bar dinnin din ya ja dogon tsaki snn ya haye sama, hkn yyi mugun bata ma Aneesah rae tayi ta xama a dinnin din har maghrib, ya sauko xae wuce masallaci yace "ke yarinyar nn banga alamar ma kin yi sllhr Azahar ba bare la'asar yau, ko baki sllh ne?" ko kallonsa Aneesah bata yi ba ya fita xuwa masallaci, ko da ya dawo a balcony ya ganta xaune, yace "me kike yi a nn kanwata?" ta mike tsaye tace "ka barni ni kadae tsoro nake ji," ya kamo hannunta suka shiga falo yace "tsoran me kanwata?" bata ce masa komai ba suka haura sama, yace "to je kiyi sllh ni wanka xanyi, ko da gsken bakya yi" ta girgixa kai kmr xata yi kuka tace "aa ni dae tsoro nake ji ni kadae," yace "wae tsoron me?" bata ce masa komai ba ya ja ta suka shiga dakinsa yace "to je kiyi alwalan ki fito ina jiranki," ta shiga ta yi ta fito ya nuna mata darduma snn ya shiga wanka, ko da ya fito tana xaune kan darduma ta idar da sllh ya xauna kan gado yana kallonta yace "xakiyi wankan ne? Don fita xamuyi," ba tare da ta kallesa ba tace "baxan yi ba," yace "to je ki canxa kayanki, xamu fita ne," tace "bbu kaya a nn," yace "oh hka ne," to tashi muje can gidan ki dauko kaya, bata yi musu ba ta shiga gaba yana biye da ita a baya suka shiga mota suka kama hanyar dayan gidan, a kofar gida yyi parkin snn suka fito mai gadi ya bude masu gate suka shiga ta dauki abinda xata dauka a gidan snn suka fito, abun mamaki sae su ka ga Abdul tsaye kofar gidan yana jiransu ashe tun daxu yake anguwar bae san takamaiman gidan da suke ba sae ga su sun shigo anguwar dae dae lkcn da yake shirin komawa gida don ya gaji, ya bi bayansu da motasa da sauri ya ajiye motar kusa da nasu ya fito ya tsaya kusa da gate yana tunanin abun yi, suna fitowa Aneesah ce ta fara yin ido hudu da shi ta kwala ihu ta fada kan Mujaheed da ya rude yana tambayarta lfya, ta shiga nuna masa Abdul jikinta na rawa, Mujaheed ya juya da sauri yana kallonsa yyi kansa ya shake sa snn ya buga sa da bango yace "don ubanka me ya kawo ka nn me kke nema daga gare mu?" Abdul ya girgixa kai yace "wllh wllh ni ba cutar ku xanyi ba, don Allah ka saurareni, ni dae nasan nasan yarinyar can, ka tambayeta kaji, kawae manta inda na santa nayi ne" dae dae nn mota tayi parkin kofar gidan, Mujaheed ya sake Abdul ya tsura ma motar ido motar gidansu Hydar ne, yace "ya salam." Like · Reply · Report · 6 minute[truncated by WhatsApp] [12/8, 21:12] ‪+234 803 751 8717‬: leesah Haiydar 79..... Mujaheed ya bude gate da sauri ya tura Aneesah da ta tsaya kallon motar ita ma ya kullo gate din, aka bude motar pretty ta fito, Mujaheed ya kirkiro murmushi yana kallonta yace "bbyn yayanta ce a gidan namu yau?" ta hade rae bata ce masa komai ba ta gaida Abdul ya amsa absent- mindedly, Mujaheed yace "ya gidan pretty daga ina hka da nyt dinnan?" ta hararesa tace "wae don kar naga budurwar taka shine kke wani tura ta cikin gate ko?" ya wara ido yace "wa? ni din, har da sharri ko bby," bata sake ce masa komai ba tayi hanyar gate din xata shiga ya rikota yace "bbu kowa ciki fa," pretty ta galla masa harara ta fixge hannunta ta bude gate din ta shige ciki abinta ya sauke ajiyar xuciya tare da sakin murmushi ya bi ta da kallo, ya juya yana kallon Abdul yace "bani nmbrka xamuyi waya ltr sae ka gaya min meye hadinka da yarinyar nn," Abdul ya basa complimentary card dinsa yyi masa gdya, Mujaheed yace "xan kira ka anjima," Abdul yace "ok" snn ya shiga motarsa yyi reverse yana kare ma gidan kallo, Mujaheed yyi murmushi yace "sae kuma ka sake ganin mu ae, amma fa kamr yana da brain disorder," ya daga kafada ya shiga gidan yana tunanin taya xa ayi yace bae gane Aneesah ba amma kuma ya santa idan ba juya masa brain aka yi ba, Aneesah kam Har lkcn tana tsakar gidan a tsaye tana kuka a hankali jin muryar pretty, ynxu sbda ita fa aka saka mata yayanta da take ji da a gidan yari, tana jin shigowarta tayi hanyar balcony da sauri xata shiga falo, Mujaheed da ya shigo gidan bayan ya sallami Abdul ya kalli pretty dake tsaye tana bin Aneesah da kallo yace "mu shiga ciki kanwata," ta girgixa kai tace "dama wucewa xanyi ne nace bari na tsaya na gaida ka, sae da safe," ta juya xata wuce yyi saurin kamo hannunta yace "ae baki isa ba sae kin shiga ciki kuma har girki ma sae kin min," bae jira mai xata ce ba ya ja ta suka shiga gidan, Aneesah na xaune falo ta hade kai da gwiwa tana kuka, ya sake pretty ya karasa kusa da ita ya durkusa yace "meye na kuka Aneesah, pretty ce tashi ku gaisa," Aneesah ta dago kai tana kallon pretty da ta tsaya da mamaki tana kallon Aneesah ta girgixa kai cikin rashin fahimta tace "ya Mujaheed, wacece wnn," Mujaheed yace "Aneesah" ta fashe da kuka tana kallonsu, Mujaheed ya mike ya kamo hannunta yace "ni bance ki min kuka ba Zainab, kar ki damu tunda muka ga Aneesah, yayanki xae fito idan Allah ya yrda, daxun nn ma muka je gunsa," pretty tace "da ita?" Mujaheed ya gyada mata kai yace "amma fa bance ki ce ma su Hajiya komai ba, duk da nasan baxa ma ki fada ba," ta gyada masa kai tace "nasani," snn ta xauna gaban Aneesah tana kallonta, Aneesah ta dago kai tana kallonta ita ma, pretty tayi murmushi tace "Aneesah," ita ma murmushin tayi bata ce mata komai ba. Pretty tana kallon Mujaheed tace "yaya tare kuke a nn?" Mujaheed yace "ko xaki dinga taya mu kwana ne? Dama gata kullum cikin tsoro take" tace "ku biyu fa kadae yaya" ya galla mata harara yace "to me ya faru?" tayi murmushi ta canxa xancen tace "aa ni baxan taya ku ba," yace "kira mum kice mata xaki kwana a nn," ya fadi hkn ne don ya san bbu ruwan Hajiyar ko kadan baxata damu ba da yake ita gantalalliya ce, pretty tayi murmushi ta girgixa kai tace "fushi take dani ae baxata ma daga kiran ba na sani," Mujaheed yace "to shknn, gobe kya xo ki taya mu kwana amma a wancan gidan ba wnn ba," hira suka dinga yi har kusan karfe goma, ita dae Aneesah sae dae tayi murmushi bata ce masu komai, da xolaya pretty tace "wllh wnn amaryar yayan nawa ta cika jin kunya," Mujaheed ya juya yana kallonta yace "waye yayan naki? Hka yace maki amaryarsa ce" pretty ta tsaya kallonsa bata ce komai ba ya dan yi tsaki ya mike tsaye yace "ynxu xaki koma gida ne ko ko, don xamu tafi gida ne," pretty bata ce komai ba ta tashi tsaye snn tace "ehh ynxu xan wuce," Mujaheed ya juya yana kallon Aneesah yace "kanwata tashi mu wuce nasan kin fara jin bacci ynxu," ita dae bata ce masa komai ba ta mike ya kama hannunta, pretty na gabansu suka fita gate. Sae da ya raka pretty har gida snn ya fito suka yi sallama ita ma ta leka mota tayi ma Aneesah sallama snn ta shiga da motarta ciki bayan mai gadi ya bude mata gate, shi ko yyi reverse suka kama hanyar gida, suna isa gida yace "dama gidansu Mudatheer xamu daxu, kinga ynxu dare yyi sae gobe," cikin murna Aneesah tace "da gske? Amma kuma yace min shi dan kano ne ae," Mujaheed bae tanka ta ba ya haura sama ta bi bayansa da sauri, ya juya yana kallonta bayan sun shiga daki yace "kije ki kwanta kanwata ni bacci nake ji," ta bata fuska tace "ni kadae xan kwana?" ya bude baki yana kallonta yace "to da ke dawa xaki kwana?" ta marairaice masa tace "ni wllh tsoro nake ji ynxu," yyi shiru yana kallonta snn yace "ajinki nawa a islamiyya?" ta wara ido tace "ni nayi sauka tun yaushe," ya gyada kai ya matso kusa da ita ya kamo hannunta yace "iyye, to naji xaki kwana nn amma kwana xakiyi kina sllh, ni kuma nayi baccina, don baxan iya bacci kina bacci ba, amma idan kina ta sllh tsaf xanyi baccina," [12/8, 21:12] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 80...... Mujaheed ya tura kofar dakin a hankali ya shigo yana kalln Aneesah yace "ke fa nake jira kanwata baki shirya ba har ynxu," bata ce masa kmai ba kuma bata kallesa ba ya karaso gefen gadon ya xauna yana kallonta yace "am tokn Aneesah," ta juya masa baya tace "bbu inda xa ni," ya xaga yana kallonta yace "haba kanwata hw many tyms xan baki hkuri, nace kiyi hkuri kin ki" ta fashe da kuka tace "ni nace maka ka kyaleni bbu inda xanje," yyi shiru yana kallnta snn yce "kada Allah yasa kije din" ya mike ya bar dakin ta bisa da kallo ta fada kan gadon ta fashe da wani kukan, throughout ranar bata fito ba shima bae shiga dakin ba, iyaka lkcn sllh na yi tayi alwala tayi sllh ta koma ta kwanta, har sae da yamma snn ya budo kofar dakin ya shigo ya ajiye mata ledan abinci ya fice, bata ko juya ba bare ta kalli ledan da ya ajiye mata, tana xaune kan darduma ta idar da sllhn Maghrib ya shigo dakin ya xauna kan gado yana kallnta, ta mike ta dauke darduman ta linke snn ta xaga xatayi kwanciyrta kan gado ya riko hannunta, "haba Aneesah wae me yasa kke min hka ne, meyasa kka cika taurin kai hka ne," ta fixge hannunta tana shirin fashewa da kuka, ya xaunar da ita gefensa yace "don Allah kiyi hkuri ki ci abinci, nace mki daga yau...." aka turo kofan dakin pretty ta shigo suka daga kai suna kallnta, Mujaheed yyi murmushi yace "sae ynxu bby, tuntuni nake kiranki baki xo ba har sae da ta huce," pretty ta dan yi murmushi tace "Hajiya ce bata barni na fito ba," ta karaso ciki ta xauna gefen Aneesah, Aneesah tayi murmushi tace "ya gidan," pretty tace "lfya lau," Mujaheed yace "to kuci abincin tare xan je gun abokina dake nn kusa," pretty kadae ta amsa masa, Aneesah ta bi sa da kallo, ya kashe mata ido ta dan yi tsaki ta hararesa ta kauda kai, yyi dariya ya fice, pretty ta xamo kasa a hankali hawaye ya cika idonta, amma in har hka ne Mujaheed bae ma yayanta adalci ba, ita kuma Aneesah bata yi masa halacci ba, Aneesah ma ta sauko kasa ta jawo abincin tace "in xuba maki," pretty ta girgixa mata kai kawae, ita ko ta xuba nata ta fara ci. Ranan tare Aneesah suka kwanta da pretty don Mujaheed yace dole sae ta kwana sbda Aneesah, can cikin dare kmr jiya tayi mafarkin su bala sun sake biyota, bata yi ihu kmr jiya ba sbda pretty, ta toshe bakinta da sauri tana kuka, ta mike ta bude kofar dakin tayi hanyar dakin Mujaheed, ta tura kofar dakin yana xaune kan gadonsa coffee a gabansa kan table, ya dago da sauri yana kallonta ta karaso cikin dakin yace "ya akayi kanwata bakiyi bacci ba," ta durkushe gabansa hawaye na ci gaba da xuba a idonta tana kallonsa tace "yayana ni tsoro suke bani kullum," ya sauka kasa ya xauna dan nisa da ita yace "ya isa kanwata ke ce bakya addu'a," ta girgixa masa kai tace "wllh ina yi," ya jawo bargon saman gadon ya shimfida mata nn kasa ya dauko filo ya ajiye mata yace "to yi kwanciyarki a nn kanwata" bata yi masa musu ba ta kwanta ya dauko wani bargon ya lullubata da shi, tace "yayana meyasa baka yi bacci ba," yace "tunaninki ne ya hanani bacci kanwata," ta wara ido tace "ni?" ya gyada mata kai yace "ina son ki da yawa kanwata," bata ce komai ba ta gyara kwanciyarta ya matso kusa da ita yace "baxa ki ce min kina sona ba," tayi murmushi bata ce komai ba yace "i luv yhu Aneesah," xata rufe fuskarta da bargon ya rike yace "kema ki ce min hka plss" ta girgixa kai tace "baxan iya ba," ya sake mata bargon a hankali bae ce komai ba ya koma inda yake ya xauna, can bayan ya manta yaji tace "i luv yhu 2 yayana," don farin ciki ma rasa me xae ce mata yyi. Washegari da pretty ta fahimce dakinsa Aneesah ta kwana hkn yasa ta kuka ssae don tausayin yayanta da irin halin da ya shiga sbda son Aneesah, taji wani irin haushin Aneesar da ma Mujaheed, ita kam bata goyi bayan yayanta ya auri Aneesah ba kuma, ko sllma bata masu ba ta bar gidan Yau Monday Aneesah ta tashi da fargaban xuwa kotu, knn fa yau baffanta da Hajiyarsu ya Hydar da kowa ma xae ganta, kila ma har da Amminta, Mujaheed ya shigo dakin yace "kanwata xaki bata min lkci mana," tace "yayana jiya da kaje gun ya Hydar me yace maka?" yyi mata mugun harara yace "ban sani ba, idan kinga dama kiyi maxa ki shirya" yana gama fadin hka ya bar mata dakin, ta bi sa da kallo, idan da sabo ta fara sabawa da saurin fushin Mujaheed idan ta kawo masa maganar wani namijin, ko da ya dawo dakin ta gama shirinta gudun masifarsa, tace "yayana to ni tsoro nake ji, bn san me baffa xae min idan ya gan ni ba da hajiyarsu ya Hydar," yace "duk bbu abinda suka isa su maki, shi baffan daga can ma xa a kama sa na sani," Aneesah tace "to Ammina fa," yace "kila ki ganta yau, xo muje muyi break" bata yi masa musu ba ya ja ta suka sauko downstairs suka karya, karfe tara saura suka bar gida, gabanta ya dinga faduwa tace "yayana ni fa tsoro nake ji," yace "kiyi ta addu'a kanwata, snn banda karya a kotu duk abinda aka tambayeki iya gskyarki xaki fadi" ta gyada masa kai kmr xa tayi kuka, ya dinga mata hira don ta kwantar da hankalinta har suka isa kotun. [12/8, 21:12] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 81.... Mujaheed ya juya yana kallon Aneesah bayan ya gama parkin yace "kar ki damu kanwata ba ynxu xaki shigo ba, sae an nemeki," ta xaro ido tace "wa xae neme ni?" Mujaheed yace "idan lkcn yyi xaki gani," ya kunna mata A.c ya sa mata karatun qur'ani, ya fita daga motar ya kulle, ta bi sa da kallo har ya shiga kotun, ohh ita fateemah ta ga lyf, tana ta xaune cikin motar tana bin duk wanda ta gani da kallo, wata katuwar mota tayi parkin Hajiya tafito cikin shiga ta alfarma da kawayenta har hudu kmr ba dan ta ke kulle a kurkuku ba, motar dake bayan tasu su meenah da pretty ne a ciki ta bi su da kallo har suka shiga kotun gaba daya, bayan shigarsu da kmr minti goma sae ga motar baffanta da abokansa suka shiga kotun suna ta surutu, can sae ga Hajiya zuwaira da nata kawayen, hka Aneesah ta dinga bin mutane dake ta shiga kotun da kallo tun daga kan 'yan uwa xuwa kan su karere, ta san ixuwa ynxu kam kotu ta cika tam, Abdul ne kadae bata gani ba, can sae ga motar gidan yari ta shigo haraban kotun tana kallo aka fito da Hydar, ya rame amma ba ssae ba, sae dai yyi haske bbu abinda ya ragu a kyansa, ta bi sa da kallon tausayi hawaye ya cika idonta har aka shiga da shi kotun 'yan sanda kusan biyar na biye da shi a baya, ta fashe da wani matsanancin kukan da bata san dalilinsa ba. Su oga Baffa sae surutu ake da abokanansa cikin kotun yana buga kirji yana fadin irin hukuncin da xa a yanke ma Hydar idan bae fito masa da 'yarsa ba don ga uwarta can hawan jini ya kamata ya sa an fita da ita waje tana karban treatment, Mujaheed da hankalinsa duk yana gun baffa duk da ba kallonsa yake ba, ya dinga murmushi yana buga kafa, Hajiya kam ko a jikinta don tasan tunda Mujaheed yana nn yau dole sae an yi bail dinn danta, don Mujaheed ba wasa ba, ba dan ba dan ba sae tace ma yafi Hydar iya aikinsa don Hydar slowly yake yin abunsa shi ko sharp sharp xae yi ya gama, sae tauna [8:14PM, 12/23/2016] Khaleesat: [12/8, 21:13] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 120..... Tun daga ranar Aneesah bata sake ganin Hydar ba sae dae taji muryarsa a gidan, kwata kwata ya daina shiga dakinta bare sabgarta iyaka idan ya dawo ya ba pretty abinda ya shigo da ta kai mata, sau dayawa sae dae ta fito da ledan da safe bata taba komai ba amma daga shi har kanwarsa bbu mai ce mata meyasa duk da ta lura Avoidin dinta ma yake da sassafe xae fice ya dawo late, duk tabi ta xama wani iri ta rame a gidan har pretty ta fara tausayinta don daga baya ta dinga nuna ma yayanta bata jin ddin abun da yake, shi kam sae yake nuna ko a jikinsa duk da ba hka bne , hkn yasa ta kan shiga ta xauna dakin Aneesah ko bata yi mata hira ba, kuma ta fara mata magana kan cewa ta dinga cin abinci dan ta rame ssae, sau dayawa Hydar kan ba pretty waya ta kai mata su gaisa da Ammi ko Abdul ko kuma faruuq, a sanyaye take karban wayar, taji kmr ta koma gun Amminta, duk sae taji bata son auren kuma da xae taimaka mata ya bata takardarta ta koma gidansu, amma tsoron yi masa magana ma take gaba daya. Ranar saturday tana kitchen da rana yunwa ya isheta tana dafa indomie, pretty bata nn ta tafi gidansu Ameera, tana jin shigowar motar Hydar gidan tayi sauri ta gama abinda take ta xuba a plate ta rufe sae kuma ta kasa fita da shi, ta fito falo ta tarda shi xaune yana danna waya, har ta manta yaushe rabon da ta gansa, ba tare da ta kallesa ba tace "ina yini," ta cigaba da tafiya abunta, ya juya yana kallonta har ta isa stairs snn yace "Aneesah" ta juya tana kallonsa yace "cum" ta komo cikin falon tana kallonsa ta dan durkusa snn tace "gani," yace "baki da lfya ne," ta sunkuyar da kanta tace "lfyata lau" yace "to kina da matsala ne," ta dan yi shiru snn tace "ehh," yana kallonta yace "ta me?" kmr xa tayi kuka tace "gidanmu nake son na wuce gun Ammina," yyi mata wani mugun kallo snn yace "to baxa ki je ba, tashi ki ban waje," tayi shiru kanta a sunkuye kuma taki tashi, ya daka mata tsawar da ta raxanata ta mike a tsorace ta fashe masa da kuka tace "wllh bana sonka ya Hydar bana sonka ka xo ka maidani gidanmu baxan sake xama gidan nn ba," ya mike tsaye yana kallonta yace "to tafi gidan naku," ya daka mata tsawa "nace ki tafi gidan naku, uban me kike tsinanamin a nn din banda bakin ciki da takaici ba, ni da xan iya da tuni na mayar dake gidanku Aneesah tsanar ki nake ji a xuciyata kawae" ta sulale kasa a hankali hawaye na bin kuncinta ta ma rasa me xata ce, ya juya a fusace ya haura sama, abincin da bata ci ba knn ranar, har washegari neman hawaye tayi ta rasa, pretty tayi tayi da ita ta gaya mata ko bata da lfya ne sae dae tace lfyarta kalau, daga karshe ma Hydar daina kwana gidan yyi sbda ita, ranar cikin kuka take ma pretty magana "pretty ni ban san me nayi ma ya Hydar ba ya tsaneni hka, ki tausayamin ki taya ni rokansa ya mayar dani gidanmu ya bani takardata don Allah," pretty tace "kinsan me kika masa Aneesah ki daina cewa baki sani ba," tana fadin hka ta fice daga dakin. Abun duniya ya ishe Aneesah ga xaxxabin da take ji kullum a jikinta, pretty na lura da hka tayi ma Hydar magana ya turo masu likita kawae ba tare da ya dawo ba, ita ce har drip uku amma hkn bae sa Hydar ya dawo dubata ko sau daya ba ita kanta pretty bata ji ddin hkn ba, bae dawo gidan ba sae rana friday da yamma ya shiga dakinta dubata ynxu kam jikin nata da sauki kwance ya tarda ta tana bacci ya dde xaune dakin yana kallonta snn ya fita. Wajen karfe goma na dare ya koma dakin yaji alamar wanka take ya fita, bayan kmr minti goma ya koma don ganinta kawae yake son yi mugun tausayinta yake amma baxae iya nuna mata ba, wnn karan tsaye ya ganta gaban madubi daure da towel tana gyara gashinta, ta juya a tsorace don bata san yana gidan ba, ya tsura mata ido daga bakin kofa duk ta yi mugun rama, ta juya da sauri ta ci gaba da abinda take gabanta na faduwa, ya karasa gaban madubin ya tsaya bayanta yan kallonta ta madubi bata dago ba bare ta kallesa, ya dafa kafadarta sae da ya dau lkci snn yace "ya jikin?" tunda ya daura hannu kan kafadunta jikinta ya dauki rawa ta kasa ce masa komai don tsoro, ya dago kanta yana kallonta ta madubi yace "magana nake," da kyar muryarta a sarke tace "da sauki," ya dan yi shiru snn ya juyo ta tana fuskantarsa yana kallon cikin idonta yace "wanka kika yi," da kyar ta shiga gyada masa kai ba tare da ta kallesa ba. A hankali yace "ki gaya min meke damunki," ta girgixa masa kai da sauri duk a rikice take tace "ba komai," ya dauko kayan barcinta da ya gani kan gado yana kallonta yace "ki sa kayanki ki kwanta," bae jira me xata ce ba ya fara kkrin kwance mata towel din idonsa cikin nata, ta rike a tsorace tace "wayyo ka bari xan sa," [12/8, 21:13] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 119..... Yau ma kmr kullum Hydar ya dawo ya xauna downstairs da kanwarsa, ta dauko masa abincinsa a dinnin ya kalleta yace "Aneesah fa," tace "tana daki," ya dan yi shiru snn yace "ita tafi karfin ta sakko tayi ma mutum sannu da xuwa ko?" pretty dae bata ce komai ba, shima bae sake cewa komai ba ya shiga cin abincinsa, suna hira da pretty, ya mike yace mata xae je yyi wanka tace masa to, ya haura sama, kallo daya yyi ma kofar dakin Aneesah ya kauda kansa ya bude dakin da ya koma kwana ya shige, wanka yyi, yyi sllh snn ya hada coffee ya shiga sha yana danna laptop, yana nn har kusan karfe sha daya snn ya sauko yyi ma pretty sae da safe ya koma ya kwanta, duk wnn abun da yake Aneesah na jinsa, ita kam ta rasa me tayi ma Hydar yake mata hka, ko sallama bae mata ba da safe ya fice sae gashi ynxu ma ya dawo bae bi ta inda take ba yaje yyi kwanciyarsa, kuka ta shiga yi a hankali wata xuciyar tace to ta je ta tambayesa taji ko laifi tayi masa, ta kai kusan minti goma xaune tana tunanin taje ko karta je, gashi ita mugun tsoronsa ma take, da kyar ta daure tana karanta addu'o'i a xuciyarta ta bude kofar dakin a hankali tayi hanyar dakinsa, murya can ciki gabanta na faduwa tayi sallama duk da tasan ba lallai bne yaji ba ma, ta turo kofar dakin a hankali ta tsaya daga bakin kofa, yana kwance ya tsura ma ceilin ido, ya maida dubansa gareta snn yace "ya dae, kina son wani abu ne," ta girgixa masa kai tana kkrin mayar da hawayen dake neman gangaro mata, a hankali tace "magana xan maka ya Hydar," ya mike xaune yana kallonta yace "ok ina jin ki," ta karaso cikin dakin a sanyaye ta xauna gefen gadon tayi shiru har sae da taji yace "ina jinki wace magana xa kiyi min," a hankali muryarta na rawa ta fara magana "ya Hydar ban san me nayi maka ba kke fushi dani ka daina kwana dakinka sbda ni, don Allah ka gaya min ko xan gyara..." tana kai wa nn ta fashe da kuka, ya kauda kansa da sauri can ya juyo ya dafa kafadarta cikin wani yanayi mae ban tausayi yace "to ya kike son nayi dake Aneesah, me xan maki, me kike bukata daga gareni, hakkin ki ko me," ya karasa maganar a fusace ta fashe da kuka don takaici ta kasa ce masa komai ta mike ta juya xata bar dakin ya fixgota a fusace yace " shi din kike so ko, kar ki damu xan baki hakkin ki amma sae na shirya," ta fixge hannunta tace "Allah ya kyauta bana bukatan hka, kuma ni bashi ya kawo ni ba, ya Hydar ka bani mamaki, dama ka auro ni ne don ka dinga cin xarafina kana musguna min Allah shine....." ta kasa karasa maganar ta fashe da wani matsanancin kuka ya mike yana kallonta yace "ae ba karya nayi ba Aneesah, ke din meye ne baki sani ba, meye baki yi ba, wlh tllh don kawae son da nake maki na ke xaune da ke ba don wani abu naki ba, komai naki baya burgeni Aneesah," Aneesah ta juya da sauri ta fice daga dakin tana da ta sanin shigan da tayi dakin, ynxu dama Hydar xarginta yake yi bata sani ba, ranar kasa bacci tayi, tai kuka tai kuka har ta gode Allah. Da safe tana xaune a daki abun duniya ya isheta Hydar ya shigo bata dago ba bare ta kallesa, ya karaso ya xauna kan kujera yace "kin tashi lfya," ta gaishesa ba tare da ta kallesa ba ya amsa snn ya mike yace "na fita office," tayi masa Allah ya kiyaye ya fice daga dakin, ta fada kan gado ta fashe da wani sabon kukan. [12/8, 21:13] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 121..... Hydar ya girgixa mata kai yana kallon cikin idonta kuma har lkcn yana rike da towel din yace "A'a i will help yhu," da ganinsa kasan ba shi bane, hankalin Aneesah ya tashi hawaye ya cika idonta muryarta na rawa tace "A'a ya Hydar wllh xan iya," ya daura yatsu biyu kan lips dinta a hankali yace "bana son musu, just stay still" bata sake yunkurin yin komai ba amma har lkcn tana rike da towel din, ya cire hannunta daga towel din ta shiga girgixa masa kai hawaye na bin kuncinta, yyi mata wani irin kallo, tana ji tana gani ya cire towel din jikinta ta fashe masa da kuka tare da durkushewa a kasan tiles duk da akwae kaya daga ciki, Hydar ya bita ya dago ta kan yace komae tace "A'a ya Hydar don Allah ka rufa min asiri ka bari bana so," yace "sbda me?" a gigice ba tare da ta sani ba tace "kunya nake ji," yace "ko" ta gyada masa kai da sauri, yace "gud! yau xan raba ki da munafukin kunyar da kike min, amma ae baki ji kunyar Mujaheed ba" bae jira mae xata ce ba ya shiga kissn dinta, kuka ssae ta shiga yi tana turasa, hkn bae sa ya saketa ba ya ci gaba da abinda yake kmr xae cinyeta, tsoro ya cika Aneesah jikinta ya dau rawa ganin abubuwan da yake mata har lkcn bata daina kukan da take tana rokansa ba, shi ma bae fasa abun da yake ba, ganin irin abinda Hydar ke mata yasa ta fasa ihu ya rufe bakin da sauri yana mata wani irin kallo yana mayar da numfashi, idonsa ya sauya launi, jikinta na rawa tace "No ya Hydar ka daina min hka tsoro nake ji kayi hkuri don Allah ka kyaleni," shaketa yyi yace "kika sake min magana xan baki mamaki, xan maki abinda baki xata ba ynxun nn," ba shiri ta hadiye kukan da take xuciyarta na mugun bugawa, ya ci gaba da abinda yake abun ma sae taga kmr mugunta yake mata, ajiyar xuciya kawae take don ynxu ta daina kukan, ganin yana shirin rabata da pride dinta kuma a walakance yasa ta kankamesa tace "No ka tsaya ya Hydar ka tausaya min kar ka min hka," da kyar ya iya ce mata plss duk da bae ma san ya fadi hkn ba, hkn yasa ta bar shi ya ci gaba da abinda yake tana kuka a hankali, gani tayi ya turata ya mike kmr wanda aka tsikara da allura ya koma kan gado yyi rub da ciki yana mayar da numfashi, ta mike xaune tana kuka a hankali, a tunanunta kukan da take ne ya basa haushi, hkn yasa ta mike tsaye da kyar ta daura towel dinta tayi hanyar gadon ta xauna gefensa muryarta na rawa tace "kayi Hkuri ya Hydar wllh baxan sake kukan ba," ganin yyi shiru yasa ta dan matso kusa da kansa tace "kaji ya Hydar baxan sake kuka ba kome xaka min, kayi hkuri," ya mike a fusace yace "nayi hkuri na cigaba ko me? Na biya maki bukatanki kike nufi ko, to karki damu ba sae kin marairaice min kina kuka xan baki hakkin ki ba," ta xaro ido kan tace komai ya fixgota ya jefar kan gadon, kuka ssae ta fashe da tace "wllh bana so, ka kyaleni kar ka taba ni idan ba hka ba xan maka ihu" bae saurareta ba ya fara aiki, kuka take tana fixge fixge tana dukansa amma yaki saketa daga karshe ma wanka mata mari yyi tayi tsit tana maida numfashin tsoro, lallai Hydar bae da imani ta shiga uku kasheta xae yi yau, rungumesa tayi ko xae ji tausayinta amma taga alamar kawae mugunta ma yake shirin mata, wani gigitattcen kara ta saka ta kankamesa, lkci daya kuma ta sake sa tayi tsit, Hydar ya kasa sarara mata duk da abinda ya lura, wani ihun ta sake yi na wahala wnn karon ma tsit tayi lkci daya kmr daxu, daga nn bata sake yin wani ba, hkn yasa ya dago ta a gigice yana kiran sunanta amma shiru, ya jawo fitila da sauri xae kunna ta rungumosa cikin murya mai ban tausayi tace "kar ka kunna plsss," sae kuma ta fashe da wani matsanancin kukan wahala tana kiransa, gefe ya koma ya xauna hade dafe kansa yana mayar da numfashi, kkrin sauka ta shiga yi daga kan gadon ya rikota da sauri muryarta na rawa tace "ya Hydar xan mutu xafi don Allah ka taimake ni," ya rungumeta ssae yana girgixa mata kai ya kasa cewa komai, hawayensa ta dinga ji a bayanta ta dago da sauri tana lalubar fuskarsa, ta fashe da kuka tace "me ya faru yayana baxan sake maka ihu ba wllh," ya rungumeta ssae da kyar har lkcn yana hawaye yace am ssrry Aneesah plss ki yafe min am beggin yhu, na cuce ki na xalunce ki..." sae ya kasa karasawa, ta girgixa masa kai tana kwance kirjinsa tace "ni baka min komai ba yayana ka daina hawaye a kai na," da kyar yace "ban maki adalci ba Aneesah na xarge ki a kan abunda ba hka bne," a hankali tace "in my nxt lyf baxan sake yin mistake din da nayi yasa kke xargina ba, ba laifinka bne Ya Hydar" ta fashe da kuka ssae ya jawo bargo ya lulluba masu, ranar daga ita har shi bbu wanda yyi bacci don nn da nn xaxxabinta ya tashi jikinta ya dau xafi ssae, hankalinsa ya tashi ya rasa abun yi, kuka ta dinga masa ta rasa inda xata sa ranta, ya dauko doguwar rigarta yace "tashi in sa maki kaya mu tafi asibiti Aneesah," ta girgixa masa kai da kyar alamar baxata ba, dole ya shiga kiran likitansa amma wayarsa a kashe, to ynxu wa xae kira, Abdul ya fado masa kome ya tuna kuma sae ya fasa kiransa. [12/8, 21:13] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 123.... Hydar ya fito ya tarda pretty tsaye yace ya dae? tace "me xa a girka mata yaya?" yace "pepper soup kawae xaki mata amma ki fara gyara dakin tukunna" yana kai wa nn ya fice xuwa dayan dakin ya shirya, ita ko ta shiga gyara dakin tana cikin moppn bayan ta daura xanin gadon kan kujera ba tare da ta lura da kmai ba nufinta in ta gama sae ta linke ta ajiye taji Aneesah na kwarara amai ta juya da sauri tayi kanta ta riketa ta dinga aman ga drip hannunta, dole pretty ta shiga kwala ma yayanta kira ya shigo da sauri yana tambayr lfya ya rike Aneesar yace ta debo masa ruwa ta debo da sauri ta kawo masa, Aneesah ta fada kansa tana mayar da numfashi, ya ciro wayarsa ya kira Dr umar yaki shiga hkn yasa ya kira Abdul kawae cikin minti ashirin ya iso gidan, sae da ya fara cire mata drip din snn Hydar ya kwantar da ita kan gado, Abdul yace "me ya sameta? Hydar yace "xaxxabi take" Abdul ya durkusa kusa da ita yana kallnta yace "ina ke maki ciwo Aneesah" tayi shiru bata ce komai ba sae hawaye, Hydar ya kirasa suka fita waje, Aneesah ta mike da kyar xata shiga bathroom taji ta kasa tafiya, pretty ta lura da hka tace "me ya sami kafar?" bata ce komai ba ta koma ta xauna, ita ko ta ci gaba da abinda take ta dauki xanin gadon xata linke taga jini, ta juya tana kallon Aneesah da tayi saurin juyawa taji kmr ta nutse kasa don kunya, pretty ta shiga bathroom da bedsheet din a sanyaye ta fito ta fita daga dakin, magunguna kadae Abdul ya bata ya bar gidan, Hydar na xaune gefenta bayan ya rakata bathroom, pretty ta shigo ta ajiye abinda ta girka ma ta ta fita, ya bita har downstairs yana kallnta yace "meyasa kika ma Aneesah sharri Zainab" ta fashe da kuka tace "yaya ni ban mata sharri ba wllh abinda na gani na gaya maka" ya juya bae ce mata komai ba ya koma sama, lallai Mujaheed na son Aneesah, kula ssae Aneesah ta dinga samu daga Hydar da kanwarsa, canxawan pretty lkci daya gareta ya bata mamaki, shiri ssae suka fara yi kmr da, Hydar kam ko da yaushe yana manne da ita amma ko da wasa bae taba nuna mata xae sake kusantar ta ba hkn yasa ta saki jikinta don da dari dari take da shi don ya gama bata tsoro, wani soyayya ta daban ya shiga nuna mata har abun ya dinga bata mamaki take ganin kmr ba Hydar ba, duk bayan kwana biyu ya kan kaita gun Amminta, wani lkcn su biya gidansu Mujaheed, Hajiyarsa na bala'in ji da ita tana sonta. Ranar wata asabar Hydar yace masu Hajiya xata iso gobe tare da Meenah, suna ta murna ita da pretty suka shiga masu girki kala kala, da yamma suka iso murna kam ba a magana gun Aneesah don taji kewan Hajiyar ssae, meenah jikinta yyi sauki kmr ba ita ba, akwatuna sha takwas ta dawo da, goma na Aneesah, takwas kuma na Mujaheed da yace tayi masa, da Hajiya tayi masu maganar biki Aneesah ca tayi ita bata so a bari kawae, Hajiya tace lallai sae anyi hkn yasa suka yi fixin date din bikin, da daddare Hajiya ta kira Mujaheed ya xo gidan ya dauki boxes dinsa yana shigowa bayan sun gaisa da Hajiya Aneesah da pretty da Meenah suka shiga bude masa kayan ciki ya gani ko sunyi, shi dae dariya kawae yake yana cewa kai amma Hajiya kin iya xabe, sae da suka gama suka rufe snn yana kallon pretty yace sun maki ko sae an karo? Duk suka tsaya kallonsa kmr sha sha shai, yyi dariya yace "to fitsararriya ai naki ne kin wani xage ko kunya bbu kina bubbudewa," duka suka sa dariya banda ita, Hajiya tace "kmr ya Mujaheed," yace "kayan lefenta ne Hajiya," da sauri pretty ta mike tayi hanyar stairs meenah da Aneesah na ta dariya, pretty bata gama yarda da batun Mujaheed ba sae da taga an kawo sadakinta, daurin aure da biki rana daya aka sa da nasu Aneesah da Hydar," tare da Abdul mujaheed ya dinga xirga xirgan bikin nasu, Abdul yace "to ni xaka bani kanwarka Ameera" Mujaheed yyi dariya yace "idan ka min alkawarin xaka daina shan wine," ana saura sati daya bikin nasu Aneesah ke ma Hydar maganar jamb dinta yace "sae ki jira nxt yr don har an xana,"Aneesah taji haushi ssae amma bata ce komi ba don tasan Hydar na sonta da karatu baxae hanata yi ba, daren ranar bikinsu suna kwance da Hydar dinta a gidansu da suka tare nn Abj bayan kowa ya watse ita ma pretty an kai ta nata gidan yace "kanwata ki gaya min me xan maki a rayuwa da xaki yafe min xargin ki da na dinga yi a baya don Allah, har yau na kasa daina jin haushin kai na," tayi murmushi tayi lamo a kirjinsa snn tace "na farko yayana ku taimaka a sakar min baffana, na biyu xan so ka taimaki mutanen da na xauna gunsu a kauye, snn lastly ka rike ni amana yayana kasan ni marainiyace," kmr xatayi kuka ta karashe maganar ya kankameta yace an gama kanwata, amma yara nawa xaki haifa min? Ta boye fuskarta tace "nima ban sani ba yayana," yyi dariya yace "sha biyu nake so," bae jira mae xata ce ba ya rufe su da bargo ya kankameta yana dariya yace "I LOVE U ANEESAH.*** To fa! Alhmdlh ni dae a nn na sauke littafina mai suna #Aneesah, Allah bar xumuncin mu ya kuma sa mu cika da imani. Taku har kullum Jiddah M. Bello, A.k.A... Khaleesat Haiydar, na barku lfya. [12/8, 21:13] ‪+234 803 751 8717‬: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 122.... Ganin bae da wani alternative yasa yyi decide gobe ya kira abokin nasa kawae da safe, ya shiga bathroom ya hada ruwan xafi ya xuba dettol ya fito ya sameta tana kwance ta dukunkune cikin bargo sae kuka take ya dauketa ya shiga da ita bathroom sae da ya tabbatar ya gasa ta ssae snn ya taimaka mata tayi wankan tsarki tayi alwala ya fito da ita, ya cire bedsheet din ya kwantar da ita ya lullubeta da bargo jikinta ya dau xafi ssae sae rawan sanyi take, duk ya rikice ya rasa abinda xae mata ga mugun tausayin ta da yake, Aneesah yarinya ce ssae da ya sani da ya barta ta kara girma kafin yyi mata komai, but hkn kuma ya kauda xargin da yake mata, yaji haushin kansa ssae kan xargin da ya dinga mata a kan abinda bata sani ba, but meyasa pretty tayi masa karya, shi dae yasan Mujaheed baya kwana daki daya da mace lafiya, ya dafe kansa duk yaji jikinsa yyi sanyi yana nn xaune kusa da ita tayi bacci har asuba, ya mike yaje yyi wanka yyi alwala snn ya fita xuwa masallaci, karfe shidda da rabi ya shigo ya tarda ta kasa tana kwarara amai, hankalinsa yyi mugun tashi ya rike ta da sauri yana mata sannu, ta fada kansa tana kuka ssae duk ta rame daga jiya xuwa yau, ga jikinta kmr wuta, ya ciro wayarsa ya shiga kiran likita yyi masa bayani snn ya ajiye wayan yana kallonta cike da tausayinta yace "am srry Aneesah na baki wahala ko?" bata ce komai ba sae mayar da numfashi da take duk ta langwabe masa da ganinta kasan taji jiki, ya dauko doguwar rigarta ya saka mata ya hado mata tea da kyar ta sha kadan snn ya rungumeta yana lallabata har likitan ya xo ya sa mata ruwa snn ya mata allurori ya ba Hydar magungunan da xae bata, Hydar yyi masa gdya ya rakasa ya dawo cikin gidan, falo ya tarda pretty ta gaishesa tace "wae jikin Aneesah ne har ynxu naga Umar ya fita," yace "eh dubata ya xo yi," yana fadin hka ya haura sama, bacci ya tarda ta tana yi, ya xauna gefenta na dan lkci yana kallonta snn ya shiga bathroom yin wanka don yana da wani case ranar, yana wanka pretty ta shigo dakin ta karasa kusa da gadon tana kallon Aneesah. Like · 4 · Reply · Report · 8 minutes ago [8:15PM, 12/23/2016] Khaleesat: ~Aneesah~ By Khaleesah Haiydar 123.... Hydar ya fito ya tarda pretty tsaye yace ya dae? tace "me xa a girka mata yaya?" yace "pepper soup kawae xaki mata amma ki fara gyara dakin tukunna" yana kai wa nn ya fice xuwa dayan dakin ya shirya, ita ko ta shiga gyara dakin tana cikin moppn bayan ta daura xanin gadon kan kujera ba tare da ta lura da kmai ba nufinta in ta gama sae ta linke ta ajiye taji Aneesah na kwarara amai ta juya da sauri tayi kanta ta riketa ta dinga aman ga drip hannunta, dole pretty ta shiga kwala ma yayanta kira ya shigo da sauri yana tambayr lfya ya rike Aneesar yace ta debo masa ruwa ta debo da sauri ta kawo masa, Aneesah ta fada kansa tana mayar da numfashi, ya ciro wayarsa ya kira Dr umar yaki shiga hkn yasa ya kira Abdul kawae cikin minti ashirin ya iso gidan, sae da ya fara cire mata drip din snn Hydar ya kwantar da ita kan gado, Abdul yace "me ya sameta? Hydar yace "xaxxabi take" Abdul ya durkusa kusa da ita yana kallnta yace "ina ke maki ciwo Aneesah" tayi shiru bata ce komai ba sae hawaye, Hydar ya kirasa suka fita waje, Aneesah ta mike da kyar xata shiga bathroom taji ta kasa tafiya, pretty ta lura da hka tace "me ya sami kafar?" bata ce komai ba ta koma ta xauna, ita ko ta ci gaba da abinda take ta dauki xanin gadon xata linke taga jini, ta juya tana kallon Aneesah da tayi saurin juyawa taji kmr ta nutse kasa don kunya, pretty ta shiga bathroom da bedsheet din a sanyaye ta fito ta fita daga dakin, magunguna kadae Abdul ya bata ya bar gidan, Hydar na xaune gefenta bayan ya rakata bathroom, pretty ta shigo ta ajiye abinda ta girka ma ta ta fita, ya bita har downstairs yana kallnta yace "meyasa kika ma Aneesah sharri Zainab" ta fashe da kuka tace "yaya ni ban mata sharri ba wllh abinda na gani na gaya maka" ya juya bae ce mata komai ba ya koma sama, lallai Mujaheed na son Aneesah, kula ssae Aneesah ta dinga samu daga Hydar da kanwarsa, canxawan pretty lkci daya gareta ya bata mamaki, shiri ssae suka fara yi kmr da, Hydar kam ko da yaushe yana manne da ita amma ko da wasa bae taba nuna mata xae sake kusantar ta ba hkn yasa ta saki jikinta don da dari dari take da shi don ya gama bata tsoro, wani soyayya ta daban ya shiga nuna mata har abun ya dinga bata mamaki take ganin kmr ba Hydar ba, duk bayan kwana biyu ya kan kaita gun Amminta, wani lkcn su biya gidansu Mujaheed, Hajiyarsa na bala'in ji da ita tana sonta. Ranar wata asabar Hydar yace masu Hajiya xata iso gobe tare da Meenah, suna ta murna ita da pretty suka shiga masu girki kala kala, da yamma suka iso murna kam ba a magana gun Aneesah don taji kewan Hajiyar ssae, meenah jikinta yyi sauki kmr ba ita ba, akwatuna sha takwas ta dawo da, goma na Aneesah, takwas kuma na Mujaheed da yace tayi masa, da Hajiya tayi masu maganar biki Aneesah ca tayi ita bata so a bari kawae, Hajiya tace lallai sae anyi hkn yasa suka yi fixin date din bikin, da daddare Hajiya ta kira Mujaheed ya xo gidan ya dauki boxes dinsa yana shigowa bayan sun gaisa da Hajiya Aneesah da pretty da Meenah suka shiga bude masa kayan ciki ya gani ko sunyi, shi dae dariya kawae yake yana cewa kai amma Hajiya kin iya xabe, sae da suka gama suka rufe snn yana kallon pretty yace sun maki ko sae an karo? Duk suka tsaya kallonsa kmr sha sha shai, yyi dariya yace "to fitsararriya ai naki ne kin wani xage ko kunya bbu kina bubbudewa," duka suka sa dariya banda ita, Hajiya tace "kmr ya Mujaheed," yace "kayan lefenta ne Hajiya," da sauri pretty ta mike tayi hanyar stairs meenah da Aneesah na ta dariya, pretty bata gama yarda da batun Mujaheed ba sae da taga an kawo sadakinta, daurin aure da biki rana daya aka sa da nasu Aneesah da Hydar," tare da Abdul mujaheed ya dinga xirga xirgan bikin nasu, Abdul yace "to ni xaka bani kanwarka Ameera" Mujaheed yyi dariya yace "idan ka min alkawarin xaka daina shan wine," ana saura sati daya bikin nasu Aneesah ke ma Hydar maganar jamb dinta yace "sae ki jira nxt yr don har an xana,"Aneesah taji haushi ssae amma bata ce komi ba don tasan Hydar na sonta da karatu baxae hanata yi ba, daren ranar bikinsu suna kwance da Hydar dinta a gidansu da suka tare nn Abj bayan kowa ya watse ita ma pretty an kai ta nata gidan yace "kanwata ki gaya min me xan maki a rayuwa da xaki yafe min xargin ki da na dinga yi a baya don Allah, har yau na kasa daina jin haushin kai na," tayi murmushi tayi lamo a kirjinsa snn tace "na farko yayana ku taimaka a sakar min baffana, na biyu xan so ka taimaki mutanen da na xauna gunsu a kauye, snn lastly ka rike ni amana yayana kasan ni marainiyace," kmr xatayi kuka ta karashe maganar ya kankameta yace an gama kanwata, amma yara nawa xaki haifa min? Ta boye fuskarta tace "nima ban sani ba yayana," yyi dariya yace "sha biyu nake so," bae jira mae xata ce ba ya rufe su da bargo ya kankameta yana dariya yace "I LOVE U ANEESAH.*** To fa! Alhmdlh ni dae a nn na sauke littafina mai suna #Aneesah, Allah bar xumuncin mu ya kuma sa mu cika da imani. Taku har kullum Jiddah M. Bello, A.k.A... Khaleesat Haiydar, na barku lfya. VISIT www.aihausanovels.com.ng For More Novel. AIHAUSANOVELS is website consists of hausa novels note, the reason of launching this site is to Entetaint, Motivate and Educate our readers. We provided hausa novels of many type, Such Adventure, love, romance, fiction, non-fiction, mystry, fantasy, action e.t.c from hausa Authors We provided a new and old novels both softcopy and hardcopy from our Author with thier permission. AIHAUSANOVELS shafin yanar gizo ne wanda yake ?auke da littattafan hausa, dalilin bude wannan shafin shine domin Kayatar masu karatu da kuma ilimantar da su. Mun samar da littattafan hausa na nau'uka daban-daban, kama daga littafin, soyayya, tatsuniya, almara, Hikayoyi, gyara kayanki (yadda mata zasu kula da kansu a gidan mijinsu) da dai sauransu, daga Marubutan hausa.