[10:34PM, 8/6/2017] ‪+234 703 448 8635‬: 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty mmn Faty July, 2017 Bismillahirrahmanirrahim, ina godia ga Allah daya bani ikon fara rubuta wannan littafi, sannan wannan qagaggen labarine banyishi dan wata ko wani ba, Allahu yasa mudace, Ameen👏🏻 0⃣1⃣ "Alhaji Abubakar Muhammad da Alhaji Usman Sanusi, aminan junane qud da qud wanda hakan yasa suka zama tamkar yan uwa na jini " " Alhaji Abubakar haifaffen garin Dambam ne ta jihar bauchi, wanda yakasance d'a na uku ga sarki Muhammad bin Abdurrahman wato sarkin dambam" "Alhaji Usman Sanusi shikuma d'ane ga malam Sanusi mai almajirai wanda ya kasancewa malamin sarkine a fada kuma limamin babban masallacin garin dambam" Tun tasowansu suke abota mai qarfi, tare suke Komai kusan ba wadda bai san da zaman abotarsu ba" "kasancewar gidansu ba nisa atsakani, tare suke cin abinci hatta bacci basa raba makwanci sabida Alhaji Abubakar bai dauki kansa da wani abuba haka zasuje gidansu Alhaji Usman suci abinci hatta kwana sunayi tare acan" "tare sukayi primary da secondary school dinsu, bayan sun qare ne daganan suka rabu amma rabuwa na wajen zama" "Alhaji Usman shi baicigaba da karatu ba daganan ya fara kasuwanci, yana kuma noma, yayinda Alhaji Abubakar kuma yasamu fita waje qasar india karatu inda yasamu gurbin karatu a jami'ar new delhi yana karatun likitanci" "Ranan da zasu rabu sai da sukayi kuka kamar wasu yara qanana, haka Alhaji Usman yayi ta zaman kadaici wadda daqyar ya saba da hakan" "acan new delhi ma haka Alhaji Abubakar da qyar yasaba da kewan gida had'i da rashin aminnsa, ya fiskanci karatunsa sosai, lokacin da yayi shekara 1 anan ne yazo gida, yana arba da aminnsa sai kukan murna, ranan kwana sukayi suna hirar yaushe gamo " " hutunsa na qarewa ya koma daganan bai sake zuwaba sai bayan Shekara guda da haka2 har ya kammala karatunsa, lokacin daya dawo gida yasanar da mahaifinsa cewar yazo ne amma zaikoma dan yasamu aiki acan sannan kuma yana da shaawar zama nawani lokaci acan, mahaifinsa baiqi ba amma yasanar masa sai dai ya tafi da iyali dan bazai je can ya auro wata qabila ba ya kuma amince da hakan " " yana fitowa gida wajen aminnsa ya nufa sai dai abin farin ciki ya tarar amininsa yayi aure watanni hud'u da suka wuce " " nan suka sha hira inda ya kawo masa alheri sosai kamar yadda yasaba dik lokacin daya zo , ya kuma sanar masa batun komawarsa hadda abinda mahaifinsa ya fad'a, ya taya shi murna kwarai " " Alhaji Abubakar ya nisa yace kasan meye aminina? Aa sai kafad'a ya amsa masa, yace wlh nibansan ta ina zan fara neman matar bama kuma na tabbata mai martaba bazai lamunce mun tafiyar nan batare da dana cika umarninsaba, Alhaji Usman yace inaga abinda zaifi kawai kabasu zabi nasan bazasu maka zaben tumun dare dare ba, nan yayi naam da shawarar aminnsa" "nan suka shiga cikin gida wajen matar aminnsa, suka gaisa ya kuma yaba da hankalin ta sosai inda yayi addu'a Allah ya bashi mata mai natsuwa kamar matar aminnsa " " lokacinda Alhaji Abubakar yajewa mahaifinsa da zancen ya basu zabin matar dazai aura sunyi farin ciki nan take mai martaba yayi shawari da uwargidansa nan suka tsaida zance akan zaa hada shi da saudah yar kanin mai martaba " Cikin qanqanin lokaci aka tsaida maganar aure, saura sati daya sutafi aka d'aura aure, cikin kwana uku aka gama shagalin biki, ana gobe zasu tafi suna sallama da amininsa sai Alhaji Usman yace shikenan yanzu inkatafi da iyalinka xumuncinmu ya qare kenan dan bawanda yasan sanda zaka sake zuwa kuma " "yace haba dai ai zumuncin mu har 'ya'yanmu sai sunyi, nidai kamun alqawarin idan Allah yasa da namiji ka haifa to motarsa acikin yara nane idan kuma nine nafara haifan da namiji to matarsa tana acikin 'ya'yanka, na amince aminina Allah yasadamu da alkhairi, nan suka rungume juna da qyar suka rabu " *INDIA* " tinda Alhaji Abubakar yatafo da matarsa saudah new delhi, bai sake waiwayan gida ba, afannin aikinsa kuwa yasamu ci gaba sabida kwazonsa, har kwatance suke da shi a asibitinsu sabida kwarewar sa akan aikinsa" "zamansa da saudah zamane na amana ahankali suka fara son junansu, cikin qanqanin lokaci Alhaji Abubakar ya kamu da son saudah fiye da tunani sabida saudah wayayyar mace ce, nan itama ta sami wata college ta ci gaba da karatunta " " Bayan shekara 1,saudah ta haifi yarta mace kyakyakyawa kamarta daya da mamanta, suka mata suna da *MABARUKHA*, sai da mabarukha ta shekara tukun suka shirya zuwa gida nigeria " *NIGERIA* " afannin hajar matar Alhaji Usman kuwa, har yau Allah bai basu haihuwa amma hakan bai d'aga hankalinsu ba dan sunyi tawakalli da Allah shine mai badawa da hanawa " " watarana Alhaji Usman yadawo kasuwa da yamma suna zaune shida hajar atsakan gida suna hira, kwatsam sukaji sallama, wazasu gani Alhaji Abubakar d matarsa harda yarsu " " sunyi murna sosai da ganinsu, nan yake cewa tin jiya da dare muka iso, dasafe kuma nasan katafi kasuwa shiyasa nace mubari sai dayamma sai mushigo, nan sukasha hiransu, hajar tana riqe da mabarukha kamar subarmata ita dan yarinyar tashiga ranta " " watansu 1 suka koma new delhi, tinda suka tafi basu sake zuwa ba sai bayan shekara uku nanma suka zo da yarsu mai watanni 9,takwarar mahaifiyar Alhaji Abubakar Maryam suna karanta niima, awannan zuwan ne da yayi ne ya biya masu hajji shida amininsa " " inda suka tsananta addu'a aka'aba akan Allah ya cika masu burinsu, na alqawarin da suka d'aukanma junansu" "Bayan sun dawo ne Alhaji Abubakar suka koma Bayan shekara 1 abin mamaki sai saudah tasamu ciki, dik da planning dasuke, haka suka reni cikin har yakai haihuwa, saudah ta haifi da namiji kyakykyawan gaske kamarsu 1 da babansa, suka saka masa suna *Muhammad Alameen* takwaran mai martaba, amma sabida babban suna gareshi yasa suka masa alkunya da *Papa* wato baba sunbi harshen india " " papa nada watanni shida suka zo nigeria, kowa yayi farin cikin qaruwan da rana suka samu, awannan zuwan ne yasaima amininsa gida mai, sunje ganin gidanne Alhaji Abubakar yace ma amininsa, kaga lamarin ubangiji ko sabida haka kada ka fidda rai Allah y rubuta matar papa daga cikin yaranka ne shiyasa Allah bai baku haihuwa ba har yanzun " " Alhaji Usman yace Allahu yashaa, inanan kullum ina addua Allah yabani haihuwa, Alhaji Abubakar yace insha Allah, Allah zai baka, bayan sati biyu suka koma india " ✍🏻Faty Mmn Faty [10:35PM, 8/6/2017] ‪+234 703 448 8635‬: 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye 🤷🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty mmn Faty July, 2017 *Wannan page nakune Mmn Faty Fans, Allah yabar qauna, Mmn Faty luvs u all 😍😘* 0⃣2⃣ "Kwanaki sun wuce, watanni sun shud'e, shekaru sunja, Allahu maji roqon bawansa " " Kwatsam ba zato, ba tsammani Allah ya azurta hajar da samun ciki, murna farin ciki ba kalan da basu yiba, hatta wani nasu ma ya taya su murna matiqa " " cikin ikon Allah suka raini cikin lfy har tasauqa lfy, ta haifi yarinya mace, kyau kam kamar ita tayi kanta, dik wadda ya kalleta sai yace masha Allah, ranan suna taci sunan mahaifiyar Alhaji Usman wato Fateema suna kiranta da Fauziyyah, tindaganan kuma basu sake samin haihuwaba " " haka suka ci gaba da rainon Fauziyyah cikin so da kulawa, Fauziyyah ta taso cikin gata sai dai son dasuke mata bai hana su tarbiyantar da ita ba " " Fauziyyah tana da shekara 4 aka sakata a makarantar allo sai dai me, albasa batai halin ruwa ba, dan Fauziyyah bata dakko halin mahaifinta na haquri ba baran mahaifiyarta dako yatsa kasa mata abaki haka zaka cireshi " " wasa, barna, tsokala dik ta had'a abin baa cewa Komai, idan taje makaranta wanda tafishi tadakeshi, wanda ya fita kuma ta tsokaleshi malam har gaji da kawo masa qarar ta da ake, gashi dududu shekarar ta 4" "Fauziyyah nada shekara 6 aka sanya ta a makarantar primary, nan danan kowa yasanta a makarantar dan Fauziyyah akwai ilmi gata yarinya qarama , uwa uba kuma tsokalalta su suka saka kowa yasanta " " tin abitace *Nawwar* nazo maka gargadi ne kafita Daga rayuwar *sameeratun* *nawwara* idan kuma ba haka ba , kai da'ita zaku fuskanci" mummunan tashin hankali arayuwar Ku, don baza mu kyale kowani bil adama ba yashiga cikin rayuwar mu. yanxu haka *sameeratun* *nawwara* tana can tana fuskantar mummunar hukunci, saboda tasaba mawa dokar mu, *nawwar* yayi saurin cewa don Allah Ku kyaleta karku" mata komai, ta daka mashi tsawa tare da cewa, kai har ka isa kafada mana abunda zamuyi, ina kara gargadin ka" akaro na biyu, Daga fita Daga cikin rayuwar da bata shafe ka ba, Idan kunne yaji Gangar jiki yatsira. zai yi magana kenan wuf ta bace mai, ya sauke ajiyar zuciya tare da hawaye mai radadi dake gangaro mai, zuciyarshi sai har bawa take kamar zata fito, sboda tsananin zafin dayake mai. jikinshi duk ya mutum kamar Wanda akamai duka, dakyar ya iya Jan mortar sa zuwa hospital" lokacin dayayi parking din mortar sa alokacin abokinsa shima yayi parking din nasa" nawwar ya bude mortar zai fito yakasa ganin halin dayake ne yasa abokinshi me suna awwal" ya karaso wajan da Sauri cikin kidimewa, yana fadin nawwara lafiya naganka haka? meke damunka? cikin karfin hali nawwar ke nuna mawa awwal zuciyar alamun ita ke mai zafi, amma yakasa magana" awwal ne ya taimaka mashi suka karasa cikin hospital din. dayake shi doctor be a fannin zuciya, ya kwantar dashi kan gadon sake office dinsa ya dubasa da kyau, tare dayi mashi allura da bashi magani" har bacci yayi awon gaba dashi" awwal ya zauna shiru yana tunanin wani irin damuwa ne abokinshi yake ciki" da har ciwon zuciya takamashi, Allah sarki nawwar, Allah ya yaye maka koma menene. *************** tun lokacin da sameeratun nawwara tabar gun nawwara ake gallaza mata azaba aduniyar su ta aljanu" don ta taka dokan da aka mata, daure take jikin wani bishiya ta tsafi duk kaca ne jikinta, yayin da wasu irin halittu ke jibgarta da bulalan wuta, tana ihu saboda tsananin azaban zafi. gefe daya kuma wani mutum ne azaune cikin kayataccen kijera ta alfarma irinta sarauta da alamu shine shugaba" sai dariyan keta yakeyi, irinta ta mugaye. yana kallon yadda ake wahalar da sameeratun nawwara, saida da ya bari tasha wahala sosai har bata motsi sannan yace adakata" ya karaso wajanta dai dai fuskarta yasa hannunshi yadago fuskarta, yace haryanxu, kina cikin bakanki na kin" aure na, tayi karfin hali tace eh, bazan aureka ba, ba zan aureka ba, koda zan rasa raina ne , kamar yadda " kuka rabani da farin cikin to kuma har abada bazaku taba samun naku farin cikin ba, don nawwar shine mijina, na har abada, *Ambar* yayi saurin ja da baya yana cewa, cewa karyanki ne kija dani sameeratun nawwara, sai kinzama tawa, banga wani bil adaman daya isa yashiga gonata ba , mahaifinki shi yaja miki sameeratun nawwara" ni nan *ambar* sai na mallake ki, duk cikin tsawa yake maganar nan, kuma sai naga bayan wannan nawwar din, tanaji ya ambato nawwar dinta , itama cikin Daga murya tace karya kake ambar , indai INA da sauran numfashi baka Isa ka halaka nawwar ba, don yafi karfinka" ji tayi an wurgo mata wani katon dutse dai dai saitin bakinta" har Saida hakorarta yafadi, ta dafe gun tare da juyowa" taga wanene , ido hudu sukayi da kanwar ambar, me suna *kiyara* tana dariyar mugunta. cikin tsawa tace baki da hankali kike fada mawa shugaban mu magana " saina koya miki darasi, cikin iska tazo da gudu zata shake" wuyan sameratun nawwara, sai taji ansha ke nata wuyan, bataganin Wanda, yashake ta" saboda wani irin guguwar iska ce" ke tashi, *kiyar* da *ambar* sunshiga rudu saka makon ganin wannan halittar, cikin yaransu wannan halittar take cewa " duk da na mutu baza kubarni na huta ba, sai kun binci koni. TAKU UMMU RUMAN *nusnim* *pyar* [1/11, 4:39 PM] ‪+234 806 448 1931‬: *ALJANA* *CE* *KO* *MUTUM* 1⃣5⃣&2⃣0⃣ duk dana mutu ma bazaKu barni na huta ba? sai kun bincikoni kun hanamin kwanciya cikin natsuwa?, bakin kiyara yafara rawa, cikin rawar murya tace kiyi hakuri sameeratun nawwara bamu san kina tare da itaba, ambar shima yashiga bata hakuri, cikin daga murya tace" ya isheku haka, meyasa zaku takura ma rayuwar ta? kun manta abunda nace kafin na mutu" kenan baku rike amanar dana barmuku ba? ambar yace a'a ba haka bane, toh inba haka ba meyasa zaku takura rayuwarta? kiyara tace Allah yaja zamanin gimbiya sameearatu, ta taka dokan da aka kafa mata ne shiyasa, soyayya taje tanayi da jinsin bil adama, wanda hakan kinsan yasabawa dokan da aka gindaya mata" gimbiya sameeratu tayi saurin zabura cikin kakkauran murya tace soyayya da bil adama, me kukeyi har tafara soyayya da bil adama? tuntuni kuka kasa daukar wani mataki da wuri sai yanxu?, duk cikin fushi da d'aga murya take maganar, nan take ran gimbiya sameeratu ya kara mugun baci, babu abinda ta tsana arayuwarta irin bil adama, saboda su sukayi ajalinta tabar duniyar su. *sai agaba zamuji wacece gimbiya sameeratu, kuma menene alakarta da sameeratul nawwara* ambar ne yayi saurin cewa kiyara janyo wancan kahon ki busa ma gimbiya sameeratu" da saurinta ta aikata abunda yace mata, tana busa kahon nan take gimbiya sameeratu tasaki wani irin hargitsatstsan kara mai karfi tare da zuwan guguwa mai karfi, har sai da su ambar suka rike bishiyar dake kusa dasu sbd karfin guguwar zata iya tafiya dasu, zuwa can wajan yayi tsit kamar ba abunda yafaru, ambar ne ya taimakama kiyara data fad'i kasa ta mike. dube duben sameeratun nawwara suka somayi, can suka ganota kwance gindin bishiya, suka karasa wajan, kiyara tayi tsafin su suka bace daga wajan. haka sameeratun nawwara taci gaba da rayuwar kunci da wahala akan nawwar dinta, duk sanda ta zauna babu abinda take sai tunanin rayuwarta tada mai dadi cikin kwanciyar hankali da y'an uwanta, hawayen fuskarta take gogewa tace kai kajamin wannan rayuwar bakin ciki da tashin hankali ayanzu babana" kaine silar komai ga rayuwata" gashi duk cikin yan uwanta aljanu ita kadai ce musulma, amma sam bata iya ibadan taba, gashi tanason bautama ubangijinta, sai dai bata san yadda zatayi ba, dalilinda yasa take matukar son hamma nawwar kenan. *mafarin haduwar tada hamma nawwar shine*, tashigo duniyar bil adama zagayawa, yakasance ranar sallar su ta EDI can ta hango wani kyakkyawar matashin saurayi yana sallah acikin natsuwa da kwanciyar hankali, bayan ya idar da sallah, taga ya daga hannayenshi sama yana kwararo kirari ga ubangijinsa" sannan yasoma rokan Allah bukatocinsa na alkhairi, ya kuma kareshi daga mugun abu. duk tana tsaye tana kallonshi yana addu'oi, ya matukar bata sha'awa' tafara tunanin kamar itama ada ta taba irin wannan addu'an, amma kuma meyasa yanxu bata iya ba" wani bangare na zuciyarta yace wani boyayyan sirri ne tattare da rayuwarki, wanda amayar da wannan sirrin bakaramin haddasa bala'i zaiyiba tsakanin bil adama da jinsin aljanu, birne wannan sirrin acikin kokonta zaifi zaman lafiya ga mutane dubu" taja wani dogon numfashi tare da karkata hankalinta gun nawwar daya gama addu'oin shi yakama hanyar gida. haka tayi ta bibiyar rayuwar nawwar da yadda yake tafiyar da ibadunshi, anan take son nawwar yasoma mamaye duka sassan jikinta, taji bazata iya rayuwa batare dashi ba" tun daga lokacin zuwa duniyar bil adama yazame ma sameeratun nawwara wajan zuwa,,tun tana zuwa ma nawwar amafarki, har takai da zuwa mai azahiri, anan ne shima yasoma kamuwa da son sameeratun nawwara, yakasa tantan cewan *Aljana ce ko mutum?* kuma taki bashi dama yamata tambayoyin dazasu gamsar dashi, taki gaya masa wacece ita, yana cikin tsaka mai wuya. *wannan shine mafarin kulluwar soyayyar su* *******************bayan nawwar yatashi daga bacci awwal yasa aka kawo mishi abinci yaci" sannan yabashi magani yasha, Dr awwal ya gyara zama da kyau ya kalli nawwar, wanda haryanxu tun tashinsa baiyi magana ba. Dr awwal yace nawwar meke damunka halan? jin yayi shuru bai amsa masa ba, yakuma cewa wani irin damuwa kasama ranka haka? wanda ke barazana da lfyr ka, duk irin amintar dake tsakaninmu ka kasa fada min matsalarka?, kana wasa da lafiyarka nawwar, gashi ciwon zuciya na kokarin kama ka, what" sai a sannan yayi mgn, ciwon zuciya fa kace doctor, kai ya d'aga masa alamar tabbatarwa, mekasa aranka haka? me kanema karasa, me kakeso wanda baka samu ba? kana so ka kashe kanka ne, kar ka manta kaifa likita ne, mai kare lafiyar al'umma, to meyasa kai kake wasa da taka lafiyar? hawayenda awwal yagani a idanun nawwar shiyasa shi saurarawa ga tambayoyinda yake jero masa, jikinsa yayi sanyi, duk yabi ya rude, yasan ba karamin abu zaiza jarumin abokinsa kuka ba" haba nawwar meye damuwarka? kafada min ko zan iya taimaka maka," nawwar ya kalli auwal, yace duk akan *SO* ne awwaal,,Allah ya jarrabi zuciyata dason *AlJANA* bama *MUTUM* ba, a tsorace Dr awwal ya mike tsaye da sauri, yana yima nawwar kallon wanda yayi gamo, yace anya nawwar kana cikin hankalin ka kuwa, kataba ganin Inda akayi soyayya tsakanin aljana da mutum , wlh nawwar kayi gamo, kana bukatar rukiyyar gaggawa, idan ma mafarki kakeyi,kara ka farka, wannan abu ne da bazai taba yuwa ba" kafin nawwar yabashi amsa sai ji sukayi ance , karya kakeyi awwal sai na auri nawwar koda zan rasa raina ne wlhy saina aureshi, ae tuni awwal ya kwasa a guje sai bayan kofa yana salati jikinsa na karkarwa" *EDITED* *BY* *UMMEE* *ADNAN* _TAKU UMMU RUMAN_ *nusnim* *pyar* [1/11, 4:39 PM] ‪+234 806 448 1931‬: *ALJANA* *CE* *KO* *MUTUM* 2⃣0⃣&2⃣5⃣ taci gaba da cewa awwal karka shiga hurumin da ba naka ba, kar kasa nawwar ya gujeni, zuciyata bazata iya jurar rashin saba" awwal ina matukar son nawwar" idan ban sameshi ba banajin zan cigaba da numfashi a duniya!! shi dai nawwar yananan akan kujera ya zuba maa sameeratun nawwara ido, cikin wani irin matsanancin sonta" dakuma jindad'in ganinta aransa' tabbacin yanxu andaina azabtar da ita kenan, kamar yadda matar nan tafad'a masa" awwal da har yanxu yananan a bayan kofa' ji yake kamar kasa ya bude yanitse aciki, saboda tsabagen tsoro' tuni ya rufe idanunshi, cikin dauriya yake cewa baiwar Allah kiyi hakuri baso nake nashiga rayuwarki ba, ina so ne inceto amini na daga hadarin daya shiga" sbd zuciyar shi tana dab da bugawa" wanda hakan zai iya rasa ranshi ako wani lokaci ta dalilin sonki" nawwar ya runtse idanunshi, ya juya da kallonshi wajan awwal, yace aboki na taho ka zauna baza ta maka komai ba!!! saneeratun nawwara tayi dan murmushi, tace awwal kenan, ni ba muguwa bace kuma banida niyyar cutar da mutane, kasaki jiki dani, kutaimaka ma rayuwata kai da nawwar. sai alokacin nawwar yafara magana yace baiwar Allah me na mikine kike wahalar da rayuwata? kin hana min sukuni"" sonki yana azalzalan zuciyata, ban taba zama nayi second guda ba tare da tunaninki ba, sannan kuma ban san ke wacece ba? ban san ke wace jinsi bace? shin ke ALJANA ce ko MUTUM? meyasa kuma kika zabe ni amatsayin nazama abokin rayuwanki? dan Allah don son annabi ki amsa min tambayoyi na, shima awwal dake mak'e haryanxu a bayan kofa yace kitaimaki abokina please. Ta numfasa tace duk naji bayaninku, tabbas baku san koni wacece ba' hakazalika nima bansan nid'in wacece ba" illa abunda nasani shine!!! sunana sameeratun nawwara, nakasan ce aduniyar aljanu' nataso naganni a fadar sarki *GULMIYANU* tare da ya'yan shi biyu mace da na miji *Ambar* da *kiyara* ambar ne yake son aure na, ni kuma bani sonshi adalilin hakan ne nake fuskantar mummunar azaba" ban san su waye iyayena ba, kawai nata so naganni awajan kanwar sarki" *gulmiyanu* wato me suna *gimbiya *sameeratu* duk fadin duniyar aljanu ana jin maganar *gimbiya samiratu* sbd ita take mulki alokacin, amma yanxu ta mutu kuma bil adama su sukayi ajalinta, wanda ban san dalili ba" nayi nayi binciki afada min ni wacece amma haryanxu ban samu amsata ba"haka rayuwata taci gaba da gudana. Akwai watarana da bazan taba mantawa ba ina zaune bakin ruwa ina wasa da tsuntsaye domin suke debe min damuwar dake zuciyata!! sai naji abayana ana min magana juyawan dazanyi, naga wata kyakkyawar matashiya kuma bafulatana" dauke da kwaryan nono tana min murmushi, tace nawwara ko zan iya zama kusa dake? na daga mata kaina tare dayin murmushi, kafin tazauna sai naji tace *bismillahi*sannan tazauna na kara kallonta, itama ta kalle ni, sai naji ta ambato sunana, tace nawwara, nasan baki sanni ba kuma baki taba ganina ba" amma ni nasanki, nasan asalinki, nasan labarinki me dauke da tausayi. kullum in zan wuce ta bakin ruwannan ina ganinki kina cikin damuwa, abun na damuna" shiyasa nace bari yau nazo nafada miki asalin wacece ke, kuma suwaye iyayenki, kuma infada miki" awani jinsi kika fito , *jinsin aljan* ko *mutum* dannasan shine abinda kikafi damuwa akai" cikin murnata na rungumeta ina cewa nagode yar uwata, tace bakomai, yar fulani taci gaba da cewa amma inaso kimin alkwarin bazaki fada ma kowa idan nafada miki asalinki ba" sbd idan akaji sai ankasheni. kuma addinina dana su ba daya bane, ni musulma ce sunana *Ameena Bintu saifullah* , taci gaba da cewa nawwara ke diya ce ga abdullahi da asma'u, kin kasan ce ajinsin _____ sameeratun nawara tayi ajiyar zuciya, awwal yace kinyi shiru baki karasa ba,ta dago idonta wanda yayi jajir ta kallesu, nawwar ya rikice yace lafiya nawwara" cikin murya mai rauni tace Aminatu bintu saifullah bata karasa fada min ba, naji tasaki wani uban ihu tafadi kasa, juya wan dazanyi naga *kiyara* ce da wasu kartan maza, su suka aikata ma ameena haka, ashe sunji abunda ameena zata fadamin shiyasa suka mata haka" nashiga rokon kiyara dasu bar azabtar da ameena amma ina, tun ameena tana cewa nawwara ki taimakeni nawwara kitaimake ni, nayi nayi iya kokarina" intaimaki ameena amma ina sun bace da ita!!! nawwar da awwal wanda hawaye yagama wanke musu fuska nawwar yace yanxu ina suka kai ameena bintu saifullah? tana raye ko bata raye? tace tana raye amma tana cikin wani ma ajiyan mu da ake kulle me lefi, tana shan azaba kala kala, banta6a mantawa lokacin dana yima ambar wayau ta sigar soyayya daya kaini wajan ameena dana ganta, da kyar ya amince" da mukaje naga duk ta canxa kamanni sbd azaba, kalmar data fadamin shine, tace nawwara kibazama duniyar bil adama kine mi addinin musulunci domin shi zai iya taimaka miki wajan gano asalin jinsin da kike. *EDITED* BY *UMMEE* *ADNAN* TAKU UMMU RUMAN *nusnim* *pyar* [1/11, 4:39 PM] ‪+234 806 448 1931‬: *ALJANA* *CE* *KO* *MUTUM* 2⃣5⃣&3⃣0⃣ Tun daga lokacin da ameenatu bintu saifullah tace nabazama duniyar bil adama don neman addinin islama"daga ranar na dau niyyar shiga duniyar bil adama, da haka rayuwata taci gaba da tafiya, ba abunda nasa agabana sai neman addinin musulunci, nayi yawo dayawa acikin duniyar bil adama, narasa wazan tunkara da wannan batu nawa" ana haka ne ranar sallar ku ta edi na hadu da kai, alokacin da kake k'ask'an da kanka wurin ubangijinka' kana addu'a, kana niman taimakon Allah. tun a lokacin naji ka burgeni' zuciyata ta aminta dakai, naji bawanda yadace na tunkara sai kai, daga ranar nafara bibiyarka, atunani na kaine zaka taima kamin gurin gano wacece ni, kuma ka koyar dani addinin islama""nawwar kataimaki rayuwata ina cikin tsaka mai wuya, ka taimakeni ka tsamoni daga duhun jahilci" ta karashe mgnr muryarta na rawa" Nawwar ya numfasa yace sameeratun nawwara naji bayaninki, amma wannan batu da kika zo dashi daidai yake darasa rayuwar mutum, ayanayin labarin da kika bada na fahimci duk wanda yayi yunkurin taimaka miki gurin gano asalinki, to shima dai dai yake da rasa tashi rayuwar gun wad'ancan azzaluman!!" amma addu'a itace takubin mumini, *innallaha laa' yamli lizholimin.* _lallai Allah baya kyale azzalumai_ da sannu zai nuna musu isar sa.... zan taimaka miki don Allah da kuma son dana ke miki, sannan da yar dan mahaifiyata" idan ta amince shikenan sai mu tsananta addu'a Allah ya mana jagora. Tace nagode nagode sosai kuma insha Allahu wani abu bazai taba samunka ba, namaka alkawarin haka" kuma mami hafsat baza ta hanaka taimako ba da yardar Allah"" dr awwal ne yayi gyaran murya yace wani hanxari ba gudu ba, kun manta abu guda daya, kar ku manta sai da taimakon ameenatu bintu saifullahi zaku samu cikan burinku, saboda ita ta turo nawwara duniyar bil adama don tasamu mutumin daya rike addu'a don suje su taimaketa tafito daga hannun su ambar, ta bakin ameena ce za agano wacece nawwara!!! yanzu dai abunda zakuyi shine kutaima keta tafito, ko ba hakaba" sameeratun nawwara tace tabbas gskyan kane awwal dole sai yar fulani tafito, amma gurin da take akwai hatsari, nawwar yace karki damu da taimakon Allah zata fito. toh yanxu dayaushe ne zaka fara koya min addininna ku?, inshaAllah nan da sati daya ok nagode, bayan sunyi sallama sai ta bace. nawwar da awwal sunshirya yadda zasuyi su samu mami hafsat da wannan zance, labari har yakai kunnan mami hafsat, sai da ta girkiza dajin labrin" amma dayake da awwal ne kuma shi yake mata bayani sai ta amince musu tare dayi musu addu'an samun nasara,nawwar yaji dadi sosai da maminsa ta amince daman mace ce mai hakuri da tawakkali!!! *wanene nawwar* da'ne ga alhaji isma'il da hafsat, alhaji isma'il haifaffan garin yola ne iyayenshi duk acan suke gaba da baya shi ba fulatani ne, yayi makarantansa tun daga primary zuwa universty abti yola, yayin daya gama ne, aminin mahaifinshi wato alhaji kasim shiyasa ma mishi aiki a jahar kaduna" isma'il tun yana karami alhaji kasim ke sonshi" anan gdan alhaji kasim na kaduna isma'l ya zauna, yana da yaya mata uku, maza biyu babban dan alhaji kasim namiji ne me suna abdalla, sai ibrahim, sai hafsat da mariya sai khadija autar su kenan, mahaifin isma'il takanas yazo kaduna wajan amininshi alhaji kasim, don ne mama dansa auren hafsat, , kasan cewar dan nasa yaje masa da batun son auren hafsat , alhaji kasim yaji dadi sosai" kuma antambayi hafsat din itama ta amince, mafarin auren iyayen nawwar kenan!!" bayan auren su da shekara biyu Allah ya albarkace su da d'a namiji wato nawwar sai kuma sulaiman, daga sulaiman sai autar mami wato, maryam wace ake ma lakani da mimi, macen ta daya tal maza biyu,, mami hafsat ta bama ya'yanta tarbiya dai dai gwargwado, ga kuma addini daya ratsa jikin su, dukkansu suna da haddan alqur'ani mai girma, don shi sulaiman ma baban malamine a islamiya, yayin da nawwar shi kuma doctor ne, sai autar su mimi itama karatun take afannin boko tana ss 1, afannin islamiya kuma tana *sanawiyya* . wannan shine lbrin su nawwar. ***************** *dunyar aljanu* sarki gulmiyanu ya tara dukkan aljanu yana shaida masu" nan da wata daya za ayi gaga rumin bikin dansa *ambar* da *sameeratun nawwara*, nan take taji gabanta yafadi, shi ko ambar da kiyara me zasuyi inba murna ba har gaban mahaifin nashi yazo yana godiya" ambar ya dago ido yana sakar ma nawwara murmushin samun nasara, sarki gulmiyanu yaci gaba da cewa' nan da sati biyu ina son akashe ameenatu bintu saifullah' cikin tashin hankali samiratu taje gaban sarki ta tsugunna tana rokonshi da abar yar fulani da ranta!!" amma ina sarki yaki amince wa, ganin sarki yaki sauraronta" tuni ta garzaya duniyar bil adama wajan nawwar don neman mafita, tafada mashi abunda ke faruwa shima hankalinshi atashe yana innalillahi wa inna ilaihi raji'un , la'ilaha illa anta subhanaka inni kuntu minal zalumin"" ai bashiri nawwar yashiga koyar da sameeratun nawwara addinin islama, addu'oi iri2 yasoma koya mata' kan kace kabo sameeratu tayi zurfi sosai, idan yana koya mata wani abun ma sai ta dinga tunanin kamar ta tabayin abun ada:!!. akwana atashi ba wuya a wajan Allah, a yaune su awwal da nawwar da sameeratun nawwara, suka shirya hanyar da za adauko *ameenatu bintu saifullah* _sai ku biyoni agaba don jin shin zasu samu nasarar ku6utar da ameenatu bin saifullah ????._ *EDITED* by *UMMEE ADNAN* ~TAKU A KULLUM UMMU RUMAN~ *nusnim* *pyar* [1/11, 4:39 PM] ‪+234 806 448 1931‬: *ALJANA* *CE* *KO* *MUTUM* 3⃣0⃣&3⃣5⃣ sameeratun nawwara ta kammala shirinta tsaf tare da daukan makaman ta, saboda tsaro , bayan tagama ne ta garzayo duniyar su nawwar , ayayin da ta iskesu suna zaman jiranta shida awwal' nawwar ke kara karfafama awwal gwiwa akan wannan tafiya daza suyi.ganin yadda duk yake a tsorace, yace haba abokina" kada kabada maza mana' kadafa kamanta *Allah yace yana nan aduk inda bayawansa yake tsammaninsa'* kasa aranka Allah yana taredamu kumashi zai taimakemu" inafatan dai kayi azkar d'in safiya, da addu'ar dana baaka jiya? murmushi awwal yayi cikeda kwarin gwiwa yace nayi Allah ya taimakemu' Ameen... Sallamar sameeratu ne ya katsesu da karatun suratul yaseen dasuke bayan sungama karanta wasu ayoyi acikin suratul baqara" takaraso ciki, dukansu suka amsa mata sallamarta,fuskarta dauke da murmushi yayin da take kallon nawwar, shima ya mai da mata martani, tace masu *masa'un khair* suka ce mata *masa'u *noor*. auwal ne yace ai nayi zaton baza kixo ba, tace tab mai zai hanani zuwa, yanxun ma duk nakosa muje, nawwar yace ' ki kwantar da hankalinki insha Allahu zamu samu nasaran zuwa wajan ameenatu bin saifullah, tace toh Allah yasa nagode sosai" awwal yace ya naganki da makamai, tace ai saboda tsaro na dauko, yayi dariya, yace haba ai ayar Allah kadai ta ishemu makami' sbd haka karki samu damuwa, to awwal, yanxu sai kutashi muje don lokaci na kurewa. nawwar yace to amma bari mugabatar da addu'a kafin mutafi, suka ce to, nan suka karanta *suratul iklas* *falaq* da *nas* sai *ayatul kursiyu* sannan suka shafa, sameeratu tace kurufe ida nuwanku, yadda ta umur ce su haka sukayi. *duniyar aljanu* awani kurmin k'ogo suka sauka' tace subude idanunsu" nawwar ne yafara budewa tare dayin addu'ar neman tsari, shiko awwal yakasa bude idonshi saboda tsoro, don bai San me zai fara gani ba idan yabude idon. nawwar da nawwara suka dubi awwal cikin mamaki, nawwar yace awwal lafiya bude idanunka mana mun isofa, cikin rawar murya awwal ya soma magana , yace nawwar wallahi tsoron budewa nakeyi" sameeratu tace kar ka damu ba abunda zaifaru da kai kabude , nawwar yace haba doctor be a man mana, Kasa aranka kana tareda sojojin kariya daga Allah , ahankali awwal ya bude ido shima tare dayin addu'a. haka sukabi wajan da kallo cikin kurmin dajine , sameeratu tace nayi mana Rabin zuwa, sauran tafiya kuma da kanmu zamu karasa, saboda bani da karfin da zanjamu a iska mukarasa wajan, suka ce to " nan da nan suka doshi hanya tafiya suke sosai kowannan su da abunda yake tunani azuciyar shi, tafiya suke babu kakkautawa, har suka gaji suna samu gefe don su zauna suhuta. Duk abunda ke faruwa su sariki *gulmiyanu* ba su sani ba' sbd kafin sameertu sutafi sai da taje ta to she madubin da suke ganin hangar da zai sadasu da ameenatu bin saifullah , cikin ikon Allah kuma dukkansu babu wanda ya hankalta da hakan, itako ameenatu tananan cikin dakin azaban da aka ijyeta, tanaji ajikinta sameeratun nawwara natunkaro wajanta don taimako. awwal yace sameeratu wai bamu iso bane! wlh nagaji nikam, sameeratu tace yi hakuri saura kadan mukarasa, Allah dai ya kaimu lafiya amin. *Ambar* ne zaune da kiyara suna hira sai sukasa ajuyo musu madubin dazai sada su da ameenatu bin saifulllah , aiko anajiyo dashi sukaga abu bakin kirin, Akbar yayi saurin mikewa, yana cewa garin yaya wannan abun yafaru?tayaya ba aganin hoto? kiyara tace lallai akwai wani bakon al'amari ayi sauri aje abin cika, sannan kuma akira sameeratun nawwara , labari yaje kunnan sarki shima hankali tashe don ba'a taba mishi irin wannan abun ba. kiyara ta dawo cikin sauri tace babu sameeratu , nan take aka bude madubin da kyar , kafin subude su nawwar sun Isa ga ameenatu , duk sun kashe masu tsaronta da ayar Allah, sameeratu ta rungume ameenatu bin sai fullah, daidai lokaci sarki dasu ambar, suka hango abunda ke faruwa, ambar yasaki wani irin gigitaccen kara nabakin ciki, saida su sameeratu sukaji , ameenatu tayi saurin cewa maza maza kuzo mu wuce dan sun ganomu, su nawwar gabansu sai faduwa yake, yana ta karanto addu'a" haka awwal ma. sarki yace garin yaya haka tafaru bil adama har suka samu damar daza su shigo mana duniyar mu, cikin huci kiyara tace wannan duk aikin sameeratun nawwara ce, ambar yace mufar musu baza abar su da rai ba. nawwar suna ganin bak'in abu natasowa da sauri duk suka tsorata , sameeratu tace ameenatu kiyi sauri kifitar da mu gasu nan zuwa, tace to ni yanxu ina zamuje, nawwar yayi saurin cewa musauka aduniyar mu kawai, aiko dafda wani guguwar iske ya kusa dasu suka mace bat, cikin nasara, sai gasu aduniyar bil adama, cikin office din doctor awwal , suka zube akasa awwal da nawwar kamar wasu matattu, can suka farfado bakinsu d'auke da addu'a' nawwar yace anya baza su iya biyo mu nan ba? aminatu tace a'a, nayi wani abun da baza su iya gano inda muke ba, nawwar yace akwai wani gdna dake kusa da asibitin nan, yakamata muje can. suka ce to kowannan su zaune awwal dai shiru yayi don sai yanxu yakejin gajiya, bayan kwana daya da dawowan su duk kan su zaune afalo, idan kuka ga sameeratu da ameena bin saifullah sai ka rantse da Allah mutanene, sbd idan zasu hadu da bil Adam sukan fito asuffan mutane , yauma hakan takasance . nawwar yace naje nasamu malamina nayi mishi bayanin komai, kuma ya amince dashima yataimaka mana , gashinan zuwa nan da yan mintuna, don agabanshi za awarware wannan kullalliyar al'amarin, amenat tace tabbas kayi tunani nawwar , hakan nada kwau ,bata gama rufe baki ba mallam yayi sallama , suka amsa nawwar yanuna mai waje ya zauna" duk suka gaisar da malamin. saida mallamin yayi doguwar addu'a sosai sannan ya bukaci ameenatu bin saifullah data bayyana wacece sameeratun nawwara" kowa ido yazuba mata donson jin abun da zata fada, tace Allah y gafarta mallam sameeratun nawwara takasan ce ajinsin_____? *kubiyoni agaba* don jin me zai faru. *EDITED by UMMEE* *ADNAN* TAKU A KULLUM UMMU RUMAN *KUYI HAKURI DAJINA SHURUN KWANA 2 HAKAN YA FARUNE ASANADIYYAN LALACEWAN WAYAR TAWA AMMAN YANXU ALHMDLLH KOMAI YA DAI²TA* *nusnim* *pyar* [1/11, 4:39 PM] ‪+234 806 448 1931‬: *ALJANA* *CE* *KO* *MUTUM* *By* *Nusnim* 3⃣6⃣➡4⃣0⃣ A hankali *Ameenatu bintu saifullah* tace Allah ya gafarta mallam hakika sameeratun nawwara ta kasance acikin jinsin bil adama gaba da baya, awwal ya zaro ido, yayi saurin cewa kina nufin asalinta mutum ce ba aljana ba? tace tabbas mutum ce ba aljana ba, nawwar da nawwara sai kallon aminat suke cikin mamaki da d'aurewar kai. Nawwar yace ameenatu munaso kifad'a mana tayaya sameeratu tazama aljana" alhalin kuma kince asalinta mutum ce, daman mutum na rikid'ewa ya koma aljan? ta dago ido ta kalli mallam da baice dasu komai ba sai kallonta yake hana nazarin wasu abubuwan" ta juya takalli su nawwar da suka zuba mata ido suna jiran amsarta, sannan ta maida kallon ga sameeratu data matsu taji ko ita wacece' dafata tayi ,tace karki damu yau zakiji asalinki" kuma zakiji ko suwaye iyayenki. 🔹🔹🔹🔹🔹🔹🔹 *shekaru bakwai* *da suka wuce* 🔸🔸🔸🔸🔸🔸🔸 Akwai wani bawan Allah me suna Alhaji idrisa da matarsa hajiya maimuna, dukkan su haifaffun garin kano ne, Alhaji idrisa dan kasuwa ne kuma Allah ya hore mashi arziki, babban danshi na mijine me suna muktar, sai nabiyu mai suna isma'il sannan na uku macece mai suna sauda sai abba, sameeratun nawwara sannan zainab, yayanshi biyar kenan ukun sunyi aure , sai yarage daga sameeratun nawwara sai zainab. sameeratun nawwara yarinya ce me hazaka sannan tana da kyanta daidai gwargwado, tsakaninta da kanwarta zainab babu wani jaa, don ba ayaye sameeratu ba aka samu cikin zainab. gidan Alhaji idrisa babba gida ne, daya gada ga iyayensa" gidan hade yake d gdan gona, ko ta ina acikin gdan akwai bishiyoyi, kama daga bishiyar mangwaro, kashu, Tsamiya, dalbejiya, zogale, kukan Fulani, da dai sauran su"" lokacinda sameeratu na karama mamanta kan shimfida taburma da yamma sai ta ijye nawwara akai ita kuma tana aiki ga kuma tsohon ciki datake fama dashi, da haka sameeratu take gangarawa cikin wayannan bishiyoyin tayita wasa da y'ay'an aljanu, duk mahaifiyarta bata sani ba, dan duk sanda ta gama aiki tazo d'aukarta, zata isketa a inda ta barta" da haka yarinyar tasaba dasu, yakasance duk lokacin dabata je wajanba ta dinga kuka kenan, tun mahaifiyarta na hanata har ta kyaleta. akwai wani rana da ake meeting na aljanu, wacce shugaban aljanu itace *gimbiya sameeratu* ta garde akan kujeranta na sarauta kowa na girmamata, ga kayan marmari anjere mata agabanta, alokacin ne hajiya maimuna ta ijye nawwara agefenta don tayi sallar magriba afalo, tafara sallah bada dadewa ba nawwara ta rarrafa tafito waje har ta Isa wajan da aljanun suke taro ba su lura da itaba, sai dataje daidai kusa da gimbiya sameeratu, sukayi ido hudu, abunka da yaro sai nawwara tasakar ma gimbiya sameeratu dariya, itama ta maida mata tare da daukan nawwara tabata kayan marmarin dake gefenta, tundaga lokacin gimbiya sameeratu taji tana son nawwara, alakacin ne ambar yaji shi bawadda yake so aduniya irin nawwara. dahaka dai nawwara tashiga ran aljanu, amma tana karamanta ne take ganin su, data fara girma sai sukayi kamar sunbarta , alhalin basu barta ba, Alhaji idrisa yasa ansare duka bishiyoyin gdansa inda yatada Gini aciki, sare bishiyoyin nan bakaramin tashin hankali ya afku a duniyar aljanu ba" don alokacin daza asare bishiyoyin gimbiya samiratu tana kwance tana hutawa, abun ya afka da ita daidai tsakiyar cikinta aka sare, sai yatsar ta mai duke da wani shegen zobe mai kyau yafado kasa, daidai saitin dakin nawwara" . anan rai yayi halinsa, duniyar aljanu sungirgixa da mutuwan gimbiya sameeratu, sarki gulmiyanu yayi takaicin rasa yar'uwar shi da sauran aljanun su," mutumin dayasare bishiyar ba ayi kwana biyu ba yarasu , mutane suka fara jita jita akan cewa ai bishiyan daya sarene agdan Alhaji idrisa na aljanune, kuma ba shakka su suka kashe shi, kuma daman sai da akace ma alhjy karyasa asare don dadewar bishiyoyin , yace shi sam bai san da wasu haittu aljanu ba, kuma koda akwaisu badai a gidansa ba" bayan mutuwan gimbiya sameeratu da sati daya, nawwara ta tsinta wannan zoben gimbiya akofar dakinta, taji yabata sha'awa tasaka a hannunta, ya mata kyau sosai. suko can duniyar aljanu sun kudirta aniyan raba alhaji idrisa da farin cikin shi kasan cewa Allah ya daura mai son nawwara, gashi yarinyar akwaita da haddan alqur'ani akanta,tana zuwa islamiya sosai. tun lokacin data sa zoben nan taji kamar bata da lafiya, kuma tayi rauni akaratunta, tun mahaifiyarta namata fada har tagaji takyaleta, ikon Allah kuma babu wanda ya ta6a lura da zoben hannun ta. akwai wata rana taje islamiya taji sam takasa zaman ajin duk ranta abace yake kuma tarasa dalili' tashi tayi tafita waje tasamu wuri ta zauna' me zai faru kawai sai jitayi ance sameeratun nawwara kitaho gareni zan yaye maki damuwarki' zan baki duk wata kulawa data dace ke tamuce har abada, a tsorace take waige² bataga kowa ba" mikewar dazatayi saiga___? *EDIDTED by UMMEE ADNAN* TAKU UMMU RUMAN *nusnim* *pyar* [1/11, 4:39 PM] ‪+234 806 448 1931‬: *ALJANA* *CE* *KO* *MUTUM* *By* *Nusnim* 4⃣1⃣➡4⃣5⃣ Mikewar dazatayi saiga maciji yayi saurin bi ta kafafunta, tasaki wani uban ihu tare da sumewa kasa , nan take yan makaranta suka rufa mata, aka kira mallamin su, yasa yan ajin sanawiya su dauke ta sukaita aji. yasa aka kawo mai ruwa a kofi yayi addu'oi aciki ya watsa mata fuska, a firgice ta farka tana cewa gasunan suna kirana, wayyo Allah zasu..... mallam yayi saurin cewa suwaye ke kiranki nawwara? kasa magana tayi ta tafi suuu zata fadi aka tare ta, shugaban makarantar ne yazo, yace yana ganin alamar jinnu ne ajikin yarinyar nan" ayimata ruqiya agani idan aljanun ne za'a gane" mallamin su yace hakane don nima nayi tunanin haka. nan aka shiga yiwa sameeratun nawwara ruqiya , nanda nan aljanun suka bayyana ajikinta, alokacin ambar ne ajikinta, abisa umurnin mahaifinsa dayace yasoma bayyana gareta " don ya isar musu sakon dasuke dashi. mallam yace kai waye' kuma me kuke nema awajen wannan baiwar Allah'n, me tamuku kukeson cutar da ita? shuru ambar yayi' mlm yace zakuyi mgn kosai na kona ku da ayar Allah, cikin wani irin murya da babu dad'inji ambar yafara magana "" yace mallam kar ka kona mu zamu fita dama sakone muke son isarwa ga mahaifinta" kiransa zakayi mufad'a masa ko kai zamu barwa sakon ka isar gareshi!" mallam yaga idan yace akira mahaifin nawwara ana iya d'aukar lokaci, ga yarinyar nabuk'atar taimakon gaggawa" tunda sunce zasu iya bada sakon aba mahaifinta ai shikenan' yace wace irin sako ne! kafad'a zamu isar zuwa gareshi" ambar yayi wata irin dariya tukum sannan yace ciki tsawa mallam muna so afadama mahaifita zamu dauke sameeratun nawwara zuwa duniyarmu...... mallam yace wa'iyazu billah meyasa zaku aikata wannan mummunan abun, ambar yace sbd mahaifinta yaraba mu da farin cikinmu, saboda haka muma zamu rabashi da farin cikinsa ta hanyar d'auke y'ar wacce yafi so aduniya" daman kuma tamuce. mallam yace menene wannan abun daya rabaku dashi!, ambar yace yasa ansare bishiyoyin dake gdansa batare daya sanar mana ba, balle mu kwashi muhimman ajiyarmu' kuma alokacin gimbiyarmu me suna sameeratu, tana kwance akan gadon hutawarta abun ya afka da ita' da sauran yan uwan mu, saboda haka baza mu yarda ba, muna so a Isar masa da wannan sakon" mun sassauta hukuncinmu akansa ne sbd sonda muke ma nawwara" badan hakaba damun dad'e da d'aukar mummunar fansa akansa" kafin mallam yace wani abu har yafita daga jikinta , ita kuma sai tari take aka bata ruwan addu'a tasha sai bacci ya dauketa. Bayan kwana daya da faruwan haka shugaban makarantansu da mallamin ajin na su suka je gdan Alhaji idrisa , bayan sun gaisa ne suke bayyana mishi abunda ke faruwa, yace sam shi bayyarda da wasu aljanu ba, yar shi kuma bazai wuce maleria bane ke damunta, ai wannan ma tatsuniya ce, aljanun banxa aljanun hufi, duk wannan ta tsuniyace, da karyan yara, mallam yace a'a Alhaji, kar kamanta fa Allah da kansa yana fad'a acinkin alqur'ani cewa ( *wama khalakatul jinna wal insa illa liya'a budun* _bamu halicci mutane da aljanu ba face dan su bauta mani_ ) Ashe kuwa kaga aljanu gskya ne, su suna ganin mu amman mu bama ganin su, kuma maganan gsky sare bishiyan nan da kayi batare da kasan matakan daya dace kayiba kafin hakan akwai matsala, sannan kasan bishiyoyinnan sunyi sama da shekara talatin da y'an doriya ba asare su ba sai yanxu? kaima kasan dole asamu matsala, zaman lafiyarka da iyalinka shine kabasu hakuri, inba haka ba, watarana zakayi kuka da idanun ka, don bakasan kaidin aljanu bane shiyasa, muna kara baka shawara da kabasu hakuri kawai" dan tsira da iyalanka" , Alhaji idrisa mutum ne mai taurin kai da kafiya akan ra'ayinsa, da kuma karyata aljanu, ya tashi cikin fushi yace mallam dan Allah kutashi kutafi sun dad'e basu dauke ta dinba makaryata kawai, cikin fushi suma suka bar gdan. aljanun sunji duk abunda Alhaji idrisa yace, kuma sun dau alwashin sai sun dauke sameeratun nawwara, duk ranar da taje islamiya sai suntashi mata kuma sai sunkara fada zasu sace ta. Ranar jumma'a sameeratun nawwara taci kwalliya zataje gdan yayar babanta ta gaidata daganan ta wuce shagon dinkin su"" dayake tana koyan dinki, bayan taje gdan goggon nata ta wuce shagon su, kawar tace khadija tace kin makara nawwara yau nariga ki zuwa , nawwara tayi murmushi" tace wlh nabiya gdan goggona ne, Ayya ke kadai ce ashagon ina aunty marry, khadija tace taje kasuwa ,ok, nan sukaci gaba da hirar su har la' asar tayi, nawwara tace Khadija bara nashiga gdansu baba rabi nayi sallah tunda ke kina fashin sallah, tace to fad'awa duniya bana sallah yau takarashe fad'a tana dariya, nawwara tayi dariya. ta kama hanyar zuwa gdan kenan sai ga wani guguwar iska yataso ya dumfaro nawwara, kiyara ce tazo ta dauke ta, tun daga lokacin nawwara bata sake sanin ita wacece ba, kawai ta ganta ne aduniyar aljanu , duk sun tsafeta da abubuwan su tazama irinsu, amma kuma kana ganin nawwara sai kace ruwa biyu ce, wato aljana da mutum, haka takoma"" wannan zoben dake hannunta shi yakara bata duk wani karfin tsafi, shiyasa tazama kamar aljana, amma kuma akwai wajajen dabaza ta iya zuwa ba aduniyar aljanu, kasan cewarta ita ba asalin aljanar bace. in baku manta ba ko wajan da aka daure ni bata karasa daku ba sai da kafa fuwanku kuka karasa, sbd batada karfin isacan, da sunyi niyyan kasheta ne sai ambar yace yana sonta , acan kuma duniyar bil adama, khadija tajiki shiru baki dawo ba. nan aka bazama neman nawwara lbrin batanta yazagaye ko ina, har makarantar islamiyar su, mallaman su sunyi takaicin haka' shiko mahaifinta kamar zaiyi hauka, yana cewa karya kuke kud'auke min yarinya ta, yayi ta sambatu yana tsine musu, abu wasa² har anfidda tsammanin ganinki, kowa ya dangana anmik'ama Allah lamuransa" sai bayan batanki ne mahaifinki yafara daya sani sai alokacin mahaifinki yayarda da akwai aljanu, shi sam daya karyata aljanu, yana ganin duk karya ne, damuwa tamasa yawa' wanda hakan ya kwanta ciwo na tsawon shekaru biyu sannan y warke duk yan uwanki sun dangana. ke kuma kina can kina rayuwa da aljanu, sun gusar miki da kwakwalwa, wannan shine abunda ya faru deke nawwara, awwal saida ya zubda hawaye , nawwar yace wai meyasa mutane ke son karyata aljanu, bayan kuma Allah yafada, da akwai, acikin aljanun ma akwai masu bauta mai, kamar yadda akwai amutane akwai musulmai a kwai kafurai, sameeratu dake zaune tazuba musu ido tarasa meke mata yawo a kwakwal warta. nawwar yace to meza ayi mata ta dawo yadda take cikakkiyar mutum,ameenatu bin saifullah tace kunga wannan zoben dake hannunta za'ayi kokarin cireshi, sannan kuma sauran aikin malllam ne yasan yadda za'ayi. mallam ne yayi magana yace nawwara ba ita kadai bace akwai gimbiya sameeratu ajikinta kuma karya wayannan asiren dake jikinta bakaramin aiki bane, zamuje da ita Maiduguri, don nikadai bazan iyaba , bai gama rufe bakinshi ba sukaji gdan y girgiza yayin da nawwara ta xube kasa wani bakin abu nafita Daga bakinta,duk kan su suka nufo kanta cikin tsoro wutan dakin ya dauke ko ina bakin kirin. *EDIDTED* BY *UMMEE* *ADNAN* TAKU UMMU RUMAN *Nusnim* *pyar* [1/11, 4:39 PM] ‪+234 806 448 1931‬: *ALJANA* *CE* *KO* *MUTUM* *By* *Nusnim* 4⃣6⃣➡5⃣0⃣ wutan dakin ya dauke ko ina bak'ik'irin baka iya ganin komai" ameenatu bin saifullah tace mallam ya kamata kayi wani abu don suna dab da isowa inda muke, kuma ga nawwara cikin wani yanayi, wannan bakin abun dake fitowa daga bakinta alamun suna son fitowa ta jikinta ne, wanda hakan daidai yake data rasa rayuwarta, nawwar yana jin haka yace mallam kataimaka dan Allah. bani son in rasa nawwara arayuwata" shikansa mallm al'amarin yasoma firgitashi' bayyi tsammanin abin yakai hakaba' karatu yasomayi cikin gaggawa, suma su nawwar suna karanto duk ayar datazo abakinsu"saida sukayi kusan minti 30, sannan hasken dakin yasoma dawowa , gdan kuma yadaina girgiza, nawwara ta bud'e ido, sai dai takasa magana, sai binsu take da kallo kamar wata tab'abb'iya. *DUNIYAR ALJANU* lokacin da su ambar suka karaso basuga su ameenat bin saifullah ba' don sunriga sun bace musu, sunyi sunyi su bisu amma ina sun kasa" sarki yayi takaicin haka sosai, suna tunanin ta ina zasubi suje duniyar bil adama, saboda wani katanga dake tsakanin su, sunyi tsafin su amma ina sunkasa rusawa, shine suka yenke shawaran fitowa ta jikin nawwara, amma ina basu sami hanyar fitowa ba, saboda karfin addu'ar da mallam keyi don saida ta kona wayansu, dole suka koma ta katangan suka fara aikin rushewa. *MAIDUGURI* Tunda suka kama hanyar zuwa mai duguri, mallam yafad'ama babban mallaminsa gasunan tafe, sun isa lfy an tarbesu cikin karamci, inda akayi musu masauki da kayan abinci' mallam ne zaune da babban mallaminsa isma'il maiduguri"" yana fayyace mishi matsalan dake tafe dasu akan nawwara"" sai daya numfasa sannan yace lallai rayuwar yarinyar nan yana cikin had'ari. amma insha Allahu komai zai daidaita zata dawo yadda take da izinin Allah, nan mallam yasa aka kawo mishi nawwara sam takasa hada ido dashi""yayi mata magana bata amsa shiba" d'aya daga cikin almajiransa yakira yace yad'au kasko yasamo garwushin wuta acikin gida" garin hantiti yad'ibo yazuba acikin kaskon, yamik'ama nawwar man jeedah y'ar saudiyya' yace yashafa mata a fuska" dakyar nawwar yasamu yashafa mata" da taimakon awwal dayarik'e mata hannaye" mallam isma'il yasa aka kira mai sauran malaman dasuke karatun dasu". yatashi yahada magani misk habbatus sauda da zaitun sai man ta farnuwa, da kuma gayen magarya duk yahada waje daya, sannan ya karanto addu'oi ya tofa aciki, ya umurci wasu malaman dasu sake riketa dakyau, ya matso yashafa mata a fuska da kafafuwanta" wani irin uban k'ara sake tana fizge fizge, tace mallam kusakeni kada ku kasheni, ni ban zamto daga cikin jinsin bil adama ba, niba jin___bata karasa ba sai ta fadi sumammiya, zoben dake hannunta yana fitar da hayaki, nan take yakoma launin ja, sai alokacin ne mallam ya hango zoben, yasa hannunta acikin wani kokon magani don cire zoben" da kyar zoben yafita. amma kuma me zai faru ana cire zoben sai sukaji kara acikin zoben kamar ana cewa kar Ku karasani tuni mallam yasaka shi cikin wani kwalbar magani ya narke , juyowar dazasuyi gareta kuma sai sukaga halittan nawwara yacanxa, bakaman da datake ruwa biyu ba, yanxu ta dawo asalin nawwararta. awwal yace mallam yanxu duk asirikan dake jikinta sun karye kenan, yace a'ah da sauran kadan dama babban matsalan itace wannan zoben, shine karfin asirin , yanxun kuma mun cire shi alhamdulillah, jira muke ta farfado sai ad'ora da ruqiya"" ameenatu Bini saifulla dake gefe, tace lallai babu abun bautawa da gsky sai ubangijin mu Allah, yanxu da ayoyin Allah akacire wannan zoben mai karfin tsafin, kuma anriga da angama halaka wannan zoben da me zoben wato gimbiya sameeratu. yanxu saura sarki gulmiyanu da mukarrabansa' dan bazai ta6a yafewa ba" gwara ma a halakasu duka, don muma musamu yancin kanmu da yadda zamu bautama ubangijinmu Allah , _Allahu sami'ul Aleem_. duniyar aljanu kuwa afadan sarki gulmiyanu' masarautar su tana girgixa yayin da wayanxu suka fadi suka mutu, saboda wannan zoben da aka kona , gininsu sai zubewa kasa sukeyi yayin da ruwa yacimma masarautan, suna neman ceto, sarki da kiyara da ambar suntsira da kyar, sarki yace ankona zoben nan shiyasa wannan abun ke faruwa, cikin huci ambar yace baza su yarda ba sai sun d'au fansa" kiyara tace mu koma jikin nawwara mudagargaza naman jikinta,munakasa ta tareda duk wanda keson ganin bayan mu, sarki yace haka za ayi.ta kalli ambar cikin 6acin rai" tace ai duk laifin kane' badan ka nuna kana sontaba aida tuni mun dad'e da mance shafinta" can kuma kowa ya bude alqur'ani donyin karatu sai sukaji ihun nawwara tana cewa wayyo zasu kasheni, ameenatu tace mallam kuyi kutaimaketa zasu kasheta wlhy,tunda hartayi silar tarwatsewar komai nasu bazasu barta da rai ba" nandanan suka fara karatu sosai, su sarki dasukaga za a kona su, sai suka fara cewa zamufita karku kona mu, itako ameenat cewa take mallam kuci gaba kada kubarsu azzalumai ne basa yafiya' zasu iyayin abinda yafi wannan idan aka barsu" duk yadda su sarki da ambar sukaso fita sun kasa' sbd yadda d'akin gaba daya yake warin magunguna ga kuma ayoyin Allah dake fita abakin manyan malaman cikin sauti" karatu suke har sai da suka tabbatar dasun konasu kurmus, sannan suka daina. ita kuma ta fadi kasa kamar matatta ,mallam yace alhamdulillah komai ya daidai ta ankona su, yanxu kawai mujira muga yanayin tashinta, ameenatu, tace mallam mun gode sosai yanxu ni zanyi tafiyata duniyar mu, tunda komai y daidai ta, idan nawwara ta farka agaisar min da ita, ta juya ta kalli nawwar da awwal tayi musu murmushi tace musu saduwar alkhairi, nawwar kari ke nawwara da amana, duk da dai nasan ayanxu idan ta farfado baza tasan waye kai ba, bazata tuna komai akan soyayyar da kukayi ba, amman nasan kai d'in jurumine, adalilin sonda kake mata ka tsamota daga aljanu zuwa asalinta (mutum) ka saida rayuwarka donka ceto abar sonka "" jarumtarka ta burgeni, sai dai kash ina mai tausaya maka saboda yanxu zaka sake shiga cikin wata jarabawar so' dan asalin nawwara bata soyayya' hasalima duk wanda yace yana sonta to daga ranar yazama makiyinta' don acewarta haryanxu bata had'u da namijinda yayi dai² da ra'ayinta ba" koda ta farfad'o yanxu batasan da soyayyar kaba, ba lalle bane ta amince maka, sai dai nasan kaid'in mijine wanda za'a kira dasunan namiji acikin jaruman maza" kayi hakuri da duk abinda zai biyo baya' inshaAllah komai zai dai²ta take anan nawwar yaji gabansa ya fadi' idanu yazaro cikin wani sabon tashin hankali" gumi tako ina ajikinsa........ _kutara agaba donjin anya nawwar yana daga cikin tsarin mazan da nawwara take so kuwa._ *EDIDTED* by *UMMEE* *ADNAN* TAKU UMMU RUMAN *Nusnim* *pyar* [1/11, 4:39 PM] ‪+234 806 448 1931‬: *ALJANA* *CE* *KO* *MUTUM* 5⃣1⃣➡5⃣5⃣ gumi yake tako ina ajikinsa' innalillahi wa'inna ilaihi raji'un kawai yake nanatawa a zuciyarsa, ameenatu tace nabarku lafiya cikin amincin ubangiji, cikeda kewar nawwara da tausayin nawwar ta tafi, ganin yadda duk ya d'aga hankalinsa akan abunda tafad'a masa" nawwar dake zaune cikin matsanancin damuwa kasa amsawa ameenatu sallamar data keyi musu yayi' sai tunanin zuccin dayake" anya zai iya jure rashin nawwara a kusa dashi kuwa? dan ba karamin illa soyayyarta yayi masa a zuciya ba; awwal ne ya dafa shi, yace kar kadamu abokina, insha Allahu kana cikin tsarin irin mazajen da nawwara zataso, kuma da yardar ubangiji sai kasamu soyayyar ta. uhummmm to Allah yasa' amman awwal na tabbatar da kaddara ce tafado min, kowani dan adam da kalar tasa kaddarar, fatana ubangiji ya kawomin agaji acikin al'amarina, awwal yace hakane doctor Allah ya shige mana gaba Ameen. nawwara dake kwance tasoma motsi alamun tashi kenan, awwal ne ya lura da hakan , da sauri ya ta6a nawwar yace kalla kaga tana motsi' barin kira mallam, su duka biyun suka shigo , mallam yace karku damu zata tashi da kanta, yana gama rufe baki, nawwara tayi mika tare dayin salati, bud'e idon dazatayi sai taga bak'in fuskoki akanta tsaye' tayi saurin waro idanu, tace nashiga uku lafiya naganku adakina, nan tafara laluben Neman hijabinta don ta kulle jikinta. karaf sukayi ido hudu da nawwar wanda yaji gabanshi yafadi, ita kuma tace mallam lafiya katsura min ido sai kace kaga sabuwar halitta? cikin tsiwa take maganar, cikinsa ne ya murna alamun kamar zaiyi zawo, nan kuma ta saki kuka tana kiran hajiya hajiya nashiga uku wasu mutane adakina' dan Allah kuyi hakuri kufitar min a d'aki" mallam yayi murmushi yace alhmdllh lallai kam sauki yasamu, sai ta juya ta kalli mallam da alamun tambaya abakinta, sannan kuma takara duban dakin data ke"" taga ashe ba gidan su bane, sai ta fashe da kuka, tana cewa ina ne nan kuka kawoni, mallam yace yi hakuri sameeratu baki da lafiya ne shiyasa, yanzu dai kitashi kiyi wanka ki canza kaya sai in miki bayani," batare data musa ba tace to, mallam yace dasu nawwar da su fito subata waje. mallam yakira yar uwarsa da ta taimaka mawa sameeratu tayi wanka, tace to mallam, tashiga tasamu nawwara ta tashi amma jikinta yana mata kamar ciwo ciwo, da taimakon matar nan tayi wanka da ruwan magani sai taji jikin nata ya mata dadi, ta fito wanka matar ta kawo mata kaya tare da abinci, bayan tagama ne , mallam yace tafito tasamesu a falo, bayan ta zauna suka kara hada ido da nawwar taga ita yake kallo sai taji ta tsane wannan nawwar din don tak'in jinin kallo , shiko zuciyarshi sai har bawa takeyi, kamar zata fashe, don ya hango tsagwaron kiyayyar sa a idanun nawwara, mallam yayi gyaran murya yace sameeratu, nasan baki San Ina ne nan ba , kuma baki san suwaye muba, wato kin dade baki da lfyane tsawon shekaru bakwai dasu ka wuce, tayi saurin zabura tace shekaru bakwai fa kace ? wannan wani irin ciwo ne dake damuna har natsawon shekara bakwai ban sani ba? mallam yace kar ki damu a sannu zaki san komai. yaci gaba da cewa zaki iya tuna yaushe rabonki da gida? tayi shiru tare dayin tunani, sai tatuna abunda yafaru lokacin daza taje sallah gdan baba rabi sai ga wani guguwar isaka yatasu, tayi saurin cewa wallahi jiya ne danabar shagon dinkin mu zanje gdan baba rabi sallah sai ga wani guguwan iska yataso. abunda kawai zan iya tunawa kenan, mallam yace yauwa, toh ba jiyabane yanxu kusan shekaru bakwai kenan da faruwan wannan al'amarin, ta dafe kirjinta tace nashiga uku mallam, toh yanxu ina iyayena? badai tsawon shekaru bakwai bana tare dasu ba! , wayyo Allah abbana, wai meya sameni hakane? Kai malam ya d'aga mata alamar bata tareda iyayenta" toh yanxu nan wani gari ne! yace maiduguri, idanu tazaro, sai kuma tasaki kuka, to waye yakawoni maiduguri! mallam yace labarine mai tsawo kuma cike da al'ajabi da tausayi: yanxu dai kibari idan kin huta zakiji komai in Allah ya yarda" kuka kawai take tana cewa dan Allah sukaita wajan iyayenta taga awani hali suke" mallam yace ya isa haka nawwara kiyi hakuri insha Allah zamu sada ki da iyayenki, tace to ngd' nawwar da awwal tabasu tausayi sosai," mallam yace tashi kije ki kwanta abunki kar kisaka damuwa aranki kinji, kai tad'aga masa tana sharar kwalla. bayan tashiga ciki mallam isma'il ya kalli mallam da su nawwar yace yakamata mukai yarinyar nan wajan iyayenta, awwal yace haka ne kam sai muje gobe ko? tunda kano ne wajan bazai yi mana wuyan ganewa ba, hakane Allah ya kai mana rai. yaune ranar dasu mallam isma'il da su awwal zasu kano da nawwara, tafiya suke cikin mota kowa da abunda yake sakawa azuciyar sa har suka isa kano. *KANO* Alhaji idrisa ne kwance Afalonsa yana tunanin rayuwa" hajiya maimuna takawo masa ruwan sha da abinci, zama tayi kusadashi, tace mallam haryanxu bazaka daina yawan tunanin nan ba! yace haba maimuna' ai tunani ya zamemin dole yau ace shekara bakwai babu nawwara babu alamar ta" yau koda gawarta nagani daya fiyemin kwanciyar hankali , bamu san awani hali take ciki ba , hakane Alhaji, haka Allah y kaddaro mana muciga ba dayin addu'a, insha allahu zamu sami mafita , suna cikin magana ne wani yaro yazo yace ana sallama da Alhaji wai baki Daga maiduguri, yace to kace su shigo. *EDIDTED* by *UMMEE* *ADNAN* TAKU UMMU RUMAN *Nusnim* *pyar* kuyi hakuri da wannan banajin DADI ne [1/11, 4:39 PM] ‪+234 806 448 1931‬: *ALJANA* *CE* *KO* *MUTUM* *By* *Nusnim* 5⃣6⃣➡6⃣0⃣ yace to kace su shigo, dan Aiken ya koma yace wasu mallam isma'il ance su shiga, nawwara tana cikin mota zaune da badan su mallam sun dakatar da itaba da tuni ta falla da gudu ta shige gdan, sai tsaki take ta ja, shiko nawwar kallon ta kawai yakeyi, yadda ta hade giran sama data kasa" azuciyarsa yace wannan yarinya za ayi daru da ita. muryan mallam ne ta katse masa tunanin sa, mllam yace sameeratu fito kimana jagora cikin gdannaku, kamar ko jira take amata magana, cikin murna ta fito waje tana washe hakora" tace to mallam, yace to bismilla mujenku, itace agaba tana tafiya cikin nutsuwa. suna karasowa tsakar gdan sukaci karo da zainab tana wanke wanke, karaf sukayi ido hudu da sameeratu, zainab ta saki kwanon hannun ta, ta arce cikin gidan da gudu tana ummu ummu ummu, gatanan gatanan, yayin data fada jikin Hjy maimuna, tace ke lafiyarki kuwa, alhajine yace zainab wakika gani kike gudu haka"" sai haki kike. ji yayi ance abba nice kunnuwan shi ce ta jiyo mishi muryar da bazai taba mantawa dashi ba, muryarda a kullum yake mafarki da tunanin Allah yasake had'a fuskokinsu kafin mutuwarsa" atare suka d'ago idanu cikin sauri shida hjy maimuna, suka zubasu ga kofa, nawwara ce tsaye tana hawayen farin ciki. Alhaji idrisa da hjy maimuna sukayi zumbur suka mike tsaye, kowanne bakinsa na rawa sun kasa furta kalma d'aya" dakyar kamar had'in baki sukace sameeratu kece kuwa, karasowa tayi falon da gudu ta rungume iyayen nata , tana kukan murna, abba umma nice nawwaran Ku, ban mutu ba inanan. su nawwar dake gefe sun basu tausayi, har sai da kwalla ya fito musu, nawwara tace zainab nice fa sis dinki wacce kuke kwana daki daya, da gudu zainab ta rungume nawwara, sister nah ina kika je nayi kukan rashinki na tsawon shekaru, amma kin dawo kenan baza ki koma ba ko?, nawwara ta share mata hawaye. tace karki damu sister zee na dawo kenan insha Allahu bazan sake tafiya na barki ba, Allah sarki dama yan magana sun ce sabo turkin wawa,sai alokacin Alhaji idrisa ya kalli bakin kofa inda su mallam isma'il ke tsaye cikin tausayi. ya karasa wajan su tareda mik'a musu hannu sukayi musabaha, sannan ya nuna musu waje suka zauna, aka gaggaisa, mallam isma'il ne yafara magana, yace Alhaji mu baki ne daga maiduguri, munxo ne don mu sadaka da yarka sameeratun nawwara, sannan kuma mufayyace maka abubuwan da muka sani, Alhaji yace ikon Allah ashe duk shekarunnan da suka shude sameeratu tana maiduguri bamu sani ba. mallam yace a'a bata maiduguri tana duniyar aljanu har natsahon shekara bakwai nawwara tazaro ido waje tareda dafe kirji tace duniyar aljanu kuma? mallam yace eh, Alhaji ya jinjina kai, yace lallai kam nayarda, sbd na tafka babban kuskurenda ko makiyina bazan masa fatar shiga halin dana shiga ba, nan dai mallam ya kwashe labarin bacewar nawwara har izuwa lokacin da aka ganta, babu abinda Hjy maimuna alhaji idrisa da ita kanta nawwaran keyi sai kuka, nawwara tana cewa yanxu nice nayi tarayya da aljanu, abbanta yace nawwara kiyafe min, duk ni naja miki na rashin d'aukar shawara da maganar malaman islamiyyarku. a'a abba ni baka min komai ba kaddara ce kawai tafado mana, Allah ya yafemu baki d'aya" ta d'aga ido tayiwa su mallam godiya, mallam yace ba sai kin mana godiya ba, kiyawa Allah godiya sannan kuma ki gode masu awwal abisa sadaukar da ransu da sukayi sbd ceto taki rayuwar, sannan kuma ameenatu bin saifulla duk da wannan tariga ta koma duniyar su. nawwara takalli su nawwar tace yaya awwal yaya nawwar , ina matukar godiya akan tsamoni da kukayi daga aljana zuwa mutum, Allah ubangiji yasaka muku da mafificin alkhari, yabaku abokanan rayuwa na har abada, yasa aljanna fiddausi ce makomar ku" kowa yace amin su nawwar sunji dadin addu'ar ta," mallam yakara yiwa Alhaji idrisa nasiha akan shiga hurumin aljanu, da yawaita addu'oin kariya,, nan dai mallam yayi tanuna musu abubuwa masu muhimmanci dakuma hanyoyinda za'abi dan gujema shed'anun aljanu, Daga bisani aka kaisu dakin bak'i tare da abinci da abunsha, ankarramasu sosai. nawwara da kanwar ta suka fad'a daki ana hiran yaushe rabo, Alhaji idrisa ya hana afadama kowa dawowan nawwara, yace sai tayi kwana biyu lokacin ta huta,, kwanan su mallam biyu suka tafi' kowa ya kama hanyar garinsa tareda abun arziki,dakyar suka amsa, nawwar ya tafi cike da begen abar sonshi. kwanan nawwara biyu a gida cikeda jindadin ganin y'an uwa da abokan arxiki anzo tayasu murnan dawowarta" harda mallaman islamiyarsu da aminiyarta khadija, wanda sai da sukayi kukan farin cikin sake ganin juna' sauda kuwa wato yayar nawwara,harda dan kwarya²n walima ta shirya ma nawwara , mami hafsa da autar ta mimi" sunyi murnan dawowan su nawwar, mimi tashirya ma yayan nata abinci kalala, bayan yayi wanka yaxo yaci abinci, sannan yabasu mami lbarin abunda ya faru"" mimi tace lallai hamma kai jarumine, da kowace mace zataso samunka amatsayin namijita, gasky aunty nah nawwara, tayi dacen gwarzon namiji dan kwalisan matasa, hamma zan so inga wannan auntyn nawa, harara yatsa mata' yace kajimin yarinya da iyayi' ke harkinsan wani jarumi! murmushi tayi tarufe idanunta tace laaa hamma aida gske nake koh mami!' mami tace gsky nima zanso inga wannan nawwaran data kad'a kwakwalwar hamman nawa. suka sa dariya, mami tace dafatan dai bakayi kauron baki wajan furta abunda ke xuciyarka ba, nawwar yace mami cikin raunanniyar murya,da wuya sameeratu ta soni, don yadda ameenatu tace mana kwata²ita bata da lokacin wani d'a namiji, sannan kuma da alamun ta tsaneni, mami tace meyasa kace haka, nan yabata labarin sbunda aminatu bin saifullah tafada masa daza ta tafi, da yadda kuma nawwaran ta nuna masa a maiduguri. mami ta tausayama d'anta, lallai jarabawa ce ke binka nawwar" abunda zan ce maka kadage da addu'a insha Allah idan nawwara alkhairi ce agareka babu makawa saika aureta, murmushin jindad'i yayi yace nagode mami nah, Allah ya barmin ke kiga jikokin ki. bayan kwana biyu da dawowansa yana kwance akan gado yana tunani nawwara, da yadda zai tunkareta maganar soyayyarsu" ya tuna yadda yaga farin cikinta a lokacin da sukaje gidansu taga iyayenta, yayi murmushi, tare da lumshe idanun shi, yace ana hubbiq tartin ya samra, ,hubbee ilaiki abadan ya samra,yakara sakin murmushi, jiyayi antab'ashi. *EDIDTED by UMMEE ADNAN* _TAKU UMMU RUMAN_ *Nusnim* *pyar* [1/11, 4:39 PM] ‪+234 806 448 1931‬: *ALJANA* *CE* *KO* *MUTUM* 6⃣1⃣➡6⃣5⃣ ji yayi anta6a shi' yayi saurin bude idanunsa yana cewa nawwara kece kikazo, sai kuma yaga ashe kanwarsa ce mimi, yace au sorry, auta ya akayi ne, mimi ta karasa zama wajenda yake, tare da cewa hamma nah lallai kayi zurfi sosai acikin son aunty sameera. yayi murmushi, hamma pls karage wannan son da kake mata" don karya maka illa, don so bala'i ne idan yayi yawa , cikin mamaki yake kallon auta mimi, yace auta badai harkin fara soyayya ba? me kagani hamma , yace to inba hakaba' tayaya kikasan so yanada illa idan yayi yawa? dariya tayi tace kai hamman aiba abin mamaki bane don nasan kalmar so' da illar zurfafawa acikinsa" idan kayi la'akari da yanayin zamaninnan namu" damu yara muke tashi da kallace² ko karance²n littafan soyayya' yace a lallai mimi naga alama kin isa aure.to ke a ina kk san ma'anar so? kai hamman ni bance aure nakeso ba, kawai dai nasan kalman sonne abakin kawayena dayake duk suna da samarai, nice dai bana kula samari ,kuma suna bani labarin samaransu da irin sonda sukema juna, baki ta turo tace sannan kuma ma ai na isa auren tunda shekarata 17 yanxu, tana fadin haka tabar dakin da gudu don kunyar yadda taga yayannata ya kafeta da ido" saida takai kofa tace Dr awwal ne ke nemanka, OK, cemasa yashigo. awwal yashigo dakin da sallama nawwar ya amsa mai, bayan ya zauna suka gaisa , awwal yace wato kananan kana wannan banzan tunanin naka ko, hmmmm ajiyar zuciya nawwar ya sauke, yace awwal ya kamata muje Kaduna plx, don zuciyata bazata iya hakura da sameera ba" ina so in fada mata abunda ke raina koda bazata amince min ba, zandai fad'a mata ne ko zuciyata ta daina zuginda take" awwal yace hakan ma yayi inshaAllahu nasan zata amince maka. kai dai kacigaba da addu'a,. yau jumma'a sameeratu zaune adaki suna hira da zainab kanwarta da umman su, khadija tayi sallama tashigo, tare da gaida umma, zainab ta gaisheta, umma ta basu waje, zainab kuma ta tashi don shirin zuwa islamiya, khadija tace sameera result dina ya fito fa, na jamp kuma nasamu, nawwara tace natayaki murna sosai, nima abbana yace yaba da kudi azana min lokacin da su zainab zasuyi, khadija tace uhumm kedai nawwara babana yace na fitar da mijin aure inyaso daga baya naci gaba da karatun adakin mijina. sameera tace haba dai' kice zamusha biki sosai, to waye gwanin naki! dry khadijat tayi" tace kema ai kinsan idan ba mallam abdullahi na islamiyar muba sai rijiya mai kwalabe, dan ustaz dina, lallaima khadija, wato auren ma yakusa, shine sai yanxu kk gayamin" tayi murmushi, kedai bari kawai zamusha bikin ustazai". Kema nawwara yakamata ace kin fidda mijin kafin abbanku ya miki maganar aure, kinsan halin tsofaffinnan namu" sameera tace kayya keleni nikam, ni haryanxu banga wanda nake soba, kai sameera baza ki daina ruwan ido ba ko,kina son zainab ta rigaki aure ne, to inta rigani sai me dubu nawa suke aure subar yayyen su, uhmm to mudai bamu fatan hakan ta kasance, sameera tace kinganni nan wlh ni soyayya ma tsoro take bani, ki kallafa kawar mu murja yadda nasan suke zabga soyayya da nasir dinta amma farad daya ya juya mata baya, ya nuna bai santa ba, sbd ya had'u da wacce tafita, duk gashi tazamo abar tausayi, kai al'amarin maza yana bani tsoro wlh" Allah dai ya zab'a mana mafi alkhairi, ya bamu mazaje nakwarai, wayanda zasu rikemu da Amana amin. sameera tace nikam ki dan rakani gdan yaya sauda mana , ina son kai mata kayan dinkinta ne wanda na karbo mata, khadija tace OK ba matsala sai muje, bayan tasanar da umma tace Allah ya kiyaye hanya , adai dinga addu'ah duk inda za aje, to umma in Allah ya yarda. suna cikin tafiya sai sukaji wani sassanyar murya mai dad'in sauraro abayan su, ana cewa Assalamu alaikum, gaba ki dayan su suka amsa tareda juyowa, zaune yake akan mashin dinsa (wanda ake ce ma wayyo kudina) sanye yake da shadda pink clr wandansa dai² idon sahu , fuskarsa dauke da saje wanda ya kwanta luff² gwanin sha'awa, idonsa sanye da tabarau' kallonsu yake cikeda annuri a fuskarsa" atakaice dai ustaz ne kyakkyawa ajin farko. ya karaso wajan su nawwara, yace inbazaku damu ba kudan bani minti biyu don Allah' nawwara tayi saurin cewa bakomai muna jinka, Khadija ta kalli nawwara da kyau cikin mamaki, abunda bata tab'a ganin nawwara tayiba kenan, yace da farko nidai sunana Yusuf mahammad ni dalibi ne a makarantar state universty (kasu)ina karantar islamic studies Kuma ni mazaunin kinkinau ne, ina yawan zuwa nan layin wajen aboki na, Allah ne ya hadani daku kuma take naji ina sonki kuma da aure nake sonki shiyasa bantsaya maki kwana2 ba' sonake kizamto uwar y'ay'ana, khadija ta katseshi da cewa wacce daga cikinmu? yace wannan kawar taki yanuna nawwara, itako nawwara tunda yafara zance shitake kallo muryarsa mai dadi take sauraro' yadda yake fitar da lafuzan cikin kwanciyar hankali, murmushi tayi, shima ya maida mata da martani, ya kuma cewa ko zan iya sanin gdan Ku do nakawo miki ziyara, naga kamar tsaida Ku danayi anan bai dace ba , nawwara tace ba matsala, nan tayi mishi kwatancen gdan nasu, tare da fada mashi sunanta, sukayi sallama suka wuce. sameeratu ta kalli khadija wacce ke binta da kallon, tace dijana yau naga irin mijin danake burin aure arayuwa ta, yusuf yamin sosai khadija, khadija tace ikon Allah , kice faraddaya har kin kamu, amma gsky zaku dace, course din dakike son karanta gashi shima shiya keyi, amma nataya ki murna Kawata, nima naji ya kwanta min arai, suka tafa nawwara kamar an sata a aljannah"" Allah sarki nawwara ko ya zaiyi. awwal ne da nawwar agaban mahaifin sameera sun zayyana mishi abunda ke tafe dasu, kuma yaji dadi sosai, dan yasan nawwar me kaunar yarsa ce, ko bayan ranshi baza tayi kuka da idanunta ba, yace musu shibashi da matsala, ya amince masa ya nimeta, idan sun sasanta kansu shikenan, sunji dadin maganar abban, Alhaji idrisa yasanar da hjy maimuna itama ta nuna murnan ta, nawwara taji lbarin zuwan su nawwar, inda ummanta tace taje su gaisa,, don ba wanda ya fada mata abunda ke faruwa, su awwal na zaune a falo , sameera ta shigo cikin sallama. ta gaishesu cikin faran faran, har suna zolayar juna, awwal yayi gyaran murya, sannan yafara jawabi game da abunda ke tafe dasu, ji yayi tace SO kuma da karfi. *EDIDTED* by *UMEE* *ADNAN* TAKU UMMU RUMAN *Nusnim* *Pyar* kuyi hakuri sungullo line suka sha gabana [1/11, 4:39 PM] ‪+234 806 448 1931‬: *ALJANA* *CE* *KO* *MUTUM* *By* *Nusnim* 6⃣6⃣➡7⃣0⃣ so kuma, gaskiya ina jin kunyar ku, abar maganan nan dan Allah, awwal ya miki don basu waje" bayan fitarshi nawwar yace sameera Allah ne ya jarabce da sonki, bani na Dora mawa kaina ba, sannan kuma ke kika shigo rayuwata. nawwara bazan takura ki soni ba, amma kuma rasaki arayuwata akwai Matsala, sameera munyi soyayya dake alokacin daki ke aljanna sosai amma yanxu wannan soyayyar ta rushe, Allah sarki dama da zata dawo, sameera ki zauna kiyi tunani sameera, idan nawwar ya dace da rayuwarki ki sanar dani idan kuma bai dace ba kisanar dani ga katin number nah, cikin raunanniyar murya yace nawwara karki manta ina sonki ina kaunar, koda baki aureni ba bazan taba mantawa dake ba. yana gama fadin haka ya fita yana share kwalla, awwal yace kayi hakuri Dr komai mukaddari ne Daga Allah, idan Allah yasa nawwara matar kace to tabbas ba makawa sai ka aure ta, idan kuma ba matar ka bace to sai ka fawwala ma allah lamarinka. jikin nawara yayi sanyi da jin kala man nawwar don ya bata tausayi, amma kuma ita zuciyar ta Yusuf yake so, baza ta iya rabuwa da Yusuf ba. bayan kwana biyu, sai ga Yusuf ya zo gdan su sameera , lokacin kuma Alhaji idrisa zai shiga GDA suka hadu Yusuf ya mai sallama, tare da durkusawa kasa yana gaishar da alhajin, Alhaji yace bawaye kaba dan samari, Yusuf yace dama nazo wajen Kane abba. to bismillah mushiga har falo suka shiga yusuf ya zauna akasa,Alhaji yace me ke tafe dakai ne dan samari, nan Yusuf yafada mawa Alhaji komai game dashi, da kuma abunda yazo nema. Alhaji ya gamsu da maganan Yusuf , kuma ya yaba da halinshi, yace yusuf inta wajenane babu matsala, sai Kane mi ita sameeran in kun daidai ta shikenan, Allah ya muku albarka, amin abba, nagode sosai. bayan shigan abba cikin gda yace zainab tafada mawa nawwara tana da bako afalo Yusuf, nawwara naji taji dadi yarufeta sosai tasha kwalliya tafeshe jikinta da turare, tashigo cikin falon cikin sallama, ya amsa mata"" yana murmushi, itama ta maida mai da martani. a'a gimbiyata kin karaso tayi murmushi barka da zuwa habibina dafatan kana lfy, lfy lau , gsky naji dadin ganinki sameera, Allah ko, eh mana malamina kenan, cikin zolaya yace taya ya nazama malaminki. ta kanne ido daya cikin shagwaba tace SBD zaka dinga koya min kalaman soyayya , kasan ance ustazai sun iya soyayya, ko ba haka ba aris dina, yayi dariya, baki da dama gimbiyata. soyyay tayi karfi tsakanin nawwara da Yusuf, har ta kai da ta manta maganan da sukayi da nawwar, abvanta yasa aka kirata, yace mamana nikam wa aka tsayar ne amatsayin mijin? tarufe fuska alamun jin kunya, abba ni Yusuf nake so , kintabbata mamana, eh abba, , Alhaji yace kije kiyi tumani dai mamans, ki nutsu, kiga waya fi dacewa da rayuwar ki, to abba, tafita dakin tana tunanin maganan abba. nawwar ne akwance cikin matsinacin wani hali yau kwana biyu bashi da lfy amma yaki yabari asani, turo kofan akayi, yana kwance cikin bargo sai rawan sanyi yakeyi, Mami hafsat ne ta karaso cikin Saudi tana nawwar lafiya naganka a kudundu ne. zaiyi magana ne sai tari ya sarke shi, jinine ya dinga fita Daga bakin sa Mami ta rude, tana hamma meke damunka, ka boye bamu sani ba, tana ganin kamar numfashin shi yana sama, tasaka kara, Allah yaso sulaiman bai fita ba, duk suka shigo harda Mimi, mami tace sulaima kusa shi amota mukaishi asibiti, , Mimi sai kuka takeyi ,nawwar yayi ma Mami alamu da hannu tazo daidai saitin bakinshi, yana cewa Mami kiyafe min, kwanana ya kare , dib sai taji shiru, Mami tasaka wani uban ihu, tuni ta sumu. innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, kulli nafsin za ikatul maut. *EDIDTED* by *UMMEE* *ADNAN* TAKU UMMU RUMAN *Nusnim* *pyar* [1/11, 4:39 PM] ‪+234 806 448 1931‬: *ALJANA* *CE* *KO* *MUTUM* 7⃣1⃣➡7⃣5⃣ An wuce da nawwar asibiti da gaggawa, sulaiman ya kira awwal yasanar dashi, sun amshe shi don ceto rayuwar sa, Mami kuma Mimi ce tayayya fa mata ruwa, ta tashi tana kuka, , tace Mimi nawwar ya rasu ko? Mimi tace suna asibiti da yaya sulaiman, Mami tace maza tashi muje, a'a Mami ki kwanta ki huta ni zanje, insha Allah hamnan zai tashi da izinin ubangiji"" kai Mimi bazan iya zama agida ba ban San awani hali nawwar yake ba. To Mami tashi muje, lokacin dasu Mami suka karasa asibitin suka CI karo da sulaiman , yana safa da marwa acikin asibitin"" , yana jirin fitowan likita, Mami tace sulaiman ya ake ciki ne, hamman ya rasu ko, yayi saurin cewa a'a Mami yananan da ransa addu'a yake bukata. suna cikin magana ne Dr awwal yafito duk suka dumfaro shi Mami tace Dr lfy. yace karku damu mun samu kanshi yanxu hakama yasamu bacci insha Allah , zai dawo yadda yake karku damu. Mami ta sauke ajiyar numfashi tace mun gode , dukkan su suka shiga dakin dayake yana kwance, Mimi ta karasa wajan gadonshi tarike hannun shi, tana Allah sarki hamman na, adalilin son nawwara ka kamu da wannan cuta, hamman na isha allahu nawwara matar kace INA ji ajikina. sameeratu zaune adakinta ita da khadija, tana bata labarin abunda abbanta yace mata, khadija tace sameera me kika gano cikin maganar abba, na lura abba yana son na mijin dazai rike mishi ke sosai kuma ya kauna ce ki, shiyasa yace kije kiyi tunani. hakane Indai wannan AI nasamu, tunda ga Yusuf yana matukar sona hakane, yauwa nawwara nikam ya zancen maganar nawwar ne, nawwara tace ni Sam na manta da wani nawwar ma. khadija ta kalleta da kyau tace sameera inda zakiji ta tawa ni aganina, duk duniyar nan babu mai sonki kamar nawwar, shi yafi dacewa da yazamo mijinki, ki kalla fa irin kasadan da yayi adalilin sonki, ya kamata kixau na ki duba zancena. sameera tayi shiru kamar mai tunani, sai alokacin ta tuna da katin numbern wayan daya bata, ta sauke ajiyar zuciyarta, Allah dai yashige mana gaba amin, cikin mafarki sameeratu taji kamar ana ce mata. sameeratun nawwara karki yada soyayyar da nawwar ya miki kimishi halarci, shine masoyinki na asali, mai kaunar ki, mai tausayinki, kuma shine mijin da iyayenki suke son ki aura ki daure ki amshi soyayyar sa, don yanxu haka yana cikin wani hali kitaimaki nawwar dan Allah. tayi saurin bude ido tana dube dube cikin tsoro ta kudundune tana addu'a. nawwar zaune a asibiti ya samu sauki Mimi na bashi abinci abaki tana mai hira yana dariya, Mimi tace hamma dan Allah ka daina dumawa in Allah y yarda sai ka auri aunty sameera, yayi murmushi, yace Allah ya yarda yar kanwata. ansaka ranar auren nawwara da Yusuf sai shirye shiryen biki akeyi, abun mamaki kuma Sam nawwara bata zumudin yin auren Yusuf din , hankalinta na kan nawwara. tana son sake ganinshi don tasan halin dayake ciki, SBD tana tayawan mafarkai mafar kai, duk ta sukurku ce. biki sai matsowa yakeyi nawwar kuma ya warke amma har yanxu yana tunanin nawwara, kuma gabanshi na yawan faduwa, addu'oi kawai yasa gaba. yau jumma'a ya kama ranar auren sameeratun nawwara da Yusuf, wajen daurin aure ya Tara mutane da dama ga ustazai ango Yusuf sai washe baki yake. *EDIDTED* by *UMMEE* *ADNAN* TAKU UMMU RUMAN *Nusnim* *PYAR* [1/11, 4:39 PM] ‪+234 806 448 1931‬: *ALJANA* *CE* *KO* *MUTUM* 7⃣6⃣➡8⃣0⃣ Ango Yusuf sai washe baki yakeyi, yayin da abangaren amarya ji take kamar tayi hauka saboda bakin ciki, jitayi bata son auren"" hankalinta y karkata kan nawwar. tana son ta kuma sashi a ido kafin akaita dakin aurenta, khadija ne ta dafata tace lfy nawwara kike irin wannan tunanin? tun da'zu nake miki magana amma hankalinki ya tafi wani wajen, gashi baki shirya ba kuma kin San ana sauko Daga daurin auren abokanan ango wajenki za su zo. sameeratu ta sauke ajiyar zuciya tace khadija kin San Allah Sam bani son auren nan da da yadda zanyi Dana warware auren, vaki galala khadija ta bita dashi cikin mamaki. tace nawwara kinsan me kike fada kuwa anya kina cikin hankalin ki kuwa?bafa auren dole ake miki ba, ke kika zaba mijin da kanki, ko kin manta ne, nawwara tayi murmushin da bai kai ciki ba, tace tabbas ni nazabi Yusuf daya zama mijina amma kuma yanxu Sam bani sonshi , hankalina y karkata kan nawwar, ina son Insan halin dayake ciki khadija. sai ga hawaye yana gangaro a idanunta, ni ban San meke damuna ba, da nayi tunanin Yusuf shi yadace da rayuwata, sai Daga baya nagane, nawwar shine mijin dayafi dacewa dani, shine mutumin daya kaunace ni tun fil azal, har gida ya biyu ni, yana rokon barar soyayyata, ayayin da idonshi cike da hawaye, muryar shi adaushashe. kalma na karshe daya furta min yace nawwara koda baki aureni ba, bazan taba daina sonki ba har abada, taci gaba da kuka , tace khadij sai yanxu nasan ina son nawwar fiye da yadda kike zato, amma ina lokaci yakure, nayi Dana sanin da banta bayi arayuwata ba khadija. takara fashewa da kuka, khadija na lallashinta da ban hakuri, dakyar tasamu kanta har tashirya, alokacin kuma abokanan ango da shi angon sun isu har an daura aure. Abangaren nawwar kuma tunda aka daura auren nawwara gabanshi ke fadi sai addu'oi yakeyi, duk kan su suna zaune afalo suna hira Mami da nawwar da sulaiman da Mimi, duk sunsha ado, Mimi tace hamman na yace na'am autar Mami, yau zan maka wani kyauta Dana Dade ina son in maka, yace Allah ko,. eh mana ko bakaso ne, me zai hanani son kyautar da autar mu zata min sai suka saka dariya, yauwa hamman nah, shiyasa nake sonka, amma menene goron albishir dina, yace duk abunda kike so zan baki. tace ko menene natambaya zaka bani , sosai ma, to shikenan Allah y kaimu anjima, Mami yaya sulaiman duk kuna shaida ko, suka ce muna sheda Mami tace Mimi yau yaushe zaki fitar mana da mijinki mugani , cikin shagwaba Mimi tace kai Mami dudu du nawa nake, amma koda yake nayi sabon saurayi very soon zaku Ganshi, sulaiman yace Allah yashirye ki Mimi Sam baki da kunya, agaban mu kike wannan zancen. cikin shagwaba mimi tace hamman kana jin yaya sulaiman ko, yi hakuri rabu da sulaiman yana kishi ne din jiya budurwar shi tace bazata auri mai gemu ba sai ya aske, duk kan su suka kwashe da dariya. karfe biyar na rana inda za awuce da amarya gdan angonta dake kaduna , bayan iyayenta sun mata nasiha sosai tayi kuka rabuwa da iyayenta jitakeyi kamar ta gudu, da zainab kanwarta akatahu da khadija sai aunty sauda da kanwar baban su. sun iso Kaduna lfy Inda aka wuce da amarya gdanta dake malali halliru dan turo, gdan da aka kai amarya ya basu mamaki, gdane tsararre komai nashi dadai, amma kuma basuyi zaton yasuf yana da kudi hakaba, SBD dan makaranta ne shi. baki an vasu dakin daza su kwana ita kuma amarya tana dakinta tsakiyar gado sai sheshshekar kuka takeyi, tana bakin cikin kasan cewarta haka amatsayin matar Yusuf. Mimi ce tace hamman kai fa muke jira sulaiman ma yashirya Mami tace nikam wai ina zaku hakane, wlh Mami wani waje zamuje, sai ga hamman ya fito cikin tsadacciyar shadda Wanda Mimi ta dinka mishi sai kamshi yakeyi, yafito a fillon shi saf, duk kansu sunyaba da kwalliyarshi, don yayi kyau, kamar wanda baida damuwa. hon din mota sukaji awaje awwal ne shima yazo dashi za atafi, dukkan su suka fito haraban gdan , suka shiga muta suka wuce, hon sukayi mai gadi ya bude musu suka shiga cikin gdan, nawwar mamaki ne yacika shi, inane nan kuma, Yusuf ne da abokinshi suka karaso cikin murna suka tarye su, yayin da aka masu ISO cikin gda. mimine tace hamman dina kaga wancen dakin to kashi ga kyatar Dana maka yana ciki , dan Allah ka isa ga kyautar nan hamma n kuma kamin alkwarin zaka karba kyautar nan. yayi murmushi me hade d mamaki yace ya amince, yakarasa wajen daki gabanshi sai faduwa yakeyi, yabude dakin tare da sallama, nawwara dake kan gado taji gabanta ya fadi don bazata iya manta muryannan ba, icon nawwar ya sauka akan abunda ya hango kan gado yana mamaki yakarasa wajen batare da ta dago ba, kirjinshi na har bawa itama haka , cikin tsoro yasaka hannu ya Daga gyalen dake rufe afuskar nawwara dago kai tayi, suka hada ido da nawwar kowannan su ya zaro ido waje cikin tsoro. *EDIDTED* by *UMMEE* *ADNAN* TKU UMMU RUMAN *Nusnim* *pyar* [1/11, 4:39 PM] ‪+234 806 448 1931‬: *ALJANA* *CE* *KO* *MUTUM* *By* *Nusnim* 8⃣1⃣➡8⃣5⃣ suka hada ido da nawwar kowannan su ya zaro ido waje, yayi saurin sake gyalen tare da mike wa tsaye, yana ja da bays, itama saurin tashi tayi tana murxa idanuwanta shin mafarki takeyi ko da gaske ne . har sai da ya Isa bakin kofa zai fita yaja burki ya tsaya, yayin da zuciyar shi ke harbawa, ya juyo don kara gasgata abunda ya gani, still dai nawwaran ce ba wata ba. yashiga tunani me kanwarsa take nufi ne, tana nufin sameeratu ce kyautar data mashi? sameera data zuba mawa nawwar ido takasa magana itama azuciyarta, tunanini take, anata zaton nawwar abokin mijinta ne Yusuf. cikin murya sassanya sameeratu tace yaya nawwar, ya juyo da dubanshi gareta, tare da kara so wa wajenta, hawaye na zuba a idanunshi, yana mata wani irin shu'umin kallo na soyayya, yayin da itama haka. takara cewa yaya nawwar kaya fe min nayi kuskuren daya zame min Dana sani, nakin amsar soyayyarka, alokacin son Yusuf ya rufe min idona, bana ganin kowa sai shi, sai da akasa mana ranar aure, sannan hankalina ya dawo gareka, gashi yau Yusuf shine matsayin mijin Dana aura takara fashewa da kuka. nawwar najin haka yaji jiri na son dibanshi zai fadi kenan, ta taho da sauri cikin kidima ta tareshi ya zauna bakin gado ya dafa kanshi da hannayen shi, yana salati" yace sameeratu lokaci ya kuri narasaki har abada, tace kayi hakuri nawwar nice da wannan kaicon don xuciyata tana tare da kai, baxan taba manta ka ba Nima sai ta fashe da kuka. ya matse wani hawaye mai radadi tare da cewa narasaki har abada nawwara, ji sukayi ance hamman dina Baka rasata ba hasalima kun kasance a inuwa daya wato mata da miji. gaba ki dayan su suka tashi don kallon mai magana, Mimi ce ke karasowa cikin dakin, yayin da Yusuf da awwal da khadija da zainab suka shigo" cikin murmushi, Yusuf yace kaji masoyan asali Mimi tace aikuwa. nawwar yace Mimi mekike nufi, tace hamman nah ina nufin aunty sameera matar kace itace kyautar Dana maka, nawwara ta kalli Yusuf don Neman Karin bayani. tace Yusuf kafahimtar dani abunda naji, yace nawwar abunda kikaji gsky ce da nawwar aka daura miki aure, ta kara kallon khadija da zainab suma suka Daga mata kai alamun haka ne. nawwar da nawwara kamar sun hada baki sukace atare, tayaya hakan ta faru, awwal yace yanxu Mimi zata fada muku. Mimi ta soma magana tace, hamman in baka manta va lokacin da aka kwantar da kai a asibiti na maka alkwarin insha allahu sai ka auri nawwara, to tunda ga lokacin nadauki aniyar nemo nawwara, SBD bana son in rasaka, da haka naje nasamu Dr awwal nafada mishi kudirina , shima ya aminta. takanas mukaje kano dashi, alokacin ma ana shirye shiryen bikin nawwara da Yusuf, lokacin ZANU shiga gdan sai muka ga zainab da khadija, muka gabatar musu da kanmu da abunda ke tafe damu, sun nuna farin cikin su sosai. kuma sun Samar mana nawwara bata son auren da Yusuf, muka rasa ya zamuyi mutunkari Yusuf da maganar, ashe Yusuf dan makarantar su yaya sulaiman ne kuma abokinshi ne, to shine nasanar masa, shikuma yafada mawa Yusuf cikin sauki Yusuf ya amince, SBD amintar dake tsakanin su da yaya sulaiman, daganan kuma muka dunguma wajan abbban nawwara muka sanar mishi. shima yayi murna dajin wannan labarin , Yusuf yace kar asanar ma nawwwara sai dai kawai taganta da nawwar, Nima haka nace kar asanar mawa nawwar, sai Mami kadai da Abban mu, to kunji yadda akayi. nawwar ya rungume yar autar su yana thank you my sister, Ashe haka kike sona daya, lallai na jinjina miki Allah ubangiji y baki miji mafi alkhairi, kowa yace amin. itako tace Allah ya bani Yusuf hamman nah, nawwar yace mene cikin dariya sulaiman yace AI Yusuf ke sonta. itako nawwara tana jikin khadija tana kukan murna da Allah ya nuna mata wannan rana, gaba ki dayansu suka fito falo don su Mimi zasu koma GDA, nawwara da nawwara sai Satan kallon juna suke. khadija taci Mimi AI nikam binku zanyi don idan na kwana gdannan zan kwashi kayan haushi SBD nasan za agurji soyayya gara nayi can, bakiga ma yadda nawwara ke harara ta va, alamun bata son inkwana don karna takura su, sameeratu takai ma khadija duka. Yusuf ya ijye musu gazan amare da su drinks yace amarya da ango mun barku lafiya, so Ku nuna mawa duniya kunfi *king* *laisu* da *rumana* na takaddan *kutausaya* *min* iya soyayya dukkan su suka kwashe da dariya. bayan tafiyan su nawwar ya janyo nawwara cikin jikinshi ya rungumeta yana ma Allah godiya daganin wannan ranar, bayan sunci sunsha sun gabatar da sallan da akeyi, tare da addu'oi, daganan kuma sai zance ya canxa salo, inda suka Lula duniyar ma'aurata, ina ganin haka nayi waje abini don kunya, amma nabar hjya seeema, zasu gano muku. kubiyoni agaba donjin wani soyayya zata kasance agdan ma'auratan nan. *EDIDTED* by *UMMEE* *ADNAN* TAKU UMMU RUMAN . *Nusnim* *pyar* [1/11, 4:40 PM] ‪+234 806 448 1931‬: *ALJANA* *CE* *KO* *MUTUM* *By* *Nusnim* 8⃣6⃣➡9⃣0⃣ su Mimi sun Isa gda tare da ba mawa Mami labarin yadda suka baro su hamman din, Mami taji dadi sosai kuma tayi musu addu'an fatan zaman lafiya da dorewa. Mimi tace Mami ina aunty sauda, Mami tace AI tun lokacin da aka kawota, ta kwanta SBD gajiyan biki, hakane kam gashi sunsha hanya. ASUBA TA GARI. nawwar ne yatashi Daga bacci don yin alwala SBD zuwa masallaci, ya tsura mawa nawwara ido"" yana kallonta, yayi murmushi tare da shafo gefen fuskarta. bayan tafiyar shine itama ta tashi donyin wanka sannan tazo tayi sallah, bayan ta idar tafara karatun alqur'ani, lokacin kuma nawwar ya dawo masallaci. ya yaba da hazakarta, don da ka take karantawa, bayan ta gamane ta juyo sukayi ido hudu dashi ta sunkuyar da kanta kasa tana gaisheshi, ya amsa mata cikin murmushi, tare dace wa y gajiyan biki da sabon wuri kuma, tace gajiya kam tabi gado. yace masha Allah haka akeso, yace nawwara ki saki jikin ki dani ni mijinki ne mai kaunar ki, in Allah y yarda bazan taba barin wani abu y same kiba , nan suka fayya ce mawa junan su irintarin son da sukeyi wa juna, daganan kuma suka koma bacci" sai wajajen karfe Tara suka tashi, ya wuce bangaran sa don ya shirya. itama tashiga wanka bayan ta fito ta tsara adonta mai kyau cikin atamfa , tana cikin shirya wane taji hayaniya a falo, su khadija ne suke hamman tsiya Mimi tace ango kasha kamshi, irin wannan kwalliya haka, sai kace za aje gasar kyau,, lallai aunty mu ta iya shirya ka"" suka kwashe da dariya" dai dai lokacin nawwara tafito. duk suka zuba mata idanuwa Mimi ce takara sa ta rungumeta tare da cewa barka da safiya auntyn mu, yauwa Mimi iyayen surutu, tundaga daki nakejin muryanki kina ma angona tsiya. khadija tace a lallai nawwara har kin samu bakin magana, zainab tace aunty khady ba dole ba, zama da masoyi dadine dashi fa,, Mimi tace hakane kam, suka bushe da dariya. Mimi tace ga breakfast dinku nan Mami tace mukawo muku, nawwar yace AI yanxu nake son dama muje wajan mamin don taga amaryata"" ya janyota jikinci tare dacewa muje muyi breakfast, suko su khady zuba musu ido sukayi cikin sha'awa. bayan sun gama suka dunguma can gdan Mami tayi murnan ganin nawwara kuma rayaba da ita'. tayi musu nasihohi masu ratsa jiki, aunty saudama tayi musu. bayan wata uku dayin bikin sameeratu akayi na khadija, alokacin ne nawwara taje ganin GDA , SBD tund tayi aure bataje ba sai da bikin khadija ya tashi, tare da sulaiman da Mimi sukaje, shi sulaiman zuwanshi da biyu yayi SBD zainab kanwar nawwara. lokacin nawwara da cikin wata biyu ajikinta, iyayenta sunyi murnan ganinta, don takara kyau alamun hankalinta akwance,, SBD nawwar na tattalinta suna gurje soyayya, daidai da girkima shi yake mata, ga Mimi kuma nataya ta wasu ayyukan SBD gata da akanuna mata. bayan wasu yan watanni nawwara ta haifo santalelen danta mai kama da babanshi, kar kuso kuga murna wajen Mami kamar zata cinye yaron, anti suna Inda yaro yaci suna Ahmad ana kiranshi da (usaimin). suna samun kula, bayan sunyi arba'in ne akayi bikin Mimi da dan ustaz Yusuf da anso a hada dana sulaiman waje daya, ska fasa SBD hidiman zayyi yawa. nawwara ta sake yin JAM na state uni dake Kaduna wato Kasu inda zata karanta Islamic studies, cikin sauki tasamu masugunni a Kasu, tafara karatun ta cikin sa'a, arzikin mijinta bunkasa take. usaimin awajen Mami yake zama SBD makarantar nawwara, anxo anyi bikin zainab da sulaiman , abun gwanin ban sha'awa . akwana atashi bawuya wajan Allah shekaran auren su nawwar 6, yau weekend duk suna gd babu aiki tare da yaran su guda biyu Ahmad (usaimin) sai maimuntu (mubina) , duk suna zaune afalo ana hira, nawwara ta kwanta acinyar nawwar, yayin da shi kuma yana mata susa akai, mubina tace, daddyna kana cirewa mummy kwarkwata ne dukkan su suka kwashe da dariya, nawwara tace, mubina a ina kika San kwarkwata? tace mummy awajen Hjy kaka wai nace ma Hjy kaka tabani dan kwalinta na daura sai tace min baza ta bani ba wai ina da kwarkwata a gashine, ta karashe maganan cikin shagwaban kuka. usaimin ya kwashe da dariya, yace hakane mana kina dashi, nan da nan tafara ihun kuka tana daddy kaga yaya usaimin ko, ya turekan nawwara y janyo mubina jikin shi yana lallashinta, bawwara tace lallai kam SBD wannan sha gwababbiyar zaka tureni bara ka gani, aiko tadare jikinshi, shima usaimin ya taho duk suka zauna jikin nawwara suka rungumeshi suna dariya yace I love you all. TAMMAT ANAN NA KAWO KARSHEN LITTAFIN ALJANA CE KO MUTUM, BADON NASO TSAYAWA ANAN BA, SBD SUNGULLO LINE SUKA SHIGE MIN GABA. *sannan* *INA* *baran* *Addu'an* *Ku* *Banda* *lafiya*. *godiya* *ga** *dukkan* *masoyana* *na* *nesa* da *kusa* *Allah* *yabar* *zumunci*. bazan manta da kuba GRP na nawa,don kunfi kowa son novel dina *ALL* *DOSTIS* *of* *NUSFULLHAYAT* da sauran grps din. *ban* *manta* *daku* *ba* *masoyana* Ummee adnan Hansai zozo hafsat rano al'eeman ummu yahaya nafee anker fati azland m jabo qurratul ayni ummu abrar jamila muhm Ali ayusha ilyasu Sheedat autar hjya *Ashnurpyar* da dukkan writers. ban mance dake ba *Ummee* *adnan* adalilinki wannan novel ya karbo, *jinjina* ta *bangirma* *Allah* ya *baki* *lafiya* *ya* *raya* su *dnan* sai kinyi ko ba poster *Ummee* *dnan*. wannan novel nawa ke na mallaka mawa *my* *shona* *shahrazad* *Allah* ya *barmin* *ke* my *shazee* soyayya cikin kwando *shahrazad*, *pyar* *hogaya* *dil* *se* *muhabbat* *se* *ana* *ashiq* *bijunun* *shahrazad* *ana* *hubbiq* ya *habibti* *lahazatil* *kalbi* *minal* *hubb* *shahrazad*. LITTATTAFEN NUSNIM *adalilin* *Sonya* *hanta* da *jini* *Kuncin* *rayuwa* *labarin* *ni'imah* *kutausaya* *min* *Aljana* *ce* *ko* *mutum*. sai kuma mai zuwa *SON* *MA* *SON* *WANI* TAKU A KULLUM UMMU RUMAN NUSNIM *BISSALAM* asa, da tsiwa yaqara harzuqashi Hannunsa ya d'aga, bata tsammaniba taji sauqar mari afiskarta Dasauri ta dafe wajen da hannunta, ta miqe tsaye tace Allah ya isa banyafe maka ba, kuma qarya nayi ba tabarmar kunyan kazo nad'ewa inba haka a ina nakai qarar ka, saika fad'a ai Cikin masifa yace dan ubanki ke har kin isa kitsareni, wlh am warning u this is the first n last da wani zaizo gidannan kiyi maganata dashi, idan kuma kinki jikinki zai fad'a maki Tace Sannu ubana, inba ka kasheniba wlh baka cika sunanka ba, nadauka da dare kake shaye2n, ashe harda ranama yi kake Aiko daya wani fincikota sai data fad'o jikinsa, lokaci guda yaji wani irin shork ajikinsa wane wuta ce takamashi ai baisan sanda ya hankad'ata ta bugu da kujeraba Wani irin ihuu ta kwala lokacin da kanta ya bugu amma ko ajikinsa saima qoqarin cire belt d'insa dayake yana cewa bari kiga aikin yan shaye2 Tinda bakida kunya sai naga qarshen rashin kunya.... ✍🏻Faty Mmn Faty [10:40PM, 8/6/2017] ‪+234 703 448 8635‬: 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye 🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty July, 2017 1⃣7⃣ Fauziyyah data riqe kanta dan azaban datakeji aiko sai takuma jin yayyafin bulala ta ko ina Dukanta yake tsakaninsa da Allah, bako tausayi, haka yake zabga mata belt d'inanan Ga zafin da kanta kamata ga kuma belt dayake zuba mata amma hakan baisa bakinta ya mutu ba Allah ya isa ta jamasa yafi cikin kwando, tana kuka tana cewa wlh sai Allah yamun sakayya tinda ban maka komaiba, mugu azzalumi kawai Sai daya tabbatar ta daku kafin ya kyaleta Sai huci yake kamar wani kumurci, hannunsa ya nuna ta dashi yace kibud'e kunnenki da kyau kijini Nafarko kisani bani bake, bana sonki haka bana qaunar ganinki bare zama tare dake Sabida haka kitabbatar kin kiyaye abinda zan fad'a maki, kinganninan bana qazanta haka bani qaunarsa Kitabbatar dik randa naga datti agiddannan wlh sai jikinki ya gaya maki, sannan dik abinda kike idan kinji qarar motana kafin nashigo kisan Inda dare yamaki sai nafita, kada ki kuskura nadawo ina zaune afalo kifito, ko ahanya bana qaunar kallon fiskan kinnan mai dauke da shegun idanuwa kamar na mayu Idan kika kuskura kika aikata 1 acikin wad'annan zakisha mamaki dan wannan flashing na maki Banziya jaka, yar qauye kawai, yana kaiwa nan ya wuce ta ya haura sama abinshi Wani kukan takaici da baqin ciki ta fashe dashi, ga kanta sai zafi yake mata, illahirin jikinta rad'ad'i yake mata dan ba dukan wasa yamataba Wani tsanarsa ce ya sake shiga zuciyarta, afili tace sai dai ka kasheni wlh ko 1 bazan aikataba kuma wlh ka daki bashi daganan zuwa shekara 100 sai na maka abinda zan qunta tamaka fiye da abinda kamun Da kyar ta miqe tahaura b'angarenta, toilet ta shiga ta had'a ruwa mai zafi sannan tayi wanka Dik jikinta yayi pink shatin duka abinka da farin mutum Wata sabuwar yunwa taji ta taso mata, kitchen ta wuce ta dakko sauran abincinta nasafe tafara ci Door bell taji ya karad'e ko ina, hijab dinta ta jawo tasaka sannan ta fito Jikin main Door din tazo ta tsaya tana kallon wane ne yazo Ganin wata matashiyar mace ce dauke da basket na abinci a hannunta yasa ta bude mata Sannu da zuwa, tace mata Bayan tashigo Yawwa, ina yini tacema Fauziyyah, lfy lau ya gida, ta amsa mata Lfy lau, hajiya ce tace nakawo maki abinci Karban basket din tayi tace nagode sosai, ki qaraso mana Asabe mai aikin momcy tace aa driver yana jirana zan koma Toh kigaida momcy nagode Side nata ta koma, Tattara wancan abincin tayi ta zuba wadda aka kawo mata taci abinta D'aki ta koma ta kwanta dan kanta ciwo yake mata har yafara daminta ******* Papa kuwa yana haurawa d'akinsa ya wuce, kayan jikinsa ya rage sannan ya shige toilet, ruwa ya sakanma kansa ko zaiji sanyi azuciyarsa amma ina, maganganunta su suke masa yawo akansa, shaye2 harda ranama yi kake shine abinda ya ke daminsa Inba rainiba ba wanda ya tab'a furta masa wannan kalmar iya tsawon rayuwarsa, sai qaramar yarinya lalle zan d'au mataki akanta Next time da kud'i aka bata bazata kuma cakamun abinda taga damaba Fitowa yayi d'aure da towel aqugunsa, sai anan ya tuna ashe ko breakfast baiyiba Tsaki ya kuma ja, sabida wata yar qauye Komai nasa ya jagule Wayarsa yajawo ganin time ya qure ya sake jan wani tsakin Ajiye wayar yayi, ya dauko white jallabiyarsa yasaka, tada sallah yayi, yana cikin sallah aka fara kiran Wayarsa Sai bayan ya idar, yana dubawa yaga TJ ne ya kirashi Kiransa ya fara bada jimawa ba ya picking, hello ango kasha mai abinda ya fada kenan ya daga wayar Tsuke fiska yayi kamar yana ganinsa, yace wlh TJ inajin kunyanka fa TJ yace kadaina jin kunyar tawa dan namaka kirari sai kawani fara dojewa bayan nasan iyanzu Komai normal Papa yace to tinda ba maganar arziqi yasa kanemeniba sai anjima Haba dakata mana mutumin yafad'a cikin sauri, me yayi zafi haba wasanefa Toh inajinka meke happening, TJ yace laufa daman inason leqowa gidane kasan tin rabibin biki rabona da amarya Aiki nad'auma wani abu mai muhimmancine to waya riqeka yanzuma TJ yace idan kana gida zuwa 4 haka zan shigo, papa yace inanan bana nan mene damuwarka tinda ba wajena zakazo ba Eh amma dai ai inason nasameka, dan akwai error fa, error name? Yatambayesa Wlh surry ta dameni da waya wai atafir saina kawota gidanki tinda baka daukan call nata Papa yace aida ka kawota, naci uwarta tukun gobe ko ahanya taganni bata nuna tasanniba, niba irin yan iskanta bane ba TJ yace aa kam taya zan kawota gidan matar aure, idan kun had'u dai ka d'aye mata amma ba agidankaba Toh naji sai zuwa jimawa zamu had'u ko kanada wani eh umm Sheqewa sukayi da dariya gaba d'ayansu TJ yace aa wlh kawai dai yau ina gida dan full house muke Ok nikam yanzuma fita zanyi, ina da wajen zuwa Toh ba yawaa, gobe insha Allah zan shigo Ok, sai munhad'u nan sukayi sallama Fitowa yayi tsaf cikin shirinsa na blue jins n red shirt, yayi kyau abinsa Canza mota yayi, yadau farar Rio ya fice, kai tsaye banila resturant ya shiga nan yaci abincinsa sannan ya wuce ya had'o wine nasa cotton cotton Bashi yadawo gida ba sai gabda magriba Yana shigowa side nasa ya shiga dasu, wasu yasa a fridge wasu ya ajiyesu haka, sai bayan ishai sannan yaci kazar daya saka aka sayo masa nan ya zauna yana kallon news yana shan wine nasa Sai wajen 12 sannan ya kwanta Washegari tun safe Fauziyyah bata fito ba sai 11 nanma kawo mata abinci akayi, nan tace Wa Asabe tafadawa momcy kada a turo mata na rana wannan ma ya isheta Ba ita ta fitoba sai wajen pass 4, nanma kitchen take da niyyar shiga taga ko akwai kayan tea dan tanason shan tea yau Saqqowa tayi qasa, tana zuwa tsakiyar falo tajiyo kamar muryan papa, matsawa tayi kusada falonsa sai taji kuma kamar shida wasu ne, ahankali ta matso ta leqa sai taganshi shida TJ dama wani wanda batasanshiba amma sunje wajen kamun aurenta da TJ Shiru tayi tana tunanin ta wuce kota koma, nan take tayi wani murmushi tace yau saina nuna maka tsiyar dan qauye Sad'af2 ta juya, d'aki takoma ta sake kwalliya, wata doguwar riga fitedgown tasaka ta shadda, dark ash, anmata aikin surfani daga sama har qasa Rigan tad'an kamata, idan kaganta tayi kyau sai dai kamar yar baby dan Fauziyyah ba jiki ko kadan ga girjinnan kamar yayan goruba, yarinta zalla kawai daka ganta zaka gani dan babu wani abu mai auki ajikinta Daurin dan kwalinnan yamata kyau dan Fauziyyah kyakykyawace sosai, fitowa tayi zuciyarta sai bugawa take, tana zuwa bakin steps sai data dai dai ta natsuwarta sannan tafara saqqowa dasdas kake jin qarar takalmin ta Falon papa ta wuce direct, tana yaye curtain d'in da sallama ta shiga dik suka juyo TJ da kb suka amsa sallaman Inda papa ya tsaya ganin mai yakawo yarinyannan yana tare da baqi Bayan dik kashedin daya mata Gunsa yaga ta nufo kadan2, idanu ya zuba mata dan ganin iyaka gudun ruwanta........ ✍🏻Faty Mmn Faty [10:40PM, 8/6/2017] ‪+234 703 448 8635‬: 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye 🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty July, 2017 *This page goes to my swt sis Aunty Hadiza, thanks 4 ur luv n support 😘😍* 1⃣8⃣ Cikin taku mai natsuwa harta iso wajen dayake zaune Kan hannun kujeran dayake ta zauna, hannayenta dik biyu tasa tasaqalo wuyansa Fiskanta ta kwanta jikin nasa, cikin wata murya dabai san tana dashiba mai tattare da shagwab'a tace Dear, ashe sun qaraso nikam inacan sai yanzun nagama Papa nan yayi mutuwar zaune, abu uku su suka hanashi magana Nafarko wannan shegen shork dayaji jiya lokacin da ta tab'a jikinsa, dik da yana huld'a da mata amma bai tab'a jin irin wannan abinba dan ya tab'a mace, amma karo na biyu kenan da Jikinsu ya had'u amma sai yaji wannan abin Na biyu kuma wani fitinannen qamshi dake fita daga dikkannin jikinta su suka kashe masa jiki Na uku shine haushi da baqin ciki yarfashi da tayi agaban su TJ, shi TJ baima damesa kamar kb ba Sanin bazai yi maganaba yasa ta juyo tana kallon su kb, da murmushi afiskanta tace sannunku da malam TJ, wlh kunzo ina ciki TJ da mamakin ashe shi Ameen yake, zagayawa soyayya suke sha da amarya fal zuciyarsa amma sai ya share Yace haba bakomai ai amarya bakya laifi ko da kinkashe d'an masu gida Dariya tayi ta sake maqale papa, tana kallon idanunsa, cikin shagwab'a tace wai haka ne swt Wani qululun baqin cikine ya sashi lumshe idanunsa yana tunanin mai zaima yarinyar nan ya huce abinda tamasa Hakan da yayi sai ya bada kamar amsa mata yayi TJ azuciyarsa yace shere Dr ashe kawai harka ya bud'e sabuwa yasamu yar shila yana morewa, sai wani pretending yake Ina yini tace da kb, lfy lau amarya ya amarci? Wani shuumin murmushi tayi wadda yasake qawata face nata tace sai dai katambayi swt TJ yace tabbas Ameen keda wannan amasan, aikaga yayi shiru baiko magana TJ yasake cewa wannan abokinmune yana nuna kb sunansa Malam kb ko tayi saurin fad'i Au kinsan sunansama ashe TJ ya fad'a Dear yacemun zakuzo tareda kb ko namanta sunan, alhalin lokacin data lab'e taga suwayene a lokacin taji TJ ya kira sunansa yace kb Nan TJ yasake tabbatar da lalle shi Alamin yake rainawa hankali Miqewa tayi barin kawo maku ruwa, bata jira amsan suba ta wuce abinta Kitchen ta shiga, tana shiga ta dafe qirji tace hmm lalle yau nayi jarumta irin wannan rashin kunyan bantab'a yin irintaba Wani dariya kuma tayi dan tasan tabbas yau ta qonawa ya Alamin zuciya Cikin sauri takama bud'e2 dan taga mene damene akwai dan wannan shine shiganta na farko Aiko nan taga ba abinda babu, freezer ma shaqare yake da nama, kifi, kaji Wata qofa tagani, tana bud'ewa taga store ne nanma ba abinda babu, dankali, doya, kwai ma ga wasu banda wadda tagani acikin fridge Aifa nan tafara jido tana kaiwa falon ta tana ajiyewa, sai da ta d'ebi dik abinda take buqata sannan ta d'auki tire ta cikashi da drinks kala daban2, cups ta wanke sannan ta d'auko ta nufi falon papa Yanda ta barshi haka tadawo tasamesa fiskarnan babu annuri Ko d'agowa baiyiba baran ya kalleta, lokacin data fita kamar ya bita amma sai yafasa tinda ai zasu tafi su barsu agidan Kuma idan har ya bita, tabbas wani tunani nadaban zasu sake tinda tagama zubarmasa da class agaban kb, shi bayajin ta TJ ma Zubawa tayi ta ajiye masu tace bismilla kusha ruwa Kb yace godia muke amarya thanks so much Bakomai ta fad'a, wajen papa ta koma ta zauna, sai dataga sunsha ruwa sannan Ta matso jikin papa tace swt nikam barin shiga ciki, na daura mana dinner Maida kallonta wajen su TJ tayi sannan tace toh nikam barin shiga ciki Saina fito TJ yace mukam ma tfy zamuyi Tace haba dai bazaku tsaya kuci abinciba TJ yace inaa kinaga yadda ango ya had'e fiska alamun mumtakuresa, gara mu wuce tin bai koramuba Suka kashe hannu shida kb, kb yace gaskiya kam Mungode madam sai wani lokaci kawai Tace to mungode Allah yasaka ya bada ladan ziyara Dik suka amsa da amin wani hot kiss ta danna masa a chicks dinsa tace Dear sai ka shigo Cikin sauri ta wuce kada cafkota, aiko tana zuwa bakin steps da gudu ta haura ta nufi side d'inta Tana shiga ta saka key, ta kulle dik wata maqata najikin qofar sannan ta zauna tana Maida numfashi Papa kuwa jiyake kamar ya fashe da kuka dan baqin cikin abinda yarinyar nan tamasa TJ ne yace ango mu zamu wuce sai munhad'u kawai Da kyar ya iya furta ok man sai munhad'u, thanks kb sai n shigo TJ ne ya ce wai mutumin har kafara kawo wutane daga zama akusa dakai sai idanu su canza Kb yace ai kasan yanzu tahau network, suka kashe hannu suna dariya Papa yace wlh zanci ubanku, cikin fushi yayi maganar TJ ya matso saitin kunnensa yace ayi dai ahankali kasan yarinyace, dannaga kadau saiti tin baaje ko inava, dftn yanzu kafahimci abinda nake fad'a maka abaya Na kaiwa nan ya wuce, suna fita shikuma yayi hanyar side d'in Fauziyyah Tsabar bacin rai har baya gani sosai, sai dai me yana zuwa yaji qofa gam akulle Wani mahaukacin bugu yake ma qofar Cikin tsiwa tace wai wayene kam Kibud'e qofar, maganane ta fad'a irin ko inkula amma azahiri atsorace take Open the door I Said, wlh don't let me repeat my self To wai na bud'e akan me, ko d'akinkane Ok, toh wlh tinda haka kikace yau saina karyaki agidannan, ina nizaki walaqanta, zan nuna maki iyakarki Tace ah haba kaji haushine, toh idan ka kamani kada kabarni d rai mtss taja dogon tsaki Ina fad'a maki Kibud'e qofannan tin dawuri fa Wai kaikam wani irin qauyanci ne yake daminki Kutt, nikike cema dan qauye ni, ni Toh inba qauyanciba har kadage na bud'e qofa baicin kana iqirarin saika karyani, aiko inkaga qofannan a bud'e sai dai inkai ka bud'e dan nikam bazan bud'eba gara kadaina b'atama kanka lokaci Tunawa yayi Da ko wacce qofa tana da extra key, d'akinsa ya wuce ya bud'e drawer dan ya d'auko extra keys d'in dan yau saiya koya mata hankali........... ✍🏻Faty Mmn Faty [10:40PM, 8/6/2017] ‪+234 703 448 8635‬: 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye 🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty July, 2017 *Wannan shafin nakune masoyan Budurwar Qauye (Fauziyyah), Mmn Faty ta gaisheku all 😍😘* 1⃣9⃣ Bincike yake amma wasa gaske ko abu mai kamada makulli babu, bai kuma ganiba Dik wata drawer dake cikin d'akin sai daya bincika but ba Komai sai takardu da wasu abubuwansa Zama yayi abakin bed, ya dafe kansa da hannu biyu yana tunanin ina keys d'inanan kam suka shiga Hannunsa ya dunqula ya naushi d'ayan hannunsa, da qarfi yace dmm it! Cos ya tuna lokacin da Daddy ya basa keys d'in gidan tare da extra din yace shi baison extra dan baiga mai zai dasuba Yanzun ga ranan su, safa da marwa kawai yake acikin d'akin yarasa abinyi Tinani yake idan yabar yarinyan nan taci bulus kenan, n wayasan abinda zata masa agaba tinda ya fahimci kunne qashi ke greta ****** Jin shiru2 har fiye da 20mins batasake jin motsinsa ba, hakan ya tabbatar mata ya bar wajen Hakan yasa hankalinta ya d'an kwanta, bedroom nata ta shige ta canza kaya, wata simple gown tasaka marar nauyi Falo ta dawo tafara kwashe kayan data zuba, tana kaiwa kitchen Sai data ajiye Komai a muhallinsa sannan, ta daura abinci indomie da kwai ta dafa, bata ko juyeba ta wuce daki dan anata kiran sallah amasallaci Saidata idar da sallah, kafin ta dakko abincinta had'i da gwangwanin sidene Zama tayi hankali kwance taci tayi nak abinta, ta kora da juice Wajen kayan kallo taje dan tagaji da zaman shiru, tana kunna socket Komai ya kawo dama ashe an saita Komai Kallo ta zauna tanayi tama manta da wani wai ya Alamin Sai da 8 tayi sannan taje tayi sallan ishai, daga tasake dawowa falo abinta sai wajen 11 sannan takashe Komai tayi d'aki dan bacci takeji sosai Asuba ta gari matar Dr ****** Ganin baya da mafi ta hakan yasa ya haqura amma da niyyar dik sanda suka had'u sai ya hukun tata Bathroom ya shige ya watsa ruwa, sannan ya fito Farar rigace mai gajeren hannu yasaka ta shan iska, sai farin wando 3quater Cikin jin kai ya fito sai wani b'ata rai yake kamar yaga abin kyama Farfajiyan gidan ya fito yana kiran Abdu mai masa hidima Cikin sauri ya qaraso, tsugunawa yayi yace gani oga Cikin isa ya saka hannunsa a aljihu, Kudi kawai ya miqo masa, kasayo maku abinci kamar kullum take away hudu naku Sai kasayomun rosted fish, da roba 1 na shaka Toh oga, ya amshi kudin sannan ya wuce, haka ya tako ya dawo ciki Kwanciya yayi afalo yana jiran dawowar Abdu, tsulum ya tashi daga kwancen ya zauna sabida wannan mayataccen qamshin jikin yarinyarnan ya damesa Abin mamaki hakan bai masaba nanma bai daina jiba, mtss yaja tsaki ya miqe Falonsa ya shiga, tab nasa ya d'auka dan awajen ya batta tsabar b'acin rai baima tunaba Nanma dai falon wannan qamshin yake, ahankali yace kin cuceni amma shiru yayi yana cizan lips nasa Waje ya fito ya zauna akan d'aya daga cikin kujerun da aka jera qarqashin wata rumfa mai domin hutawa Chat yakeyi hankali kwance amma wannan qamshin yanajinsa kuma yarasa daga ina ne Basarwa yayi yace May b ma hancinane tinda baso nakeba Yana nan zaune Abdu ya dawo, sai daya tsugunna yace gashi yallab'ai Ko d'ago da kansa baiba, ya masa nuni da hannu alamun ya ajiye akan table din gabansa Cikin girmamawa Abdu ya ajiye, sannan yace atashi lfy oga sannan ya wuce Ko amsashi baiba, amma inda sabo yasaba da halin ogansa, dan indai jin kaine da yarfa mutane to papa no 1 ne, shiyasa ko a office ma special mutane yake gani dan shi consultant ne Sai da aka fara kiran sallah sannan ya miqe ya shige ciki, direct side nasa ya nufa baiko kalli side na Fauziyyah ba dan yasan bata bud'eba Alwala yayi, sannan yayi sallah, fitowa falo yayi ya kunna sport tv yana kallo, sai dai me wannan qamshi yakumaji ya damesa Oh Allah, wannan wani irin damuwane kam, shidai yasan kullum dakinsa a kulle ne baran yace ko kawo masa turaren tayi, n yasan batama tab'a shigo masa d'akiba How comes to haka ya faru, sharewa yayi kawai ya faracin kifinsa, sai daya gama sannan yaje ya wanko hannunsa, ya sunkuya yana brush sai yaji kamar awuyansane qamshin Aiko tabbas ajikinsane, nan ya tuna lokacin data riqesa ne wato ta shafa masa Cire kayan jikinsa yayi ya zuba su a cikin laundry basket Cika jacuzzi yayi da ruwa, ya shiga yaringa dirzan jikinsa kamar mai canza fata Yakai 30mins kafin ya fito, Farar singlet da white boxer yasaka, kwanciiya yayi akan 3sitter, remote ya d'auka yana canza channel Amma kuma dik irin yadda yasake wanka ya canza kaya baidaina jin wannan qamshinba Rai b'ace ya jawo kwalbar wine nasa, yafara sha , amma tsabar ransa ajagule ne yasa ko dad'inta baiji Tunani yake waikam mene ne yasa, da jikin yarinyannan ya tab'a sa sai yaji wani irin shork ajikinsa, n gawani mayataccen qamshi da jikinta keyi harta shafa masa Bawai qamshin badad'i bane kawai baison dik wani abu daya shafetane Lumshe idanuwansa yayi yana tunanin tin randa ya fara ganinta, har zuwa yau da tamasa abinda ya kasa mantawa Tsaki yaja ahankali ya furta pagal, gyara kwanciyarsa yayi kawai yana shaqan wannan qamshin lokaci guda yaji wani kasala ya lullub'eshi Ga wani baqon abu dayakeji, ya kuma kasa gane kome ne ne, kawai abinda yasani yana buqatar mace akusa dashi Wannan shine rana ta farko a rayuwarsa dayaji shaawan kusantar mace kuma baisan daliliba Yana nan kwance ahaka har bacci yayi gaba dashi, ranan ko abun sabon baishaba dan jiyayi Komai ya fice masa arai ***** Wasa gaske yau kwanan Fauziyyah biyu bata fitoba Hakan yasa basu had'uba, shima baikuma bi takanta ba Idan gari ya waye yayi wanka ya fice gidansa dake sokoto road, yamma nayi ya dawo gida, bai yarda su had'u da TJ Fauziyyah kuwa tinda gano tsayuwa asaman barandan falon ta nan take ganin dik wani abinda ake awaje Yanzun tana sanin fitansa da dawowarsa, dataga ya fita zata sakko tayi abinda take sonyi ta koma abinta Yau satinsu guda da aure, kuma tun jiya takejin alamun kamar period dinta zaizo Damuwarta 1 yadda yake wahalar da ita shiyasa ta bud'e qofarta tace ko kasheni zaiyi gara nabar qofarnan a bud'e Falon taga yayi qura, tace barin gyara falon nan ko shara bai tab'a ganiba Wani wando d'an qarami wadda ko guiwanta bai kaiba da yar qaramar riga tasaka Mopper da tsintsiya ta d'auko tafara gyara wajen Sai taji cikinta ya murd'e nan ta durqusa awajen Tayi2 ta miqe amma ina fir ta gagara, ga wani irin murd'ewa da mararta takeyi Qanqame stick d'in Mopper na hannunta tasake dan azaban datakeji Papa kuwa yau dawuri ya dawo gida dan akwai inda zashi Yana shigowa falo ya hangota adurqushe da Mopper a hannunta Wani Murmushin mugunta yayi yace idan kere na yawo zabo na yawo wataran zasu gamu Kingama boyen naki, yau sai kin gane shayi ruwane Nufota yayi yana tunanin wani kalan mugunta zai mata......... ✍🏻Faty Mmn Faty [10:40PM, 8/6/2017] ‪+234 703 448 8635‬: 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye 🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty July, 2017 2⃣0⃣ Tsayauwa yayi akanta, cikin gadara da isa yace kingama boyen naki marar kunyan qarya Tana jinsa amma bazata iya masa maganaba, dan wani irin ciwo takeji tin daga kafafunta har kanta Ganin bata kulashiba, yace oh nizaki rainama hankali kinaji ina maki magana bazaki amsaba Nanma bata kulashiba, azuciye ya fincikota, aiko datasa wata uwar qara , take ta sanqame awajen Yace waw that's good, lalle kin iya dramer to gara ki tashi inba haka ba funishment naki ninkuwa zaiyi Dan atunaninsa likimo tamasa Hannuunta ya damqe cikin mugunta yace zaki gane bakida wayyo... Maganarsa ce ta maqale jin hannun asake Tsuramata idanu yayi Da kyau, nanfa abin ya bashi tsoro dan inba kuskure yayi ba kamar bata numfashi Subhanallah shine abinda ya furta, a rud'e yace ke, ke tashi niba abinda zan maki Nan ya kama jijiyar hannunta nan ya fahimci suma tayi Ai baisan sanda ya saka hannunsa biyu ya d'agota cid'ak ya nufi d'akinta Cikin sauri ya kwantar da ita akan bed ya dawo kitchen, ruwa mai sanyi ya dauka sannan ya dawo dakin Yanda ya barta amiqe haka yadawo ya sameta Balle murfin bottle d'in yayi ya yayyafa mata ruwan, amma bako alamun ruwan ya shige ta Ya salam shine abinda ya furta, tsoronsa kada wani abu ya sameta yasan Daddy bazai yafe masaba Hankalinta ya matuqar tashi sosai, sauran ruwan ya juye mata akanta nan taja wani dogon numfashi Alhamdulillah shine abinda ya furta, amma kuma sai yaga sai murd'e2 da shure2 takeyi, tana kuma riqe da cikinta Matsowa yayi kusa da ita cikin husky voice nasa yace meye haka kikeyi, ko wani abu na daminki ne Sai anan ta bud'e idanunta ahankali jin muryarsa, nan tafahimci ad'aki take, mai makon ta amsa masa sai ma hawaye dakebin fiskanta Cikin takaici yace ana maki magana bazaki amsaba sai kifara mun kuka, idan bazaki mun maganaba ke kika sani ni tafiyata zanyi Ganin sai wani miqewa take hannunta akan mararta kuma batai maganaba sai uban hawaye dake ambaliya afiskanta Sanin taurin kanta, zaiyi wuya tayi magana inhar ahakane, zuciyarsa ta bashi shawara ya tambayeta cikin sigan lallashi ko zata fad'i damuwanta dan tabbas akwai abinda ke daminta Kada wani abu yasami yar mutane Cikin sigan lallashi, ya tausasa murya, umm pls talk to me mana, mene ke damunki, ina ke maki ciwo? Da kyar ta iya cewa cikina, qafana kaina sai takuma fashewa da kuka Is ok, ya isa haka umm, kiyi shiru zai bari, shiru yayi yana nazarin ta ahankali yace dama yana maki haka ne ko wannan time dinne yamaki haka Girgiza kanta tayi, yace yana maki kenan Nanma nodding kanta tasake masa Ok to barin muga sai nasamo maki magani ko, hannunsa yasa aqasan marar ta yadan danna, dayan gefen yasake dannanwa Nan tasa qara, is ok nabari dazafi ko Barin zo, kiyi haquri yanzun dan dawo ko Cikin sauri ya fice, da mugun gudu ya figi motarsa, wani babban phermacy ya shiga nan ya had'o mata magani da allurai Har yazo zai fita, sai kuma ya dawo baya yana tunanin yasaya mata pad Wata zuciya tace masa, ba girmanka bane ka tsaya sayan pad, pad d'inma ma wata qaramar yarinya Juyawa yayi ya sayi dika roll din dan yanzu baida lokacin tunani sabida halin daya barta Dasauri ya shiga mota, ya nufi gida, cikin sauri ya zari ledan maganin ya shiga cikin gida Direct d'akinta ya nufa, agalabaice yasameta har ta fita ahankalinta Baiwata wataba yaja ruwan allura, guda biyu ya mata daya na bacci daya na ciwon ciki Ahankali ciwon ya fara sauqa, har tadawo hayyacinta Ganin ta tsura masa idanu tana kallonsa, yace kinsamu sauqi, daga kanta tayi Yace ok to ga pad nan ki tashi kishirya jikinki ko Yunquri tayi zata tashi amma sai takasa dan dik jikinta ciwo yake mata Kare mata kallo yake sai anan ya lura d kayan jikinta, wani tunanine yazo masa, nan yayi saurin kawardashi Hannunsa ya miqo mata yace riqeni kitashi dan baqaramin tausayi ta basaba Daganinta ba tambaya, taji jiki lokaci 1 dik tayi wani iri Ganin zata bata masa tym kawai ya d'agota, kiris ya hana ya saketa ta fad'i sabida wani shork da yaji tin daga yatsan qafarsa har kansa Cikin sauri ya matseta ajikinsa dan kada ta fad'i, itama sabida batada qarfi sai takuma lafewa ajikinsa Hanyar toilet ya nufa, ahankali tace zan dau abu acan ta nuna sif da hannunta Baiyi maganaba sai juyawa da yayi, budewa tayi cikin kunya ta dauki pants Shima baice komaiba ya wuce toilet da ita, ajiyeta yayi yace ina zuwa Daki ya dawo sannan ya miqo mata pad din,oya kishirya kizo kisha magani yace da ita Ganin idanunta sai lumshewa suke alamun bacci yasa yadanja wani siririn tsaki, taimaka mata yayi tayi wanka, sannan ya fice yana cewa 3mins nabaki kishirya Yana tsaye abakin toilet yaji alamun bude qofar, tana bud'ewa kamar anhankad'o ta, ta taho zata fad'i Cikin sauri ya riqota ta fad'o jikinsa, lumshe idanunsa yayi kafin ya dagota har kan bed ya kwantar da ita Nan ya lura ashema bacci tayi, girgiza kansa kawai yayi yace rikicecceciya daga allura sai bacci ashema jininki bayada qarfi, rikici ne kawai Qare mata kallo yake daga ita sai towel iyaka cinyanta, dik ya jiqe da ruwan jikinta Ahankali ya miqe ya nufi sif dinta inda ta bude shima nan ya bude cikin saa yaga sleeping dress dinta Wata coffee doguwar riga marar nauyi, ya dakko yadawo, warware towel din yayi zai samata rigan nan idanunsa suka sauqa akan qirjinta dasuke atsaye cak Qura idanu yayi dikda qanqantarsu amma fa sai yaga sun burgeshi Baisan lokacin daya kai hannunsa kaiba wani yanayi yaji sabo da baisan yadda zai fassaraba Nan take idanuwansa suka canja launi, jikinsa ya mutu, wani abu yaji yana fizgarsa, lokaci guda yakai bakinsa Nanfa yafara birkicewa, ga lallausan fatarta data sha gyara, ga wannan fitannanen qamshi dake fita daga jikinta, su suka qara shagaltar dashi har yamanta wacece akusa dashi Lokaci guda ya matsa kamar an tsunkuleshi, da kyar ya saka mata rigar ya miqe Ahankali yake takawa sabida illahirin jikinsa amace yake, wani kasala yaji ya saqqo masa da baisan dalili ba ga wani irin feeling dake taso masa ahaka ya fice ya nufi d'akinsa....... ✍🏻Faty Mmn Faty [10:40PM, 8/6/2017] ‪+234 703 448 8635‬: 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye 🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty July, 2017 2⃣1⃣ Yana shiga falonsa, zama yayi akan cussion, hannunsa ya nutsa acikin lallausan gashin kansa Cikin jin haushin kansa yake magana, yanzun mene na aikata ma kaina, meyasa zanyi haka why why Wani irin zogi da zuciyarsa kemasa ga kuma wani irin mugun feeling dayake ji su suka saka idanunsa sukayi jazur kaman gauta Tunani yake yanzun shikenan yagama jama kansa raini kenan, gashin dama tagama rainashi kuma haka ya faru ya Kenan Wani abune yaji ya taso ya tokare masa qirji, ji yake inama yana da halin da zai dawo da lokaci baya da bai bari har zuciyarsa ta rinjayesaba Shiru yayi kawai dan baida mafita, amma ya yanke ma kansa kawai bazai kuma shiga inda takeba baran tamasa abinda zai sakashi ya aikata abinda zaiyi dana sani dan bazai dauki rainiba Wata zuciyar tace kawai ka rabu da ita amma kada kad'aga mata qafa dan kada ta rainaka, tinda bata cikin hankalinta batasan maiya faruba so kada ka nuna mata wani abu ya faru Sai anan yaji hankalinsa ya d'an kwanta amma bai daina jin tsanar kansaba Ya jima azaune awajen har bacci yayi gaba dashi Bayan yayi sallar magriba ya sauqo down stairs, kiran wayar abdu yayi yace ya shigo ya aikesa Dan yau baya cikin mood mai dad'i shiyasa ko son fita baiyi Kud'in abincinsu ya bashi as usual, harya juya zai fice sai ya tuna da waccar yarinyan dake kwance Kuma ga sauran alluranta da baa mata ba, ya kamata sai taci abinci da amaata Tsaki yadanyi ganin tazame masa damuwa, kamar baiso yace Abdu Dawowa yayi cikin sauri gani oga, kudi ya sake miqo masa ga wannan kabiya ta bauchi club ka karbo gas meat da kaza Karb'a yayi yace to oga sannan ya fice Sai da yayi sallan ishai ya danci wani dan gaba 1 bai shaawan Komai sannan ya fara tunanin yazai da waccar yarinyan ya mata nocking ne ya wurga mata abincin ita ta sani Maganintafa wata zuciyar ta tambayesa, tsaki yaja sannan ya dauki ledar ya fice ******** Fauziyyah kuwa tinda tafara bacci ba ita ta farkaba sai da akayi sallan ishai, ahankali tafara bud'e idanunta har ta wartsake tass Yunqurawa tayi ta tashi zaune amma sai taga wata riga ajikinta wadda bata tab'a sawaba Tinani take taya tasaka wannan rigar, shiru tayi takasa tuno Komai tace toh wazai samun kawai nina saka mana abina Yunqurawa tayi ta tashi tsaye haba nan taji cikinta yayi wani murd'awan yunwa Daurewa tayi ta nufi toilet tasake wanka, sannan ta canza kaya izuwa riga da zani na courtdivoir mai kalan ruwan zuma Dikda ba kwalliya tayiba amma tayi kyau tunani take taje tasha koda tea nema Inyaso sai tadafa indomie taci Ahankali ta riqe handle d'in qofar zata bud'e kawai taji gau an turo qofar anbige mata kai Cikin sauri ta dafe kanta tana cewa wash Allah na Qarasa shigowa yayi ya maida qofar ya rufe, ko kulata baiba ya wuce kan resting chair ya zauna, cikin had'e rai yace keh zonan Ko kulasa bataiba sabida haushi taya ya buge mutum ko Sannu bazai iya fad'a masa ba sannan ya hau wani kiran gadara Cikin d'aga murya yace keh wlh idan nafice bazankuma bi takanki tinda ciwon ajikin kine ba nawaba Turo baki tayi tana qunquni to ni sunana keh ne, ai dai bansan dani kake ba, ahaka har taqaraso gabansa Dubanta yayi yace me kikace, sarai yaji abinda tace kawai so yake yaji mai zatace agabansa zata mai2 ta ko zata doje Sake turo baki tayi, tace ni bance komaiba fa Bata ankara ba taji ya kai hannu ya buge bakin da qarfi, yace marar kunyan qarya kisake mun rashin kunya kigani sai na fasa wannan bakin wawiya kawai yaja tsuka Allah ya isa tafad'a amma acikin zuciyarta, kaman ya jita yace me kikace Ni bance wani abuba, yace ai sai dai kifad'a acikin zuciyarki Ledan hannunsa ya turo mata gashi only 10mins nabaki kici ki karb'i maganinki dan inada abinyi Tsurama Ledan idanu tayi kuma bata d'auka ba, afusace yace ke kinsan Allah ko bakiciba dole ki karbi maganin nan dan bazaki mun asarar kudi ba, gara ma kici inkinqi kece zaki wahala ni baruwana Ayatsine tajawo ledar dan kada yace ta damu, amma azahiri taji dad'i sabida dama wata baqar yunwa takeji Bud'e ledar tayi, wata gashashsheyar kaza tagani tasha gashin oven nan yawunta ya tsinke, dan Fauziyyah ba bayaba wajen kwad'ayi, sai data yago zata kai baki ya buge hannun Dago da idanunta tayi tana masa kallon meye haka Yace to kwad'ayayya kin sauqe idanun kosaina tsokanesu, ba wannan yakamata kiciba, ki bud'e d'ayan Ledan Wani haushinsamne ya kamata, haka ta bud'e dayan ledar, gas meat tagani, saima taji tafi shaawarsa sabida d'an romon dake jiki Nan tafaraci abinta hankali kwance tama manta dayana wajen Wayarsa yake dannawa, amma hankalinsa na akanta yadda yaga takecin naman tana lasan romon shiya basa dariya a zuciyarsa A zuciyarsa yace au ashe kwad'ayayyace dubeta sai kace kura Dago kanta tayi dan taji ajikinta kamar ana kallonta, suna had'a idanu ya wani tsuke fuska yace ke idan kin qoshi ne kitashi ki karbi alluranki dan inada abinyi kada kib'atamun lokaci Zaro idanu tayi tace me kace, miqewa yayi yana cewa abinda kikaji nace Cikin tsoro tace sai kanemo wadda zakama allura badai niba Sai kiyi kuma dan sisi na bazaiyi ciwon kaiba garama kitsaya if not kezaki sha wahala idan tabaci Cikin tsiwa na qarya dan tsoron gaske ya rufeta sabida aduniya ba abinda ta tsana take kuma tsoro kamar allura Tace to nina saka ka kashe kud'innaka, kawaifa ni ba alluran dazaka mun mugu kawai Yace haka kikace to banga abinda zai hana namaki alluran nan ba, ko sauraronta baiba ya d'au ledar maganin Sirinji ya d'auko ya fara jan ruwan alluran Ganin dagaske yake yasa tafara tunanin taya zata kwaci kanta dan wannan mugun ba tantama sai ya zurkud'amun wannan shegiyar alluran......... ✍🏻Faty Mmn Faty [10:40PM, 8/6/2017] ‪+234 703 448 8635‬: 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye 🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty August, 2017 *Wannan shafin nakine Sis Nussaiba ('yar mutanen Nijer), Nagode da kulawarki gareni da kuma yadda kike qaunar littafi na, Mmn Faty luvs u too 😍😘* 2⃣2⃣ Yana gama jan ruwan alluran, ya nufota gadan2 Aifa nan ido ya raina fata, cikin muryan tausayi tace dan Allah ya Alamin kayi haquri wlh tsoron allura nake, kuma ko agida baa mun Cikin tsukewar fuska yace to ainan ba gidanku bane, so kada kijama kanki dogon ciwo dan wlh sai anyi alluran Jin abinda ya fad'a kawai sai hawaye shar suka fara zuba afiskanta Ko ajikinsa saima Matsowa daya sakeyi, cikin rawar murya tace pls mana ya Alamin ka kyaleni wlh gara kamun duka akan kamun allura Yace au kinfison dukan, cikin sauri tace eh nafiso Wani Murmushin mugunta ya sakeyi yace eyyerh sai kuma abinda bakison zanmaki ba Oyah juya, ko motsawa taqiyi baran ta juya yace wlh idan na caunting 3 baki juyaba matseki zanyi da qarfi Ek(1), doo(2), yana cewa tin(3), kawai ya riqo hanneyenta, aiko da iyaka qarfinta tafara fizge2, ko sauraranta baiba ya riqe hannayenta da hannu 1, amma sai mutsu2 take Hannunta tasamu ta fizge, ta shiga jikinsa ta cukuikuyesa, gagam ta maqalesa tana cewa nika kyaleni ko dole ne tinda nace banso Wannan shegen shork d'in yaji ta ko ina yana ratsashi, gashi sai qara maqalesa take dik ta dabaibayesa da shegen qamshin jikinta mai matuqar kashe masa jiki da haifar masa da kasala Jin tana neman tayar masa da hankali yasa iya karfinsa ya b'anb'areta daga jikinsa, ya d'auketa cak ya d'aura akan gado Danneta yayi yadda ko motsi takasa, batayi auneba taji ya zurkud'a mata allura Wata uwar qara ta danna lokacin dataji shigar alluran, shiko yana gama mata ya miqe ya d'au wayarsa yayi hanyar fita Wani kuka tafashe dashi tanajin zafin wajen, sai daya kai bakin qofar fita sannan ya juyo yace ga maganin nan inkin gadama kisha inkinaso kibari damuwarki Cikin kuka tace eh d'in kuma bazanshaba mugu azzulumi, Allah ya isah banyafeba D'aga kafd'arsa yayi irin idon't care nan yayi waje abinsa Itakuma tana nan tana kukanta har bacci yayi gaba da ita ****** Papa kuwa bedroom nasa ya wuce, toilet ya shiga ya watsa ruwa, boxer kawai yasaka ya fito falo Amma dik atakure yakejinsa tinda waccar fitinanniyar yarinyan ta rugumesa dik yakejin wani yana yi, shi yarasa wannan wace irin damuwace tazamar masa Ta shigo rayuwarsa ta takuresa, ga wani yana yi datake haifar masa adik lokacin da suka kusanci juna Tabarsa ya jawo ya kunna, nan danan ya zuqe kara 1, lokaci qanqani ya turniqe wajen da hayaki wane anhura wutar damina Amma dik da irin shan daya mata baiji hankalinsa ya kwanta ba, sam sabida haka ya balle murfin wine nasa ya kafa kai, lokaci guda yafara jin natsuwa Kwanciya yayi awajen, yanajin dik samywarsa ta yaye, yana nan awajen har 11 shiba bacci ba, bakuma ido biyuba Nidai mmn Faty nace Allah ya shirya ****** Kwanan Fauziyyah hudu period nata ya d'auke amma tin ranan farko cikin bai sake ciwo ba, haka bata sake saka papa a idanunta ba Ranan da aurensu ya cika sati biyu, kuma monday mai zuwa papa zai resuming office, aranan da safe Daddy ya kirasa awaya Hello Daddy ya gida, yacema Daddy Bayan ya picking call d'in Lfy lau son, ya daugther inlaw na Sai daya ya tsine fuska sannan yace fine Daddy Daddy yace haba son saina roqi a kawomun yar tawace naganta Toh Daddy nikuma nahanata zuwane, ka turo driver ya kaita mana Daddy yace driver kuma kai me kake da bazaka kawota ba Haba Daddy nadaukota amota ta, amatsayinta nawaye kenan har tashigarmun mota kawai to zansa akawota tinda ka matsa Daddy yace Alamin wai yaushe zakayi hankaline, kodai baka cikin hankalinkane, toh koma yaya ne zuwa yamma ka kawomun ita kuma da kanka that's all, yana fad'in haka ya kashe Itakuma tana tashi tayi wanka tayi breakfast, sannan ta sauqo down stairs dan tad'an gyara wajen Sai data gama ayyukanta tsaf, har data wuce sai kuma ta kalli falon papa tace dan Allah badan halinkaba barin gyara maka Tana shiga kuwa da wannan kyakykyawan photon nasa taci karo, murmushi tayi dan haka kawai wannan photon yake birgeta Tagama gyarawa ko ina sai sheqi da qamshi yake, tana fitowa taci karo da papa y saqqo kuma ita yake nema dan yayi ta norcking qofar ta baiji motsin ta b Qaremata kallo yayi, tana sanye da wani swiss army green colour da milk ya mata kyau sosai, amma shi haushima ta basa azuciyarsa yace dubeta kamar yar baby Yi tayi kamar bata gansaba tazo data wuce shi, hakan ya qara b'ata masa rai, cikin sauri ya saka hannunsa ya riqo mopper dake hannunta ya dawo d ita baya Tace lfy malam meye haka Duban walaqanci yamata yace bansaniba kuma ubanme ya kaiki falona Tace oho nima bansan niba inhar bakasan me ake da wannan ba, ta nuna masa moppern hannunta Yace ni kike fad'a ma haka ina tambayarki, wani wawan rankwashi ya zuba mata akanta Tace me Namaka zaka rankwasheni, yace d more bazaki daina mun fitsaraba d more bazan daina dukankiba yar qauye kawai mai kamada mayu Tace nicema kai, bata qarasaba ya doke bakin ya kuma qara mata rankwashi, sannan yace kikuma shirya da yamma muje gida amma wlh kitabbatar kinyi wanka dan bazakishiga mun mota da qazanta ba qazama kawai yana kaiwa nan ya wuce ta abinsa Shiru tayi tana tunanin mai ya Alamin yakeji da shine kam yake mata irin wannan walaqancin...... ✍🏻Faty Mmn Faty [10:40PM, 8/6/2017] ‪+234 703 448 8635‬: 🌾🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty Augusf, 2017 2⃣3⃣ Shiru tayi awajen tanajin wani d'aci aranta wasu hawayene masu zafi suka zubo mata gogewa tayi da bayan hannnunta cikin sauri ta haura side nata tana shiga falonta tafashe da wani irin kuka mai ban tausayi wadda itama batasan dalilin yinsaba sai datayi mai isarta sannan ta lallami kanta tayi shiru dikda damuwanta yananan maqale a ranta amma kashi hamsin cikin darii ya ragu Bayan tayi sallan laasar tayi wanka, ta tsantsara kwalliya,cikin wata jar super,mai ratsin fari da baqi kwalliya tayi sosai wadda tinda tazo gidan batai irinsa ba Wani danqareren gwal tasaka na cikin kayan aurenta,sannan ta feshe ko ina na jikinta da turaruka mmasu qamshi baqin takalmi tasaka hadi da baqar jakarsa,sannan ta yafa wani black veil ,habawa sai wadda yagani ko maqiyi sai dai yayi shiru badai yace bataiba Down stairs ta saqqo tazauna gudun yace ta bata masa lokaci tana zaune fiye da 20mins kafin ya fito,tinda taji takunsa tasunkuyar da kanta dan tin abinda yamata dazuma bata huce ba,kuma bata qaunar ganinsa kawai ba yadda ta iyane Sanye yake cikin qananun kaya as usual, black troser n white shirt mai layin baqi ,idanunsa sanye cikin wani baqin glass ,wasu baqaqen covers ne aqafarsa masu tsadar gaske, suman kansannan sai sheqi yake alamun yasha gyara,sai wani uban qamshi dayake zubawa ,gaskiya papa qarshene dan haduwa ya hadu ,shikansa shiyasa yakeji da kansa qare mata kallo yayi tsaf ta cikin glass ,yana nazarin ta,amma sai ya tabe baki ,yace jibeta yadda tayi kamar gaske qarasowa yayi wajen datake ,amma ko magana bai mataba ya wuce hanyar fita ganin baikulataba yasa itama tai kamar bata gansaba sai daya kai baqin qofa ,sannan ya juyo fiska ahade yace keh idan bazakiba nayi tafiyata,ko kina tunanin zanfita na jiraki ne cikin rashin kula tace ayyah ai banga wucewarka ba baran maganarka hakan yasake shaqarshi waima bataga wucewarsaba, toh kiqara 2mins kiga wlh barin jiraki ba yanafadin haka ya wuce wani wawan tsaki taja ,afili tace aifa dan wajen momcy zamuje aida ba inda zani haka ta fito ,lokacin yana qoqarin shiga mota,gidan baya ta bude zata shiga wani mugun kallo ya bita dashi ,yace cemaki akayi ni driver ne mai daukar mutane tace nibanceba,yace toh ki rufemun mota kidawo gaba ko kikona gida ,yafi maki sauqi turo baki tayi ,tace komai sai anyima mutum masifa mtss,yana kallon bakinta amma baidaiji abinda taceba ko kulata baiba ,yatada mota,ganin dagaske tafiya zaiyi ta bude motar tashigo haba wani sanyi da qamshi suka daki hancinta ,lumshe idanunta tayi tana jinjina haduwa irinta papa,moatarsa ma abin shaawa komai nasa unique abinsa shiyasa yake walaqanta mutane son ransa,dubi yadda masu gadi kemasa adawo lfy kamar su kwant masa amma ko yasan sunayi Allah ya shirye da wannana halayen nasa yana fitowa layinsu zai sha kwana nan sukayi clashing da TJ ,gefen hanya ya sauqa yayi parking,fitowa yayi ya barta aciki TJ ma parking yayi ,yana fitowa papa na qarasowa,abinda suka saba da sun hadu shi suka fara suka kashe hannu TJ yace man kabuya kawai abinka ,meye duniyarma Papa yace kaidai bari wlh naso naleqaka so bansami damaba TJ yace ina zaka sami dama tinda yanzu kasamu duniya bata fiska papa yayi dan ya fahimci inda maganar ta dosa,kaifa baa maganar arziqi dakai sai kabatawa mutum rai TJ yace nikuma anyi walqiya tahaska ba ,nifa ba abinda zaka fadamun yanzu tunda ashe ni kake mayarwa dan iska papa yace bazaka ganebane , TJ yace nayarda bazan ganeba ashe shegen kaya kanaso kanaiwa kasuwa,kuma banda iskanci harnima saika rainamun hankali cikin takaicii papa yace to anrainmaka hankalin sai yaya tinda kai bazaka ganeba koda anmaka bayni TJ yace niko nagane tinga zahiri nagani ba a bakiba papa yace nizan wuce sai munhadu monday ma zan resuming office ,inaga idan nataso zan leqoka baikaiga bashi amsa wayarsa dake aljihunsa tafara ruri, saida yagama wayar sannan ya dubi papa yace ok ba matsala Allah kaimu ,kagaida madam kacemata insha Allah zanshigo na musamman papa yace kana iya zuwa kafada mata dakanka,amma azahirii dama yana gudun kada yace bari yaqarasa wajenta ,dan bai sancewar tabama cikin motaba dake glass din tintic ne TJ yace daga baya kuma,kasan dawace nayi waya yanzun papa yace ina zan sani baban kaya,mai buhu2 yace toh batawa bace jarababbiyar yarinyar kace ,jammy ,baicin nasanar mata kayi aure shine yanzun takirani wai takiraka baka picking ba akan zata fada maka tashigo gari jiya papa yace wayar tana mota barin zan calling nata back TJ yace kada kabatawa kanka lokaci wlh karabu da mata yanzu ,dan kasamu dik abinda ake nema saura mu yan baya Allah yabamu irin naku takaici yasa bai ko kulashiba ya wuce yace Allah yasa kagane 。。。。。 Fauziyyah tana zaune kamar tafita ta tafi takeji,tsabar tagaji sai taji wayarsa tana ringing matsowa tayi taga waye ke kiransa, taga Jammy arubuce ,tabe baki tayi tace wahala tasameki dakike bin wannan bada jimawaba ,ya shigo ko kallo bata isheshiba ,sai daya tada motar ya hau hanya sosai sannan ya dago wayarsa yafara dialling no Jammy Hello, baby ya akayi batadaiji me akaceba yace umm bani kusa da wayar ne ,so ya hanya batakumajin mai akacw ba sai taji yace ba matsala sai goben ,uhum bye aranta tace itama kenan bazaa sake mata fuskaba ,daga haka ta juyar da kanta bata sake bi takan saba har suka iso basu suka dawoba har bayan ishai, inda taji kamar kada tadawo sabida yadda daddy da momcy suka nuna mata qauna dazasu tafi daddy ya bata kudi masu yawa ,da kyarma ta karba momcy kuma ta bata dambun naman zabbi cikin wani madaidaicin bokiti tunda suka shiga mota ba wadda yama dan uwansa magana har suka iso gida tana fita ta bude gidan baya zata dau bucket data ajiye ,yace keh meye haka zaki budemun mota tace na bude tinda ajiyata zan dauka ,yace toh kwadayayya kikamun rashin kunya nazubar wlh ko kulasa bataiba saima daukan abinta datayi ta wuce ciki..... KUYI HAQURI DA WANNAN BANIDA CHARGY NE ✍🏻Faty Mmn Faty [10:40PM, 8/6/2017] ‪+234 703 448 8635‬: 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty August, 2017 2⃣4⃣ Yana fitowa ya hangi su Abdu suna hira tare da masu gadi,sai alokacin ya lura da Abdu ke zaune,sam lokacin daya wuce bai lura dashiba dafe goshinsa yayi sakamakon tunawa dayayi yau bai bada kudin abincin darensuba gashi har pass 8,wucewa yayi ciki aransa yace tinda asanadinki mukayi dare har haka tafaru wlh sai kinmasu girki dan bamai fita neman abinci at this tym Direct site nata ya wuce ,gam gam yaketa buga mata qofa itakuma tana shiga tafara rage kayan jikinta dan tayi shirin bacci tinda tayi sallah ganin bugun bana hankali bane yasa tayi saurin zura wata yar yaloluwar riga ta fito tana budewa tace wai meyene kaketa damina kam daga shigowata aiko tana fitowa idanunsa kyar akan qirjinta wadda babu ko bra dan tariga da tacire, gashi rigar kana ganin jikin mutum ita kawai ganin yadameta yasa ta zura rigar ta fito ganin tafito tana kuma masa magana amma bai amsata ba, cikin jin haushi tace inbakada abin fadi kaga tafiyata dan inada abinyi yadda tayi maganar afusace yasashi maida hankalinsa kanta, yace toh mai bakin rashin kunya nayi shirune naji mezakice,kuma dai kinsan bakida abinda zanzo nema ko toh oya kifito kidafama su Abdu abinci yanzun kada kuma kibata lokaci Abinci?yace yes abinci koda wani yare nafada tace awannan daren toh banmaka qaryan zanyiba wlh sai dai su kwana da yunw.... bata qarasaba ya buge bakin yace baamun jayayya wlh kifito kiyi abinda nace kokuma jiki magayi dafe bakinta tayi tanajin zafin wajen amma bata risinaba ,juya masa idanuwa tayi tace toh ni yar aikinsu ce yace to meye amfaninki kima daina batama kanki tym kifito,kuma tinda abinnaki iskancine daga yau kexakina masu abinci sau uku arana barin sake saya masu abinciba tinda gakinan bakida aiki sai rashin kunya da kwadayi wani duba tamasa tace nayanzun dai zanyi amna banyi alqawarin yimasu kullum ba atow yace toh kigwada qinyi kigani sai namaki abinda baki tunani ,injuninki rashin kunya muzuba yana fadin haka ya juya,har ya juya yakuma juyowa kuma kinemi kaya kisaka kada kifitomun ahaka ,bako dadin gani , kuma bai birgeniba tinda bannemaba haka banson akawomun tayi duban jikinta tayi ganin yadda jikinta ya fito ga kuma abinda yafada sai kunya ya kamat ,amma sai ta dake tace to wayakai idanunka wajen yace toh tinda nema kike Allah yasa kifito ahaka kiga yadda zan kunto karena yamaki yana kaiwa nan yayi tafiyarsa abinsa itakuma kunyane ya lullubeta yadda yaganta ,daki ta koma ta watsa ruwa tukun sanban tadan shafa mai sai humra ajikinta, ta sauya riga da wando ,wandon iyaka guiwa sai rigar bata gama rufe mata bayanta ba saqqowa tayi tana kunkuni dan bacci takeji ,tana saqqowa falo tako hangesa zaune afalo yana waya ,kamar ta juya taji amma saita dake ta wuce kitchen tinda ta fito yake kallonta harta wuce ,yace lalle yarinyar nan zankoya mata hankali gaba kosata akayi bazata faraba cikin mituna qalilan ta hada masu taliya da macaroni wadda yaji nama da kifi ta juye a qaton flaks sannan ta fito dashi a hannunta a inda ta barshi anan tasamesa,tsuke fuska tayi sannan tace nagama ko kulata baiba ya miqe kamar mai karban kulan sai ya damqe hannunta da qarfi ,yasa dayan hannunsa ya karbi kulan ya ajiye zaro idanu tayi tace lfy mai namaka ,badai abinciba ainadafa ko,toh saika sakeni na wuce nan tafaki idanunsa ta warce hannunta zata gudu cikin sauri ya sake damqota saida tafado jikinsa,nan ya shaqi qamshin turarenta hadi da wani yarr dayaji ajikinsa sake matseta yayi ajikinsa,cikin tsoro tace meye haka yaya Alamin cikin muryarsa data fara sauyawa yace ba abinda kike nemaba shine zan maki wlh ni ba abinda nake nema,pls kayi haquri kasakeni yace yau ina rashin kunyar naki dama na qaryane kenan ganin baida niyyar sakinta saima dada matseta dayayi har sunajin numfashin juna,cikin tsiwwa tace wlh kasakeni kona cijeka banda mugunta mai namaka zaka shaqureni bata ankaraba taji bakinsa cikin nata,mutsumutsu tafara amma ina yadda yake tsotsan bakin kamar yasamu swt shiya fara kashe mata jiki har jikinta yasaki papa kuwa nan yafara sauqa a network,nan yakai hannunsa kan qirjinta yafara sarrafasu sosai ya shagala inda fauziyya jikinta yafara rawa dan ta tsorata da lamarinsa ,ganin yadda yake tsotsar bakinta harda mugunta yasa tafara kuka saidaya tabbatar ta risina sannan yasaketa ya tunkudata gefe yace wannan kadan kenan kika sakemun rashin kunya zakiga fiye da haka ko kisake tsallake maganata wawiya kawai wuce kibani waje cikin sauri ta wuce saidata je bakin step ta juyo da qarfi tace Allah ya isa na mugu kawai mai muguntar tsiya sannan ta ranta ana kare.... ✍🏻Faty Mmn Faty [10:40PM, 8/6/2017] ‪+234 703 448 8635‬: 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty August, 2017 2⃣5⃣ Dagudu ta shiga falonta ta kulle gagam,sai data shiga bedroom nata sannan tazauna abakin gado tana maida numfashi zamewa tayi ta kwanta ,tanajin radadin da bakinta da qirjinta suke mata mirginawa tayi tana tuna yadda papa yadinga....,afili ta furta dan iska kawai mugu dahaka har bacci yai gaba da ita,washegari tana tashi datayi sallah bata komaba saqqowa tayi ta hada masu breakfast sai qunquni take amma da tabari papa yamata abinda daya mata jiya gara tayi ko wanni irin aikine yafi mata tana gamawa ta koma daki sai datayi wanka tafito da hijab ajikinta, flask dinsu Abdu tadauka ta fito waje lokacin 8 tayi,wajen masu gadi taje cikin mutunci suka gaisa inda har suna mamakin hajiyar baruwanta ba irin alhajinba tace ga abincinsu ta kawo masu,sukayi godia suka karba daukan nata tayi ta wuce daki abinta sai wajen 10 ya fito domin yabama Abdu kudin abincinsu,cikin ladabi kamar kullum ya gaidashi,shima haka ya amsa a daqile miqo masa kudi yayi yace gashi barin baka na 1week,cikin sauri abdu yace ai ankawo mana abincin wakenan ya kawo maku?ya tambayesa hajiyace,ya amsa tabe baki yayi,yace ok ahikenan jeka abinka zataringa aiko maku dawowa ciki yayi,yace au ashe matsoraciyace,wani,murmushine ya subce masa dan dama yajima da ganota tana da tsoroo kawai dai bata barin takwana ne kwanciyarsa ya koma yayi sai wajen 12 ya fice eatry yayi break, acan jammy tasamesa suka dawo gida tare lokacin to 1 ya shiho gida,lokacin ta gama abinci ta kaima su Abdu,taga shigowar motarsa,zata shiga cikin gida taga yafito shida wata farar yarinya daganinta zaka gane farin kantine,tana sanye da riga da skert english wears,kanta yane da wani veil mai shegen kyau ,adokam iya ado ta zuba daganinta kuma tasha boko ta qoshi kallo 1 tamasu ta wuce abinta,kitchen ta shiga tadauko abincinta,afalo suka hadu su har sun hau kanbene papa na rungume da ita qaran bode qofar kitchen datayi shiya juyo da jammy, kallon fauziyyah tayi sosai sai kuma ta bata fusja ashagwabe tace my darling who is dat girl duban fauziyyah yayi yaja wani gajeren tsaki,yace muje rabu da wannar nima bbansantaba jammy tace oh,ko itace matar taka ? waiba ammafa bantabbatarba,ya amsa mata ta bude baki data sake magana,yace enought muje inkuma tammbayoyi daki tsaya na wuce abina maqale kafadarsa tayi takaimasa wani hot kiss a chicks nasa tace sorry my darling muje,baice da ita komaiba sai juyawadayayi suka wuce suka barta nan itama bayansu tabi tayi side nata,tana mamakin dama ashe haka ya Alamin yake bayan shaye2n,harda neman mata ,tabe bakinta tayi tace ruwansa tafara cin abincjnta tama manta da kashinsu Jammy kuwa suna shiga falon papa,tafara santin wajen tace waw my darling gidannan yamun kyau,Allako ya tambayeta tace sosaima kuwa,yace toh kullum kinso saiki zoba ur always wlcm cijin jin dadi jammy ta zame gyalan kanta,cikin salo ta qaraso wajensa ta wani rungumesa tsam amma abinda yabama papa mamaki bawani abinda yaji ajikinsa bakaman idan jikinsa ya taba na fauziyyah ba yana cikin wannan tunanj yaji jami tana masa wasu salo na musamman nan ya manta komai, sai dai kamar yadda ya saba iykansa romance ya rabu da ita, tin abin na qonama jammy rai harta haqura tasaba dan tanason muamala dashi sosai kodan yadda yake sake mata naira gashi yamata alqawarin mota idan tadawo daga tafin datayi Jammy asalinta yar nasarawa state ce, bautar qasa ya kawota bauchi ,watarana su papa sunje wani glub da dare acan ya hadu da jammy,dafarko jammy bata gane inda ya dosa anma dake tana da wayo sai take biyema halinsa harta samu karbuwa sosai awajensa kuma ko nawa bai tsoron kashe mata,lokacin bikinsama taje gida hutu ne kuma yamata alqawarin idan tadawo zai saya mata mota dan tana masa yadda yake so 100% basu suka fitoba sai wajen 5 lokacin fauziyyah tana kitchen tana hada abincin dare,taji fitansu, aikinta taci gaba dayi dan uban gayyarma bai gabanta baran waccce ya kawo har yakai mota ya tuna da ya manta tab dinsa dawowa yayi ya dauka,ya dawo zai wuce itakuma tafito a kitchen suka hadu,kallo daya tamasa takauda kanta dan masifa sai ya tsaya yace keh mani kekima wannan kallon, tace au kaine dama ai banganekaba zaro idanu yayi yace lalle kinsamu sake harni kike fada ma haka ko,to inma baqin ciki kike sai dai ya kasheki dan nida gidana dole nakawo abinda nagadama atsiyace tace ka tsargu kenan to idan kanaso kamaida gidanka mamin ko sabonlayi dik kaita shafa ,sai dai kasani kada kasake garajen hada jikinka mai tattare da najasa da nawa dan wlh dik danyan kan dana maka kaika saya da kudinka borouba nikike cema qazamin jiki,ni batai auneba taji ya damqota mari lafiyayyu biyu ya bata afiska,idanunsa sunyi jajur dan bacin rai yace inhar ni banfadamaki kazamaba harke kyafadamun, zafin marin da baqin cikin abinda yamata yasa ta rarimo hannynsa ta gantsara masa wani lafiyayyan cizo saida haqoranta suka shiga sosai ciki auch yafada yana yarfe dayan hannunsa,sannan tasakeshi tace kuma ba inda zani saidai ka kasheni mugu azzalumi cikin zafin rai ya dinga marinta sai daya dakata sosai sannan ya fice yana huci ranan kam tasha kuka harta gode Allah kuma ranan ce tafara nadamar aurensa da kyar tasauqe abincin amma bata iya kaimusuba sai ajiyewa datayi abakin qofa ta wuce daki,rufe kanta tayi tana kuka tana tunowa da yasir yanzun ko awani hali yake ,itama abincin dabata ciba kenan tin daga ranan fauziyyah tayi alqawarin ko papa zai kasheta bazata sake kulasaba,sau da dama zasu hadu afalo amma ko kallonsa batayi baran magana dama can bamasa takeba sai inya takalota haka kawai zai shigo ya zazzageta amna ko dago kanta batayi baran ta amsa ,hakan shikuma kona masa rai yakeyi sosai yanzun inbaije gida ya sami jammyba ita zatazo tasamesa,mota kuwa ya saya mata, haka take fantamawa abinta wasawasa har sunyi wata biyu da aure amma har yanzu ba abinda ke hada ta papa tafita harkansa ,shima haka sai inya bushi iska ya zazzageta ya wuce abinsa acikin haka daga wajen aiki aka turasa singafore zaiyi wani couse na wata shida lokacin dayaje wajen daddy da maganar yayi murna ,yace toh saiya samarwa fauziyyah school taci gaba da karatunta amma fir yaqi yace sai yadawo ai shima yana da niyyar hakan,daddy yace to sai dai tadawo wajensu da zama kafin ya dawo nan yace ya amince ,idan ana gobe zai tafi inyaso sai driver yakawota nan yafara shirin tafiya,bayan sati biyu komai ya kammala,ana gobe zai tafi da safe ya leqa fauziyya yace keh kishirya da yamma driver zaizo yakaiki gidan momcy kuma wata shida zakiyi saikisan abin dauka yadda yasameta tana game awayarta haka ko dagowa bataiba,shima wucewa yayi dan yasan bazata kulasaba tinda har dukanta ya tabayi akan sai ta amsa masa haka ya haqura ya kyaleta bata kulaba da murna su momcy ssuka tarbeta inda aka bata daki da falo nata, sai awajen momcy taji inda zashi yasa tadawo nan da zama ,tace Allah yaraka taki gona washegari shima ya daga zuwa singafore .... ✍🏻Faty Mmn Faty[8:39AM, 8/17/2017] ‪+234 803 157 5758‬: 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty August, 2017 Wannan shafin nakine ked'anki AUNTY NAJAH DAMBAM,nagode da kulawarki gareni thanks a lot 😍😘 2⃣6⃣ Tinda papa ya saka qafarsa ya tafi fauziyyah bata sakeji daga garesa ba,ko waya ya kira momcy idan tace ganan fauziyyah kugaisa mana sai yace aa zai kirata a wayarta daganan kuwa ko kalar no vaima saniba itama kuma hakan ya fimata,dan mantawa take dashi sai idan taji suna waya da momcy ko daddy take tunawa dashi zamanta takeyi cikin nunna mata so da kulawa wadda daddy da momcy suke mata,sai abinda takeso takeyi bamai takurata hakan yasa hankalinta kwance,saima haske da kyau data qara ,tai bulbul da ita abinta,gwanin shaawa watan papa biyu cur da tafiya, daddy yace ta shirya suje dambam weekend,murna awajenta baa magana ranan friday ana saqqowa daga masallaci,suka wuce suna isa daddy yacema driver nasa su fara zuwa gidan amininsa dan sun kwana biyu basu haduba aiko suna isa qofar gida da gudu tafito tayi cikin gida bako sallama ta fara kiran mama,mamana mama tana cikin daki zatayi alwala taji muryar fauziyyah kamar daga sama aiko da sauri ta fito,tana cewa wanakeji,kamar mangana da gudu ta qarasa ta rungume mama tana cewa nice mama Abba ya fito da niyyar tafiya masallaci sai yaji mama tanata dariya adaki tana cewa ba tsamnani kawai sai zuwa leqawa yayi dan yaga ita dawayene,sai yaga fauziyyah,da murnansa yace mamana kece yuwar haka bako waya sake mama tayi taje jikiin abba tace abbanafa nadau daddy ya fadamaka zamuzo yace yanzun keda waye tinda Alamin bayanan tace nidasu daddy nefa,mama tace amma shine baki fadamunba na biyeki Abba yace toh barinje wajensu ,yana fitowa suka hadu a tsakar gida dan har sun shigo daddy da abba sukayi musabiha suna murnar ganin junansu momcy kuwa wucewa dakin mama tayi mama tana mata sannu da zuwa daddy da abba juyawa sukayi dan tafiya masallaci,momcyma anan tayi sallah bayan sunci abinci, daddy yace hajiya mutafiko kinga dare ta fara,momcy cikiin zolaya ta dubi fauziyyah wadda ta maqale jikin mama tace daugther zamu tafi ko cikin shagwaba tace nikam momcy kibarni na kwana anan wajjen mama daddy yace yau anga abba zaa gudu manako,dik sukayi dariya sannan suka musu sai da safe sannan suks tafi Abbama yau afalon mama ya zauna suka sha hira,amma yaji dadin ganin yartasa dan daga ganinta batada matsala tinda jikinta bai nunaba,amma kullum da tunaninta yake kwana yake tashi tinda yasan ga halin mijinnata sunsha hira sosai sai wajen 11 sannan ya masu sallama ya wuce ya wuce sashinsa suma shirin kwanciyar sukayi, amma hiransu suke,mama ta dubi fauziyyah da kyau tace fauziyyah dftn dai babu wata matsala agidannaki fauziyyah tayi murmushi tace me kika gani mama aa tambayarki nayi ko kina fiskantar wata matsala dangane da mijinki tinda dai nasan su daddy kam bazaki taba fiskantar wata matsalaba tunowa da maganar abba tayi lokacin dayake mata nasiha yace kimin alqawari baxaki taba fadama wani sirrin mijinkiba koda mahaifitarki sake murmushi tayi tace aa mama babu komai munazananmu lfy lau,mama tace toh Alhamdulillah haka akeso Allah ya rufa mana asiri fauziyyah tace amin nan tajuya tace mama saida safe baccinakeji mama tace nima haka Allah ya bamu alkhairi shiru tayi tana ta tunane tunane har bacci ya d'auketa kwanansu biyu ranan sunday zasu wuce amma fauziyyah sai kuka take wai abarta bayanzuba Abba yace ba barinta da zaayi tazo su tafi kawai,momcy tace dama tazo da kaya soaaine saita zauna ta kwana biyu tinda Alamin dinma bainan daddy yace zonan yata,kinason kijima ne,tace eh yace to namaki alqawari nan da wata biyu dama akwai biki acikin gida idan munzo saikinyi wata kafin ki koma ko kin amince dasauri tace eh ta amince,nan suka tafi ammma bata bar hawayeba har suka tafi tana kewan gida sosai bayan tafiyarsu mama tacema Abba sai naga kamar da mataala atsakanin fauziyyah da mijinta Alhaji Abba yace kamar me kenan? tace tinda tazo harta tafi banji ko sau daya ya kirata awayaba Abba yayi dariyarsu na manya yace nadauka ko wani abu tafada maki,wannan kuma baiwuce shaanin aikiba amma bakomai kimasu fatan alkhairi kawai tace to Allah ya kyauta kamar yadda daddy yayi alqawari bayan watanni biyu suka zo damban biki anan suka batta sai datayi 5weeks sannan driver yazo ya daukota 。。。。。 Papa kuwa yana can singafore,cikin ikon Allah baisamun matsala akan abinda ya kaishi amma halayensa sai abinda ya qaru,haka nan yamanta da fauziyyah ashafin rayuwarsa amma lokaci zuwa lokaci yakan tunata da rashin kunyarta da tsiwanta har sukan sanyashi murmushi,dan yajima tsiwarta da masifanta sukan birgesa har su sashi dariya amma bai nuna mata dan kada ta rainasa a times da gangan yakan tsikaleta kawai danyaga masifarta amma daga baya fir taqima kulasa baran yaga abinda ke birgesa yanzun tunda yakusan dawowa sai yake yawan tunaninta aransa,kuma sai alokacin yakejin yayi missing fadanta dake basa dariya da tsoronta idan tamasa rashin kunya ta diiba da gudu ,shi gudunma dariya yake basa shalaushalau kamar data karye yanzun yanaji aransa zai iya zama da ita amma amatsayin qanwarsa kodan tana sashi,nishadi amma baxai iya zama da ita amatsayin mataba iya abinda yasani kawai dik randa yaga matar data isa ya aureta takuma dace da rayuwarsa inyaso zai aureta ammma bazai iya rayuwar aure da fauziyyah ba ,dan tamasa qanqanta sannab ita bata cikin test dinsa vata kuma da abinda yakeso ajikin mace uwa uba kuma batai boko ba bata wayeba so bazai ma iya daukarta amatsayin matarsa har ya iya nuna ma waniba cikin ikon Alla saura kwana goma ya dawo nijeria so yanzun yafara shirin dawowa gida da murnan ganin momcynsa da daddynsa dakuma su didinsa nikuma nace fauziyyah fa🤔 acan gida Nigeria kuwa tinda momcy taga saura 8days papa ya dawoo ta dauko mai gyaran jiki na musamman akafara gyara mata fauziyyah cikin kwana shida ta canza sam tayi wani irin kyau na musamman,ranan da aka cika saati aranan aka gyarra mata kanta akamata wani kitso kananu mai shegen kyau nan suka kwanta har gadon baya dan Allah yayiwa fauziyyah yalwar gashi momcy dakanta data dubi fauziyyah tace masha Allah Ranan da papa zai dawo bai shigo jirgi da wuriba har yaso ya makara cikin sauri ya shigo,ahankali ya qaraso seat nasa,kuma shine na jikin window amma har seat patnernsa tana zaune a seat nata kanta a sunkuye bata lura da mutum atsaye akantaba shikuma idan yace zai wuce zai iya buge jikinta,so ahankali cikin muryarsa mai dadi yace excuse me pls jin mmurya mai dadi tareda wani daddan qamshi yasa ta dago kanta ya salam shine abinda ta furta acikin zuciyarta dan ganiin wannan kyakykyawan saurayin wani lumshe idanu yayi ya bude kokacin da sukayi 4eye,nan take yaji ta burgeshi....... ✍🏻Faty Mmn Faty [10:15AM, 8/17/2017] ‪+234 803 157 5758‬: 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty August, 2017 2⃣7⃣ Wani qayataccen murmushi tamasa, tace am sorry kafin tajanye jikinta wani dadi na musamman yaji muryarta take dashi,shima ahankali yace no brobs sannan ya wuce wajen zamansa ya zauna wannan yarinyar kuwa tunda papa ya zauna take satan kallinsa,cos taji nan take ya birgeta har taji zuciyarta ta kwadaitu da inama yazama mallakinta aida tasami mijin nunama saa shima acikin zuciyarsa haka yake tunani lokaci guda yaji tamasa aransa,kuma haryaji shaawan aurenta dan tamasa dari bisa dari, kuma yanayinta yayi daidai da kalar matar,dayakeso juyowa yayi yasake kallonta akayi saa kuwa itama shitake kallo,lokaci guda,suka sakarma junansu murmushi mai qayatar da xuciya sai anan yamata kallon tsaf,farace ba har canba danma ya hadu da mayuka da hutune, tanada round face idanuwanta yan dadaidai,hakama batada dogon karan hanci,sai dan qaramin bakinta amma awaye take sosai kuma daganinta yar passion ce lura da kayan jikinta da kuma dakuma yananyin fiskanta kuma daganinta, doguwace,qirjinta acike sosai dan sun ciko riga, ahankali ya sauqe idanunsa qasa shiru dikkaninsu sukayi bamaiwa dan uwansa magana amma kuma kowa yanason yasake jin muryan dan uwansa dahaka ahankali har dai magana ya shiga tsakinsu,papa ya tambayeta a ina takeda zama sai data wani juya idanuwa cikin yanga tace ita yar nijer ce karatu ya kawota dingapore amma yanzun tagama gida zata koma da zama,kuma iyayenta a kaduna suke cikin gamsuwa ya kada kansa yace kinga nima dan nijer ne ina zaune a garin bauchi nan ya fada mara abinda ya kawosa singapore tace ah kacemun kai babban mutum ne,murmushi yayi yace aa kedai kike big girl dik sukayi dariya,salon matan da suka waye tawani lankwadhe kai ashagwabectace bankumaji sunan Dr ba hakan datayi tasake kasheshi dan baqaramun birgesa salon yanganta yakeba,anatse yace MUHAMMAD ALAMIN waw nice name gaskiya sunanka mai dadi da kyau kamar yadda kake murmushi yayi yace haka ko nodding kanta tayi tacr yeah,yace thanks ammafa nibaki fadamun sunankiba tace eyyer nadau baka buqatar sani shiyasa amma tunda kana buqata sunana JUHAINA JUHAINA ya maimata ahankali dan sunan yamasa dadi sosai yace swt name tace thanks Dr Ameen yace ur wlcm ,nan sukata hiransu kamar sun saba inda juhaina ta ringa yimasa hira cikin janhankali ,shikuma sai biye mata yake dan kawai shiyagama yankema zuciyarsa yasami matar aure sai da suka sauqa a Abuja sannan suka exchanging contact nasu na nijer, a abuja sukayi sallama inda tashiga jirgin KD,shikuma ya shiga na BH Daddy da momcy da didi niima sune sukaje airport taransa, suna isowa jirginsu na sauqa lokacin misalin qarfe shadaya na safe dan sauqar safiya sukayi a abuja Papa nahango cikin fararen suit,wanda suka matuqar karban jikinsa,komai na jikinsa farine hadda takalman qafarsa farare tass yana saqqowa didi niima dasauri taqarasa wajensa ta rungusa tace oyoyo bross,shima cikin murnan ganinta yace oyoyo swt sis i miss so much nan suka qaraso wajensu daddy ,ya rungumesa yace miss u son,shima yace miss u daddy momcy ya rungume yace miss a lot momcy,tace miss u too my dear daganan driver ya saka kayansa a mota suka nufo gda direct gidan daddy suka wuce,afalo suka yada zango inda suka fara hirran yaushe gamo nan masu aikin gidan kowa yazo ya gaisheshi,sai dai baiga wannan villager ba,aransa yace Allah yasama batanan momcy tace son kashiga side naka angyara sai kayi wanka kaci abinci ko yace ok momcy wlh agajiye nake sosai zaman jirgi ba dadi dik takurane daddy yace idan kayi wanka saika dan wartsake ai miqewa yayi ya wuce side nasa nada nacikim gidan yana shiga yaji wani qamshin dadi ko ina agyare tsaf,toilet ya wuce dan ya watsa ruwa momcy kuwa papa na wucewa ta nufi dakin fauziyyah azaune tasameta tana kallon cartoon,murmushi tayi ganin yadda fauziyyah tayi balain kyau yadda ba namijin da zai ganta baiji....ba ganin momcy yasa tayi murmushi tace momcy banji shigowarkiba hankalina na akam TV momcy tace never mind daugther ,kije kidauki abincin papa kikai mads side nasa ,amma wataqil yana wanka so kijirasa ya fito saiki masa sannu dacdawowa ko cikin girmamawa tace to momcy ,amma barin dauko hijab dina momcy tace wani hijab kuma abu dik cikin gida ko dan kwalima banyarda kisaba tinda kayan bamai dankwalibane cikin jin kunya tace toh sannan ta fice kitchen ta shigavta dauko babban tiren da aka hada abinsa ajai ta wuce ta wuce ta nufi side nasa falonsa ta shiga amma shiru ba kowa,sai ta wuce🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty August, 2017 2⃣7⃣ Wani qayataccen murmushi tamasa, tace am sorry kafin tajanye jikinta wani dadi na musamman yaji muryarta take dashi,shima ahankali yace no probs sannan ya wuce wajen zamansa ya zauna wannan yarinyar kuwa tunda papa ya zauna take satan kallonsa,cos taji nan take ya birgeta har taji zuciyarta ta kwadaitu da inama yazama mallakinta aida tasami mijin nunama saa shima acikin zuciyarsa haka yake tunani lokaci guda yaji tamasa aransa,kuma haryaji shaawan aurenta dan tamasa dari bisa dari, kuma yanayinta yayi daidai da kalar matar,dayakeso juyowa yayi yasake kallonta akayi saa kuwa itama shitake kallo,lokaci guda,suka sakarma junansu murmushi mai qayatar da xuciya sai anan yamata kallon tsaf,farace ba har canba danma ya hadu da mayuka da hutune, tanada round face idanuwanta yan dadaidai,hakama batada dogon karan hanci,sai dan qaramin bakinta amma awaye take sosai kuma daganinta yar passion ce lura da kayan jikinta da kuma dakuma yananyin fiskanta kuma daganinta, doguwace,qirjinta acike sosai dan sun ciko riga, ahankali ya sauqe idanunsa qasa shiru dikkaninsu sukayi bamaiwa dan uwansa magana amma kuma kowa yanason yasake jin muryan dan uwansa dahaka ahankali har dai magana ya shiga tsakinsu,papa ya tambayeta a ina takeda zama sai data wani juya idanuwa cikin yanga tace ita yar nijer ce karatu ya kawota singapore amma yanzun tagama gida zata koma da zama,kuma iyayenta a kaduna suke cikin gamsuwa ya kada kansa yace kinga nima dan nijer ne ina zaune a garin bauchi nan ya fada mata abinda ya kawosa singapore tace ah kacemun kai babban mutum ne,murmushi yayi yace aa kedai kike big girl dik sukayi dariya,salon matan da suka waye tawani lankwashevkai ashagwabe tace bankumaji sunan Dr ba hakan datayi tasake kasheshi dan baqaramun birgesa salon yanganta yakeba,anatse yace MUHAMMAD ALAMIN waw nice name gaskiya sunanka mai dadi da kyau kamar yadda kake murmushi yayi yace haka ko nodding kanta tayi tacr yeah,yace thanks ammafa nibaki fadamun sunankiba tace eyyer nadau baka buqatar sani shiyasa amma tunda kana buqata sunana JUHAINA JUHAINA ya maimata ahankali dan sunan yamasa dadi sosai yace swt name tace thanks Dr Ameen yace ur wlcm ,nan sukata hiransu kamar sun saba inda juhaina ta ringa yimasa hira cikin janhankali ,shikuma sai biye mata yake dan kawai shiyagama yankema zuciyarsa yasami matar aure sai da suka sauqa a Abuja sannan suka exchanging contact nasu na nijer, a abuja sukayi sallama inda tashiga jirgin KD,shikuma ya shiga na BH Daddy da momcy da didi niima sune sukaje airport taransa, suna isowa jirginsu na sauqa lokacin misalin qarfe shadaya na safe dan sauqar safiya sukayi a abuja Papa nahango cikin fararen suit,wanda suka matuqar karban jikinsa,komai na jikinsa farine hadda takalman qafarsa farare tass yana saqqowa didi niima dasauri taqarasa wajensa ta rungusa tace oyoyo bross,shima cikin murnan ganinta yace oyoyo swt sis i miss so much nan suka qaraso wajensu daddy ,ya rungumesa yace miss u son,shima yace miss u daddy momcy ya rungume yace miss a lot momcy,tace miss u too my dear daganan driver ya saka kayansa a mota suka nufo gda direct gidan daddy suka wuce,afalo suka yada zango inda suka fara hirran yaushe gamo nan masu aikin gidan kowa yazo ya gaisheshi,sai dai baiga wannan villager ba,aransa yace Allah yasama batanan momcy tace son kashiga side naka angyara sai kayi wanka kaci abinci ko yace ok momcy wlh agajiye nake sosai zaman jirgi ba dadi dik takurane daddy yace idan kayi wanka saika dan wartsake ai miqewa yayi ya wuce side nasa nada nacikim gidan yana shiga yaji wani qamshin dadi ko ina agyare tsaf,toilet ya wuce dan ya watsa ruwa momcy kuwa papa na wucewa ta nufi dakin fauziyyah azaune tasameta tana kallon cartoon,murmushi tayi ganin yadda fauziyyah tayi balain kyau yadda ba namijin da zai ganta baiji....ba sanye take cikin qananun kaya riga da skert yan ubansu,coppee brown masu adon duwarwatsu,sun matuqar yimata kyau, kantannan yasha kitso saiya sake fito da kyan fiskanta tasaka pink janbaki,tayi kyau iya kyau kaman ka dauketa ka gudu,ga wani qamshi na musamman dake fita daga jikinta ganin momcy yasa tayi murmushi tace momcy banji shigowarkiba hankalina na akam TV momcy tace never mind daugther ,kije kidauki abincin papa kikai masa side nasa ,amma wataqil yana wanka so kijirasa ya fito saiki masa sannu da dawowa ko cikin girmamawa tace to momcy ,amma barin dauko hijab dina momcy tace wani hijab kuma abu dik cikin gida ko dan kwalima banyarda kisaba tinda kayan bamai dankwalibane cikin jin kunya tace toh sannan ta fice kitchen ta shiga ta dauko babban tiren da aka hada abinsa akai ta wuce ta wuce ta nufi side nasa falonsa ta shiga amma shiru ba kowa,sai ta wuce bedroom nasa ,tana shiga yana fitowa daga wanka dagashi sai towel daure ajikinsa hannunsa riqe da dan qarami yana tsane ruwan kansa dago kansa yayi idanunsa ya sauqa akanta,kallonta kawai yake ba kyaftawa ganin yadda tayi kyau fatanta ya murje, qirjinta sun wani ciko ganin ita yake kallo yasa dasauri ta juya bayanta ta sunkuya zata ajiye tiren dake hannunta nan yasake rikicewa da mamaki dan yadda yaga bayanta baran data sunkuya,gashi sharp dinsu sunfito tass nan take yaji wani irin abu na fisgarsa,yace anya kuwa itace ,ga kanta daya sake daukar hankalinsa,yace ashe tana da gashi takowa yayi ahankali yaxo jikin qofar ya tstaya ,itakuma tana ajiyewa ta juya dasauri dan ta fice sabida baxata iya ganinsa awannan yanayinba tinda baida ko riga tana juyowa taganshi jikin qofa atsaye yana mata wani shuumin kallo...... ✍🏻Faty Mmn Fatyasa ,tana shiga yana fitowa daga wanka dagashi sai towel daure ajikinsa hannunsa riqe da dan qarami yana tsane ruwan kansa dago kansa yayi idanunsa yacsauqa akanta,kallonta kawai yake ba kyaftawa ganin yadda tayi kyau fatanta ya murje, qirjinta sun wani ciko ganin ita yake kallo yasa dasauri ta juya bayanta ta sunkuya zata ajiye tiren dake hannunta nan yasake rikicewa da mamaki dan yadda yaga bayanta baran data sunkuya,gashi sharp dinsuvsunfito tass nan take yaji wani irin abu na fisgarsa,yace anya kuwa itace ,ga kanta daya sake daukar hankalinsa,yace ashe tana da gashi takowa yayi ahankali yaxo jikin qofar yavtsaya ,itakuma tana ajiyewa ta juya dasauri dan fice sabida baxata iya wannan yanayinba tinda baida ko riga tana juyowa taganshi jikin qofa atsaye yana mata wani shuumin kallo...... ✍🏻Faty Mmn Faty [8:40AM, 8/17/2017] ‪+234 803 157 5758‬: 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty MAMmn Faty August, 2017 Banmanta dake ba Qawar Arziqi, wannan shafin nakine AISHA JIGAWA, nagode ALLAH ya bar qauna😍😘 2⃣8⃣ Cikin sauri takauda kanta dan bazata iya jure irin kallon dayake mata ba Papa harwani lumshe idanu yayi ya bude lokacin lokacin da yasake kallon qirjinta,ga wani sheqi da fatanta yakeyi na daukar hankali nan yaji zuciyarsa harma da gangan jikinsa suna shaawar kusantanta ko zai sami saukin abinda yakeji acikin jikinsa ganin bai matsa ahanyarba baran ta wuce gashi dik atakure takejinta,ahankali ta dago kyawawan fararen idanuwanta masu kamar madara,sunsha kajol sunyi daradara cikin sanyin murya tace ya Alamin zanwuce ya salam shine abinda ya furta azuciyarsa dan sai yaji muryarta yau tadabance kodan yau ba acikin masifa tayi maganarba kallon cikin idanunta yake,ahankali ta sauqe idanta qasa dan yau wani masifan kunyarsa takeji dan bata taba ganin namiji ahaka ba yace toh kizo kiwuce mana ko na riqekine amma ai katare hanyar tafada kanta asunkuye ok,zoki wuce nima kina wasting mun time inason na shirya kinzo kin wani tsareni yafada yana matsawa da jikin qofar ganin ya matsa yasa ta tako ahankali,sai daya bari ta kama handle qofar zata bude,yayi saurin riqe hannunta cikin sauri ta dago kanta tana dubansa amna ta gaza cewa komai sai ma kawar da kanta gefe guda tayi ganin batai maganaba yasa ya matso ta sosai,nanfa ta gagara fahimtar meyake nufi cikin sarqewar murya tace meye haka ya Alamin baice komaiba saima rungumota da yayi ta baya,dan qamshin turarenta da laushin hannunta su sukasa ya gagara haqura har saida ya hada jikinsa da nata pls mana ya Alamin ka barni na tafi tafada murya na rawa dan jin yadda yaketa sun sunan wuyanta kamar wani sabon maye hannunsa yakai kanta yana shafa qananun kitsonta,cikin wani salon murya yace kinfamun laifine shiyasa na hanaki tafiya amma idan kingoge laifinki yanzun zaki tafi cikin sauri tace toh menamaka dan tafara tsoraya da abinda yake mata hannunsa ya kai kan cikinta yana murzawa yace toh haka ake tarban miji nadawo daga tafiya bazaki iya cemun koda sannu da dawowa ba turo baki tayi tace au bakanan ne dama ,aini bansan kayi tafiyaba shiyasa sake matseta yayi ajikinsa har saida tayi yar qara,yace au bakisan nayi tafiyaba ko tace to kafadamunne,yace au kinji haushine tace akan me zanji haushi yace gaskiya kam naga alama tinda har shirin dawowata kikayi,dik wannan adon mani akayiwa kinga dole na biya ladan abinda kikeso ko batai auneba taji yawani mirginota,suna fiskantan juna hannunsa yakai kan hips nata yana wani shafawa cikin salon kwarewarsa,qoqarin hanasa ta shigayi ganin zata kawo masa wargi yasa yadauketa cidak sai kan bed yana direta agado ya biyota,bakinsa yakai kan nata yafara tsotsa,nan yafara fita ahayyacinsa dan wani irin dadi dayakeji har cikin kwakwalwarsa hannunsa yakai kan abinda yafi tsone masa idanu yafara murzasu yana wani irin gurnani kamar zaki fauziyyakuwa wadda tsoro ya cikata dan jin yadda yake murzata yana wani irin numfashi,saita sake tsorata ga ba halin yimasa magiya ya riqe bakin kamar yasamu swt cikin saa yasaketa mata bakin yana kokuwar cire mata riga,cikin hawaye tafara rokonsa dan Allah kayi haquri wlh indai sannu da dawowane zan maka kayi haquri pls ganin yadda take kuka tsakaninta da Allah gashi ba agida ukeba yasa yadan dakata da abinda yayi niyyah,cikin wata murya mai wuyar fassara yace kin amince zakimun sannu da wowar kokuwa haryanzun bakisan nayi tafiyaba cikin sauri tace na amince wlh,nasani bakanan kaje singapore amma dan Allah kasakeni yadda tai maganar yaso bashi dariya amma sai ya dake yace toh amma sai munkoma gida kin amince cikin sauri ta daga kanta tace na amince nanma bai kyaletaba dik maganar da suke hannunsa nakan kirjinta ahankali ya janye jikinsa ya murgina gefe dan baya da kuzarin da zai tashi zaune,ga wani irin murdawa da mararsa take masa wadda yaune rana tsfarko dayaji irin wannan abin itakuma cikin sauri ta miqe hartana tuntube da carfet dake gaban gadon tayi waje momcy dake zaune afalo ganin fauxiyyah ta fito abirkice yasa tayi murmushi,dan hakanta yafara cimma ruwa ,tun rananda fauziyyah takwanta rashin lfy sukaje asibiti likita ya tabbatar masu da zaran anyimata aure zata daina irin wannan ciwon cikin ,anan tafahimci ba abinda yashiga tsakanisu sai ta quduri aniyar kawo masu qarshen wannan zaman ya jima kwance ahaka da kyar yasamu natsuwa har bacci ya daukesa bashi ya tashiba sai laasar,bayan yayi sallah ya fito cikin shirinsa,momcy tace son gafa lunch naka akawo maka nan ko zaka haura dinning ya mutsa fuska yayi yace aa kawaima bashshi dan banjin yunwa,inaga ma zan wuce gida dan har yanzun banji na wartsakeba moncy tace to shikenan kana iya tafiya,zuwa ko gobe driver zai dawo da fauziyyah sake yamutsa fuska yayi yace no tazo mutafi kawai,murmushi momcy tayi dama da gangan tafadi hakan tace toh sai kubari da daddare saiku tafi daddy yana falonsa dan yace akwai maganar da zakuyi haka dai ransa baisoba ya wuce falon daddy 8:30pm suka shigo haraban gidansu dake dasspark,papa zuciyarsa wasai koba komai zai kashe qishin dake damunsa inda fauziyya take a tsorace amma taci alwashin baxata bari papa yaci galaba akanta ba tinda ba ita yakeso jikinta yakeso kuma kwalelensa suna shiga falo kowa yayi hanyar side nasa,cikin sauri ta nufi bangarenta har tana juyowa kada ya biyota abaya shikuma side nasa ya shiga hankali kwance,nan yayi wanka ya kira TJ awaya suka danyi hira,sai wajen 10 ya miqe ya lalimo aljihun wandon daya dawo dashi ya dauki extra keys din daya karba awajen daddy ya fito ya nufi side din fauxiyyah fauziyya kuwa tana shiga ta saka key aqofarta,harda zare keys din tariqe ahannunta,tana hamdala ga Allah daya tseratar da ita ,daki ta shiga ta dan gyara inda yayi qura sannan taje tayi wanka,wata yar yaloluwar riga tasaka iyaka cinyarta, kitchen taje tadafa ruwan tea tadawo falo ta kunna TV tana kallo tana shan tea dinta kamar amafarki taji ana bude mata qofar falo, cikin razana ta miqe dan ganin wazai shigo abinda baa taba mataba aiko ba zato taga papa ya turo qofar ya shigo..... ✍🏻Faty Mmn Faty [9:57AM, 8/17/2017] ‪+234 803 157 5758‬: 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty August, 2017 Ina kuke qawayen kirki, kuma Aunties na Fauziyya ga shafinku, UMMIN HANIF, AUNTY MARYAM NTC, HAJARA YAU ALIYU N MMN AISHA YOLA, na gode da qaunarku gareni, Mmn Faty luvs u😍😘 2⃣9⃣ Kallonsa take har ya shigo ya maida qofar ya rufe,sanye yake dagashi sai farar singlet da boxer gaba daya dik jikinta yahau bari dan tagama tsorata wani mayataccen kallo yake binta dashi, cos rigar jikinta takuma tafiya dashi sosai ahankali ya tako har inda take a tsaye,bai ceda ita kumoiba sai rungumeta da yayi tsam akan faffadan qirjinsa wani ajiyar zuciya mai qarfi ya saki lokacinda na fulaninta suka sauka akan chest nasa itakuma jin yadda ya hugging nata yasa hannayensa biyu ya holding nata tied sai tasake tsorata har jikinta na rawa papa cikin wani yanayi mai wuyar fassara daya,tsinci kansa lokaci guda yaji wani kasala ya lullubesa gawami yarr dayakeji acikin jikinsa sabida shaking datakeyi sai yayi kamar tana goga masa breast nata ne akan kirjinsa,sai jiyake tsikar jikinsa suna tashi yarrr cikin wata murya mai dauke da zallar kwadayi yace yadai kike shaking or ar u afraid? girgiza kanta tayi alamun aa,bakinsa ya kawo saitin kunnenta yace then why ar shaking umm cikin murya mai rawa tace babu fa yace ok to idan babu kisaki jikinki ninefa amma kina abu kamar kinga dodo hannunsa yakai yana shafa bayanta ahankali ya gangaro har kan hips nata,cikin rikitacciyar murya yace wai kam bakiyi missing nawa ba da baninan da siririyar muryarta tace umum nikam banyi missing naka ba ko,sau 1 yadda tayi maganar cikin lashin kulawa sai yaji zuciyarsa ta sosu amma sai ya dake ,ya tsarsa ya kai kan lips nata yana wasa dashi yace nikam nayi missing bakinnan mai tsiwa bai ankaraba sai yaji ta janyo yatsarsa da harshenta tana tsotsa kamar tasamu swt, sannan ta saka hannayenta ta qanqamesa haba nan yafarajin wani abu tin daga qafarsa har tsakiyar kansa,wadda shima bazai iya tantance ko meneneba hannunsa yasa ya zame hannun rigar tata,nan na fulanin suka bayyana nan ya tabbatar lallai komai ya canza awatanni shida kacal hannunsa yakai yafara shafarsu ya jin kamar zai shide,nan ya dada sunkuyowa ya lalimo bakinta cikin dabara take matsawa har tazo saitin kujera 3seater nan taxame ta zauna atare suka zauna,cikin shagwaba tana wani yauqi ta kwanto kansa,nan yafara tunanin ta kamu itama bai ankaraba yaji ta hau kan laps nasa ta zauna tana wani shafarshi,da haka har tasamu saitin kunnensa tana hura masa iskan bakinsa nan papa ya rasa awacce duniya yake ga wani,tafiyan tsutsa da take masa tindaga bayansa har cikinsa,dikda yana harka da mata ammavya tabbatar wannan yarinyar ta dabance dan komai nata daban yakejinsa idan ya taba shikuma hannunsa nakan nafulani kamar wadda yasamu saniya yana tatsa haka ya riqesu gam sai data tabbatar ya gama kamuwa ya fita aruwan hankalinsa sai tsulum ta shammacesa ta miqe tsaye dago jajayen idanuwansa yayi yana kallonta,da shakekkiyar muryarsa yace meye haka kuma ina zakije kika tashi wani dan iskan kallo tamasa tace toh me kakeso awajena cikin rashin fahimta yace kamarya menakeso,pls imma wasa kikemun banson irinsa tace wasa wanne irin wasa kuma,naga kana baccine shine naga ya dace kafarka, cikin jin haushin yadda take nema taraina masa hankali, yace keh banason iskancifa tinda magana kike nema HAQQINAH zaki bani period wani kallon uku saura kwata ta wtsa masa tace,kamanta dawa kake tarene wannan qazamar qaramar yarinya yar qauyen nancefa wadda batada komai bare abin shaawah ko kamantane toh mezaka xo kana hada jikinka daita yanzukam ya fusata dan yafahimci inda ta dosa wato itama zata rama abinda ya mata tinda yakawo kansa,amma sai yace mata pls mubar wannan maganar agefe,kawai kibani HAQQINAH cikin dadin rai ko na karba ta,tsiya kinsan zan iya ko wata dariya ta sheqe dashi lalle su HAQQI MANYA yanzun bakaji kunyar fadan maganar nanba,toh bari kaji nafada maka idan kai zaka iya hada jiki da yar qauye kuma kazama toh nibazan iya hada jiki da mashayi kuma mazinaci wadda baisan darajan mutane ba aiko bata tsammaniba taji wasu lafiyyayun mari guda biyu cikin bacin rai yace keh har kin isah nazo wajenki kifadamun magana son ranki,wace ce ke dan ubanki nifa naxo nataimaka mikine dan kin nuna kwadayinki afili,shiyasa kuma ina gudun kada Allah ya kamani da hakkinki akaina amma tinda kikace haka kozaki mutu sai na biya buqatata na yayyagaki yadda gaba zskisan irin maganar dazaki fadamun cikin rashin karaya tace na nuna kwadayina ko kai ka nuna naka to wannan yana daga cikin abinda zaisa kozaka mutu bazan bari ka kusanceniba ,daka kusanceni gara kare ya kusanceni domin shi dama dabba ne cikin fusatar zuciya ya doketa sai data fadi qasa amma bakin bai mutuba sai cewa take ai abudayawa wadda idan baka bariba randa Allah ya kamaka wlh bakada mafita tsabar bacin rai sai da idanunsa suka qanqance,cikin tsantsar bakin ciki yarasa mai zaima yarinyar nan ya huce yace lalle zan nuna maki ni namijin gaskene kuma nafi qarfinki,baki kai matsayin da zanyi tarayya dakeba, kuma zan maidake baiwa yadda idan wanda yasanki yaganki bazai gane kiba amma kafin nan saina miki abinda gara karen da kika ambata ya miki fyade akan abinda zan maki yana fadin haka yasa kafarsa ya taka ruwan cikinta sai datayi qara mai ban tausayi,nan yasa hannu ya keta rigar jikinta,kafarsa yasa atsakanin kafafunta ya wara su sai dai mezai gani,sake sunkuyowa yayi da kyau tabbas pad ne ajikinta amma bai yadda ba sai dayasa qafarsa ya fincike sai yaga jini ajiki..... ✍🏻Faty Mmn Faty [3:51PM, 8/19/2017] ‪+234 803 341 6395‬: 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty August, 2017 3⃣1⃣ Bashi ya tashiba sai wajen 12 wanka yayi ya shirya cikin wasu qananun kaya masu kyau da tsada ash colour sun matuqar karbarsa gashin kansa ma kawai abin kallo ne,ya dakko glass nasa ya manna a idanunsa wasu takalma masu tsadar gaske yasaka aqafarsa,sannan yazo wajen car keys nasa ya tunanin wacce zai fita da ita key na mercides ya dauka,har yakai qofa ya juyo,wata drawer ya bude ya dauko kudi wadda shima baisan adadinsuba yasa aljihunsa sannan ya dau wayoyinsa yayi hanyar fita cikin isah da taqama yake tafiya (niko mmn faty nace ko sarautar ce yau ta motsa) ahankali ya sauko matakalar benen kamar wadda baiso haka yake tafiya tsayawa yayi ganin ta akwance afalo tana bacci,tawani duqunqune kamar mai tsoron kar wani abu ya kamata wata,doguwar tsaki yaja kansa daya ya wuce kitchen nan ya bude fridge, ya kuma bude freezer,sannan ya wuce store, nanma ya duba komai sannan ya dawo falo tsayawa yayi akanta,hannunsa yasaka ya jawo yatsar kafanta ya murde hadi da danna mata wata uwar tsawa keh tashi nace afirgice ta miqe sabida tsawar da ya daka mata,ga zogi da taji ajikin yatsar kafanta tashi zaune tayi sai jikinta dake rawa dan tsoron batasan mai zai mata ba cikin daurewar fuska yace keh dan uwarki nan wajen baccine ,kinwani zo kin kwanta ma mutane akan hanya cikin girgiza kanta tace aa yace toh kada ki kuma zuwa ki zauna anan baran ki kwanta, idan kuma kinqi ya karkada mata yatsun hannunsa biyu murya na rawa tace barin sakeba, yace kima sake saikinyi nadamar ranan da aka haifeki sannan yace kinajina,bai saurari mai zata ceba yace daga yau kada ki kuma dafa abinci da kowa agidannan kiyi naki kekadai tace toh,sai kuma tayi shiru dama tanason tafada masa akwai abubuwan da babu a kitcthen amma tana tsoro gashi yanzun ma bataga fiska ba bai kuma saurarontaba yayi waje abinsa,wajen motocinsa ya nufa ko wacce an wanke sai kyalli take dan dokarsace kullum sai an wankesu duka inya fito ya zabi wacce dai fita da ita cikin girmamawa dik sukazo suka gaidashi,amma haka dik ya amsa masu adaqile motarsa ya shiga,mai gadi ya bude masa gate ya fice,direct EATRY ya nufa yayi breakfast daganan wajen hutawa ya wuce,qarqashin wasu bishiyoyi masu sanyi ya zauna akan daya daga cikin kujerun dake wajen wayarsa ya ciro ya shiga contact, dialling wata no naga yafara leqowa nayi dan naga waye yake kira,akan screen din naga MY JUHAINA wayar tajima tana ringing sannan aka dauka cikin wata murya mai jan hankali akace hello sai daya wani lumshe idanu ya bude sannan yace hello yan mata cikin yanga tace barka da rana DR wani murmushi mai tsada yayi sannan yace au kingane mai magana ayangance tace haba dai aiko bana da no naka ,voice naka bazai bacemunba cikin jin dadi yace thanks dana samu wannan matsayi tace ai kawuce haka ,dftn kasauqa gida lfy yace lfy lau n u, tace same yace thats gud so ya mutanen gida tace wlh all ar fine yace am glad to hear that,dama nace barin kira queen naji ta sauqa lfy n idan badamuwa zan ringa kira time to time muna gaisawa cikin jin dadin kalamansa tace badamuwa ur always wlcm yace ok, nagode barin barki haka later tace its my pleassure nan sukayi sallama kowa zuciyarsa cikin jin dadi WACE CE JUHAINA Asalin sunanta JUHAINA MUKHTAR, mahaifinta shine deputy governor na kaduna state amma wannan zaben da akayi sun sauqa dan suncinye tenure nasu, asau biyu suna cin zabe su hudu ne awajen iyayensu, amma ita kadaice mace awajen iyayenta, tana da yayu maza biyu sai ita sannan autansu wadda shima namijine suntaso cikin gata da kula musamman juhaina wacce ita kadaice mace,bayan ta qare secondary school nata shine ta tafi singapore tayi degree nata acan yanzun tagama tadawo gida inda anan suka hadu da Dr Alamin juhaina wayayyar mace ce ajin qarshe,ga kwalliya da iya gayu,sannan yar duniya ce dan tsabar gata yamata yawa harta sangarce yahadu da zaman waje dan ita atsarinta ma batun aure yanzun, amma ganin Dr Alamin yasa lokaci guda taji kwadayin aurensa dan yadace da mijin datake burin aure idan ta tashi wannan kenan.... Ranan haka fauziyyah ta yini cikin ciwo ga yunwa dan ta gagara cin abincin sam, sai black tea data dan hada tadan sha washe gari da safe tadan tashi da dan sauqi,sakkowa tayi ta nufi kitchen sai ta tuna ashefa yace kada tasake girki da wani tunanin mezataci ta fara dan wata masifaffiyar yunwace ke damunta,gashi daga shinkafa sai taliya da macaroni ,indomie ma baifi guda hudu ba ya rage bandasu ba komai sai mangyada dasu maggi indomie tadauko guda biyu ta dafa bako albasa dan bata dashi da kyar tadanci kadan dan bai mata dadi ba tana cikin wanke plate din taji muryar papa yanacewa keh keh ,cikin sauri ta dauraye hannunta tayi waje dan tasan da ita yake tana fitowa ta tsaya agefe tace gani yace au kinajina dama ashe inata kiranki dan iskanci bazaki amsa ba wata katuwar leda mai kamar jaka tagani ahannunsa, dangwala mata yayi agabanta yace oya kafin naje nayi wanka na fito ki tabbatar kin wanke jakar nan sannan kin mun folish na takalmana,idan kuma har na fito baki gama ba hmmm sorrynki bai sauraretaba ya wuce,zazzage takalman tayi tun tana qirgawa harta daina dan yawansu haka taje ta wanke jakar ta dawo tafara goge takalman,ga ba dadi takejiba ga yunwa ga aiki sai zufa takeyi ahaka har ta kammala tsaf yana fitowa yasamu tana shiryasu acikin jakan dan kamar leda take tana kadeta ta bushe cikin shirin fita ya sauqo ashe tsabar walaqanci bama sakawa zaiba kawai yabata wahala yasa yayi hakan tace gashi nagama,yace toh sai yaya kidauka kikaimun qofar falona ki ajiye yana fadin haka ya fice abinsa Cikin sati biyu fauziyyah wahala da damuwa ga bata iya cin abinci kota girka hakan yasa ta rame ta lalace papa kuwa izuwa yanzu soyayya mai karfi ya shiga tsakaninsa da juhaina,yini suke suna waya da charting dayake sai next week zai resuming office,kuma aqsrshen sati yaima juhaina alqawatin zuwa kd dan yaganta..... ✍🏻Faty Mmn Faty [3:52PM, 8/19/2017] ‪+234 803 341 6395‬: 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty August, 2017 3⃣2⃣ Ranar Friday yaje gida ya yima su momcy sallama akan zashi kd Momcy tace son mezakaje yi a kd kuma? Yace daurin auren abokinsa zashi Nan suka masa fatan alkairi da sauqa lfy Washegari early morning ya wuce,Inda ko takan fauziyyah baibiba Kafin azahar yajima da shiga kd, sai daya huta a hotel din daya sauqa Bayan asr prayer yasake kwalliya ya caka ado sannan ya nufi unguwar su juhaina Da waya maqale akunnensa tana masa kwantance har ya isoh Gidane qato na gani na fada, dagani masu gidan suna cikin daula Horn yayi maigadi ya bude masa kamar yadda tace ansan da zuwansa Yana shiga yayi parking sannan ya kira wayarta Bada jimawaba ya hango ta tafito cikin shiga ta alfarma Wata doguwar rigace ajikinta, dark purple, ya matuqar yimata kyau,saman rigar ya kamata qirjinnan ya fito afili,gyalen kayan ta yane kanta dashi Tana isowa ya bude mota ya fito, tana isowa da murmushi afiskanta tace wlcm my king Shima murmushin yayi yace aha my queen Muqarasa tace dashi Wani qaton falo wadda aka qawatashi da kayan ado na zamani ta kaishi Nan ta cikashi da kayan chi dana sha,spring rolls yadauka yana ci Guda biyu yaci sannan yasha juice yace Alhamdulillah Dubansa tayi cikin shagwaba tace haba my king bakafa ciba Yadda tai maganar ya burgeshi sosai haryasanya shi wani murmushi na musamman yace eyyer my gueen nafa qoshi ne cos banjin yunwa Tace dik da haka sai ka qara Yace do not worry my queen as u wish, but not now Tace OK so ya hanya Yace well um hanya normal fa Tace wonderful haka akeso,yasu momcy, daddy n others Yace all ar fine my darling, ya nasameku hop kowa lfy Absolutely fine ,ta amsa masa Yace masha Allah Shiru suka danyi cikin soft voice nasa yakira sunanta juhaina Naam my king ta amsa tana kallonsa Yace nazo kd sabida ke,kuma nibanazo dawasa ba dagaske nake aurenki zanyi ammafa idan kin amince Cikin murya mai Jan hankali tace na amince my king Yace naji dadi ammafa akwai abinda banfada maki ba Tace uhum go on am all ears Yace inada mata Daram taji gabanta ya Fadi Dan abazata taji maganar Yaci gaba da fadin sai dainibani sonta auren hadi aka mana,kuma bazan hadaku gida 1ba Gidanki daban zan maki ,kuma kece wacce nakeso kece zabina so kada tadameki Dan nima bata gabana Sai anan taji hankalinta ya kwanta amma ta qudiri aniyar saita koreta kota halin qaqa cikin kissa da kisisina tace kada kadamu aini kaina keso kuma dakai zan zauna bada itaba cikin jin dadi ya dada tabbatar lalle juhaina tana sonsa sannan ita wayayyar mace ce ba irin haukan kishin nan akanta Sunsha hira sosai da zai tafi yashiga suka gaisa da dad da mom din juhaina Sai data rakoshi har bakin Mota sannan ya bata tsarabarta da yayi mata Nan sukayi sallama akan washegari zai shigo su gaisa kafin ya wuce Washegari kuwa kamar yadda yayi alqawari sai daya shigo kafin ya wuce Haka suka rabu cikin shauqin so ***** Watan papa 1 da dawowa daga Singapore amma kamar ya shekara awajen fauziyyah sabida uquban dayake gana mata Yau yakama saturday tinsafe ta gagara cin komai, harwani zazzabi takeji Dan yunwa Tana cikin wanan yanayin har bayan laasar,kamar daya sama taji shigowar mota Jin ana nocking yasa taje ta bude,aiko wazata gani momcy da Dady Cikin murna ta taresu, saida suka zauna momcy da tun shigowarsu take kallon fauziyyah Tace daughter na bakida lfy ne Cikin sanyin murya fauziyyah tace eh momcy banida lfy daddy yace ayyah amma Alamin bai fada manaba,yaya jikinnaki tace dasauqi Wani dadi ne ya lullube momcy atunaninta ciki fauziyyah take dashi Daddy ne yace Alamin bainan ne Ahankali tace yana nan Daddy yace jekice masa munzo ko Miqewa tayi jik ba kwari ta haura dakinsa Tsayawa tayi abakin falon tana tinanin Mezai mata idan tashigar masa daki Shahada tayi ta murda handle din aiko cikin saa abude qofar take Ahankali ta tura ta shiga,nan wani sanyi da qamshi suka welcoming nata Qarema wajen kallo take yadda ya hadu iya haduwa tace lalle ya Alamin dan gayene tundatake bata taba shiga waje mai kyau da tsaruwa irin nanba Ganin bainan yasa ta wuce cikin dakin, fitowarsa daga wanka kenan yaganta kamar dagasamma Daure fuska yayi cikin masifa yace keh meya kawoki dakina Adiririce tace su Daddy ne suka zo,shine sukace namaka magana Toh naji wuce kifita banza qazama kafin kibatamun daki Cikin Sauri tafice,sai data tsaya ta goge hawayenta sannan ta saqqo Tazo daidai step na qarshe kawai sai su momcy sukaji Tim Abu ya Fadi Aiko wazasu gani fauziyce tayanki jiki ta Fadi,cikin sauri suka nufota hankali tashe Daidaida papa yake qoqarin saqqowa Ganin su abirkice ga Kuma fauziyyah akwance a qasa, yasa shima ya saqqo da sauri..... ✍🏻Faty Mmn Faty [3:53PM, 8/19/2017] ‪+234 803 341 6395‬: 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty August, 2017 3⃣3⃣ Fauziyyah, Fauziyyah shine abinda momcy take fada cikin tashin hankali Daddy yace Alamin dagota mutafi hospital Cikin sauri ya dagota ba bata lokaci suka tafi asibitin daddy Direct emergency suka wuce da ita, daddy dakansa ya shiga dubata inda papa yarasa meke masa daddy Dan baisan amsan da zai bawa daddy ba idn yatambayesa Momcy kuwa ta gagara zama sai sintiri takeyi awajen Cikin mintuna 35 daddy ya fito amma fuskarsa a daure da alamu ransa abace take Da sauri momcy ta nufoshi,daddy meyasa meta shine tambayar data fara masa Sauqe ajiyar zuciya yayi yace muje office,papa da yarasa ta cewa shima ya biyo bayansu Sai da momcy ta shiga ,papa yazo zai shiga cikin sauri daddy ya daga masa hannun da kakkausan murya yace tairo(dakata) Afusace ya rufo qofar,momcy dake tsaye tace Ya jikin nata ? Daddy yace relax momcy ,munshawo kan matsalar,yanzun numfashinta ya dawo normal, ansamata ruwa zaa maidata dakin hutawa Momcy tace to meyasa meta haka wlh hankalina ya matuqar tashi Daddy cikin takaici yace YUNWA Yunwa? Wacce irin yunwa kuma Yace to a iya bincikena Nagano lfyrta qalau sai yunwa da damuwa wadda sanadin haka ta yanki jiki tafadi Momcy tace to batacin abincine kenan,daddy yace wayasani niban yarda da Alamin ba,yanzu kije driver ya kaiki gidan nasu kidauko mata kayanda zata saka idan ta tashi saiki bincikamun gidannasu akwai abinci ko kuwa Momcy tace to bari naje nadawo amma kuwa matuqar Alamin yana da hannu aciwon yarinnan sai ya raina kansa, tana fadin haka tai waje Tana fitowa papa ya biyo bayanta, yana mata magana ko kulasa bataiba ta wuce abinta Direct dakin fauziyyah ta shiga ta dauko mata kaya acikin sannan ta duba kitchen din falonta,wayam ba komai,sakowa downstairs tayi ta shiga kitchen da store ,rai bace ta fito suka nufi asibiti Office din daddy ta shiga nan ta labarta masa komai cikin takaici tace Alamin yaci amanar yarinyannan ,bakomai banda shinkafa da mai da maggi kuma INA zaton tun garan bikinsu nema Daddy yayi shiru yace balaifi ya kyauta muje wajenta kada ta farka ba kowa Dakinda aka kaita suka shiga,basufi minti goma ba tafarka ,tana bude idanunta sai kuma ta fashe da kuka Momcy tamatso kusa da ita tana shafa kanta,cikin lallashi tace kiyi shiru daughter gani nan kusa dake ba abinda zai sameki Asabe mai aikin momcy ce tashigo,da basket na abinci da flask ahannunta, ajiyewa tayi tana tambayar ya mai jikin Momcy tace dasauqi ,kikoma gida saimun dawo kawai inaga nan zamu kwana Tace toh Allah ya sauwaqa sannan ta tafi Tea mai kauri momcy ta hada sannan tace daughter muje kiyi brush kiyi wanka saiki sha ko Ba musu ta tashi,saida ta kaita har toilet sannan ta a fito ta barta Tana fitowa ta bata kaya taje tacanza, bayan tacanza kayan tafito zama tayi a bakin gado tayi shiru Daddy ya ce ya jikin,ahankali tace dasauqi Miqo mata tea momcy tayi amma maimako takarba sai tafashe da kuka Rarrashin duniya sunyi amma taqiyin shiru, cikin lallami daddy yace mekikeso daugther nah fadamun amma kibar kuka kinji Cikin kuka tace nikam wajen Abba da Mama zanje Daddy yace toh kiyi shiru zan kira maki Abba awaya amma fa sai kinyi shiru kuma kinsha tea kinci abinci kin yarda Cikin sauri tace na yadda Daddy yashafa kanta yace good girl Momcy ta matso tafara bata tea aiko nan da nan tashanye tass dan yamata dad'i, rabon data sha mai dad'i haka ai harta manta Plate momcy ta dauka ta zuba mata fried rice wadda tasha kayan lambu da papper chicken Nan tahauci hannu baka hannu kwarya,daddy juyawa kawai yayi dan takaici ace kamar fauziyyah dan tasamu abinci takeci kamar almajira Momcy ma haka shiru kawai tayi amma baqin ciki ne fal ranta Tass tacinye ta kora juice mai sanyi, haba sai wani natsuwa yaxo mata,har wani lumshe idanu tayi tanajin wani natsuwa ajikinta Daddy ne ya kira Abba awaya bayan sungaisa yace masa ga fauziyya zasuyi magana, Abba yace lfy dai ko Daddy yace lfy ba lfy ba itance bata da lfy amma dasauqima shine take rigima wai sai dai akawota gida shine nakira taji muryarka ko hankalinta zai kwanta Ok toh bani ita, tana karban wayar tace ina yini Abba Lfy lau mama na ya jikin dai, Tace dasauqi,yace to kuma sai rigima kice sai kinzo gida Cikin shagwaba tace ai inason ganinku ne Abba yace toh ai basai kinzoba gobe insha Allahu zamuzo mudubaki Cikin jin dadi tace dagaske Abba Yace insha Allah ga mama kugaisa Nanma cikin murna suka gaisa da mama , mama tace harda khairy zamuxo dan tazomun hutu Cikin doki tace Allah ya kawoku lfy Mama tace amin sannan sukayi sallama Daddy yayi murmushi yace rigima ta qare ko Sunkuyar da kanta tayi sai taji kunya kuma Daddy yace momcy inaga muwuce gida kawai tunda tasami sauqi Momcy tace to bakomai nan tafara hada kayayyakin su Daddy ne ya dubi fauziyyah cikin kulawa yace daugther na zaki bimu ko zaki koma gida Dasauri tace aa zanbiku Nan yadada tabbstarwa lalle abunda papa yayiwa yarinyan nan bakadanba ne tunda har take gudun gidansa Driver ya kira yazo ya saka musu kayansu a mota sannan suka wuce gida Ranan fauziyyah tayi kwanan natsuwa dan kafinta ta kwanta sai da momcy tasa aka dafa mata farfesun zabuwa wadda yaji kayan qamshi nn taci tayi nak dama fauziyyah badai son dadi ba😜 Momcy ce ta shigo dakin daddy cikin shirin bacci nan tasameshi yayi shiru Zama tayi agefensa ta dafashi tace daddy lfy kuwa kayi shiru tunanin me kake Saida ya sauqe numfashi sannan yace tunanin wanne irin hukunci zanma Alamin nake tunda baida mutunci har yana neman kashe yar mutane saboda son zuciya Momcy tace nima tunanin danake kenan amma kabarni dashi fauziyyah kuma baxata koma ba harsai ya gane kurensa Daddy yace hakan zaayi amma ahankali kitambayeta medame ya ke mata Momcy tace badamuwa bari ta warware Washegari su Abba sukaxo murna awajen fauziyya ba magana Tare sukazo da khairy Nan suka shiga dakinta inda momcy da su mama suna falon daddy ***** Papa kuwa ganin sunqi sauraronsa gashi baifito da wayaba da yakira TJ yazo ya maidashi gida Drivern daddy yasa ya maidashi gida Washegari bayan yayi wanka yafara tunanin yaje ne ko kar yaje Sai yace gara yaje kada yasake laifi amma bari ya kira TJ yazo suje TJ ya kira awaya yace yaxo rakashi wani wajemana Tj yace badamuwa in d next 30mins yana zuwa Bada jimawaba sai gashi agidan papa yayi parking motarsa suka shigata ta papa suka fice Suna tafe ahanya amma papa hankalinsa yana can tunanin ko momcy data saurareshi Tj ne ya katse masa tunani yana cewa man kadakkoni rakiya bakafadamun inda zamujeba sannan kayi shiru baka ko magana lfy kam Baibashi amsa ba saima yaga sun dau hanyar asibitin daddy TJ yace man kamun bayani mana kuma gashi mundau hanyar asibiti Papa yace kaidai bari wlh waccar yarinyan ce batada lfy kawai shikenan su momcy suka fara fushi dani suna nuna kamar nina saka mata rashin lfyr TJ yace wai wace badai fauziyyah ba Papa yace ita mana ni wlh yarinyannan tazamamun liability TJ yace i know u very well friend anya kuwa ba wani abu kamata ba Cikin fushi yace toh mezan mata nikuma Tj yace Allah yasa dagaskene kake kuma indai da hannunka nima ba ruwana Daidai da shigowarsu cikin asibiti nan ya hango wata nurse kiranta yayi ya tambayeta tace ai tunjiya suka tafi gida Shiru yayi TJ yace ai saimuje gidan to Nan suka wuce gida, Falon daddy suka fara shiga nan suka samu su Abba Cikin girmamawa papa yagaida Abba da mama Sannan ya gaida daddy da momcy haka dai suka amsa ba yabo ba fallasa sabida gabansu Abba nema yasa suka amsa Wucewa cikin gida sukayi ganin ba kowa a falo yasa suka nufi dakin da yasan zai samu fauziyyah...... ✍🏻Faty Mmn Faty [3:53PM, 8/19/2017] ‪+234 803 341 6395‬: 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty August, 2017 3⃣4⃣ Bako sallama haka ya hankada qofar dakin ya shige ciki TJ ne dake bayansa yayi sallama Khairy dake zaune afalo tana danna wayarta tadago tana amsa sallamar TJ ko yana ganin khairy yagane ta da faraa yace manyan bakine haka Itama da faraarta tace sannu da zuwa dan taganesa Amutunce ta gaidasu, TJ yace ya maijiki Dasauqi ta amsa ,yace Allah ya qara sauqi tace amin Ina fauziyyah Tj ya tambaya Tace tana bacci amma barin tasota Cikin sauri papa yace aa kibarta kawai sai anan yayi magana tun shigowarsa Samun waje TJ yayi ya zauna dan shifa ya kyasa baran yau saiyaga taqara masa girma da kyau Amma kuma bansan sunan malamarba yafada yana kallon khairy Murmushi tayi cikin kunya tace khairy Yace waw nice name khairy ya maimaita Papa da haushi ya kasheshi yace oya man muje idan ta tashi madawo yafadi hakan dan sutafi TJ yace ok muje amma malama khairy kozan sami no wayarki dan muringa gaisawa Shiru tadanyi , qasa da murya yayi yace ko zaamun rowa ne Tace aa sannan ta bashi Godia nake sosai yafada sannan ya fice lokacin papa har yakai qofa Suna fita papa yace kaidai Allah ya shiryaka mai zakayi da no wayar wannan yarinyar TJ yace abinda kake da taka yarinyar dan ubanka Papa yace lalle nayarda kanka aduhu yake kuma bakasan me duniya take cikiba TJ cikin rashin fahimta yace toh wayar mun dakai mana Baikuma cewa komaiba sai da suka shiga mota ya dago tab dinsa yace kallo nan Karba yayi adakile yace wannan mai idon yan chines dinfa?wace ce ita harda samun matsayin hawa wallpaper Papa yace buu, dan iska marar mutunci aifa nasan kai dan adawane shiyasa ban shafa maka ba amma tunda kafito fili da rashin mutuncinka to matar da zan aura ce kuma kada ka gwada gigin aibatata TJ da ya daskare yanajin papa yace man me kake fada aure akan wani dalili Yes aure ko haram ne ko kamanta ni mijin mace hudu ne TJ yace nasani but inasonjin dalilinka na neman aure Cikin rashin damuwa yace sabida nasamu test dita kuma ta dace da kalar matar da nakeso Jinjina kai yayi yace ah lalle Alamin yakamata ka farka idan bacci kake Amma mezakayi da wannan yarinyar wlh gara ka natsu ka rungumi matarka yafimaka,ni har ina maka murna nadauka komai ya wuce kundaidaita kanku sai ka tsiro da wani zance kuma haba Papa yace to ubana barin qarqare maka sabida banason dogon magana Kasan Allah wannan auren babu fashi idan bazakasa albarka ba just chup(kawai kayi shiru) TJ yafahimci wanda yayi nisa baijin kira sai yace hakane toh Allah ya sanya albarka yasa ayi damu Papa yace ahaa yanzun naji magana tunda kabi hanya next week tare zamuje TJ yace a ina take da zama? Yace sunanta Juhaina kuma a kd take da zama Nan suka wuce gidasu TJ suna tattunawa ahanya Cikin sati biyu TJ yagama shigarda kansa awajen khairy kuma yasamu karbuwa awajenta Dan yafada mata bada wasa yakeba zai turo iyayensa Amma taqi amincewa sabida karatunta Yace indai maganar karatune ya amince taci gaba agidansa Cikin qanqane lokaci ya samu soyayyar ta dan TJ badai iya zanceba kuma yagaji da gararamba da mata sabida haka yaga gara ya rufawama kansa asiri yayi aure gashi agidama sun dameshi har mmansa tana cewa zata samo masa mata inhar bazai natsu ya fidda mata ba Hakan yasa dayaga khairy ta masa baxaiyi wasa ba gara kawai ya lallaba ya aureta ***** Wasawa watan fauziyyah 1 agidan momcy harta maida kibanta ta murmure sabida kula na musamman datake samu daga wajen momcy da daddy Kuma har yau ba labarin komarta gidan papa,sabida haryanzu papa bai samun fuska awajensu daddy danko gaisuwarsa basa amsawa Idanma zuwa gidan yayi haka zai qaraci zamansa ya tafi bamai cemasa cikanka Tin abin baidamunsa har yafara daminsa,ga gidan yamasa shiru idan yadawo office sai dai ya wuce wani wajen dan ya debe masa kewa Yauma kamar kullum ya taso office gida ya dawo amma sam sai yaji bai shaawar zama acikin gidan danko bakomai wannanar villager tana debe masa kewa ko masifan da walaqancin daya ke mata ma amma yau ba wanda zaima Cikin sauri yayi wanka ya shirya ya nufi gidan momcy dan ya basu haquri cos ya gaji da shareshi da suke akan abinda baima san dalili ba Cikin saa kuwa yasamesu dik afalon momcy suna ta hira harda fauziyyah Tana ganinsa ta miqe zata bar wajen ,daddy yace da ita ina zuwa daugther na Tace zan shiga dakine Daddy yace aa muna hiranmu ba inda zakije dawo kiyi xamanki Cikin sanyin jiki ta dawo ta zauna Shima qarasowa yayi ya zauna kusa da momcy yace ina yini momcy Yitayi kamar batajisaba,ganin bazata amsa ba yasa ya juya wajen daddy shima haka bai amsaba Nanfa yaji zuciyarsa tana masa zafi Cikin damuwa yace wai mena makune kukemun irin wannan punishment din, baku kulani baku amsa koda gaisuwata akan abinda bansan dalili ba Momcyne ta harziqo tace au bakamasan mekayiba lalle dasauranka toh kaje rananda kasan laifinka sai ka dawo Cikin fushi daddy yace lalle Alamin dasauranka yanzu dik abinda ka aikta bkasani ba wlh ka kiyayi duniya kabita ahankali Ka cuci yarinya ka zalunceta dik kace bakasan laifinka ba toh kashiga taitayinka kuma wlh kaguji sakayyah ranan da zata.... Kuyi manage da wannan ✍🏻Faty Mmn faty🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty August, 2017 3⃣5⃣ Kamaka dan wlh dik wadda ya dau hakkin wani Allah bazai barshiba Amma kai ko ajikinka sabida bakasan wannan ba Momcy tace kuma duk abinda ka aikata kaje kanka kayiwa bamuba tunda ka nuna bamu isa dakai ba Cikin tsukewar fuska yace wane irin baku isa dani ba kuma ,dan ransa ya soma baci agaban yarinya qarama zasu ajiyeshi suna masa shouting abanza Daddy yace to inba ka nuna mana cewar bamu isa dakai ba taya zaka ajiye matarka cikin yunwa wanda abanza da wofi na shaye2nka kake kashe kudi fiye da misali Au cewa tayi ina barinta da yunwa yayi maganar fiskarsa a murtuqe alamun bacin rai Momcy tace qaniyanka nace qaniyanka dake bamu muka gani da idanunba ko wlh papa ka kiyayeni zanci mutuncinka akan maganar nan dama na zuba maka idanu ne inga gudun ruwanka Cikin fushi shima yace dama akan wannan munafukan yarinyan tafada maku qarya d gaskiya yasa ko gaisuwata baku amsawa, dama nasan kunfi sonta akan ni shiyasa akan ta akemun abunda aka dama Bayan antauyemun haqqina an hadani da ita na haqura ina zaune da ita hakan baiyiba sai kuma anxo anacewa nayi laifi Daddy ne ya taso akansa yace kai har ka isa ka ajiyemu kana fadan magana san ranka Sabida ka kafi karfin kayi laifi ka amsa laifinka ko toh kayi kadan to ta inda yake shiga ba tanan yake fita nan ya wankeshi tass Ganin dagaske ran daddy ya baci yasa ya sassauta murya sa Yace toh yanzu me kukeso nayi muku Momcy tace ka amsa laifinka kuma ka gyara gaba dan bazamu lamunci tozarciba, yanzu idan iyayen yarinyannan sukaji wani irin kallo zasu mana Danma Fauziyyah yar albarka ce bata taba fada masu halinda take cikiba Sake qasa da murya yayi yace toh naji nayi laifi kuma bazan sakeba kuyi haquri Allah ya huci zuciyarku Daddy yace nadai fadamaka da gigin wasa kada ka kuma mafarkin maimaita abinda kayi Yana fadin haka ya miqe ya wuce side nasa rai bace Fauziyyah kuwa tunda suka fara magana take kuka Momcy tace kiyi shiru daugther share hawayenki bamai cimaki mutunci mu kyalesa tashi kije kiyi alwala ankusa kiran sallah Tana tashi momcy ta dubi papa tace son wannan yazama na qarshe kada ka kuma gangancin yin abinda ka aikata kaji nafada maka tunda aure ba hauka bane Naji shine binda ya fada ya miqe yace nawuce gida Allah ya kiyaye tace dashi kamun itama ta wuce dakinta ta kuma qudira azuciyarta fauziyyah bazata komaba har sai ranan da yazo da kansa yace ta koma *1month later* Papa nazaune a office yana duba xray da akayima wata yarinya a cinyanyanta,watanni uku kenan da yin accident dinta ta karye amma kashin yaqi hadewa shine aka turota wajen Dr Alamin Wayarsa ce ta fara rurin neman agaji Tsaki yayi kamar bazai dagaba dan yana aiki amma sai ya daure ya jawo wayar Ganin sunan mai kiran yasa ya ajiye file din hannunsa ya picking call din Hello yane toh shine abinda yafada Daga dayan bangaren akace normal fa ya aiki Yace aiki ba dadi wlh namagaji ga wani case da aka turomun mtss yaja wani guntun tsaki TJ yace eyyer sowwie shaanin aikine niyau tun 1 na gudu cos bama da wani aiki shiyasa Yanzun muka gama magana d popsy nace bara nafara maka albishir kafin muhadu Cikin kulawa yace inajinka mutumin Saida yayi wata dariya sannan yace next week fa su popsy zasujemun dambam tambayan aure Papa yace waw what a great news nayi murna sosai abokina dole nazo gida idan nataso office amma kuma natausaya maka zubewar girmanka TJ yace toh nagode sai dai kafin nawa ya zube nakane yafara zubewa tunda kaika fara Papa yace hhh dakenan aini yanzu free nake tunda nasamu su momcy suka riqeta awajensu tunda tayi rashin lfy ni yanzu ai banada matsala TJ yace kai wlh mutumina bakada kyau dama ashe bata dawo ba tun wancan lokacin toh wlh gara kaje kayi qaramar murya abaka matarka yafi maka Papa yace wucenan wlh tayi ta zamanta acan har qarshen rayuwarta danni this week ms kd zanje nafada ma queen zanturo dan aure nake buqataryi nan da 3months masu zuwa kafin wannan stomach pain din yamun illah TJ ya sheqe da dariya yace kaidai kajama kanka tunda da matarka kake daurama kanka ciwo Kai haba god forbid nahada jiki da wannan villager kuma mai zansamu kawai saina shigo bayan magrib TJ yace Allahu yahdika abonkina sai kashigo din Nan sukayi sallama inda TJ yake jiyema abokinsa kokarin barin damarsa dayake shirin aikatawa Ranan saturday papa ya shirya ya tafi kd wajen sarauniyarsa Kamar kullum haka suka sha hirar soyayyarsu nan yake fada mata zai turo iyayensa so ya tagani Murna wajen juhaina baa magana amma sai ta boye tace bakomai ta amince Yace toh idan ya koma dik yanda yayi dasu daddy zai sanar mata sai tafadama dad dinta ya basu ranan zuwa Washegari ya dawo bayan ya huta yamma lis yayi wankansa ya chaka ado cikin blue jins da red shirt sun masa kyau sosai Qafarsa sanye da red bufalinos Motarsa camry LE ya shiga kalar navy blue ya nufi gida Falon daddy ya wuce nan ya samu momcy sunashan fruit ita da daddy suna hiransu abin shaawa Zama yayi ya gaidasu sannan yasa hannu ya dauki grabes guda daya yasa abakinsa Shiru yayi sai yayi kamar zaiyi magana saiya fasa Momcy tana lura dashi sai tayi wani murmushi atunaninta yanason tambayar abashi fauziyyah ne kuma yakasa fada Daddy ma ashe yana lura dashi dubansa yayi da kyau sannan yace yadai babana bakin kannan kamar akwai magana amma kayi shiru Dan murmushi yayi yace umm daddy wajenka nazo Daddy yace toh lfy dai ko Sai da ya dan sosa kansa yace umm lfy lau daddy dama sai kuma yayi shiru Uhum go on inajinka daddy yace dashi Dama daddy akwai yarinyar da muka daidaita da ita ne shine nakeson ajemun tambayar aurenta Cikin sauri momcy ta dubeshi dan maganar yazo mata abazata kuma bata taba tunaniba Daddy ma haka yaji maganar watairi shiru yayi kawai yana kallonsa cos he is totatly speechless dan yarasa ma mai zaice masa nan take yaji wani irin baqin ciki ya lullubeshi Dubansa kawai yake cikin takaichi kafin..... ✍🏻Faty Mmn Faty [6:13AM, 8/19/2017] ‪+234 705 319 5189‬: 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty August, 2017 3⃣6⃣ Cikin takaici yace Alamin kana cikin hankalinka kuwa? Kodai kwakwalwar ka ta tab'u ne? Momcy tace wanne irin ya tab'u da hankalinsa sarai sai cin mutunci dayakeso ya mana Daddy yace ok, toh kabud'e kunnenka da kyau kajini idan har nina haifeka ban aminceba ban kuma yarda ba da wannan magana Idan kuma kaqi toh saidai kanemi wasu iyayen su shige maka gaba kuma bani ba kai that's all Nan da nan fiskansa ta canza damuwa qarara ya bayyana bude baki yayi zaiyi magana cikin sauri daddy yace i don't want to hear anything from u kawai katashi katafi tunda ba arziqine ya kawoka ba sha3 wadda bai san meke masa ciwoba haryanzun Rai bace ya mike ya fito motarsa ya fada ya nufi gida ranan kwana yayi cikin damuwa sabida haka ya kashe wayoyinsa baki 1 dan baisan mezaicema juhaina ba idan sukayi waya ***** Papa yana fita momcy ta dubi daddy tace lalle papa baijin magana ashe bai haquraba yana nan akan bakansa tunda har wani maganar aure zai tsiro Daddy yace kibarni dashi yanason yaga bacin raina ne fiye da zatonsa Cikin sati1 dik abun duniya ya dami papa Baijin zai iya rabuwa da juhaina gashi abinda daddy ya fada yarasa ta inda zai bullo ma lamarin Ko waya sukayi da juhaina ta tambayesa yatajisa wani iri cemata yayi baijin dadine kawai Yanzun haka yana zaune a office tunani yake amma yarasa mafita Qarar wayarsa ita ya dawo dashi daga dogon tunani daya tafi Murya ahankali yace hello baby Wani murmushi tayi sannan tace naam likitana, badai jikinba naji voice naka so cool haka Sake gyarawa yayi ya kwantar da kansa yace kedai bari my queen fever ne yake damina amma yayi sauqi Tace eyyer Allah ya qara sauqi n pls karage zama cikin AC da kuma shan abu mai sanyi dan nasan su zasu sakamaka fever Cikin jindadin yadda ta damu dashi yace insha Allah my queen i promised u zan rage Tace yawwa my king har kasa naji dadi amma kwana biyu ko waya mai dadi bamuyi Yace no kada kidamu am feeling better fa Tace toh shikenan sannan tasake qasa da murya cikin yanga tace am my king tinda kazo kacemun idan ka koma zakuyi magana da daddy kuma har yau bakacemun komaiba Rintse idanuwansa yayi ya bude ahankali gamida danne damuwarsa yace wlh tunda kikaga banfada maki ba akwai dalili Washegarin dawowana daddy yayi tafiya kuma two weeks zaiyi so idan ya dawo dik yadda mukayi zan sanar maki Cikin jin dadi da gamsuwa tace Allah ya dawo dashi lfy Ahankali yace amin ***** Afannin TJ kuma su dad dinsa sunje masa tambaya inda baffansa da baban khairy suka gane juna dan abokaine sosai Nan suka gabatar da abinda ya kawosu Baban khairy yace tabbas da baida niyyar auren khairy nan kusa dan yafison ta kammala karatunta kamar sauran yan uwanta Amma tunda yanzu abu yazama na gida ya amince amma dan Allah abarta taci gaba da karatunta Nan suka yi godia sosai har aka tsaida ranan biki nan da wata biyu Cikin ikon Allah lokaci na tafiya har aka fara hidimar bikin TJ Inda naira tayi kuka kasancewarsa dan fari agidansu itakuma auta ce a mata Sati guda ana shagali aka daura aure aka taho da amarya gidanta dake bauchi unguwar sokoto road Sai muce Allah ya bada zaman lfy Amin ***** Cikin watanni biyu nan papa hankalinsa ba akwanceba sabida kullum haka yakema juhaina hanya hanya akan maganar turowa gashi har yau baisami mafita ba Fauziyya kuwa tana gidan momcy har yanxu sai bikin khairy da sukaje dambam sukayi sati 1 harda momcy Auren TJ da kwana biyu juhaina ta kira papa awaya tana masa kuka akan ashe yaudaranta yakeyi ba sonta yakeba tunda gashi rabonsa da zuwa ma sati hudu kenan kullum yace aiki ya masa yawa idan baisontane ya fada mata yafi akan ya ringa yaudararta Haka da kyar yasamu ya lallameta ta haqura ya kuma mata alqawarin nan da 2weeks zaa zo maganar bikinsu Yau ya qudiri aniyar komawa wajen daddy akan maganar aurensa da juhaina dan gaskiya baxai iya haqura da itaba Yamma lis ya nufi gidansu cikin saa ya samu momcy da daddy afalo suna waya da aunty mabarukha akan tace zatazo nan da 1week dan yara sun sami hutun makaranta Sai da suka qare wayar sannan ya gaidasu adaqile suka amsa dan tun akan maganar fauziyya baya samun fuska Shima cikin daurewar fuska yace daddy nadawo akan maganar munefa Daddy ya dubesa yace wanne magana kenan Maganar auren danace maka ina sonyi ya fada kai tsaye daddy yace akan baka haqura ba kenan da abinda nafada maka Yace gaskiya daddy tana sona inasonta to akan me zaa hanani aurenta bayan halal ne ba haramba Daddy yace toh ai naga bazaka iya riqe mata biyu bane shiyasa tunda guda 1 ma ta gagareka ka riqe Cikin bushewar ido yace wannan fa ku kuka riqeta agidannan ba ninace tadawo nan da zama ba kuma koma mene ne dai kawai nifa nafada maku aure nakesonyi Momcy ta dubeshi cikin takaici da mamaki dan batayi zaton rashin kunyarsa da rashin mutuncinsa sunkai nanba Tace papa ka maimaita abinda kace Cikin rashin damuwa yace haba momcy, kumafa kun hada abinnan ne batare da neman shawrina ba Fisabilillahi ina zankai wannan qazamar qaramar yarinyan yar qauye wlh abin kunya ne innunata amatsayin matata, god forbid Amma ga juhaina wayayya mai ilmi amma kuce baku yabba ba, to nidai nafada maku waccar zabinkuce ba test dina ba so saikusan yadda zakuyi da ita Momcy takaici da baqin ciki su suka hanata magana Daddy ya nisa sannan yace naji batunka, amma saika ban takardan sakin fauziyyah sannan na amince da batunka Kawai daddy na saketa saki 1, shikenan toh yaushe zaajemun KD tambayar?...... ✍🏻Faty Mmn Faty [3:01PM, 8/19/2017] ‪+98 903 074 3573‬: 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty August,2017 3⃣7⃣ & 3⃣8⃣ Momcy salati kawai takeyi da jin maganganunsa,cikin kuka tace ashe papa har iskancinka yakai haka Kaje indai matan mazamanine saikayi dana sani Daddy cikin fushi yace kaje saina nemeka Papa yace zuwa yaushe kenan daddy Daddy cikin tsawa yace nace kaje saina nemeka get out i said Yana fita momcy tasaka kuka tana cewa ka haifi dan yafiqarfinka Riqota daddy yayi yace haba saudah, meye hakan Kirabu dashi badai duniyaba, kuma namaki alqawari watarana sai yayi kuka da hawayensa akan Fauziyyah sabida haka ki kwantar da hankalinki sannan nasan aminina zai fahimceni wannan bazai shiga tsakanina dashiba Share hawayenta tayi tace shikenan Allah ya kyauta yanzun mezamuce wa fauziyyah da iyayenta Daddy yayi shiru sannan ya nisa yace yanzu muje musameta mukwantar mata da hankali sai mufada mata inyaso gobe insha Allahu zanbar dik abinda nake natafi dambam nasanar da mahaifanta Momcy cikin jimami tace toh Allah ya kaimu daganan suka nufi dakin fauziyyah Zaune take tana shirya kayanta acikin akwati wadda aka wanke aka goge mata Taji sallamar momcy tana amsawa taga daddy ma ya shigo ,dasauri ta miqe sai taji zuciyarta na bugawa ganin daddy har dakinta Murmushin dole daddy yayi yace aa daugther kiyi zamanki muma zama zamuyi Komawa qasa tayi ta zauna tana sauraronsu Shiru sukayi nadan lokaci kafin daddy yayi gyaran murya yace Fauziyyah Dagowa kanta tayi tace naam daddy Yace kinsan cewa yana daga cikin rukunnan imani yarda da kaddara alkhairi ko sharri ko Qirjintane ya tsananta bugawa dakai ta iya amsawa dan sai taji magana ta gagareta Yace Alhamdulillah ,toh abinda zanfadamaki kidaukeshi kaddarace kuma mai wucewa Sannan yaci gaba da fadin kwanakin baya Alamin yazomun da wata magana wai yanason yaqara aure Cikin sauri ta dago kanta tana maimata aure azuciyarta Daddy yace toh nan nace banyardaba daganan baikuma tada zancenba sai yau dinnan yasake dawowa da maganar Fauziyyah dai tunani take aranta itakuwa me tayima ya Alamin ya tsaneta har haka baicin yayi watsi da ita baikuma isheshiba har kuma wani maganar aure zai tsiro Maganar daddy ce ta dawo da ita daga tunanin dake Yana cewa nikuma nace inhar bazai gaquraba sai dai ya sakeki inyaso yayi auren amma dake dan yaune shine ya furtamun kalmar ya sakeki Wani razana da tayi yasa momcy tayi saurin riqota Momcy tace kiyi haquri Fauziyyah tabbas papa ya cutar dake amma Allah zai saka maki kiyi haquri kinji Shiru tayi batace komaiba sai take ganin kamar amafarkine ko ido biyune Cikin dauriya tace sagaske kenan ya Alamin ya sakeni momcy tace kansa ya yima kiyi haquri Aifa nan taji wasu hawaye masu zafi suna mata zarya afuska Nan su daddy suka ta rarrashinta har suka samu tayi shiru Washegari ta tashi da matsanancin zazzabi wanda yasa daddy ya fasa zuwa dambam dan tare yake son sutafi da ita Kwananta biyu da taimakon Allah da rarrashi har suka samu ta sami natsuwa ta kuma dangana tunda har abinci ta karba taci sosai bakaman kwanaki biyun da suka wuceba Ranan kwana na uku da faruwar alamarin daddy yace fauziyyah ta shirya sutafi dambam Hakan ko akayi suna isa direct gidansu fauziyyah suka wuce Agida yasami Abba dan yamasa awaya akan yana tafe Afalon Abba dik sunyi shiru shida daddy dan maganar tazoma Abba abazata Cikin damuwa daddy yace wlh nibansanma wacce kalma zanyi amfani da itaba wajen baku haquri Abba ya nisa yace kada damu nafahimce komai kuma wlh ni bandauki zafi da maganar nanba bakomai Allah yasa haka shiyafi alkhairi ka kwantar da hankalinka aminina maganar yara bazata raba tsakanina da kaiba Daddy yace nagode nagode Allaha bar zumunci sai dai kuma ina neman alfarma awajenka Abba yace tsakaninmu kawuci haka fadi komeneneshi inhar baifi qarfinaba Daddy yace inason nakoma da fauziyyah amma baxata cigaba da zama awajenaba sai nan da wani lokaci kafinnan nacika alqawarin dana daukarma zuciyata Nan da kwana hudu mabarukha zata zo kuma sati daya kacal zatayi ta koma dan mijinta zaiyi tafiya zuwa Australia Toh inso sutafi tare da fauziyyah ta koma makaranta acan wajenta Shiru Abba yayi kafin yace bakomai Allah ya shige mana gaba damacan ai baa gabana takeba Cikin farinciki daddy yayi tayiwa Abba godia sannan suka shiga ciki ya gaisa da mama Sannan yafito ya nufi fada akan bayan sallan laasar zai dawo sutafi Fauziyyah kuwa tun zuwanta mama take kwakwarta akan anya kuwa lfyrta kalau amma haka taqi fada mama maike faruwa dan har yanzun sai tanaga kamar bahaka bane yayane itama dai batasan yadda zata kwatanta abinba Abbama daya shigo shiru yayi baice komaiba har daddy ya dawo Abba ya kira fauziyyah ya mata nasiha sosai sannan yace kuma tare zasu koma da daddy Harga Allah ranta baisoba amma haka ta haqura ta bishi Bayan suntafi sannan Abba ya mayarma mama abinda ya faru Nan mama tace batasan zancenba ita atafam saidai adawo mata da yarta tunda abin walaqancine Ita dama tajima jikinta yana bata ba lafy fauziyyah takeba Da kyar da nasiha Abba yashawo kanta ta haqura dan yasan zuciyar iyaye mata da rauni take shiyasa bai fada mata ba sai bayan sun tafi ya kuma godema Allah daya bashi ya mai jin maganarsa Bayan dawowarsu fauziyyah da kwana hudu aunty mabarukha ta zo bauchi ita da yaranta uku dik maza Ranta ya matuqar baci da taji labarin abinda ya faru Daddy yace sabida haka nakeso kitafi da fauziyyah wajenki kisama mata makaranta ta koma daga naira 1 zuwa biliyan 1 zan kashe dan fauziyyah tasami ingantaccen ilmi Aunty mabarukha tace tace insha Allahu daddy namaka alqawarin kula da fauziyyah yadda ko kai idan kaganta sai kasan lalle mace ce mai ilmi Kuma gashi dama yanzun ne zaa koma first term so kafin hutun ya qare zaa sama mata lesson teacher Shikuma yaje Allah ya shiryeshi amma saiya ga sakayyah Cikin jin daddy yace haka nakeso Allah ya taimakemu Momcy ta shigo nan suka cigaba da tattunawa Sannan ta kira fauziyyah tafada mata tare da aunty mabarukha zasu tafi Taji dadin hakan dan gaba daya zaman bauchi ya fita aranta Ana gobe zasu tafi taroqi momcy tabarta taje gidan aunty niima da kuma gidan khairy Momcy tace sai dai driver yakaiki gidan khairy amma niima kanma zataxo anjima Sai dayamma sannan ta shirya ta tafi gidan khairy Agida tasamu TJ sai taji kamar ta koma dan bata qaunar abinda zai kuma hadata da ya Alamin so dataga TJ sai taga kamar tare data gansu Bayan sun gaisa TJ yace ashe abinda yafaru kenan Allah yasa haka shiyafi alkhairi amma gaskiya Dr bai kyautaba sam Murmushi tayi tace lah bakomaifa nihakanma yafimun TJ yace idan da rabo saiku sasanta kuma shimuke fata Fauziyyah tace hmmm kaidai mubar maganan nan kawai kada na furta abunda ba kyau Shiryawa yayi ya fice nan yabarsu da khairy suna tada abinda ya wuce Sai gab da magriba driver ya dawo daukarta Sai anan take fadama khairy tazo mata sallama ne amma ta roqeta ko mujinta kada tafadawa gashi gashi Khairy tamata fatan alkhairy ta rakota har bakin mota sannan ta tafi Washegari sukabi jirgi sai birnin tarayya Abuja ***** *2weeks later* Papa yana kwance yana tunanin sati biyun da yayima juhaina alqawari ya cika kuma har yau daddy bai nemeshiba sai yaji qarar wayarsa Sai daya tashi zaune ganin sunan maikiransa amma haka ya bude idanunsa da toka ya dau wayar yana cewa Barka da yamma Abba Yawwa Alamin ya aiki Yace lfy lau Abba Abba yace batun yarinyar da kake so nakira inji awanne gari ko unguwa take dan insha Allahu jibi zamuje maka tambayar Dik iskancinsa dayaji kunya ta kamashi cikin sanyin murya yace akaduna take Abba yace toh inyaso kashirya gobe zamu shigo bauchi nida Alhaji Sabo qanin daddyne inyaso jibin sai mu wuce tare dakai harda daddynma Toh nagode Abba Allah ya qara girma Abba yace bakomai nan sukayi sallama ya kashe wayar kuma yayi hakane dan jin irin furucin da daddy yayi akan shi baruwansa da wannan auren Da kyar su Abba suka shawo kan daddy ya amince suka tafi kaduna tare Atare da papa suka tafi kaduna kuma anmasu tarba ta mutunci nan suka tsaida magana maganar aure nan da wata 1 kacal dan ko wani fanni ashirye suke Papa da juhaina suna zaune acikin garden din gidansu juhaina ta dubi papa cikin shagwaba tace my king Naama my queen ya amsa Tace umm ya maganar dakace kowa gidansa da banne ko inace bakacanzaba Murmushi yayi ya riqo hannunta yana duban idanunta yace ki kwantar da hankalinki Alamin nakine kekadanki Cikin rashin fahimta tace kamarya likitana fahimtar dani bakacemun kanada mata ba Yes amma dakenan yanzu single nake cos na yanka mata red card nata so kinga ni nakine ke kadanki Nan taji wani dadi ya mamayeta koba komai yanzu aikin dake gabanta ya ragu sai dai tayi qoqarin ganin bai dawo da itaba dan gaskiya batajin zata iya zama da Dr Alamin tana ganinsa da wata mata..... ✍🏻Faty Mmn Faty [3:01PM, 8/19/2017] ‪+98 903 074 3573‬: 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty August, 2017 3⃣9⃣ Washegari dasafe suka biyo jirgi suka dawo bh Gida papa ya wuce dan Abdu yazo daukarsa Bayan yayi wanka ya kwanta dan ya huta amma sai da yajima yana waya da queen nasa kafin yayi bacci Bashi ya tashiba sai wajen5 tukunna Cikin sauri ya gabatar da sallan laasar sannan kira TJ awaya ya sanar masa yana zuwa gidansa anjima kadan Sake wanka yayi ya shirya tsaf abinsa ya nufi gidan TJ Afalo yasamesa shida amarya suna zaune suna kallon wani film a setlite Fiskannan ba yabo ba fallasa ya qaraso ya zauna Nan suka kashe hannu TJ yana cewa ashe kana kusa kenan mutumin Yace no inafa gida nakira ka kawai dai ban biya ko ina bane Khairy ce tace ina yini ya Alamin Lfy lau ya amsa mata Tashi tayi ta fice kitche ta kawo masa ruwa da juice ,tana ajiyewa ta juya abinta daki dan ita haushi papa yake bata ko yaushe fiska kamar an aiko masa da saqon mutuwa Ya hanya toh TJ ya tambayesa Umm normal fa kuma albishirinka Toh goro fari tass ma kuwa Papa yace anfa tsaida magana nan da 1 months juhaina tazama mallakina Kashe hannu sukayi TJ yace shege mutumina kace kawai komai ya kankama Atare sukayi dariya papa yace kai dai yanzu kawai shiri zamu fara dan kasan dole muyi party kalakala sabida baqin da zasu zo TJ yace tabbas yanzu dai muje kaci abinci dan nasan kyar inkayi lunch ma inyaso sai muduba muga yadda abin zai kasance dan bama da enough time Papa yace wlh kuwa kaman zanbiya Eatry sai nace barindai fara zuwa nan sai mufita tare TJ yace ai zanci abinci saiga wayarka nace toh barin bari saika zo sai muci Ok muje to,dinning suka qarisa Ya bubbude masu wamers yace bismillah Dr Aroma ne yaji ya bugi hancinsa ga kuma ya birgesa a ido nan yadauki plate ya debi white rice wadda taji vegetables da chips sai stew wadda tasha naman dajajatun Spoon 1 yakai bakinsa yaji abincin yamasa 100💯 Shiru yayi kawai yanacin abincin dan har yamafi na resturant dayake zuwa cin abinci Gagara haqura yayi yace man wai a ina kuka sami mai aiki wadda ta iya girki haka Murmushi TJ yayi yace haba wuce nan nayi aure kuma nazo inacin abincin mai girki never Papa cikin mamaki yace kana nufin wife nakace tayi wannan girkin TJ yace yeah itace dan bamuma da mai aiki agidannan komai ita takeyi Shiru papa yayi yana tunanin wannan yarinyan itace ta iya abinci haka sannan gidan ko ina tsaf sai qamshi kawai , da atunaninsa mai aikice ta gyara gidan dan wannan tayi qanqanta tayi haka sannan kuma yar qauye inama tasan wani gyara haka Maganar TJ ce ta katse masa tunani yana cewa aikasan Allah nifa kullum sake godema Allah nakeyi Dan wlh bani da matsalar komai , gata da haquri ga tsafta dik abinda dik abinda nakeso shitakemun Shiyasa na shafama kaina ruwa na tattara dik wata sabga nafakata a gefe dan wlh yadda yarinyarnan takemun biyayya har kunya nakeji tasan halayena nada kuma kullum inaroqon Allah ya yafemun zunubaina dan da dan hali nane bazan samu ta gariba Papa yayi shiru yana sauraronsa axuciyarsa yace lalle ashe shima zai more tinda wadda ya auri qaramar yarinya ma gashi dik ya canza sabida kwanciyar hankali baran shida matarsa wayayya wadda ta mallaki hankalin kanta Nidai Mmn Faty nace lalle dasauranka papa dan abin badaga nan takeba wai andanne ma bodari kai Suna cikin hiransu wayar daddy ta shigo masa Hello daddy yafada bayan ya dau wayar Inaon ganinka yanzun shine abinda daddy yafada masa ya kashecwayarsa Alamin ya dubi TJ yace man zan wuce yanzun daddyne ya kira kuma yanason ganina Ok sai gobe insha Allahu zan shigo gida Harka fara fita kenan TJ yace no sai nanda two weeks zanje sayama khairy form din school ne Tabe baki yayi yace ok saika shigo na wuce Harbakin mota ya rakashi sannan ya tafi ***** Daddy da momcy suna zaune afalo inda papa yake gefensu azaune yayi shiru yana sauraron daddy Alamin ya kira sunansa Naam daddy ya amsa yana kallon daddy Daddy yace toh nakirakane dan inmaka godia ka kyauta sosai akan abindakayi Kaci nasara ko ,great ,welldone amma kasani wannan auren tinda kai kaga zaka iya toh kasani ba nairana ko daya da zai shiga ciki Saika hada masu lefe sannan ka tanadi wajen ajiye matar dan ina buqatar gidana Papa yace ok daddy wannan bamatsala bace zaayi komai yadda ya dace shikenan zan iya tafiya Daddy yace eh kana iya tafiya Bayan ya fita daddy ya dubi momcy yace saudah anya kuwa yaronnan yana cikin hankalinsa Momcy tace mekagani Yace gashi baiko damuwa da fushinmu baran yagane abinda yakeyi ba daidai bane Momcy tace Alhaji nifa abinda yasa kaga nayi shiru bana magana wlh nafiganin laifinmu akan na papa Daddy yace kamar ya laifinmu kuma Tace toh icce tun yana qarami ake tankwarashi amma mu dik abinda papa zaiyi bama tsawatar masa baran mu nuna masa kuskurensa Yanzu gashi yaxo yafi qsrfinmu tunda bamu isa dashiba Daddy yace wannan gaskiyane amma yanzukam lokaci yaqure sai dai muyi ta masa addua Allah ya shiryesa ***** Kwanan Fauziyyah biyar da zuwa abuja aka kawo mata lesson teacher Cikin ikon Allah kuwa tana gane karatun sosai dan dama fauziyya tana da ilmi Hankalinta akwance batada matsalan komai dan Aunty mabarukha ta maidata kamar qanwatta ciki 1 Cikin wata guda tayi wani kyau ta qara haske Gashi tasamu admission nan da sati biyu zata fara zuwa makaranta Yanzu bikin papa ya rage saura sati 1 hakan yasa aunty mabarukha ta shirya ta tafi bauchi amma ita kadai tatafi tabar su fauziyyah a gida A bangaren papa kuwa yagama dik wani shirin biki ,gidansa dake sokoto road ya dauki kamfani ya basu contract su ronobeting gidan Lefe kuwa nagani nafada aunty niima ta hada masa a dubai Aunty mabarukha nazuwa suka wuce kd suka kai lefe Biki ya rage saura kwana biyar aka fara hidima ta alfarma Ango da abokansa da yan uwansa kwanamsu biyu a kd ana shagali sai da aka daura aure aka dawo bh Nan aka dora daga inda aka tsaya Gidan amarya idan kashiga kamar kada ka fita dan kyau da tsari gashi anzuba kaya na alfarma Kwanan mutanen kd biyu suma suka tattara suka koma aka bar amarya daga iya sai halinta Papa kuwa kai na rawa yau gashi ga juhaina amatsayin mata sa miji Qarfe tara abokai suka rako ango gidansa ....... ✍🏻Faty Mmm Faty [3:02PM, 8/19/2017] ‪+98 903 074 3573‬: 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty August, 2017 4⃣0⃣ Shiru bakowa afalo sai qarar AC hadi da daddan qamshi Wani lumshe idanu papa yayi yana hasashen yanayin da zai tsinci kansa acikin daren yau Zama sukayi afalon farko yace bari ya dubo ta aciki Sai da ya wuce wani falo daganan yabi wani corridor ya shiga room nata Tana zaune adaki ya sameta , tasha lillbi daga kanta har qafanta Shigowa yayi yana wani murmushi na musamman dahaka ya qaraso har gabanta Cikin murya mai taushi yace my queen bazaki dago fuskarki naganiba baran ki amsa mun sallamar da nayi ko dai saina biya ne Wani sanyi taji har cikin ranta yadda yakirata cikin soyayya Ahankali ta dago kanta tanacewa aa my king barka da shigowa Nan papa yayi suman tsaye cos tasha kwalliya ta alfarma , wani yadine ajikinta mai kyallin gaske da kyau da tsada golding colour Ya mutuqar karbarta, face nata anqawatashi da kyakykyawar kwalliya ta musamman Ganin yadda yake binta da wani mayen kallo yasa ta jefeshi da wani shuumin murmushi Wadda yasa dakyar ya lalimo natsuwarsa yace my drling muje falo atare dasu TJ nake Cikin wata siririyar murya tace ok sannan tafara qoqarin tashi Hannunsa yasaka ya dagota inda itakuma dagantan tasake jikinta tafado akan chest nasa qirjinta ya mannu ajikinsa Sai ya gagara dagota yasake ma manna ta ajikinsa cos arayuwarsa yanason mace mai manyan booms Kuma yafison wannan abin fiye da komai ajikin mace hakan yasa juhaina take burgesa dan yaga tanada wannan kayan Sunkai 5mins ahaka yana wani shashshafata Itakuma sai wani ahh take hadi da wani irin numfashi mai sauti wadda yasake sauqeshi a network out of service Cikin wata murya qasa2 tace my king munbar baqifa afalo Sai anan yadawo duniyar zahiriyyah dan yama manta sam da wasu wai afalo Dagota yayi ya lakaci hancinta yana cewa it is not my fault,dik kece kika rudani Ashagwabe tace toh kayi haquri muje aidai yanzunkam muna tare ko Baice komaiba sai hannunta daya riqe suka fice TJ kuwa har yafara qulewa dan ajima kadan ya duba wach na hannunsa cos yanason komawa gida sabida babynsa ita kadaice danma basu da nisa sosai Yana cikin shawarin ko ya taboshi awayane yaji idan bazai iya fitowa ba su qara mai kawai sai yaji takun tafiyansu Qarasowa sukayi suka zauna akan kujera guda sun wani mnne ma juna kamar wani zai rabasu Nan suka gaisa hade da dan barkwanci agurguje sukayi addua kowa yacika ma rigarsa iska dan sun lura da angon ahannu yake Binbayansu yayi zai kulle falo nan yadan tsaya shida TJ bandaiji mai suka fadaba sai naga sun kashe hannu suna dariya Kulle falon yayi ya dawo ciki sai dai baigantaba Daukar ledar daya shigo da ita yayi ya koma dakinta Nanma baigantaba sai yaji qaran ruwa a toilet hakan yasa ya ajiye abin hannunsa ya fice dakinsa Wanka yayi ya shirya cikin wasu kayan bacci na alfarma farare tass dasu Sannan ya dawo dakinta ,azaune yasameta agaban mirror tana shafa turare ajikinta, sanye take da wata shegiyar rigar bacci milk colour iyaka cinyanta Tamatuqar yimata kyau sosai Juyowa tayi tasakar masa wani murmushi mai kashe zuciya Shima mayar mata yayi sannan ya tako ahankali har indabtake Rungumeta yayi ta baya cikin murya mai kama da rada Yace rigarnan tamaki kyau sosai yana yasa hannunsa yana wasa da hannun rigar Hannunsa ta riqe takai bakinta tana lashewa ahankali tace kaima kayi kyau harma ka fini Yadda tayi maganar irin dagaskennan shiya bashi dariya Yace kai darling wayace maki maza suna da kyau Juya idanuwa tayi tace umm gaskiya mafi yawancin maza basa da kyau but kai nadabanne king of my hrt Cikin murmushi yace hakane Nodding kanta tayi tace yeah Yace thanks my luvely wife muje muci abinci ko Dagota yayi tamiqe sannan suka nufi darduman dake gaban gado suka zauna Jawo ledar yayi kafin yace ah my darling pls helf us mana ki kawo mana plates n cups Shagwabe fiska tayi tace haba hooney nifa amarya ce ai yau ranan hidimanka ne Fiskanta ya shafa yace gaskiiya fa yakamata nizan feeding nakima barinzo Baijima ba ya shigo ya zauna a inda ya tashi Wasu gasassun kaji ne wadda suka gane kurensu acikin oven guda uku sai ya ciro daya ya saka akan plate Sannan ya zuba masu fresh milk a cikin cups Dubanta yayi yace my baby matso muci abinci ko Ashagwabe tace kamar kasan wlh yunwa nakeji cos rabona da abinci tun dasafe dan bani iya cin abinci idan ana hayaniya Yace eyyerh sowwie matso na feeding naki toh Hannunsa yasa ya yago tsoka mai laushi yace umm Miqo bakinta tayi ta amsa maimakon ta sake masa hannu sai tasa harshenta ta riqe masa yatsu tana wani tsotsa Hakan yasa yaji wani feeling na taso masa Ahankali ta saki masa hannun itama tasaka nata tafara cin naman hankali kwance kamar ba gobe saida suka qoshi tukun sanna ta matsa gefe Dubanta yayi yana cewa kin qoshi daiko Tace yeah am full Gyada kansa yayi yana shan fresh milk Niko nace oh inda ranka kasha kallo wannan wacce irin amarya ce marar kunya haka🤔 Tattara abubuwan yayi yakai kitchen sanna ya dawo dakinsa yayi brush kafin ya wuce dakinta Yana shigowa tana fitowa daga toilet itama da alamu brush tayi Ahankali ya iso kan gado ya zauna kafin yamata nuni da hannu akan tazo wajensa Cikin salo ta tako har wajensa Hannunsa yasa yajawota tafado kansa Baice da ita komaiba sai mirginata da yayi ya juya ya kai bakinsa kan nata yana wani shafata Nanfa ya tayar mata da tsumi nanfa tafara tsotsar bakinsa kamar ta cinyeshi Hannunsa yakai yazame hannun rigarta saime sai kuma yaji bra namma baiyi qasa a quiba ya samu ya cireta dan burinsa bai wuce yasamu ya kai hannunsa kan abinda yafi soba Ga mamakinsa sai yaji abu kamar na wasan yara Dago kansa yayi ya kalli qirjinta da idanuwansa da suka fara canza launi sai dai tabbas abinda yaji haka yagani Ganinsu yayi basuma kai na fauziyyaba ashe batada qirji shine take saka bra na acuci gara Sai yaji zuciyarsa tamasa wani iri amma dake amaryace sai yakai bakinsa kawai yacigaba da shan shaaninsa Dik sun fice a hankalinsu sai romancing junansu suke cikin dabara yakai hannunsa yakashe fitilar dakin sai deem light kawai ya bari Cire kayan jikinsa yayi kafin itama ya rabata da nata rigar da dama tagama zamewa Abinka da sabon shiga har wani rawa jikinsa yakeyi nan yafara neman hanyan shiga Amma me aliqe tsaf wani irin shauqi kawai yakeji inda juhaina kuwa taketa wani irin nishi dayake sake tayar masa da hankali Aifa nan daya dan saka qarfi kadan sai yajishi zurum ya shige ashe saman ne a kulle amma cikin abude yake Nan yaji wani irin zafi acikin zuciyarsa dik da baitaba kusantar mace ba amma yasan cewa budurwa ba haka takeba to kenan juhaina ba cikakkiyar budurwa bace Tambayar da yayi wa kansa nan yaji kamar ya tureta gefe ya matsa dan baqin ciki amma me sai yaji tasake qanqameshi alamun yaci gaba da abinda yake Cikin baqinciki da fusatar zuciya ya samu ya raba jinkinsa da nata ya miqe ya bar mata dakin tsabar takaici ko kayansa bai tsaya dauka ba baran yasaka Yana fita juhaina tace na shiga uku ni juhaina yanzun ashe hajiya yar ficika mai da tsohuwa yarinya kudi na taci bayan tamin alqawarin wannan hadin bazai taba ganewa ba yanzun ya zanyi ai kawai saita fara kuka Dan tarasa mafita kuma tasan dik abinda zata fada bazai yadda ba Har asuba idanunta biyu tana ta tunanin wacce hanya zatabi domin ganin tashawo kan Dr Alamin ya yarda da abinda zata fada masa ....... ✍🏻 Faty Mmn Faty [5:20PM, 8/20/2017] ‪+234 814 477 8681‬: 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty August, 2017 4⃣1⃣ Ahankali tafara jin natsuwa sabida ta amince da shawarar da zuciyarta ta bata Amma dik da haka bata daina zullumiba , tana nan zaune har wajen6 kafin ta tashi taje ta watsa ruwa ta fito tayi sallah Sai da gari yadanyi haske kafin ta sake wanka ta yi kwalliya sosai Tasaka wasu riga da wando masu kyan gaske, ta feshe jikinta da turaruka masu qamshi Balaifi tayi kyau sosai,cikin bugun zuciya ta fito ta nufi dakin papa ***** Papa kuwa cikin tsananin baqin ciki wadda tunda uwarsa ta haifeshi bai taba jin irinsa ba ya baro dakin juhaina Dakinsa ya shiga ya turo qofar ko rufewa bai iya yiba Zama yayi abakin bed ya dafe kansa da hannayensa biyu Kallo daya zaka masa ka fahimci yana cikin matsanan ciyar damuwa Idanusa sun kada sunyi jajur kamar bushashshen gauta Tunani yake taya haka ta faru, juhaina ta yaudareshi ta cuceshi kenan Maiyasa zata masa haka haka ya dinga zancen zuci Dakyar har yasamu ya miqe ya dauki boxer yasa ajikinsa Amma zuciyarsa kamar zata fito waje yakeji dan baqin ciki Fridge ya bude ya dauko wine nasa, cikin sauri ya rintse idonsa lokacin daya tuno kalan qirjinta Daqarfi yace nooo nan yadaga kwalbar yayi firo da ita sai jikake tass ta fashe Haka ya dauko sigari shima gagara sha yayi gaba daya yarasa meke masa dafi fatansa idan mafarki yake Allah yasa ya farka yaga haka bata faruba Ahankali ya lallaba yaje ya kwanta ko zai sami natsuwa dan yama rasa meke masa dadi ga wani irin ciwo da mararsa ke masa Kwanciya yayi ya shiru yana riqe da mararsa yana kuma tunanin abubuwan da suka faru daya bayan daya Yajima ahaka wadda shikansa baisan har tsawon wani lokaci yakaiba kafin bacci barawo ya daukeshi Amma asuban fari ya farka sabida baccinma ba na natsuwa yayiba Jin har an shiga masallacin dake kusa dasu yasa ya yunqura ya tashi dan yayi sallah Wani dogon tsaki yaja lokacin daya tuna ashe sai yayi wanka kafin yayi sallah Wanka yayi ya fito yayi sallah kafin ya tashi ya gyara wajen daya fasa kwalba jiya Amma balaifi yadanji sauqin damuwarsa tinda mararsa ma ta daina ciwo Kwanciya yayi amma idanunsa biyu , dan baccin safen daya saba ma idan ba office zashiba yau ya gagaresa Yana kwance kamar daga sama yaji ana bude masa qofar daki Idanunsa akan qofar har ta shigo, ganin juhaina yasa ya juya kwanciyarsa dan ganinta sai yafama masa gyanbon dake daminsa Cikin sanyin jiki ta qaraso gaban gadon dayake kwance ta durqusa Cikin murya mai nuna tsantsar damuwa da tausayi tafara magana My king tabbas nasan ni mai laifice agareka da naboyemaka gaskiyan alamari ban sanar makaba Sabida gudun kada ka gujeni gashi kuma abinda nake gudun ya sameni Nan muryarta tafara rawa cikin kuka tace amma ya kamata katambayeni kafin ka yankemun hukunci Shidai yana dai jinta amma ko matsi baiba baran ya tanka mata Cikin kuka taci gaba da fadin Wannan halin da kasameni aciki badason raina baneba nima Tun ina jss wani ciwo ya tsiro mun agaba na shine akaini asibiti likitoci sukace sai anmun aiki awajen Sanadin wannan aiki sukace zan iya rasa budurcina, bayanda aka iya haka akamun aikin dan nasamu lfy Tasake fashewa da kuka mai tsuma zuciya, cikin sheshsheqa tace lokacinda maganar aurenmu ta taso saida mama tace nafada maka gaskiyar abinda ya faru dani amma sai naji tsoron kada ka rabu dani dan nariga da nakamu da matsanancin sonka Dan Allah Dr kayafemun laifin dana maka da ban fada maka ba Nan tadage taketa rusa kuka wane uwarta ce ta mutu cikin kirsa ta dago wayarta tana cewa barin kira mama nafada mata halin dana ke ciki danaqi jin maganarta ta turo ya muzammil ya kawo takardun aikin da aka mun kozaisa kayarda dani Dik maganar dake cikin kuka takeyi Tana saka wayar akunnenta sai taji ya wabce wayar ya wurgar akan bed cikin tausayinta ya rungumeta tsam ajikinsa Itakuwa ganin tarkonta yakama sai tadada lafewa tana cigaba da kukanta Cikin sigan lallashi yasa hannunsa yana shafa kanta Yana cewa is ok my queen kiyi shiru nafahimceki nima kiyafemun dana maki mummunan fahimta Dama nasan bazakitaba aikata abinda zuciya take tunaniba Maimakon tayi shiru sai sake fashewa da kuka tayi Wani irin tausayinta ne ya kamshi tabbas baimata adalciba daya bari zciyarsa ta amince da abinda ba gaskiyaba Ganin yadda take kuka ta gagara yin shiru kawai ya saka bakinsa acikin nata yafara mata salo na musamman Jin yadda yake bata wasu darusa yasa jikinta ya mutu murus har tayi shiru tana sauraronsa kawai Shikuma ganin tafara samun natsuwa yasa ya dora daga inda ya tsaya Ganin labari yafara sauyawa yasa na tattara nawa yanawa na fice na basu waje........ Pls kuyi haquri da wannan ✍🏻Faty Mmn Faty [5:20PM, 8/20/2017] ‪+234 814 477 8681‬: 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty August, 2017 4⃣2⃣ *3 hours later* Ahankali na lallaba nadawo dakin papa Atsaye naganshi gaban mirror yana daure da towel a waist nasa Da alamu wanka yafito, yana gyara suman kansa Ta cikin mirror ya hangi juhaina wacce ta bashi full attention nata , ta zura masa idanu sai kallonsa take Murmushi kawai yayi yaci gaba da abinda yake Sai da yagama shafe jikinsa tsaf da cream n spray sannan ya wuce wajen kayan daya ciro Black trouser ne da brown shirt, sun matuqar amsan jikinsa Dik abinda yake har yanzu idon juhaina na akansa Yana lura da ita amma ya kamar bai ganta ba saida ya qare shirin sa tsaf sannan ya tako ahankali har bakin bed inda take kwance cikin blanket Sunkuyo wa yayi saitin fuskarta , hura mata iskar bakinsa yayi afiskanta Cikin soft voice nasa yace my queen baki gajiya da kallona ne Sauqe idanunta qasa tayi cikin murya mai cike da shauqin so tace bani gajiya n kuma ban jin akwai ranan da zangaji da ganin kyakyawar fuskar mijina Cikin murmushi ya kai hannunsa yana shafa fiskanta yace kada kidamu my darling am all urs Qanqame hannunsa tayi tace thanks my luv thanks a lot Yace oh no my queen do not say that mana umm, u deserve morethan that, now kifadi mene kikeso kiyi break dashi Cikin shagwaba tace anything Umum kifadamun dai mene kikeso yanzun zan tura ayiyo mana take away Sake shagwabewa tayi tace toh abinda zakaci shizanci Yace umum my darling kifadi naki inyaso sai muci nawanma kada kizo bakisonshi Tace toh chips da salad nakeso N what? Ya sake tambayanta Tace shikenan Yace ok barin aika abdu inyaso sai naxo na maki wankan dan naga kingaji dayawa Yana fadin haka ya juya zai fita sai yaji ringing na wayarta Amma sai ta share kamar batajiba, shikuma ya zaci batajibane sabida ringing tone ba mai volume bane Harta katse bata dauka ba Yakai bakin qofa kenan sai yasakejin qarar wayar kuma batayi yunqurin dauka ba Atunaninsa ko bataga inda ya ajiye mata wayarbane shiyasa ya dawo baya ya dau wayar ya miqo mata yace gashi aunty safna na kira Amsa tayi cikin inina tace ko, to, thanks ta qaqalo wani murmushin dabai kai zuciba Yana fita kira na uku yakuma shigowa,cikin sauri tadauka har hannunta na rawa Daga dayan bangaren aka ce barka da safiya amarya, dafatan kintashi lfy Cikin murya qasaqasa tace haba munnir ya zaka kirani da sassafen nan baicin kasan da wuya idan mijina ya fita kuma da kaga kamin missed call daya ban dauka ba ai sai ka haqura tunda kasan dole zan nemeka Wata dariya yayi yace toh naji yanzu nayi laifi kenan Tace aa bawai nace kayi laifi bane ba amma pls kada kana kirana Nizan rinqa kiranka tinda alqawari namaka Yace toh naji amma dai saiki san yadda zakiyi dani nan da 1 week dan wlh bazan juri rashin kiba Itama cikin fada fada tace waime ke daminka ne munnir kabani time mana inafa sane dakai kuma wani plan nake son shiryawa yadda zaikasance kullum muna tare kuma gida daya Murmushi yayi yace yawwa tawan yanzu naji zance mai dadi Tace toh sai anjima idan nasami sukuni zankira ka anjima Yace toh bye miss u Ahankali tace miss u too sannan takashe wayar Nan tashiga tunanin hanyar da zatabi da munnir kada ya balle mata aure dan tasan zai iyah Tana cikin wannan tunanin papa ya shigo Ahankali ta yunqura zata tashi dasauri yaxo ya kamata yace barin taimaka maki kiyi wanka ko Murmushi tayi kawai dan gaba daya hankalinta na agun munnir wacce hanya zatabi ta kaucewa wayarsa Haka suka shiga toilet ya taimaka mata tayi wanka Itama shiryawa tayi cikin wando 3quater da wata qaramar top ta fesa kwalliya nan tyi dass da ita Tanagamawa papa na shigowa yace madam muje muyi break ko Murmushi tayi tace ok Qarasowa yayi ya manna mata kiss a forehead nata yace kinyi kyau my darling Kwantowa tayi jikinsa tace thanks baby Atare suka fito inda suka zauna afalo sukayi break cikin kwanciyar hankali Bayan sun karya maimakon ta tattara tarkacen takai kitchen na dostbeen ta zubar son samuma ta wanke na wankewa Amma saita ture su gefe gefe ta gyara kwanciyarta akan laps nasa Duban ta yayi yace my queen pls da kin daga wannan tarkacen anan mana ko Turo baki tayi cikin shagwaba tace wlh nagaji sosai ga hidimar biki ga taka shiyasa ko motsi banson yi Shiru yadanyi yace ok barin kaisu kitchen naxo na maki tausa ko zaki dan ware Yana shiga kichen sai yaga cups da plate na jiyama ba awankeba dan baimayi tsammanin ta shiga kitchen ba Hadasu yayi ya wanke sannan ya fito Yana zama ta matso shi sosai tace yanaga kajima yace umm na dan gyara wajen ne shiyaa Tabe baki tayi tace ok Nan yadan fara matsa mata qafa ammafa ina juhaina saita canza layi dan ita bata gajiya da wannan lamarin nan suka tattara sukayi bedroom nasa acan suka gama shaaninsu kuma balaifi papa yana samun natsuwa dan baqaramin gyara tasha ba kawai dai waccan abinne da bai taba gyaruwa amma balaifi tana da niima Sai bayan azahar suka tashi nanma ya aika akamusu take away Da dare ma haka take away ya masu Haka haka har kwanansu uku da aure kullum dare da rana sai dai take away kuma idan sunci bazata iya gyara wajenva baran ta wanke abinda suka bata Daya mata magana sai tace itafa gara dik abinda suka bata asashi a shara inyaso asai wasu amma ita bazata iya wanke wanke ba Yace toh zai dauko mata mai aiki harta amince amma daga baya datayi tunani saita ce bataso ba yanxu ba Afannin munir kuwa tace ranan friday ya shigo bh ya kwana a hotel inyaso ranan saturday sai ya qaraso gidanta kafinnan dr yana gida Nan ta shirya masa plan nata Kwanan su shida da aure amma gaba daya papa ya kasa gane juhaina wacce irin mata ce Komai ba ruwanta bata shara bata wankewanke bata girki ko daidai da rana daya bata taba tunanin ta shiga kitchen tamasu girki ba Haka baruwanta da gyaran daki abinta sai dai toilet kam zata wanke tsaf ta fesa wanka da kwalliya koyaushe tana qamshi abinta Ga danbanzan son yawo kullum itakam sufita suje nan suje can Amma bata taba zuwa gidan momcy ba koda yamata zancen sai tace bayanzu ba Washegari saturday wajen 12 bayan sun karya suna zaune afalo sai juhaina ta dubi papa tace my king anjima kadan wani cousin nawa zai zo fa Yace ok wane kenan Tace sunansa munnir yasamu admission anan ATBU Papa yace ok amma baki taba ban labarinsa ba Tace umm mamarsa qanwar daddy ce Yace toh badamuwa sai ya shigo Bada jiwaba kuwa aka norcking qofa Papa ya tashi ya bude ganin saurayi matashi amma bazai kai papa ahaifeba yasa papa yagane shine munnir Hannu ya miqa masa da murmushi yace barka da zuwa Yawwa barka dai ya fada suna shigowa cikin falon Da murmushi afuskarta tace yau malam munnir ne agidana Shima da murmushi afiskansa yace nine dai amarya ba kya laifi Tashi tayi ta kawo masa ruwa da juice harda snacks da papa yasaya masu sabida baqi Ganin yadda take wani rawar qafa da baqon daga zuwansa harta kawo masa ruwa ya fahimci lalle baqon yana da muhimmanci awajenta Nan suka rinqa hira inda takecewa yaushe zaku fara lectures ne Tabe baki yayi yace wlh nifa kamarma na haqura da school dinnan Juhaina tace mai yasa kake yin hakane munnir yanzu wannan shekara na uku fa kenan kanasamun admission amma sai kayi wasa tomeye dalilin daxaka bar school din Yatsina fiska yayi yace nifa kinsan barin iya zama acikin school ba So inda zamu samu renting din kuma wai lokaci ya qure dik ankama Sai wani waje da aka nuna mun shikuma gaskiya bai munba so kawai gara na haqura Juhaina tace lalle ma akan wajen zama sai ka haqura da karatu dama dai bakason ATBU Yace ahto ba sunqi sukai mutum wajeba sharp2 yaqare ya dawo Juhaina tace aikaine baka nuna kanason karatun da gaskeba shiyasa amma badamuwa indai wajen zamane zamuyi magana da my king Anan sukaci abinci rana sannan ya tafi wajen laasar Da daddre juhaina tana kwance ajikin papa sunyi shirin bacci Ahankali tace my king Naam baby na akwai damuwane Daga kanta tayi alamar eh Cikin sauri yace damuwa kuma wacce irice baki fadamunba Marairaice murya tayi tace wlh kaga munnir shine babba agidansu kannensa mata ne acikin su daga wacce yanzu take service sai wacce take shirin gama skull amma shi yaqi yadda da karatu sai yanzun nema aka samu ya yarda Gashi shine namiji babba kuma shine hope din daddynsu Pls ka taimaka kabarmasa BQ mana yazauna kona wannan semester mana Shiru yadanyi kamar mai nazari Jin yayi shiru yasa juhaina tace pls mana my king kataimaka Yace ok badamuwa inyaso saiki fada masa gobe yayi parking ba matsala dik abinda kikeso nima inaso Cikin jindadi ta qanqameshi tace nagode nagode my king Daga nan suka lula duniyar maji dadi.... Wai wanene *MUNNIR*? Kubiyoni a next page dan jin wanene munnir kuma meye hadinsa da *JUHAINA* ✍🏻Faty Mmn Faty 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty August, 2017 4⃣3⃣ Washegari da safe juhaina ta kira munnir a waya tasanar masa saqon papa Da yamma kuwa lis sai gashi nan da kayansa ya dawo inda yasamu ansaka halliru mai wanki da guga ya gyara masa ko ina *WANENE MUNNIR* Mnnir shuaibu shine ainahin sunansa, iyayensa sun jima da rasuwa tun yana dan qarami Ahannun baffansa ya taso wato qanin mahaifin sa Tun tasowan munnir ya taso da rigima ba ta kadanba Gashi da son karyan kudi sai dai Allah bai bashi ba Tunda ya kammala makarantar sakandire bai cigaba ba sabida halin rashin kudi Daganan bashida aiki sai bin yaran masu kudi sune party sune biki ahaka ya tabe Watara sunje birthday party na wata budurwar abokin abokinsa anan ya hadu da juhaina lokacin tazo hutun qarshe wadda daga shi ta kammala karatunta Lokacin da juhaina ta kyalla idanu taga munnir sai taji ya birgeta har tana sonyin alaqa dashi Daga nan tazo tasameshi inda yake zaune nan ta nuna masa cewar tana sonsa Shikuma tunda yaganta ya fahimci akwai yayan banki atare da ita nan ya bada kai bori ya hau Tundaga ranan juhaina suka dinke da munnir itace kemasa komai na hidimar rayuwa Tasaya masa waya mai tsada Ta saya masa kayan sawa ta bashi kudin kashewa Har lokacin komawarta singapore yayi Bayan ta komane ashe tana da shigar ciki na wata daya, acan ta zubar dashi bayan tafadawa munnir abinsa ya farru Juhaina sosai takeson munnir dan araayinta idan ta tashiyin aure shidata aura haka shima ya amince da batun aurenta tinda shikam ya samu tana masa komai Bayan ta qare karatunta ta dawo nan suka dora daga inda suka tsaya itada munnir Lokacin da papa yazo mata da maganar aure bata boyewa munnir ba Amma shi saiya ce sam baisan zancen ba kuma ba auren da zatayi ta barshi Nan tace masa wane shi harya isa ya hanata aure dama itace tace data aureshi kuma tafasa sai yaya Duban bakida wayo yamata yace wlh intayi aure sai da yardarsa dan zaije ya samu saurayin nata yafada masa gaskiyar abinda ke takaninsu inyaso yaga yanda zatayi Sanin munnir zai iya bin diddigi ya samu inda papa yake yasa ta lallaba shi dan tana matuqar son papa sosai Dakyar tashawo kan munnir ya amince amma da sharadin suna tare koda tayi aure Haka ta amince akan bayan bikinta zata sama masa koda gidane inda zai zauna saiya dawo bh da zama harma ya fara karatu Wannan kenan ***** Bayan sallar magribah papa da juhaina suka fita basu jimaba suka dawo dama abinci sukaje sayowa Bayan sunyi parking Abdu yazo dasauri ko da akwai abinda zai shiga dashi ciki Cikin girmamawa yace barka da dawowa oga Aha Abdu shine abinda yafada yana miqo masa abincinsu adaqike yace gashi na hutar dakai fita Juhaina ta fito da leda guda uku ahannunta yayinda uban gayyar shima ya fito Har zata wuce sai papa yace my queen Juyowa tayi ta amsa da yess my king Inaga mu miqama munnir abincinsa idan munshiga ciki basai munfitoba ko Ok muje to tashi dashi Munnir kuwa tunda suka shigo yake tsaye ajikin window yana kallonsu cikin baqin ciki Dan wani haushin papa yakeji cos y rage masa jin dadi ganin sun nufo wajensa yasa cikin sauri yasauqe curtain ya koma kan cussion ya zauna yana latsa wayarsa Norcking suka masa Daga ciki yace yess come in Suna shigowa dasauri ya tashi cikin murmushin dole yace barkanku da shigowa Papa yace yawwa amma yana tsaye cos baxama zaiyiba Miqomasa take away nasa tayi tace bross ga abincinka sai da safe Allah ya kaimu yafada yana bin bayanta da kallo Nace sai kayi ai matar wani ce🙄 Bayan sun ci abinci papa ya dubi juhaina amma bada wasa ba yace my queen yakamata kifara dafa mana abinci tunda kinga yanzu ga munnir ma bai dace kullum muriqa bashi abincin wajeba Ganin yadda yayi maganar bada wasa ba ya kuma sha murr yasa tace shikenan Allah ya kaimu Washegari da safe ta dafa masu indomie Sai dai satisfactory haka sukaci dan bai wani test ba Da rana kuma haka aka kwaba white rice da stew dikda kajin dake ciki amma sam kasa ci sukayi dagashi har ita Sauran mutanen gidan kuwa banbi takansuba Ai daga kan dinning yace mata kada tamasu dinner tabari kawai dan yafahimci bata iya girkiba Haka sukaci gaba da zama ahaka inda azuwa yanzu yafara gajiya da halayenta sam Gashi bata kunyar idan yace tamasa abu tace bayanzuba Satin bikinsu biyu TJ ya kwanta rashin lfy fever mai tsanani har saida papa yaje ya saka masa ruwa agida da allurai Amma abinda ya birgeshi da gidan TJ shine tsaftar matarsa ko ina kyalkyal kamar baa takawa sai qamshi kawai dake tashi ta ko ina Gashi ya lura da tana son TJ sosai ba irin sonda juhaina kemasa ba tinda dik abinda yakeso shi take masa Agidan ya wuni ranan bayan tagama abinci ta kawo masu amma TJ sai ya gagara ci Papa kuwa haka yaci yaqoshi yana santi aransa har yana inama ace matarsa haka take Ganin yakasa cin abinci dik ta damu sai tambayarsa take mezaici adafa masa Yace tamasa faten irish potatoe da hanta da alayyahu Nan da nan ta daho ta kawo masa balaifi yadanci kuwa sai anan hankalinta ya kwanta Sai gab da magriba ya tafi yana fitowa wayar juhaina ta shigowa Doguwar tsuka yaja kafin yadau wayar dan Tun bayan laasar juhaina take kiransa awaya yaushe zai dawo Cikin jin haushi yace wai meyene kika dameni aidai zandawo ko ko ancemaki bata zanyi yana fadin haka ya kashe wayar dan wani haushinta yakeji yanzu dayaga yarinya qarama yadda ta iya komai da kula da miji Ita kuwa banda abiya mata buqta batada aiki Yana tafiya yana tunanin gaskiya dole dasake inma makarantar koyan girki da gyaran gida zata shiga sai dai tashiga dan zamansu ahaka bazai yiyuba Itakuwa tasamu dama suna sheqe ayarsu da munnir shiyasa ajima kadan ta kira taji koya kusa dawowa kada ya dawo yasamesu atare Amurtuqe ya shigo gida direct room nasa ya shige sai bayan yayi wanka sannan ya fito Juhaina ta dubeshi tana zaune afalo tana kallo tace wai lfy kuwa hooney kaketa bata rai Nakira ka awaya kana wasu magana gashi kadawo kuma ranka abace Yace eh kawai zamanmu ne yakamata mu gyara Gyara zama tayi tace toh kamar me kenan Yace yanxu ace ko girki baza ki iya yimana ba komai idan inason nagani da kyau sai dai inni nayi haba Kawai nayanke shawara zan maki register a school na koyan girki da kula da gida Dubansa tayi nan taji ranta ya baci wato raini ne yasa zai zo yana fada mata haka So kawai gobe zanje na mak........ Hannu ta daga masa tace heeyheey ya isa haka Alamin kul karkasoma wannan maganar Da mamaki ya dubeta yace ni kikecema hey har kina dagamun hannu Tace anfada maka din so what Kuma ko cemaka akayi mai aikice ni da zaka fara tsiro da wani abu aidai ciyar dani dolenkane Ko ance maka agidanmu inayin girkine har zakazo kanamun wasu surutai da shouting Cikin bacin rai ya dubeta yace lalle juhaina nikike fadama haka ba kunya Tace nice ma kai kajiko Hannu ya daga zai mareta sai yafasa Wata dariya ta sheqe dashi tace ya kafasa lalle da kamari mai tsada dan wlh ramawa zanyi tsaf ni banza bazata shani ba Ko ashaye kazo kada ka taba kwatanta dukana dan ni bazan tolarating nonsense ba Dubanta yatsaya yi dan baitaba tunanin tasan yana shan wani abu ba tunda boye mata yake Itama dubansa tayi ido cikin ido tace yess ko ka dauka bansan kana shayeshaye bane kawai kallonka nake so kada kafara abinda zai dameka kaji nafada maka tana fadin haka ta wuce shi tabarshi awajen Tsabar mamaki da bacin rai yakasa koda motsi kamar wadda aka dasa...... Wai ina labarin mutan Abujane kam🤔 Kubiyoni a next page domin jin labarin *Swt Fauzy* ✍🏻Faty Mmn Faty 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty August, 2017 4⃣4⃣ Ahankali ya wuce ya nufi room nasa yama rasa wanne irin tunani zaiyi guda daya Tun daga ranan ya shareta ya fita aharkarta shi atunaninsa zatazo ta basa haquri Amma har sukayi 5days ahaka itama bata kulashi kamar yadda bai kulata Abincima sai dai ta tura asayo mata Papa kuwa abin ya masa yawa wai suna yana da mata amma babu abu daya dayake amfanuwa dashi ata bangarenta Dan abinda yake samunma yanzu baisamu tunda sun kancake Gajiya yayi yaje yasameta ya lallaba ta suka shirya 2weeks later Yanzu hutun daya dauka awajen aiki ya qare hakan yasa juhaina ta bude sabon babin walawanta Sassafe kafin papa ya tafi aiki munnir yake fita amma yana fita zata kirashi awaya ya dawo Ta back door yake shiga wajenta yadda bawanda yake sanin shigarsa Kullum suna shan shagalinsu da munnir hakan yasa yanzu ko papa bako yaushe yake samun biyan buqatarsa Dan taringa masa hanya2 kenan aa daga tace batajin dadi sai tace bacci takeji Idan ya matsa mata sai tace toh bata cikin mood din wannan abin Gashi yanzu tamaidashi kamar ATM mashen sabida kullum acikin ya bata kudi take Ga yawon tsiya da koyaushe sai dai ta dauki motarta ta shiga gari Sau da dama haka zai dawo bai sameta ba Yau dama tun bai fita ba yamata kashedin kada ta fita ko ina idan yadawo office zasuje gida sugaida daddy baiji daddy ba Bayan ya dawo suka shirya sukaje basu jima ba ta dameshi da sutafi sabida yadda bata samu fuska awajen momcy ba haka aunty niima bata sake mata ba Bayan sun tafi aunty niima ta dibi momcy tace momcy wlh matar papa ashe bayarinya bace yanzu naqare mata kallo da kyau Cikin takaici momcy tace wannan ai idan bata girme masa ba toh saidai suzo saanni dan bai isah ya girmetaba Aunty niima tace wai ya labarin fauziyya ne kam nakai 3days banyi waya dasuba Momcy lfyrta qalau dazunma munyi waya da mabarukha tacemun tatafi makaranta Aunty niima tace Allah sarki Allah ya bata miji nagari yarinya mai haquri Momcy tace insha Allahu Allah zai canza mata da mutumin kirki Haka sukayita hiransu suna jajanta abinda ya wuce ***** Juhaina ce tsaye gaban papa ta riqe qugu ranta abace Fiska a tsuke tace wai Alamin maeke damunka ne dannace kabani kudi shikenan sai kafaramun kididdiga kuma kana dashi bawai baka dashiba Shima cikin fada yace ai banace bazan bakiba but i just want to know mezakiyi da kudinne ke kullum cikin abaki kudi kuma banga me kikeyi dasuba Ahasale tace idan bazaka bani bane kawai kafadamum bawai kana wani kwana ba Kallonta yayi dakyau sannan yace toh bazan bayarba ki kwata Ok is that what u said tace dashi tana wani turo qirji Yeah haka nace kin wani tsareni kamar wani danki kina turomun tsumma Kutt qirjinawa ne tsumma ta fada cike da bacin rai Adaqile yace toh meye acikin ido banda ruwa ni bani hanya kiga ina da abinyi Naqi nabaka hanyan marar mutunchi kawai kuma ahakan kake kwantar da kwadayinka ba Ya tsina fiska yayi yace eh arashin uwa ba Nan sukayi tsiya tsiya kamar zasu daki junansu Da kyar yasamu ya shige dakinsa ya kulle dan shakkar juhaina yake kuma ya tabbata idan ya daketa zata iya ramawa shiyasa bayi attempting dukanta Kwanaki na tafiya, watanni sun shude Haka rayuwa yaci gaba da tafiya tsakanin papa da juhaina Zaman lfy da kwanciyar hankali sun qauracem papa kullum yana yawon wajen cin abinci kuma itama dole ya kawo mata nata inba haka ba bayi da kwanciyar hankali Kudi kuwa ko yaso ko yaqi dolensa ya bata Abunda yafi daminsa yanzu yawo da ta qara couse akai yakuma rasa inda take zuwa tunda bata da yan uwa bauchi amma kusan kullum bata yini agida Munnir kuwa yanzu yayi sabuwar budurwa Dazaran juhaina ta bashi kudi ita yaje zuwa ya kashewa shiyasa kullum acikin tambayarta kudi yake Time to time kuwa yana zuwa kd yayi two weeks harma fiye da haka Yanzu haka mota juhaina tamasa alqawarin zata canza masa Itama can wajen yawonta tayi sabon kwarto shiyasa yanzu bata damu da mumnir ba Ita yanzu hanyar da zata samu ta koreshi take nema shiyasa takeson tacanza masa mota ta lallaba shi ya koma kd Wasa gaske yanzu aurensu ya doshi shekara amma shiru ko batan wata bata tabayiba sabida kwayoyin hana daukar ciki datakesha Dan bata shirya haihuwa yanzuba acewarta zata tsufa da wuri kuma ma ita bata shaawar yara dan wai takura garesu Ya zuwa yanzu dik wadda yake tare da papa zai fahimci akwai abinda ke daminsa kawai dai bai fito ya fada bane Amma acikin zuciyarsa yafara danasanin auren juhaina tunda bai qareshi d komaiba ***** Aunty mabarukha nagani tsaye ajikin mota da alamu fita zatayi unguwa sai dai kamar jiran wani abu take Fauziyyah ce ta fito cikin shiga ta alfarma wadda sai danayi da gaske naganeta Taqara haske taqara girma Wata arabian gown ce pusher pink wacce ta matuqar shan adon duwarwatsu masu kyallin gaske Ta rolling veil din rigan akanta hannunta riqe da wata waya mai dan banzan kyau Cikin sauri ta qaraso wajen aunty Tana cewa am sorry aunty nabarki kina jirana Aunty tayi murmushi tace no badai kin gamaba muje bazama mujima ba zamu dawo sabida kada su daddy sudawo daga islamiyya Ok ta fada tana shiga mota Gidan wata qawar aunty sukaje suka karbo wasu kaya tadawo daga dubai Bayan sundawo yara ma sundawo daga islamiyya suna hira afalo Aunty ta dubi fauziyyah tace Fauziyyah inaga tinda yanzu kina SS2 kawai kizana SSCE inyaso bazaki fasa zuwa school ba Idan paper yayi kyau sai munemi admission kawai Fauziyyah tace toh Allah ya kaimu Aunty tace inyaso idan anyi hutu bazuwa dambam sabida kisamu kiyi karatu sosai Cikin ikon Allah fauziyyah tana cikin shekaranta na biyu da komawa makaranta ta zana SSCE Kuma da ikon Allah papers nata sukayi kyau dan fauziyyah dagaske take karatu idan kuna magana da ita zaka dauka tagama university sabida yadda takware a turanci Kuma tana daukar shawara da nasihar da aunty take mata akan karatu Takan cemata kiqara maida hankali akan karatunki sabida kizama wani abu kema arayuwa kinga dai abinda namiji yamaki akan rashin karatu Hakan yasa ita kuma tayi alwashin sai tayi karatu mai zurfi Lokacin da paper suka fito dikkansu suka taho bh Daddy yayi murna sosai Sannan yace meye shawarin aunty Aunty tace yanzu dama sun sayi jamb form sun kuma sayi form na gwagwalada university Daddu yayi shiru yace jiya sunyi magana da mr khan wani friend nasa dake india Kuma yamasa magana akan asamawa fauziyyah gurbin karatu a jami'ar new delhi Kuma ya tabbatar masa wannan badamuwa zai trying best nasa yace atura masa takardunta Sosai sunji dadin shawaran da daddy ya yanke Kwanansu daya ta wuce dambam abinta dan bata kaunar abinda zai hada ta da papa Cikin watanni uku komai ya kankama na tafiyar fauziyya dan tasamu admission kuma agidan mr khan zata zauna dan abokin daddy ne sosai Ranan talata su daddy suka kaita airport dake lagos dan tacan zasu tashi Qarfe uku na rana jirgin su fauziyyah ya bar nigeria ya nufi india...[truncated by WhatsApp] [7:12PM, 8/26/2017] ‪+234 803 082 4581‬: 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty August, 2017 *I dedicated this page to Zainab Abdulmumini(Mmn Samha) n My Swt Sis Fauzy, Allahu ya barni daku Mmn Faty 😍😘* 4⃣5⃣ Dawuri ya dawo gida cos yana da sugery da yamma a asibitin daddy Akwai wani mutum da zaamasa aiki a spinal cord nasa Yana shigowa tin daga parking space ya gane juhaina bata nan sabida he did not see her car Key nasa ya bude qofa ya shiga ciki dan inda sabo ya saba da hakan Dik randa ya kuskure ya bar key nasa kuwa to zai zauna a gate jiranta Sabida rana daddaya ne zai dawo yasameta agida Room nasa ya shiga ya kwanta nan bacci ya kwasheshi sai pass 3 ya tashi Cikin dauri ya shirya ya fito sabida 4:30pm zai shiga aikin Fitowa yayi ya kulle dakinsa dan ya kuskura ya bari abude sai tamasa barna Amma ga mamakinsa bata dawoba ficewarsa yayi kawai abinsa Bashi ya fitoba sai wajen 7 sallah yayi sannan ya nufi gida amma sai daya tsaya a resturant yaci abincinsa sannan ya wuce gida Dagangan yaqi saya mata yace taci yawon taqoshi yau bazai saya ba Har lokacin daya koma gida nanma bata dawoba Tabe bakinsa yayi yaje yayi wankansa yayi sallah sannan ya fito ya kunna press tv yana kallon wani program da sukeyi Har wajen 9 sannan yaji shigowarta Gyalenta a hannu ta shigo falo Ganinsa azaune sai tayi kamar bata ganshiba zata wuce Keh daga ina kike da wannan daran yafada yana kallonta Ko cikanka bata ce dashiba zata wuce ta gefensa Cikin sauri ya riqo hannunta yace bada ke nake maganaba nace daga ina kike Hannunta zata fisge yayi saurin sake riqeta sosai sannan ya miqe tsaye Yace juhaina wai me kika maidanine dan iskanci ina maki magana sai kiqikulani toh inkinga kinbar wajennan sai kinfada mun daga gidan ubanwa kike at this time Wani walaqantaccen kallo ta wurga masa sannan tace daga gidan uban mai tambayar nake Nan take yaji xuciya ta debeshi watoma harshi zata zaga Aiko nan take ya daga hannu ya wanka mata mari mai kyau Yana sauqe hannunsa itama ta daga hannunta ta zabga masa mari tana huci tace kai har ka isa kadakeni to ko ubana bai dukana baran kai banza a banza ta fisge hannunta ta wucectabarshi Shikuwa mamaki ne da baqinci suka hanashi cewa komai ko ya tanka mata Wani zafi ne kawai yakeji yana taso masa daga kasan zuciyarsa kamarshi ace matarsa har tadaga hannu ta mareshi Tsabar bakin ciki nan take idanunsa suka caza launi suka qanqance Dakinsa ya nufa ya bude fridge ya dakko wine nasa ko takan cup baibi ba Ya dannan bakin kwalbar amma maimakon tamasa dadin sha sai yaji wani daci sabida yadda zucitarsa ke tafasa Nan take sai tunanin fauziyyah ya fado masa Yaune rana tafarko daya fara tunota tinda ya saketa Tunanin yadda yake nada mata duka yakeyi amma koda wasa bata taba tunanin fada masa magana mai muniba baran tarama Ya walaqanqanta ta son ransa amma yarinyar nan haka zata haqura sai dai tayi kukanta tayi shiru bata taba fada ma waniba Anya kuwa yamata adalci kuwa nan yaji xuciyarsa tasake quntata Kotana ina yanzu ko wani hali ta shiga lokacin daya saketa bada haqqinta ba Nan take zuciyarsa tafara bugawa da sauri sauri Nan yafara tuno irin yanayinta kyan fuskarta yanayin jikinta Tuno rananda yafara ganin qirjinta yayi nan take yaji wani kewanta marar misaltuwa yana shigansa Zuciyarsa take raya masa inama har yanzun itace matarsa ba juhainaba daya rungumeta tsakani da Allah da bai cutar da ita ba Nan ya tuno qamshin girkinta idan tana dafa abinci amma zuciyarsa ta cuceshi ta hanshi aminta da ita Cikin qunan rai yake zargin kansa da mai yasa tunda baiga wannan abubuwanba sai yanxu da bai masan inda takeba Nan wata zuciyar tace wataqilanma tayi aure abinta Damm yaji zuciysrsa ta buga wani zafi yasakejin yana mamayeshi har yana zufa dikda sanyin AC dake bugawa Haka ya ajiye kwalbar giyar dan bazai iyama shaba Yadda yaga rana haka yaga dare sabida tunani daya addabeshi ya kuma tabbatar ma kansa zuciya takaishi tabaro tunda gashi yau yarasa tudun dafawa Tundaga wannan ranan tsanan juhaina ya dasu a azuciyarsa amma haka yake zaune da ita ya kuma kasa saketa Hakadai suke zama marar dadi Sai abinda yafi daminsa wato yadda tunanin fauziyyah ya addabi rayuwarsa ba dare ba rana Wani matsanancin son kasancewa tare da ita yakeji At last ya tabbatar ma kansa sonta yakeyi Rasa mafita yayi yaje yasami TJ ya fada masa abinda ke faruwa TJ yaso yayi masa dariya amma ganin halin dayake ciki sai ya danne Yace toh wai bakada labarinta ne Papa yace banma san inda takeba ko agidan momcy ban sake ganintaba TJ ya nisa yace toh yanzu shawarn da zan baka kadage da addu a idan rabon kace tadawo gareka Nikuma zan tambayi khairy tunda yar uwartace dole nasan tana da labarinta inma aure tayi inma ko me nene zamuji Godia yayi ma TJ sosai dan har yadan sami natsuwa Amma da TJ ya tambayi khairy hanya hanya tamasa kawai taqi fada masa gaskiaya Shima haka dai yayima walawala ya qi sanar masa khairy taqi fada masa dan kada yaji haushinta Haka rayuwa tayi ta tafiya inda papa yake cikin wani hali yakumayi dana sanin abinda ya aikata abaya kuma har gobe fatansa Allah ya nuna masa fauxiyyah ya roqi gafararta dan yanxu yagane cewar alhakinta ya ke bibiyarsa Ba abinda ke qara daga masa hankali kamar yarda kullum sonta yake qaruwa acikin zuciyarsa Watarana ankawo wata yarinya asibitinsu tasamu matsala a guiwarta daga faduwa Aifa tun dayaji sunanta fauziyyah shikenan haka yaringa hidima da ita har aka sallamesu sabida yarda yake qaunar mai sunan Kuma yasama ransa dik ranada yasan inda fauziyyah take kuma bata da aure tabbas koza ayi yaqi sai an maida masa da matarsa idan kuma basu sake haduwaba yasan sontane zaiyi ajalinsa ***** Fauziyyah ta sauqa lfy, inda tasamu tarba na mutunchi awajen mr khan da matarsa da yaransa yan mata guda biyu Kwanan ta biyu da zuwa tafara xuwa makaranta tanajin dadin karatunta sosai gashi Amisha tana taimaka sosai akan abinda bata ganeba Cikin ikon Allah karatunta yana tafiya yadda akeso Da haka har tacinye shekarar farko *Bayan shekara biyu* Fauziyyah ce zaune tana hada kayanta cikin farin cikin sabida gobe zata koma gida nigeria cikin nasarar uban giji ta kammala karatunta da saka mako mai kyau Yanzu tazama cikakkiyar *PAMACIEST* Cikin shekaru ukun datayi sau biyu kawai taje nigeria Washegari jirgin qarfe 9 nasafe ta biyo sai gida Acan nigeria kuwa su daddy ne da momcy da su aunty mabarukha harda aunty niima sukazo taronta dan akwai liyafar da daddy ya shirya mata a nan abuja Jirgin na sauqa na hangota cikin jerin fasinjoji amma zaka rantse da Allah baquwace tazo daga india kuma zata koma sabida yadda fatarta ta murje tayi wani haske na musamman kyanta yasake fitowa Kallo daya zaka mata kafimci zallan wayewa atare da ita dan tana daga cikin jerin mata masu class Ko yadda take saqqowa cikin natsuwa kawai ya isa ya tabbatar maka cewa lalle wannan mace ce mai jida kanta Daddy kuwa murmushi kawai yakeyi Cikin sauri aunty ta qarasa ta rungumeta tana mata oyoyo Wani daddan murya naji ya daki dodon kunnena hausa takeyi amma kamar maiyin indianci sabida yadda harshenta ya juye Cikin farin ciki ta gaisa da kowa sannan suka nufi gida Da yamma aka gabatar da liyafa mai kyau acikin gida Sunsha hira sosai da daddare daddy ya kirata yace washe gari zasu wuce bh tare amma ita zata wuce dambam gida dagacan zai tura driver ya maidata abuja sai service nata ya fito sai tadawo bh tayi acan Haka koh akayi watanta daya a dambam ta koma Abuja Watanta biyu a Abuja service dinta ya fito amma jos aka turata nan daddy yamata cukucuku amaida ta bh Tsabar tanada daurin gindi ko camp bata shiga ba Sai byan an musu posting aka duba nata anturata teaching hospital na bh Ana saura sati daya ta dawo bh uncle salim qanin mijin aunty yazo da abokinsa Barrister Nabil Abdullahi gidan aunty mabarukha Wajen aikinsu daya a bh yanzuma wani aikine ya kawo su abuja kuma babansa shine commissioner for works n houses na bh Tunda ya kyalla idanu yaganta ya nacewa uncle salim shifa yaga wata balarabiya kuma tamasa Har saida ya kira aunty awaya yafada mata abokinsa dasuka zo tare yaga fauziyyah yana so kuma ya fada masa ta taba aure yace ko dik yaran duniya ita ta haifa yaji ya gani Aunty kuwa hakan yamata dadi nan take ta tura masa phone no fauziyyah Tunda yasamu no shikenan waya ba dare ba rana text ne meyene amma sam fauziyyah bata kulashi dan ba namiji aranta sam Ranan sunday ta taho bh dan monday zata fara fita aikinta na service Isowan yamma tayi lis dan basu taso da wuri ba hakan yasa tayi bacci da wuri **** Papa kuwa yau tun daya tashi yakejin zuciyarsa wani iri kuncine meye ne baima saniba gashi yana da aiki a office gashi akwai maganar da zasuyi da daddy kafin ya fita office Dolee yasa da wuri ya shirya ya taho gida daga can ya wuce office Fauziyyah kuma qarfe bakwai ta tashi tayi wanka ta shirya amma tayi ligh make up sai pink jambaki data goga a lips nata Kayan su na coppers tasaka ajikinta nan naqare mata kallo da kyau Rigat ta kamata sosai inda na fulaninta da suke a cike dam gasu atsaye suka cika mata gaban rigan hakama wandon hips nata da bayanta sunfito sosai dan ya kamata sosai Gaskiya wadda yasan fauziyyah lokacin tana gidan papa yaganta yanzu bazi ganeta sabida yadda tacanza komai najikinta ya canza ga wani kyau na musamman data qara Kallon kanta tayi tsaf a madubi sai taji kunya bazata iya fita waje ahakaba farar qaramar hijab ta dauka iya guiwa amma bata saka ba sai ta riqo ahannunta Nima sake kallonta nayi da kyau nan naga zallan kaman datake da *Arti matar Yash na cikin film din married again* Cikin natsuwa ta dakko yar qaramar jakarta mai kamar purse ta rataya hannuntabriqe da hijab Tana fitowa falo da momcy tafara haduwa bayan tagaisheta momcy tayi murmushi tace masha Allah kiyi maza kije wajen daddy sai kizo kiyi break ko Cikin muryarta mai dadi tace ok sannan ta mufi bangaren daddy Da sallama ta shiga cikin faraa ya amsa bayan ta gaidashi Yadan mata nasiha sannan ya miqo mata key din motarta sabuwa dal daya saya mata yace motarki tana waje Allah ya kiaye hanya ki kula da tuki Nan taringa godia sabisa baqaramin dadi taji ba Daddy yace kada kidamu jeki abinki kada kimakara Papa kuwa yana zuwa gida afalo ya samu momcy bayan sungaisa yace bari yaje wajen daddy Tace toh sannan ya wuce Momcy kuwa jin fauziyyah shiru gashi kada time ya wure mata yasa ta kwala mata kira Dauther kiyi sauri kizo kiyi break kada kimakara Fauziyyah kuwa ta fito tazo daidai kan steps da zata sakko falo taji kiran momcy Dama sauri take taxo ta nuna ma momcyn kyautar da daddy yamata Itama cikin daddan voice nata mai dadin sauri tace yess me arihoo momcy(ina zuwa momcy) Daidai papa yasaka qafarsa zai haura kan steps da zai kaishi side din daddy yaji wata murya mai dadin gaske cikin harshen indianci tana magana Saida yadan matsa baya data bugeshi dan cikin sauri ta wuce batama lura da mutum ba Papa kuwa ganin kyakykyawar mace kuma ba india yasa yabi bayanta da kallo amma dake tariga da wuce sai bayanta daya kallah Wadda hips nata yake masa gwaliyo Lumshe idanu yayi ya bude gashi ta buleshi da qamshin turarenta Cikin sauri ya riqe gini dan baisan yayi missing step ba Jiki a mace ya shige dakin dadi amma muryarta sai yawo yake masa akwanyarsa Bayan sun gaisa gagara haqura yayi yace daddy baquwa akayi agidanne Daddy yace baquwa kuma Papa yace eh kamar ma ba india ce kuma daga nan ta fito Wani murmushi daddy yayi yace aa kam indai wacce tabar nan yanzune sai dai qanwarka Papa yace qanwata kuma wacce qanwata nikuma inada qanwace Daddy yace qanwarka fauziyyah mana yar gidan Abbanku na dambam Cikin sauri ya dubi daddy yace Fauziyyah kuma itace ta fita anan Daddy yace yawuce wai itace mana amma bar wannan maganar ina jinka yadda abin zai kasance yasa na ce kazo da safe Ina papa hankali yayi gaba baimasan daddy yana yiba Saida daddy ya lura baima tare dashi sannan ya tabashi yace kana jina Alamin Cikin sauri ya firgita yace me kace daddy Wani murmushi daddy yayi wanda shikadai yasan maanarsa........ ✍🏻Faty Mmn Faty [7:13PM, 8/26/2017] ‪+234 803 082 4581‬: 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty August, 2017 4⃣6⃣ Daddy yace maganar bude asibitin nan ne dama najika shiru haryanzu baka fadi wani suna zaa sama ba sannan wacce rana ya dace sabida buga IV Papa dai yayi shiru yana jin dadi amma harga Allah dakyar ya tsinci kadan daga abinda yake fada masa Sabida hankalinsa da tunaninsa baya tare da daddy Cikin wani yanayi yace zanyi tunani akai zuwa gobe zan sanar maka Yafadi hakan ne kawai dan yasamu ya tashi awajen dan ya tabbata bazai samu natsuwa ba har sai yayi tozali da farin cikin rayuwarsa dan yana da good assurance batayi aure ba tinda ya ganta agida da wannan lokacin Daddy yace is ok sai najika toh Aiko daddy na rufe bakinsa ya miqe cikin sauri yana cewa barinje office Daddy yace Allah ya kiyaye hanya Yana tafiya ya amsa da Amin ***** Fauziyyah kuwa cikin sauri ta nufi wajen momcy tana murna Rungume momcy tayi tana cewa dekho momcy meri gari key (kalli momcy key din motata) daddy ne ya bani kitayani godia Cikin faraa momcy tace masha Allah, Allahu ya tsare hanya Amin ya Allah ta Amsa Momcy tace kije kiyi break kada kimakara Toh ta amsa sannan ta wuce dinning, dan kadan ta iya ci sabida murna tadawo falo tace zata wuce Har bakin qofa momcy ta rakota tana cewa ganan motar taki jiya dare aka kawota Allah ya tsare sai kindawo sannan ta juya ta koma ciki Itakuma qarasa wajen motar tayi sannan ta bude ta shiga tana jin wani dadi aranta Ahankali tamata key sannan tafara tafiya cikin natsuwa har bakin gate inda mai gadi ya bude mata gate ta fice Direct NYSC office ta wuce sabida akwai abinda zatayi acan kafin ta wuce asibiti ***** Papa yana fitowa yaga wayam bakowa afalo sai motsi dayaji acikin kitchen Leqawa yayi sai yaga momcy ce itakadai Ziciyarsa ce yaji ba dadi dan fauziyyah yaso yasake kallo Asanyaye yace na wuce office amma idan nadawo zan biyo Toh adawo lfy tace dashi sannan ya fice Motarsa ya shiga ya wuce asibiti driving yake amma hankalinsa na wani waje Tinani yake yanzu fauziyyah ce tadawo haka yarinyar da ya raina yanzu itace tazama big girl haka Ikon Allah ne kawai ya kawoshi lfy yana parking ya wuce office nasa Zaune yake amma yakasa tabuka komai tunani kawai ya addabi zuciyarsa har yafarajin yarasa maike masa dadi Ya jima azaune amma ko file daya baigama dubawa cikin sauri ya ture su gefe ya miqe Dan jin kansa yakeyi yamasa nauyi ga wani irin faduwar gaba da kunci dake damunsa Gara ya tafi gida ya kwanta kawai Wayoyinsa da key nasa ya zara ya fito Cleaners da masinja suna gaisheshima amma hannu kawai yake daga masu Yana fitowa ya nufi parking space sai yaga wata mota mai kyau kalar mata ta tsaya agefen motarsa Kafin ya qaraso sai yaga ta fito tana rataya jakarta Sake zuba mata idanu yayi tabbas fauziyyah ce amma badan daddy yafada masa ba bazai ganetaba Sai alokacin ya lura ashe kayan NYSC ne ajikinta tambayar kansa yake yaushe kenan haka tafaru Fauziyyah kuwa dago kanta dazatayi wazata hango yana nufota ya Alamin Tabbas shine dan bazai taba bace mata ba dik da yadan canza yaqara kyau yadanyi qiba kadan sannan daganinsa naira tazauna masa fiye da da Ahankali tasauqe idanunta tanajin zuciyarta tana bugawa da sauri sauri Nan take taji wani zafi azuciyarta dan bata qaunar abinda zai hada ta papa ko ahanyane Daidai da ya qaraso jikin motarsa amma ya qudira aransa zai mata magana dan bazai iyah ganinta ya wuceba Itakuma yitayi kamar bata ganshiba zata wuce kamar daga sama taji muryarsa wadda kodaga bacci tafarka bazata manceba Yan mata shine abinda ya furta yana kallonta Cak ta tsaya dan jitayi kamar ya caka mata wuqa wai yan mata Dagoda kanta tayi ta sauqe dara2n idanuwanta farare tas masu kamar madara akansa Nan yaji wani abu wadda bai san mene ne ba kawai yasamu kansa da lumshe idanuwansa yana tasbihi ga ubangijin halitta dan fauziyyah ta tafi dashi gaba daya Muryarta ta dawo dashi daga duniyar tunani daya tafi Cikin halin ko inkula da rashin damuwa tayi kamar bata sanshiba Ya tsina fiskanta tayi tana masa duban rashin sani tace konhei tum(wane ne kai) Kutt dan zaro idanu kadan yayi sabida mamaki wai harshine fauziyyah zatace bata ganeshiba Amma sai yadaure yayi wani qayataccen murmushi yace mera naam Dr Muhammad Alamin Abubakar(suna na Muhammad Alamin Abubakar) Ya tsina fuska tayi ta wani juya idanuwanta tace eyyerh sowwie am not talking with people that i dont know Tana fadin haka ta wuce abinta bata sake koda kallonsa ba Shiru kawai yayi yabi bayanta da kallo Cikin qunan rai ya bude motarsa ya fada yana tuna irin walaqancin da fauziyyah tamasa ta yankwanashi Afusace yafigi motar wadda dakyar yataka birki yabawa scurity pass sannan ya wuce ***** Juhaina ce ta dubi munnir tace wai saurin me kakeyi ne kamar wadda ba agidan zaka kwana ba Yace kinsan najima bangankiba wlh ina kewarki sosai muje ciki narage zafi Murmushi tayi sannan tace haba dai kaida zakayi 1 week me zai dameka kuma Dr sai yamma shida yadawo Yace ai har tunani nke next idan zanzo wacce qarya zamu masa tunda munce nazo gyara carry over ne Dariya tayi tace wannan mai sauqine tunda shi baho ne inba hakaba sai kace ba mutumin daya shiga ajin ABCD ba Komai aka fada masa sai ya yadda Shima dariya yayi yace nidai muje toh pls mana Riqe hannunta yayi suka shige bedroom nata Nan suka fara mashaarsu da suka saba Tsabar sunyi nisa basa cikin hankalinsu ko jin shigowar mota basuyiba Papa kuwa ko parking mai kyau baiyiba haka ya fito ya nufi cikin gida Ahargitse ya shigo falo dakinsa ya nufa Yazo daidai dakin juhaina harzai wuce sao yaji kamar nishi Saurarawa yayi da kyau sai yaji tabbas ba kunnensabane nishintane Cikin sauri ya bude dakin dan atunaninsa ko batada lfy ne Yana shiga yayi turus wani jirine yaji ya debeshi yayi saurin riqe qofar sabida abinda idanunsa ya gane masa Juhaina da munnir kwance haihuwar uwarsu suna aikata zinah Abinda bai taba tunaninba juhaina zataci amanarsa kuma ma da dan uwanta Su juhaina kuwa jin anbude qofa yasa cikin sauri suka juyo ganin papa atsaye yana musu wani kallo cike da baqin ciki har idanunsa sukoma jajaye kamar gaunta bushashshe Dasauri munnir ya tashi akanta itakuma cikin razana ta tashi zaune tanajan mayafi tana kare jikinta Ahankali yasamu nutsuwarsa ta dawo maida qofar yayi ya rufe da key sannan ya nufo su gadangadan tsabar tsoro ba juhaina ba hatta munnir jikinsa rawa yake Yana zuwa ya shaqo wuyan juhaina yace cikin kakkausan murya kifadamun wane ne munnir kuma meye atsakaninku Aifa cikin tsoro da firgita tace dan Allah kayi.... Wani gigitaccen mari daya zabga mata saida taga wuta shiya katseta Cikin tsawa yace wane ne munnir zaki fadamun da bakinki kosaina kasheki shegiya tsinanniyah macucuciya Allah ya isa tsakanina da keh wlh kinci amanata Ganin yadda kamanninsa suka sauya fiskarsa tayi jajur tsabar bacin rai Murya na rawa tafada masa tsakaninta da munnir tace amma kayafemun wlh bazan sake ba Bata gama rufe bakintaba ya saka hannunsa ya makata da gini nan tafadi a asume Munnir kuwa tsabar tsoro ganin yadda yayima juhaina saida ya saki fitsari ajikinsa Aikuwa da papa ya damqoshi yafara dukansa yana cewa munafiki kana zaune agidana kana zaluntata ashe ina tare da kwarto bansaniba Mari duka harbi haka yake masa saida kansa bakinsa hancinsa ko ina jini yake amma zuciya ta hana papa ya kyaleshi Hannunsa yasa yakamo gabansa da iyah qsrfinsa ya jawota ya murde wadda saida ya saki kashin azaba Hannunsa ya kama ya buga da jikin drower ji kake kass kass ya karyashi Axaba iya azaba saida yakasa motsi sannan ya kyaleshi ya nufi toilet ya debo ruwa a bucket Zuwa kan juhaina yayi wacce ke kwance asume ya sheqa mata Nan ta firgita ta farka aiko itama nan yahau jibgarta da waya yana harbinta Saida jikinta ya faffashe fiskarta ta kumbura tayi sumtum tsabar duka Tsabar azaba har saida ta kasa kuka cikin baqin ciki ya jawota har waje tana nade acikin zanin gado amma saida kamanninta ya canza dan ba dukan wasa ya mata ba Sannan yace tsinanniyah kada nafito nasameki kificemun agida na sakeki saki uku muna fuka Itadai batada bakin kuka ma bare bashi haquri Mai gadi ya kira yace suzo suna biye dashi har dakin juhaina yace su fitar masa da munnir agida su kaishi can waje Haka suka jawoshi kamar har sun kai qofa paoa yace ganan haqorinsa biyu kuhada dashi kufitamun dasu Suna fita ya nufi dakinsa yafada agado ya fashe da kuka.... ✍🏻Faty Mmn Faty 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty August, 2017 *Gaisuwa mai tarin yawa musamman zuwaga Members na Mmn Faty Novel Group, Ina matuqar jin dadin yadda kuke bada gudumawarku da nuna jindadin ku akan littafin BUDURWAR QAUYE nagode sosai Allah ya bar qauna 😘😍* 4⃣7⃣ Kuka yake mai cike da nadama, hawaye wani nabin wani haka suke zuba akan face nasa Zuciyarsa cunkushe da zallar dana sani akan abinda ya aikata abaya Tabbas yau ya tabbar alhakin iyayensa ne dana fauziyyah ke bibiyarsa Kuma ya qara daukan darasi akan bijirema iyaye ba abune mai kyauba tunda gashi yaga saka makon abinda bai taba tunani ba Wani irin nauyi yaji qirjinsa yamasa Kuka yake sosai har abin tausayi domin dik abinda mutun ya aika matuqar yagane kuskurensa har yayi nadama nagaske ba tuban baqin muzuru ba dole ya baka tausayi Sambatu kawai yakeyi yana cewa daddy, momcy, fauziyyah kuyafemun ashe gata kukamun na auramun yarinya yar mutunci kuma mai mutunci Amma son zuciya yasa na bijire muku yau gashi abinda yasameni wayyo kaicona kaicon halina dama duk masu hali irin nawa... Maganarce tasarqe qirjinsa ya cushe numafashi yafara masa wahalar fita Dakyar ya dauki wayarsa yafara kiran layin TJ TJ yana office saiya ga kiran abokinsa Hello man shine abinda ya fada yana daukar wayar Cikin wata raunanniyar murya datake nuna mai ita yana cikin wani hali Yace pls kazo gida kasameni ina cikin wani hali TJ baisan sanda ya miqe tsayeba cikin razana jin yadda muryar abokinsa take a hargitse Meyasameka??? Shine abinda ya maimaita harsau uku Ahankali papa yace TJ banida lfy juhaina zata kasheni kazo pls kataimakeni Afirgice TJ yace ganinan zuwa ganinan zuwa am on my way yana fadin haka ya suri key din motarsa ya fito cikin sauri yacema scretery nasa idan bandawoba zuwa 2 ka kulle office kawai Baijira amsar shiba ya fice cikin sauri da tashin hankali dan baisan yadda zai sameshiba Cikin gudun balai har ya iso gidan papa wani mahaukacin horn yake dannawa Maigadima saida ya tsorata dajin irin horn dake masa Aiko baibata lokaciba ya bude TJ yana shigowa ko cikkakken parking baiyiba ya hnyar cikin gida daidai qofar falo yayi turus ya tsaya ganin juhaina lullube da zanin gado tana rizgar kuka dan sai alokacin tasamu kuka yaxo mata gashi ya kulle qofa bare ko kaya tasama jikinta baran tasannayi Juhaina ina Alamin yake kekuma meya sameki naganki haka Gagara magana tayi sai da hannu ta nuna masa qofar falo Tura qofar yayi ya jita gam akulle bubbugawa yafara da iyaka qarfinsa dan abin yaqara bashi tsoro Papa yanajin bugun qofa gakuma wayar TJ tashigo masa yasa ya taso ya fito falo ya bude qofar Yanaganin TJ kawai saiya fada jikinsa yaqara saka kuka mai tsuma zuciya Cikin rudani TJ yace waime ke faruwane man kamin bayani mana kozanji sauqin abinda nakeji Sake qanqame TJ yayi yana cewa na cuci kaina na biyema san zuciyata na cutar da matata ta gaskiya na baqanta ran mahaifana yaugashi naga abinda bazan taba mantawaba TJ ma kawai saiyafara hawaye nafarko tausayin papa dikda baisan meya faruba amma yadda yaganshi a hargitse yana kuka da idanunsa tabbas babban abune Sannan murnan abokinsa ya gane gaskiya Share hawayen fiskansa yayi yafara lallashin papa da kalamai masu dadi har papa yayi shiru Sannan yafara bawa TJ labarin abinda ya faru yana furta abinda yagani sai da wasu hawaye masu zafi suka zubo masa Cikin tashin hankali TJ yakejin abin kamarca mafarki Nan ya fara tausan papa da banbaki akan ya kwantar da hankalinsa komai zai wuce Papa yace hankalina bazai kwantaba har sai ka kaini asibiti anmin test na HIV tukunna TJ yace insha Allahu babu abinda zaisameka ka kwantar da hankalinka Taya hankalina zai kwanta matuqar ina dauke da wani mugun ciwo wlh jujaina ta cuceni ta shiga tsakanina da fauziyyah dan bayadda fauziyyah zata dawo gareni ina halin jinya Tj yace ya isa haka muje asibitin inhar hankalinka zai kwanta dan yaga har numfashinsa yana samasama Amma kabar juhaina ta suturta jikinta kafin ta tafi Da kyar ya yarda yace amma kada yadawo ya sameta Nan suka fito TJ ya kalleta yace kitashi kije kisuturta jikinki amma yace kada yadawo yasameki gidansa yanafadin haka ya wuce abinsa dan dama papa ya riga da ya wuce Sai bayan sunfito TJ yace wanne hospital zamujene Ka kaini asibitin daddy shine kawai abinda ya iya fada Suna isa asibiti lab suka wuce Maaikatan wajen suna gaisheshi baiko amsaba yace subashi abin gwajin HIV kawai Damamaki kowa ke kallonsa cikin tsawa ya maimaita masu nan take suka miqo masa Alluraya dauka ya caka wa hannunsa nan take sai jini yazuba yafara zaman zullumi Bada jimaba saka mako ya nuna negetalive TJ dake tsaye agefe yace Alhamdulillah bana fada makaba gashi ai d answer is negetive dafatan hankalinka ya kwanta Shiru kawai yayi ya miqe dan baijin zai iya magana Tashin da zaiyi ya yanki jiki ya fadi sumamme Cikin razana TJ ya sumkuya yana kiransa amma ina baimasan yana yiba Cikin sauri aka kawo abin daukar marar lfy aka turashi sai emergency Nan suka bashi taimakon gaggawa har Allah yasa numfashinsa ya daidaita sannan aka maidashi dakin hutu amma dai bai farka ba tukun In hankalin TJ yayi dubu to atashe suke Sai a lokacin ya tuna yadauki wayar papa dake aljihunsa ya fara kiran momcy Bugu uku ta dauka tana cewa hello son Cikin natsuwa TJ yace ba Alamin bane Tijjani ne Momcy tace ayya ya khairy da mubeen (dansune wadda bai wuce shekara biyuba) Lfy qalau umm dama Alamin dinne bashida lfy yanzu haka muna asibiti Salati momcy ta fara tace mai yasamu papa kuna wanne asibiti Asibitin daddy muke naje wajensama bayanan Momcy tace eh yau bai fita ba amma muna zuwa yanzu Daddy ne ya dubeta yana cewa wai meya sami Alamin din Cikin damuwa momcy tace nima bansaniba kam Toh dauko mayafinki muje Suna zuwa suka shige inda aka kwantar dashi TJ suka sami yayi shiru yana zaune Bayan yamasu sannu da zuwa daddy yace wai meke faruwane kam Nan TJ yafada masu abinda yafaru yace shine dai sanadin sumansa Sannan TJ yace dan Allah daddy kuyafe masa wlh yayi nadama kuma yanzu damuwarsa qaruwa zatayi matuqar baku yafe masa ba Daddy yace hakane Allah ya yafemu gaba daya ya kuma kiyaye na gaba Dik suka amsa da amin Suna nan zaune ahankali ya fara motsi Kadankadan idanunsa suka washe yafara ganin komai tass Aiko yana ganin su momcy sai yafara hawaye zaiyi magana Daddy ya kamo hannunsa yace kada kace komai Alamin munyafe maka duniya da lahira saifatan wannan yazama darasi agareka Momcy ta matso kusa dashi tana shafa kansa tace ya wuce papa ka kwantar da hankalinka sannan matakin daka dauka akanta yayi daidai Allah yasaka maka sukuma Allah ya shiryesu Cikin jin dadi ya yunqura zaune yace nagode daddy na gode momcy nagode sosai Momcy tace sai mutafi gida tunda yasami sauqi Daddy yace muje amaidaka gida sai muwuce Girgiza kansa yayi yace bazan iya zama acikin wannan gidanba ni gida zan koma Momcy tace toh shikenan kutaho a motar tijjani inyaso sai kuje kadauko kayanka Ahankali ya miqe TJ na riqe da hannunsa har mota Momcyma gida suka wuce Sukuma suna zuwa gida basu tarar da juhaina ba Nan TJ ya hada masa kayansa suka fito sai anan yayi magana yabawa maigai key yace idan tazo kwasan kayanta ya bude idan tagama ya kulle ya ajiye key din awajensa Suna tafiya a mota ba mai magana acikinsu Papa ya kwanta ajikin kujera ya tallafe fiskarsa da hannunsa yayi nisa cikin tunani TJ yace haba man karage tunanin nan mana haka yanzu ai saidai ka godema Allah tunda kagane gaskiya sannan Allah ya toni asirin munafukai Cikin damuwa yake kallon TJ yace man damuwata fauziyyah tafi qarfina ta wuce tinanina fauziyyah ta nuna batama sanniba yazanyi wlh idan ban auri fauziyyah ba mutuwa zanyi sabida ina sonta sonda bantaba jin inayima wata ya maceba aduniya ashe juhaina ma ba sonta nakeba fauziyyah nakeso na yaudari kaina nan idanunsa suka sake kadawa sukayi jajur Cikin mamaki TJ yacecfauziyyah kuma a ina ka ganta Nan yafada masa iya abinda yasani da haduwarsu Tirqashi shine abinda TJ yafada dan yasan tabbas zaayi haka rananda papa ya komwa fauziyyah da sunan so Papa cikin damuwa yace komai ya jagulemun man,kyiu wati hai bahaa??? Kyiu kyiu (mai yasa wannan canjin yanayin maiyasa maiyasa) ya qarashe maganar kamar zaiyi kuka TJ yace komai zaidaidaita kaci gaba da addu a kakuma kwantar da hankalinka Maganar fauziyyah zamu zauna muga yadda zamu bullowa abin Da haka har suka qaraso gida... ***** Fauziyyah kuwa tana wucewa awajen tamanta da shafinsa dan sam baya gabanta sannan tunaninsa tsabar tsanan data masa batayi Qarfe uku ta iso gida sai dai bakowa su momcy basa nan Wanka tayi ta daura alwala Sai datayi sallan laasar sannan tayi kwalliya ta shirya cikin wata doguwar riga yar kanti lokacin da zata dawo nigeria tasayeta Coppee da milk tasha ado mai kyau Bata saka dankwaliba sai gashinta data kama da milk ribbon ta fesa turare tafito Tana zuwa falo taga momcy tadawo tace sannu da dawowa momcy Momcy tace yawwa kindawo baki samemuba munje asibiti ne papa bayada lfy amma ansallamesa ma Allah ya sauwaqa shine abinda ta furta albarkacin momcy Momcy tace naga motarki shine na leqa dakinki kina wanka Tace eh wlh sai danayi sallah tukun nafito Momcy tace kinci abinci kuwa Yanzu zanci ta amsa Kai daugther bakyason cin abinci ko mai yasa toh kije kici Toh ta amsa sannan ta wuce dinning taci abinci Falo ta dawo ta zauna kenan su papa suka shigo Aiko yana kyalla idonsa akan fauziyyah yaji wani sanyi aransa dan baqaramin kyau tamasa ba TJ ma haka yake kallonta da mamaki ya kuma jinjina abin lalle akwai aiki agaban abokinsa dan yada ko kanta bata dagoba bare tasan da shigowarsu saima wayarta dataketa latsawa Momcy tace sannu tijjani Allah yabar zumunci papa kushiga mana katsaya anan Wajema yasamu yazauna yana cewa aa zansha iska kadan anan Fauziyyah kuwa kamar ta bar wajen amma sai taga kada ya rainata kawai ta matse abinta Acikinsu ba maimagana dan shi papa kallonta ma yasashi farin ciki sai yaji tsoro kada yamata magana tama bar wajen shiyasa yaja bakinsa ya tsuke TJ kuwa shakkar mata magana yake kada shima tace bata ganeshiba Wayarta ce tafara ringing dubawa tayi taja tsaki axuciyarta ganin no Brr.Nabil ne Yau batasan iya adadin kiran daya mataba kuma bata dauka ba shikuma bai haqura ba Harta katse bata daukaba sake kira yayi sai taji shaawar ta dauka kodan tasamu hanyar barin wajen Momcy kuwa miqewa tayi tace barin turo muku da abinci Fauziyyah cikin daddar muryarta tadau wayar da sallama jin muryarta mai sanyi yasa papa lumshe idanu..... ✍🏻Faty Mmn Faty 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty August, 2017 *Wai maiyasa mutane bakwa uzuri ma mutum ne? Idan kukaji shiru kunsan aidai da dalili kuma dai bazanyi typing ban turoshiba idan kuwa har hakane saikuyima mutum kyakykyawan zato masu cewa wai dan andamu nake masu yanga toh ai mai sauqine tinda ku kuka dami kanku ba nina saku ba, sabida haka saiku daina karantawa tunda ba wanda nasaka saiya karanta dole* 4⃣8⃣ Murmushi yayi sannan ya amsa sallaman Cikin natsuwa tace ina yini Fara arsa ya fadada yace lfy dan wani dadine ya lillibesa jin yadda ta amsa da faraa sannan yau har gaisuwa ya samu Cikin murya mai sanyi yace gimbiyar mata asassautamun mana aidai ko haka na wahala Juya idanuwa tayi cikin murya mai jan hankali tace namefa Murmushi yayi sannan yace tinsafe nake kira baki dau wayata ba pls ko shiruma nikiyi amma dai kidauka sai hankalina ya kwanta Hakan daya fada shiyasa ta wani qayattacen murmushi wadda ya qawata face nata tace ayyah aifa ba dagangan bane ba bani kusane kuma yanzun bagashi nadauka ba Cikin murmushi yace hakane nagode da kika bani lokacinki amma da zaa taimakamun abani dama nazo gida mugaisa Shiru tadanyi dan harga Allah bata san takuri amma kuma yau sai takejin nauyinsa sosai Maganarsa ce ta katse mata tunani yana cewa ya kikayi shiru pls fauziyyah kibani dama na bayyana maki irin sonda nake maki wlh tunda nake arayuwana bantaba jin son wata mace aduniya kamar yadda nake sonkiba kuma ni inkika amince mun insha Allah zan zamar maki alheri arayuwa amma kibani dama domin kitabbatar da maganata Jikintane taji ya mutu murus kuma ya tuno mata da wasu kalaman da papa ya taba fada mata abaya Cikin sanyin murya tace bakomai ur always wellcome Wani dadine ya lillibeshi yace thanks a lot my life insha Allah gobe da yamma zanzo Cikin murya mai kamada shagwaba tace gobe kuma gaskiya is to early Cikin rarrashi yace haba my life ai da zafi2 akan bugi qarfe amin haquri dai nazo goben kinji my life Murmushi mai dan sauti tace ok Allah ya kaimu Papa dayakai har wuya dan takaici dan tini ya fahimci da wani take waya Jiyake kamar ya shige cikin wayar yazugamasa rashin mutunci dan wani kishine ya tirniqeshi dan ya fahimci ya samu waje tinda taketa zuba murmushi Cikin qunar rai ya miqe afusace yayi side nasa Ganin yadda ya tashi afuce nan danan fiskarsa ta canja hakan yasa TJ ya tashi yabi bayansa Adaki yasameshi sai safa da marwa dayakeyi acikin daki TJ yana shiga yace yadai man lfy kuwa lokaci daya kacanza Cikin damuwa yace badole nacanba kana kallo cin fuskan da fauziyyah tamun TJ yace haba man kada wannan ya dameka kabi ahankli mana kadaina bata ranka Cikin fushi yace wani irin kada na damu bayan fauziyyah ta nuna batasanniba then gashi tana hira da wani awaya harda yimasa murmushi haba haba Ya qarashe maganar kamar zaiyi kuka TJ yace pls man cool down ur temper komai zaizo dasauqi da yardar Allah ammafa saikabi komai ahankali kuma daki2 Cikin sauri yace kamar me kenan pls tell me abokina wlh ruwan kaina ya qare i dont know what to do TJ yace zauna kaji yadda zamu bullo wa lamarin Zama yayi ya paying full attention nasa akan TJ TJ yace dafarko abinda nakeso dakai kasauqe dik wani abinda kakeji dashi agefe sannan ka cire saurin fushi kadau hakuri kasa ma ranka Wannan shine matakin farko dan dole sai kayi haquri Sannan kasameta anatse kabata haquri akan abinda kamata kanemi yafiyarta dan inba hakaba bazaka taba samun fiska awajentaba matuqar tanajin haushinka tana kuma tuna abinda ya faru abaya Amma idan har tayafe maka ta haqura to komai zaizo dasauqi Papa yace wlh nima inada niyyar bata haquri saidai bansan ta ina zan fara ba tunda lokacin data gannima cewa tayi bata sanniba kuma wlh abin yacimun rai ya dameni kuma ya dagamun hankali TJ yace tafada ne kawai sabida tanajin haushin abinda kamata shiyasa nace kafara bata haquri tukunna Sannan katattara dik wani halin banza ka zubarshi agefe wannan shaye shayen banza da wofin ka haqura dashi dan ba macen arziqi da zataso mijinta da wannan halin Papa yaja wani dogon numfashi yace hakane kamtunba yauba dama komai ya ficemun arai kuma dayardar Allah nabar shan komai tinda suma basa qaran mutum da komai TJ yace good abokina naji dadin yadda ka yadda da shawarina da haka harya kwantar masa da hankali kafin yamasa sallama ya wuce Fauziyyah kuwa cikin qunan rai bayan takashe wayar ta nufi dakinta dan aduniya ta tsani abinda zai tuno mata da papa baran tasashi a idanunta Washe gari da safe papa baiko tashiba ta wuce hospital abinta sai 3 kafin ta dawo gida Bayan tayi sallah taci abinci sannan ta tsantsara kwalliya sosai Wajen qarfe biyar saiga wayar Brr. Nabil kan cewar ya iso fa Mayafinta ta dauka sannan ta fice Wani murmushi tasake sabida yadda yamatuqar birgeta Yana jingine jikin motarsa fara tass , sanye yake cikin wani danyen boyel mai kyau da tsada farare sol wanda sin matuqar amsanshi Fularsa ta dace da kayan jikinsa haka takalnan qafarsa farare sol, hannunsa daure da agogon azurfa sai kyalli yake Haka kurum taji ya matuqar birgeta dan harga Allah tana matuqar son mutum mai kamala da shiga ta mutunci Ahankali cikin takunta mai natsuwa harta qaraso wajensa sallama tamasa cikin siririyar muryarta mai dadin sauraro Lumshe idanunsa yayi ya bude ahankali dan ta tafi da dikkan tunaninsa kwalliyarta kyan fiskanta uwa uba dirinta sannan daddadan muryanta su suka qara narkar masa da zuciya Waalaikumussalam barka da fitowa sarauniyar mata Murmushi tayi sannan ta sunkuyar da kanta ahankaki tace ina yini Lfy lau ya gida da aiki Tace dik lfy lau ya naka Yace well um gaskiya aikinmu ba dadi sai dai shukrah Tace ayyah Allah ya taimaka, Amin ya amsa Gyara tsayuwarsa yayi yana cewa yau gani ga gimbiyata dafatan zan samu mazauni acikin zuciyarki Murmushi kawai tayi batace komaiba dan nauyinsa takeji sosai Nan yasake gabatar mata da kansa ya kuma tabbatar mata ba dawasa yakeba kuma bashida mata dan baitaba aureba Cikin gamsuwa da baya nansa tace bakomai amma yabata time tadanyi nazari Yace badamuwa ya bata kwana biyu ammafa zai ringa kiranta suna gaisawa awaya tace badamuwa Papa ne ya shigo gida kamar wadda akace ya duba gefensa kawai yaga fauziyyah da wani mutum atsaye sai faman kallonta yake yana murmushi kamar zai cinyeta Nan take yaji qirjinsa ya buga wani kishi ya taso masa,jiyake kamar yaje shaqesa Da kyar ya lallami zuciyarsa yayi parkin motarsa ya fito Cikin gida ya wuce zuciyarsa adagule Brr Nabil yace to madam nizan wuce naga kamarma na takureki kinyi shiru bakiyin ko magana Dubansa tayi aa nibaka takurenba kawai dai nagajine yau awajen aiki Yace eyyerh kishiga gida kihuta toh inyaso da daddre zankiraki Tace toh nagode sosai Allah ya kiyaye hanya agaida gida Insha Allahu zasuji bude mota yayi ya miqo mata wata shopping bag mai kyau baby pink colour yace ga wannan bayawa kisha swt Aa nikam kabarshi nagode Bata fiska yayi da sigan lallashi yace haba dai pls kikarba badanniba Yadda ya tsareta da idanuwansa yasa tasa hannu biyu ta amsa tace nagode Yawwa dear saikin jini yafada yana tada motar Itakuma juyawa tayi ta nufi cikin gida tana bude qofar falo zata wuce taji anjawo veil nata hakan yasa tayi saurin juyowa Papa kuwa tunda ya shigo ya gagara shiga ciki dan gaba daya jiyake kamar yaje shaqe wanda yaganshi yana tsaye da fauzinsa Ganin papa ne yasa ta tsuke fuska tace lfy malam wani abu kake nema Dubanta yayi da kyau cikin shan mur yace wayene waccan dana ganku tare Kallon uku saura kwata ta watsa masa tace mene damuwarka da son sanin wayeshi kumama kaidin wayene dazaka tsareni kanamun wasu silly question Cikin zafin zuciya yace au bakisan niba kikecewa ma Tace eh banma taba ganinka tunda kadamu kaji wayeshi mijin dazan aurane ar u satisfied now Yace lalle kinyaudari kanki barin fada maki bakida miji saini kuma ke matata tace sabida haka da kin daiba yaudarin kanki Wani murmushi tayi na takaici tace Allah ya sauwaqa ni nazama matarka kuma ma kaga mundace dakai ne Kadubi yanayin Brr. da shigarsa ta mutunci da kamala shine yadace da mijina ba kai wadda ko shigar mutunci baka iyaba dan shayeshaye kawai mazinaci Allah ya mun katangar qarfe tsakani na da kai kuma ni kadaina iqirarin matarka ce bansankaba bantaba saninkaba arayuwata tana fadin haka ta wucesa abinta ......... ✍🏻Faty Mmn Faty 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty August, 2017 4⃣9⃣ Jikinsane yayi sanyi jin yadda take fadan munanan halayensa wadda ashe tana riqe dasu acikin ranta Yadan jima kafin ya nufi side nasa cikin tunani kalakala Zama yayi yana nazarin hanyar da zaibi ya wanke kansa awajen fauziyyah Yanason ya shafe dik wani tunanin dake akansa na halayen banza ta daukeshi a mutumin kirki Shiru yayi yana nazarin hanyar da zaibi kuma tabbas dole ya dauki shawaran da TJ yabasa idan yanason gane kanta tinda haryanzu tana riqe dashi da abinda ya mata acikin zuciyarta Cikin sanyin jiki ya dauko wayarsa ya lalimo layin TJ yafa kira Bayan sun gaisa papa yace TJ pls gobe irin 10am inason karakani wani waje mana Ok Allah ya kaimu ya jikin dai Dasauqi sosai thanks saimun hadun Yana ajiye wayar yafara tunanin gara yafara shigan mutanen kirki wataqil fauziyyah tacanza tunaninta akansa tunda har take kwatance da wani ****** Itakuwa tana wucewa dakinta ta shige zuciyarta namata zafi cos tunawa da irin azaban da papa ya mata abaya Allah ya qara ta furta afili dan momcy ta bata labarin matar papa Tunani take wani irin mataki zata dauka akan katsalandan dayakeson ya mata arayuwarta Shiru tayi kafin ta miqe ta shige toilet dan kanta harya mata nauyi gashi dama a gajiye take Washegari bayan papa ya fita office ya dan duba patients nasa ten thirty ya fito ya nufi office din su TJ A office ya sameshi yace ya zamuje ne ko kana da ayyuka mubari sai da yamma TJ yace ina zamuje ne kam Papa yace inda kake sayan kaya daka rakani saimuje wajen tailor naka dinki nakeso amun TJ yace lalle nayarda abokina kacanza Papa yace wlh jiya fauziyyah tafadamun abinda ranta yakeso nan yabasa labarin yadda sukayi TJ yace ainafada maka ajiye fushi zakayi agefe har kasamu kanta dan wlh dama can kasanta yar zafin kaice baran yanzu data san ciwon kanta Nan suka fito suka nufi shago inda TJ ke sayayya nan yasayi shaddodi da boyel kala ashirin sannan yasayi huluna masu kyau da tsadar gaske Daganan suka wuce wajen tailor inda suka bashi dinkuna suka biya shi kudin express dan basason ya jima Office ya maidashi akan sai da yamma zai shigo gida Fauziyyah kuwa da wuri ta dawo gida yau da yamma ta shirya tsaf cikin wani sari sky blue wadda idan kaganta zaka rantse da Allah kace yar india ce Nan tacema momcy zataje gidan khairy tinda tadawo batajeba Momcy tace toh saikin dawo amma kada kiyi dare tinda ke kadaice zaki fita Cikin ladabi tace toh momcy me abi ayaho (saina dawo) Momcy tace Allah ya kiyaye hanya adawo lfy Tana fita gidan khairy ta wuce cikin murna khairy ta tarbeta nan suka zauna afalo suka fara hiran yaushe gamo TJ ne ya fito dan khairy ta fada masa zuwan fauziyyah Zama yayi agefen khairy yana cewa hajiya fauziyyah ce agidanmu kodama bata gane mutane amma dai kekam nasan bata mantakiba yafada yana kallon khairy Murmushi tayi dan tafahimci inda maganarsa ta dosa Tace habaya Tijjani ni na isa nace banganekaba Yace ah ranan agidan momcy kikayu kamar bakisanmuba Tace kasan kazauna kusa da baqon fuska shiyasa kaima sai kabacemun amma yanzun bagashiba nazo har gidanka Fauzy kenan kinzo dai wajen khairy Tace dikkanku dai wajen ku nazo Yace toh ya aiki da haquri damu Tace aiki mungode Allah saita juta zancen da fadin banga mubeen bafa ko baccin yamma yake Khairy tace aa baya nanma tun jiya yaje gidan hajiya (gidansu TJ) Tace ayyah nan sukayi ta hiransu dik akan karatu nema dan khairyma tayi jamb admission take jira Can wajen magriba fauziyyah tace bari ta tafi TJ kuwa da tun dazu ya fita ashe suna tare da papa awaje Nan sukayi sallama ta rakota har bakin mota tana cemata tagaida momcy itama zatazo TJ kuwa ganin fauziyyah ta fito yasa yayi sallama ma papa ya wuce cikin gida dan dama yafadama papa tazo Shima cikin sauri ya mufo inda take tana qoqarin bude mota ga hadari ya hadu baqiqirin ashe suna ciki basusan da hadarin ba Assalamu alaikum yamata sallama juyowa tayi dan bata taba tunanin shibane tinda a iya tsawon zaman da sukayi har zuwa yau bai taba yimata sallama ba Juyowa tayi dan ganin waye acikin gidan kuma dai ba muryar TJ ba kawai sai taga papa tsaye ya harde hannayensa aqirji Tana ganin shine ta wani hade rai ta tsuke fiska tayi kamar bada ita yakeba ta bude motarta ta shige Hannunsa yasaka ya riqe murfin motar yace pls ba danniba ba dan halina ba kiyi haquri kisaurareni Dagoda manyan idanuwanta tayi ta watsa masa wani kallo batace masa qala ba tasa hannu ta jawo murfin motarta Saurin janye hannunsa yayi da ta buge masa hannu Key tayi ma motar zata wuce ta barshi Shiru yayi yarasa abin ma zaice saiyaji sauqar yayyafa akansa hakan yasa ya juya ya shiga motarsa yabi bayanta Suna fita ruwa ya kece kamar da bakin kwarya hakan yasa tafiya take ahankali shima yana bin bayanta har suka iso gida Yana shigowa gate ko cikakken parking baiyiba ya fito ya nufi wajenta Ita kuma tanayin parking tunani tafara ta fito acikin ruwanne ko ta zauna ya dan ragu Kura idanu tayi tana ganin yadda ruwan ke sauka sai ta hango papa ya nufota Cikin sauri ta bude qofar motar ta gwammaci ruwan ya jiqata than ace yazo wajenta Aiko tana bude qofar motar ta zura qafarta kenan ya qaraso ganin haka yasa tajawo qofar zata kulle Cikin azama ya saka hannu ya riqe, ganin haka yasa ta maida qafarta ciki batace masa qala ba Shima baiyi magana ba sai ruwa dake dukansa haryafara diqa Yakai 5mins ahaka yana tunanin mai zaima fauzy ta saurareshi kawai saiya durqusa awajen cikin ruwa ga kuma tasama ruwa na dukansa Kallonsa kawai takeyi Cikin murya mai rauni yace fauziyyah banida bakin da zan baki haquri akan abubuwan dana maki abaya wadda son zuciyata ya jani aikata hakan Kuma nasani bacin ran abinda namaki ne yasa kike nuna baki sanniba Amma kiyi haquri badan niba sabida Allah kiyafemun abinda namaki kozan samu salama arayuwata domin alhakinki yayita bibiyana kuma nagane kuskurena Fauziyyah saima ta juyar da kanta dan bataji alamun zata sauraresa ba kuma ita dama matsa mata yayi ta wuce abinta dan batajin zata iya yafe masa abinda yamata Ganin bata tankashi ba saima juyarda kanta datayi sake qasa da murya yayi kaman zaiyi kuka yace kefa musulma ce na roqeqi kiyafemun sabida Allah badan niba Yadda ya marairaice murya saitaji tausayinsa ya kamata amma data tuna irin walaqancin daya mata abaya duka zagi azabtarwa sai taji wani sabon tsanarsa Jakarta ta jawo afusace ta hankada murfin motar ta wuce tagefensa tayi cikin gida da gudu tana shiga falo wani kuka ya kubce mata direct dakinta ta wuce tana zubda hawaye Papa kuwa yadda ta barshi awajen yakai minti goma baiko motsa ba yarasa wacce hanya zaibi ya samu yafiyarta wasu hawaye masu zafi yaji suna zuba akan fuskarsa Kuma hakan datayi ko kadan baiji haushintaba sabida yasan abinda yamata bana kadan bane Tashi yayi ahankali ya nufi cikin gida yana shiga shima ya wuce dakinsa cikin qunan rai ya dauko sigari ya kunna amma sam ko zuqa daya kasawa yayi haka ya kashe sabida alqawarin da yayima zuciyarsa yabar shan komai Momcy da daddy suna tsaye jikin window suna kallon dik abinda sukeyi har suka shiga cikin gida Momcy ta juyo tace daddy kaga papa ko tun bayauba nafahimci taketakensa kawai kallonsa nake naga iyaka gudun ruwansa Daddy yayi murmushi yace aini tun rananda yafara ganinta nafahimci inda ya dosa sabida yadda lokaci daya ya birkice nan yafada mata yadda sukayi dashi Momcy tace zaici qaniyarsa ai dan kuwa akwai wadda fauziyyah takeso har jiyama yazo da yamma Daddy yace good haka nakeso Allah ya daidaita su shikuma zaigane kurensa ***** Tana shiga daki ta kwanta akan gado tai kuka harta gode Allah kuma tarasa dalilin kukanta TJ ne ya kirasa dan yaji yadda suka qare cikin damuwa ya zayyanema sa yadda sukayi yace TJ i dont know what to do nayi iyaka qoqarina amma ko saurarana batayi pls TJ help me out TJ yayi shiru yace shikenan zansan abinyi amma kaci gaba da addua dakuma lallaminta harta amince Suna gama waya TJ yasamu khairy ya fada mata halin da ake ciki ya roqeta taje gidan momcy gobe ta taushi fauziyyah Da yamma washegari bayan fauziyyah ta taso aiki sukayi waya da khairy TJ ya kawota Saida suka shiga daki bayan sun gaisa da momcy nan khairy tafara bawa fauziyyah baki akan ta haura tayafewa papa Fauziyyah tace dake bake akaciwa mutunciba ko dole mijinki ya dauko yakawo mana saboda abokinsa Khairy tace wlh ko kadan nibadan haka bane kefa musulmace kuma kada kimanta Allah ma muna masa laifi kuma muroqi yafiyarsa ya yafe mana Kiyi haquri komai ya wuce wlh Dr yayi danasanin abinda yamaki kuma tunda harya baki haquri saiki hakura kodan albarkacin su daddy Shiru tayi tana tuna irin walaqancin daya mata sai hawaye Nan khairy taita lallashinta tace kimanta abinda yafaru abaya matuqar kina tunawa to bazaki taba haquraba Tabbas kowa yasan abinda papa yamaki bai kyautaba amma ai yaga sakayyah nishawara nabakk ba doleba amma kiyi tunani akai Fauziyyah tace nagode khairy Allah ya bar zumunci kuma insha Allahu komai ya wuce amma nance kifadama mijinki ba Khairy tace oh miye laifin Abban mubeen wlh har kullum shi yana bayanki fa Ya tsina fiska tayi tace tunda abokin ya Alamin ne shiyasa baruwana daku ai Khairy ta sheqe da dariya tace toh amana afuwa Dariya sukayi gaba dayansu sai bayan magriba sannan tamata sallama ta tafi..... ✍🏻Faty Mmn Faty 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty August, 2017 5⃣0⃣ Aranan bayan tafiyan khairy taita tunani takuma gamsu da shawarin da khairy ta bata kodansu daddy ma ya cancanci ta yafe masa kuma kodan tasamu yarabu da ita zata furta masa kalmar yafiya Tindaga ranan suka shiga wasan boye, dik hanyar datasan zai hada ta da papa ta kaurace masa Papa kuwa dik yadda yasan zai hadu da ita yanayi amma abin ya faskara Har sati biyu rabonda su hadu, a hospital kuwa baiyi gigin zuwa wajenta ba dan kada ta yankwanasa acikin mutane gashi kowa yana ganin girmansa Amma ya qudiri aniyar kota halin qaqa sai yayi magana da ita sabida haka yau da wuri ya shirya saida ya daidaici lokacin fitanta sannan ya fito Cikin saa kuwa yasamu momcy da daddy ma dik suna break fast sabida daddy zaifita shima Assalamu alaikum ya masu sallama yana ajiye jakar system nasa akan kujera a falo Dik tsayawa kallonsa sukayi Fauziyyah data debo abinci zata kai bakinta sai ta daga idanunta ta kalloshi itama abin mamaki ya bata Yau sanye yake da wata dakakkiyar shadda army green tasha aiki mai tsadar gaske Hularsa kalan kayansa ga wani agogon azurfa dagani ba tambaya kasan kudinsa dayawa Abinka da farin mutum sai yafito kwarjininsa ya qaru akanna nada dan kayan baqaramun karbansa sukayiba Abinda ya basu mamaki shine rabonsa da saka manyan kaya haka tun bikinsa da juhaina wadda shine na biyu daya taba saka jumper arayuwarsa Amma kuwa saiya karbeshi sosai ya fito masa da kamalarsa na cikakken mutum Qarasowa dinning din yayi yana cewa mornimg daddy morning momcy Momcy tayi murmushi ganin sauyin da take gani awajen danta tace morning son har anfito yau da wuri haka Umm inada wani aiki shiyasa na fito da wuri Daddy yace Dr yaukuma aure zakaje daurowane ba katin gayyata Murmushi yayi yana sosa keyarsa yace haba daddy kawai dan nasaka saiya zama aure zanyi Daddy yace ah toh nasani tunda baswa kakeyiba saida dalili Murmushi yayi yace aa kam kawai nayi shaawar sawane Daddy yace ko kaifa amma mutum kullum cikin qananun kaya dik jiki atakure amma nasan yau kafi jinka very compotable haina(koba haka ba) Hakane daddy ya fada yana daukan fork dan shima abincin zaici Fauziyyah kuwa da tunda ta kallesa sau daya bata qara bin takansa ba bata kuma cemasa kala ba saima ajiye cokalinta tayi ta miqe zata bar wajen Momcy tace badai kin qoshiba Cikin shagwaba tace naqoshi momcy zan wuce office Daddy natafi saina dawo Momcy tace toh Allah ya tsare hanya daddy ma yamata addua adawo lfy sannan ta fice Papa kuwa harta fice kallonta yake sabida komai nata birgesa yake baran ya kwan biyu baiganta ba Haka muryarta baqaramun dadi take masa ba koda masifa take muryarta dadi takeyi baran yanzu dayaji yadda tayi magana ashagwabe sai yaji taqara birgesa Zama yayi ya break nasa hankali kwance koba komai ganinta da yayi yasami natsuwa Yau aiki ya riqe masa wuta sosai gashi ranan saturday mai zuwa zaayi bikin sabon asibitin da suka bude mai suna *NAMSA MEDICAL CENTER* Tinda ya dawo suna tare da daddy har suka fita masallaci tare Ranan saturday aka bude sabon asibiti hadi da walima Manyan mutane sun hallarta sosai sannan abin ya qayatar abin birgewa Da yamma momcy ta shirya walimanta acikin gida inda itama ta gayyaci yan uwa da abokan arziqi Fauziyyah kuwa tinda aunty mabarukha tazo suna tare har aunty niima tana mata tsiya Papa kuwa tinda ya dawo yana kwance adakinsa dan yagaji sosai tashi yayi ya wanka ya shirya cikin wani danyan boyel ash colour wanda yamatuqar amsan fatar jikinsa ya kafa hulan nan kamar wani ango Har ya juya zai fita sai yaje jikin window ya daga curtain dan yagani kozai samu ya fice dan tun daxu yakejin hayaniyar mutane Kamar wasa ya hangi fauziyyah tasha ado da kwalliyah cikin wani matetial maroon colur dinkin doguwar riga Ta kafa dauri tayi kyau sosai Tana tahowa kallonta yake yaga inda ta nufa saiyaga ta shige lambu ta qofar baya inda ake shiga bayin fulawa aiko cikin sauri ya fito ya nufi lambu shikuma ya shiga tacikin falo Can ya hango ta zaune akan kujera da waya akunnenta Itakuma wayarta da aka kira yasata shigowa lambun Qarasowa yayi inda take zaune yaja kujeran gefenta ya zauna Dagowa tayi ta kallesa sai tayi kamar bata gansaba taci gaba da wayanta ita da Barr.Nabeel Daure zuciyarsa kawai yayi yanajin yadda take fadan kalaman soyayyah dikda baisan itada wayeba amma yana tunani itada wanda yataba ganinsu tarennan ne Takai tsawon minti goma tana waya sannan tayi sallama tana sauqe wayar akunnenta ta miqe zata bar wajen Cikin sauri ya riqo hannunta juyowa tayi afusace ta wurgesa da wani matsiyacin kallo Saketa yayi da sauri wanda abu biyu yasa yayi saurin sakemata hannun Nafarko wani danbanzan shorck dayaji kamar wadda wuta ta jashi na biyu wani kallo data watsa masa Fiska atsuke tace malam wayabaka izinin riqemun hannu Atausashe yace am sorry pls badagangan bane Juyawa tayi zata wuce yayi saurin cewa pls Fauziyyah kisaurareni mana tunda nazo wajenki kinsan da magana nazo Ko kulashi batayiba ta wuce abinta shan gabanta yayi hakan yasa dole ta tsaya Pls fauziyyah nasan cewa namaki laifi amma mutum idan yagane kuskure ya roqi yafiya aisai ayafe masa Kifadi abinda kikeso namaki danki yafemun Shiru tayi tana sauraronsa yadda yake bata haquri kamar zaiyi kuka tabbas ya Alamin ya sauya fiye da tunaninta Roqo yake magiya yake haka ya durqusa awajen Wani iri taji aranta tana tunanin yadda mutum ke sabawa Allah yaroqeshi gafara ya kuma gafarta masa asheko inhakne dole ta yafe masa Cikin sanyin murya tace ya isa haka ya Alamin yawuce har abada Allah ya yafemu gaba daya amma dan Allah na roqeka daga wannan kada ka kuma shiga harkata koda magana bana buqatar yahadamu Wani zufane ya yanko masa yace ashe ko inhakane baki haquraba kada kimanta kefa yar uwatace nidan uwankine Tace yau kenan kasan da wannan yafiyakam nayafemaka har zuciyata kawai alaqa dakaine bana buqata tana fadin haka ta wuce abinta Jiki asanyaye ya tashi ya wuce dakinsa yaji dadin yadda ta yafe masa amma yadda ta furta wai bata qaunar alaqa dashi shiya damesa gashi riqe hannunta da yayi shiya tuno masa wasu lokuta daya samu kansa acikin zamansu nabaya Fitan dabaiyiba kenan ya kwanta jikinsa amace..... *Alhamdulillah anan zandakata sai ALLAH ya kaimu ya nuna mana bayan sallah lafiya sannan mucigaba* *Inayima dikkannin Al'umman musulman duniya fata da addu'ar yin sallah lafiya* *Allah yasa muyi hidiman sallah lfy cikin kwanciyar hankali Ameen* ✍🏻Faty Mmn Faty Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty September, 2017 *Alhamdulillah Taqabalallahu minna wa minkum, dafatan munyi sallah lfy Allah ya maimaita mana, EID-EL KHABIR MUBARAKH* 5⃣1⃣ Soyayyah mai karfice ta shiga tsakanin Barr. Nabil da Fauziyyah Soyayyah mai tsafta suke gudanarwa atsakaninsu Kamar wasa son Brr. Nabil ya shiga zuciyar Fauziyyah sabida kyawawan halayensa da son addininsa da kuma yanda yake nuna mata zallar kauna da baya gajiyawa da dik irin abinda take masa na halin ko inkula Ayanzu ta amince da aurensa kuma tayi naam dahakan har zuciyarta Afannin Barr. Nabil shima yayi farin cikin amincewarta Inda yanzu har gidansu sun san yana nemanta Ummansa tayi farin ciki sosai sabida bata da burin daya wuce ganin dannata yayi aure Kusan kullum sai yazo gida sunsha hira abinsu dan momcy da daddy ma sunsan da zamansa haryazo ya gaidasu kuma sun amince dashi dan sun yaba da natsuwarsa Wani lokaci yakanzo asibiti ya sameta sabida yanda yake qaunarta dik lokacinda yaji yana son ganinta saiya taho abinsa Dik abinda kefaruwa papa yana sane kawai ba yadda ya iyane kuma abinna daminsa kawai baya da mafita ne Dik lokacin dayayi niyyar yimata magana idan ya tuna kalmar datace wai bata buqatar yin alaqa dashi sai yaji zuciyarsa ta masa zafi Yauma kamar kullum Brr. Yazo sun hira kasancewar saturday ne dik suna gida Tun zuwansa papa yake tsaye jikin window yana kallonsu yana jin wani zogi acikin zuciyarsa dan ahar kullum son fauziyyah qaruwa yake axuciyarsa Yakuma yi niyyar dik abinda zai faru saidai ya faru amma yagaji da wannan walaqancin da cin fuskar da take masa sabida zuciyarsa ta aminta kawai dagangan take masa haka Itakuwa batamasan yana yiba dan baya gabanta baran tamasa abu da gangan Yana nan tsaye yanajin zuciyarsa kamar tafashe dan baqin cikin yadda yahango su suna ta dariya abinsu basa da matsalar komai Tinda yahango Brr. Zai tafi ya fito ya tsaya aqofar falo ya harde hannuwansa aqirji yana jiran isowanta Kamar wadda akace Brr. Ya juyo aiko ya hangi papa fiskannan ba annuri Duban fauziyyah yayi yace my life nikam wancan yayan nakin haka yake bai magana ma mutane ne Cikin ko inkula tace me kagani Yace sau uku muna haduwa ina masa sallama amma ko ya kulani last zuwana hospital wajenkima mun hadu zan fita shikuma zai shigo ina daga masa hannu amma yayi kamar bai ganniba Tabe baki tayi tace next time kada kasake kulasa ka rabu dashi kawai Yazakice haka baicin dan uwankine yafada yana kallonta Tace to halinsa ne haka idan baiga dama ba kozaka kwana kana masa idan baiga dama ba bazai kulaka ba Jinjina kai yayi azuciyarsa yace amma ko baida hali afili kuma yace Allah ya kyauta nizan wuce sai munyi waya Tace toh Allah ya kiyayae hanya agaida umma dasu sis raudah Toh zasuje sannan ya tafi Aiko tana nufowa cikin gida tinkafin ta qaraso papa ya taho ganin haka yasa ta kauce ta wucesa Fauziyyah Fauziyyah Fauziyyah yake kiran sunanta amma ko ta amsa baran ta tsaya Pls kisaurareni mana ya ina maki magana zaki maidani dan iska Har takai qofar falo tasa hannu zata bude dan bata da niyyar amsashi Cikin zafin nama yasa hannu ya fincikota baya Aiko nan tayo baya kamar zata fadi sabida da iyaka qarfinsa ya janyota dan ransa yagama baci Cikin sauri ya tarota ta fado akan chest nasa Wani yarr gaba dayansu sukaji lokaci guda wadda hkan yasa papa sauqe wata wahalalliyar ajiyar zuciya hadi da lumshe idanu Wani kasalane ya sauqo mata jin yadda ya maqale hannunsa ya zagaye waist nata Kome ta tuna cikin sauri tasa hannu biyu da iyaka qarfinta ta turesa Amma kuma takasa barin wajen sabida yadda qafafunta suka mata nauyi Cikin dakewar murya tace meyasa bazaka rabu dani nasha iska ba abaya kace yafiyata kake buqata kuma na yafe maka to yanzu kuma what else kake buqata ta qarashe maganar cikin fada Shima da fada fada yafara magana dik da irin yanayin dayake ciki amma dake ta tabomasa indake masa kaikayi yace Nagaji da irin azabtar dani da zuciyata da kike yi nagaji da ganin walanqancin da kike mun agabana kina tsayawa da wani da wani noo wlh kadana kuma ganinki da wani dan iska agidannan ko awani waje Da mamaki take kallonsa kawai yadda ya haqiqance yana masifa kamar zai daketa Cikin jin haushi tace toh miye damuwarka kuma miye hadinka dani dazakazo kanamun wasu magana marasa maana da dadin sauraro Oh maganan tawace marar maana ya tambayi kansa wani haushi ne yasake kamasa kallonta yake ido cikin ido yace becouse meh tumse pyarr kartahoo( sabida inasonki) Wani wawan kallo take binsa dashi tagagara cewa komai sai idanu kawai take binsa dashi cos she is totaly speechless Ahankali bakinta ya furta pyarr(so) Yess hah kahona pyarr hai(eh inasonki) Girgiza kanta tayi cikin wani qunan rai dan ji take kamar ya watsa mata dafi Tace kayi gaggawar fadin istigfari sabo nayi yafada yana kallonta Tace aiya wuce saboma inka manta na tuna maka Kaikuwa mai zakayi da yar qauye qazama wawiya jaka yarinya qarama wadda batada abin shaawa baran na marmari Wani zufane ya fara tsatsafo masa ta ko ina jin yadda take jero abinda ya dinga fada mata abaya wato bata manta ba Gagara magana kawai yayi dan baya da tacewa bai kuma san ta ina zai fara ba Tsabar bacin rai idanunta sunyi qanana da kakkausan murya tace wlh ka cuceni kuma baa taba fadamun baqar magana irin wadda kafadamun ayanzuba wai kana sona bakaji kunyar fadin haka ba Nace bakaji kunya ba toh koda maza sun qare kaikam nayafe akai kaya masauqi Sai anan yayi magana yace dik abinda zakifadamun kifada matuqar zaki huce all i know is i luv u with all my hrt Tace nikuma i hate u n i really hate u ta zuga masa wani wawan tsaki ta wuce tace kana wasting mun time da alama bakada abinyi Tana wucewa shikuma ya koma da baya ya nufi lambu cikin damuwa kozai samu sauqi da zogim da zuciyarsa takemasa Tin daga ranan yake binta kullum cikin roqo da ban baki yake akan tasaurareshi amma sam baya samun fiskanta abin duniya yamata zafi yarasa madafa baran taka maimai Ya rame ya fada sabida ko abinci bai iya ci damuwarsa fauziyyah ta aminta dashi ganin bashida mafita yasa ya yanke shawaran zuwa wajen daddy dik abinda zaayi ayi kawai shidai adawo masa da matarsa.... ✍🏻Faty Mmn Faty 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty September, 2017 5⃣2⃣ Kwanansa biyu yana shawarin taya zai tinkari su daddy baicin abinda ya faru abaya Cikin kwanaki biyun nan damuwarsa ta tsananta sosai Har momcy ta gaza haquri sunayin dinner tace baba na lfyrka kuwa two days dinnan Dagoda kansa yayi hadi da qaqalo murmushin dole yace mene kika gani swt momcy Naga dik kacanza irin u look so sad haka kamar bakada walwala Sake murmushi yayi yace babu komai sai dai stress din aiki kawai Toh Allah ya taimaka tafada amma badan ta yarda da abinda yace ba Washegari bayan sallan ishai ya yanke shawarin zuwa wajen daddy Bayan yayi sallah gami da adduoi akan Allah ya dorasa akan daddy dan yasan idan daddy ya amince zance ya qare Falon daddy ya nufa zuciyarsa na dukan uku2 da sallama ya shigo yasami waje ya zauna Daddy ne kadai yana kishingide yana kallon tashar CNN Dago kansa yayi yana amsa sallamar Zama yayi yayi shiru yana tunanin ta ina zai soma magana Daddy ne ya katse masa tunani da fadin yadai Alamin kaxo tayani hira ne Dan sosa kansa yayi yace um eh daddy naxo taya ka hirane sannan akwai maganar danazo da ita Ok inajinka ya akayi Cikin dakewar murya yace umm dama daddy alfarma nazo nema wajenka Uhum go on name fa daddy yafada yana kallonsa Cikin sanyin murya yafara magana daddy dan Allah badan niba kataimakamun yadda Allah ya taimakeka kadawomun da matata wlh nayi nadama kuma nagane kuskurena bazan sake aikata makamacin abinda yafaru abaya ba Kallonsa daddy yake sosai yace Alamin banfahimcekaba explain to me further Cikin murya mai rauni yace daddy nayi nayi iyaka qoqarina fauziyyah taqi ta saurareni wlh daddy inasonta zan iyah shiga wani hali matuqar fauziyyah ta gujemun Dan Allah kasa baki daddy kataimakeni tunda tanajin maganarka yaqara maganar kamar zaiyi kuka Daddy yace kafazomun damagana adunkule kafito straigh forward kayi magana mana Toh daddy gaskiya matata fauziyyah nakeson adawomun da ita Wani kallo daddy yake binsa dashi kamun ya tashi daga kishingidar dayake ya zauna dakyau yana dubansa Yakai minti biyu kafin yace Alamin kana da hankali kuwa kasan me kake fadi kuwa tohma ta ina tazama matarka ko kamanta da ba aure atsakaninku Daidai shogowar momcy kenan Zama tayi agefen daddy tace lfy kuwa meya faru daddy? Daddy yace wai cewa yake adawo masa da matarsa Cikin takaici momcy ta dubesa tace ashe bakada hankali bansaniba Ta ina kataba ganin anmaida aure akan saki uku eye? Nadauka kayi hankali ashe dasaurnka haryanzu daka samu Allah ya taimakeka ya rabaka da raqai dakuma lfyrka shine zaka tono wani abinda baxai yiyuba Daddy yace baki fahimcesa ba ashe ai gara yace amayar masa da matar da yayima saki uku akan abinda yazo dashi amma gaki gashi ya maki bayani da bakinsa Duban papa tayi cikin rashin fahimta tace nifa kunasani aduhu wai meke faruwane Kansa tsaye yace matata fauziyyah nakeso adawomun da ita What? Shine abinda momcy tafada tana kallonsa kafin tace toh gaka ga daddy wannan ba magana ta bace Daddy ya kallesa da kyau yace kasaurareni da kyau kaji abinda zanfada maka Abinda nakeso dakai kada nasakejin wannan maganar abakinka koda kuwa awasane Daddy dan .... Daga masa hannu yayi yace banason jin wata magana daga bakinka ingar akan shirmen banzan nanne Juyawa yayi wajen momcy yace pls momcy kitaimaka mun ki.... Itama katsesa tayi tace papa tashi kafita saida safe dan banason damuwa kajiko Daddy yace oyah tashi kabani waje stupid kawai Jiki asabule ya miqe ya fito harjinsa yake kamar bashida nauyi tsabar yarasa tudun dafawa Ranan haka ya kwana idonsa biyu cur tsabar damuwa da rashin madafa Tunani iya tunani yayi amma yaga bayada mafita dole wajen daddy zai koma amma bari ya bari sai bayan kwana biyu Cikin kwana biyun nan dik wanda yagansa yasan yana cikin damuwa matsanan ciya Idan ya fita aiki acan zai wuni daya dawo ya shige side nasa sai dai sallah ke fito dashi ko cin abinci bai zuwa yadawo shiru abinsa iya da safe ya gaidasu kafin ya fita ko break bai tsayawayi Bayan kwana uku yauma yasake dawowa wajen daddy Daddy naganinsa ya bata fiska yace yadai kagama fishin da kake damune? Girgiza kansa yayi yace wlh ko daya nibana fushi daku taya zanyi fushi daku kuma Dan Allah daddy kasaurareni kataimakeni kamayar mun da matata kuma ko wanne irin sharadi ka shimfidamun na amince zanbi zanbi Daddy yace kai banace banason sake jin wannar maganar ba Idan har aure kake buqata ko a inane ka nemo zan shige maka gaba amma banda fauziyyah Yarinya mai hankali da natsuwa ba irinkaba ai kaikam da ita kunyi hannun riga dan bata dace dakaiba baka dace da ita sabida haka kwarya tabi kwarya Kuma aidai kana sane cewar aurenta ma ya kusa ko Dam yaji gabansa ya buga Yace yes aurenta ya kusa ko atunaninka zaa maimaita irin abinda ya wucene asake rabata da masoyinta na gaskiya abaka kaje ka wulaqan tata aidai ko kulya mutum ya ajiye zai kula da ita bare mutum dan adam bayan kagama azabtar da ita hakan bai makaba sannan kazo gabana kamata sakin walaqanci ka tozartani ko kana tsammanin na mantane wannan cin mutuncin dakamun haba haba cikin tsawa yace katshi kafita agabana kada kasa nayi abinda banyi niyyaba kafita nace Durqusawa yayi yana hawaye ya riqe kafar daddy yana cewa nasan nayi kuskure kuma ban kyautawa kainaba daddy nayi danasanin abinda na aika ka taimakeni daddy kada karabani da fauziyyah wlh inasonta kuma itace rayuwata kada karabani da rayuwata Daddy yace baka sotaba saida kaga tazama mutum ko kuma aikai kanisanta kanka da ita sabida haka kaje kasamo uwar mata ka aura wannan yarinyar ba saarka bace Riqe daddy yayi yana kuka yana roqonsa amma daddy sam bai saurareshiba saima kwace qafarsa yayi ya wuce abinsa yabarshi durqushe awajen yana kuka ..... ✍🏻Faty Mmn Faty Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty September, 2017 5⃣3⃣ Momcy da ta taho wajen daddy tinkafin taqaraso taji kamar alamun gunjin mutum na kuka Cikin sauri ta qarasa hankali tashe bako sallama ta fado cikin falo Turus tayi ganin papa durqushe yana kuka Dasauri ta qarasa wajensa tana tambayarsa papa meya faru nace meya faru Bai amsataba sai rungumeta da yayi yana kuka Cikin tsanin tashin hankali dan batasan meke faruwa ba tace am asking u kya hua(ina tambayarka meke faruwa) Da kyar ya iya furta momcy pls help me wlh inasonta inasonta bazan iya rayuwa ba ita ba kitaimakeni ki lallashi daddy yayi fushi dani yana magana yana kuka kamar qaramin yaro Wani iri taji har cikin ranta kuma yadda taga papa ya gigice tabbas yanzu yanason fsuziyyah kuma so mai tsanani sai dai ba yadda zaiyi saidai yayi haquri tunda dama shiya sake damarsa tun farko Wani irin tausayinsane ya kamata haka takejin kukansa har cikin ranta amma haka ta danne zuciyarta Tace toh me kakeso namaka papa baicin what ever happens is all ur fault Yace i know momcy nina janyo ma kaina kuma wlh nayi dana sanin kuma tun fauziyyah bata dawo nagantaba nake fama da matsanancin sonta bawai yanzune nafara sonta ba kiyi wani abu momcy Ganin yadda ya birkice yaketa surutai yasa ta saka hannunta tana patting bayansa smoothly hadi da lallshi Haba papa ya kana abu kamar qaramun yaro uum Ya isa haka nan ka kwantar da hankalinka ko so kake wani ciwon ya kamaka Look at ur self ya kacanza just in two days haba Nidai kawai kitayani bama daddy haquri sannan hankalina ya kwanta Naji amma saika kwantar da hankalinka tukunna Shiru yayi ya kwantar da kansa akan cinyanta yana sauqe numfashi Miqewa tayi tariqe hannunsa suka nufi side nasa Fauziyyah dataji maganar momcy cikin firgici baicin tare suke zaune ta wuce wajen daddy ta barta hakan yasa tabi bayanta da sauri Tana zuwa bakin qofa ta tsaya jin maganar dasukeyi akantane Cikin damuwa itama ta fara hawaye kuma jin yadda alamu momcy zatabi bayan danta tunda gashi ta nuna damuwarta akansa Wani iri taji har ranta yadda momcy ta dauketa tamkar yarda ta haifa acikinta amma ace tasanadinta ta janyo mata tashin hankali Sai dai duk da haka batajin zata iya komawa gidan papa gara ta sanarma Brr. Ya turo kawai tinda dama ya matsanta mata itace take dan jan abin Jin takun fitowansu yasa tayi saurin barin wajen ta nufi dakinta tana hawayen da batasan dalilin yinsa ba Dakinsa sukaje tace maza jekayi wanka barinzo ko Abinci ta kawo masa ta lallabashi yaci sosai sannan tace ya bari zuwa kwana biyu zata lallami daddy amma sai inhar ya kwantar da hankalinsa Bayan kwana biyu da faruwan haka suna zaune da daddare dikkansu afalo daddy yace ma fauziyyah daugther dama inason sanar dake kifadama Nabeel ya turo iyayensa maganar aurenku amma kafinnan zanyi magana da Abba muji wacce rana ya dace asaka zuwannasu Wani irin tsinkewar zuciya taji wadda batasan dalilin hakanba Papa kuwa da kyar yasamu ya lalimo numfashinsa wadda yayi barazanar daukewa Ahankali ta furta toh daddy Momcy kuwa shiru tayi harga Allah tanason papa da fauziyyah tunda yagane kurensa amma kuma tunda ita fauziyyah bata sonsa bawani mafita ya haqura shine kawai Saidai tana tunanin irin halinda dannata zai shiga kallonsa kawai take tana nazarin yanayin dayake ciki Fauziyyah ma dakinta tawuce tafada gado tana kuka tabbas tasan tanason Brr. Amma kuma batajinsa aranta kamar yadda taso Yasir Nan tasakejin tabbas tayin rashin masoyinda takeso har abada Papa ma haka ya miqe ya nufi dakinsa ya sanya makulli ranan kwana yayi acikin wani yanayi marar dadi Washegari kasancewar saturday yasa har yamma bai fitoba Zazzabi mai zafine ya rufesa shiyasa ya wuni a kwance Gashi daddy yahana momcy zuwa ta duba lfy bai fitoba Sai da yamma tukun ya lallaba ya fito Fita yayi ya nemo magani awani pharmacy dake kusa dasu Bayan yadawo da kyar ya sha dan ruwan tea yasha maganin namma saida momcy ta matsa masa afalonta ya kwanta Daddy ya shigo momcy tace yanzu zanshiga wajenka dama Alamin ne baida lfy Cikin ko inkula yace Allah ya sauwaqa kicema fauziyyah tafada ma nabil ranan saturday suna iyah zuwa dazu munyi magana da Abba Yana fadin haka ya juya Nan papa yasake birkicewa zazzabi ciwon qirji momcy harta tsorata Amma cikin ikon Allah washegari yadan samu sauqi dan yasha magani Kullum cikin lissafa kwanaki yake har anci kwana uku Tunani badare ba rana yakeyi ta ina zaisamu mafita Yanzu hanya dayace ta rage masa baibiba shine Abba Kuma gaskiya yanajinjina taya zai kalleshi bayan abinda ya aikata abaya S ai dai kuma yaduba yaga baya da wani option gara yaje yasami Abba wataqil yadace acan tunda yasan Abba mutumin kirkine... ✍🏻Faty Mmn Faty 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty September, 2017 5⃣4⃣ Shikadansa ya gama shawarinsa baikuma fada ma kowaba Gari na wayewa sassafe asuban fari ya dauki hanyar dambam Cikin ikon Allah qarfe tara ya shiga garin dambam Gidan Abba ya nufa saidai zuciyarsa tana ta bugawa dan baisan yadda Abba zai karbi maganar ba shinko zai sauraresa ko zaimasa irin abinda daddy yamasa Da haka harya qaraso qofar gidan yana isowa Abbah yana qoqarin fita Parkin yayi cikin dauri ya fito dan harya shiga mota Saida yazo har jikin motar sannan Abba ya ganesa dan yasha jumfer har qasa ga hula hakan yasa Abba baikawo shibane Da faraarsa ya bude motar yana qoqarin fitowa cikin sauri papa ya tsugunna yana cewa sannu Abba Aa tashi tashi zaka bata jikinka ai tashi muje cikin gida mana Tare suka shiga side din Abba dan mama bata gari sunje biki jos Harqasa ya duqa ya gaisheshi Shima da faraa ya amsa yace amma dai agarin ka kwana ko Cikin ladabi yace aa yanzu isowana Ah lalle kayi sammako yasu daddy dasu hajiya Dik lfynsu qalau ya amsa Masha Allahu yayi kyau Shiru ya danyi kafin yace dama wajenka nazo Abba Abba ya gyara zama yace toh lfy daikam inasauraronka Qasa da murya yayi yafara magana cikin nadama yace Abba tabbas nimai laifine awajenku kuma nasan nayi kuskure amma kuyafemun badan halina ba kuyi haquri... Katseshi Abba yayi da cewa ya isa haka Alamin kaifa danane kum ni bakamun komaiba sabida haka komai ya wuce kuma naji dadin yadda naganka cikin kamala ubangiji Allah ya yafemu gaba daya Cikin jin dadi yayita godia Abba yace bakomai ya wuce Sannan yasake qasa da murya yace dama Abba nazo roqon alfarmace awajenka Abba yace namefa Aminullah Yace dama Abba fauziyyah ce nakeso tadawo dakinta shikuma daddy yaqi amincewa nan ya zayyane masa yadda sukayi da daddy Abba dan Allah badan halina ba kutausayamun yanafadin haka yayi shiru dan jinsa yake kamar zaiyi kuka Abba ya nisa ya dubesa cikin kulawa kafin yafara magana Yace da darko sai ince Alhamdulillahi daka fahimci kuskurenka kuma naji dadin yadda kaxo kasameni kaitsaye tun abubuwa basu kwabe Kuma gida bai qoshiba aibazaa bawa dawo ba Amma alhji bai kyautamunba yana sane da kanason maida matarka ya hana sannan ya shigoda wata magana Kuma shi wadda yake neman nata aibaasan halinsa ba Tunda Allah yasa kazo kasanarmun halinda ake ciki to tazo gidan sauqi insha Allahu gobe zanzo bauchin muyi magana da Alhajin Wani dadine marar misaltuwa yaji yana ratsashi ta ko ina Sake risinawa yayi yana godia sosai Abba yace dakaida fauziyyah dik daya kuke awajena sabida haka ka koma abinka kasa aranka fauziyyah matarka ce insha Allahu Godia sosai haryasa kalmar dazaiyi amfani da ita tsabar murna Haka yayima Abba sallama ya kamo hanya zuciyarsa wasai Rabonsa dayaji farin ciki irinna yau harya manta ranan Gabda laasar ya iso gida wanka yayi ya fito yaci abincinsa hankali kwance Momcy dai tayi mamakin canzawarsa amma dai tayi shiru batace komaiba Yana nan zaune afalo tafito ta wucesa tinda yaga fitanta awannan lokacin yasan wannan man dinne yazo ko ajikinsa saida yagadama sannan ya tashi ya dauko car key nasa da wayoyinsa yayi waje Motarsa ya shiga saida yazo dafda su sannan ya sauqe glass ya nunasa da hannu yace hey kada kabari nadawo nasameka tareda matata kuma zaifi maka sauqi idan katafi kada kasake dawowa Duban papa yayi da kyau yace matar ka kuma ta ina tazama matarka Yace bani da tym inada wajen zuwa amma katambayeta ita zata amsa maka ai yana fadin haka ya daga glass din motarsa ya wuce abinsa Fauziyyah kuwa abu biyu su suka dameta nafarko yadda ta boyema Brr cewar papa shine mijinta na farko sannan yadda papa yake iqirarin wai ita matarsa ce Brr. Ya kalleta da kyau yace wane ne wannan awajenki Ahankali tace yaya nane Yace kada kimaidani bitacan mana inason kifadamun gaskiya miye alaqarki dashi dan najima da fahimtar akwai abinda kika boyemum game dashi Nan idanunta sukayi raurau tace wlh ba abinda nake boye maka kawai dai banason tuna abinda yafaru abayane Yace naji amma kada kifadamum shine mijin da kuka rabu Murya na rawa tace shi shine Wani baqin kishine ya taso masa cikin fada yace i see shiyasa ashe yakemum abinda ya gadama kekuma kikaqi sanar dani ashe dama tsakaninmu akwai yar boye Tace bahaka bane Yace toh ya ne inba haka ba kawai bakida abinda zaki fadamun Haka taita bashi haquri dan ta lura ransa ya baci shima haka ya tafi yana tunani kalakala Washegari Abba yazo inda suka zauna da daddy akan maganar su papa Amma fir daddy yace baisan zancenba idan har papa aure yakeso ya nemo awani waje Abba yace toh shikuma baiga dalilin da zaa hana papa fauziyyah ba Nan dai suka ringa muhawara har Abba yayi nasaran shawo kan daddy amma da sharadin sai fauziyyah ta amince Abba yace batun wannan yaron sai adakar su amma aini har raina ya baci ace taya zaka hana alamin fauziyyah Daddy yace bawai hanashi nayiba kawai abinda ya aikatawa kansane Abba yace aiyawuce Allah ya kiyaye nagaba Abba yace toh shizai tafi amma yanason magana da fauziyyah Bayan tazo Abba ya dubeta yace mama na ya aiki Lfy lau Abba ya mama sai gobe zadu dawo tacemun ko Yace eh sai gobe insha Allahu ai anyi biki kam kuma sunyi ziyra Tace hakanekan Abba yace mamana ya maganar yaronda yake zuwa wajennaki kinsanar masa ya turo dinne Shiru tayi tana tunanin dama akan jiyane zata sanar masa saikuma yatafi cikin bacin rai hakan yasa bata fada masa ba Abba yace baki amsamunba Ahankali tace aa banfada masa ba tukunna Abba yace Alhamdulillah dabaki fada masaba amma kisaurareni kiji abinda zanfada maki Dafarko nahadaki aure da dan uwanki baason rankiba wadda zan iyacewa dole namaki Toh yanzun lokaci yayi daya kamata ace kina da aure tunda dik abinda ake nema na rayuwar duniya kinsamu daidai gwargwado Toh wannan karon bazance ga miji na zaba mikiba amma amatsayina na mahaifinki zanbaki shawara idan har ta miki Batun maganar Alamin ason raina shine ki amince ki koma dakinki Cikim sauri ta dago kanta tana kallon Abba Abba yace bafa nace lallai bane aa shawarace kiduba kiga yanda iyayensa suka daukeki tamkar su suka haifeki Sannan dik yadda suke tayaki kin Alamin kisani bayadda suka iyane tunda kema kin nuna bakyaso amma suna son dansu kuma sunason farin cikinsa Kuma nima har zuciyata inasonki da alamin sabida haka kije kiyi tunani da kyau akan maganata Kuma tunda mutum ya maka laifi ya kuna nemi gafara aisaika yafemasa Fauziyyah dai nan take tafara hawaye Abba yace aa nifa banace tilas bane inhar kinfison wancan din shikenan amma ni shawara nake baki kuma kije kiyi tunani mai zurfi Tsabar kuka gagara magana tayi har Abba ya miqe yace zaitafi shikam Dakyar ta iya cemasa Allah ya kiyaye hanya Ranan kasa runtsawa tayi lalle maganar Abba gaskiyane kodan su daddy yakamata ta amince da ya Alamin saidai kuma bata sonsa Wata zuciyar tace shima Brr. Aiba wani sonsa kikeba Tunani kawai take taya zata koma zaman aure da ya Alamin tayi kuka har idanunta ya kumbura Kwana biyu da zuwan Abba abubuwa sun dameta gashi Brr koya kirata awaya bata dauka dan batasan mezata cemasa ba Shikuma yadauka bata huce bane tun abinda ya faru Kwanan Abba hudu da zuwa tayanke shawaran amincewa da Alamin amma badan tana sonsa ba saidan farin cikin Abba dan tafahimci yanasonta da Alamin ya boyene sabida kawaici Haka su daddy ma tasan kawaici kawai suke mata Ranan tayi kukan rabuwa da Brr hartaji ba dadi Waya ta kira Abba ta sanar masa ta amince ta zabi ya Alamin Abba ya ringa samata albarka da mata adduoi sannan yace toh tasanar ma daddynsu shiba ruwansa kada daddy yace shiya tursasata Suna zaune afalo da daddare tasamu momcy tace tafasa auren Brr. Ita ya alamin zata aura Momcy tace aa fauziyyah kada kitauyema kanki haqqifa Tace aa ta amince har zuciyarta Tashi momcy tayi taje tasamu daddy da maganar Yace ta kira masa fauziyyah tana fita papa ya shigo bada jimawba suka dawo tare Bayan ta gaida daddy daddy yace yanzu mom dinku tazomun da wata magana inasonjinta daga bakin Qasa tayi da kanta sannan tace haa daddy me tayyarki shaadi ya Alamin(hakane daddy na amince da auren ya Alamin) Wani lamarine mai sanyi papa yaji yana shigarsa tindaga qafarsa kamar anjiqashi da ruwan qanqara Idanu kawai ya zubawa fauziyyah yanajin wani sabon sonta har cikin ransa.... ✍🏻Faty Mmn Faty 🌾🌾🌾🌾🌾?🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty September, 2017 *Wannan shafin nakune kudanku masoya Budurwar Qauye, Mmn Faty tana godia kuma tana qaunarku adik inda kuke,wadanda banisamun damar mayar masu da reply na messages nasu suyi haquri banmanta dasu ba abinne dayawa amma nagode sosai Allahu ya bar qauna 😍😘* 5⃣5⃣ Wani farin cikine ya ziyarci daddy jin abinda fauziyyah tafada da bakinta Murmushi yayi mai cike da annushuwa yace zonan yar gidan daddy matso kusa dani Babu musu ta tashi tamatso kusa da qafafunsa ta zauna ta sunkuyar da kanta Cikin murya mai taushi daddy yace daugther na kifadamun gaskiya dakanki kika amince zaki auri Alamin ko kuma Abbane ya tursasaki Girgiza kanta tayi cikin natsuwa tace aa bashibane ba baima da masaniya akan hakan Alhamdulillah Allahu ya hada kanku ya kuma kauda fitina ALLAH ya maki albarka ya baki yara masu biyayya kamar yadda kika mana Momcy tace amin ya Allah dan itama wani farin ciki takeji marar misaltuwa tana kuma jin son fauziyyah har ranta Daddy yace tashi kije abinki Allah ya maki albarka Asanyaye tace amin sannan ta miqe ta fice dakinta tana shiga tafada kan gado ta bude sabon shafin kuka Daddy kuwa tana fita ya maida hankalinsa kan papa wadda shikuma yabada full attention nasa akan hanyar waje inda ta fice ya bita da kallo ya kuma gagara dauke idanunsa Daddy yace toh nadawo kanka yafada yana kallonsa Jin muryar daddy yasa ya juyo yana kallon daddy Kasaurareni da kyau kaji abinda zanfada maka Nafarko kagodewa Allah da mahaifin fauziyyah mutumin kirkine sannan itakuma yarinyace mai biyayya Toh kagama bin kafa har kasamu burinka ya cika Amma kasani bazan lamunci kwatankwacin abinda ya faru abaya ba Matuqar kanason zama inuwa daya da ita saika sake halayenka tass Cikin ladabi papa yace insha Allahu zankiyaye daddy Daddy yace Allah yasa sannan tunda burinka ya cika saika tattara kakoma gidanka gobe dan bazaka zauna karinga takura mata ba Ko ajikinsa yace shikenan daddy Allah ya kaimu Daga haka ya musu saida safe ya fice zuciyarsa fari qal qal Yana fitowa ya nufi dakin fauziyyah cikin saa kuwa qofar abude take Falon shiru sai qaran AC gami da wani sansanyan qamshi wucewa yayi har cikin bedroom nata Da sallama ya shiga kwance ya hangota tayi rubda ciki akan bed kuma bata amsashiba Wani kasalane yaji ya sauqo masa ta dalilin abubuwa uku Nafarko sanyi da qamshin daya doki hancinsa na biyu tsaftan dake tattare da dakin kamar kada ya fita haka yakeji Na uku yanayin kwanciyar da tayi saiyaji kamar ya qarsa ya kwanta ajikinta dan saiyaji dik hankalinsa ya tashi Gashi dama wata yaloluwar doguwar rigace ajikinta dazataje wajen daddyne ta daura hijab akai tana shigowa kuwa ta cire Dik tabi jikinta ta manne sannan ta bayyana illahirin suran jikinta Wani yawu ya hadiya yana godema Allah daya sanya fauziyyah zata zama mallakinsa Itakuma tanajin motsin bude qofa da sautin muryarsa taji wani baqin ciki yasake kamata Banza tayi dashi kamar batasan da shigowarsa ba Ahankali ya tako har bakin gadon leqa fuskanta yayi nan yagane idanunta biyu kuma kuka mq takeyi dan ganan hawaye shabeshabe akan fiskanta Nan take yaji ya damu gashi baisan dalilin kukan nata ba Cikin murya mai tattare da natsuwa da kulawa ya kira sunanta My Fauzy Wani dam taji zuciyarta ta buga sakamakon tuno mata da yasir da yayi dan shine kadai ke kiranta da wannan Anatse yasake kiranta My Fauzy sunotoo(kinajina) Nanma banza tayi dashi kamar da dutse yake magana Zama yayi agefenta ya riqo hannunta dake gefensa ya sake qasa da murya cikin sanyi yace My Fauzy pls jababdo(ki amsamun) Bata kulasaba sai yunqurin kwatan hannunta daya riqe takeyi Saqe riqe hannunta yayi gagam ganin baya da niyyar sakinta saita rabu dashi kawai Tambayarkifa nake why ar u crying n baki amsaniba yafada atausashe Ganin batada niyyar yimasa magana yasa ya cigaba da fadin Koma meke daminki pls kiyi haquri kibar kuka banson kanki yayi ciwo ko idanunki yayi ja Nazo namaki godia ne akan amincewa da kiyayi zaki aureni Inkuma qara baki haquri akan abinda namaki abaya My fauzy inaroqonki kibani dama na nuna maki irin sonda nake maki Nayi nadamar abinda na aikatamaki abaya U don't know how much i regret everything that i have done to u I luv u my fauzy i luv u with all my hrt Magana yake yana murza dan yatsun hannunta masu laushi da taushi kamar na jarirai Maimakon taji sanyi aranta sai tasakejin wani zafi aranta nan tasake fashewa da wani sabon kuka mai sauti ahankali Nam yayita lallami da maganganu masu dadi amma abanza harya fahimci maganarsane batasonji akan dole ya miqe ya fita yanajin kukanta har cikin zuciyarsa Adaren ya kira TJ ya shafa masa halin da ake ciki TJ yayi murna sosai ya kuma sake bashi shawara mai kyau akan kada gaba ya kuma gangancin kwatanta abinda ya faru abaya ******* Washegari daddy ya tafi dambam nan suka zartar da maganar biki sai nan da watanni biyar masu zuwa Kafinnan angama ginin sabon gidan da zaa kai fauziyyah Yan uwa kowa yayi murna da samun labarin komawar fauziyyah musamman saida aunty mabarukha tazo bh takuma dauki nauyin gyaran amarya idan lokaci yayi Haka maman fauziyyah da farko taqi yadda saida Abba yamata nasiha sannan ta amince takuma sanya Albarka Da aka sanarda papa lokacin auren sai cewa yayi shifa lokacin yamasa tsayi gaskiya Momcy harta qulu tace tosaika rage tunda ka isa da hakan Cikin sati daya magana tagama kankama har daddy yabada contract na ginin gidan sabon gidan papa amma wanna karon a kusa dasu nan *Gida Dubu* Wani filin daddy dake kusa da gidan Aunty naja dambam sukayi shawaran gina masa Momcy tace gara kusa da auntynsa tunda koba komai yafi shiri da ita kuma zatana leqasu akaiakai taga inda yayi ba daidaiba tasashi ahanya Dan abinda ya faru abayama harda rashin wani babba akusa wanda yake leqasu Daddy ya amince da shawarin momcy Daddy ganin har sati guda papa baida niyar komawa gidansa yasa ya kirasa yace ayau dinnan yayi parking inba so yake ya saba masa ba Babu musu ya hada kayansa ya loda a mota sai abinda baa rasaba ya bari saidaga baya zaizo ya dauka nan ya nufi gidansa dake sokoto road wadda rabonsa da gidan tun rabuwarsa da j uhaina.... *Wai ina labarin juhaina kam[truncated by WhatsApp] 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty September, 2017 *This page goes to Aunty Faty G Dambam, Nagode da qaunar da kike nunama littafina, Insha Allah 2019 Bauchi sai Proffessor, Mmn Faty Luvs u 😍😘* 5⃣6⃣ Hankali kwance yake driving har ya qaraso Amma yana isowa gate sai yaji ransa ya baci cos nan take kwakwalwarsa tafara recalling masa abinsa yafaru lokacin rayuwar da yayi da ex wife nasa juhaina Horn yafara mai gadi ya bude masa gate dan yasan da zuwan ogan nasa cos ya kirasa awaya kan cewar agyara gidan before ya yazo Qarasa shiga yayi har parking space yayi parking motarsa Qarema gidan kallo yake saiyaga ya canza masa kodan ya jima rabonsa da gidanne oho Koda kudin buqatar maigadi da sauransu saidai suyi waya yazo ya karba Wani iska mai zafi ya furzar kafin ya bude qofar motan yana tattara wayoyinsa Yana fitowa daidai da isowar maigadi kenan Sannu da zuwa yallabai ya fada yana risinawa Cikin kulawa yace yawwa ya gidan dai hope babu wata damuwa Aa babu konai yallabai ankuma gyara ko ina kamar yadda ka umarta sai dai daki daya wadda yake akullene da baa gyara ba sabida acikin keys da suke wajena babu nasa aciki Ok babu damuwa i think key din yana wajena barin qarasa ciki zan fito saika shigar mun da kayana idan kuma Abdu ya iso shikenan Toh yallabai afito lfy Wucewa yayi ciki inda yabar maigadi da mamakin canzawar ogan nasu Tun bayauba ya lura da sauyin idan yaje wajensa but nayau dabanne lura da yadda ya bada time nasa sukayi magana ta fahimta Falo ya bude ko ina tsaf sai qamshin room freshner da sanyin AC Ba komai acikin falon sai carpet dake tsakiyar falon Wucewa yayi falonsa nanma komai agyare yadda yake ba kuma abinda aka taba Kallon dakin juhaina yayi kamar ya wuce amma sai ya qarasa ya bude nanma bakomai ciki da sauri ya jawo qofar ya rife hadida rintse idanu sabida tuno da abinda ya faru da yayi Cikin sanyin jiki ya wuce dakinsa key yasa ya bude qofar Qurakam baa magana ko ina yayi qura kallon dakin yake sosai fridge ya bude nanma da sauri ya kulle ganin kwalaben wine iri da ban daban Ga wasu kwalabe a zube aqasa ga kuma kwalayen sigari da dai sauran kayan shaye shayensa Lokaci guda yaji kyaman dakin ya kamasa fitowa yayi ya shiga kiran layin Abdu bada jimawaba ya daga hello oga sir am sorry pls na kusa isowa Ok am ka tsaya ahanya kasamomin kwalaye manya mana ammafa empty Ok badamuwa ya fada Bada jimawaba ya qaraso da manyan kwalaye kamar yadda aka sashi Karba yayi ya shiga loda tarkacen aciki saida ya kwashe su tas sannan ya manne su tass ya kira Abdu yace yayi waje dasu ya loda su a boot Falo ya dawo ya zauna ya jira Abdu ya gyara masa dakin nan ko ina ya tsaftatu kamar bashiba Kayansa suka shigo masa dasu daganan ya wuce toilet ya watsa ruwa hadi da alwala Agurguje ya shirya ya nufi masallaci Sai da yayi ishai sannan ya dawo Yabawa Abdu kudi ya samo masu abinci Bayan yayi dinner ya jawo system nasa ya kunna ya duba wasu abubuwa sai dai ya gagara samun natsuwa Jingina yayi da jikin kujera ya lumshe idanunsa ya tuno fiskar luv of his lyf Jiyake inama yana da no wayarta daya kira yaji muryarta ko zaisami sukuni Gashi ya na zaune shiru shikadansa dik kadaici ya damesa Wayarsa ya jawo ya kira TJ Amma baidaukaba harta katse sake kira yayi akaro na biyu sannan ya dauka Hello man how far Papa yace cool ya khairy n mubeen All ar fine ya amarya Wani murmushi yayi mai natsuwa kafin yace tana gida amma dai lfyrta lau Kaikuma kana ina kenan at this tym Ina sokoto road daxu nayi parking wlh daddy ya matsamun wai sai dai na qaura Hhh Tj ya sheqe da dariya yace aikam daddy ya birgeni dan wlh nasan takurin fauziyyah zakanayi Tsaki ya danyi yace aikaiba nasan iya abinda zakace kenan tokoma mene ne dai nikasamun no wayarta now now TJ yace toh nikuma a ina zansamomaka kuma yanzu adaren nan Tsuke fuska yayi kamar yana kallonsa yace banason iskancifa kawai inajira tinda komai saika maida shi wasa Toh naji naji barin karba awajen madam saina turo maka shikenan Eh shikenan thanks Nyt saika ganito Ok nyt yafada yana sauqe wayar amma bai ajiyeba jira kawai yake yaga message ya shigo Aiko bada jimawaba saiga message cikin sauri ya bude ya dauko dayar wayarsa ya shigarda no din Dialling no yafara saidai yaji user busy Sake kira yayi nanma yaji user busy Nanfa ransa ya fara baci todawa take waya awannan daren haka Itakuwa fauziyyah Brr nabil ne ya kirata awaya harda kukansa akan maiyasa ta yaudaresa tasan ba aurensa datayiba gidan mijinta data koma Daddy ya kirasa ya masa bayani akan yayi haquri shinefa ya shiga cikin damuwa zuciyarsa take ganin yaudaransa kawai fauziyyah take shiyasa bata daukar wayarsa Dik iya bayani da rantsuwa data masa yaqi ya yarda sabida kishi ya rife masa idanu kawai gani yake dagangan tamasa haka Shinefa suka dauki time suna magana har ya kira yaji busy Ya kira yafi sau ashirin cikin saa yaji wayar ta shiga Harta kusa katsewa sannan yaji ta dauka cikin sanyin murya tace pls ka amince dani wlh wannan auren sabida iyayena zanyi badan so ko wani abuba nifa kaine araina kuma kaina keso bayadda na iyane kawai na amince da auren ya Alamin Itakuma tadauka Brr ne ya sake kiranta dake da wata no ya kirata shiyasa dataga no ne yanzuma saikawai tadauka shine tafara magana Wani daci yaji maqoqoronsa ya masa jin yadda take jadda da bata sonsa kuma mawani take fadama haka Lallai akwai aiki agabansa dole ya danne zuciyarsa haryasamu gurbi acikin zuciyarta Jin yayi shiru yasa tace pls talk to me mana ka amince da maganata muyi rabuwar mutunci bakadaukeni mayaudariya ba Cikin sanyin murya papa yace My Fauzy Alamin ne Abazata taji maganar hakan yasa tayi shiru ta gagara magana Sharewa yayi yace My Fauzy kina jina Nanma shiru ba responde Yace nasan kinajina meyasa bakiyi bacciba har yanzun while dasafe zaki fita aiki Dama na kirane naji muryanki mai dadi mai sanyani natsuwa kuma gashi kinqi kimin magana amma da kika picking call nawa i appreciate it so ki kwanta kiyi bacci but do not forget kiyi addua kafin ki kwanta Allah ya tashemu lfy kiyi bacci mai dadi n swt dreamz Dik yadda yake maganar cikin wani salo mai matuqar dadin sauraro Hakan yasa tabar dai wayar akunnenta tanajinsa bata kuma kasheba Yana fadin haka ya zame wayar akunnensa ya kashe yana tunanin ta yadda zai samo hanyar dazai shawo kan fauziyyah dan tabbas yasan akwai ga garumin aiki agabansa Itakuma jin ya katse wayar ta sauqe daga kunnenta hadi da jan tsakin dabatasan miye dalilin yinsa ba Message ta rubutawa Brr ta tura masa sannan ta blocking layukansa kafin ta kwanta amma batayi bacciba tana tunanin abubuwa da dama ******** *Waikam ina juhaina ta bace ne???* Tunda tasamu ya amince mata akan tashiga tacanza kaya amma kada ya sameta agidansa Suna fita itama taja jikinta cikin wahala taje tahada abubuwanta masu amfani ta canza kaya kafin ta fito Motatta ta shiga ta fito tana waigen inda zataga munnir sai tahangoshi kwance aqasa baya ko motsi agefen wani lungu bakowa kasancewar yanayi. Layinnasu da bayawan mutane Fitowa tayi ta koma cikin gidan ta shiga dakinsa ta dauko jakar kayansa ta dawo da kyar tasamu tasaka masa kaya sannan ta koma ta ringa roqon mai gadi har ya amince yazo yasaka matashi a mota ta nufi asibiti dashi Wani private hospital ta kaishi amma sukaki karbansa saida ta zube masu kudi masu yawa sannan suka amince suka dubashi Nan itama ta kwana sai washegari ya farfado Tana samun ya farfado tace dashi toh yanzu alaqansu ya qare tinda yamata sanadin aure kuma ta kawo shi asibitine dan bayida mai taimakonsa sabida haka ita yau zata tafi gida kada ya kuma tunanin yasanta arayuwa idan yaji sauqi yaje yadauki motarsa acan sannan idan yana buqata ya kwashe kayan dakinta yasayar ya san inda dare yamasa kada ya kuma nemanta Tana fadin haka ta fice ta barshi yana kukan danasani ga jinya ga karaya ga babu haqora guda biyu Itakuwa tasha taje tasamu fasinjan daya iya mota yajasu zuwa kaduna Gida ta nufa tana shiga ta ringa kurma ihu dik su mom dinta suka rude gashi duk jikinta shatin duka ya faffashe Dakyar tafada masu ai papane ya saketa yamata dan banzan duka Mom dinta tace tabbas saitayi qaransa dan bai isa ya dakar mata ya abanzaba Dad ne yace aa anemi iyayensa dai aji kanmagana Nan juhaina tace ai agaban iyayensa yamata haka da saninsu Mom tace kajiko saina daureshi dan ubansa ta inda take shiga batanan take fitaba Dad yace indai hakane baiga amfanin wata sharia ba kawai abarsu da Allah su suka sani Da kyar ya shawo kan mom ta amince inda juhaina taji dadin hakan dan kada asirinta ya tonu..... ✍🏻Faty Mmn Faty 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty September, 2017 5⃣7⃣ The following morning after ya tashi yayi subh prayer baikoma bacciba Wajen seven ya shiga bathroom ya taking bath Shirinsa yayi tsaf cikin wata sky blue half jumfer wadda tasha dinkin zirii Kansa ba hula sai suman nan tayi lufluf which means tasha gyara sosai Agogon gucci ya daura as usual then yasaka baqaqen half shoes nasa na zallar fata Designers perfoms ya feshe jikinsa nan da nan ya karade ko ina da qamshi Breif case nasa ya dauka da woyoyinsa ya fito hannunsa riqe da car key nasa Babu wadda zai kallesa bai sake ba koda kuwa tare suke kwana daki daya dan papa yayi no lie Yana fitowa ya tarar anwanke masa mota sai sheqi take Maaikatansa sukazo one by one suka gaidasa sannan ya bama Abdu kudin Abincinsu yace idan yaqare yayi magana shi ya wuce office idan ya dawo zaije gida ya taho masa da motocinsa Ya amsa cikin ladabi sannan ya masa adawo lfy Motarsa ya shiga ya kunna Ac hadi da wani daddan music Ahankali yake tafiya harya fice direct gidan daddy ya nufa cos he wanna see his darkan(heart beat) Lokacin daya shiga bakowa afalo sai talatu mai aiki Bayan sun gaisa yace ina masu gidan Tace yanzu hajiya ta koma amma bada jimawa ba zasu fito karyawa tunda 8 tawuce Zama yayi abinsa ya danna wayarsa Momcy ce ta fito daga side din daddy ganin papa zaune yasa tace papa lfy kuwa kaxo early morning Dago kansa yayi yana murmushi yace morning momcy Morning dear baka ansamun tambayar danayi maka ba Dan shagwabe fiska yayi yace haba momcy mutum da gidansu danyazo sai antambayesa kawai nayimissing naku a lot that's why naxo early morning naganku kafin na tafi office Dariyama abin ya bata cos ta fahimci abinda yake nufi Tabe baki tayi tace good saikataso kayi break toh Yana tashi daddy na fitowa shima cikin mamaki yace Alamin qalau kuwa naganka sassafe Lfy lau daddy nazoyin breakfast ne fa Yace yayi kyau to muje Saida ya gaidashi kafin ya haura dinning ya zauna a permanent seat nasa Fauziyyah ce ta fito cikin shirinta yau takusa makara dan jiya batasamu bacci da wuri ba Ganin papa yasa tadan hade rai shikuma sai wani mayetaccen kallo yakebinta dashi Saida ta gaida daddy da momcy tukun tadanyi kasa da murya kamar dole tace morning ya Alamin hakanma dan su momcy na zaune ne yasa ta gaishesa Da faraasa yace morning dear kesi ho tum(yaya kike) Me tikke ta amsa masa(lfyna lau) That's great ya fada sannan ya cigaba da cin abincinsa Itama zama tayi tayi break nata kafin ta miqe ta masu daddy sallama wadda dama shi ya koma falo ya zauna Tsulum papa ya miqe yace shima ya tafi idan ya biyo to idan kuma bai biyoba sai gobe Suna fita ya nufi motar fauziyyah tana budewa ya shige gefenta ya zauna abinsa Juyowa tayi tana kallonsa akufule tace yeh he kya karehe tum(meye haka kake aikatawa) Dubanta yayi yace kyah(kamar yaya) Tace taya zaka shigomun mota haka baicin kanaga fita zanyi Oh sorry dear nima ai fitan zanyi shine nakeso kuragemun hanya Tace pls kafitamun amotana Yace eyyerh pls kiragemun hanya mana tinda office zani Tace no i cant pls kafita if not gashi ta miqo masa key namotar tace nisai infita Qarema hannunta kallo yake wadda yasha lallen rani Yace aakam keda motarki daman tawance tasami problem amma tinda kinqi shikena Duban jerin motocin sa takeyi amma yace baya da motar da zaifita tabe baki tayi tace shikenan kafin ta tada motar suka tafi Ahanya ba yadda baiba kan tayi maganar amma sam taqi Haka ya haqura ya kyaleta...... ✍🏻Faty Mmn Faty Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty September, 2017 *I dedicated this page to Rahima Aminu Azare (Ummu Afreen), thanks 4 ur prayers, luv n support, I really appreciate,Mmn Faty 😘😍* 5⃣8⃣ Har suka iso hospital kallonta kawai yake yana murmushi cos ta matuqar birgesa D way take driving anatse shiyasake birgesa gashi ta tsuke dan qaramun cute bakinta Saida tayi parking tana daukan jakarta sannan ya bude ya fita Zagayowa yayi ta side nata ya sunkuyo sosai lokacin itama ta bude zata fita Wani killer smile ya mata cikin wani soft voice yace mata shukhriya(nagode) Yana fadin hka ya wuce abinsa baijira amsarta ba dan yasan abune mai wahala ta kulasa Kallo ta bisa dashi kafin ta dauke idanunta ahankali Azuciyarta tace jibesa kamar mutumin kirki baicin dik wata kalar iskanci babu wadda bai iyaba Tsaki tayi kafin ta fice itama dan kada ta makara Shikuna yau hankali kwance ya shiga office nasa koba komai yau ya jima kusa da pyarinsa(mosoyiyarsa) Saida ya kusa tashi kafin ya kira Abdu yazo office ya samesa ya bashi key din motarsa akan yaje ya kawo masa ****** Kwanci tashi babu wuya awajen Allah kwanaki sun shude hakama satittika tareda watanni Yanzu biki saura sati uku kacal duk wasu shirye shirye babu wadda baa gamaba Kama daga kan gidan da zasu zauna su lefe komai anshirya masa sai sauran abinda baa raasa ba Papa kuwa yafi kowa doki da murnan karatowan bikin sai dai haryanzun ya gagara gane kan amarya Daidai da maganar fatan baki bata hadsu sai yazama dole Bayadda baibi da itaba taxo suje gidanta tagani amma fir taqi yadda Haka ya haqura saidai shirye shiryensa bai fasa ba dan biki zaayi na kece raini Biki saura sati dasu wuce dambam acan zaayi hidimar biki sai bayan biki dasu dawo bh Aunty mabarukha kuwa yau take hanya yaranta kuma sai saura two days biki zasuzo da babansu sabida exams dasuke a school Acan dambam ma baa barsu abaya ba dan shiri sosai su Abba suke suma Momcy kuwa tunba yauba tafara hidimar gyara yarta ta kuma surkarta Ita dai fauziyyah dik abinda ake bai dametaba hasalima ma da zaa qara lokacin tanaso Kullum tunaninta ko wanne irin zama dasuyi da ya Alamin Dik da sosai tana ganin canji atare dashi amma dik da haka zuciyarta taqi aminta da shi sabida sanin halinsa boyayye datayi Ita tasan kawai jikinta yakeso yadda kullum bai gajiya da fada mata da turo mata messages na soyayyar qarya Tabarwa Allah zabin alkhairi kawai amma batajin zata yadda tasakeyin zaman qunci agidansa Da daddare suna zaune afalo tare da aunty mabarukha suna ta hira harda aunty niima itama tazo masu sai anjima mijinta zaizo sutafi Aunty mabarukha tace mata sis dubamun abinda na daura awuta mana kada ruwan ya qone sosai idan yayi kauri kawai kisauqeshi ya huce Tace toh sannan ta miqe Tana shiga kitchen papa nashigowa hangota da yayi saiko yayi saurin wucewa yabi bayanta Tana sauqe tukunyar yana shigowa Juyowa tayi taga wane ne ganin shine yasa ta dauke kanta ta kunna famfo tana wanke hannunta Qarasowa yayi ya tsaya abayanta matsota yayi sosai hartana jin sauqar numfashinsa akan dokin wuyanta Shiru tayi tanajin wani iri hakanan ajikinta Murya qasaqasa yace meri darkan(my hrt beat) Menayi ne kike guduna uumm Shiru tayi batace komaiba Sake maimaita mata yayi cikin wata iriyar murya mai kashe jiki yace yakamata ya zuwa yanzun kimfahimci kyakykyawar manufata gamedake Wlh bantaba tunanin na aureki dan na walaqantaki ko wata manufa ta daban ba Inason kisan cewar dik wani hali nawa da kika sani ada yanzun munyi hannun riga dashi Idanma wannan kike tunani toh ki cireshi daga ranki Jin tayi shiru ganan ruwa na zuba takasa qarisa wanke hannunta yasa ya qara samun courage dan yaga kamar magangannunsa sun shigeta kuma sunyi tasiri akanta Sake matsota yayi har kirjinsa na gugan bayanta ya saka hannunsa biyu ya riqo nata yafara wanke mata hannayen dashi baiga wani abu ajikiba da harta tsaya wankewa Santsin hannunta acikin ruwan shiya masa dadi har ya rajaa yana murzawa ahankali Bakinsa ya kawo daidai kunnenta yana cewa idan kina tunanin wani abu nakeso ajikinki kinyi kuskure Nafara sonkine tun kina yanda kike abaya tunkuma banganki ayanzuba Sonki acikin jinina yake pls My Fauzy kibani dama na nuna maki irin kalan sonda nake maki na kuma wanke laifina na baya Yana fadin haka ya kashe ruwan yace i luv u my pretty sannan ya juya ya fice Nan ya barta kamar andasata dan gabadaya maganganunsa kemata yawo akwanyarta Saidai dik da haka bataji wani canjin akan tsanar da tamasa ba ***** Washegari da safe ya kira aunty mabarukha akan ta lallama masa fauziyyah da yamma zaizo su fita zata rakashi wani waje Saida aunty ta wanasa kafin ta amince Haka ta fadama fauziyyah ta shirya 4pm papa zaizo sufita Batayima ta musu ba dan tana matuqar ganin girmnta Haka badan ranta yasoba ta shirya cikin wata doguwar rigar material rainbow colour wacce ta matuqar qarbanta Earing dogi tasaka blue colour sai bangles nata suma passion design ne combination colour Saita yane kanta da blue veil madaidaici Waya ya kirata yace pls ta fito yana mota yana jiranta Takalmanta masu tsini tasaka suma blue colour saita riqe yar qaramar purse nata itama blue colour Masha Allah nan tafito kamar asaceta agudu dan kyau Tunda ta fito ya zuba mata idanu yana kallon takunta cikin natsuwa dan tamatuqar birgesa kuma kwalliyar tayimasa 100% Saida takusa qarasowa ya fito ya bude mata motar Tana isowa yace bismillah My preety Shiga tayi ta zauna sannan ya rufe ya zagayo Ko kallonsa bataiba baran ta gaidashi Inayini rankishi dade yafada yana kallonta Shiru tayi kamar bada ita yakeba Marairaice murya yayi yace haba My Fauzy ko gaisuwan nawama bazaki amsaba Sai anan ta juyo ta kallesa tace pls idan abinda yasa katakureni nafito kenan toh sai anjima tafada tana kokarin bude motar Da sauri yace aa am sorry idan ranki ya baci daga haka baikuma cewa komaiba Ahankali yake tafiya dan yanajin dadin yanayin yau sosai Saida ya iso wani babban super market yayi parking awajen Kallonta yayi yace mujeko n pls kidauki abinda kikeso kinji Rai ahade tace bana buqatar komai I know baki buqatar komai amma irin kinmin rakiyan nan aibai kamata kikoma empty hand ba Tace toh bani buqata Muje to yafada atare suka shiga inda yayima kansa shopping abinda ya kawosa sanna yacigaba jibga kayan ciyeciye da wasu abubuwan amfani na qamshi wannan na fauziyyah ne Harta gaji tace nafa gaji Yace ainagama muje sunzo daidai wajen teddy sai wata baby girl wadda shekatunta bazasu fice uku ba tazo tasha gabansu tanata dariya tana cewa daddy ganan teddyna Daga bayansu sukaji ana cewa fauziyya stop there stop there Jin an ambaci sunan fauziyyah yasa dik suka juya Saidai wa fauziyyah zatagani mutuminda ko ta shekara dari rabonta dashi zata ganeshi dikda kuwa canzawar dataga yayi Shima kallonta ya tsayayi yana tabbatarma kansa itace bawai dikda rabonsa da ita yayi shekaru amma kamanninta bazai bace masa cos her immage is in his heart Qarasowa sukayi shida matar dake gefensa wata black beauty amma ita saita qarasa ta dauki babyn tana cewa oh My Fauzy meyasa bakijin magana kinason kinasani gudune eh Kallon babyn papa ya kumayi jin ankirata da sunan dayafi qauna Murmushi Fauziyyah tayi masa tace uncle yasir dama zansake ganinka arayuwa Shima murmushi yayi yace Fatima Papa ne ya juyo yana masa murmushi tare da miqa masa hannu jin yadda fauziyyah ta kira sunan saiya tuno masa da me wannan sunan Gaisawa sukayi kamar sunsan juna Bayan sungaisa da fauziyyah ya nuna mata matar dake riqe da baby yace this is my wife Jalila n my dauther Fauziyyah Kallonsa tayi tace wannan babynkane kuma sunanta fauziyyah Murmushi yayi sannan yace yeah Gaisawa tayi da matarsa tana kuma mamakin yadda yasir baimanta da itaba tasan kobai fada mataba takwara ya mata Ganin tadanyi shiru yasa yace wannan ne maigidannaki yafada yana nuna papa Gyada masa kanta tayi tace eh nan suka sake gaisawa da papa sannan ya dauki little fauzy Yace mata babyna kinason teddyne Eh uncle tafada tana maqalesa yace ok zabi wadda kikeso insaya maki ko Da fara arta ta dauki manya guda biyu yace sukadai kikeso Tace eh uncle Yana riqe da ita ya qarisa wajen biyan kudi katinsa ya bayar nan aka hadamusu kayayyakin Yariqowa little fauzy nata ya dawo da ita wajen daddynta sannan sukayi sallama suka tafi Haushin yasir ne ya kama papa ganin yadda mood din fauziyyah ya canza daga ganin yasir saikuma aside guda yanajin son babynsu inama su barmasa ita...... ✍🏻 Faty Mmn Faty 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty September, 2017 5⃣9⃣ Fitowa sukayi daya daga cikin masu daukan kaya na biye dasu har mota Saida aka loda kayan a mota sannan ya zagayo side din datake tsaye ta jingina da jikin motar da alamun hankalinta yayi nisa awajen tunani Bude mata qofar yayi kafin yace shall we Saida yasake maimaitawa kafin ahankali ta matso ta shiga ya rufe Zagayowa yayi ya zauna sannan yama motar key yafara tafiya yana tunanin yanayin data shiga one time Zuciyarsa ce ta aminta kan ya tambayeta mene ne damuwarta Juyowa kadan yayi ya kalleta kafin ya maida hankalinsa kan titi Cikin sanyin murya yace My Fauzy kya hua(meke faruwa)naga mood naki ya canza Shiru tayi kamar bada ita yake ba Sake maimaita mata tambayar yayi yana cewa lokacin damuka fito ba haka yanayinki yake ba but lokaci guda kincanza kyiu(meyasa) Pls My Fauzy ki amsamun mana wlh bani qaunar ganinki cikin damuwa Ahankali ta kallesa kadan tace ya Alamin dan Allah kadaina kirana da wannan sunan na roqeqa ta karisa maganar kamar zatayi kuka hawaye na ciko idanuwanta Meye laifi danna kiraki da My Fauzy keba tawa bace uum ko kina manta cewar remain few days kizama mallakina so banga wani damuwaba danna kiraki da My Fa... Baikaiga qarisawa ba yaji tafashe da kuka sosai Subhanallahi haba dear danna fada maki wannan sunan shine bakiso harda kuka to kiyi haquri i promissed u barin sakeba Ganin yanata surutansa ko kulasa bataiba saima cigaba da kukanta da tayi yasa ahankali ya gangara gefen titi yayi parking Lallaminta yafara hadi da bata haquri kancewar bazai kuma mata abinda batasoba kuma tayafe masa Amma fir taqi sauraronsa saima kuka datake sosai Shikuma jin kukan yake har cikin zuciyarsa ganin baya da option kawai saiya dan matso ya jawota jikinsa ya rungume Cikin muryar lallashi yafara magana yana cewa swt hrt am begging u kiyi haquri kibar kukan nan namaki alqawarin koda wasa barin kuma fada makiba tunda bakiso Banason jin kukanki yana tabamun zuciya har cikin raina nakeji Cikin kuka tafara qoqarin janye jikinta tana cewa kadaina bani haquri kabarni nayi kuka shikadaine zai ragemum radadin abinda nakeji Sake riqeta yayi sosai ajikinsa yana patting bayanta smootly Yace nasan abinda yasaki kuka n banson tuna maki kuma saidai inason roqonki kibani damar na gwada maki kalar sonda nake maki wlh nayi alqawarin zan kula dake har qarshen rayuwata bazan taba cutardake ba Kuma da kike kuka sabida ganin yasir bagashiba shima harda matarsa da yarsa So pls kimanta da baya da abinda yafaru kidauka komai Rubutaccen Alamarine bazai kuma canzuba Haka yaita lallaminta da kalamai masu dadi harya samu ta tsagaita kukan sai ajiyar zuciya datakeyi Sunfi 30mins kafin yasamu kanta ahankali ya janye jikinsa daga nata ya tashi motar Suna isowa gida tafice cikin saa tasamu bakowa acikin falo sabida haka ta wuce dakinta kawai ta kwanta Shikuma fitowa yayi ya dauki iyaka kayanta ya wuce ciki dasu Dakinta ya shiga nan yasameta kwance Baice da ita komaiba ya ya ajiye mata ya fice ***** Afannin yasirma ganin fauziyyah ya tayar masa da abinda ya jima yana damunsa amma haka ya danne zuciyarsa ya haqura gudun kada matarsa ta fahimta Kuma baya samum matsala da ita so baison tawajensa asamu rashin jituwa tunda dama tasan da labarin fauziyyah yaukuma taganta ido da ido Kimanin shekaru hudu kenan da auren yasir Bayan sundawo daga dambam akan baisamu auren fauziyyah ba lokacin ya shiga matsanancin hali sosai Saida ya kwanta jinya tun abin yanabawa iyeyensa haushi yafara basu tausayi Da kyar suka samu kansa yadan warware shinefa baffansa ya bashi yarsa ya aura Baiyi musuba ya amince dan yanason ya manta fauziyyah aransa tunda yasan tamasa nisa har abada Itama bataqiba dan dama tajima tanason yasir babanta yana fada mata ta amince Bayan bikinsu da yadda take kula dashi take nuna masa qauna har ta shiga cikin ransa yafara sonta Koda ta haihuma baiboye mataba yace sunan yarsa fatima yakeso kuma ana kiranta da fauziyyah Nanma bataqiba dan burinta ta faranta masa Wannan kenan ***** Tunda aunty mabarukha tazo bata zaunaba sai hidimar gyaran amarya take musamman da wadanda ta dakko masu gyara Dinkunanta ma dik ita ta bada wadda zatayi fitan biki Kuma tundaga ranan papa baikuna saka fauziyyah a idonsaba Saidai yaqaraci surutansa awaya nanma text dan bata daukar wayarsa kam Cikin sati biyu babu abinda ya rage na shirin biki komai ya kankama sai ranan biki kawai ake jira Fauziyyah kuwa tayi natuqar kyau na birgewa dan baqaramin gyara tashaba ga wani sheqi da da santsi da fatarta tayi Washe gari suka tattara suka nufi dambam amma gidan Abba aka kaita sabida dagacan zaa dauki amarya Kuma washegari zaa fara shagalin biki Papa kuma sai aure saura 3days zai iso sabida wasu abokansu sa zasu taho tare kuma ananne zaayi hidimarda zai halatta..... ✍🏻Faty Mmn Faty 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty September, 2017 *This page goes to Mmn Faty Novel Fans, Mmn Faty ta 👍🏻 maku 😘😍* 6⃣0⃣ Washe hari aka fara hidimar biki amma na gargajiyar aladarsu Amarya tayi kyau kamar ba gobe,dikkannin wadan da suka halarcin wannan hidima sunyi san barka dayima papa murnan samun mace kam tare damasa adduar Allah yasa yadda yanayinta yake haka halayenta suke The following day ma haka akasake wani hidimar nanma haka aka watse taro lfy lau Papa nacan bauchi jiyake wane yayi tsuntsu ya taho yaga gimbiyarsa Bayadda baiyiba da Aunty Mabarukha kan ta turo masa pics din Fauziyyah na hidimar biki amma fir taqi tace mene kake sauri badai kaima daka xoba kuma gidanka zaakawo maka ita so nothing to worry about Haka ya dami aunty niima itanma sammaqal dan hada baki sukayi sunfison yaganta azahiri yaga yadda tadawo akwanakin da baiganta ba Ana gobe papa zasu iso da abokanansa akayi sakun lalle namma guri ya burge dan yan uwa anhadu both side na ango da amarya Sai wajen 10pm aka tashi daga taro Jamaar garin dambam sun shaida ana biki afada dan yadda tako ina manyan motoci ke shawagi abinka da bikin manyan mutane maaikata da yan kasuwa Ga yan uwan Abba dana Mama gari gari dik sonzo saikace shine aurenta na fari Papa kuwa yayi juyin duniya akan tadau wayarsa koda muryartane yaji kozaiji sauqin abinda yakeji azuciyarsa Amma sam taqi text kan text daya dametama saita kashe wayartama dan gaba daya bata son damuwa ***** Tunsafe suka kamo hanya inkagansu kace daukar amarya akatafi yadda sukayi comboy na motoci Zumudin papa har bai boyuwa burinsa kawai yasaka tauraruwarsa a idanunsa 12:30pm suka shigo dambam Direct gidan daddy suka wuce inda zasu zauna da friends nasa acan tunda su daddy afada suka sauqa Bayan sunci abinci suka dan kwanta kafin lokacin tafiya KAMU Amma sam papa ya gagara kwanciya burinsa kawai 4pm tayi su wuce wajen KAMUN Ana kiran sallan laasar sunayin sallah suka fara shiri daya daga cikin abokansa guda uku da sukazo daga india yace shikam yau jumper zaisa dan yana shaawar kayan shiyasa yasaka aka dinka masa dan yayi shigar hausawa Ango ne nagani ya dau wanka cikin wani coppee brown yard mai kyau da sheqi Kyansa shiya bayyana tsadarsa Sum matuqar karban fatan jikinsa abinka da farin mutum Ya kafa wata tsadaddiyar huwa Brown covvers yasaka aqafarsa sai agogon azurfa dake daure ahannunsa Ga wani uban qamshi dayake xubawa na musamman Tabbas ya fito a Ango sak👌🏻 Nan fa su Dr khalid suka fara tsokalansa anata barkwanci TJ ne ya kirasa awaya yana dauka yace yane kuna inane Papa yace muna gida amma yanzun zamu wuce TJ yace shine ka azalzalemu ashema baku fitoba to gashinan yanzun haka muna hanya mun dakko amarya Papa yace to sarkin mita naga dai munfiku kusa dawajen ko kafin ku qaraso mun iso muma Ok toh saimun hadu Nan suka fito suka shishshiga motocinsu suka wuce wajen da zaayi KAMUN Su papa suna isowa su TJ ma suka iso Sunsamu angama taruwa amarya kawi da ango ake jira TJ yace basai kunfitoba barin su qaraso naga suna tahowa sannan shima ya fice Ta cikin glass take hangosa shida abokansa suna tahowa sunkuyarda kanta kawai tayi wadda ita kadai tasan yanayin datake ciki Suna qarasowa yasa hannu ya bude motar datake ciki Ya salam shine abinda ya furta ahankali ganin irin kyan datayi Sanye take cikin wani less pich colour mai toches na coppee brown Dinkin riqa a siket wadda yamatuqar qarbanta kaman ba gobe Fiskantannan yasha makeup Dan qaramin bakinnan anlailayesa da pinks jambaki Kyaukam baa magana gashin kantannan sai sheqi da qamshi yake andaureshi waje guda da pich ribbon Sai head na kanta shima coppee brown jeweries natama wasu passion ne dik suma coppee brown masu adon duwarwatsu pich n white Takalminta da purse nata dik coppee brown Ahankali yake sakin wani murmushi wadda shikadai yasan maanarsa Daurewa yayi ya daidaita muryarsa ya kira sunanta cikin wani tattausan murya yace my princess Dago daradaran idanuwanta masu yarwar lashes tayi ta amsa da muryarta mai dadin gaske naam Wani lumshe idanu yayi sannan ya bude yana kallon kwayar idonta wadda yasha kajol da maskara tare da siririn line eye liner Sannan yace meet my friends yana kirga mata sunansu Dik saida suka gaisa kuma sun yaba da zaben abokin nasu Daga qarshe ya introducing mata abokansa uku da sukazo daga india yace yeh he Himesh(wannan shine Himesh), Salman aur Imran(da) Cikin sakin fuska suka gaisa nan TJ ya qaraso yace man kukadai ake jirafa Papa yace ok muje toh duban Fauziyyah yayi yace my princess muje ko Cikin natsuwa ta sako qafarta nan yasake shagala wajen kallon lallen da aka qawata qafarta dashi na zallan jan rani Jerawa sukayi cikin takun qasaita dan jin kansa yake asama qasaisatar ta motsa jinin sarautar ya tsinke Fauziyyah kuwa dik saita jita atakure dake ita bawasu qawaye ke gareta ba kwakwata su shidane sai Suna shiga cikin hall din waje ya kaure da tattausan waqa mai dadin gaske Wajenda aka qawatashi da ado sosai kuma kalan kayansu hatta ballons da aka decourating wajen pich n coppee brown ne Wasu kujeru ne guda biyu iri daya masu kyan gaske suka qarasa suka zauna sai kuma na abokanai da qawaye da aka ajiye daga bayansu Kowa ya shashe ranan angwangwaje naira tayi kuka ko motsi tayi saiyace yadai baby kingaji ne sabida yadda yakeji kamar ya maida ciki dan so Fans na Mmn Faty Novel ma baa bassu abayaba dan sun nuna murnansu sunkuma nunama ma fauziyyah gata Kodagakan irin liki da sukaringa mata shima abin ajinjina masu ne Baa tashi ba sai gabda magriba sannan taro ya watse Ahanyar su ta komawa gidane papa yaga canji yayi juyin duniya fauziyyah tayi magana amma taqi sam shikuma harga Allah baison shirunta shifa ko zaginsane garatayi yasan tayi magana dan baimanta lokacin data kullaci abu aranta tadaina masa magana Haka suka sauqeta suka dawo gida Washe gari Thursday akayi Family n Friends day Nanma sunyi kyau ba qarya Ranan friday akayi Hafla Sai washe gari Saturday misalin Qarfe sha daya na safe dubban jamaa manyan mutane maaikata yankasuwa hadda sarakuna da sauran Alumma suka shaida daurin Auren Dr Muhammad Alamin Abubakar n Fatima Usman abisa sadaki 100k lakadan ba ajalanba Papa dai bakinsa bai rufuwa daka ganshi kasan yana yanayin farin ciki lura daga kayan jikinsa komai fari tass Sai gaisawa yake da jamaa kawai Makada da maroka kuwa sai wasashi sukeyi abindai abin birgewa sai muce Allah ya kade fitina kawai Da yamma akazo daukan amarya Wata goggonsu papa wadda take yace awajensu daddy ita tabada wata Alkyabba ta musamman tace asawa amarya ita Fauziyyah tai kuka harta gode Allah sabida nasihan da su Abba suka mata mai ratsa zuciya da dikkan gangan jiki Da mata adduan Allah yasa sai gawanta zaa fitar agidan Alamin Haka aka wuce da ita fada su anty papa aka samu a side din da zaa sauqi amarya Nan suka karbi amarya da murna da farin ciki gami da mutunchi Nan suka shiga hidima da baki dan Aunty naja(Auntyn Papa ) batada rowa kuma batason harkan qaranta Dik wadda yazo kawo amarya ya yaba da irin kaunar da yan uwan papa kema Fauziyyah sai fatan alheri suke musu Bangare guda Aunty papa ta sauqi Fauziyyahs' team Kuma sun yaba sosai dan Aunty papa bata musu qarantaba ta nuna musu cewar biki ake na dan gata Har wajen magriba fauziyyah taqi yin shiru sai kuka take Saida Aunties dinta suka shigo suka lallasheta sannan tayi shiru Anayin sallan ishai Aunty mabarukha ta kawo mai kwalliya akayima Fauziyyah Wani mterial ne dinkin doguwar riga milk n golding colour tasaka wadda yasha ado sosai yakuma matuqar yimata kyau Kwalliya sosai aka mata sai dan veil din rigar wadda shima golding colour ne tayane kanta dashi Wani danqareren saitin gold Aunty Mabatukha takawo mata tasaka hadda bangkes dinsa manya guda biyu Takalmin hill ne sosai da purse dinsa suma golding colour Wasu turaruka na musamman tafesa wadda dik aunty Mabarukha ce takawo mata su Nan tafito a amaryarta ba qarya Members na Mmn Faty Group sunsha anko dinsu na material Fauziyyahs's team sunyi ankon material golding colour Sai papas' team sukuma ankon material milk colour sukayi Nan aka fara tafiya dinner kowa ya tafi sai Fauziyyah ita kadai akabari dan wannan umarnin Ango ne Tana zaune abakin bed shiru itakadai sai taji motsin bude qofa Bata dago kanta ba amma qamshin turarensa daya gauraye dakin shiya tabbatar mata papa ne Sanye yake da wani dhegen gezna maih danbanzan kyau da tsada Milk colour Dikin yamatuqar amsansa ga hularsa da ta dace da kayan hafi da takalminsa Qaremata kallo kawai ya tsaya yi yana yima ubangiji tasbihi acikin zuciyarsa daya mallaka masa ita amatsayin mata Ahankali ya tako har bakin gadon datake zaune Maganama ya kasa kawai hannunta ya kamo ya riqe gam acikin nasa Wani taushi dayaji shiya haifar masa da kasala lis ajikinsa Dayan hannunsa yasaka yana murza bangles din hannunta Da wata iriyar murya yace my princess pls na roqeki kimun magana kinji Kallonsa tadanyi ta kasan idanunta ta dan turo baki tace to mai zance maka pls kasakemun hannuna Cos yadda yake wasa da hannun nata dik sai taji ta takura Shikuma gyara zamansa yayi yama manta da yabar mutum awaje nan yafara barbada mata maganganun soyayya Qarar wayarsa yasashi yin dan qaramin tsaki dan yana tsaka da jin dadin yadda yake manne da ita bata kuma turesaba Ganin TJ ne yasa yace yane akayi TJ yace lallema toh kawai kace inje insallami mutane tunda kai kasamu waje bazaka fitoba Papa yace oh yaushema nashigo to naji gamunan fitowa Baby nah mujeko kinga wannan dan damuwar da takurin yafara mita Batace dashi komaiba hannunta ya riqo ta miqe suka tako ahankali suka fito.... ✍🏻Faty Mmn Faty Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty September, 2017 *Banmanta dakeba takwarata Fatima Muhammad(Miyatti Allah), nagode da kulawarki gareni Allahu ya bar qauna, Mmn Faty 😘😍* 6⃣1⃣ Hannunsa riqe acikin anata har bakin mota TJ dake tsaye yana jiransu shiya bude mata Da murmushi afiskansa yace bismillah Amaryanmu Batace komaiba sai murmushi datayi sannan ta shiga tazauna Ya rufe kafin ya zagaya ya shiga shima Papama ta gefenta ya zagaya ya zauna Tafiya suke suke bamai cewa komai itadai ta sunkuyar dakanta tana wasa da ring din yatsanta Papa kuwa ya wani matso jikinta kamar wadda zai shige cikinta amma baicewa komai cos hakanma he is totaly satisfied TJ kuwa katse shurun yayi da kunna wani tattausan music mai dadin sauraro Da haka har suka iso Batare da bata lokaciba abokai da qawaye suka rufa musu baya zuwa cikin hall din Lokacin da suka shigo nan aka fara musu ruwan wasu flowers masu kyan gaske da qamshi mai dadi DJ kuwa waqar da aka masu ta biki ya kunna nan waje ya birge sosai Cikin takun natsuwa suka qarasa wajen zamansu kafin kowa ya sami waje ya zauna Baqarya wajen ya qayatu ya kuma matuqar birgewa dan naira tayi kuka Nan aka fara gudanar da programs iri da ban da ban Idan ka kalli Amarya da Ango ka rantse kace wasu couples ne masu mutuwar son junansu Yadda fauziyyah tasake fiskarta kamar bawani abu aqasa Shikuma uban gayyar dama sai faraa yake kamar gonan auduga yana wani shige mata ganin yadda ta saki jikinta tamkar ba itaba Kowa ka gani awajen yasha ado da kwalliya gaskiya bikinsu papa ya matuqar tsaruwa sai fatan zaman lfy Sai wajen 12 aka tashi Saida kowa ya watse ya rage su papa aka bari kafin suka taho suma Ahanya papa yacema TJ man kadaukomin saqona daiko TJ yace waneni namanta yana gaba nan qasan seat Papa yace ok thanks Suna isowa gida TJ ya bude mota ya miqo masa ledan take away sannan ya fice Itama bude qofar motar take qoqarin zata fice Riqo hannunta yayi Juyowa tayi ta sauqe daradaran idanuwanta akansa kafin dan qaramin bakinta ya motsa gami furta lfy daiko Yadda tai maganar ba walwala afiskanta yasa ya marairaice murya yace pls kiban 15mins acikin lokacinki Pls mana dear badan niba dan Allah Komawa tayi tazauna Thanks yafada sannan yasake mata hannu Take away din ya bude pepper chikchen ne wadda yasha hadi sosai Kallonta yayi da kyau kafin yace baby pls bawasa nakeba kici abinci kuma kada kice aa dan nasan wunin yau kaf da wuya idan kinci wani abin Shiru tayi tana tuna tabbas yau bataci wani abinkirkiba Bude motar yayi ya balle bottle din ruwa ya dauraye hannunsa Naman ya kutsiro ya miqo mata saitin bakinta Ba musu ta karba tafara tauna ahankali Ganin yadda batai gardama yasa yaci gaba da bata abaki tanaci Matsowa yayi sosai yana lallabata harta ci sosai kafin ta kauda kanta Ruwa ya bata tasha sannan ya bude mata roban juice sai anan ta kauda kanta tace umum Murmushi yayi yace thanks a lot wifey nagode muje narakaki ko Aa kawai tace dashi tafice abinta ***** Washe gari sunday akayi walimah dasafe daganan wasu suka fara tafiya garuruwansu Amma su papa sai gobe dasu koma bh Abdu yasa ya maida su Himesh bh sabida gobe jirgin safe zasubi zuwa lagos dagacan su wuce Abokanansu dik sun koma TJ ne bai tafiba sai gobe zasu wuce tare da Ango Itama qawayenta dasukazo daga bh guda biyu sun koma sauran ukun dama yan uwane Haka ta yini shiru itakadai su aunty mabarukha ma basu zannaba sabida sallamar baqi Shima haka ya wuni sallama da baqi gashi sunje gidan Abbama sunjima acan Sai dare aunty mabarukha ta shigo nan tace tana da magana da ita Gyara zamanta tana sauraronta Aunty mabarukha tace abinda zan fada maki kidauka ni yar uwarkice kuma ciki daya kikuma dauka bansan papa banida alaqa dashi Taci gaba dacewa inason kidauki wannan auren yana cikin kaddaranki arayuwa wanda baki isa kikaucewaba Kuma tunda har Allah ya rubuta haka inason ki haqura kidauki qaddara ki rungumi mijinki kimasa biyayyar aure Dik halin da kuke ciki da papa ina sane amma yanzun tunda andaura maku aure zance ya qare Kuma bama fata abinda zai kuma rabaku sai dai mutuwa Jikintane yayi sanyi kuma ko itama tunanin datake aranta kenan tunda Allah ya qaddari haka tafaru gara ta dau haquri suzauna lfy Aunty mabarukha tace sabida haka kidauka dik abinda yafaru abaya kamar bai faruba kuma bama fatan ya kuma faruwa Kuma ina da tabbacin hakan bazai faruba sabida yanzun papa yana sonki so mai tsananin gaske kuma zai iya komai akanki Amma bawai ina nufin dakunkoma bh kibada kai bori ya hauba aa ki nuna masa cewar kema mace ce Saikin dan wanasa tukun saiki saqqo ku zauna lfy Allah ya albarkaceku Sannan kada ki kuskura kiyadda kunya ta cuceki dan matuqar zakiji kunyan yin wani abin toko zaki kwari kanki Gobe akwai kayan dazan kawo maki idan kinkoma bh Su zaki ringa sawa agida kina kwalliya tareda yin qayataccen girki kuma kada kihanasa Kibashi dik tarkone yadda zaiji kawai bazai iya rayuwa bakeba kuma komai kikace yamaki zai maki Amma kada kimanta kina riqe da class naki harsai yagane kuransa yadda koda kudi akabasa bazai tabayin gigin batamaki raiba Dafatan kinfahimceni Cikin sanyin murya tace insha Allahu aunty zanyi yadda kikafada Aunty tace yawwa qanwata Allah ya maku albarka sannan zanyi magana da Aunty naja(Aunty Papa )tace zatana aiko maku da abinci zance tabari kawai sabida musamu tarkon ya kamashi Tace toh aunty nagode Allah yabar zumunci Miqewa tayi tace barinje wajen momcy sabida shirin tafiya amma zandawo mukwana tare Tace toh saikin dawo itakuma ta fice Shiru tayi tana tuna maganganun da aunty tafada mata tabbas gaskiyane Da haka har bacci ya kwasheta sabida dama agajiye take batamaji shigowar Aunty ba Washegari wajen laasar suka iso bh Direct gidanta aka wuce ta da ita wannan umarnin daddy ne Shima papa gidan ya taho yayi wanka sannan ya fita amsa kiran daddy baiko leqa taba dan yasan tana tare da mutane Aunty ma cewa tayi bari taje gida zata aiko hannatu mai aikinta wadda tare sukazo da driver su kawo mata wannan sakon Nan sukayi sallama akan suma gobe zasu wuce Su Aunty niima ma cewa sukayi tafiya zasuyi dik suka watse suka barta ita kadai Suna zolayarta ainty ce tace Allah ya kaimu next year kamar haka muzo musha suna Aunty niima tace aikin kai da nisa dama cewa kikayi nanda 9months kinaga yadda papa ke rawan kannan ai kinsan basauqi Itadai batace komaiba dan kunyama suka bata Bayan sun tafi itama ta fito tafara zagaya gidan Tana kallon yadda aka barar da dukiya tundaga kan ginin har izuwa kayan cikin gidan Ta jinjinama daddy takuma gode masa dan baqaramin rawar gani ya takaba Tsayawa fasalta kyan gidanma bata lokane mai karatu fasalta da kanka kawai Sai datayi sallan magriba da ishai sannan tashiga qayataccen toilet dinta ta sheqa wanka Kwalliya tayi sosai cikin atamfa lemon green mai matuqar kyau Tayi kyau abinta dambun naman da momcy ta aiko mata lokacin da aka kawo mata saqon aunty mabarukha shitaci ta koshi abinta Lfyr gado tabi tadau wayarta ta hau facebook tana maida saqon fatan alkhairi da aka turo mata na biki Papa kuwa ahanyarsa ta dawowa gida saida ya tsaya ya sai masu tsaraban irin wadda ango ke kawoma Amarya Hankalinsa dik yana wajen Fauzynsa dan yasan ita kadaice agida Yana zuwa bakin gate ya danna horn maigadi ya bude masa ya shige Parking yayi sannan ya dauko ledodin daya saya ahanya ya nufo gida Kamar zai wuce dakinsa amma saiyaji ina baxai iyaba saiyaga lfyrta tukun Tana kwance taji anturo qofar anshigo tare da sallama Dago kanta tayi kallo daya taimasa tasauqe kanta Cikiciki ta amsa sallamarma Shikuma wani murmushi yayi ganin yadda kwalliyar tamata kyau saita sake shiga ransa Takowa yayi ya ajiye ledodin hannunsa ya qarasa bakin gadon ya zauna kusa da ita Sai anan ta dago kanta fiska atamke take kallon yadda ya wani zauna kamar zai rugumeta Why have u come here? Tafada tana kallonsa Murmushi yayi mai qayatarda face nasa yace nazo ne naga yadda kika yini nakuma miki bangajiya konayi laifine yin hakan baby na Eh,tafada Cikin sauri ya dubeta yace bakiso kenan na duba lfyrki Banaso nanma tafada kanta tsaye tareda juya masa baya Jikinsane yayi sanyi cikin sanyin murya ya fara magana I really understand why u ar very angry Juyowa tayi tace ya Alamin i don't want any discussion, it will be better for u to getout of my room, pls go now Shiru ya danyi kafin yafara magana da muryar nadama yace baby i do not have the courage to look in to ur eyes N there's no doubt that i had made a mistake n it is true that i regret everything that i have done Naji naji pls saida safe banason dogon zance tafada tana juyawa Yace to kifadamun abinda zanmaki wanda zai zama punishment agareni ke kuma ki huce Tace maganace banason kamun inhar ba nice na nema ba thats all Shiru yayi yana jinjina maganar amma bayadda ya iya dole ya amince Cikin murya mai sanyi yace ok naji inhar hakan zaisa kihuce kuma kiyafemun i accept this punishment Yana fadin haka ya miqe jiki amace tare dace mata ga Abinci kici kada ki kwanta da yunwa kafin yafice zuciyarsa wani iri yana sakejin tsanar kansa dan yasan shiya jama kansa..... ✍🏻Faty Mmn Faty Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty September, 2017 *Wannan shafin nakine PA ta (Ummy Danees), Banmanta dake ba kina raina Allah ya barmu tare da Qaunar juna Mmn Faty luvs u 😘😍* 6⃣2⃣ Yana fita ta gyara kwanciyarta abinta taci gaba da abinda takeyi da wayarta Sai wajen 10 sannan ta kashe data ta sauqa, kayanta ta canja zuwa na bacci tabi lfyr gado abinta Baccinta tasha hankali kwance ko juyi bataiba har asuba sabida gajiyar hayaniyar biki Kiran sallan farko alarm na wayarta ya tasheta Ita kanta tayi mamakin yadda tasha bacci babu ko farkawa Toilet taje ta dauro Alwala tadawo tafara nafila kamar yadda kullum tasaba Saida aka kira sallan asuba sannan tayi rakaa tainil fajr Tayi sallar asuba kafin ta bude Alquraninta tafara karatu har haske ya fito sannan ta rufe tayi adduo inta ****** Papa kuwa yana fita dakinsa ya wuce Yana shiga ya rage kayan jikinsa ya fice toilet Ruwa ya watsa ya dauro towel ya fito, dik abinda yake zuciyarsa a jagule yakejinta Dan cream ya shafa nanma samasama sannan ya saka kayan baccinsa ya kwanta Tunani kalakala su suka addabi zuciyarsa Tuno kalaman daddy yayi akan gargadin daya masa kan kada koda wasa yaji wani abu marar dadi wadda yayima fauziyyah Idan kuma haka tafaru to tabbas zai fiskanci fushinsa kuma fushi mai tsanani Afili ya furta babu abinda zai faru da yardar Allah Da tunanin ko yaushe fauziyyah zata saqqo ta daina fushi dashi har bacci ya daukesa amma bada wuriba Sai asuba ya farka agurguje ya shiga toilet ya watsa ruwa hadi da alwala ya fito Wata milk jallabiya ya saka sannan ya fice masallacin kusa dasu 5:30am ya shigo gida Upstairs ya haura ziciyarsa tana kokwanton shin ya leqa fauziyyah yaga ta tashine kuma ya ta kwana Amma kuma yana tuna alqawarinda yamata Haka ya haqura ya wuce dakinsa amma zuciyarsa tana can wajen Fauzynsa Falonsa ya kwanta ya kunna BBC news ***** Wajen six ta tashi ta maida Alquraninta wajen zamansa Ta nade sallayar da hijab dinta ta dan kwanta Sai 8 sannan ta tashi ta fito falo ko mai tsaf yake amma haka tadan gyara Daganan tasaqqo downstairs nanma tadan gyara kafin ta kunna bourner da aquarium Nan da nan ko ina ya hade da qamshi mai sanyaya zuciya Sama ta koma ta fesa wanka tazauna ta fesa kwalliya sosai Jakar kayan da Aunty ta aiko mata ta bude Dik wadda ta dago saitaji bazata iya sakawa ajikintaba dan gaba daya kayan kunya suka bata Shiru tayi tana tuna maganganun Auntyn kawai ta dauki wani brown tied troser da coppee top Wandon har qasa sai dai yabi jikinta ya lafe sai top din ta kusa guiwanta mai guntun hannu Sunmata kyau sosai, dan qaramin coppee veil ta dauka ta daura akanta Nan tafito cass da ita Flat brown shoes tasaka ta fesa turare ta fito Kitchen ta shiga lokacin har 9 Breakfast mai rai da motsi ta hada nan kitchen ya karade da qamshin girki bada jimawaba ta hada komai ta kai dinning ta jere komai 10:30am ta zauna ta zuba nata tafaraci hankali kwance 10am ya fito awanka ya shirya cikin wata boyel silver colour da layin brown half jumber ce dinkin Sunmasa kyau baisa hula ba sai gyara kansa da yayi wadda yaketa sheqi da qamshi Turarensa ya fesa mai dadi sannan ya fito da niyyar ya leqata ya tamvayeta dame zata karya yasa akawo masu Yana fitowa daga falonsa yaji ya shaqi wani lallausan qamshi Lumshe manyan idanunwansa yayi ya bude ahankali Yana zuwa wajen steps nan ya fahimci lalle ta tashi dan wani qamshi nadaban yake jiyowa daga qasa sabida haka ya saqqo qasa shima Ko ina ya kalla sai sheqi da qamshi yake hakan yasa yasakejin wani sabon sonta aransa Kamar motsi ya jiyo a dinning room shiyasa ya wuce can Nanfa yayi mutuwar tsaye yadda yaganta cikin irin kwalliyar dayafison ganin mace dashi Tanacin abincinta hankali kwance cikin natsuwa Azuciyarsa yace komai nata unique Sarai ta fahimci zuwansa wajen dan taji takun tafiyarsa sannan taji qamshin turarensa Amma saita basar kawai abinta da tattausan muryansa mai dadi yace Assalamu alaikum Waalaikumussalam ta amsa batareda ta dago kanta ba Murmushi yayi jin muryarta mai dadi Qarasowa yayi ya dafa kujeran gefenta da hannunsa biyu yana zuba wani niimtaccen murmushi Ahankali tace ina kwana Lfy lau my princess kintashi lfy Shiru bata amsashiba cos batason dogon magana Hakanma yaji dadi koba komai ta mutuntashi Umm baby badai girki kikayiba am so sorry namakara ko Daman yanzun zan tambayeki abinda kikesone sai akawo mana ashe kintashi nine namakara Da wata murya mai jan hankali tace no ba komai kawai bani buqatar abincin wani waje bismillah idan kanada buqata Wani sanyi yaji acikin ransa yadda muryar take sauqa acikin kunnensa ok thanks baby yafada yana jan kujeran Zama yayi ya serving kansa yafaracin abincin Dadi sosai abincin ya masa kuma ya bata lambar yabo afagen girki dan baitaba tunanin ta iya girki haka ba Itakuma ajiye spoon nata tayi tasha tea dinta sannan ta miqe Ta dauke plate din tayi kitchen Idanunsa qur akanta yana kallon salon tafiyanta Jiyayi inama yaje ya rungumeta yaji dumin jikinta kozaiji sanyi aransa Fitowa tayi ta wucesa yana ta saqa wasiqar jaki Nanfa yaji anya zai iya zuba mata idanu kawai yana kallonta tana masa kwalele Wata zuciyar tace toya zaka mata forcing nata zakayi Shiru yadanyi yaga gara yabita ahankali harta saqqo yafi masa sauqi Tunda ta koma daki take waya da mutane har wajen 11:39 Sannan ta kwanta nan bacci yayi gaba da ita Sai azahar ta tashi tayi sallah ta fito kitchen Lunch mai lafiya ta shirya masu sannan ta dawo daki tayi wanka tare da sallan laasar Shiryawa tayi cikin wata swiss orange colour dinkin riga da zani Tayi kyau iyaka kyau sannan ta fito dan taci abinci Tana sauqowa falon qasa yana shigowa daga masallaci Wani kallon qurillah yake binta dashi harta iso kan steps din dining kusa da inda yake tsaye Kamar bataso tace ga nan lunch inkana da buqata tana fadin haka ta wuce Yama gagara magana sai bin bayanta da yayi Fried rice ce tasha kayan lambu da chips sai pepper chikchen ta masu Zama yayi yaci abinsa amma kaf hankalinsa yana kanta Ta rigasa tashi ta dawo falo ta zauna ta kunna cinema tana kallo Saida ya kammala sannan ya dawo falo Direct inda take ya nufo ya zauna agefenta dab da ita kafin ya saka hannunsa ya jawota jikinsa ya matseta gam Wani kallo ta watsa masa tace meye haka ya Alamin baqaramin kasala ne ya sauqo masa ba jinta ajikinsa ga wani taushi da fatanta keda dawani qamshi na musamman Murya can qasan maqoshi yace mene kuma baby kawai zanbada tukuicin kwalliyannan ne Bata ankaraba taji ya kai bakinsa kan nata yana wani sauqe numfashi hadi da sake matseta sosai Mutsu mutsu tafara dan yadda ya matseta sosai cikin haka har suka dunguro kasan carfet Nan ya kuma samun yadda yakeso Saida ya kashe mata jiki sosai yadanji natsuwa yazo masa kafin yafahimci ashe hawaye takeyi ba halin kuka tunda ya riqe baqin kamar mintin lolly pop Dagota yayi yafara lallashi da kasalalliyar muryarsa yake fadin pls babyna kiyi haquri ba yadda zanyui ne nakasa controlling kaina I luv u baby pls kada kiyi fushi dani wlh sonkine sanadi Cikin muryar kuka tace nikasakeni Naji amma saikin cemun kin haqura kuma bakiyi fushiba Nodding kanta tayi Yace u mean kinhaqura Sake nodding kanta tayi yace thanks babyna thanks i luv u sannan yasaketa Itakuma daki ta wuce tana shiga tafada agado tana maida numfashi Dan baqaramin kashe mata jiki yayiba Sannan tanajin wani abu acikin dikkannin jikinta wanda batasan mene ne ba Tana nan kwance tana tunanin abinda papa ya mata cikin sauri ta rufe idanunta saitaji kunya ya kamata Amma abin mamaki ko kadan bataji haushinsa ba saidai kawai batason hakan Papane ya shigo har bakin gadon ya tsugunnan da murya mai dadi yace babyna bacci kikejine Shiru batace komaiba yace pls kidanzo mana Aunty naja ne tazo inyaso idan ta tafi saiki dawo ki kwanta kinjiko Turo baki tayi tace niba bacci nakejiba Yace toh zakizo kugaisako Tace naji katafi aidai zanzo Murmushi yayi dan yafahimci batason suhada ido ne Miqewa yayi ya fice Dan gyara fiskanta tayi ta fito Da faraa suka gaisa Dan dama sunsan juna fauziyyah tace inasu sopy Tace suntafi islamiyyah amma ai zasuzo ranan da ba islamiyya Nan sukadanyi hira kafin tace zata koma kada yan makaranta sudawo bata nan Papa ne yarakota har bakin gate din gidanta tunda tsakaninsu gida biyune kawai Nan tasake fada masa dabarun zaman aure baran ma dake tasan cewar yanayin dasuke ciki dan itace abokiyar shawaransa Abinda taita maimaita masa shine ya lallamata karya gajiya ya kuma ringa kyautata mata komai zaiyi setling da yardar Allah...... ✍🏻Faty Mmn Faty . 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty September, 2017 6⃣3⃣ Godiya yamata sosai sannan ya dawo gida Azaune ya sameta tana waya dankwalinta ahannu sai dariya take ko ita dawa oho Shagala yayi wajen kallon yalwataccen gashin kanta Wanda yasha gyara sai sheqi yake Kamar yaqarasa ya shafa haka yakejin wani abu na fisgarsa amma sai ya daure zuciyarsa ya wuce kitchen Plates da sukaci abinci ya hada ya wanke sannan ya fara mopping kitchen din Itakuma abinda ya zaunar da ita afalon kenan wayar datake akan data qare zatazo ta gyara komai Yana cikin mopping din ta shigo Dago kansa yayi yana mata murmushi kafin yace kina buqatar wani abune akawo maki Cikin mamaki take kallonsa amma saita dake tace umum Nanma murmushi ya sake mata yace ok kada nabata maki jiki da ruwa ko baby barin qarasa Juyawa tayi tana mamaki aranta lalle tabbas ya Alamin ya canza Dakinta ta koma ta shirya kayayyakinta dasuke cikin jakukkuna a drawer har aka kira sallan magrib bata gamaba Bari tayi tayi sallah sannan ta qarasa Sai bayan tayi sallan ishai sannan tayi wanka Simple makeup tayi amma tayi kyqu abinta, wani black boonshort tasaka da wata yar miciciyar riga milk colour wacce dakadan ta wuce cibiyarta Afalonta tazauna tana kallon ZEE CINEMA a DSTV batada niyyar fita that's why tasaka wadannan kayan n she didn't think akan shima zai shigo mata dakiba tunda rabonsa da dakin tun jiya Tashagala tana kallonta kawai taji an turo qofar anshigo Cikin sauri ta dago kanta tana kallon qofan Shikuma yana shigowa ya daskare awajen sabida tana zaune akujeran dake kallon qofa so dik wadda ke zaune awajen kana shigowa zaka ganshi Dauke kanta tayi tana tunanin ta tashi ne tanemi abinda zata lulluba jikinta amma sai taga gara ta haqura kanta tashin White T-shirt ce ajikinsa da black 3quater sai qamshi yake zubawa hannunsa riqe da leather Shigowa yayi har kusa da ita kafin ya zauna yana ajiye abin hannunsa akan table dake gabanta Wani mayen kallo dayake binta dashi lokaci guda zuciyarsa ta kwadaitu da abubuwa da dama Matsota yayi sosai kamar zai shige jikinta Itakuma banda qirjinta dake dukan uku uku hadi dawani yarr dataji lokacin da jikinsu ya hadu Hannunsa yasa ya zagayo neck nata yana wasa da hannun rigarta Dan zamewa yayi yamaida tsayinsu daidai ya kwantarda kansa akan arms nata Ganin yadda yakanainayeta yasa ta daure tace ya Alamin maiyasa kakemun hakane Hancinsa yakai yana shinshina wuyanta yace mekenan namaki umm Batarai tayi kamar zatayi kuka tace abinda banaso kakemun Allah kana takurin rayuwata sai hawaye sharr Bakinsa yakai ya lashe hawayen tass sannan yace baby maganafa kawai kikace kada nasake maki kuma tunda nashigo bance dake komaiba Hasalima abinci nakawo maki amma bansan yadda zan fadamaki kizo kiciba Yana maganar yanabin laps nata da tafiyan tsutsa Taushin dayakeji yasa yasake matsanta sosai Toh naji pls kasakeni kuma ni aqoshe nake Ok naji kinqoshi toh ina zakije ba kallo naga kinayiba Nidai daki zanje dama nagaji da kallon Kallon bakinta kawai yake yana murmushi dan komai tayi birgesa take Hannunsa yakai ya shafi labbanta yana fadin bansan danqaramin bakinnan da qarya bafa Turo baki tayi tana yunqurin tashi aiko yasa hannu yamaidata yadan kifo kadan yamata rumfa da faffadan kirjinsa Sai idanu take zarewa tsabar tsoro hadi da numfarfashi kamar wacce tai wasan tsere Shi dariyama tabasa aransa yace oh ashe haryanzun tsorontannan yana nan Cikin wata kasalalliyar murya yace baby lfy kike sauqe numfashi kamar kindau abu mai nauyi baicin ni ban dannekiba Yana maganar ya kwantar da kansa a Kan qirjinta Wani niimane ya sauqo masa nan yakai hannunsa yazame ribbon dake kanta yana shafa gashin kanta Bari jikinta yafara gawani irin abu datakeji tundaga dan yatsan kafarta hat kanta Shima abinda yakeji kenan har yafara rasa natsuwarsa hannunsa ya sauqe daga kanta ya daura akan qirjinta ya salam wani yanayi na musamman yasamu kansa aciki Nanfa suka fara kokuwa ala tilas wai zata hanasa Shikuma yadda hankalisa ya tashi idanunsa suka qanqance baiko saurara mata ba saima danneta da yayi sosai yasamu ya rabata da dan rigar jikinta wacce dama tafi babu Aiko idanunsa sunakaiwa wannan waje yasakejin wani feeling ba bata lokaci yakai bakisa da hannunsa dumudumu kamar kura ta samu nama haka yashiga hidima Salon dayake mata yasa jikinta ya mutu murus sai hawaye kawai dake ambaliya afiskanta Hannunsa ya sauqe kan qugunta zuwa cinyoyinta yana shafawa bakinsa na lasan... Saida yasha budurinsa sosai kafin yasamu yaji yayi.... Sannan ya qanqameta lokaci guda jikinsa yayi laasar ko motsin kirki kasawa yayi Ganin yayi shiru yadaina abinda yake mata yasa tayi tunanin kukantane ya kwaceta bayan batasan cewar alqawari yayima kansa kan zai daure zuciyarsa bazai kusancetaba har saita aminta dashi komai ya daidaita atsakaninsu Amma zaike rage zafi kuma da haka yakeso ya dasa mata qaunarsa aranta Yakai 10mins ahaka kafin ya dago kansa yana kallon kyakykyawar fiskanta Idanunta arufe sai ruwan hawaye Dan hada rai yayi kafin yace baby zakici abincin ko har yanzun aqoshe kike Zumburo masa baki tayi tace nikadagani bazanciba Yace ok baki gamsuba kenan amaimaita class amma kuma tazarce zamuyi har inda kike tsoron Jin abinda yafada yasa tafara bashi haquri Yace najito amma saikinci abinnan dan bazaki kwana da yunwa ba Cikin sauri tace zanci Yace good amma yanzun zakici agabana Murya can kasa tace Allah zanci amma bayanzuba Murmushi yayi dan yafahimci jikinta yayi weak sosai sai yace ok amma kimin alqawarin zakici Ahankali tace nayi Tashi yayi yanajin jikinsa amace ya ce goodnight my princess sannan ya fice Kaitsaye toilet ya shige yana shiga dakinsa Wanka yayi ya tsaftace jikinsa sannan y sauya kaya zuwa kayam bacci kafin yakwanta zuciyarsa fess sai murmushi yakeyi yana tuna yanayin daya samu kansa aciki Lalle Allah yayima Fauziyyah baiwa iri da ban da ban Da tunaninta bacci yayi gaba dashi harda mafarki barkatai ***** Yana fita tasamu ta miqe da kyar ta shiga cikin bedroom nata Wanka tayi itam cos taga baqon abu atattare da ita sai anan tadanji qarfin jikinta Falo tadawo ta zauna bude abinda ya kawo mata Shawarma ce anade da duminta sai aroma dake tashi Dayan kuma takeaway na gasmeat ne Haka taci ta qoshi ta kora ruwa mai sanyi sai bacci nan tashige daki abinta ta kwanta Sai dai sam bacci ya gagareta sai tunani papa daya addabeta lalle ya alamin ya iya luv abinda tafada aranta kenan Tundaga ranan tasauya salonta bata taba yadda papa yayi koda qaramin wasa da ita Daya kusantota zata fara kuka tana cewa idan yana qaunar Allah yarabu da ita tunda ba dole Shikuma bai kaunar yabata mata rai haka zai kyaleta Gashi kullum cikin tayar masa da hankali take wajen daukar wanka da kaya masu jan hankali Kullum burinsa ya kyautata mata aikin gidama kusan 50-50 sukeyi kafin ta tashi zai rigata tashi yayi shara mopping ya kunna burner ko ina ya bule da qamshi Amma abanza Fauziyyah batada niyyar sauqowama dan yanzu maganama bata cika hadasu ba yayi iyaka yinsa harya haqura ya kyaleta saidai baifasa kyautata mata da fada mata kalamai masu dadi na soyayyah ba *2months later* Yanzu kimanin watansu biyu da aure kenan Kullum papa baida abinda ya fice ganin ya kyautatamata ya sanyata farinciki Ko office ya fita harya dawo hankalinsa yana gunta Ya sayo mata wannan wancan dik dan ya birgeta yakeyin hakan Damuwarsa daya yadda yake fama da shaawarta amma ita batada niyyar saurara masa haka yake danne zuciyarsa Afannin fauziyyah kuwa tun tanajin wani baqon Alamari gameda papa Tunbatasan mene neba harta fahimci zuciyarta takamu da sonsa Ahankali ta fahimci lalle zuciya tana son maisonta kuma mai kyautata mata Wani irinso takejin tana masa wadda bata taba yima wani mahaluqi ba Takuma gane ashe yasirma son yarinta tamasa Saida kuma ta gagara daina quntata masa dikda komai zata masa bai nunawa at last ta realizing cewa lalle papa yanasonta sona haqiqa na gaskiya Amma ta gagara nuna masa hakan koyaushe saita ringa nuna masa baigabanta sam kuma ta gagara daina hakan dan yanzun dakanta idan tamasa abu saiya dameta taji dama bata aikata hakanba Amma abubuwa da dama taragemasa tunda idan tamasu abinci komabai kusa data leqa dakinsa dikda iyakarta bakin qofa tace yazo suci abinci sabanin da sai dai insanda yafito dan kansa Yau dawuri ya taso office itakuma batajeba kasancewar Friday ne Da yamma lis yasmeta zaune afalo Barka da hutawa baby yafada fiskansa dauke da qayataccen murmushi Uhum kawai tafada batareda da ta dago ba daga danna wayarta datake Barinje gidan aunty naja dagacan zanwuce masjid sai after isha zandawo Ok kawai tafada shikuma ya wuce dan inda sabo yasaba da halin ko inkula datake nuna masa Yana wucewa tabi bayansa da kallo harya fice sannan ta zame ta kwanta tana roqon Allah yasa ta sassauta zuciyarta ta kyautatawa mijinta Yana fita gidan Aunty Naja ya nufa afalo yasameta suna kallo itada da yara kasancewar friday babu islamiyyah Yana sallama oga ya taso da gudu ya rungumesa yana oyoyo uncle Papa ya dgashi sama yana cewa oyoyo my boy Zama yayi ya daura oga akan cinyansa suna gaisawa da aunty Bayana sun gaisa tacema su sopy oya kuwuce dakinku kuje kuyi kallon acan Ta dubi oga daya dane cinya tace harkaima dakake wani lafewa tashi kabisu Papa yace da anbarmin abokuna ai Tace rabu dashi damunka zaiyi da qiriniya Bayan sun wucene ta dubi papa tace ya Fauziyyah dai yanzunkam komai normal ko Dan sosa qeyarsa yayi yana cewa umm ai rikicecciyace ammadai yanzun tarage fitina Tace banganeba wai haryanzun bakasamo kantaba Cikin muryar tausayi yace ai aunty rikicinta sai a hankali Da mamaki ta dubesa tace kada kacemun kaikuma zuba mata idanu kayi kake kallonta Yace to yazan mata ninafison saita fara sona ta aminta dani Tace so na biyu ko na nawa ai dik wanda yaje gidanku yazauna daku na awa daya zai fahimci fauziyyaha tana sonka kawai pretending takeyi kaikuma idanunka sun rufe ka kasa fahimtar haka Yace to nidai kawai ina lallabatane muzauna lfy tinda banida option Tace kana da option kuma cikin ruwan sanyi zaka samu kanta Nan tafada masa yadda zaibi Nidai banji maitaceba dan yadda tayi maganar ahankali Sai kawai naga yanata dariya dan mganar dariya tabashi Yace kai aunty bakida dama Itanma dariya tayi tace kaidai kawai kayi yadda nafada maka Saida aka kira sallan magriba yatafi Baikoma gidaba sai bayan da yayi sallan isha tukun Lokcin daya shigo bata falo yaji dadin haka sai ya wuce dakinsa Toilet ya shiga yayi wanka da ruwa mai zafin gaske dik da shiba maabocin muamala da ruwa mai zafi bane sosai amma haka ya daure nan jikinsa ya dau dumi Cikin sauri yasaka kaya ya shige bargo ya rufu Baifi 5mins ba da kwanciya ta leqo falonsa taga bayanan saita leqo dakinsa taga koya dawo yafito suci abinci Ahankali ta tura qofar ganin wutan dakin akunne yasa tafahimci ya dawo Shiga tayi ta tsaya abakin qofa ganinsa akwance akuma qudundune cikin bargo yasa tayi tunanin lfy Cikin sanyin murya tace kafito muci abinci Murya na rawa kamar mai zazzabin daya masa mummunan kamu yace kije kici kawai bazan iya ciba Harya juya saita kasa tafiya dan yadda tai voice nasa tasan ba lfy ba to amma mai yasamesa lokaci guda baicin dazun ya fita lfy lfy ta tambayi kanta Juyowa tayi ta tako har bakin bed inda yake kwance sai rawar sanyi yake kamar gaske Nanmada ta tsorata dayanayin data gansa Hankali tashe tace ya Alamin mene yasa meka Jin yadda tai maganar adame yasan tarkonsa ya kama bushiya Sake shaqe murya yayi yace baby am sick banajin dadi fever ke damina Fever tafada tana zare idanu Daga kansa yayi irin bai iya amsawannan Nam take taji wani tausayinsa ya dirar mata dan bata taba ganinsa cikin wannan yanayi hakaba Sannu Allah ya sauwaqa amma lfy kafita ko dama kanajinsa ajikinka Tai magnar tana miqa hannunta jikin wuyansa ta taba Nan taji zafi zau..... *Gaisuwa mai tarin yawa agareki Auntyn Papa Mmn Faty ta👍🏻* ✍🏻Faty Mmn Faty 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty September, 2017 6⃣4⃣ Wani sabon tausayinsane ya dirar mata lokaci guda Banda shaking ba abinda jikinsa keyi, kansa kawai ya iya gyada mata Haka kawai taji bazata iya tafiya ta barshi awannan yanayinba Zama tayi akan bedside drawer tadaura hannunta akan goshinsa Murya ahankali tace toh kanemi magani kasha kaji tafada tana kallonsa Murya ashaqe yace nasha bayan nashigo Cikin tausayi tace toh Allah ya sauwaqa Ganin yadda gabadaya yanayinta ya sauya ta shiga damuwa sai kawai yadan razana kamar wani abin tsoro yagani Cikin sauri ta riqosa ta qanqamesa tana cewa subhanalillahi ya Alamin menene? Sake razana yayi ya qanqameta shima aifa nan tafara kuka hawaye wani nabin wani tana cewa meya sameka kamin magana mana sai kuka take dik tafirgita da yanayinsa Yadda hankalinta ya tashi sosai saiyaji tausayinta ya kamasa Ahankali yake cemata relax baby ba abinda zaisameni haka fever na yake so ki kwantar da hankali kinji Da muryar kuka tace aa kam kodai nakira momcy awayane akaika hospital Aa baby kada kitayar masu da hankali nafarajin sauqi ma da yardar Allah zansami sauqi Ganin yafara samun natsuwa ya kuma rungumeta ya lafe ajikinta yana sauqe numfashi yasa tadan tsagaita da kukan amma batabar hawayeba Sunkai 10mins ahaka kafin ahankali yace baby zafi nakeji sosai Zafi kakeji ya Alamin tafada tana goge masa zufan goshinsa Gyada kansa yayi yace sosaima Yaye masa blanket din tayi ganin dik jikinsa ya jike da zufa irin alamun sauqan zazzabi Tace Alhamdulillah aizafin nasauqan zazzabin ne sannu ya Alamin Allah ya sauwaqa Lumshe idanunsa yayi yace Amin baby nagode da kulawarki gareni Murmushi mai sanyi tamasa tace bakomai kona qaramaka qarfin AC dinne Yace qaramun baby , toh tafada tadauki remote din taqara masa qarfin AC din Nan da nan sanyi mai dadi ya karade dakin Cikin kulawa tace ko zakayi wankane kadan sami qarfin jikinka Kwantarda kansa yayi akan laps nata yace as u wish baby amma banjin qarfin jikinane yanzun Ayyah sorry kasan jiki da jini barin hada maka ruwan wankan ko Amma banson warm water baby Tace i know but tinda da fever ajikinka kada yakuma dawomaka dashi Cikin shagwaba kamar qaramin yaro yace pls baby Allah banson ruwan zafi Tace is ok shikenan barinzo nan tazame kansa ahankali ta daura akan pillow ta fice toilet Yaune shigarta na farko toilet dinsa nan takuma tabbatar lalle ya Alamin mutum ne mai tsabtar gaske komai tsaf saikace baa amfani dashi Bathtub ta cika masa da ruwa tasaka masa turaren wankansa sannan ta fito da towel ahannunta Tsayawa tayi akusa dashi tace ya Alamin shiru bai amsaba sake kiransa tayi akaro nabiyu Uum yafada yana bude lumsassun idanunsa Jikinne ta tambayesa No kawai banjin karfin jikinane yafada Let me help u tafada tana miqo masa hannunta kan ya riqe Aiko bai bata lokaciba ya riqe tattausan hannunta ya tashi ahankaki tana riqe da towel din tarakasa har toilet Miqa masa towel din tayi sannan ta fice cikin sauri Murmushi yayi ganin haqansa ya kusa cimma ruwa ya kuma gaskata maganar Aunty Naja dan tabbas yanda tanuna damuwarta qarara akansa hakan ya nuna tana sonsane Baiwani jimaba ya fito daure da towel a waist nasa Sunkuyar da kanta tayi tana wasa da yatsun hannunta Basarwa yayi kamar baisana da itaba ya wuce yadan shafa cream kadan ya fesa spray ajikinsa Wasu kayan shan iska ya saka kafin ya dawo kusa da ita ya kwanta gamida lumshe idanunsa Ya Alamin muje kadanci wani abin mana kada ka kwanta da yunwa No bani shaawan komai baby just black tea nake buqata Marairaice murya tayi tace aa pls don't say that mana kobayawa kadanci inyaso saina hada maka black tea n inbakason fitane nakawo maka nan inyaso Dan yamutsa fiska yayi yace shikenan muje toh amma saidai kidan riqemun hannuna cos am feeling dizzy Allah barin kawo maka nan idan bazaka iya zuwaba Aa muje kawai yafada yana yunqurin tashi zaune Tana riqe da hannunsa suka fito har dinning room Nan tayi serving nasa kafin itama tadan zuba kadan dan batajin cin abincin itama Kawai dan yadancine yasa itama tadan zuba Bayan sun kammala wadda dukkanninsu kowa yadan chakulane ya bari Bayan yasha tea din tace zaka koma dakine Aa muje falo dai nadan kwanta acan Ok tafada kafin suka koma falo shiya kwanta itakuma tana zaune agefensa sai faman sannu take masa Can taji yayi shiru irin bacci yadan daukesa while idanunsa biyu likimo kawai yayi Xubama kyakykyawar fiskansa idanu tayi tana jin wani sabon sonsa da tausayinsa suna ratsata Sunjima ahaka hartafara jin bacci shikuma dagangan yaqi ya tashi yafison tagaji danknta Ganin bacci na neman kwasheta awajen yasa tasa hannunta tadan bubbuga hannunsa Ya Alamin katshi ka koma daki kada jikinka yayi ciwo Bude idanunsa yayi ahankali cikin murya kamar mai bacci yace umum kibarni kawai anan zankwana Anan kuma?ta tambayesa Umm anan zan kwanta bani shaawan kwana a room nawa har garamun nan Shiru tadanyi harga Allah ita bacci takeji kuma bazata iya tafiya tabarsa afalo shikadai ba ga ba lfy ce dashi ba Cikin sigan lallami tace haba ya Alamin taya zaka kwana anan baicin dik yawan dakunan gidan nan Idan can baimakaba saika canza wani dakin bawai ka kwanta anan ba Sai dai muje room naki ya fada kansa tsaye Shiru danyi tana nazarin maganarsa No kada kisama kanki tunani kije ki kwanta abinki sai da safe yana fadin haka ya juya mata baya Shiru ta danyi nadan lokaci kafin murya asanyaye tace katashi to muje Aa barin takureki bafa kije kawai abinki Umum baka takurenba muje ka kwanta acan din badamuwa Yunqurawa yayi ya miqe zaune tare da miqo mata hannunsa Riqesa tayi ya miqe ta kashe komai suka wuce Har bakin gado takaisa saida ya kwanta sannan ta juya nan ta tsinkayi muryarsa yana cewa inazaki Batare da tajuyo ba tace zancanza kaya nane ta wuce ta dauki kayan baccinta ta shige toilet Acan ta canza kayanta sannan ta fito blanket ta dauka ta nufi kan sofa ta kwanta Dik abinda take yana kallonta Mene haka kuma zakije can kikwanta Eh kai ka kwanta akan bed ni nanma ya isheni tafada tana lulluban jikinta Tashi zaune yayi yace aa kam keda dakinki barinzo intakurekiba, kidawo nan sai ni na koma falo inyaso inkuma ba hakaba kizo kikwanta abinki, inbakuma guduna kikeba Tace ya Alamin na roqeka ka kwanta abinka ni hakanm yamun Ganin ya miqe dagaske zaifita yasa tace shikenan zandawo ka kwanta toh Tasowa tayi tawuce can qarshen gado ta kwanta sannan shima yazo ya kwanta abaki baki Amma yana tunanin hanyar da zaibi ya jawota jikinsa Itakuma tana kwanciya bada jimawaba bacci ya dauketa Kamar amafarki taji nishin mutum kuma bana lfy ba cikin firgita ta tashi zaune ta waiwaya ind yake kwance Nan taganshi qudundune acikin blanket sai rawan sanyi yake yana nishi samasama Batasan sanda ta isa gabansaba tana kiran sunansa ya Alamin jikinne ganin ya gagara amsa mata kawai saita fashe da kuka tana cewa saida nace inkira momcy ka hana yanzun gashi dare yafara yazanyi Murya ashaqe yace sanyi nakeji pls kitaimakamun sanyi Tace inqara maka bargonne, murya narawa yace koma mene kimun kitaremun sanyin nan Qara masa bargon tayi amma still baidaina shaking ba Hankalinta inyayi dubu ya tashi sai hawaye datakeyi wani nabin wani Cikin kuka tace katashi mutafo asibiti kaji Girgiza mata kai yayi yace yace aa sanyi kawai nakeji banjin zazzabin Tace ai shine alamun zazzabin nanan kenan nidai mutafi asbiti adubaka Yace aa abu daya zakimun nasamu sauqin sanyinnan shine dumin jikinki pls ki kwanta ajikina Ba musu ta yaye bargon zata kwanta yace saikin cire rigarki sannan nasamu dumin jikinki Tsabar yadda take adame ganin halin dayake ciki batai musuba ta cire doguwar rigar baccin dake jikinta ta kwanta ajikinsa Lumshe idanu yayi yana jin sauqan niima har cikin bargonsa Gyara kwanciyarsa yayi ya matseta sosai akan qirjinsa lokaci guda yaji wani kasala ya dirar masa har idanunsa na rufuwa Itama wani yanayi ta tsinci kanta aciki amma ganin yadda yake cikin halin rashin lfy saita haqura ta kwanta sosai Ahankali hankali yadaina rawan sanyin ya kuma daidaita natsuwarsa dan bacci sosai yafaraji Itama bada jimawaba baccin yasake dauketa Ranan shima kwanan farin ciki yayi koba komai yanzun yana ganin nesa tazo kusa Sassanyar iskan sanyin asubane daya karade sararin samaniya wanda ya sanadin sanyaya duniyar baki daya shiya qara sanyaya dakin daya hadu da sanyin AC Hakan yasa taji sanyi yamata yawa har yayi sanadiyar farkawarta Sannu ahankali ta bude idanunta nan taganta kwance tayi daidai ajikin papa Yinquri tayi cikin sauri zata matsa sai taga ya motsa aifa nan tasake lafewa ajikinsa dan batason yafarka yagan ta awannan yanayin Daga ita sai dan guntun wando ajikinta..... ✍🏻Faty Mmn Faty 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Fat Mmn Faty September, 2017 6⃣5⃣ Batasan cewar ya rigata farkawaba kawai baison jikinsu ya rabune yasa yayi kamar bacci yake Cikin dabara ahankali ta zame jikinta daga nasa ta jawo rigarta ta saka Lallabawa tayi ta sauqa ta nufi toilet Alawala tayi tadawo tafara sallolinta kamar yadda tasaba Shikuma tun data tashi yaqura mata idanu yana kallonta harta shige toilet Lumshe idanunsa yayi yana yaba surar da Allah yai mata, wani murmushi yasaki daya tuno yanayin qirjinta Ganin har zai makara sallan asuba yasa shima ya miqe Ahankali ya fice dakinsa Wanka yayi sannan ya daura alawala ya fito yayi sallansa adaki Sai wajen 6 sannan ya dawo room nata lokacin ta idar da adduointa tana ninke sallayan Bakin bed ya qarasa ya zauna saidata maida komai wajen zamansa sannan ta dawo ta zauna aqasa jikin qafafunsa Murya Ahankali tace ina kwana ya Alamin Da murmushi afiskansa yace lfy lau babyna Ya jiki?tafada ahankali Dasauqi sosai baby dafatan kintashi lfy daiko Tace lfy Allah ya sauwaqa Amin yafada yana kallon yadda ta sunkui da kanta irin batason su hada idanun nan Baby ya kira sunanta da wani salo Har cikin zuciyarta taji sautin muryarsa,naam ta amsa asansaye Taso kiji wata magana Babu musu ta dawo gefensa ta zauna Zamewa yayi ya kwanta akan laps nata cikin sanyin murya yace baby nagode nagode da kulawar da kika bani Allah yabani ikon kyautata maki nima Murmushi tayi dan taji dadin kalamansa tace bakomai ai haqqinane na kula da kai lokacin dakake buqatar hakan Yace toh nagode Dame zakayi break nadafa maka ta tambayesa Shiru ya danyi yace nibanjin shaawan komai dan nayi loosing apatatide Da muryar lallami tana dan shafa kansa tace haba dai daurewa zakayi badan dadiba kadanci wani abin Aidai bai yiyuwa kazauna da yunwa daiko Dan yatsina fiska yayi yace shikenan naji Tace to mezakaci Anything ya amsa yana lumshe idanunsa dan yanajin dadin yadda take sosa masa kansa Shikenan barinje nadanyi aiki, aa baby kibari bayanzuba mana Tace toh shikenan naji Dahaka har bacci ya daukesa sannan tazameshi ahankali tafice danyin ayyukanta Sai 10 taqare komai tadawo dan tayi wanka nan ta tarar baya dakinta Wanka tayi fess tafito ta shirya cikin atampa dinkin doguwar riga wanda tamata matuqar kyau Dinkin yazauna sosai ajikinta kamar kasaceta ka gudu haka tayi kyau Fitowa tayi sai qamshin humra ke tashi ajikinta ta nufi dakin papa kan yafito ya karya Tasaka hannu zata bude qofar falon shikuma ya rigada ya bude aiko saita afko ciki dan tabada qarfinta wajen jingina ajikin qofar Nan tafada kan faffadan qirjinsa tana sauqe numfashi dan ta tsorata, zatonta aqasa data fadi Shikuma tana sauqa kan qirjinsa ya shaqi wani niimtaccen kamshinda ya haifarmasa da kasala lokaci guda Hannunsa ya daura akan bayanta yace am so sorry baby bansan kina wajenba Kanta ta kwantar sosai ajikinsa kafin tace bakomai nasan bakasaniba ai ammafa na tsorata Eyyer am sorry my dear kada kitsorata am here kinji Kanta ta gyada kawai sabida yadda yake wani shafan kunnenta da hannunsa harya gangaro zuwa wuyanta Cikin wata iriyar murya saitin kunnenta yace baby sarqannan tamiki kyau sosaifa yana shafan jikin wuyanta Wani yarr taji harcikin jikinta yadda yake maganar yana wani shafanta kasa jurewa tayi cikin qarfin hali tace ur breakfast is ready Ok thanks a lot mujeko yasake maqaleta ajikinsa Ahaka suka sauqo sai wani shafata yake yana sunsunan jikinta kaman wani sabon maye itakuma dik jikinta yasake tawani lafe ajikinsa Kujera ta jawo masa ya zauna sannan itama ta zauna agefensa Faten irish potatoe tamasa mai dan ruwaruwa yasha alayyahu da hanta irin namarasa lfyn nan Zuba masa tayi tace bismillah maqe kafada yayi yace umum Tace why tana kallonsa Yace saidai muci tare Murmushi tayi tace toh muci, tare sukaci yana cewa ya qoshi tana lallaminsa ya daure yaci Batasan cewar dadin abincin yakeji sosaiba kawai yana pretending ne irin patient dinnan lol Bayan sungama ta tattara wajen suka dawo falo yana maqale da ita Haka suka yini sai shagwaba yake zuba mata irin wai baida lfyannan Itakuma ta biye masa ajikinta ya wuni zur abincima hanata dafawa yayi yasa akayiyo masu takeaway Da daddarema haka ya maqale mata wai sanyi yakeji Haka suka kwana tare yana maqale ajikinta amma baimata komaiba sai dan abinda baa raasaba Wannan weekend din cur haka sukayishi manne da juna, sai wani shaquwa daya shiga tsakaninsu mai qarfin gaske Mai zazzabikuma ya ware yaukam yace garau ya tashi baijin komai Sai daifa yaukam yayi niyyar karban haqqinsa dan akwana biyun dayayi suna tare baqaramin daurewa zuciyarsa yayiba Kamar kullum sunyi dinner abinsu sungama Tadubesa tace ya Alamin saida safe nizanje na kwanta gobe monday inason fita da wuri Dago kansa yayi yana kallonta yace ok nima ina shigowa Qirjintane taji yace dam dan dama tunda yamma taga taketakensa ya canza tace ba yaukam tinda kaji sauqiba saika koma dakinka ba Oh hakanefa toh goodnight mukwana lfy ya fada mata Tace Allah ya kaimu tawucesa Shikuma jiran Abdu yake ya kawo masa saqon da ya aikesa Abdu na dawowa ya karba saqon ya wuce bedroom nasa Saida ya shirya tsaf yasa kayan baccinsa kafin ya dau wayoyinsa da ledar da yayi aika ya fito ya nufi dakinta Kwance yasameta tana game da wayarta Ganinsa saida ta zabura ta tashi zaune Shi dariyama tabasa yace lfy baby irin wannan miqewa zaunen kamar wadda bera ya zungurin kafarki Batace komaiba shikuma ya qaraso inda take zaune ya zauna shima Baby matso kici naman da kikafiso naga bakici abinci sosaiba Nikam naci kuma na qoshi tafada tana dada lankwashewa Aa kam Allah saikinci konamaki dure Ganin yana dada matsota yasa tace naji zanci Ko kefa yafada yana bude ledar Tare sukaci kuma tadanci balaifi dan tana matuqar son naman BAUCHI CLUB Fita yayi da ledar yace kafin nadawo kiyi alwala muyi sallah bai jira amsantaba ya fice abinsa Daki ya koma yayi brush da alwala sannan ya dawo Sallah yajasu kasancewar yasamu tayi alwalan Rakaa biyu sukayi kafin ya musu addoin neman zaman lfy da tsari daga dikkan abinqi Hannunsa yadaura akanta yayi addua sosai kafin suka shafa Fauziyyah dai dik atsorace take dashi dan yaukam tasan Allah ne kadai zai kwaceta ahannunsa Wucewa yayi ya kwanta abinsa Itajuma tarasa meke mata dadi takuma kasa zuwa ta kwanta Dik abinda take yana kallonta dago idanu yayi yace baby lfy kuwa kizo kikwanta mana Kamar marar gaskiya taje tarabe acan qarshen gado Mirginowa yayi ya sameta ya rumgumeta Yana qoqarin cusa hannunsa acikin rigarta Hannunsa ta riqe tace meye haka ya Alamin nifa bacci nakeji Yace mekikagani aizakiyi baccinki ko Yana kaima wuyanta wani hot kiss Murya na rawa tace toh kamatsa mana ko kulata baiyiba yafara qoqarin zame mata hannun rigarta Turesa tafara idanunta sun cicciko da hawaye tace dan Allah ka kyaleni nibanason abinda kakemun Barin abinda yakeyi yayi yafara magana cikin tausayi yace pls baby kada kihanani wlh haqurina ya qare haqqina nakeso kuma kema kinsan hukuncin matarda tahana mininta haqqinsa Amma bazan tursasakiba idan kince baki yardaba na haqura amma dai kisani inacutuwa haquri kawai nakeyi Tuni tafara hawaye ganin batace komaiba yasa yafara aikamata da muhimman saqonni masu kashe gabobi da dikkan jiki Ahankaki ya rabata da kayan jikinta Nanfa hankalinsa yayi qololuwar tashi Haka yaringa jagulata yana budirinsa son ransa Qirjinta kam sunga abu baki nayi hannu nayi Itakam banda kuka ba abinda takeyi dan abinda yake mata yawuce tunaninta Hankalinta baigama tashiba saidataga yana neman hanyar shiga Shikuma awannan lokacin baimasan duniyar dayakeba dan ko kukanta baiji Adduar ma gagara yinta yayi gaba daya jikinsa rawa yakeyi Nanma yafara qoqarin shiga amma ina ba hanya da kyar da sudin goshi yasamu ya shiga amma amatse tsam yakejinsa kamar kuma ya shiga kogi Wata duniyar dabai taba jinsa acikiba yasamu kansa har yagaza haquri ya fara kuka kawai yana kiran fatima wayyo fatimana haka yaringa sambatu yana fadin wasu kalamai masu wuyar fadi Fauziyyah kuwa radadi da azaba susukasata sakin wani kuka mai ban tausayi Tsabar kukan wahala har muryarta ya dashe amma bashi da niyyar saurara mata saima qara cika mata kunne da ihunsa da yayi Hakan yasa tausayinta ya kamani simisimi na juya na fice daga dakin..... ✍🏻Fat Mmn faty 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty September, 2017 6⃣6⃣ Tsabar wahala har bata iya kuka mai sauti sai hawaye dasuke gangara daga idanuwanta Papa kuwa tsabar yasamu duniya irin wacce bai taba samuba yasa yakasa controlling kansa yake aikin abu guda Sai yayi kamar zai haqura amma irin dadin da yakeji saiyasakejin kamar yanzu yafara Sai wajen 1 sannan yasamu nutsuwa irin wacce baitaba jintaba tsawon rayuwarsa Kwanciya yayi agefenta yadaura hannunsa akan ruwan cikinta yana maida numfashi Yanason ya dagota jikinsa amma sai yakejin kamar bazai iya koda daga hannunsa ba dan wani irin gajiya yakeji da mutuwar jiki Qoqarin gyara kwanciyarta take amma takasa sabida yadda takejin jikinta yaimata tsami gawani radadin azaba datakeji Yakai wajen 20mins kafin yadanji qarfi ajikinsa Sai alokacin yasamu kuzarin tashi zaune Hannunsa yakai ya shafo face nata sai yajisa ajiqe sharqaf da hawaye Cikin sauri yajanyota jikinsa aifa nan ta kwalla qara wadda dakyar ake iyajinsa sabida muryarta yadda ta dashe Am sorry babyna am really sorry babyna Allah yamaki albarka my princess ketadabance arayuwata baby i luv u i really luv u Haka yaringa fada mata kalamai masu dadi yana rarrashinta Lafewa tayi ajikinsa koba komai maganganunsa sun sanyaya mata zuciya sannu ahankali wani baccin wahala yayi gaba da ita Ganin tayi bacci ya zameta ya gyara mata kwanciya ahankali Dakyar yasamu yaja jikinsa ya nufi toilet wanka yayi ya tsaftace jikinsa Wani farin ciki yakeji marar misaltuwa aransa dan Fauziyyah tagama masa komai arayuwa Dawowa yayi ya kwanta zuciyarsa haske tarwal kamar farin wata daren shabiyar Matsota yayi sosai ya rumgumeta ajikinsa yana shafar lallausan gashin kanta mai tsayi da santsi Murmushine kwance kan fiskarsa sabida tuna irin zallar niiman daya samu kansa aciki Dahaka wani bacci mai dadi ya daukesa wadda bashi ya farkaba har wajen 6 Sannu ahankali ya bude idanunsa lokaci guda komai yafara dawomasa tar acikin kansa na abinda ya fatu daren jiya Hannunsa ya miqa ya kunna bedside lamp Leqa fiskarta yayi yaga har lokacin baccinta takeyi Zame jikinsa yayi daga nata ya miqe ya nufi toilet Alwala yayi yadawo wayarsa ya dauka yaga time yana neman quresa Cikin sauri yatada sallah Jikintane yayi tsami sabida kwanciya gefe daya hakan yayi sanadiyyar farkarwarta Yunquri tayi zata tashi wani zogi dataji ajikinta shiya tuna mata abinda yafaru Komawa tayi ahankali ta kwanta lokaci guda hawaye yafara zarya akan fiskanta Motsin dayaji yasashi saurin juyowa ya kalli inda take kwance Tasowa yayi ganin tana motsi ya iso inda take amma me saiyaga ashe kuka take Hawowa yayi kan gadon ya dago kanta ya aza akan qirjinsa hannunsa yana shafa bayanta ahankali Babyna ya kirata cikin nutsatstsiyar murya Kintashi ne bakyajin dadin jikinki ko? Kiyi haquri zai daina barin hada maki ruwa mai zafi namaki wanka zakiji kin wartsake saikiyi sallah kisha magani kinjiko my princess amma pls kidaina kuka Allah yamaki albarka yasaka maki da gidan aljannatul firdausi Kinmin komai arayuwa bana da abinda zan biyaki farincikin da kika shayardani sai dai naroqi Allah yabani ikon kyautatamaki arayuwa Paking goshinta yayi ya zameta ahankali ya nufi toilet Ruwa mai zafi daidai bazai koni mutum ba ya hada mata ya dawo Dagota yayi cilak ya nufi toilet da ita Lumshe idanunta tayi dan batason suhada idanu wani irin sabon kunyarsa takeji dabadan batajin zata iya tafiyaba da bazata bari ya dauketa bama Ahankali ya direta cikin ruwan daya hada mata hakan yasa cikin razana da azaban zafi yasa ta matse kafafunta hadi da kwallah ihu Nan ya rude sosai yafara aikin lallashi Itabatamasan sunshigo toilet dinba tanacan duniyar tunani sai jinta tayi acikin ruwan zafi Nan tafara yunqurin tashi tafita Lallaminta yafara yana bata haquri am sorry baby nine ko to barinsakeba Amma kiyi haquri kidan jima acikin ruwan zakiji qarfin jikinki Turo baki tayi cikin kukan shagwaba tace nidai dazafi kasakeni nafita Aa baby kiyi haquri koda 5mins kiqara inyaso sai namaki wanka shikenan Nidai banson wankanka nidakaina zanyi tafada idanunta akulle Toh naji zakiyi da kanki shikenan toh kada kiyi kuka Ahaka harya samu tadan jima aruwan kafin ya zubar ya canza wani shima mai zafin amma baikai nadaba kafin ya fice ya barta Bed din ya kalla yaga yanda bedsheed din ya baci sosai saiya sakejin tausayinta dan lalle baqaramin wahala tashaba Cireshi yayi yakai cikin injin wanki sannan yadawo ya canza wani ya kuma ciro mata wata doguwar riga da hijab Cikin dingishi ta fito daga bayin kanta asunkuye Yana ganinta yataso da sauri ya riqota har bakin gado taimaka mata yayi tasaka riga da hijab din tazauna dan tayi sallah sabida taji ciwo sosai har takasa tsayuwa Komawa yayi yaje ya wankevzanin gadon ya shanya sannan ya dawo hannunsa riqeda cup da wani tablet Inda yabarta anan yasameta tana zaune sai aikin hawaye cos tayi tayi takasa tashi sabida wajen yayi tsami data jima azaune Rungumeta yayi yana tambayarta baby lfy kike kuka ko jikinne Bata amsashiba saima cigaba da kikanta datayi Dik hankalinsa ya tashi pls baby stop crying bakisan kukanki yana dagamun hankakiba ko pls talk to me Cikin kuka tace bakai bane gashin yanzun nakasa tashi tasake fashewa da wani sabon kuka Kiyi shiru kidaina kuka ganan pain reliever nakawo maki dakinsha zakiji sauqi kinji Dagota yayi ya ajiyeta akan bed kafin ya miqo mata tea din amma dakyar yasamu tadansha kadan sannan ya bata maganin namma sai datagama darunta sannan takarba tasha Kanta ya kwantar ajikinsa yana lallabata har tafarajin bacci dan yunquri tayi ta gyara kwanciyarta namfa ta kwalla qaran azaba lokaci guda tafashe da kuka Oh sorry baby zaki kwantane kiyi shiru kinji zaibari ko Gyara mata kwanciyar yayi shima ya zame ya kwanta yana lallaminta har tayi shiru Ganin tayi shiru yasa yace mezakici baby Babu kawai tafada Dawowa yayi tagabanta yana kallon yanda fiskanta yakoma dan kuka sakejin tausayinta yayu har cikin ransa Bayadda baiba amma taqi magana sai cewa tayi ya kyaleta ya rabu da ita taji da abinda yake damunta Rasa maike masa dadi yayi dan shima dik abinda yakeyi cikin qarfin hali yakeyinsa dan baijin dadin jikinsa sam Kamar feverne menene wani iri haka yakejinsa sam baida qarfin kirki ga ciwon da bayansa yake masa Wayarsa ya dauka yafara kiran momcy gara yafada mata basuda lfy amma sai yafara kira saiya katse dan bashida amsar da zaifada mata idan ta tambayesa meke daminsu Har sau uku yana katse kiran sai yaga gara ya kira aunty naja zaifi masa rufin asiri kuma tasan komai Kiranta yayi amma dakyar yafada mata fauziyyah batada lfy fa nan tafahimci meke faruwa tace to tana zuwa Yana nan kwance haka wani iri dai har fiye da one hour sannan tazo jin qaran door bell ya tashi yaje ya bude mata qofar Tare suka haura har bedroom na fauziyyah tace kadan bamu waje zamuyi magana Dakinsa ya wuce yaje yayi wanka ya shirya Itakuma bayan ya fita suka gaisa da fauziyyah tace mata ya jikin Dasauqi tafada cikin kunya nan aunty naja tabata shawari masu kyau takuma bata tsarabar data kawo mata na hadin bagaruwa da ganyen magarya Tafada mata yadda zatayi amfani dashi Godia tamata sosai tace bakomai yanzunma muje kizauna aciki saikiyi wanka gacan breakfast nakawo maku Ba musu ta fara qowarin tashi itakuma ta taimaka mata Bayan tafito daga toilet tayi kwalliya sosai tana sake godema aunty naja dan taji dadin jikinta sosai yanzunkam Tare suka sauqo falon qasa nan suka tarar da papa kwance akan kujera ya takure kamar mai zazzabi yana dafe da goshinsa Aunty tace yadai papa kaima kamar bakada lfyn Tashi zaune yayi yace wlh aunty inajin kamar fever kedamuna banjin dadi sam Allah ya sauwaqa tafada ta wuce kitchen ta dauko plates da cups Basket din datazo dashi ta bude dankali da kwaine soyayye ta zuba masu sai dayan flaks din farfesun zallan naman ragone wanda yaji kayan qamshi sai aroma dake tashi shitace fauziyyah taci sosai Tace toh zata tafi wannan kuma kunun gyadane yana dakyau susha Godia sosai suka mata sannan ta tafi Kallon fauziyyah yayi yamata murmushi mai kyau yace ya jikin baby Dasauqi ta amsa masa kanta aqasa Bayan sunci abincine yakwashe kayan yamayar kitchen Hannunsa ya riqe ya danna stop wach nan ya gwada kansa yafahimci yana buqatar qarin ruwa dan har jiri yakeji Wani abokinsa likita ya kira dasuke aiki tare akan yazo ya saka masa ruwa mana Bada jimawaba kuwa yazo nan ya tambayesa meyasamesa haka ruwan jikinsa ya qare sosai yace fever da vomitting ya kwana dashi kawai yafada masa Fatan sauqi yamasa yasamasa drip din yace idan ya qare sai ya saka dayan inkuma bazai iyaba ya dawo yasaka masa dayan Godia yamasa yace badamuwa wife nasa ma zata saka masa Nan ya musu sallama da fatan sauqi ya tafi.... ✍🏻Faty Mmn Faty 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty September, 2017 6⃣7⃣ Dr Basheer yana fita fauziyyah ta matso gefensa tazauna Cikin damuwa ta kamo hannunsa wadda ba ajiki aka jona masa drip dinba ta riqe gagam cikin nata Da murya mai sanyi tace ya Alamin daman ashe fevern bai sakeka ba haryanzun Murmushi mai sanyi yamata yana daga kwance yace no fever yasakeni wannan wani sabone daban kuma kece sanadi Cikin sauri ta kallesa tace me tana pointing kanta da dan yatsanta Lumshe idanunsa yayi ya bude yace yess kece kikasaka jiya nakasa controlling kaina harsaida ruwan jikina ya qareba Aifa cikin cikin sauri ta juyarda kanta gefe sabida kunyar maganansa dan sai alokacin tafahimci nufinsa Babyna kijuyo mana naringa kallon wannan kyakykyawan fiskannaki mai sanyani natsuwa Sake juyawa gefe tayi cos batason sake hada idanu dashi Pls mana my princess yafada ashagwabe Ahankali tace kayi bacci ka huta mana aidai yafi ko Oh haka ma zakice ko baby shikenan amma karki tafi kibarni kinji Nodding kanta tayi tare dafadin naji ahankali Lumshe idanunsa yayi sannu ahankali bacci yayi gaba dashi Tana zaune riqe da hannunsa hartafahimci yayi bacci sannan tasake hannunsa ta gyara masa kwanciyarsa Kallon fiskansa take tana jin wani irin fitinannen sonsa yana ratsata ta ko ina Murmushi take tana tuna yadda papa ya kware afagen luv ya kuma iya sarrafa mace Lumshe idanunta tayi lokacin data tuna irin maganganun daya ringa fada mata adaren jiya saitaji kunya ya kamata Tajima tana zaune kafin ruwan ya qare tacire ta saka masa dayan Ganin azahar tayi yasa ta tashi taje tayi sallah tadawo har lokacin bai tashiba Kuma ruwan da saura sosai shiyasa tafito da niyyar shiga kitchen tasama musu abinda zasuci Tana saqqowa falo taji qaran door bell sai tawuce ta bude qofar Mai aikin aunty naja tagani riqe da basket na abinci Gaisheta tayi cikin ladabi sannan tace wai gashi inji aunty Godia tayi sosai ta karba taje ta ajiye sai takoma dakin nasa ta zauna Tagumi tayi tana tunanin rayuwarsu nabaya inda koda wasa idan anfada mata haka zai shiga tsakaninsu bazata taba yarda ba Can tadubi agogo taga har 3 tayi gashi tagaji dazaman tana tsoron tatafi tabarsa ruwan yaqare yana bacci kuma Tana cikin wannan tunanin sai taga yafara motsi Ahankali ya bude idanunsa tass ya sauqesu akan fiskanta lokaci guda yasakar mata murmushi Matsowa tayi jikinsa tace sannu katashi Umm natashi haryanzun baiqareba ruwannan gaskiya nifa nagaji dashi yafada da alamun gajiya a fiskarsa Ayyah ya Alamin kadanyi haquri kadan yamafa kusa qarewa saura kadan kaji tafada cikin lallami Naji amma gaskiya bazaa samun waniba wannanma ya isa Tace ai nafarkon yaqare wannan ne nabiyun Kutt nabiyunne ashe lalle nayi bacci sosai kenan Tace eh yanzunfa har 3 tawuce Tanadan jansa da hira har yarage saura kadan nanfa yatada rikici saidai acire ya gaji Ganin yaqi yarda yasa taciremasa ruwan da canola din takai dostbeen ta yasar Ruwan wanka ta hada masa yaje yayi wanka yayi sallolinsa lokacin har laasar tayi Itama sallah tayi tasake wanka sannan tadanji qarfin jikinta Yar sassauqar riga marar nauyi tasaka tafito Afalonta tasameshi akwance Dago kansa yayi yace nashigo kina toilet Tace eh wanka nayi ya jikinnaka Yace am feeling better gaskiya yanzun naji na warware sosai Allah ya sauwaqa tafada sannan tace muje muci abinci koh Yace haba baby wayace kiwahalarmin da kanki aida turawa kikayi akayi mana takeaway dayafi Tace aa banice nadafa bama aunty naja ce ta aiko daxun Ok tomuje yafada yana miqewa dan yanzun yaji ya warware kuma baijin wani ciwo ajikinsa Suna zuwa falo tace umm ya Alamin dan Allah nakawo mana muci anan wlh banason zama acan dinne Yizamanki zandauko mana muci anan kada kidamu yafada yana zaunar da ita akan lallausan catfet din dake malale atsakiyar kujerun Shiya kawo masu komai sukaci sannan ya tattara yaje wanke komai hardana safe kafin yadawo Tana kwance yasameta Ganin zata tashi yasa yace aa yikwanciyanki babyna nima zama zanyi Agefenta yazauna aqasa ya dago kanta ya daura akan cinyarsa Hira mai dadi yake mata tareda dan mata tausa mai dadi hakan kuwa baqaramun dadi yamata ba dan jikinta dik ciwo yake mata 8:00pm Tafito daga wanka tadanyi shafefenta wadda yawancima turarukane ta shafe jikinta dasu sannan ta dauki rigar baccinta iyaka cikinta saidan wandonsa 3quater baby pink colour sunmata kyau sosai Tana gaban mirror tana daura ribbon akanta ya shigo Tacikin mirror take kallonsa sai murmushi yake harya iso gareta Rungumeta yayi tabaya yana shaqar kamshin jikinta Da wata kasalalliyar murya yace babyna kinyi kyau kuma turarenki yamun dadi sosai Yaqarasa maganar yana sunsunan wuyanta Wani yar taji ajikinta saida tsikar jikinta ya tashi lokaci guda wani kasala ya sauqo mata Saitin kunnenta yakai yakai bakinsa close ur eyes baby yace da ita Lumshe idanunta tayi Hannu yasaka acikin aljihunsa ya ciro wani container ya budeshi saitin fiskanta kafin yace bude idonki to Ahankali ta bude idanunta nan tayi arba dawani hadadden kuma tsadadden zoben azurfa mai sharp din hrt guda biyu manne da juna sai tsakiyar kuma wani dan dutsen diamond ne mai masifar kyalli Waw yeh sab kyahei ya Alamin?(kai mene ne wannan) tafada da irin abin ya birgeta Acchihona?(yanada kyau) ya tambayeta yana kallon idanunta tacikin madubi Haa bohoot acchihei(eh yana da kyau sosai)ta amsashi tana kallon zoben Cikin murmushi yace tumare liye meri dil(nakine zuciyata) Meri liye?(nawa ne)tasake tambayarsa da mamaki Haa tumare liye(eh nakine) yabata amsa yana dago right hand nata Yatsanta na kusa da danqaramin ya riqo yaciro zoben yasaka mata Nan yahaska mata hannun yayi kyau sosai Juyowa tayi ta rungumesa tana cewa nagode nagode ya Alamin Shshsh ya isa haka baby u deserved morethan that my princess i luv u Tsabar yadda taji dadi batasan lokacin datace i luv u too Dago fiskanta yayi yana cewa kahona baby pls kahona(kisake fada pls kisake fada) Kallon cikin idanunsa tayi tace kahana pyar hai(nace inasonka) Wani yanayin farin ciki yasamu kansa lokaci 1 Hade bakinsu yayi yana kissing nata anatse Sunjima ahaka kafin ya dagota yace babyna nagode sosai da kika bani soyayyarki nagode Ya isa haka ya Alamin Falo suka dawo sukaci abincinsu sannan sukadan taba hira Ganin tafara bacci yasa yadagota har dakinsa brush sukayi tareda dauro alwala sannan suka kwanta Haka ya rungumeta gagam kamar wani zai kwace masa ita Yaso ya batta amma saiya kasa hakan nan yafara wasa da ita sosai Ganin abinnasa bana qare bane yasa tafara kuka Barin abinda yakeyi yayi yafara lallashinta Babyna kiyi shiru abinki ba abinda zanmaki kinjiko Nasan cewar bakya da lfy barin maki komaiba amma kibarni nayi wasa dake kozan samu natsuwa Jin abinda yafada yasa ta juyo tana kallonsa Ganin hakan yasa yacigaba da shaaninsa saida ya jagwalgwalata son ransa haryajisa yasamu natsuwa sannan ya kyaleta ******* Kwanansa uku yana jinyar babynsa banda zallar qauna da shagwabata ba abinda yake Officema report yayi kancewar baida lfy Itakuma sai wani shagwabe masa take dadayi Cikin kwana ukunnan tayi lfy rass takoma normal abinta Shikuma adaddafe yayisu sabida wani matsanancin shaawarta kedamunsa Saidai yadan rage zafi tafannin wasanni Amma yaukam yaga tayi lfy sosai shiyasa ya danji sanyi aransa koba komai zai kashe qishirwarsa Aiko dare nayi dawuri ya fito da maitarsa afili Da farko ta tsorata sanda ya lallabata tukun ta amince Kuma batasha wahalaba sai dai shikam kuka da kuka hadi da sambatu ya ringa yimata lokacin daya samu shiga Headquater.[truncated by WhatsApp] 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty September, 2017 6⃣8⃣ Bashiya saurara mataba saida yajisa he's totaly satisfied tukun ya kwanta agefenta yana maida numfashi hannunsa daya acikin gashin kanta yana sosawa ahankali Itakuma bawai taji wahala baneba aa sai dai jikinta yayi tsami dan wani irin gajiya takeji sosai Banda ruwa babu abinda take buqata,murya can qasa tace fanii(ruwa) Baijitaba saida tamaimaita sau biyu sannan yaji kamar magana takeyi amma muryarta can qasa Kunnensa ya kawo saitin bakinta yace baby na me kike fadane Meh fiji fanii(zansha ruwa) tafada tana qoqarain tashi zaune Ok babyna barin kawomaki yafada yana dagota zaune Tashi yayi ya zura rigarsa ya fito kitchen din cikin falonta Ruwa mai sanyi da cup ya dauko Gefenta ya hawo ya zauna ya zuba mata ruwan ya miqo mata Dakansa yabata tashanye tass Kallonta yayi yace aqarane,girgiza kanta kawai tayi tace aa Ajiyewa yayi akan bedside drawer sannan ya gyara mata kwanciya akan qirjinsa yana shafa bayanta ahankali Babyna ya kirata,uum ta amsa tana sake kwantar da kanta akan chest nasa Me kike buqata namaki arayuwa dan kincancanci namaki komai Dakinsan irin natsuwar dakike bani ko hmmm Cikin shagwaba tace nidai so da qaunarka nake buqata inkabani wannanma ya isheni komai arayuwa Baby kifadi wani abu daban dan wannan kinriga da kinsamesa tuntuni Sake shagwabewa tayi tace to nidai nidai ba... saikuma tayi shiru Say it babyna komene inhar baisaba shari'aba zanmaki baranma nasan bazaki fadi abinda badaidai ba So fadamun abinda kikeso Toh nidai Allah kada kamun kishiya Dariya abin yabasa harsaida ya dara yace oh babyna meyasa bakyason kishiyan? Turo baki tayi kamar zatayi kuka tace dan gaskiya barin iya kallon kana shiga dakinta kuma nasan abinda kakemun shizakana mata Shine yasa bakyason kishiyar umm my princess Tace umm shine ai, murmushi yayi sosai yace toh kinason abinda nake makinne? Shiru tayi bata amsashiba cos maganar tamata nauyi Toh shikenan ashe kinason kishiyar kenan tunda nazaki amsaniba ya fada kamar gaske Nidai Allah banaso kadaina fadama tafada kamar zatayi kuka Yace ok ok shikenan naji toh kibani amsana nace kinason abinda nakemakin Umm inaso tafada tana cusa kanta cikin qirjinsa kamar zata shige ciki Murmushin jin dadi yayi yace toh dik sanda nanemeki bazaki hanani ba Gyada kanta tayi alamar eh Yace yawwa babyna toh tinda hakane kuwa kisa aranki keda kishiya har abada Tace dagaske ya Alamin Gyada kansa yayi yace gaske babyna banyin magana biyu kekadanki kin isheni rayuwa dik abinda akeso awajen mace nasamu so akan me zan daga maki hankali nadaga ma kaina Kikwantar da hankali insha Allahu bakya cikin layin matan da suke zama da kishiya Har abada baxan taba maki kishiyaba cos sonda nake maki bazan iya hadashi da wataba kece komaina ur my everything fatana kihaifamun yara kyawawamasu kama dake Wani dadine taji ya mamaye mata zuciya hakan yasa ta qanqamesa tana cewa thankyou ya Alamin nagode Abinda yasa yaketa janta damaganar sabida shagwabanta birgesa takeyi matuqa Yace toh idan kinason nayarda kinji dadi saikinmin abu daya tak Dago kanta tayi tana kallon fiskansa tace mene ne Yace nidai gaskiya yanzun yakamata acanzamun suna nabar yayannan ko sweetyna Murmushi tayi sosai tace indai wannan ne kazaba dakanka me kakeso inna kiranka dashi Aa kam kedai kizaba da kanki Tace toh muga muga one n only yamaka Yace yes yamun beautyna Tace toh shikenan one n only na tafada tana kaimasa wani special kiss a chiks nasa Yace banyardaba amun kiss dingaskiya nidai Lips nasa takai bakinta tafara tsotsa cikin wani salo dabaisan yadda zai fassara yadda yakejiba Saidata rikitashi da kalan salonta wadda yasauqarsa a network out of service dan gagara haqura yayi saida yayi second round tukun ****** Kwanci tashi ba wuya awajen Allah yau watansu uku harda doriya dayin aure Yanzun kowa ya gansu yasan hankalinsu akwance yake kuma suna matuqar zaman lfy da son junansu Har basu iya boye yadda suke ji akan junansu Babu wadda yakai su daddy farin cikin zamansu lfy gashi kusan dik sati sai sunje masu Dikkanninsu sunyi kyau sunqara haske sunyi kyau sai sheqi suke Cikin ikon Allah kuma acikin satin daya wuce Fauziyyah ta kammala service nata Har liyafa papa ya hada mata kuma suka shirya suka tafi dambam Sunje akan idan sunyi weekend sai yatafo ya barta ita tayi one week Abba da mama sunyi farin cikin ganinsu kuma yanzunkam kobaa fada makaba kasan suna zaman lfy Ranan sunday papa gagara tafiya yayi yabar fauzynsa gashi yana da ayyuka sosai a office Ta lallamasa akan yayi haquri sati daya kamar yaune amma yace yaji saida yamma zai tafi Tunda rana suke tare dashi adakin baqi wai yazo suyi sallama zai tafi har aka kira laasar shiru Abba yacema mama ina fauziyyah kam najita shiru kotaje unguwane Mama tace tana wajen mijinta kasan yau zaikoma shine yazo suyi sallama Abba yace amma kuwa ai zaiyi tafiyar dare har ankira laasarfa Fitowa tayi tazo tayi sallah shikuma yaje masallaci bayan yadawone yayima Abba sallama zaitafi Abba yamasa fatan sauqa lfy yace amma kuwa zakayi tafiyan dare kam Yace anjima kadan zantafi ai Abba yace aunan gabama sannan katafi Dan sosa keya yayi yace aigida zankoma Abba babu damuwa Nan Abba ya fahimci baison tafiya yabar matarsane saiyace jirani inaxuwa Cikin gida ya shiga yace fauziyyah ta dauko kayanta tabi mijinta Fauziyyah harda kukanta wai bazata tafiba Mama tace banson gulma aidai kinzo kuma kinganmu kuma kema bakison barin mijinki tinda tunsafe kike wani bata rai sabida zai tafi Abba ya tasata agaba har waje Nan yamasu fatan alkhairi suka tafi Papa kuwa zuciyarsa wasai dan murna sabida kwana biyun dasukayi baa tareba daurewa kawai yayi Itakuma ta bata rai tawani tsume irin batason tafiyannan Papa yadan dubeta kadan yace babyna yadai kika wani bata fiska inlaifi nayi inbada haquri Turo dan qaramin bakinta tayi tace Allah one n only ya isheka hakannan karabu dani tunda dai kasa Abba ya hanani yin sati agida Murmushi yayi sosai sannan yace haba yan matana nifa baruwana Abba dakansa yafahimci damuwar dansa yabashi magani amma bani ne nace mutafiba Tace aidai yanzunkam shikenan tunda kamun alaska Dariya yayi sosai yace nine me miki alaskan Eh din tafada tana murguda masa baki cikin shagwaba Yace toh naji na yarda amun haquri baby idan mun isa gida zan baki special haquri kinji my princess Dahaka har ya lallamata suka shirya tun basu isa gida ba Bayan dawowarsu da kwana goma papa yagama masu shiry shiryen tafiyansu *NEWZALAND* dagacan zasu biyo ta *QASA MAI TSARKI* suyi umra sannan su dawo Ranan da zasu tafi su daddyne suka rakasu har AIRPORT Basu tafiba saida jirginsu ya daga tukun suka dawo Qarfe 3am suka sauqa acikin garin *NEWZALAND* ✍🏻Faty Mmn Faty 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty September, 2017 *Ina kira da babbar murya zuwaga wadda idannayi posting yake had'amun DOCUMENT, toh banaso adaina saiki/ka bari idan nakane kayi yadda kagadama, dafarko banyi maganaba amma yanzun anason abab'atamun tsarin littafina, maimakon adinga tambayar page nagaba sai adinga tambayar wai part 2, bayan nikuma littafina guda 1 ne kuma banma qarasaba yanzun nakeyinsa pls naroqi koma wanene yabarmun abina yadda yake inyaso daga baya idan ina ra'ayin maidashi DOCUMENT sai nayi da kaina inafata anfahimchi nufina!!!* 6⃣9⃣ Direct wani babban HOTEL suka nufa inda acan sukayi masauqi Room nasu mai kyan gaske 2flat bedroom ne mai girma da tsari, suna hawa na 20 Agajiye suka shiga cikin dakin nasu dan sunsha zama a jirgi sabida tazaran dake tsakanin *Nigeria da Newzaland* Akan bed ta zube tana cewa wash Allah Dubanta yayi yana ajiye masu jakarsu yace yadai babyna? Wlh am tired tafada tana bata fiska Eyyer am sowwie barin muyi wanka muci abinci then saina maki tausa zakiji gajiyan ya gudu ko Toh kawai tace dashi tana sake gyara kwanciyarta Rage kayan jikinsa yayi ya rage dagashi sai boxer sannan ya nufuto Dagota yayi ya rage mata kayan jikinta itama suka wuce toilet Atare sukayi wanka sannan yana dota a towel suka fito Dan cream da spray ya shafa mata ya sakamata doguwar rigar baccinta da qatuwar hijab sukayi sallolin da basuyiba sannan yayi masu ordern abinci Bayan sunci abincine yadagota ya kwantar akan bed Cikin salon kwarewarsa yake dan matsa mata jikinta aiko bada jimaba wani bacci mai dadin gaske yayi gaba da ita Ganin tati bacci yayi murmushi ya rungumeta tsam ajikinsa shima bai dau wani lokaciba yabi bayanta Washegari bayan sunyi breakfast sukayi waya da mutanen gida da yamma suka shiga gari dan zagawa Baqarya sunajin dadin qasar sosai basu da aiki sai dai suci abinci su qoshi suyi bacci Idan suntashi su shiga gari yawo Hakan yasa wani shaquwa na musamman yasake shiga tsakaninsu sosai Gawani matsanancin qaunar da suke nuna ma junansu Cikin sati biyu sun wani irin canzawa hadi da kyau namusamman Especially Fauziyya tasake wani haske da kyau wanda shikansa papa bai gajiya da kallonta Rananda suka cika sati biyu suka wuce *SAUDI QASA MAI TSARKI* Nanma sunji dadin zuwansu can dan sunyi ibada yadda yakamata Haka sun zazzaga wuraren ziyara da dama Kwanansu goma suka fara shirin dawowa gida Inda suka shiga kasuwa suka jibgo tsaraba kamar ba gobe Ranan da suka cika sati biyu cur ranan suka nufo gida Nigeria Su momcyne sukaje taransu a Airport Jirginsu na sauqa suna fitowa suka hangi su daddy da momcy harda Aunty Niima Aifa dasauri fauziyyah ta qaraso ta rungume momcy Cikin shagwaba tace nayi kewarki momcy Momcy ma tace nima haka daugther gani nake kamar kun shekara bakunan Haka ta rungume Aunty Niima tana cewa i miss u Aunty Aunty tace nima haka ammafa honeymoon dinnan ya karbeku bakeba bashi ba masha Allah tafada tana murmushi Sannan taje tagaida daddyma yana tasaka musu Albarka Papa yace oh nikam yanzun andaina yayina babu wadda ya kulani Dariya suka masa momcy tace bagashinan mungankaba Shagwabewa yayi yace oh haka abin yakoma ko Dariya daddy yayi yace muje gida babana dik munyi kewarku shikenan no more qorafi Gidan momcy suka nufa sai dare kafin suka wuce gidansu Ko ina tsaf suka samu dan aunty niima tazo da masu aiki angyaramasu ko ina shiyasa ko ina fess kanar dama suna nan Bayan sungama abubuwan dasuka saba kafin sukwanta sannan sukayi shirin bacci Aifa suna kwanciya papa yawani kanainayeta Cikin shagwaba tace pls one n only kabari sai gobe agajiye nakejina Dan tasan abinda yakeso Cikin lallashi yace haba my princess kitausayinmana kema kinsanfa ina buqatarki sosai Tinda mukaje saudi ba sosai bafa ummm Kuma gaskiya inaso kiyi haquri kadan zanyi Turo baki tayi tace um wai kadan aidai nasan kadan dinkafa Yace gaskefa ainasan kingaji Tace toh shikenan Nan yafara aika mata da saqonni namusamman Sunjima suna wasanni da junansu kafin ya zame hannunsa daga kan qirjinta yana qoqarin shiga Aifa dasauri ta riqo hannunsa cikin wani yanayi tace pls kacigaba damin bangajibafa Kallon fiskanta yakeyi yanda take wani lumshe idanu tana maida hannunsa kan qirjinta Babyna ya kira sunanta da muryarsa kamar wadda mura ya kama Umm ta amsa tana bude lumsassun idanuwanta Meyasa kwana biyunnan kikeson naringa wasa da qirjinki sosaine? Nidai kawai dadi yakemun kuma kana sosamun Yace qaiqayine yake maki toh da kikeso nake sosa makin? Eh sosaima yakemunfa amma idan kanamum sai inji yadaina Murmushi kawai yayi danyafahimci kawai tanajin dadin abinne yaci gaba damata yadda takeso ****** Washegarin dawowarsu basu tashi da wuriba Sabida momcy tace zata aiko masu da breakfast bayan sunyi wanka sun shirya ta wuce dakinta dan tasaka kaya Kwalbar humranta ta dauko tana budewa ta rufeda sauri saitaji tamata wani iri Sai tayi tunanin kodan tajima arufe baa budewa ne oho Wata doguwar rigar shadda tasaka light blue tasha aiki da zare dark blue Kayan sun matuqar karbanta sosai ta kafa daurin dankwalin kamar wanda aka nadama gwagwgwaro Dauko humranta tayi tasake budewa akaro na biyu namma taji qamshinta ya mata wani iri kamar zaisata amai saikawai ta ajiyeta Tana cikin saka dankunnenta ya shigo Wata farar boyel ce ajikinsa mai tsadar gaske dinkin boda Ta matuqar fito masa da cikar zatinsa sai wani sheqi yakeyi Juyowa tayi suna hada idanu suka sakarma junansu niimtaccen murmushi mai faranta zuciya Kowa yana ganin kyan dan uwansa Bude mata hannayensa yayi ya mata alama dakansa ta taho Dan yadda ta birgesa kawai burinsa yajita acikin jiginsa Tahowa tayi tashige jikinsa amma cikin sauri ta matsa baya tana riqe hannunsa dayake qoqarin rungumeta Sabida shaqan qamshin turarensa datayi sai taji tashin zuciya kamar zatayi amai Da mamaki afiskarsa yace baby lfy kuwa kodai zolayane ya tashi Yatsina fiska tayi tace aa turarenkane banaso yayi qarfi dayawa Turarena kuma? Ya fada yana kallon yadda take bata fiska Taceceh wlh kai bakajisabane Yace ammafa baby normal perfume nanefa dakika sani Tace eh inaga dan sunjima a ajiyene baa amfani dasu shiyasa Kai baby rigima dai kawai saikace mun shekara bamunan just fa one month ne mukayi bamunan Tace Allah dagaske nake haka humrata ma tayi warin ajiya sai dai nacanza wata Tabe baki yayi ganin dagaske takeyi yace anyway shikenan barin canzo kayan kifito muci abinci momcy ta turo Toh kawai tafada ta biyo bayansa shiya wuce dakinsa itakuma tasauqa qasa Baifi 5mins ba ya fito a dinning yasameta tana zaune Murmushi yamata yace shikenan nacanzo inyaso saimu sake wasu turarukanko Tace aa ai wadanda muka saya amakka suna da dadi Ok shikenan yafada yana qoqarin zuba masu abinci Zuba musu yayi a plate daya yace baby muci kona baki abakine dannaga yau rigimar ta tashi gara nayi lallami Tace kai one n only harda tsokalane Aifa tana shaqan qamshin abincin tajisa wani iri harma batasan yadda zata kwatantaba Miqo mata yayi tabude baki saime kamar zai dawo haka ta hadiye da kyar tana jagula fiska Yaya dai ya tambayeta One n only nikam banson wannan abincin gaskiya tafada kamar zatayi kuka Riqo kafadunta yayi yace shikenan inbakiso aiba saikinyi kuka ba fadamun me kikeso kici Nidai irin abincin makka nakeso Tairkashi shine abinda yafada yana kallonta yace to wanne iri kenan Tace koma wanne iri amma mai garlic aciki Shiru yadanyi yace toh barin fita nasamomaki kinji ko Maqe kafada tayi tace aa niba nasayarwa nakesoba Yace toh nizan dafa maki kenan Nanma tace aa Dafe goshinsa yayi yace oh Allah toh wanne kikeso baby Tace nidai nagidan momcy nakeso irin wadda talatu takeyi tafada ashagwabe Takwana gidan sauqi yafada aransa yana ciro wayarsa ya shiga kiran layin momcy Tana dagawa bayan sungaisa Yace momcyfa yarkice takeson abincin gidanki Momcy tace ah malam bala bai kawo bane ba? Yace yakawo amma tace batason wannan wai mai garlic takeso irin abincin makka kinsan tasaba dashi kwana biyu Momcy nan take wani farin ciki ya lillibeta tace toh shikenan dakainama zandafamata Amma wanne iri takeso Yace tacefa na talatu takeso kuma ko wanne iri Momcy tace shikenan kabata haquri yanzun zaa dafa akawo kagaisheta Tana ajiye wayar daddy dake gefenta yace ya dai kiketa faraa haka maman yara Tace ai dolene daddy nida papane nan ta zayyane masa yadda sukayi Ta qarashe da cewar aifa nitun a airport nafahimci kamar tana da pregnancy Daddyma da faraasa yace Alhamdulillah Allah ya sauqeta lfy aisai amata abincin akai kada yunwa ya dameta Momcy ta miqe tace yanzukuwa sannan tafice zuciyarsu fal murna ****** Yana ajiye wayar yace toh madam zaa kawo maki amma kafinnan me zakici umm Dasauri tace popcorn din *BANILA* nakeso amma bamai milk acikiba Dame kuma ? Shikenan tafada, yace ok barinje nadawo toh Nan ya dauko car key nasa ya fice Manyan kwalaye biyar ya sayo mata ahanyarsa ta dawowane yake tunanin Meke damun babynsa kam dik tacanza haka Tun a makka ya fahimci canzawarta iri daban daban Gashi yaukuma irin abinda takeyi cikin qanqanin lokaci zuciyarsa ta amince masa lalle babynsa is pregnant Aifa wani dadine ya lullubesa lokaci guda dan yanzu yafahimci tana nuna alamun masu ciki ta abubuwa da dama kawai zuciyarsa batakawo hakanba sai yanzun Allah Allah yake ya isa gida yadauketa suje hospital ya cheking nata sosai..[truncated by WhatsApp] 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty September, 2017 7⃣0⃣ Tana kwance afalo ya shigo da sallamarsa Dago kanta tayi ta amsa fiskarta dauke da murmushi Babyna nabarki da yunwa ko yafada yana zama agefenta Miqewa zaune tayi tana cewa umum ai baka jimaba Riqota yayi ta zauna, ganan popcorn din yafada yana miqo mata ledar Cikin sauri ta karba ta bude kwali daya tafara ci hannu baka hannu kwarya dan gani take kamar bazai ishetaba Kallonta kawai ya tsaya yanayi ganin yadda take cinsa ba wasa My princess ya kirata yana kallonta Naam uum kawai tafada har wani lumshe idanu take sabida dadi Murmushi yayi sosai dan ba shakka abinda yake zargi zai zama gaskiya Babyna kigama cin popcorn din kirakani hospital Tsayawa da cin popcorn din tayi tace hospital kuma? Gyada kansa yayi yace eh hospital mana kobazaki rakani ba Zanje mana ta amsa sannan ta tambayesa to wane ba lfy? Kallon cikin idanunta yakeyi yace babyna zan duba naga lfyrta Nikuma tafada da alamun tambaya Yace yess ko inada wata baby baicin ke To aini lfy ta qalau ta amsa tana kallonsa Yace eh nasani kawai inason duba lfyr little babyna dake cikin kine yaqarashe maganar yana shafan cikinta Aiko batasan sanda dariya ya kufce mata ba Dariya yabata sosai tana dariya tace ah lallekam bayan kafitane kayi mafarkin hakan daiko Matsowa yayi jikinta sosai yakai hannunsa yana shafan cikinta yafara magana ahankli Baby bamarfaki bane gaskene kina dauke da ajiyata acikin cikinki Jin yadda yake maganar da iyaka gaskiyarsa yasa ta natsu tana sauraronsa, saida tabari yayi shiru sannan tadago ta dubesa da kyau tace pls mubar wannan wasan Baby am not joking fa dgaske nake alamunki sun nuna kina dauke da cikina ajikinki Tace to meyasa kayi wannan tunanin baicin masu ciki bahaka sukeba Yace baby kowacce mace da irin sign n symptoms dinta Itadai jinsa take dan bata yardaba sam sabida haka yasa tace meye hujjarka nayin wannan tunanin Murmushi yasakeyi yace haba baby bakiga yadda kika canzaba, abinda da bakiyi yanzun dik kinfarayi Kinfara zaben abinci sannan kince bakison turarena da naki n kuma gashi kincin abinci sai popcorn da kika ritsa kamar dawani kukeci alhalin da ba haka kikeba sam Sannan abinda ya tabbatarmum shine rabonki da yin mentruation yanzun 2months kenen Saida ya qare tace ah lalle kuwa toh nikam banda komai batun menstruation nawa kuma ai dai kasan daman yanamun wasa Yea i know baby but kituna rabonki da shan maganin ciwon cikinki tun bamu tafi newzaland ba, kuma watanmu guda bamunan dake cikim baiyi ciwoba shiyasa bamu ma tunaba Tace oh yanzun kawai dan ciki yayi arha sai yazama inadashi Yace nidai yanzun mubar magananan kawai muje hospital acan zamugani koma mene ne Hankali kwance tace nifa ba inda zani kawai Sassauta murya yayi haba babyna bafa jimawa zamuyiba kiyi haquri kirakani Toh wai naga ikon Allah ni fatyma mutum lfyrsa lau acw saiya wanije asibiti Aifa bance bakyada lfy ba rakiya nace kimun pla baby na kada kiqi Da kyar yasamu ya lallamata ta amince amma da sharadin bazujimaba ****** Bayan gwaji da scarning ya tabbatar masu tana dauke da ciki har natsawon 7weeks Habawa murna da farin ciki baa magaba papa bakinnan bai rufuwa Mamaki kawai yake wai irin shima zaizama baba Godia ya dingayima Allah da wannan kyauta daya masa wadda kudi bazai saya masa ba Fauziyyahma yanzun ta yadda kuma ta amince da cikin dake jikinta wadda bata taba tunanin haka ba koda kuwa da wasa ne Lokaci guda taji qaunar abinda ke cikinta yana ratsa ta Tun daga asibiti papa ya ringa waya yana fadin fauzynsa nada ciki Itakuma gaba daya kunya ya kamata yadda yaketa fadama mutane Bayadda batai dashiba kada ya fadawa momcy amma fir yaqi saida ya fada masu Su momcy jisuke kamar ba wadda yakaisu farin ciki Haka suka dawo gida papa yarasa inda zaisaka kansa dan tsabar farin ciki Wani tattali dabkulawa na musamman yashiga nunama babynsa Ko kwakwkwaran motsi tayi sai tambayeta meta keso ko kuma ina ke mata ciwo Tun abin nabata mamaki har yafara bata dariya Bayan sun dawo driver daga gidan momcy ya kawo mata abincin datace takeso Namma haka ya ringa lallmata yana bata abaki harta qoshi Dubansa tayi cikin shagwaba tace my one n only nikam kabarni zanfa iya yin komaina da kaina cos ba inda kemun ciwo Dubanta yayi yace tab sanadin kiwahalarmun babyna kenan ko Hade fiskabtayi tace lallema yanzunkam ai nafara ganinma kafidon babynka dani Jawota yayi jikinsa yace inji wane yace haka kadama kisake wannan tunanin dik abinda zanso abayankine so kada kidamu shima yana buqatar kulawan daddynsa ne kingane ai Ya qarasa maganar yana shafan cikinta Dahaka itakam bacci yayi gaba da ita Gyara mata kwanciya yayi sai anan ya tuna ashe baiyi break ba Sauqowa yayi yazauna amma sam yakasa cin abincin sai dan kadan yataba ya tashi Da yamma momcy tasake aiko mata da abinci nanma lfy lfy taci Sai dai me cikin dare matsanancin amai ya tasheta Haka takwana tana abu daya Gashi bata iya cin komai sai drip kawai daake saka mata Cikin sati biyu ta re ta canza sai haske kawai data qara Momcy tace ma papa ya maido mata da Fauziyyah gida ta ringa kula da ita tunda su kadaine agidan Amma sam yaqi yarda yace aa abarta ai yana kula shima da ita Amma idan ka kallesa zaka rantse kace shima baida lfyn sabida yadda yayi rama ko aiki ba kullum yake zuwaba Hakan yasa daddy ya kirasa yace ya maido Fauziyyah gida tunda jikinnata yaqi dadi Amma sam ya keqashe idanunsa yace aa shidai abar masa matarsa Daddy yace toh kai haka zaka zauna bka zuwa ko aiki bayan bawai bayadda zakayibane Toh umarni nake baka mom dinku zatazo ta dauketa Aifa ba kunya papa yace toh saidai shima ya hada kayansa su taho tare...... ✍🏻Faty Mmn Faty 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty September, 2017 7⃣1⃣ Daddy yana sauraronsa sai dayayi shiru tukun yace, Alamin waikai baka girmane kam? Daddy me nayi to kawai dannace nima zan dawo gida shikenan Daddy yace aifa ba kawai bane yakamata yanzun kagane da da yanzun the different is clear What's the different daddy kunefa iyayena n nima kuma nine dai bacanzuwa mukayiba Murmushi daddy yayi yace yess haka abin yake but now u r going to be a father, so kamata yayi kafara gane ka girma yanzun so kayi zamanka agidanku inyaso kana zuwa kana duba matarka babu wanda zai hanaka Shikenan daddy dayamman zankawota dakaina yafada amma dai ransa baisoba babu yanda ya iyane kawai Ransa ajagule haka ya dawo gida, bedroom nata ya nufa, bacci yasamu takeyi sai bai tashetaba ya wuce yafara hada mata kayanta Motsinsane ya tasheta ahankali ta bude idanunta kallonsa takeyi sai faman shirya kaya yakeyi Murya can qasa tace ya Alamin lfy kuwa ina zamuje? Jin muryarta yasa yajuyo cikin sauri Barin abinda yakeyi yayi ya nufota Hawowa kan gadon yayi ya janyota jikinsa baby kintashine Gyada kanta tayi tasake tambayarsa ina zamuje? Baby gida zan maidake wajen momcy amma wlh ni raina baisoba kawai ba yadda na iyane umarnin daddyne Tausayinsa ne yakamata jin yadda yake maganar cikin damuwa kuma koda bai fada bama tasan zai shiga damuwa sosai sabida bai qaunar abinda zai nesan tasu Shiru tayi kawai ta kwantar da kanta ajikinsa tana son komawa gida sabida wannan gidan ta tsaneshi dama amma sai bata nuna masa hakanba Baby ya zanyi ne, idan kikayi nesa dani, tabbas zanshiga damuwa amma inhar hakan yafi kuma zakiji dadin zama acan shikenan zanyi qoqarin danne zuciyata Ahankali ta rungumesa ajikinta tana cewa dabadan daddyne yace inkomaba niba inda zani Nasani babyna nasani kinajin tausayina fatana Allah ya baki lfy Amin ta amsa tana narkewa ajikinsa har bacci yasake daukanta Bayan ta tashi ya mata wanka ya shiryata sannan yakai kayanta mota yadawo ya riqeta suka fita ***** Kwance take akan makeken gadonta na gidan momcy Papa yana zaune agefenta hannunsa cikin nata yariqe gagam Momcy ce ta shigo tana cewa oh papa dagazangar ka tambayeta mezataci adafa mata shikenan sai najika shiru Dago kansa yayi yace momcy tun dazun lallaminta nakeyi taqi tace wai bazataci komaiba Momcy tace aa aikuwa ciwo da yunwa ai saisu nakasa mutum Sassauta murya tayi tace daugther na fadamun me zakici kinji Nifa momcy banason komai Cikin lallami tace haba daugther kifada dai amaki ko kadannce kici aiyafi hakan ko Toh zanci wainar fulawa amma kada asaka kwai kuma na manja da yaji mai tafarnuwa nakeso Momcy tace to shikenan barinje yanzun zaa maki ko kefa Papa ya dubi momcy yace yace mene ne kuma wainar fulawa Momcy ta dubesa tace oh ahakan kake cewa zaka iya jinyarta baicin dan abubuwanda takeso bakama sansuba baran dafasu shiyada take zaune da yunwa tana fadin haka ta fice Bada jimawa sosaiba momcy ta kawo mata aifa nan ta tashi tafaraci babu laifi taci mai dan dama kuma bataji tashin zuciya ba Yaune gobene papa shiru yaqi ya fito ya tafi yana zaune wai sai tayi bacci ya tafi Har wajen 11 sannan ya fito lokacin tayi bacci, afalo ya tarar dasu daddy ko ajikinsa ya masu saida safe ya wuce abinsa Dikkansu bayansa sukabi da kallo Momcy tace oh lalle papa baya da kunya sam shikam Daddy yayi murmushi yace aikam abinnasa sai kallo yadda yakeji da Fauziyyah Allah ya bata lfy su koma gidansu Momcy tace shine fata kawai ****** Washegari sassafe kafin ya tafi office saida yazo ya ganta hakannan daya dawo anan ya yada zango sai pass 10 sannan ya tafi Haka kullum dasafe zaizo da yamma ma zaizo kuma ba kunya abinsa haka zai namiqe mata sai dai wadda yake dakin ya fita ya barsu danshi ko ajikinsa Satinta biyu tafara sun sauqi domin dama hadda yunwa suka hadu mata Yanzun kuma dik da dai batacin abinci amma kayan kwalama kam tanaci kuma momcy na kula da ita sosai Kullum papa yazo qorafi yake mata yafa gaji wlh yanzunkam tunda taji sauqi zasu tafi Itadai batace masa komaiba amma batason tafiya dan tanajin dadin zaman gidan momcy Haka dai addaddafe yabarta tayi wata 1 Ranan kuwa yasamu daddy yace zasu tafi tunda taji sauqi Momcy tace sam bai isaba yabarta tawarware sosai yadda komai zata iyaci amma banda yadauketa akoma gidan jiya to bazai yiyuba Daddy ma yace nikam lfyrka kuwa toh ba inda zataje inhar dik zuwan da kake kagama rashin kunyarka bamai kulaka bai ishekaba saina hanaka zuwama gaba daya Nan suka masa fatafata ya tashi rai bace yayi dakinta Yana shiga ya dannama qofar key Tana kwance akan bed tadago tana masa murmushi Fiskansa ahade ya qaraso ya zauna abakin gadon Tashi zaune tayi tace my one n only yadai naga kamar ranka abace Dan gajeren tsaki yayi yace wlh nagaji haqurina ya qarefa yanzunkam Matsowa tayi jikinsa ta kwantar da kanta abayansa tace da akayime hooney Sauqe murya yayi dan yadda ta rungumesa ta baya saiyaji kasala ya sauqo masa yace haba baby kinsanfa ina haquri da rashinki amma sam su daddy basa ganewa wlh a buqace nake daurewa kawai nake sabida bakyada lfy but now Alhamdulillah kinsami lfy daidai gwargwado amma sunqi subarmin matata haba why yaqarashe maganar kamar zaiyi kuka Wani tausayinsa ne yakamata tasake qanqamesa da murya mai kwantar da zuciya tace nasani kana haquri amma ka qara akan wanda kakeda komin daren dadewa zsmu koma gidanmu ai so kada ka tada hankalinka Bazaki ganeba kema yafada Tace niko nagane toya kakeso nace Yace shikenan amma dai tunda kinji sauqi sai kibani haqqina ko Zaro idanu tayi tamatsa baya kadan tace wlh kafaye wasa dayawa Hawowa yayi ya kwanto jikinta yace au wasa kikace wlh am serious Tace tab so kake azo asamemu ince me kenan Kai baby babu wanda zaishigo na kulle qofarfa kai toma saime idan ansamemun zina mukayi ko haramne nida matata ta haka zasu gane abinda suka kasa ganewa su barmin matata Tace tab tobadaniba gaskiya tafada ashagwabe Kansa ya dan dora akan cikinta yace kinji little babyna yana fadama daddynsa wai yayi missing nasa shima Tace ah lalle kam toyani banjiba Yace aidani yake magana ba dakeba so yaukam zan gaisa da little babyna naji lfyrsa Batayi auneba tajisa yawani rungumeta yana wani shafata Zip din rigarta ya zuge yana qoqarin balle mata bra ta riqe hannunsa da sauri tace haba ya Alamin meye haka bafa agida mukeba So what idan ba agida mukeba pls sakemun hannuna kiga yafada yana zame hannunsa daga nata Ganin dagaske yakeyifa yasa ta turesa ta matsa gefe tace gaskiya kayi haquri wlh nikam kunya nakeji bazan iyaba Ransa ne yaji ya baci cikin bacin rai Yace oh kema kinabin bayansu kenan ko bakya tausayina ko good ya maki kyau dan kinga ina binki yadda kikeso shiyasa zaki walaqantani ko Rai bace ya miqe zaune yana hada bottons nasa daya cire Ganin yadda ransa ya baci lokaci guda fiskansa ta koma fiskan shanu sai taji kamar bata kyautamasa ba lokaci guda zuciyarta ta karye amma batajin zata iya biyesa suyi wannan rashin kunyan kam gara ta basa haquri ta lallamesa yafi kawai Sauqa yayi daga kan gadon zai fice cikin sauri tace tafiya zakayi kuma kamar zatayi kuka Afusace ya juyo yace ina ruwanki toh dani Dan Allah.... Hannu ya daga mata yace nabarki kiyi yadda kikeso kuma indai nine bazan kuma zuwa neman wani abuba inkuma haka tafaru call me what u want yafada cikin masifa sannan ya fice afusace Shiru tayi tana tunanin rabon dataga fushinsa haka harta manta amma tasan zai huce inyazo saita basa haquri Papa kuwa baibi takan kowaba ya fice, gida ya wuce ransa amatuqar bace amma zaiyi maganinta ya fada aransa Washegari tunsafe har dare ba papa ba labarinsa Tun abin bai damunta harya fara damunta Haka aka kwana aka sake yini baizoba bai kuma kirata awayaba itakuma ta kira wayarsa amma busy take gani batasan yayi diverting line nata ba Wasa wasa har tsawon sati guda bata kuma ganin saba hakan ya tabbatar mata lalle yayi fushi bana wasaba bakuma yadda zatayi Damuwa sosai ta shiga gashi cikin ikon Allah tasamu sauqi sosai Ahaka har akayi sati biyu nankanfa bata iya boye damuwarta dan dan abincin data fara cima yanzun gagaranta yake Afannin papa kuwa da kyar ya daure zuciyarsa yake haqurin rashin jin da ganin babynsa Yayi hakane dan yasata adamuwa ko hakan zaisa su momcy su maido masa da matarsa amma fushin dayake da ita ya jima da hucewa Matsanancin kewanta ke daminsa, gidan yamasa fadi shikadai haka yake rayuwa cikin kadaici har abin tausayi ya koma ....... ✍🏻Faty Mmn Faty 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty September, 2017 7⃣2⃣ Momcy ta dubi daddy tace daddy inagafa abinda yafi da yamma zan maida fauziyyah gidanta Meyasa kikayi wannan tunanin kodan fushin da Alamin yayi? Aa kokadan badanshibane, ita kanta Fauziyyah yanzun tashiga damuwar rashinsa akusa da ita Ina lura da ita tacanza kwana biyunnan kuma dik bai wuce rashin mijinta bane Hatta abincin bata iyaci koda kadan din datakeci, tunda tayi sauqi inaga kawai ta tattara ta koma Allah ya bata lfy kawai Daddy yace shikenan ba damuwa Allah ya kaimu yamman, amma wazai namata dan ayyukan gida kuma? Momcy tace wannan bamai damuwa bane nayi magana da talatu akwai qanwarta wadda aurenta ya mutu to dama tamin magana akan idan ansamu aiki ataimaka wa qanwar tata Toh shine nace taje ta taho da ita sai su tafi tare take mata ayyukan ko me kagani Daddy yayi murmushi yace momyn yara kenan ashe dik kin tsara komai abinki Toh hakan yayi bamatsalan komai nan suka cigaba da hiransu Sai bayan azahar tasaka talatu ta hada kayan fauziyyah lokacin sundawo Bayan laasar takira papa ta tambayesa yana gidane Yace eh yana gida tace shikenan sai anjima ta kashe wayarta Papa kuwa dayaga wayan momcy yadauka zatace yazo yadauki matarsa amma sai take wani tambayarsa wai yana gida ne nan haushi yasake kamasa ya kuma rasa tudun dafawa ***** Momcy datagama wayar dama tana dakin fauziyyah ne tace toh tashi kisa mayafinki mutafi Fauziyyah tace ina kuma momcy Momcy tace gidanki mana kafin mijinki yakawo mana sammaci kuma da alama kina bayansa tun wuri gara namaidaki Wani dadi fauziyyah taji amma sai ta sunne kanta qasa ganin yadda momcy ke kallonta sai kunya ta kamata Momcy tace ganan hannatu qanwar talatuce tare zamu tafi zata ke maki ayyukan gida Itadai fauziyyah qala bataceba sai hijab nata ta dauko tasaka tabi bayan momcy dan ita tafice Afalo ta samesu sai tace momcy barinje nayima daddy sallama Momcy tace aiko ya fita tun dazu, dawowa tayi suka fice Suna isowa mai gadi ya bude musu gate suka wuce Atare suka nufi cikin gidan inda hannatu ke jaye da jakar kayan fauziyyah Yana kwance afalo da system agabansa yana wani aiki saiyaji qarar door bell Waye kuma ya tambayi kansa lokaci guda ya miqe yayi hanyar qofa Aifa yana yaye cuttain din yagansu kasancewar glass ne awajen Cikin sauri ya bude qofar yana kurema babynsa kallo Momcy tace toh bamu hanya mana mu wuce ko Dan sosa qeyarsa yayi dan kunyace taka masa dai yawance da runguman momcy yana cewa oyoyo momcy, nan take yaji baqin cikinsa yaye Momcy tace harka hucene daga fishin dakake damu, haba nina isa nayi fushi daku kawai ayyukane sukamin yawa Yayi agogo sarkin aiki tafada tana dan turesa gefe Falo suka zauna bayan sun gaisa tasake musu bayanin hannatu sannan tace zata tafi Har mota papa ya rakata sannan ya dawo Amma saiya dawo fiska abace, duban fauziyyah yayi inda yabarta anan take zaune yace madam kinuna mata room nata daga haka ya wuce yana janye dakayanta zuwa dakinta Wani room dake qasa mai kyau wadda komai na amfani akwai ta kaita tace to ganan dakinki kihuta zan dawo idan nayi wanka Toh Hajiya tafada cikin girmamawa dan gabadaya ruwan kanta ya qare tinda tashigo gidan take maimaitawa aranta Aljannar duniya Dakinta tafito ta wuce, papa dake labe yana jiran yaji tahowarta ya fice danya dan wanata sai yaji motsin tahowarta Bude qofar yayi ya fito baiko kalletaba zai wuce da sauri tariqo hannunta hakan yasanyashi tsayawa amma bai juyoba bai kuma cewa komaiba Dawowa jikinsa tayi ta rungumesa sosai tafara magana da raunanniyar murya Haba my one n only fushi kake dani har yanzun kenan, koma menamaka ban cancanci wannan punishment dinba tafada muryarta na rawa Baby yafa wuce yafada anatse Tace aa kam yanayinka ya nuna haryanzun baka haquraba Shikenana naji pls don't cry y wuce yafada yana qoqarin zameta ajikinsa ya wuce Aifa saita fashe da kuka tana cewa abakine kacemun ya wuce amma azuciyarka baka haquraba tunda gashi wucewa zakayi ko ya jikina baka tambayaba Ganin dagaske kuka takeyi yasa ya rungumeta tsam ajikinsa yana cewa am really sorry babyna am sorry ki yarda dani bana fushi dake kiyi shiru Bana qaurace maki dan wani abubane sai dan ina da dalili kuma gashi yanzun andawo mun dake Nan tafihimci abinda yake nufi itama Baby kinsan irin wahalan rashinki danake fama kuwa wlh na azabtu sosai bana fatan abinda zai kuma nesantani dake har qarshen rayuwata Sai anan taji sanyi aranta tasake narkewa ajikinsa Sunkuyawa yayi dai2 cikinsa yana kissing dinsa yana cewa am sorry my little baby Daddy yayi laifiko baije ya dubaka bako sowwie ba laifin daddy bane laifin su garrany momcy ne Dagowa idanunsa yayi yana kallon idanunta yace kinji my little babyma ya fahimci dadynsa so yakamata mom dinsa ma ta fahimta ko yana daga mata giransa daya Dariya ya bata saita rungume kansa ajikin cikinta tana cewa i miss u my luv i miss u so much Dagowa yayi yace missing u more n more my princess Cidak ya daga har bed room nata ya dire ta akan bed Yafara qoqarin gaisawa da little babynsa cikin shagwaba tace haba baby baxaka bari sai anjimaba I can't shine abinda yafada murya ashaqe Ganin haka simisimi na fice nabarsu..... ✍🏻Faty Mmn Faty 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty September, 2017 7⃣3⃣ Har akayi sallan magrib suna daki dan atare sukayi sallah ma Sai alokacin Fauziyyah tace ya salam tana dafe goshinta Papa yace lfy baby yana riqota Tace sam bakaine kasa namanta da hannatu ba Waye kuma hannatu? Ya tambayeta dan sam yama manta dawata agidan Mai aikin da momcy tabamu mana tafada tana kallonsa Afalo kika bartane ? Aa nakaita dakinta amma nace mata zandawo To miye aciki tunda tana dakinta kika wani tada hankalinki Da shagwababbiyar murya tace bafa nata da hankalina bane ko ruwa ban bata bafa gashin har dare yayi baran abinci Haba babyna kada kidamu aidai tasan kina tare da mijinkine ko yanzun muje ki kai mata juice da akwai nama a kitchen wanda nasa aka sayomun banciba inyaso saina fita na samo mana abinci Toh shikenan muje tafada tana tashi daga jikinsa Riqeta ya kumayi yace me babyna zataci Shiru tadanyi tace umm QUNDUN Bauchi Club zanci da graves Dadi yaji sosai jin tafadi abinda zataci ba gardama Amma kuma tabasa dariya yadda tace wai qundu, dan qaramin bakinta yaja yace oh baby kwadayi kenan Bata rai tayi tace nikam bana kwadayi kuma tunda kace haka nama fasa barin ciba Cikin sauri yace am so sorry bafa dake nakeba nida little babynanefa Cikin sangarta tace aidai nadauka dani kake Yace waneni nace maki mai kwadayi muje yanzun nakawo maki ko shalelena Atare suka fito kitchen ya riqo mata abinda zata kawoma hannatu har bakin qofarta sannan ya miqa mata tare da manna mata kiss a forehead nata ya fice Washe gari da kyar ya fita office sai wani nan nan yake da ita har bata gajiya da kallon yadda yake mata hidima Bayan yafita ma ajima kadan ya kirata awaya yana tambayar ya suke ita da little babynsa Ita kuwa tai ta zuba masa shagwaba tana narke masa Adaddafe yakai 4pm a hospital sannan ya nufo gida Ita kuwa tana bararraje afalon qasa hannatu ta mata danmalele ta baza mata a plate, yasha manja da yaji ga kuma robar yajin agefenta Tafaraci kenan ya dawo Hannatu tana gaishesa ta wuce dakinta Shikuma zama yayi agefenta aqasan carpet yana cewa babyna nayi missing naki sosai Ita murmushi tayi tace me too only, munyi kewarka muma Tana maganar tana kaiwa loma abakinta Kallon abinda takeci yakeyi da kyau sannan ya dubeta baby mene ne wannan Itakuwa tsabar dadi har wani lumshe idanu takeyi tace danmalele zakacine Kai baby a ina kika koyi cin wadannan abubuwan amma dai dafatan bazaima little babyna illah badaiko Bata fiska tayi tace nifa wato yamun komaima badamuwarka baneba saita babynka kake ko No bahaka bane baby ke ai babbace amma babynmu baiyi kwaribafa kike wannan ciye ciye Tace to nidai inzakacine muci inka qoshi kuma shikenan Tafada tana qara gumbuda yaji Kutt baby irin wannan cin yajin haka fa yafada yana daukar roban yajin Marairaice murya tayi tace pls kabani yajina inbakason yajin barin saka maka agabankaba Yace nikam barinciba kici dadi lfy amma dai yajin nan ya isheki haka nan Tace nikam kaban kayana tunda baci zakayiba Yace ko baxan ciba bazan bakiba Ganin dagaske yakeyi yasa tace toh naji dan qaramun kadan tai maganar tana langabe kai Yadda tai maganar yabasa dariya yace shikenan debi kadan to tana diba ya rufe yamayar kitchen Baby barinje na watsa ruwa kafin kigama ko Toh afito lfy tafada tana cigaba da cin kayanta Girgiza kansa yayi kawai yana murmushi yadda tabada hankalinta wajen cin wannan abin ***** Haka rayuwa yaci gaba tafiya masu cikin kwanciyar hankali da natsuwa Dan yanzun fauziyyah ta murmure sosai daga laulayin datake ba abinda ke daminta Sai dai kwadayi kam kamar kullum qara mata akeyi Hannatu kuwa mutumiyar kirki bata gajiya da yimata wannan da wancan Hankalin papa ya kwanta tunda tasamu lfy batada matsala yanzun Rainon cikinsu sukeyi cikin tattali da kulawa Sannu ahankali cikinta yake girma har yakai yanzu watanni shida Ya fito yayi mata das dan gaskiya cikin ya qarbeta sosai yaqara mata kyau idan tayi kwalliya sai cikin ya fito yamata gwadas ajikinta Wani sontane kullum ya ke qaruwa acikin zuciyar papa yadda kullum itama take tattalinsa ta take bashi kulawa dikda cikin dake jikinta bai hanata ta bashi haqqinsa yadda yakamata Yanzun har girki tana masa hakan yasa hankalinsa ya kwanta sosai yayi wani haske harda wata yar qiba yayi wadda tamasa kyau sosai Kullum adduar su momcy dasu Abba bai wuce Allah ya sauqeta lfy ba ***** Yaukuma da shagwaba ta tashi Kwance tasamesa a bedroom nasa yana nade acikin wani milk blanket mai laushin gaske Doguwar rigace ajikinta ta atampa mai laushi Tamata kyau sosai sai qamshi takeyi Bakin bed din tazauna tana kallon kyakykyawan fiskansa mai matuqar annuri Wani kyau taga ya sake mata dikda baccinsa yakesha peacefully Sannu ahankaki takai dan yatsanta kan bakinsa tana shafawa ahankali Dan motsi kadan yayi alamun yanajin ana tabasa Jikin kunnensa takai dan qaramin yatsanta tana sosawa Bude idanunsa yayi ahankali yana kallonta da alamu bai gaji da baccinba Cikin muryar bacci yace yadai akayi babyna Ashagwabe tace nidai katashi hakannan Pls baby kibarni sai anjima kadan ko kema kizo muyi baccin atare Nidai nidai banjin bacci Allah kuma kaima katashi Oh baby pls fa nace , tace umum fa nace tana janye bargon nasa Toh naji zantashi amma saikin bani .....yaqarashe maganar ahankali Cikin sauri ta waro idanunta tace aa wasa nake maka yi kwanciyarka Bude idanunsa yayi yace ai tunda kikasani natashi saifa kinbani Miqewa tazoyi yayi saurin riqe hannunta ya daura hannunsa akan cikinta yanajin yadda yake motsi Baby kinji little babyna yanason gaisawa da daddynsa, nima kuma inasonjin ya babyna ya kwana Kwantawa tayi ajikinsa da murya mai sanyin shagwaba tace ba jiyama kaji lfyrsaba nidai bayanzunba Aa baby jiya ai good night namasa yanzun kuma zan masa good morning yafada yana shafan cikin nata Narkewa takumayi ajikinsa tana cewa nidai katashi kayi wanka kayi break Aa baby wani break kuma bayan kinzo kin tayarmun da hankali jifa yadda kike qara kashemun jiki da salon shagwabarki, kuma kemafa kinaso kina kaiwa kasuwa jibi yadda jikinki yayi... Bai qarasaba takai hannunta tana dukan qirjinsa cikin wasa nidai kasakeni intashi Aifa nafada ba inda zakije baiqarasaba tace wash cikina tana riqe cikin Ai baisan ya akayiba yagansa azaune cikin rudewa yake cewa mai yasameki baby mene ne Cikina kadagani zaune tafada kamar zatayi kuka Ok ok yafada yana miqar da ita zaune Kafin ya zame blanket din jikinsa ta tashi da sauri tayi hanyar fita tana cewa saika fito kuma 20mins nabaka Baby au dama bagaske kikeyiba kika tsoratani ko Tana bakin qofa tace bakaki katashiba Good kinmun 1-0 ko bakomai zamu hadu yafada yana miqewa Ita kuma ta fice.... ✍🏻Faty Mmn Faty 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty October, 2017 7⃣5⃣ Bayan dawowarsa da kwana biyu,dasafe bayan sun karya zai fita office,saida yagama dik abinda yakeyi sannan yadawo bakin bed inda fauziyyah kezaune,yana zama ta kauda kanta gefe fiskanta babu walwala da alamun fushi takeyi dashi, ganin yadda taci magani tawani juyarda kanta gefe guda saita basa dariya,aifa tanajin yadda yake mata dariya saita qara qulewa,hannunsa yasa ya juyo da face nata yana kallonta kuma baibar dariyar ba,cikin fushi tace nikakema dariya ko saboda ganan mental agabanka, sai anan yayi magana yace no nibadake nakeba baby,to inbadani kakeba kaidawa tunda dagani sai kai ne adakinannan,yadda tai maganar tana murguda mai baki shiyasake basa dariya,haushine yasake kamata ta rarumo pillow tana kwada masa,riqe pillow din yayi yana cewa nadaina baby nadaina barinsakeba kuma bafa dake nakeba,kamar zatayi kuka tace nidai kakyaleni naji da guda daya bakawai kazauna kanamun dariyaba baicin ka hanani fita, baby kece kikasakani dariya da kike fushin rashin gaskiya,tace naji banada gaskiyan katashi katafi abinka ba ruwanka dani sai hawaye sharr,ahankali yace ya salam babyna akan nace kizauna agidane kike fushi hadda kuka?,ita dai bata kulasaba saima cigaba da hawayenta datakeyi,hannunsa yasaka yana goge mata hawayen da murya mai taushi yake cewa ya isa hakanan badai unguwaba zamu tafi tare amma kigane badagangan ne nahanaki zuwaba aa saidan yanayin da kike ayanzun,da kinfita qafafunki sufara ciwo shiyasa amma kinsan ai inda badan haka taya zan hanaki zuwa gidan TJ,tunda kinason zuwa barin hanakiba amma on one condition,dasauri tace nayarda fadi naji,bazaki yini azaune waje dayaba kitakuramun babyna yaqarashe maganar yanajan dogon hancinta,eh nayarda nayarda,yace toh muje kisaka mayafinki muje nasauqeqi kada na makara,cikin zumudi ta miqe ta fice zuwa bedroom nata,murmushi yayi yana kallon yadda tafita da murnanta sai ya tsinci kansa cikin nishadi dan dik abinda takeyi birgesa takeyi har cikin ransa kuma bai qaunar bacin ranta Aqofar gida ya sauqeta yace kigaida mmn mubeen saina dawo da yamma zanshigo mugaisa,tace toh Allah ya tsare tamasa kiss a chiks nasa har data fita yace emm baby jimana,juyowa tayi tana kallonsa,cikin kallon soyayyah mai narka zuciyar wadda akema yace tum apna kayalakna(kikularmun da kanki),cikin murmushi tace i will insha Allah,good my princess yafada ,itakuma tace bye sannan ta fice shikuma yaja motarsa ya wuce,tana shiga khairy da murna ta tareta tana zolayarta barka da zuw mai sarauta,uwargida kuma amarya agidan likita,cikin dariya tace fadi kanki tsaye wannan haka yake,bayan sungaisa sukayita hiransu na yan uwa abin shaawah,haka suka wuni tate har TJ yadawo sai wajen4:30pm sannan papa yadawo amma haka TJ ya hanasu tafiya wai sai sunyi dinner tukun sutafi,haka suka haqura sai bayan ishai sannan sukafi amma kaginnan fauziyyah ta matuqar gajiya sabida yadda qafafunta ke mata ciwo, kawai sotake su isah gida dan tagaji da zaman motanma, tun amotan tafara kuka tana wayyo qafarta,haka yadinga lallaminta har suka iso gida,tundaga ranan fita inba yazama doleba ko antinatal bata zuwa ko ina Haka suka cigaba da rainon cikinsu, inda papa yake matuqar bata kulawa na musamman irin wadda mai ciki take buqata,cikin yana rayuwa.cikin halin lfy har Alah yasa ta cika EDD nata sai dai haihuwa shiru,ganin ta wuce EDD nata kuma haihuwa shiru yasa tafara damuwa dan batada damuwar data wuce ganin tarabu da cikin jikinta cos tagaji dashi sai baqar wahala datake sha,ga ciwon qafafu idan tazauna dakyar zata rarrafa ta tashi,ganin yadda hankalinta ya tashi sosai yasaka papa damuwa amma bai nuna mataba sai lallaminta dayake hadi da rarrashi,yanzunma suna kwance har wajen 12 nadare taqiyin bacci,babyna yakira sunanta ahankali cikin natsuwa,umm kawai ta amsa, meya hanaki bacci har wannan lokacin umm yana shafan gashin kanta,cikin damuwa tace nibanasonyin bacci dawurine saina farka cikin dare nagagara bacci idanuna su bushe,baby damuwar da kikasama rankinefa yasa har baki iya bacci,tace aiba dole nadamuba khairyfa lokacin data haihu batama cika EDD nataba ammma ni harna wuce da kwana biyu sai kuma tafara kuka,haba baby ya kike abu kamar wacce bakisan cewar shifa EDD dama 2weeks before or 2weeks after bane,pls naroqeqi ki kwantar da hankalinki kda kije BP naki ya hau baicin bakidashi,haka yasamu hartayi shiru da haka har bacci ya dauketa, washe gari bayan yadawo daga office suna zaune yace baby yadai jikin bakinjin komai,tace babu abinda nakenakeji nikam,yace shikenan Allah ya kawo haihuwan cikin sauqi,tace amin ya Allah Bayan sallan ishah suna zaune suna cin abinci sai ya lura bataci sai juya spoon din takeyi ,cikin kulawa yace babyna yadai bakicin abincin koba kyason asamomaki wani, aa kawai maratane ta kulle,marakuma baby, tace eh Allah kuwa yace to kidaure kici abincin,tace sai anjima idan tasakeni amma yanzun barin iyaciba,hankalinsane yaji ya tashi amma bai nuna mataba dan tunda yamma daya dawo yaga alamun haihuwa ajikinta yadda cikin yayi qasa sosai fiye dana kullum,shima abincin da bai qarasa ciba kenan Wasa farin girki tun tanajin abu kamar wasa har yazama gaskiya dan wani matsanancin ciwon mara da qafafu takeji kuma batsan taya zata misaltashiba bama,12am abunfa yaci tura bashiri yadauketa sai hospital akanhanya yakira momcy yafda mata sunkusa isa asibiti fauziyyah tana labour ,aifa nan itada da daddy suka taho asibiti ba shiri,papa suna isowa sibiti aka wuce da ita labour room,shima bayansu yabi ya shiga ciki,sai dai tashin farko ana gwada BP nata akasamu yahau sosai har 160,nanfa hankalinsa ya tashi dik yasan cewan hakan tana faruwa amma dai yadamu sosai sabida tsoron kada eclemsia ya shigeta Har akayi sallan asuba shiru bata haihuba sai dan karen azaba datake shafawa,nanfa papa yasake inda yakama ya birkice shima lallashi hadi da nasiha su momcy sukai tamasa haryasamu natsuwa,amma ya gagara komawa labour room din cos bazai iya ganinta awannan halinba,suna zaune saiaddua dasuke mata amma babu wanda akafadama around6:30am ta haiho qaton danta namiji,wani saeedah taji lokaci guda,jin kukan jariri yasa papa miqewa cikin sauri yashige labour room din,kanta ya nufa ya riqe hannunta yana mata sannu tare da adduoi,sai daime anasake gwada BP nata akaga yasake hawa sosai180,aifa nan hankalin papa ya kuma tashi take ashiga bata taimakon gaggawa gudun abinda zaije yazo..... ✍🏻Faty Mmn Faty 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty October, 2017 7⃣6⃣ Hannunsa sarqe cikin nata ya riqe gagam kamar za'a kwace masa ita,bakinsa yakai saitin kunnenta yana kiran sunanta cikin natsuwa da sanyi,babyna kina jina babyna,da kai ta amsa masa alamun eh tana jinsa, ajiyar zuciyah mai qarfi ya sauqe jin tana cikin hayyacinta,wasu allurai Dr Zainab tamata sabida BP nata kafin tasa aka miqo babyn saitin fiskanta tace mata madam ganan babynki mene kika samu?, kallonta takai kan babyn nata fari sol dashi kuma qato nan take wani qaunarsa taji yaratsa dikkannin jiki da bargo nata, cikin sanyin murya tace baby boy ne,murmushi Dr tayi tace good,sannan aka wuce da babyn dan agyarashi,haka papama sai alokacin yaqarema abinda ta haifa kallo sabida hnkalinsa na akan matarsa da lfyrta,murmushi kawai yake yana dad'a hamdala ma ubangiji abisa kyautar daya masa,yana rungume da ita har aka gyarata aka d'inketa dan ta qaru sosai kasan cewar girman yaron,dikda anmata alluran rage zafi amma baihana papa lallaminta yana shafar knta cikin salon soyayya da kwantar mata da hankali har aka gama mata komai,dakansa ya shigar da ita toilet dake cikin labour room din yamata wanka tsaf sannan ya fito wajen su momcy ya dan karb'an kayanta momcy tana ganinsa tace yadai papa su fauziyyah suke,da murmushi sosai afiskansa yace momcy lfynsu qalau kayanta ma zaki bani dan zaa maidata obstatric room,cikin murna tace masha Allah shikuma angonnawafa dan nurse tacemun namijine,sake fad'ad'a fara'arsa yayi sannan yace shima lfyrsa qalau suna shiryashine amma saikinganshi farisol dashi kyakykyawa kuma qato shiyasa ya bata wahala,momcy takama baki tace oh papa babu ko kunya kake jero wad'anannan bayanai haka,d'an sosa qeyarsa yayi yace kai momcy yawanefa yanzun wane kunya kuma ai gara mutum ya nuna jin dad'insa tunda kud'i baxai saya masaba,kayan tamiqo masa tace Allahu ya shiryeka papa kaikam kunyarka da sauqi tafada tana cewa kafin kufito barinje office d'in daddy toh nasanar masa lfynsu qalau sannan ta wuce, shima ya koma ciki Dakansa ya shiryata tsaf,sannan ya sunkuyo da kansa dai2 face nata yace my princess sannuko, murmushi tamasa kawai sabida batajin qarfin jikinta,ina kemaki ciwo? ya tambayeta yana shafan kanta, babu tafad'a, sai dai banjin qarfin jikina ne kawai, Alhamdulillah idan kin huta zakiji kinware kinjiko my life, gyad'a masa kanta tayi dai2 da nurse ta qaraso wajensu hannunta d'aukeda babyn, cikin girmamawa tace Dr ganan babyn tana miqo masa,hannu biyu yasa ya karb'i d'ansa kuma gudan jininsa,cikin so da qauna marar misaltuwa yake kallonsa ga yalwatatticiyar fara'a kwance kan fiskansa,lokaci guda yasakejin qaunar yaron kamar ya maidashi cikin cikinsa,yaro qato kyakykyawa mai kama da babansa dan babu ko tantama kamanninsa sak papa,sai qamshi mayukan jarirai yakeyi,an saka masa kayan sanyi farare sol masu sirkin light blue,ankuma nadesa cikin light blue showel sai qamshi yakeyi,nan take ya tofa masa adduo'i tareda sumbatarsa ta ko ina,fauziyyah kuwa kallonsu take cike da zallar qauna dan sun matuqar birgeta,kallonta yayi yace madam ganan babynmu karb'esa kisa masa albarka ya miqo matashi,karbansa tayi tana murmushi sannan itama ta tofa masa adduo'i nurse ce tadawo tace yallaba'ai za'a maidata dkin hutu sabida ta huta sosai, is ok yafada yana karba'an babyn, itakuma tadawo kan wilchair aka turata,abakin qofa sukaci karo da momcy dawowarta kenan sai suka wuce room da aka kai fauziyyahn,papane ya jawo plask ya had'a mata tea mai kauri ya tallafota yana bata inda momcy ke riqeda yaron tanata kan buga waya tanasanar da haihuwan,bayan tasha tea sai anan bacci yafara fisgarta sabida alluran da aka mata,bada jimawaba bacci ya d'auketa,sai anan papa yaji natsuwarsa yadawo jikinsa,daddyne ya shigo momcy ta miqo masa babyn tana cewa ganan abokinka sai bacci yake da alamu zaiyi haquri ba irinsu ooba,tafad'a tana kallon papa,dariya kawai yayi ya fice dan yagane dashi momcy take,yana fita yafara buga waya yana sanarda qaruwan da yasamu, haka ma'aikatan asibitin wad'anda suka sami labari sukaita masa murna,shikuwa bakinnan bai rufuwa tsabaragen farin ciki Kwananta d'aya da haihuwa suka koma gida inda yan uwa da abokan arziqi suka dinga zuwa asibiti gaisheta,hakanan dik wata kulawa da maijego da yaronta ke buqata momcy tana basu,hakan yasa basuda matsala,cikin ikon Allah BP nata ya sauqa sosai dikda bai dawo normal ba Kwanansu Abba da mama da qanwar maman umma hajja wadda itake binta amma bata da aure mijinta rasuwa yayi suka zo bh kuma ita zata zaunama fauziyyah zuwa arba'in,fauziyyah taji dad'in zuwansu sosai haka suka yini lis sai yamma suka tafi,bayan magriba ya maida momcyma gida tunda ganan umma hajja,suna shiga falo zaune suka sami daddy yana kallon Aljazeerah news, momcy tace barita watsa ruwa tukun data zauna sannan ta wuce,bayan papa sun gaisa da daddy nan yake tambayarsa umm daddy dama inason tambayarka wanne suna za'a sanyawa yaron,murmushi daddy yayi had'i da gyara zamansa yace kaji kafa Alamin dawani zance,aikai zaka zabi sunan daka yadace saika masa hud'uba dashi,shiru yad'anyi yace shikenan daddy zanmasa hud'uban da sunanka,kallonsa daddy yayi yace anyakuwa bakaso kankaba banason kazamo cikin mutane masu son kansufa,kallon daddy yake cikin rashin fahimta yace menayi daddy?, daddy yace inhar dacewane to sunan Abbanku shiya dace da yaronnan sabida haka nina yafe asanyawa masa sunan Abban fauziyyah dan aminina ya cancanci fiye da haka,papa yace insha Allahu sunan Abba zaa saka masa ,cikin jin dad'i daddy yace masha Allah, Allah ya muku albarka,ya amsa da amin, nan sukaita hira har momcy ta fito kafin yamusu sallama ya tafi ***** Washegari dasafe kamar kullum ya shiga ya dubasu yaga yadda suka kwana,cikin sa'a yau yasamu fauziyyah idanunta biyu harma tayi wanka, dan yau jikinta da sauqi sosai takeji,shima babyn an masa wanka ana saka masa kaya kenan ya shigo, har qasa ya duqa yagaida umma hajjah,bayan sungaisa ta miqo masa yaron dan tagama shiryashi sannan zata fice, cikin girmamawa yace umma nifa fita zanyi nashigo mugaisane dama, tace lah bakomai zanhado mata abin karine kayi zamanka sannan tafice, tana fita ya maida kallonsa kan fauzynsa wanda shigowarsa yakejin wani shauqinta na d'ibarsa amma ya matse sabida idanun umma hajja, wani kyau yaga tamasa tayi wani bulbul da ita irin cikar jegonnan, matsowa yayi bakin bed inda take zaune ya kwantar da yaron abayanta kafin ya rungumeya ajikinsa yanajin tabbas yayi keawarta dan rabonda ya kebe da ita haka tun randa ta haihu,itama sake narkewa tayi ajikinsa cikin salon murya mai sanyi tave momrning myonly, saida yabata wani hot kiss sannan yace morning my princess,kuntashi lfy dai, lfy lau muke n u?,yace nima haka sai matsanancin keawarki dake damina baby i missed u so much yafada yana kissing dogon hancinta,tace nima hakafa yace eyyah kice zamuna dan fakan idanun umma mudamke rage zafiko yafada yana kashe mata idanu,zaro idanu tayi tace waa tab nikam banceba,dariya yayi yace sarkin tsoro meye nawani zaro idanu, tace bawai tsoro bane kawai banmanta labour room bane,yace indannan wannan ne kada kidamu next nizanyi labour d'in tinda kinyi naki ko sweety, tace ah lalle kuwa naqi wayon,yace toya jikin dai?, tace dasauqi sosai,yace good amma ba inda kemaki ciwo ko? aa babu komai yanzunkam,yace yayi kyau tinda har kinwarke kawai kifara shirin karban new baby tunda yazunma babu wanda zai ganki yace kinhaihu,tace lallekuwa ainida haihuwa bayanzuba, yace tab kisake lale danni dik shekara sai kin haihu sonake natara yara masu yawa yafada yana miqewa tareda d'aukar babyn ahannunsa,tace umm maganarka batada amsa, yace ko,tace yess,yace zamugani to,baby barinje da my little baby inason zan masa huduba, tace toh, sannan ya fice......... ✍🏻Faty Mmn Faty 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty October,2017 7⃣7⃣ Baifi 30mins ba ya dawo dashi sai kuka yake zabgawa,afalo yasameta tana breakfast,jin kukansa yasa ta ajiye spoon d'in hnnunta ta karb'esa,baby sauri kibsa bincinsa ko yunwane yake dminsa yayi maganar yana kallonta,tace is possible ma hakan cos yayi wanka baishaba kuka fita,cikin tausayin yaron yace ayyah my little baby am sorry daddyne ko yaqarasa maganar yana shafa kan babyn,shikuwa tunda yasamu ya cafke abincinsa yayi shiru sai zuqa yake abinsa,papa cikin qaunarsu ya zuba masu idanu yana kallon yadda take shayar da yaron,qirjinnan acike taf kuma atsaye cak kamar bata haihuba nan yaji ransa ya biya take ya miqa hannunsa yana shafan samansu,d'agoda fararen idanuwanta tayi tana kallonsa kafin tace my one kanason ya kwarene?,aiko cikin sauri ya d'auke hannunsa yana cewa Allah baby nayi missing nimafa gaskiya that's y nad'anji duminsu yaqarashe maganar murya qasaqasa,murmushi tayi sosai tace toko zaka shane?,d'an zaro idanu yayi yace aikam da zuqa 1 dan zuqe masa candy candyn,atare sukayi dariya sabida d way yayi maganar irin so funny d'innan,ahankali yace baby bakitamb ayi sunan da za'a sakama babynmu bafa gashin harna masa hud'uba batareda neman shawarinkiba,cikin natsuwa tace nikam dik sunan daka zab'a masa is ok awajena sai dai ince Allahu yamasa albarka ya kuma raya manashi rayuwar addinin musulunci,cikin jindad'in addu'arta yace amin ya Allah my wife,nagode da kika fahimceni sosai nasan kuma zakiyi farin ciki da sunan dana zab'armasa cos sunan mutum mai matuqar daraja da qima da kuma dattaku wanda nake fatan yadauko halayen maisunan,dan yanada kyau idan zakayi takwara kayima mutumin kirki,kodan kwad'ayin yasamu halayen kirki irinna mai sunan,cikin jinjina kai tace wannan haka yake kuma tayi na'am da zancensa,yace mata kicanki wanni sunane,batareda tunanin komaiba tace sunan daddyn mune dan har ga Allah tada'au sunan daddyne akasamasa,murmushi yayi had'i da girgiza kansa yace nop wifey bataciba,da mamaki ta dubesa kafin tace komai yace sunan Abbanmune wato SA'EED,kallonsa takeyi kurr yayinda taji wani sanyi aranta yadda papa ya mutunta mata mahaifinta,lumshe idanunsa yayi ya bud'e kafin yace yess sunan Abbanmune inyaso zab'i yana wajenki saiki masa alkunya dan bamai kiramun sunan mahaifi direct atow,rasama mezatace masa tayi zata fara godia,yace shshssh ya isa hakanan baby nimafa mahaifinane muyi fatan Allah ya albarkaci rayuwarsa,cikin murya mai sanyi tace ameen my only,sannan tace to zamuna kiransa da FAWWAZ,yace nice name shikenan tunda yamiki nima yamun,miqewa yayi yace barinje office madam zanbiya gida tacan so sai yamma zandawo tunda naga bakwa rabo da baqi,tace Allahu ya kiyaye adawo lfy akuma gaida su momcy dikdama d'azun munyi waya,yace amern babyna saina dawo saida ya paking forehead nata da swt kiss.kafin ya fice yabarga tanajin wani sabon qaunarsa har cikin ranta Bashi ya dawoba sai yamma lis,sabida ayyukan dasuka riqesa a office,ga TJ yamasa waya kancewar zaishigo d'aukar madam nasa dan awajen fauziyyah ta yini dikda itama tsohon cikinne da ita,kaya niki niki sukaga ana shigowa dasu wadda tunda akayi haihuwar kullum acikin hidima yake baiko gajiya,saida ya gaida umma sannan ya wuce side nasa ya watsa ruwa ya fito falonsa na qasa dan TJ najiransa,yana shigowa TJ yafara yayi dai ngon qarni,kashe hannu sukayi papa nacewa fad'i kanka tsayeka qara,yace anahaka ango na fauziyyah mai komai dozen,yace toya son ranka saidawa,TJ yace yakuwa inba nace Allah yaqara dankwan soyayyah, papa yace oho nad'au sab'anin haka zakace ai,TJ yace waneni nan suka sheqe da dariya sukayita hiransu har aka kira sallan magrib, saida sukayi dinner tukun suka tafi Haka kwanaki na tafiya har yau ana gobe suna arananne kuma jama'ar dambam suka iso, aunty mabarukhama yau ta iso aunty niima kuwa kusan kullum saitazo,washegarin suna akayi taro lafiyyen taro wadda fad'in irin kyau da fauziyyah da fawwaz sikayi b'ata lokacine,haka zalika irin kudi da kayan da suka samu abin sai son barka dan Abba sun taka rawar gani matuqa haka yan uwata ba,a barsu abayaba, kaxalika su momcy da daddy sunyi bajinta sosai,haka abokan papa tasamu kyaututtuka daga wajensu,mai kankat d'in kuwa wato uban gayyar DR ALAMIN,kayane na kece raini abin har bazai qirguba,kudi yakashe kamar ba gobe haka ya baje ya nuna farin cikinsa sosai,haka akayi hidima sosai akayi taro lfy akawatse lfy bayan anyi walima da yamma anraba kyaututtuka na abubuwa mai d'aukeda photon fawwaz,jama'a sunata saka albarka haka,kowa ya koma gida cike da farin ciki Sai bayan sallan isha'i sannan tasamu natsuwarta ga wani uban gajiya dake daminta, fawwaz kuwa tuni yayi bacci dan yasamu anmasa wanka da ruwa mai d'umi yaji dad'in jikinsa sai bacci,itamma wankan tayi ta foto ta shirin bacci harta kwant saiga wayar papa,da sallam tad'auka,wani sanyi yaji har cikin ransa sabida yau yini guda baigantaba baikumaji koda muryartaba,cikin murya qasa qasa yace my hrt i missed u so much,nazama maraya gani kwance nikad'ai,gyara kwanciyarta tayi tace me too baby nayi missing kwanciya afaffad'an qirjinka mai daukeda dayalwataccen ni'ima,sake lumshe idanu yayi cos taqara kashe masa jiki sosai d ydda take salon maganarta,ahankali yace pls baby kizo side nawa dad'anji duminki kozan sami natsuwa,murya asanyaye tace haba my one taya harna kwanta zanfito na ratsa mutane nataho wajenka,yace pls mana baby kice nayi baqine zaki kawomun fawwaz,yafayi bacci tin dazunamma barin dakkosa ahakan ,yawwa my wife that's y nake qara sonki, snnan ya kashe wayar,qatuwarhijab nata tasakaakan kay an baccinta tarungumo fawwaz akfad'antata fito falo nan tasamu su umma suna hira,kamar munafuka tace umma dama ya Alamain yayi baqi barin kaimusu fawwaz suganshi,umma tac e tokaishi mana gashima har yayi bacci,tace toh sannan tafice ta nufi d'akin papa......... ✍🏻Faty Mmn Faty 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty October, 2017 *Nayi kuskuren sunan FAWWAZ na ainahi nace SA'EED, tunda takwaran Abbane kenan sunansa USMAN tunda sunan Abban kenan,dafatan zakumin afuwa tunda babu wadda yafi qarfin kuskure* 7⃣8⃣ Tana shiga side nasa, direct bedroom nasa ta wuce,ahankali ta tura qofar ta shiga lokaci guda sanyi da qamshi mai dad'i ya bugi hancinta,tasowa yayi ya karbi fawwaz sannan ya kwanto da ita jikinsa,ahaka suka qarasa bakin bed ya kwantarda fawwaz tareda manna masa kiss afiskansa,baice da ita komaiba saima d'aukan remote da yayi ya rage qarfin AC, sabida fawwaz,kafin ya jawota jikinsa ya zare hijab dake jikinta, ya nufi kan resting chair dake gefen gadon ya zaunarta shikuma ya miqe ya kwan tareda daura kansa akan laps nata,lumshe idanu yayi yana shaqan qamshin dake fita daga jikinta tamkar bamai jegoba,jin yayi shiru yasa takira sunansa cikin daddad'an muryantamy one,bud'e lumsassun idanuwansa yayi yana kallonta yace umm babyna ya akayine,cikin shagwab'a tace naji kayi shirunefa,sake gyara kwanciyarsa yayi yace badolenaba nasami natsuwa,rabonada najini ajikinki haka sati guda kenanfa,gaskiya kisan yadda zakiyi dan wlh akame nake,d'an zaro idanu kad'an tayi tace ammadai kasan haihuwa nayiko kumama koba hakaba aidai banada tsarki,yace aibacewa nayi zanje canba kawai kimun irin abinda kikemun d'innan kozansami sauqin abinda nakeji, turo baki tad'anyi tace inda natafi wankan gidafa?,aifa tashi yayi zaune yace wankan me aiko da ba inda zakije lalle baby kindaina sona datausayina, tace meya kawo wannan mganar kuma, yace ahto inba hakaba taya zakice wai inda kuntafi to nikuma kubarni nayi yaya kenan, tace cikin zolaya saikayi zamanka agidankaman, yace ah lallaikam kedai Allah ya taqaita umma ta fansheni shiyasa nake dad'a ganin girmanta sosai dan Allah badan itaba birkicewa zanyi kawai ince bamai daukarmun mata wani wai wankan gida,dariya yabata kuma tasan zai aikata hakan,yace au dariya nabakima,yace aa nibanceba ta lumshe idanuwanta ta jingina da jikin kujeran dan bacci tafaraji sosai,jin tayi shiru yasa yace babyna kema kingajiko,nagaji dik jikina ciwo yakemun tai maganar idanunta alumshe,ayyah sannuko barin maki tausa yana maganar yana.....nanfa itama ta biyesa sabida tasan halin mijinta inhar akantane baya kure abubuwa da dama,shiyasa take qoqarin samar masa natsuwa,takai fiyeda awa guda kafin ta miqe itama jiki amace ta d'auki fawwaz da kyar ya miqe sabida shima jikinsa yayi weak sosai harwani bacci yakeji ya rakota har bakin qofa yanata zuba mata albarka sannan yamata saida safe ta wuce b'angarenta,shima juyawa yayi ya wuce toilet, wanka yayi ya fito ya bi lfyr gado lokaci guda bacci mai dad'i yayi gaba dashi zuciyarsa fess Kwanaki na tafiya inda Fauziyyah da Fawwaz kesamun kulawa na mussan daga wajen ma hajja,gashi kullum acikin yimata had'i na mussam take sabida gyaran jikinta, cikin sati uku suncanza sunyi kyau na mussamman,haka fawwaz ya cika yayi bulnul dashi,ga wayo da kullum yake qarawa, haka afannin papa kullum cikin basu kulawa yake har umma hajja tasaba da halinsa, tun tana jin kunyarsa harta wate yanzu,tunda zaishigo ya dauki fawwaz ya masa wasa kafin ya fice office haka idan yadawoma,kullum burinsa ya faranta masu, momcy ma tana yawan zuwa dubasu akai2,cikin ikon Allah har saura kwana uku suyi arba'in, fawwaz ya qara girma yayi kumatu inka ganshi zakace d'an wata uku ne,ga kyau da kullum yake qarawa,ranan da suka cika arba'in ranan suka tafi dambam,papa dakansa ya kaisu bai kwanaba aranan ya juyo bbayan yayima umma hajja shatara ta arziqi,yabarsu sai bayan sati biyu zaidawo ya daukesu,haka ya dawo bh cikin keawarsu Cikin sati biyu da tayi. adambam babu inda baya zagaba,gidajen yan uwa da abokan arziqi,tindaga kan danginta harna papa,wadanda suka jima basu gantaba idan sunganta sai dai suce masha Allah,kullum Abba indai yana gida to yana tiqe damai sunansa, dan wani iri son yaron yakeyi abin sai wanda yagani,ana gobe zasu tafi kusan kwana sukayi suna hira dasu mama,washegari papa yazo yadaukesu inda takejin kewar gida dan tasaba asati biyun datayi,papa kuwa zuciyarsa cike da farin ciki koba komai farin cikinsa ya dawo,aranan suka sake barje amarci dan papa jinta yayi kamar yau ya bareta aleda dan baqaramin gyara tashaba bayan taje dambam ma, Rayuwa sukeyi mai tsafta cike da so da qauna,kowannensu yana qoqarin kyautatama dan uwansa, kullum papa yana sake godema Allah daya sake malaka mada fauziyyah,haka suke kula da d'ansu da tattalinsa, gashi sai girma yakeyi kamar wadda ake masa pampon iska,watanninsa takwas cur yafara tafiya abin shaawa,kullum rayuwarsu abin shaawa gashi Allah ya sake budama papa hanyoyin arziqi da dama, yana kuma qoqarin sauqe dik wani nauyinta dake kansa, amma yahanata aiki yace dik abinda takeso zai mata amma banda batun aiki,ita ma taamince tinda bairageta da komaiba Watannin Fawwaz 13 gudu ko ina ba inda baya shiga,saiyaje gidan momcy ma ya wuni acan dan ba abinda bayaci kamar ya yayyen yato sabisa girmansa,ana cikin haka tsulum saiga ciki na watanni uku murna wajen papa baa magana amma fauziyyah hankalinta ya tashi matuqa...... ✍🏻Faty Mmn Faty 🌾🌾🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾🌾 🌾🌾🌾 Budurwar Qauye🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀ Written by Faty Mmn Faty October, 2017 🔚🔚🔚 7⃣9⃣ Tunsafe bayan dawowarsu daga hospital take rizgar kuka akan cikin jikinta,tun ahanyarsu ta dawowa yake lallaminta amma kamar zugata yakeyi,hakan yasa haushi ya kamasa ya rabuda ita dan gani yake mene zai dameta tinda Fawwaz qalau yake, sai dai inkuma tana cikin layin matan da basason haihuwa dayawane kuma, shiyasa ya rabuda ita, suna isowa gida bai sauraretaba ya wuce ciki ya had'oma Fawwaz abubuwan da zai buqata ya kaishi wajen momcy ya wuni,yakai irin 3hours kafin ya dawo amma da mamakinsa har lokacin tana kwance a room nata tana aikin kuka,mamaki abin yabasa ya qaraso har bakin bed inda take kwance ya zauna,janyota yayi ya d'aura kanta akan laps nasa,kafin yafara magana anatse akuma tausashe, shalelena wai har yanzun baki haquraba haka kina ta kuka har kanki zaiyi ciwo babyna,batayi shiruba saima qara sauti datayi, hawayenta yafara share mata cikin lallami yace no wifey ya isa hakanan kukan kiyi shiru kifad'amun damuwarki kinji,amma kibar kukannan cos har cikin raina nakejinsa,ahankali ta tsagaita da kukan da dasashshiyar muryarta datasha kuka tace ni ka kyaleni naji da abinda keda muna sai hawaye sharr,haba baby dik akan kinada ciki yasa kika tada hankalinki saikace shine na farko haba my fauzy kada kiyi haka mana ki butulcema Allah akan kyautar da yamana bayan akwai dubunmu da basu samuba,kamata yayi mugode masa bawai kitada hankalinki ba ko kuma dai haihuwarce ba kyaso ko danine bakison haihuwar?, jikintane yayi sanyi yadda yake magana cikin damuwa hakan yasa dasauri ta girgiza kanta tace aa nibance banson haihuwaba ko dakaine banso, yace to fad'amun damuwarki, cikin sanyi tace fawwaz mafa shekarasa daya sannan kuma wlh nibanmanta wahalanda nashaba ko hutawa banyiba ace kuma cikine dani sai hawaye suka shiga zarya akuncinta, is ok baby ya isa haka indan wannanne kada yadameki tunda ya girma abinsa yana gudu ko ina, batun wahala kuma bana cemaki idan kinyi daya nima zanyi dayaba,so kada kidamu yanzu turn nawane nizanyi laulayi da labour iyaka kihaifo mana babynmu kyakykyawa mai kamada keh ya qarashe yanajan dogon hancinta,yanda yake maganar da lallami da taushi dik da tasan cewar bamai yiwuwa baneba amma taji sanyi har cikin ranta lokaci guda murmushi ya kubce mata,ganin tafara sakkowa yasa yace yawwa 'yan matana ko kefa amma da kintda hankalinki da nawa pls yawuce haka mu rungumi abinmu da addu'ar Allah ya kawoshi lfy,ahankali ta amsa da amin Tin daga lokacin ta kwantar da hankakinta, ta haqura ta rungumi qaddara wacce tariga fata, da yardar Allah haka ta cigaba da rainon fawwaz da kuma cikinta,gashi tayi sa'a wannan karon batashan wahalan laulayi sai d'an abinda ba'a rasaba, cikinta nada watansa shida cur sannan ta yaye fawwaz lokacin watanninsa 16, dake yana samun kulawa sosai bazama ace yasha nonon cikiba, ana yayeshi momcy ta d'aukesa ya koma wajenta,haka papa yacigaba da kulada fauzynsa da kuma unborn child nasu,har Allah yasa yakai watannin haihuwarsa,nan suka fara tsammanin haihuwa kuma kullum suna addu'ar haihuwar tazo da sauqi,Allahu maji roqon bawansa wata ranan talata da misalin qarfe 12am naquda ya tashi fauziyyah wacce dama baccin rabi da rabi take tinda cikin ya tsufa, ba b'ata lokaci suka tafi asibiti cikin ikon Allah asuban fari ta haifo yarinyarta mace, batada maraba da mamanta dan tsabar kama wane antsaga kara,murna wajen papa ba'a magana saikace wannan ne haihuwar fari da aka masa,haka su momcy suma murna,washe gari yan uwa da abokan arziqi suka cika anata murna,ranan suna yarinya taci sunan momcy SAUDAH zasuna kiranta da FAIHA, nanma ansha hidima sosai dan baqaramin kud'i papa ya b'ararba,abin sai son barka tare da fatan Allah ya raya baby Faiha *2 YEARS LATER* Fauziyyah ce zaune awani tangamamen falo na alfarma,tana riqeda jariri tana shayardashi wadda dagani baifice kwana arba'inba,papane ya shigo d'aukeda Faiha akafad'arsa, hannunsa riqeda hannun Fawwaz wadda kesanye da uniform da alamu tasowarsa daga school kenan,da sallama ya shigo fiskansa d'aukeda qayataccen murmushi,d'agowa tayi ta amsa itama da murmushi tace oyoyo har kundawo,zaunarda Faiha yayi yana cewa mundawo kinsan yau friday shiyasa,tace hakanefa ai sai malam saminu yayi magana kancewar zai tafi d'akko fawwaz, nace yau kana gida kama fita daukosa lokacin bainan shiyasa baka sanar masaba,yace ok yaukam nahutar dashi, lami mai aiki takira tadauki fawwaz tacanza masa kaya,sauqarda faiha yayi yace mamana koma nan kizauna barin d'auki daddynako,nan tab'ata rai zatayi kuka, fauziyyah tace kada kiyi kuka momcyna rabuda daddy shida FARHAN (mesunan daddyne) bazasusha ice cream namubako,gyada kanta tayi tana hawa jikin umminta,papa yace haba mamana kinfa girmane shiyasa, fauziyyah tace rikiciba idan bakwanan dik gidannan yamun wani iri gashi nakasa sabawa da sabon unguwannan,papa yace idan sunanan kuma kice sundamekiba tunma bakiyi komaiba,wani kallo tamasa wadda yasashi dariya har itama yabata dariyan tace dole kayi dariya mana,yace aidai ni kece kikasani dariyan da wani kallo da kika nausheni dashi,cikin dariya tace dafatan bakaji ciwoba to?, yace ciwo kai harya ma kunbura wajen, tace oh sorry amma kacancanci fiye da hakama,yace to miye aciki keda bawaan haihuwa kike shaba,turo dan qaramin bakinta tayi tace nifa nagaji dayin kunika yanzunkam, yace to miye aciki bakiga kuma haihuwarsu yafi sauqiba,tace umm nidai yanzunkam dan huta atow tai maganar tana juya manyan idanuwanta,yace muyi fatan samun masu albarka koma yaushene,tace hakane my only,yace yawwa matana nidai ba abinda zancemaki sai Allah ya biyaki da gidan aljanna dan kinmun komai arayuwa ,kinbani so, qaunar, da kulawa ga kuma kyawan yara, kinga banada damuwa sai fatan Allah ya bani ikon sauqe nauyinku dake rataye awuyana,cikin tsantsar shauqin qaunar mijinnta tasaka hannunta ta saqalo wuyansa had'i da kwantowa jikinsa ta amsa da amin ya Allah mijina abin alfarina akoda yaushe,saka d'ayan hannunsa yayi ya rungumeta tsam ajikinsa sunajin wani yanayi na musmman wadda sukad'ai sukasan ma'anarsa atattare dasu....... TAMMAT BI HAMDILLAH... *GODIYA* DIKKAN YA BO DAGODIYA SUN TABBATA GA ALLAH UBANGIJIN, NAGODEMA ALLAH DA YABANI DAMAR FARA WANNAN LITTAFI DAKUMA GAMASHI, KUSKUREN DAKE CIKI ALLAH YA YAFEMUN, ALKHAIRIN DAKECIKI KUMA ALLAH YABAMU LADANSA BAKI D'AYANMU AMEEN... *JINJINA* INA MIQA SAQON JINJINATA AGAREKU MEMBERS NA NA MMN FATY NOVELS GROUP,WADDA ABISA KWARIN GUIWAR DA KUKE BANI HAR ALLAH YASA NAKAIGA CIN NASARA,GISUWARKU TAMUSAMMANCE DON KUN TAKA RAWAR GANI MARAR MISALTUWA AKAN WANNAN NOVEL DIN NAGODE ALLAHU YABARMU TARE DA QAUNAR JUNA... HAKA BANTAKUBA MEMBERS NA JUST HAUSA NOVEL,NA GODE DA QAUNAR DA KUKA NUNAMA LITTAFINA,HAKA BANMANTA DA SAURAN MASOYANABA ADIK INDA KUKE, WAD'ANDA NASANI DA WAD'ANDA BANSANKUBA,DA WAD'ANDA SAQONNINKU YAKE ISOWA GARENI DA WANDA NAKU BAI ISOBA, DIK NAGODE KUMA NIMA INA QAUNARKU ADIK INDA KUKE MMN FATY LUVS U ALL 😘😍 ✍🏻Faty Mmn Faty