[10/09, 22:14] +234 803 697 8511: 🌸SHAHAAB🌸 (Romance) Writing By Amnah El Yaqoub Dedicated to Aisha's Name Like my Page On Facebook👇🏻 https://www.facebook.com/amnahel 1&2 ______ Chamo,Dutse Area (Jigawa State) Wata tsohuwa ce me kimanin shekaru Sittin da Shida tashiga cikin wani madedecin gida na masu qaramin qarfi, Sai mita take tana sababi "Haba! Wannan aba da'ake ganin darajarta, ake saka mata d'an kamfai, asaka mata siket, sannan ad'aura zani akai,yau itace a wangale wannan Yara na Asbiti Sai leqawa suke" Ta qarasa maganar tanajan kujera 'yar tsugunno tana zama, Ummah dake Gefe a zaune tana yanka albasa akan qanzo tace "Sannu da Zuwa Hajja, bade har yanzu bata haihu ba?" Wadda aka kira da Hajja tace "bata haihu ba har yanzu,wannan yarinya tana ganin azaba, sunce fa tasamu yaga har waje hud'u" Ummah ta zaro ido tace "Hud'u?"😳 Ta6e baki tayi tace "yaga Hudu Hadiza, wata yarinya tana nan Sai leqawa take, takasa tsinana mata abun Arziqi, nide nataho nabar jummai acan Sai dawurwuri take tana tsoro kar jikarta ta mutu" "kode wata yarinya ce siririya, zaki ganta 'yar doguwa itace take kar6ar haihuwar?" cewar Ummah Hajja tace "itace inajin, tana nan wata Mai kamar Sanda de" Ummah tace "Hajja tokode Sandar cema?" Wadda aka kira da Hajja tace "Fad'i kanki tsaye Sandar cema, wannan qirji ashafe, ga uban tsawo, tun dazu take cewa ga kainan yataho Amma shiru kakeji, nikam nataho, idan ta sauka saina koma" Wata yarinya ce tafuto daga d'akin Hajja,bazata wuce shekara goma Sha takwas ba, fara ce tas Me matsagaicin tsawo, tana Sanye da Hijabi madedeci ajikinta, kasancewar hijabin ba dogo bane hakanne yabawa bajajjan hips dinta damar bayyana, kallon su tayi duka su biyun, ta zabgawa Hajja Harara, sannan ta d'auki buta ta wuce bandaki, cikin ranta tana tunani tabbas zama da mad'aukin kanwa.... Gashi yanzu itama Ummah ta biyewa Hajja suna zagin baiwar Allah, fisabillillah banda sharrin Hajja tayaya za'ayi a cewa mutum Sanda?🤔 Hajja databi Bayan yarinyar da kallo tasaki ajiyar zuciya tace "mesunan qawa da masifa take, tunda tafara qirgen dangi muka shiga uku da saka hijabi acikin gidannan, kullum tana cikin Hijabi kamar abun masifa, d'an girgen dangin ne bataso mugani, inba hakaba mutum yayi ta yawo da hijabi muba had'a dangi mukai da limamai ba, wannan jaraba har Ina, da wannan zafin duniyar mutum zaiji koda yawo da Hijabi " Ummah tayi murmushi ba tace da'ita uffan ba, saide cikin ranta tace"kunfi kusa" Adede lokacin yarinyar tafuto daga bandaki, har yanzu hararar Hajja take, tsugunna wa tayi tafara alwala, saida tazo wanke fuska sannan ta janye hijabin dake jikinta, lokaci d'aya tulun gashinta me santsi da tsawo ya bayyana, gashin har qyalli yake saboda yasha wanki, Hajja ta kalleta ta Ta6e baki sannan ta shige cikin dakinta inda yarinyar tafuto Ummah ta kalleta tace "AISHA, idan kin idar da sallar ga qanzonku Nan keda Hajja" Kafin ta amsa mata, Hajja tafuto daga cikin dakinta da robar Vanillah a hannunta tace "A a nikam bazan iyacin qanzon Nan ba, Jikar Jummai tana can a Asbiti rai a hannun Allah, Ina Naga tacin qanzo" Wadda aka kira da Aisha, ta bude d'an qaramin bakinta Mai launin pink, cikin siririyar muryarta ta kalli Hajja tace "Amma ai gashinan hakan bai hanaki qulla Vanillah ba" Kafin Hajja tabata amsa wani yaro yayi sallama yashigo yace "Hajja A'i, abani kunun Aya na Hamsin" Kudin ta kar6a, tabashi kunun ayar tana fad'a masa "kadawo min da jarkar kaji" Yaron yace "To" sannan yafice daga gidan Aisha ta'idar da sallar, sannan tafuto tsakar gidan hannunta d'aukeda Radio tana kunna wa. qanzon dake gaban Ummah ta d'auka, ta zauna akusa da Hajja, sannan ta ajiye Radion agefe, tayi Bismillah tafara cin qanzon,had'in qanzon yayi mata dad'i sosai, batasan lokacin data tamiqa hannunta taqara sautin Radion ba, Adede lokacin ne me karanta labarai take cewa"to masu sauraro kuci gaba Sauraron Freedom Radio dake Nan jihar Jigawa domin samun rahotannin bidiyo da hotuna kan labarun Najeriya da Nijar da ma sauran sassan duniya baki daya,ayau ne Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kafa dokar hukuncin kisa ga duk wanda aka kama da laifin yi wa ƙaramar yarinya fyaɗe, acikin birnin tarayya Abuja kuwa, Shahararran d'an kasuwa, Kuma matashin Shugaban E.F.C.C, Wanda akafi Sani da MAHMUD WAKILI, ya Bawa Yan qungiyar qwallon qafa ta Nigeria kyautar nera million talatin, sakamakon samun nasara dasukai har suka samu kyautar kofun zakarun nahiyar Africa, matashin de yaqware wajan aikin sa, inda yake aiki ka'in da na'in wajan ganin ya daqile cin hanci da rashawa acikin wannan qasar, MAHMUD WAKILI ya kasance..... " Cikin sauri takashe radion,batare dataji qarshan labaran ba,qasa tayi da kanta ta zubawa qanzon dake gabanta ido Batasan meyasa ba kawai taji mutumin bai wani birgeta ba, menene abun birgewa anan da har gidan Radio zasu dinga yayatawa? saboda Allah duk cikin Wanda ya Bawa kudin Nan tasan cewa sunada Hali, ga talakawa barkatai suna buqatar taimako Amma manyan qasar basayi musu, saide a qarawa me qarfi wani qarfin, mutum ne zaka ganshi da 'ya'ya samada guda shida, Amma bashida cin yau bare na gobe,yanzu Yan Ball za'a dauki kudi a basu har million talatin, jijjiga kanta tayi, cikin ranta tace "Allah yahad'ani dakai ko sau d'ayane arayuwa,a ranar zan manta cewa sunanka d'aya da mahaifina" Hajja dake Gefe tace "masu abu da abunsu, yawanci zakiga masu suna Mahmud sunada kud'i, Amma ni nawa mahmud din Sai godiar Allah" Daga Ummah har Aisha babu Wanda ya tanka mata, asalima Aisha ji tayi gaba daya ranta ya6aci Dajin labarin wannan mutumin, d'an qanzon datake ci taji yafita daga ranta, tashi tayi ta shige daki, tasauya hijabi domin shirin tafiya makaranta Tana jiyo wayar Hajja tayi ringing, Hajjan ta d'auka tace "jummai ya'akayi? Me naqudar tasauka?" Daga d'ayan bangaren jummai tace "tasauka Hajja, ansamu d'a namiji, yanzu ma gida nazo nadauka mata d'an kunun kanwa, nace ko za'a samu d'an sauran sikari (suger) awajanki zan zuba mata acikin kunun?" Hajja tace "wallahi babu jummai, saide zuwa anjima zan siyo" Jummai tace "to shikkenan" daga Nan takashe wayar Aisha dake shirin futowa daga d'akin cikin ranta tace "Kai wannan mata da jarabar roqo take wallahi, jikar ki ta haihu Amma kikasa siyan sigan daza'a zuba mata acikin kunu Bayan ba kudin kika Rasa ba?🤔 Sallama tayi musu ta wuce makaranta, tanajin Hajja tana cewa"to me sunan qawa saikin dawo" Tana fita tahangi qaninta jabir, kana ganinsa zakagano tsantsar kamar dasuke da juna, batace dashi uffan ba tawuceshi, shine yaga yanayinta kamar ranta a 6ace yace"me sunan qawar Hajja antafi ne?" Share shi, cikin sauri ya qaraso wajanta ya fizge jakar littattafanta, cikin 6acin rai ta Kalleshi tace "JB Bani jakata Dan Allah, wallahi raina ne babu nishadi" "keda Hajja ne?" yajefo mata wannan tambayar, ajiyar zuciya ta sauke tace "Wacce Hajja? Labari naji a Radio Wai shugaban EFCC MAHMUD WAKILI yabawa Yan qwallo kyautar kudi har million talatin jb, wallahi banason mutumin Nan, haka kawai naji bai kwanta minba" Kwashewa da dariya jabir yayi yace "toke menene abun damuwa anan? Ke suna qoqari fa Yan Ball din, akwai su Big Brother manyan Yan ball ne,inde sunci ball menene aciki Dan anbasu kyautar kudi? Hakan zaisa su sake dagewa, muje na rakaki makarantar" Ya qarasa maganar yana Jan hannunta, qwace hannunta tayi tace "yanzu Kai hakan be 6ata ma raiba? Nikam haushi yabani wallahi, Ina laifin ma yabawa talakawa kokuma nakasassu,har yanzu nema muke Asamu atara Maka kud'in registration katafi makaranta ko 'yar legal Ringim dinnan ne kaima kaje kayi,Amma Yan Ball fa jb, jinake da zan ganshi sainayi masa tatas wallahi, wannan ya wuce kashe kudi saide almubazzaranci" Dariya jabir yasake yi akaro na biyu yace "Wai wa Zaki Gani? Shi Mahmud din? Ke irin wannan mutanan waye yafada miki suna zama a qasar? Mutumin daya shahara afannin kasuwanci, ga Kuma Babban muqami a Gwamnati shine kike tunanin Zaki Gani a wannan qauyen? To banqi ba in waya Zaki Ara kiyi search din photonsa a opera kigani, Amma inba hakaba Ina muke da hanyar ganinsa" Cikin masifa tace "in ari waya inyi searching din photonsa me hakan zai tsinana min?" Cikin murmushi jabir yace "Arziqi zai tsinana miki" Cikin 6acin rai tace "saide tsiya wallahi" Suna wannan musun suka qaraso islamiya inda take koyarwa, abakin get din makarantar tahadu da qawarta Walida wadda suke koyarwa tare a makarantar,Walida tace "Aysha Mahmud yaude munzo tare" Cikin son kawarda 6acin ranta ta amsa mata, sannan suka shige cikin makarantar shikuma jabir yajuya zuwa gida Wani yaro ne yashigo gidan yace "Hajja A'i abani ruwa na nera goma me Sanyi" Cikin masifa tace "bazan bayarba, yankare masu shegen iyayi..., idan ruwa babu Sanyi kuce abaku me Sanyi, idan ruwa me Sanyi ne kuce abaku marar Sanyi, inada me sanyin bazan siyar ba, har a cinikin nera gomane mutum yakeda za6in kalar Wanda yakeso"(🤭) Yaron yajuya yatafi, Adede lokacin Jabir daya Raka Aisha makaranta yashigo gidan, Hajja na ganinsa tace "yauwa Jabir meqamin niqan Aya Dan Allah" Kar6a yayi yajuya yatafi. Sai karfe shida saura su Aisha suka tashi daga islamiya, suna tafiya ahankali itada Walida, ta Dubi Walida tace "Walida Dan Allah kinsan inda zanga shugaban EFCC?" Walida ta zaro ido(😳)sannan tace''shugaban EFCC?" Kai tsaye Aisha tace"Eh, shifa" Cikin mamaki Walida ta kalleta tace "kinsan inda zakiga me kanfanin MTN?" Aisha tace "Ina tambyarki kema kina tambayata, Ina zanga me kamfanin mtn Walida?" Walida tace "to Alhamdulillah, Nima bansan inda Zakiga shugaban EFCC ba, nemansa abune me wahala,shiyasa nabaki misali dame kamfanin mtn, shugaban EFCC niko ganinsa ma bantaba yiba ko a photo,koke kintaba ganinsa?" Tace "bantaba ganinsa ba, sonake de na ganshi azahiri...." Kafin Walida tayi magana wata budurwa yar Gayu taqara so wajan su, daganinta kasan Gayu ya zauna, Kuma da alama ba'a qauyen take ba, budurwar ta kalli Aisha tace"qanwata Dan Allah a'ina kika siyo air lashes din idonki?" Daga ita har walida murmushi sukayi, walida tace"ba air lashes bane, haka gashin idonta yake" Murmushi budurwar tayi tareda yimusu godia ta wuce Haka sukaci gaba da tafiya har sukazo inda zasu rabu kowa yatafi gidansu, Aisha tana komawa gida taga Hajja tana Dama kunun Aya, Jakarta kawai ta ajiye ta zauna tana tayata aikin Sallama jummai tayi, Bayan sun gaisa suka sake yimata barka akan haihuwar jikarta, Hajja tace "Salaha Kuma ansauka, Allah sarki Allah yaraya, yaya yagar Tata Kuma?" Jummai tace "ai infada miki Hajja A'i an dinketa tsaf, tana nan a kwance de" Hajja tace "to Alhamdulillah Allah yaraya" Jummai tace "Amin,Hajja A'i nace zan samu sauran sigan kuwa?" (🤭) Mamaki yakama Aisha da Ummah, tun kafin tatafi makaranta taji Ana zancen sigan Nan, har yanzu kenan Qin siya tayi tana jira Hajja tasiyo na kunun Aya Sai tazo ta kar6a, harta bude baki zatace babu, Sai taji Hajja tace" Wallahi jummai babu sigan, duka najuyeshi acikin kunun aya saide a tsamo miki aciki "(😂) Jummai tace" innalillahi wa inna ilaihirraji'un....Inkaji Ana haka Kuma ai masifar takai masifa, tayaya za'a tsamo min siga acikin kunun Aya, nabar ki lafiya Hajja A'i" Daga Nan tatashi tayi gida, Hajja tace"inbanda masifa jikar ki ta haihu kikasa zare kudi ki mata abun Arziqi, me jummai zatai da kudi ne?" tajuya tana tambayar Ummah, Ummah tayi murmushi tace"Sai haquri Hajja A'i" LABARIN SU: Aisha da Aisha qawaye ne, Wanda sukai karatu tare,tundaga js one, har candy a makarantar goron dutse dake jihar kano Gaba d'ayansu Yan kano ne,Aysha Sulaiman Bompai, dakuma Aysha Yakubu Sagagi, sun shaqu mutuqar shaquwa, idan akazowa mutum daya visiting tare suke tafiya, haka dayar ma, babu Wanda yata6a jin kansu acikin makarantar, mutane dadama suna tunanin sudin yan'uwa ne, saide basuda wata alaqa illa qawance dakuma soyaiyar juna da Allah yasaka wa dukkaninsu, tun kafin suyi candy sukayi wa juna alqawari idan sukai aure daya ta haifi namiji, daya Kuma ta haifi mace to zasu hada yaransu aure, idan Kuma duka mata suka Haifa, zasu saka musu suna AISHA , ma'ana zasuci sunansu, idan Kuma kowacce namiji ta Haifa acikinsu, to zasu sakawa wadannan mazan suna MAHMUD, Alokacin dasuke wannan karatu ko uniform babu, atamfa suke sakawa a matsayin uniform, makaranta zata baki Riga da zani dakuma wani zanin spire, Sai suke yafa dayan zanin a matsayin mayafi, awanan lokacin babu waya, saide wasiqa idan kana buqatar tura saqo. Aisha da Aisha suna tsaka da wannan qawance nasu lokacin candy yazo, sukayi candy cikeda kewar juna, Bayan kowa yakoma gida Aysha Sulaiman Bompai dayake iyayenta sunada Hali, tasa direban gidansu yakaita unguwar Sagagi ta kaiwa qawarta Aysha Yakubu Sagagi ziyara,Bayan wahala dasuka Sha kafin su samu gidan, saboda babu waya, Aysha Yakubu Sagagi taji dadin ziyarar qawar Tata, sun dade suna zantukansu na yanmata inda anan ma suka sake jaddada alqawarinsu na makaranta, Bayan sunyi aure idan daya tahaifi mace, daya ta haifi namiji, zasu hadasu aure, idan mata suka Haifa zasu saka musu suna AISHA, idan maza suka Haifa zasu saka musu suna MAHMUD, da tunanin wannan alqawari Aysha Sulaiman Bompai tadawo gida, rabuwar dasukai kenan, har yau, har gobe, babu Wanda yasake saka dayansu acikin idon juna, tsawon shekara sittin da shida kenan kowa yana neman dan'uwansa, Amma babu wani labari Bayan ziyarar Aysha Sulaiman Bompai data kaiwa qawarta, Bayan wasu kwanaki aka maida mahaifin ta aiki Garin jigawa, Alokacin jigawa da kano ahad'e suke ba'a rababa, Aysha Yakubu Sagagi taji shiru tashirya taje ta nemi qawarta Aysha Sulaiman Bompai,saide tana zuwa mutanan unguwar suka sanar mata cewa ai sun saida gidan,sun koma Jigawa dazama,haka ta dinga zarya harta gaji. Ahankali rayuwa ta dinga juyawa, kwanaki suka koma Satuka, Satuka suka koma watanni, watanni suka koma shekaru, Aysha Yakubu Sagagi ta auri wani Dan Nijar me kudi Wanda yazo kasuwanci Garin kano Aysha Sulaiman Bompai kuwa agarin Jigawan Allah ya hadata da Miji tayi aure, ya aureta daga Garin Hadejia, yakaita wani qauye a dutse, mesuna Chamo, mahaifin ta Kuma daga baya yakoma kano da zama gaba daya, Bayan yayi retired, inda yasai wani gidan a unguwar yankaba Aysha Sulaiman, haka tayi hakurin rashin mahaifin ta, ta rungumi mijinta, suna Zaman su lafiya, har Allah yabata ciki, Bayan doguwar naquda tahaifi danta Namiji, babu 6ata lokaci kuwa ta fadawa mijinta cewa tanaso ya sakawa Yaron suna MAHMUD, Haka akayi kuwa Aka sakawa Yaron suna Mahmud, shine yafara kiranta da Hajja, daga baya Kuma sauran mutanan qauyen suke ce mata Hajja A'i, Bayan haihuwarsa bata sake haihuwa ba, har Mahmud yakai munzalin aure, ya samu mata Mai suna Hadiza, mafulatanar asali ya aura, Bayan aurensa da wata hudu, Allah yayiwa mijin Hajja rasuwa, anan taci gaba da Kula da Mahmud dinta, Wanda Yan qauyen suke kiransa da Mamuda, Mamuda bai dade da aure ba, matarsa Hadiza ta haifi 'ya mace Mai Kama da'ita sak kamar an tsaga kara,alokacin mamuda yace zaiyi wa Hajja takwara, Amma Hajja A'i wato Aysha Sulaiman bompai tayi tsalle ta dire tace wannan yarinya sunan qawarta Aysha za'a saka mata, shikuma Mamuda yadage sunanta zai sakawa yarsa, Amma ba sunan qawarta ba, haka Hajja ta dage tace inde sunan tane bata so, itade a sakawa yarinyar sunan qawarta wadda take burin su sake haduwa inda rabo, haka Mamuda ya sakawa yarsa suna Aisha, Bayan matarsa Hadiza ta tausheshi, tunda duka de sunan Nan iri dayane, saide ita Hajja har gobe tana fada bafa sunanta aka sakawa yarinya ba, sunan qawarta ne, wannan dalilin ne yasa take Kiran Jikar Tata da MESUNAN QAWA. wato me sunan qawarta Aysha Yakubu Sagagi, Bayan haihuwar Aisha da shekara daya da rabi, Allah yabawa Ummah ciki, ta haifi Jabir, tsiransa da Aisha baida yawa, daga Nan bata sake haihuwa ba, Aisha taja qaninta Jabir ajiki, sun shaqu sosai, tunda tayi candy bataci gaba da karatu ba, saboda babu Hali, saide bata fitar da ran zuwa gaba zatayi karatun koda a Dakin mijinta ne, Jabir yana candy Shima ya zauna baici gaba da karatun ba, hakan yasa Hajja A'i tafara sana'ar kunun Aya, tana Tara kudinta, saboda karatun Jabir dakuma auren MESUNAN QAWA. Suna Zaman su lafiya lafiya, saide wataran idan gigin tsufan Hajja yatashi, haka take tada hankalin kowa na gidan, mesunan qawarta ce kawai take taka mata birki azauna lafiya, Idan taso Kuma zakiga gidan kalau, idan Yan mulkin suka tashi kuwa Tofa Sai abunda tace. Aisha tana zuwa wata makarantar islamiya, Ana biyanta nera dubu biyu a wata, wannan dubu biyun haka tatara na wata hudu tasiyo akuya take kiwonta, tana so Sai Jabir yasamu Addmissoin zata siyar da'ita ta siya masa kayan provisions dashi, batada yawan magana, Amma idan tafadi wata maganar saikinyi mamaki, kyakykyawa ce ajin qarshe, tanada dogon gashi irinna fulani me kyau da tsantsi, bakinta Dan qarami ne me launin pink, tanada dogon gashin ido, Wanda mutane dayawa suke tunanin sakawa take banata bane, tanada innocent face, zata aikata ma laifi Amma idan tayi kalar tausayi Kai ba zakace itace ta aikata ba, a'ido zakayi tunanin saliha ce,saide idan aka ta6ota Tofa babu haquri, masifaffiya ce, wannan Kuma bamu Sani ba halin Hajja ne tad'auko, wato Aysha Sulaiman bompai, kokuma Halin takwararta ta Dauko wato Aysha Yakubu Sagagi? Saimun nutsa cikin labari zamu tantance(😃) Back to story Fan's ya Bayan kwana biyu? Ina fatan duk Wanda ya karanta wannan labari ya qayatar dashi SHAHAAB littafin kudi ne, nera 300 ne babu yawa,kullum zaku dinga samun update, zaku turo nera 300 ta wannan account number👇🏻 0164549488 Amina muhammad GTbank Zaku turo shedar biya ta wannan number 08033300034 Amnah El Yaqoub ✍🏻 [10/09, 22:14] +234 803 697 8511: 🌸SHAHAAB🌸 (Romance) Writing By Amnah El Yaqoub Dedicated to Aisha's Name Like my Page On Facebook👇🏻 https://www.facebook.com/amnahel 3&4 ABUJA mutane ne kusan guda biyar suke take masa baya, kowannensu yana Sanye da baqin glass a'idonsa,hakan bai Hana mutane rissinawa suna gaidashi ba. cikin sauri yake tafiya kunnan sa guda d'aya manne da Bluetooth, daga yanda yake tafiya kadai zaisa kagane cewa matashi ne Mai jini ajika, ko kadan bayajin nauyin jikinsa, Sanye yake cikin suit launin ash, saide yacire jacket din Saman ya riqeta ahannunsa, hakan ne yabawa murdaddan dantsan hannun sa damar futowa, faffad'an qirjinsa yasamu yabaje yanda ya kamata acikin rigar, hannunsa daya, yana Sanye cikin aljihun wandon sa, fuskarsa a daure take, babu alamun fara'a kokadan, Amma hakan baisa kyawun fuskarsa damar bayyana ba, magana yake cikin aji, Amma dimple dinsa futowa suke duk da ba dariya yake ba, yanada hasken Fata yanda ya kamata, mutanen dake take masa baya basu barshi ba, saida suka kusan kaishi har gaban office dinsa, daga Nan ya daga musu hannu kawai batare Dayayi magana ba, yana shiga cikin office din Adede lokacin ne yake cewa "duk kayaiyayin mu dasuke kasuwa asake saukar musu da farashi yanda talakawa zasu iya siya, banaso sukai lokacin azumi" yana gama fadar haka yasaka Dan yatsansa ya danna agogon dake daure a tsintsiyar hannunsa touch, Nan da Nan wayar ta katse Wasu file yaduba, ko ten minutes baiyi ba, yad'auki wata takarda, yatashi yasaka suite dinsa,I'd card dinsa ya saqala agaban suite din nasa setin qirjinsa,anrubuta MAHMUD WAKILI, EFCC CHIRMAN. Kai tsaye d'akin da zasuyi taro yanufa, dogon daki ne Wanda yaji kujeru masu mutuwar kyau tareda dogon table, an ajiyewa kowa gorar ruwa a gabansa, fuskar kowa d'aukeda face maks, office din yayi kyau sosai, gaba dayansu maza ne, Sai mata guda biyu, suna ganin shigowarsa cikeda ladabi suka miqe tsaye, saida ya zauna akan kujerar sa wadda take d'aukeda tambarin hukumar, dakuma manyan rubutu Wanda aka rubuta EFCC ajiki, sannan kowa ya zauna. daga Bayan kujerar daya zauna sojoji ne guda biyu sun qame waje daya, Sai babbar tutar tambarin hukumar EFCC, dakuma wata babbar tuta ta qasar Nigeria, daga can sama Kuma Babban photonsa ne yayi kyau cikin suit yana murmushi, dakuma wani photon daban na shugaban qasa. Basu bata lokaci ba suka fara tattaunawa akan abunda ya tarasu, zasu fitar da wani salon na yaqi dacin hanci da rashawa a Nigeria. Saikuma maganar sunayen wadanda hukumar ta d'auka,a matsayin Wanda zasu bawa horo, zasu fitar da sunayen su zuwa wani watan ta manhajar hukumar, dakuma kafafen yad'a labarai. Basu dauki lokaci Mai tsawoba suka tashi daga meeting din, daga Nan office dinsa yakoma yafara ganin mutane kowa da irin maganar dayake zuwa da'ita Sai yamma yayi shirin tafiya gida, yana futowa kuwa mutanan nasa suka take masa baya har zuwa mota, mutum dayane yabude masa mota yashiga, Alokacin har anfara yayyafi kasancewar kudancin qasar sunfi arewacin Nigeria saurin samun ruwan sama, yana shiga motar ya Lumshe Idonsa, ga qamshin ruwan sama me dadi yana busowa cikin motar, yagaji sosai, zaiso ace yasamu anyi masa massage Ayanzu (🤭) Tafiya Mai Nisa sukayi, kafin su qarasa gida, Alokacin har ruwan yafara qarfi, sojoji ne awajan gidan, dakuma daidai kun Yan sanda, get man nabude musu get, driver ya danna hancin motar zuwa cikin gidan, gida ne babba gari guda, ba zakayi tunanin ma acikin qasar Nan gidan yake ba, acikin harabar gidan ma sojoji ne suke shawagi, motarsa tana tsayawa daga me gadi har sojojin wajansa suka nufa kowa yanayi masa sannu da zuwa, hannunsa yadaga musu kawai,kasancewar Ana Dan ruwa yasa yayi sauri Kai tsaye yawuce part din MAMA. Yana shigowa falon yafara cire jacket dinsa, tareda necktie din wuyansa, duk da girman falon Nata, wani kafet ne Mai masifar laushi yake malale a falon, ga wata katuwar plasma tana aiki, daga fentin falon har kujerun da labulaye duka milk colour ne, wata tsohuwa ce mai kimanin shekaru sittin da shida a zaune, saikuma wata yarinya a tsugunne a gabanta, tana matsa mata qafafu Cikin fad'a-fad'a tadubi yarinyar "ke! Kidena matsa min qafa da qarfi mana kamar kinsamu wani dutsi, nagaji dayin complain a kanki, Nan gaba kad'an zan'iya sallamar ki idan baki gyara halinki ba" Cikin ladabi tace "kiyi hakuri Hajiya" Cikin muryarsa Mai cikeda miskilanci yace "mama" Kallan sa tayi tace "SHAHAAB kadawo?" Bai bata amsa ba saida ya zauna yana fadin "wash! Allah na mama nagaji" Yarinyar datake matsawa wadda aka kira da mama qafafu, cikin tsantsar ladabi kanta asunkuye, batare data hada ido dashi ba tace "yalla6ai barka da dawowa" Bece da'ita uffan ba, Sai mama ce data watsa mata wani irin kallo tace "saiki tashi kije, zan gana da Dana" Cikin sauri yarinyar tatashi tabar wajan har qafafunta na hardewa Kallan sa tayi tace "Shahaab ya aikin? Kadawo lafiya?" Kafin yabata amsa agogon hannunsa ya nuna alamun Ana kiransa, ta6a agogon yayi ya amsa Kiran dake shigowa, daga dayan bangaren muryar wani mutum ne yake tashi "ranka yadade kanada baqi daga bayelsa" Dafe Kansa yayi, kwata kwata ya manta da Zuwansu, ahankali ya kalli mama, shide yasan be'isa yasake fita yanzu ba, cikin muryarsa Mai dadi yace "kafada musu muhadu dasu gobe misalin karfe goma nasafe" daga Nan yakashe wayar, ya maida dubansa zuwaga mama Hankalin tane taji ya kwanta Bayan taji bazai sake fitaba, taqi jinin ta ganshi nesa da'ita Tafison kullum ta kasance tareda dannata qwaya daya tal a duniya, batason yawan rashin zamansa agida ko kad'an, cikin kulawa yace "waye yata6aki mama? Keda waye?" Ajiyar zuciya ta sauke tace "ai kasan damuwa ta, rashin dawowarka ne gida dawuri, saikuma batun qawata Aysha Sulaiman bompai, dakamin alqwari zaka nemomin ita" Kansa ya sunkuyar qasa, wannan qawa ta mama! Wannan qawa ta mama!! Da yanada halin dazai mantar da'ita wannan qawar Tata datuni yayi, saboda babu Wanda yasani tana Raye har yanzu kokuma ta mutu, ahankali ya d'ago Kansa ya kalleta, yakama hannayenta yariqe yace "za'a duba agani" Shiru mama tayi tana Kallan sa, tarasa meyasa Shahab baison maganar qawarta, tun lokacin data fada masa inde taga qawarta Aysha to zata hadashi aure da 'yarta idan mace ta Haifa, tun daga lokacin yaqi jinin tayi masa maganar qawar Tata, saboda bashida ra'ayin yin wani aure yanzu, idan ba bayason Nemo mata qawar Tata ba yaushe zata yi masa maganar amma yace Wai za'a duba, hakan yana nufin Bama shine zai dubaba kenan, ko meyasa yake gudun yin wani auren? Kokuma baida cikakkiyar lafiya irinta maza oho masa, rashin haihuwar sa yana damunta, ga Kuma rashin qawarta wadda take Fata, take Kuma burin tahadu da'ita kafin Takoma ga mahaliccinta, wadannan burikan Nata guda biyu su take Fata su kasance, yau ace taga jinin Shahaab, sannan Kuma taga qawarta Aysha Sulaiman Ajiyar zuciya ta sauke tace "Yaya labarin Munirat? Har yanzu haihuwa shiru babu ciki bare ayi tunanin labarin haihuwa ko?" "Ana Addu'ah de" Shine abinda yafada mata Kallan sa tayi dakyau Kai tsaye tace "inaso kafin namutu, Inga qawata Aysha, sannan Kuma Inga yayanka, Qawata Aysha de Ina Nan Ina nemanta, Kuma nasan insha Allah watarana zan ganta, Amma Kai haihuwa bakada tabbas,matarka ba haihuwa zatayi ba, yakamata kayiwa kanka fada, saboda haka yaushe zaka sake aure? " Gabansa ne yafadi,cikin sauri ya d'ago Kansa ya kalleta, Dan qaramin bakinsa ya bude kamar Mai shirin cewa wani abu, Amma Kuma yakasa magana, ganin yazuba mata ido yana Kallan ta yasa taci gaba da fadin "yakamata kabi shawara ta, ka 6oye kanka kanemi aure, kafuto a matsayin SHAHAAB kanemi aure da soyaiyar tsakani da Allah bata kudi ba, muddin kace zakaje wajan yanmata a matsayin MAHMUD WAKILI,to bazaka ta6a samun soyaiyar gaskiya ba" Tamkar Wanda zai Fashe da Kuka yace "mama itama Munirat din tana sona, nida ita ai sai Allah mama" Batace dashi komai ba saboda taqaici kawai wayarta ta d'auka dake Gefe, tawuce dakinta tabarshi anan, hakan yana nufin shiru ma amsa ce game Hankali. Yana ganin shigewarta daki yaji kamar ya kurma ihu kozaiji dadi, tayaya mama zatace yayi aure Bayan irin dunbin soyaiyar Da Munirat take nuna masa? Jikinsa a sanyaye yamiqe yanufi part dinsu, duk ruwan dayake sauka akansa ko kad'an baya jinsa, yasan cewa idan yabi Bayan mama ma to bazata saurare Shiba, yana zuwa falon ya hangota gaban TV da remote a hannunta, Riga da siket ne ajikinta dinkin ya zauna Das ajikinta,munirat chocolate beauty ce, Amma hutu, dakuma jin dadin datake samu, da shafa mayuka masu mutuqar tsada yasa gaba daya bazaka ce mata chocolate ba, fatarta tayi wani irin luwai luwai kamar ka latsa jini yafuto, mace ce har mace, Mai aji dakuma wadatar ilmin boko,Daurin ture kaga tsiya tayi, hakan yabawa gashin dokin data saka damar futowa sosai Kai kace halalinta ne, falon bashida wani tarkace, kujerun falon Kala biyu ne, akwai yellow, dakuma ash colour, Sai aka hadasu akayiwa falon qawanya dasu Tsayawa yayi yana qare mata kallo, haqiqa yana qaunar munirat, Kuma itama ya tabbatar tana mutuqar sonsa, babu abinda ta rageshi dashi, sannan tana mutuqar qoqarinta wajan ganin ta kyautata wa mama, Amma mama bata Gani Jin alamun kamar Ana kallon ta ne yasa tajuya, tana ganinsa tatafi dawani irin taku me daukar hankali, ta qarasa wajan sa "barka da zuwa my Dear" Cikin damuwa ya Lumshe Idonsa ya bude, alamun amsawa, murdaddan dantsan hannunsa ta kama tace "muje kayi wanka, meyake damunka ne Naga kamar kana cikin damuwa, gashi katsaya ruwa ya ta6amin kai" Ta qarasa maganar tana janshi ciki, ahankali ya janye jikinsa yace "kije kiyi kallonki, yaude na hutar dake, idan nagama zan futo" Murmushi tasaki, ta rungume shi tasakar masa kiss a kumatu, sannan tasake shi tajuya, saqon Nata yashige shi sosai, har saida hakan yasa shi Lumshe Idonsa, batare daya shirya ba Washegari da safe bai tashi dawuri ba, sakamakon gajiyar da yayi cikin dare,tun kafin yatashi daga baccin munirat ta silale tatafi part din mama,yau tana so tayi wa mijin ta girki Wanda zaisa yaji dadi sosai kamar yanda yajiyar da'ita dadi adaren yau, ma'aikatan part din ta had'a gaba d'ayansu tasakasu su girka mata irin abunda takeso, cikin qanqanin lokaci suka kammala komai suka jereshi a Babban dinning din na mama, Wanda aqalla zai dauki mutane samada mutum takwas Har zuwa lokacin Hajiya Mama Ana daki bata futo ba, munirat kuwa zama tayi akan kujera ta sallami masu aikin, wayarta ta d'auka tana chatting da qawayenta, dayawansu tallar magungunan mata suke mata, Wanda ita kanta batasan Dame aka hadasu ba "menake Gani haka?!!!" Mama data futo daga daki tafada, Bayan taga abinda aka ajiye a dinning, ta qarasa maganar idonta nakan munirat, fuskarta kuwa shimfide take da 6acin rai Cikin sauri munirat ta kalleta, gabanta yafadi, da sauri ta sakko daga kan kujerarar ta tsugunna har wayar hannunta na faduwa, cikin ladabi da rawar murya tace "Barka da futowa mama, Ina kwana?" "daban kwana ba kya ganni? Munirat yaushe Ina cikin gidannan har Zaki shigo min part dina kina bada umarni? Kinyi hauka ne?" Adede lokacin yashigo part din, yashirya cikin suit kamar kowacce rana Munirat da idonta yakawo ruwa, qwalla tataru tacika idon, ta girgiza kanta batare da tayi magana ba Nunata mama tayi da d'an yatsa, tace"maza maza tashi kije tas ki cinye abinda kikasa aka girka, tun kafin ranki Dana iyayenki ya6aci.... " Cikin sauri ya qaraso falon, cikin ladabi yace"mama kiyi hakuri Dan Allah" Kallan sa tayi tace "Alhamdulillah... Gara da Allah yakawo ka" Ta nuna masa munirat da hawaye ya wanke mata fuska tace "tun kafin namutu matarka ce mebada umarni...., to gatanan kasaketa" Jiyayi kamar mama ta doka masa guduma a qirjinsa, munirat kuwa tanajin wannan furucin, tafice daga falon da gudu tana kuka. LABARINSU: Hajiya Mama, sunanta Aysha Yakubu Sagagi, tun Bayan rabuwar su da qawarta Aysha Sulaiman bompai Sai iyayenta suka rasu, daga Nan mijinta ya dauke ta suka tafi Nijar wajan dangin sa, sun dade acan yana kasuwancin sa, daga Nan suka sake dawowa Nigeria, ahankali ahankali har Allah yasa Arziqinsa yasake ha6aka, Bai Barta tayi maraicin iyayenta ba, janta yayi ajiki, ya dinga Koya mata harkokin kasuwancin sa, ahankali harta gane komai, lokaci zuwa lokaci yana tura ta wasu qasashen sarin kayaiyaki, har Allah yasa Shima yabude kamfanoni dadama, anan Nigeria da Kuma Nijar inda danginsa suke Lokaci daya, sunansa yafuto acikin jerin sunayen masu kudin qasar Dama Africa baki daya, akwai wata Rana daya shirya zaije yataho da danginsa na Nijar, su dawo Abuja da zama gaba daya, yaje yataho dasu a hanyar su ta dawowa jirginsu yayi hatsari suka mutu gaba dayansu. Mama tayi kuka tayi kuka kamar ranta zai fita, har kwantar da ita akayi a Asbiti, anan ne aka Gano tana d'aukeda ciki na wata uku, haka taci gaba da Kula da cikinta,tasamu mutane amintattu suka tayata kula da dukiyar mijin Nata,kamfanin sa dasuke Nijar tasa akai gwanjon su,Alokacin da cikinta yakusa haihuwa saita shirya tatafi Saudia,acan ta haifi danta namiji kyakykyawa Mai Kama da mahaifinsa sak, ranar suna taso sakawa Yaron sunan mahaifinsa, to Amma data tuna alqawarinsu itada qawarta Aysha Sulaiman bompai, saita sakawa Yaron suna MAHMUD, mutane suke kiransa da MAHMUD WAKILI, ita kadaice bata fadar sunansa, saboda Dan fari ne, Sai take masa alkunya take kiransa da SHAHAAB. A India yayi degree dinsa na farko, ya karanci bangaren medicine Haka mama ta hanashi aikin asbiti duk da yanaso, ta dorashi akan harkokin mahaifinsa, kasancewar yanada hazaqa hakan yasa Nan da Nan yasan kan harkar, dukiyar Kuma tasake ha6aka,daga baya Kuma yatafi malesia yayi karatu akan harkar kasuwanci, hakanne yasake bashi damar gogewa akan harkar kasuwancin nasu,sannan ya dawo Nigeria yayi wani karatun afannin economic, daga Nan yafara aiki da hukumar efcc, yafara da matakin karamin ma'aikaci, har Allah yasa sukaga kokarin sa akan aiki dakuma jajir cewarsa,shugaban qasa ya nad'ashi shugaban hukumar, baya had'a kasuwancin su da aikinsa, aikinsa daban, harkar kula da dukiyar da mahaifinsa yabar masa Shima dabam, Kuma yana kula da hakan yana taka tsantsan akan duk wani abu dazai hada aikinsa dakuma kasuwancin sa, yana samun wannan matsayi yahadu da munirat, tanada samarinta sosai, Wanda suka sota tun tana qarama, suka Sha wahala Akanta, suka hidimta mata, Amma tana ganin Shahaab yafuto a matsayin jerin masu neman aurenta saita liqe masa, harma soyaiyar datake masa ta danne tashi soyaiyar, ta Kuma zabeshi a matsayin Wanda zata aura, acewarta yafi sauran samarin Nata nagarta. Mama bataso yanemi yarinyar ba,taso ace yasamu yarinya da batasan waye Shiba, batasan kudinsa ba, itace zatayi masa soyaiyar gaskiya, Amma tana ganin idon munirat tasan cewa idon yarinyar abude yake akan son kudi, ta fahimtar dashi Amma soyaiyar munirat din data Gani acikin Idonsa yasa tarabu dashi ya aureta, abokan mahaifinsa suka shige masa gaba, Nan da Nan aka bashi ita, kasancewar sa Babban mutum Kuma sananne a qasar. shekarar su Tara kenan da aure, haka Kuma a tarihin aikin nasu shine matashi na farko daya dade a matsayin shugaban hukumar, ba'a dade da dorashi ba ya auri munirat,a dadin shekarun sa a matsayin shugaba, a dadin shekarun aurensa, gaba daya shekarun sa 39, yayi aure yanada shekara talatin a duniya, Amma babu Wanda zaice yayi wannan shekarun kasancewar yanda yake motsa jiki, yake Kuma kula da jikin nasa, yasan cewa da yana candy yayi aure to tabbas da yanzu yarinyar sa kokuma yaronsa zaikai shekara Ashirin kokuma shatara,to Amma gashi har yanzu shiru babu haihuwa, Kuma yaga munirat abun baya damunta, shikuma yanason yaga yanada yaronda zai gajeshi koda ace baya Raye, kamar yanda Shima yagaji mahaifinsa. Shahaab bai iya soyaiya ba, idan yanason mutum Tofa yana sonsa, da gaske yake saka mutum acikin zuciyar sa, shiyasa munirat tayi Kane Kane acikin tasa zuciyar, yanason mace Mai gashi, asali ma shine abinda yagani awajan munirat haryaja ra'ayin sa akanta, Bayan sunyi aure yagane gashin dokine take sakawa, maimakon ya hanata saiya qyale ta taci gaba da sakawa saboda Shima yanaso. Bangaren munirat Kam Bahaka bane, rashin haihuwarsu baya damunta, kullum qawaye take biyewa suna kawo mata magungunan mata Kala Kala, dayawa daga cikin su batasan Dame aka hada akayi suba, kudi Kuma duk lokacin data so samu tana samu awajan mijinta, wani lokacin saita tsokano masa sha'awar sa cikin kissa zata Fashe da Kuka, yana tambaya abinda take wa kuka zata fada masa kudi takeso Kuma gashi account dinta yayi qasa, shikuma jinsa cikin wannan yanayin yasa zai bata kudade, Sannna ne zata bashi hadin Kai su Raya Sunnah yanda ya kamata Shahaab yana yiwa mama biyaiya, tun tasowarsa yana qarami ita yake Gani, itace take masa komai,baisan mahaifinsa ba, mama itace komai nasa, tana sadaukar da Nata farincikin akan nasa, yana kiyaye duk wani abu dazai sata 6acin rai, yasan cewa Sarai batason munirat, akwai lokacin daya tambayeta meyasa batason munirat Kai tsaye tafuto tafada masa cewa matarsa kudinsa tagani shiyasa ta aure shi, sannan akwai alqawarin dasukai itada qawarta cewa zasu hada yayansu aure, Kuma yasani muddin Aysha ta bayyana Tofa saiya auri yarta inde mace ta Haifa, idan Kuma ba mace ta Haifa ba shikkenan. Tun daga lokacin idan tasashi yayi wani kokari akai Dan agano qawarta, Sai yayi mursisi da batun, saboda bayason maganar hadin auren Nan datake yi kokadan. Akwai lokacin data dameshi akan maganar, Amma Shahaab yaqi yayi mata binciken, tayi zuciya tafice tabar gidan a hanya kidnappers suka saceta (😂) Saida yasha wahala kasancewar sa sannane yasa hukumar tsaro ta qasar tabashi hadin Kai har saida aka kamota daga hannunsu, tundaga lokacin ya zubawa gidansa tsaro, sojoji ne suke gadin mama, banda Yan sanda dasuke Gefe suma suna nasu aikin. To dayaga de mama da gaske take, shine yabada sanarwa a kafafen sadarwa dakuma yanar gizo, ganin yanzu harkar yanar gizo kowa yanayin ta, shiyasa yayi tunanin za'a iya samun labarin qawar ta mama, abinda bai saniba shine Hajja A'i Kam vivo gareta itama screen din duk ya Fashe, wannan gidan ta abincin dazasuci sukeyi, bata yanar gizo ba(☹️) To ganin haka yasa hankalin mama ya kwanta, Amma idan ta tuna qawarta, ranar haukace masa take, tun yana bata haquri harya dawo Shima yazama kamar ta, ya dinga zigata, to saita sauko su zauna lafiya. Tsawon wannan shekarun munirat ko 6atan wata bata taba yiba, data fahimci hankalin mama dakuma shi Kansa Shahaab din yana kan haihuwa, saita shiga damuwa, akan yanda suke nuna son haihuwar, danhaka Sai take jinyar qarya, dasu amai, mama da Shahaab hankalin su yatashi, suce taje Asbiti taga likita ko ciki ne, saita kar6i maqudan kudade awajansa daga baya Sai tace ai ba ciki bane, tayi haka yakai sau uku, mama kuwa tariga tagane kawai kudin yarinyar takeso, bawai Shahaab din ne da haihuwar suka Dame taba Tarasa Yaya zatayi, aure tsawon shekara Tara babu ciki, but ita hakan bai dameta ba saboda tana cikin daula, ko neman magani batayi, shikuma duk lokacin daya shirya yatafi Saudia Tofa addu'arsa daya ce akan Allah yabashi haihuwa, ita kuwa mama burinta guda biyu ne, nafarko taga qawarta, na biyu Kuma taga Shahaab ya haihu. Duk juma'ah Ana bada abincin sadaka a gidan, kunu, abinci, dakuma bread tareda nera Dari biyar, wannan Kuma aikin mama ne, tana bada sadakar ne saboda Allah yakaiwa mijinta dakuma ahlinsa ladan. Ta bangaren Shahaab kuwa lokaci zuwa lokaci yana yin tasa sadakar, Amma yafiyi lokacin zuwan azumi, yana sauke farashin kayan da kamfanonin sa suke sarrafawa domin talakawa su iya siya. Back to story 👌🏻 ****** Jigawa Aisha ce take sallah, Hajja na gefenta tana Jan carbi, ta kalleta tace "mesunan qawa kiji tsoron Allah, wannan ba sallah kikeba, sallah batafi minti goma ba an idar" Aisha batace mata komai ba, Sai abincin ta data Dauko tafara ci,batare data cire hijabin jikintaba, qwaine guda daya akan abincin Nata Wanda qawarta Walida tabata, Hajja taleqa kwanon abincin Aishan tace "Menene wannan nake Gani aciki?" Cikin gatse tace "gishiri" Hajja tata6e baki, Sannna taja bakinta tayi shiru tana kallon yanda gumi yake jiqa mata fuska, har gashin gaban goshin ta ya kwanta yayi luf-luf dashi, Amma Dan masifa Taki tacire hijabin jikin Nata, bacci ma wani lokacin da hijabi takeyi, tarasa Ina mesunan qawa tad'auki wannan dabi'ah Wani yaro ne yayi sallama yashigo gidan yace "Hajja A'i abani kunun Aya na nera Dari" Tace "idan Sadiya ce ta aikoka kakoma kace mata akwai kudin rannan ma" Yaron yajuya yatafi, baifi minti biyar ba Sai gashi ya dawo, yace "Wai tace babu,bakya Binta bashi" "au haka tace?, to shikkenan taje na rataya awuyanta, kawo Darin abaka" Kudin yabata, Aisha tamiqe ta bude Dan qaramin fridge din Hajja tabashi kunun ayar, yatafi Jabir ne yashigo gidan, Bai nufi wajan Ummah ba Kai tsaye rumfar dasu Hajja suke zaune yaje, ya kalleta yace "Hajja Dan Allah kisiyar min da wayar ki dubu uku" Tace "kawo dubu biyar de saina baka" Dariya yayi yace "wayarda batafi dubu uku ba?" "aikuwa bazan siyar ba saide dubu biyar" Aisha ta Kalle su tace "kawai kabata dubu ukun in taga Dama ta kar6a kokuma tabarshi" Hajja ta yatsina fuska tace "yo Ina yaga dubu ukun ma?" "Arziqi Aina Allah ne, Shima wataran zaiyi" Hajja najin wannan furucin na Aisha saita Fashe da Kuka, da gudu umma tafuto daga daki tana tambaya "Hajja meyafaru kike kuka? Keda waye?" Cikin kuka tace "nida mesunan qawa ne, nariga nadade da sanin me sunan qawa d'auka ta take a matsayin sa'arta, tunda taga ta girma tafara nono shikkenan ban'isa inyi magana ba acikin gidannan, saide in fad'a itama tafad'a,inda ace nasan haka halin yarinyar Nan yake tun farko daban Bari ansaka mata sunan qawata ba, saboda Bahaka halin qawata yake ba, saide in uwarta ce take Koya mata rashin kunya"(😂) Ummah tanajin haka tafara hawaye, duk lokacin da fadan Aisha da Hajja zai tashi, to akanta take hucewa, Kuma ita bata Isa tahana Aisha zuwa wajan Hajja ba, Kota hanata ma Sai taje, Kuma ko tayi zuciya taqi zuwa inda Hajja take to Hajjan da kanta take zuwa sutafi Ganin Ummah na kuka Sai hankalin Aisha yatashi, menene laifin Ummah anan daza'a ce itace take Koya mata rashin kunya, cikin 6acin rai ta kalli Hajja sannan tace "niba abinda Ummah ta take koyamin, gaba daya halin me sunana nabiyo, haka kawai antashi ansaka min sunan matarda banma santaba, qila ma tamutu" (🙆🏻‍♀️) Abbansu ne yashigo gidan dawowarsa kenan daga rumfarsu inda yake aikin facin tayar mota Kota machine, kukan Hajja ne yaqaru, cikin kuka ta kalli Aisha tace "ta Allah ba Taki ba, insha Allahu qawata tana nan da ranta, Kuma tana bayyana zan tattara kayana intafi inbar miki gidan ubanki" Abba ne ya kalli Aisha yace "ke rufemin baki anan, marar kunya kawai" Sannan ya kalli Hajja yace "Hajja Dan Allah kiyi hakuri Kidena kukan Nan, mesunan qawarki batada Hankali yarinya ce Kidena biye mata Kuna sa'insa Dan Allah" Jan zuciya tayi tace "ai tashen balaga takeji,Kuma wallahi Mamuda bazan haqura ba saika Nemo min qawata kokuma kaje ka siyomin ruwan Roba" Jabir da dariya ta kamashi saiya silale yabar gidan, Abba kuwa shiru yayi yana tunani, toshi yanzu Ina zaije neman wannan qawar ta Hajja? Shida ba aljani ba tayaya zai dinga yawo gari gari yana neman Aysha Yakubu sagagi, toma Aysha Yakubu nawane a Nigeria?🤔 Har gara ruwan ma, danhaka ya kalleta yace "kiyi hakuri to, zan siyo miki ruwan, wanne iri kike so?" Babu kunya tace "Faro" (🤣) Yace "to kiyi hakuri yanzu zanje nasiyo miki" daga Nan yajuya yafita daga gidan, itama ta dakawa Aisha Harara, Sannna tashige cikin dakinta. SHAHAAB littafin kudi ne, Naira 300 kacal babu yawa,kibiya kafin free page su qare, zaki turo 300 ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Zaki turomin shedar biya ta Number ta 08033300034 🌸SHAHAAB🌸 (Romance) Writing By Amnah El Yaqoub Dedicated to Aisha's Name Like my Page On Facebook 👇🏻 https://www.facebook.com/amnahel 5&6 Baifi minti talatin ba ya dawo hannunsa d'aukeda baqar leda, yana zuwa yawuce Dakin Hajja yakai mata ruwan, budewa tayi taga faro ne guda biyu, tasaka hannu ta bude dayan tafara Sha, Sai da yaga fishin dake kan fuskarta yadan Kauce, sannan yatashi yafuto daga d'akin. Aisha yasake yiwa fada sannan yashige dakinsa ****** ABUJA Atamfofi ne a gabanta da shaddodi masu shegen kyau, d'ad'd'agasu takeyi tana magana cikin Isa "kayan sunyi kyau, Kuma sun kawo min su daidai kamar yanda nayi oder" Ta kalli daya daga cikin ma'aikatanta tace "jeki kiramin munirat" Cikin ladabi ta amsa sannan tajuya, Bayan wasu mintuna tadawo tace "Hajiya tace gatanan zuwa" Jijjiga kanta tayi cikin ranta tana fadin lalle munirat ta'isa,intura aikiranta Amma saboda ta nunamin ita yar zamani ce batazata biyo yarinyar sutaho tare ba, saita nunamin itama tanada iko saboda tana auren Shahaab Saida aka dauki kusan minti talatin sannan taqara so part din na mama,aqasan kafet din ta zauna tareda fadin "Gani mama" Saida takusa minti goma, ta tabbatar ta6ata mata lokaci kamar yanda Itama tayimata, sannan tatura mata kayan tace "ga kayanki Nan, kidauki kikai wajan dinki" Cikin ladabi ta d'auka tareda yimata godia, Sannna Takoma part dinta Tana zuwa dakinta ta zubar da kayan tafada kan gadonta tareda fashewa da Kuka, ita kenan suturar dazata saka ma batada ikon dazata siyo da kanta taza6i irin Wanda take so saide sirika tasiyo takawo mata? Yaya zatayi da wannan tsohuwar ne? Bata Rasa komai a gidan mijinta ba, wannan matar ita kad'ai ce ta tsaye mata, tarasa Yaya zatayi da'ita, wayarta ta janyo takira qawarta Mery, saide jin wayar Tata akashe yasa takira mamanta, cikin kuka ta zayyane mata komai, daga qarshe mahaifiyar Tata shawara tabata akan hanyoyin dazata dinga samun kudi ta hannun Shahaab, saita dinga siyar kalar kayan Dayayi mata, jin wannan shawarar ne yad'an sanyaya mata ranta. ****** Zaune yake a Babban office din companyn sa na takalma dake lagos, Sai wasu mutane guda biyar dasuke fuskantar sa, cup din tea ne a gabansa Sai turiri yake da alama yanzu aka had'ashi Wata takarda ce agaban su Mai d'aukeda zanen taswira ta wani qaune dake jihar oyo, daya daga cikin su ne yake tsaye, gaban wata babbar TV dake manne abangon office din, yana Sanye cikin suit kamar yanda gaba dayansu itace Sanye ajikinsu, saide Shahaab yacire jacket dinsa yasakata a jikin kujerar dayake zaune, yad'ora Kansa a jikin kujerar ya kishingida kujerar Sai juyawa dashi take, Hankalinsa gaba daya yana kan matashin dake yin bayanin wajan daki-daki, wani ruwa matashin ya nuna yace "kwata kwata bangaren da zamu Gina company bashida ruwa, Amma a opposite dinsa akwai ruwa sosai Wanda yake wucewa, saide akwai titi a tsakani, sannan kamar yanda muka tattauna da gwamnan jihar, yabamu tabbacin cewa inde zamu ninkawa masu gonakin wajan kudin gonarsu to zasu siyar mana da gonakin, saboda Nan ne yafi da cewa da Gina company shinkafa, dazaran mungama zamu yi gada, wadda motocin zasu dinga bi ta wannan kan gadar, mukuma saimuja ruwan ta qarqashin gadar, wannan shine zanan wajan dakuma yanda yake, ga Kuma yanda tsarin ginin company zai kasance Bayan an kammala ginawa " Ajiyar zuciya Shahaab yasaki, yace" duk Wanda zamu sayi gonarsu dake wannan dajin, ba ninki biyu na kudin gonarsu zamu basu ba, zamu basu ninki uku insha Allah " Tafi sauran mutanan sukayi, saikuma daya daga cikin su yace"amma akwai yar qaramar matsala fa oga, nafarko daji muka yanka zamu fara wannan aiki, Amma munyi bincike mungano ginin yayi daji dayawa, yakamata ace wajen ya kasance na jama'ah dayawa ta yanda muma zamu amfanesu, suma Kuma su amfane mu, hakan zaisa kamfanin mu yazama kamar wata kasuwa ce ta daban da kowa zaiyi burin zuwa wajan, duk Wanda yazo wajan, dole zaiso jin farashin shinkafar mu, daga Nan mukuma zamuyi kokarin janyo shi jikin mu harya zama Babban customer awajan mu " Kallan su Shahaab yayi yace" why not mu qirqiri gari awajan?" Wani ne daban yace"tayaya?" Shahaab yace" tunda wajan daji ne, saimu qirqiri gidaje,kamar guda Dari biyu, daidai Zaman mutum daya zuwa biyu, Sai mu rabawa mutane mabuqata, Wanda muka tabbatar basuda gidan kansu saina haya, kaga saisu dawo Nan suci gaba da rayuwar su" Nan da Nan sukayi na'am da shawarar tasa. Sign yayi akan takardar dazasu bada kwangilar aikin gidajen, saboda yanaso aikin ya kammala cikin Dan qanqanin lokaci, ba kowa yake son mallaka wa kamfanin ba face munirat, yasan cewa zatayi farinciki sosai, bayason ita kanta tasan da aikin, saide kawai ya gabatar da'ita a matsayin mamallakiyar kamfanin. ****** Da azahar suna zaune atsakar gida cikin yar qaramar rumfarsu, Almajiri ne yayi sallama gidan, yakawo mata jarkokin da aka siya kunun Aya a kofar gida tace"dan malam koma kasake dubamin akwai wasu jarkokin,ba dukane ba" Almajiri yace "babu jarka Sai guda daya,Kuma Haladu me p.o.s ne yaturata cikin shagonsa yatafi masallaci" Cikin jin haushi tace "ai shikkenan, qyaleshi, Sai yaje ya kaiwa uwarsa ta dinga d'ura kalanzir aciki, dama sana'ar tace" (😂) Ummah da Abba sukai murmushi, sude basu Tanka mata ba, suna tsoron tahuce akansu Tashi tayi tashiga Dan qaramin kitchen dinsu na ginin qasa, tafara zuba abinci, Wanda Aisha tagama girkawa yanzu, Alokacin itama Aishan tazo zata sakawa Abba nasa abincin acikin kula, Hajja ta kalleta tace "yanaga kinata raragefe, zoki dauki abinda Zaki dauka mana, keda gidan ubanki?" Ganin Abba yana Nan yasa Aisha bata ce mata komai ba, kawai ajiye kular tayi, Takoma Dakin Ummah tayi Zaman ta Ko minti uku batayi ba saiga Hajja tabiyo ta Dakin, hannunta dauke da ruwan faro Wanda Abba yasiyo mata jiya, Tasha daya, dayan Kuma tabar wa mesunan qawa😂 Bata tayi tace "ga ruwanki na jiya, na jira kizo kwana da daddare naji shiru bakizo ba, shine na ajiye miki" Kar6ar ruwan tayi tana cika tana batsewa, Hajja tata6e baki tace "yar Albarka me sunan qawa, ga niqan Aya ta can zoki tacemin ita, sonake na durashi a jarka yanzun Nan" Murya can ciki tace "to" Hajja tafuto daga d'akin Takoma Nata Dakin, shiru shiru tana jiran Taga Aisha tazo tayi mata aikin data sakata Amma taji shiru, daga murya tayi tace "mesunan qawa idan bazaki Dena dauremin fuska Ki futo ki tacemin ayar nanba toki dawomin da abata daki, kar akuyarki ta kunce tazo ta shanyemin kijanyomin nayi asarar ayata" Ummah dake zaune awaje itada Abba, tace "kifuto kiyi abinda aka sakaki mana" Futowa tayi tana mita qasa qasa, "asara tanawa Kuma, aikuwa itace tasai asara tunda batada qanqara Kuma basu kawo wuta ba, kullum mutum yana abu daya, idan baya gindin murhu to yana wajan Tatar kunun Aya, kwana biyu da mukai fadan ma ni harna huta" Hajja datake jiyota tana mita tace "to mesunan qawa idan baki tacemin ba waye zai tacemin? Ko mamuda zansa ya tacemin ayar?, saboda wa nake sana'ar? Saboda auren ki ne" Aisha batace mata komai ba,haka ta tatace mata kunun ayar tsaf, takai mata shi gabanta, Hajja tabata kujera tace "sannu me sunan qawa, zauna anan to" Zama tayi cikin shagwa6a tace "Allah Hajja nikidena min zancen aure na" Murmushi Hajja tayi tace "to shikkenan yawuce, yanzu de shawara Zaki Bani, sonake nasiyo tinkiya ko Rago, da Dan kudin Dana Tara na ciniki, idan Allah yasa jabir yasamu gurbin karatu, Sai a siyar da'ita abiya masa kudin makaranta, idan Kuma auren ki yariga karatun nasa tashi, Sai a siyar acika ayimiki kayan daki Mai kyau, Amma ke Yaya kika Gani? " Ummah dake zaune wajan Abba tayi murmushi duk da bata ji amsar da Aishan ta bayar ba, cikin ranta tana mamakin shaquwar Hajja da Aisha Da yammah Hajja tasa Abba yasiyo musu kifi, da kanta tashiga kitchen din nasu tana dafawa, saboda tasan cewa me sunan qawa yau taje makaranta Kuma tagaji, Aisha datake duba jarabawar Yara kasancewar sun kusa hutu sakamakon gabatowar watan azumi, tace "Hajja me kike dafa mana ne?" Cikin tsokana Hajja tace "Kifi ne qwaya biyu nake dafawa bawani abun kasawa a faranti bane" Itama Aisha tace "Alhamdulillah tosaikici daya kibani daya" ****** Zaune yake akan wasu lafiyayyun kujeru masu laushi a balcony din falon Mama, Wando ne ajikinsa three quarter, da wata Riga yar qarama wadda ta kama jikinsa, kana hango yanda faffadan qirjinsa zuwa jikinsa yayi wani layi layi, dantsan hannunsa yafuto sosai, coffee ne a gabansa Amma yakasa Sha ya zubawa sojojin dake shawagi a harabar gidan ido, azahiri su yake kallo, Amma badini tunanin rashin haihuwar sane yake damunsa, yayi tunani sosai, amma yarasa mafita, maganar Babban abokinsa Ramadan Wanda yaje Italy yake shirin dawowa jibi, itace take masa yawo acikin qwaqwalwar sa, (Yakamata ka qara aure Shahaab, mutum baya cire rai da Rahmar Allah,tsawon shekaru kaji shiru daga bangaren munirat why not kasake auren wata yarinyar ka gwada kagani ko zaka dace? Wani lokacin idan ta cikin gida ta dade bata haihu ba Ana auran ta biyun idan tasamu ciki zakaga itama dayar Allah yabata idan da rabo, sannan karka kuskura ka nunawa yarinyar dazaka aura kanada kudi, tahakanne zaka samawa yayanka uwa tagari....) Ajiyar zuciya yasaki, Sannna yafara magana cikin zuciyar sa "matarda zan aura, kowa de matarda zan aura, mama kullum maganar ta, matarda zan aura, Ramadan kullum maganar sa Matarda zan aura, tayaya zan'iya yin shigar talakawa saboda neman aure?, inde tana sona menene hadinta da kudi na? Dama a yanzu akwai yarinyar dazata iya auran wani Bayan ya nuna mata bashida kudi? Tayaya mama da Ramadan suke tunanin wata zata Iya sonsa badon abun hannunsa ba? Zata so shi koba kudi? Wacece? A'ina take? Idan yayi hakan Anya yayiwa munirat adalci kuwa?) Mama tada Jima a tsaye tana kallon sa, duk yanda akai yana cikin damuwa, duk da tasan Dama ba magana ce ta dameshi ba, Kuma tasan cewa Shiba neman aure yake ba bare tace yana tunanin budurwa, to tunanin me zaiyi? Ta tambayi kanta Kafadarsa ta dafa tace "kode ansamo min sabuwar suruka ne, Ana Nan Ana tunanin ta?" Murmushi yayi, dimples dinsa suka futo duka biyun, hannunta data maida cikin sumar Kansa ta Yan asalin Nijar yad'ora nasa hannun akan Nata, ya d'ago Kansa yana Kallan ta yace "idan akwai kece mutum ta farko dazan fara sanarwa mama" SHAHAAB littafin kudi ne, ki biya naira 300 kacal ki karanta abinki Hankali kwance kafin free page yaqare, siyan nagari maida kudi gida💃🏻 Zaki tura 300 ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Zaki tura shedar biya ta wannan number 08033300034 Amnah El Yaqoub ✍🏻 [13/09, 20:50] +234 803 697 8511: 🌸SHAHAAB🌸 (Romance) Writing By Amnah El Yaqoub Dedicated to Aisha's Name Like my Page On Facebook👇🏻 https://www.facebook.com/amnahel 7&8 Munirat datazo part din maman domin yin dinner, ta tsinkayi zancen dasuke shida mama, gabanta ne yafadi, ahankali tajuya zuwa part dinsu, kwata kwata saitaji abincin ma ya isheta, ko inda take saka qafarta bata Gani, daqyar takai kanta d'akinta. Numfashin tane yake sama sama kamar Wanda zai dauke. Ahankali taji hawaye sun zubo mata, tarasa meta tsarewaa tsohuwar Nan datake so taga Bayan auren ta, tayi biyaiyar, a banza, tayi kissar a banza, daga ganin mutum a zaune Zaki d'ago masa da maganar aure? Idan bashida ra'ayin auren ma ta tabbatar wannan matar saita saka shi yayi, tana son Shahaab tana kishin sa, bazata taba jurar ganinsa da wata yarinyar ba, hakan bazai taba iyuwa ba, Mahmud natane ita kadai. Lokaci daya taji tatsani mama, duk mutumin dazaisa dansa yaqara aure, a yimata kishiya tabbas wannan mutumin Babban maqiyinta ne. Ahankali mama ta sunkuya tayi kissing goshinsa, sannan tace "Allah ya nuna mana, zuwa nayi infada ma na sallami me kula Dani, saboda batada kunya, Kuma bata iya aikinta ba" Murmushi yayi, idan bai manta ba wannan me kula da maman itace ta kusan Tara, kowa yakawo mata to akwai irin complain din datake masa, Kuma Sai Bayan ta sallamesu ne take fada masa, yanzu idan yayi mata magana to zata fara yimasa mita ne, shiyasa yasaki murmushi ya nuna mata Shima hakan yamasa, ahankali yace "hakan yayi mama, duk wadda bazata miki yanda kike soba, kawai ki sallameta, insha Allah zansa a duba miki wata" Kansa ta shafa tace "Allah yayi Maka Albarka" Sannna ta zauna akujerar gefensa tad'auki coffee din tafara bashi da kanta. Sai wajan shadaya nadare Sannan yabar wajan mama yatafi part dinsu, yana zuwa ya ganta taci wata arniyar rigar bacci, kasa d'auke Idonsa yayi akanta, tana ganinsa ta gefen idonta, cikin ranta tace "tarko na zaiyi aiki da alama" Perfume tad'auka tafara fesawa, ko Kallan inda yake batayi ba, ahankali yatako yaqara so wajan ta, ta bayanta ya rungume ta tareda dora kansa akan kafadarta, wani irin kiss yasakar mata awuyanta, duk da saqon nasa yashige ta, hakan baisa tayi masa magana ba Laushin jikinta, dakuma yanda hannunsa yake yawo akan abubuwan dayake so a jikin Nata, shine yasake saka shi tafiya wata irin duniya, cikin shaqaqqiyar murya yace "waye ya ta6amin ke?" Meza tace masa? Taje wajan mama ne taji suna maganar yimata kishiya? Hakan yana nufin la6e take musu kenan?batare data bashi amsa ba, tajuya ta fuskance shi, zaiyi magana tahade bakinsu waje daya, yana qaunar kiss, shiyasa baiyi mata musu ba yabada Kai, saida sukai Nisa, hankalin sa yagama tashi, tasaki wani irin kukan kissa tajanye jikinta, Takoma Kan gado ta kwanta tana wani irin kuka, cikin tashin Hankali ya kalleta da lumsassun Idonsa,ahankali yataka ya zaune a gefenta tareda janyota jikinsa, can Qasan maqoshinsa yace "meyafaru Kuma? Kiyi hakuri Dan Allah, keda waye Wai? Nine ko?" Yanda ya rikice yake zuba mata tambayoyi kadai ya'isa kagane cewa acikin tsananin buqata yake, cikin kuka tace "ni inada abubuwan danake son yi da wasu kud'ad'e ne, Kuma account dina yayi qasa sosai saboda nayi wa wasu Yara a family dinmu hidima da kudin" Hannu yasa ya fuzgota jikinsa har saida qashinta yayi qara, yayi mata rumfa da faffadan qirjinsa, yace "naji, zanbaki duk abinda kike so, Kidena kuka saboda wannan, nawa kike ganin zai isheki?" Cikin shagwa6a tace "ko ten million ne" "zan baki" Shine abinda yafada, daga Nan yaci gaba da abinda yake, tasan cewa ko samada haka tanema awajansa to zai batan, danhaka cikin farinciki tasakar masa jiki yayi yanda yaga Dama da'ita, saide duk yanda yake abu daya, Bai ji yasamu gamsuwa yanda yakamata ba, but duk da hakan yafi ace yana cikin wannan halin na masifar sha'awa, Bayan komai ya lafa tayi tunanin zaiyi mata magana akan kud'ad'en data nema, saitaji yayi shiru, shi kuwa ko ajikinsa, asalima baiga laifin taba ko kadan, menene aciki danta tambayeshi kudi? Haka kuma sigar yanda take neman kudin awajansa yayinda yake cikin tsananin sha'awa Shima bai taba damunsa ba, yaso de ya tambaye ta ko tana amfani da wasu magungunan ne yanzu, yana jinta tana sauya wa a wasu lokutan, shikuma hakan cutar dashi yakeyi, baya samun gamsuwa yanda ya kamata. ****** Gaba dayansu suna zaune acikin rumfar gidan suna shan iska kamar yanda suka saba, Yara ne guda uku suka shigo gidan hannun su d'aukeda doya, manja, dakuma sabulu Dan kamaru. Bayan sun gaida su Daya acikinsu yace "Wai gashi, daga gidan Alhaji Audu ne" Godia Ummah da Abba sukayi wa yaran, Hajja ta basu Dari biyu kudin tukwici Zama tayi tana jujjuya jarkar manjan tana cewa "wannan bawan Allah yanada kirki wallahi, duk zuwa saiya kawo mana abun Arziqi, duk unguwar Nan kowa Alkhairin sa yake fada" Aisha tafuto daga daki jikinta Sanye da hijabi Dan qarami Amma yarufe mata qirjinta, jarabar son jin radio ne da ita, yanzu ma redio ce a hannunta tana kokarin kunnawa, Hajja tace "mesunan qawa zoki dauke kayan Nan" Radion ta ajiye ta dauke kayan, Hajja ta qarasa kunna mata, Adede lokacin kuwa kamar ansan Aisha ce take son jin radion adede lokacin ta tsinci muryar me bada labarin yana cewa "ma'aikatan hukumar efcc sun cafke wani sanata, suna tuhumarsa akan cinye kudaden wasu ma'aikata kimanin nera billion ashirin, inda shugaban hukumar MAHMUD WAKILI, ya basu umarni suci gaba da tsare shi harsai sun gama tabbatar da abun da suke zargi" Ahankali tasaki wani siririn tsaki, Takoma cikin d'aki, tana jiyo Abban ta yana yabonsa "ai yana kokari sosai wannnan bawan Allah , Kuma yaro ne matashi bazai fimu shekaru ba, duk wasu 6arayin Gwamnatin qasar ahankali yake zaqulo su" Sotake taje ta kashe radion, to Amma Abba yana wajan, Kuma duk suna jin labaran, batasan Yaya zatayi ba, wata dabara ce tafado mata, Ahankali tace "Hajja Dan Allah Zaki Bani kudi insiyo sabon battery? Nacikin radion yayi Sanyi wallahi" Hajja tace "mekikace mesunan qawa? Ban fada miki ba, da nice na saki jarabar son Jin redion? Zoki dauki abarki" Takashe radion tana miqo mata abarta, cikin farinciki Aisha ta kar6e radionta, cikin ranta tana fadin "yau son kudin Hajja Nima yamin amfani"(😃) ****** Yau babu inda yafita,mama tace bata so yayi nesa da'ita, tagaji da rashin ganinsa, hakan yasa ya zauna afalo yad'auki system yana chatting,kasancewar babu inda zai fita, saiyayi zamansa da wata Riga marar hannu, gaban rigar an rubuta Adidas, Sai wando three quarter Dayayi masifar yimasa kyau, mama tana daga Gefe tana kallo hannunta d'aukeda Inab tanaci, munirat tana Gefe a zaune tana fadawa qawayenta yau gasu surukar su tasaka su agaba, bataso danta yafita, Kuma taqi yarda yaje part dinsa barema Tasha soyaiyarta da mijinta, wata acikinsu Mai suna zuly ce ta turo mata emogi na dariya, tace mata akwai wasu magungunan da tagani Ana siyarwa na mallaka ne, idan ta siya Sai yanda tayi dashi, mama bata Isa tayi mata katanga tsakaninta da mijinta ba Nan da Nan tanemi account number, suka turo mata, kudin tatura musu, Nan da Nan sunga ruwan kudi, suka bata tabbacin zasu aiko mata dashi har gida Dayan group dinsu dasuka bude suka koma, kudin data turo suka raba a junansu, inda daya daga cikin su tad'auki nauyin turo mata ararra6i dakuma tazargade, a matsayin maganin mallakar.(☺️) Daya daga cikin Yan sandan dake gadin gidanne yashigo ya kalli mama yace "Hajiya yalla6ai yanada baqi awaje" Kafin mama tayi magana Batareda daya d'ago Kansa ba yace "akaisu falon baqi" Mama ta zubawa munirat data qanqame waya a hannu idanu,ta6e baki tayi cikin ranta tace "ko uban me take da wayar?" tayi tunanin zataji tayi magana akaiwa baqin mijinta ruwa, Amma sai taji shiru, ahankali ta watsa mata harara qasa qasa tace "Babu Tarbiyya agida"(😂) Ita Kuma munirat tsoro take kartasa akai musu lemuka mama tace tana bada umarni tunda ranta, shiyasa ta manna mata(🤷🏻‍♀️) Mama ta daga murya takira me girkinta, da sauri ta qaraso ta tsugunna a gabanta, cikin Isa da Kuma tsantsar iko tace "akaiwa baqi ruwa, suna falon baqi" Aqalla saida yad'auki kusan minti goma Sha biyar, Sannna yatashi yatafi wajan baqin Wani Babban falo ne Mai d'aukeda manyan kujeru masu launin ash dakuma dark blue, Kala biyu ne kujerun haka akai adon falon dasu, manyan mutane yagani su uku, kowanne yana Sanye da Babbar Riga, suna shan lemukan da aka kawo musu Yana shigowa suka zuba masa ido cikin mamaki, jisuke zasuga wani Babban mutum ne qaton tumbi, Sai sukaga yaro matashi, shi Kansa saida yaga baqin nasa sun manyan ta, Sai yaji kunyar yanayin shigar dayazo wajan su da'ita, sumar Kansa yashafa, cikin kunya ya zauna a kujera yana fuskantar su, Bayan sun gaisa daya daga cikin su yace "Nasan baka ganemu ba, baqi nemu daga yobe state muke, akwai Wanda yaturo mu wajan ka ne yace akwai gidaje dakake bayarwa haya anan Abuja, shine mukeso zamu za6i Mai kyau dan qarami guda daya" Cikin girmamawa yace "eh hakane, akwai gidaje, qananun gidaje muna bada hayarsu a million daya da dubu Dari biyu da hamsin, saikuma manyan, ya danganta de da yanayin irin Wanda mutum yakeso" Daya daga cikin su yace "ato mezai Hana mugansu, inda yiyuwar mu sauya ai saimu za6i Wanda yamana" "ok babu damuwa, ga wannan katin, kunemi me number dakuka Gani ajiki, duk zai nuna muku komai, har kudin ma duk shi zaku Bawa" Katin suka kar6a, tareda yimasa godia, daga Nan suka tafi Shima tashi yayi, yana amsa wayar Ramadan, dayake sake sanar dashi gobe de yana hanya insha Allah ****** Washe gari dawuri ya shirya yafita wajan aikinsa, Bai dade da zuwa office dinba, aka sanar dashi anyi approved latter sa, yau yanada ganawa da shugaban qasa, muhimman abubuwa yad'auka, sannan yabar office din nasu, security suna take masa baya, Kai tsaye suka nufi fadar shugaban qasa, sun tattauna dashi akan manya manyan cases da'ake Fama dasu a qasar, daga Nan suka dudduba wasu muhimman takardu, akayi musu photuna Sannna yayi shirin tafiya, inda yasamu kyakykyawar Jinjina dakuma yabo daga shugaban qasa, yana futowa Yan jarida sukai masa caaaaa, kowa so yake ya amsa tambayoyin sa, gaba dayansu amsa daya ya basu wadatacciya, yayi gaba, security Sai kare shi suke kamar suna tsoron wani mutum zai iya cutar dashi Kai tsaye office din nasu yakoma, inda yaci Karo da wani file daya girgiza tunanin sa, Ana zargi mutum biyu daga cikin hukumar tasu, suna kar6ar cin hanci da rashawa awajan qananun ma'aikatan dasuke shirin fitar da list din sunayen su wannan watan Mai kamawa, Jiyayi Kansa yasara, baisan lokacin daya dauki wayarsa yakira Ramadan ba, yana dauka ya tabbatar masa da cewa yanzu yanzu jirginsu ya sauka, zai wuce gida ya huta, zuwa gobe zai futo bakin aiki insha Allah Sai yanzu ne yaji dadi, ko banza Wanda suke warware matsalolinsu tare ya dawo ****** Tafe suke a hanyarsu ta dawowa daga makaranta, Aisha ta kalli qawar Tata tace "Walida, wallahi naji dadin hutun Nan a wannan lokacin, nafarko ankusa azumi, zamuyi hutunmu cikin azumi, sannan Kuma abun yazo mana a qarshan wata, kinga wannan dubu biyun tawa, wallahi asusu zan siya nasaka aciki" Walida tasaki ajiyar tace "hmm Aysha kenan, nikam Dama da mamana muke shawarar abinda zanyi da kudina, to itama Hankalinta atashe yake yanzu, tun jiya Abbanah bai dawo ba yana Abuja, Wai EFCC tasaka abokinsa acikin jerin mutanan da ake zargi, Kuma wallahi mutumin kirki ne, bakiga yanda yake yiwa Abbanmu hidima ba" Aisha tace "Walida kenan, nifa kinga ko sunan mutumin Nan banaso naji, kinga de irin sunan mahaifina gareshi, to wallahi Bana ma son jin sunan, saboda na lura bashida Imani ko kadan, kullum labarinsa ne yake yawo yakama wannan, yakama wancen, jiyama inajin Abbana Sai yabonsa yake, kenifa saboda jin labarinsa ma nadena kunna radio na, ba zanje inyi asarar battery na akan wannan marar mutuncin ba " Walida tace"A a Aisha, kidena ce masa marar mutunci, Shimafa baban wasu ne, Kuma muma idan wani ya cewa babanmu marar mutunci ba zamuji dadi ba" Cikin 6acin rai ta kalli Walida tace "to tunda ke yanada mutunci a'idonki, Sai kije mutuncin nasa yasa yasaki abokin Abban ki" daga Nan tayi gaba ta qyale ta, wajan masu saida asusu ta wuce, tasiyo na nera hamsin, ta basu dubu dayan suka dauki hamsin din aciki, sannan tasaka dubu daya da Dari Tara da hamsin din aciki Tana zuwa gida taga Hajja da jummai a tsaye acan gefen katangar gidan dede tiken dabobi, tanajin Jummai tana cewa "lalle Hajja A'i Jari yanata hauhawa, yanzu kece da tinkiya, Nan gaba kadan wannan tinkiyar Taki tsaf zatayi dubu ashirin" Hajja tace "kemafa jummai Zaki ki iya siyan tinkiyar Nan, jarabar son kudinki ne bazata barki kisiya ba, Dan Allah Jummai kirage son kudi" Jummai tace "Hajja A'i ai Ina kokari ma hakan, kullum fa Sai munyi miya da man nera hamsin, kashe kudin yayi yawa" Baqin ciki ne yasa Hajja takasa magana, ganin shigowa Aisha yasa tace "Wannan akuyar Kuma me kaman kifi ta Mesunan qawa ce" (😂) Aisha ta kalli Hajja batace mata komai ba, ganin taqi tankawa yasa Hajja tasake cewa "jummai kin ganta ai, wannan me kamar kifin de, itace ta Me sunan qawa" Girgiza Kai Aisha tayi ta wuce Dakin Ummah, taga alama Hajja neman magana takeji dashi Ummanta tabawa Asusun Nata ajiya, takuma fada mata kudin albashin ta na wanna watan yana ciki, idan zatayi amfani dashi tafasa Asusun ta d'auka, Sai asiyo Sabo amaida canjin ciki Godia umman tayi mata, tareda samata Albarka, Sannna tatura Asusun Qasan gadonta. SHAHAAB littafin kudi ne,naira 300 ne kacal 👌🏻,yar'uwa siyan nagari maida kudi gida, ki biya ki kiranta abinki cikin salama Zaki tura 300 ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Zaki turo shedar biya ta wannan number 08033300034 Mrs Usman ce✍🏻 [13/09, 20:51] +234 803 697 8511: 🌸SHAHAAB🌸 (Romance) Writing By Amnah El Yaqoub Dedicated to Aisha's Name Like my Page On Facebook👇🏻 https://www.facebook.com/amnahel 9&10 Yauda sassafe yafita aiki, ko break bai tsaya yiba, wajan mama nede bai Isa yafita batare daya shiga yaga halin datake ciki ba, saida tasa masa Albarka sannan yafice a gurguje sakamakon wani zazzafan case dasuke dashi akan kama wani tsohon gwamna da sukayi, Ana tuhumarsa da cinye wasu kudade daya kamata ace anyi aiki dasu acikin jihar tasa beyi ba, banda Dan Karen bashi daya biyo baya Wanda akebin jihar, gaba daya dukkan kadarorinsa sun kama sun riqe, yana zuwa Yan jarida sukayi Kansa da tambayoyi, kasancewar labarin ya watsu acikin qasar, kowa da irin abunda yake fada, wasu na ganin laifin hukumar, wasu Kuma na ganin laifin gwamnan Sai Bayan yagama tattaunawa da yan jarida sannan yawuce office dinsa, masu take masa baya Kuma suka dakata, ganin Ramadan na jiransa yasa yasaki murmushin dabai shirya ba, suka qarasa cikin office din "mutanan Italy" Cewar Shahaab Ramadan yace "na'am Angon munirat ya ayyuka, jiya baka shigo office ba" Kafadarsa buyu yadaga yace "wanne ango Kuma Ramadan, jiya mama ce taqi dadi, tace sotake na zauna taita kallo na" Dariya Ramadan yayi "Hajiya Mama kenan, tana son wannan dannata qwaya daya" "har mamaki takebani wani lokacin Ramadan, nikaina nasan idan babu ni Tofa babu mama" ya qarasa maganar yana murmushi dinmple dinsa yafuto Ramadan yace "no, karka ga laifin ta, idan kaine a matsayin datake, nasan saika fita son Yara, saboda ita bata dauki lokaci Mai tsawo ba ta sameka, kaikuma ka dauki wasu shekaru kana jiran haihuwar baka samu ba, kaga kuwa Kai zaka fita son Yara,Kanada lafiya, aure kawai zaka qara, kafara zubo mana Yara, kaima kasan da hakan" Cikin sanyin jiki yace "Allah yasa mudace" Cikin rashin mamaki Ramadan ya Kalle shi, wato da gaske de bayason maganar aure, kamar Wanda munirat ta riqe masa zuciya ita kadai, akan suyi maganar auren shine ya kawar da zancen nasu Wai Allah yasa mudace, ajiyar zuciya yasauke yace "Amin, ga wannan file din, nagama aikinsu jiya Dana shigo office, binciken da'aka turani komai yayi daidai, idan kaduba zaka Gani, Bari in barka kayi aiki" Batare da yace komai ba yaja file din gabansa, shikuma Ramadan yafice daga d'akin office din ****** Aisha data futo sassafe, tafara tattare kayan gidan ta share shi tas,radio ta kunna, Bayan tagama jin labaran safiya tana shirin kashe radio taji hukumar efcc ta damqe wani tsohon gwamna, girgiza kanta tayi ta kashe radion,al'amarin Mahmud Wakili Kuma yanzu yadena bata mamaki, tsoro yake bata,tadebi ruwan wanka a bokiti takai banda ki, Sannna Takoma Dakin Hajja tad'auki Dan qaramin brush dinta da makilin, saida ta kalli Hajja dake kan gado taga bacci takeyi sosai, sannan tasaki labulen Dakin tazare hijabin jikinta ahankali ta ajiye,sannan tacire yar yaluluwar doguwar rigar jikinta ta bacci wacce Taji jiki, Nan da Nan farar fatar jikinta ta bayyana, abinda take 6oyewa cikin hijabi Shima yafuto muraran, gaban tsohon madubin Dakin taje ta tsaya tana qarewa qirjinta kallo,itade tunda tafara wannan abu takejin zafi, bata Isa tabigi wajanba Sai taji kamar Tai ihu,ga tauri bata Isa ko cikin bacci ta kwanta akansu ba, Kuma Sai qaruwa suke kamar tana saka musu wani abu, a tsaye suke qyam a qirjinta Yan madedeta da basufi madedecin lemon zaqi ba, ko yaushe zasu daina ciwon? Ta tambayi kanta Jin kamar Hajja zata motsa yasa tayi sauri ta daura zanin wanka, sannan ta ajiye kayan data cire Hajja data dade da bude ido ta kalleta tace "Mesunan qawa, idan kingama kallon kanki amadubin dage min labulen Nan zafi ya isheni, munafuka.... Idan Zaki kalli kanka saiki tasheni daga bacci kice Hajja A'i fice zanyi amfani da Dakin" (🙆🏻‍♀️😂🙈🙊) Jitayi kamar ta nutse acikin qasa Dan Kunya, Dan qaramin bakinta ta turo gaba, sannan tafice daga d'akin tana bubbuga qafa cikin shagwa6a, ko labulen bata dauke ba (😃) ****** Da daddare suna zaune a dinning, Mai aikin mama takawo musu abinci tana jerawa, mama tace "Shahaab nifa nafara gajiya da Zaman dinning dinnan, takura nake yi, nafison na zauna aqasa" Cikin ladabi yace "mama to mukoma Qasan mana, saina baki abincin dakaina" "a a, yaushe zan saka wahala Shahaab, yakamata de ka nemo min wata yarinyar, wannan din aiki zaiyi mata wahala, ga girki gakuma kula Dani, ita Kuma munirat babu abinda ta'iya Sai danna waya" Shiru yayi kamar ruwa ya cinye shi, yasan idan yaja maganar to ba'a Kansa zata huceba saide akan munirat din. Mai aikin ce takawo musu lemon data Dauko a kitchen, zata zuba wa mama Nata, Sai munirat ta dakatar da'ita, tace "jeki, Bari in zuba mata" Mai aiki tafice daga falon, mama ta kalli munirat tace "duk inda kissa take ni banason ta, nida ba namiji ba tayaya za'a min kissa nakasa ganewa? Dacan baki ta6a zuba min abincinba, Sai yanzu? Babu uwar da kike tsinana min a gidan Nan munirat, shiyasa Nima nafi ganin mutunci da qimar wadda take kula Dani akan ki, koba komai ita zata Dauko abinci na takawo min tunda tasan banason Zaman dinning, zata zauna ta dinga matsamin qafafu na saboda kumburi, zata zauna Dani tayi fira Dani ta debemin kewa idan d'ana baya Nan, duk abinda zakumin yanzu daga ke har mijin naki ai duk a banza, tunda Shima gashinan a zaune yakasa nemo min Qawata, Amma da neman 6arayin Gwamnati ne jikinsa yana rawa zaije yakamo su, anan yafi qarfi, saikace Gwamnatin ce ta haifeshi baniba"(🤭🙆🏻‍♀️) 'Dago Kansa yayi zai bata haquri ta dakatar dashi ta hanyar d'aga masa hannu, "dakata Shahaab, banason jin komai...idan kuma zayyanomin abinda kata6a yimin zakayi danka wanke kanka saboda rashin nemo min qawata dakayi to Shima Bana buqatar ji, to mema kata6a yimin? Fadamin abinda kata6a yimin abaya, saina biyaka, barema nikam mekata6a yimin a duniyar Nan ne Shahaab?"(😂) Girgiza Kansa yayi da sauri yace"A a, banta6a yimiki komai ba mama, kiyi hakuri" Bata sake magana ba daga Nan, abincin da yar aikin tazuba mata ta d'auka tafara ci, munirat kuwa cikin ranta mamakin masifar mama take, akan wannan shegiyar qawar Tata da babu Wanda ya Santa, dannata ma datake mutuqar so bataqi ta6ata masa rai ba ****** Washe gari maqocin su Hajja Alhaji Audu yasake aiko musu da kayan Azumi sadaka, buhun shinkafa three brothers Dan madaidaici, da madara qaramin gongoni da siga kusan kwano biyu, Abba yafita da Kansa zaije har gida yayi masa godia, dama ya kammala sabon gidan mansa daya Gina akano, Mekai ashirin, Amma ba'a kaiga bude shi ba, duk saiya hada yayi masa Allah yasanya alkhairi tunda yazo Garin, dama Ana tunanin gobe za'a tashi da Azumi, gashi babu abinda suka siya a gidan, Sai Hajja ce take cewa zata siyo musu shinkafa awajan qawarta jummai ko kwano goma ce, Amma gashi sama taka sun samu wannan kyauta, sukam Dame zasu sakawa wannan bawan Allah? Ummah tace "Hajja Dama wallahi babu komai a gidan Nan, Bari adiba Sai adafa" Hajja tace "sosai kuwa, Mesunan qawa tashi kinemi wuqa kibudeta ki dauka kidafa mana, saide mu qaro macaroni da yar taliya ko guda biyar biyar ne Kuma" Aisha tatashi ta kama buhun ta bude, Nan da Nan kuwa tadafa musu, aka zubawa kowa da Mai da yaji, suna cin abincin Hajja tace "Mesunan qawa wannan shinkafar Taki tadahu kuwa, three brothers cefa, Amma kinyi mata tahuwar three sisters" Aisha datake hada gumi tace "tadahu mana Hajja, kede kinfi son kiji shinkafa tayi luguf, kodan ke tsohuwa ce, haqorin duk ya mutu" Kafin Hajja tayi magana Ummah ta kalli Aisha tace "Dan Allah kicire hijabin nan, kewai bakya jin zafi ajikinki ne? Sai hada uwar zuffa kike Amma bazaki cire hijabin ba?" Hajja ta kwashe da dariya tace "Wanne dare ne jemage bai Gani ba?" Aisha tayi shiru, duk yanda takai da Bawa Hajja martani yau kasa mayar mata tayi, taga alama idan tayi magana to tsaf Hajja zata tona mata asiri akan abinda taga tana kallo yauda safe, haka ta kama hijabin tacire,lokaci daya taji iska me dadi tana shigarta, tsefaffan kanta me tsawo da qyalli Sai kad'awa yake saboda iskar datake shigarsa ****** Da daddare yayi shirin tafiya masallaci sallar magrib, Sanye yake da jallabiya ruwan toka, Sai carbi ahannunsa, baisaka hula ba, Amma jallabiyar tasa tayi mutuqar yimasa kyau,fatarsa tayi wani irin fresh, yana ganin musulman sojojin gidan suma suna alwala, da aqafa yake tafiya Amma yau mota yahau, kasancewar akwai kwalayen alqur'ani dazai raba, ko Allah zaisa yasamu Lada saboda gobe za'a kama azumi, Ana idarda sallar magrib din yatashi yafara Rabon alqur'ani, mutanensa suna tayashi. Limamin masallacin ne yayi masa addu'ah, Sannna yafara yin wa'azi kafin lokacin sallar ishsha'i, wasu mutane ne guda biyu dasuke zaune asahun bayansa, yaji suna zance qasa-qasa, da alama ba'a Garin sukeba, zuwa sukayi, gaba daya Sai hankalin sa yabar kan wa'azin da akeyi, yakoma kansu, dayan yaceda dayan "yanzu Mansur kaduba kagani yanda masu kudi suke jin dadi a wannan Garin? Amma kwata kwata basa taimaka wa talakawan dasuke wasu qauyukan, kaduba kaga haduwar wannan masallacin fa, ni idan nasamu Nan ma ai naji dadi, wannan shi ake kira aljannar duniya" Wanda aka kira shi da Mansur yace "wallahi hakane zakarai, kaga fa har kyautar alqur'ani ake bayarwa, mukam Bana zamuyi azumi a dadi, tunda ba yanzu zamu koma arewa ba, gashi babu zafi, ga ruwan sama, can Kuma Sai zafi" Zakarai yasake yin qasa da murya yace "wallahi saida nazo Garin Nan nasan cewa bazan mutu acikin wahala ba, gaskiya kudi yayi, saboda yanzu rashin kudi yayi yawa, marasa qarfi suna buqatar taimako, inda ace masu kudi zasu dinga taimaka musu Aida sun samu Lada, wani ma baisan irin addu'ar da za'ayi masa ba, qarshan ta wani yana masa addu'ah kaga Allah ya amsa masa, saboda kowa da irin baiwar da Allah yabashi, wancen azumin fa, gidan wani maqoci na, kullum gero sukeci, safe rana dare, shine abincin, idan aka Sha ruwa kuwa farau-farau suke hadawa, dayake Ina Dan taba sana'ar qanqara to shine Nima nake Dan taimaka musu, Amma wallahi kafin akama azumi geron ne, haka cikin azumin ma de shine abincin " Jikin Shahaab yayi Sanyi kalau, yanzu acikin wannan qasar ne za'a samu masu cin gero da azumi? Kuma Ahaka suke rayuwa? Har aka idarda sallar Isha'i, yana wannan tunanin a ransa, daya koma gida ma suna yin dinner mama taga kamar hankalin sa baya kan abincin, kawai de yana cine Shikuma tunani yakeyi a ransa, mutum yaci gero da Azumi? Mama kuwa Kallan sa take,tun daga fuskarsa har zuwa faffadan qirjinsa, tambayar kanta take Anya kuwa Mahmud lafiya kalau yake? Kokuma bashida lafiya? Kwata kwata Bahaka mahaifinsa yakeba,saboda idan de bata manta ba, lokacin da sukai aure idan babansa yafara abu daya saita gudu(🙈) Kuma idan de Shima ubansa yabiyo, to jarabar sama kadai zatasa matarsa tasamu ciki duk dade haihuwa tsari ne na Allah, to Amma shi shiru kakeji da alama de ba qalau din yakeba, duba da yanda yatsani ayi masa maganar qarin aure. Ruwa yadauka yasha, Sannna yad'auki tissue ya goge bakinsa, zuwa yanzu yagama yanke shawarar rabawa talakawan wasu garuruwan kayan abinci, ko Allah zaisa Shima wani yayi Masa addu'ah Allah yabashi magaji, Kallan munirat yayi, ya qifta mata ido alamun yana jiranta, Sannna yayiwa mama sallama yatafi part dinsa Bayan sunyi shirin bacci yaja munirat jikinsa ya rungume ta,ganin kamar baida damuwa yasa ta bijiro masa da maganar ten million din Dayayi mata alqawari zai bata. Kallan ta yayi, "idan kina buqatane yanzu, to nayi Miki izni kibude loka ki dauka, ten million din Kuma tunda nayi Miki alqawarin baki to zan baki, but ba yanzu ba, akwai abubuwan dasuke gabana yanzu" Rantane yayi baqiqqirin, Amma dayake yar duniya ce, bata nuna masa ba, saima kissing din wuyansa data hauyi, alamun furucin nasa yayi mata dad'i, dayaga tana neman janyo masa ruwa, saiya rungume ta yayi mata rad'a a kunne, yasan cewa idan tatada masa Hankali ma wahala kawai zaisha, saboda kwana biyun Nan gaba daya tasauya masa, jinta yake tamkar abinci ce medadi Amma Kuma babu Maggi da gishiri acikinsa(😲) daga Nan yayi bacci, munirat kuwa, kasa baccin tayi, baqin ciki ne fall ranta, Sai gab da lokacin sahur bacci me dadi ya dauketa, shi kuwa tun qarfe uku da rabi yatashi yafara nafilfili, yana roqon Allah yasadashi da alkhairin dayake cikin wannan wata Mai Rahma daya kama yau Sai shine yatashe ta tahada musu abunda zasuyi sahur dashi, shikam kawai baqin tea yasha, Bayan ankira sallah yafice masallaci. Dasafe yana tsaye gaban mirror din dakinsa, agogo yake daurawa ahannunsa,kamar kullum yana Sanye cikin suit wadda ta kar6i fatar jikinsa, ya maqala waya a kafadar sa yana magana cikin aji "Ramadan kayi magana da MD na company yahada manaTrella ta macaroni da taliya guda goma " "yanzu ake buqatar trella goman?" "no, cikin satin nan nakeso agama hadawa, Sai kayi magana da Baba yahuza, zai hadaka da mutanan dazasu dauka, Sai araba duk garuruwan daya kamata" "ok to shikkenan, jiya naje ganin sabon company, komai yayi kyau sosai Abokina, Sai aiki ake wuta-wuta,da alama kana buqatar sa yanzu ne cikin qanqanin lokaci" Murmushi yayi, Bayan yagama daura agogon yace "A a, ni Bani zanyi amfani dashi ba, akwai wacce zan Bawa, zan Bawa wata wadda Takeda mutuqar muhimmanci awajena" Munirat data qaraso cikin Dakin nasa hannunta d'aukeda brief case dinsa, tasaki wani murmushi Mai qayatar wa Sannna tashigo cikin Dakin, tasan cewa itace, ta Kuma San Bayan ita, babu wadda Shahaab zaiyi wa wannan kyautar, Nan da Nan taji duk wani 6acin rai datake ciki yakau, bacin ran Data kwana dashi Daren jiya taji yatafi. Ganin munirat din tashigo dakinsa yasa yakashe wayar, bayaso ko kadan tasan shirin dayake akanta, yafi son saide taga yabata takardun companyn ****** Hajja ce zaune cikin inuwa tana wanke jarkokin kunun Aya, tunda ankama azumi yau, tofa tarufe yin kunun Aya Kuma, Aisha na gefenta tana tsefe kalbar da'akayi mata wadda duk jelar tagama warware wa, ta kalli Hajja tace "Dan Allah Hajja kimin kitso, kullum saide amin kalba, ni wallahi nagaji kitso nakeso" Hajja tace "haba 'yar Nan, kika Bari saida muka dauki azumi Sannan Zaki kama Kai ki tsefe saboda kina tutiya Hajja A'i ta'iya kitso, aikuwa saide kije maqota a miki" Kafin Aisha tayi magana wani yaro yashigo gidan yace "Hajja A'i Wai inji jummai idan kinada yar ashana kibata zata hura wuta" Hajja tace "wacce irin ashana Kuma da wannan safiyar ko bata dauki azumin ba ita?" Yaron yace"bansani ba " Tace" kace mata banida ashana, saide kwalin ashanar idan tana so saikazo ka kar6a mata, saita nemi ashanar awani gidan " Aisha tace" Hajja Dan Allah nikiji Dani " Tace" ke bazan miki kitso yanzu ba, kanki yayi santsi dayawa, tsautsayin dayasa kika tsefe shi zaisa ki kitse abinki da kanki " Aisha bata qara mata magana ba, tagama tsefe kanta, Sannna tadaureshi da Dan kwali, Dan batada ribom ko daya ****** Zaune suke shida mama dakinta, yanda Dakin ya tsaru, saika rantse Dakin wata budurwa ne, Kansa yana kan cinyarta, so yake yafada mata yanaso idan yagama ginin companyn yabawa munirat to Amma yana tsoro, danhaka saiya sauya shawara yace "mama akwai kayan Azumi dazan raba, idan akwai Wanda kike so akaiwa saiki fadamin Inyi musu magana" Mama tace "A a Shahaab, banason komai, abu daya nakeso awajanka kawai" Cikin Sanyi jiki ya kalleta, yana tsoro karta ce masa yaqara aure, yace "mekikeso mama?" Tace "nariga na fitar da rai da ganin Qawata Aysha,inajin Sai a darussalam zamu hadu,lokacin danaje gidansu neman ta, mutanan unguwar sun fadamin babanta yakoma jigawa da aiki,danhaka inaso kasamu lokaci, kaje jihar kaginamin gidan marayu acan, inajin Aysha tarasu, bansan Kuma tayaya zan taimaki wani Nata ba, qila tarasu tabar marayu, idan Allah yasa yayanta suna daga cikin Wanda za'a kawo su gidan marayun shikkenan kaga Nima na taimaka mata, qila haka Allah ya qaddara mana nida ita, Allah baiyi zamu cika alqawarin mu, muhada Yayanmu aure ba" Shahaab ya Lumshe Idonsa, yabude, shifa wannan maganar hadin auren ne yasa bayason aga matar Nan, to Amma Yaya zaiyi? Ahankali yace "to, za'ayi" Tace "yaushe?" Kallan ta yayi yakasa magana, Nan da Nan ranta ya6aci tace "nifa Naga alama bakasan nemomin qawata Shahaab, Kuma muddin a kaga Aysha, saika auri yarta inde mace ta Haifa, saide in ta aurar da'ita ne, daga min cinyata tunda ban'isa insaka kayi ba"(😅) Sake rungume mata cinyoyi yayi,tamkar zaiyi kuka cikin shagwa6a yace "Allah bazan tashi ba, to yanzu ni mama yakike so inyi, aiki yamin yawa, da wanne zanji? Ga company's, ga office dinmu, ga gida" Kallan sa tayi yana magana kamar zaiyi kuka, ahankali tace "Shahaab, koba Dan qawata Aysha ba, zaka samu Lada kaima idan kayi" Cikin gajiya da maganar yace "zansa ayi" Cikin damuwa tace "to yaushe zakaje? Zanbaka kudin ma, nide fatana kawai ayi" Jikinsa ne yayi Sanyi lokaci daya, lalle mama da gaske take, sake rungume ta yayi yace "mama kibar kudinki, awanne gari kike so ayi a Jigawan? Wanne Gari qawar Taki take?" Tace "bansan garinda takeba Shahaab, kawai kayi a inda kaga ya dace" "to mama zan shirya naje cikin satin nan tunda zan raba kayan Azumi, zanyi magana da Ramadan acikin jerin garuruwan da za'a raba kayan azumin, su saka da Garin jigawa, ni sai naje Jigawan da kaina, in raba musu kayan azumin, inyi maganar gina gidan marayun da Gwamnatin Jihar " Ahankali mama tasaki wata irin ajiyar zuciya tace"nagode MAHMUD, Allah yayi Maka Albarka" Tamiqa hannunta Qasan fillo, tad'auki kudi bandir daya tabashi tace "ungo wannan nakane" Murmushi yayi, dimples dinsa suka futo, yatashi daga kan cinyarta, yayi kissing kumatunta, sannan yace "nagode mama" yatashi yatafi part dinsa cikin murna yana jin dadi kamar tayi masa kyautar miliyoyin kudi. Bayan Ansha ruwa yana zaune agaban mama, munirat na Gefe tana danna waya kamar kullum, wayar Ramadan yakira, cikin zolaya Ramadan yace"kaga Angon munirah ita kadai " Murmushi yasaki yace" Ramadan, a cikin kayan daza'a raba na dinnan, atura mota biyu zuwa jigawa, a Kwai aikin da zanje inyi acan, Nima inaso inshiga cikin masu rabawar araba Dani, inason in Dan wara jinin jikina" Hakanan munirat ta tsinci kanta da faduwar gaba, batasan dalili ba, har saida ta daina danna wayar datake tazuba masa ido tana kallon sa, menene Kuma zai kaishi wata jigawa? Waye nashi a jihar? Ganin babu Mai bata amsa Sai shi, shiyasa tabar maganar har zuwa lokacin da zasuje kwanciya. Cikin murmushi Ramadan yace "Tofa, yauda kanka Abokina? Amma dakayi zamanka, duk abinda kakeso umarni kawai zaka Bani, zanje inyi ma shi, meyasa zaka wahalar da kanka kana Rabon abincin sadaka?" "inason yine Ramadan, may be wasu suyimin addu'ah Allah ya amsa" Ramadan yace "hakane, Allah yasa mudace, idan Kuma Rabon wata ne zai kaika shikkenan" "babu wannan maganar" Abinda yace kenan. Ramadan yace "to ai shikkenan saika koyi cire suite, tunda kace da kanka kakeso ka bayar, kaga bai kamata kayi aiki da suit ba ranar" "okay" shine kawai abinda yace Sannan yakashe wayar Washe gari yana gab da barin office aka kawo masa wani file akan case din gidan man fetir din wani bawan Allah da'aka kama akano,Me Kai ashirin,Bai tsaya ya duba file din yanda yakamata ba,ya turashi zuwa wani office din,suje suyi aikin komai ****** Hajja da Aisha suna tafe, rana Sai dukansu take, ga azumi, dawowarsu kenan daga gidan Alhaji Audu maqocin su, Wanda suka je masa jaje sakamakon qwace masa sabon gidan mansa da hukumar efcc tayi, daga Nan Kuma suka biya suka gaisa da jummai, Sannna suka taho gida, Hajja Sai mita take "Kai wannan bawan Allah, Allah kadubeshi su sakar masa gidan mansa, mutum Mai mutunci, me sunan qawa kiduba kiga yanda yake dawainiya da duka mutanan unguwar Nan, akawo mana wannan akawo mana wancen, Allah yasaka masa, Allah yakwato masa haqqin sa, Dan baka Isa fada da Gwamnati ba, saide ka hadata da Allah " Aisha tayi shiru tana tunani a ranta, tasan cewa de idan ba wannan Mahmud wakilin ne yakama ba to tabbas Shima zai iya sakawa akamawa Alhaji Audu gidan mansa, tunda shi kowama kamawa yake, bashida wani motsi saina kama kayan mutane, to gaba-gaba ma tsaf zai iya kama babansa, tunda kowama tuhumar sa yake. (🙆🏻‍♀️) Ranar haka ta wuni tana tunanin wannan mutumin, ko abincin shan ruwa bata iya dorawa ba, shi kuwa wannan wanne irin mutum ne? ****** Yau azumi anyi sati daya kenan, Sai yanzu ne Kuma abubuwa sukayi masa d'an sauqi, duk garuruwan daya ce aza6a araba kayan Azumi ko'ina anbasu banda jigawa, Shima Dan yace yanaso yaraba da Kansa ne, yanar gizo, gidan TV, dakuma gidajen redio Sai maganar sa ake, Ana Jinjina wa namijin qoqorin Dayayi,su Hajja Kam dasuka ji Ana fada a gidan redio cewa tayi "mukam Rabon Naka baizo mana nanba mesunan mamuda" Aisha kuwa haushi hajjan ma tabata, Wai mesunan mamuda, ko Yaya ma za'ayi ta had'a wannan mutumin da baban ta?(🤔). Kamar kullum Sanye yake cikin suit Tayi masa kyau sosai, munirat dake fesa masa perfume, gabanta Sai qara tsananta faduwa yake, batasan meyasa ba haka kawai itade batason tafiyar Nan tashi, ta Kalle shi cikin kissa tace "my dear, nifa banson tafiyar Nan taka,I don't know why" Fuskarta yakama yariqe ta tafukan hannunsa biyu yace "bafa dadewa zanyi ba, kema kinsan banson yin nesa dakeda mama, Amma nayi Miki alqawarin duk inda nake, kina Nan acikin zuciya ta," Cikin shagwa6a tafara yimasa wani irin kuka, baisan Yaya zaiyi mata ba, rarrashin ma kamar 6ata lokaci ne, lokaci daya yahade bakinsa danata, wayarsa dake kan gado ce tasa yadaina abinda yake, sakamakon Kiran Ramadan daya shigo. Cikin kunnan ta ya rad'a mata "ki gyara min abuna sosai kafin nadawo" Cikin kunya tasake boye fuskarta a qirjinsa. Shi yana nufin tasake gyara yanda ya kamata tadawo kamar da, ita Kuma kunyar dataji tayi tunanin yaji ta yanda yakeso ne,magungunan datake Sha sun kar6eta, shiyasa yake fadar hakan hannunta yakama cikin murmushi suka futo falo, daga Nan yayi mata sallama yatafi Saida yabiya wajan mama yamata sallama, tayi masa addu'ah Sannna yatafi. A Airport suka hadu da Ramadan, duk Wanda yasan shi saiya yi masa gaisuwa kafin yawuce, yau baisaka I'd card dinsa agaban suit din tasaba, a tsaye suke ko wajan Zama basu nema ba, kafin jirgi yatashi wasu daga cikin ma'aikatan efcc dakuma folice suka ruqo wani mutum kana ganinsa kasan badan qasar bane, Sai magana yake musu da Harshan turanci Amma yanda suka maqala baqin glass a'idon su babu ma Wanda yake saurarensa,hayaniyar datake tashi ne yasa suka juya shida Ramadan, suma ma'aikatan ganin MAHMUD din yasa cikin ladabi suka nufeshi, kudaden dasuke cikin jakunkunan suka juyesu aqasa, sun kamashi ne da kudi zai fita dasu wata qasar kimanin million Dari biyu na Dalar amurka cikin jakunkuna, me Yan jarida zasuyi inba dauka ba, shikam Shahaab kasa magana yayi, saboda da alama wani 6arawon Gwamnatin ne yayi amfani da Yaron domin a turashi da kudin yakaishi wata qasar. ya kalli Yan jaridar yaga sun taru anaso yayi magana Kai kace Dama awajan suke suna jiran akama mutumin Haquri ya basu yanemi uzuri tafiya ta kamashi, yanada ganawar da zaiyi tareda gwamnan jigawa nanda awa uku, wannan Kuma wani Babban case ne, idan ya dawo zasu zauna suyi tsatsauran bincike akan case din Yana fadar haka yayi gaba, yana jin yanda Yan jarida suke kira "yalla6ai tambaya daya, please tambaya daya yalla6ai kawai" Suna cikin jirgi Ramadan yana gefensa yana duba jarida, shikuwa Shahaab Lumshe Idonsa yayi, Qalubalen dasuke gabansa akan wannan matsayin dayake ciki shi yake tunani, yasan cewa tabbas baza'a Rasa masu shirya masa gadar zare ba, duba da yanda yake kama duk wani Mai sa hannu akan cin hanci da rashawa. Kamar yanda yafada hakance ta kasance, suna sauka Kai tsaye Tahir guest palace (Annex) suka sauka, Sai lokacin dazasu ga gwamnan Sannan suka tafi, basu dauki lokaci Mai tsawo ba ya tabbatar musu za'a samu Dajin daya dace agina gidan marayun, acan kusa da Garin Kiyawa, saida aka nuna musu komai a photo dakuma wasu garuruwan ma daban, suka Kuma tabbatar masa kamar yanda ya za6a din, ayi adajin kiyawa Amma wajan da zai kasance kusa da cikin Gari suke so. sunji dadin yanda aka kar6esu,Kuma abun yazo musu da sauqi kasancewar filin na Gwamnatin Jihar ne,Bayan sungama akayi musu photo Sannna suka koma masauqinsu Suna zuwa Shahaab ya daura towel yashiga wanka, Bai dade da futowa ba aka kira sallar magrib, shida Ramadan suka tafi masallaci Bayan sun dawo suka Sha Fruit da sauran abubuwan buda baki Bayan sun dawo daga sallar tarawih sun dade suna kallon labarai shida Ramadan, saida matar Ramadan din ta kirashi awaya Sannna yayi masa sallama yatafi dakinsa, shi kuwa da mama kawai yayi waya, yafada mata yanda sukai, taji dadi sosai, munirat kuwa wayarta akashe, tunda yayi try bata shigaba saiya haqura ya kwanta. Washe gari sukaje sukaga wajan, aka auna yanda abubuwan zasu kasance, suka tsara yanda aikin zai dinga gudana, dakuma mutanen da aka damqa aikin a hannun su Awajan suka wuni Sai gab da shan ruwa suka koma hotel, washe gari aka fara tono, manyan motoci suna kawo bulo, wasu yashi, wasu siminti, saida yaga aikin yafara kankama Sannna suka tafi, da magrib suna shan ruwa Shahaab duk tunanin matarsa ya isheshi, duk rashin dadinta yana rage zafi da'ita a hakan, cikin kwana ukun Nan da sukayi shi yasan yanda yakeji, wata irin sha'awa yake ji kamar zaici babu, sauqin sa daya yataho da qananun wandunansa masu kamar pant, yana sakawa, Amma badan hakaba ya tabbatar wataran idan yafita Sai yaji kunya,saide yadinga tafiya yana bude qafa saboda tsaro(😎) Saboda haka Gara suyi abinda yarage musu kawai yakoma gida, yajuya ya kalli Ramadan yace "yakamata mu raba kayan azumin Nan Ramadan, yau ankai azumi na goma kenan,sonake gobe mu wuce gida" Ramadan yace "Dasafe zamu raba kayan ne?" Girgiza Kai yayi "da nayi niyyar mu raba da safe da yamma saimu tafi gida, to nariga nasai mana tickets Dasafe jirgin mu zai tashi" Cikin sauri Ramadan yatashi zaune yace "Wai kana nufin yanzu daga shan ruwa zamu fara daukar kwalin taliya da macaroni muda yakamata ace mun huta?" Murmushi yayi yace "ba Lada muke nema ba? Yazakayi?" Kamar zaiyi kuka yace "to yanzu Yaya zamuyi?" "kira mun Wanda kayan yake hannunsu kagani" cewar Shahaab Babu musu Ramadan yakira su, yasaka wayar a hands-free sannan ya ajiye ta a tsakanin su Cikin aji Shahaab yace "yawwa kana Jina, muna sone muwuce gida gobe insha Allah, so kayan Nan za'a rabashi yanzu, Wanda basu qare ba saiku qarasa gobe, Ramadan zai kar6i account number ku, insha Allah Zakuga saqona" Cikin ladabi Yaron yace "to yalla6ai, yanzu Yaya za'ayi Rabon kenan?" Shahaab yace "akai trella daya yankin Hadejia da gumel, dayar Kuma abarta anan yankin dutse,ku dauki Rabin trella ku raba a wasu qauyukan saiku saka mana Rabin acikin mota, direban yazo Nan Tahir guest palace ya daukemu muje mufara rabawa" Cikin biyaiya yace "to wanne qauyukan zamuje yalla6ai?" Murmushi yayi yace "aika fini sanin yanayin garin, ku kukasan yanda zakuyi, but mude mungaji,kafadawa direban qauyukan dazai kaimu, Amma qauyukan dasuke kusa, Wanda muna gamawa zai dawo damu hotel" Nan da Nan Yaron yace "yalla6ai akwai, Dan masara, da Chai-Chai, Abaya, Baranda, dakuma Chamo, da.... " Cikin sauri Shahaab yatareshi yace"kai Kai kai kaga ya'isa haka, kafada masa yakaimu chai-chai, idan mungama dasu saiya kaimu inane kace na qarshen?" Cikin sauri yace "CHAMO yalla6ai" Cikin yatsina fuska yace "to yakaimu chai-chai da chamo, nagode" daga haka yayi masa godia suka kashe wayar Kallan sa Ramadan yayi yace "wanne irin Rabon kayan abinci ne wannan da daddare kamar munafukai?, yaushe zamu tafi mufara to?" Murmushi yayi yace "sahabban manzon Allah (S.a.w.) haka suke yi, suna ajiyewa talakawan su kayan abincin aqofar gida, duk Wanda yafuto Dasafe anan zai Gani, idan muka idar da sallar tarawih Sai mutafi, kafin Nan direban yazo, idan mun samu mutum aqofar gidansa saimu bashi, idan baya Nan saimu ajiye masa aqofar gidansa" Suna wannan maganar aka kira sallah, futowa sukai suka tafi masallaci, tun kafin su idar direban yazo yake jiran su, suna futowa daga masallaci suka wuce, Ramadan ya kalli Shahaab ya kwashe da dariya Kallan sa yayi yace "lafiya?" Ramdan yace "kawai shigarka ce tabani dariya, yau babu suit, Kaci wani jallabiya kamar balarabe" Murmushi yayi suna shiga motar Shahaab yace "aini dadin hakan nakeji, Jina nake wani iri, babu masu tsaro, babu sojoji, babu Yan sanda, sainake ganina kamar kowa" Ramdan yace "gaskiya hakane ai Naga alama jihar akwai Zaman lafiya kowa yana harkar sa babu wani tashin Hankali" Suna tattaunawa har suka Isa chai-chai, Shahaab Kam kallon mutane yake kamar yaga sabun halitta, idan yaga wani gidan Sai yaji kamar yayi kuka, Ahaka harsu ka sauka, aka hadasu Dame unguwar Garin, ya gayya to musu wasu mutanan, Shahaab da qura tafara tashi saiya nemi face-maks dinsa yasaka, shida Kansa yace "duk mutum daya abashi taliya katan biyar, macaroni katan hudu" Nan da Nan masu unguwa suka fara rabawa mutane abincin gida gida, Shima yad'auki wani Ana kaiwa dashi, Ramadan ma haka, basu suka bar Garin ba Sai daya saura, Ramadan ya kalli Shahaab yace "Abokina bakasan wani abu ba, nifa Garin Nan ya birgeni, gashi dare yayi Amma muna tafiya cikin kwanciyar Hankali babu kidnappers, babu masu fashi, babu 6arayi, Dan Allah kagani" Kafin Shahaab yayi magana Direban ya jiyo ya Kalle su yace "yalla6ai zamuje can chamo din?" Agogon hannunsa ya kalla yace "muje" Babu musu yaqara gudun motar suka dauki hanya, Sai qarfe daya da wani abu suka qarasa cikin Garin chamo, Garin yayi shiru babu motsin mutane, Shahaab ya kalli gidajen Garin yana qare musu kallo, baisan meyasa ba, Bai kuma San dalili ba haka Nan yaji gabansa yana wata irin faduwa, Bai kawo komai a ransa ba haka ya share, suka tsaya a tsakiyar Garin, duk suka futo daga cikin motar, motar datake binsu da Kayan itama ta faka Samarin dasuka zo da motar kayan suka Kalle shi "yanzu yalla6ai ya za'ayi? Garin nanfa sun kwanta wallahi, zaku tafi gida ne mu saimu kwana Dasafe muraba musu kokuma akwai shawara?" Agogonsa ya kalla yace "no, kawai muraba musu, kowa idan yatashi saiya Gani da asuba" Nan da Nan suka fara rabawa, babu motsin kowa saina su, wasu suna saukewa daga cikin motar, wasu Kuma suna rabawa, Ramadan ya tsugunna yadauka yanufi wani gidan yana tunani a ransa gaskiya sahabai sunyi kokari, Kuma suna neman aljannarsu da gaske Shahaab ma dauka yayi yanufi wani gidan can daban, ya ajiye a kofar gidan, sannan ya dawo yasake dauka yakai qofar gidan Jummai qawar Hajja, sannan yasake dawowa ya dauka yakai gidan Alhaji Audu Wanda hukumar efcc ta qwacewa gidan mansa, dawowa yayi yarungumi taliya guda hudu ya jibge a kofar gidansu Aisha, Sannna yakoma zai Dauko sauran Cikin baccinta taji wani irin fitsari, cikin sauri ta tashi tad'auki buta da gudu tashige bandaki Dan kwalinta a hannu,ta tsugunna tana fitsari tana daura dankwali, mamaki take wanne irin fitsari ne wannan kodan ta dirki ruwa da yawa Bayan tadawo daga masallaci sallar tarawih dazu. Jitayi kamar an ajiye wani abu aqofar gida, mamaki ya kamata, saida tayi tsarki Sannan tafuto daga bandakin, cikin sand'a ta nufi hanyar kofar gida tana so ta leqa taga qaran menene wannan, tana zuwa bakin kyauren nasu Sai taji takun mutum, gabanta ne yafadi to kode 6arayi ne? Matsawa ta sake yi, ta sunkuya taleqa ta cikin wata yar qaramar 6ula inda kyauren yafara cire wa, mutum tagani ya tsaya a kofar gidan, Amma bataga fuskarsa ba, Adede lokacin shikuma Shahaab ya ajiye sauran macaronin daya Dauko, yana ajiyewa kwalin macaronin ya bugi kyauren, jikake garam Sai a fuskar Aisha (😂) Cikin azaba tace "wayyo goshina" Mamaki yakama Shahaab, mutum, Kuma muryar mace acikin wannan Daren? Fitilar wayarsa ya kunna, sannan yasaka Hannunsa yatura kyauren cikin mamaki yaganshi yabude alamun basuda Sakata a gidan, yana budewa Idonsa ya sauka akan dogon gashinta Wanda yarufe mata fuska, dankwalin Nata na hannunta, yayinda hannunta guda daya yake kan goshinta tana mulmula wajan data bige, gabansa ne yafadi, wannan kwa mutum ce? Wanne irin gashi ne wannan? Hannunta tad'auke daga kan goshinta ta d'ago fuskarta ta Kalle shi tace "waye?" Baisan metake fad'a ba,gaba d'aya hankalin sa, tunanin sa, dakuma Idonsa yanakan kyakykyawar fuskarta yana qare mata kallo, hannunta ya kalla yaganshi fari tas, yasake kallon hannun ko zaiga alamun shafe-shafe, Nan ma yaga babu, ya kalli Dan qaramin bakinta Mai launin pink, mamaki yasake kamashi, tayaya? wannan kyakykyawar yarinyar acikin wannan qauyen? Ganin tana magana yayi shiru yasa ta meqa hannu dede fuskarsa ta had'a hannayenta suka bata sautin d'as d'as, cikin sauri ya dawo hayyacinsa ya kalleta, cikin masifa tace "waye ya aikoka da wannan kayan?" Yayi mamaki yar qarama da'ita Amma ta'iya masifa da wani Dan qaramin bakinta kamar gidan tsuntsu, abun mamaki Wai shi ake tambaya waye? Lalle Allah daya gari bambam,dama akwai mutanan da zasuce wai basusan waye MAHMUD WAKILI ba? Baisan meyasa ba, baisan Yaya akai ba, lokaci daya ya tsinci Kansa dabin shawarar mama da Ramadan, maimakon yafada mata waye shi, saiyace "sunana SHAHAAB" Cikin 6acin rai tace "to koma de waye, Mahmud Wakili ne kaima yaturo ka Rabon kayan abinci kamar yanda yaraba a wasu jihohin ko?" Mamaki ya kamashi, Yaya akai tasan sunansa Amma batasan waye Shiba? Bai iya bata amsa ba Sai kansa daya daga mata kawai Hannu tasa ta gyara dogon gashinta yakoma baya, Cikin jin dadi tace "Alhamdulillah, dama na Dade inaso na ganshi, ka dauki tsiyarsa ka maida masa, Bama so, kafin yabamu abinci Dama can muna rayuwa, shine matsiyaci Mai Kama kudin talakawan Allah yana riqewa,Kuma dayake kama mutane yana qwace musu Kaya Shima ai abun atuhumeshi ne, tunda bamusan daga Ina yasamu kudin dayake facaka dashi ba, qila ma kudin talakawan ne, saboda haka bamaso, Kuma kakoma kafada masa muddin nahadu dashi to haduwar mu bazatai kyaub......" kafin ta qarasa ya dakatar da ita ta hanyar daga mata hannu.(✋🏻) Bai saba ganiba, Bai taba ganin Wanda ya tunkareshi fuska da fuska yafada masa baqar magana haka ba, asalima kowa girmamashi yake Ana ganin qimarsa, babu Wanda yake masa rashin kunya saide lallashi, inda ace yana candy yayi aure ya tabbatar da tuni ya haifi kamar wannan yarinyar, cikin 6acin rai da daure fuska ya matso da fuskarsa dab da Tata har sunajin hucin numfashin juna, yace"ke!!!, marar kunyar yarinya, yar qanqanuwa dake kin'iya masifa, idan naqaraji kin zagi ogana saina kakkarya qasusuwanki na zubar anan wajan, maza dauke wannan kayan kikai ciki " Mutara zuwa gobe 🙏🏻 SHAHAAB littafin kudi ne, babu tsada nera 300 ne kacal, Yar'uwa kibiya tun kafin free page yaqare. Zaki tura 300 ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Zaki tura shedar biyan kudi ta wannan number 08033300034 Mrs Usman ce✍🏻 🌸SHAHAAB🌸 (Romance) Writing By Amnah El Yaqoub Dedicated to Aisha's Name Like my Page On Facebook👇🏻 https://www.facebook.com/amnahel 11&12 Tsoro ne yakamata, idonta yayi tsilli-tsilli tana Kallan sa,duk da bata sanshi ba,yanda taga ransa ya6aci tsaf zai iya aikata abinda yafada,wani tsoron ne yasake shigarta, gashi cikin dare ne kartaje haka kawai yakasheta a banza awofi, bare taga yanda yake da kyau, bata Sani Bama ko aljani ne, to sune akace suna shigar mutane su shigo cikin su, gabanta ne yafara faduwa ganin yanda ya matso kusa da'ita kamar zai shige mata jiki Batare datace masa komai ba ta sunkuya,dogon gashinta ne ya dawo fuskarta sakamakon sunkuyawar da tayi,yasake rufe mata fuska, kwalin taliyar ta d'auka tayi ciki. Kallan ta yayi yaga yanda uban hips dinta yake juyawa,girgiza Kansa yayi, yafara magana cikin zuciyar sa, inaga fa yarinyar Nan ba mutum bace, yar qaramar yarinya da'ita Amma ta mallaki abubuwan more rayuwa, Kuma inba aljana bace tayaya yanda yakewa mutane kwarjini Amma ita baiyi mataba Sai rashin kunya take zuba masa? Kaiii Gara yayi sauri yabar gidan, idanma aljanar ce to aniyarta tabita,cikin sauri yafuto daga gidan, Aisha kuwa tana ajiye kwalin taliyar tashige cikin Dakin Hajja da sauri gabanta yana faduwa, runtse idonta tayi, Amma shi take Gani a'idon zuciyarta yanda ya matso kusa da'ita ya nuna ta da hannu, yake zare mata ido, dak! dak!! Haka gabanta yake faduwa, Allah yasa ba Gamo tayi ba, Allah yasa ba aljani ne yabude mata idoba. Sai wajan karfe hudu saura suka gama, har suka koma hotel kuwa jikinsa a sanyaye yake,maganganun yarinyar ne suke masa yawo a zuciya,saida yayi nafila sannan yayi sahur ya kwanta, da asuba kuwa tunda suka tashi basu koma bacci ba sukai shirin komawa Abuja Da asuba Abbah yana tashin su Aisha sahur, saiyaci Karo da kwalin taliya guda daya, Wanda Aisha tashigo dashi, mamaki ya kamashi, jiyake kwali ne, Amma yana ta6awa yaji nauyi, Hajja tana futowa itama ta tsaya tana Kallan sa, fita yayi daga gidan saboda hayaniya da yaji tana tashi awaje, yana zuwa bakin kofar gida yaci Karo da sauran kayan,fita yayi daga gidan inda yaga mutane Ana tsatstsaye kowa yana fadar Albarkacin bakinsa, wannan yace yaji tsayawar motoci to yayi tunanin Yan fashi ne shiyasa yaqi futowa, wannan yace kaza wannan yace kaza, haka de, Abba yajuyo yashigo da sauran, anan yaga duk mutanan gidan sun tashi, Hajja ta Kalle shi tace "mamuda ashe Wai kaji ita Me sunan qawa taji lokacin da aka ajiye kayan tafuto fitsari lokacin, to Kuma Wai kafin taje bakin qofar har Wanda ya ajiye yatafi, bataga kowa ba, shine tashigo da guda daya taji tsoro kartaje ko aljannu ne" (😲) Murmushi Abba yayi yace "ba aljannu bane Hajja, Ina Yaron Nan Dan kasuwar Nan? Me sunana?" Hajja tace "waye Dan kasuwa Kuma?" Yace "shugaban EFCC da'ake maganar sa a gidan redio yana raba kayan abinci gari-gari, ai shi nake nufi, to wai shine ya aiko wasu mutane suka raba mana muma" Fashewa da Kuka Hajja tayi tana goge hawaye da gefen zaninta, cikin kuka tace "Allahu akbar, Allah yasaka masa da alkhairi, Allah yabiya masa buqatunsa na alkhairi, mamuda kaima bancire rai zakayi kudi ba, kaima Naka kudin yana Nan tafe" (😂) Aisha ta harareta tajuya tad'auki buta da brush tayi bandaki, har Bayan gama sahur dinsu,zancen aketa maimaitawa, Garin chamo babu sunan Wanda yake yawo saina MAHMUD WAKILI 👌🏻 ****** Bayan sun koma Abuja Kai tsaye office suka wuce, saida yarage wasu ayyukan sannan yatafi gida, Bai nufi part dinsu ba, saboda yasan Idonsa idon munirat to yau babu batun daga qafa awajansa, kwana ukun Nan Dayayi jiyake kamar yayi shekara uku ne batareda mace ba. Sai Bayan Ansha ruwa yaga lafiya lafiya yakai azumin sa, sannan yatafi part din nasu, a wannan Daren munirat tagane kurenta, domin kuwa taji jiki yanda ya kamata Saide abun mamakin shine kwata kwata baiji wani canji awajanta ba, tana nan kamar de yanda yatafi yabarta,ko kadan bai samu gamsuwa ba, shiyasa Bayan yahuta saiya sake nemanta Bayan wasu awannin, Amma idan yasake maimaita wa dinma duk hakan yakeji, yayi tunanin idan yayi dayawa hakan zaisa yaji shi zam-zam, to Amma sai yaji sa6anin haka. A 6angaren munirat kuwa tayi tunanin yanda yadage yake abu daya tun farkon dare har tsakiyarsa yaji tayi masa dadi ne, saboda Shahaab irin mazan Nan ne Wanda suke shiru yayinda suka kasance da matansu, tun tana amarya takeso ta rikitashi ta karya wannan dabi'ar tasa taqin yin kukan dadi, Amma duk yanda takai da gyara haka zata jishi shiru, shi Dan sumbatun Nan ma ba yayi, bata saniba dadin tane baikai yayi kukan ba kokuma haka dabi'ar sa take, dataga sun kwashi shekaru masu tsawo Ahaka, kawai saita sallama, tabarshi a hakan dabi'ar sa take, shiyasa yanzu ma bata kawo komai acikin ranta ba, saide Bayan komai ya gama wakana ta isheshi da kukan kissa, shikuma Nan da Nan ya lalace wajan lallashin ta, ko kadan baison abinda zai 6ata ran munirat. ****** Yau satin su daya da dawowa daga jigawa, Amma tunani d'aya yabi yadameshi, yana son ya yakice maganganun da yarinyar tafad'a masa Amma yakasa, 'Dan qaramin tsaki yasaki, yafi awa daya a kwance a gadon mama, so yake tadawo yaji duminta Amma taqi dawowa tana can tana kula da Abincin da ake rabawa sadaka,Lumshe Idonsa yayi yana jin dadin yanda sanyin esi yake ratsa jikinsa, ko kadan bayajin wahalar azumin, sake sakin wani tsakin yayi Bayan tunanin yarinyar yasake fad'o masa, alqur'ani yadauka yafara karanta wa ko zai kawarda tunanin a ransa. Sai gab da shan ruwa mama tadawo, alqur'anin ya ajiye ya dawo ya kwanta akan cinyarta, Kallan sa kawai tayi takasa magana, wani lokacin idan yayi mata wani abun kamar qaramin yaro, babu yanda zatayi dashi tunda shi kadai gareta, dan haka ta share shi tad'auki remote takamo tashar Sunnah TV tana kalla, saida aka Sha ruwa sannan suka dawo falo, anan ya tarar da munirat tana hada fruit salat, suna zama kuwa ta ajiyewa kowa nasa, wannan Karon mama batayi halin Nata ba, kawai dauka tayi Tasha, kodan saboda azumi ne yasa kwana biyu tayi shiru oho. Bayan ya dawo daga sallar tarawih ma wajan mama yawuce, har lokacin suna tareda munirat, Sai wajan karfe goma sukayi mata sallama suka tafi part dinsu. Kai tsaye dakinsa yawuce yayi wanka sannan ya kwanta, so yake yayi bacci da wuri, to Amma saide me? Dan qaramin pink lips din yarinyar yake tunowa, yasake tuna yanda take tafiya da sauri zatakai kwalin taliya cikin gida gaba daya hips dinta wani irin juyawa yake, yatunada dogon gashinta Wanda yafara daukan hankalin sa. Meyasa ta tsaneshi? Meyasa take hamdala ga Rabbi saboda yace mata shi Yaron Mahmud Wakili ne? Hakan yana nufin akwai abinda ya yi mata, Kuma take neman sa ido rufe Amma bata sameshi ba, laifin meyayi dahar take fada masa cewa Shima ya kamata atuhume shi? Meyasa ta tsaneshi har haka? Wata zuciyar tace dashi yakamata kasan dalili. Gyara kwanciyar sa yayi ya dawo yana kallon p.o.p din 'Dakin, tabbas inason jin dalilan yarinyar,gashi tanada masifa Amma da alama tanada tsoro, tunda tsawa d'aya kawai yayi mata, yaga idonta yayi tsilli-tsilli kamar ace kyarat ta gudu,idan ita din marar kunyar gaske ce to tsayawa zatayi ta fuskance shi yafada, itama ta fada, ya tuna yanda take zare ido cikin tsoro, baisan lokacin da wani irin murmushi ya qwace masa ba, cikin zuciyar sa yasake cewa yar qarama... Yasake sakin wani murmushin har dimples dinsa yana futowa, a fili yace "me qaramin baki kawai...." Munirat data dade da shigowa Dakin tana fesa turaren sa,cikin iyayi tajuyo ta Kalle shi tace"My Dear ni d'in?" (😳🙊) Firgigit yayi ya dawo cikin hayyacinsa,yasaki wata nannauyar ajiyar zuciya, yaushe tashigo Dakin bai Sani ba? cikin salon basarwa yace"yes" Tareda miqa mata hannu yana daga kwancen. (kaii jama'ah, shegiya yaudara 🙄) Babu musu ta qarasa tana wani irin taku tana karkad'a jikinta, hakanne yad'auki hankalin sa, har me aukuwa ta auku, tayi tunanin zaiyi mata godia Bayan komai yagama wakana saboda dazu dazun Nan tagama shan wasu magunguna data siya wajan qawayenta, a jikin maganin ma saida akai kashedi idan kinsan kinada kishiya to karkiyi amfani dashi Dan Zaki gigita maigida. Shikam Shahaab daqyar yasamu yayi released, zuwa yanzu Kam yariga ya saduda,ya daina qorafin komai, danhaka yauma bai nuna mata komai ba. ****** Zaune suke da Hajja, tunani take a ranta hartana cizon yatsa, Sai yanzu ne takejin haushin kanta kan rashin maidawa wannan mutumin martani. daya ce mata ogonsa ne ya aiko shi, meyasa bata maida masa martani tace yaje ya fadawa ogan nasaba? Takaici yazo wuyan ta ya tsaya, Sai yanzu haushin kanta duk yabi ya isheta, mutumin datake nema ruwa ajallo Kuma yanzu tasamu Damar da saqonta zaije gareshi Amma tayi watsi da damar ta. Hajja dake Gefe tace "me sunan qawa yau me Zaki dafa mana a gidan?" Taji shiru, ita kuwa Aisha tunani ne yayi Nisa batasan ma Hajja tana yimata magana ba. Saida Hajja tata6ota tace "mesunan qawa!" Sannan ne ta kalleta, Amma batayi Mata magana ba, cikin sauri Hajja tace "idan de akan naqi yimiki kitso ne kika fara gaba Dani har Ina miki magana kina qyaleni to dauko mataji nayi Miki, saikiyi gabar da mamuda ko Hadiza"(🤭) "Hajja menene Kuma ummah da Abba na suka miki Zaki sakosu aciki?" Hajja tace "kidauko nace, ni banason mita wallahi, dama azumi ne yasa nace bazan miki ba, saboda ranar Bana Gani sosai yunwa tasa duhu duhu kawai nake Gani" Tashi tayi ta dauko mata matajin tabata, sannan ta zauna suka fara, manyan kitso suka fara guda goma, kasancewar gashin baida cika saide tsawo, Sai yarfe hannu take saboda zafi. Jummai ce tashigo gidan tasamu waje ta zauna, Bayan sun gaisa tace "Hajja babu Dan sauran abinci awajanku nabawa jikana"(😂) Hajja tace "Ina zamu samu sauran abinci jummai, muda ba Yara ne damu ba, Hadiza ta daina haihuwa, danma mamudan nawa jarumi ne gashi harda yaransa biyu, Amma ni har nayi zamani na nagama aishi kadai na Haifa, tundaga Kansa ko 6atan wata ban qara ba, Amma shi kinga yayansa biyu " Jummai tace"um aikuwa mamudan naki ya'iya haihuwa jummai, ga 'Ya'ya nan kyawawa kamar yayan larabawan labanu" Aisha da takaici ya cikata tataba sauran gashin taji saura guda biyu agama,batason jin takaicin firar Hajja da jummai Wai labanu... Can Kuma Sai jummai tace "oh nikam Hajja ya mukaji da labarin taliya, har yanzu tana nan muna Jan dafaduka da'ita, wannan yaro Allah de yabiya shi,masu kudi dazasu dinga haka dasun samu Lada awajan Allah" Hajja tace "masu kudi sunada kudi infada miki, Amma Kuma suna qara son kudin su, kiduba kiga Yan siyasa sunada kudin, wani ma har jikokin sa bazasu taba talauci ba, Amma a hakan nema suke susake Hawa kan mulki, mukuma talakawa muna Nan Sai godiar Allah, ni yanzu ko dubu talatin aka Bani ai jikinane zai fara karkarwa, wallahi zazza6i zai sakani " Jummai tace"aikuwa in hakane Hajja A'i kakarki ta yanke saqa, Ina Yaron Nan inusa me kanti na qofar gidana?" Hajja tace "wai inusa wannan me shago?" Jummai tace "shide, jiya jiyan Nan yazo ya sameni yace tunda ke aminiyata ce inyi masa hanya mana yazo wajan mesunan qawarki, Kuma Hajja A'i inde Aisha ta amince ba abunda bazai muku ba, yanada sakin hannu" Aisha tanajin haka kunya ta kamata, tatashi da gudu tatafi daki Jummai tace "laaa Hajja A'i kode harta amince ne, Naga tatafi daki cikin kunya" Hajja tace "ai mungama amincewa jummai" "to Alhamdulillah zan sameshi nafada masa, saiki fada mata idan zaizo ta dinga kwalliya, 'Dan janbakin Nan ta dinga shafawa, taci kwalliyarta da mayafi" Hajja tace "Ina me sunan qawa zata saka miki mayafi? Dan qirgen dangin take 6oyewa, Kuma kinsan Yara inde suna wannan matakin Tofa ko yayan limamai Albarka, Amma inda tana kwalliya ai samari Sai mun kori wasu,tun yanzu ma gashi anfara aike, kinsan Kuma farinjinina ta Dauko da alama, Saboda Nima alokacina saida aka kawomin Goro d'aid'ai har guda sittin"(😳) Jummai tace "to aikuwa zan fada masa dangin farinjini yake so, tun kafin wani yazo yatureshi Gara yadage, 'Dan man Nan ya dinga siyo mata tana shafawa duk Dama Naga jikar Taki fara ce sol ga hanci har baka inni mayya ce incinye kaina" (😂) Hajja tace "fada masa Kam gaskiya" Jummai tasake Kallan Hajja tace "Hajja Kuma Yaya kikayi da Goron da aka kawo miki?"(🤔) Hajja tace "ai inafada miki a makaranta ma malamai fada suke akaina, da sukaga Bana kulasu kawai saide kiga sun shirya sun Kai Goro gidanmu, Ahaka Ahaka har guda sittin kinji zancen gaskiya, Amma dayake aure rabo ne duk masu son Nan nawa babu wanda na za6a Sai uban mamuda Allah yaji qan rai " Jummai tace" ikon Allah, banta6ajin irin wannan labari nakiba ko a hikaya" Hajja takauda kanta Gefe tace"to yanzu kinji" ****** Yau Shahaab da munirat sun Lula qasar Saudia umara, munirat kamar ta zuba ruwa aqasa Tasha Dan murna, saboda tarabu da jarabar mama, yau itama de take6e itada mijinta. A hotel suka sauka, kwanansu biyar da zuwa qasar Amma munirat har wata qiba tayi, jikinta yayi wani irin fresh, kasancewar bata tafi da kayan magungunan ta Wanda ta siya awajan qawayenta ba, Sai jikinta yake sauya wa, ita akaran kanta tasan ni'ima ta saukar mata, tunda kullum cikin hutu take babu tunanin mama, saide taita cin fruit masu kyau tana kwanciya, shiyasa a kwanansu na shida tarasa gane kan Shahaab, tunda ya ratsata yaji ta sauya Nan da Nan ya rikice mata, kamar mahaukaci haka ya dinga abu daya. Yanda take samun hutu a qasar Sai take jin Dama su dauwama Ahaka,ga Kuma uwa uba Mahmud dinta yana tare da'ita, shiyasa gaba daya addu'ar ta taqare 6angare daya, wato Allah yabar mata Mahmud, ya mallaka mata zuciyar sa ya kasance ita kadai yake Gani acikin mata, duk wata mace dazata mata shamaki da mijinta to Allah yasa Shahaab ya dinga kallon ta a namiji Sa6anin Shahaab daya duqufa wajan yin addu'ah Allah yabashi 'Ya'ya nagari idan yanada rabo,saikuma mama datace masa yadinga yimata adduah Allah yasa kafin ta mutu tahadu da qawarta Aysha Sulaiman Bompai, wuni yake a masallaci yana wannan addu'ar, idan tare suka tafi da munirat gajiya take da jiransa Takoma masauqin su, shikuma daga baya Bayan yagama addu'ar sa saiya dawo shi kadai. ****** Yau gaba d'ayansu atsakar gida sukai sahur, Abba yana Gefe yana karatun alqur'ani, Ummah da jabir da Hajja suna zaune atsakar gida, Aisha kuwa adaki taci Nata abincin, saida tagama tafuto,ta bude fridge din Hajja dayake cike da qanqarar sayarwa, tad'auki ruwan Sanyi ta tsugunna tanasha, Hajja ta bita da kallo tace "kaga shafaffiya damai, inajin bata mayi sahur dinba" Jabir yace "aikuwa kamar kinsani Hajja batayiba" Hajja tace "Ahaf! Aini tabiyo, Nima fa wannan sahur din bawani damuna yayi ba, Amma jiya duk da nayi sahur azumin Nan yabani wahala, ko yaya na sunkuya kawai duhu nake Gani, duk jijiyoyin jikina saki sukayi, sallar la'asar ma a zaune nayi ta" Gaba dayansu dariya suka sa, harda Abba, Hajja kenan me abun mamaki, tace sahur bai dameta ba Amma Kuma mutumin da sahur bai dameshi ba shine yake sallah a zaune tsabar wahalar azumi, Kuma sude asaninsu da Hajja kullum Saitayi sahur, wannan ladan baya wuce ta. Ta kalli Aisha data gama shan ruwa tace "debomin ruwa a kafara na qulla nasaka a fridge, babu pure water yaqare, harna fara kewar azumi wallahi, tunda muka shiga goman qarshan Nan" Aisha tatashi zata bata ruwan tace "ai dole kiyi kewar azumi, tunda kina cafkar kudin qanqara" Sarai taji abunda Aishan tace Amma Saitayi shiru, saboda tasan tabbas tana samun kudin qanqarar, Kuma tsaf me sunan qawa zata fadawa mamuda abinda take samu kullum, danhaka Saitayi shiru taqi ta tanka mata, saima cewa da tayi "Bani ruwan sanyi a fridge Nasha jabir, wadannan masu gaggawar yanzu zakaji sun fara Kiran sallah, idan shan ruwa ne Sai sun gama Jan ajinsu sannan su kiramana sallah, Amma idan lokacin sahur ne abincin ma baya tsirga musu suke tafiya masallaci sukira sallah " Jabir yayi murmushi yad'auki ruwan yabata ****** Ana azumi na Ashirin da d'aya, sannan su Shahaab sukai shirin tafiya, munirat tasashi agaba tana so tayi wa yan'uwan ta da qawayenta tsaraba, dole yad'auki maqudan kudade yabata, tasashi ya shirya domin suje super market da boutique tayi siyaiyar acan, haka badon yasoba ya shirya suka tafi. Kai tsaye BIN DAWOOD HYPERMARKET sukaje, shide babu abunda zai siya, kawai Kallan ta yake tana za6ar duk abinda taga yayi mata. Ajiyar zuciya yasauke, yarasa meyasa yake tunanin ta, tun Bayan tahowar su daga Garin yake nema ya yakice tunanin ta a ransa Amma yakasa, gaba daya taqi barinsa ya huta, yarasa Yaya zaiyi da ransa.(🤦🏻‍♂️) Kayan yaci gaba da kalla, anan yaga wani ribbon dark green Mai masifar kyau, babu Wanda yasake fad'o masa Arai face ita, ya tuna yanda dogon gashinta yake ko ribbon babu, cikin ransa yafara magana "marar kunya 'yar qarama...." hannu yasa yad'auki ribbon din yaga ansaka shi cikin wani gida, kana Gani kasan yanada tsada, price dinsa yagani,kudin ribbon din kadai yafi kudin daya Bawa munirat tayi siyaiya dashi.(🙆🏻‍♀️) Batare da tunanin komai ba yadauka matashi. (😲🤔tabdi sorry Munirat😥) SHAHAAB littafin kudi ne,naira 300 ne kacal 👌🏻yar'uwa siyan nagari maida kudi gida, ki biya naira 300 ki karanta abinki Hankali kwance Zaki tura 300 ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Zaki tura shedar biya ta wannan number 08033300034 Amnah El Yaqoub ✍🏻 [10/09, 22:14] +234 803 697 8511: 🌸SHAHAAB🌸 (Romance) Writing By Amnah El Yaqoub Dedicated to Aisha's Name https://www.facebook.com/amnahel 13&14 'Boyeshi yayi a Bayan hannunsa, Karo na farko kenan daya fara 6oyewa matarsa wani abu, Kallan ta yayi yace "munirat idan kin gama kisameni awaje,I'm tired" Juyowa tayi tace "okay my dear five minutes" daga Nan taci gaba da tafiya tana za6ar abinda takeso tana sakawa acikin kwando. Juyawa yayi cikin sauri, yaje ya basu atm dinsa suka dauki kudin ta dollar account d'insa, sannan ya 6oye abun acikin aljihunsa, yakoma cikin mota yana jiranta. Bayan tagama siyaiyar tafuto,hotel suka koma, saida yaga tashiga wanka sannan yasaka ribbon din cikin jakar kayansa data had'a masa tun Daren jiya. Cikin dare jirginsu yatashi zuwa qasar Nigeria,Bayan sun sauka munirat Kam bacci ta kwanta, shikuma yatafi wajan mama, saida ya ganta tana bacci sannan ya dawo part dinsa. Ganin baccin munirat din yayi Nisa yasa ahankali yatashi, yabude cikin jakarsa ya dauke abun kama gashin daya siyo, yasaka shi cikin wata akwati, sannan ya danna wasu numbobi security din jikin akwatin yakoma yarufe, sannan ya ra6a gefen munirat din shima ya kwanta tareda sakin wata irin ajiyar zuciya ya Lumshe Idonsa Sai bacci. Dasafe baije wajan aiki ba, tun safe da suka tafi wajan mama bai dawo ba, munirat ce tadawo ita kadai saboda tana shirin kar6ar baqin qawayenta Wanda zasu zo mata sannu da zuwa. Sai yamma yakoma part dinsu, anan yaci Karo da baqin munirat da basu dade da zuwa ba,har hada baki suke suna gaida shi, ya amsa musu fuskarsa adan daure, sannan yawuce daki 'Daya daga cikin su mesuna meji (maijidda) tayi qasa-qasa da muryarta cikin sigar rad'a tace "tabdi, lalle munirat kina qoqari, irin wannan ingarman mijin naki yaushe wasu matan zasu iya dashi, kema fa Dan kina dagewa ne da shan magungunan damuke baki, Amma wallahi da idan ya riqeki, Sai kinyi kuka da idonki" Murmushi tayi tace"Meji kenan, to waya fada miki baya sakani kukan? Ai ranar dakuka aikomin da magungunan kasa gane Kansa nayi, Nasha wahala ranar harda kuka, har mukaje Saudia a haukace yake " Dariya suka saki harda shewa, ikee (iklima) data cika bakinta da naman kaza kasancewar tana period bata azumi, tace" ahh waya fada miki mudin na wasa ne? Ai inde kinbi wannan magungunan kina shansu akai akai, wallahi keda kishiya saide kiji anayi a maqota" Munirat tace "hmm kude kubari kawai, Bari inje insame shi, kunsan shi da shagwa6a yanzu saiya fara min rigima nabarshi shi kad'ai" Hauwi (Hauwa) tace "A a jeki Kam, adeyi ahankali kar akaryawa megida azumi, Amma fara sallamar mu dadan abun ta6awa saboda shan ruwa, saimu tafi" Tace "karki damu Hauwi, harda tsarabar ku ta Saudia zan kawo muku yanzu yanzu" tana fadar haka tajuya zuwa dakinta, sukuma suka hada ido tareda ta6e baki, kowaccensu haushi takeji Dama itace a matsayin da munirat din take. Tunda yashigo yaga munirat bata biyo shi ba, saiya kwanta agadonsa tareda d'ora Kansa akan hannayensa ya zubawa Saman Dakin ido ya fad'a duniyar tunani, tunanin sa yayi zurfi ko shewar da qawayen munirat suke yi ba yajin su. Mamakin Kansa yake, yana jinsa kamar bashi ba, haka Nan yakeji kamar ansauya shi, Bai ta6a tunanin akwai wata yarinya dazata tsaya masa a ransa Bayan munirat ba,saboda yasan Kansa, yasan bazai ta6a son wata yarinya bayantaba. To Amma meyasa tunanin yarinyar yakasa barin qwaqwalwar sa? Wata zuciyar tace dashi "may be Dan kanason Yara ne, Kuma ka ganta yar qarama kamar Baby shiyasa kake tunanin ta" Wata zuciyar Kuma tace dashi "kokuma saboda maganganun data fada Maka ba" to kuwa in hakane dole ya nemeta domin yaji dalilin dazaisa tace masa matsiyaci, Shima abun atuhume shine, shi me yayi? But ta wacce hanya zai sake ganin ta? Cikin jin haushin Kansa yace "Wai meyasa zan damu kainane, saboda wata qanqanuwar yarinya? Munirat ce tashigo Dakin Bayan ta sallami qawayenta. Jin shigowar Tata ne yasa Shima ya watsar da tunanin yarinyar, saboda shide yasan cewa ba sonta yake ba, to menene zaisa yadamu Kansa akanta? Kwanciya tayi agefen sa ta dora kanta akan dantsan hannun sa, cikin kulawa tace "tunanin mekake my Dear?" Kai tsaye yace "Haihuwa" Gabanta ne yafadi, tatashi zaune tana Kallan sa tace "My Dear haihuwa ta Allah ce, nide nasan lafiya ta kalau, Kuma kaima haka, sannan sisters dina dasukai aure kowa tana haihuwa a gidanta, Kuma my dear ni banga abunda zai saka tunani ba, kanada komai na rayuwa, meyasa zaka damu saboda haihuwa, ni Bana tunani akan haihuwa, saboda nasan lafiya ta kalau, Kuma haihuwa gadon Miji takebi ba gadon mata ba, inda gadon mata takebi to da tuni na haihu,tunda Bani kadai momy na ta Haifa ba, so nasan matsalar daga kaine, tunda mama ma Kai kadai ta Haifa......" (✋🏻)hannu kawai yadaga mata, batare daya kalleta ba yace"please Leave me alone ok?" Babu musu tatashi tafice daga d'akin Sai mita take cikin ranta, Dame ta rageshi a rayuwa? Kullum cikin neman magunguna take saboda ta gyara kanta yasamu yaji dadi, Amma duk da haka baya Gani, yaje wajan masifaffiyar tsohuwar sa ta hure masa kunne akan haihuwa, Nima zaizo ya dameni. Shikam tana fita runtse Idonsa yayi, me munirat take nufi? Kenan shine baya haihuwa ba'ita ba? Duk haqurin Dayayi akanta yake zaune da'ita shekara da shekaru bai ta6a yunqurin qarin aure ba shine take fada masa shi kadai mama ta Haifa? Tsaki yasaki yatashi yafita daga gidan gaba daya, ko ruwa baisha tareda su ba, a masallaci yasha, Bayan an idar da sallah ma bai dawo gidan ba Sai wajan shadayan dare,munirat tun tana jiran dawowar sa taji shirun yayi yawa saboda Bahaka yasa baba, saita zargi kanta, kanta tayi wa fada karfa taje yakoyi Zaman waje duk da tasan ayyukan sa bazasu barshi ba, Amma idan ya Koya lokaci daya zasu zigashi yafara neman aure, ita Kuma abinda bazata juraba kenan, shiyasa yana shigowa ta rungume shi tareda fashewa da kukan kissa, tun yana shareta har tayi nasarar shawo Kansa yahuce ****** Yau Aisha gajiya tayi da girkin, gashi Ummah batada lafiya, itama Kuma tagaji, ita Kuma Hajja tana kulada sana'ar qanqarar ta, Dan haka itama yau tayi fuska ta wuce Dakin Hajja tayi kwanciyar ta Saida Hajja tagama siyar da qanqara lokacin har hud'u na yamma ta gota sannan ta nemi waje ta zauna, taleqa daki tace "me sunan qawa, futo kije ki siyo mana Dan tattasai kidafa macaroni ko jallop ce" Cikin shagwa6a tace "wallahi Hajja nagaji sosai, jinake kamar na fadi" Hajja ta Jinjina kanta tace "ai shikkenan Naga alama yau iskanci kikeji tonima nazama yar'iska, kowa ya zauna da yunwar sa" (🤭) Aisha tace "A a Hajja, abun bekai nanba,ni Bana fada da Azumi, saide in qarshe aka kaini" daga Nan tafuto daga d'akin tasaka hannu acikin cinikin Hajja tad'auki kudin tattasan,sannan tafita taje tasiyo tadawo ta dora musu abincin ****** Kwana daya Shahaab yayi yana yaqi akan tunanin Aisha, daqyar ya'iya yin wuni daya, da yaji zuciyar sa tana so ta kawo masa tunanin yarinyar, Sai yayi sauri yad'auki wani abun dazai dauke masa Hankali,acikin kwana dayan Nan wuni yayi da jarida a hannunsa,har munirat tana mamakin sa, to Amma Kuma karatun jaridar ma daya fara zata Fado masa, baisan lokacin Dayayi wulli da jaridar ba aikuwa tayi d'aid'ai a falon nasu (😅) Yau tunda sassafe ya shirya yafita office, yanaso ya tsiri aiyuka dayawa ko hakan zaisa ya yakiceta a ransa, saide yana zuwa ma aikata suka shaida masa cewa yaune ranar dayasa zasuyi meeting akan sabbabin masu bada horo daya gayyato daga qasar Germany domin su sake wayar wa da sabbabin ma'aikatan su dasuka dauka wannan watan Kai. Hamdala yayi a ransa, yaji dadin hakan sosai saboda shaf Yama manta da wannan batun, shadaya daidai na safe suka fara meeting din. Qwararrun masu bada horon ne suke bayani cikin salon birgewa dakuma sanin makamar aiki dangane da yaqi dacin hanci da rashawa, Dafarko Kam a nutse yake, yana kallon komai daki-daki yanda yakamata, Amma basufi minti talatin ba da fara meeting din ya Lula duniyar tunanin ta....,wata zuciyar tace dashi "kotayi dinkin sallah?" Magana masu bada horon suke masa Amma inaaaa... Hankalinsa yariga yatafi, Ramadan dake gefensa yata6ashi, firgigit yayi ya dawo cikin hayyacinsa, Kansa yadafe ya kallesu yace "am.. Idan babu damuwa Dan Allah kuyi hakuri kuci gaba da metting d'in, inada wani Babban uzuri agabana" Daya daga cikin ma'aikatan efcc din yace "Amma Boss maganar dasuke fa tanada muhimmanci, yakamata ka tsaya..." Agogon hannunsa ya kalla yace "kuyi hakuri please, Babban uzuri gareni" yajuya ya kalli baqin nasu yace "mr Jone next time ok?" Kafin wani yasake magana yad'auki jacket dinsa, tareda zira hannunsa guda daya cikin aljihun wandonsa, cikin sauri yafice. Gaba d'ayansu da Kallan mamaki suka bishi, Bai ta6a yin hakan ba, kowa yasan inde akan aiki ne yana tsayawa ayi komai a gabansa, su kansu baqin basu so yatafi ba, saboda sun so ace yana Nan suka gama bayanin komai, koba komai zasu samu Jinjina daga gareshi. Ramadan ne yasake basu haquri yace "may be baida lafiya ne, Bari in bishi" Sun yarda da abunda Ramadan din yafada, tabbas Mahmud Wakili ba qalau yake ba yau. Tunda yabar Dakin meeting din nasu, Kai tsaye office dinsa yawuce yafara dube-dube cikin loka yana tunani a ransa, ba lalle ne yar qarama tayi dinkin sallah ba, wata loka yabude yafuto da kudi bandir biyu, Yan dubu dubu, aqalla zasu Kai nera dubu Dari biyu,Adede lokacin Ramadan yashigo, yayi mamakin ganin kudi ahannunsa, cikin damuwa yace "meyake faruwa ne Abokina?" Bai iya qarya ba, haka Kuma bayason yakoya yanzu, danhaka batare dawani 6oye-6oye ba yace "wata yarinya zanje nakaiwa" Ramadan Kam baisan lokacin daya kwashe da wata irin dariya ba, kujera ya gyara ya zauna yadinga dariya harda Tari. Baqin ciki ne yakama Shahaab, yazubar da kudin akan table din gabansa, sannan ya zauna a kujera ya jinginar da Kansa a jikin kujerar yana Kallan rufin office din, saida yagama dariyar sa son ransa, sannan yajuya ya kalli Shahaab, baya buqatar yayi wani bincike yasan cewa abokin nasa yagama kamuwa cikin tarkon wata yarinyar, ahankali cikin nutsuwa ta sigar lallashi yace"Shahaab kode kafara son wata yarinya ne?" Ransa ne ya6aci, cikin fishi yace" wacce irin banzar magana ce wannan Ramadan? Dama tunanin dakake akaina kenan? Yarinya qarama cefa, 'yar cikina, nama haifi wannan yarinyar, sannan Kuma.... Ba data kunya ma.... " ya qarasa maganar qasa-qasa kamar baison Ramadan din yaji, fuskar Nan yahade ta kamar sabon hadari Ramadan da yaga Shahaab bai gama yarda son yarinyar yake ba, Sai yayi haquri ya bishi a yanda yake so din, cikin hikima yace" okay,naji, kadena cewa yar cikinka, tunda ba kaine ka haifeta ba, ai Dafarko nayi tunanin budurwa kayi mana, but koma de menene kada ka nuna mata cewa Kaidin kanada Hali " "menene danna nuna mata inada kudi Ramadan?saboda me zanyi mata qarya Bayan ba sonta nake ba? Idan tagano nayi mata qarya mutunci na zubewa zaiyi a'idonta, yanzun ma abinda yasa kaga na dauki kudin Nan Ina tunanin ba lalle ne tayi dinkin sallah ba, shine zan Kai mata tayi " Ramadan yace"A'ina yarinyar take ne? Tasan Kai waye?" Girgiza Kansa yayi yace "no, bata sanni ba, tana jigawa, qauyen damuka raba kayan Azumi, harni take cewa ni abun atuhume ni ne?sainaje nasaka tafadi abinda yake ranta da bakinta" Mamaki yakama Ramadan, gashi babu damar tambaya kar abokin nasa ya harbo jirginsa,yanzu awannan qauyen Kuma cikin dare har yaga yarinyar datasa yake wannan rawar jikin? Cikin kwantar da Hankali yace "Abokina, inde wannan qauyen ne wallahi kana bata wannan kudin, guduwa zatayi, zatayi tunanin saceta kazo yi, kokuma kaidin Dan yankan kaine, tayaya zaka dauki kudi haka a fili kawai kabawa yarinya Bayan kace bata sanka ba?aikuwa kana bata wannan kudin yanzu nema zatace tabbas kaidin abun atuhumeka ne, Kayi hakuri ka dauki ko dubu biyar ne kabata, ahankali ahankali zata saba dakai harka bata kudaden masu yawa, Amma bade lokacin farko ba, tunda Naga kanaso ka taimaka mata ai nasan ganin ta kake kamar 'yarka, shiyasa kake tausayin ta, Amma Kuma yanada kyau koda abota zakayi da'ita to kasan halaiyarta kafin kufara, yakamata kasamu Mai sonka da abota ta tsakani da Allah bawai don kudinka ba " Cikin damuwa yace "Ramadan tayaya zan'iya mata kyautan dubu biyar? Kamar Almajira? Banason qarya, bazan zo daga baya tasan koni waye qarshe tamin rashin kunya ba, Gara infada mata gaskiyar koni waye, sannan inji dalilin dazaisa tacemin matsayaci, idan taqi fada Kuma sainasa ankama ta na zaneta dakyau yanda zata Dena rashin kunya" Ramadan da jikinsa yayi yayi Sanyi akan maganganun Shahaab saiya tafi duniyar tunani, tabbas Shahaab yanason wannan yarinyar koma wacece,to da alama akwai abinda yahadasu har tayi masa rashin kunya, Wanda 6acin ran hakan yasa yakasa gane sonta yake. bazai iyu yanaji yana Gani yabarshi yasake aure irinna munirat ba, Gara yafara gwada yarinyar yaga hankalin ta, to Amma shi Shahaab yadage baison qarya, ahankali yasaki ajiyar zuciya yace "zaka iya Abokina, mu gwada hakan" Badon yasoba haka ya yarda da shawarar Ramadan akan zai 6oye mata koshi waye yaje mata Ahaka, Amma da yayi niyyar yaje ya fuskance ta, yafada mata shine Mahmud Wakili ba Shahaab ba, kamar yanda yafada mata ranar, sannan Kuma yasa tafada masa dalilin ta na zaginsa, Kuma yabata kudin takar6a Dan dolenta (tofa😲) ****** Da daddare inusa yazo, yaturo wani yaro Akira masa Aisha, gaba dayansu suna zaune atsakar gida, Yaron yayi sallama yace "Wai Ana Kiran Aisha inji Inusa me Kanti" Hajja tace "hmm Kaikuwa yaro daga Kai har Inusa me katin Baku iya sakaya suna bane? Aisha haka gatsau ko dadin ji babu? To daga yau karna qaraji,jekace masa gatanan zuwa" Yaron ya amsa da "to" sannan yafita Aisha kuwa tanajin Kiran ranta ya6aci, saboda shirin tafiya sallar Ashan take yi, batason yin fashi kullum Sai taje, Kuma hakan baya hanata anjima ma karfe daya da rabi na dare tasake komawa sallar tahajjud,Amma yarasa yaushe zaizo Sai yanzu? To kode shi baya zuwa tarawih din? Hajja tace "ba kiranki ake bane me sunan qawa?" Tashi tayi tad'auki hijabin Sai turo dan qaramin bakinta take gaba, tana saka takalmi Hajja tace "zoki dauki dan ruwan Sanyi a fridge kitafi masa dashi, idan kinje Kuma kifada masa karya sake cemiki Aisha, uwarki da ubanki ma me sunan qawar Hajja suke cewa, danhaka karya sake cemiki Aisha, qawata tanada daraja ba sa'ar uwarsa bace" (😅🤭) Itade Aisha batace komai ba tad'auki ruwan tafice, da sallama ta qarasa suka gaisa, tace masa "Inusa ga ruwan Sanyi inji Hajja" Murmushi yayi yace "Haba Aisha, Inusa Kuma? Kuma kowa yana cewa Inusa kema Inusan zakice?" Tace "Tome zance?" "a a, Yunus zakice, ai awajanki sunan na daban ne" Zuciyar ta daya tace "Nima to kadena cemin Aisha, sunan qawar Hajja gareni, Kuma su Abba ma basa fadar sunan saboda irin sunan Hajja ne" "ikon Allah, to Amma Aisha arasa sunan wadda za'a saka miki Sai sunan qawar kakarki?" Tace "Um Haka Hajja taso, Kuma Nima duk abinda Hajja takeso to inaso, saboda inason kakata, itama tana sona" Murmushi yayi yace "Alhamdulillah kice Nima kinasona Kenan, tunda ai Dama kafin nazo saida akamin iso awajan Hajjan, yaushe zata fara kunun Ayar tane?akwai wani sikari (Suger) Dana dade da ajiye matashi, zan kawo miki shi saiki bata, tunda kince kina qaunar Hajja, nikuma kenake so, kinga Nima dole ne naso abinda kike so " Ahankali tace" A a mungode Amma ka barshi " "to ai kinji abinda yake had'ani dake, aini ne nayi niyyar baki,idan kikaqi kar6a ba zanji dadi ba, yanzu de Dama zuwa nayi naganki, ko zanji Sanyi araina, nasan zakije sallah, Bari nabarki haka Naga munyi kusan minti talatin, ga wannan naki ne, ki Kai a dinka miki da sallah, kudin dinkin yana ciki "yafadi haka yana bata wata baqar leda Girgiza Kai tayi tace"a a nagode Amma ka barshi" Tace "meyasa? Kode kin Rena?" Kanta ta Girgiza masa, yace "to kar6i" Hannu biyu tasa ta kar6a sannan tayi masa godia, yace "to yimin murmushi mana" Kunya ce ta kamata, tasa hannu biyu tarufe fuskarta, cikin sauri ta wuce gida Tana zuwa tabawa Hajja ledar , ta wuce ta dauki buta tayi alwala, Tai shirin tafiya masallaci Hajja ta bud'e ledar atamfa ta bayyana, da kudi nera dubu biyu, atamfar irin ledar Nan ce me sauqin kudi (labona) Hajja tasaki guda tace "Alhamdulillah, jikata tayi goshi, Hadiza, mamuda kunga abin Arziqin daya kawo mata, harda dubu biyu, tashi daya, yabata kudin albashin ta na wata guda" Abba yace "Allah yasaka masa da alkhairi" Ummah tace "ya kyauta, Allah yasa ayi damu, ai inusa bashida laifi, yana ganin girman manya duk inda yaganni saiya tsugunna yake gaisheni" ****** Yaso ace yanzu haka yana jigawa, yanaso yasake Sakata acikin Idonsa yaji dalilin dayasa take zaginsa, to Ramadan ya hanashi tafiya yace yabari su shirya sutafi tare. Shikuma Ramadan dalilin dayasa yayi haka yanaso ne sutafi tare dashi danya dinga cusa masa ra'ayin yarinyar ahankali, harga Allah so yake Shahaab yayi aure ko Shima zai samu magaji Mama ta kallashi, tunda ya dawo daga wajan aiki take lura dashi acikin tunani yake, kuma yakasa tashi yaje yayi wanka yacire wannan suit din ta jikinsa, hannu bibbiyu yayi tagumi yana kallo, Amma hankalin sa ba akan kallon yake ba,sau uku tana sauya Tasha Amma tana lura dashi ko motsi ba yayi Idonsa yana waje daya Ahankali tace "Shahaab" Cikin damuwa yajuyo ya kalleta yace "na'am mama" Tace "har yanzu baka nemomin mekula Dani ba, koka manta ne?" Maimakon yabata amsa saiya miqe tsaye, cikin damuwa yace "mama abubuwa sunmin yawa, kisa a duba miki kawai" Daga yanayin yanda yake magana kad'ai zaisa kagane yana cikin matsananciyar damuwa Ahankali tasake cewa "Shahaab" Yajuyo yace "na'am" "zonan" Abinda tace dashi kenan, babu musu ya dawo gabanta zai zauna aqasan kafet din, cikin sauri tataroshi, ya dawo kan kujera, ahankali tajashi jikinta ta rungume shi, wata irin ajiyar zuciya yasauke, yasake qanqameta, sumar Kansa ta dinga shafa masa, ahankali har wani bacci me dadi ya dauke shi Jin yasaki jikinsa yana bacci yasa tata6e baki, cikin zuciyar ta tace "banga amfanin munirat ba, mijinki yana cikin damuwa Amma ko ajikinki, yanzu haka damuwar akan office dinsu ne, tariga tasan inde akan wannan aikin nasu ne to baya kula da cikinsa ma kamar yanda yake kula da wannan office din" Kusan awarsa d'aya yana bacci, mama da Hankalinta yakoma kan kallo can qasa-qasa taji Shahaab yana cewa " 'yar qarama...., 'yar qarama...." Mamaki yakama mama, batasan lokacin data Kai dubanta gareshi ba, cikin zuciyar ta take cewa "wacece Kuma 'yar qarama?" SHAHAAB littafin kudi ne,naira 300 ne kacal 👌🏻yar'uwa siyan nagari maida kudi gida, ki biya naira 300 ki karanta abinki Hankali kwance Zaki tura 300 ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Zaki tura shedar biya ta wannan number 08033300034 Amnah El Yaqoub✍🏻 [10/09, 22:14] +234 803 697 8511: 🌸SHAHAAB🌸 (Romance) Writing By Amnah El Yaqoub Dedicated to Aisha's Name Like my Page On Facebook👇🏻 https://www.facebook.com/amnahel 15&16 Kallan sa tasake yi, itade tasan cewa Shahaab baya kula mata, yanda yad'auki son duniya ya d'orawa munirat batajin wannan 'yar qaramar dayake fad'a da mace yake, takai shekara da shekaru tana fad'a masa yanemo yarinya ya aura, Amma har Zuwa yanzu saide yace mata shida munirat Sai Allah, tarasa Yaya zatayi dashi, shiyasa ta tattara shi ta watsa. Ta6e bakinta tayi tad'auki remote tasake sauya Tasha Sai yanzu ne yayi wani juyi, yaci gaba da baccinsa, yad'ad'e yana baccin sa me dad'i cikeda mafarkin Aisha, sannan ahankali yabud'e Idonsa,mama ta Kalle shi tace "katashi?" Cikin shagwa6a yace "um" Tace "to sannu da mafarki, d'agamin cinyata" Gabansa ne yayi wata irin faduwa "karde mafarkin Dayayi yanzu mama tajishi" shiru yayi yakasa cewa komai, yasan cewa Saitayi masa tatas saboda yanda yaqi jinin a had'ashi da wata yarinyar, Amma yau gashi shine da mafarkin wata qanqanuwar yarinya, haushin Kansa ne ya kamashi, to Shima miye na mafarkin Nata? Daga kwanciya bacci, cikin baccin ma bazata barshi ya sarara ba? Mama tace "karufawa kanka Asiri Shahaab, kar aikin ku yasaka ka koma qaramin mahaukaci, toma 'yar qaramar me kake kira?" Cikin qaramar murya kamar baison magana yace "no mama kawai mafarki ne, akwai wata yar qaramar flower ne dana dad'e Ina nema" (🤭) "toshi fure har wani muhimmanci ne dashi dakuke neman sa yanzu? Wasa kakeji dashi, kaga tashi kaje kayi wanka,babu abinda munirat take Sai riqe waya, saika sata ta duba ma furen" Hamdala yayi cikin ransa ganin bata ganoshi ba,daga mata Kai yayi sannan yatashi yatafi Yana tafiya tad'auki wayarta tasa wata mata akano ta bincika mata yarinya wadda zata dinga kula da ita, Amma anan arewa takeson yarinyar, saboda ta gwada na kudu dayawa Amma babu abun Arziqi Matar kuwa cikin ladabi ta amsa mata, sannan sukai sallama ****** Yau jummai ce tazo musu gidan tunda sanyin safiya, dukansu kuwa suna gida babu Wanda yafita, Abba ma yana kwance yana jin taskar labarai a redion Aisha. Bayan sun gaisa ta nemi waje ta zauna sannan tace "Hajja A'i gulma ajali inba'ayi ba amutu, wani zance ne nazo muku dashi keda mamuda Da Hadiza, Amma kafin Nan kunada Dan magi kubani? Saboda yau dafaduka zanyi" Hajja tace "bamudashi jummai, fad'amin meyafaru?" Jummai Tace "Ina wannan bawan Allah mejin tausayi da jinqan al'uma? To dazu dazu yayata Datake kano tamin magana tace itama maqociyarta ce wata Mai kudi, tace Dan Allah ayi mata ciki yar aiki, zata turawa wata Hajiya datake zaune a Abuja yarinyar, to Amma hajiyar Abujan ance tanada mugun kudi sosai, Dan da yan kudu take dauka aiki Kuma kasancewar anga tana bada kudi kamar ruwa, Sai mutane suka fara asiri, kowa so yake dansa yaje yayi aiki a gidanta " Hajja tace" ikon Allah na kwance yafadi..., to ita kwa wannan wanne irin kudi ne da'ita haka kamar yayi?wacece? " Jummai tace"ai hajiyar Kanon tace wadda take neman yar aikin Mahaifiyar shugaban EFCC ce wannan Yaron de MAHMUD WAKILI, Wanda yamana Rabon kayan Azumi, Amma fa Ana bala'i sosai idan mutum zaiyi aiki a gidan, sannan Kuma akwai kudi sosai,Kuma ance matar tanada izzah sosai, saide Kuma duk masu aikin gidan ma kadai, suna cikin kulawa saboda akwai tsaro a gidan na sojoji da yan sanda, sannan masu aikin ma inde a gidan suke to sun riga sunyi kudi, sainake ganin ko Zaku tura mesunan qawarki, tunda zataci Tasha, ta dinga aiko muku da kudade Kuma" Hajja tayi ajiyar zuciya tace"ai jummai kin 6ata zance tunda kikace Ana bala'i sosai idan mutum zaiyi aiki a gidan, menene abun bala'i a neman aiki duk dade itama mesunan qawartawa yar bala'i ce?"(🤭🤣) Jummai ta kalli Abba da Ummah tace"mamuda bakace komai ba, Hadiza kiyi magana mana" Ummah tace "nikam duk abinda Hajja tace ai ya zauna, Hajja ai itace komai na mesunan qawarta, nikam ai kawai haifarta nayi" Abba yace"gaskiya hakane Kam, saboda haka iya jummai da anyi hakuri da maganar aikin Nan, tunda de yanzu gashi inusa yafuto Kuma naga alama da gaske yake, to kawai babu damuwa zan hadata aure dashi, Nima Hankali na zaifi kwanciya, koba hakaba Hajja?" ya qarasa maganar yajuya yana Kallan Hajja Hajja tace"Gaskiya hakane Kam, idan takwarar ta taji Natura ta wata uwa duniya Abuja ma nasan bazata yafeni ba, Nasan halin Aysha Yakubu sagagi, cewa zatayi inrasa wazan tura aiki Sai takwarar ta? Nasan halin abata tsaf zata aikata, danhaka jummai ayi hakuri da wannan batu, me sunan qawa kawai zamu hadata da inusa" Jummai tace "to shikkenan Hajja, Amma Dan kunqi ne, nikam naso Aisha taje komuma wataran maje Abujan mu dandani Arziqi" Haka tadinga mita harta fice daga gidan, Sai Alokacin Aisha tasaki wata irin ajiyar zuciya, saboda harga Allah batajin zata Iya yiwa uwar wani bauta, itama Tata uwar tana buqatar kulawar ta, haka kawai saita tsallake mahaifiyar ta da Hajja tatafi tana yiwa wata mata aiki? Matar ma uwar mutumin daba birgeta yake ba, mutumin da taqi jinin taji sunansa, mutumin da saboda shi tadena jin redionta kwata kwata, bazai iyu ba (tofa🥺) ****** Yau makara sukai a sahur, saura minti shida Akira sallah Sannan suka tashi, Ahankali Aisha ta bude idonta, taga babu Wanda yatashi sahur, Kuma wani lokacin bacci yana cikin dad'i za'a tasheta ace lokacin sahur yayi, Amma yau Kuma taga ta danyi baccin sosai, hannunta ta miqa tad'auki wayar Hajja, tana ganin lokaci tazaro idonta, durowa tayi daga gadon tace "Hajja....kunyi sahur ne nice Baku tasheni ba?" Hajja tace "innalillahi wa inna ilaihirraji'un....ankira sallah ko?" Aisha tace "A a, ankusa de, waidama babu Wanda yatashi kenan?" Cikin sauri tafita taje tatashi Ummah da jabir, tasake tashin Abba, ai kowa a gurguje yatashi, Aisha yau babu batun brush, kawai bakinta ta kuskure tadauko musu kular dasuka zuba taliya aciki, da Ummah, da Hajja, da Aisha, da Jabir, gaba dayansu kowa hannu yasaka yafara ci, babu batun zubawa kowa, Abba yayi murmushi yaga yanda suka hade Kai kowa tura abincin yake, Ummah ta Kalle shi tace "kaidama ba sahur kake ba, duba mana saura minti nawa Akira sallah?" Agogonsa ya kalla yace "saura minti biyu" Cikin sauri suka qarasa cin abincin, ruwa kuwa kowa tashi yayi yake nema yanasha, kowa sauri yake inbakayi ban waje.... Suna gama shan ruwa kuwa aka kira sallah, Sai Alokacin Hajja tayi magana (😂) "Oni Aishatu... Da yanzu yau munyi shige, wannan azumin na Bana Inkayi sahur ma Yaya aka qare bare Kuma bakayi ba" Jabir ya kalleta yace "Hajja keda kikace sahur ba damunki yayi ba?" "Kai da Allah Ina nufin Alokacin danake Aysha Sulaiman Bompai kenan, yanzu kuwa Hajja A'i nake" Dariya Aisha tasaki tace "Hajja nifa jinake kun tasheni naqi tashi ne, shine kukai abunku kuka rabu Dani, ashe duka gidan yau makara mukayi" Hajja tace "aini Gara hakan ma,nasan da yanzu kina Nan kina d'ora abincin a harshanki" Cikin shagwa6a tace "kaii Hajja, aike nabiyo, kece kike cin abinci kamar bakya so" Hajja tace "wa?.... Lalle yau na yarda bakisan wacece takwararki ba, ai Aysha Yakubu sagagi, idan tanacin abinci ke kyace yar sarki ce, Aysha inda ace me kudi ce ita bansan wanne irin mulki zatayi ba, Ada canma damuna boarding school dinmu ta Goron dutse idan aka zomin visiting mukaje muka kar6i abincin da aka kawomin, wato idan muka koma daki tafara cin abincin Nan saiki dauka yar wani gwamnan ce, saboda Aysha Yakubu sagagi akwai yanga, gashi batada 6oye 6oye, saide kaji haushin ta, Amma tana fadar gaskiya komin dacinta " Jabir yasako musu baki cikin firar tasu yace"to Hajja ita qawar Taki ba'a zuwa mata visiting dinne ita? " Tace"Ana zuwa mata mana, Yan gidansu suna zuwa, idan sukazo tare muke zuwa, kawai de Alokacin ne tafi yimin rakiya gaskiya, saboda kaga a wancen lokacin iyayena sunada kudi, ita Kuma nata iyayen basuda qarfi sosai, to saiya kasance Ana zuwamin visiting din sosai, da Azumi kullum Sai ankawo min abinci daga gida, Kuma idan natashi komawa makaranta Bayan motar Sai ancika min shi taf da Kaya, harnaje nadawo Bana iya cin wani abun, direban dayake kaini makaranta idan ya saukeni har dauke min wasu kayan yake yanamin wayo yana cewa ai wannan ma ba lalle kici ba, nikuma babu wayo, Sai ince eh, to haka mukai karatun mu babu abinda yake rabani da'ita, mutane dayawa suna tunanin ma gidanmu daya, saboda Bama fada, koda munyi fada to a ranar zamu shirya, ita babu rufi, idan na 6ata mata rai fadamin take, nikuma da masifa, inhauta da fada, anan de Sai mutane sun shiga tsakani sun raba mu, Amma kabamu awa uku, saide kaga mun shirya, ko ban kulata ba, to ita Kam saita kulani, tundaga Nan da mutane suka gane halin mu, ko sunga suna fadan saisu qyalemu saboda sunsan zamu shirya" Aisha tace"to Hajja bakida photon tane kinuna mana? " Tace"inada shi mana, yana cikin adaka ta aqasan gado na, zan nuna miki takwararki, har saurayinta na makaranta ma duk inada photon sa, Shima zan nuna miki " Cikin sauri Aisha tace"au Hajja har soyaiya kuke a makaranta? " Hajja tace" emana, kafin muyi candy kowacce tanada saurayi, mudinga rubuta wasiqa muna aika musu, suma suna aiko mana, Bayan munyi candy ne Kuma muka rabu da samarin kowa tafara tunanin aure, ni muka dawo jigawa, ita Kuma suna kano " Jin ankira sallar asuba yasa firar tasu ta tsaya, Abba yatafi masallaci, sukuma kowa yafara kokarin daura Alwala. ****** Yau saura kwana uku sallah, tunda sassafe yatashi yayi wanka, yadauko suit takai Kala biyar, duk wadda yad'aga saiya ga batayi ba, daga qarshe yasaka wata ruwan toka wadda ta qarfi fatar jikinsa Yayi mutuqar kyau shi Kansa daya kalli Kansa a mirror yasan yayi kyau, murmushi yayi yad'auki turarensa yafara feshi dashi ajikinsa Munirat data shigo Dakin saita zubawa sarautar Allah ido tana kallo Cikin mamaki tace "my Dear yanaga ka zubar da kayaiyaki akan gado, lafiya?" Batare daya kalleta ba yace "naza6i Wanda zan saka ne" "to yanzu duk wannan daka zubar akan gadon basu Maka ba? Dubafa kagani harda suit din Dana siyoma a Cairo" Yatsina fuska yayi sannan ya kalleta yace "wannan naza6a" Hannu tasa a qirjinta ta hardesu, sannan ta fuskance shi sosai tace "zakaje wajan Mr President ne?" Gabansa ne yafadi, Sai alokacin yadago Kansa ya kalleta "no, zamuje jigawa nida Ramadan,ganin aikin gidan marayun Nan" Wata wawuyar ajiyar zuciya tasaki sannan tace "Alhamdulillah....na yi tunanin wajan wata zakaje wallahi, yanda kake zuba kwalliyar Nan ai sai kasa jinina yahau, nasan inde kafita saiwata ta kallemin Kai, Amma tunda qauye zakaje, nasan banda damuwa,nasan Babu wadda tayi daidai da kalar mijina a wannan baqauyen Garin, babu ita, ba Kuma za'a yitaba" Kansa ya girgiza yace"hakane" Bakinsa yad'ora akan goshinta yasakar mata kiss, sannan yafice daga d'akin cikin sauri Kai tsaye wajan mama yatafi, ganin ta yayi tana matsa qafafunta da kanta, cikin sauri ya qaraso ya tsugunna yaci gaba da matsa mata qafa fun, Kallan sa tayi tace "masha Allah,Dan mama yau Kuma Sai Ina? Ko qasar zaka Bari Amma baka sanar Dani ba?" Murmushi yayi, dimples dinsa suka futo, yace "Wai nayi kyau ne mama?" Tace "sosai ma kuwa, kamar Ango" Murmushi yayi tare dayin qasa da Kansa, yad'ora hannunsa akan sumar Kansa ya Dan Sosa qeyarsa, sannan yace "haka munirat ma tace Wai nayi kyau, babu inda zanje mama, jigawa kawai nakeson zuwa saboda ganin aikin gidan marayun dakika sakani" Cikin farinciki mama tace "Allahu akbar, Allah yayi Maka Albarka Mahmud, yanda kakemin biyaiya kaima Allah yabaka Wanda zasuma fiyeda haka, Allah yasa kafin nabar doron duniyar Nan Inga jikokina Kuma Inga Qawata Aysha Sulaiman Bompai" Cikin sanyin jiki yace "Amin mama, Bari intafi, Ramadan yana jirana a Airport" Tace "to Allah ya dawo daku lafiya, ABINDA KAJE YI ALLAH YABAKA NASARA AKANSA" Ahankali yace "Amin mama" sannan yakama hannunta yayi kissing Bayan hannun, yafice daga falon cikin sauri, binsa tayi da kallo tana jin dadi a ranta, cikin zuciyar ta tace "Allah ka qara aramin lokacin dazanga yayan Mahmud dina...." Motoci biyu ne suka rakashi Airport, daya yana ciki, dayar Kuma sojoji ne, suna zuwa Ramadan yazo da sauri yatareshi, sannan suka qarasa cikin Airport din. Bayan sun sauka a dutse, wani direban ne yasake daukar su, Kai tsaye wajan aikin gidan marayu suka wuce, komai yayi, suna aikinsu yanda ya kamata, saida sukai sallar la'asar awajan, Shahaab ya dubi Ramadan yace "muje ko?" Ramadan yace "Ina?" Kai tsaye yace "Abinda yakawo mu" Wayarsa ce tafara ringing Kiran munirat, Bayan sun gaisa tana masa qorafi bai ta6a tafiya yaqi kiranta ba, Sai wannan tafiyar, goshinsa yadan shafa yayi shiru, shi Kansa yasan gaskiya ta fad'a masa, baisan menene yake damunsa ba yau din, haquri kawai yabata, sannan yafada mata aiki ne yamasa yawa, zasuyi waya anjima, daga Nan yakashe wayar Kallan sa Ramadan yake lokacin dayake waya da Munirat, gaskiya Shahaab ya sauya sosai, Kuma yasan cewa duk a dalilin wannan yarinyar ne, kowacce irin yarinya ce haka data sauya masa tunani lokaci daya? Shikam zai so yaga wannan yar baiwa, to matsalar Kuma shine shi yaqi yarda son yarinyar yake, Amma babu damuwa ai lokaci zai nuna komai. Shahaab yace "Ramadan bakajini bane?" Ramadan yace "najika Sarai, kaine de kunnanka yadena aiki, idonka yarufe, kwata kwata ka manta waye Kai, ka manta cewa kaine MAHMUD WAKILI...." cikin rashin fahimta yace "mekake nufi?" "Abokina kaine kace min yarinyar Nan batasan waye kaiba, asalima ce mata kayi kaidin Yaron Mahmud Wakili ne, Kuma Sarai ta ganka, Kuma yanzu Sai muje garinsu da yamma, mu parker mota aqofar gidansu, muyi magana da'ita, karka manta ita kadai ce batasan waye kaiba, bawai mutanan Garin ba, itama nayi mamaki dakacemin bata sanka ba, to yanzu kuwa muna zuwa, idan wani yaganka ya ganeka, zai fadawa na kusa dashi, Shima ya fadawa wani, dahaka mutanan qauye su taru azo wajan Mahmud Wakili ayi masa godia saboda kwanaki ya aiko musu kayan abinci, Shahaab kana buqatar privacy, karka manta a Abuja ba Kai kadai kake yawo ba, Nan dinma kwanciyar hankalin jihar ne yasa kake yawo ko'ina haka " Ajiyar zuciya ya sauke yace "to aini banga abun damuwa ba, saboda bawai zama zanyi da yarinyar har mutane suzo su taru akaina ba, kawai de Naga suna cikin yanayi na rashi, shiyasa zan taimaka mata, sannan Kuma ta fada min abinda yasa take min rashin kunya, idan batada hujja saina mata hukunci daidai da rashin kunyarta inkama gabana, shikkenan fa " Ramadan yace"idan kuwa ka temaka mata ai zataso kudinga zumunci, ko yar wayar nan idan tana cikin halin buqata zata Iya kiranka ai, kayi hakuri muje da daddare yafi sirri gaskiya, babu wanda yasan munje, babu Wanda yasan mundawo" Badon ransa yasoba haka yayi shiru, Bai qara magana ba saboda 6acin rai Wanda shi Kansa baisan dalilin hakan ba, Ramadan yadan juyo ya Kalle shi qasa-qasa dariya ta kamashi ganin yanda abokin nasa yahad'e girar sama data qasa Karfe biyar na yamma suka koma masauqin su, saida aka Sha ruwa, suka huta, wajan qarfe bakwai da rabi suka futo, Ramadan ne yake driving, shikam Shahaab a sonsa, driver yakawo su, Amma Ramadan Sai yaqi yarda yace babu damuwa shi zai kawo su Garin. Haka suka taho su biyu, da tambaya da komai Allah yakawo su Garin CHAMO, mutane dayawa Sai kallon motar suke saboda yanda take daukan ido tana wani irin qyalli na sabunta, Ramadan ya juyo ya Kalle shi yace "inane gidan?" Kalle-Kalle yafara, can yace "danyi gaba kadan" Ramadan yayi gaba, yasamu wani waje can Gefe ya Parker mota, Shahaab ya kalli Ramadan yace "Anya ba zamu koma ba kuwa Ramadan? Gabana faduwa yake, karnaje aljana ce" Ramadan ya riqe hannunsa yace "mutum ce, duk da banganta ba nasan mutum ce, Ana daure duk wani shedanin aljani lokacin azumi, saboda haka kayi addu'ah kawai ka qarasa gidan" "tokai bazakaje ba?" Ramadan yace "Ina jiranka amota, ka dauki Bluetooth dinka saimu dinga magana ta waya" Girgiza masa Kai yayi, sannan yasaka hannu yabude gidan Bluetooth din yad'auki guda daya,yacire jacket din suit din jikinsa, yacire Agogonsa Mai tsada, niktie din wuyansa ma yacire shi, Jiyayi botir din gaban rigar tasa ya kamashi, yasaka hannu ya6alle guda uku, Nan da Nan kuwa lallausar sumar qirjinsa tafara bayyana kadan, saida yagama gyarawa tsaf sannan yafita daga motar yana tunani a ransa yaushe zai iya bata kyautar dubu biyar saboda ya gwadata kamar yanda Ramadan yabashi shawara? Yanzu Yaya za'ayi ya ganta?. Tafiya yake ahankali hannunsa daya zube cikin aljihun wandonsa, Sai Kalle Kalle yake kamar yana tsoron wani Wanda yasan shi ya ganshi Har yaqara so qofar gidansu Aisha, yaja ya tsaya agefen wata bishiya dake kofar gidan, yadade a tsaye awajan yana tunanin wazai tura gidan Akira masa ita?to wazaice Akira masa shida baisan sunan taba? Ramadan yakirashi yace "kakirata?" "no, Ina jiran yaro de" Yace "okay" sannan yakashe wayar Shiru shiru babu wani yaro dayazo wucewa ta qofar gidan, bishiyar yasake kalla yanemi waje ya zauna ko Allah zaisa wani Yaron yazo wuce wa, har qarfe takwas da rabi babu alamun mutum Kuma unguwar tafara yin shiru saboda sallar tarawih da aka fara mutane duk suna can suna Sallah Wani sauro ne yarafka masa cizo abayansa cikin sauri yamiqe tsaye yakai hannun sa wajan yana sosawa, tunani yafara a ransa yaushe Rabonsa ma da cizon sauro? Kafin yagama tunanin yaga wata tafuto daga gidan, hannunta d'aukeda sallaya,da alama wajan sallah zataje. Hankalinsa ne yakoma kanta, Hasken wayar Hajja dake hannun ta tana dannawa shine yasake bayyana kyakykyawar fuskarta, hijabin Nata dogo ne har qasa, yanada hula hijabin Sai hular tayiwa doguwar fuskarta kyau sosai, gabansa ne yafadi, kafin zuciyar sa tayi masa tunanin wani abu yayi sauri ya qarasa wajan tareda fuzgota can Gefe, sakamakon fuzgotan Dayayi har jikinsu yana haduwa Dana juna, wayar Hajja tayi Gefe tafadi aqasa, gabanta ne yafadi, abinda takawo ranta kawai masu satar mutane ne zasu saceta, ganin kafafun mutane sun dauke babu wani Wanda zai ceceta yasa tafara kokarin qwace hannunta daya riqe Wanda tuni yafara yimata zafi, Bayan ta qwace hannunta ta kwasa da sauri zata koma gida, cikin sauri shima yakai mata wani irin ruqo bai samu nasarar kama hannunta ba, hakan yasa hannunsa ya sauka akan Bajajjan Qugunta, baisan lokacin daya sake yimasa wani irin ruqoba,tsoro ne yasake kamata, har zuwa lokacin batasan waye ba, cikin sauri ta bud'e dan qaramin bakinta zata masa ihu,tun kafin tasaki ihun cikin sauri Shima yasaka tattausan tafin hannunsa na Dama yatoshe mata baki,hannunsa na hagu Kuma yana riqe da Qugunta, kallanta takai gareshi, lokaci d'aya tagane shi,zuba mata ido yayi yana qare mata kallo acikin duhun, haka itama shid'in take kallo. Alhamdulillah free fage yaqare💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 Yaya makomar soyaiyar Inusa Mai Kanti awajan Aisha? Yaya alaqar ta da Mahmud Wakili zata kasance? Yaya haduwar Aysha Sulaiman Bompai wato Hajja A'i, dakuma qawarta Aysha Yakubu Sagagi wato Hajiya Mama? Yaya alwashin munirat zai kasance?🤔 Ba'iya wannan ce gwagwar mayar da littafin ya qunsaba,akwai drama iri iri, Kashi daban daban, domin kuwa littafin Shahaab yazo da wani Salo na daban, kede kawai karki Bari abaki labari, bahaushe yace da abaka labari, Gara kabayar 😍 Duk me buqatar cigaban littafin SHAHAAB, zai tura nera 300 kacal👌🏻ki karanta abinki Hankali kwance 🥰 Zaki tura 300 ta wannan account din 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma kitura katin MTN na nera 300 kacal, tareda shedar biya ta wannan number 08033300034 😇 Amnah El Yaqoub ✍🏻 17&18 Cikin damuwa takira wayar mahaifiyar ta, Bayan sun gaisa da juna tace "Momy Mahmud ya sauya min gaba daya" Cikin kulawa tace "sauya wa kamar Yaya munirat? Banason shashanci, yanda Mahmud yake sonki banajin zai iya aikata miki wani abu" Cikin shagwa6a tace "momy yanzu yarage nemana, koda yayi tafiya baicika nemana kamar da ba, idan yana gida saide yayi shiru yadinga tunani, ni bansan meyake damunsa ba" "kinjiki da shirme munirat, yaushe Zaki barshi da damuwa to? Kema kinsan abinda muke samu awajansa idan kikayi watsi dashi to zamu daina samu, kici gaba da bashi kulawa, 'yar kissar Nan, kina sake janye hankalin sa, Sai kiga komai yayi daidai" "to shikkenan Momy, zanyi" "yauwa, kina Dan adana wasu abubuwan de ko?" Tace "momy wanne irin abu?" "munirat banason shirme, kina matar Mahmud Wakili Amma ace ke d'an gidajen Nan ma bakida shi, bakida wata kadara daza'a siyar miliyoyin kudade, kina zaune ba Cas, ba as, yana mutuwa bakida komai kenan saide tumunin takaba, danhaka kishiga hankalin ki" Jijjiga Kai munirat tayi, alamun ta gane inda momy tasa gaba, cikin murna tace "nagane momy, zakiji kyakykyawan bayani awajena momy, ki kulamin da kanki bye" Tafadi hakan tareda kashe wayar. (duk wacce ta karanta min novel batareda tabiya ba, nabar ta da ALLAH, domin nide ban yafe ba) ****** Hannu tasa tacire masa nasa hannun daya rufe mata baki dashi, cikin 6acin rai tace "ka qyaleni" Lokaci d'aya yasake ta,tsugunna wa tayi tad'auki wayar Hajja da screen din yasake fashewa, cikin tashin Hankali ta dora hannunta duka biyun aka tace "innalillahi..." cikin sauri ta juya zata koma gida da alama ma ta manta da mutum akusa da'ita Da sauri ya ruqo hannunta, juyowa tayi cikin fishi ta Kalli yanda yariqe mata hannu, gaba daya ma Sai mamaki ya kamata ganin yanda yake riqeta babu wata shakka ko tsoro atare dashi, ranta ne yayi baqiqqirin, ahankali tasaki ajiyar zuciya, sannan tadawo kusa dashi tace "sakarmin hannu malam, ko Bayan kama abubuwan bayin Allah Wanda basujiba basu Gani ba da ogan Naka yakeyi yanzu Kuma harda kama mutane yafara?" Wata irin iska ya furzar daga bakinsa, Bayan tunawa Dayayi ashefa yafada mata shi din Yaron Mahmud Wakili ne, to Amma shi menene laifin sa danya sa an kama kayan 6arayin Gwamnati? Meyasa take masa haka ne? Hannunsa yatura cikin aljihun wandonsa, dayan hannun Kuma yana riqe da tsintsiyar hannunta, batare daya saketa ba yace "kifadamin menene oga na yamiki?" Aisha ta Kalle shi tace "toka sakarmin hannu saina fada Maka" Hannun yasaki, sannan ya nuna mata Qasan bishiya inda ya zauna kafin tafuto, babu musu ta zauna, Shima zama yayi, yana mamakin yanda yake zaune da wannan qanqanuwar yarinyar Kuma awani gari qauye irin wannan, Aisha ta juya ta Kalle shi, cikin zazzaqar muryarta tace "Kanaji ko Yaron oga, Mahmud Wakili bashida mutunci" (🙆🏻‍♀️) Cikin sauri yajuyo ya kalleta, ransa ne ya 6aci, Amma saiya danne yace "meyasa?" Gyara zamanta tayi kamar Dama jira take ya tambayeta, cikin sauri tace "Alhamdulillah, Gara da Allah yasa ka tambayeni,kullum shi bashida aiki saide kaji yakama abubuwan mutane yarufe, kullum maganar da akeyi kenan a gidan redio, sannan Kuma ga mutane Nan mabuqata bazai taimaka musu ba, saide yabawa Yan ball, Dan Allah Kai a ganinka wannan mutunci ne? " Baqin ciki ne ya kamashi, yanzu Dama saboda wannnan dalilin yarinyar Nan take zaginsa? Jiyayi kamar ya kwada mata Mari, Kallan ta yayi akaron farko tunda suka zauna, ahankali yace"shine kawai?" Cikin sauri tajuyo tana Kallan sa sosai tace "Ina kuwa, haka yakama gidan man Alhaji Audu maqocinmu, bawan Allah gashi da taimako, kullum idan ya dawo daga kudu saiya kawo mana tsarabar kayan abinci da manja, Amma shine yasa aka kama masa gidan mansa" Tana fadar haka ta dora kanta akan qafafunta tafashe da Kuka Shahaab Sai yayi shiru yana Kallan ikon Allah, yanzu yanzu yarinya ki gama bayani Amma kifashe da Kuka? Kamar wata tsohuwa? to kode da tsofaffi take zaune? Ahankali ya motsa lips dinsa kamar bayason magana yace "Menene abun kuka? Sannan waye yafada miki Mahmud Wakili ne yakama gidan mansa? A Abuja gidan man yake?" Cikin kuka ta d'ago kanta tace "akano gidan mansa yake,kuma efcc ne suka kama masa, tunda aka kama masa har yanzu ko shinkafa kwano daya bai qara aiko mana ba, muda muke samun abinci ta qarqashin sa aimu Mahmud Wakili yacuta, Kuma insha Allah idona Idonsa saina fada masa baqar magana har ya mutu bazai manta Dani ba " Cikin ransa yace"baqar magana na nawa Kuma "(😒)Gara yatafi, yaga alama gaba daya zallar yarintace a tareda'ita Hannunsa yazura cikin aljihun sa yadauko dubu biyar, kamar yana tsoron bata yace"gashi" Kallan kudin tayi ta girgiza Masa Kai tace "um Um, ankusa idar da sallah natafi saida safe" tamiqe zata saka gudu Cikin sauri ya ruqo hannunta, sannan yamiqe tsaye, yazare wayar Hajja dake hannunta, yasaka mata kudin cikin tafin hannun, sannan yayi danne danne a wayar kamar yana neman wani abu, yabata wayar tareda cewa "kisai ice-cream" Daga haka bai qara cewa komai ba yajuya yatafi cikin sauri,saboda shi harga Allah kunyar bata kudin yake, kudin yayi qanqanta dayawa. Aisha ta riqe kudin ta bishi da kallo, harya shiga mota, suka tashi, akan idonta, cikin zuciyar ta tace "nikam inani Ina wani ice-cream, banta6a Sha Bama" Ahankali ta juya ta nufi masallaci jiki a sanyaye kamar kazarda qwai yafashe wa, tunani take aranta Yaya za'ayi ta nuna wannan kudin agida? Tace musu wa yabata? Duk da bata dubaba tasan kudi ne masu yawa,tana wannan tunanin harta ta'isa masallaci, bata samu mafita ba ****** Suna cikin tafiya Ramadan ya Kalle shi yace "kaganta ne?" Kai tsaye yace "Eh" "tafada ma abinda yasa tazageka?" Dan qaramin tsaki yasaki yace "Shirman tane kawai" "Yaya sunan tane yarinyar?" cewar Ramadan "I don't know" Yafada a gajarce Murmushi Ramadan yayi, cikin ransa yana fatan ace su sake dawowa Garin Bayan sun idar da sallar Kai tsaye gida ta wuce, Hajja tana cikin dakinta, Ummah Kuma tana Dakin Abba, danhaka saita wuce Dakin Ummah, da wayar Hajja ta haska ta duba kudin, gabanta ne yafadi, lokaci daya ta zaro idonta waje tace "dubu biyar?" Tunda take, bata ta6a riqe kudin daya Haura dubu biyu ba, Amma yau gashi Wai ita aka Bawa dubu biyar, Tome zatayi da wannan kudin? Tasan cewa idan Ummah ko Abba suka Gani kashinta ya bushe, hatta Hajja ma saita tambayeta waye yabata wannan uban kudin? Wani tunani ne yazo kanta, tasan babu me bude mata asusunta, koda tace umma ta d'auka toba ta6a mata kudi take ba, Dan haka cikin sauri tatura kudin cikin asusunta sannan tafuto ta wuce Dakin Hajja ****** Bayan sun koma hotel sunyi shirin kwanciya, yad'auki wayarsa yakira wata number, Bayan mutumin yadaga wayar Shahaab yace "Alhaji Inuwa akwai wani case din gidan Mai na wani Alhaji Audu, I don't know who his father... Please kadubamin file dinsa menene abunda yake faruwa" Alhaji unuwa yace "Angama yalla6ai, yanzu hakama Ina office akwai aikin danake, Bari aje yanzu yanzu aduba" Kashe wayar yayi batare daya ce masa komai ba Baifi minti talatin ba dayin wayar su Sai gashi Alhaji unuwa yasake kira, cikin ladabi yace "yalla6ai file dinsa baya wajan mu, anturashi Abuja, abinda bincike ya tabbatar kenan" Ahankali yace "ok" tareda kashe wayar Addu'ah yayi ya kwanta tareda Lumshe Idonsa, Sai yanzu ne yake jin wata irin nutsuwa tana shigarsa, wadda shi Kansa baisan dalili ba. Washe gari suka koma Abuja, Kai tsaye office suka wuce dagashi har Ramadan,magana yayi a duba masa file din Alhaji Audu, aka duba aka Gano, sannan suka kawo masa, saida yaduba yaga shine file din da aka kawo masa kwanaki yace akai shi wani office din suduba Kar6a yayi sannan yabawa Ramadan yace suje suyi binciken dazasu akan file din, idan sun gama saisu sanar dashi. Kasance war kwana daya baizo office ba Sai ayyuka suka taru suka masa yawa, Bai koma gida ba Sai Bayan sallar la'asar. Da daddare Bayan yagama komai, yad'auko wasu takardun mama na wasu filaye daya siya mata da kudin ta daya saka hannun Jari awani company, takardun sunkai guda goma, yasan cewa idan yabata kudin ma cewa zatayi ya ajiye, shiyasa yayi dabara yasai mata manyan filaye dasu, daya Bayan daya yagama dubasu, zai dauke kenan Sai aka kira wayarsa, yayi mamaki ganin Kiran daga office dinsu ne, Bayan ya dauka suka tabbatar masa cewa wannan file din daya basu sungama bincike akansa, tabbas kudin Alhaji Audu ne, ba kudin sata bane, ya saida wasu kadarorin sane, sannan ya Gina gidan man, umarni ya basu cewa atura file din zuwa kano, Sai asakar masa gidan mansa. Wani irin farinciki ne ya kamashi Bayan yagama wayar, shi Kansa baisan dalilin yin farincikin ba, maganar tace tafado masa Arai, "kanaji ko Yaron oga... Mahmud Wakili bashida mutunci" Murmushi yayi, yamiqe tsam yashige toilet domin watsa ruwa, kwata kwata ya manta bai dauke takardun filayen mama ba. Munirat data shigo Dakin domin kawo masa coffee,taci Karo da takardun azube atsakar d'aki, juyawa tayi ta kalli cikin Dakin kamar tana tsoron wani zai ganta, tsugunna wa tayi tadudduba takardun taga na filaye ne, mamaki ya kamata, ta ajiye coffee din hannun ta, ta sake duba takardun dakyau, take hudubar mahaifiyar ta tafado cikin ranta, cikin sauri ta dauke takardun manyan filaye guda biyu, sannan tayi gaggawar ficewa daga d'akin batare data ajiye masa coffee dinba. Shahaab kuwa ya dade yana wanka sannan yafuto jikinsa daureda towel, hannu yasa yadauke takardun batareda yasake dubasu ba, Kai tsaye yabude wata yar qaramar akwatin sa ta adana sirri, yasaka takardun agefen inda ya ajiye ribbon din daya siyowa Aisha,kallon ribbon din yayi na Yan seconds sannan yasaka wasu numbers yarufe akwatin, ya shirya tsaf, sannan yafada kan gado tareda daukar wayarsa, number daya dauka a wayarta yakamo ya zubawa ido yana kallo, cikin zuciyar sa yace "ko tayi bacci yanzu?" Har zai kirata saiya fasa, Tome zaice mata? (nikam nace idan ka kira ma dandalewa zakayi da Hajja 🤣) Ahankali yace "idan taji labarin Mahmud Wakili yasa ansaki gidan man Alhaji Audun nasu, nasan zatayi farinciki" fillo yaja yarungume a qirjinsa, da wannan tunanin bacci me dadi ya dauke shi, saida yatashi sahur mamaki ya kamashi yau meya hanashi neman munirat har yayi bacci shi kadai? (🤔) ****** Zaune suke atsakar gida, Aisha da Jummai suna tsince shinkafa, jummai ta kalli Hajja tace "Amma Hajja A'i wannan 6arawo naku da rashin kunya yake, Dan tsabar rashin mutunci ga mamuda yana kwance atsakar gida Amma har ya'iya dirowa cikin gida irin wannan me tsaro?"(🤣) Aisha takwashe da dariya tace "infada miki iya jummai nice nafara jinsa lokacin daya shigo, Ina tsugunne aqofar bandaki naji kamar andiro ta cikin bandakin, aikuwa nayi tsilak natashi nadawo kusa da Abba" Jummai tace "ahaf, to inaga Dama yasaba shigowa yana muku dauke dauke, Amma naso kun kamashi, da Sai mun Tara masa jama'ah" Kafin su bata amsa daya daga cikin jikokin ta yazo Yakirata, daga Nan tayi wa su Hajja sallama tatafi gida. Hajja tacewa Aisha"nikam da 6arawon Nan yashigo ya kwashe min kudin qanqara Aida bazanyi azumi ba gobe, wuni za'ayi Ana yaiyafa min ruwa" Ummah data futo daga daki tace "Gobe jajiberan mutane Sai shiri suke yi, azumi yatafi kamar yau muka d'auka" Aisha tace "au Wai Ummah da gaske gobe jajiberan kasuwa zataci kenan?" Hajja tace "insha Allah jibi zamuyi sallah, mun kusa muhuta, gobe Kuma kasuwa zataci, inada cinikin qanqara gobe" Aisha tace "dole ki riqe lokacin kasuwa ai, saboda kina samun kudi, larabawa suna kuka azumi zai tafi, kekuma murna kike jibi zakiyi sallah" Hajja tace "ke suma kukan munafurci suke, wannan wahalar azumin idan dan'adam yakaishi lafiya ai abun azo har gida ayi masa barka ne, insha Allah jibi sallah" Aisha tace "Wai Hajja waye yacemiki jibi sallah? Idan kuma ba'aga wata bafa?" Hajja tace "ke Bari kiji, duk masifarki daga gobe de mungama azumin Nan, ke koba'a gamaba nikam na sauke, Kuma babu uban daya Isa yasa nayi, ai kowa kabarinsa daban" Aisha tace "yanzu ma babu Wanda yahanaki saukewa, walakiri ne zai kamaki yadinga jibgarki kekadai babu me cetonki Sai Allah...." Lokaci daya Hajja A'i tafashe da Kuka, ihun datasa ne yaja hankalin wasu samari daga waje suka shigo gidan sunyi tunanin mutuwa akayi, Ummah kuwa cikin ranta cewa take innalillahi wa inna ilaihirraji'un, yau Kuma abun na Hajja yatashi, tambayarta samarin suka farayi waye yamutu? cikin kuka Hajja tace "yanzu munzali, nime sunan qawa zatayi wa fatan walakiri yakamani da jibga kamar wata kafura" Kafin su munzali subata amsa ta juya ta kalli Aisha tace "insha Allah babu abinda walakiri zaimin, fatan ki yaqare akan Hadiza da Mamuda..." hawaye ne ya taru a'idon Ummah, ahankali ta juya ta shige cikin dakinta, sumasu munzali suka Bawa Hajja haquri sannan suka juya Aisha kuwa harara ta zubawa Hajja, sannan ta wuce Dakin Hajjan kaitsaye, duk wani kayanta dayake Dakin Hajja yau saida tafitar dashi tas..., ko dankwali bata Bari ba, ta wuce ta maida shi Dakin Ummah, Ummah tana kallanta batace mata komai ba, ahankali ta zauna abakin gadon ta kalli mahaifiyar Tata tace "Ummah Dan Allah Kidena kuka saboda wannan tsohuwar, kiyi hakuri insha Allah ni nariga na yanke alaqata da Hajja, hakan bazata sake faruwa ba" Ummah batace da Aisha komai ba, abinda tasani shine idan tabiye mata suks taru suka zagi Hajja, to Ana jimawa zasu shirya da Hajjan, menene amfanin ka daurewa yaro gindi? Ita kanta tasan cewa haifar Aisha kawai tayi, Amma duk wata wahalar ta da rainon ta Hajja ce tayi, shiyasa suka shaqu, koka shiga tsakanin suma kaine zakaji kunya. ****** Kayane masu mutuqar kyau da tsada azube agaban mama, dubasu tayi sosai sannan ta ware wasu, wayarta dake gefenta ta d'auka takira Shahaab Wanda ya dawo daga wajan aiki yake shirin shiga wanka, yanaso yatafi masallaci wajan tafsir, cikin ladabi ya dauka kamar yana gabanta, munirat data gama debe kayan daya cire Sai jinsa tayi yana fadin "to mama, gatanan zuwa" Cikin zuciyar ta tace "kome take buqata Kuma? Jarababbiyar tsohuwa kawai" Kallanta yayi yace "kije inji mama" Daga Nan yawuce toilet. Bata dauki dogon lokaci ba ta wuce wajan mama, tana zuwa mama tabata kayan data ware tace "ga kayan sallarki Nan, wannan Kuma ki aikawa tsohuwa, inji Dan Albarka Mahmud Wakili" Maganar tamata ciwo, domin kuwa wani qullutun baqin ciki ne yatokare mata maqoshi, ahankali ta daga mata Kai, cikin ladabi tace "to mama mungode, Allah yaqara Arziqi" "tun kafin kizo Arziqi Kam Dama can yana qaruwa, ke kanki Arziqin ne ya janyo ki, tashi kibani waje" Wannan Karon munirat batace komai ba, tatashi tatafi. Tana zuwa Kai tsaye d'akin sa ta wuce ta zubar da kayaiyakin akan gado, sannan ta zauna aqasan gadon tafashe da Kuka, yana futowa daga wanka yaganta tana kuka, ya kalli kayan dake kan gado, sannan ya dawo da kallon sa gareta yace "menene yake faruwa?" Cikin kuka tace "yanzu abunda akemin a gidan Nan hakan adalci ne? Ni banida ikon siyo abinda nakeso kullum saide asiyo abani? Mama tayi Kane Kane akan komai nikuma anmaida ni saniyar ware" Ajiyar zuciya yasaki, baice da'ita komai ba,Dan qaramin towel din hannunsa yad'ora a lallausar fatarsa datake shinning,saida yagama goge jikinsa sannan ya zauna abakin gadon dab da munirat Ahankali yace "munirat... Mama mahaifiyata ce, nayi tunanin yanda na dauki momynki a matsayin uwa, kema hakane,wani lokacin rikicin mama harda na tsufa, ni abinda nasani arayuwata shine inason mama, Kuma inason duk abinda takeso, karki manta dede da second daya banta6a ganin fuskar mahaifi naba saide a photo, mama itace komai nawa, itace uwata, itace ubana, tamin gatanda ko mahaifina yana Raye abinda zaimin kenan, duk lokacin da mama ta 6ata miki rai kidauka momy ce ta6ata miki, babu yanda zakiyi da'ita, a koda yaushe inaso ne kitayani yimata biyaiya nasamu narabu da'ita lafiya.... Ta hanyar biyaiyar danake mata ne zaisa inshiga aljanna munirat, nikaina nasan wani lokacin Rikici ne kawai irinna mama Amma a hakan nake goyon bayanta Dan in rabu da'ita lafiya, Amma ke kin kasa gane hakan, idan momy ce ta zazzageki wazaki kaiwa qara? Babu Wanda Zaki fadawa saide ma kibata haquri, to inaso kidauki mama kamar momy, idan kikamin hakan kingama min komai munirat.... " Jikinta ne yayi Sanyi Bayan tagama Sauraron kalamansa, lokaci daya ta sauya kukan Nata ya dawo na kissa, cikin wani irin Salo tace"ainima Bahaka nake nufi ba, Ina kuka ne akan irin wariyar da mama take nunamin, yanzu wannan kayan waye zai dinka min insaka su jibi? Ai Yanzu ni a ganina mama ta wuce ace itace zata dinga siyo mana Kaya, a matsayi na namatarka ainice yakamata ace nasiyo mana, ita Kuma mama ta huta, ni bansan meyasa mama bata sona ba" Runtse Idonsa yayi, bayason jin kalmar Nan datake fada akan mama, cikin sigar lallashi yace "yanzu me kike so?" Ahankali tace "ni wannan kayan basumin ba, Kuma momy ma ta dade da dinka irinsu, saide nabawa ma'aikata su, inyaso nida momy muhaqura" Ahankali yace "a a, ki dauki kudi acikin briefcase dina, saiki siyo muku Wanda kike so, shikkenan?" Cikin murna da farinciki tace "eh, nagode my Dear" Tafadi hakan tareda rungume shi ta manna masa kiss akan lallausan lips dinsa. Cikin wata irin murya yace "Bari mana munirat azumi fa" Murmushi tayi, tazuba masa wata irin hararar masoya, sannan tafice daga d'akin. Mutara zuwa anjima, insha Allah zaku samu update 🙏🏻 To Aisha de tace ta yanke alaqa tsakanin ta da Hajja😂 Ko Yaya za'a qare akan takardun filayen mama? 🤔 Bazan tsaya Ina Allah ya'isa akan novel ba, Amma duk wacce ta karanta min littafi batareda ta biya ba nabarta da mahaliccinta, saboda nide ban yafe mataba Mrs Usman ce ✍🏻 Page 19&20 Atamfa ce turmi uku da wani yadi irinna maza Mai kyau agaban Ummah da Abba, Bayan Ummah tagama Gani tace "mukam kasan ba zamu samu dinki yanzu ba, saide Bayan sallah mesunan qawar Hajja sai takai mana, Amma Naka Dana Jabir bansani ba ko zaku iya samu" Aisha datake kwance akan gadon Ummah tana Kallan su batace musu komai ba, har yanzu idan tatuna fad'an da sukai da Hajja jiya ranta sake 6aci yake, kullum sukai fada da'ita saita sako iyayenta aciki. Kafin Abba yayi magana Hajja ta doko sallama cikin d'akin, kallanta yayi yace "Hajja sannu da zuwa" Tace "sannu mamuda, a zaune kuke?" bata jira amsar dazai bata ba tad'auki jakar kayan Aisha, Aisha tana ganin haka ta juyar dakanta Gefe ko kallon Hajja batayi ba, Hajja ta kamo hannunta tace "tashi mutafi mana mesunan qawa, duk fadan da mukai dake ai Bama raba makwanci, Amma jiya har kayanki saida kika kwashe, meyayi zafi haka? Tashi mutafi madubinki yana Nan nasake goge miki shi kiji dadin Kallan Kallan da kike" (🤭🙆🏻‍♀️) Cikin sauri Aisha tatashi, ganin irin kato6arar da Hajja takeson yimata agaban Abba, Wai mutum da abunsa danya kalla shikkenan Hajja ta dinga magana daya, saukowa tayi daga gadon tana tura baki gaba, suka futo daga d'akin Kai tsaye suka koma cikin Dakin Hajja. Suna zama Hajja tace "yanzu mesunan qawa abinda kikai ya kamata kenan? Ki hadani da walakiri, aiko maqiyi na bazai min irin wannan fatan ba" Aisha tayi shiru batace mata komai ba, Hajja tasaki ajiyar zuciya tace "shirya muje kasuwa musiyo kaji da d'an kayan miya muzo mu gyara gobe Sai ai miyar sallah dasu" Tashi tayi tad'auki hijabin ta tasaka sannan cikin qasa-qasa da murya tace "muje" ****** Yana zaune a office dinsa Bayan yagama ganin mutanan office din nasu Wanda suka masa sallama saboda tafiya garuruwan su hutun sallah, Shima tunani yake Ina yakamata ace yaje ya huta? Itace tafad'o masa, to kode ziyara zaiKai matane? Mamakin Kansa yake, duk lokacin dasuke samun hutu irin wannan babu abinda yake tunawa illa munirat, yanda zai dauketa sutafi wata qasar suje Sud'an huta sannan su dawo, Amma yau kwata kwata yakasa tunawa da'ita, cikin zuciyar sa yace "tunda ba sonta nake ba menene zai dameni dannakai mata ziyara?, to Amma idan naje mezance mata? Wancen Karon akwai dalilin daya kaini, Amma yanzu fa?" Afili ya furta "babu dalilin zuwan" duk yanda zuciyarsa taso hanashi, haka yaqi yarda, ahankali yad'auki wayarsa yadubo number ta daya d'auka ranar dayaje, batareda tunanin komai ba ya danna mata kira. ****** Suna futowa daga gida sukaga wani me adedeta, cikin sauri Hajja tace "Tsaya! tsaya!! d'an sahu" Tsayawa yayi, Aisha tace masa "kasuwa zaka qarasa damu" Yace "ba haya nake yi ba" Cikin sauri Hajja tace "haba kaikuwa yaro, Nima nasan ba hayar kakeyi ba tunda mukam agarin Nan Ina mukaga wani adedeta sahu, saboda Allah zaka kaimu saina baka 'yar nera hamsin kasayi gasara Kasha ruwa da magariba" Murmushi yayi yace "tokushigo" Shiga sukayi, sun fara tafiya kenan wayar Hajja tad'auki qara, cikin mita tace "Kai wannan jaraba da yawa take, da ranar ma baza'a bar mutum ya huta ba?" Aisha tace "to idan ba'a kiraki da rana ba cikin dare kike so a kiraki?" Cikin mita tace "aikuwa koma waye bazan dauka ba,da azumin zanji koda Kiran waya?" tafadi haka tareda kashe wayar Daga nasan bangaren mamaki ne ya kamashi, kamar fa rejecting din Kiran akayi? Metake da wayar zata katse masa kira? Wata zuciyar tace "kasani ko game takeyi?" Ahankali yace "may be" sannan yasake Dialing number, wannan Karon Kiran yana shigowa Hajja tasa hannu zata kashe Aisha tace "Bani In dauka" Babu musu Hajja ta bata wayar, ahankali cikin zazzaqar muryarta tace "Hello Salamu Alaikum" Atsaye yake, Amma yanda yaji muryar Tata tana neman kashe masa jiki, saiya nemi kujera ya zauna tareda Lumshe Idonsa A 6angaren Aisha kuwa dataji shiru saita sake cewa "Ba'a jinane? Wake magana ne?" Hajja tace "maganinki kenan, kina ganin number special kece mecewa Zaki dauka, baki Sani Bama ko masu shan jini ne" Dariyace ta kamashi, Kuma bayason taji shi, Sai yayi sauri yakashe wayar, yana cikin murmushi Ramadan yashigo office dinsa, cikin mamaki yace "Abokina lafiya?" Saboda Rabon daya ganshi yana irin wannan farincikin harya manta, ahankali ya girgiza masa Kai, sannan yace "nothing" Aisha kuwa dataji an kashe wayar, saita Bawa Hajja wayarta, me adedeta yace "Hajiya Kidena futowa da waya fa, kinganni Nan, to yau -yau dinnan nafuto daga gidan yari, Kuma satar waya ce takaini, gobe sallah idan kinsan ma zakije wajan idi toki tafi da paper da biro duk Wanda yace kibashi number ki saiki bashi paper ya rubuta miki, kema ki rubuta masa, saboda zamuyi patroll goben" Cikin sauri Hajja tasake qanqame Jakarta, tace" innalillahi.... Aikuwa Gara daka fada mana Kai 6arawo ne, tsaya ka saukemu anan " Cikin dariya yace"mama ni bazan muku komai ba, inda zan muku da tuni na zubar daku, kawai de fada muku nake ku kiyaye " Cikin tsoro tace"to mungode, Kuma zata kiyaye, kasan jikar tawa farinjini ne da'ita kamar kudi, Yanzu haka me Kiran ma inka bibiya mashinshi nintane". Suna zuwa kasuwa ya saukesu, Bai kar6i kudin su ba, godia suka masa sannan suka shige suka sayi abinda yakawo su, sannan suka juyo gida,ummah ce ta gyara kayan miyan jabir yakai wajan niqa, Aisha Kuma ta gyara kajin ta soya su, Hajja Kuma tadafa musu jallop din macaroni da sauran man da Aisha tayi suyar kajin dashi, sannan sukai wanka suka zauna kowa yana jira Asha ruwa. Washe gari sallah, karfe bakwai da rabi Aisha da jabir da Hajja A'i suka shirya suka tafi masallaci wajan sallar idi, aqafa suke tafiya ahankali suna tafe kowa bakinsa d'aukeda zikiri, jabir yana Sanye da yadi ajikinsa medan sauqin kudi, Hajja ma taci atamfar ta sabuwa wadda ta dinka da kanta, Aisha kuwa atamfar da inusa ya dinka mata, itace ajikinta, sun sanya sabon hijabi iri daya itada Hajja, Wanda Hajjan ce ta dinka musu. Suna zuwa masallacin Hajja ta dubesu tace "ikon Allah, dama wannan ne sabon masallacin da'aka Gina?" Jabir yace "shine Hajja, ga wajan mata can, saiku qarasa, idan an idar kujirani zanzo mutafi" Hajja tace "to ni yanzu wannan danqareren masallaci da Bismillah zan fara shiga kokuwa?" Aisha da taqaici ya kamata ta juya fararen idonta tace "Da zagi Zaki shiga, haba Hajja, wani lokacin kidinga abu kamar wata tsohuwa" Murmushi tayi tace "Allah sarki, mesunan qawa menene Kuma yarage? Tsufa kan ai mun tsufa, saide fatan Inga takwararki, Kuma incika da Imani" Hannunta Aisha taja batare datace komai ba, suka shige cikin masallacin, sallaya ta shimfida musu suka zauna, basu sake magana ba kowa zikiri yake cikin ransa,basu dade da zama ba wani mutum yazo yana kar6ar sadaka, Hajja ta bude gefen zaninta tabashi nera Dari, Aisha tayi murmushi tareda jijjiga Kai, cikin ranta tace "lalle Hajja yau take sallah" Bayan sun idar sun koma gida, anan sukaga har Ummah takusa kammala abinci, Aisha ce tacire hijabinta ta kama mata aikin, Nan da Nan suka gama, mutane Sai shigowa suke anata gaisawa, masu shagunan caji Sai kunna waqa suke a mp, Bayan sunci abincin Aisha tayi wa Ummah magana tana so taje gidansu Walida, abinci Hajja tabata tace "kafin ki wuce kishiga ki kaiwa jummai abincin Nan" Kar6a tayi sannan ta wuce. ****** Acan gidansu mama kuwa hidima tayi yawa, kamar Wanda ake dan qaramin biki, mama tana zaune tana ganawa da mutane masu zuwa yimata barka da sallah, kudi ne masu yawa agefen Dan qaramin fillon kujerar datake Kai, duk Wanda ya tsugunna ya kwashi gaisuwa idan yatashi tafiya haka zata dauki kudin tabashi, Shahaab kuwa bata ganshi ba, tasan yana can waje yana Fama da nasa mutanan, abinci ma bai samu damar zuwa yaci ba, Kuma tasan munirat bata nemeshi akan hakan ba, to itama dasuke zaune gida daya batazo ta gaishe taba bare tayi mata barka da sallah, batasan wacce irin mata Allah yabawa Mahmud ba, kafin tagama tunanin Nata yashigo cikin falon Nata yana Sanye cikin manyan Kaya farare tas,shadda ce dataji dinki Mai kyau da tsari, yasaka babbar Riga, hatta takalmin qafarsa fari ne, yayi mutuqar kyau kamar ka sace shi ka gudu, kasancewar baya saka manyan Kaya kullum Sai suit, Sai hakan yaqara qawata kyan halittarsa, Sai tashin qamshi yake Mai dadi, yana qaraso wa kusa da'ita duk mutanan falon suka tashi suka fice, Kallan sa tayi cikin farinciki tace "masha Allah, Mahmud kayi kyau sosai, yanda kake da kyan Nan Allah yabaka kyakykyawar amarya ku haifomin kyawawan jikoki" Inda Dane tafada masa hakan bazai ji dadi ba, Amma yanzu wani irin murmushi yayi, tana cewa kyakykyawar amarya, itace ta Fado masa, baisan Ina yarinyar ta kwaso kyau irin haka ba, saikace aljana, cikin murmushi yace "Amin mama, dafatan kinyi sallah lafiya" "Alhamdulillah Shahaab, ya munirat? Tayi sallah lafiya?" Cikin mamaki ya kalleta "kamarya? Batazo bane?" Tace "a a, nida ba nice na haife ta ba, Yaya za'ayi tazo ta gaishe ni, Amma nasan idan mahaifiyar ta tana cikin gidannan bazai iyu a kwana atashi, taqi zuwa ta gaishe ta ba" "mama kiyi hakuri, zanyi mata magana" "a a, rabu da'ita, inda Sabo ai yaci ace nasaba da halin munirat, dama kaina ke jira, inaso kasiyomin ticket,gobe zanje marad'i ganin dangin babanka, idan zakaje Kuma saika siyo mana mutafi" Cikin sauri yace "a a mama, kijeki, ni jigawa zanje" Cikin mamaki tace "jigawa Kuma?" Sai yanzu ne ya gane irin Shirman Dayayi, cikin sauri yasake cewa "Eh... Eh.... Ina nufin akan aikin gidan marayun Nan" Ajiyar zuciya ta sauke tace "to Alhamdulillah, nayi tunanin wani abun ne yataso" Ahankali yace "a a, Amma mama kwana nawa zakiyi kidawo? Kwana uku yayi?" "haba Shahaab , har yanzu de kana Nan da halinka bakason inje unguwa in zauna? Kwana biyar nakeso nayi, idan kajini shiru Kuma to sati daya zanyi" Cikin ladabi yace "to shikkenan mama, Allah ya dawomin dake lafiya,saimu fita goben Nima gobe nakeson wucewa" Tace "Allah yakaimu, tashi muje nabaka abinci" Babu musu yatashi suka nufi dinning Bayan yagama cin abinci fita yayi daga gidan, baije part dinsu ba Sai Bayan ya dawo da daddare, baiyi wa munirat maganar mama ba, yasan Bayan fitarsa zataje su gaisa, abinda bai saniba kuwa shine mama ko idon munirat bata Gani ba, washe gari karfe goma suka shirya shida mama suka tafi, Bai fadawa munirat inda zaije ba, yadai fada mata cewa sunyi tafiya shida mama, mama tayi tunanin Dasafe kafin su tafi munirat zatazo, shiru shiru bata zoba harta fidda rai, haka motoci guda biyu suka rakasu Airport, mama ta wuce Niger, shikuma yawuce Jigawa. Wannan Karon ma a hotel ya sauka, tunda yamma yake shirin tafiya wajan ta, Amma idan ya tuna maganar Ramadan cewa akwai Wanda suka sanshi agarin, Sai yaji wani irin taqaici,yanason yaganta dawuri kodan yasata agaba yadinga kallonta harya gaji, shi Kansa yarasa meyasa yake murna da zumudin zuwa wajan ta. Da daddare wata shigar yasake kamar ta jiya, manyan Kaya yasaka harda babbar riga, saide jiya shigar fararen Kaya yayi, yau Kuma light blue ne, shi Kansa daya kalli Kansa a madubi saida ya jinjinawa Hajja data iya auren kyakykyawan babansa Dan Nijar har Allah yasa Shima ya'iyo kamar baban nasa, saikuma yayiwa Allah godia bisa ni'imomin Dayayi masa, turare yafara fesawa kamar wani sabon ango, sannan yasaka face mask,yafuto a gurguje yashiga motarsa, rabonsa da driving harya manta, Sai yake jin wani irin nishadi a ransa, yana tafiya ahankali yana Sauraron yanda gidan Radio suke labarai na gaishe gaishen sallah, Ahaka harya qarasa cikin Garin, yau Garin yaga Yacika da mutane Kuma ga manyan motoci Nan alamun duk wasu wanda basa zama agarin ma sunzo gida bikin sallah, a'inda suka tsaya rannan shida Ramadan yauma anan yayi parking, face mask dinsa ya danja qasa, sannan yad'auki wayarsa yafara Kiran number ta, saida yaji tashiga sannan cikin ransa yace "yanzu da wayar akashe take Yaya zanyi? Ahankali yasake cewa" Sai inje gidan inyi sallama idan mungaisa dasu infada musu wajan yar qarama nazo"(🤭) Saida wayar takusa katsewa sannan yaji an dauka, ahankali kamar Wanda yake rad'a yace "inajiranki a kofar gida" "waye?" Shine abinda tace, cikeda tsananin mamaki Kai tsaye yace "SHAHAAB" gabantane yafadi harsaida tasa hannu akan qirjinta, idan bata manta ba mutumin dayazo da Azumi yakawo musu kayan abinci har yace mata shi Yaron Mahmud Wakili ne, shine Shahaab, toba rannan yazo ba? Meya dawo yi wajan ta? Kafin tagama tunani taji yace "I'm waiting for you" Sannan ya katse wayar, ahankali ta dauki dogon hijab dinta Wanda yazo mata har qasa,haka tafuto daga d'akin kamar kazarda qwai ya fashewa, Ummah na banda ki danhaka ta kalli Hajja tace "Hajja inada baqo a kofar gida, zanje wajan sa daga Nan natafi gidansu Walida, yanzu zan dawo" Hajja zuciyar ta daya tayi tunanin Inusa ne, Kai tsaye batare da tantama ba tace"ki gaishe ta" Tana futowa qofar gida ta hango motarsa, Kai tsaye wajan ta nufa, tana zuwa ta Qwanqwasa masa glass din motar, ahankali ya sauke glass din, yana ganinta gabansa yafadi, cikin zuciyar sa yace "yasalam!" Sannan yabude motar yafuto, ganin wajan babu mutane sosai yasa yakama hannunta yajata ta dayan site din, samun Kansa yayi da bude mata motar, sannan yasaki hannunta ya kalleta tareda nuna mata cikin motar yace "Bismillah" Kallan sa tayi,tana mamakin yanda Babban mutum dashi Amma yake bude mata mota, yakamata ace tatakawa mutumin Nan birgi akan yanda yake riqe mata hannu kamar wata matarsa, kallansa tayi wata zuciyar tana hanata shiga, Amma ganin shi din Babban mutum ne, a shekaru ma zai iyayin na Abban ta, Saitayi Bismillah tashiga, rufewa yayi, sannan ya zagaya yashiga shima ya zauna tareda rufo motar, juyowa yayi yana fuskantar ta,Kallan ta yafara kamar zai had'iyeta, fuskarta babu kwalliya Amma saiyaga tamasa kyau sosai, cikin ransa yace "yar qarama Kyakykyawa". Aisha kuwa jitayi motar wani irin sanyi, ga qamshi yana tashi, ahankali ta kama yatsun hannunta tana wasa dasu, kanta yana qasa, ko kadan takasa kallansa,wani irin kwarjini yayi mata musanman yau data ganshi cikin manyan Kaya, tana ganinsa ta Qasan idonta yanda ya zuba mata Ido kamar yanason Gano wani abu a fuskarta, Itakam tana zaune ne, Amma azahiri gabanta faduwa yake, saboda bata taba shiga mota mekyau irin wannan ba tunda take a rayuwar ta, acikin motar ma Kuma da wani namiji, ganin har yanzu yakasa yimata magana yasa tace "Ina wuni" Saitaji yayi shiru,ahankali tad'an d'ago kanta ta kalleshi tace "Ina wuni" Cikin sauri ya dawo hayyacinsa, ajiyar zuciya yasaki sannan ya gyara zamansa, ya kalleta cikin qasa-qasa da murya yace "Lafiya" Daga Nan babu Wanda yasake magana, kusan minti takwas shiru, taga babu abinda yace, Sai aikin kallonta kawai yake,ahankali ta motsa d'an qaramin lips dinta tace "zan'iya tafiya?" (tab! yaufa Ana zance anan😍🤣😂) Amnah El Yaqoub ✍🏻 Page 21&22 Cikin sigar rad'a yace mata "meyasa?" "gidansu Walida nakeso naje Dama, inaso ta rakani shago" "what will you buy?" Kai tsaye tace "biro" Mamaki ne ya kamashi, gata de yar qarama, Kuma tatashi acikin qauye, Amma tana danjin Dan qaramin turancin dayake mata, samun Kansa yayi da cewa "muje na rakaki?" Cikin sauri ta kalleshi, tab, Ina zata Iya tafiya dashi acikin Garin Nan, ai kowa kallon dazai mata daban, ahankali ta girgiza masa kanta alamun a a, sannan tasa hannu zata bude motar tafita, cikin sauri yamiqo hannunsa yad'ora akan Nata hannun da nufin hanata fita daga motar, juyowa tayi ta kalleshi har kusancin nasu yayi kusanci tana iya jiyo daddadan qamshin turaren dake tashi ajikinsa, ganin kamar tana tsorace dashi ne yasa ahankali cikin sigar lallashi yace "kina jin tsoro nane?" Girgiza masa Kai tayi, ahankali yasake cewa "to meyasa kike son ficewa daga motar?" Ahankali tace "toka matsa mana" Wani irin murmushi yasaki, sannan yadauke hannunsa dake kan Nata hannun, sosai yayi mamakin furucin ta, ita yanzu tsoro take kartaje yayi mata wani abu, Sai maganar Tata tabashi dariya saboda shi yar qaramar yarinya yake ganin ta, babu yanda za'ayi yayi mata wani abu makamancin Wanda take tunani, yana jin nishadi atare dashine idan yana tareda ita, Sai yake ganin ta kamar wata 'yarsa, inda ace a gidansa take bayajin akwai yarinyar dazata nuna mata gata, to Amma Yaya zaiyi? Allah bai bashi haihuwar ba. Cikin murmushi yace "Na matsa, shikkenan?" Kallan sa tayi, taga yanda dimples dinsa suka futo, Sai taga yayi mata kyau, ahankali tace "to intafi?" "meyasa kike son tafiya ne? Kinsan tundaga Ina nazo wajanki? To tundaga maiduguri" Zaro idonta tayi,(😳)cikin mamaki tajuyo tana fuskantar sa batama San tayi hakan ba,tace "maiduguri? Tome kazoyi Nan Garin?" Sosai yaji dadin yanda tafara sakewa dashi, cikin farinciki yace "wajanki nazo" Tace "wajena Kuma?,to meyasa?" Yace "wancen Karon nazo natafi, ban tambayeki sunanki ba, shine nazo kifada min yanzu" Cikin tsananin mamaki tace "sunana kawai? Saboda sunana kayi wannan doguwar tafiyar? aikuwa da matarka taji dalilin zuwanka wajena, dasai tayi fishi dakai" Cikin mamaki yace "waye yace miki inada mata?" Tace "aikai babba ne, nasan kanada mata, da Yara" Jikinsa ne yayi Sanyi, haka kawai saiya samu Kansa da fada mata gaskiya "banida Yara" Cikin tausayawa tace "to Allah yakawo masu Albarka, insha Allah watarana matarka zata haihu" "Wai waye yace miki inada aure ne? Ni banda aure, very soon de nakeson yin auren" Sai Bayan yafada mata hakan, Sai yake tambayar Kansa menene ma abun 6oye 6oye? Meyasa zai 6oye mata yanada mata? To Amma yanzu idan ya dawo yasake ce mata yanada aure zata raina shi, zata dinga ganinsa kamar qaramin yaro me magana biyu, danhaka kawai saiya share zancen. Aisha tad'an kalleshi tace "insha Allah zan fara azumin sitta shawwal, inyi ma addu'ah idan kayi aure Allah yabaka 'Ya'ya masu Albarka" Cikin tsananin mamaki ya kalleta, zatayi azumi tayi masa addu'ah akan Yara? Abun mamaki, munirat bata ta6a fada masa hakan ba, gashi de itace wadda zata Haifa masa yaran, Amma ko kadan haihuwar bata gabanta, ganin kallon dayake mata ne yasa tace "lafiya?" Ajiyar zuciya yasauke yace "no, babu komai, kawai... Kawai... de inajin dadin kasancewar ki atare Dani yanzu" Yafadi hakan yana Lumshe Idonsa. Yanda yafadi maganar yake Lumshe ido Sai hakan yasa taji wani iri ajikinta, cikin kunya tasa tafukan hannunta tarufe fuskarta cikeda kunya. Murmushi yayi, cikin dabara yace "Ina Alhajinku megidan Mai?" Cikin sanyin jiki tace "yana Nan, yazo sallah ma" Kansa ya Jinjina, tunda yaji batayi masa maganar gidan man ba, yasan har yanzu basu saki gidan man nasaba, Amma yayi mamaki sosai, tunda shine yabada umarni zuwa wannan lokacin ai ya kamata ace anbashi gidan mansa. Yace "aikuwa nayi wa ogana maganar gidan mansa, insha Allah zaiyi magana, nasan zasu saki gidan man" Tace "hmm, kaifa bakasan halin wannan ogan Naka bane, nafada maka bashida mutunci, uhmm... Inama zan ganshi, wallahi dasai yagane kurensa" (🙆🏻‍♀️) Runtse Idonsa yayi, cikin zuciyar sa yace "to masifar Tata tazo" Kafin yabude baki yace wani abu tace "Bari natafi, zanje Walida ta rakani siyan biro, nagode da ziyara" Ahankali yace "sunanki" Cikin murmushi tace "A'ISHA" yace "what!?" Cikin mamaki tace "meyafaru?" Cikin farinciki yace "sunan mamana gareki,kiyi hakuri bazan iya fadar sunanki ba, Amma zan dinga kiranki da Maaama" Murmushi tayi tace "nagode" Baice mata komai ba, yasaka hannunsa cikin babbar rigarsa yadauko dubu biyar din daya ware tun hotel, yace "gashi,kudinbarka da sallanki ne, duk da ba'a nunamin kwalliyarba" Rufe fuskarta tayi cikin kunya, tace "a a ka barshi nagode" Tace "banason musu, ki Kar6a, kisai chocolate, biro Kuma kibari karki siyo, zan kawo miki next time, karki kashe wayarki, zan kira ki idan nakoma masaukina, oya kar6i kitafi" Hannu biyu tasa ta karba, sannan tace "to nagode" sannan cikin sauri tafice daga cikin motar. Lumshe Idonsa yayi yana jin wani irin nishadi ta ko'ina. ****** Gidansu Walida taje, saide bata dade da zuwa ba tace gida zata tafi, kasancewar duk firar da walidan take mata bata jinta, sotake tasamu waje ta ke6e ita kadai tayi nazari akan wannan bawan Allah. Har gida Walida ta rakota, su Hajja basuyi tunanin komai ba, saboda dama gidansu walidan tace zataje, saida suka gaisa dasu Ummah sannan Walida ta musu sallama tatafi gida. Kai tsaye d'akin umman ta tatafi, kamar jira Yan nefa suke, tana shiga Dakin suka kawo wuta, kwanciya tayi akan gadon Ummah sannan ta duba kudin daya bata yauma dubu biyar ne, Nan take tafada duniyar tunani, shikam wannan wacce irin sana'ah yake dazai dinga yimata kyautar dubu biyar har sau biyu?, lalle in hakane Mahmud Wakili ba qaramin mutum bane, tunda gashi de Yaronsa ne yake yin kyautar dubu biyar, Amma kudin ai yayi yawa, mutumin Nan Dama fad'a ne yafara hadani dashi, idan nasake zagin ogansa Mahmud Wakili muka sake wani fadan daga baya yace nabiyashi kudinsa fa? Idan ma bamuyi fada ba Yaya za'ayi na tunkari iyayena da wannan uban kudin? Cikin sanyin jiki tasauko daga gadon tasaka kudin acikin asusunta, sannan Takoma Dakin Hajja tasaka mata wayar ta acaji. Yana tafiya a hanya Ramadan yakira shi, harzaiqi d'auka, saikuma yafasa yad'auki wayar, daga dayan bangaren Ramadan yace "oga jiya naje gida bansamu ganinka ba, yau Kuma nakoma madam tace min kunyi tafiya kaida mama, lafiya dai ko?" Cikin muryarsa Mai aji yace "Bana Nan naje Jigawa" Mamaki yakama Ramadan, cikin jin dadi yace "masha Allah, kacemin kaje qauye kana kokarin hada kan takardu domin bude sabon account" (🤭) Murmushi yayi yace "ba account zan bude ba, cbn zan bude, Wai mekake tunani akai nane Ramadan? Kawai zuwa nayi inji sunanta, last time ban tambayeta menene sunan taba" Ramadan yayi murmushi yace "ok nagane, to Yaya sunan qanwar tamu?" "sunan mama gareta" "Kai kai Kai, kace me Babban suna ce, to Abokina, Allah yabar zumunci tsakanin ka da Ummi" Cikin sauri Shahaab yace "no, ba ummi ba MAA-MA" Ramadan da mamaki yagama cikashi yayi murmushi yace "to d'an autan MAMA abokin MAAMA, yanzu de Sai yaushe zaka dawo?" "gobe babu inda zanje, zan huta, Ina tunanin jibi zan dawo insha Allah" "ok to shikkenan, Allah ya dawo dakai lafiya, saika dawo din" Batare daya sake maganaba yakashe wayar yaci gaba da driving, acan bangaren Ramadan kuwa murna yake, ta tabbata de Shahaab yana son yarinyar Nan, oh daga zuwa saudaya harya zare jiki yakoma batare da kowa yasani ba, ko Yaya wannan zance nasu ya kasance Bayan Shiba magana yakeba? Ko yabude baki yayi mata magana? Dariya yasaki yace "Abokina kenan, Allah yakaimu lokacin musha biki" (SHAHAAB LITTAFIN KUDI NE, IDAN KIKA KARANTA BATARE DA KIN BIYA BA NABARKI KEDA MAHALICCINKI, NIDE BAN YAFEBA) ****** Bayan yagama komai ya kwanta, yakira mama suka sake gaisawa, cikin kulawa tace "kakoma gida ne?" Cikin sigar shagwa6a yace "um Um mama ban komaba, saina huta de" Mamaki ne yakamata,tasan cewa Shahaab da munirat Sai Allah, kamar yanda Shima yake fada, Amma yau shine awani gari daban batare da munirat ba, Kuma yake fadar haka, ajiyar zuciya tasauke tace "munirat din tabiyoka ne?" Yatsina fuska yayi yace "no, bamuyi waya Bama tunda nataso, zande kirata yanzu Bayan mungama wayar nan, kawai inajin dadin inda nake ne mama, babu hayaniya, babu takurawa, babu Wanda yasan Dani, Ina rayuwa ta yanda nakeso, saina huta zan koma" Cikin tsoro mama tace "akwai Wanda zaice baisan kaba bane Shahaab? Banason damuwa, idan hutun kakeso ka shirya katafi wata qasar mana, canma ai babu Wanda yasanka, kakoma gida ka dauki matarka kutafi hutunku kamar yanda kuka saba" Cikin shagwa6a yace "mama ki kwantar da hankalin ki, babu abinda zai sameni kinji?" Tace "to shikkenan, idan kunyi wayar ka gaisheta" Tace "to mama" sannan yakashe wayar Kamar wanda aka sakawa cutar mantau, yana kashe wayar Yama manta da batun munirat kwata-kwata, cikin sauri yakira Aisha (🙆🏻‍♀️) Tana zaune agefen gadon Hajja tayi shiru tana tunanin al'amarin Shahaab, tarasa meyasa yake zuwa wajanta? Yakamata ace ta tambayeshi meyasa yake zuwa inda take? Ko wani aikin ogansa yaturo shi Garin? Wayar Hajja dake caji tad'auki qara, Hajja dake kwance atsakar gida ita dasu Ummah ta daga murya tace "me sunan qawa Bani wayar nan Ana kirana" Bakinta ta turo gaba tace "ni ake kira" Hajja tace "au to, ko inusa me shago ne?" Ahankali tace "um" tareda daga wayar Zama tayi agefen gado tanajin yanda yake magana kamar mace, ahankali tayi qasa da murya yanda su Hajja bazasu jitaba tace "Wai Kai meyasa kake magana ne kana shagwa6a kamar wani Dan auta" "mama nah nikadai ta Haifa" Cikin mamaki tace "shiyasa kake shagwa6a?" Murmushi yayi cikin shagwa6a yace "ni banyi miki shagwa6a ba" Tace "ba gashinan ka nayi ba" Lumshe idonsa yayi, yana jin wani irin dadi cikin zuciyarsa, yace "mama na kawai nakewa shagwa6a saike" "kaifa ba yaro bane" cewar Aisha "shine awajanki" Cikin mamaki tace "kamarya?" Cikin basarwa yace "babu komai, yau nahanaki bacci, ki kwanta kihuta" Babu musu tace "to Amma inaso in tambayeka, meyasa kake zuwa garinmu?" Murmushi yayi yace "ki adana tambayoyin ki, idan nadawo saiki tambayeni,insha Allah zanbaki amsa" Cikin nutsuwa tace "to nagode sosai" "Okay" shine abinda yace, tareda kashe wayar gaba dayanta, ko kadan baiyi yunkurin Kiran munirat ba, itama Kuma bata nemeshi ba. ****** Yau kwanan su mama biyu da tafiya, tunda suka tafi munirat bata kira mama awaya ba, shide Shahaab Yakirata yau da safe, Amma bata dauka ba, Shima Kuma bai sake kira ba. Da rana, masu aikin gidan suka shirya abinci kamar yanda suka sabayi idan mama tana gari, cikin takun qasaita tataho tana tafe tana danna wayarta, Kai tsaye part din maman taje, abincin da aka shirya a dinning ta bubbude, cikin masifa tace "bazan iyacin wannan abincin ba, waye yabada umarni ayi wannan girkin?" Cikin sauri daya daga cikin masu aikin ta d'ago kanta tace "Anty Idan Hajiya Mama tana nan haka mukeyi, dama kowacce rana akwai irin abincin da muke sauya wa, shiyasa yauma muka yi hakan" Cikin masifa tace "okay, to yau nice ba mama ba, kuma bazanci wannan ba, saiku dauke kuje kusan yanda zakuyi dashi, saboda tsabar samun waje Ina zaune acikin gidan ban'isa ku tambayeni menake so adafa min ba? Maza maza ku kwashe minsu daga gabana aje azubar adafa Sabo a kawomin" Cikin sauri suka kwashe abincin basu bar ko drinks ba, suna shiga kitchen suka Rasa Yaya zasuyi da abincin, daya daga cikin su ce tace "Bari nafita dashi ta kofar baya saina bayar awaje" Dukansu na'am sukai da shawarar Tata, saboda zubar da abincin kamar almubazzaranci ne, Bayan suma dasuke zaune a gidan saboda neman abincin ne yasa suka nemi aikin a gidan. Bayan sun shirya mata abinda takeso, part dinta ta wuce, akan kujera ta zauna tafara Kiran qawayenta, takira wannan takira waccan, duk da taga Kiran Shahaab, batabi ta Kansa ba, asali ma dadi taji yanda sukayi tafiyar Nan shida mama, yanzu gida ya dawo hannunta, Sai abinda takeso za'ayi, tasan suntafi Niger, inda ace de wani Garin yatafi daban to dole zata damu, saboda tana tsoron karya hadu da wata yarinyar ta dauke masa Hankali, Amma yanzu tunda tare yake da mama, batada damuwa, batada haufi akan mijinta tasan ita kadai ce acikin zuciyar sa, daga ita babu qari.(tofa🙄) Da daddare inusa yakira Aisha a wayar Hajja,sunsha hirarsu cikin kulawa, saide rabi zancen duk shine yakeyi, idan yayi mata maganar Hajja nema zaiga Nan da Nan ta ware tanata masa surutu, daga Nan ya fahimci cewa dole zai sake cusa Kansa awajan Hajja duba da yanda Ita kanta Aishan ta dauki Kakar Tata. ****** Washe gari ya shirya yatafi Abuja, tun ranar dayaje wajan Aisha har sukai waya da daddare, baisake kirantaba. Yana zuwa gida kuwa munirat Sai Gani tayi Ana shigowa da jakarsa cikin falonta, cikin mamaki tafuto daga kitchen hannunta d'aukeda apple, tace "a a, my Dear daga Ina haka babu sanarwa? Harkun dawo?" Zama yayi akan kujera tareda dora fillo akan cikin sa yace "nide nadawo, Amma mama tana can, Sai nanda 4 day's zata dawo, bata fada miki bane?" Cikin yaqe tace "Dama...dama....ba Niger kuka tafi tare ba?" Girgiza Kansa yayi, sannan yad'auki remote yana kokarin sauya Tasha, yace "tatafi ita kadai ne, nikuma naje Jigawa" Gabanta ne yayi mugun faduwa, tarasa meyasa yake zarya a wannan qauyen, zama tayi akan hannun kujerar daya kwanta tace "Wai kana nufin Kai kadai katafi jigawa? Dan Allah my dear mekake yi a wannan qauyen ne? Wajan wa kake zuwa?" Cikin mamaki yadago kyawawan idanunsa ya kalleta, sannan ya maida Kallan sa TV yace "to sarkin kishi, naje ganin aikin gidan marayu ne" Haka kawai taji zuciyarta taqi yarda da maganar tasa, cikin tsananin kishi tace "idan ma wajan wata kaje, to wallahi kafada mata nafi karfin kishi da yar qauye, mijina yafi qarfin ta" Murmushi yasaki tareda janyo ta tafado Kansa, dankwalin kanta yacire,gashin dokin datake sakawa yasakko kan fuskarta, kwata kwata yanzu jiyake gashin datake sakawar baya birgeshi, yafi son irinna Aisha, ahankali yad'ora kannata akan faffadan qirjinsa ya rungume ta tsamm ajikinsa tareda Lumshe Idonsa, wannan kishin datake yi akansa, saiya tuna masa da Aisha, sake rungume ta yayi yanaji kamar Aishan ya rungume (🙆🏻‍♀️🤭) munirat kuwa ganin irin rungumar daya mata yasa tayi shiru tareda yin luf a qirjinsa, dama akusa take, saboda kwana biyun Nan abuqace take dashi. Cikin jin dadi yace"waye ya'isa yaja da uwargida? Um? Fadamin me kike so?" Dukda itama idonta a Lumshe suke, saida jikinta ya danyi Sanyi kadan, duba da yanda koda yaushe burinsa shine tafada masa metake so? Kuma tasan cewa inda tafadi wata buqatar to babu tantama yimata ita zaiyi, ahankali tasake qanqameshi ajikinta ****** Ummah ce da Hajja suka dawo daga gidan Alhaji Audu, Bayan sunje sunyi wa matarsa murna akan gidan mansa da aka saki, suna zama Hajja ta kalli Abba dazai fita tace "mamuda kaje kayiwa Alhaji Audu murna kuwa akan gidan mansa?" "eh naje tunda safe, saide Allah yaqara kiyayewa gaba" Aisha tana jinsu gabanta yafadi, hakan yana nufin kenan da gaske Shahaab, ya fadawa ogan sa maganar gidan man Alhaji Audu? Kenan da gaske shidin Yaron Mahmud Wakili ne? Wani irin farinciki taji ya kamata, wayar Hajja ta d'auka zata kirashi, Sai Bayan takira taji wayar tasa akashe, a fili tace "Allah ya dawo dashi watarana Sai nayi masa godia" Hajja tace "me sunan qawa zoki siyomin Goro a gidan iya hansai" Futowa tayi, fuskarta d'aukeda murmushi tace "kawo kudin" Kudin tabata, Aisha ta kar6i kudin ta duba da kyau, sannan tace "Hajja riqe ashirin dinki, kudin Nan bazai kar6u ba" Hajja ta bude baki ta kalleta tace "to kawo insauya miki wannan din Sai mamuda ya rufata a qirjinsa yana yawo" (🤭🤣) Babu musu tabata, saida ta sauya mata, sannan taje tasiyo mata Goron takawo mata. Yau Kwanansa biyar da dawowa Abuja, mama kwanan ta takwas a Niger Kiran wayarta yayi, yasan duk inda take yanzu de jirginsu yakusa tasowa, Bayan ta d'auka yace "mama kun kusa tasowa ne?" Ta6e baki tayi tace "to Shahaab matar gida ta tsaneni saboda Allah Ina Naga ta dawowa?" Shiru yayi, cikin ransa yace "to akwai matsala kenan" Mama kuwa dataji yayi shiru taci gaba da cewa "matarka bata sona Mahmud, tun cikin azumi Rabon danasa ta a'idona, ranar sallah ma batazo inda nake ba, awayama bansamu matsayin data kirani tamin barka da sallah ba,haka dazanyi tafiyar Nan, batamin Allah yakiyaye ba, yau kwanana takwas awajan dangin mahaifinka nanma batamin waya ba, Nima Kuma anan duk lokacin dasuka tambayeni Ina matarka Sai ince musu bansan inda take ba, saboda Allah idan tana Sona ai zata zo Niger din tayi bikona, Amma zanyi maganin ta, Dani take zancen" Ran Shahaab idan yayi dubu Toya 6aci yau, yanzu abubuwan na munirat har yakai haka? Mahaifiyarsa? Idan yafara Bawa mama haquri qara tunzurata zaiyi, Gara yabi da'ita yanda takeso, inyaso ita Kuma munirat, su gauraya shi da'ita. Ajiyar zuciya ya sauke yace "eh gaskiya hakane mama, kinada gaskiya bakya dawo ba, inda ake sonka ai Nan kake zuwa" Mama tace "ato, Nima abinda nagani kenan, ni yanzu na tattara munirat na zubar, Ina dalili?Gara inyi zamana anan" Cikin sauri yace "a a mama, ba za'ayi hakaba, kiyi hakuri, ni zanzo indaukoki, idan kowa yaqiki aini bazan qikiba mama" Tace "yawwa, Gara kazo dinma, kazo ka nuna mata Nina haifeka" Yace "angama mama" Sannan sukai sallama, munirat ce tafado masa Arai, kina zaune gida daya da mahaifiyata Amma kikasa zuwa ki gaishe ta? Meyake damunta ne? Agogo ya kalla karfe shadaya na safe, waya yayi atanadar masa ticket din tafiya jigawa. Tashi yayi yafara zuba kayansa a wata yar qaramar jaka, yasan idan yaje Niger bazai iyu su barshi ya dawo a ranar ba, dole zai musu kwana biyu, daga Nan saiya taho da mama, Amma kafin Nan zaije ya kaiwa Aisha biro dakuma ribbon din daya siyo mata daga Saudia. Saida yagama hada komai har ribbon din yana cikin jaka, sannan munirat tashigo Dakin, ganinsa da Kaya yasa ta tambayeshi, "my dear Ina zakaje?" Fuskar sa babu alamun wasa yace "jigawa" Ranta ne ya6aci jin inda zaije, gashi bataga fuskar yimasa ihu ba. Gaba daya ya tamke fuska kamar ma haushinta yakeji, Shikuwa Shahaab abinda tayiwa mama ne yasa yake jin inda yana duka Toda ya rufe munirat da duka yau, da niyya yaqi 6oye mata inda zaije, saboda yasan ta tsani yaje jigawa, yarasa dalilin ta akan hakan. Ko Kallan inda take baiyi ba yafice yabar mata Dakin, yana fita driver yadaukeshi, Biron Dayayi order Nan suka fara zuwa ya Kar6a, sannan yawuce Airport, basu dade da zamaba jirginsu yatashi, har yanzu jin ransa yake adagule, Bayan jirginsu ya sauka wani driver ne yasake kaishi hotel, Sai Bayan yayi wanka ya huta ne sannan yayi order abinci, spoon biyu yayi, yaji abincin babu teste, tureshi yayi, sannan yafada kan gado yakira Ramadan kozai bashi shawara akan abubuwan da munirat takeyi akan mama,Amma wayarsa akashe. Dafe Kansa yayi, yarasa meyake masa dadi, Aisha ce tafado masa, ahankali yasake daukan wayar Yakirata. Bugu daya, Hajja ta dauki wayar,batayi magana ba yaji tana cewa "ke ungo wannan wayar, inajin inusa ne, dankare da shegiyar rowa, har yanzu baikawo miki kudin barka da sallah ba, tayaya ma zan dauke ki nabashi?"(🤔) Bakinta ta turo gaba, cikin shagwa6a tace "Kai Hajja Dan Allah, to Ina ruwanki da kudin dazai Bani? Naga baya Nan yaje dutse" Hajja tace "oh... Ai jinake rowar samarin zamanin ce tatashi" Cikin daki tashige, saida ta kwanta akan gado sannan tayi qasa da murya tace "Hello" "who is Yunusa?" Aisha tace "na'am?" alamun bata jishi ba Cikin wani irin 6acin rai da tsananin kishi yace "nace waye Yunusa?" Bakinta ta turo gaba kamar yana ganin ta, cikin shagwa6a tace "saurayi nanefa" Cikin masifa yace "maaama, ni kike fadawa saurayinki ne? Waye ma yabaki damar dazaki dinga magana da maza? Waye yace ki saurare shi?" Har yanzun bakinta yana gaba, tace "Hajja ce" "okay kina sonsa kenan, yar qarama dake samari zasu fara zuwa wajan ki, kema Kuma har kulashi kike tunda gashinan har wayama kunayi ko?" Tace "nito ya zanyi?" Baqin ciki ne yasake kama Shahaab, Yakirata danya danji sauqi Amma gashi yasamu wani baqin labarin, cikin masifa yace "look... Maama You know what? Idan nasake jin kince min saurayinki ne, Sai ranki ya6aci, karatu zakiyi, babu wani aure da zakiyi, ko shekara Dari kikai babu aure bazaki Rasa mijin aure ba" Cikin sauri tace "eh bazan Rasa ba Amma ai saide Tsoho" Cikin sigar lallashi yace "kenan kina son saurayinki, bazaki rabu dashi ba ko?" Murya can ciki tace "to ai Shima yana sona, Kuma yanason Hajja" Wata irin wawiyar ajiyar zuciya yasauke, domin kuwa amsar data bashi ka kadai ta'isa yasa ya gane cewa ita din ba lalle tanason Yaron ba, duk dade bata futo fili tafada masa tana son inusan ko bata sonsa ba, lalle ya kamata yad'auki mataki akan Yaron koma waye shi, bazai iyu yana abota da yarinya wani Kuma daban yazo yana soyaiya da'ita ba, a ko'ina abota gaba take da soyaiya 🙄🙄 Ahankali yace "kina gida ne?" Tace "um..." "Anjima zanzo, kibar wayarki awajanki," Tace "to" Har zai kashe, saiyace "fishi kike Dani?" Cikin shagwa6a tace "nifa ba fishi nake ba, bakaine ba kake tamin fada..." tana fadar haka Sai kuka Dafe Kansa yayi, cikin qasa qasa da murya yace "shikkenan to yi hakuri, nadena, shikkenan?" Tace "eh, saikazo" Kashe wayar yayi, yana mamakin yanda kuka baya mata wahala, kamar wanda take zaune cikin tsofaffi, kokuma yarintace take damunta waya Sani. Allah Allah yake dare yayi yatafi, jiyake kamar yana kan qaya, dazaran yatuno da maganar Yunusa Sai yaji sabon 6acin rai acikin zuciyar sa, wata zuciyar tace tokai menene abun damuwa tunda ba sonta kake ba? A fili yace "Bana sonta, Amma duk da haka ai tayi qanqanta da soyaiya yanzu" Haka yadinga zirga zirga yakasa zaune, yakasa tsaye, dare nayi, yad'auki hanyar garinsu, tun kafin a shiga sallar ishsha'i yaje Garin, inda yasaba ajiye motar sa anan yayi parking yauma, Kiran wayarta yayi, wayar na hannunta, tana dauka tace "Gani nan" Wajan Ummah taje, saboda Hajja tafita gidan qawarta jummai, cikin nutsuwa tace "Ummah zanje gidansu Walida na kar6o saqo nadawo" Ummah tace "karki dade, kinga dare yayi" Tace "to Ummah, sannan tafuto, a kofar gida taci Karo da Hajja, tace"Hajja natafi gidansu Walida yanzu zan dawo" Hajja tace "konazo narakaki?" Cikin sauri tace "A a nayafe" Hajja ta wuce cikin gidan tana mita, Aisha kuwa Kai tsaye wajansa ta nufa, yauma dakansa yafuto yabude mata motar, sannan tashiga yarufe, Shima yashiga ya zauna tareda rufe motar, kanta aqasa tace "Ina wuni" Cikin wata irin murya yace "maama" Tace "um" "bakya jin magana ta ko?" Dan qaramin bakinta ta turo gaba, bata bashi amsa ba, Sai yatsun hannunta data fara wasa dasu Cikin sigar rad'a yace "mekikeji aranki game Dani?" Ahankali tace "Babban mutum, Mai kima da mutunci a'idona" Jinjina Kansa yayi, sannan yace "Bayan wannan fa?" Cikin murna ta d'ago kanta ta kalleshi tace "saikuma godia danake so nayi ma, ansaki gidan man Alhaji Audu, kayiwa oganka godia, a tarihin rayuwa ta, yau Mahmud Wakili yayimin abinda yasakani farinciki" Murmushi yayi yace "da gaske?" Cikin farinciki tace "sosai, kafadamin, meyasa kake zuwa Garin Nan?" Batare da 6oye 6oye ba,yace "saboda ke" "nikuma?" Tace "saboda ke nake zuwa, inajin dadi idan Ina Kallan kyakykyawar fuskarki" Cikin kunya ta rufe idonta Murmushi yayi yace "Kidena kula samari, kinji ko?" Daga masa Kai tayi, ya matso kusa da 'ita yace "kinyi alqawari?" Tasake daga masa Kai,yace "tayaya zan gane kinyi min alqawari babu Wanda Zaki sake kulawa?" Yatsun hannunta tahada guda biyu sannan ta bashi tace "mu daura alqawari" Dariya ce ta kamashi, wannan abun datayi saiya tuna masa da lokacin dasuke Yara, haka suke yi shida Ramadan, saida yagama dariya sannan ya kalleta yaga tana kallon sa da mamaki, da alama bata ta6a ganinsa yana irin wannan dariyar ba, hannunsa yad'ora akan Nata, suka qulla hannun su waje daya, sannan yace "shikkenan, kiriqe min alqawari na" Tace "insha Allah,zan tafi gida, Ummah tace karna dade" Yace "Okay, gashi" yafadi hakan tareda miqa mata wani sabon biro mai mutuqar kyau, cikin wani Dan qaramin kwali Kar6a tayi, ta bude kwalin sannan tad'auki Biron tareda ajiye kwalin, cikin murna tace"nagode sosai, gaskiya yayi kyau, banta6a ganin biro Mai kyansa ba,Allah yasaka da alkhairi yaqara budi" Cikin jin dadin addu'ar data masa yace "Amin,banga kitson sallar ki ba" Cikin mamaki tace "kitso? Aini Bana kitso sosai, da sallah ma banyi kitso ba" Cikin jin dadi yace "mugani" Batare da tunanin komai ba, tad'an zame dankwalin kanta, tace "kagani?" ribbon din daya siyo mata a Saudia yadauko ya nuna mata yace "indaure miki gashin da wannan?" Tace "eh" Matsowa yayi dab da'ita, sannan ya janye hijabinta zuwa kan kafadarta, dankwalin yacire, lokaci daya yayi tozali da dogon gashinta me laushi, saida gabansa yafadi saboda ganin yawan gashin Nata, babu ribbon akan Nata, saide takame shi waje daya ta daure, zamansa ya gyara, yadan janyo kanta yad'ora akan cinyarsa, jitayi kayan nasa yana qamshi me dadi, batare da tsoron komai ba ta Lumshe idonta. Hannunsa yasaka ya warware gashin Nata, laushin dayaji a gashin ne yasa yafara shafashi ahankali,sannan yadauko ribbon din ya daure mata gashin dashi, maimakon yasaki gashin Nata, saiyaci gaba da wasa da gashin, yana shafa gefen fuskarta,yanayin daya fara tsintar Kansa aciki ne yasa ahankali yasake hade qafafunsa waje daya, but duk da hakan Sanadin dora kanta Dayayi awajan, saida ya haddasa masa shiga cikin wani yanayi. Ahankali ta d'ago kanta tace "waye yabaka ribbon?" Cikin Lumshe ido, murya a dashe yace "kena siyowa" Cikin murna tace "nagode" Kallan ta yayi, yanda ribbon din yayi mata kyau da yanda yayi mata parking din gashin Saitayi kyau kamar ba yar hausawa ba. Cikin wata irin murya yace "tashi kije gida, idan zanzo zamuyi waya okay?" Cikin jin dadi tace "to nagode" sannan tafara kokarin daura dankwalin ta Cikin mutuwar jiki yasaka hannunsa ya daura mata Dan kwalin, sannan ita Kuma taja wuyan hijabinta tamayar dashi, tayi masa sallama tatafi gida. Lumshe Idonsa yayi Bayan fitarta daga motar, saida yaji yanayin sa yadan daidaita sannan yaja motar yabar Garin. Alhamdulillah mutara zuwa gobe🙏 (to wannan mu'amula ko Yaya zata Kaya? 🤔🤔) Anya Shahaab baiyi kuskure ba akan qaryar dayake yiwa Aisha?🤔🤔 Littafin Shahaab na kudi ne,idan kika karanta min batare da kin biyaba keda mahaliccinki tunda littafi de ba tsada yayi ba,ki biya ki karanta halak dinki Bana Allah ya'isa ba, ga Wanda suke nemana su nemeni ta wannan number 08033300034 El Yaqoub ✍🏻 Tana shiga gida taga ummanta a tsakar gida tace "Ummah nadawo" batareda tajira amsar da umman zata bata ba, ta wuce Dakin Hajja Kai tsaye, batareda sanin muhimmancin Biron daya bata ba, ta jefashi cikin jakar makarantar ta, fitilar wayar takunna sannan ta matsa gaban madubi ta haska fuskarta da fitilar, juyawa tayi ta Dan kalli parking din gashinta Wanda Shahaab yayi mata, ahankali tasaka hannu ta shafa ribbon din, sannan tace "yanada kyau sosai" Hajja data futo daga bandaki ta ajiye buta tashigo dakin, ganin Aisha agaban madubi tace "to me akeyi Kuma da wannan Daren ko Kallan abun ake yau ma?" Cikin sauri ta juyo tace "eh, idan nagani ma ai nawane ko?" Hajja tace "naki ne Kam, tsaya inkar6o miki fitilar Hadiza saiki sake haskawa yanda zamufi Gani da kyau..." (😄) Hararar ta tayi, sannan tafice tabar mata d'akin. ****** Kasa bacci yayi kwata kwata, duk yanda yaso ya runtsa cikin dadin rai, kasawa yayi, Kiran wayar mama ne yashigo, cikin wata irin murya kamar ta d'an maye, wadda kanaji zakayi tunanin yana tare ne da mace, kokuma yana cikin wani yanayi,Ahaka yadauka, mama tace "Shahaab lafiya naji ka shiru baka zoba?" "zanzo gobe" yafadi hakan tareda sakin wani irin numfashi Cikin zuciyar ta tace "lafiya yake kuwa?" Afili saitace"kana tareda munirat ne? " Kai tsaye yace"Eh" Tace "to Allah yakaimu goben, saikazo" bata jira amsarsa ba takashe wayar Lumshe Idonsa yayi, tareda sake rungume fillon dake hannunsa, tsawon wani lokaci yana haka, sannan yabude Idonsa yakira number wani mutum, daga dayan bangaren akace "Barka da dare Mr Mahmud" Ahankali yace "Doctor babu wani magani dazaka Bani ne Wanda zaisa indaina jin feeling ko Yaya ne?" Doctor yace "subhanallahi, meyayi zafi haka? Tun akwanakin baya kayi min wannan tambayar nace shan magani irin wannan baida amfani, saboda kanada mata, sannan ka godewa Allah ma, kanada lafiya, samun maza irin haka, abune Mai mutuqar wahala, Kaci gaba da saka wannan panties din, suma is okay, banaso in doraka akan wani magani Wanda zai iya zame Maka matsala wata Rana, musanman ma damuke fatan kasamu haihuwa a kowanne lokaci.... " Dif Shahaab yakashe wayarsa, yarasa meyasa likitansa yake masa haka? Dan yanada mata saiyaqi shan magani saboda sha'awa? Inda yana samun cikakkiyar gamsuwa awajan matar tasane to Shima babu abinda zaisa yanemi wani magani, to Amma baya samu,dole yanemi magani, shikuma Doctor yakasa gane hakan. Daqyar yasamu bacci ya dauke shi a wannan dare, da sassafe yayi shiri yatafi Niger. ****** Kwanansa biyu a Niger,suka dawo Abuja shida mama,tun Bayan saukarsu a gidan mutane suke sallama falon Nata, daga wannan yafita Sai wannan yashigo, kowa zuwa yake yana yi mata barka da zuwa, ma'aikatan gidan kuwa kamar su zuba ruwa aqasa susha saboda murna, duk yanda mama takai ga yin mulki da izza, sunfi jin dadin zama da'ita akan munirat, mama tana komai ne cikin aji da Kuma tinqaho ita mahaifiyar me gidan ce, munirat kuwa kullum cikin yimusu masifa take, ga tsawa, kwata kwata bata kama girmanta na matar Mahmud Wakili. Dukansu suka hado kansu sukazo yimata barka da zuwa, Shahaab yana Gefe yana danne danne awaya, yana Sanye cikin suit, jacket din suit din tana riqe a hannunsa, Adede lokacin munirat tashigo, ganin mama da Kuma ma'aikatan gida suna zaune agaban mama, yasa ahankali yatashi yayi wa munirat wani irin kallo Wanda shi kadai ne yasan ma'anar sa, sannan yayi part dinsu. Mama kuwa nunawa tayi batasan munirat tana wajan ba, haka tabawa banza ajiyarta, ta kalli ma'aikatan sannan ta bude babbar jakar hannunta wadda take cikeda kudade,tadaga jakar ta zazzage kukaden ciki aqasa sannan tace musu "kudebe wannan kuje kuyi shagali na murnar dawowa ta...." Kafin tarufe baki suka kama wawar kudin, Nan da Nan fuskar kowa tacika da farinciki Sai zuba mata godia suke, hannu kawai ta daga musu alamun su tashi suje, Nan da Nan kuwa kowa ya watse. Harara ta watsawa munirat datake zaune agefen kujera tana kallon ikon Allah, sannan tatashi zata shige daki, cikin sanyin jiki munirat tace"mama ya hanya?" Mama ta juyo ta kalleta tace"Dama kinsan nayi tafiya ne?" Ahankali tace"kiyi haquri mama, nayita kiran wayarki but bata shiga, Amma insha Allah hakan bazai sake faruwa ba, I'm sorry mama" Tafadi hakan tana dora hannayenta akan kunnan ta. Mama tasaki ajiyar zuciya tace"tashi kije wajan mijinki, yana'iya dake?" Daga Nan ta wuce dakinta, cikin sanyin jiki itama munirat tatafi part dinsu. ****** Yau tunda safe, Aisha take aikin tunanin Shahaab, tarasa meyasa inde ta tunoshi Sai taji wani irin farinciki, har so take ta dinga tunanin sa, jiya da daddare Inusa yazo zance Qin fita tayi, acewarta ita batada lafiya (🙆🏻‍♀️😳) Cikin zuciyar ta tace "yakamata nafara azumin sitta shawwal kodan addu'ar danace zanyi wa Shahaab, Allah yabashi haihuwa idan yayi aure," Tunanin tasake tafiya, tambayar kanta take ko wa zai aura?, itade tasan baya sonta, inda yana sonta dole zai fadawa Abbanta ai, kamar yanda inusa yanemi izni agida, to Amma meyasa yake zarya awajanta? Wata zuciyar tace" zumunci " Da wannan tunanin na zuciyarta, yarinta tasa tadinga yaudaran kanta cewa zumunci ne yake kawo Shahaab wajan ta. Ko kadan acikin Yan kwanakin Nan bata ma son ayi mata maganar inusa, gaba daya Shahaab yashiga cikin qwaqwalwar ta yayi mata format din komai,kasancewar ta yarinya qarama, babu cikakken Hankali, saita dauki yarda Dari bisa Dari tabashi, ta yarda dashi yanda baya zato. Washe gari kuwa tad'auki azumin sitta shawwal, Hajja data gama yin dumamen tuwo, tazubo musu tace "me sunan qawa tun dazu kin shiga daki kinata hada kan takardu kokema littafi Zaki fara rubutawa kamar takwarar ki?" Dago kanta tayi ta kalli Hajja sannan tace "littafi take rubutawa takwarar tawa?" "littafi kuwa, tun kafin muyi candy haka zakiga tatara Yan ajinmu tana karanta musu Bayan tagama rubutawa, idan akwai inda tayi kuskure saisu gyara mata, inajin su Alokacin nikam daukar komai nake shirme" Aisha tace "Bayan kinqi nunamin photon ta" "me kike ci nabaka na zuba? Zan nuna miki ita ai, yanzu de taho muci tuwon Nan tukunna" Yatsina fuska tayi tace "saide kici, nikam azumi nake" Cikin sauri Hajja tace"azumin me?" "sitta shawwal"cewar Aisha " wanne irin sitta shawwal? Kinga... Ba sitta ba, ko kamsa ne bazanyi ba, kema inajin bakya jin ranar da ake zubawa ne shiyasa, ingama Ramadan cif, sannan inzo inyi wannan?" Aisha ta kalleta kawai ta girgiza Kai batare da tayi magana ba Bayan ankira sallar magrib Aisha Tasha ruwa sosai tayi wa Shahaab addu'ah, Amma addu'ar Tata tafi karkata ne akan Allah yabashi haihuwa idan yayi aure, kasancewar ya6oye mata cewa yana da aure, shiyasa koda wasa batace Allah yabawa matarsa ciki ba, fatan ta idan yayi auren Allah yabashi haihuwa Mai Albarka. Washegari Hajja ta dauki azumin sitta shawwal, babu Wanda ta fadawa tana azumi, da azahar Ummah takawo mata abinci saitace Sai anjima zata ci, kunun Ayane a gabanta tana hadawa, saida ta zubasu acikin jarkoki sannan tasaka su a fridge da rufe. Wani yaro ne yayi sallama yace "Wai abani kunun Aya na Dari bakwai" Cikin murna Hajja tatashi, tadauko leda babba, ta zuba masa Yan Dari-Dari guda bakwai tabawa Yaron, shikuma yabata dubu daya, tad'auki canji tabashi tana cewa "idan sun shanye kadawo min da jarkokin kaji" Yaron ya amsa, sannan yafice daga gidan. Baifi minti ashirin da tafiya ba ya dawo yace "Wai abani pure water na nera ashirin" Hajja tace "babu pure water yaqare, Ina jarkokin da'aka Sai kunun Ayar?" Yaron yace "sun tafi dasu" Cikin sauri jabir dayake zaune agefe yace "Alhamdulillah... inda nine ma Yan hamsin-hamsin zan siya yanda zaki Rasa jarkokin dayawa, haba Adinga maganar jarka de, kasai abu ai shikkenan jarka tazama taka" Kafin Hajja tayi magana wani Almajiri yashigo da wasu jarkoki a hannunsa yace "Hajja ga jarka inzaki siya" Jarkokin ta karba tafara dubasu, saida tagama dubasu tas sannan tace "wannan ai duk irin jarkokina ne dasuke 6ata, waye yabaka?" (🙆🏻‍♀️😂) Yaron yafara rantsuwa yace "wallahi abakin kasuwa na tsinto su, banaki bane" Cikin masifa tace "Kai jeka da abunka, sunyi qazanta dayawa, bazan siya ba, a tsinto jarkoki abakin kasuwa a kawowa Hajja mahaukaciya tasiya, debe su daga gabana bazan siya ba" Aisha ta futo daga d'aki kanta babu dankwali, Sai qyalli gashin Nata yake kasancewar tashiga rana, ta kalli Hajja tace "keda kikace duk irin jarkokin kine?" Hajja tace "mesunan qawa Ina kika samu wannan abun daure gashin? Sai daukan ido yake daga Gani yanada tsada" Cikin ko'in kula tace "Walida ce tabani" Hajja tace "tunda babanta yanada Hali zata Iya baki wannan Kam, jeki kar6omin wayata a gidan Jummai, dazu nabayar takaimin maqotansu naji sun kunna inji, 95 ne Dani shine nakeso subatse min ita" Jabir yace "Hajja waya a 95 kika Kai wajan caji?" Cikin masifa tace "to Ina ruwanka? Wayar nan fa saboda mesunan qawa nake kaiwa caji, idan tafara waya da inusa Kai kace akansu aka fara soyaiya" Jabir bai sake magana ba, yaga yau Hajja masifa takeji, komai akayi mata Sai masifa, baisan azumi take ba (🤣) Aisha kuwa hijabi tasaka, sannan taje ta kar6o wayar tabawa Hajja, Hajja tana Gani tace "ya haka? Menake Gani kamar 50 percent?" Aisha tace "Wai data cikane shine jikan iya jummai yake kallo kafin kizo ki Kar6a" Hajja ta Jinjina kanta tace "Amma kuwa jummai anyi marar zuciya da bazata iya futo na futo da jikokin ta akaina ba" Ta juya ta kalli jabir tace "ga wayar inzaka siya kawo dubu biyun kawai" Jabir yace "banaso akai kasuwa" Cikin jin haushi tace "ai shikkenan" Tajuya ta kalli Aisha tace "me sunan qawa ki shirya kije kano gobe, kisiyomin kayan hadin kunun Aya a singa, idan kikai wa su Malam kwana biyu saiki dawo" (malam mahaifin Hajja) Tace "to Hajja Allah yakaimu" ****** Washe gari da yamma Aisha tatafi kano, dayake sun dan kwana biyu ba suje Garin ba Sai take murna da tafiyar Tata, gab da magrib ta qarasa kano, kasancewar a yankaba baban Hajja yake, kawai napep tashiga aka kaita har gida, malam da matarsa guda daya kishiyar mahaifiyar Hajja, dayake mahaifiyar Hajja ta rasu, Sai kishiyar ta, sunyi murna da zuwan Aisha, Fati jikar qanin Hajja datake zama a gidan tana tayasu Dan aikace aikace Nan da Nan ta janye Aisha da surutu, dayake Dama akwai Sabo a tsakanin su, Bayan sunci abinci Nan suka shige daki suka fara zancen samari, Fati tace "Aisha Ina samarin ki, nasan yanzu ankusa aurenki, tunda ku ba'a barin yarinya ta girma sosai kamar Nan" Aisha tace "samari suna Nan, ni besan ma nataho ba, saide Hajja tafada masa idan yaje gida" Faty takama ha6arta tace "tafiya babu yiwa saurayi sallama? Anya kwa dashi za'ayi?" Dariya Aisha tayi tace "ke Ina naki saurayin?" "Auwal yana Nan Shima, ai Yanzu tunda kinzo, zan kirashi yazo ku gaisa," Aisha tace "to Allah yakawo shi lafiya, yawwa Fati nikam in tambayeki mana, wata qawata ce tanada saurayi, to agida ansan shi, Kuma tana sonsa da farko, to Kuma Sai wani mutum yazo, batasan ko waye ba, Amma shi Dan maiduguri ne, duk Bayan kwanaki saiya kawo mata ziyara, Kuma har kudi yake bata, to seta fara tunanin sa, Kuma fa bece yana sonta ba, Wai yafi so kawai su zauna tare yadinga kallon ta, to dan Allah me hakan yake nufi" Fati tayi fari da idonta cikeda yarinta kasancewar batafi Aishan shekaru ba tace"toshi meyasa ba zaije gidansu yace yana sonta ba?ai babu zumunci tsakanin mace da namiji, inde namiji yanason yarinya da gaske to zakiga wajan mahaifin yarinyar yake fara zuwa, saboda haka Ita qawar Taki, tace masa tanason wancen Wanda Yan gidansu suka sanshi, Shima tace masa inde yana sonta yafuto" Cikin sauri Aisha tace"to ai bece yana sonta ba, itace take sonsa " Fati tace" rainin wayo ma, Kuma baya sonta yake zuwa wajan ta? kawai idan ita tana sonsa zata Iya auren sa, tayi wuff dashi kawai " Dariya sukasa, Aisha tace"ke babba nefa" Fati kuwa cikin rashin kulawa tace"Babban,ai anfi yimusu shagwa6a, kiga sunata siyo Maka abinda kakeso" Aisha tace"to shikkenan zan fada mata" Fati tace"kifada mata wallahi" haka suka kwanta bacci gaba dayansu daga ita har Aishan babu me hankalin da zaiyi tunanin meyasa to namiji zai dinga zuwa wajan ka kawai yana 6ata Maka lokaci shibece yana sonka ba, shibe futo fili yabari iyayen yarinyar sunsan dashi ba, itama fatin dayake yarinya ce kwata kwata bata gane cewa Labarin da Aishan tabata ba'akan qawatar Aishan ne ba. ****** Tsaye yake ahabar gidan nasa, tunda ya dawo daga sallar la'asar baifi ta ko'ina ba kasancewar yau juma'ah, Sanye yake da wando three quarter Sai Riga yar qarama wadda tasa farar fatarsa futowa sosai,sojoji Sai zagaya gidan suke suna zare ido, Bluetooth ne amaqale a kunnan sa yana magana da Ramadan, ahankali cikin qasa qasa da murya yace "ok saika qaraso" Ajiyar zuciya yasauke yazira hannayensa cikin aljihun wandon nasa, sannan ya qarasa wajan wata yar qaramar tumfa da aka qawata ta da kujeru masu kyau, lemuka ne a ajiye awajan da ruwa dakuma fruit, Sai wata wayar tasa datake ajiye awajan, zama yayi tareda Dialing number Aisha, yadade baiji shirmanta ba, yanaso ya ganta yajita akusa dashi, fiyeda yanda yake son jin muryarta, yaga alama idan bashine Yakirata ba, ita bazata kirashi ba, yana kira Alokacin wayar tana hannun me ita, Hajja ta d'auka tareda sallama, jin ba muryar Aisha bace yasa yayi sauri yakashe wayar, yana d'ago wa yaga Ramadan ya qaraso, hannu yabashi suka gaisa, sannan yace "nasamu saqo ta Email dina Gwamnatin kano tana gayyata taron daza'a yi na Yan kasuwa, sannan akwai Daurin auren wata yarinya da mahaifin ta yake aiki a qarqashin hukumar mu dake jihar kano, mahaifin yarinyar ya turomin saqo cewa yanaso inyi masa waliyin yarinyar, so Naga duk rana daya za'a yi, shine nakeso ka rakani" Ramadan yace "ok babu damuwa ai, yaushe ne tafiyar?" "gobe insha Allah" Ramadan yace "Allah yakaimu" Fork ya dauka yad'auki yankakkiyar pineapple din dake gabansa, cikin aji yake taunawa kamar bayaso, sannan ya kalli Ramadan dake tsiyaya ruwa a cup yace "Naje Jigawa" Ramadan batareda daya kalli Shahaab ba yace "eh aika fadamin kaje saboda kaji sunan yarinyar Nan ko?" Shahaab yace "nakoma" (😍) Cikin mamaki Ramadan yace "Tofa, yaushe?" Kafadarsa yadaga alamun rashin damuwa yace "kaide tunda nacema naje, ai shikkenan, dole Sai kaji ranar?" Murmushi Ramadan yayi yace "a a babu dole, amma wannan Karon zuwa kayi domin kaji shekarun ta nawa ko?" (🤣) "no, tacemin tanason biro, shine naje nakai mata" Cikin sauri Ramadan yace "yanzu saboda biro ka6ata kudin jirgi kawai kaje kakai mata kadawo?" "to ai tana sone, Dame zatayi rubutu idan bankai mata ba?" Ramadan ya jinjina Kansa, tsananin mamaki ya hanashi magana, shikam zai so ganin wannan yarinya, gaba daya tatafi da hankalin Shahaab, ya tabbatar inda ace bai bashi shawara ya6oye mata Kansa ba, da tuni iyayen yarinyar da'ita kanta yarinyar sun dade a Abuja, idan kayi masa magana ko sonta yake saiyace shi temakon ta yake, koma wacece ba qaramin so yake mataba, idan kuwa ya aure ta,Toya tabbatar Sai abinda tace, saboda ko lokacin dayake neman munirat, baiyi wannan haukan ba, fisabilillahi saboda biro?(🤔) Ajiyar zuciya yasauke sannan yace "gaskiya Abokina kanason yarinyar Nan" Cikin sauri yace "no, kawai de birgeni takeyi, tana birgeni sosai gata yar qarama, Amma tanada abubuwan more rayuwa najin dadin aure" Ramadan ya katse shi da cewa "to tunda hakane mezai Hana ka aureta? Abubuwan dakake fada tana dasu saika more abunka Kai kadai?" Kai tsaye yace "munirat fa?" Haushi ne yakama Ramadan, baisake ce masa komai ba, saiya Dauko masa wata hirar, wadda ta danganci aikinsu(😂) ****** Washe gari asabat fati tatafi islamiya, Kuma basa tashi da wuri Sai karfe hudu da rabi, Aisha datake San tafiya jibi ta kalli malam shida matarsa tace "Baba malam nikam zanje insiyowa Hajja saqonta, jibi nakeso natafi" Malam yace "to ai Zaki de gane ko?" Murmushi tayi tace "zan gane mana, ai wajan bashida wahala" Kudi yadauka yabata yace "to ga kudin adedeta, saikin dawo" Sallama tayi musu, sannan ta shirya cikin wata doguwar Riga ta atamfa, tasaka hijabi sannan tatafi, tun kafin tafiyar su tayi nisa taga Garin Yacika da goslow, gashi de tafiyar bawata me Nisa bace Amma sun kusa awa daya a hanya, Dan adedetan ne yasaki tsaki yace "wannan hanyar akwai go slow sosai Bari mu sauya hanya" Cikin damuwa Aisha tace"ni banaso ma karfe shida tamin a waje wallahi, da nasan haka Garin yake da go slow da tun safe nafuto nayi abinda yakawo ni" Dan sahun bece mata komai ba,ya sauya hanya, Shima dakyar suka qarasa, bata dade awajan ba ta siyowa Hajja duk abinda take buqata, sannan tafara neman abun Hawa, tun tana tarewa harta Dena, saboda duk Wanda tatare saide yayi gaba yabarta, haquri tayi kawai tafara tafiya da qafar ta batare da tasan hanyar dazata kaita gida ba, tana cikin tafiya harta gaji ta nemi waje ta zauna, gashi yamma tayi, kowa nema yake yatafi gida, wani me adedeta ne ya tsaya yace "yanmata Ina zakije?" Fada masa tayi, saiyace "gaskiya hanyar akwai go slow saide musauya hanya idan zakije shigo" Cikin sauri tace "inde zaka kaini gida ai shikkenan" Cikin gajiya ta shige cikin adedetan, sun fara tafiya kenan ya tsaya ya dauki wani fasinja, irin cikar da hanyar yayi ne yasa kowa Sai tsaki yake saki, Aisha taga duk hanyar dasuka bi motoci ne da adedeta suke layi babu wadatacciyar hanya, cikin 6acin rai tace "Wai meyasa yau Garin Yacika da yawa ne?" Dan sahun ne yace "manyan qasar ne suka shigo Garin, gaba daya sunzo sun haddasa mana cunkoso agari, tun safe jiragen sama suke yawo agarin Nan, idan wannan yatashi Sai wannan ya sauka" Daya fasinjan ne dayake gefen Aisha yace"Eh wallahi, Wai manyan Yan kasuwa ne suke taro, Kuma Dama yau din akwai aurarraki da'ake yi" Aisha batace komai ba, saida suka zo wucewa ta wani layi taga gaba daya anhade motocin a hannu daya, ankashe daya hanyar, Dan sahu yace "to munyi gudun Gara.... Muda muka guji go slow kaga ashe gidansa mukazo, ita wannan hanyar ma ai kwata kwata ba'a bin dayan hannun" Dayan fasinjan yace"Eh wallahi ance shugaban EFCC Mahmud Wakili aka sauka a daya daga cikin gidajen, Wai saboda bayason hayaniya shine aka Hana wuce wa ta dayan hannun gaba daya" Gaban Aisha ne yafadi,cikin faduwar gaba tace"to meyasa ba zaije hotel ba tsakani da Allah Sai Nan hanyar" Fasinjan ne yace "ance babu manyan hotel sun qare Sai qanana, inda kinsan waye Mahmud Wakili ma toda bakiyi maganar hotel ba, saboda ance baya sauka a qaramin hotel" Haushi ne ya hanata magana, ahankali ta juya ta kalli hannun Daman ta, taga titin gaba daya babu motar datake bi,asalima sojoji ne suke shawagi atitin kowa hannunsa d'aukeda bindiga, ta kalli manyan gidajen da'akace ansauki Mahmud Wakili aciki,mutum daya jal saboda shi ankashe titi babba kamar wannan, bayason hayaniya to me zaisa yazo Garin? Sukuma manyan qasar suka biye masa akayi masa abinda yakeso aka shiga haqqin talakawa, yanzu irin wannan layin adedetan dayake gabansu yaushe zasu qare har tasamu taje gida? Lokaci daya Shahaab yafado mata, ko yana Ina? Tunda yace shi Yaron Mahmud Wakili ne ko tare sukazo? Ko yana maidugurin? Juya fararen idanuwanta tayi tace "tsaya Dan sahu" Babu musu ya dakata, dama bawani sauri tafiyar tasu take ba, futowa tayi daga ciki hannunta d'aukeda ledar kayan data siyo, kudinsa tabashi tace "ga kudinka, zan qarasa da qafa ta, shikuma Wanda ya haddasa mana go slow din yaje mun rataya a wuyansa"(😂) Murmushi yayi yakar6i kudin, Aisha kuwa haushi ne fal ranta, tafiya take Amma ta nayi tana waigowa tana Kallan gidan da akace ansauki Mahmud Wakili aciki, Sai yau tasake tabbatar wa shi din ba qaramin mutum bane, ganinsa zaiyi wahala,haka taci gaba da tafiya har taje gida, qafafunta kuwa sunyi bud'u-bud'u da qura, bata dade da zuwaba aka kira sallar magrib. Washe gari saurayin fati yazo, kasancewar Aishan tace gobe zata tafi gida, shiyasa yazo da yamma,shirya wa sukayi Fati tayi kyau sosai cikin abaya baqa, Aishan ma Abaya tasaka wadda fati tabata jiya,saide Tata launin dark green ce, hijabi tayi niyyar dorawa akan abayar, Sai faty ta hanata, da magiya da komai tasa Aisha ta yafa mayafin rigar, ba rolling tayi ba, kawai parking din gashinta tayi, tayafa mayafin abayar sannan ta mayar dashi Bayan kafadunta, abayar tayi mata kyau sosai, Kuma tsawonta yayi mata daidai, irin abayar Nan ce wadda akewa shaf daga qirji, Qasan Kuma yabude sosai, batada wani ado sosai Amma Kuma tayi kyau rigar sosai, yanda Allah ya wadatata da Babban Hips, Sai ya sake bajewa acikin abayar, madedetan Breast dinta suka Dan taso daga gaban rigar, jakar Walida ta riqe tasaka can jin kudinta Dari biyar aciki, sannan suka fita wajan Auwal saurayin fati. Suna zuwa suka sameshi zaune akan motar sa,Dafarko da yaga Aisha tsorata yayi, musanman da yaga gashin gaban goshinta yafuto yaga gashin yalala kamar Bana bahaushiya ba, saida fati ta yi masa bayanin Aishan sannan yasaki jiki da'ita suka gaisa sosai, daga Nan Kuma Sai hira ta 6arke a tsakanin su, ganinsu duka Yara daga ita har fatin saiya biye musu suka dinga zance wani yayi dariya, wani Kuma ya girgiza Kai cikin ransa yace quruci.... Bayan sungama shan labarinsu fati tace "Yaya Auwal kakaimu wajan yawo Dan Allah, kaga gobe Aisha zata tafi" Cikin farinciki yace "tokuje ku tambaya agida saiku futo muje" Babu musu suka koma gida suka fada, kasancewar ansan Auwal din, ba 6oyaiye bane Sai aka barsu, Kai tsaye suka shige motarsa yaja suka tafi, park yafara kaisu, daga Nan Kuma suka tafi wani Babban Mall, domin siyo ice-cream, Aisha cikin ranta Sai murna take yau de zatasha ice-cream itama. Basu dade da shigaba sukaga mutane sunata futowa, basu kawo komai aransu ba suka dinga shiga waje waje suna ganin mall din,Auwal dayake biye dasu abaya yace "fatima kudauki abinda kuke sofa kunji ko" Cikin murna tace "to ya Auwal" Hannun Aisha taja suka je wajan perfume, Aisha de guda daya ta d'auka, Fatima Kuma tazabi irin Wanda takeso, ta kalli Aisha tace "ki qara mana, bashi ne yace mu dauka ba?" Aisha tace "A a, nifa nafison ice-cream,kede ki za6a Sai muje in dauki ice-cream din" Fatima batace komai ba Sai za6ar turaruka take, sannan ta kama hannun Aisha sukabi ta wata hanya suna neman inda ake ajiye ice-cream din, cikin rashin Sani Aisha tabige wasu setin glass cups, qaran da abun yayi ne yaja hankalin ma'aikatan mall din. Gaban Aisha yafadi, ta dora hannayenta aka tace "nashiga uku" (🙆🏻‍♀️) Kafin Auwal ya qaraso wajan wasu Yan sanda su biyu, da wasu security mata sun qaraso wajan Aisha, suna zuwa basuyi wata wataba suka kamata, cikin 6acin rai Auwal yace "miye haka, ya zaku kama yarinya ku riqe kamar wanda tayi muku sata? Kufadi nawane kudin kayan ku saina baku" Cikin 6acin rai daya daga cikin security yace "ba damuwar mu bane abinda tafasa, abun damuwar shine wanene ma yabaku iznin shigowa cikin wannan mall din Adede wannan lokacin da muka sallami kowa?" Auwal yace "oho, ta sama muka Fado tunda abude muka ga qofar" Jin furucin Auwal yasa ransu yaqara 6aci, memakon ya basu haquri baiyi ba saima raina musu Hankali yake, wata security ce mace tace "ai kawai a wuce dasu folice station, bazai iyu munada Babban customer, haka kawai saboda masu shigowa yin photo susa hankalin customer mu yatashi ba, a tafi dasu kawai" Jin wannan furucin ne yasa Fatima ta Fashe da Kuka tana basu haquri Tunda suka shigo Mall din shida Ramadan da sauran guard dinsa, baiji motsin kowa ba, dama Kuma hakan yakeso, shiyasa ma tun kafin yazo yaturo musu saqo ta Email cewa zaizo shopping mall din, yanaso abashi awa biyu yagama abinda zaiyi, idan yafita, Sai subar sauran mutane su shigo,yarinyar da yayiwa waliyi jiya, ita yazo ya siyawa gift yanaso yabata. Kukan Fatima dakuma hayaniyar datake tashi tsakanin Auwal da sauran security shine yad'auki hankalin sa, ransa ne ya6aci, kwata kwata baison hayaniya arayuwarsa, cikin 6acin rai ya kalli Ramadan tareda nufar inda yake jin hayaniyar tana tashi, sannan yace "muje" Jijjiga Kai Ramadan yayi sannan suka nufi wajan, guard din dake bayansa cikin sauri suka rufa masa baya. Shan kwanar da zaiyi, Idonsa ya sauka akan Aisha(🙆🏻‍♀️) Wata irin faduwar gaba ce ta ziyarceshi, Jiyayi Kansa yayi wata irin sarawa cikin sauri ya damqe hannun Ramadan yaja shi sukayi wata irin kwana suka dawo baya,duk da sunbar layin dasu Aisha suke gabansa bai daina faduwa ba, menene zai faru data ganshi? Mezai ce mata? Hakan yana nufin da yanzu asirinsa ya tonu kenan tasan cewa da Mahmud Wakili take mu'amula batare data saniba....., meya yakawota kano? 6oye fuskar sa yafara yi a Bayan Ramadan kamar wani 6arawo(😂) Daga Ramadan har sauran body guard Kallan Shahaab suke da mutuqar mamaki, zare ido suka fara suna dube dube atunaninsu wani abun cutar wa Shahaab din yagani. Cikin tsananin mamaki Ramadan yace "Shahaab lafiya? Meyasame ka?" Yana 6oye a Bayan Ramadan din cikin fada yace "dalla malam Kamin shiru, duk ba kaine kajamin ba?" Mutara zuwa gobe 🙏🏻 Ramadan yace "kamarya?, mekake nufi ninaja?" "Tura musu mutum daya kace su sallami yaran can injini, sannan subata haquri" Ramadan da mamaki yagama kasheshi, yace "okay" sannan yajuya ya kalli daya daga cikin guard dinsu yace "kace a sallami yaran can, sannan abasu haquri inji Mahmud Wakili" Cikin sauri yanufi wajan da su Aisha suke, yana zuwa yayiwa daya cikin security din dasuke fada da Auwal magana. Ramadan yadan leqo yaga abinda Shahaab yake gudu, anan yayi tozali da wata kyakykyawar yarinya, shagala yayi da Kallan yarinyar, fada dakuma tashin Hankali yasa Dan qaramin da kwalin abayar data yafa akanta yasa yayi qasa, dogon gashinta yafuto fili muraran, Shahaab daya d'an leqo da Kansa ta Qasan Ramadan Shima ya leqo yana ganin ta, ransa ne yayi baqiqqirin ganin dogon gashinta awaje, ribbon din daya daura mata shine akanta, haushin mazan wajan yafara ji dasuke tsaya tareda ita, yanzu haka kowama kallon gashinta yake, yasake Kallan Auwal da'ake fada dashi, cikin tsananin kishi yace "ko wanne yaro ne Kuma wancen?" Ramadan ya juyo ya kalleshi, yaga fuskar Nan tasa tayi kicin kicin hankalinsa kacokam yana kan wancen yarinyar. Su Aisha basu San menene yafaru ba Sai Gani tayi wannan securities din duk sun sunkuyar da kansu qasa suna fuskantar ta, har rige-rigen bata haquri suke, haushi da Kuma mamakin su ya kamata, yanzu yanzu suka gama cewa zasu kaisu folice station Amma Kuma suna bata haquri yanzu, kamar wasu masu Fama da aljannu, taqaici da 6acin ran da aka bata ne yasa tayi jifa da turaren data dauka, tajuya tafice cikin fishi, ice-cream dinma tafasa Sha,har suka fice daga mall din Ramadan bai daina kallonta ba, yarinyar tahadu ta ko'ina, babu wani namiji me lafiya dazai ganta yakasa yabawa. Shahaab kuwa yana ganin yanda tafice cikin fishi yace"to 'Yan masifar sunzo" Ramadan yajuyo yasake Kallan Shahaab daya 6uya abayansa Sai magana yake shi kadai, Kallan rashin fahimta yayi masa sannan yace "meyake faruwa ne?" Wata irin ajiyar zuciya yasauke tareda Lumshe ido yabude, sannan yace "MAAMA" Ramadan daya dauki haske cikin sauri ya zaro Idonsa yace "what...?" Shahaab bai iya bashi amsa ba Sai Kansa daya daga masa kawai Suna shiga mota Auwal yafara lallashin fati saboda kukan datake yi, saida tayi shiru sannan yaqara Bawa Aishan ma haquri, Bai qyalesu ba saida ya tabbatar sun Dan saki ransu, sannan sukai sallama suka shiga gida, Bayan sunyi shirin kwanciya Aisha banda tsinewa masu mall dinnan babu abinda take yi,ta nayi itama fati tana tayata, daqyar suka samu bacci ya dauke su (Shahaab littafin kudine, idan kika karanta batareda kin biya ba, nabarki keda mahaliccinki, nide ban yafe a) ****** Tunda suka dawo masaukinsu Shahaab yayi shiru yana tunani shi kadai, Babban abinda yafi 6ata masa rai shine yanda ya ganta dawani yaro. Ramadan ya kalleshi yace "Wai Dama haka yarinyar Nan take?, Shahaab Anya kuwa bahaushiya ce?" Kansa ya jijjiga masa alamun hakane, ajiyar zuciya ya sauke yace "gaskiya tanada kyau sosai, amma Kuma yarinya ce sosai ya'akai Takeda kyan diri haka?" Cikin masifa Shahaab yace "bansaniba, meya Hana kabita ka tambayeta?" Murmushi Ramadan yayi, Bayan yagano kishi ne yake cin abokin nasa, ajiyar zuciya yasauke sannan yace "menene abun 6acin rai Kuma a magana ta?" Cikin fishi yace "to kazo gabana Sai wani yabon ta kake, kaiba matarka ba, ba komai ba, ni abinda yafi 6atamin rai ma shine Yaron Dana gansu tare, bansan Yaya zanyi in tambayeta Shiba, zatace min Yaya akai nasan taje mall, idan nace Ina tareda ogana tace Amma nakasa yimata magana Ina Gani security suka ka masu, Ramadan duk kaine kajamin wannan abun, inda kabarni naje mata a Mahmud Wakili na, daduk haka bata faru ba, daga Kai har mama kira kuke idan zanyi mu'amula da mace tona 6oye mata kaina, na6oye mata koni waye, ta hakane zansan mesona tsakani da Allah, Ramadan ni banga amfani 6oyewa MAAMA kaina ba, saboda yarinya ce qarama, batada wani ilmi akan Zaman takewar rayuwa, yanda yarinyar ta yarda Dani idan saceta zanyi da tuni na saceta, na lura batasan komai ba akan soyaiya Sai abinda aka Koya mata,nafada mata banda aure, ta yarda, nafada mata nidan maiduguri ne, tayarda, nafada mata ni Yaron Mahmud Wakili ne, tayarda, duk wani abu Dana fada mata yarda take saboda tasan bazanyi mata qarya ba,nafada mata inason haihuwa idan nayi aure da bakinta tace zata fara azumin sitta shawwal tayi min addu'ah ko Allah zai ban haihuwa, yanzu Mena aikata haka? Inda nafada mata gaskiya tunda farko dazan iya futowa a ko'ina ne in kare ta amatsayina na Mahmud Wakili" Jikin Ramadan ne yayi Sanyi,kafadarsa yadan bubbuga yace "kayi hakuri Shahaab...,Amma shawarar damuka baka nida mama itace mafita,inda bakayi hakan ba, zaka San halaiyar yarinyar ne kamar haka? Ni banga laifin taba dakake cewa baka sonta, wannan yarinyar babu inda bazaka shiga da'ita ba, asalima yarinya ce qarama Sai abinda ka dorata akai zatayi, Amma tunda baka sonta, kadena zuwa inda take, kanisanceta, idan Kai kasan zuciyar ka, ita bakasan Tata ba, zata Iya sonka, qarshe karabu da'ita, hakan bai kamata ba, karabu da yarinyar mutane kawai " Cikin tsananin kishi Shahaab yace"Nina Rasa gane inda kanufa Ramadan, saika dinga nunamin kamar so kake narabu da yarinyar kaikuma kaje ka aure ta" Dariya ce ta kama Ramadan, Amma saiya danne, yace "Aure kuwa da gudu" Shahaab yayi masa wani irin kallo, cikin zuciyar sa yace zan dauki mataki, dole zan kawo qarshan komai, haka suka kwana babu wanda yasake magana, kowa da abunda yake saqawa acikin ransa, shikam Ramadan ransa fes yayi bacci, ko banza yasan ya tunzura Shahaab, dama da niyya yafadi hakan danya ga gudun ruwan abokin nasa. ****** Washe gari tunda safe, Aisha tatafi gida, tana zuwa Hajja ta tareta cikin murna, tsarabar Lemo da bread din data kawo musu suka rarraba har jummai saida aka kaiwa, cikin sauri ta shige dakin Hajja ta dauki wayarta tafara duddubawa ko Shahaab Yakirata, saide bataga komai ba, tunani tafara me zata siyo masa idan yazo tabashi Shima a matsayin tsarabar kano? Wani tunani tayi, cikin sauri Takoma Dakin Umman ta, asusunta dayake Qasan gado tafasa,dubu biyar biyar din daya bata sau biyu, dakuma dubu biyunta na albashin ta, tahada dubu goma Sha biyu, tasaka hijab dinta ta cewa Ummah da Hajja "natafi gidansu Walida yanzu zan dawo" Hajja tace "dole kije Kam kwana biyu Baku hadu ba, itama rannan tazo nace mata ai kin tafi kano" Aisha batace komai ba tafice, tana fita kofar gida bata nufi gidansu Walida ba Kai tsaye wata hanya ta d'auka, saida taci tafiya sosai, sannan taje wani Babban shago, tabawa me shagon kudin tace "gashi abani agogo da links" Cikin sauri ya d'ago ya kalleta yace "to wanne Kala kikeso?" Tace "Nima bansaniba ba, kawai kabani me kyau" Murmushi yayi yace "to Wanda zai saka fari ne ko baqi?" Tace "fari ne" Cikin farinciki yabata agogon da links din tuwan toka yace "to wannan zaifi kyau" Kar6a tayi sannan tafice, acikin hijabinta ta 6oye su, sannan Takoma gida tasaka su acikin kayanta ****** Da yamma yaga Shahaab sai shiri yake, manyan Kaya ne ajikinsa na wani yadi Mai mutuqar kyau, cikin mamaki ya sake Kallan sa yace "fita zamuyi ne? Naga Kanata shiri" Cikin sauri yajuyo ya kalli Ramadan din sannan yace "fita zanyi de" Daria ce ta kama Ramadan, yayi murmushi yace "to naji, Ina zakaje?" Kai tsaye yace "jigawa" "Amma Shahaab kasan fa jirgin safiya zamubi mutafi Abuja, yanzu karfe hudu, idan katafi yaushe zakaje harka dawo?" Kallan sa yayi yace "akwai tafiyar dazanyi zuwa Australia goben da yamma idan mun koma Abuja Dasafe, tafiyar zata daukeni wasu Yan kwanaki masu yawa, dole zanje inyi sallama da Maama, ko zan tafi ne batare data Sani ba?" Ramadan yayi murmushi yace "a a, Amma Dan Allah katafi Dani danna sake ganin ta" (😂) Cikin daure fuska yace "zanyi sallama da yarinya kana cewa zakaje, idan kaje a'ina zaka zauna? Ka zauna anan kawai, zan saka face mask inje dakaina indawo" Yana gama fadar haka yafice daga d'akin, Ramadan yasaki murmushi cikin ransa yace "Allah yakai damo ga harawa...." Idar da sallar magrib dinta kenan, tafada duniyar tunaninsa, sotake ta kirashi, Amma Kuma tasan idan ta ta6awa Hajja katin waya to zata gane, Kuma ta dinga yimata mita kenan,kamar almara taji wayar tana qara,tana dubawa taga number shice, cikin sauri ta d'auka sannan tashige Dakin Hajja, cikin wata irin murya wadda zaka tabbatar yayi kewarta yace "Maaaamah" Wani irin yarrrr taji ajikinta, ahankali tace "na'am" Kai tsaye yace "Ina kofar gida" Cikin murna tace "da gaske?" Yace "sosai, kifuto yanzu" Tace "to" sannan takashe wayar Daki ta wuce tadauko abunda ta siyo masa dazu, sannan tafuto tana Sanye da hijabi dogo, Ummah ta kalla tace "Ummah zanje wajan Walida" Kafin Ummah tayi magana Hajja tace "keni narasa gane wannan zarya da kike a gidansu Walida, kusan kullum Sai kinje inji de lafiya?" Dan qaramin bakinta ta turo gaba tace "littafi zan kar6o fa" Ummah tace "kuma kullum bakida aiki Sai zuwa da daddare? Kishiga hankalin kifa" Hajja tace "Allah ya kyauta, toki tabbatar kina kar6owa Zaki dawo" Cikin murna tace "to Hajja" Sannan tafice daga gidan cikin murna, wannan motar bada ita yake zuwaba, Amma kasancewar tasan anan yake ajiye motarsa, saita nufi wajan, tana zuwa bata jira yafuto yabude mata ba, tazagaya ta bude tashiga, sannan tarufe, Kallan sa tayi cikin farinciki tace "Dama wallahi sonake naganka, na Dade inason muyi waya inbaka labari" Cikin mamakin farincikinta yace "meyasa baki kirani ba to?" Cikin shagwa6a tace "to ai idan na kiraka Hajja zata gane, Kuma zata San nata6a mata katin waya" Cikin ransa yace Kati Kuma? A fili saiyace "Dama ba wayarki bace?" Girgiza kanta tayi tace "wayar Hajja ce" "wace Hajja?" ya tambayeta Tace "kaka tace, Amma Kuma wayar a hannu na take wuni, inayin game da'ita, yanzu Kuma Dana dawo Naga duk ta gogesu daga wayarta" ta qarasa maganar idonta na cikowa da qwalla Cikin sigar rad'a yace mata "menene na kukan Kuma? Kincika shagwa6a Maama, Kidena yin game, kici gaba da karatu yafi" Murmushi tayi tace "kasan me? Inaso inyi karatu inzama likita, indinga aiki a Asbiti, inkai babana Saudia, nikuma saina tafi tareda Ummah na da Hajja" Wani irin daci yaji acikin ransa, saboda idan akwai abinda yatsana to shine matarsa tayi aiki, baya fatan ma ace yarage ta tawani Fannin bare har tayi tunanin yin aiki domin samun kudi, matsayin matarsa yawuce tayi aiki abata kudi, saide ta dauki kudin tabawa ma'aikata, wata zuciyar tace dashi to ita matarka ce? Acan Qasan maqoshinsa yace "yes" saboda kada ta gane yanayin dayake ciki na rashin son karatu,Sai yayi Murmushi yace "nikuma fa? Bazaki kaini ba?" Dariya tayi, tace"kaima saimu tafi dakai to,kabani wayarka nayi game kaji" Cikin ransa yace"kodan yarinya ce? Yanzu inashi Ina wani game a wayarsa? Kallan ta yayi a fili yace "banda game" Cikin sauri tace "to cartoon" Murmushi yayi yace "Shima babu" Bakinta ta turo gaba tace "to photuna" Daukan wayar yayi batareda tunanin komai ba yabata, saboda yasan shide babu pictures dinsa aciki, haka babu wata shaida dazata Gani ta tabbatar mata cewa shine Mahmud Wakili. Kallan pictures takeyi dayawa na takardu ne Wanda batasan kona menene ba, wajan videos tashiga, anan taci Karo da video na wata mata da'akayi mata operation, cikin sauri tabashi wayar tareda fashewa da Kuka, cikin kuka tace "Dama haka ake ciro yaro? Bazan iya aikin asbitin Nan ba, nafasa, saide indinga saida Kati" Dariya ce ta kamashi, cikin dariyar yace "da kudin katin Zaki kaimu Saudia kenan?" Batace Masa komai ba Sai kuka datake, wayar yakashe gaba daya, sannan ya gyara zamansa yajuyo yana fuskan tarta, yarasa Yaya zaiyi mata, tacika shagwa6a dayawa, yanzu tayaya zai fara lallashin ta? Ahankali yad'ora tafukan hannunsa a fuskarta yariqe fuskar Tata dakyau sannan yace "kiyi shiru, bafa haka akeba, kawai hadawa akayi, yi hakuri kinji?" Kanta ta daga masa, hawaye ya silalo daga idonta, ahankali yasaka hannunsa guda daya ya share mata Hawayen, duk yanda yaso daqin ta6a dogon hancin ta, kasawa yayi, hannunsa yad'ora akan Karan hancinta yafara shafawa ahankali, rufe idonta tayi, hakan saiya qara yiwa fuskar Tata kyau, gashin idonta daya hadu da dan'uwansa yajiqe saiya kwanta yayi luf,cikin wata irin murya Mai Kama da rad'a yace "ogana zai turani qasar waje maama, Dan Allah karki kula kowa kafin nadawo kinji..." Cikin sauri ta bude idonta, sannan ta janye hannunsa daga fuskarta tace "yaushe zaka dawo?" Yace "zan'iya yin wata daya, mezaki Bani Wanda zan dinga tunawa dake?" Cikin sauri tad'auko agogo da links din data siyo masa, ta ajiye akan cinyarsa tace "gashi" Mamaki yakama Shahaab, ya kalli abinda ta ajiye masa akan cinya yace"na menene wannan?" Ahankali tace "siyo Maka nayi, kaima kasaka a hannun ka, tsarabar kano ce, kasan naje kano, tona siyowa su Hajja bread da Lemo, shine kaima nasiyo ma" Mamaki ne yahana Shahaab magana, ya zuba mata ido yana kallon ta, yanaso ya tambayeta wanne yaro ne ya gansu akano Amma yarasa ta wacce hanya zai tambayeta? Sake Kallan agogon yayi, sannan yasaka hannu yacire agogon dake daure a tsintsiyar hannunsa ya ajiye shi agefe, links dinma ya ciresu, sannan ya maida kallon sa gareta yace "to dauki kisaka min" Kallan sa tayi tace "ai ban'iya sakawa ba" Ahankali cikin qasa da murya yace "dauki saina gwada miki" Babu musu ta dora hannunta acinyarsa tad'auki agogon, sannan ta dora tafin hannun ta akan nasa, wanne irin laushi taji hannun nasa nayi, agogon ta dora akan hannunsa Wanda gashi Yacika shi sosai, shagala yayi da kallon ta, dogon hancinta yake Gani dakuma yanda take qoqarin daura masa agogon, cikin shaqaqqiyar murya yace "wannan dayan zaki saka acikin wannan qofar, shikkenan" Kallan sa tayi jin yanayin muryarsa tad'an sauya, sannan ta Girgiza masa Kai, tayi abinda yace, tana dauke hannunta yad'ora bakinsa akan agogon yayin kissing dinsa, sannan ya kalleta yace "nagode, saura link's din" Babu musu Shima ta d'auka tasaka masa da temakon sa, suma saida yayi kissing dinsu, Aisha de tana ganin ikon Allah, sannan taga ya juyo yace mata "Ina kika samu kudi kika siyomin wadannan abubuwan?" Cikin rashin damuwa tace "kudin daka Bani ne, nahada da Wanda nake Tarawa saboda qanina yatafi makaranta, shine nasiyo ma dasu" Jiyayi wani irin shock ya kamashi, kudin da take Tarawa saboda qaninta yatafi makaranta? Hakan yana nufin shita sadaukarwa da kudin kenan saboda tayi masa kyauta yaji dadi,wacce irin yarda yarinyar Nan tabashi? Dama ashe akwai yarinyar dazai samu yanzu ta dinga bashi irin wannan kulawar? Ashe akwai yarinyar datake sonsa da gaskiya? Hakan yana nufin mama da Ramadan sunyi gaskiya kenan, yakamata zuwa yanzu ace yafada mata abinda yake ransa, ga Ramadan ma dayake kusa yana cewa tsaf zai iya aurenta, cikin sanyin jiki yamatso dab da ita, ahankali yad'ora Kansa akan cinyoyinta Zaro ido tayi cikeda faduwar gaba, menene haka Shahaab yake mata? Hannu tasa tafara janye masa Kansa, Amma sai yaqi bata damar hakan,saina hips dinta daya riqe yajin kamar su dauwama Ahaka, dagewa tayi ta janye Kansa, cikin sauri yakama hannayenta yariqe da hannunsa biyu, Kallan qwayar idonta yayi sannan yace "maama kinason aure yanzu?" Mamakin tambayar tasa tayi, saida tad'an juya idonta sannan tace "inaso Amma banason kishiya" Gabansa ne yafadi, cikin sauri yace "meyasa?" "saboda Hajja ita kadai ce, Ummah nama ita kadai ce, Nima nikadai zan zauna da mijina, banason hada komai nawa da wata, yaje can Dakin, yazo Nan dakin, nifa ko tunawa nayi anayin kishiya raina 6aci yake, Ina Gani a cewa wata mijina shine mijinta, idan yayi wani abu a Dakin amarya, yaje Dakin uwar gida yafada mata" Cikin sauri Shahaab yace "koda mijin baida surutu?" Itama cikin sauri tace "koda kurma ne, idan zan kirashi to inde yana gaban matarsa bazai dauka ba, nifa banason damuwa ko kadan musanman akan kishiya,namiji yaje wajan kishiya ta, Nima yazo wajena"(🙈) "yazo wajan ki yamiki mei?"(😳) Yafadi maganar yana zaro Idonsa Sai a lokacin tatuna dawa take magana, cikin wata irin masifaffiyar kunya tayi sauri ta 6oye fuskarta da tafukan hannunta Murmushi yayi, sosai maganar Tata tabashi dariya, yar qanqanuwa da'ita har tasan kishi, idanu yazuba mata yana sake qare mata kallo, ahankali yamiqa hannayensa yakama fuskarta, Kallan sa tayi taga yanayin Idonsa yana sauya wa, ahankali tadora hannunta akan nasa hannayen daya riqe fuskar ta tana so ta janye masa hannayensa,Kansa ya Girgiza mata, yayinda yake sake matso da fuskar sa dab da Tata, gabansa ne yake faduwa, zuciyarsa na sake zigashi akan yafada mata abinda yake ransa,dogon hancinsa yad'ora akan Nata hancin, yahade goshinsu waje daya, lips dinsa yana gogor Nata, ahankali cikin muryar rad'a yace "maamaaaah....,maama Ina sonki" Yanda yafadi maganar cikin wata irin murya, dakuma yanda take jin lips dinsa yana ta6a Nata, hakan ne yasa tashiga wani irin yanayi Wanda bata ta6a tsintar kanta aciki ba, cikin salon shagwa6a da narkewa yace "kema kina sona?" Gabanta ne yafadi, numfashinta yana fita da sauri da sauri, idan tace bata sonsa tabbas tayi qarya, ahankali ta bude Dan qaramin bakinta tace "Nima Ina sonk...."kasa jurewa yayi, Bai Bari ta qarasa ba yahade bakinsu waje daya. Wani irin qarfi taji yazo mata, Nan take tafara kokarin hanashi abinda yake, Amma ruqon Dayayi mata yasa takasa qwacewa, tanajin yanda yake tsotsar bakinta ahankali kamar yasamu sweet. Jikinta ne yafara rawa, bata sababa, bata ta6a aikata hakan ba, wannan ne dalilin dayasa take jin komai Sabo agareta, bata iya yimasa komai ba, tana jinsa yana shan bakinta son ransa, saida yagama kissing din Dan Kansa, sannan ya zare bakinsa ahankali, har yanzu hannunsa yana riqeda fuskarta, cikin qasa qasa da murya yace "ki kula min da kanki maama,karki kula kowanne saurayi Dan Allah, Ina dawowa daga qasar waje zanzo inyi magana da Abban ki" Daga masa Kai tayi cikin mutuwar jiki, batareda tace komai ba ta bude motar tafuto sannan tarufe, akan idon malam Manu maqocinsu, Wanda tun shigar ta cikin motar ya ganta, haka Kuma yaga futowar ta (🙆🏻‍♀️😳) Kai tsaye gida ta shige tana tafiya hannunta yana kan lips dinta Wanda yaji tsotsa, tunani take Dama wannan ne kiss din?. Kai tsaye d'akin Hajja ta wuce, tanajin Hajja tana cewa "mesunan qawa fira tayi dadi yau kin dade awajan Walida" Bata amsa mataba ta qarasa shigewa daki tareda fadawa kan gado, wani irin yanayi takeji ajikinta Wanda tarasa gane Kansa A 6angaren Shahaab kuwa daqyar ya'iya komawa kano, Alokacin shadaya da kwata na dare, hannunsa akan mararsa yashiga gidan da akayi musu masauqi,yadade acikin motar yana kar6ar caji kafin yabude motar yafuto, duk yanda yake jin azaba daga ciki, Bai Bari Ramadan yagane halin dayake ciki ba (😂) Kai tsaye toilet yashige domin tsaftace jikinsa. ****** Yau kwana biyu kenan da tafiyar Shahaab Australia, tana lura da Abban ta tun washe Garin ranar da Shahaab yazo wajan ta take ganin yanayin sa ya sauya, komai yana yinsa ne a sanyaye, yau ma zaune suke a tsakar gida gaba dayansu, Hajja tana dura kunun Aya, jabir yana zaune kusa da Ummah, Abba kuwa yana Gefe ya zubawa Aisha ido itada qawarta Walida yana kallon su, tun shekaran jiya da malam Manu ya shaida masa cewa yaga Aisha tashiga motar wani, sun dauki lokaci acikin motar, sannan tafuto, shikkenan yashiga damuwa, yarasa waye yake son rushe wa yarsa tarbiyar daya bata tsawon shekaru, a yanda yakeji yanzu, zai iya yi mata dukan lahani idan ya tambayeta motar ubanwa tashiga taqi fada masa gaskiya Walida ta kalli Aisha tace "tabdi, wallahi na manta ban taho da biro naba, Kuma sonake yau kisake koyamin lesson plan dinnan Dan inyi sauri in qarasa, jibi muke son komawa makaranta hutu yaqare Kuma" Hajja tace "ai kun samu ma kundan huta, Amma da ace lokacin azumi Kuna zuwa Aida jikinku Yagaya muku" Aisha tasaka hannunta cikin jakar makarantar ta tana cewa "Bari inbaki nawa Biron, saikiyi dashi Amma Sabo ne, Baiyi laushi sosai ba" Walida tace "Bani" Zuciya daya Aisha tadauko Biron da Shahaab yabata, ta miqawa Walida Biro, Walida tana ganin wannan biro tazaro idonta waje, cikin tsananin razana tace "la'ila....waye yabaki wannan Biron? Wallahi irinna babanmu ne sak, Shima gwamna ne yaraba musu shi Kuma yace mana biro ne Mai mutuqar kyau da tsada, dubu Dari biyar ake saida shi" (🙆🏻‍♀️) Hajja ce tazaro idonta waje (😳) Abba kuwa Aisha ya zubawa ido yana jira yaji daga gidan ubanwa tasamu Biron, Ummah da jabir ma idonsu yana kan Aisha, yayinda kan Aisha yasara, tarasa asama take ko'a qasa, gabanta yahau luguden faduwa. (tofa Al'amari ya lalace yau 😂🥹) Littafin Shahaab na kudi ne, ki biya naira 300 kacal ki karanta abinki Hankali kwance, idan kika karanta batareda kin biyaba, keda mahaliccinki,. 08033300034 Amnah El Yaqoub✍🏻 Page 21 Kafin Aisha tayi magana Hajja tace"kekuwa Walida da masifar qarya kike, yanzu inbanda qarya, wanne irin biro ne za'a ce dubu Dari biyar saikace kudin qaramin gida?" Aisha da idonta ya furfuto ta juya ta kalli Hajja, jitake kamar babu nauyi ajikinta, Sai takeji kamar tana tashi sama ne saboda tsabar rashin nauyi, har zuwa yanzu idon Abba yana kanta, duk wani motsi datayi, idonsa yana kanta Walida kuwa kallon Hajja tayi tace" Hajja.... Wallahi Allah da gaske nake, nasan Abbana bazai mana qarya ba, lokacin ma agaban mu yabawa Alhaji Ali yace aje a saida Biron zai sayi fili da kudin" Hajja ta kalli Aisha datayi tsumu-tsumi tana zare ido tace"mesunan qawa a'ina kika siyo Biron?" Cikin faduwar gaba tace "Hajja ni Bani akayi, Kuma Wanda yabani bashida kudin da Walida take fada bare harya'iya siyoshi" Abba daya zubawa Walida ido yana kallon ta yace"tashi kije gida Walida, qawar Taki zatazo ta sameki" Babu musu Walida tatashi tana cewa Aisha "to wallahi ki binciki Wanda yabaki karkije na sata ne, idan kinzo saimu qarasa rubutun" Daga Nan tasakai tafice daga gidan Abba ya kalli Aisha fuska babu Fara'ah yace "bani Biron" Babu musu ta dauki biro tabashi, Kai tsaye yatafi gidan Alhaji Ali domin jin gaskiyar magana,ko kadan bai yarda da maganar da Aisha tafada akan Biron ba, Ummah datake tsoron yiwa Aisha fada Hajja Tahau kanta da masifa tace "Allah yarufa asiri" Aikuwa cikin sauri Hajja tace "Amin, aiya dade da rufawa" Cikin sauri Aisha tatashi ta shige dakin Hajja, gaba daya fuskarta ta sauya tunani take da kokonto akan maganar da Walida tafada mata, Ina Shahaab zai samu kudi har nera dubu Dari biyar? Lokaci daya ranar da sukaje mall itada fati yafado mata Arai, da fad'an da masu mall din suke mata, Kuma lokaci daya suka dawo suna bata hakuri saboda wani body guard datagani da baqin glass yazo yayi magana dasu, ta tuna lokacin dasuke cewa Babban customer dinsu ne yazo Kuma bayason hayaniya. Fadawa tayi kan gado tana Girgiza kanta, tasake tuna lokacin datake cikin adedeta ance mata Mahmud Wakili yazo shi aka sauka acikin gidajen data Gani,gabanta ne yake faduwa, meyake shirin faruwa ne?To Amma Kuma ai yace mata shi Yaron Mahmud Wakili ne bare tayi tunanin ko qarya yake mata, tasan cewa Shahaab bazai ta6a yimata qarya ba, Shahaab bazai fada mata abinda bashine ba, yanada Hankali, Kuma yanada nutsuwa, sannan babba ne yanada shekaru, bazai yi mata qarya ba, lokaci daya kanta ya d'aure, tarasa waye zai bata amsa, wayar Hajja ta d'auka cikin sauri har hannayenta na karkarwa tafara Kiran layinsa, saide Kuma wayar tasa akashe(🤦🏻‍♀️) Tana daga d'akin tajiyo Abba ya dawo, kujera yar tsugunno yaja ya zauna agaban Hajja dasu Ummah, sannan yace "naje na kaiwa Alhaji Ali Biron, yace zai Kai a siyar dashi,zan jira shi inji Yaya ake ciki" Hajja tace "nifa mamuda itama Walidan data fadi maganar kallon mahaukaciya nake mata, tsakani da Allah tayaya me sunan qawa zata samo wani biro har dubu Dari biyar?to kaima tun kafin infara yima kallon mahaukaci kawai kayi shiru" Abba yace "Hajja kenan,bakisan abinda yarinyar Nan take qullawa bane" Jin abinda Abba yace yasa gaban Aisha faduwa, kode Abba yasan tana kula Shahaab? Kafin Hajja tayi magana suka jiyo sallama daga kofar gida, jabir ne yatashi yafita, Sai gashi ya dawo yace "Abba Ana sallama dakai" Kallan jabir yayi yace "nikuma? Suwaye?" Jabir yace "wasu baqi ne, Amma Naga tare suke da Bulama" Abba yace "baqi tareda Bulaman Gari? to Bari naje," Yafadi hakan tareda nufar kofar gida. Yana zuwa yaga baqi su hudu, tareda bulaman Garin,hannu ya basu suka gaisa, daya daga cikin baqin ya kalleshi yace "kaine mamuda?" Abba yace "eh nine,meyake faruwa?" Yace "karka damu babu komai, munzo ne daga National Hajj commission,ma'aikatar aikin Hajji, muna farincikin sanar dakai sunanka yafuto acikin jerin Wanda zasuje Umara cikin wannan satin, sannan danka yasamu gurbin karatu a qasar Australia, zamu wuce daku dutse domin yimuku international passport" Abba yayi shiruu kamar baiji abinda suka fada daidai ba, cikin tsananin mamaki yace"ranka yadade Saudia de Dana Sani?Kai inaga de kuskuren adreshi kuka samu" Daya daga cikinsu yace"Muma Umarni ne muka Kar6a daga sama,kashiga kasanar agida muje mucika umarnin da'aka bamu" Cikin mutuwar jiki Abba yajuya cikin gida tunani fal ransa, dama mutum yana samun karatu ne batareda yanema ba?jabir din dasuke fafutuka yasamu ko legal Ringim ne yatafi yayi diploma shine yanzu yasamu gurbin karatu a qasar waje? Tayaya? Yanzu a wannan zamanin har akwai mutumin dazai biyama Saudia ne batare da yasankaba? Kuma sunce umarni aka basu daga sama, hakan na nufin koma wanene yasaka su to wani Babban ne a qasar, Kuma yayi bincike sosai akansa tunda gashi har yasan yanada d'a namiji Yana qarasawa cikin gidan yafadawa Ummah da Hajja abinda yake faruwa, Hajja tace "to mamuda, dayake Saudia de Kiran Allah ne bazan hanaka zuwa ba, Amma abun da mamaki ace an dauki nauyin karatun jabir, kaikuma anbi Yama Umara, to waye ne wannan?" Ummah tace "Hajja koma wanene ba qaramin masoyinmu bane, wataqila lokacin da zamuji dadi ne yazo, Allah yasaka masa da alkhairi, yasa ladan abunda yayi yadinga binsa har qabarinsa" Abba ya jijjiga Kai yace "hakane, Amin ya Allah" Cikin sauri Aisha tafuto daga daki tace "Abba Allah yasanya alkhairi" Baice da'ita uffan ba, Sai kallon jabir da yayi yace "Kai taso muje" Cikin sauri jabir yatashi suka fita, Kai tsaye dutse sukaje kamar yanda mutanan suka fada, anyi musu passport duka su biyun,Wanda sukaje gida suka Dauko su sune suka kar6i passport din, sannan suka dubi Abba, daya daga cikinsu yace "Zaku iya komawa gida, yanzu zamu Kai passport din Abuja, za'a yi muku visa" Abba de da yaga abun nasu da gaske ne, saiya tsugunna yafara yimusu godia, cikin sauri suka tarbeshi yatashi tsaye, sannan sukace babu komai, Abba har hawaye yake yana qara yimusu godia, daqyar suka samu yayi shiru, sannan sukai sallama dasu Basu koma gida ba Sai dare, agida ma magana daya aketa maimaita wa, mata Sai sallama suke yi a gidan anayiwa Hajja Allah yasanya alkhairi mamuda zai tafi Umara, Abba yarasa Ina Yan gari suka samu labari, Amma daya tuna da Bulama saiya Dena tunani akan hakan. (Shahaab littafin kudi ne, ki biya naira 300 kacal ki karanta abinki, duk wadda ta karanta batare data biyani haqqina ba nabarta itada mahaliccinta, 0164549488 Amina muhammad GTbank) ****** Cikin dare hadari yahadu sosai, Nan da Nan aka tsinke da ruwan sama, acikin wannan ruwa Aisha tatashi tafuto tayi alwala, kafin Takoma daki duk ta jiqe, Dakin Takoma ta kunna wayar Hajja ta shimfida sallaya, sannan ta kashe hasken wayar tacire kayan jikinta, ta dauki wani kayan tafara sakawa, cikin rashin Sani tad'an bigi breast dinta,cikin sauri ta runtse idonta saboda zafin dataji, tarasa meyasa wani lokacin suke mata ciwo, sannan Kuma kullum cikin qaruwa suke, hijabi tasaka sannan tatada sallah, Bayan ta idar haka ta dinga addu'ah Allah ya dawo da Shahaab lafiya domin ya wanketa akan wannan biro, yazo yafada musu Bahaka bane, sannan tayi wa Allah godia akan abun farincikin daya samu Abban ta da jabir, tayi musu addu'oi sosai, sannan ta kwanta awajan tana istigfari, batasan lokacin da bacci ya dauketa ba, saiji tayi Hajja tana tashin ta sallar asuba. Tunda suka tashi da safe ta gaida Abban ta taga ya amsa mata daqyar, jikinta yayi sanyi, haka Takoma Dakin Hajja ta kwanta batareda kowa ya lura da yanayin datake ciki ba, da yamma Alhaji Ali yazo gidan yayi sallama da Abba, Abba na fita suka gaisa da Alhaji Ali, anan Alhaji Alin yaqara tayashi murna saboda samun labarin Dayayi Abba yasamu kujerar umara, sannan yaqara da cewa "Mamuda ga wannan kudin, jiya nakira wayar ka akashe, dama inaso in fadama ne Wanda yake siyan Biron baya Nan, Sai yaransa nasamu, sukuma sunce bazasu siyeshi haka ba saboda babu kwalin Biron, danhaka zasu iya siya dubu Dari hudu da hamsin, ga kudin Naka" Jikin Abba ne yafara rawa ganin wannan uban kudi, ,qafafunsa suka fara karkarwa yana neman faduwa, ahankali yasaka hannu ya kar6i kudin sannan yace "nagode Alhaji Ali, zanzo gidanka anjima" Alhaji Ali yayi godia yajuya yatafi, Abba kuwa duhu duhu yake Gani daqyar yakai Kansa gida,yana zuwa ya zauna akan tabarmar da Hajja da Ummah dakuma jabir suke zaune, ya ajiye kudi agaban Hajja, tsorata sukai da yawan kudin, cikin 6arin jiki Hajja tace" mamuda Ina kasamu wannan uban kudin?" Baice da'ita komai ba, ya kalli jabir yace"kiramin yayarka" Jabir yaje Dakin Hajja yace "qawar Hajja kizo inji Abba" Haka kawai taji faduwar gaba ta ziyarceta, cikin sanyin jiki tafuto ta zauna akusa da Hajja, ahankali tace "Abba Gani" Abba yajuya ya kalli Hajja yace "to Hajja gatanan, wannan kudi da kike Gani kudin biro ne, saboda haka ta bude baki tafada mana waye yabata Biron? Saboda ni kwata kwata ban yarda da yarinyar Nan ba" Yajuya yasake kallon Aisha da kanta yake qasa, idonta Yacika taf da hawaye, sannan yace "AISHA...., fadamin waye yabaki wannan Biron? Sannan Ina kike zuwa da daddare?" Cikin sauri Hajja tace "bangane Aisha haka Kai tsaye ba mamuda, sunan qawar tawa kake kira haka? Ashe zaka iya kirana Kai tsaye Nima? To Bari kaji idan baka yarda da wannan yarinyar ba mamuda Nina yarda da'ita,tayaya za'ace biro qwaya daya jal nera dubu Dari hudu da hamsin? To shi Biron baya qarewa ne?"(🤔) Abba yace"Hajja wannan biro haka kudinsa yake, kuma qarya take tasan inda taje ta Nemo shi, saboda ban yarda da ita ba, ta bude baki ta fadamin gaskiya kokuma yanzun Nan inyi mata dan'iskan duka wallahi" Hawaye ne ya zubo daga idonta, ahankali tafara shashshekar kuka, cikin wata irin murya tace "Abba Dan Allah kayi hakuri" Cikin 6acin rai Abba yace "ta tabbata kenan abinda malam Manu ya fadamin gaskiya ne ko? Irin tarbiyar Dana baki kenan ko?" Hajja ta kalli Aisha tafara tafa hannu tana salati, tace "Nina Rasa abun damuwa anan mamuda, waime kake nufi da wannan maganar taka ne? Memakon kayi murna yarinya tafara samo mana kudi Amma Naga Kai tuhumar ta ma kake, ni idan hakane ai jummai rufata tayi, inusa ba mijin aure bane, duk Wanda yabawa mesunan qawa wannan biro ai shine mijin aure "(🙄😂🙆🏻‍♀️) Ummah ta zubawa Aisha ido tana kallonta, Sarai tasan akwai abinda take 6oye musu, yanayin ta kawai zaka kalla kasan batada gaskiya,tsoronta daya kartaje wani marar tsoron Allah yayi amfani da rashin wayon 'yartata yana amfani da'ita awani waje, saboda babu Wanda zaiga qirar Aisha yaji bai kwadaitu akanta ba,share Hawayen idonta tayi,cikin muryar kuka Ummah tace"waye yabaki Biron? Sannan Ina kike fita da daddare?" Cikin kuka tace" Ummah ni gidansu Walida nake zuwa" Abba yasa hannu yad'auki wayar hajja dake ajiye agefe, number Walida yadubo yakira Walida yasa ta a amsa kuwwa yanda kowa zaiji abinda take fada, Walida tana daukan waya Abba yace "Walida mamuda ne" Cikin ladabi ta gaishe shi, Shima ya amsa mata, sannan yayi mata ta manya yace "meyasa bazaki yiwa qawar ki fada bane ta dinga zuwa gidanku da rana, Amma kullum saide tazo da daddare, mu kinga munyi mata fada, taqi jin maganar mu" Walida bata gane shan cikinta Abba yake ba, tayi murmushi tace "Abba da daddare Kuma? Ai Aisha bata zuwa da daddare, sau daya tata6a zuwa wajena da daddare Kuma Shima narakota har gida, ka tambayi su Hajja zasu fadama ma nazo gidan" Abba yace "eh anyi haka fa, na manta wallahi, toki gaida mutanan gidan" daga Nan yakashe waya. Kukan Aisha ne yake tashi awajan, sosai take kuka harda Jan zuciya. Abba ya kalleta yace "muna jinki, wajan wa kike zuwa?" Cikin kuka tace "SHAHAAB" Hajja tanajin haka tafara tafa hannu,Nan da Nan hawaye yafara sauka akan kumatunta, cikin mamaki tace "mesunan qawa?,to kode shine yabaki ribbon din Dana Gani a kanki kikace Walida ce tabaki?" Babu musu ta daga kanta alamun hakane, Cikin 6acin rai Abba yatashi ya wanketa da Mari yace "waye SHAHAAB?" Zafin Marin ne yasa tasaka hannu ta dafe kuncinta, muryarta na rawa cikin kuka tace "shi.... Shin.. Shine yake zuwa yake kirana awaya Sai naje, Abba Allah Ina sonsa nide" Wani Marin Abba yasake mata, cikin 6acin rai da takaici yace "shine kike binsa har cikin mota yana hure miki kunne ko? Ai kinsan da maganar inusa, wato irin mayaudaran samarin Nan ne yake zuwa wajan ki yana hure miki kunne harni Zaki kalla kina cewa ke kina sonsa ko? Idan na qara ji kince kina sonsa saina kakkarya ki a gidannan, Kuma daga yau babu ke babu shi,inusan damuka Sani shi zamu baki" Cikin kuka tace "Allah banason inusa, nide Shahaab nakeso" Jin abinda tace yasa Abba yayo kanta zai rufe ta da duka, cikin sauri Hajja tajanyota jikinta, Hawaye ne suka sulalo daga idanun Ummah,koma waye wannan Shahaab haqiqa yariga yagama hurewa yarsu kunne, tunda gashi har mahaifin ta yana fada itama tana fada. Hajja tasaka salati tana sake rushewa da Kuka, cikin kukan tace "wannan masifa Dame tayi kama? Mesunan qawa Ina kika samo wani Shahaab Kuma? Yaushe Zaki bi saurayi har cikin mota? Kifadamin su waye iyayensa inje inji Dame suke taqama da dansu zaizo wajanki batareda ubanki yasani ba?" Cikin kuka tace "Hajja ni bansan iyayensa ba, Kuma nide Allah Shahaab nakeso" Hajja tace "to inajin de aljani ne, Danni banta6a jin irin wannan sunan ba, saide a jinsin aljannu, ninasan ba zakiyi haka da niyya ba mesunan qawa, Gamo kikai da aljan" Abba yace "babu wani aljani Hajja, Sai iskanci dayake damunta, Kuma ni bazata 6atamin suna ba, bazata janyomin abun kunya agida ba...." Jin furucin Abba yasa Hajja tasake rushewa da Kuka tace"mummunan bakinka ba'a kan mesunan qawa ba, inda zatayi ciki da tuni tayi, jinake can unguwar gabar Yara suna Nan sunkai su talatin kowacce cikin shege ne da'ita, ita kanta Malamar asbitin dasuke zuwa wajanta take zubar musu cikin itama cikin shegen ne da'ita, Bayan Wanda ta haife, Amma ninasan Mesunan qawa inde tabiyo halin takwararta to ba zatayi cikin shege ba" Ummah ta kalli Hajja da sauri, yaushe akayi ciki agarin har mutum talatin? (😂🤔) Tagama lura cewa soyaiyar Aisha tasa kwata kwata Hajja bata ganin laifin yarinyar,ko kadan bazata iya tsawatar mata ba,Abba yace "tunda kince kina sonsa, tona tabbatar kona miki katangar qarfe tsakanin keda shi watarana bazan San lokacin dazaki tsallake kije wajan sa ba, danhaka ki shirya, zanje in samu jummai infada mata ta shirya takaiki can kano, daga Nan kuwuce Abuja akai ki gidan Mahmud Wakili aiki, tunda da naji tausayin ki nace ba zakije ba Gara ki zauna agaban mu abaki inusa, to yanzu Gara kije, dade ki zauna agari kina satar fita kina shiga motar saurayi bansan meyake miki ba, Gara kije can kikama aiki" Yana fadin haka yafice daga gidan, Bai Zame ko'inaba Sai gidan Jummai qawar Hajja. Aisha kuwa kuka tasa harda burburwa a jikin Hajja, "Hajja ki masa magana, Allah ni bazanje ko'inaba,Ina ruwana da wani Mahmud Wakili da zanje gidansa aiki, Kuma arasa gidan Wanda zanje aiki Sai wani Mahmud Wakili?, aini ba baiwar sa bace...." Hajja ta share Hawayen idonta ta kama hannunta zasu shige daki, Aisha ta qwace hannunta taci gaba da kuka, Ummah tatashi ta wuce daki, domin kuwa ita hukuncin da mamuda ya yanke yayi mata daidai,babu Wanda zai nuna mata son Aisha kaf duniyar, Amma hakan ba zaisa taqi Bawa mijinta goyon baya akan tarbiyar yarinyar ba. Jabir ne ya matso wajan ta yad'ora hannunsa akan dogon gashinta daya barbaje saboda kukan datasha, kannata yake shafawa tareda bubbuga bayanta alamun tayi hakuri, Shima kukan yake bashida bakin dazai iya lallashin yayar tasa, tana jinsa tafada jikinsa sukaci gaba da kukan gaba daya. Awannna rana wuni sukai gidan babu dadi, Aisha banda Jan zuciya babu abinda take, abinci ma taqi Ci, Sai sharar hawaye take, Hajja tabata haquri harta gaji, ta qanqame wayar Hajja tana ta gwada Kiran Shahaab Amma abun baqin ciki waya taqi shiga, har dare Aisha tana daki taqi futowa waje, tana jiyo Abba yana shaida musu gobe jummai zatazo ta dauketa su tafi, jin babu Wanda yayi masa magana akan hukuncin nasa yasa wani sabon hawaye ya silalo daga idonta, baqin ciki yataru yazame mata goma da Ashirin, har gara ace wani gidan zataje aiki akan de taje gidan Mahmud Wakili,mutumin da kullum burinsa shine kamawa talakawa kayansu da kudaden su shine abinda ya'iya? Banda gidan man malam Audu daya saki bata ta6ajin inda akace yasaki gidan man wani ba, wayar Hajja tasake d'auka tafara Kiran layin Shahaab, saida ta kirashi yakai Sau goma,saide amsar guda daya ce, shine wayarsa akashe take. Haka kowa yayi bacci Amma idon Aisha biyu, mutumin da taqi jininsa, Wai itace zataje gidansa aiki, Shahaab ne kawai zai fiddata daga wannan qulli, shikuma baya Nan, shin yasan Biron Dama haka kudinsa yake? Shine yasiyo mata da Kansa? Ko wanine yabashi? Shida yake Yaron Mahmud Wakili yaushe har zai samu wannan uban kudin? Anya ma kuwa yasan wanne irin Biro yabata? Haka ta dinga tunani tana yiwa kanta tambaya Wanda babu me amsa mata su Sai Shahaab, shikuma yamata Nisa. Tana cikin wannan hali batasan yaushe bacci ya dauketa ba, washe gari haka ta zauna adaki taqi futowa, abinci ma qinci tayi, tun hajja tana lallashinta harta gaji taqyaleta, wajan qarfe goma Sha daya Abba yashigo tareda jummai, yana zuwa yacewa Ummah "kira mata Wannan yarinyar zasu tafi yanzu" Cikin sauri Hajja tace"innalillahi wa inna ilaihirraji'un.... Yanzu mamuda da gaske kake ashe,? Yanzu rabani zakayi da me sunan qawa,?to babu inda yarinyar Nan zataje " Cikin nutsuwa yace" Hajja, tafiyar ta shine yafi alkhairi, zamanta anan bansan wacce irin magana zata Dauko min ba" yana fadar haka yashige Dakin Hajja yakamo hannun Aisha suka futo, kuka take tana Kiran Hajja, Hajja ta kama hannunta ta riqe itama tana kuka, daqyar Abba ya fizgeta suka fita waje, wata yar qaramar mota ce a kofar gidan, cikin motar yasaka ta, sannan jummai tashiga, shikuma yarufe musu motar, yasunkuyo da Kansa ta window yace "idan kunje kano, Akira hajiyar a tambayeta aji koda tasamu yar aikin to asake tura mata Aishan ko bude get ne ta dinga yi musu, zamanta acan din Hankali na zaifi kwanciya, nasan babu ita babu haduwa da wannan Yaron dayake hure mata kunne" Aisha tana jinsa saide ko d'ago kanta batayi ta kalleshi ba, kanta na cikin qafafunta tana kuka. Jummai tace "karka damu mamuda, nasan ma za'a dace insha Allah, bazan dawo gida Bama Sai an tabbatar min sunje Abujan lafiya, kayi mata addu'ah" Cikin sanyin jiki yayi murmushin qarfin Hali, tareda barin jikin motar yana juyawa gida, shi Kansa bazai so yarsa mace qwaya daya jal tayi nesa dashi ba, Sai dole, yana tare da'ita gida daya bai ta6a sanin akwai Wanda yake zuwa yana Kiran yarsa ba, zancen ma yawuce kofar gida agaban jama'ah saide a mota, Allah ne kadai yasan abinda zai faru inba Allah ne yakiyaye ba, juyawa yayi ya kalli motar yayinda suka fara tafiya, cikin ransa yana Binta da kyakkyawar addu'ah, Idonsa nakan motar har suka yi Nisa yadena hangosu. Da alama Jummai ta shirya yin futo na futo tsakanin ta da Hajja😎😎 to, takwara tatafi wajan takwararta🙄, rashin kunya tatafi wajan masifa da iko🥹🥹 Wannan shi ake kira, angudu ba'a tsiraba 💁🏻‍♀️mahaifi yatura 'yarsa inda yake gudu 😇 Menene zai kasance Idan Shahaab ya dawo yaga Aisha acikin gidansa?🤔 Yaya makomar qaryaiyakin daya dinga shuka mata?🤔 (SHAHAAB littafin kudi ne, idan kika karanta min batareda kin biya ba, nabarki keda mahaliccinki,nera 300 Ne kacal bansaka kudi me yawa ba 0164549488 Amina muhammad GTbank My number 08033300034 Mutara zuwa gobe 🙏🏻 Amnah El Yaqoub✍🏻 Salam Alaikum,masu fitar min da littafi nagode, masu karanta wa batareda sisinsu ba nabarku kuda ALLAH,nide ban yafe muku ba, bazan yafe ba Kuma har abada, nabarku da futowar rana da faduwarta. Masu cewa indinga yin posting biyu a rana kuyi haquri gaskiya bazan iyaba, Alokacin danace zan dinga yin posting biyu a rana, nayi tunanin yin VIP group 500, shine nace zan dinga yin posting biyu, to yanzu 300 dinma wasu suna cewa ta musu tsada,shiyasa nafasa yin VIP din, maganar posting biyu ta rushe, duk page guda daya, Ina bata awa hudu ne akansa, awa uku typing, awa daya editing, tayaya zan dinga bata awa takwas a rana inyi page guda biyu? Ayyukan gidan Ina zan kaisu? Masu min magana ta private inyi Yaya dasu? Masu kirana inyi Yaya dasu? Gaskiya kuyi haquri, kullum zamu dinga posting daya, idan Allah yasa nasamu lokaci zakuga posting biyu, idan bansamu ba zakuga daya, duk lokacin dakuka ga guda daya please 🙏🏻kuce Allah yayi masa Albarka Faqad👌🏻. Page 22 Ganin tafiya de tazama dole yasa tabawa kanta haquri tayi shiru har Allah yakaisu kano lafiya, Bayan sun huta sun d'anci abinci Hajiya Amina tace "baba jummai ai nayi zaton kunfasa kawo yarinyar ma, itama Kuma Hajiyan bata sake kirana akan maganar ba, Amma gaskiya Ina tunanin tariga tasamu ma, Bari de inkirata inji Yaya ake ciki" Addu'ah Aisha take a ranta Allah yasa tariga tasamu din, ba komai ne yasa take kukan barin gida ba Sai rabuwa da Hajja dakuma tunanin yanda Shahaab zai dawo yaji labarin bata Garin. Jin Hajiya Amina tana magana awaya yasa tamaida Hankalinta kanta, Bayan sun gaisa cikin ladabi Hajiya Amina tace "Hajiya Mama Dama akan maganar me kula dakene, nace gashi ansamu wata yarinya idan har yanzu baki samu ba" Daga can 6angaren mama tayi magana, Sai Hajiya Amina tace "a a wallahi yarinya ce qarama baki ganta ba, Kuma babu qazanta a tareda ita, ke kanki Sai hankalin yarinyar ya birgeki, babu wani datti tsaf take, babu Wanda zaice yar aiki ce" Mama ce tasake magana, Sai Hajiya Amina tasake cewa "to.... To shikkenan, saisun zo d'in, babu komai wallahi Nima nagode" Aisha tanajin haka ta Lumshe idon ta, shikkenan tafaru ta qare. Kallan su tayi tace "to Alhamdulillah tace ba'a samu ba, Aisha saiki huta yau, gobe zansa driver daga Nan yatafi dake, zai Kaiki har can insha Allah" Jummai tace"to yanzu Amina Yaya batun kudin aikin ta?saboda idan nakoma inshaida wa mahaifinta yanda mukai dake " Murmushi tayi tace"idan taje gidan Hajiya Mama zata fad'a mata yanda zata dinga biyanta, Nima tace zata turomin wani abu ta account dina, Baba jummai Aida kinsan gidan da Aisha zata tafi da bakiyi min maganar kudin aikinta ba, saboda duk Wanda suke aiki a gidan suna samun alkhairi sosai, bare Kuma Nata aikin special ne, bawani aikin wahala zata dinga yiba," Tajuya ta kalli Aisha sannan tace"Aisha idan kikaje babu ruwanki da harkar kowa kinji ko? Mahmud yanason mamansa, zai iya yin komai saboda wannan tsohuwar matar, bayason abinda zai 6ata ranta, Kuma zai iya 6atawa da kowa saboda ita" Iya jummai tace "yawwa to ai Gara kifada mata tun yanzu kinga idan taje gidan shikkenan tahuta da bincike akan halaiyar 'Yan gidan, menene ma zai had'ata da wannan matar bare har ta 6ata mata rai?" Hajiya Amina tace "inde ta kiyaye tsakaninta da mama to ai batada wata matsalar komai, saboda a yanda naji shine, Mahmud din yana son matarsa sosai, amma duk soyaiyar dayake mata inde ta 6atawa mama rai to sa6ani take samu dashi" Tunda suka fara magana Aisha bata saka musu baki ba Sai yanzu, ahankali tace "yanada mata?" Murmushi Hajiya Amina tayi tace "haba Aisha, Babban mutum kamar Mahmud Wakili ai dole ya ajiye iyali, Amma ke ai ba 6angaren matarsa zakije ba, kefa kina wajan Hajiya mama, duk ayyukan da zakiyi to abinda ya shafi mama ne" "wanne irin aiki ne?" tasake tambaya Hajiya Amina tace "Zaki dinga kula da'ita, zaki dinga riqe hannunta kudinga Dan tattaki a gidan saboda ciwon qafafunta, zaki dinga matsa mata qafafunta, idan angama abinci Zaki zubo mata ki kawo mata, zaki dinga yimata hira saboda karki Barta cikin tunani" Aisha ta Jinjina kanta tayi shiru, irin wannan hidima haka saikace basarakiya?(🤔) Iya jummai tace"saboda Allah yanzu wannan har aiki ne?ai wannan bazaka kirashi aiki ba tunda kince matar ta manyanta wannan aikin ai idan ka taimaka mata kaima zaka samu Lada,tobakada aikin fari bare na baqi kawai zama fa zakayi tareda ita," Tajuya ta kalli Aisha tace"me sunan Hajja,kisa aranki saboda Allah Zaki mata komai, sannan ki kalleta kamar Hajjanki, insha Allah sakamakon ki yana wajan ubangiji" Haka suka dinga zancen gidan har dare, kasancewar akwai kayan kallo a gidan Sai Aisha tad'an saki ranta tana kallo,lokaci zuwa lokaci Hajja da Ummah suna Fado mata Arai. ****** Hajja ta kalli Ummah da Abba tace"yanzu mamuda abinda ka aikata kayi daidai kenan? Yarka guda daya jal 'ya mace ka dauketa ka rabamu da'ita? Mamuda kodan yanda na shaqu da mesunan qawa ashe bazaka Gani ba?bansan cewa bakada mutunci ba Sai yau, Ina kuka yarinyar Nan tana kuka haka ka rabani da'ita, ai shikkenan babu komai, yau ka nunamin kafini iko akan AISHA" Tana qarasa fadar haka ta Fashe da Kuka, cikin sauri Ummah ta kalleta jin sunan AISHA data fada Kai tsaye, abinda bazaka ta6aji Hajja tafada ba, ahankali tace"Hajja kiyi hakuri, abinda yasa bansaka baki ba akan maganar yarinyar Nan, Hajja ke kanki sheda ce munbawa Aisha tarbiya, kema kin bata, Aisha tana da Hankali, Barta de da rashin kunya wani lokacin, Amma abun mamaki da tsoro shine yanda ta'iya kallon idon mahaifin ta tace ita Shahaab take so, yana Dukan ta Amma yarinyar Nan haka take sake fada ita Shahaab take so, Sai abun Nata yabani tsoro, lokacin da akazo da maganar inusa ko musu batayi da mu ba, Amma zuwan wannan yaro Shahaab cikin rayuwar ta gaba daya ya sauya mana tunanin Aisha, yanzu dasuke shiga mota suna zance bamu San yaushe take zuwa wajan sa ba, inda ciki nema haka zaiyi amfani da qananun shekarun ta yayi mata, Amma Kuma saida tatafi nake jin kamar mun aikata kuskare, Ina tsoron kar Yaron Nan Shahaab yabita can Abujan suci gaba da abinda suke" tana fadar haka tafara share hawaye Hajja datake kuka tace"kul Hadiza, banaso na qara ji kince mesunan qawa zata aikata wannan mummunan aikin, inde halin takwararta ta'iyo babu abinda zata aikata, kuskure de ubanta gashinan yariga yayi, duk abinda yabiyo baya, saiya kuka da Kansa" Tana fadar haka, ta share Hawayen idonta tatashi tashige dakinta tanajin kamar zataga Aisha tana game a wayarta. Ajiyar zuciya Abba ya sauke yana sake gaskata wa zuciyar sa cewa dade ace yabar Aisha anan, Gara tatafi Abujan yafi masa kwanciyar Hankali, ko banza idan Yaron yazo yagaji da zuwa zai haqura yabar masa yarsa ****** Washe gari karfe Goma nasafe suka tafi, jummai bata tafi ba saida taga tashin su Aisha sannan itama tafara haramar tafiya gida. Sai Bayan la'asar suka Isa Abuja, Aisha tun tana bacci tana farkawa harta daina,bata ta6a tafiya me Nisa irin wannan ba, Sai abun yazame mata Sabo, tunda suka shigo cikin Garin kuwa tabaza ido tana kallo, sunyi tafiya me Nisa sosai acikin Garin sannan suka qaraso wani tanfatsetsen gida, baki bude take ganin tsaruwar gidan, yanayin unguwar babu hayaniya, Babban titin daya kawoka har bakin get din gidan ta kalla babu wasu mutane dasuke zama awaje kamar yanda akeyi a garinsu, Lema ce a kwance akoi'na alamun ruwa aka gama yimusu, Sai yanayin Garin yasake yin kyau, bata gama mamaki ba taga sojoji sun bude musu get din gidan, saida direban ya basu wani I'd card suka Gani sannan suka barsu suka shiga, batasan dalili ba haka Nan ta tsinci kanta da faduwar gaba har Sai tafara karanta "hasbunallahu wani'imal wakeel" acikin ranta. Motar su tana tsayawa aharabar gidan taga sojoji ta ko'ina suna shawagi, Sai yanzu tasake ganin kyan gidan, tashin Hankali ne ya wanzu akan fuskar ta, yanzu wannan gidan mutane ne suke rayuwa aciki gida kamar aljannar duniya? Sai yanzu ne tasake tabbatar wa Mahmud Wakili ba qaramin mutum bane, duk yanda ake bata labarinsa ashe yawuce haka, wannan shi ake kira jinka yafi ganinka. Direban ne yafuto yabude mata motar yace "futo muje" yanda yabata girma harda su bude mata mota yasa Shahaab yafado mata Arai, duk yanda yake da kyau dakuma shekaru bude mata mota yake kamar itace shugabar sa, kawar da tunanin tayi daga cikin ranta suka qarasa cikin part din Hajiya Mama. Tsaruwar falon Nata ne yasa Aisha tasake daga kanta ta kalli falon sosai, batace komai ba face Jinjina kanta datayi, wata mata ce zaune acikin daya daga cikin kujerun falon ta dora kafarta daya Kan daya,banana ce a hannunta tana karya kamar bata son ci, hankalin ta nakan abinda ake yi a TV. duk da daga nesa ta hangeta saita ga batafi Hajja shekaru da tsufa ba, daya daga cikin masu aikinta dake tsaye abakin kofar itace tace dasu "sannunku da zuwa, ku qaraso" Direban ne ya amsa da "yawwa" sannan tayi musu jagora zuwa wajan mama, qasa ta tsugunna tayi wa mama magana sannan ta juya zuwa kitchen Cikin farinciki mama ta juyo ta Kalle su tace "sannunku da zuwa,mutanan kano ne?" Aisha batayi magana ba Sai kallon matar take, haka kawai taji matar ta kwanta a ranta,kwata kwata a shekaru batafi Hajja ba, saide kana ganin ta kaga hutu da jin dadi daram ajikinta, tayi tunanin zata yi musu kallon wulaqanci a yanda ake bada labarin izzarta. Zama sukai har suna hada baki wajan gaida ta, cikin murmushi tace"sannunku da zuwa," ta maida kallonta ga Aisha tace"yar kyakykyawa kece Mai aikin?" Cikin sauri Aisha ta kalleta sannan tayi qasa da kanta, cikin ladabi tace "eh nice MAMA" Jin yanda ta kirata da mama Sai hakan yayi mata dad'i, duk yanda akai yarinyar tanada nutsuwa, cikin jin dadi tace "masha Allah, kema daga kano kike?" Kanta aqasa tace "A a Jigawa" Gaban mama ne yafadi,jin sunan Garin yasa ta tuna da qawarta Aysha Sulaiman Bompai, Sai taji a ranta koda batada ra'ayin yarinyar to dole zata sake riqeta saboda tafuto daga jihar da qawarta tayi aure, dalilin Garin dole zata dauketa, cikin murmushi tace "menene sunanki?" "AISHA" tafadi hakan kanta tsaye. Mama tace "masha Allah,kice tsohuwa ce" Murmushi su Aisha sukayi, Adede lokacin Mai aikin takawo musu abun motsa baki, mama tace "kikai masa Dakin baki saiki dawo kitafi da Aisha" Cikin ladabi tace "to mama" Tashi Direban yayi yabi Bayan me aikin, Bayan sun tafi mama tasake kallon Aisha tace "Aisha kisaki jikinki kinji? Maganar gaskiya Ada maiyi min hidima nace akawo min, to Amma kasancewar kinfuto daga jihar datake da dumbun tarihi awajena, saina ji bazan iya sakaki aiki ba, idan babu damuwa zan dauke ki kamar jikata, Nan gidanku ne, kidaukeni kamar mahaifiyar ki, ni banida matsala inde anyi min abinda nakeso, abu daya nakeso kikula dashi shine banaso idan Dana yazo inda nake Inga wani mahaluqi awajena, inde Mahmud yana tare Dani inaso inganni nida shi mu biyu" Cikin ladabi Aisha tace"insha Allah zan kiyaye mama" Mama tace"kinada account ne Wanda za'a dinga tura miki kudin aikinki aciki?" Cikin mamaki tace "kibarshi mama, ba saboda kudi Abbana yaturo ni aiki ba saidon laifi Dana aikata masa Kuma yake hukuntani ta wannan Fannin, koba Dan haka Bama Ina ganinkine kamar Hajja ta, saboda haka zan yi miki komai tsakani na da Allah Kuma saboda Allah" Cikin mamaki mama ta kalleta, awannna zamanin har za'a samu yarinya wadda abun duniya bai rufe mata ido ba kamar wannan yarinyar? Jitayi yarinyar tasake birgeta, tun farko irinta taso Allah yabawa Mahmud dinta,Amma Allah baiyi ba. murmushi tayi tace"Aisha ai ba'awa iyaye laifi, biyaiya ake musu sosai, yanda Mahmud yake kyautata min yakemin biyaiya inda yaji cewa kinyi wa iyayenki laifi har suke hukuntaki toda saiya zaneki"(😄) Murmushi Aisha tayi tafara wasa da yatsun hannunta, (nikam nace me zanewa ai shine maqasudin me laifi mama 😂) Adede lokacin yar aikin tadawo, mama ta kalli Aisha tace"za'a bude miki account Sai Adinga saka miki kudinki aciki, wannan haqqin ki ne, bazan tauye miki haqqi ba, tashi kuje zata nuna miki d'akin ki, kiyi wanka kici abinci kihuta, zuwa gobe" Tajuya ta kalli Mai aikinta tace"Mansura baquwa ta ce wannan, takawo min ziyara ne daga jigawa, a kaita daki na musamman" Cikin ladabi mansura ta amsawa mama, itama Aisha tayi wa mama godia tana tunani fal ranta, wacce irin mata ce wannan? Ita datazo aiki meyasa ta 6oyewa yar aikinta tace ita din ziyara ta kawo mata? To menene na jihar Jigawan tayi mata dahar take ganin qimarta saboda kawai tace daga jigawa take? Haka ta dinga yiwa kanta tambaya har suka bar wajan maman. Acikin falon maman Dakin yake daga can Gefe, tsaruwar Dakin ne yasa Aisha ta shagala da kallon komai, daki saikace baza'a mutu ba, akwai komai na more rayuwa aciki, nuna mata komai tayi, sannan ta juya ta fita domin kawo mata abinci, tana fita Aisha ta zauna jagwab akan gadon Dakin, cikin zuciyar ta tace"duk wannan daular gidan saboda wannan tsohuwar? Aikuwa yanda na'iya zama da Hajja Toda kowama zan zauna" Har dare tana daki bata sake gigin futowa falon ba, tunda taji mama tayi mata kashedi akan idan danta yana Nan tana buqatar kebewa, saita rufawa kanta asiri tayi zamanta adaki, bata fatan ace ma ta ganshi, menene ma hadinta dawani danta bare har zaizo tazo tasasu agaba? Haka ta dinga tunani, daga qarshe Takoma tunanin gida, gashi de tana cikin gida har gida, Amma Kuma tana tunanin su Hajja, Sai yau taji taqaicin rashin waya, da yanzu kiransu zatayi taji muryar su, ko Hajja tayi kunun Aya yau? Haka ta dinga tunani har bacci ya dauketa Bayan tayi sallolin dake kanta Washe gari tunda tayi sallar asuba bata koma bacci ba, kitchen tashiga tana taya masu aikin yin wasu ayyukan, anan suka Dan saba da'ita ganin tanada budadden baki har suka sake wayar mata da kai akan yanayin gidan,yanda tasake dasu sosai ta basu mamaki, saboda Hajiya Mama bata ta6a yin baquwa wadda tashiga ransu kamar Aisha ba, gashi ita ba yar aiki ba Amma tashiga cikin su kamar wasu yan'uwanta, basu gama aikin ba Sai karfe bakwai da rabi, sukam kowa daki Takoma, tunda sungama aikinsu, saide idan mutanan gidan sungama bacci sun futo shine zasuzo su zuba musu, Aisha Kam bata koma ba, afalo ta zauna tana kallo har mama tafuto, less ne ajikinta wuyanta da hannunta d'aukeda sarqa da zoben gold,kana ganin ta kasan kudi, hutu, Dajin dadi ya zauna mata, cikin sauri Aisha ta gaishe ta, sannan tace "akawo miki abincin yanzu?" Mama tayi murmushi tace"nace kisaki jikinki tsohuwa, kidinga yin abunda yadace kawai basai kin tambayeni ba, saide idan kinyi idan Bana buqata zan sanar miki" Aisha tayi murmushi jin sunan da mama ta kirata tace "to insha Allah" sannan tanufi dinning tafara zuba mata abincin. Abincin takawo mata, maimakon ta zauna aqasan kujera, saita zauna akan kujera kusa da mama(😳🤭) Mama ta kalleta cikin mamaki, saboda ba'a ta6a yimata hakan ba, koda yaushe masu mutanan gidan girmamata suke, kafin tagama tunanin Aisha ta debo abincin a spoon tace "mama bude bakinki dakaina zan baki abincin" Wani irin shock ne yakama mama,lokaci daya Mahmud yafado mata Arai, inda ace tayi masa aure da wuri, da yanzu tanada Jika kamar wannan yarinyar, inama yanda halayen yarinyar yake, haka halin munirat yake? Da menene zaisa ta dinga Yiwa Shahaab maganar qarin aure? Murmushi tayi tace "Aisha Anya kuwa baki ta6a aiki awani gida ba kafin Nan?" Cikin sauri tace"a a mama,banta6a yiba,inajin ki araina ne kamar kakata Hajja, kiyi hakuri Bana daukar ki a matsayin uwar gidana, Ina daukar ki ne a matsayin kakata Hajja, inda Hajja ce take matsayin ki, Tozan iya goyata ma, saboda Hajja tana sona" Murmushi mama tayi, tarasa meyasa yarinyar ta kwanta mata fiyeda sauran Wanda take dauka aiki, ganin ta take kamar jikar ta, wani lokacin Kuma Sai halaiyarta ta dinga birgeta taji Dama ace Mahmud da'ita yafara haduwa, babu musu ta bude mata bakin, ahankali cikin kulawa Aisha tafara bata abincin, harta kammala munirat bata shigo part din na mama ba, dama Kuma Aisha batasan cewa akwai Wanda suke zuwa cin abinci part din maman ba ****** Tun karfe takwas munirat ta shirya cikin dinkin shadda Wanda aka kashewa kudi wajan dinki, mayafi ta yafa, tad'auki hand bag dinta tareda takardun filayen mama Wanda ta dauke batareda Shahaab din yasani ba, fita tayi tasa driver yakaita wajan wasu mutane, yana daga cikin mota ita kadai ce tafita, sun dade a tsaye da mutanan sannan ta basu takardun filayen, aka dauki kudi acikin wata jaka aka bata, kudin ta karba Takoma cikin mota, daga Nan banki suka wuce tabayar a saka mata kudin acikin asusun ta, bata dawo gidaba Sai wajan karfe goma Sha daya, Kai tsaye Part din mama ta wuce. Adede lokacin Aisha tana qasan kujera, mama tana zaune a kujera tana kallo, Aisha Kuma tana matsa mata qafafunta, hira suke kad'an kad'an mama tana sake yabawa da yarinyar acikin ranta, kodan irin sunanta Dana qawarta Aysha Sulaiman Bompai gareta? Ahankali tace"Takwara ta akwai kayan danayi miki order na sakawa, Naga bakizo da Kaya ba, idan aka kawo miki saiki dinga amfani dashi, Amma ai bazai iyu ace yanmata babu kwalliya ba" Aisha tayi murmushi kafin tayi magana munirat tayi sallama falon, daga Aisha har mama, kallon su suka Kai gareta, Aisha tana ganin ta haka kawai taji matar bata mataba, saide Kuma kallo daya zaka mata kasan cewa yar Gayu ce, tanaji da ado da wayewa ta Yan birni, qasa tayi da kanta, munirat ta qaraso kusa da mama ta zauna, tace "barka da safiya mama, nafita unguwa ne bansamu Dama nazo munyi break ba" Babu yabo babu fallasa Aisha tace mata "Ina kwana" "lafiya," munirat ta amsa a daqile Mama tace "Munirat munyi baquwa Baku haduba jiya, daga Jigawa State take, sunanta AISHA,nafada miki ne saboda ki kiyaye fadar irin sunan surukar ki,ga abinci can a dinning Zaki iya tashi" Munirat tayi shiru kanta aqasa, idan ta fahimci mama tana nufin karta kira sunan wannan bafulatanar yarinyar kenan, saboda irin sunanta gareta, to yanzu sotake ta kirata da ANTY AISHA kokuma MOMY AISHA? cikin danne fishin ta tamiqe tana cewa "wallahi na qoshi mama, saide ko anjima inyi lunch, a hanya Naga Goro har zan siyo miki Kuma wani abu ya dauki Hankali na bansiyo miki ba" Mama batace da'ita uffan ba, Aisha tayi tunanin zata tanka, Sai taji maman tayi shiru, anan tasake tabbatar wa mama akwai cikakken iko, Bayan munirat tafita Aisha tayi ajiyar zuciya tace "idan anyi niyar siyo miki ai saide kawai kigani mama"(😲) Mama tace "Aisha kenan,Allah yayi miki Albarka, Sai hakuri al'amarin, wannan itace surukata matar Dana MAHMUD WAKILI" Haka Nan Aisha taji gabanta yafadi, Amma bata kawo komai a ranta ba, saita kama addu'ah cikin zuciyar ta ****** Washagari jirgin Abba da jabir yatashi, Abba yatafi Saudia, jabir Kuma yawuce Australia, tunda aka fara musu hidimar tafiyar babu wata hanya da'aka Bari har su kasan ga sahihin mutumin daya dauki nauyin tafiyar tasu,tundaga ranar da sukaje dutse Abba Kam Yama manta da batun su, saboda kawai ganin abun yake kamar wasa, Amma haka mutanan suka sake dawowa tareda Mai Garin Garin, aka gama musu komai har suka tafi. gidansu Hajja shiru babu wani dadi saboda Abba baya Nan, jabir baya Nan, Aisha bata Nan, daga Ummah Sai Hajja, kullum jummai tana zuwa wajan Hajja domin Sudan zanta, Amma Hajja bata kulata, haushinta takeji saboda da'ita mamuda yahada Kai suka tura mesunan qawarta Abuja. Tunda Abba yatafi kullum saiya kira su ta wayar Hajja sun gaisa, har yau daya cika kwana takwas, yana shirin cika sati biyu sannan ya dawo gida. A bangaren Aisha kuwa yau tacika kwana goma a gidan, batada damuwar komai, tana zaune lafiya a gidan, Kuma har zuwa yanzun bata ta6a saka Mahmud Wakili a idonta ba, damuwar ta de guda daya ce rashin jin muryar Hajja dasu Ummah, saikuma tunanin Shahaab, tana tunanin ranar dazaije gidansu bai sameta ba. Yauma munirat da mama suna zaune afalo, munirat da wayarta a hannunta tana tura kudade tana order kayaiyaki da kudin filin mama data siyar (🙆🏻‍♀️) Mama tana mata kallon gefen ido tana mamakin shegen danne dannen waya irinna munirat, Aisha ce tafuto falon tayi kyau sosai cikin doguwar Riga irin kayan da mama ta siya mata, cikin ladabi tace "mama nagama gyara miki Dakin, yanzu saukowa qasa zakiyi, kokuma ki kwanta in tsefe miki kanki, kitsonki ya tsufa mama" Mama tayi murmushi tace "Bani abinci de infara ci tukunna, nagode da qoqari, Allah yasaka miki da alkhairi" Murmushi tayi ta nufi dinning tazubo mata abincin, sannan tadawo ta zauna tafara bata abincin abaki, munirat ta Kalle su, wani irin baqin ciki ya to kare mata maqoshi, ta maida Hankalinta kan wayar ta. saida tagama bata abincin sannan tafara tsefe mata kanta, cikin kulawa tace "mama idan kinajin zafi fa kifadamin saina dinga yi miki ahankali" Mama tayi murmushi tace "babu zafi Aisha, inda nake zuwa kitso ma suma kamar hakan suke min, Allah yayi miki Albarka" Cikin jin dadi tace "Amin mama" Munirat ta kalli Aisha, taga Sai wani qara yin fresh take, cikin kwanakin datayi a gidan yarinyar gaba daya sauya wa take kamar wanda ake mata wankan inji, haushinta takeji musanman wannan dogon gashin Nata dayake tsokale mata ido, kwata kwata yarinyar bata kwanta mata ba, tacika rawar Kai da fi'ili dakuma cusa Kai, jide yanda ta shige wa mama daga baqunta kamar wanda suka shekara tare. Tashi munirat tayi tatafi Part dinta, mama ta kalleta tace"munirat bazata sauya ba, yanzu kiduba kigani ko sallama batamin ba tatafi, tun lokacin da Mahmud zai aure ta naqi yarda, to kinsan sha'anin Dan yau, bazan iya hanashi ba saboda shi kadai Allah yabani, dole in so abinda yake so, dayake sonta yake kamar ransa, saina bashi Dama ya aure ta, tunda akai auren nide banji wani dadi ba, Amma shi Ahaka yake son abarsa" Aisha cikin ranta tace"Allah yaqara, ai Shima dannaki bawani mutunci ne dashi ba, Gara daya auri daidai dashi, nida zan ganshi ba Dana tambayeshi Ina Yaronsa SHAHAAB? (tofa😂) Amma a fili saitace "kiyi hakuri mama, watarana Sai labari" Mama tayi shiru batace komai ba, domin kuwa inda Sabo yaci ace tasaba da halin munirat. (idan kinsan baki biya kudin littafin nanba kika karanta to nabarki da futowar rana da faduwarta, harga Allah banyafe ba) Yau satinta biyu a gidan, Kuma yau Abbanta ya dawo daga Saudia, saide ita Kam batasani ba, har Zuwa wannan lokacin batayi waya da kowa ba, Amma takai maqura wajan kewar Yan gidansu, yau jitake kamar ta qwaci waya takira Hajja, batason kar6ar wayar mama saboda kartace mata tana mata shishshigi, haka ta daure tafita wajan mama domin yimata aikin data saba. Yau mama tashi tayi da son ganin qawarta Aysha Sulaiman Bompai, tayi nisa a tunani, tana tunanin irin rayuwar da sukai itada Aysha Sulaiman, yanzu sun kusa shekara saba'in, Amma da alama basuda Rabon haduwa da juna, shi Shahaab yayi mata alqawarin yin aikin gidan marayun ta akan lokaci, to yatafi Australia har yanzu shiru bai dawo ba, waya Sani ma ko tunda yatafi baya yiwa masu aikin waya?yakamata ya dawo haka, domin ayi sauri a qarasa a saka marayun aciki. Tana wannan tunanin batasan har Aisha tazo wajan ta ba, tasan yanzu lokacin matsa mata qafafu yayi, danhaka ta zauna tafara matsa mata qafafun Cikin damuwa mama tafara Girgiza qafafunta, ga damuwar rashin qawarta, ga Kuma shi Shahaab yatafi yayi zamansa, ta dade Rabon Dayayi tafiya yad'auki tsawon lokaci haka batareda sun kasance tare ba, taqi jinin ganinsa nesa da'ita, Aisha ta jijjiga kanta, ganin tana matsa mata qafafun Amma ita Sai jijjiga qafa take, ahankali tace "mama ki tsaya inyi miki tausar, kada qafafunki su kumbura," Ciki-ciki ta amsa mata dacewa"Yaya kike so inyi ne? Haka zan tsaida qafata niba itace ba, ba katako ba?tashi kije idan kingaji" Cikin fishi Aisha ta kalleta tace"babu inda zanje... Rikitacciyar tsohuwa kawai, Ana kokarin nema miki lafiya Amma bakya Gani,"(🙆🏻‍♀️🙆🏻‍♀️😳😲) Mama tayi shiruuu tana kallon Aisha da mamaki, da alama da gaske de yarinyar Nan daukar ta take a matsayin kakarta kamar yanda tafada. Aisha tasake kallon mama cikin fishi tace"sai kallo na kike kamar baki sanni ba, bazan Dena matsa miki qafafun ba tunda lafiyarki ake nema" Tana fadar haka tad'auki qafar Tata ta dora akan cinyarta, sannan taci gaba da matsa mata qafafun (tofa..... 🤔😇, Hali zanen dutse, me Hali...... ) Mutara zuwa yamma insha Allah 🙏🏻 Littafin Shahaab na kudi ne, ki biya naira 300 kacal ki karanta,idan baki biyaba kika karanta wallahi banyafe ba. 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034 Mrs Usman ce✍🏻 Page 22 Banda kallo babu abinda mama take wa Aisha, Wai yau itace wata yar yarinya take fada mata wadannan maganganun, Kuma abun mamakin da d'aure Kai ko kadan bataga laifin yarinyar ba, ta lura tsakani da Allah yarinyar take zaune da'ita, tunda duk abinda tafada mata made akan lafiyar ta take fadan, Dan qaramin tsaki tasaki, Aisha ta kalleta, ahankali ta ajiye mata qafar ta, sannan ta wuce Dakin maman tad'auko wani Mai datake mata amfani dashi, tadawo falon ta zauna tasake daukan qafar Tata ta dora akan cinyarta ta dinga shafa mata man, saida tagama sannan ta ajiye mata qafar ta ko sallama bata mata ba ta wuce dakinta Mama ta bita da kallo harta shige daki, wayarta ta d'auka takira Shahaab, yana dauka cikin damuwa tace "yaushe zaka dawo?" Murmushi yasaki dimple dinsa suka futo, shi Kansa yanaso yadawo kodan Aishan sa, yace "mama nakusa dawowa kiyi hakuri, Ina fatan de babu wata matsala ko?" "yakamata kadawo saboda aikin gidan marayun Nan" "mama komai yana tafiya daidai, duk wasu ayyukan Dana Bari Ramadan yana kula da komai, Kuma yana sanar Dani halin da ake ciki, kiyi hakuri nakusa dawowa kinji?" Tace "yaushe?" "nanda ten day's insha Allah" "kwana goma ai yayi yawa Shahaab, please kadawo dawuri" Yace "to mama insha Allah, ki kula da kanki" dif yakashe wayarsa. ****** Ruwan zam-zam ne a gabanta cikin wata babbar gora tana qulla shi a leda, Jikan iya jummai ne a tsugunne a gabanta, saida tagama qullawa sannan ta kalli Ummah datake kakkarya bagaruwa tace "kawo idan kingama" Ummah tabata, Kar6a tayi ta kalli Yaron tace "kanajina ko ididi, kakai duk gidajen Dana lissafa Maka, kace inji Hajja A'i tsarabar mamuda ce ta Saudia , kaji nafada Maka karka Bawa jummai ruwan zam-zam dina, har yanzu a hanci na take, kadan nake jira in fato ta" (😂) Ummah tace "Hajja da kinyi hakuri anbata Shima baisan zaije Saudian Nan bafa, Kuma mu aiki jikanta Amma muhanata ko ladan ganin ido?" Cikin masifa hajja ta kalli Ummah tace "to Hadiza fadamin abinda yakamata inyi, waini tare kika ganni da jummai ne kokuma kece kika hadani da'ita? Nan tazo har gida ta samfe min jikata tayi gaba da'ita, har yanzu ko d'uriyar yarinyar banqara jiba, ai wallahi tsakanina da jummai saide kallo, da Hankali na ba zanje har gida in dauki jikar ta in kaita uwa duniya aikatau ba, ci muka Rasa ko Sha?" Ummah tace"kiyi hakuri" Hajja tace "haka de" Yaron ne yad'auki robar yafita, Hajja tatashi tafara tace niqan kunun ayarta da'aka kawo mata yanzu ****** Kamar kullum Yauma da safe tatashi tafada kitchen kamar yanda tasaba, suna cikin aiki ta kalli daya daga cikin masu aikin tace "mansura Dan Allah Aron wayarki Zaki Bani inaso nakira mamanah" Mansura tace "wayata tana d'akin mu, jeki dauka" Cikin murna tatafi Dakin,wayar tana caji, ta cireta takira Hajja, a lokacin tashin su kenan daga bacci Ummah tana kokarin dora musu abincin Kari, Abba yana Gefe yana jin redio yayi fresh dashi har wata yar qiba yaqara, Hajja tanajin qaran wayar ta, ta d'auka tareda cewa "wannan kira da sanyin safiya kode mutuwa akayi?" Wani irin farinciki ne yakama Aisha jin muryar Hajja, muryarta ta bude tayi magana cikin sigar tsoratar wa tace "Aljana manuba ceeee" Hajja tasaki dariya tace "tazo takamamu nida ke, yar bantan uba" Dariya Aisha tasaki tace "waisaida kika ganeni? Ke Hajja" Cikin farinciki Hajja tace "haba mesunan qawa, ko a mafarki kika sauya murya kika min magana ai dole nagane,mesunan qawa shikkenan jummai ta rabani dake, mamuda yashiga tsakanin mu, kina samun abinci de kinaci Kina qoshi ko?" Cikin sauri tace "Hajja inacin duk abinda nakeso, bakiga gidan ba, qaaaaato, ga abun dadi sunaci kullum wani abun ma bansan sunan saba, Kuma ko Hajja har bread ake rabawa duk juma'ah baki gansu ba manya manya fulawa zirrr" Hajja ta zaro ido tace "kice daqyar kike iya daukan guda daya?" Zaro ido tayi tace "Biredin?" Hajja tace "emana, naji kince fulawa zirrr..." haushi ne yakama Aisha tace "Kai Hajja Dan Allah, kinfara ko?" Cikin sauri tace "Allah yabaki hakuri me sunan qawa, kullum inata kewarki, inji de matar gidan tabaki madubi babba?"😂😂 Fari tayi da idonta, sarai tasan Inda maganar Hajja ta dosa, murmushi tasaki tace "akwai,kuma kullum saina kalla abuna, tunda banaki bane nawane" Hajja tasa dariya tace "toga Hadiza, Amma bazan baki mamuda ba, har yanzu a wuyana suke shida jummai" Murmushi tayi tace "tobata" Ummah ta kar6i wayar suka gaisa, tayi qasa da murya yanda su Hajja bazasu jitaba tace "ki kama kanki de aduk inda kika tsinci kanki, banda shiririta, banda kula maza, ki tsare mutuncin ki, Kuma bance kiyi musu rashin kunyar Nan Taki ba" Cikin sanyin jiki tace "insha Allah Ummah" Hajja ce ta qwace wayar tace "zan ajiye number, idan inaso inyi magana dake saina dinga kiranki tanan ko?" Cikin farinciki tace "to Hajja, Sai anjima" Bayanta ta jinginar a jikin gadon Dakin tatafi tunani, rayuwa kenan, yau itace take rayuwa awani waje daban, su Hajja suna wani waje daban, Allah yaso tama tariqe number su. Kitchen din Takoma suka qarasa aikin, bata koma dakinta ba afalo ta zauna ta jira mama tafuto, daga Nan tafara yimata aikin data saba, saide fuskarta adan daure take, ta lura gigin tsufa ne yake damun mama kamar de Hajja idan ta rikice musu wata Rana. Haka taci gaba da Kula da mama, bata fasa kyautata mata ba, koda tayi niyyar yimata tsiya idan ta tuna nasihar da Ummah ta yi mata saita fasa, mama tanajin dadin yanda Aisha take bata kulawa, yarinya qarama da'ita Amma tasan yanda take kula daduk wasu al'amuranta, da alama Dama can tana aiki a gidansu, ta lura kwata kwata yarinyar tadena sakin jiki da'ita kodan saboda Dan Sa6anin dasuka samu kwanaki ne? Toyaya zatayi? Tunanin qawarta ne ya janyo hakan, duk lokacin data tuna Aysha Sulaiman Bompai tanajin ranta yana 6aci, Gani take kawai mutuwa zatayi batare data ganta ba, burinsu na hada 'ya'yansu Aure, bazai tabbata ba, duk lokacin datake cikin wannan yanayin shi Kansa Shahaab dinnata uzuri yake mata, saboda ta dinga 6acin rai kenan. Yau satin Aisha hudu daidai a gidan,Kuma yau ne Shahaab yayi wata daya da kwana biyar da tafiyar sa,yau Aisha tana matsa wa mama qafafu mama tace "Aisha yau yakamatakuje ki bude account kema,Amma Naga Sai fishi kike Dani har yanzu" Cikin ladabi tace "kiyi hakuri mama, Bana fishi dake, Amma maganar kudin Nan kibar ta" Mama tayi shiru tana kallon ta, tayaya zata bar yarinya tana mata aiki babu ko sisi Aida shiga haqqi, dole zasuje su bude Adinga saka mata kudinta, taga har yanzu yarinyar tana fishi da'ita, duk da bata futo fili tafada mata gaskiya ba, bazai iyu tafada mata dalilin dayasa ta 6ata mata rai rannan ba, abinda ya shafi tsakaninta da Aysha Sulaiman Bompai wannan tsakanin sune, Bai shafi masu aikinta ba, tana wannan tunanin taji Aisha tace "mama kihuta lafiya" Daga Nan tatafi daki, saboda wani irin zazza6i datake ji tunda safe,ga qirjinta ciwo yake har cikin boobs dinta Wanda takejin wani irin abu aciki me zafi, haka bayanta ma yana mata ciwo kadan kadan (Allah karabu da rashin sanin ciwon kudin mu 😖😖😖in samu kudi na daqyar insai abu, Kuma in zauna Ina fitar dashi saboda shirme, duk wadda tasan bata biyani haqqi naba nabar ta da Allah, bazan taba yafe mata ba) ****** Yau cinema akwai wasa, Ball za'a buga me zafi, tun rana Hajja tagama harhada komai na kunun Aya, da yamma ta zauna zata Fata d'urawa acikin jarkoki, Kallan uban kunun ayar dake gabanta tayi, ta juya ta kalli Abba dayake shirin fita qofar gida tace "mamuda ai bakaga ta fita ba, zuwa zakayi ka zauna ka duramin wannan kunun ayar, tunda ka sallami Wadda take min" Abba baiyi musu ba yadawo ya tsugunna yafara d'ura mata kunun ayar, koda wasa ba zaiyi kuskuren yin maganar Aisha da'ita ba yanzu, saboda yanzu saita fara yimasa bori tace lalle lalle Sai yaje yadawo mata da'ita Hajja tasaki tsaki tace "tunda Wanda nake Tarawa kudin registration din yatafi makarantar ai sai infara tattara kudina inje dakaina in dawo da Mai sunan qawa, bazai iyu duk lokacin dazanyi durin kunun Aya sainaje majalissa-majalissa Ina nemanka ba"😂😂 Ummah ta ajiye tsintsiyar hannunta tawanke hannayenta, sannan tazo ta zauna itama sukaci gaba da dura mata, saida suka gama tsaf... Suka saka mata shi cikin babbar kula sannan Abba yamiqe zai fita, Hajja tace"Ai baka gama ba, jeka nemomin me mashin"😂 Bai iya cewa komai ba Sai "to Hajja" Sannan yafice daga gidan cikin sauri. ****** Kallon Yaron dake gabansa yayi, yau Yacika sati na uku kenan a qasar Amma yaro harya fara sauya wa, fatarsa tasake fresh Sai wani irin haske yake yi, jaridar dake hannunsa ya ajiye yace "jabir ka tsaya ka nutsu kayi karatu kaji? Kaga wannan karatun shine gatanka, idan kayi karatu iyayenka ma zasuji dadi su sakama Albarka, karka sa tunanin gida a ranka, kasa karatu agaba kayi abinda yakawo ka kakoma gida lafiya" Cikin ladabi jabir yace "to Alhaji nagode sosai, Allah yasaka da alkhairi, abunda kayi mana Allah yabiyama da gidan aljanna" Murmushi yayi yace "jabir aiba nine nadauki nauyin zuwanka qasar nan dakuma karatun kaba, oga nane, Shima yana tare damu acikin qasar saide ayyuka dasuka yi masa yawa yasa baisamu lokaci ya ganka ba, yanzu haka Nigeria zamu wuce, wannan wayar ma shine yace akawo ma, idan yasamu lokaci zai kira layinka " Cikin mamaki jabir ya kalli mutumin da tsananin alhini, tunda suka fara hidimar tafiyar su shida Abba wannan mutumin yake Gani, yayi tunanin shine yad'auki nauyin karatun nasa, ashe bashi bane, to waye wannan? Murmushi mutumin yayi kamar yasan abinda yake cikin zuciyar jabir yace "nasan kanaso kasan waye yakai Abban ka Saudia,sannan kaima yakawo ka qasar nan karatu, to zaka sanshi very soon, ya tabbatar min idan yasamu lokaci zai kiraka, idan ya kiraka saika yi masa kowanne irin tambayoyi" Jabir yace "to shikkenan Alhaji nagode, Allah yakaiku lafiya, Allah yasadamu da alkhairi" Mutumin ya amsa masa da "Amin" sannan sukai sallama yatafi gidan da'aka kama masa, shikuma mutumin yanufi Airport. ****** Nnamdi Azikiwe International Airport Abuja. Tsaye yake yana jiran motoci su qaraso daga gida,kasancewar babu wanda yasan da zuwansa, saida ya sauka sannan ya kirasu, Sanye yake cikin Riga da wando, baqin wando, da Riga Ruwan toka me ratsin baqi, Sai glass din Idonsa baqi, dakuma agogo baqi,Wanda yasake haska farar fatarsa, Sai takalmin qafarsa kambos fari, gashin kannan nasa yasha gyara Sai sheqi yake,Bai 6alle botir din gaban rigar tasa duka ba, yabar guda uku a bude, hakan ne yasa ake iya hango lallausan gashin daya kwanta akan faffad'an qirjinsa, hannuwansa zube cikin aljihun wandon sa, Dan qaramin tsaki yasaki Bayan yasake kallon agogon hannunsa, yadubi Alhaji Ibrahim Wanda suka dawo tare yace"Alhaji zaka iya tafiya, gasunan sun qaraso" Alhaji Ibrahim yabashi wani Kati tareda cewa"to oga, ga wannan katin, number wannan Yaron ne jabir" Katin ya Kar6a, tareda turashi cikin aljihunsa yayi gaba batareda yasake cewa komai ba, wajan da aka Parker motocinsa ya qarasa, cikin sauri aka bude masa motar yashiga, sannan suka dauki hanyar gida, Kansa ya jinginar a jikin kujera yana jin yanda bugun zuciyarsa yake sauya wa Zuwa faduwar gaba matsananciya. Bai dauki hakan a matsayin komai ba, tunda yasan mama tana lafiya, munirat ma haka, saide Aisha ce bai saniba, itama Kuma so yake ya qarasa gida yabude wayarsa datake kiransa da'ita Yakirata yaji muryarta ko zai samu ya'iya runtsa wa a Daren yau din.(😇) Suna qarasa wa gidan Kai tsaye yawuce part din mama, tana zaune afalon ita kadai, abinci ne a gabanta tana kokarin hadawa, cikin jin dadi dakuma shagwa6ar daya saba ya rungume ta tabaya yace"mamaaaa.....I miss you" Mama da batasan da zuwansa ba cikin farinciki da jin dadi tajuyo tace"mahmud?'' Murmushi yake saki kamar bashi ba dayake daure fuska kowanne lokaci, kwanciya yayi akan kujerar tareda dora Kansa akan cinyarta yace"mama nayi kewarki dayawa, nayi kewar cinyarki " Dogon hancinsa taja, cikin farinciki tace"ai gashinan kadawo, Bari inzuba Maka abinci Dama yanzu nake shirin cin abincin Nima" Cikin sauri yatashi zaune yana fuskantarta, cikin 6acin rai yace "mama bangane ba? Kece Zaki zuba abincin da kanki? Ina masu aikin suke?" "masu aiki suna Nan Shahaab, sukam ai sungama aikinsu sabuwar yarinyar datake kula Dani wadda na dauka itace de batazo tabani ba,Kai ni rabona da'ita ma tun Daren jiya, kwata kwata yau bansata a'idona ba, fishi take Dani na babu gaira babu dalili, datage ala dole saita dinga kula Dani ta qarfi da yaji kamar likita ta, yanda kasan kudi ake biyanta idan tanamin fada akan matsa qafafun Nan nawa" Cikin 6acin rai yace "what...?, fada Kuma? To idan qafar tana miki ciwo sosai fa?" Ganin yanda ya rikice yasa mama Tace"A a tanada gaskiya ai,yanda take kulawar Dani yasa ma yanzu banajin ciwon qafar sosai " Badan ya gamsu da maganar tataba yace"to waye yayi miki ayyukanki na yau kenan?" "waye zaimin tunda d'an Dana Haifa baya Nan bare yamin?" cewar mama Ransa ne yasake 6aci,yanzu idan me kula da mama batayi mata komai ba hakan yana nufin munirat bazata zo tadinga temaka mataba? Kenan ko Bayan ransa munirat bazata ci gaba da Kula masa da maman saba? Wayarsa ya d'auka yakira number munirat, bugu uku ta d'auka, tayi tunanin baizo qasar ba, saboda acan dinma da number sa yake kiranta, cikin 6acin rai yace "yau kinje kinga mama ne kinji ko tana buqatar wani abu?" Munirat tafara kame kame, cikin borin kunya tace "yanzun Nan nake shirin zuwa ingano ta, Allah yasa de bacemaka tayi nayi mata laifi ba" Baice mata komai ba kawai kashe wayar yayi, yadaga murya cikin fishi da 6acin rai ya kwalawa daya daga cikin masu aiki kira, jin muryar Mahmud Wakili yau da Kansa yana kiran me aiki yasa jikin masu aikin yakama karkarwa Saboda ba kulasu yake ba,baya shiga shirginsu, idan yazo falon kowa nemansa kake karasa saide dagashi Sai mama, Amma yau gashi yana kira Kuma da alama akusa yake, ransa a6ace yake, cikin sassarfa wata yarinya ta qaraso, ya kalleta yace "jeki kiramin me kula da mama"(🙆🏻‍♀️) Cikin sauri ta juya zuwa Dakin Aisha. Mama ta kalleshi tace "Aida karabu da'ita, yanzu kana 6ata mata rai zata dinga daure min fuska tana shamin qamshi, nagama lura haushi na takeji saboda Dan sabanin da muka samu rannan,nikuma hakan damuna yake narasa dalili" 'Yar aikin tana zuwa ta ganta cikin blanket, yaye bargon tayi,jikinta na karkarwa muryarta na rawa tace "Aisha kizo inji yalla6ai , yanason ganinki" Aisha ko bude idonta batayi ba, saboda bayanta dayake mata mugun ciwo, ga ciwon qirji ko dogon numfashi takasa ja, ahankali ta bude Dan qaramin bakinta tace "banda lafiya..., kije kice masa banida lafiya bazan iya tashi ba" Gaban yarinyar ne yafadi, yaushe zata Iya Kallan idon yalla6ai da Hajiya Mama tace musu Aisha tace bazata iya zuwa ba? To Amma ganin yanayin datake cikin yasa ta juya tafice daga d'akin cikin sanyin jiki, tana zuwa falon ta tsugunna qasa, kanta qasa tace "yalla6ai tana kwance, batada lafiya ne" Cikin sauri mama tace "subhanallah.... Ashe shiyasa batazo ba" Duk yanda mama takai da rashin kirki, tana tsoron jinya, bare Kuma Aisha datake bata kulawa yanda ya dace, ta juya ta kalli Shahaab tace"muje kadubamin ita Dan Allah, idan Kuma Asbiti zamuje saimu tafi yanzu" Tsananin mamaki yakama Shahaab, Wai wacce irin yarinya mama tasamu haka? Yaga fuskar maman ta sauya alamun tausayawa, wacce yarinya ce me sa'ah haka? Kallan me aikin yayi, har yanzu fuskarsa a daure take, yace"kije kice nace tazo" Juyawa me aikin tayi cikin sauri Takoma Dakin Aisha, Badon ranta yasoba haka ta daure tatashi, Riga da siket ne ajikinta na atamfa,kayan sunyi mata daidai, hips dinta yayi dass acikin siket din, rigar yar qarama daidai da'ita,dan kwalin kayan yadan Zame alamun kawai dorashi tayi bai gama dauruwa ba, gashin kanta me santsi yafara futowa tagaban goshinta, futowa sukai zuwa falon, Bayan ciwon baya da qirji da takeji harda wata irin faduwar gaba da takeji tun safe. Kanta yana qasa har suka qaraso kusa da mama, me aikin data kirata ta kalleshi tace "yalla6ai gata" sannan ta juya cikin sauri tabar falon Hankalinsa yana kan wayarsa yana dannawa, Mama ta kalleta tace "sannu AISHA" Jin sunan Aisha da'aka kira yasa yadago Kansa cikin sauri, Adede lokacin itama ta d'ago kanta ta kalleshi,(🙆🏻‍♀️) Idonsu ne yasarqe cikin na juna, cikin wata irin faduwar gaba Aisha ta bude bakinta, cikin zuciyarta tace "Shahaab...." cikin sauri yatashi tsaye haryana wullar da wayar hannunsa. Mama ta kallashi da tsananin mamaki tace "MAHMUD lafiya?" Jin sunan da mama takirashi dashi ne yasa gaban Aisha yayi wata irin Fad'uwa,cikin tsananin mamaki ta motsa dan qaramin bakinta cikin sigar rad'a tace "MAHMUD?" narasa ta cewa yau... 🏃🏻‍♀️😆 Idan kinsan baki Sai Shahaab ba kika karanta, wallahi tallahi ban yafe miki ba, nabarki keda ubangijinki, warana zai mana sakayya 0164549488 Amina muhammad GTbank 08033300034 Amnah✍🏻 ASH~HAB Kasa Bawa mama amsa yayi, Sai kallon Aisha dayake Idonsa sun furfuto alamun rashin gaskiya, cikin ransa yafara karanta "innalillahi wa inna ilaihirraji'un...." Jin bai bata amsa ba yasa tasake kallon sa tace "SHAHAAB mekake kallo ne?" Ahankali Aisha ta sunkuyar da kanta, cikin ranta tasake maimaita sunan SHAHAAB, ta tabbata de shine Mahmud Wakili. Kansa ya sunkuyar qasa, jiyake kamar qasa ta bude yashige Dan kunya, tun haduwar idonsu na farko ko kadan yakasa hada ido da Aisha, mama ta janyo Aisha kusa da'ita tace "Aisha meyake damunki? Menene yake miki ciwo?" ta qarasa maganar tana Kai hannunta wuyan Aishan ko zataji zazza6i, cikin sauri kuwa ta janye hannunta tace "Subhanallah, aikuwa jikin naki da zafi sosai, zazza6i ne yake damunki?" Magana takeson yi Amma kuka ne yakeson qwace mata, wani irin qullutun abu takeji ya tsaya mata a maqoshi Shahaab ya cuceta....tana bude baki da nufin magana saita saki wani irin kuka harda shashsheka. Lokaci daya mama tasake rikicewa, tace"irin wannan kukan Aisha kamar anyi miki mutuwa, kinga muje Asbiti kawai, yafi sauqi" Cikin tsananin kuka tace"mama Gara kibarni inmutu" Kansa yana qasa, Amma jin wannan furucin Nata yasa ya runtse Idonsa, yasan cewa Dashi take. Mama tayi ajiyar zuciya sannan ta sassauta murya tace "fadamin meyake damunki?" cikin kuka tace "bayana ne yake ciwo, da qirjina, Kuma wani irin abu nakeji aciki" Mama tasaki salati kamar de yanda Hajja takeyi,ta qare da fadin"innalillahi... " Tajuya ta kalli Shahaab da Kansa yake qasa har yanzu, saide idanunsa sunyi wani ja kamar me shirin kuka, tace" dubamin ita gani karfa aje ko cancer ce" Jin sunan jinyar data fada yasa Aisha tasake sakin wani irin kuka, Shikuwa Shahaab Kansa aqasa ya Girgiza wa mama Kai, mama tace"tsoronta kake jine?" Kafin yabata amsa ta janyo Aisha jikinta, tasaka hannu tayi qasa da zip din rigarta, sannan tayi qasa da rigar, Allah yaso tasaka vest,Amma babu brezia, lokaci daya baqar vest dinta tafuto fili, mama ta kalli Shahaab tace"duba kagani Shahaab" Runtse Idonsa yayi,😖mama taqi tadena Kiran sunansa, magana daya biyu saita kira sunansa, taqi tagane cewa yau bayason Kiran sunan Nan nasa. Ahankali yadago Kansa ya kalli inda take, Idonsa ya sauka akan tsayaiyun qirjinta, tunda yake zuwa garinsu , kullum cikin hijab yake ganinta, baita6a ganin baiwar da Allah yayi mata ta qirjinta ba,kasa janye Idonsa yayi daga kallon su, jiyake kamar ya fusgota jikinsa kozaiji dadin lallashin ta Daqyar ya Girgiza Kansa yace "babu komai mama,basai na dubaba nasan ba cancer bane" Mama tace "a a ta6a kaji de, kar naje yar mutane ta gamu da cuta awajena" Har zuwa wannan lokacin Aisha taqi yarda tasake kallon sa, kwata-kwata jitayi batason ganinsa, ahankali tafara Girgiza wa mama Kai jin furucin datayi, cikin tausaya wa mama tace"bari Aisha,Mahmud likita ne,zai dubaki yanda yakamata, idan mukaje Asbiti ma kina fadar abinda yake damunki kamar yanda kika fadamin yanzu, to suma dole zasu duba, a Asbiti wajan doctor zan tura ki bansan mezai miki ba, Amma shi wannan agabana yake, Kuma akan idona zai dubaki, idan ba cancer bane shikkenan" Tajuya ta kalleshi tace"dubata" Ahankali yafara takowa kusa da'ita,wani irin baqin ciki taji yakamata, meyasa mama zata mata haka? Shikkenan daga cewa tanajin abu me zafi a qirjinta Sai ace yazo yaduba ta? To me zai duba? Bata gama tunanin taba taji yad'ora hannunsa akan vest dinta, runtse idonta tasake yi wasu hawaye masu zafi suna sake zubo mata, wani irin kuka tasaki lokacin dataji hannunsa akan boobs dinta. Shi Kansa hannunsa rawa yake kamar yana ta6a wani abu me shocking, duk da tasaman vest yad'ora hannun nasa, hakan bai hanashi jin wani irin mugun dadi ba, wani irin abu yaji tundaga Kansa har zuwa tafin qafarsa, lokaci daya yanayin sa yafara sauya wa, baisan lokacin daya dora d'ayan hannunsa akan dayan Breast dinba, murzawa yake ahankali yana jin wani irin dadi na fitar Hankali. Hawaye ne suke zuba daga idonta, gashi mama ta riqeta, tanaji tana Gani mutumin daya cuceta, ya yaudare ta, shine yake ta6a mata nono, idonta a rufe suke taqi yarda ta bude idonta bare ta kalleshi, tabbas tayi Dana sanin mu'amula da mutum mayaudari kamar sa. Shahaab kuwa gaba daya ya manta mama tana wajan,dede nipples dinta yake murzawa ahankali,duk yanda zuciyar sa take hanashi kwata-kwata yakasa dainawa, jiyake kamar ya fuzgota jikinsa yad'ora bakinsa akansu(🙆🏻‍♀️😳) Adede wannan lokacin munirat ta riskesu, dama tazo duba mama ne saboda Kiran da Shahaab yayi mata awaya yana fada ko taje tagano mama yau? Gabanta ne yayi wata irin faduwa ganin mama riqeda baquwarta, shikuma hannuwansa duka biyun suna kan qirjin yarinyar yana murzawa, idon yarinyar ta kalla taga idonta a rufe, Amma bata gama tantance wa dadi takeji yasa tarufe idon, kokuma kuka takeyi ba,lokaci d'aya taji ta tsani yarinyar, yanzu me mama take aikata wa haka? Kuka ta Fashe dashi, sannan Tajuya tafice da gudu daga falon, mama tabita da kallo ta saki tsaki tace "kishin banza,kishin wofi,inda ace nabarshi yana zuwa asbitin saiki hanashi duba kowacce mace kenan, ni Dana badan iska bane" Tajuya ta kalli Aisha cikin fada tace "kekuma koki tsaya ko cancer ta kama ki, Dana likita ne badan iska ba" Tajuya ta kalli Shahaab Wanda kwata kwata baisan ma mama tana magana ba,cikin qaguwa da abinda yake tace "Wai baka gama bane?"(😂🙈) Cikin sauri yadan kalleta sannan cikin shaqaqqiyar murya yace "Ina dubawa ne...."(🙆🏻‍♀️) Ahankali yasake kama breast din Gaba dayansa, Saida yasake murzasu sosai, sannan ya janye hannunsa Badon yaso ba, ya kalli mama, cikin wani irin yanayi na kasala da sha'awa yace "ba cancer bane mama, ciwon Bayan ma nafi tunanin mp ne ya janyo haka,zanyi magana akawo mata magunguna" Yana fadar haka yayi sauri yafice daga falon cikin tashin hankali, yana cikin yanayi, gashi mama tasake sashi yafada cikin yanayin da yafi nada. Kai tsaye d'akin sa yawuce bai nufi inda munirat take ba, yana shiga ya kulle Dakin tare zubar da duk kayan dayake gaban mirror, shi shi kadai yake watsi da kayan Dakin su fillo da bedsheet din Dakin babu abinda baiyi wurgi dashi ba, cikin tashin hankali ya zauna akan gado tare hargitsa sumar Kansa, cikin wata irin murya kamar zai Fashe da Kuka yace "innalillahi wa inna ilaihirraji'un.... Ya Allah, komai yazo qarshe, na tabbatar tadena yarda Dani...." Wayarsa yadauka yakira Ramadan, bugu daya ya amsa, cikin rawar murya yace "Ramadan komai ya lalace, yau maaama nagani acikin gidana Ramadan" Daga can 6angaren Ramadan yace "innalillahi... Garin Yaya? Metazo yi Abuja Kuma?" Bai iya Bawa Ramadan amsa ba Sai wani abu da yaji me dumi yana sakko wa akan kumatunsa, hannunsa yakai ya goge Hawayen, sannan yace "yarinya tana ganin girmana, kunsa nayi mata qarya, yanzu nasan bazata sake yarda Dani ba, kunyar kallon idonta nake Ramadan, saida nace zan fada mata gaskiya, banga amfanin 6oye mata gaskiya ba, kasani nayi mata qarya" Cikin kwantar da Hankali Ramadan yace"amma aika gane tana sonka da gaskiya ko?" Haushi ne yasa Shahaab yakashe wayarsa, kwanciya yayi akan gadon tareda dora hannunsa akan mararsa, wannan masifa Dame tayi kama?(🤔) (idan kinsan baki biyaba kika karanta Allah ya'isa nah, Kuma bazan taba yafe miki ba, tun Bana Allah ya'isa kunsa nafara, duk wadda ta takaranta inde bata biyaba wallahi itada MAHALICCINTA) ****** Har dare, Aisha tana kuka, idonta yayi jajir saboda kukan da Tasha, abincin da aka kawo mata da magungunan ko Sha batayi ba, daqyar ta lalla6a tayi sallah sannan ta rafka uban tagumi hannu biyu, hawaye ne yasake zubo mata lokacin data tuna da Hajja, inda tare Takeda Hajja ko hannunta bazata Bari ata6a mata ba, gashinan yakama Sai murza mata qirji yake gaba daya Sai ciwo suke mata, hartana cewa danta ba dan iska bane Inba Dan iska bane shida akace yata6a yaji menene aciki, to menene zaisa yakai hannunsa kan nipples dinta?. Hawaye ne suka sake zubo mata, dole zata tafi gida, bazai iyu ta zauna Ana ta6a mata nono ba, gashinan yayi mata da zafi Sai ciwo suke mata, idan taci gaba da zama a gidan tsaf wataran zata masa abinda bai Ta6a zato ba, dama can bada gaskiya yake mu'amulantar taba, hauka da shirme yasa takasa gane cewa me Shahaab zaiyi da yar qauye kamar ta? Dama yaudara ce takawo shi, tunda dayazo ma 6oye mata koshi waye yayi, hatta garinsu ce mata yayi shidan maiduguri ne, yace bashida aure ashe yana mata, haka Kuma yaqi yarda yahadu da mahaifinta koda yaushe saide Yakirata mota koda wasa bai ta6a cewa yanaso yaga Abban taba Sai lokacin dayazo yace mata zaiyi tafiya, Shima Dan yasha bakinta ne shiyasa ya shirya mata wannan yaudarar,kaiii yaudarar tayi yawa, tasa hannu ta share Hawayen idonta, Sai yanzu ne takejin haushin kanta, taji ta tsani kanta sakamakon tunawa datayi har bijrewa iyayenta tayi, saboda shi, daga qarshe ga abunda yafaru, dama ance duk Wanda baiji maganar iyayensa ba,to yana tareda matsala, tun kafin taci gaba da ganin wannan matsalar Gara Takoma gida ta roqi iyayenta gafara sannan Kuma tashawo kan inusa, tana zaune tana tunani har qarfe shadaya da rabi na dare yayi batare data Sani ba Shabiyu daidai yafuto daga d'akin sa, tun Bayan barinsa part din mama daya shiga daki baisake futowa ba Sai yanzu, Kai tsaye d'akin munirat yawuce, tana kwance akan gadonta, ta dora hannunta daya akan goshinta Wanda yake mata barazanar rabewa biyu, idonnan ya kumbura suntum saboda kuka, tanajin shigowar sa Amma tayi masa mursisi ta nuna kamar batason yashigo dakinba, zama yayi akan gadon tareda janyo ta jikinsa, ahankali yabude bakinsa yace "munirat...." Cikin sauri ta qwace jikinta tareda matsawa can Gefe, Bai saurare taba yajata jikinsa ya rungume ta, kuka tasaki Mai cin rai, baice mata komai ba Sai bayanta daya Dan bubbuga alamun tayi shiru, daga Nan yajata suka kwanta, tun yana jin kukan ta har yaji tayi shiru jikinta yasaki alamun tayi bacci. Har qarfe daya saura Idonsa biyu bai runtsa ba, Ada idan yadawo daga tafiya qarfe goma yayi yawa ya kwanta, Amma yau shine har daya saura Idonsa ko alamun bacci babu, inda Dane yadade bai kasance da matarsa ba to kwana biyu ne zuwa uku, idan tashiga hannunsa kuwa saita koka, Amma yanzu shine yayi tafiyar wata daya da 'Yan kwanaki Amma ko kadan baiji yana sha'awar munirat ba, tunanin sa gaba daya yana wajan Aisha,ya dade rabonsa da matarsa, yadawo daga doguwar tafiya Kuma mama ta tarbeshi da wadannan abubuwan na Aisha masu wuyar mantawa. Ya tabbatar da cewa bazata taba saurarensa ba koda yaje inda take yanzu, Amma Kuma tayaya zai tunkareta yabata haquri agaban mutane da rana? Idan mama ta ganshi ta'ina zai fara yimata bayani? Ahankali yazame munirat daga jikinsa, batareda tunanin komai ba yafice daga d'akin, Kai tsaye yanufi part din mama. Yana zuwa yaga part din shiru alamun duk sunyi bacci, saida yasake kallon ko'ina ya tabbatar babu wani mahaluqi dayake falon sannan yawuce Dakin da yaga Aisha tafuto daga ciki dazu, kama handle din Dakin yayi yatura, yashiga cikin Dakin sannan ya maida Dakin yarufe, baiyi mamakin ganin ta a zaune akan sallaya ba, kanta yana cikin cinyoyinta, qamshin turaren dataji ne yasa taqi d'ago kanta bare ta kalli inda yake. Jin gina yayi da jikin qofar Dakin yazuba mata ido yana kallon ta, gabansa faduwa yake yarasa ta'ina zai fara yimata magana? Ahankali yasaki ajiyar zuciya sannan ya qaraso wajan ta ya tsugunna gab da'ita har tanajin yanda hannunsa yake gogar Nata, cikin muryar rad'a yace "ki... kki... kiyi hakuri" Tana jinsa, Amma taqi d'ago kanta ta kalleshi, wani irin haushin sa takeji, ko menene yakawo shi dakinta cikin dare? Wata zuciyar tace da'ita abinda bai gamaba yazo ya qarasa, wani irin tsaki tasaki cikin ranta, tasake cusa kanta cikin cinyoyinta, ganin hakan datayi yasa yasan cewa ba bacci take ba, ajiyar zuciya yasauke yasake cewa"nasan cewa nime laifi ne awajanki, banyi komai ba saida dalili Maaamah, Dan girman Allah kiyi hakuri ki yafemin..." Wani irin kuka me sauti tasaki, batace masa komai ba Sai hannu data daga masa. (🖐️) Kallanta yayi, babu musu ya jijjiga Kansa tareda miqewa yafice daga d'akin, dama yasan cewa bazata saurare shi ba, haka yakoma part dinsa jikinsa a sanyaye, kan gadon yakoma ya kwanta, munirat tanajin kwanciyar sa tace "daga Ina kake? Ko yanzun ma wajan ta kakoma zaka sake taba mata nonon?" Runtse idon sa yayi, ahankali yace "me kike nufi Danine munirat? Kina nufin zan iya neman mata awaje?" Cikin fishi tace "idan ba neman matan kafara ba, kwanan ka nawa rabona dakai?Dakazo ka nemi wani abu awajena ne? An tura Maka tsayaiyan nono kana ta6awa yaushe zaka nemi nawa?kun cuceni wallahi, Kuma dole kasa yarinya qarama tadena ganina da qima da mutunci" Murmushi yasaki kamar wanda baya cikin damuwa, ahankali ya fusgota jikinsa tareda tura hannunsa cikin yaluluwar rigar baccinta, yayiwa breast dinta wani irin kamu, sannan yafara kissing dinta. Sosai yayi Nisa wajan nuna mata yanda yayi kewar ta, soyake ya mantar da'ita abunda tagani dazu, saide shi Kansa kawai yanayin Hakanne Amma kokadan bayajin sha'awar, saboda tashin hankalin dayake ciki,daga Nata bangaren itama Qin bashi hadin Kai tayi, Dan dole yarabu da'ita tareda juya mata baya yayi kwanciyar rub da ciki, itama kwanciyar ta ta gyara tarabu dashi, saide ko minti goma batayi ba taji Hankalinta yaqi kwanciya, yariga yata6o mata inda yake mata qaiqayi, ahankali ta juya ta rungume shi tabaya, yanajinta yarabu da'ita, sake Matsowa jikinsa tayi tana goga masa qirjinta a bayansa, saide hakan datake masa ma ba komai tatuna masa ba Sai Wanda yata6a dazu, ahankali yasaka hannunsa ya janye ta daga jikinsa, sannan yaja fillo ya rungume a qirjinsa. Mamaki ne yakamata, yau itace take neman Mahmud Amma yana janye ta da hannunsa? Babu yanda ta'ita duk yanda take jin sha'awar sa haka ta qyaleshi. Washe gari da safe tsaf ya shirya cikin suit dinsa, baisaka jacket dinba Sai zuba uban qamshi yake,soyake yafita domin shirye shiryen sabon company dazai bude, Wanda yayi alqawari zai Bawa matar datake da muhimmanci awajansa wato munirat ,tun qarfe takwas na safe suke masa waya, already har sun gama tsara komai, kawai jiransa ake yazo yasaka ranar daza'a bude companyn, baisan daliliba, haka kawai yake jin wani irin farinciki acikin ransa, Kuma yasan cewa hakan baya Rasa nasaba da kasancewar Aisha acikin gidansa,yarasa menene yakawo ta gidan a matsayin maiyiwa mama hidima, tayaya tazo? Dole itace zata bashi labari Kuma tana fishi, inda Dane ba lalle ya tsaya yin break fast ba saboda jiransa da ake, Amma yau Kam dole zai tsaya yaci abinci kodan yaganta ma. Munirat tana wanka danhaka yafice shi kadai, Kai tsaye part din maman yanufa, yana zuwa kuwa yaga ma'aikatan sun gama shirya komai akan dinning, mama tana zaune, yayinda Aisha take tsaye tana qoqarin hada mata tea, yau taji jikin Nata dadan qarfi, babu zazza6in ya sauka tun Bayan datasha magani cikin dare, wani irin dadi yaji, cikin takunsa me aji ya qarasa dinning din tareda sallama, mama ta kalleshi tace "nayi tunanin zaka huta ne bazaka fita ba?" Saida yadan kalli Aisha yaga tahade girar sama data qasa, yasaki murmushi sannan yace "akwai mutanan dasuke jirana ne dangane da bude wannan sabon companyn, shiyasa zan fita, Amma bazan dade ba zan dawo" Kafin mama tabashi amsa, qasa-qasa Aisha tace "Ina kwana" Murmushi yasaki, yasan cewa Dan kada mama taji taqi gaida shi ne, shiyasa tayi masa wannan gaisuwar, Amma Badon hakaba Shima yasan bazai samu gaisuwa agareta ba Maimakon ya amsa Sai yayi shiru tareda zuba mata ido yana Binta da wani irin mayen kallo,har zuwa wannan lokacin bai zauna ba, yanda Aisha take a tsaye tana qoqarin hada tea din, haka shima yakama daya daga cikin kujerar dinning din yariqe, wani irin nishadi yake ji a ransa harma ya manta cewa mama tana wajan. Mama ta d'ago zata masa magana taji Aisha ta gaishe shi Amma yaqi amsawa saita kamashi yana kallon ta, cikin mamaki tace "menene kake kallon ta,kokuma yanda kake tuhumar 6arayin Gwamnati itama tuhumar ta kake?,to wannan de Batada abun dazaka tuhumeta akansa" Murmushi yasaki, dimples dinsa suka futo, yaja kujerar yana qoqarin zama, Hips dinta ya kalla yanda suka sake bajewa fiyeda ranar daya fara ganin ta, ya tuna tsayaiyun breast dinta yanda yake matsa su cikin nishadi kamar karya daina, cikin qasa-qasa da murya yace "tana dashi mana" Mama tace "au tanada abun tuhumar kace?" Cikin sauri Aisha tabar wajan, domin kuwa Dama mama tace inde danta yana waje toka Barta tagana da danta,qasa-qasa yabi bayanta da kallo, cikin zuciyar sa yace "wannan ai itace yakamata a tuhumeta, tunda harta mallaki wad'annan abubuwan Kuma ta sace Min zuciya ai dole na tuhumeta, kamata yayi ma nasaka ta adaki na kulle kofar nafara tuhumar ta tayaya akai ta mallaki wannan kayan alatun?(😍) Mama dataji yayi shiru itama saita share shi tafara cin abincinta, sun kusa gamawa kenan sannan munirat tafuto itama taja kujera ta zauna tafara cin abinci Bayan ta gaida mama. ****** Da yamma Bayan yadawo yana zaune a part dinsa yanashan Lemo, ya kalli munirat yayi mata magana, ciki ciki ta amsa masa, ahankali yasake ce mata "ki shirya jibi zamuyi taron bude sabon company, kece nafara fadawa, idan da wadanda Zaki gayyata saiki sanar dasu" Wani irin farinciki ne yakama munirat, batasan lokacin data rungume Shiba, nuna masa tayi batasan cewa ita zai mallaka wa kamfanin ba, cikin kissa tace "Congratulation my Dear, Ina tayaka murnar bude sabon company, Allah yasa mu mora" Mamaki ya kamashi,tabbas yasan yamata laifi saboda abinda tagani jiya yana yiwa Aisha, Amma Kuma yanda tad'auki zafi da fishi akan hakan kawai lokaci daya yanzu daga jin maganar company harta manta abinda yafaru? Cikin mamakin sauyinta na lokaci daya yace "Amin ya Allah" Tashi yayi yatafi wajan mama domin itama ya sanar da'ita, yana fita munirat tad'auki wayarta tafara Kiran Yan gidansu tana sanar dasu jibi akwai taro, Shahaab zai mallaka mata sabon company, Bayan takira yan'uwanta, saita koma kan qawayenta, babu Wanda bata kiraba, acikin danginta ma wanda ta dade bata kirashi ba yau ta kirashi, saboda tana so ta kankarowa kanta daraja a'idon duniya. Murmushi take ta saki ita kadai tana lissafa irin mutanan dazata dauka aiki a qarqashin companynta. Tun daga ranar dasuka hadu a dinning bai sake ganin Aisha ba, yasan kuma Sarai fishi take dashi, shi Kansa idan ya tuna da yawan qaryaiyakin Dayayi mata saiya ji tabbas duk hukuncin data masa din hakan yayi, koda yazo wajan mama baya ganin ta, gaba daya a kwana dayan dabai ganta ba, duk Sai Idonsa suka fada. anar bude company Shahaab tun sassafe yafita, Aisha kuwa tana d'akin mama, yau tasaki ranta ganin yanda maman take janta ajiki, itace ta fesa mata turare sannan ta kalleta tace "mama kinyi kyau sosai, nasan idan kikaje wajan Nan Sai kowa yace mama nah tafi ta kowa kyau" Murmushi tayi tace "ki shirya muje" Cikin sauri tace"a a mama, zan zauna agida inyi miki girki me dadi kafin ki dawo" Bakomai ne yasa tafadi hakan ba Sai Shahaab da batason Gani, sosai ranta yabaci saboda abunda yamata, Sanadin sa tafara ja'inja da mahaifinta, duk yanda take da kunya saboda Shahaab tafuto fili ta fadawa Abban ta cewa itade Shahaab take so. Cikin farinciki mama tace "to shikkenan" Hannunta Aisha ta kama suma futo har compound din gidan, driver yad'auki mama, sannan ita Kuma tajuyo cikin gida. Wajan taro yayi tsari da kyau yanda yakamata, manyan mutane Yan kasuwa da sauran abokan huldarsa sun halarci taron, Bayan anbude taro da addu'ah anyi Yan jawabai, daya daga cikin masu ruwa da tsaki akan aikin companyn yatashi yafara bayanin yanda sukayi aikin companyn cikeda inganci dakuma ingantattun kayan aiki daga qasar waje. Munirat tana hakimce agefe guda ita da bataliyar mutanan ta, taci Gayu harta gaji, ta matsu a kirata a matsayin mamallakiyar company, momynta Sai zungurinta take alamun itama ta matsu Akira munirat din. Ramadan yana kusa da mama, acan Gefe Kuma Shahaab ne yayi masifar kyau cikin manyan Kaya, Ramadan yasake kallon girman wannan company Amma cikin ransa yana mamakin irin son da Shahaab yakewa munirat, tun ranar dayace zai mallakawa wani mutum Mai mutuqar muhimmanci yasan cewa ba kowa zai Bawa ba face munirat. Bayan gama bayanin company da abundaya qunsa aka Bawa Shahaab damar magana domin nunawa mutanan dasuka halarci taron jin dadinsa dakuma godia agaresu. Tashi yayi cikin nutsuwa yafara da gaida mutanan wajan sannan yad'ora da cewa "a rayuwa inajin dadin yanda mamana take Bani kulawa, da yanda ta tsaya tsayin daka wajan ganin ta inganta min rayuwa ta, banida abinda zance da mama face godia, sune jin dadina itada matata munirat" Munirat tayi wani fari da idonta tana sake hura hanci,wajan yayi tsit kowa yana jin yanda Mahmud din yake magana kamar bayaso, saida yasake kallon kowa sannan yaci gaba da cewa "saide wannan company, ban ginashi da sunana ba, tun farko akwai wadda nayi niyyar mallakawa, ita din mace ce mai mutuqar muhimmanci a gareni, zan'iya sadaukar da rayuwata domin ta.... Dalilin hakane yasa na mallaka mata wannan company, ba kowa bace face AISHA" Daukacin mutanan wajan Nan da Nan suka dauki tafi. Ramadan yajuya ya kalli munirat da gumi ya wanke wa fuska, ya kalli Shahaab yasaki wani irin murmushi, yasan mutane dayawa zasuyi tunanin mama yabawa company duba da yanda yafara da yabon ta, sannan Kuma da kasancewar ta itama sunanta AISHA, wata irin dariya ce ta kama Ramadan yayi qasa da Kansa ya tuntsire da dariya domin Gano inda maganar abokin nasa tanufa. Dam dam, gaban munirat yafadi, lokaci daya gumi ya wanke mata fuska, mutanan data gayyata kuwa gaba dayansu juyowa sukai suna kallonta jin labari yasha bambam Shahaab kuwa yana gama wannan jawabi yad'auki takardun company, wajan da mamallakin company zaiyi sign yakalla, shiru yayi yarasa wanne irin sign zaiyi mata? Baisan Yaya take signature dinta ba, danhaka yabi shawarar zuciyar sa yayi mata sign da ASH~HAB (yau Shahaab yataro December awajan munirat 😂🏃🏻‍♀️Dan yawuce march) Littafin SHAHAAB na kudi ne, duk wadda taqi biyan kudi ta karanta bazan ta6a yafe mata ba, har abada, ki biya naira 300 kacal ta account dina 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN ta Katsura shedar biya ta wannan number 08033300034 Mrs Usman ce✍🏻 Page 27 Mama tagirgiza kanta, tasan de bada ita Shahaab yake ba, domin kuwa idan itace bazaice Aisha Kai tsaye ba. ta juya ta kalli Ramadan, taga yanata dariya,ahankali ta rage muryarta tace "wacece Aisha?" Cikin sauri Ramadan ya kalleta, dahar zaice Aisha ai tana tare dake mama, Sai yayi tunani Gara taji daga bakin Shahaab din, tunda yasan dole zaiyi mata magana cikin fahimta, Girgiza Kansa yayi yace "jinake ke yake nufi mama" Mama ta kalleshi tayi murmushi, tasan Dama bazai fada mata gaskiya ba, Amma babu abinda bai saniba akan Shahaab tunda tare suke komai. Cikin iya kissa munirat tatashi tana dariya wadda tafi kama da yaqe, Sai firfita take da hannunta ta silale tabar wajan, Qawayanta suka Mara mata baya. Mama kuwa bata tafi ba, saida aka gama taro da'ita, har zuwa lokacin Ramadan yana tare da'ita, mutane Sai zuwa suke suna gaishe ta, saida mutane suka Dan ragu, sannan Ramadan ya rakata mota tatafi gida. Mama tana zuwa gida tasamu Aisha afalo tana kallo, tana ganin Zuwan mama tatashi tsaye, cikin ladabi tace "mama sannu da zuwa" Mama ta zauna a kujera tana cire agogon dake daure a hannunta tace "sannu Aisha, yagida? Kina zaune ke kadai bakya gajiya da wannan kallon ne?" Murmushi tayi tace"mama agida Bama kallo, shiyasa yanzu yake birgeni, Amma idan bakya so insha Allah zan Dena" Cikin sauri tace"a a, yi abinki, idan nahanaki kallo menene ribata? " Cikin ladabi tace"to mama nagode, nakawo miki abincin danayi miki?" Murmushi mama tayi tace"saida kika yi girkin de, tojeki kawomin " Cikin murna ta wuce kitchen tazubowa mama dambun shinkafar datayi Wanda yaji kayan hadi harda su hanta yanata turiri, mama tace "masha Allah, Aisha kece kikai wannan?" Murmushi tayi tace"nice nayi mama, ko nazauna nabaki?" Tace"A a karki damu, zanci dakaina,Amma ki ajiyemin shi da daddare zan sake ci, yanzu de jeki kiramin Munirat" Cikin sauri ta kalli mama, itafa batason shiga sabgar wannan matar tasa,ko kadan batasan abinda zai hada su, cikin sanyin jiki tace"mama ai bansan part dinba" Mama tayi murmushi tace"a a, baki ta6a zuwa bane?" Daga mata Kai tayi,mama tace" a a baki kyautaba Aisha, masu suna Aisha fa sunada kirki, ko baki San Nima sunana Aisha ba?" Kallon tayi tace"bansani ba mama, ashe haka sunan ki" "haka sunana, Kuma nasan duk me suna irin nawa tanada kirki, saboda haka kede baki kyautaba da baki ta6a zuwa kun gaisa da munirat ba,karki damu da halin ta,haka take, Nima haquri nake da'ita,idan kika fita zakiga wani part daga hannun damanki, kije kice mata tazo in jini" Tace "to mama" sannan ta juya tafita. Ta danyi tafiya medan Nisa sannan ta qaraso part din, wasu ma'aikata tagani a tsaye daga Gefe, gulma ta rufe musu ido ko lura da Aisha basuyi ba, daya daga cikin su yace"ai yau yalla6ai yayi maganin wannan matar tasa, muda mukaje muka tsatstsara wajan muka share, mu akai komai akan idonmu, kamfanin fa ta fadawa mutane ita zai Bawa, habaaa! yalla6ai yana tashi saiya Bawa Hajiya Mama kamfani, bakuga yanda take gumi ba" Wani zai sake magana Aisha tace"dan Allah inane qofar shiga part dinnan?" Juyowa sukai suka kalleta, saikuma suka fara kuskurin kunya, suna tunanin taji abinda suke fada Kuma suna tsoron taje ta fadawa mama, ita kuwa suna nuna mata ta wuce, tana shiga part din taga yasha bambam da'irin na mama, tsaruwar Kam harta yi yawa, idan anan part din take 6ata lokaci zatayi wajan kallon part din kawai. Munirat tagani a zaune da wasu mutane su su hudu, Dan kwalin kanta yana riqe ahannunta, ta hargitsa gashin dokin kanta, masifa ta rufe musu ido basu maji shigowar Aisha da sallamar taba, ikee tace "waima wacce shegiya ce wannan Aishan?" Kai tsaye munirat tace"uwarsa ce mana, da'ita yake" Ajiyar zuciya ikee tayi sannan tace"ni narasa abun damuwa anan munirat....tun farko fa kece kikai wasa da damar ki da har Zaki Bari yadinga fifita wannan tsohuwar sama dake" Hauwi tace "Allah natuba mezatai dawani company yanzu? Taci zamaninta tana neman shiga naki zamanin keda mijinki, Shima da niyya yabata ai, yasan tana mutuwa kudin de nasane" Qanwarta Maryam tace"amma Anty ya Yaya Mahmud zai mana haka? Mommy tana can gida fa tayi gayya, tun jiya muke hada abincin baqi saboda mutanan data gayya ta" Munirat ta goge Hawayen idonta tace"Dama mamarsa ta tsaneni, narasa Mena tsare mata, da kunne na naji yana cewa zai Bani, Amma nasan inde yafada mata Dama zata hanashi yabani,tunda gashinan anrubuta sunanta akan takardun ai shikkenan,Kuma wallahi Saita gane...." Maganar ta ce ta maqale ganin Aisha a tsaye abakin qofar Dakin, cikin masifa tace"kekuma ubanme kike akanmu? Munafuka muna magana kinzo kin tsaya mana aka wato Zaki kwasa kije kifada mata ko?" Cikin sauri tace"mama ce tace kizo tana kiranki " Cikin tsawa munirat tace"fice kibarmin Nan kona tashi na kakkarya ki,annamimiya" Cikin fishi Aisha ta juya tabar mata part dinta, qasa qasa tace"wallahi Bani ba saide ke" Ikee tace "wacece wannan din Kuma?" Munirat tace "baquwar uwarsa ce, shegen cusa kaine da yarinyar natsane ta wallahi" Maryam tace "tabdi, lalle Anty akwai aiki a gabanki, kina zaune da wannan yarinyar a gidan Nan? To Bari kiji daga baqunta tana Dan kula da mahaifiyar sa zata zarce kulada mijinki, ke bakiga dirin yarinyar bane?" Munirat tace "nikuwa ninaga uban diri ma,ai Ina ganin iya duniyanci awajan wannan tsohuwar, rannan daga zuwa na part din zuciyata daya Naga takama yarinyar ta rirriqe masa shikuma Sai ta6awa yarinyar nono yake" Hade baki sukai atare sukace "nono?" Tace "nono kuwa, tundaga ranar nasan banida maqiyiya irin mama, yaza'ai yarinya danya sharaf kamar wannan zaka turawa namiji baligi kamar Mahmud ita yana ta6a mata nonuwa,yanda nasan mijina idan yagani ma Hankalinsa tashi yake, bare Kuma ace anbashi yata6a, Sai kinga gashin tama shegiya kamar aljanna, sauqi na daya nasan Mahmud din yanmata basa gabansa, Aida yanda zai dinga Binta saina raina kaina" Hauwi tace "tabdi, yanzun made karki zauna kisa musu ido, tashi zakiyi tsaye munirat" Haka suka dinga tattaunawa suna zagin mama da Mahmud din Kansa. Tana komawa wajan mama tace "mama tana tareda qawayenta, nace kina nemanta to Amma sai fada takemin" Mama ta Girgiza kanta tace "Allah ya shirya, Dauko Mai ki shafamin a qafafuna" Cikin sanyin jiki tace"to mama"sannan ta wuce d'akin. Bayan ta Dauko man zama tayi ta dinga shafa mata suna hira kad'an kad'an, saida yamma taraka mama daki itama tatafi dakinta, har zuwa lokacin munirat batazo Kiran da mama tayi mataba. Da daddare suna zaune afalo, mama ta kalleta tace"Aisha jeki zubomin sauran dambun Nan danace ki ajiyemin zanci da daddare " Cikin ladabi tace" to mama " Kitchen din ta wuce, anan ta tarar da masu aiki suna wanke wanke kwanukan dasuka gama amfani dashi na girkin dare, abincin ta zubowa mama sannan tahado mata da lemuka da ruwa, cikin nutsuwa ta ajiye mata sannan ta zauna tace"in baki ne mama ko zakici da kanki?" Murmushi tayi tace"zoki Bani" Zama tayi akan kujerar, tafara bata abincin, mama tace"Aisha girkin yayi dadi sosai, kinsan rabona da dambu na Dade, duk wadannan masu aikin basu iya irin wannan girkin ba, yawanci saide qauye" Aisha tayi murmushi batace komai ba, mama tasake cewa"qirjin de yadena miki ciwo ko?" Cikin kunya tace"eh yadena" "to Bayan fa?" Aisha tace"Shima yadena" Kafin tasake jefo mata wata tambayar yayi sallama yashigo falon, wani soja ne a bayansa yabiyo shi da wata breaf case me kyau,wani irin farinciki ne yakama shi yanda yaga tana Bawa mama Abinci, Kota wannan Fannin bazai ta6a hadata da munirat ba, saboda tana kula da mahaifarsa ,tana daga gefen hannun Daman mama, shikuma yazaune agefen hagun ta,tareda kallon Aisha Qasa qasa, ajiye masa brief case din sojan yayi, sannan yajuya yafice,Suna hada ido tayi sauri tayi qasa da kanta, ahankali ta ajiye abincin zata tashi, cikin sauri mama tace "Aisha zauna mana, Ina zakije kina Bani abinci?" Ido yazuba mata kamar yasamu TV, ita kuwa kanta yana qasa tace "mama jinake Zaki qarasa da kanki" Cikin sauri mama Tace"A a zauna kibani,saida kika sangarta ni dabani abinci sannan Zaki gudu? Wannan dakike Gani ba Bani zaiyi ba saide ma yafara min shagwa6a nabashi" Ta qarasa maganar tana nuna mata Shahaab, batayi gigin kallon inda yake ba tace"yalla6ai Ina wuni" Wani iri yaji, yalla6ai? Me yarinyar Nan take nufi? Jin yayi shiru yasa Mama ta kalleshi tace"narasa meyasa idan Aisha ta gaishe ka bakason amsawa, Karage qiyaiyarka ga mata mana" Murmushi yayi cikin shagwa6a yace"mamaaah..."sannna yad'ora Kansa a cinyar ta, yazagayo da hannunsa ta hips dinta, ahankali Aisha ta zauna, tana zama taji ya mintsineta Adede kan hips dinta, kallon sa tayi taga Idonsa a Lumshe kamar bashi ba, mama ta kalleshi tace"baka rabo da fitina Mahmud,mekakeso yanzu?" Wani irin taqaici ne yakama Aisha, tad'an kalli mama taga Sai wani riritashi take kamar wani jariri, tunanin tane ya tsaya lokacin dataji yana shafa hips dinta,gabanta ne yafadi, tasake kallon sa taga Idonsa a rufe, shi ko tsoron mama ma bayaji, Bayan tsoron taji motsin hannunsa, ahankali taji yace"mama nagaji ne" Mama tace"tun safe kunata aiki ai dole agaji " Tajuya ta halli Aisha tace"Aisha laifin me kikayi wa Abbanki ne ya turo ki aiki wajena?" Cak Shahaab ya tsaya da abunda yake, sakamakon tambayar ta mama ta shige shi, shi Kansa yanaso yaji dalilin zuwan ta gidan, yasan idan ya tambayeta bazata kulashi ba, tunda yaga alama har yanzu bata huce ba. Gaban tane yafadi, cikin sanyin jiki tace"Mama wani suke son su auramin, nikuma Bana sonsa, akwai Wanda nakeso, shine Abbana yace Gara yaturani aiki inyi nesa da gida saboda karna dinga haduwa da Wanda nakeso din" Mama tace"subhanallah, Aisha ai ba'a bijirewa iyaye, duk abinda suke so shi akeyi, Amma menene laifin shi Wanda suke so subakin?" Cikin sanyin jiki tace"bashida laifi mama, yanzu ma nakoma sonsa, shizan aura" Cikin sauri Shahaab yabude Idonsa ya kalleta, lokaci daya fuskarsa tayi kicin kicin 6acin rai da tsananin kishi yafuto qarara, mama kuwa murmushi tayi tace"ikon Allah, har tsuntsun yatashi daga kan Wanda kike so din? To meyasa kika haqura da za6in naki? Inde har yanzu kina sonsa, Sai muje dake har Garin naku inyi musu magana cikin fahimta subarki ki auri Wanda kike so din" Cikin sauri tace"A a mama, Aina haqura dashi, saboda ya yaudareni, ya6oyemin gaskiyar waye shi, Bayan nagane Kuma naji duk na tsaneshi"(🙆🏻‍♀️😂) Runtse Idonsa yayi, cikin 6acin rai ya d'ago Kansa daga cinyar mama ya kalleta yace"kozaki danyi shiru please?, banson jin wannan shirmen " Mama ta kallashi da tsananin mamaki tace"menene abun 6acin rai anan? Kai take Bawa labarin?" Cikin masifa yace"mama I'm tired... tazo tasani agaba tanamin wani zancen banza da wofi... " Idon Aisha yaciko da qwallah, yanda taga ransa ya6acin Nan saita tunada ranar dasuka fara fada yake mata kashedi akan ogonsa Mahmud Wakili, cikin kuka tatashi da gudu ta wuce daki, bayanta yabi da kallo, yanda take gudun yasa hips dinta suke rawa,wani irin jarabben yawu ya hadiye saida yaga shigewarta daki sannan yasaki wani irin tsaki. Mama ta kalleshi fuskarta d'aukeda damuwa tace"meyake damunka ne? Yarinya tana bakin qoqorin ta akaina bata gajiya, sannan muna Dan zancen mu kazo kasata kuka ka Koreta, haka kawai badakai take magana ba kahauta da fada, ko tunda kake zuwa falon Nan ka ta6a ganin ta tazauna?" Cikin kishi yace"mama Kuma saita zauna tanata cewa ta tsaneshi ta tsaneshi kinajin ta bazaki hanata ba? Tace ya yaudare ta kinyi shiru baki dauki mataki ba, tadawo tace ta tsaneshi Shima baki hanata ba, Kuma idan tace bata sonsa fa kwata kwata?"(🤣) Mama tace"saime? Dakai take? Kai tace ta tsana?" Cikin kumburi yace"a a " Tace"to banaso, yanzu kasa tana kuka idan tafara wannan shegen fishin Nata Allah ne kadai yasan ranar dazata sauko, tashi kaje dinning Kaci abinci katafi part dinku" Cikin shagwa6a yace"mama korata kike ko?" Tace"nibana korarka,Kai dinne wani lokacin kacika rigima,kabar matarka acan nikuma kazo Nan ka dameni" Murmushi yayi yace "shikkenan naji zan tafi, tashi muje kibani abinci" Cikin sauri tace"me amfanin matarka?Nima Aisha ce tabani" Murmushi yayi cikin ransa yace"aikuwa Nima saita Bani" Amma a fili saiyace"to Bari in Dan kalli labarai idan zan tafi inkwnta saina ci abincin" Tace"toshikkenan saida safe zanje in kwanta Nima,tunda ka kori yar hirar tawa," Cikin jin dadi yace"to mama saida safe" Harta juya zata tafi saita dawo tace"yawwa wacece Aisha ne?" Cikin sauri yajuyo ya kalleta yakasa bata amsa, tace"ka tsareni da ido baka Bani amsar tambaya taba" Cikin wata irin kunya ya sunkuyar da qansa tareda shafa sumarsa yace"mama ai kece" Murmushi tayi tace"banason qarya Mahmud, wacece Aisha?" Cikin kunya yacigaba da shafa sumar sa,saide Kuma yaqi kallon ta, ahankali yace"wata ma'aikaciyar muce" Murmushi tasake yi cikin ranta tana qara godewa Allah Dan da alama Mahmud din Nata soyaiya yake batare data Sani ba, cikin murmushin tace"ma'aikaciyar takuce zaka iya sadaukar da ranka saboda ita?" Cikin shagwa6a yace "mamaaaah...." Dariya tayi tace"to in tayi tsami naji, saida safe " Cikin sauri yace"to Allah yakaimu mama" Saida tashige daki sannan yasaki wata irin ajiyar zuciya, saida yayi Zaman minti ashirin shi kadai a falon, sannan yatashi yanufi dinning, yau da Kansa yazuba abincin acikin wani plate Mai kyau. Sannan yad'auki gorar ruwa guda daya, yad'auki brief case dinsa yawuce Dakin Aisha. Handle din dakin yakama sannan yashiga tareda rufowa, duhu ne ya wanzu a Dakin da alama ta kashe wutar ne ta kwanta, kunna wutar yayi lokaci daya ya hangeta kwance akan gadon jikinta a rufe ruf da blanket. Hasken data Gani a idonta ne yasa ta bude idonta, lokaci daya idonta ya sauka akansa yana kokarin ajiye kayan dake hannunsa. Shahaab littafin kudi ne, nera 300 na kacal Zaki tura 300 ta wannan account 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN tareda shedar biya ta wannan number 08033300034 Mutara zuwa gobe🙏🏻 El Yaqoub ✍🏻 BASAJA TAKU NA BIYU Ummah da Abba suna tsatstsaye atsakar gida suna kallon ikon Allah, Hajja ta riqe waya a hannu Sai zagaya tsakar gida take tana mita. Abba ya kalleta yace"Hajja da haquri kikai da Kiran wayar nan haka, yanzu karfe goma saura, itama idan kin sameta ma may be basa tare Dame wayar, kokuma sunyi bacci" Cikeda masifa tace"mamuda kaifa nariga nagama sanin baka damu da yarinyar Nan ba, inda kadamu da'ita lokacin data bugomin waya nace bazan bata kaiba Aida haquri yakamata kabani inhadaka da'ita, Amma saika yi mursisi kakara redio a kunne, nafi sati Ina Kiran yarinyar wayar taqi shiga, tayaya Hankali na zai kwanta?" Umma ta kalleta tace"Hajja to tunda taqi shiga kibari mana gobe saiki kirata" "bazan Bari ba Hadiza,kunga banfa riqeku ba, kuje kuyi kwanciyar ku, Amma nikam yau saina ji muryar mesunan qawa zan iya runtsa wa, haba dadewar ai tayi yawa, Yan birni da suka 6aci dason duniya waya Sani ma kohar sunyi tsiren ta" Ummah ta sunkuyar da kanta tayi shiru, Abba kuwa kujera yaja ya zauna, Ina ya'isa yaje yabar Hajja awaje? Aikuwa da basu wanye lafiya ba gobe. ****** Bayan ya ajiye kayan zama yayi aqasan d'akin tareda daure fuska yace"sauko magana nazo muyi" Babu musu taja hijabinta tasaka, sannan ta sakko Qasan Dakin ta zauna kanta aqasa hannunta duka biyun suna cikin hijab dinta. Ajiyar zuciya yasauke yace"ba gaisuwa?" Kanta aqasa tace"yalla6ai Aina gaisheka dazu" Cikin sauri ya katseta "ke da Allah banason wannan yalla6ai-yalla6ai din,shikkenan dan abu yafaru bazaki tsaya ki saurari abinda zan fada miki ba, saiki yanke min hukunci, agabana kina cewa Wai wani kike so, ni kin tsaneni ko maaamah?" Yaqare maganar da wata irin murya kamar zai Fashe da Kuka. Hakanne yasa zuciyarta ta karye, Nan da Nan tafara hawaye, cikin kuka tace"bakaine ka yaudare niba, kasa Abbana ya rabani da Hajja yakawo ni wani waje aiki,aidama baka sona matarka kakeso tunda Qin fadamin kokai waye kayi" taqare maganar tana turo bakinta gaba Cikin sigar rad'a yace"Amma nabaki haquri..." Cikin kuka tace"ainima bance komai ba,kawai de karabu Dani kafita daga rayuwa ta, tun farko ma da nasan cewa kaine Mahmud Wakili bazan saurareka ba, sawun giwa ai ya take na....." Cikin sauri ya katseta"maaamah.... Tun farko nasan cewa bakya sona, ranar Dana fara haduwa dake ma nasan cewa bakya sona..." matsowa yayi gab da ita, yasaka hannunsa biyu yariqe fuskarta,yasake yin qasa da murya yaci gaba da fadin"amma ni Ina sonki maaamah..." Lumshe idonta tayi, Hakanne yabawa Hawayen idonta damar zubowa akan kumatunta, ahankali ta bude idonta, sannan tasaka hannu ta janye nasa hannun daga kan fuskarta, ta kalleshi tace"bazai iyu ba, saboda Abba na bazai baka niba, maqocinmu yaganni lokacin dana shiga motar ka, Kuma yaganni lokacin Dana futo, Abba na yayi fishi Dani Kuma duk kaine sila, tun farko inda kayi magana dashi dole zai fahimceni" Tunda tafara magana ya zubawa lips dinta ido yana kallo, kawai moment dinsu na cikin mota yake tunowa lokacin dayake kissing dinta. Ajiyar zuciya yayi shibaiga abun damuwa anan ba, ahankali yace "to maaama munshiga mota me mukayi? Meyasa Dan kin shiga motata Abba zaiyi miki wata fahimtar, ai babu abinda mukai..." Cikin kuka ta daga murya tace"basaida ka tsotsi bakinaba, Kuma aina hanaka Amma shine kaqi denawa" Murmushi yayi, yace"ni nama dade da mantawa maaamah, jinake kema kin manta, maaama akwai dalilin dayasa na 6oye miki kaina, mama da Ramadan sune suka sakani hakan" Cikin sauri ta d'ago ta Kalle shi, jijjiga Kansa yayi yace"yes.... Saboda wani dalilin su Wanda nikaina banga amfanin saba, Sai Bayan nahadu dake ne Naga amfanin hakan tunda gashi nagane kina sona da gaskiya, ba kudina kikeso ba, bakisan waye niba Ina dashi banida shi Amma ahakan kika saurareni, maaamah...Ramadan koda yaushe bashida burin yaga naqara aure, mama kuwa tayi maganar tayi maganar harta gaji,kiduba shekaru na maaamah har yanzu banda yaro ko daya, mama kullum burinta shine taga naqara aure ko Allah zaisa na haihu, Amma naqi yarda saboda inason matata munirat banason nayi abinda zaisa hankalin ta yatashi har tayi tunanin nadena sonta, naje Asbiti andubani, doctor's dayawa sun tabbatar min qwayoyin halittana lafiya suke, zan iya haihuwa a kowanne lokaci, Amma munirat bataje ba, koda yaushe tana fadamin haihuwa ta Allah ce,yafimu sanin halin damuke ciki, Kuma ita gidansu sunada gadon haihuwa tunda ba'ita kadai mamarta tahaifa ba, muma idan mukai haquri Allah zai bamu watarana, tafi tunanin rashin lafiyar daga nine, hakanne yasa na shirya har qasar waje naje akan hakan suma sun tabbatar min lafiya ta kalau, hakan Dana fadawa mama da Ramadan shine yabasu damar da suka sake damuna akan maganar aure. Bayan haduwa ta dake, ban 6oyewa Ramadan komai ba, saboda a ranar ma dashi muka fara zuwa garinku, har fadan mu saida nafada masa, daga lokacin da nabar garinku ban sake tunanin komawa ba, saida tunanin ki yamin yawa sannan, tunda Ramadan ya lura da tunanin danake nakuma fada masa komai daga Nan yafara cusa min ra'ayin ki araina daga qarshe harna gane Ina sonki, kullum Ramadan fadamin yake karna kuskura nafada miki koni waye, yakamata ace nagama sanin halin ki, shin zamuyi abota dake ta Amana kokuwa? Banta6a tunanin akwai soyaiyar gaskiya a duniya ba Sai ranar dakika Bani kyauta kika fadamin kudin karatun qaninki ne da kike Tarawa kika siyomin agogo dashi, kin sake shiga raina a ranar, kin birgeni yanda bakya zato, na fadawa Ramadan komai, shine yasake Bani qwarin gwiwar dazan tunkareki da maganar soyaiya, inba hakaba to shi zaizo har gidanku yace yana sonki, hakan ne yasa nafada miki Ina sonki, Sai Bayan kin amince da soyaiya ta shine Zaki gujeni?" Sauran Hawayen idonta ta share, sannan tace"kaine kaje super market akano koba kai hane? " Ahankali yace"nine, kuma tun a ranar nayi DANA SANI akan rufe miki koni waye danayi, inda kinsan cewa nine Mahmud Wakili da tuni na bayyana a gabanki na tambayeki waye wannan Yaron dayake tare dake?" Cikin shagwa6a ta turo bakinta gaba tace"niba saurayi na bane, saurayin fati ne" Cikin kishi yace"koma waye maamah banason kisake sauraren kowanne namiji, Rasa control din kaina nake, Bana son sake ganinki da kowanne namiji this is the first and last kinji ko?" Cikeda yarinta tace"um" Wayarsa yadauko dake gefe, yayi Dialing wata number, yasaka ta a hands-free, ringing hudu aka amsa cikeda nutsuwa, kallansa tayi tarasa bakin magana, ahankali ya jijjiga mata Kai yace"your brother..." tareda bata wayar. Cikin mamaki ta kar6i wayar tace"jabir...." Saita Fashe da Kuka Shahaab ya Girgiza Kansa, cikin ransa yace"Yarinyar Nan batada damuwa, abu kadan kuka na farinciki Dana baqinciki" Daga d'ayan bangaren cikin wani irin farinciki jabir yace"takwarar Hajja,Wai kece?" Cikin sauri Kuma tasaki dariya tace"Dalla nice" Cikin mamaki tace"amma Yaya akai Naga kin kirani da number Yaya Mahmud?" Cikin sauri tace"yaya akai kasan shi?" Yace"muna waya dashi sosai, amma ban fada masa yayata tana aiki a gidansa ba, yacemin ogansa ne yad'auki nauyin karatu na" Hararar wayar tayi, sannan ta juya ta harari Shahaab, cikin sauri tace"bawani ogansa, shine, Kuma idan nakoma gida ma saina fadawa Abba da Hajja da Umm...." Kafin taqarasa maganar Shahaab yayi sauri zai qwace wayar, itama tafara kokarin hanashi,basusan sun kashe wayar ba Garin kokawa kowa yanaso ya kar6i wayar, saida ya Kar6a sannan yace"miye haka? Meyasa Zaki fada masa?" Hawaye ne yasilalo daga idonta, cikin kuka tace"to meyasa Shima zaka masa irin nawa?" Wayar yasakar mata, sannan yariqe fuskarta da hannu biyu yace"sokike nafada masa nine na dauki nauyin karatun sa? Menene abun birgewa to? Nayi ne Dan Allah,sannan Kuma danke, dakika dauke kudinsa da kike Tarawa zai tafi makaranta kika min kyauta dashi, to gashinan nahutar dake, Saudia Kuma Dama ai kece Zaki kaimu ko...?" Yaqarasa maganar cikin sigar tsokana, cikin farinciki takai masa Dukan wasa a hannunsa, sakinta yayi yana murmushi, sannan yadauko abincin sa ya ajiye akan cinyarta yace"dazu kinbawa mama, nikuma kika hanani, yanzu saiki Bani Nima" Cikin sauri tace"kaje Kaci afalo, kaga yanzu goma da kwata, dare yayi, baka tsoron matarka tasan kana zuwa dakina?" Fuskarsa yadan daure yace"kinaso na kwana da yunwa?" Cikin sauri ta Girgiza masa Kai, yace"to bani" Kallan abincin tayi tace"to ai babu spoon" Cikin shagwa6a yace"da hannu" Cikin ranta tace"nashiga uku" Afili kuwa saita Girgiza masa Kai tace"um um ni bazan iyabb....." Kafin ta qarasa maganar cikin sigar rad'a yace"please" Badon tasoba tasaka hannunta tafara bashi abincin, duk lokacin dazata saka masa a bakinsa saiya Lumshe Idonsa sannan zai fara ci, mamaki ne ya kamata ganin yanda yakecin abinci kamar bayaso, har qaguwa tayi yagama saboda ita Bahaka mama take cin Nata ba, wanne irin cin abinci ne wannan saikace mace. Saida yaci yaqoshi, sannan yariqe tsintsiyar hannunta, yafara tsotsar Yan yatsun data bashi abincin, Idonsa a Lumshe suke yana tsotsar yatsun kamar wanda yake shan sweet, kallansa tayi tanajin gabanta yana faduwa, wani irin yanayi yana shiga jikinta, ahankali tazame hannunta daga bakinsa, babu musu yasaki, cikin wata irin murya yace"Albishirin ki" Cikin sauri tace"goro" "to menene Goron albashir dina?" Fari tayi da idonta tace"duk abinda kake so" Yace"kinyi alqawari?" Tace"inde baifi qarfi naba" Briefcase dinsa yabude, yad'auko wasu takardu yad'ora mata akan cinyarta yace"kyauta ce daga masoyi zuwa masoyiyarsa, kyautar amsa tayin soyaiya ta dakikai, fatana ki kasance tare dake da dadi ba dadi,da kudi ba kudi,kici gaba da sona fiyeda kowa a duniyar Nan Bayan iyayenki, kibani kulawa fiyeda wadda Zaki Bawa 'ya'yanki,kijani ajikinki, muyi rayuwa tare har abada, kyautar sabon company n Dana bude yau ne" Yad'ora hannunsa akan takardun tareda bude wani shafi, can qasan page din ya nuna mata yace"kinga sign dinki daga yau, a ko'ina haka Zaki dinga yi,Ash-hab sunan yamiki dadi ko?" Yaqarasa maganar tareda Dagowa yana kallon ta, tunda yafara maganar Aisha take kallon sa, wanne irin mutum ne Shahaab? Dama haka halaiyarsa take? Duk wannan abun dayake saboda kawai tana sonsa ne? Yakai mahaifin ta umara, yakai qaninta karatu qasar waje, duk wannan abubuwan da wannan facaka da kudin dayake bashida d'a nashi na Kansa, tausayin sane ya kamata,itakam Dame zata sakawa wannan mutumin a rayuwa? batasan lokacin da hawaye ya wanke mata fuska ba, dama ita Aishan yake nufi? Ashe sunanta yasaka Bana matarsa ba, Bana mahaifiyar saba, wacce irin soyaiya ce wannan? Cikin kuka tafara Girgiza masa Kai Tace"A a, ban cancanci haka daga gareka ba, matsayi na baikai Nan ba, abun yayi yawa, ka barshi Dan Allah" Matsowa yayi jikinta, kamar wanda zai rungume ta, Cikin sigar rad'a yace "haba kekuwa,menene abun kuka Kuma? Kinaso kimin asarar Hawayen ki kooo?" yaqare maganar cikin wata irin murya me cikeda fitina, Matsowa yasake, ahankali yad'ora hannayensa a fuskarta, yariqe fuskar, sannan ya matso da bakinsa dab da fuskarta yad'ora harshansa akan kumatunta, yafara lashe Hawayen datake zubar wa, jin abinda yake ne yasa tarufe idonta ruf..., ta nemi kukan datake tarasa, saida yaji tadena kuka, sannan yahade bakinsu waje daya,al'amarin daya saka duka zukatan masoyan cikin wani Hali na shauqi da begen juna, hakan yasa wannan Karon batasan lokacin data bashi hadin kaiba,Dan qaramin lips dinsa take Sha ahankali, hakan datayi ne yasake gigita Shahaab, cikin fitar wani irin numfashi da tsantsar soyaiya, yake yimata wani irin kiss,gaba daya ya manta acikin dakinta yake, zuciyar sace take zigashi akan yata6a abubuwan Nan guda biyu masu dadin shafawa, wata zuciyar Kuma tana hanashi, daqyar ya'iya zare bakinsa, gudun kada ya aikata abun kunya acikin gidansa yasa cikin mutuwar jiki, yasakar mata kiss a goshinta, tareda miqewa ya fice daga d'akin cikin sauri. Haka yakoma part dinsu Idonsa cikeda jaraba, yayi mamakin ganin munirat zaune afalo ta dora qafa daya Kan daya, yana sallama ko d'ago kanta batayi ba bare ta amsa, cikin mamaki ya qaraso wajan ta ya tsaya yace"munirat bakiji Ina sallama bane?" Kamar da dutsi yake magana haka munirat tayi masa banza, ajiyar zuciya yayi, yarasa dalilin yin fishin ta, yace"meyafaru kike fishi?" Nanma batace masa komai ba tayi shiru, Kansa ya Girgiza kawai yawuce dakinsa, idan ma akan rade radin dayake ji ne matarsa tana fishi saboda yabawa mama company ai yana ganin hakan ba zaisa tayi fishi ba, tunda shide bai futo fili yace budurwarsa yabawa ba, Yan kalamai yayi sannan Kuma yabayar da company, yanzu inda maman yabawa ma kenan haka zata yi fishi? Hakan na nufin idan mama yabawa munirat tana daga cikin Wanda zasuyi fishi akan yayiwa mahaifiyar sa kyauta, maimakon itama tayi kokari tasamu abinda yafi company awajansa, Girgiza Kansa yayi yashige toilet ya watsa ruwa,domin yanayin da yakeji ajikinsa Sai ahankali, Bayan yayi wanka yafuto ya shirya sannan ya kwanta tareda rungume fillo tsam a qirjinsa ya Lumshe Idonsa. Bayan ya idar da sallar asuba yana dawowa part dinsu yakoma ya kwanta, Bai dade da kwanciya ba akayi masa Kiran gaggawa daga kamfanin su dake lagos, cikin sauri ya shirya ko sallama baiyi da munirat ba yafita yayi part din mama, itama yaga bata tashi ba Sai ma'aikata dasuke aiki a falon, Bai kula gaisuwar dasuke masa ba yajuya cikin sauri yafita, Kai tsaye Airport yawuce daga Nan yawuce lagos. Meeting suke akan wani tallafi dayake son yiwa mata Wadanda basuda sana'ah. Saida meeting yayi Nisa aka tambayeshi takardun dasuka fara tsara komai aciki a last Zaman da sukai yadafe Kansa sannan yace"wallahi na manta, Bari nakira Sai abayar akawo" Munirat yakira, Amma yayi mata missed call kusan hudu bata dauka ba, tunawa yayi tana fishi dashi, saiya Girgiza Kansa kawai yakira wayar mama, mama tana dauka yace"mama barka da safiya" "barka Mahmud, nafuto yin break Yara suke fadamin kazo" "eh mama nazo, Ina sauri ne anyi min Kiran gaggawa daga office dinmu na lagos, gashi Ina sauri ma namanta da wasu takardu agida" "to yanzu Yaya za'ayi? Katuro Ramadan ya dauka" Tashi yayi yakoma can Gefe, cikin shagwa6a yace"mama kibawa wannan yarinyar takawo min mana" "wacce yarinya Kuma Shahaab? Inada wata yar ne Bayan Kai?" Saida yasake yin qasa da murya sannan yace"wannan yarinyar fa....me kula dake " Mama tasaki Dan qaramin tsaki tace"wai Aisha kake nufi? Shahaab tayaya zan turo ta lagos Bayan bata ta6a zuwa ba? Koba haka Bama agabana jiya kasa yarinyar Nan kuka, idan tazo inda kake Kuma ai sai duka" Murmushi yayi yace"shikkenan mama, Bari nakira Ramadan din" Wayar yakashe, yadokawa Ramadan kira, yana dauka Yace"Ramadan wasu takardu nakeso kaje gida kadauko ka kawo min su lagos kokuma kabawa wani daga cikin ma'aikatanmu yakawo min" Ramadan yace"abokina wallahi Bana gida, madam ta matsa, muntafi yankari, tana so tayi kallo" Runtse Idonsa yayi, ahankali yace"jarababbe kullum kana gida, ai hutu yaqare saika dawo bakin aiki" Murmushi Ramadan yayi yace"abar kaza de acikin gashin ta" Wayar yakashe yasake Kiran mama ta d'auka tace"zaizo?" Yace"mama baya Nan, yaje Bauchi state" "tunda kadage Sai yarinyar Nan ta taho de nasan ko yana Abuja abinda zakace kenan,ka fadawa matarka takawo takardun, Sai akawo" Cikin murna yace"to mama"sannna yakashe wayar Daya daga cikin sojojin gidan yakira, ya turashi part dinsu sannan ya turawa munirat text, Bayan taga text din saida tagama shan qamshin ta, sannan ta Dauko tabashi, shikuma yaje ya kaiwa mama. Mama tasa aka kira mata Aisha adaki, Bayan tazo tace"Ki shirya zan aikeki yanzu, zaki kaiwa Mahmud wadannan takardun" Cikin ladabi ta amsa mata, Sannan ta juya daki, tana tafiya mama ta dauki wayarta tadubo mata wasu dogayen Riguna Masu kyau, tayi oder, Bayan Tashirya tafuto mama tace"zauna akwai kayan daza'a kawo miki yanzu" Zama tayi tareda fadawa cikin tunani inane mama zata aiketa itada ba ko'ina tasani ba, wani form mama tabata tace"Aisha ga form din banki nasa an kar6o miki, kicikeshi, idan ansamu lokaci saikuje kiyi bvn abude miki bankin" Cikin ladabi tace"to mama nagode, Allah yasaka da alkhairi " Cikin jin dadi mama tace" Amin ya Allah " Sun Dan dade suna jira sannan aka kawo kayan, mama tad'auki ledar tabata tace" to gashi kije kisake shirya wa saiki futo kutafi " Har qasa ta sunkuya ta karba cikin murna tana yiwa maman godia. Kai tsaye d'akin Takoma tafara bude kayan, cikin farinciki tasaki wani irin ihun murna tareda fadawa kan gadon, dogayen riguna ne Yan Dubai masu kama da abaya har guda biyar,Sai jaka da takalmi guda bibbiyu, wadda tafi daukan Hankalinta ta d'auka wata baqar abaya wadda akayiwa adon stone a hannu dakuma Qasan a bayar da qirjinta,gaban madubi Takoma tasake taje dogon gashinta, ta daure shi, sannan tasaka rigar, fuskarta babu kwalliya ko kadan kawai lipstick tad'an shafa alips dinta, tayafa mayafin a bayar, tad'auki jakar ta riqe ta kalli kanta a madubi, lokaci daya gabanta yafadi saboda gaba daya ta sauya kamar ba'itaba, ita kanta tasan zuwan ta Abuja ta sauya nesa ba kusa ba. Futowa tayi zuwa wajan mama, tundaga nesa mama ta qare mata kallo cikin ranta tace"masha Allah " Aisha tanada kyau, babu Wanda zaiqi Aisha, gata yarinya qarama ga Hankali, Kuma batada girman Kai kasancewar ta yarinya Sai yanda akai da'ita akan komai, saboda idonta bai bude da sanin rayuwa ba, tana wannan tunanin Aishan ta qaraso ta tsugunna awajanta tace"mama nafuto " Mama tace" masha Allah takwarata kinyi kyau, toga wannan takardun zakije lagos ki kaiwa Mahmud " Cikin sauri ta d'ago ta Kalle ta"mama lagos Kuma? Ai bansan hanya ba" Murmushi mama tayi"nasan bakisan hanya ba Aisha, ajirgi Zaki tafi, direba zai kaiki Airport, sannan Kuna sauka a lagos ga wayata Zaki tafi da'ita saiki kirashi kifada masa kinzo" Hankalin tane yadan kwanta sannan tace"to mama" Tareda karbar takardun da wayar, direba ne yashigo mama tayi masa bayanin komai daga Nan suka tafi. Suna zuwa Airport yahadata da wani, cikin kulawa da girmamawa mutumin ya kalleta yace"muje ko" Aisha tayi mamakin yanda ake bata kulawa awajan kamar yar wani, itade tasan bakowan kowa bace face yar gidan mamuda da Hadiza, Amma sauran mutanan dake wajan kowa Kallan yar gidan Mahmud Wakili yake mata, duba da yanayin shigar ta, dakuma kalar fatar ta, uwa uba yanda ta riqe babbar wayar mama qirar iPhone tana Kallan pictures, kai kace wani abu muhinmi takeyi, tunda ta zauna babu Wanda yayi kasadar qaraso wa inda take, saboda kallo daya zaka mata kasan cewa irin yayan masu kudin Nan ne Wanda ake 6atasu Ana basu manyan wayoyi suna abinda suke so, bata Jima da zama ba jirginsu yatashi zuwa lagos, acikin jirgin de duk Wanda yayi mata kallon qwaqwaf, zaisan atsorace take, kamar ace kyat tazura da gudu, Amma Kuma yanda take kallon window tad'an basar, Sai hakan yasa babu hankalin Wanda yadawo kanta, tunanin rayuwar ta take Wai yau itace a jirgi a dalilin wa dalili ta, basu dauki tsawon lokaci ba suka sauqa a lagos,miqewa tayi tsaye tana daukan takardun, saide dayawa daga cikin mutane kowa yana dauke da jakar Kaya ne, Sa6anin ita da kawai takardu ne a hannun ta Sai yar qaramar handbag dinta, shiyasa kowa kallo daya zaiyi mata yasan cewa lalle yar wani ce, tafiya daga ke Sai takardu? (🤔) Ita kuwa ko ajikinta saboda batasan yanayin ma yanda ake tafiyar ba, wajan sakkowa daga jirgin ma ahankali ta sakko harta futo cikin mutane kamar yanda taga kowa yanayi, wayar mama ta dauko ajaka Takoma Gefe. Dakanta ta rubuta number,Nan da Nan kuwa sunansa yafuto,MY SON, wayar na shiga yadauka cikin sauri saboda Dama jira suke tun dazu, cikin sauri yace"mama anbata ne?" Cikin sanyin murya tace"nazo,Ina filin jirgin" Murmushi amsar ta tabashi, cikin jin dadi yace"Welcome Baby, bani 5 minutes kinji" Tace"to" Tana nan a tsaye tsawon wani lokaci saiga kira yashigo wayar, tana dauka direba yayi mata magana akan yazo daukan ta ne, fada masa inda take tsaye tayi, shikuma ya qaraso suka tafi, basu dade suna tafiya ba suka qaraso cikin Babban company, suna tsayawa driver yace"ga hanyar dazakibi Nan" Ta'amsa masa,sannan ta nufi hanyar tana tafiya, daga can nesa ta hango shi a tsaye agaban wata qofa, yayi kyau sosai cikin suit Amma babu jacket, hannunsa duka biyu zube cikin aljihun wandonsa, ita yake qarewa kallo yayinda bugun zuciyarsa yake sauya wa, Sai yanzu ne yayi danasanin zuwan ta, haka ta taho da wannan shigar tundaga Abuja kowa yana qare mata kallo? Lokaci daya yaji wani irin kishi ya kamashi, ahankali yajuya yashige cikin office din, Aisha kuwa tana ganin shigar sa cikin ranta tace"yayi kyau kamar saurayi" Ta qarasa wajan kenan zata shiga, wani Dan sanda yataho da sauri yace"ke Ina Zaki shiga?" Cikin rashin Sabo da shiga waje irin wannan tace"ciki zan shiga" "kamarya ciki zakishiga, Ina I'd card dinki?" Bude kofar da akai ne yasa ta kalli kofar, Mahmud dinne yafuto ya kalli Dan sandan, sannan yayi mata alama data shigo cikin office din, cikin sauri Dan sandan ya russuna yace"kiyi haquri Dan Allah, kinji" Aisha batace masa komai ba, tabi Bayan Shahaab suka shige, suna shiga wani irin Sanyi ya bugeta, Babban office ne Mai d'aukeda manyan dinning table guda biyu, daya kalar baqi ne, dayan Kuma milk ne, a shimfide yake da carpet tareda wani dogon esi a tsaye daga Gefe, ga wata uwar plasma a jikin bango, Sai manya manyan pictures dinsa guda biyu a manne abango, mutane hudu ne a zaune a dogon table din, dukansu suna Sanye da suit, kallon ta suka tsaya yi, cikin ladabi yace"ina kwananku" Cikin sauri suka amsa mata, Shahaab kuwa ya daure fuska yasa hannu ya kar6i takardun tare nuna mata dayan table din da hannu alamun ga wajan zama, zama tayi tareda zubawa TV ido, inda ake haska yanda yanmajalissa suke meeting akan yanda za'a qara inganta tsaro aqasa, Shima zama yayi, Amma shi fuskantar mutum hudun yake, takardun yaduba sannan ya basu suka fara dubawa suma. Saida yaga hankalin su yakoma kan takardun sannan yatashi yadauko mata wani Babban tire me d'aukeda flask din ruwan zafi, da Green tea, da madara da bournvita da Nescafe dakuma suger Dan kwali, ya ajiye a gabanta, sannan yad'auki qaramin glass cup da spoon yajefa mata green tea din guda daya acikin cup din,ya sunkuya kamar zai bata, yayi qasa da murya cikin sigar rad'a yace"meyasa kika futo da wannan kayan?" Itama cikin qasa da murya tace"mama cefa tabani" Girgiza Kansa yayi, sannan yace"kihada tea Kisha" Daga masa Kai tayi, shikuma yajuya yakoma dayan table din dasuke zaune, ganyen shayin tacire, tamaidata cikin kwali, ta zuba madara kusan cikin cup din, ta bude bournvita Shima tazuba dayawa, sannan tazuba ruwan zafi tadamasu da kauri kamar chocolate sannan tafara Sha,(😄) Shahaab dayake kallon ta ta gefen Idonsa cikin ransa yace"quruci dangin hauka... Ko tsoron ciwon ciki batayi Tanajinsu daya daga cikin su ya kalli Shahaab yace"mutum Dari ne a jikin takardar mu,za'a basu horo acikin camp Bayan an sallami masu bautar qasa" Yajuya ya kalli na gefensa yace "kayi waya da masu kula da camp, nawa zamu basu tsawon sati daya?" Cikin sauri yace"aini already munyi waya dasu, sunce abada ko nawane, shine nake Gani why not mubashi kudin Dan kadan, inyaso kowacce Sai a sallameta da dubu ashirin ashirin?" Shahaab dayake sauraron su yace"amma idan akai haka lissafinmu zai rushe, lissafin da mukai last time kusan million biyar zamu kashe,abashi kudinsa kawai yanda ya kamata, sukuma matan tsawon sati dayan da zasuje suyi a camp din Nan za'a Koya musu cake,popcorn,dakuma donut, ranar dasuka gama abawa kowacce injin aiki dakuma jarin dubu goma,dole za'a rage yawan masu Zaman banza babu sana'ah agari" Daya daga cikin su dayake rubuce rubuce ya d'ago yace"duk da haka de kudin yafi million biyar, saboda a Kwai kudin abincin su,abinsha, sutura dakuma fetir din daza'a siya saboda kunna inji daddare, sannan matar Nan daga wata qasa zata zo domin training dinnan, itama dole za'a saka kudin sallamarta aciki" Dariya suka saka gaba daya, daya na gefen yace"wallahi wannan Yacika qaqalo abubuwa" Aisha data gama shanye hadin madararta, tazuba ruwan zafi a cup din Dan kadan tahada tea dashi marar madara tafara Sha ahankali, cikin zuciyar ta tace"kowa kata6a yacema babu tayi yawa Amma su gasu suna qirga millions" Kallo ta maida Hankalinta Kai, har suka gama meeting dinsu,baqin suka fita, Shima ya tattara kayansa yace mata"muje ko " Cikin sauri ta dauki Jakarta tayi gaba, takusa zuwa kofar yasa hannu ya fuzgota, batayi wata wataba tafada cikin faffan qirjinsa, Bai tsaya jiran komai ba yasaka hannunsa ta baya ya rungume ta tsam a qirjinsa, wata irin ajiyar zuciya yake saki kamar Yaron daya dade baisha nonon uwarsa ba, tsawon minti biyu suna haka, ahankali yasakar mata kiss agoshi, sannan yace"good morning" Murmushi tasaki, bata amsa masaba ta qwace jikinta daga nasa ta nufi kofar, babu musu Shima yabita, Dan Sandan dake waje a tsaye, shi yabawa key din sannan suka tafi shida ita, suna shirin shiga mota driver ya qaraso, cikin kulawa Shahaab yace"malam Hassan babu damuwa ka zauna, zankaita Airport ne" Cikin girmamawa yace"to yalla6ai a dawo lafiya" Tunda suka fara tafiya babu Wanda yayi magana, hannu yasa ya kunna karatun alqur'ani suna saurara har suka qaraso wani super Market, kallon ta yayi, yace"muga jakar taki" Cikin alamun tambaya tabashi jakar, budewa yayi babu komai cikin jakar kamar yanda ya tsammata,hannu yasa a aljihunsa sannan yasaka rafar kudi Yan nera hamsin hamsin kimanin dubu hamsin, sannan yace"kiyi amfani dashi idan kin koma gida" Mamaki yakama Aisha, kafin tayi magana yafice daga motar tareda shigewa cikin super market din, kayan kwalliya yad'auko mata,da ice-cream dakuma turaruka, sannan yadawo cikin motar yad'ora mata akan cinyarta yace "kiyi hakuri bazan iya kaiki wajan cin abinci ba, saboda yanayin shigar ki, zan iya fada daduk Wanda ya kalleki, haka Kuma ban'isa in Hana a kalleki ba, sannan ko agida ne kidinga saka hijab banaso ko a falon mama nadinga ganinki babu hijab saboda kowanne lokaci mama cikin baqi take maza da mata" Cikin ladabi tace"insha Allah, Amma wannan kudin yamin yawa, ka ajiyemin awajanka to, idan zan kashe saina dinga karba" Murmushi yayi baice mata komai ba Kuma bai Kar6a ba, yaja motar suka tafi Airport din, Allah ya temaketa akwai jirgin dazai sake tashi nanda minti arba'in, danhaka yayi parking a cikin airport din suka zauna amota, kasancewar glass din motar tinted ne babu Wanda ma yake lura da motar, ajiyar zuciya yasauke yace"akwai ice-cream aciki ki dauka Kisha kafin kuwuce" Wani irin farinciki ne ya kamata har yana mamaki, cikin sauri ta bude ledar tadauko babbar robar ice-cream din tadebo a spoon takai masa bakinsa tace"haa" Murmushi yayi yabude bakin babu musu, cikin ransa yana farinciki kasancewar karatun dayake dora mata yana shiga cikin kanta tun kafin tashigo cikin hannunsa, saida tabashi yasha sannan itama Tasha, saida Tasha ta qoshi ta d'ago ta kalle shi tace "nagode sosai, Allah yasaka da alkhairi" Cikin sauri yace"wait.... Meyasa ne bakya son Kiran sunana?" Kallan sa tayi tace"sunan Abbana gareka, bazan iya fadar sunan ba" Murmushi yayi yace"kamar yanda kike da sunan mama nah,kinga shikkenan nahuta saiki za6amin suna Mai dadi Wanda ya dace Dani" Murmushi tayi cikin kunya tarufe fuskarta, kallon ta yasake yi cikeda nishadi yace"meyasa baki saka zobe ko agogo a hannunkiba Amma Kuma gashi kin siya kinyi kyauta dashi?" Ta6e baki tayi tace"babu komai" Batare da damuwa ba yabude wani waje cikin motar yadauko wani agogo Dan qarami na mata Mai kyau, daga Bayan agogon yaduba yasake gyara na'urar datake jikin agogon, sannan yakama hannunta ya daura mata agogon, cikin jin dadi tace"nagode" Cikin rashin damuwa yace"ban yarda ba, banason godiar ki, idan kinji dadin kyautar Dana miki yakamata ki nuna min nagani" Tace"tayaya?" Kafada yadaga yace"lokacin dakika Bani kyautar naki agogon menayi?" Idonsa ta sunkuyar qasa sannan tace"kiss" Murmushi yayi sannan yace "uhm bissimillah" Babu musu ta dora Dan qaramin bakinta akan agogon tayi kissing dinsa, cikin wani irin kallon soyaiya yace"bahaka zakiyi ba" yamiqa hannu yakamo hannunta me agogon yad'ora bakinsa yasakar wa agogon wani irin kiss Mai tsayawa Arai, sannan ya maida bakinsa kan Bayan tafin hannunta yafara tsotsar sa ahankali, gabanta ne yafadi, tarasa wanne irin d'a mama ta Haifa, ko kadan baya gajiya da kiss, tanajin sa yanda yake tsotsar Bayan hannun Nata ahankali, salon yanda yake Sha ne yasa taji yanayin ta yana sauya wa, cikin sauri ta qwace hannunta, cikin qanqan da ido yace"why?" Dan qaramin bakinta ta turo gaba tace"ni.... Nifa wani iri nakeji" Murmushi yayi yace"Nima haka nakeji, gashi Nima kimin" Yafadi hakan tareda miqo mata hannunsa Cikin shagwa6a tace"nide a a, haka kawai daga kawo takardu Kuma mama ta gane abinda nayi, nide tsoro nakeji" Kansa ya maida kan kujerar dayake zaune yace"Aisha" Yakirata da wata irin murya cikin rad'a. Kallonsa tayi tace"na'am" "inason ki sosai, please karki rabu Dani Dan Allah, kiyi tunani kisa min lokaci inaso inje Inga Abbanki" Jikinta ne yayi Sanyi, ahankali ta daga masa Kai, tace"insha Allah zanyi tunanin, Kuma zanci gaba da sonka har qarshen rayuwata" cikin jin dadi yace"kinyi alqawari?" Cikin sauri tace"eh" Agogon hannunsa ya kalla yace"nagode, muje na rakaki, lokacin tashin ku yayi" Mutara zuwa gobe insha Allah 🙏🏻 SHAHAAB, littafin kudi ne, idan kika karanta batareda Kin biyani haqqi naba, to ban yafe ba, nabarki keda mahaliccinki Nera 300 kacal, zaki turo ta account dina kokuma katin MTN ta wannan number 0164549488 Amina muhammad GTbank Number 08033300034 Mrs Usman ce✍🏻 Bata sake tabbatar da cewa Mahmud Wakili Babban mutum bane saida yariqo hannunta suka qarasa cikin Airport din,mutanan dasuke bashi girma awajan kadai ya'isa ya tabbatar Maka da cewa shi din Mai fada aji ne acikin qasar, yanda yake riqeda hannun Nata hakanne zaisa kagane cewa kode budurwarsa ce, kokuma masoyiyar 'yarsa da yakeji da'ita, mayafin kanta ne yadan zame kadan, gashin gaban goshin ta yadan futo, Dakatawa yayi da tafiya ya fuskanceta ya tsaya ya danja mata mayafin abayar har kan goshinta, yanda gashin zai rufu, sannan sukaci gaba da tafiya, Hauwi dake Gefe itada ikee suka saki wani irin murmushin kissa, cikin sauri batareda Shahaab yasani ba, suka dauki photonsa shida Aisha,ko minti biyar baiyi ba ma'aikatan wajan suka qwace Aisha daga hannunsa acewarsu tunda suna Nan ai babu amfanin zuwan sa wajan da Kansa,😚 hannu ya basu sukai musabaha daga Nan yajuya cikin sauri da wannan takun nasa na jarumai Kuma jajurtattun mazaje. Wani ke6an tattacen waje aka kaita, tana zaune tana tunani kode takira Hajja da wayar mama su gaisa dasu Ummah kafin tabawa mama wayarta? Wata zuciyar tace meyakaiki? Kina yar aiki meyasa bazaki karbi wayar masu aiki yan'uwanki ba? Saita sake tunanin cewa tana gama wayar Kuma ai zata goge number, cikin sauri tad'auki shawarar zuciyar ta, ta danna number Hajja aikuwa waya tashiga, saide harta katse, Hajja bata dauka ba, tsaki tasaki, tana kewar Yan gidansu sosai, tunda tazo saudaya sukai waya, jitake kamar tayi tsuntsu taganta acikin gidansu. Sake Kiran tayi, Shima harta gama ba'a dauka ba, wasa wasa har saida takira Hajja sau hudu, bata dauka ba, daga qarshe Sai hakura tayi tadena Kiran, tayi saurin goge number Hajja din, d'ago kanta tayi tana kallon ma'aikatan wajan yanda kowa yake abun gabansa, wani irin haske tagani kamar na camera anyi mata photo, tajujjuya taga bataga komai ba, saita daga kafadunta alamun shikkenan, Adede lokacin Kuma wani ma'aikacin yazo yace tatashi suje, jirginsu zai tashi. Hauwi ta kalli ikee tace"kinga abinda muke fada ko? Wannan yarinyar ba itace munirat tace mana baquwar mama ceba?" Ikee tace"ai gashinan tana zaune yarinya qarama zata qwace mata mijin, Dan Allah kiga yanda yawani riqo ta harda gyara mata mayafi saikace wata matarsa, waya San ma daga Ina suke? Idan kika bincika ma may be yarinyar tasaba zuwa suna sheqe ayarsu anan, inba hakaba Ina baquwa ina Hawa jirgi?" Hauwi tace"nima tunanin danayi kenan, yariqe hannunta qam yaki saki ko kunyar mutane bayaji, ai daga Gani ma Dama can kinsan tasaba dashi, aini tundaga lokacin da munirat tacemin mahaifiyar sa tariqe yarinyar shikuma yana ta6a mata nono, nasan da walakin Goro amiya, ai uwarsa ce ta daure masa gindi" Ikee tace"bakiga suma ma'aikatan wajan yanda jikinsu yake rawa ba? Suna wani bata girma saikace yar gwamna, basusan baquwa ce tazo cin Arziqi ba, kiduba kigafa ko kayan hannunta basu dubaba suka Barta tashige dashi" Hauwi tasaki ajiyar zuciya tace"yanzu Yaya zamuyi da wannan pictures din? Muturawa munirat kawai, taga abinda mijinta yakeyi da baquwar datake cewa tasan mijinta baya kula mata Dan haka bazai kula wannan yarinyar ba" Ikee tasaki dariya tace"bakida Hankali, tunda kikaga yana rawar jiki yana Bawa yarinyar Nan kulawa daga qarshe aure ta zaiyi mu muna zaune, uwarsa bazata hanashi ba tunda Dama so take yayi auren, ga shawara, mezai Hana muyi amfani da fuskokin su, mudora fuskar akan wani vedio din kawai sai mu turawa uwarsa da Kuma munirat din, suna Gani kinga mun tada fitina, daga qarshe mu ziga munirat yanda zata daga Hankalinta hartasa yasake ta, shikuma uwarsa ta hanashi mu'amula da wannan yarinyar, kinga daga qarshe mu saimuyi wuf dashi" Dariya suka saka harda tafi, suna wannan dariyar sukaji sanarwar jirgin rivers zai tashi, cikin zumudi suka tashi, dama kowacce ta gaqu ta ganta awajan Nata Alhajin. Suna sauka taga driver daya kawo ta yana jiranta, da alama Shahaab yafada musu sun taso ne,wajan sa ta nufa tashiga motar suka tafi gida, suna zuwa gida ta wuce part din mama, cikin murna mama ta kalleta tace"um um kaga yanmata, yau anhau jirgi Sai Fara'ah kike kamar gonar auduga" Cikin murna ta zauna aqasan kujerar da mama take zaune tace"wallahi mama naji tsoro sosai,amma daga baya sainaga abun ma babu wahala Kuma Nan da Nan Naga har munje" Mama tace"to Alhamdulillah, ya hanya?, nasan halinsa,inji de baiyi miki fada ba?" "A a mama, baimin komai ba, yayimin magana de akan mayafin dana yafa, Wai meyasa bansaka hijab ba,? sainace masa aikece kika Bani kayan, shikkenan Sai yayi shiru, kinga ma abunda yasiyamin" Tafadi hakan tana miqawa mama ledar hannun ta, mama ta kar6i ledar ta bude, turarukan data ganine yasa gabanta yafadi, idan bata manta ba akwai lokacin dasuka fita yawo ita dashi zuwa Cairo, tata6a ganin irin wannan turaren tace masa ya siyawa munirat shi, Amma firr yaqi siya yace turaren yayi kudi dayawa, Amma abun mamaki gashi ya siyawa Aisha, tasake duban kayan kwalliyar taga kayan kwalliya ne masu mutuqar tsada Wanda ita kanta Aishan ma tana da tabbacin batasan Yaya ake amfani dasu ba, kafin tagama tunani taji Aisha tace"harda wannan agogon na hannu na ma mama, shine duk yasiyamin, kiyi masa godia mama" Mama ta kalli Aisha da sauri, tasake Kallan agogon hannunta Wanda kallo daya ta masa ta tabbatar da na gold ne, lokaci daya Kan mama ya d'aure(😂) Cikin mamaki Tace"A a, Wai duk Shahaab dinne yabaki wannan kayan?" Aisha da bata gane yanayin fuskar mama ba tace"shine mama" Mama ta kalleta tace"toki adana agogon ki dakyau kinji? Karki Bari wata tayi miki wayo ta qwace miki, yanada tsada sosai" Cikin sauri ta d'ago ta Kalle mama tace"mama toki Kar6a kisaka a hannun ki, nabaki duka" Ta qarasa maganar tana murmushi tana qoqorin ciro agogon, mama tayi murmushi ta Girgiza kanta tace"haba Aisha, meyasa wani lokacin bakida wayo ne? Yanzun Nan ince karki Bawa kowa Amma Zaki ciro kice kinbani?" Murmushi tayi tace"mama aike kakata ce, nafada miki Ina ganinki kamar kakata Hajja, danna baki ai babu komai, Nima ai bansan zan samu ba saida kika aikeni" Mama tace"toki riqe, Nima Ina dasu Aisha, Allah yamiki Albarka yahuci gajiya, tashi kije kiyi sallah kici abinci kihuta" Cikin ladabi ta amsa mata, sannan tad'auki kayanta tayi dakinta, mama tabi Bayan Aisha da kallo, Aisha yarinya ce qarama, Kuma tana zaune dasu tsakani da Allah, sannan da alama yarinyar batada 6oye 6oye, uwa uba abun duniya bai rufe mata ido ba, to Amma abun tambayar menene yasa Mahmud yayi mata wannan siyaiyar? Gashi yarinyar tana cewa yayi mata fada akan saka mayafi, gaban mama yayanke yafadi, hakan na nufin kishin yarinyar yake kenan? Tatuna lokacin daya bude sabon company yayi maganganu dayawa harda zai iya sadaukar da rayuwar sa saboda Aisha, to wacce Aisha yabawa Company kenan?tasake tunawa da lokacin da Aisha take bata labarin saurayinta, taga kishi qarara a'idon Shahaab. Idan Aishan daya Bawa company daban, to meyasa zai Bawa Wannan Aishan kulawa haka? Abunda baka siyawa matarka ba ka siyawa yarinya? Zataso ace Shahaab ya auri Aisha,Kodan hankalin yarinyar, gashi tana bata kulawa yanda ya kamata, tun farko irin Aisha taso Shahaab ya aura, to Amma abunda take tsoro shine karfa ace Shahaab yana kula wata yarinyar daban, Nan Kuma yazo yana yaudarar yarinya, yarinya ce qarama bai kamata ace wata alaqa marar kyau tashiga tsakanin ta da Shahaab Bayan alaqa ta gaskiya da Kuma Amana ba, wadannan tunanin Nata babu me amsa mata su Sai Shahaab, Dan haka ta kawar da komai Gefe, tana jiran lokacin dazai dawo gida.😳 Wayarta ce tayi ringing, cikin sauri ta duba taga number ce, cikin mamaki ta d'auka tareda sallama, saide qara kawai takeji alamun babu network, tsaki tasaki takashe wayar, daga dayan bangaren kuwa Hajja tasake kira Akaro na biyu, mama ta d'auka tareda sallama, Nan ma qaran taji, Dan dole takashe wayar ta zubawa TV ido, Amma Kuma tarasa dalilin dayasa gabanta yake faduwa tun shigowar Kiran na farko.... Acan gida jigawa Kuwa. Hajja tasaki tsaki tace"oho, qila wani qaton arnen ne yadameni da kira, dazu nabar wayar naje gidan Jummai Dana dawo Kuma na riski kira har kusan hudu, inajin arne ne ya kirani dan Naga number special ce" Ummah dake Gefe Tace"A a Hajja kikira de kiji" Hajja tace"Aina kira, banaji, rabu dashi kawai" Ummah bata sake magana ba, Hajja ta zauna a kujera tayi tagumi tana kallon Ummah, sannan tayi ajiyar zuciya tace"nikam Hadiza keko 'Dan tunanin 'yar Nan Taki ma bakya yi?" Ummah tayi murmushin qarfin Hali, Dan zuwa wannan lokacin ita kanta tana so taga yar Tata, Amma Yaya zatayi? Hajja tace"kyayi murmushi Kam,tunda har dake aka d'aure gindi aka tura yarinyar uwa duniya, nide nagama yanke shawara, nagama hada kudi na jibi zan hau mota inje abujan dakaina a nuna min gidan me sunan mamuda inje in taho da jikata" Murmushi Ummah tayi, domin kuwa ita kanta tayi na'am da shawarar Hajjan, ajiyar zuciya tasaki tace"to Hajja Allah yakaimu jibin" Washe gari Aisha tatashi sassafe, ta gyara dakinta tayi wanka, daya daga cikin rigunan da mama ta siya mata tad'auki wata tasaka, tana gyara fuskarta agaban mirror aka turo qofar d'akin aka shigo, wata me kula da ayyukan kitchen ce tashigo jikinta Sai rawa yake tace"Aisha kizo yanzu yanzu inji Hajiya Mama" Mamaki yakama Aisha, lafiya mama harta tashi yanzu Bayan lokacin futowar ta baima qarasa ba? Ajiyar powder hannunta tayi, sannan tafuto daga d'akin, saide batasan dalili ba haka Nan take jin gabanta yana faduwa, tun kafin ta qarasa wajan mama, ta hango munirat tsugunne agaban mama tana ruskar kuka, ga wayarta ayashe aqasa, mama kuwa rigar bacci ne ajikinta me kauri da yar qaramar hula tana tsaye wayarta na hannunta idan ranta yayi dubu to duk sun 6aci, qarasa wa tayi wajan ta tsugunna sannan tace"gani mama" Munirat ta zuba mata wani irin kallon banza sannan tace"munafuka, yar'iska, wadda tagama watsewa take neman lalata min mijina, wallahi tallahi hukuma ce zata rabani dake, Shima Kuma yazo saide ya za6a ni koke, kokuma yasakeni...." Gaban Aisha yafadi, ta kalli munirat cikin ranta tace tasan Ina soyaiya da mijinta kenan,cikin 6acin rai tace"karki sake cemin zan lalata miki Miji, shi banyi masa wannan furucin ba Sai kece Zaki min?" Mama da ranta yagama 6aci tace"Aisha acikin furucin ki kinaso kicemin idan ke baki lalata Shahaab ba, shi yana lalata ki kenan, ashe abinda munirat ta fadamin gaskiya ne? Yanzu wannan aikin kuke aikata wa keda Mahmud Amma kikayi shiru baki sanar Dani ba Aisha? Wallahi kin Bani mamaki" Cikin sauri ta d'ago ta kalli abinda mama take nuna mata,vedio ne nasu itada Shahaab tsirara haihuwar uwarsu suna aikata sa6on Allah, ko kadan Hankalinsu ma baya tare dasu, gabanta ne yayi wata irin faduwa, kanta yasara, duhu duhu yanemi rufe mata ido, numfashinta yafara dauke wa Amma haka tayi qarfin halin janyo shi, lokaci daya ta Fashe da Kuka tace"mama...wallahi.... Tallahi bansan wannan vedion ba, ban aikata ba, bantaba aikata hakan da kowanne namiji ba, mama ki yarda Dani, wallahi Bani bace" Tafadi hakan tana sake rushewa da Kuka,munirat tace"idan bake bace, waye zaiyi miki qarya? Mijina baya hulda da kowacce yarinya Amma kina zuwa gidan Nan kika maida shi yazama mazinaci" Kuka ne ya taru yayiwa Aisha yawa, bata iya Bawa munirat amsa ba Sai kuka datake tana Girgiza kanta, mama tace"Aisha kifadamin gaskiya, yaushe irin wannan alaqar tashiga tsakanin ki da Mahmud?" Cikin kuka ta kalli mama da jajayen idonta, sannan ta Girgiza mata Kai, kwata kwata takasa magana, daqyar ta'iya cewa"bani bace mama" Mama tasake Kallan idonta tace"to waye ce?" Wani irin kuka ne yazo mata, tsananin nadamar sakin jikinta ga mama yarufe ta, tayi tunanin idan akwai wacce zata fara shedar ta acikin gidan to Bayan mama ne, hakan ne yasa ta Girgiza kanta, cikin kuka tatashi tayi dakinta da gudu, tana zuwa daki tafada kan gado tana kuka mecin rai, Sai yau tayi takaicin rashin waya a hannunta, data kira shi yazo ya wanke ta a'idon mama, babu Wanda zaibi bayanta awannan lokacin sai shi, wani hawaye ne me zafi yazubo daga idanuwanta, tasaka hannu ta share, Zaman me zatayi Kuma? Wacce take zaune saboda ita bata yarda da'ita ba, asali ma tuhumar ta take tana lalata da danta, wannan tashin hankalin ya'isa, bata ta6a kokarin yin abinda bai kamata ba da Shahaab asali ma shine yake Koya mata wasu abubuwan Wanda bata ta6a aikata hakan akan kowanne namiji ba,da daddare yabiyo ta daki, safe, rana, yadinga Binta da wannan shegen kallon nasa, duk da haka ita ake tuhuma bashi ba, Zaman me zata zauna tayi? Me zaisa taci gaba da zama dasu? Gara tatafi gida Dama tayi kewar Hajja, idan tanada amfani ma, Bayan tatafi zasu Gani. Tana gama wannan tunanin tatashi tashige toilet, alwala ta dauro, tazo tayi sallah raka'ah biyu, tasake yiwa Allah godia da Shahaab yabata kudi jiya, sannan tayi addu'ah Allah yakare ta akan duk wani sharrin abun qi dazata hadu dashi a hanya, tana kuka tad'auki handbag dinta guda daya, tasaka kudin da Shahaab yabata aciki, sannan ta juya zata bar Dakin hawaye yana fita daga idonta, idonta ne ya sauka akan takardun daya bata na company, har zata fita, saita dawo ta dauke takardun, ko banza bai kamata tabar masa takardun sa ahakan ba, wani zai iya shigowa Dakin ya dauke su, ahankali Tajuya ta dauke takardun, har zata fita, kawai saita sauya shawara ta dawo ta ajiye masa takardun sa akan gado, tafice daga d'akin cikin sauri, tana futowa falo bataga kowa ba, itama bata nemi kowa ba tafice zuwa compound, kasancewar sojojin sun San a gidan take, tana cemusu an aiketa ne, suka bude mata get tafice. Mama na zaune abakin gadonta hawaye take sharewa,idan ya kasance wannan vedion na Shahaab da Aisha gaskiya ne, Yaya zatayi da wannan yarinyar? Anbata amanar yarinya Amma danta na cikinta yadinga lalata da'ita, Ina tarbiyar data Bawa Mahmud? Ina yayi watsi da aikinsa dahar yafara irin wannan mu'amular Bayan yasan cewa shi din mashahurin mutum ne acikin qasar,?tanajin Aisha a ranta kamar jikar ta, bazata lamunci wani ya lalata mata rayuwa ba tun tana yar qarama,bare Kuma Shahaab,koba komai ita Amana ce awajanta, gashi yarinyar taqi fad'a mata gaskiya bare tasan yanda zata 6ullowa lamarin, abinda tasani shine tunda har yagama lalata yarinya to babu fashi saiya aure ta, idonta cikeda hawaye tafuto falo domin daukar wayarta ta kirashi. (Shahaab littafin kudi ne, idan kika karanta baki biyaba, nabarki da Allah, Allah ya qwato min haqqi na) ****** "Ramadan aure nakeso,zan fadawa mama gaskiya tamin aure" Ramadan ya kwashe da dariya yace"ikon Allah, Shahaab yau kaine da kanka kake cewa aure kakeso? To munirat dinfa?" Dan qaramin tsaki yasaki yace"Ramadan banason wulaqanci, nide nafadama aure nakeso, karkaji ansaka rana kaitsaye kace ban fadama ba" Cikin mamaki Ramadan yace"a a, Wai to har angama magana da iyayen yarinyar ne? Naji kana batun saka rana" Idonsa ya Lumshe yace"no, nayi mata magana tayi tunani taga yaushe yadace naje nasamu mahaifin ta" Ramadan yace"Saitayi tunani? Kawai ka shirya kaje ka sameshi, inde tana so kanaso menene abun tunani Kuma?" Kafin yabashi amsa wayarsa dake ajiye agefen sa tad'auki qara, excuse ya nema awajan Ramadan sannan yad'auki daya wayar yace"Malam Auwali yakake ya kwanan iyali" Daga d'ayan bangaren Wanda aka kira da Auwali yace"Alhamdulillah yalla6ai, nace wannan filayen Naka danake gadinsu Naga ka turo anfara gini har katanga tayi nisa Amma nikuma baka fadamin za'a ginaba shine nace Bari na kiraka naji Allah yasa de ba laifi mukai ba, kayi hakuri wannan aikin dashi nadogara Kuma dashi nake ciyar da ahlina" Kan Shahaab ya daure, shide yasan baida wani fili da malam Auwali yake gadinsa Bayan filayen mama guda goma daya siya ya ajiye mata, baida fili ko daya a unguwar saide na wajan mama daya siya mata, shikuma yasan cewa Bayan yagama duba takardun Nan da hannunsa yasaka su acikin ma'adanar sirrin sa ya 6oye mata su, Kuma shide baisa kowa ya Gina suba, cikin mamaki yace"wai wanne filaye kake magana akai malam Auwali?" Cikin girmama wa da ladabi malam Auwali yace"wannan filayen de daka siyesu kwanaki, to Ana gina manya manya aciki, guda biyu, Kuma gini har yayi Nisa" Cikin sauri Shahaab yace"bansan da wannan maganar ba malam Auwali, menene amfanin ka awajan za'a fara aikin gini baka kirani kafadamin ba?" Cikin sauri yace"wallahi tallahi yalla6ai jinake kaine ka turo ayi, shiyasa yanzu ma nakira inji ko laifi nayi" Shahaab yace"kaje ka samesu kuyi magana, kayi musu bayani saisu fadama Wanda yaturo suyi aikin" Yana fad'ar haka yakashe wayar, fada yafara yana sababi shi kadai, har wani Kiran yasake shigowa ya d'auka, malam Auwali yace"yalla6ai, sun fadamin wani Alhaji ne ya basu kwangilar aikin, yanzu haka yana cikin Abuja, nace su dakatar da aikin sunqi yarda sunce saka su akayi bazai iyu su daina ba, nace su Bani number Alhajin daya saka su sunce bazasu Bani ba" Cikin 6acin rai yace"okay haka sukace? Rabu dasu kakoma wajan ka ka zauna, Alhajin zaizo da Kansa ya sameka har wajan gadinka, bazan sake nemansa ba saide shi ya nemeni " Wayar yakashe, malam Auwali kuwa waje yasamu ya zauna cikin ransa yana fadin to fadan nasu na manya ne, yana kallon yanda masu aiki suke ta kwa6a cement suna aiki, shide ya zauna daga Gefe yana kallon ikon Allah, baifi minti goma Sha biyar da zama ba Sai ganin manyan motoci yayi sun nufo wajan gadan gadan, koda suka qaraso wajan basu saurari mutanan dasuke aiki asaman katanga ba suka nufi ginin suka fara zubar dashi, Nan da Nan masu aiki kowa yake ta ransa, nasama sukayi gaggawar saukowa qasa,anata ihu Ana hayaniya Amma masu motocin Nan kamar wanda suka saka Bluetooth akunne, ko kallon mutane basayi saida suka rushe ginin Nan gaba daya, malam Auwali dayake Gefe yana kallon ikon Allah ya tuntsire da dariya yace"shegiya nera..." Kamar wanda akai ruwa aka dauke, suna gama baje ginin suka kada kan motocinsu sukayi gaba, masu aiki cikin sauri suka nufi malam Auwali suka bashi waya, yana sallama Wanda yasa ayi masa aikin filin yadinga roqonsa akan yafada masa waye uban gidansa, babu 6oye 6oye yafada masa MAHMUD WAKILI ne. (littafin kudine,ki karanta abinki yafiya Kuma ban yafeba, nabarki da Allah, zai isar min" ****** Tana daukan wayarta afalo Kai tsaye ta nufi Dakin Aisha tana so ta lalla6a yarinyar ko zata fada mata gaskiyar abinda yake faruwa, saide tana shiga Dakin taga babu ita, babu dalilin ta, Sai wasu takardu data Gani azube akan gado, dauka tayi ta duba takardun, faduwar da gabanta yayi ne yasa cikin sauri ta dafe qirjinta tareda zama akan gadon, takardun tasake kalla cikin sauri tace"wannan ai takardun sabon companyn da Mahmud yabude ne, Yaya akai Aisha tasamu? (tun farko akwai wadda nayi niyyar mallakawa, ita din mace ce mai mutuqar muhimmanci a gareni,zan'iya sadaukar da rayuwa ta domin ta,dalilin hakane yasa na mallaka mata wannan company,ba kowa bace face AISHA). maganganun Mahmud suka Fado mata acikin rai lokacin daya bude company, ta tuna kallon dayake bin yarinyar dashi washe Garin ranar lokacin da Aishan take hada mata tea, cikin tsananin mamaki tace"kaiii tayaya? Yaushe har suka hadu acikin gidan Nan suka fara soyaiya bansani ba?hakan yana nufin wannan Aishan yake nufi kenan? Idan ba ita yake nufi ba tayaya zata ga takardun acikin Dakin Aishan?. Cikin sauri tafara qwala mata kira, saide duk inda yakamata ta duba, ta duba babu Aisha kwata kwata, cikin sauri ta doka wa Shahaab kira, Yana d'auka tace"yaushe zaka dawo?" Cikin mamaki yace"mama meyafaru?" Cikin tashin hankali tace"komai ma yafaru, narasa Aisha, kazo ka Nemo min ita, duk inda yarinyar Nan take kaine silar 6acewar ta, na nuna mata vedion da kukayi, daga Nan na nemeta narasa" Cikin mamaki yace"vedio Kuma mama? Wanne irin vedio?" Cikin sauri tace"kome kake a lagos kabari kazo gida yanzu-yanzu" Cikin sauri ya amsa mata, domin kuwa Shima Kansa Hankalinsa atashe yake, yanaso yasan waye yasa agina masa filayen mama, sannan yanaso yasan wanne irin vedio ne mama take magana akai, babu 6ata lokaci ya shirya yanufi Airport. Awa daya da wani abu ce takawo shi gida, a compound ya hango munirat ranta a6ace, tana ganin zuwansa Ana bude masa kofar mota tayi sauri Takoma daki, idan a Kwai Wanda batason Gani bai wuce Shidin ba. Kai tsaye part din mama yanufa, yana zuwa bata barshi ya zauna ba tamiqa masa takardun company tace"yaya akai wadannan takardun sukaje wajan Aisha?" Ta qarasa maganar tana tsare shi da idonta. Gabansa ne yafadi, ya hadiye wani irin yawu sannan yace"mama ki zauna nayi Miki bayani, please zauna" Babu musu ta zauna, tad'auki wayarta ta bude vedio tace"shikuma wannan vedion mezaka ce akansa? Shahaab Ina Hankalinka yake? Abinda kakeyi da yarinyar Nan kenan shiyasa kake mata 6arin kudi kayi mata siyaiya, ka dauki company kabata, menene ribar irin wannan rayuwar daka jefa Aisha aciki? Yanzu gashi tagudu, na nemeta narasa, shikkenan tashiga duniya kaji dadi" ta qarasa maganar tana fashewa da Kuka... Kansa yadafe yace"innalillahi wa'inna ilaihirraji'un...." Yazubawa vedio ido yana kallo,saida yagama Gani sannan yabude breafcase dinsa, yadauko computer sa aciki,sannan yatura vedio yayi Yan danne danne tsawon lokaci, sannan yatura mata computer gabanta yace"mama, idan kikaga irin wannan vedion nutsuwa yakamata kiyi ki kalla dakyau mama, yanzu duba kigani Bani bane, ba Kuma Aisha bane, dora fuskar mu akayi akan vedio,kiduba jikinsu kigani, mama wannan yarinyar tafi Aisha girma, ki kalli surar jikinta dakyau, sannan ki kalli ta namijin Shima kigani, ga zahiri nan computer ta nuna miki, duba kigani mama" Ajiyar zuciya tayi, ta share Hawayen idonta sannan tafara kallo, lokaci daya tasaki salati tace"yanzu Dama anayin haka Mahmud?" Yace"gashi kuwa kingani mama?, bani number da'aka turo miki vedion, zansa ayimin tracking dinta" Babu musu mama tabashi number, murmushi yayi har dimple dinsa suka futo yace"yanzu shikkenan Hankalinki ya kwanta?" Sake goge idonta tayi tace"AISHA" Murmushin yayi, sannan ya shafa sumar Kansa yace"mama nida Aisha mun dade muna tare" Cikin sauri ta Kalleshi, Shima ya Girgiza mata Kai sannan yace"qwarai kuwa mama,nahadu da Aisha tun cikin azumi,Kuma kece silar haduwa ta da Aisha mama, tun lokacin dakika umarceni naje Jigawa State in bude miki gidan marayu saboda qawar ki, tun Alokacin nahadu da'ita, idan Zaki tuna mama Alokacin banda magana saide ince zanje jigawa, ki gafarceni mama, Amma wani lokacin ba wajan wannan aikin nake zuwa ba, wajan Aisha nake zuwa, nadauki shawarar ki data Ramadan cewa in6oyewa budurwar danakeso kaina, hakan nayi akan Aisha, ban nuna mata inada kudi ba naje mata a matsayin Yaron Mahmud Wakili, ahakan ta amince Dani take soyaiya Dani, iyayen Aisha talakawane mama, suna rayuwa cikin kwanciyar Hankali zuwana cikin rayuwar ta saida hakan yata6a wannan farincikin na ahlinsu, duk abinda nasaka ta shi take min,kudin dan'uwan ta datake aiki take Tarawa tana so Yaron yakoma makaranta shita dauka tamin kyauta dashi mama, A'ina zan samu irin wannan soyaiyar mama?akwai Wanda akeso abata agida tace ita Shahaab take so,dalilin hakane yasa babanta yaturo ta aiki Abuja, baisan cewa gidana yasake turo taba, ranar Dana dawo daga Australia a ranar na ganta a gidan Nan idan zaki tuna Alokacin nashiga cikin wani irin yanayi, kiyi hakuri mama, Amma inason Aisha, bantaba son kowacce yarinya kamar son danake mata ba Bayan ke, inaso Dan girman Allah mama kinemomin Aurenta please" Ya qarasa maganar yana hade hannayensa waje daya, mama data zuba masa ido tana kallon sa tasaki ajiyar zuciya tace"amma kukan anyi munafukai, daga Kai har Aishan ba qananun munafukai bane, ni Ina zaune ashe ku soyaiya kuke shiyasa kake wa yarinyar mutane ihu saboda tace tadena son Wanda ya yaudare ta? Yanzu ashe Dama dakai take? Yanzu fisabilillahi ka kyauta abinda Kamin Shahaab? Kasan Sarai kanason yarinyar Nan Amma shine lokacin da batada lafiya na riqeta kadinga ta6awa yarinya nonuwa kod'an musu babu? Yarinyar Nan bata so Amma haka nasa ta tsaya saida kagama abinda kaga Dama sannan karabu da'ita,meyasa lokacin ko dukanka zanyi bazaka cemin bazaka ta6aba?" Wata irin matsananciyar kunya ce ta kamashi, yayi sauri ya sunkuyar da Kansa qasa tareda Sosa qeyarsa yace"mama saida nace Miki a a...fa" Cikin sauri tayi masa daquwa tace"qarya kake Shahaab,cemin kayi dubawa de kake,nasan hakane yaushe zanyi wannan danyan aiki?" Kansa yana qasa yayi Dan qaramin murmushi, sannan yadan kalleta cikin kunya yace"mama to Zaki nemamin auren Nata?" Fillon dake gefenta ta d'auka takai masa duka dashi tace"Wato Aisha ta maida Kai marar kunya, aini babu abinda zance, idan kaga zaka iya yiwa munirat kishiya shikkenan, dama kaine kake cewa kaida munirat Sai Allah, yanzu Yaya za'ai Naga Aisha?" Cikin nutsuwa yace"za'a ganta mama,ki kwantar da Hankalinki,mutuqar agogon Dana daura mata yana hannunta, to dole zansan inda take" Mama tasaki wata irin ajiyar zuciya tace "Alhamdulillah, Allah abun Godia, to tashi kaje kabawa matarka haquri Dan itama anturo mata wannan vedion, kabata haquri ka fahimtar da'ita cewa videon hadawa akayi" Cikin ladabi ya amsa mata, sannan yatashi yad'auki kayansa, yawuce part dinsa, yana zuwa falonsu yayi sallama tareda shigowa, tana zaune afalon saide ko kallon inda yake batayi ba, cikin zuciyar yace"fishi kan fishi kenan, Dama da fishin company yanzu Kuma ga wani ya qaru" Murmushi yasakar mata, sannan yace"Bari inzo inyi lallashi" Munirat ko kallon sa batayi ba,Shima Kai tsaye dakinsa yawuce yana tunanin irin lallashin dazai mata kozai samu yau tasakar masa jikinta yayi yanda yakeso da'ita, saboda a matse yake, kwana biyun Nan kawai yana daurewa ne,yana shiga Dakin yacire kayan jikinsa,dagashi Sai Dan qaramin towel a daure a qugunsa, murd'ad'd'an jikinsa yafuto fili, fatar jikinsa tayi wani irin fresh, lallausan gashi kwance akan faffad'an qirjinsa,yana shirin shiga wanka kenan wayarsa tad'auki qara, dawowa yayi ya zauna abakin gado tareda daukar wayar yayi sallama, daga dayan bangaren akace "Ranka yadad'e sunana Alhaji Umar Amare, nine mamallakin filayen Nan guda biyu danasa afara ginamin Kuma yanzu Yara sun kirani sun fadamin katuro a rushe ginin, shine nace ai babu Wanda baisanka ba a qasar, na bincika nasamu number ka awajan yaronka Auwali, nace Bari in kiraka inbaka haquri, Dan manzon Allah kayi hakuri, Nima wannan fili, siyarsa nayi, Kuma nadauki kudi nabawa wadda nasiya awajanta da shedu na dakomai, tasa hannu Nima nasa hannu, tabani takardun filaye Nima nadauki kudi nabata" Cikin tsananin mamaki yace"wacece ta siyar Maka?" Cikin tabbatar wa yace"Sunanta Munirat Abdul Salam,domin kuwa Alokacin ma ban sayi filayen ba saida ta tabbatar min cewa mijinta ne yabata su kyauta, saboda kasan harkar ciniki da mata" Wani irin duhu duhu Shahaab yafara Gani, duk bayanin da mutumin yake masa kwata kwata baya jinsa, tun lokacin daya ce masa munirat Abdul Salam, tundaga lokacin yanemi nutsuwarsa yarasa, cikin tashin hankali yace"Kanaji na? Zanbaka kudin filayenka, da kudin daka kashe na aiki, saika Bani takardun filayen" Cikin sauri Alhaji Umar yace"to yalla6ai babu damuwa godia nake" Daga Nan yakashe wayar. Wasu irin hawayene masu mutuqar zafi suka zubo daga idanun Shahaab, cikin ransa yace"munirat?" Da alama zancen lallashi ya rushe 🤣🏃🏻‍♀️🏃🏻‍♀️🏃🏻‍♀️ Shahaab littafin kudi ne, idan kika karanta baki biyaba nabarki keda mahaliccin ki,inde ubangiji yana sakayya na tabbatar zai Sakamin 300 0164549488 Amina muhammad GTbank Ko katin mtn Shedar biya ta wannan number 08033300034 Amnah El Yaqoub✍🏻 Page 37 Gaba daya saiya nemi 'yar sha'awar data addabeshi yarasa(😂) Kansa yariqe da hannunsa guda biyu yafad'a Kan gadon tareda furta"innalillahi wa inna ilaihirraji'un" Wani Hawayen ne suka sake zubo masa,yaji duniyar tayi masa zafi gaba daya, Dame yarage ta? Meta nema tarasa awajansa?meyasa zata masa haka? Har tasan tad'auki takardun filaye ta siyar, me zatayi da kudin? Meyasa mutumin daka daukakeshi fiyeda kowa yake cin amanarka daga baya?menene baiyiwa munirat ba? Haduwarsa da Aisha ne kad'ai yasan cewa yaraba soyaiyar dayake mata gida biyu yabawa Aisha d'aya,jin wayarsa tana ringing ne yasa yayi saurin goge Hawayen Idonsa, a fili ya furta, "dole zan dauki mataki akan munirat". Wayar dake shirin katsewa yayi saurin dauka, daga dayan bangaren mama tace"Shahaab kaduba kagano inda Aishan take?" Saida ya daidaita muryarsa yanda bazata gane yana cikin wani Hali ba, sannan yace"ban dubaba mama" Cikin sauri Tace"A a, Tome kake nufi?shikkenan daga shiga wajan matarka harka manta da batun yarinya?yarinya qarama tafice tabar gidanka kacemin zaka duba Amma kayi biris harka samu munirat ka manta da Aisha,?Anya kuwa Shahaab zan'iya nema Maka auren yarinyar Nan? Tun yanzu ma kana shiga wajan matarka ka manta da batunta, tayaya za'a yi maganar aure tsakani da Allah?" Duk da yana cikin halin damuwa saida ya danyi qaramar dariya yace"mama wanka zanyi saina duba nagani, karki damu mama, Aisha bazata 6ata acikin qasar nan nakasa dubo taba aduk inda take" Cikin sauri tace"to hanzarta kayi wankan" Wayar ya kashe, batareda tunanin komai ba ya lalubo number Hajja, wannan ne kiransa na farko wayar Hajja tun Bayan zuwan Aisha gidansa, kamar jira Hajja take, wayar tana shiga ta d'auka tareda sallama, cikin ladabi yace"Hajja barka da wannan lokaci" Hajja tace"yawwa barkanmu dai, dawa nake magana?" Murmushi yayi yace"Sunana Shahaab" Cikin sauri Hajja tace"kacewa? Shahaab koba Shahaab ba?" Cikin sauri Shima yace"eh haka nace, nine Shahaab, dama Ina neman Aisha ne" Hajja tayi ajiyar zuciya tace"wacce Aisha?saida ka salwantar min da jika zaka debo jiki kana tambaya ta Ina Aisha? Nan kazo har gida ka hure mata kunne yarinya tayi tsalle ta dire tace Nan duniya saikai, kasa mamuda yaturata aiki har yau bansan inda jikata take ba, wallahi Shahaab idan Namutu bansake saka jikata a'idona ba hakuma ce zata rabani dakai...." daganan saita Fashe da Kuka Runtse Idonsa yayi,cikin ransa yace"kuka!,kamar de Aishan" Cikin nutsuwa yace"kinga, kiyi hakuri, insha Allah zata dawo gida lafiya, kiyi hakuri Dan Allah" Cikin masifa Hajja tace"zaka rufemin baki ko saina wankeka da Mari? Kashe waya!" Cikin sauri yakashe wayar yana Girgiza Kansa, da alama rikitacciya ce kamar mama, ajiyar zuciya yasauke, hakan yana nufin bataje gidaba kenan, dole zai bincika yagani, cikin sauri yatashi yashiga wanka (idan kika karanta baki biyaba nabarki da mahaliccinki) ****** Bayan gwagwar mayar da Tasha, daqyar da d'an turancinta tasamu aka kaita inda zata shiga motar dazata kawo ta kano,suna cikin tafiya tana share hawaye daga idonta kad'an kad'an, waye yayi mata wannan sharrin? Abinda take tambayar kanta kenan, tun tana share hawaye harta Dena,tana addu'ah tana kallon garuruwa da dajujjukan dasuke wucewa har Allah yakawo su kano lafiya,yamma tayi sosai kasancewar hanyar akwai go slow, anan ma bata Sha wahala ba kawai napep ta tare tafada masa tana so yakaita inda zata hau motar dazata kaita dutse, yafada mata kudin, ta d'auka tabashi, sannan tashiga suka tafi, can ma tana zuwa tashar ake tambayar ta Ina zataje? Tafada musu dutse zataje, suka nuna mata wajan da ake lodin motocin dutse, taje tashiga, mutum biyu ne suka shiga Bayan shigar ta, aka kar6i kudin kowa, sannan driver yaja suka tafi, basu zo dutse ba Sai wajan karfe biyar da rabi, zuwa wannan lokacin duk ta gama galabaita, qafafunta sun dauki ciwo, ga yunwa, tunda tataho babu abinda tasaka acikin bakinta, ko tayi niyyar siyan wani abun idan ta tuna irin sharrin da aka mata saita ji duk duniyar ma tafita akanta, yanzu wannan vedio idan aka turawa wasu awaya shikkenan ita Kuma tagama watsuwa a duniya, lokaci daya, taji wani irin hawaye yasake zubo mata, cikin sauri tasaka hannu ta share, sannan ta nufi inda zata hau motar dazata kaita cikin garinsu, wato Garin CHAMO. ****** Bayan yagama wanka ya shirya, yad'auki computer sa, Adede lokacin munirat tashigo Dakin nasa, fuskarta babu walwala ta Wulla masa wayarta wadda ta kunna vedion da aka turo mata itada mama,wayar ya kalla yaga de irin vedion da mama ta nuna masa ne dazu, yasake kallon vedion ya kalleta, sannan ya Ta6e bakinsa yara6a ta gefenta yawuce, har yanzu idan ya tuna irin ta'asar data masa, wani irin qullutun baqin ciki yakeji a ransa, tabashi mamaki yanda baya zato, ko kadan bayason sake ganin ta, hakanne yasa daya futo zuwa falon su ma bai tsaya anan ba, Kai tsaye yafice zuwa compound din gidan cikin yar qaramar rumfarsu ta hutawa, wadda aka gama qwatata da tsari Mai kyau, ya zauna, sannan ya ajiye computer sa a gabansa yafara binciken location din da Aisha take, fuskar Nan tasa ahad'e, babu alamun farinciki ko walwala atare dashi, fatansa daya, Allah yasa bata cire agogon daga hannun taba, ko minti uku baiyi da zama awajan ba, Mai aiki tazo da sauri ta ajiye masa fruit da Kuma gorar ruwa tareda glass cup a gabansa ta juya cikin sauri. Munirat kuwa mamaki da taqaicinsa ne suka sake kamata, tunani take a ranta me Mahmud yataka dayake mata wannan abubuwan?tana tunanin ai ayau din ta cancanci yayi mata komai domin ya lallashe ta saboda wannan vedio din, Amma sai gashi yagani, Amma yawuce yarabu da'ita, harda cewa zaizo ya lallashe ta ashe duk qarya ce Da yaudara, dama tariga tasan muddin yafara shiga wajan waccan tsohuwar, to Sai abinda ta kitsa masa, dama can ai itace tabashi lasisin iskanci da yarinyar, tunda itada kanta ta kama yarinyar ta riqe masa, yake ta6a mata nono, to yanzu kuwa dan ya aikata Zina da'ita ai ba zatayi masa fada ba, lokaci daya tasake jin tsanar mama acikin zuciyar ta, Fata take Dama ace ta mutu, kowama ya huta, tunanin da munirat ta dinga yi kenan Bayan fitar Shahaab daga cikin dakinsa. Acan compound kuwa Shahaab baima kalli abinda aka gabatar masa ba, nutsuwa yayi yakafa Idonsa a computer yana aikin bincike, wata irin ajiyar zuciya yasauke Mai karfi, cikin tsananin farinciki ya furta"Alhamdulillah"sannan ne yad'auki inab guda daya yafara Sha ahankali, saida yasha fruit din sosai, sannan yatashi yanufi part din mama. ****** Lokacin datazo Garin duk mutane sun shiga sallar magrib, kasancewar Adede lokacin ta sauka, Garin take kallo kamar wanda tayi shekara bata cikin sa, wani irin farinciki ne ya kamata, jitake kamar tayi ihu, har gudu-gudu take hadawa dashi domin tayi sauri ta qarasa gida, tana shiga gidan kuwa ta kwasa a guje, Adede lokacin Hajja tana Zaman tahiya a sallarta, Ummah Kuma ta idar da alwala kenan ta miqe zata shige daki, cikin wani irin ihun murna ta daka tsalle ta d'ane umman ta, cikin jin dadi tace"Ummah...." Cikin sauri Ummah ta juyo tana kallon ta baki bude, mamaki ya hanata yin magana, dariya tayi ta ce"ummah nadawo" Hajja datayi sallama cikin tsananin mamaki tace"me sunan qawa?" Cikin sauri tasaki Ummah tafada jikin Hajja tace"Hajja nah" Sai a lokacin Ummah tayi magana tace"Wai kece Anya kuwa kokwade mafarkin Dana saba ne?" Cikin sauri tace"Ummah nice mana, Zona mintsine ki kiji" taqarasa maganar cikin sigar tsokana. Ummah tayi dariya ta Girgiza Kanta,tad'auki hijab tatada kabbarar sallah. Hajja kuwa hannu ta daga sama ta kalli gabas tace"Alhamdulillah....Allah nagode Maka daka dawomin da jikata gida lafiya,su jummai Yan baqin ciki saide su mutu"(🤭😂) ****** Cikin farinciki mama tace"ikon Allah, ashe tana Jigawan, ninama Rasa Yaya akai kayi dabarar saka mata agogo me d'aukeda na'ura Shahaab,kodan kasaba yin dabara kana kama 6arayin gwamnati shiyasa yanzu ma kayi dabara kakamo 6arauniyar zuciyar ka?" Cikin sauri ya sunkuyar da Kansa qasa saboda wata irin kunya data kamashi, saida yadan Sosa kansa, sannan ya kalleta yaga ita zuciyarta daya tayi maganar ko ajikinta, ahankali yace"a a mama, ainasan batada waya a hannun ta, nasaka na'urar a jikin agogon ne saboda idan inason ganin ta, zan duba Inga halin datake ciki, banyi hakan da wata manufa ba, Amma Kuma gashi cikin ikon Allah hakan yayi amfani, Bari inkira kakarta inji Yaya ta sauka, dafatan ta'isa lafiya, dazu nakira ta tanata fada, mama bakiji yanda ta rufeni da fada ba, halin ta sak irin na mamanah"(😂) Cikin dariya mama takai masa duka tace"d'an mutum wasa ne Shahaab? Ai tanada gaskiya, karabu da'ita karka kirata, kabari gobe mushirya mubi jirgi, Sai muje a basu haquri, daga Nan Kuma Sai ayi maganar aurenku, kaga hakan zaifi, suma zasuji dadi Susan cewa sun turo yarsu gidan karamci" Cikin jin dadi yace"to mama Allah yakaimu, saimu tafi sassafe ko?" Mama ta kallashi,Shima kallon ta yayi, Sai a lokacin yaga kallon Fassara take masa, cikin sauri yatashi yabar falon Nata cikeda kunya, Sai aikin shafa lallausar sumar Kansa yake. Mama data bishi da kallo tana ganin fitarsa tasaki murmushi, ta daga hannunta sama tana yiwa Allah godia daya karkato mata hankalin danta yake son aure yanzu, tana fatan ace anayin wannan aure Aisha tasamu ciki ko Allah zaisa itama taga jikokin ta kafin tarasu. ****** Gaba dayansu su ukun atsakiya suka saka Aisha sunajin yanda take basu labari, Abba ya kalleta yace"amma qawar Hajja banda Shirman ki Dan kun samu Sa6ani da uwar Dakin naki saiki niqo irin wannan hanyar kitaho ke kadai? Bakya tsoron asaceki a hanya?" Ummah tace"hanya Kam babu kyau, yanda ake diban mutane kamar wasu dabbobi,qasar nan anmaida rai ba'a bakin komai ba" Murmushi tayi tace"wallahi Ummah Ina mata komai,Bana mata rashin kunya saboda tsohuwa ce, yanda kikaga Hajja itama haka take, Amma idan ta rikice saiki Rasa gane kanta, shiyasa Nima nataho gida, dama nagaji,ga sauran kudina ma kuyi amfani dashi Ummah" Ta qarasa maganar tana bude handbag dinta, duk sauran kudin dake ciki ta fitar dashi ta basu, Hajja ta kalli kudin tace"me sunan qawa wannan kudin ai yayi yawa,duk na menene haka? Ko kudin aikin naki ne?" Kanta ta Girgiza Tace"A a Hajja,me gidan ne yabani kudin da Kansa, ban roqeshi ba" Abba ya Jinjina Kansa, Hajja tace"yawwa nikin tuna min ma, dazu wannan saurayin naki ya kirani, Wai sunansa Shahaab, ke yake nema in baki waya idan kina kusa, na qare masa tatas nace idan yasake kirana sainaci masa mutunci, shida yayi silar barinki gida?" Murmushi tayi tace" Hajja Aida baki masa haka ba" Kafin Hajja tayi magana Abba yace"har yanzu de baki rabu dashi ba kenan, bamu Isa mu fada miki magana ki saurari maganar mu ba, ai shikkenan Allah yabada sa'a" Jikin Ummah yayi Sanyi jin furucin Abba, ta kalli Aisha taga yarinyar tanata Fara'ah, Sai can Aishan ta d'ago kanta ta kalli Abba Tace"Abba Bahaka bane, Amma kayi haquri, duk bayanin dazan Maka ba lalle ka ganeba" Daga Nan bata sake cewa komai ba tafada duniyar tunani batason taga yanda Abban ta zaiji kunya, Amma data fada masa cewa Shahaab din de dayake qi shine Mahmud Wakili, Shahaab din dayake qi gidansa yasake tura ta aiki, tasan Hajja zata masa wankin Babban Bargo, ahankali tasake cewa "Abba jabir bai fada muku Mahmud Wakili ne ya turashi qasar waje karatu ba? Bai fada Maka shine yatura ka umara ba?" Cikin tsananin mamaki Abba yace"mahmud Wakili Kuma?" Hajja tace"jabir bai fada mana koma ba, Amma menene dalilin yimana wannan abun? Keda kike gidansa bai fada miki saboda me yayi mana haka ba?" Murmushi tayi ta Girgiza, sannan tace" tunda nafada muku yanzu saiku shirya kuje kuyi masa godia, saiya fada muku da dalilin da Kansa" Hajja tace"tokode daga zuwa yaganki ya qyasa? Fadamin gaskiya" Hararar Hajja tayi, tatashi tashige Dakin Hajjan tafara shirin wanka, Hajja tatashi tabiyo bayanta taga harta daura zani da alama wanka zata shiga, kallon ta tayi tace"mesunan qawa Habujan Nan ta kar6eki, jikinki yayi wani mulmul kamar matar kansila, kode kaji kikeci ne kullum?" Cikin dariya tace"kullum sunake ci, abinci Kala Kala Hajja Sai Wanda naza6a, nama kuwa kamar abun banza" Hajja tace"ikon Allah, kice naman kaji yana Nan kayan qarfi..." Aisha tayi dariya tace" karfin ne kawai bakida shi Hajja da kinje kema kinci" Murmushi Hajja tayi ta qaraso Dakin, ita Kuma ta juya tashige wanka. ****** Yau yariga mama futowa falo,tun sassafe yafuto su kansu ma'aikatan sunyi mamakin ganinsa afalo, yad'ora kafa daya Kan daya yana kallo, yayi mutuqar kyau cikin suit, Sai qamshi yake zubawa, Sai wajan karfe takwas mama tafuto, ta shirya cikin less Mai ruwan golden, hannunta da wuyan ta sunsha sarqa da zoben gold, kana ganin ta kasan daula ta zauna, cikin mamaki ta kalleshi Tace"A a, yana ganka anan Kai kadai?" Cikin sauri ya sunkuyar da Kansa qasa, yadan shafa sumar Kansa yace"mama ai nagama shirya wane" Murmushi tasaki, ta nemi waje ta zauna tace"tokoma kacire wannan kayan kasako manyan Kaya, haba Mahmud, wajan surukanka zakaje fa ba wajan Aisha ba" Kansa yadan shafa, sannan yatashi yakoma part dinsu, itama dinning ta nufa tafara cin abinci,don bazata iya wannan azalzalar ta Shahaab ba, Dan idan tabiye masa taga alama abincin ma bazasuci ba. Tare suka dawo shida Munirat, shadda yasaka fara tareda babbar riga, kayan sunyi Masa kyau sosai fiyeda qananun kayan, Wanda bai saniba tsaf zaiyi tunanin wani sabon angon ne, agogon hannunsa ya daura sannan yaja kujera ya zauna, munirat ma ta zauna tareda gaida mama, cikin kulawa mama tace "Barka munirat" Abincin suke ci Hankali kwance, mama data gama tana shirin tashi ta kalleshi tace"jirgin karfe nawa zamubi?" Cikin sauri ya Kalle ta, saida ya ajiye spoon din dayake shan tea sannan yace mata"jirgi bazai tashi ba yau, saboda yanayin hazo, saide mutafi a mota" Kanta ta Jinjina tace"to ai saimu wuce ko?" Tissue yadauka ya goge bakinsa, dama kawai yana tura abincin ne, Amma ya matsu sutafi, cikin sauri yace"toshikkenan muje" Munirat tayi mamakin sa, tafiya zaiyi Amma ko fada mata baiyi ba, batasan meyasa tsakanin jiya zuwa yau, yake share taba, har zata tambayesu Ina zasuje, Sai taga mama ta kalleta tace"to Munirat zamuje jigawa, kinsan yanayin tafiya bamusan Yaya zata Kaya ba, saboda haka kimana addu'ah,idan daga Nan Kuma kinji anyi masa mata acan saiki shirya kar6ar abokiyar zama" Cikin sauri Shahaab ya kalli mama, baiso ta fadawa munirat zancen auren ba, yasan tanada kishi dole zata daga hankalin ta, shiyasa yaso saiya dawo saiya sanar da'ita ta cikin ruwan Sanyi. Dam! dam!! dam!!! Gaban munirat yayi wata irin faduwa, hannunta datake cin wainar qwai yad'auki karkarwa har batasan lokacin da fork din yafadi daga hannun taba,ta zubawa mama ido tana kallon ta, mama dataga yanayin munirat ya sauya tace"ikon Allah, menene abun rawar jiki daga maganar kishiya munirat? Dama yamiki alqawari zai zauna dake kadai ne? Banda abinki munirat yanda Shahaab yakeda kyau irin wannan ai kema kinsan dole yanmata zasu so shi,ballantana ma wannan yarinyar kin Riga kinsanta, Aisha ce, idan ya auro tama itade ba baquwa bace awajanki, dama gida daya kuke zaune shikkenan saiku dora daga inda kuka tsaya, may be Rabon muga qananun Yara agidan ne shiyasa Allah yakawo maganar auren, kema ai zakiso ganin yaran Shahaab suna kuka, suna fada, suna Rikici akan sweet..." Jikin Shahaab yayi Sanyi, yasaki ajiyar zuciya, yaga alama idan bai katse maganar ta mama ba, Tofa bazata dainaba,Wai ahakan ma Dan batasan da case din filayenta da munirat din ta dauke taje ta siyar ba, dama suna yar tsama to idan tasan da batun filayen Allah ne kadai yasan inda rigimar tasu zata qare, ahankali yace"muje mama" Yajuya ya kalli munirat, fuskarsa babu yabo babu fallasa yace"saimun dawo" Munirat dai batasan cewa Shahaab yayi mata magana ba, tadaisan yayi magana Amma kwata kwata bata cikin nutsuwar dazata gane meyake fada, wani irin tashin Hankali ne ya wanzu a Saman fuskarta, baqin ciki ya tokare mata maqoshi, suna fita takifa kanta akan dinning table tasaki wani irin kuka maicin rai, dama ashe Aisha baquwar mama zai aura? Kenan ita ya mallakawa company? Ita Mahmud zaiyi wa haka? Dama tasan hakan zai iya faruwa, tunda har uwarsa ta riqe masa yarinyar ya matsa yaji ba'irin na matarsa bane ai dole ya rikice yabibiyi yarinyar. (🙈) Kuka take me mutuqar cin rai, kwata kwata tunanin ta ya tsaya cak, tarasa Ina zata samu mafita, Amma abinda takeji acikin ranta Gani take dazata samu wuqa Toda tsaf zata Iya da6awa wannan tsohuwar(🙆🏻‍♀️) Mota biyu sukayi, daya suna ciki ita dashi a zaune abaya, Sai driver dayake jansu, dayar Kuma securities ne aciki saboda tsaro. Suna hanya yake turawa Ramadan text cewa suntafi jigawa shida mama, Sai tsiya Ramadan yake masa shikuma yana murmushi. (nabarki da Allah keda kika karanta batareda kin biyaba) ****** Aisha ta kalli Hajja tace"Hajja meyake damunki ne Naga kinyi shiru, ko bakya jin dadi?" Ajiyar zuciya tayi tace"inafa jin dadi mesunan qawa, gaba daya yau Jina nake jikina Sanyi kalau, tun asuba gabana yake faduwa, bansani ba ko mutuwa zanyi" Cikin tashin hankali Ummah tace"Hajja Dan Allah Kidena wannan maganar, idan bakida lafiya tashi muje nakai ki chemist din Mubarak dogo" Cikin sauri Aisha ta kalli Hajja tace" Ko wani abu kike so kici saina siyo miki?" Ganin yanda duk suka daga hankalin su yasa tad'an kwantar da Hankalinta tace"lafiya ta kalau wallahi, kawai gaba nane yake faduwa" Ummah tace"to kidinga addu'ah Hajja, insha Allah Sai alkhairi" Kallan Aisha Hajjan tayi tace"mesunan qawa, dauki kudi aqasan fillo na kije bakin kasuwa ki siyo mana kaji, da nasan da zuwanki jiya Aida tun safe zanje insiyo miki, Amma tunda bansani ba kije yanzu ki siyo mana" Cikin sauri Ummah tace"Hajja aiga kudin datazo dashi jiya, kusan dubu talatin dawani abu, ta d'auka aciki taje tasiyo" Hajja tace"to jeki dauka ki siyo, kudin bironki da'aka siyar ma mamuda fili yasiya miki dashi,Sai Dan gyare-gyare da'aka yi mana a gidan, yace idan aurenki da inusa yatashi Sai asiyar ayi hidimar biki dashi " Dan qaramin bakinta ta turo gaba ta juya tana Hararar Hajja, cikin lallashi Hajja tace"to uwar masifa, tashi kije Dan Allah, kibiya gidan qawar ki Walida saita rakaki, tunda batasan kinzo Garin ba, kisiyo harda kayan miya, da kaji guda uku, yau Walima zamuyi, jikata tadawo gida" Cikin murmushi Ummah ta Kalle su, cikin ranta kuwa dadi takeji yanda Hajjan tasaki ranta tadena maganar mutuwa. ****** Sunci tafiya sosai a hanya, Sai yamma suka shigo jigawa, suna kokarin shiga garinsu Aisha mama ta hangi wani Tsoho yana tafiya akan Keke, itace ya'iyo abayan gari, daqyar yake tuqa keken da alama yajigata dayawa,cikin sauri tace"driver tsaya" Shahaab ya kalleta da mamaki, glass din ta sauke qasa ta kalli wannan tsohon tace"bawan Allah cikin Garin zaka qarasa ne?" Cikin sauri ya tsaya ya kalleta yace"hakane Hajiya,ciki zan shiga" Tace"toshigo mota saimu qarasa dakai" Tsohon ya kalli motar yaga mota Sai sheqi takeyi tana daukar ido, yaji tsoro karyaje Yan yankan kaine, cikin tsoro yace"a a Hajiya, nagode, Aina qaraso ma, nagode sosai" Murmushi tayi, ta bude Jakarta tad'auki kudi Yan dubu dubu tabashi tace"to ungo wannan kasai itacen dayawa kadena zuwa da kanka" Jiki na rawa tsohon ya kar6i kudin hannunsa Sai rawa suke, cikin jin dadi tace"nagode Hajiya, Allah yasaka da alkhairi, Allah yahadamu a aljanna mafificiya, ubangiji yabiya miki buqatunki na alkhairi, Allah Yacika miki burinki" Cikin jin dadi mama tace"Amin ya Allah, kasan ni wacece?" Tsohon yace"a a Hajiya saikin fada" Tace"amma ai kasan Mahmud Wakili ko?" Cikin sauri yace"ranki ya dade duk qasar nan waye zaice baisan Mahmud Wakili ba? Ko baka sanshi a'ido ba ai zaka sanshi a suna" Murmushi tasake yi tace"toni mahaifiyarsa ce, sunana Aysha Yakubu Sagagi, qawar Aysha Sulaiman Bompai" Cikin sauri tsohon ya tsugunna yana zuba mata addu'ah, mama tarufe glass din motar suka cigaba da tafiya, Shahaab ya kalleta yayi murmushi tareda Sosa girarsa guda daya, mama kuwa tunanin qawarta Aysha Sulaiman ne yafado mata, rayuwa kenan, yaude gata acikin jigawa Amma batada Hali ko hanyar dazata hadu da qawarta, lokaci daya jikinta yayi Sanyi, tana wannan tunanin batasan har sun qaraso kofar gidan su Aisha ba, Shahaab ya kalleta sannan yace "mama ga gidan Nan munzo" Kallonsa tayi tace"mekake nufi? Futowa zakayi muje tare dakai kabawa iyayen ta haquri akan abubuwan dasuka faru abaya, Nima nabawa Aisha haquri akan abinda yafaru" Cikin kunya Shahaab yafuto daga cikin motar, securities sukazo da sauri suna gyara masa babbar rigar jikinsa, aka budewa mama kofa itama tafuto, manyan motocin dasuka tsaya a qofar gidanne suka dauki hankalin Yan qauyen, Wanda suka sanshi Nan da Nan suka fara qus-qus suna nuna shi da hannu anaso a tabbatar Mahmud wakilin daya ta6a aiko musu kayan abinci ne, kokuma wani ne daban? Wani yaro ne dayazo wucewa mama ta tare tace"shiga Nan gidan kace Ana sallama Dame gidan" Yaron yajuya yashiga gidan, Sai gashi sun futo daga gidan shida Abba. Abba yana ganin Shahaab sai mamaki ya wanzu a fuskarsa, cikin mamakin yace"sannunku da zuwa, kamar yalla6ai Mahmud nake Gani ko?" Shahaab yayi murmushi tareda sunkuyar da Kansa qasa cikin kunya irinta surukai, cikin ransa yana mamakin mahaifin na Aisha ashe ma yaro ne kamar shi,Mama tayi murmushi ganin yanda Shahaab yake sunkuyar dakai tace"kaine mahaifin Aisha?" Cikin sauri Abba yace"Eh nine Hajiya, sannunku da hanya, nace Allah yasa de ba wani laifin tayi muku tataho gida ba?, mu munata qoqarin zuwa har gida muyi godia akan abun alkhairin da yalla6ai yayi mana Kuma saina ganku kunzo?" Mama tayi murmushi Tace"A a Aisha batayi laifin komai ba, mune ma mukai laifi mukazo bada haquri, Yaya sunan Kane?" Cikin murmushi Abba yace"sunana Mamuda Hajiya" Cikin farinciki mama tace"Mahmud de ko?" Tanuna masa Shahaab da Kansa yake qasa tace"shima wannan danane, kamar yanda kasani Mahmud Wakili sunansa, Amma Ina kiransa da SHAHAAB..." gaban Abba ya yanke yafadi, cikin sauri ya kalli Shahaab, cikin daburcewa Shahaab ya russina tareda Bawa Abba hannu yace"Barka da yammah" Kan Abba gaba daya saiya kulle, dama Shahaab shine Mahmud Wakili? Wannan shi ake kira an yanka tatashi....,kenan shine yake zuwa wajan Aisha? Kuma shine yasake tura Aisha gidansa aiki? Shine yakaishi Umarah, yakai jabir qasar waje karatu?cikin son sake tabbatar wa Yace"Shahaab-shahaab de Danakeji awajan Aisha?" Shahaab yayi shiru ganin lokaci daya surukin nasa ya d'agoshi, Dan haka yayi saurin yin qasa da Kansa yana 'Dan Sosa qeyarsa. Mama tayi murmushi tace"shide,idan babu damuwa ka bamu wajan zama Dan maganganu muke tafe dasu dayawa" Cikin sauri jikin Abba yad'auki rawa, Wai yau Mahmud Wakili ne da Kansa a kofar gidansa, Mahmud Wakili ne yake zuwa wajan 'yarsa,cikeda mamaki yace"a a, to hajiya ku qaraso ciki mana, ku shigo daga ciki kawai..." Mama Tace"toshikkenan Takwaran Mahmud mushiga" Abba yajuya cikin gidan da sauri, mama da Shahaab suka doru abayansa. Hajja tana sunkuye tana gyara hadaddan kunun ayar data zuba acikin fridge, Aisha tana zaune da abinci agabanta tanaci kamar bataso, Ummah tana Gefe da pure water ahannunta tanasha,saiji sukai Abba yana cewa "kushigo Hajiya, ku qaraso, sannunku da zuwa" Shahaab yana daga Kansa Idonsa ya sauka akan Aisha, tana hada ido dashi gabanta yayanke yafadi, ta tsaya cak tadena cin abincin, yayinda gaban mama ya yanke yafadi ganin fuskar da bazata ta6a mantawa da'itaba a tarihin rayuwar ta,lokaci daya handbag din data riqe a hannun ta tafadi qasa, qaran faduwar jakar ne yasa Hajja tarufe fridge din ta d'ago kanta, gabanta ne yafadi, hannunta yana karkarwa tafara nuna mama,cikin rawar murya tace"Aysha Yakubu?" Jin sunan data kirane yasa gaba d'ayansu suka maida kallon su ga Hajiya Mama. Masha Allah, mutara zuwa gobe🙏 Littafin kudi ne, nera 300 kibiya ki karanta kada ki karanta abun Allah ya'isa 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN Shedar biya ta wannan number 08033300034 Mutara zuwa gobe🙏🏻 Mrs Usman ce✍🏻 Page 24 Wani Irin hawaye ne yazubo daga idon mama,cikin rawar murya tace"Aysha Sulaiman? Aysha kenake Gani haka kokuma idonane?Dan Allah kifadamin kode irin mafarkan danake yi ne?" ta qarasa maganar hawaye na gudu daga idanuwanta. Ahankali Hajja tatako tazo gaban mama, tace"nice Aysha" Cikin sauri mama ta rungume ta,kuka Hajja tasaki mecin rai, mama kuka, Hajja kuka, cikin kukan Hajja tace"Aysha, ashe da Rabon zan sake ganinki a doron duniya?" Cikin sauri tasaki mama ta daga hannunta sama tace"ya Allah nagode Maka, Allah Ina qara yima Godiya bisa nunamin qawata dakayi wadda na Dade Ina nema tsawon shekaru masu yawa" Hajiya Mama ma Hawayen ta share, itama ta daga hannunta kamar de yanda Hajja tayi tace"ubangiji na gode Maka, yau Naga Aysha Sulaiman bompai,Babban burinmu guda daya Yacika, saura Kuma d'ayan, Allah nagode maka" Cikin sauri Ummah ta goge qwallar idonta, itade batasan wannan baqi ba, Amma duk da babu bayani tariga tasan cewa wannan matar itace qawar Hajja, yaude ga qawar Hajja tazo har gida, ikon Allah kenan, kullum labari-labari yau gashi Allah yahadasu. Aisha kuwa gabanta ne yafadi, duk wannan dramar dasuke idonta yana kan mama, Tun lokacin da Hajja tace Aysha Yakubu, daga Nan wani irin shock yakamata, yanzu dama Hajiya Mama itace qawar Hajja?. Shikuwa Shahaab wata irin wawuyar ajiyar zuciya yasauke Mai karfi,domin kuwa abinda ya lura dashi shine Abban Aisha bashida qanwa mace bare Mama tace dole saiya aure ta Yacika mata burinta, dama abinda yake gudu kenan, mama tadage muddin taga Aysha Sulaiman Tofa Sai sun hada yayansu aure, Kuma Alhamdulillah shi bai taba jin Aisha tace abban ta yanada qanwa ba bare abashi, Gara de ita Aishan, ahakan ma tunda gashinan Allah ya hadashi da Aishan cikin hikimar sa ai shikkenan Shima de dan'uwan burin maman ne, tunda jikar qawarta ce. Abba kuwa ajiyar zuciya yasaki ahankali, cikin sauri ya goge qwallar Idonsa,sannan yayi gyaran murya yace"Alhamdulillah....,Hajja kuyi hakuri kudena kukan Nan haka, ku qaraso ku zauna" Yajuya ya kalli Aisha da abincinta ke gabanta ta gagara ci, cikin fada yace"ke tashi ki Dauko babbar tabarmar Nan ki shimfida mana, kinfi awa daya kina cin wannan abincin, ga baqi sunzo ko abun zama baki shimfida musu ba" Cikin sauri Shahaab yayi qasa da Kansa tareda Sosa qeyarsa Ummah ta kalli Aisha Tace"Ai inta fara dora abinci a harshe saikace basarakiya, na hanata irin wannan cin abincin taqi ji " Cikin sauri tatashi ta wuce Dakin Ummah tad'auko babbar tabarmar ta shimfida musu. Ummah ta kalli su Hajja tace"ku qaraso ku zauna" Tajuya ta kalli Shahaab da batasan waye shi dinba, ita de taga Sai sunkuyar dakai yake yaqi kallon idon kowa, tace"bawan Allah qaraso mana" Cikin sauri Shima Abba yace"bissmillah yalla6ai" Yanda yace yalla6ai dinnan Sai abun yayiwa Shahaab nauyi, ahankali yace"to nagode" Suka qaraso suka zazzauna a tabarma,Aisha tana daga Gefe, duk jinta take a takure, saboda yanda Shahaab yazuba mata mayun Idonsa, ko tsoron su Ummah su kamashi yana kallon ta ba yayi, duk motsin datayi akan Idonsa. Hajja ta kalli mama, sannan ta nuna Aisha da hannu tace"kinganta Nan,? Babu abinda tabari naki,masifa,rashin kunya, yanga saikace yar wani, wannan cin abinci dakike a makaranta haka itama takeyinsa kamar kin zauna da'ita kin Koya mata yanda kike yi, lokacin da aka haife ta uban yadage sunana zai saka, nikuma nace a a, munyi alkawarin zamu sakawa Yayanmu Aisha, idan Kuma maza muka haifawa to zamu saka musu suna Mahmud, to Alhamdulillah, Dana guda daya ne a duniya gashinan mamuda, ban haifi mace ba bare nasaka mata sunanki, shiyasa Ana haifar ta daya ce sunana zaisaka nadage nace a a, saide yasaka sunanki, to daqyar de mamuda ya yarda, saboda kallon ta6a66iya sukemim Alokacin, tayaya qawar daban masan inda take ba, bansan a'ina zan ganta ba, zan dage ince sunanta zan saka? To dayake de sunan naki duk irin nawa ne, shine yasa mamuda yasaka mata sunanki,idan masifar ta tatashi fada mukeyi akan wannan suna Nata, fada takeyi tana min sababi kawai natashi nasa mata sunan qawata qilama ta mutu, ban'isa ince tanada masifa ba saitacemin ai nice nace asaka mata sunan qawata, danhaka halin qawata ta Dauko..." Cikin sauri Aisha ta sunkuyar da idonta qasa, wannan tonon silili na Hajja har Ina? Da alama batasan waye wannan yake tareda mama ba, da tasan shine Shahaab dabata mata wannan tonon asirin ba. Ahankali kuwa ya kalli Hajja yace"nima haka tamin Hajja, ranar Dana kawo muku abinci da Azumi rashin kunya ta dinga zubamin, saura kadan ma ta dungure min kai na...."yaqarasa maganar cikin sigar tsokana. Aisha ta d'ago ta daka masa harara da fareren idonta tareda murguda masa d'an qaramin bakinta,yana ganin abinda tamasa yafaki idonsu Hajja ya motsa fatar bakinsa yasakar mata kiss ahankali,karaf akan idon Abba (🤭🙆🏻‍♀️🙈) Aisha kuwa tana ganin abinda yayi tayi sauri ta sunkuyar da idonta, Abba kuwa cikin sauri ya kawar da Idonsa yayi murmushi cikin ransa yace"dole yarinya tadinga bijiremin tadage lalle Sai Kai" Ummah da mamaki yagama kamata ta kalli Shahaab tace"wanne irin abinci kake magana bawan Allah?" Abba ya kalli Ummah da Hajja yace"wannan fa Mahmud Wakili ne, Wanda yaturo da Azumi akayi Rabon abinci agarin Nan?" Hajja ta kalli mama tanuna Shahaab tace"wannan shine Mahmud dinki?" Cikin sauri mama ta daga Kai tace"shine Aysha, shi kadai nahaifa, inde kinji Ana cewa Mahmud Wakili to Mahmud dinane, ashe de alqawarin mu nasaka sunaye ya tabbata, Rabon abinci Kuma babu Wanda yaturo, shida Kansa yazo, a lokacin nariga na fidda rai da ganin Aysha Sulaiman, sainayi masa magana akan yazo jihar Jigawa yagina gidan marayu, ko Allah zaisa watan watarana Yaya, kokuma jikokin Aysha zasu kasance a gidan, ta wannan hanyar ne zan iya taimakonta saboda bansan inda zan ganta ba, Nasaka anyi cigiyar duk a banza,Bayan yazo sunyi maganar aikin shida Gwamnatin Jihar, saiya raba kayan abinci, to kunji dalilin zuwansa Nan Garin, dama shine Wanda nake dashi Wanda zai tsayamin akan nemanki, toshi tunda yaji nace masa muddin naganki Sai na aura masa yarki, Tofa shikkenan yayi biris da maganar neman naki, saboda bayason nabashi wadda bayaso, yad'auki son duniya yad'ora wa matarsa, shi Dan boko, ba zaiyi wa matarsa kishiya ba, Amma dayake Allah yaso kamashi, saiya saka masa son Aisha, soyaiya ta kamashi dumu-dumu, Idonsa yarufe,ya manta da batun Qin qarin aure,Sai gashi da Kansa yazo min da maganar inzo in nema masa auren Aisha, inkikaga yanda yake son Aisha saikiyi mamaki, harfa company yabata, Alokacin da akayi kyautar na tambayi abokinsa wacece Aisha? Nasan tare suke qulla komai, Amma Shima saiya 6oyemin, akace mama ai jinake dake yake, waini za'a yiwa wayo, Amma da aka 6oyemin din Sai gashi de anzo wajena inzo neman aure, to Dama mun samu Sa6ani da takwarar tawa, sainace zanzo inbata haquri, ashe ni Allah ne yayi zan hadu dake...." Tajuya ta kalli Shahaab tace"idan baka auri yar qawata ba ai gashinan zaka auri jikar qawata" Cikin sauri Hajja tace"kamfani fa kikace Aysha?shiyasa da yarinyar Nan tadawo tazo da kudi ajakarta tace mana Wai me gidan ne yabata naji tsoro, saboda kar ace daga zuwa aiki yarinya ta qwacewa matar gida Miji, saide Kuma bakisan wani abu ba, ai ita takwarar Taki akwai Wanda takeso, tad'auki son duniya ta dorawa wannan jarababban yaro(😳) Uban Nata har dukanta yayi akansa, saboda Dafarko akwai Wanda mukeso mubata inusa, yarinyar Nan tunda tahadu da wannan saurayi ta bijire tace lalle saishi, ita batason inusa, to yanzu ma idan muka bata Mahmud din naki muna Nan dake wannan Yaron zai dawo yaqara hure mata kunne, qarshe tazo tace bazata auri Mahmud dinba, Amma wata kusan ai tafi wata, shi wancen saurayin biro yabata shikkenan ta rikice akansa, Amma ga Wanda yabaka kyautar kamfani banda rashin Hankali me akai-akai wani biro? Aini idona idon Shahaab, hakuma ce zata rabani dashi, Kuma infada miki yaqi futowa fa? Shirme ne kawai irinna takwarar ki" Cikin sauri Abba da yasan komai yayi qasa da Kansa, Aisha kuwa murmushi tayi Shikuwa Shahaab yana jin haka yayi qasa da Kansa, yaude yakawo Kansa wajan Hajja Sai ta Allah Kuma. Mama tayi dariya ta kalli Hajja tace"to yanzu ai gashinan yafuto, Mahmud din nawa Aishine Shahaab din" Cikin sauri Hajja ta zaro idonta(😳) tace"Shahaab?" Cikin sauri yayi qasa da Kansa yafara Sosa qeyarsa, Ummah kuwa dariya ce ta kamata, Sai yanzu ne ta gane dalilin dayasa tun dazu yake sunkuyar dakai, ashe suruki ne dakansa. Mama tayi dariya tace"to yanzu mun futo Aysha, Sai abamu auren Aisha" Hajja tayi dariya tace"narasa ma mezance wallahi" Tajuya ta d'akawa Aisha duka abaya har saida tad'an yi qara, sannan tace"dan gidanku kinaji inata zuba ko zunguri na bakyayi ba?" Ummah tayi dariya tace"Hajja Ai zancen yaqare" Mama ta kalli Shahaab da Kansa ke qasa tace"narasa gane wannan kunya daka aro ka yafa wa kanka Shahaab, agida fa sassafe kazo min falo ka zauna kanaso muyi muzo gidansu Aisha, yanzu Kuma gamu a gidan Amma kakasa kallon Aishan ma, to ai shikkenan ga abokinka Nan, saika bashi haquri ka nemi auren awajansa, yau aboki yazo wajan abokinsa neman auren yarsa" Dariya sukai gaba dayansu, Abba yace"nikam babu komai wallahi, dama komai an ai katashi ne cikin rashin Sani, Amma komai ai yawuce, Allah ya nuna mana lokacin ya basu Zaman lafiya" Ummah tace"Amin-Amin, aimune da godia Hajiya, Allah yasaka da alkhairi anata dawainiya damu, bagamu ba, baga yaran muba, Allah yasaka da alkhairi" Mama tace"duk abinda Shahaab yamuku ai Kansa yayi wa, idan zai dauki duniya yabawa jinin Aysha Sulaiman, wallahi banida damuwa, yayiwa wasu ma bare Kuma Aysha? Aysha ai mahaifiyar sa ce, yanda nake da iko akansa itama haka take dashi" Tajuya ta kalli Aisha tace"takwara ta matso kusa Dani mana,Allah sarki kullum saita dinga Cewa a kakarta ta daukeni, ganina take kamar Hajja kakarta, ashe kuwa yarinya da gaske take nidin kakarta ce" Murmushi sukayi, Aisha ta taso ta zauna agefen mama kanta sunkuye aqasa, Hajja tace"Aisha kenan, sarkin tsiwa, waini Kam Aysha Mahmud dinki yaransa nawa yanzu? Ni nawa Mahmud din Aisha ce ta farko, saikuma jabir yana qasashen waje Mahmud dinki ya turashi karatu, sukenan su biyu" Jikin mama ne yayi Sanyi, ahankali tace"wadannan jikokin naki su zan kalla Nima ince ga jikokina, saboda har yanzu Allah bai Bawa Shahaab haihuwa ba, shiyasa na damu akan yaqara aure, saboda likitoci sun tabbatar lafiyarsa kalau, shikuma yaqi yayi auren ko Allah zaisa Shima muga yayansa, to yanzu de Ina fatan idan akayi auren da Aishan, ko Allah zaisa ita tasamu cikin" Hajja tace"ciki kuwa,insha Allah anayin auren zata samu,auren yanzu da anakai yarinya zakiga tasamu ciki kamar Dama abakin qofa tayi tuntu6e dashi?yo Allah natuba jikar qawata jummai fa watanta Tara cif-cif ta haihu, idan kikai lissafi zakiga inajin a ranar damuka Kai yarinyar a ranar tasamu ciki, shegiyar jaraba duk ta cika mazan, dama akan ga6a suke, shiyasa anakai musu yarinyar suke haike mata...."(🙈🤭) Ummah najin haka tatashi Dasauri tace"bari azuba muku ruwan alwala naji Ana Kiran sallar magrib" Shahaab kuwa kunya ce ta kamashi cikin sauri yadan Sosa Kansa, Shima abban cikin kunya ya kalleshi yace"muje masallaci yalla6ai" Aikuwa cikin sauri yatashi suka fice. Mama tayi murmushi tace"kinga Kin kori yaran naki, gaba d'ayansu sun watse" Hajja tace"Allah nake fada miki haka mazan suke, watama da za'a yi jinkiri adan daga Daurin auren to da a gidansu zai fara rage zafi, wannan fitina har Ina?" Cikin sauri itama Aisha ta silale tayi dakin Hajja, tanajin mama ta cewa Hajja"aikuwa Shima dannaki Ina tunanin haka yake, Dan mahaifinsa ba sauqi, idan kikaga yanda yakebin takwarata da kallo Sai abun yabaki tsoro,shiyasa nake jin tsoro kar aure yazo abawa yarinya magunguna Tasha yazo yayi 6arna" Hajja tace"to Aysha itada zataje gidan kishiya akaita haka babu Dan tsumi?, itama matar tasa ai kinsan kintsawa zata sake yi" Mama tace"Eh da wannan Kuma,toki bata maganin Mai kyau da inganci, inkanada kyau saika qara da wanka, yanda yake rawar jiki akan takwarar Nan tawa Gara yajita da zaqinta" Haushi ne yakama Aisha, wannan mutanen basuda damuwa wallahi, dama de halinsu ne yazo daya shiyasa abotar tasu ta Dore, Wai mutum ake cewa yayi zaqi saikace wani chocolate(😂) Ruwan alwala da Ummah ta gabatar musu a buta, shine ya katse musu zancen nasu, Kuma ko ajikinsu Ummah tana jinsu suke wannan maganganun, Kuma ahakan ita surukar su ce(😂). ****** Su Abba suna fita kofar gida sukaga cincirindon mutane suntaru a kofar gidan, cikinsu harda Mai Gari, mamaki yakama Abba, kafin yayi magana maigari ya kalli Abba yace"mamuda yanzu Yara suke fada mana anga Mahmud Wakili agidanka, shine mukayi gayya mukazo mu shaida, saikuma muyi musa godia akan abun alkhairi daya aiko mana kwanaki" Shahaab yana jin haka yayi murmushi yace"babu komai baba, Bana buqatar godiar ku, ai komai Dan Allah nayi, Allah yaqara hore mana domin mu samu qwarin gwiwar taimakon naqasa damu" Gaba dayansu suka amsa da ''amin'', daga Nan Kuma suka babbashi hannu sukai musabaha suka wuce masallaci gaba dayansu. Bayan su Hajja sun idar da sallah aka kawo wutar nefa, Dakin Hajja suka koma gaba d'ayansu har Ummah, Aisha ta zubowa mama abincin data gama dafawa me miyar kaji, ta zauna tafara bata abincin kamar de a Abuja, tanacin abincinta fanka tana fifitasu, Hajja ta kama ha6a tace"ikon Allah,kaga wani sabon Salo yanzu Aysha abincin ma abaki takwarar Taki take baki? Shiyasa fa idan Naga Aisha tana cin abinci nake tunawa dake, komai kina yinsa kamar yar sarki, Kuma Sai akayi dace kinyi kudi, mulki Kuma Sai Allah" Murmushi mama tayi tace"ai Aysha, shiyasa kullum nake qara godewa Allah, Shahaab yana sona, yanamin biyaiya yanda bakya zato, shida Kansa yake nemomin Mai kula Dani, Kuma duk cikin Wanda yake kawo min nafijin dadin aikin Aisha fiye da kowa, saboda itace take min komai tsakani da Allah babu 6oye-6oye, tana kulawa Dani kamar Nina haife ta, cin abinci Kuma Aysha ai Yanzu na rage yanga, tunda Wakili yarasu na watsar da Gayu, yanzu Shahaab ne yake wannan cin abinci kamar bayaso, haka zai Sani agaba wataran lalle saina bashi abinci dakaina, nikuma ince Ina matarka, jeka ta baka" Hajja tace"ai shikkenan,idan akai auren saita dora daga inda ta tsaya" Saida sukai sallar ishsha'i sannan suka dawo gida, Abba ne yayi waya aka kawo wa securities lemuka da ruwa, sannan Shahaab yace suje hotel cikin dutse su kwana, zasuyi waya gobe, direban daya kawo su yabawa kudi masu yawa, daga Nan suka tafi gaba dayansu. suna zuwa gida Kai tsaye d'akin Abba suka wuce, Abba yafuto yayiwa Ummah magana aka kaiwa Shahaab ruwan wanka, sannan yaje yayi masa magana, ankai ruwan wanka bandaki, shikuma yawuce Dakin Ummah, saida sukaji shigar sa bandakin sannan Abba yace"bari infita asiyo kayan shayi, idan yafuto saiki sa Aisha takai masa abinci, saiya kwanta acan, nikuma saina taho Nan mukwanta" Ummah tace"to saika dawo, ataho mana da qwai da Dan dankalin turawa in za'a samu, Sai ahada ayi amfani dashi" Amsa mata yayi, sannan yafuto daga d'akin, dakinsa yakoma ya futowa da Shahaab wata sabuwar jallabiya daya siyo ta tundaga Saudia a zuwansa Umarah, ya ajiye masa ita akan gadon, sannan ya ajiye masa turare da man shafawa, yafice daga gidan cikin sauri. Yana futowa daga wanka Dama tunanin kayan sakawa yake, Sai yayi tozali da kayan akan gado, murmushi yayi, yarufe Dakin sannan yacire kayan jikinsa gaba daya, yasaka jallabiyar yafeshe jikinsa da turare,Sai a lokacin yasaki ajiyar zuciya yad'auki wayarsa yakira Ramadan yana bashi labarin komai. Saida Ummah ta danja lokaci sosai Wanda Takeda tabbacin yagama shirya wa sannan ta zuba masa abincin da kanta, ta bude fridge din Hajja tad'auki kunun Aya masu sanya ta juye su a jug, tahada komai, tashiga Dakin Hajja, duk suna fira Aisha tana game a wayar Hajja, Ummah ta kalleta Tace"Qawar Hajja ga abinci Nan tashi kikai masa Dakin Abbanki" Cikin nutsuwa tace"to Ummah" tatashi tasaka hijab dinta, Tajuya zata fita. Cikin sauri mama Tace"A a takwara, dawo ki fesa turare Sai kije, dama can danake barinki kina haduwa dashi babu shiri, bansan menene a tsakanin Kuba, yanzu Kam dole yaga canji ai" Murmushi Ummah tayi,Cikin kunya Aisha ta fesa turaren sannan tafuto ta dauki abincin ta wuce Dakin Abba, saida tayi sallama kafin tashiga, waya yake Amma yana jin sallamar ta yakashe wayar yace"shigo mana" Shiga Dakin tayi, ta'ajiye abincin aqasa, sannan tafara zuba masa, ko kadan taqi kallon sa, Shikuwa tun shigowar ta yakafeta da ido yana kallonta, saida tagama zubawa sannan Ahankali tace masa"gashi" Murmushi yayi babu musu ya kar6i abincin yafara ci, dadin abincin yasa yadan Lumshe Idonsa, sannan yabude ya kalleta yace"abincin yayi dadi " Murmushi tayi batace komai ba, Shima bai sake magana ba, saida yagama cin abincin, yaci sosai kuwa, sannan ta tsiyaya masa kunun ayar adan qaramin cup tamiqa masa, hannu biyu yasa yakarbi cup din yahada da hannunta yariqe, sannan yakai bakinsa ya shanye,yaji kunun ayar akwai dadi, yasaki hannunta yace"qaromin" Cikin sauri taqara masa, yasake hadawa da hannunta yashanye, sannan ya zare kofin da dayan hannunsa, hannunsa dayake riqe da'ita Kuma bai saketa, cikin sauri tafara kokarin qwace hannunta , shikuma yaqi sakinta saima gefen hijabinta daya riqe yana tsoron karta gudu, cikin faduwar gaba tace"dakin Abba nefa, kasakar min hannu karyazo, Allah idan yaganni duka zaimin" Idonsa ya Lumshe sannan yabude, cikin sigar rad'a yace"bazai zoba fa, meyasa kike wahalar Dani?kika gudo gida bakya tsoron a sacemin ke a hanya ko?" Cikin shagwa6a tace"toba mamace ba" Cikin wani irin yanayi na buqata yace"metayi?" Saida ta turo bakinta gaba sannan tace"video fa ta nunamin, Wai nice dakai" Hannunsa dake riqeda ita yasa ya shafa dogon hancinta, cikin sauri ta Lumshe idonta, yayi kasa da bakinsa yad'ora lips dinsa daidai kunnanta yace"kinga videon?" Cikin sauri ta daga masa Kai alamun tagani, murmushi yayi yace"saiki shirya, dannima saikinmin irinsa" Wata irin kunya ce ta kamata, cikin sauri tarufe idonta da hannunta,yanayinsa yaji yana sauya wa, cikin rad'a yasake ce mata"me kika Sakamin acikin kunun Aya?" Cikin sauri ta Girgiza kanta, yadage mata girarsa guda yace"really? To meyasa nake jina wani irin?" Kallan sa tayi tace"menene wani iri?" Yace"bakisan wani iri ba?" Cikin rashin Sani tace"ni bansani ba" Murmushi yayi yace"to infada miki yanda yake?" Cikin sauri Tace"A a " cikin yanayin rad'a yace mata "why?" Kanta ta Girgiza masa tace"dakin Abba nefa, tsoro nakeji, Nika denamin wannan maganar cikin rad'a, wani iri nakeji " Dariya ce ta kamashi, babu musu yasake ta sannan yace"yanzu kinsan wani iri kenan ko?Maaama na lura bakya tausayi na,kinfi tausayin mama akaina,shiyasa kika zama tauraruwa awajanta,dakika taho haka ta dinga tambayata naduba Naga inda kike? Ajima tasake cewa anga Aishan kuwa?saida nakawo ta har gida, sannan nasamawa kaina , da zuciyata lafiya, Amma Kuma gashi ke Sai wahalar mata Dani kike...." Yaya labarin Anty munirat ne? 🤔 Mutara zuwa anjima 🙏 Idan kika karanta baki biyaba nabarki keda mahaliccinki, littafin kudi ne, 300 ne kacal, ki biya ki karanta karki karanta haqqin wani 0164549488 Amina muhammad GTbank Number 08033300034 Amnah El Yaqoub ✍ BASAJA TAKU NA UKU "momy wallahi bazan iyaba,nariga nagama yanke hukunci akan zamana dashi, bazan ta6a bude idona a gidannan Inga Mahmud yana tareda wata matar Bayan niba, mahaifiyar sa itace matsala ta, Kuma yanzu nagama da wannan matsalar, saikuma yarinyar, agabana fa yarinyar tazo gidannan Amma saboda qiyaiyar da mahaifiyar sa take nunamin harta cusa masa ra'ayin yarinyar, wallahi anayin kuskuren daura musu aure wallahi saide yayi biyu babu.... Babu nidin, babu itan..." taqarasa maganar cikin matsanancin kuka. Saida tayi kukan ta sosai, sannan momynta tasaki ajiyar zuciya tace"mekike shirin aikata wa munirat?,kifadamin menene shirin ki nagaba? Ni tunda kika fadamin maganar abunda nakawo raina shine kawai muje wajan malamai ayi roqon Allah akan Allah ya watsa lamarin, ya fitar masa da yarinyar daga Kansa, a cireta acikin zuciyar sa, Amma ita mahaifiyar sa menene Nata aciki? Shifa shine me auren, duk tsiya shine yakai mata maganar zaiyi auren harta samu take fada miki magana akan haka, Amma yanzu de fadamin shirin ki nagaba, idan naji yayi daidai da nawa shikkenan" Cikin kuka tace"momy kamar ni? Ai abun kunya ne ace mijina zai qara aure, momy kishiya fa zaimin, qawayena dariya zasumin suce Dama Bana kula dashi yanda ya kamata,momy dame na ragi Mahmud? Kullum cikin gyara nake, ita mahaifiyar tasa ai itace take kitsa masa komai, idan tace yau ya auri mata uku, to adaran zai aura saboda yana jin maganar ta" Cikin sauri momy ta katseta tace"yanzu mekika yanke akan hakan?" Cikin 6acin rai tace"zaki Gani momy" daga Nan takashe wayarta. Zagaya Dakin taci gaba dayi, idonta yayi jajir saboda kuka da 6acin rai, ahankali tasake Kai hannu ta share Hawayen daya sake zubo mata, tunda taga har dare yayi basu dawo ba, hakan yana nufin acan zasu kwana kenan, bata kirashi ba, haka Shima bai nemeta ba, abunda yaqara qona mata rai kenan, yanzu haka yana can tareda wannan yarinyar me cusa kan masifa, kokuma yanzu ma yana can tana bashi abinda tafara bashi anan hartaja Hankalinsa akanta. To ni made bansaniba munirat, bari muje mugani idan hakane ko bashin ake😂🙈🏃🏻‍♀️ (littafin kudi ne, idan kika karanta baki biyaba nabarki keda ALLAH) ****** Harararsa tayi,cikin qasa qasa da murya tace"ni ban wahalar dakai ba" Cikin sauri yace"gashinan kuwa,Bayan abunda nakoya miki ma yau ko tayani bakiyi ba,Amma last time saboda mugunta haka kike ta tsotsar bakina, ko tausayamin bakiyi ba,bakiyi tunanin zan iya fita daga dakinki nahadu dawani afalo yaga yanayi na, yayi tunanin wani abu a tsakanin muba" Cikin sauri ta kalleshi tace"bakaine Kamin ba" Cikin sauri Shima yace"yawwa to tunda hakane meyasa ni yau din bazakimin ba?" Kafin tabashi amsa, suka jiyo muryar mama akusa da qofar Dakin tace"Aisha taso mutafi zamu rufe qofa, lokacin bacci yayi"😂😳 Cikin sauri ta matsa daga kusa dashi tareda zare hannunta daga cikin nashi hannun, Shima murmushi yayi ya shafa sumar Kansa, yasan mama saboda shi takeso Aisha tatafi, kafin tafuto daga d'akin suka jiyo muryar Hajja tana cewa mama"harsun gama zancen ne? Dakin rabu dasu tunda yau din basu samu waje sun zanta ba" Cikin sauri mama Tace"A a,bakisan Shahaab bane, saurin bacci gareshi, yanzu haka idan agida ne datuni yayi bacci"🙊 Tasake daga murya tace"Aisha!" Cikin sauri Aisha dasukai shiru sunajin surutun mama da Hajja tatashi tsaye zata fice, ahankali Shima yamiqe tsaye yabiyo bayanta, zata bude labulan Dakin kenan yayi saurin fuzgota tafada jikinsa, wata irin wawuyar runguma yayi mata tareda d'ora Kansa akan kafadar ta, kamar jaririn da uwarsa ta dade bata bashi nono ba, haka yake sakin ajiyar zuciya, yanda yake jin tudun dukiyar fulaninta akan qirjinsa, hakan ne yasa yasake matseta sosai ajikinsa yanda zaifi jin abun sosai a qirjinsa, shiru tayi ko kadan batayi gigin hanashi ba, Idonsa a Lumshe, yad'ora bakinsa akan kunanta,cikin rad'a yace"ina sonki,kici gaba da sonah please" Daga masa Kai tayi alamun to, saide itama kanta tarasa meyasa taqi raba jikinta da nashi,yanda tayi luf akan faffadan qirjinsa jitayi kamar su dauwama Ahaka, Adede lokacin Kuma Hajja tace"kode basa cikin Dakin ne? Naji shiru...."(😂) Sai Alokacin taraba jikinta da nashi, tafice ahankali,mama tana ganin futowar ta tasaki ajiyar zuciya, tasan halin danta, akan idonta ma Yaya aka kare da wannan shegen kallon nasa dayake yiwa yarinyar, har Mahmud din za'a cewa a barshi da Aisha su zanta?🤔 Kuma acikin daki su biyu?🤔 Hannun Aishan takama suka wuce Dakin Hajja,yanda taji qamshin turaren yarinyar ya sauya akan Wanda tafita dashi, shine ya tabbatar mata da cewa Mahmud ba ido yazuba mata ba, Amma taji dadi tunda taga Hajja bata fahimci komai ba, Gara ayi magana guda daya gobe Dasafe, abawa Mahmud yarinyar Nan tun kafin azo ayi abun kunya. Suna zuwa daki Aisha tahaye gadon Hajja ta kwanta tareda Lumshe idonta, sukan sabuwar hira suka dasa, yanayin yanda ya rungume tane yafado mata Arai,tasake tuna yanda ya furta mata cewa yana sonta ,wani irin yanayi take jinta aciki, cikin zuciyar ta tace"nima Ina sonka..." Tun tana tunanin sa, har batasan bacci ya dauketa ba, Sai cikin dare ta farka taji su mama sunata zance itada Hajja, mamaki ya kamata, lalle an dade ba'a hadu ba, ita Kam juyi tasake yi taci gaba da baccinta. A 6angaren Shahaab kuwa daqyar yasamu ya runtsa, Sai juyi yake yana murqususu shi kadai, yadade rabonsa da mace, yana fuskantar matsala ta kowacce jijiya ta jikinsa, yasan duk lokacin daya kama munirat a hannu, bazai mata da sauqi ba, saboda an dade ba'a hadu ba.(🙈) Haka ya daure, yaci gaba da yakice tunanin Aishan daga ransa, Bai yarda tunanin Nata yajanyo masa wanka ba, saboda agidan surukai da kunya katashi da asuba aji kana wanka.😎 Su mama kuwa saida sukai sallar asuba sannan suka kwanta, Alokacin Kuma Aisha bata koma bacci ba, azkar takeyi har gari yayi haske,kowa yana bacci duk basu tashi ba,tafuto tad'auki tsintsinya tafara share gidan, yana jin qaran shara yafarka, wayarsa yaduba yaga bakwai da rabi na safe, tunda suka dawo daga masallaci da asuba shida Abba ya kwanta Sai bacci yasake daukansa saboda gajiya, wayar ya ajiye yatashi yayi miqa tareda salati, sannan ahankali yazo bakin kofar Dakin ya tsaya, yadan daga labulen kadan yaga waye yake shara, karyaje yafuto Kuma yaga Ummah. Ahankali yadan leqa,saiya ga Aisha ce, ajiyar zuciya yasauke yanda ta sunkuya tana sharar hakanne yabashi damar hango tsayaiyun boobs dinta, wani irin abu yaji ya tsirga masa tundaga Kansa har qafafunsa,ya hadiye wani irin yawu,lokaci daya yanayin sa yafara sauya wa, hannunsa yatura cikin aljihun jallabiyar jikinsa, Gara sutafi daga gidannan, inba hakaba idan sukace zasu sake wasu kwanakin to yanada tabbacin wataran bazai iya Hana hannunsa ta6a wadannan abubuwan ba.(😲🙈 ) Domin yaci gaba da kallon su sosai, saiya daga labulen yafuto ya tsaya abakin kofar Dakin, yaharde hannunsa a qirjinsa yana kallon ta, yadade a tsaye yana kallon ta, sannan yayi gyaran murya, cikin sauri ta d'ago kanta ta kalleshi, hannunsa yatura cikin aljihun jallabiyar jikinsa sannan yatako ahankali zuwa kusa da'ita yace"ina kwana?" Kanta ta sunkuyar qasa,Babban mutum kamar wannan shine yake gaishe ta, Sai taji kunya ta kamata tace"lafiya kalau, dafatan kana lafiya" Yace"um Gani nan de" Kallan sa tayi da sauri, kafin tayi magana ya matso kusa da'ita, dan kwalin kanta ya janye qasa, lokaci daya dogon gashinta yafuto fili, cikin sauri tajujjuya ta kalli dakunan gidan, kar wani yafuto ya gansu, tana juyawa tana Kallan dakinsu Ummah hakanne yasa ta turo masa qeyarta, cikin sauri yasaka hannu yacire ribbon din kanta, dogon gashinta yabazu akan fuskarta, kallon sa tayi da sauri, kafin tayi magana yace"kinfi kyau ahaka" Idonta ta furfuto dashi waje, tsoro takeji kar wani yafuto ya gansu Ahaka, cikin takunsa me aji yaqaraso wajan ta, yad'ora hannunsa akanta, yafara wasa da gashin kamar zaiyi mata kalba dashi, cikin jin dadi yace"kawo tsintsiyar na tayaki sharar...."jin takun mutum ne yasa ya tsaya cak! Shibe cigaba da wasa da gashin ba, shibe saki gashin ba, gyaran murya Abba yayi, cikin sauri suka juya, wata irin kunya ta kama Aisha, Shahaab kuwa cikin sauri yasaki gashin Nata tareda komawa Gefe yana Dan shafa sumar Kansa, Amma ko kadan yaqi kallon Idon Abba, Dan kwalinta ta maida kanta ta tsugunna Tace"Abba Ina kwana" Ataqaice yace"lafiya" Cikin sauri tashige daki, Shikuwa Shahaab Kansa yana qasa,yace"barka da futowa" Abba yayi murmushi, a ransa yana mamakin yanda Shahaab baya iya 6oye soyaiyar dayake wa Aisha, yanzu inda tabashi tsintsinyar sharar zaiyi kenan?🤔 Kansa ya Girgiza tareda bashi hannu yace"yalla6ai ya gajiya?" Shahaab bai bashi hannun ba, ganin yanda yake jin kunya yasa abban yakama hannunsa sukayi hanyar waje, yana fada masa akwai yan'uwan mahaifinsa, yakamata suje su gaisa dasu. Aisha kuwa saida taji fitarsu sannan tafuto tana qarasa sharar, hararar inda suka tsaya itada Shahaab tayi, cikin ranta tace"bashida kunya, gashinan yaja Abba yaganmu" Saida tagama sharar, sannan taje ta tambayi Ummah abinda za'a dora, Sai umman tafuto suka fara harhada abun Karin kummallon tare,har zuwa lokacin Hajja da mama,Sunata bacci, basu tashi ba. Sai wajan karfe goma su mama suka tashi, basu zauna Zaman cin abinci ba Sai wajan shadaya na safe, Alokacin harsu Abba sun dawo shida Shahaab, yakaishi yaga dangi, yaga iyayensa, sun kuma yi maganar neman auren Aisha da Shahaab yakeyi, anan suka tabbatar masa zasuzo har gida Sai ayi maganar agaban Hajja, Bayan sun dawo gida wanka yayi, ya maida kayansa na jiya, Amma baisaka babbar rigar ba, ta cikin kawai yabari Sai hularsa daya dora, Sai hakan yaqara yimasa kyau yakoma tamkar saurayi, anan tsakar gida sukaci abinci shida Abba, Aisha tana cikin daki bata futo wajan su ba, Shahaab Kansa na qasa yana danna wayarsa,Mama ta kalli Hajja tace"to Aysha ai sai kuyi shiri mutafi ko?" Cikin sauri Hajja tace"ina zamuje?" Mama tace"Abuja mana, kina tunanin zan Barku kuci gaba da rayuwa anan ne?" Hajja Tace"A a, banfada miki ba, dade Ina cewa duk lokacin Dana ganki to wajanki zan koma kodan in rabu da jarabar mesunanki ,Amma Kuma yanzu tunda akwai alaqa, akwai dalili, bazan biki ba, zan jinkirta idan aka daura auren takwarar ki, sainabi Yan kaiwa amarya mutaho tare, kude turo motoci masu yawa, Dan inada jama'ah, kinga jummai ma nasan itama zatayi gayya,tunda ta dalilin ta ne har Allah ya hadani dake koba haka ba"(😂) Mama tayi dariya tace"to uwar gayya,har yanzu de kina Nan da jama'arki kamar baya,to aini banice meturo muku motoci ba, kin ganshi Nan, kifada masa" Hajja ta juya ta kalli Shahaab tace"Kai Shahaabu, kanajina nida uwarka aiko?" Murmushi yayi yace"Hajja hanya fa babu tsaro yanzu, za'a iya saceku acikin daji,kigama lissafin mutanan ki tsaf, saiki fadawa amaryar,duk yanda kukayi da'ita saita fadamin ta waya, inyaso saikubi jirgi, Amma kude bazaku dawo ba idan kunje, saboda haka kuyi sallama da kowa kafin kutafin" Abba ya Girgiza Kansa yace"haba yalla6ai, a a baza'a yi hakaba, zamu dorama nauyi yalla6ai" Batare daya hada ido da abban ba yace"Babu damuwa,koba Dan Aisha ba, dole zaku bimu kodan amintar mama da Hajja" Ummah ce tafashe da Kuka tace"mungode Allah yasaka da alkhairi, Allah yaji qan mahaifin ka" Gaba dayansu suka amsa da "Amin" Hajja Tace"A a to tunda jirgi zamubi, bazanyi gayya ba, tun Ana abu na Hankali karkuma a koma na rashin Hankali, saboda haka duk Wanda yake min mutunci dashi za'ayi tafiyar Nan, lalla6a jummai zanyi inyi shiruuuu, tanamin abu komin qanqantar sa zan cireta daga list..."(😂😲) Dariya suka saki gaba dayansu, mama tace"ni bakima kiramin ita mun gaisa ba" Kafin Hajja tayi magana yan'uwan mijin Hajja suka shigo gidan susu uku, Hajja Tace"A a malam baqori kune a gidan? Sannunku da zuwa" Ummah ce tasake shinfida musu wata tabarmar suka zauna, Bayan sunyi gaishe gaishe dakuma bayanin juna, anan aka tsaida lokacin biki sati uku masu zuwa, shi Shahaab asan ransa ma a saka sati biyu, saboda shi kadai yasan meyake ji, jiyake kamar ya hadiye Aishan kowama ya huta, Amma Hajja ta daddage tace saide a saka sati uku, kafin Nan sungama kintsawa. Mama ce tad'auki kudin komai tabayar kamar yanda al'adar Garin take,daga Nan Kuma Shahaab yayiwa securities dinsa waya suzo su tafi, daga Nan shida Abba suka raka tsofaffin gida. mama da Hajja suna zaune arumfa suna qulla Goro, Wanda za'a rabawa mutane, nasaka ranar Aisha,mama ta kalli Hajja tace"oh bakiga idon Shahaab ba da'aka saka sati ukun Nan, inajin da Kuka zai saki" Hajja tayi dariya tace"naganshi,Dan qaniyarsa ai gata nake masa, a wannan lokacin nefa zan Dan samu Tasha magungunan Sanyi,muda muke neman haihuwa ai dole mu nemi maganin Sanyi, Shima idan kun koma akwai maganin dazan baki kitafi dashi saiki bashi yadinga Sha,idan akwai sanyin ma to zai rabu dashi insha Allah" Mama yace"aikuwa zan bashi, zan dinga zaunar dashi Ina bashi yanasha,har komai ma bashi zanyi, ai ba ita kadai yakamata Tasha maganin matan ba, Shima saiya Sha irin Wanda yadace" Haka suka dinga zancen su har mamakinsu Ummah takeyi, ko gajiya basayi da zance. karfe biyu daidai sukayi shirin tafiya,Aisha tana daki tanaso ta ganshi Amma Kuma tana kunyar futowa, mama da Hajja sukayi gaba, Abba ya kalli Ummah yace"kira masa ita suyi sallama" Daga Nan Shima yafice daga gidan, Ummah ta kalli Shahaab dayake tafiya kamar bayaso Dama Kuma Shima abinda yake ransa kenan, jira yake ko Yaya ne yadan kalleta kafin yatafi, Ummah tace"bari Akira ta" Babu musu kuwa yaja ya tsaya, a gabansa tashiga d'akin Hajja sannan tafuto itama tafice daga gidan, yana tsaye tafuto daga daki tana Sanye cikin hijab, Kallan ta yayi yace"Maa-mah, banda yawo, banaso kina fita kowa yana kallon ki kinji ko?" Daga masa Kai tayi sannan tace"insha Allah, Allah yakaiku lafiya" Yace"Amin,saiki fara shirin tar6ata nanda sati uku, ni banso ma akasa lokacin har haka ba, kefa?" Cikin kunya tace"jinake ma wata uku za'a saka" Girgiza Kansa yayi, ya matso kusa da'ita yayi kissing goshinta yace"ki kulamin da kanki, banda kula maza, Sai munyi waya" Tace"to insha Allah" Daga Nan yafuto daga gidan cikin sauri, saida yagama sallama da mutanan dasuka zazzo Yan Garin yayi musu ihsani , sannan yashiga motar suka tafi, har lokacin Hajja da mama labari suke, saida mota taja, sannan suka juyo cikin gida, tundaga Nan Kuma mutane suke zuwa gidan Ana yiwa Hajja Allah yasanya alkhairi, jikar ta takusa aure. (littafin kudi ne, idan kika karanta min baki biyaba nabarki da Allah) ****** Wannan Karon kawai Airport suka wuce sukabi jirgi shida mama, suna sauka a Abuja Kai tsaye gida suka wuce shida mama, munirat tana part dinta batasan sun dawo ba, zama yayi akan kujera cikeda gajiya, mama ta wuce wajan ma'aikatan gidan tana sanar dasu auren me gidansu nanda sati uku, yana zaune Idonsa a Lumshe aka masa waya, daukar wayar yayi tareda sallama"ranka yadade mungama tracking din number Nan daka turo mana,angama bincike akan number, yanzu haka yarinyar tana hannun mu, Amma tafada mana ba'ita kadai bace, itada qawarta ne, zamu turo Maka pictures dinsu da sauran information din damuka dauka awajansu ta Email dinka, sauran bayanin Kuma sai abinda kace" Cikin sauri yace"babu damuwa,Sai munyi waya" Kai tsaye Email din yaduba Yana ganin fuskar su yarasa Ina yasan su, mama data dawo falon tayi magana taji shiru, tasake yimasa magana taji shiru, mamaki ya kamata, yazuba wa waya ido yana kallo kome yake kallo? Hannu tasa ta ta6oshi, cikin sauri ya kalleta, tace"tunanin me kakeyi haka?" Wayar yabata yace"mama wannan sune Wanda suka hada wannan vedion da aka turo muku keda munirat, Amma Kuma narasa Ina nasan fuskokinsu, kamar de qawayen munirat ne" Mama ta kar6i wayar, tana ganinsu tace"sune mana, qawayen tane, ai wani lokacin idan sunzo Ina ganinsu, tosu menene amfanin hada wannan shirmen? Menene ribarsu nayin hakan?shiyasa banaso munirat ta dinga mu'amula da qawayen banza irin wannan, yanzu banda raini yaza'ai suyiwa mijin qawar su haka?" Cikin damuwa yace"shine abinda nagani Nima" Tace"kaje ka sameta kuyi maganar, Amma su din karka yi musu komai, kabar su Suda mahaliccinsu, idan sunyi hakan ne da wata manufar ai gashinan Allah yatoni asirinsu, kodan mutuncin dasuke yi Suda matarka, karabu dasu, Amma kasa a qwace wayoyin su a duba sosai idan akwai irin vedion agogeshi, wannan 6ata suna ne, ita Kuma saika fada mata tasan irin mu'amular dazata dinga yi dasu" Cikin gamsuwa da bayanin Nata yace"to mama" Daga Nan yatashi yanufi part dinsu, yana tunanin tayaya zai iya yiwa munirat din maganar aurensa da Aisha? Yana shiga falon nasu yaga TV a kunne ta nayi, Kai tsaye dakinta yanufa, yanaso ya nuna mata kuskuren ta akan laifin data masa na saida filayen mama, sannan Kuma ya hanata mu'amula da wannan qawayen Nata, saboda karsu dinga Zua suna hure mata kunne har taqi yarda suyi Zaman lafiya itada Aisha, gefe guda Kuma ga wata irin masifaffiyar sha'awa da yakeji, yadade-yadade, abun yamasa yawa, yana buqatar mace,da tunanin maganar auren nasa yashiga Dakin Nata, saide abun mamakin yana tura qofar yaji ta abude, tana zaune akan gado tabawa qofar Dakin baya,dinkin dake jikintane yamasa kyau, shiyasa ya tsaya daga bayanta yajingina da jikin qofar Dakin yana qare mata kallo, wannan ne Karon farko da yaji tsoron yiwa matarsa magana saboda auren dayake shirin yi, munirat kuwa waya take, kwata kwata ba taji shigowar saba, tariga tasan cewa baya gidan shida mahaifiyar tasa, shiyasa Hankalinta kwance taci gaba da fadin"suna dawowa zan sanar daku, zan San yanda zanyi in sakawa securities din maganin bacci alemo susha, Kuna ganin wayata kuzo ku kashe ta"(🙆🏻‍♀️) Cikin tsananin tsoro, mamaki, dakuma firgici, Shahaab yazaro Idonsa waje(😳) waza'a kashe? Gabansa ne yafara faduwa, magana zaiyi mata, Amma saitaci gaba da cewa"karku damu, nafada muku babu matsalar komai, zan turo muku photon gidan, da inda zaku shiga har cikin dakinta, nafada muku Kuna zuwa kawai ku kashe ta, na tsaneta!, na tsaneta!!, na tsaneta!!!, tashiga cikin rayuwa ta tayi min Kane-Kane, ta hanani Zaman lafiya da mijina, harni zata bude baki tana fadawa zai qara aure, lalle-lalle ku tabbatar kun aiwatar da abinda nasaku,tsohuwa ce bazata muku wahalar kisa ba, Kuna kashe ta kushigo Nan Nima ku yanke ni, yanda baza'a gane dasa hannu na aciki ba, itama yarinyar dazai aura zan dawo kanta, karku kira wayata zan dinga kiranku idan buqatar hakan tataso" Ruf idon Shahaab suka rufe, kwata kwata saiya daina ganin komai, baisan lokacin da qafafun sa suka fara rawa ba, saiji yayi yafadi qasa jagwab, salati yake acikin zuciyar sa, banda hannunsa guda daya da yakeji yana masa rawa, dayan Kuma ba yayi, saikace Wanda cutar 6arin jiki takeso ta kamashi, cikin ikon Allah yana motsa hannunsa yana salati har yaji hannun nasa yadena rawa, Idonsa yabude ras!. Tun lokacin daya fadi tajuyo ta kalleshi, idan qirjinta yayi dubu, to yau gaba dayansu saida suka fadi, yanda gabanta yake luguden faduwa harji tayi kamar wani abu yafada cikinta, lokaci daya jikinta yad'auki karkarwa. Shikuwa Shahaab wani irin kallo yake mata na tsoro, kisa!? Kisan mutum Kuma mutum dinma ba kowa ba Sai mahaifiyar sa? Lokaci daya Idonsa yayi jajir! Cikin sauri yatashi yawuce dakinsa, yana zuwa ya zauna akan gado tare riqe Kansa dayake masa barazanar rabewa gida biyu, wani irin kuka ne yazo masa Wanda Rabon Dayayi wannan kukan harya manta, kuka yake sosai harda shashsheka, acikin wannan halin tashigo Dakin nasa ta sameshi, tana zuwa ta zuba gwiwarta aqasa tareda sakin wani irin kukan, tsawon lokaci suka dauka Ahaka, shi yana kuka itama tanayi, saida taga bashida niyyar ce mata komai sannan tasa hannu ta riqe qafafun sa tace"my Dear, Dan Allah kayi hakuri, wallahi nadena, natuba kayafemin, bada nufi nayi hakan ba, kayi hakuri bazan sake ba" Taqarasa maganar tana dora kanta akan tafin qafafun sa, cikin sauri ya d'ago Kansa tareda goge Hawayen Idonsa, muryarsa adake, kamar bashine yayi kukaba yace"MUNIRAT, kitashi kitafi gidanku daga yau Bana buqatar ki acikin rayuwa ta" Cikin sauri ta d'ago ta kalleshi, hannunta tahade waje daya tace"mahmud nikake Kora daga gidanka yau?idan nayi niyyar aikata kuskure ashe bazaka Jani a jikinka ka nunamin illar hakan ba?Saboda kasamu wadda tafini?" Runtse Idonsa yayi, cikin tsawa yace"munirat na tsaneki, nadauki yarda nabaki, na amince dake, nasoki fiyeda kowa abaya, banajin maganar mahaifiyata saboda soyaiyar danake miki, mama na itace komai nawa, itace mahaifina itace mahaifiyata, ban rageki dakomai ba amma kin dauki filayenta kinje kin siyar,banyi miki magana ba, kinsan ko saboda me? Saboda Ina sonki, qawayenki sun hada min vedio na banza da 6atanci nida yarinyar datake ganin darajar mahaifiyata kamar Tata mahaifiyar, sun turo miki, kin dauki gaba Dani, kin hanani haqqi na, now saboda maganar aure Harkina cewa kin tsani mama,aje akashe ta, akashe min mahaifiya ta munirat? Sakamakon dazaki nunamin kenan? Wannan shine tukwicin soyaiyar Dana nuna miki abaya? Yanda kikace kin tsaneta Nima na tsaneki munirat, kiyi hakuri bazan iya cigaba da zama da wadda bata qaunar mahaifiya taba, kifice daga gidannan, kifice daga unguwar Nan,kifice daga cikin rayuwa ta" Gabanta ne yasake faduwa, dama yasan da maganar takardun data sace? Wata irin tsananin kunya ce tasake rufeta, taji kamar qasa ta tsage ta shige ciki, lokaci daya jikinta yayi Sanyi kalau, bata taba nadamar abinda take aikata masaba Sai yanzu, ta Kuma yi Imani tabbas Mahmud yana sonta, domin kuwa Mai sonta ne kawai zai'iya yin haquri da maganar filayen Nan batare Dayayi mata hukunci ba, ta kalleshi Tace"Mahmud...." Kafin taci gaba da magana ya dakatar da'ita ta hanyar daga mata hannu(🤚🏻) yace"munirat, namiki saki daya, kitashi kitafi gidanku" Cikin tsananin firgici tasake cewa "Mahmud...." Idonsa ya runtse, ko kadan baison sake ganin fuskarta, cikin 6acin rai yasake cewa"munirat, namiki saki na biyu kitashi kibar min gidana" Zaro idonta tayi, mamakine yasa tasake cewa "mahmu...." kafin ta qarasa cewa Mahmud din, yasake cewa "munirat.....namiki...." Cikin sauri tatashi tafice daga d'akin tana kuka mecin rai, ta tabbatar idan bata fitaba, yanda ransa yake a6ace, to idan Ana saki goma, yau zai iya yimata shi. Ko Kallan dakinta bata Kuma yiba, ta warware Dan qaramin mayafin data daura akanta, ta nufi bakin get tana kuka me tsananin ciwo (haba Shahaab.... 😭😭😭) (wayyo Anty Munirat 🥹🥹🥹) Allah ka rabamu da sharrin zuciya 🤲🏻 Shahaab littafin kudi ne, idan kika karanta baki biyaba nabarki keda Allah, nide ban yafe ba 300 kacal 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN tareda shedar biya ta wannan number 08033300034 Mrs Usman ce✍🏻 Page 25 Kasancewar ta matar megidan yasa kokusa basuyi kuskuren hanata fita daga gidan ba, hankalin megadi yaqi kwanciya, ya hanzarta zuwa cikin gidan, yasamu mama tana dudduba kayan da Hajja ta hado mata tataho dashi a leda, cikin rawar jiki Yace"Hajiya...ga Hajiya qarama can tafita tana kuka, da alamun ba lafiya ba, shine nace Bari nazo na sanar dake" Cikin sauri mama tatashi tace"subhanallahi, Bari inje part din nasu" Tashi tayi tafice ta nufi part dinsu, zata Iya cewa rabonta data zo part din Shahaab harta manta, saboda bata zuwa gudun kar taga abin 6acin rai, ita Kuma bazata iya yin shiru ba. Saide tana zuwa tayi sallama taji shiru, Kai tsaye dakinsa ta nufa, yanayin data ganshi aciki ne yasa gabanta faduwa, wani irin numfashi Shahaab yake fitar wa kamar wanda yake gab da shirin mutuwa, salati tasaka tafara tatta6a jikinsa taga abu yaqi qarewa, cikin sauri tad'auki wayarsa ta sanarwa da doctor halin da ake ciki, sannan takira Ramadan shima tafada masa. Zama tayi tajashi jikinta daqyar, ta dora Kansa akan cinyarta tafara Tofa masa addu'ah, cikin Yan mintuna qalilan doctor yazo, cikin sauri yafara dudduba shi, dayake yazo da kayan aikinsa Kai tsaye ruwa yafara daura masa, yayi masa allurar bacci, sannan yafara harhada wasu alluran, Adede lokacin Ramadan yashigo Dakin da gudu, kan Shahaab din yanufa gabansa banda faduwa babu abinda yake, ko kallon mama baiyi ba yadubi doctor yace"yaya ake ciki? Meyasame shi?dazu dazu fa mukai waya dashi" Saida yagama hada alluran yayi masa, sannan ya kallesu yace"bawata matsala bace babba, damuwa ce ta masa yawa, saide Kuma kuyi haquri, hawan jini ya kamashi, Dan da ba'a kirani akan lokaci Bama yanayin dayake ciki, zai iya haifar masa da cutar paralyzed, Amma nayi masa allurai,idan yagama baccin zai tashi lafiya insha Allah, Sai abashi wannan magungunan yasha, please Hajiya akula da abunda zai sashi damuwa Dan Allah" Cikin damuwa mama tace"likita idan akwai damuwa afita dashi qasar waje kawai" Murmushi yayi yace"Hajiya mama idan abun yayi tsanani nida kaina zance akai shi, nafada miki babu komai, damuwa ce tamasa yawa" Cikin sauri tace"to wacce irin damuwa ce zata dameshi shida yake shirin zama ango? Nafi tunanin dawowar mu gida ne yanzu, saboda matarsa tafita tana kuka" Cikin ladabi yace"idan kinyi min izni zan iya tafiya?" Cikin sauri ta d'aga masa Kai tace"babu damuwa, idan yafarka,zan kiraka" Daga haka yajuya yafita, mama ta kalli Ramadan daya dafe goshinsa da hannunsa Kansa yana sunkuye, duk wannan batun da ake Kansa yana qasa, yayi Nisa cikin tunani menene yake damun abokin nasa har ya haifar masa da hawan jini? Mama ta kalleshi Tace"Ramadan ko kunyi magana dashi ne yafada Maka wani abu?" Ajiyar zuciya yasauke yace"mama munyi magana dashi de ansaka ranar aurensu, Bayan haka yacemin idan yadawo gida zai nemeni,Amma ni Hankali na yaqi kwanciya kode zamu dauke shi daga Nan ne? Gara a fitar dashi mama, banason abinda zai ta6a lafiyarsa, saboda ta ko'ina muna buqatar sa acikin rayuwar mu" Mama tace"dawowarmu kenan, ni Ina zaune megadi yacemin inzo munirat tafuta tana kuka, Ina zuwa saina ganshi a wannan hali Sai numfashi yake ja baima San inda Kansa yake, Amma mu bari yafarka din mugani, idan da sauqi shikkenan, idan Kuma da damuwa kawai saimu tafi" Ajiyar zuciya yasaki yace"toshikkenan" Saida tashafa fuskarsa, tata6a wuyansa taji babu zazza6i sosai, sannan tayi kissing goshinsa, ta gyara zamanta akan gadon itama ta zauna tayi shiru, tsawon awa uku suna haka,Amma Bai farka ba. (banyafewa duk wacce ta karanta min batare data biyaba) ****** Zaune suke a Dakin Ummah itada Walida, Walida ta kalleta Tace"amarya, har kin fara wani irin haske kina sheqe" Murmushi tayi, ta daga murya tace"Hajja Dan Allah kibani wayar inkira mama inji ko sunje" Hajja datake daka mata gumba tace"kede kawai kice abaki waya kikira shahab, Nina Rasa wacce irin amarya cema babu waya" Walida tayi qasa da muryarta tace"ai yanzu Zaki samu waya, saikin shiga tukunna"taqare maganar cikin wata manufar Harararta Aisha tayi tace"kyaji dashi" Hajja ce tad'auki wayar takawo mata, cikin sauri takira mama, saide Alokacin wayar tana daki, ita Kuma tana can tareda Ramadan adakin Shahaab. Saida tagama dakan gumbar, sannan tahada mata wani magani cikin Dan qaramin bokiti tace"gashinan maganin Sanyi ne, saiki dinga Sha kullum" Hankalinta yana kan waya tace"to Hajja" Saida tayi wa mama 3missed call, bata dauka ba, sannan tabawa Hajja wayarta ****** Sai Bayan sallar magrib yafarka, Adede lokacin Kuma Ramadan yadawo daga masallaci, mama kuwa acikin Dakin tayi sallah. Yatsina fuskarsa yayi tareda dora hannunsa akan goshinsa ya runtse Idonsa, cikin sauri Ramadan yace"Shahaab katashi?" Mama kuwa jikinsa tafara ta6awa tana fadin" Alhamdulillah, Bari inkira likita" Kokarin tashi yake zaune, Ramadan yayi saurin riqeshi tareda saka masa fillo a bayansa yanda zaiji dadin zama, kallon mama yayi, cikin shagwa6a yace"mama kaina yana ciwo" Cikin sigar lallashi tace"nasani, yi hakuri, yi hakuri kaji, nakira doctor yanzu zaizo" Bata dade da rufe bakintaba kuwa doctor yashigo, sake dubashi yayi ya kalli mama Yace"Hajiya mama jikinsa yayi sauqi sosai," yasake russunawa cikin ladabi yace"Allah yaqara afwa yalla6ai" Shahaab ya Jinjina Kansa alamun amsawa, mama tace"amma Dr. Yacemin fa Kansa yana ciwo, kana ganin babu matsala ne?" Cikin sauri yace"babu damuwa Hajiya, inde kun bashi magungunan Dana bayar dazu, zai warware, saide a kiyaye abinda zai sake 6ata masa rai" Cikin sauri tace"insha Allah" Dr. Nafita, mama tabi bayansa ta wuce part dinta domin kawo masa abinci. Ramadan kuwa tashi yayi yabude fridge din dakin yadauko masa fresh milk, yazuba masa acup yabashi, ahankali ya Kar6a yasha yar kadan, sannan yabashi sauran ya ajiye. Idonsa ya Lumshe, yafara tunanin irin abinda yafaru tsakaninsa da munirat dazu, Ramadan ya kalleshi yace"yakamata katashi kayi sallah" Babu musu yatashi yashige toilet, saida ya watsa ruwa a gurguje, sannan yafuto jikinsa daure da towel, wardrobe Ramadan yabude yadauko masa kayan sakawa, yabashi tareda fadin "in fadama gaskiya?wallahi bazan iya baka auren qanwata ba, saboda na tabbatar adaren farko saita ga likita" Harararsa yayi, tareda karban kayan yasaka, sannan yace"idan baka Bani ba, ai gashinan Abokina yabani" Yana fadin haka yatada sallah, saida ya idar sannan ya Ramadan yace"abokina a koda yaushe kaime sa'ah ne,kanada babbar mace, me Hankali, ilmin boko, wayewa,tareda budar ido wato munirat, sannan gashi yanzu zaka auri yar qaramar yarinya, wadda komai ma saika Koya mata, batada wayewa, batada budar ido,akwai kyan diri, uwa uba meson ka tsakani da Allah wadda ba dukiyar ka tagani ta nuna tana yinka ba" Shahaab daya zauna agado ya zubawa Ramadan ido yana jin bayanansa, yasaki ajiyar zuciya yace"hakane Kam, Nima na lura Aisha batasan komai ba, saboda kaga yanayin society din data tashi,saide Yaya zanyi? Allah yariga yasakamin soyaiyar ta acikin zuciyata, dole nine zan dinga Koya mata komai harta saba wataran ta dinga yin wasu abubuwan da kanta, Amma nikaina shaida ne, batasan komai ba yarinyar hatta a 6angaren soyaiya ma, nine nakoya mata kiss,Amma last time data min, wallahi jinayi kamar zan mutu....inda ace, tasan ire iren wadannan abubuwan, maganar Allah banajin zan dinga fita wani waje Bayan aurenmu" Ramadan yazaro Idonsa yace"kiss?yaushe hakan tafaru?" Kallan mamaki yamasa yace"hakan baya faruwa a tsakanin masoya ne? Kokuma bayan shi nacema namata wani abu ne?" Cikin tsokana Ramadan yace"wannan abu aduhu, a baqar leda, waya Sani?" Girgiza Kansa yayi, Adede lokacin mama takawo masa abinci ta zauna sannan tafara bashi, babu laifi yaci daidai gwargwado, Ramadan yabashi magani yasha, sannan mama tace"meyafaru ne akacemin munirat tafuto tana kuka?" Ransa ne ya6aci, lokaci daya yayi kicin-kicin da fuskarsa yace"mun samu Sa6ani ne mama,Allah yasa baki hanata tafiya ba" Mama tace"aini batazo ma inda nake ba,yanzu saboda kun samu Sa6ani da'ita saita tafi batareda tasanar Dani ba?nasan bazai wuce akan batun aurenka neba, inbanda munirat ai itace babba, Sai abunda tace zakayi, saboda kamar ita aka yiwa abu marar dadi, Amma idan ta kwantar da Hankalin ta Aisha ai kamar yarta take,Ina Rasa control dina wani lokacin Ina fada mata maganganu saboda nariga nasan cewa Dama can kudinka yasa ta aure ka, to Amma Yaya zanyi? Tunda kana sonta, dole haka zan haqura ai, bansan meyasa bata dauka ta a matsayin mahaifiya ba" Ahankali yace"hakane Kam, inda ace tana daukar ki kamar momynta, da bazata turo mutane tace suzo su kashe ki ba" Spoon din hannunta ne yazame yafadi qasa, gaban Ramadan yafadi, dagashi har mama, hada baki suke suna fadin "kisa Kuma?" Nan take ya basu labarin komai,mama da hawaye yake kwaranya a'idonta tace"amma har saki biyu Shahaab? Meyasa bazaka nemi shawara ta ba?" Cikin 6acin rai yace" mama duk Wanda yanemi yayi shamaki tsakanin ni dake wannan kadanne daga cikin sakamakon dazai Kar6a ahannunsa, bazan iya hadaki da kowacce mace ba,naji haushin kaina daya kasance Bana Dukan mata,Amma dayau sainayi mata duka kafin tabar gidannan" Dukan sa mama tayi akan murdaddan dantsan hannunsa, cikin sauri yasaki qara, cikeda shagwa6a yace"mama akwai zafi fa" Hawayen idonta ta share sannan ta dora kanta akan kafadarsa ta rungume shi sosai, Ramadan ma qwallah ya goge yace"gaskiya hukuncin daka yanke Shine daidai, duk mutumin da bazai so mahaifiyar ka ba, babu amfanin zama dashi, ko a addini mahaifiya aka fara ambata kafin mahaifi,bazai iyu mu hada soyaiyar iyayenmu mata data kowa ba,uwa uwa ce ako'ina" Mama ta Kalle su tace"Allah yayi muku Albarka "daga Nan ta dauke sauran abincin tafice daga d'akin Tana fita Ramadan yace"wannan dalilin ne yasa nake sake nunama muhimmancin Aisha awajanka, yarinyar tana sonka sosai, Kuma kun dace yanda baka zato, shiyasa tun farko nake cusa ma ra'ayin ta" Shahaab yace"gashinan Kuma kacusota dayawa tana nema ta zautar Dani ba" Kafin Ramadan yabashi amsa mama takawo masa magani acikin wani cup guda biyu, daya maganin Sanyi ne, dayan Kuma na tsumi ne, zama tayi ta ajiye maganin tsumin sannan tabashi na sanyin tace"gashi, Aysha Sulaiman ce tabani shi indinga baka kana Sha, maganin infection ne" Babu musu ya Kar6a yashanye, yana bata cup din, tabashi dayan maganin tsumin tace"shanye wannan dinma" Jiyayi kamar yayi ihu, tana ganin yanayin fuskarsa ya sauya tasan zai iya yimata gardama,baikuma Isa yarusa mata aikintaba,danhaka cikin sauri takai cup din bakinsa, bata dauke ba saida taga yashanye, sannan tamiqe tsaye tace"to saida safenku, zanje inkira qawata, tunda muka sauka ban kirasu ba" Ramadan yace"to mama saida safe" Shahaab kuwa runtse Idonsa yayi, Ramadan ya kalleshi yace"abokina Yaya ne?" Cikin damuwa yace" mama batasan halin danake ciki ba take Bani wannan abun ne?" Ramadan yace"maganin infection nefa,ko bakada shi ai baida matsala maganin" Cikin sauri yace"Shima dayan data qara Bani duk na sanyin ne?saida nace su saka sati biyu ayi-ayi ayi abunnan, Amma suka daddage itada qawarta, Wai sati uku, Kuma yanzu gashinan tana Bani wannan abun, Yaya takeso nayi ne?" Dariya Ramadan yasaki yace"to yanzu kuka zakayi?ai itama mama gata takewa Aishan,tsuma mata Kai take yi" Fillo yadauka yadokawa Ramadan ajikinsa, haka sukaci gaba da zance, har suka gangaro kan batun yanda shirye shiryen auren zai kasance (keda Allah idan kika karanta batare da kin biyaba) ****** Saida tayi wanka ta shirya, tasa ma'aikata su shirya abinci sukai part din Shahaab saboda Ramadan, sannan tashige daki takira wayar su Hajja, saida ta gaisa da kowa sukayi mata bangajiya, sannan sukaci gaba da magana da Hajja,yawanci zancen nasu duk akan labarin Yan makarantar sune, daga Nan Kuma suka koma kan batun auren Aisha, saida dare yayi sosai sannan sukai sallama, Hajja ta kalli Aisha taga idonta a rufe, a fili tace"mesunan qawa har anyi bacci" Aisha kuwa tana jinta tayi shiru, ba bacci take ba, kewarsa take, tana so Yakirata, tana so taji muryarsa ko kadanne, bataso Hajja tasan idonta biyu, Dan tsaf zata Dauko mata wata hirar ta hanata tunanin sa.🙈🙊 Acan Abuja kuwa kallo Ramadan ya kunna musu, saida suka gama ganin labarai sannan Ramadan yaci abincin da aka kawo,shirin kwanciya sukayi, yakashe musu wutar Dakin sannan yakoma kan gadon ya kwanta, yana kwanciya matarsa takira wayarsa, yad'auki wayar yafita daga d'akin yana sanar da'ita zai kwana tareda Mahmud ne, baijin dadi. Shiru shiru Shahaab yaji Ramadan bai dawo Dakin ba, dama tunanin ta yayi masa yawa, cikin sauri yad'auki wayarsa yakira layin Hajja, Alokacin Hajja tafara bacci taji waya tana ringing dalilin haka ne yasa tafarka, Aisha kuwa cikin sauri tad'auki wayar, tanaso taga waye yake kira a wannan lokacin kusan karfe daya saura na dare? Tana ganin number sa, tasaki wata irin ajiyar zuciya, cikin sauri ta dauki wayar "kinyi bacci?" shine abinda yafara fada mata Saida tasake yin qasa da muryarta yanda Hajja bazata jita ba, sannan tace"idan wayar tana hannun Hajja fa?" Yace"ainasan tayi bacci" Saida tasake yin qasa da murya sannan tace"yanzu suka gama waya da mama fa" Mamaki ya kamashi, ya dauke wayar daga kunnan sa ya kalli lokaci, sannan yamaida ta yace"su basa gajiya da zance ne?shine tasa mama tazo ta dinga dura min wasu irin magunguna, Kuma idan nace ayi aurenmu da wuri tace Bahaka ba" Cikin sauri Aisha tace"itama mamanka cede" Murmushi yayi yace"ni kaka nake yi da'ita, tunda tabani auren jikar ta,Nima nabar dan, nakoma jikanta kamar ke,fadamin meyasa bakiyi bacci ba? Tunani na kike? " Ahankali tace"Um.." Ajiyar zuciya yasaki yace"kiyi hakuri, Dana dawo nagaji ne dayawa, saina kwanta bacci bansamu damar kiranki ba,kin haqura?" Cikin shagwa6a tace"Uhm... nide ban haqura ba" Yanda tayi masa maganar cikin shagwa6a hakane yasa yaja fillo ya rungume a qirjinsa tareda Lumshe Idonsa, ahankali cikin lallashi yace"tome kike so?" Cikin sauri tace"saika cemin kana sona sau Dari" Murmushi yasaki yace"shikkenan?" Tace"eh" Babu musu yafara furta"i luv you, I luv you.....saida yafada sau d'ari cif, kamar yanda ta buqata, sannan yace"nagama" Ajiyar zuciya tasaki Tace"ka fanshi kanka,to ya gajiya?" Ahankali yace"Alhamdulillah, but nagaji sosai maaamah, please kizo" Cikin sauri tace"ina?" Yace"kizo yanzu....wajena....inason tausa" Murmushi tayi tace"aiban iyaba" Cikin sauri yace"aizan Koya miki, Amma nafison kimin iya cinyoyina" Cikin sauri tarufe fuskarta taqi bashi amsa, yace"kinji? Zakimin?" Cikin sauri tace"zan mintsineka idan kasake fadamin haka" Murmushi yayi yace"wacce qasa kike so aje ahado miki kayan lefe?" Sai taji tambayar tasa tazo mata a bazata, har yanzu idan yayi wani abun mamaki ne yake sake kamata, Amma idan ta tuna da Mahmud Wakili take tare, saita daina mamaki, ajiyar zuciya tayi tace"nanan qasar ma yayi" Cikin sauri yace"no, kifadamin qasar dakikeso Sai ahado miki,kinga bamuda isasshen lokaci dayawa" Ahankali tace"ni bansan na inane yake da kyau ba, nabaka za6i, kayimin duk abinda Allah yahore ma, Amma karka takura kanka, kayi abinda Allah yahore ma kawai" Wani irin sonta yaji yasake shiga ransa, yar qarama da'ita Amma sai Hankali, cikin jin dadi yace"toshikkenan za'a kawo insha Allah,please kiss me Maaamah, Ina kewarki" Tace"kaiii, tayaya to? Waima Ina matarka kakirani a'irin wannan lokacin?" Yace"tana dakinta, nide kimin abuna" Yaqare maganar cikin sigar shagwa6a. Ahankali tace"to tayaya?" Yace"Ahakan" Ahankali ta juya ta kalli Hajja, taga bangon Dakin take kallo tana bacci, ajiyar zuciya tasake yi sannan ta Lumshe idonta tasakar masa kiss tacikin wayar Lumshe Idonsa yayi, cikin sigar rad'a yace"please maaamah cigaba, karki dena kinji...." Ahankali taci gaba da kissing din wayar akai-akai yana jinta, jiyake kamar shi takeyi wa,babu musu Shima yafara maida mata, lokaci daya taji yanayin ta yana neman sauya wa, cak ta tsaya ta daina abinda take yi, Idonsa a Lumshe yace"why?" Cikin shagwa6a tace"ni ... Nifa...uhm ni wallahi..." "wani iri kikeji?" Ya katse mata maganar Tata ta hanyar jefa mata wannan tambayar, babu musu tace"um" Murmushi yasaki yace"Nima haka nakeji, shiyasa na matsu naganki acikin gidana, matsayin matata, mekikeso nayi Miki a rayuwa Maaamah?" Cikin rashin Sani tace"kamarya?" Fillonsa yasake rungume wa yace"kome kike so kifadamin" Cikin shagwa6a tace"ni kainakeso" Cikin jin dadi yace"sai Kuma me?" Cikin jin nauyi tace" Sai waya idan Allah ya hore " Murmushi yasaki yace"waya kike so?" Cikin sauri Tace"eh" Yace"kibari idan muka tafi Dubai honeymoon saiki za6i wadda kike so" Ahankali tace"to" Yace"todan sake min kiss din sainayi bacci kinji?" Wani irin kukan shagwa6a tasaka masa, Wanda ita kanta batasan ta'iya shi ba,Adede lokacin Ramadan yadawo Dakin, ganin hakan Shima yasa yayi murmushi cikin sauri yace"to shikkenan,naji... Na haqura,Kidena min kuka, mayi magana gobe,please kiyi addu'ah" Ahankali tace"to"tareda Lumshe idonta, kiss yasakar mata ta cikin wayar me ratsa jiki, sannan yakashe wayar. Ahankali ta ajiye wayar itama, tafara shafa addu'ah ajikinta, Hajja tasaki ajiyar zuciya tace"ummm qarshan duniya yazo, irin wannan sumba azahiri qiri-qiri munaji muna Gani fisabilillahi kamar ba 'ya'yan hausawa ba?mesunan qawa kina masa irin wannan shagwa6ar ba waya ba ko duniya kikace kinaso ai dole yabaki"(🙆🏻‍♀️🙈😳😲🤭) Lokaci daya Aisha ta runtse idonta,😖 shikkenan Kuma Hajja taji komai(🤦🏻‍♀️) Please kuyi haquri da wannan ba yawa, mu hadu zuwa yammah insha Allah🙏 Shahaab littafin kudi ne, ki biya naira 300 kacal ki karanta halak dinki, muddin kika karanta baki biyaba wallahi tallahi nabarki da MAHALICCINKI ban yafeba🙅💁 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN tareda shedar biya ta wannan number 08033300034 Mrs Usman✍🏻 Page 40 "wannan d'a na Aysha da jaraba yake,yazo Nan yasaki agaba da naci ko Ina yabar matar tasa?" Shiru Aisha tayi takasa bata amsa Taci gaba da cewa "ai kina Jina Sarai,kishirya gobe dutse zamu tafi,akwai wajan wadda zan kaiki 'yar'uwar jummai ce, munyi waya tace nakai ki gobe, bansaniba inaga 'Dan gyare gyare zatasa a miki" Sai a lokacin tace"Allah yakaimu" Sannan ta ajiye wayar agefen fillo tashafa addu'ah tareda juyawa ta kwanta. Saide baccin kwata kwata yaqi zuwa, tunanin sa ne yadawo mata Sabo fill,tanajin yanda yanayin ta yake sauya wa zuwa sha'awa, lokaci daya dukiyar fulaninta suka fara yimata qaiqayi, haka tayi haquri har batasan lokacin da bacci ya dauketa ba. ****** Shima a nasa 6angaren Lumshe Idonsa yayi, ya tabbatar cewa inda tana kusa dashi, babu abinda zai Hana ya kaiwa boobs dinta hannu, ya matsu sosai, halin da yake ciki yayi masa zafi dayawa, yadaiji lokacin da Ramadan ya dauro alwala yazo yacire kayan jikinsa ya kwanta, Amma shi Kansa baisan inda Hankalinsa yatafi ba, yana rungume da fillo kawai juya Kansa yake ahankali, Ramadan ya juya ya kalleshi duk da cikin duhu suke saida yaga halinda yake ciki, tausayi yabashi, yadaisan ba ciwon kan da yakeyi ne yasa shi haka ba, saboda ciwon Kai ba zaisa mutum ya rungume fillo haka cikin yanayi ba, ajiyar zuciya yasauke yace"kayi haquri mana, ai ankusa, Kuma....bata Nan, dasai kaje kaganta may be kasamu relief" Ahankali yace"gara da batanan ai,Gara da Bana ganinta,because komai ma zai iya faruwa idan Ina ganinta" Ramadan ya Girgiza Kansa yace"kuma da hakan ma,kadinga azumi kafin lokacin, zaka Dan samu sauqi ko Yaya ne" Cikin sauri yadaga masa Kai batare da yace komai ba, daqyar bacci yayi nasarar dauke shi. Asubar fari yatashi yashige wanka kasancewar yayi mafarkin ta tana masa tausa,Sanadin haka yaji shi jalaf... Dole saida yayi wanka sannan yatada kabbarar sallah, saida ya idar yafara lazimi sannan yaji za'a shiga sallar asuba, Ramadan ya tasa, Shima ya'iyo alwala sannan suka wuce masallaci, basu dawo gida ba saida gari yayi haske, suna zuwa Ramadan yahada masa tea Mai kauri yasha tareda magungunan sa, sannan suka kwanta, sosai Shahaab yayi bacci yanda ya kamata kasancewar bai samu yayi baccin ba da daddare, Sai wajan Sha daya da kwata na safe yatashi, Alokacin har Ramadan yayi wanka ya shirya yana kwance yana kallo, Shima tashi yayi yashige toilet yayi wanka, sannan yafuto ya shirya, sosai yaji shi garau kamar bashine jiya baida lafiya ba, ko kadan bayajin ciwon komai yanzu, Kai tsaye part din mama suka wuce, tana zaune afalo tana ganinsu tatashi tanufeshi, hannayenta ta miqa ta riqe fuskarsa tana fadin"yaya jikin Naka?tun dazu nake zuwa Naga Kuna bacci Baku tashi ba" Murmushi yayi yariqe hannayenta data kama fuskarsa dashi yace"naji sauqi mama, Ramadan yabani magani Nasha, banajin ciwon komai yanzu" Cikin jin dadi tace"Alhamdulillah" Tajuya ta kalli Ramadan dayake kallon su yana murmushi, har yanzu yarasa gane waye yafi son wani acikinsu? Mama Tace"Ramadan muje kuci abinci" Bayanta sukabi, Kai tsaye suka wuce dinning, saida suka gama cin abinci suka danyi firar duniya, sannan Ramadan yawuce gida, Shikuwa Shahaab Kansa yad'ora kan cinyar mama, duk masu aikin dasuke zuwa wajan ta idan suka ganshi mamaki suke, Babban mutum kamar shi Amma har gobe kamar yaro yake awajan mahaifiyarsa, ganin masu yimata sallamar ba qarewa zasuyi ba yasa yatashi yashige dakinta yaci gaba da kallon acan. (banyafewa Wanda ya karanta batareda ya biyaba) ****** Tafe suke da Hajja hannun Aisha d'aukeda kayanta, duk inda suka wuce Sai an gaishe da Hajja, tagaban shagon inusa suka wuce yataso da sauri suka gaisa da Hajja, Sai kallon Aisha yake qasa-qasa, yaso ace ita kadai ce dasun 'Dan zanta, suna wucewa Hajja tace "mesunan qawa mubi titi kawai,zaifi sauri" Aisha tace"haba Hajja, aqasa ma Ana miki irin wannan gaisuwar idan muka hau titi Kuma ai sai ta Allah" Hajja tace"ai nafiso inganni atitin Ana Hajja A'i, Ina d'aga hannu Inacewa na'am" Dariya Aisha tayi tace"Saikace wata 'yar siyasa?wallahi bazamubi titi ba" Haka suka dinga tafiya ta lungu da saqo har suka qarasa inda zasuhau mota, basu dade da zuwaba suka samu mota suka wuce dutse, Bayan sunje gidan sun huta Hajja tayi haramar dawowa gida, inda taqara yiwa Aisha fada akan magungunan ta na Sanyi ta dinga Sha kullum kartayi wasa dashi, matar mesuna Anty Mariya itace taraka Hajja, sannan tadawo gidan, sosai takejan Aisha da zance harta saki jikinta suke dan firarsu, washe gari tafara yimata gyaran jiki safe da Kuma yammah. ****** Yau Kam da shirin office yatashi, har mamaki yabawa mama yanda yake kokarin kula da aikinsa, inda wanine wannan rashin lafiyar tasa saiya dauka mata hutu awajan aiki, ko abinci baici ba saboda azumi daya dauka,yana kokarin shiga mota aka fara ruwan sama kamar da bakin kwarya, haka yashige suka wuce saide babu damar gudu, awajan aikin ma sunyi mamakin ganinsa duba da yanda Ramadan yake fada musu cewa bayajin dadi kwana biyu, sosai yayi aiki ranar,su kansu ma'aikatan sunsan Mahmud Wakili yadawo aiki, saboda yanda yasa aka riqe mutane basu tafi gida akan lokaci ba, Amma duk da hakan sun riga shi tafiya gida, shi bai tashi ba Sai yamma lis, koda wasa baiyi gigin Kiran Aisha ba, yasan cewa yana jin muryarta zai shagala ya manta da komai, Kuma ga azumi dayake, shiyasa ya tsaya tsayin daka wajan ganin yayi aikin yanda ya kamata, hakan ne yasa Hankalinsa yakoma kan aikin, Bayan yadawo gida wanka kawai yayi, ya shirya cikin qananun Kaya, wandon Jeans dakuma qaramar Riga wadda tayi masa mutuqar kyau,lokaci daya ya rikide yakoma tamkar saurayi Dan shekara talatin da uku, yasa hannu yad'auki system dinsa yayi wajan mama,zama tayi akusa dashi ta ajiye masa takardun companyn daya Bawa Aisha tace"Shahaab kayan Nan sunyi Maka kyau sosai kodan basaka qananun kayan kakeba?kullum daga suit Sai suit, manyan kayan ma basakasu kake ba" Murmushi yayi baice mata komai ba, itama tasan ba lalle ne Dama ya tanka ba, danhaka tace"ga wannan takardun, ka ajiye mata awajanka, idan tazo saika bata" Hankalinsa yana kan computer yayi murmushi yace"to mama" Tace"bakaci abinci bafa, gashi ankusa Kiran sallar magrib, kaje office kawuni kana aiki, yanzu kadawo gida maimakon kahuta Kuma ka dora dawani aikin" Tsayawa yayi da abinda yake yace"azumi nake yi,saide ahadamin tea idan nadawo daga masallaci Kuma zanci farfesun kaza medan yaji" Cikin sauri tace"to" sannan ta wuce kitchen, Dakanta tahado masa tea din, sannan tasa me aiki tayi masa farfesun kaza, a gabansa ta ajiye masa tea din Sai turiri yake, saida ya jira aka kira sallah sannan yasha tea din, yawuce masallaci, baidawo ba saida yayi sallar ishsha'i, mama ce Dakanta tafara bashi farfesun, ta kalli yanda yake neman cinyewa, cikin jin dadi tace"kaida bakason yaji meyasa yau kakeci?" Yace"mama banajin testing abakina, shiyasa" Tace"may be saboda rashin lafiyar kane,wacce qasa zamu tafi ne nida Hajiya Zaliha, saboda hado kayan lefen takwara?" Kafadunsa yadaga yace"duk inda ya muku mama, na tambayeta tace na Nan qasar takeso" Mama Tace"A a, bazai iyuba, saide asiyo komai acan abunda babu Kuma Sai Asiya anan din" Yace"toshikkenan Allah yakaiku lafiya" Kafin tayi magana momy tayi sallama cikin falon itada munirat, lokaci daya Shahaab yature hannun mama datake bashi farfesu, fuskarsa ta sauya,yanda kasan bai ta6a yin dariya ba haka yakoma, yad'ora kafa daya Kan daya, yad'auki computer sa yaci gaba da aikin dayake, ganinta ne yasa gaba daya yaji komai yafita daga ransa Mama ta Kalle su Bayan sun qaraso tace"sannunku da zuwa" Momy tace"yauwa Hajiya Aisha, Ina wuninmu?" Cikin sakin fuska mama tace"lafiya kalau Alhamdulillahi" ta kalli munirat da kanta ke qasa tace"munirat?" Cikin sauri tace"ina wuni mama" Mama tace"lafiya kalau munirat, Kuma yanzu munirat dankun samu Sa6ani keda mutumin naki saiki tafi gida maimakon kizo ki sanar Dani?" Munirat ta daga Kai ta kalli Shahaab, taga Hankalinsa yana kan computer ko kallon inda suke baiyi ba,Sai taga yaqara yin wani kyau yakoma kamar bashi ba, yanda ya daure fuska kad'ai yasa taji wani irin kwarjinin sa yashige ta, cikin sauri tayi qasa da kanta Momy kuwa baqin ciki ne ya kamata, banda munirat tana son Yaron Nan babu abinda zaisa tazo gidannan, idan dukiyar ce ai sun samu abinda suka samu a qarqashin sa, yanzu saboda Allah a matsayin ta na mahaifiyar munirat yadaga Kai ya kalleta ma ya gagara, bare tayi tunanin samun gaisuwa,ajiyar zuciya tayi tace"Hajiya Aisha ayi hakuri Dan Allah,kinsan halin 'Dan yau, ka haife shi baka haifi halinsa ba,ni nafi tunanin anshiga tsakanin Mahmoud da munirat ne, banda haka yanda yarannan suke son junansu yaushe har Mahmud zai iya sakin munirat,tunda yafara neman aure de kema kinsan iyayen yarinyar bazasu zauna ba, dole zasu shiga su fita domin araba Mahmud da matarsa,abinda yaji tana waya akai Kuma asalin abun ma badake take ba, da wata mata take,tana so tad'auki nauyin wani film na ita matar, saboda haka ga yarinya Nan nadawo da'ita, yayi hakuri ya maida ta dakinta tunda akwai sauran igiya guda daya" Mama ta kalli momy tace"Wato Hajiya zan'iya daukar komai akan baqar magana Amma banda cin zarafin qawata, wannan yarinyar da Shahaab yake nema jikar qawata ce danayi shekara da shekaru Ina nemanta, kinga kuwa ni nake da alaqa da Aisha,nasan halin qawata, batasan ma akwai malaman tsubbu a duniya ba bare taje tasa araba Mahmud da munirat, koba wannan Bama bai kamata kice Wai anshiga anfita tsakanin sa da munirat ba,wannan kamar daukan haqqi ne tunda ba Gani kikai da idonki ba" Munirat ta kalli mama cikin sauri, dama Aisha jikar qawar mama ce? Qawarta datake 6ata ran Shahaab saboda ita,? qawarta datake sa ta ajiye soyaiyar datakeyi wa Shahaab tayi masa cin mutunci saboda yaqi Nemo mata ita? Inhakane Kam dole ran mama ya6aci, tunda akan wannan qawar Tata harta iya 6ata ran danta na cikinta, to kuwa babu ran Wanda bazata 6ataba, cikin 6acin rai momy tace"to Hajiya Aisha menene laifi danna fadi haka?ranar wanka ba'a 6oyon cibi, yakamata ki fadi abinda yake ranki Kai tsaye, Nima na fadi nawa inyaso asan inda za'a Nemo maslaha, Munirat fa ta fadamin komai, tacemin tun farko kece kika daure masa gindi yanemi yarinyar,ni Ina ganin dama can kin Riga kinsan jikar qawar kice, shiyasa qarfi da yaji saida kikasan yanda kikai kika cusa masa ra'ayin yarinyar, Kuma wannan de ba soyaiya yake mata ba, sha'awar ta yake, banda haka Yaya za'ayi ace daga ta6a nonon yarinya shikkenan saiya dage saiya aure ta,? soyaiya guda daya ce, Kuma ita Mahmud yakewa munirat sannan...." Bata qarasa maganar datake ba Shahaab yayi jifa da computer sa dake kan cinyarsa, cikin 6acin rai ya kalli momy sannan yafara kokarin tashi tsaye, cikin sauri mama tasa hannu ta riqe shi, tajashi yakoma kan kujera ya zauna, munirat kuwa hawaye tafara ganin yanda momynta ta lalata komai, cikin sauri itama ta riqe hannun momynta. Cikin 6acin rai momy ta kalli Shahaab dayake huci tace"fitsararre dukana zakayi ne?idan ma bazaka maida ta dakinta bane menene abun tasowa haka kamar hayaqi zaka iyo kanmu? sanin kanka ne munirat haqurin zama take dakai, meza'ai da namiji juya, marar haihuwa?a wannan lokacin shekara biyar tayi yawa zaku rabu saboda rashin haihuwar ka, Amma haka ta zauna dakai shekara da shekaru duk da tasan baka haihuwa, Amma ita kowa yasan gadon haihuwa tayi,ai rufa Maka asiri take, kaje ka auri yarinyar kagani idan zata Iya zama dakai Ahaka baka haihuwa" Hannunsa ya dunqule waje guda,yarasa meyasa mama ta riqe shi, yaso ta rabu dashi da tuni labari yasha bam-bam,wayar sa yadauka yayi danne-danne sannan yayi jifa da wayar. mama ta runtse idonta cikeda dacin zuciya sannan ta kalli momy tace"kingama?" Munirat ta Fashe da Kuka tace"momy kin 6atamin komai, inason Mahmud momy Amma kinzo kin rusamin farinciki na,mama Dan Allah kiyi hakuri sharrin shaidan ne, Dan Allah mama ki hanashi auren Aisha, wallahi nayi alqawarin zan gyara komai, zanyi masa duk abinda yakeso, Amma Dan Allah mama karki barshi ya auri Aisha, wallahi banason ganin da Aisha, saboda Ina ganin tane a matsayin wadda tashigo cikin rayuwar mu tayi mana katangar qarfe nida Mahmud" Mama ta Girgiza kanta ta kalli momy tace"idan kun gama zaku iya tafiya,Mahmud de d'anane, to bazai maida munirat ba tunda babu dole, Kuma kusa aranku INSHA ALLAHU Sai kunga 'ya'yan Mahmud da idanunku" Kafin momy tasake magana sojoji guda biyu suka shigo bisa umarni Mahmud, kallansu momy sukai daya daga cikin su Yace"Hajiya please go out" Cikin sauri momy ta Kalle su, sannan ta kalli Mahmud, Shikuwa Mahmud baice komai ba, dayan sojan yakai hannu yana kokarin ta6a momy yana fadin "idan bazaku fitaba zamu iya fita daku" Cikin sauri munirat tafice tana share hawaye, momy ma tabi bayanta tana d'ura ashar. Saida yaga fitarsu sannan yahade hannayensa waje daya, yad'ora goshinsa akan hannun nasa daya hade, mama tasaki ajiyar zuciya ta kalleshi tace"wannan dalilin ne yasa naso tun farko ka qara aure matarka ta haihu akan idon munirat Sai tasan cewa lafiyarka kalau itace juya, to soyaiya ta rufe Maka ido kakasa gane Ina na dosa, banda rashin mutunci kije ki fadawa mahaifiyar ki qarya da gaskiya sannan kizo Nan kinamin kuka inyi haquri?, inda ace Aisha ta bayyana da wuri wallahi da ko zaka mutu ita zaka fara aura,nasan cewa nida Aysha mun wuce qawaye saide yan'uwa, danhaka koda jikar ta tayi Maka Gorin haihuwa kanta tayiwa tunda kun Riga kun zama daya" Jin yayi shiru ne yasa takai hannu tata6ashi, yana d'ago Kansa taga hawaye yana zuba A'idonsa,(🙆🏻‍♀️) cikin sauri tace"subhanallah...." Sannan tamatsa kusa dashi tajashi jikinta tana bubbuga bayansa alamar lallashi, Sai Alokacin yasaki wani irin kuka mecin rai, sosai yake kuka harda shashsheka,cikin sigar lallashi mama tace"menene abun kukan Kuma?" Cikin kuka yace"mama da gaske ni juya ne Bana haihuwa ko?da gaske itama Aisha zata gujeni saboda rashin haihuwa ta?zatace narabu da'ita ko mama?" ya qarasa maganar cikin hawaye Cikin sauri tajashi jikinta ta rungume shi sosai, saboda gaba daya ya karya mata zuciya, batasan lokacin dataji qwalla tacika mata idonta ba, cikin sauri tasa hannu ta goge, sannan cikin lallashi tace"mahmuuuud" taja sunan nasa, sannan taci gaba da cewa "waye yace Maka baka haihuwa?ni lafiyar Dana kalau,kana haihuwa, idan ka auri Aisha zata Haifa Maka Yara dozin-dozin,insha Allah kunayin aure Aisha zatasamu ciki, shiyasa nake baka maganin Sanyi ai, akwai sanyin dayake Hana mutum haihuwa, idan ma kanada shi maganin zai taimaka Maka wajan warkewa Sai kaga andace,kayi hakuri kadena kuka kaji?" Tafadi hakan cikin lallashi Cikin sauri ya Girgiza mata Kai sannan yazare jikinsa daga Nata yace"to mama kibani maganin zansha ,jiya ma baki Bani ba" Murmushi tayi tatashi tad'auke masa computer tarufe ta, sannan ta wuce kitchen tafara hada masa maganin tana dariya, yau Gori yasa Shahaab dakansa yana neman magani, Amma ranar data bashi har wani yamutsa fuska yake shi ala dole bayason shan maganin, abinda bata saniba shine wannan maganin na qarfin maza data bashi shine yasa yake yatsina fuska, saboda shi yasan cewa yanzu hakama da qarfin sa🙊🙈 asalima tun munirat tana d'akin ta idan yayi kwana biyu zuwa uku bai nemeta ba Tofa suna haduwa babu sauqi, akan irin haka har taimakon Dr. yanema, to Amma Kuma ita mama bata Sani ba, gashi Sai sake d'ura masa maganin take, tana sake tunzurashi(🙈) Maganin takawo masa na sanyin,babu musu yadauka ya shanye, cup din ta dauke sannan takai kitchen Sai gata ta dawo da tsumi, shima bashi tayi, saida yayi kamar zaiyi kuka sannan ya Kar6a Badon yaso ba, yashanye, mamaki yakama mama, hakan yana nufin maganin tsumin datake bashi shine bayaso, to meyasa bayaso? Wata zuciyar tace Gara de yasha koma lafiyarsa kalau, yanzu yanzu aka gama yimusu Gorin haihuwa, Gara ta tsumashi dakyau yanda zai dinga aiki babu kama hannun yaro, duk da tasan cewa yawan yin wannan abun bashine yake kawo cikin ba. (banyafewa wadda ta karanta min littafi na free ba) ****** Da daddare yana kwance a falon dake part dinsa, kallo yake yana Dan daddana waya, yayinda yad'auki fillon kujera yad'ora akan cikin sa, kiran wayar Hajja yayi,Bayan sun gaisa yace"maamah bata kusane?" Hajja tace"Aisha nasani ba maa-mah ba, shegen iyayi da kwainane ku ala dole Yan zamani bazaku kira sunayen ku ba,ina uwar taka? Bata wayar zanyi magana da'ita"(😂) Kwanciyar sa ya gyara yace"kikira layinta mana, ni banida Kati bazaku cinye min sauran na cikin ba,magana nakeson yi da maamah" Hajja tace"to Bari kaji inzaka ce Aisha ma kafada,bata Nan tatafi dutse, bansan Kuma ranar da zata dawo ba,inta dawo ma bazan bata wayar ba saboda damuna kuke Kuna hanani bacci" Cikin sauri yace"tatafi dutse?Kuma kika Barta tatafi bata kirani ta tambayeni ba?" Cikin sauri itama tace"andaura auren ne?Shahaab kafita daga idona in rufe, inbansa andaga auren Nan ba kace niba Hajja A'i bace" Cikin sauri yace"shikkenan, ni Allah yabaki haquri saida safe" Cikin sauri yakashe wayar, yasan Sarai zata Iya aikata wa, Gara yakashe wayar yabarta da hatsaniyar ta. Haka kawai yaji ransa ya6aci, mezatai a dutse? Yanzu haka tana can kowa yana kallon ta, haka yadinga tsaki shi kadai kallonma kashe wa yayi, yasake Kiran waya yayi oder kayan furnitures komai da komai Wanda za'a zubawa Aisha, harda na part din mama gaba daya, dakuma nasa Dakin, sannan yatashi yaje ya kwanta. (littafin kudi ne, ban yafeba idan kika karanta shi free) ****** Cikin kwanakin da basu wuce ashirin ba,Idan Kaga Aisha dole kasake kallon ta,Tasha gyaran jiki yanda ya kamata, magungunan mata kuwa Anty Mariya ce take hada mata su masu kyau tana bata ciki harda na qarin breast, Nan da Nan kuwa suka sake cika suka tsaya qyam, tayi haske tayi kyau sosai, kamar ba'itaba, gyara kawai ake mata saikuma nau'in girke girke datake sake Koya mata, tsawon wannan lokacin bata kira Shahaab ba, Shima daya gaji da tambayar Hajja yanda za'ayi ya sameta yaga de batada niyar hadashi da'ita, saiya denakira, yau kwana biyu kenan da kawo lefenta akwatunan ta goma Sha biyu, yanaso yakira yaji ko kayan sunyi mata kyau Amma Kuma babu yanda za'ayi ya sameta awaya, tareda Anty Mariya suka taho gida, Alokacin biki yarage saura kwana uku, Ummanta Sai kallon ta take tana ganin yanda taqara yin kyau sosai,dogon gashin Nan Nata yasha gyara Sai qyalli yake, Hajja kuwa kasa rufe baki tayi Sai Fara'ah take,tana qara yiwa Anty Mariya godia, daga Nan Hajja tajata suka shige daki zata nuna mata kayan lefe, itama Aishan Dakin Ummanta tatafi Dan tabar Hajja da Anty Mariya Sud'an gaggaisa, batayi tunanin har ankawo lefen ba, Ummah tabiyo ta daki tace"kin kira Mahmud kuwa tunda kika tafi?" Cikin sauri tace"Ummah bamuyi waya ba, itace ta hanani kiransa tace nabari yafara haduwa Dani tukunna zaifi doki na" Murmushi Ummah tayi tace"ai komai yazo qarshe, kikira shi idan kin huta, Dan kullum saiya kira wayar Hajja Ina jinsu suna fada" Murmushi tayi tace"to Ummah" Wani magani ta Dauko tabata tace"kitashi kije bayangida kiyi tsugunno da wannan, kibari yashiga jikinki sosai" Tace"to Ummah" Sai dare tashiga Dakin Hajja anan taci Karo da akwatuna, saitayi turus ta tsaya daga bakin kofar, Hajja ta kalleta tace"kayan lefen ki ne,shekaran jiya aka kawo su" Shigowa tayi ta zauna batare data budeba tace"sunyi kyau sosai" Hajja tafara budesu tace" keda baki dubaba? Bari ki gansu, harda sarqar gold aciki kusan Kala uku, saina dauke miki su na 6oye saboda Yan kallon Kaya kar a dauke a nemeta arasa, Dan kullum Sai mutane sunzo ganin Kaya, Amma ni me sunan qawa banga rigar nono ko daya acikin kayan naki ba"(🙈) Bakinta tata6e tace"shikkenan kawai,inajin anmanta, Hajja kibani waya nakirashi," Hajja tace"um kirashi Kam, yanda yake bugomin safe, rana, dare, Gara ki kirashi Nima nahuta" ta qarasa maganar tana bata wayar, sannan tafice tabar mata d'akin Yana ganin Kiran yayi rejecting, yakira, tana dauka da yaji muryarta ce yasaki wata irin ajiyar zuciya a6oye,cikin nutsuwa tace"ina wuni" "lafiya" yabata amsa a taqaice, tanajin haka tasan cewa fishi yake, murmushi tayi tace"fishi?" "uhm" shine kawai abinda yace Kwanciya tayi a gadon tazare wayar daga kunnan ta, ta dora bakinta akai tasakar masa kiss guda uku, Sannan ta maida wayar kan kunnan tace"Daya agoshi, daya akumatu, daya akan lips dinka" Murmushi yasaki yace"keko....,kinma raina min Hankali, ni zakiyi wa wayo? Kikama hanya kitafi wani gari, keda kike da hidima a gabanki, me zakije kiyi awani gari har kusan sati uku? Kuma koki kirani, inma mutuwa zanyi inmutu ke babu ruwanki" Cikin sauri Tace"A a, bazaka mutu ba,insha Allah kana Nan araye tare Dani, saina Haifa Maka 'yanbiyu ka gansu kayi rayuwa tare dasu" Wannan kalmar ta haihuwa daga fada masa, itace tasa yamanta da laifin data masa, yasaki ransa, cikin sauri yace"da gaske Zaki haifamin Yara maamah?" Fari tayi da idonta tace"insha Allah" Ajiyar zuciya yasauke yace"ina sonki sosai, kinga kayan naki komai yayi?" Tace"nagani sunyi kyau sosai, kayi kokari, Allah yaqara budi, Allah yasa gaba kafi haka, sunyi kyau, Kuma sun birgeni, Amma Wanda yasiyo kayan yafimin kyau fiyeda kayan...." Cikin jin dadi yace"da gaske?" Tayi qasa da murya tace"sosai" Murmushi yayi yace"zakiga babu bra aciki, saida mama ta tambayeni menene size dinki nace bakya gida, Bama waya, idan kinzo Garin Sai muje ki siyo Wanda tamiki, nikuma nafada mata haka ne kawai danta rabu Dani,da niyya naqi sanar da'ita" Tace"meyasa to?" Qasa yayi da muryarsa cikin sigar rad'a Yace"tonariga nasan size din abuna, tun lokacin Dana riqesu a hannuna naji yanayin girman su, kawai de banso a saka brezian ne, nafison ki zauna Ahaka, banason abinda zaimin shamaki dasu...." Cikin sauri tace"dan Allah nide kayi shiru...." Dariya yayi yace"nayi shiru, shikkenan? Ya shirye shiryen biki?" Bakinta ta turo gaba tace"yanzu zan fara,inaso zamuyi Walima nida malaman makarantar Dana koyar,sannan zansa gobe ayi saukar alqur'ani, zan basu sadaka idan sun gama suyi mana addu'ah Allah yabamu Zaman lafiya Kuma yabani haihuwa Mai Albarka, yanzu zaka Bani kudin Walima, da kudin fita daga dandali, da kudin gyaran jiki, da kudin uwa da uba" Jan zuciya yayi, yarasa Yaya akai yarinyar Nan Takeda Hankali da hangen nesa, ko kadan shi baiyi wannan tunanin ba na saukar alqur'ani, Amma gashi yarinyar yar cikinsa tana cewa za'a musu, wanne irin so take masa ne? Dame ya kamata yasaka mata? Cikin tsokana yace"hardasu kudin uwa da uba? To ai mama ce zata baki wannan Bani ba,itace uwar, Kuma itace uban, kudin gyaran jiki Kuma babu maganar sa, aure saura kwana uku wanne irin gyaran jiki? Ki zauna Ahaka yanda kike,karki gyara min komai ahakan kinfi kyau, Shima na fita daga dandali kiyafemin shi kawai" Kamar zatayi kuka tace"tabdi, duk wadda zatai aure fa mijin ko abokan sa suna bayarwa, Kuma ni sai kace a a, to Yaya zanyi da mutanan da zasuzo walimar?" Cikin sauri yace"yanzu de abun Bana zafi bane,zan turo miki number Ramadan ki kirashi shine Abokina zai baki duk wannan kudin, akwai number mama itama ki tambayeta na uwa da uba,nikuma zanbada kudin gyaran jikin, Dana saukar alqur'ani da za'ayi, Amma ai gyaran jikin na kwana uku ne, tunda bikin saura kwana uku, Dan haka kudin kwana uku zan turo" Cikin sauri tace"ai baka bada kudin anko bama, harshi" Yace"kuma de? Kinga kimin lissafin komai kawai kifadamin, wannan Garin naku bidi'ar tayi yawa maamah, fadamin nawane kudin gaba daya?" Tace"kudin uwa da uba dubu biyu, na gyaran jiki dubu hamsin, na anko dubu ashirin,na fita daga dandali dubu biyar, na Walima Kuma duk yanda yasamu, abinda Allah yahore, nasauka Kuma zan basu dakaina" Murmushi yayi,komai zatayi tsakaninta da Allah take fada, babu ruwanta da zuga kudi akan komai kasancewar tasan yana dashi, ya tabbatar inda watace kudin dazata yanka masa Sai yayi yawa sosai, amma ita gashi tana fadar komai yanda yake, abinda bata saniba shine ba kudi ba, inda Ana bada rai, dazai iya mallaka mata nasa, tariga tagama siyeshi da kyawawan halayenta, cikin tsokana yace"yanzu maamah duk wannan uban kudin nine zan bayar?gaskiya yayi yawa, Ina laifin ma gaba daya dubu hamsin atalauce? Albarka ake nema ai" Cikin shagwa6a tace"Allah kowa fa Ana bashi,Kuma gyaran jiki bakai akeyiwa ba" Murmushi yayi yace"nibance kimin gyaran jiki ba,yanda kike da kimfi kyau, kinsan yanda kikeda kyau kuwa?" Cikin shagwa6a tace"nide gaskiya kabamu" Yace"shikkenan, zan turo miki number Ramadan,kifada masa, zai Baku" Cikin sauri tace"to,saida safe" Yace"to kiss me..." Ahankali tasakar masa kiss din, ya Lumshe Idonsa yace"nifa banji ba" Sake yimasa wani tayi,nanma yace baiji ba, saida tayi masa sau uku, sannan sukai sallama, daga Nan tatafi gidansu Walida suka fara tsare tsaren yanda walimar tasu zata kasance. Washe gari kuwa akayi saukar alqur'ani a gidan limamin Garin, tafadi buqatar Mahmud Nason haihuwa aka saka shi acikin addu'ah, saikuma addu'ar Zaman lafiya da kwanciyar Hankali Mai dorewa da akayi musu, Bayan angama suka nufi wajan Walima inda aka rabawa mutane snacks,kowacce take away ansaka Rabin kaza, da doughnut, meat fie, cake, saikuma lemo da ruwa, awajan walimar faty ta sameta, domin kuwa isowarsu kenan daga kano RANA BATA QARYA Tun safe aketa kafa rumfuna a filin ball din Garin,yayinda manyan motoci suke sake buda hanyoyi yanda motocin baqi masu zuwa Daurin aure, zasu Sakata su wala, Abba yashiga busy sosai, Sai siyan qwaryar nono yake Ana turasu gida, acan gidan Kuma Ummah da mutanan ta sunata Dama nonon tareda fura da kwakwa wadda suka gogata tun Daren jiya, amarya tana wajan kwalliya tareda qawarta Walida da Faty,gaba daya Garin cika yayi da baqi, daga kan Yan kasuwa, Yan siyasa, harma da ma'aikatansu na hukumar efcc. Ana dab da daura aure motar daya Dauko shata tundaga dutse tafaso Kai cikin Garin, yasake girma, yazama saurayi, yayi wani irin fari kamar ba jabir din Ummah da Abba da Hajja ba, Kai tsaye yace wa direban taxi din suwuce wajan Daurin aure, suna zuwa kuwa yafuto yabashi kudinsa, ya rataya school bag dinsa Mai kyau a bayansa, Shima yafada cikin wata rumfa ya tsugunna kamar yanda mutanan cikin rumfar suke zaune, daga nesa yake hango Abba yaci babbar riga dinkin shadda fara qal, Sai Fara'ah yakeyi, Allah Allah yake adaura auren yasamu ya qarasa wajan mahaifinsa,ango kuwa baisamu damar ganinsa ba, rabonsa dashi tunda sukai waya yasanar dashi yaduba account dinsa yatura masa kudin jirgi ya shirya yazo bikin shima. aikuwa ko minti ashirin jabir baiyi ba, aka daura auren Aisha Mahmud, da angonta Mahmud Wakili, akan sadaki naira dubu Dari biyu lakadan ba ajalan ba. (to masu son shiga jirgi fa su shirya kar Hajja A'i tarufe qofa 🤣) Littafin kudi ne, idan kika karanta baki biyaba nabarki keda MAHALICCINKI, Saboda nide ban yafe miki ba. 300 ne kacal 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN tareda shedar biya ta wannan number 08033300034 Mrs Usman ce✍🏻 Page 19 'Daurin auren daya kawo surutu da kace-nace a tsakanin mutanan qauyen, dayawa daga cikin su Badon sunsan waye mijin ba, zasu iya cewa anriga ansaida Aisha ne. Inusa dayake tsugunne agefe yayi saurin goge qwallar Idonsa, rayuwa kenan, yana son Aisha ashe ita ba matarsa bace, yariga yasan tayi masa Nisa, babu yanda zaiyi yanzu saide yayi mata fatan alkhairi. Ango kuwa yana tareda manyan mutane Bayan Daurin aure anata gaggaisa wa,dayawa daga cikin mutanan suit ce ajikinsu hancinsu manne da takunkumi, Wanda hakan zai baka tabbacin cewa Yan hukumar efcc ne,kawai ruwan pictures ake ta d'auka tareda shi,yayi masifar kyau cikin shadda fara sol, iri daya data Abba, Ramadan dayake Fama da wasu mutanan shima farar shaddar yasaka Sai sukai kyau susu ukun kamar Dama can har Abban abokinsu ne. Ana Rabon Goro Abba yatashi yafuto yanufi gida wannan babbar riga Sai tashi sama take(😄) Cikin sauri jabir ya bishi ya rungume shi tabaya, Abba yana juyowa yaga jabir, cikin tsananin murna yace"jabir?,Wai Kai dinne da gaske?" Cikin murna yace"nine Abba, angon ne yace Nima in shirya inzo Daurin aure" Abba ya Girgiza Kansa cikin farinciki yaruqoshi tareda fadin"ikon Allah, to muje, muqarasa cikin gidan" Adede lokacin su Aisha suka dawo daga wajan kwalliya, anyi mata kwalliya daidai misali bamai yawa ba, tana Sanye cikin farin leshi Riga da zani, dinkin rigar anyi mata bubu,ta daura zanin akan rigar, da farin mayafi me girma, qafar ta taci wani takalmi me tsinin gaske, wuyan ta da hannayenta yasha Adon gold, Sai Jan lallen da aka mata da zanen fulawa na baqin lalle Wanda farar fatarta tasake haska lallen, sosai ta dauki hankalin mutane, jabir yana ganin ta yace"qawar Hajja amarya" Tanajin muryarsa ta yaye mayafin kanta tatafi da sauri ta rungume shi, gaba daya mutanan wajan Sai dariya suke musu, Abba kuwa bai kulasu ba samari yake kira suka shiga cikin gidan suna futowa da furar da aka Dama wadda taji qanqara tayi Sanyi sosai, Kai tsaye wajan Daurin auren suke kaita, yayinda gidan Jummai Kuma aketa futowa da take aways na abinci Wanda Abba yasa aka kira masa masu girkin hotel's takanas tundaga dutse, sukazo tun asuba suka fara aikin girkin Yan Daurin aure, girki me dadi da tsafta Wanda kowa yaci saiya so yaqara. Su Aisha suna shiga cikin gidan aka fara amarya, amarya, amarya Ansha kyau, kowa da irin abunda yake fada, mutane da Yara Yan unguwa Sai Binta suke duk inda tayi, yayinda jabir yayi wajan Ummah yashige jikinta, cikin farinciki tajashi sukayi wajan Hajja. Anan tsakar gidansu aka fara yimata photuna da mutane, kowa soyake yayi photon da'ita, ita kuwa magana take Ina Hajja, Amma Hajja tana can Kai yadau zafi tana Fama da mutane, daqyar fatin kano taje ta janyota, itama leshi ne ajikin ta Wanda Hajiya Mama ta aiko matashi da wasu kayaiyakin Wanda zata saka ranar auren, photon aka fara yimusu itada Aisha, anyi musu yafi a dadi, mutane Sai jira suke Hajja tafita sunaso ayi musu da amaryar, Amma Hajja ta kame Sai style take sauya wa, ango ne yashigo tareda abokan su, Sai Alokacin Hajja tayi can tana musu sannu da zuwa, a tsatstsaye aka kawo musu fura basu Sha Bama, suka gaggaisa da iyayen dakuma sauran dangi, wanda basu ganshi ba suka ganshi, sannan Ramadan yajashi yahade su da Aisha ya kalli me daukar photo yace"yimusu da sauri kafin muwuce" Shahaab de kunya ce ta kama shi ganin yanda dangin Aishan gaba daya hankalin su yadawo Kansa, shiyasa tunda yashigo bai yarda ya Kalle taba, Amma yanzu da Ramadan yahada su, sosai ya shagala akallonta, harma ya manta inda suke, ya manta da akwai mutane awajan, ya rungume ta tabaya, tundaga Nan masu waya suka fara sana'ah, hannunsa yad'ora akan hips dinta, sannan yazuba mata ido, aka fara daukar photon, Hajja ta Girgiza kanta, cikin qasa da murya tace"fitsararre Dama yasa ba, ni nayi mamakin wannan kunyar"(😂) Yayi tunanin angama photon, yasaketa yayi hanyar fita, me camera yasake cewa a a ya dakata Sud'an sauya style tukunna, dole haka yadawo yariqe hannayenta aka sake yimusu, sannan cikin dabara ya mintsine ta ahannun suka fice shida Ramadan, da sauran mutanan dasuka shigo. Sauran mutane Yan Daurin aure sukai ta masa Allah yasanya alkhairi yayinda wayarsa datake cikin aljihunsa alert yake ta shigowa na mutane daban daban babu qaqqautawa, banda masu turo masa message na Allah ya sanya Alkhairi Saida yagama da jama'arsa, sannan sukayi shirin tafiya, inda yayi magana da Abba agefe, sannan yashige mota suka dauki hanya, daga Nan sauran mutane Yan Daurin aure kowa yafara tafiya, Sai mutanan Garin kawai. (nabarki da Allah inde kika krnta baki biyaba) ****** Mutanene a zazzaune acikin Babban falon Hajiya Mama, duk Wanda ka kalla kasan gogaggun masu kudi ne sukazo, kowa takama kujera ta hakimce daga masu danna waya Sai masu fira, Sai masu daukar pictures a falon, Sai yanmata masu Hawa tiktok Ana vedio, yayinda ma'aikatan gidan suke kawowa kowa abinci Wanda yaji nama da ganyaiyaki, yanda ciki da wajan gidan yatara Jama'ah hakanne zaisa kasan cewa Ana gagarumin biki a gidan. Hajiya zaliha dake Gefe a zaune itada mama wadda take Sanye da leshi irinna Hajja sak, tace"gaskiya Hajiya Aisha tsarin gidan naki yasake kyau, sainaga baki ta6a gyaran gida yayi kyau sosai kamar wannan lokacin ba,ansake fenti ansake komai duk acikin wannan qanqanin lokacin" Mama tayi ajiyar zuciya tace"duk aikin Dan gidanki ne, shifa tunda wannan aure yazo, yakasa zaune yakasa tsaye,ko zumudin Dayayi a aurensa na farko,bakai wannan ba,abun har mamaki da tsoro yake bani" Hajiya zaliha tayi murmushi tace"nikam Hajiya Aisha, gulma ajali inba'ayi ba amutu, tun tafiyar mu Dubai hado lefen Nan nakeso na tambayeki meyasa yasaki munirat ne?karfa mutane su zagemu ace Dan zai qara aure ne" Mama tasaki ajiyar zuciya tace"Hajiya Zaliha munirat rabuwa da'ita ai shine yafi, idan bai rabu da'ita Bama to muddin yakawo wannan amaryar cikin gidannan to tashin Hankali za'a yi, bazasu zauna lafiya ba, sofa tayi ta kasheni" Hajiya zaliha ta zaro idonta waje(😳) sannan tace"kisa?" Mama tace"kisa fa, shine da yaji tana wayar tana fadawa masu zuwa su kashenin yanda zasu shigo har dakina, saiya saketa, bnda sata datake qunduma masa a wannan Zaman nasu, infada miki, Nan sukazo itada uwarta suka gama borin kunyar su, daga qarshe da sukaga babu Riba suka qarewa Mahmud Gorin haihuwa suka tashi suka tafi" Hajiya Zaliha tasaki ajiyar zuciya tace"tabdi, lalle munirat anyi butulu, menene Shahaab baiyi mata ba? Kullum suna yawo qasa qasa saikace tsuntsaye, banji dadi ba wallahi, Amma dakika min maganar Gorin haihuwa, saiki tunamin da wani magani da aka kawowa wata yarinya saqo ta hannu na, shekararta Tara babu haihuwa,Amma tana shan wannan magani, wallahi saiga ciki, sauran sa yana Nan agidana, idan ankawo amaryar,zanzo har gida inbata Tasha,in Allah ya yarda Shima zai haihu, haihuwa lokaci ce ai" Mama tace"to Allah yasa adace Hajiya zaliha" Haka suka dinga firarsu Sai yamma masu kidan qwarya suka zo, mama ta sauya Kaya suka fita compound aka sake shagalin biki anan, Sai wajan magrib masu kidan suka tashi, daga Nan Kuma Yan yinin biki kowa yayi haramar tafiya, Hajiya zaliha ta dinga bin kowa tana fada masa akwai dinner da za'ayi Bayan ankawo amarya. Su Shahaab kuwa basu dawo gidaba Sai dare,baima nemi mama ba, kwanciya yayi cikeda gajiya batareda 6ata lokaci ba bacci yayi awon gaba dashi. ****** Kwana biyu Bayan biki, su Hajja sukai shirin tafiya Abuja Bayan sun gama sallamar kowa, fridge dinta tabawa jummai shi, anyi Rabon robobi da dubulan da alkaki na biki, Abba Kam har kuka saida yayi lokacin dayake sallama da mutanan Arziqi Wanda akai Zaman mutunci dasu, gaba dayansu mutum goma ne masu tafiyar, Ummah, Abba, Hajja, Aisha, jabir, jummai, Walida, fati, da mutum daya dangin baban Abba, da mutum daya dangin Ummah, shatar mota suka dauka aka kaisu kano, saboda tacan zasu tashi,Aisha tana Sanye cikin material fuskarta tayi kyau sosai duk da ba kwalliya tayi ba, Amma kana ganin ta kaga amarya, karfe goma shadaya jirginsu yatashi, Sai shabiyu dawani abu suka gama komai Bayan saukarsu, motoci guda biyu sukazo suka dauke su Sai gidan Hajiya Mama. Aisha dayake tasan gidan tad'an zauna agarin nadan lokaci, batayi wani Kalle Kalle ba, Amma Hajja Kam hanci ta bude da ido tana kallo, Sai surutu suke itada jummai, gashi sun riqe Aisha sun sata atsakiya su Ala dole awajansu amarya zata zauna. Suna zuwa gida Hajja taga ruwan sojoji Ta kalli jummai tace"jummai irin wannan sojojin Ina mutum zai iya watayawa yanda yakeso, kinga Dadin qauye fa kenan" Jummai tace"um ai Hajja A'i wannan dinma wata sabuwar duniyar ce, kiduba kiga gida fa kamar baza'a mutu ba" Aisha de tana jinsu kanta yana lullu6e cikin mayafi, driver yana tsayawa Hajja takamo hannunta tace"futo da qafar Dama, ki karanta addu'oi aranki harmu shiga" Haka akayi kuwa, hannunta cikin na Hajja suka qarasa falon bakinta d'aukeda addu'ah, suna zuwa Hajiya Mama tareda Hajiya zaliha suka tashi suka tar6esu cikin farinciki, zama sukai a falon nanfa fira ta 6arke yayinda baqi suka zama Yan kallo Sai kallon aljannar duniyar gidan suke, Hajja ta kalli Mama tace"Aysha Yakubu Wai Dama anan kike rayuwa?" Mama tayi murmushi Tace"Anan nake, kema yanzu ai kinzo kenan" Hajja tayi ajiyar zuciya tace"to irin wannan gida inji de bakya mantawa da sallah ko?"(🤣) Dariya tabawa mutanan falon gaba dayansu, Hajiya zaliha tamiqe taja hannun Aisha Suka wuce Dakin mama, suna zuwa Aisha tasake gaishe ta, cikin jin dadi tace"ke bude idonki Kisha iska, wadancen tsofaffin babu me cewa bude mayafinki ta firarsu suke" Cikin murmushi tacire mayafin Nata, Hajiya zaliha tace"masha Allah" ganin yanda amaryar tasu Takeda kyau kamar ita tayi kanta. Waya Hajiya zaliha tayi, Mai gyaran Kai tazo har gida, Kai tsaye d'akin mama tashigo suka wuce toilet itada Aisha,kanta dayasha wanki aka sake warware wa, aka wanke shi, sannan tabarta a toilet din, Hajiya zaliha takai mata ruwan dafaffan lalle Wanda yaji humra yar ubansu, tace ta daure kanta sannan tayi wanka dashi, wankan tashiga tana tunani a ranta wanne irin so mutanan Nan sukewa Shahaab ne? Kowa kokari yake yaga yayi mata abu duk de Dan saboda shi, tana gama wankan tafuto, matar tasake gyara mata kanta, tashafa mata mayuka masu qamshi, sannan tayi musu sallama tatafi, wata hadaddiyar shadda dataji aiki tabata tace"saka wannan kayan, Bari inje kitchen in dawo" Aisha tace"to nagode" Ta kar6i kayan tafara kokarin sakawa, yayinda Hajiya zaliha ta wuce kitchen tahado mata fruit Wanda ta hadashi da maganin mata, sannan ta fasa mata madara peak ta ruwa aciki, takawo mata tace Tashanye shi tas, cikin ladabi ta karba tafara Sha, dadin dataji ne yasa ta shanye shi duka, Nan da Nan ta nemi yunwar da takeji tarasa, Hajiya zaliha tace"toki kwanta kihuta, anjima za'a tafi dinner, idan me kwalliya tazo saiki shirya ku fara" Tace"toshikkenan Anty Nagode" Cikin jin dadi Hajiya zaliha tafice tareda rufo mata Dakin, tana zuwa falon taga Shahaab a tsugunne yana gaida mutanan jigawa, shadda ce ajikinsa milk colour, wadda taqara qawata kyakykyawan zatinsa, Bayan sungama gaisawa da baqin yadan daga Kai yana Kalle Kalle ko zaisa Aisha Amma shiru ne babu bayani, Kuma babu Wanda yace masa tana daki yashiga,Mama kuwa da tasan ma'anar Kallen Kallen dayake saitace"ka manta wani abu ne?" Cikin sauri ya Girgiza Kansa yace"a a mama" Sannan ya kalli agogon hannunsa yace"bari inje" Cikin sauri yatashi yafice daga falon,jabir yayi sauri yabi bayansa. Hajja tayi murmushi Dan itama ta gane wayake nema. Bakinta cikeda naman kaza Wanda aka kawo musu hade da lemuka da abinci, tace"Aysha, takwararki fa yake nema" Abba da Ummah sukai murmushi, yayinda Walida da faty suka hada ido suma suke qus-qus daga Gefe,sauran baqin maza da'akazo dasu kuwa daya daga cikin su ya ajiye lemon dayake Sha yace"to Hajiya Atura masa ita mana" Mama kuwa saita basar dasu ta hanyar fada musu cewa"tana daki na, shirya wa take, inajin bata gama bane" Nan da Nan kuwa taga sun yarda da maganar Tata, tasan halin danta Sarai, yanda yarinya Tasha gyara idonta idon Shahaab tsaf zai iyayin abun kunya ga surukai Baja-Baja agida, Gara tayi zamanta adaki idan ankai masa ita saiya ganta(😇). Firarsu sukaci gaba dayi anan Hajja take tambayar Ina surukarta matar Shahaab, Nan take mama tafara Basu labarin mutuwar auren Shahaab da munirat, sosai labarin yadakesu kasancewar sude a qauye abune me girma kaji zancen kisan Kai. Aisha kuwa tana ganin fitar Hajiya zaliha tatashi ta kunna kallo, Nan Hankalinta yayi kan kallon tun tana fahimta har bacci yafara fizgarta daga qarshe ta gyara kwanciyar ta tafara bacci, bata tashi ba Sai wajan karfe biyu da kwata, cikin sauri tayi sallah, tana zaune tana azkar Walida da faty suka shigo suka kawo mata abinci, tana faracin abincin suka fara bata labarin zuwan Shahaab,Sai dariya suke, faty tace"ni wallahi tausayi ma yabani, yad'an kakkalli mutanan falon yaga bata Nan Kuma abun tausayi mama tana cewa wayake nema saiya ce babu komai, inda nice ai saide suga nagudu wajan mijina" Walida tace"to Rasa kunya, shi din cemiki akai ya haqura ne? Rabu da abinda kake so kinji, yanzu haka muna fita zai lalla6o wajan matarsa" Aisha tace"kude wallahi kuncika sa ido, a falon ma Kuna zaune gulma kuke? Ninasan Bani yake nemaba, idan nemana yake bazai 6oyewa mama ba, fada mata zaiyi" Faty tace"wallahi ke yake nema, abinda mutane yagani a falon gamu Nan reras shiyasa yafita da sauri? Bafa waya kuke ba, rabonki dashi tun ranar Daurin aurenku, Shima Ina ganin ku ba magana kukai ba, Shima narasa dalilin sa naqin siya miki waya" Walida tace"tunda kikaga haka may be bayason tayi waya da maza ne, kin Kuma San waya da daukan Hankali, tana haduwa da wani saurayin yanzu zaija hankalin ta kamar yanda Shima ya janyewa inusa hankalin ta"(😄) Dariya sukayi, Aisha tace"wallahi Bahaka bane, zai siyamin, yace Sai lokacin da muka tafi honeymoon Dubai, dakaina ma yace zan za6i wadda tamin" Walida da faty suka hada baki sukace"wowww!" Sannan faty tace"kinsan Allah?, kima shirya,yanda mutumin Nan yakashe kudi wajan aurenki, to ajikinki zai fanshe, nasan jikinki saiya fada miki, tas saiya huce gajiyarsa infada miki, barema yanzu babu matarsa, aikuma Saita Allah" Cikin mamaki ta kalli faty fuskarta d'aukeda tsananin mamaki tace"kamarya babu matarsa?" Nan take suka fada mata labarin da mama ta basu akan rabuwa auren nasu, jikinta ne yayi Sanyi sosai, tausayin sa ya kamata, Kuma koda wasa bai ta6a fada mata cewa yasaki munirat ba, itade tunda take dashi bata ta6ajin ya kushe matarsa a gabanta ba, ko maganar ta ma ba yayi, yana kokarin ganin ya mantar da'ita cewa yanada aure, Kuma hakan shine daidai, shine tabbacin mutum yasan darajar matarsa saboda bai 6atata awajan yarinyar dayake nema ba, ajiyar zuciya tayi tace"Allah yarufa asiri,idan akwai alkhairi a zamansu tare Allah yadawo da'ita dakinta, idan Kuma babu Allah yasa tabarmin abuna nikadai" Dariya suka saka gaba dayansu,haka sukaci gaba da firarsu suna kallo kad'an kad'an, har Mai kwalliya tazo, anan tace subasu waje zata yiwa amarya kwalliya,idan angama Nata Sai ayi wa qawaye dasu mama, haka suka futo daga d'akin tareda rufo musu qofar. Hajiya zaliha ce tadawo Dakin ta kawowa Aisha kayan sakawa, wani material ne Mai kyau dinkin doguwar Riga, taimaka mata tayi tasaka kayan, dinkin kuwa yayi Mata d'as ajikinta, sannan tafuto daga d'akin, suka fara kwalliyar, andauki lokaci sosai Ana wannan kwalliya, sannan akayi mata dauri Mai kyau, dogon gashin kanta akayi mata wani irin style dashi. Ba'a gamawa mutane kwalliya da dawuri ba kasancewar a nutse takeyin komai,aikuwa tuni motocin dazasu kaisu wajan dinner sunzo, mama da Hajja kuwa basu tafi ba saida Shahaab yazo mama takama hannun Aisha tasaka ta acikin motar dazasu tafi, sannan itama driver yadaukesu itada Hajja, su kansu ma'aikatan gidan sunsan Ana biki a gidan domin kuwa mama saida tabawa kowa pass din shiga. Tunda tashiga motar kanta yake qasa takasa kallon sa, batasan meyasa ba, haka kawai ta tsinci kanta da kunyar sa, wani irin kwarjini yayi mata badan kadan ba, tun shigowar ta yake waya bai daina ba har saida tafiya tayi nisa,hukumar suce tad'auki nauyin yin dinner, shi Kansa direban daya dauki amarya da ango Shima daga hukumar aka turo shi, yanaso yajata jikinsa Amma Kuma yana son jan girman sa saboda wannan ma'aikacin nasu dayake driving, ahankali yamatsa kusa da'ita tareda Dan daga net din data yafa akanta, yana kallon fuskarta yafara tasbihi ga Allah, tabbas yasan tayi kyau sosai ranar Daurin aurensu, Amma Kuma daya ganta yau, saiya ga ranar Daurin auren ba komai tayi ba, Dan qaramin bakinta ya kalla yaji kamar yahade bakinsu, shiyasa yaji taqaicin rashin Ramadan akusa, yaso ace shine yake driving, da saide yarufe Idonsa, Amma babu abinda zai hanashi hade bakinsa da Nata, idonta dayake Lumshe ya kalla, gashin idonta ya kwanta yayi luf...,ahankali yad'ora lips dinsa akan kumatunta yasakar mata kiss, cikin rad'a yace"kinyi kyau" Sannan yasaki net din, yajuya yana kallon titi kamar bashine yayi abinda ya aikata yanzu ba, azahiri kallon titi yake, kasancewar shine yake zaune agefen Dama ita Kuma tana hagu, hakan ne yasa yazura hannun sa na hagu ta bayanta, yayinda hannunsa na Dama yake danna waye, shi Kansa baisan meyake danna waba (😲) Hips dinta yariqe da hannun daya zura ta bayanta, ahankali tad'an motsa alamun bata so,cikin nutsuwa yayi sama da hannunsa ya dorashi akan dukiyar fulaninta guda d'aya yayi masa wata irin matsa, lokaci daya Aisha taqame a zaune, gabanta ne yafadi, cikin sauri ta juya ta kalleshi, Amma sai taga Hankalinsa yana kan waya, ganin ta firgita dayawa tana nema ta tona masa asiri yasa yasake ta, Adede lokacin Kuma suka qaraso wajan, kasancewar lokaci yaja yasa suna zuwa yakama hannunta suka shige ciki, ta ko'ina girma ake bashi, waje ya tsaru iya tsaruwa, duk Wanda ka kalla saide kaga yatsuke cikin suit,ango da amarya dakuma mutanan gida sune kawai basu saka suit ba, Amma jabir ma tasa suit din yasaka. Suna qarasa wa ciki kawai haske kake Gani na camera tako Ina yana tashi, an gudanar da taro lafiya,anyi Rabon kayaiyaki yanda ya kamata, amarya da ango sunsha pictures da video, lamarin dayasa kafafen sada zumunta suke ta surutu akan bikin, yanda masoyan sa suke posting din vedion bikin ne yasa munirat tagani, Wanda taji kamar tahadiyi zuciya ta mutu, yayinda qawayenta dasuke gefenta suna mata dannar qirji suke sake zigata, dayawa daga cikin su tunzurata suke har hakan yasa tayi wani quduri marar kyau acikin zuciyarta. Sai qarfe goma na dare, suka nufi gida,hannun Aisha yana cikin na mama har suka qaraso gida, anan part din mama gaba dayansu baqin suka kwana, kowa yariga yagaji, Kuma babu Wanda yake tareda yunwa kasancewar anci Ansha awajan dinner, shiyasa suna dawowa kowa ya kwanta, su faty ne basuyi bacci da wuri ba itada Walida sunata aikin danna waya suna posting pictures din amarya da ango. Sai shadaya da wani abu Shahaab yadawo gida, yariga yasan cewa Aisha tana tare da iyayenta, shiyasa yayi tunanin tafiya part dinsa Shima,saide duk yanda yaso yayi bacci bai samu ya runtsa ba Sai gab da asuba, hakan ne yasa ya makara a sallar asuba. Bayan yadawo daga masallaci kuwa kwanciya yasake yi yana ramakon bacci, Sai wajan azahar yashiga part din mama, Fata yake yaga Aisha Amma yana zuwa yaga bata Nan, abinci mama tabashi yaci, saida yaci, sannan ya kalleta yana goge bakinsa da tissue yace"Akwai driver yana jiransu, zai kaisu gidansu idan sungama abinda suke saisu shirya sutafi" Cikin jin dadi mama tace"to insha Allah, suma baqin ai munyi magana dasu anjima zasu tafi, idan sukaje sukaga gidan nasu saisu shirya subi jirgin dazai tashi anjima" Cikin kulawa yace"dawuri haka? Nayi tunanin zasu kwana biyu har muje dasu suga sabon office din Abba dayake lagos?" Cikin farinciki tace"office ka bashi?" Yace"Eh ai bazai ji dadin Zaman Garin ba tunda ba sabawa yayi ba, Amma idan akwai abinda zai dinga dauke masa kewa hakan zaisa ya kwantar da Hankalinsa ya zauna agarin" Cikin jin dadi tace"ka kyauta, Allah yasaka da alkhairi, Allah yayi maka Albarka" Cikin jin dadi Shima yace"Amin" Daga Nan yajuya yafita. Saida kowa yagama shirya wa sannan suka tafi gidan da Shahaab ya basu, Wanda yake kusa Dana mama, asalin gidan munirat yayi niyyar sakawa aciki, Kuma duba da yanda mama take zaune ita kadai yasa yafasa, ya zauna akusa da'ita awani part din daban, yanzu Kuma da Allah yakawo su Abba, kawai saiya basu gidan. Sunje sunga gida, gida yayi gida komai yayi yanda ya kamata, ankashe kudi sosai a gidan, akwai abubuwan buqata aciki babu abinda zasu nema, dakuna kuwa kowa da nasa, Hajja ce tafara za6ar dakinta, sannan Ummah da Abba ma kowa ya za6a, jabir ma ya za6a yakai kayansa ciki, aka barwa Aisha daya, sauran dakunan Kuma aka rufesu ko Allah zai kawo musu baqi gidan a matsayin ziyara, Ummah da Abba Kam zama sukayi, yayinda Hajja tace gidan qawarta zata koma Sai ranar dasuka ganta kawai(🤣) Sukuma su Walida suka dawo gidan mama da sauran baqin, karfe biyar na yamma kuwa driver yayi magana su futo, haka suka futo da tarin abun Arziqin da mama tayi musu, Shikuwa oga kwata kwata kudi yabawa kowa acikinsu Mai yawan gaske, sunsha ruwan godia tareda sanya Albarka,jummai tana kuka Hajja ma haka, Ahaka suka rabu, sannan suka shiga mota suka tafi Airport, mama da Hajja suka juya cikin gidan, Hajiya zaliha kuwa tana falo, suma zama sukai har dare suna firarsu, qarfe Tara na dare tasake hadawa Aisha ruwan lalle tayi wanka dashi, tasake bata wani hadin fruit din Tasha, sannan tabata maganin datayi alqawari na haihuwa, sannan tabata kayan sakawa ta fesheta da turare, takama hannunta takawo ta wajan su Hajja, 'Dan fada Hajja tasake yimata sannan suka rakata part din Shahaab gaba dayansu su ukun,har cikin dakinsa suka kaita sannan sukayi mata sallama suka futo, itama Hajiya zaliha ta yiwa direbanta waya yazo ya dauketa tatafi gida Bai dawo gidaba Sai qarfe goma Sha daya na dare, yunwa yakeji sosai,Kai tsaye part din mama yanufa Yana tunanin a ransa yakamata yau de mama ta tausaya masa tabashi matarsa, haqurinsa yagama karewa, idan ma bata bashi itaba yau Kam bazai kwanta ba Sai yaga matarsa, yana wannan tunanin yashiga falon, Alokacin mama da Hajja suna zaune, Girgiza Kansa yayi lokacin da yaji mama tana cewa Hajja "aike Aysha Sulaiman kin iya math, Kin tuna duk ajinmu kece kikafi kowa iyawa?" Hajja tace"natuna mana, aini yanzu sonake Inga jamila Sani,ko Yaya Takoma yanzu?Alokacin Nan fa baqin ciki takeji ayi tambaya akan math taga nabada amsa, shegiya uwar Yan baqin Hali, Alokacin exam tahana kowa ya copy Nata" Shahaab yayi ajiyar zuciya tareda zama akan kujera, sunzo Nan suna ta zance ko gajiya da zance basayi, shikuma sun hanashi matarsa, Kuma sunyi mursisi hankalin su kwance, cikin shagwa6a yace"mama yunwa nakeji" Saida tagama zancen ta sannan tace"ga abinci can a dinning kaje kaci" Babu musu yaje yaci abincin sa, sannan yamiqe yakoma wajan su, saida yadan shafa sumar Kansa sannan ya kalli Mama yace"mama,Wannan yarinyar tayi bacci ne?" Tana sane Sarai da Aisha yake, saita nuna bata gane ba tace"wacce yarinya?" Kallon idonta yayi sannan yace "Ina nufin Maaamah" Cikin rashin fahimta yace"Maaamah?" Hajja tayi dariya tace"takwararki yake nufi, keda bakisan wannan sabon salon ba?" Cikin sauri ya kalli Hajja yace"Hajjjjah" Yakirata yanajan sunan nata Cikin sauri itama tace"ga Hajja A'i anan,yaude babu wayar dare,nayi murna Nima andena hanani baccin dare,kaje tana d'akin ka" Cikin sauri ya sunkuyar da Kansa, Sai yaji kunya ta kamashi yaji Dama bai tambaye su Ina take ba, ahankali yajuya yana Sosa qeyarsa yace musu "saida safe" Yana fita suka saka dariya, Shima daya fitan bai nufi part dinba, mota yashiga yaje yasiyo mata kaji da wata madara special, sannan yadawo gidan yawuce part dinsa. Wannan Aminan Kam tagaji.... Mutara zuwa Yammah🙏🏻 Littafin Shahaab na kudi ne, idan kika karanta baki biyaba nabarki keda Allah 300 ne kacal 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN tareda shedar biya ta wannan number 08033300034 Mrs Usman ce✍🏻 Page 44 Gajiya tayi da mayafin dasuka lullu6e mata fuska dashi, ahankali ta yaye shi tana kallon tsarin 'Dakin nasa, ko ba'a fada ba tasan d'akinsa ne wannan duba da yanda taga takardu da computer sa a ajiye agefe, wannan shine karonta na farko data ta6a zuwa dakinsa, saboda lokacin da munirat tana nan ko kallon 'Dakin bata Isa tayi ba,yanda aka tsara d'akin komai da komai yayi, Kuma da alama sababbi ne,tunani tafara Wai yau itace a gidan Mahmud Wakili, acikin dakinsa, akan gadon sa, a matsayin matarsa. Saida yatofe ko'ina da addu'ah kamar kullum, sannan Yarufe ko'ina, Kai tsaye yawuce dakinta, yana turawa yaga bata ciki, Kuma baiga alamun anshigo dakinba, danhaka kai tsaye yawuce nasa d'akin. Alamun kama handle dataji yasa cikin sauri taja mayafin tarufe fuskarta dashi. ****** "takwarata Kuma Ana can ko awanne Hali take?"(🤔) cewar mama Hajja data gama Tofa addu'ar bacci tace"tana can Sai abinda Hali yayi,yanda kika Hanashi matarsa akan lokaci idan ya kamata ai sai Allah Sai ma'aiki"(😂) Mama tace"gaskiya Kam, Allah yasa de Ana abun Nan yarinyar Nan tasamu ciki, da bansan wanne irin farinciki zanyi ba,abun yana mun ciwo idan natuna lokacin da munirat tazo da mahaifiyar ta har gida suka gorantawa Shahaab haihuwa, yana Bani tausayi sosai yaron" Hajja tace"dole muyi murna Kam idan Allah yabata ciki, gida har gida irin wannan Amma ace babu Yara ai akwai damuwa,yanda Yaron Nan yake taimakon bayin Allah, Shima Allah ya temake shi yasamu haihuwa Mai Albarka" Mama tace"Amin ya Allah, Aida wuri zan tashi indafa musu ruwan zafi dakaina,nasan halin Shahaab, ita Kuma nasan bazata iya gyara kanta yanda ya kamata ba" Hajja ta kalleta da sauri tace"ruwan zafin Zaki Kai musu sekace mejego?"(🤔) Mama tace"idan bankai musu ba,zakije ne?" Cikin sauri Hajja Tace"A a, o o,inani Ina wannan danyen aiki, kedin de kiyi tunda kece kika haife shi da cikin ki" Suna wannan maganganun har bacci yayi gaba dasu (idan kika karanta baki biyaba nabarki keda Allah) ****** Tana zaune daram Akan cinyarsa, babu komai ajikinsa dagashi Sai gajeren wando, gashin dake qirjinsa ya kwanta yayi luf, murdaddun dantsan hannunsa sun baiyana muraran, gaba daya a takure take jinta,takasa kallon sa kokadan, salon yanda suke Zaman yasha bambam Dana kowacce rana, tanajin yanda abunsa yake harbawa,gashi ya tsatstsareta da ido tarasa Yaya zatayi dashi, gaba daya Sai hakan yasa ta awani hali, gabanta banda faduwa babu abinda yake, tsoro da fargaba suka kamata, yayinda anasa 6angaren cikin zumudi yake tura mata naman kazar daya shigo dashi cikin bakinta, sosai yake danna mata naman meyawa, Yacika mata baki dashi sosai, yadauko zai sake bata cikin sauri ta Girgiza masa Kai tareda fadin"naqoshi" Cikin wani Salo yace"meyasa?Ina lura dake Tun dazu kinqi sakin jikinki dani, ki kwantar da Hankalinki, a jikin mijinki kike,Dani din, da jikinnawa,komai da komai naki ne, menene abun tsoro Kuma?" Cikin fargaba tace"babu komai, inaji gabana yana faduwa ne" Wani irin murmushi yasaki har dimple dinsa suna futowa,ahankali yasa hannunsa na hagun yazuge zip din rigarta, cikin sauri ta kalleshi idonta ya furfuto, Shikuwa bai kalleta ba yazura hannunsa cikin rigar yad'ora shi atsakiyar qirjinta,lokaci daya yaji yanda gabanta yake luguden faduwa, mamaki ya kamashi duk wannan tsoron na menene? Kafin yadawo daga tunanin dayake yaji tasaka hannu ta fitar masa da nasa hannun daga kan qirjinta. Ajiyar zuciya yayi yace"kinga...., Kidena tsoro na, ni babu abinda zan miki, Amma idan kinaso narabu dake, kibani naman naci, shikkenan saikiyi kwanciyar ki, Amma ni Kidena damuwa akaina,koda munirat tana nan ni Bana takura mata"🙊🙊 Kallonsa tayi har zata tambayeshi meyasa baiyi haquri yabarta a dakinta ba yasake ta? Amma kuma Saitayi shiru tana tsoron yana cikin farinciki ta dagula masa lissafi, Ahankali ta daga masa Kai, sannan tasaki wata irin ajiyar zuciya, Nan da Nan Kuma saita sake, har mamaki yakashe Shahaab, wato de da gaske tsoron nasa take,ahankali tafara bashi yanaci yana Lumshe Idonsa,kadan yaci yace mata yaqoshi, tad'auki madarar tazuba acup zata bashi yayi saurin riqe mata hannu yace"bazan shaba" Tace"meyasa?" Idonsa Adan Lumshe yace"banashan madarar ruwa sosai, Gara ta gari, idan Nasha ta ruwan akwai damuwa, saboda yanzu haka ma tamin yawa ajikina"(🙈) Cikin rashin fahimta tace"to Bari in zuba Maka drink" Bai hanata ba, saide yanda ta motsa jikinta akan cinyarsa wajan zuba lemon, saida hakan yasa yakusa sakin Dan qaramin ihu, shiyasa tana bashi lemon cikin sauri yariqe har hannunta yakafa cup din a bakinsa saida ya shanye shi tas, har hakan yabawa Aisha mamaki, kallon ta yayi yace"ya'isa, kije ki kwanta" Tace"bari in tattare kayan Nan" Cikin sauri yace"waye yace miki amarya tana aiki?wuce ki kwanta"yafadi hakan yana yimata nuni da kan gadon. Ajiyar zuciya tasaki, ahankali tatashi daga kan cinyarsa, tahaye gadon ta kwanta, tareda takure kanta waje daya, ko kayan jikinta bata cire ba, tunda suka idar da sallah yayi yayi ta rage kayan jikinta Amma fafur taqi, Sai rabuwa yayi da'ita yafara bata nama. Shida Kansa ya kwashe komai yakai kitchen, sannan yadawo Dakin yakashe musu wuta, ya kunna esi, yahaye gadon ya kwanta tareda ja musu Bargo me laushi, sannan yasaka hannu ya janyo ta, yad'ora ta akansa, jin kanta akan faffadan qirjinsa yasa tasake yin luf, Dan kwalin kanta yazame ya wulloshi Qasan gado, sannan yatura hannunsa cikin gashin kanta yana mata wasa dashi yana Dan Sosa mata kan ahankali, yanda yake wasa da gashin yasa taji dadi harta fara Lumshe idonta, cikin muryarsa da bata fita sosai yace"bazaki cire kayan ba?" Cikin shagwa6a tace"um um ni dashi zan kwanta" Cikin dabara yace"to ai ni Bana kwana da Kaya, Kuma duk Wanda ya kwanta Dani da Kaya ajikinsa to ranar Bana bacci, mafarkai nake na abun tsoro, nadinga ihu Ina buge buge, tunda nace bazan miki komai ba kema idan kinaso muyi bacci Hankali kwance to kawai kicire su" Cikin sauri tace"ihu Kuma?duk saboda kayan?" Yace"emana" Cikin rashin wayo tatashi zata cire, cikin sauri yadawo da'ita jikinsa, yanayi mata labarin qanzon kurege akan kwana da Kaya, cikin dabara yaraba ta da kayan jikinta, ahankali yafara shafa gadon bayanta,cikin sarqewar murya yace"meyasa kikasa wannan abun?" Yafadi hakan yana 6alle mata brar datake jikinta, cikin sauri tafara motsi zata sauka daga jikinsa, sake riqeta yayi qam,hannunsa guda daya yad'ora akan boobs dinta yafara murzawa cikin wani irin Salo,lokaci daya ya gigice yarasa gane su dinne de daya ta6a kwana ki kokuma sauya mata su akai? Yanda yake murzawa ahankali yasa ko kadan bataji zafi ba, Sai wani irin yanayi ma data fara jinta aciki me mutuqar dadi ,shiyasa tayi shiru tana kar6ar saqon, bakinsa yad'ora akan kunnan ta cikin rawar murya yace"maaamahhhhh" Tace"um" Yace"insha 'Dan kad'an?" Ahankali tace"anayi Dama?" Wani irin yawu ya hadiye, yasake damqe dukiyar fulaninta duka guda biyun, sannan yace"bakisan anasha ba? " Kanta ta daga masa alamun eh,yana jin haka, yahade bakinsu waje daya, yayinda hannunsa yake kan qirjinta yana Squeeze,sosai yake kissing dinta har hakan yasa hankalinsu yafara barin jikinsu, kamar yanda yafada mata abaya ba zaiyi mata komai ba, hakan yaso ta kasance kodan su mama da Hajja, yana ganin aikata wani abu zaisa su San sirrin sa da Aisha, shikuma bayaso su Sani, shiyasa yaso suyi wasa kawai ko Yaya ne yasamu relief, saide Kuma yanayin yanda yaji sauyi ajikinsa, Kuma yasamu Kar6uwa awajanta, yasa notikan Kansa suka kunce, gaba daya ya manta da komai, shi Kansa ya manta waye shi, ya manta wacce duniya yake,shan bakinta kawai yake fatansa daya Yanda yakejinsa yazo har wuya, Allah yasa yasamu gamsuwa yanda ya kamata, Allah yasa karya jita kamar munirat, Allah yayanke masa wahala, yana wannan tunanin yazare bakinsa daga Nata, ahankali ya maida bakinsa kan boobs dinta yafara tsotsa ahankali, yanda taji dadi ne yasa ta kama Kansa ta riqe sosai,idonta a Lumshe suke tanajin wani irin dadi yana shiga jikinta,hakan datayi masa yayi masa dadi sosai,Sai yake jinsa kamar jariri Wanda mamansa ta riqe Kansa take bashi nono yake Sha,sosai yake shan guda daya, dayan Kuma yana hannunsa yana wasa da nipple din, yadade yana abu daya, sannan yasaka hannunsa yabude qafafunta, yafara dosar hanyar sa yana karanta addu'ar saduwa, tanajin abinda yake karanta wa tadawo hayyacinta, tariga tasan wannan addu'ar tun tana zuwa islamiya, shida yace babu abinda zaiyi meyasa zai karanta ta? Hannunsa tafara kokarin janyewa daga kan cinyarta, cikin tsananin tashin Hankali tafara buge buge tana kokarin qwatar kanta, cikin rawar jiki yasake riqeta, gaba daya karkarwa jikinsa yake, itama a rude take, tanajin yanda yake sake mannewa a jikinta ko Kaya babu ajikinsa tarasa yaushe yacire dan gajeren wandon nasa, yanda ya liqe mata yasa taji yana 6ata mata jikinta da wani irin ruwa, cikin karkarwa yaja hannunta yad'ora shi akan abunsa,tareda fadin "please maaamah,natara dayawa, kibarni inyi Dan Allah...." yana qarasa fadar hakan yafashe mata dawani irin kuka. Jin hannunta akan abinda bata ta6a tsammani ba yasa cikin sauri ta janye hannunta tareda dunquleshi danma karya sake bata abun, dama haka auren yake? Take tambayar kanta, itama hawaye tafara tace"Dan girman Allah kabarni, ni wallahi bansaniba...,bansan haka bane" Kansa ya Girgiza cikin hawaye yace"zan mutu inde baki Bani ba maaamah" Batare daya jira mezata ce ba, yaci gaba da abunda yake, kuka take tana qoqari tureshi Amma takasa, wata irin azaba tajii tashin farko a rayuwar ta dataji wani irin zafi ya keta ta qasanta, cikin tsananin tashin Hankali da azaba tasaki wata irin qara, daga Nan bata sake yin wani qaran ba sakamakon rufe mata baki da yayi da nasa bakin. Wannan ihun Nata har part din mama,tana cikin bacci taji kamar acikin kunnan ta aka saki wannan ihu, cikin sauri ta bude idonta, tajuya ta kalli Hajja taga bacci take ita bata farkaba, ko tantama batayi wannan ihun na Aisha ne, agogon Dakin ta kalla karfe uku saura, ahankali ta zuro qafafunta qasa, ta sakko daga gadon tafuto falo, zagaye falon takeyi ita bata nufi part din Shahaab ba, ita bata koma daki ta kwanta ba, tausayin yarinyar ne yake cinta Arai, Aisha yarinya ce qarama wadda ita kanta tasan cewa kafin ta goge ta'iya dauke nauyin Shahaab, Sai an dade, ganin de batada mafita yasa Takoma dakinta, ta wuce toilet ta dauro alwala tafara nafila tana sake roqon Allah, Allah yasa wannan al'amari na Aisha da Shahaab daya faru yasa yarinyar tasamu ciki a Daren yau(🤲🏻) Ko kadan Shahaab ya manta da Aisha yake tare, aiki yake yanda ya kamata, yanayin da yakeji yawuce yanda yake zato, zai iya rantsuwa bai ta6a jin dadi irin Wanda yakeji ba yanzu, shide yasan kuka da ihu ba al'adar sa bace, baiga dadin da mace zata jiyar dashi harya sashi yin ihu da Kuka ba, Amma gashi tashin farko qanqanuwar yarinya kamar Aisha tasa yana kuka wiwi da Idonsa,Sai surutai yake barkatai banda tarin kyaututtuka dayake mata cikin fitar hayyaci, Amma duk wannan abun dayake Aisha ko motsi batayi, asalima tariga ta suma, batasan inda kanta yake ba, lokacin dazai samu nutsuwa rirriqeta yayi kamar zai 6allata, fuskar Nan tasa tacika da hawaye, yasaki wani irin ihu Wanda yasa part din ya amsa, sannan yasake rirriqeta yakawo, lokaci daya yaji Kansa ya Sara, zazza6i me zafi yarufe shi,ahankali yasa hannu yasake rungume ta, kanta yake shafawa sababbin hawaye suna fita daga Idonsa, cikin sanyin murya Yace"Allah yayi miki Albarka Aisha, Allah Yacika miki burinki, Allah yasaki a aljanna,kinmin komai, kingama min komai a rayuwa, you're so so so sweet....bantaba jin gamsuwa irin tayau ba,daga yau sunanki me abun dadi, nagode nagode nagode" Yana jiran yaji tabashi amsa Sai yaji shiru, cikin sauri yaduba fuskarta, yana tatta6a jikinta yaji shiru babu motsi kamar matacciya, gabansa ne yayi wata irin faduwa, Kansa yasake sarawa akan ciwon dayake masa, duk da shidin likita ne kasa gane wa yayi shin mutuwa tayi ko suma,? Cikin sauri yatashi, yamaida gajeren wandonsa jikinsa, yadauko gorar ruwa yazuba mata, Amma shiru bata farkaba, tsoro ne ya kamashi kode mutuwar tayi? Cikin rawar jiki yasake zuba mata ruwan Amma ko motsi bata sake ba, gabansa yayi wata irin mummunar faduwa, yajanyota jikinsa yana magana kamar zararre, Adede lokacin aka kira sallar asuba, cikin sauri yad'auki wayarsa yakira mama, tana ganin kiransa tad'auki wayar, cikin tashin hankali yace"mama" Tace"na'am, yanaji muryarka wani iri kamar kana kuka" Saida yaja zuciya sannan yace"mama Aisha ce...." Cikin sauri tace"me tayi?" Hawaye ne yafuto daga Idonsa yace"tamutu mama,Nima kaina ciwo yake, zazza6i ya rufeni,inajin Nima mutuwa zanyi mama" Gaban mama yayanke yafadi, da qarfi tace"tamutu?" Hajja tayi firgigit tatashi daga bacci gabanta yana faduwa tana tunani waye yamutu? Cikin sauri mama tace"gani Nan Zuwa" sannan ta kashe wayar Hajja tace"Aysha lafiya?" Mama tace"inafa lafiya? Yakirani yana kuka Wai Aisha tamutu, Shima mutuwa zaiyi" Hajja tasaki salati Tace"A a,to tashi muje, karmu dauki zancen sa da wasa, tunda kikace yana kuka, inajin tacika, lokacin ta yariga yayi"(😭) Jikin mama yayi Sanyi kalau, tatashi suka nufi party din Shahaab, ko takan ruwan zafin bata biba, suna zuwa ko nocking basuyi ba suka shiga Dakin, ganinsa sukai zaune, ga Aisha akan cinyarsa, cikin sauri mama ta qarasa tafara tatta6a jikinta, Hajja ta tsaya daga Gefe gabanta banda faduwa babu abinda yake, mama ta kalli Hajja tace"inajin Asbiti zamu tafi" Cikin sauri Hajja tace"bari mugani" Jikinta ta tatta6a taji zafi sosai, ta kalli Mama tace"nafi tunanin doguwar suma tayi, ai zuciyarta tana bugawa kadan, muje dakinta Sai azuba mata ruwa" Mama ta kalli Shahaab tace"toka Dena kukan mana,ni ban ta6a ganin likita haka ba, daukota muje dakinta" Cikin sauri ya goge Hawayen Idonsa ya dauke ta Kai tsaye d'akin ta suka nufa, toilet mama ta wuce ta kunna ruwan zafi, ta karbeta sannan tace masa yaje yayi wanka Shima, badan yaso ba, haka yafita zuwa dakinsa. Saida ruwan yataru dayawa suka Sakata aciki, Hajja tafara yimata wasu Yan dabaru, nanda Nan kuwa tafarka, wani irin kuka tasaki idonta a rufe Sai surutu take. "nacema banaso.... Zaka kashe ni, Hajja nashiga uku zan mutu, Ummah kizo, zai kasheni" Mama ta Girgiza kanta cikin tausayi, ta kalli Hajja tace"bata hayyacinta fa, Bari nakira doctor Sai tazo ta dubata" Hajja tace"to ba damuwa "ta qarasa wajan ta tafara yimata magana, ahankali ta bude idonta, ganin Hajja atare da'ita yasa tasake fashewa da Kuka, Hajja ta gasa mata jikin Nata, sannan ta kamota suka futo Sai bubbuda qafa take tana runtse idonta, agefen gadon ta zauna Hajja tadauko mata Kaya tasaka, tace"to tashi kiyi sallah mesunan qawa, Nima Bari inshiga bayin naki inyi Alwala ko sallah banyi ba gashi gari harya fara haske, Kidena kukan ya'isa haka, Aysha tatafi tad'auki waya takira miki likita" Cikin sauri tarirriqe Hajja, ta Fashe da Kuka tace"Hajja nide mutafi, Dan Allah ki daukeni mubar gidannan, Allah idan kika barni zai kasheni,ni tsoransa nakeji, bazan zauna ba" Hajja tace"ikon Allah, yau naji yarinya..., to waye yafada miki da Daren farkon sauqi gareshi? Haka zakiyi haquri kidinga bashi haqqin sa harki saba" Tanajin abinda Hajja tafada tasake rushewa da kuka Adede lokacin mama tadawo d'akin, zama tayi akan gadon tafara lallashin Aisha, Hajja Kuma tashige toilet ta dauro alwala tafara gabatar da sallah, saida ta idar ta kalli Mama tace"batayi sallah bafa,tatashi tayi sallah saita kwanta kafin likitar tazo" Mama ta dagata tsaye tace"hau sallaya kiyi sallah " Daqyar tatashi ta zauna akan sallayar tayi sallar a zaune, tana idarwa taji bazata iya tafiya ba, da rarrafe tafara tahowa wajan gadon, cikin tausayi sukayi saurin riqeta, mama tana kallon sallayar taga ta6aci da jini, runtse idonta tayi, wanne irin aiki Yaron Nan yayiwa Aisha ne?(🤔) Sallayar ta dauke, tasake dubo mata wani kayan ta sauya mata, Adede lokacin Dr. Tashigo Dakin tareda Shahaab, babbar mace ce sosai kana ganin ta kasan itama uwa ce, yana Sanye cikin fara qal din jallabiya, fuskarsa Sai wani shinning take yasake yin wani irin fresh, Aisha tana kallon sa tayi gaggawar runtse idonta, tasake kama hannun mama ta riqe gam(😲😂) Dr. Tace"hajiya mama kudan bamu waje Bari induba ta" Cikin sauri mama tace"to Dr." Tatashi zata fita taji Aisha ta riqeta gam, daqyar ta qwace hannunta suka futo daga d'akin, falon suka koma suka zauna, Shima futowa yayi daga d'akin yaja musu qofar, wajan su mama yanufa saide kafin ya qarasa jiri ya debeshi, Kansa ya Sara, yana dora hannunsa akansa yayi baya zai fadi, cikin sauri Hajja da mama sukai Kansa suna fadin"subhanallahi...." Adede lokacin Dr. Ta bude kofar Dakin tafuto, tana ganin su a wannan hali tace"Dama bashida lafiya ne Shima?" Mama tace"eh yana zazza6i da ciwon kai" Cikin sauri tace"tokushigo dashi Dakin Sai nayi masa allura" Babu musu suka kamoshi, suka shigo Dakin, kan gadon suka kwantar dashi, Aisha Kuma tana Gefe tana share hawaye domin tuno bayanin da likitan tayi mata, allurai ta had'a tayi wa Shahaab a hannu, sannan tabawa mama magani tace"gashi abashi yasha kafin bacci yadaukeshi, nayi masa da allurar bacci, insha Allah idan yatashi daga baccin zaiji relief" Mama ta Kar6a tace"to ita Kuma Aishan fa?" Dr. Tace"dinki za'ayi mata Hajiya,zanje in Dauko kayaiya ki in dawo yanzu" Hajja ta zaro ido😳 Tace"dinki likita?wallahi har kinsa natuno da jikar jummai ita Kuma a haihuwa saida akayi mata dinki har guda hudu,ashe ni abun yana Nan zuwa kan jikata" Tajuya ta kalli Aisha tace"me sunan qawa kekuma tun a Daren farko za'a miki dinki, idan kika haihu Kuma inajin Sai abunda Hali yayi"(😂) Litafin kudi ne, idan kika karanta baki biyaba nabarki keda ALLAH 0164549488 Amina muhammad GTbank 300 tareda shedar biya ta wannan number 08033300034 Amnah El Yaqoub✍🏻 Page 50 Ita kad'ai taci gaba da cewa"shiyasa ba'aso kayiwa mutum surutu idan wani abu yasame shi,kawai kayi masa addu'ah, Nan muka zauna nida Hadiza muna zancen wannan jika ta jummai, ashe ashe muma abu yana Nan tafe awajanmu mubama a haihuwar bane Karon farko ne"(😂) Dr. Tayi murmushi ta juya tafice daga d'akin, mama ta kalleta tace"Allah ya shiryeki Aysha, Dan Allah Kidena tsorata min takwara ta" Tajuya ta kalli Aisha da kanta ke qasa tana share hawaye tace"kidena kuka Aisha, dakaina zan samo bulala saina Zane Shahaab tunda yasaki kuka, dinkin Kuma babu zafi yanzu zata miki tunda wajan bai dade sosai ba, kiyi shiru kinji?" Ta qarasa zancen cikin sigar lallashi, sannan tafice zuwa kitchen din part din, tea tahado musu Mai kauri, tabawa Aisha Nata, sannan Tajuya ta kalli Shahaab da Idonsa yake rufe kunya ta hanashi budewa, ga zazza6in dayake ji sosai, ajiye cup din tayi ta kamashi yatashi zaune, sannan tabashi maganin yasha, tasa shi ya shanye sauran tea din ya kwanta, Nan da Nan kuwa Idonsa yafara rufewa, ahankali yake kallon Aisha wadda taqi Kallonsa kokadan, tausayinta ya kamashi, yanaso yajata jikinsa ya lallashe ta Amma Kuma babu damar hakan, ahankali ahankali yafara ganin dishi dishi, itama yafara ganin ta haka harde baccin yayi nasarar daukar sa. Sosai taji dadin tea din,bata dade da gama shaba Dr. Tadawo tayi mata allura sannan tafara yimata dinkin, su Hajja suna zaune afalon har Dr. Tagama tafuto tayi musu bayanin yanda zasu bata Yan kulawa, sannan tayi musu sallama tatafi, Dakin suka wuce mama ta dora kan Aishan akan cinyarta tana mata sannu, Hajja kuwa Shahaab ta kalla dake bacci tace"Angama aiki Sai bacci kuma"(😂🤭) Mama da dariya ta kamata ta kalli Aisha taga har tayi bacci sakamakon allurar da aka mata, ta kwantar da ita akan gadon sannan taja hannun Hajja suka futo suka rufe musu d'akin. Kai tsaye part din mama suka wuce, zama sukai a kujera suna firar duniya, mama takira masu aikinta tasasu su dafawa su Aisha farfesu da Dan girki medan ruwa ruwa, cikin ladabi suka juya. Mama tayi ajiyar zuciya tace"natausayawa wannan yarinya" Hajja tace"toya zatayi,? Girman kenan ai, kowa da haka yafara" Sai wajan karfe daya da rabi sannan suka kawowa mama abincin, tashi tayi da kanta tad'auki abincin nasu Takoma part din nasu, tana zuwa Dakin taga har lokacin bacci suke gaba d'ayansu, abincin ta ajiye musu sannan taja Bargo ta rufesu, ta juya tafice daga d'akin (na kudi ne, idan kika karanta baki biyaba nabarki keda ALLAH) ****** Abba ya kalli jabir dayake kwance cikin daya daga cikin kujerun dasuka mamaye Babban falon nasu yana daddanna waya "jabir kagama shirya komai da komai deko? Naga tun dazu bakada aikin komai Sai danna waya" Kallan Abbansu yayi "Abba nagama hada komai, anjima ma zanje gidan, yacemin muhadu yau, Kuma Dama inaso inyi wa su Hajja sallama da takwarar mama" Ummah tace"idan katashi tafiya akwai leda tana nan agefen gado na ka dauka katafi mata dashi" Kansa yadaga mata, sannan yaci gaba da danna wayarsa. ****** Sun dauki tsawon lokaci suna bacci, Sai Bayan sallar azahar Shahaab yafarka, ahankali yake bude Idonsa harya bude shi gaba daya,kokadan bayajin ciwon komai yanzu, kalau yake jin shi kamar yanda yake Ada,wata irin miqa yayi tajin dadi, sannan yafara murza idanunsa da hannunsa, Idonsa yabude ras akanta,fuskarta tayi mutuqar kyau yayinda take baccin, Amma tad'an kumbura kadan Kuma taqara fari, Idonsa ne ya sauka akan lips dinta Wanda sukayi jajir saboda tsabar tsotsar su Dayayi, Daren su na jiya yafado masa, ahankali ya Lumshe Idonsa, wani irin farinciki yana sake wanzuwa akan fuskar sa, bude Idonsa yayi, yasake kallon ta tareda furta sunan"me abun dadi" akan lips dinsa (🙈🤭) Tashi yayi, ya matsa kusa da ita sannan yad'ora hannunsa akan fuskarta yana shafawa ahankali, saide kokadan Aisha bata farka ba, murmushi yasaki ya dauketa cimak yad'ora ta akan qirjinsa, sannan yasake Jan bargon yarufesu, gashinta daya Dan sakko jikinsa yasa hannu ya tattare mata shi waje daya,sannan cikin jin dadi yafara yimata kitso guda daya da gashin, saiyayi Sai yaga bai iyaba, ya warware shi yasake yin wani, daqyar yayi wani guda daya, Amma ko jimawa bai yiba dakansa yafara kuncewa kasancewar gashin da tsantsi, cikin baccin ta taji kamar Ana ta6a mata gashi, ahankali tayi wata ajiyar zuciya, sannan tafara yunkurin tashi, gabanta ne yayi wata irin muguwar faduwa jinta a jikin mutum Wanda tasan ba kowa bane face Shahaab, lokaci daya ta qame ko numfashin kirki takasa, kallon ta yayi cikin sigar rad'a yace"me abun dadi kin tashi?" Wata irin kunya ce ta kamata sakamakon jin wani irin suna daya kirata dashi,agefe daya Kuma wani irin tsoransa takeji kamar wanda zai yankata, kokadan batayi yunkurin hada ido dashi ba, ta d'aga masa Kai alamun eh tatashi, sannan tafara kokarin sauka daga Kansa, cikin sauri yasaka hannayensa yaqara rungume ta tsam tsam, sannan ya mirgina da'ita Takoma kan katifar yanda zaiji dadin ganin ta, ido yazuba mata kamar yau ne Karon farko daya fara ganin ta, sannan ya janye gashinta daya Dan rufe mata ido yafara kawo fuskarsa dab da Tata zaiyi kissing dinta, ganin abinda yake shirin yi ne yasa tafara Girgiza masa Kai, lokaci daya hawaye yazubo daga idonta, cikin tashin hankali yace"subhanallah, menene yafaru?kohar yanzu ciwon ne?" Kamar Dama jira take, lokaci daya ta Fashe masa da wani irin kuka,harda shashsheka, cikin kuka tace"karkayi,wallahi idan kasake yi mutuwa zanyi, ni wallahi nagaji da auren,da nasan haka akeji ma wallahi nida bazanyi auren ba har abada" Wata irin dariya ce take son qwace masa, Amma saiya danne, yasake janta jikinsa yace"kiyi haquri, bazan sake ba,Nima kaina banyi niyar yimiki komai ba,Kinsan da inada mata, Kuma dole zan dinga rage zafi awajanta,to yanzu kinga tun kafin aurenmu dake matar tawa tafice, Kuma tun kafin murabu nida ita,mun samu Sa6ani harta Kai ga bata Bani haqqi na,maaamah ni mabuqaci ne, nasan kaina, bazan iya barin mata ta ban nemeta ba har tsawon kwana uku, idan hakan ta kasance kuwa to ninasan wahalar danake Sha,abunnan najima banyi ba, Kuma yanzu nasame ki,kwata kwata Rasa control din komai nayi,dadin kine yayi miki yawa maaamah, shiyasa ban saurara miki ba, nayi tunanin ma mutuwa kikai, shiyasa nakira mama nafada mata,saboda arikice nake Alokacin bazan iya dubaki sosai ba, Amma da nasan ba mutuwa kikai ba, Toda dakaina zan gyara ki, in dinkeki, sannan Kuma mudora daga inda muka tsaya" Yaqare maganar cikin sigar tsokana, Aisha kuwa tanajin furucin sa tasake sakin wani irin kuka tace"wallahi gida zan tafi,bazan zauna ka kasheni ba" Tana fadar haka tafara qoqarin tashi, cikin sauri yaruqota tafara fizge fizge, daqyar ya matse ta ajikinsa, bargon yasake rufa musu sannan yafara yimata rad'a akunne"wasafa nake miki,bazan sake ba, ki kwantar da Hankalinki Nima bazan sake yimiki wannan abun ba,idan kika mutu ainima mutuwar zanyi, kisaki jikinki bazan miki komai ba kinji?" Cikin sauri tace"kayi alqawari?" Cikin ransa yace"yarinya me wayo"(😂) Murmushi yasaki a fili, sannan yace"baki yarda da maganar Dana fada miki ba?" Hawaye ta goge sannan tace"jiyama haka kace bazaka min komai ba" Ysce"jiya aita Riga ta wuce,yanzu muke magana, ki kwantar da Hankalinki, bazanyi miki komai ba, maaamah Kin gamamin komai a rayuwa, kin kawomin budurcin ki lafiya,Allah yabar min ke a matsayin mata ta har abada duniya da lahira,Dame kike so na saka miki?mekikeso a rayuwar Nan fadamin kinji?" Shiru tayi bata bashi amsa ba,menene Kuma abun kyauta abunda yariga yabada sadaki? Jin tayi shiru yasa yace"kiyi magana mana, kinji me abun dadi nahhh" Yaqare maganar cikin wani irin Salo Wanda saida hakan yasa taji wani irin yanayi ya shigeta, cikin shagwa6a tace"nide kadena fadamin sunan Nan, banaso" Murmushi yayi yace"aikinada abun dadin ne,dole in fada,daga yanzu Sai abinda kikace za'ayi, Sai abinda kike so Nima zanyi,hakan yamiki?" Ahankali ta daga masa kanta alamun eh, murmushi yasake yi sannan yace"ina lura dakefa bakya kallo na, meyasa bazaki kalleni ba?" Tunowa da Daren jiya tayi, yanda yazage babu Kaya yana mata kuka, saita sake jin wata kunyar tasake kamata, tayaya zata Iya hada ido dashi? Murmushi tayi sannan takai masa duka kan faffadan qirjinsa, cikin dariya yariqe hannunta sannan yace"maamah kina sona?" Cikin sauri ta daga masa kanta, ajiyar zuciya yasauke sannan yace"zaki iya zama da Wanda baya haihuwa?" Jikinta ne yayi Sanyi,taji wani irin tausayin sa ya kamata, batayi kuskuren hada ido dashi ba,cikin sanyin jiki tace"haihuwa aita Allah ce,Wanda ya basu haihuwar bawai yafi sonsu a kanka bane,idan kaduba rayuwar ka kaima yayi ma ni'imomi dayawa Wanda acikin mutane bila'adadin ba kowa yayiwa wannan ni'imomi ba, idan Allah yabawa wasu haihuwa kaikuma bai baka ba, ai kaima yabaka kudi, Kuma ba wayonka ne yasa yabaka kudin ba,akwai Kuma Wanda Allah yake hada musu gaba daya biyun, kaima Kuma insha Allah watarana zai baka, duk yanayin da Bawa ya tsinci Kansa aciki saiya godewa ubangijinsa, Sai kaga Allah yaqara masa" Wata irin runguma yayi mata, ahankali hawaye ya sakko daga Idonsa, cikin sauri yasaka hannunsa ya goge Dan karta Gani, sosai ya matse ta ajikinsa yana jin wani irin dadi a ransa,koda yaushe tunanin Aisha daban yake,Bai saba jin irin wannan kalaman awajan munirat ba, Sai yaji nutsuwa tasake shigar sa, koba komai ya auri wacce zata dinga tunatar dashi Allah ne maiyin komai, idan yaso Shima zai bashi haihuwar, cikin jin dadi yace"inasonki maaamah" Ahankali itama tasaka hannu tasake rungume shi tace"inasonka Baby" Cikin sauri ya kalleta yace"da gaske ni Babynki ne?" Daga masa Kai tayi cikeda kunya, murmushi yasaki, kafin yace wani abu yaji tasaka masa hannunta a'inda dimples dinsa suka lotsa, tayi hakanne Dan ya saki ransa, yadena wannan damuwar saboda batun haihuwa, saide abinda bata Sani ba shine hakan datayi yayi masa dadi sosai, harya manta din Kuma, cikin farinciki yace"kinason dimples ne?" Kai tsaye tace"banaso,shi Kansa me dimples din nakeso" Wani irin dadi ne yasake kamashi, cikin shagwa6a yace"maamah" Wani iri taji ajikinta, batasan lokacin data rungume shi ba,bargon yadan janye kadan, kansu yafuto waje, yasaka hannunsa akan tsayaiyun breast dinta yace"tunda kince ni Babynki ne toki Bani wannan abun nasha" Yaqare maganar yana matsa mata su ahankali, cikin shagwa6ar da ita kanta batasan ta'iya taba tace"nide Uncle kabari, akwai zafi fa, Allah banaso ni" Cikin shagwa6a Shima yace"niba wani uncle bakece kikace nine Babynki ba" Bakinta ta turo gaba tace"nide kabari Allah kuwa" Cikin sigar lallashi yace"nacefa bazan miki dayan ba,Kuma wannan dinma baza'a ji tausayi na abani ba?" Bakinta tasake turowa gaba sannan tace"kata6a, Amma Dan qadan" Cikin jin dadi yace"A a,ni bazan ta6a ba, kibawa Babynki dakanki yasha" Mata da Miji Sai Allah,dadin soyaiya dakuma dadin zafafan kalaman Shahaab yasa ta manta da azabar datasha Daren jiya, ahankali taciro masa guda daya, sannan ta nufi bakinsa dashi, dadi ne yasa Shahaab ya Lumshe Idonsa, yana jin yanda take goga masa nipple din akan lips dinsa, cikin sauri yakama sannan yafara tsotsa ahankali, koda wasa baiyi gigin Sha da zafi ba, ahankali yake Sha saboda tasaki ranta tasaki jikinta dashi tadena tsoronsa, yanda yake Sha ahankali Kuma cikin Salo yasa ta Lumshe idonta, taja bargon tarufe musu kansu duka, sannan ta dora hannunta akan cikakkiyar sumar Kansa me laushi tana shafawa,hakan datayi ba qaramin dadi yayi wa Shahaab ba, sosai takejin dadin abinda yake mata, inda ace iya wasan kadai zai dinga yimata ai bazata qiba, dadi ne yasa Dakanta tacire masa Wanda yake tsotsan ta maida masa dayan cikin bakinsa, kusan haukacewa Shahaab yaso yi,gade yar qaramar yarinya tana neman gigitashi da salonta, yanda take saka masa boobs din cikin bakinsa kamar wani Babynta Dan jariri datake shayarwa, cikin dabara yaja hannunta yad'ora a Qasan mararsa, lokaci daya ta tsorata jin hannunta akan abinda bata ta6a tsammani ba, Amma Kuma duk da ta tsorata hakan baisa ta janye hannunta ba,Amma Kuma haka ta tsaya bata ta6uka masa komai, Sai shi dakansa yariqe hannunta yana gwada mata yanda zatayi, babu musu ta dinga yimasa, acewarta Gara ta kwana tana masa haka inde bazai nemeta ba, bata fatan ace tasake jin azabar dataji Daren jiya. Suna tsaka Dajin dadi Wayarsa tad'auki qara, cikin sauri Aisha tadena abinda take masa, kamar zaiyi kuka haka yafuto da hannunsa daga cikin Bargo yad'auki wayar, cikin yanayin buqata yace"kai ya akayi?" Daga d'ayan bangaren Ramadan yace"yau bamu gaisa ba, Kuma baka shigo office ba, mutane sunata kawomin gudunmawa nabaka idan ka shigo, shiru shiru Kuma baka shigo ba" Hannun Aisha yasake maida wa inda yake da,yayi mata alama dataci gaba da abinda take, ahankali taci gaba dayi masa wasan, cikin jin dadi yace"wallahi bansamu shigowa ba yau" Ramadan yace"ai kamar ma bacci kake, Yaya batun aikin da muka fara last week? Yaushe zamu qarasa shi?" Idonsa a Lumshe yace"sai yanda hali yayi Ramadan"(🙊😲😄) Aisha datake jinsu batasan lokacin data saki murmushi ba,cikin salon tsokana tasake damqe abinda ke hannunta, lokaci daya Shahaab yabude baki zai saki ihu, cikin sauri ta rufe masa bakinsa sannan ta kashe wayar, Ramadan dayake jiyo alamun motsi ta cikin wayar yayi murmushi tareda saka wayarsa cikin aljihunsa, Shahaab da aiki Amma yau shine yake cewa Sai abinda Hali yayi?(🤔) Lalle ya yarda yanzu ne abokinsa yayi aure. Shahaab kuwa hannunta yacire daga bakinsa, cikin fitar hayyaci yace"please maaamah cigaba karki Dena kinji" Cikin sauri tace"bamuyi sallah bafa" Hannunta yasake riqewa yace"karki Dena, nakusa, yanzu zamuyi ai" Babu yanda ta'ita haka taci gaba da abinda take, saide duk da hakan, Bai gamsheshi ba saida yasake dora hannunsa Saman Nata suka dinga yi tare, sannan ne yadan samu nutsuwa, yajata jikinsa ya rungume ta, cikin jin dadi yake tunani a ransa ta yanda zai dinga yimata dabara yana samun abinda yakeso, yariga yasan lagwanta, daga Gani tana son yadinga sucking breast dinta, Kuma zai dinga Binta ta wannan salon tana masa abinda yake buqata Shima,har yasamu ta saba, bayanta yake shafawa kamar wata baby, saida yaji yadanji qarfi ajikinsa, sannan ya dauketa suka wuce toilet, saida yasake gasata sosai a ruwan dumi, sannan yayi mata wanka, Shima yazage yace lalle Saitayi masa, haka ta dinga kawar da kanta Dan dolenta tayi masa wankan, yadauko ta ahannunsa suka dawo Dakin, kayanta yabata tasaka sannan Shima yakoma dakinsa yasauya Kaya yadawo Dakin suka gabatar da sallar, karatun alqur'ani sukayi har aka kira sallar la'asar kasancewar Dama lokacin ta yakusa, Bayan sun gabatar da sallar yad'ora ta kan cinyarsa sannan yafara bata farfesun itama tana bashi, saida suka ci suka qoshi, sannan ya dauketa kamar baby sukayi kitchen yadauko musu madara, sannan suka dawo falo ya kunna musu kallo yasaka ta cikin jikinsa yana bata madarar, saiya bata Tasha, sannan shima yasha, mamaki ya kamata tace"bakai kace baka Shan madarar ba?" Murmushi yayi yace"ai yanzu na rage ta jikina, kinga saina qara wata" (🙈) Kunya ce ta kamata, cikin sauri ta cusa kanta cikin qirjinsa, bude kofar falon akayi aka shigo, mamaki yakama Shahaab waye zai shigo musu part babu neman izni babu komai, idan Kuma yana wani abu da matarsa nefa? Kujera ma badan zama kadai yasaka musu afalon ba,akan kujera ma akwai style din dazai dinga yi da matarsa shiyasa yake jin dadi duk yanda yake da mama bata ta6a zuwa part dinsa saida dalili, duk wani abu datake nema awajansa saide ta masa waya yazo inda take, lokaci daya ransa yayi baqiqqirin, atare suka juya shida Aisha suka kalli kofar,ganin wacce take tsaye a kofar ne yasa Aisha tayi saurin tashi daga jikinsa, Shikuwa cikin 6acin rai yajata yamaidata jikinsa, kanta ta Girgiza tayi kasa da murya tace"Anty munirat cefa...." Tsaki yasaki cikin 6acin rai yasake maida ta jikinsa ya rungume ta sannan yace"sai me? Tamiki sallama ne dazata shigo?" Ganin yanda ransa ya6aci, Sai kwarjinin sa ya kamata, babu musu ta kwantar da kanta akan qirjinsa, batareda yasake kallon munirat ba yaci gaba da Bawa Aisha madarar Baqin ciki ne yakama munirat Taji kamar tad'auki wuqa ta caka wa Aisha,tasake kallon yanda Aisha ta dora kanta akan qirjinsa, tasaki tsaki, Shahaab kuwa uffan bece mata ba, danya sake tura mata haushi yasa ya ajiye madarar datake hannunsa, sannan yatashi tsaye yace"muje daki ki kwanta kihuta,gaba daya yau baki samu hutu ba"(😲) Aisha ta kalleshi da tsananin mamaki, dama maza ma sun iya kissa?(🤔😂) Shahaab da yaga ta zuba masa ido yace"kina kallo na konayi qarya ne?gaba daya kin hanamu bacci da rakin Nan naki kamar Ina yankaki" Kasa magana Aisha tayi, domin kuwa gaba daya maganganun sa sun sata a shakku, tabbas da munirat yake, inba hakaba itada ta suma Ina taga ta kuka? Takawa tafarayi ahankali tana bubbuda qafa har suka kusa shigewa daki, sannan ne Shahaab yasaka hannunsa ya dauketa cimak Sai cikin dakinsa. Suna shiga munirat ta dora hannunta aka tasaki kuka tareda tsugunna wa awajan, saida Tasha kukan ta sosai, sannan ta wuce tsohon dakinta tad'auki gaba daya kayaiyakinta da tasan tabari a gidan, sannan tafice daga gidan cikin qunan zuciya. Cikin Salo da dabara irinna mata Aisha tasa Shahaab ya manta da zuwan munirat, haka suka dinga Bawa junansu kulawa har dare, Kuma har lokacin mama da Hajja basu dawo ba, karfe Tara na dare jabir yatashi zai tafi gida Bayan yagama sallama dasu mama, kasancewar da sassafe zaibi jirgi yakoma makaranta, mama tabashi abincin su Aisha yakai musu tunda zai shiga suyi sallama. Lokacin dayazo part din baiyi gigin shiga ba, saiya kira wayar Shahaab, saida suka gaisa yafada masa yana waje, sannan yace yashigo mana, yana shiga kuwa ya gansu afalo a zaune, waya ce ahannunsa yana nuna mata photuna, abincin ya ajiye musu sannan yace"gashi inji mama" Cikin sauri ta d'ago ta Kalle shi tace"Hajja tana nan?" Yace"tana can suna kallo,Nima gobe zan tafi" Shahaab yace"bazaka tsaya ka qara mana kwana biyu ba?" Murmushi yayi yace"ai karatu yanata wuceni uncle" Cikin gamsuwa yace"Eh hakane Kuma, to Allah yakaimu goben,zan tura ma saqo ta account dinka ko akwai abubuwan dazaka siya katafi dasu, idan kagama shirya wa Kuma goben saikamin waya muje mu rakaka Airport" Cikin ladabi yace"to Uncle nagode, Allah yasaka da alkhairi yaqara budi" Yajuya ya kalli Aisha yace"gashi inji Ummah tace nakawo miki" Kar6ar ledar tayi tace"to kace mata nagode zan kirata ma anjima" Amsa mata yayi, sannan yayi musu sallama yatafi, yana tafiya Shahaab yace"kinga guraren ai ko? Wanne ne yafi birgeki?" Saida ta danyi Jim sannan ta nuna masa wani tace"wannan" Murmushi yayi yace"Dubai din kenan,Nima Dama Nan nayi mana sha'awar zuwa,kawai saimu wuce din tunda kema kinaso, idan akwai isasshen lokaci Saimu biya ta Doha, (Qatar)" Cikin jin dadi ta matsa kusa dashi sannan ta manna masa kiss a kumatunsa, cikin jin dadi yaci gaba da nuna mata wajajan birgewa yana mata alqawari Kuma idan sukaje zai kaita taga wajan. Washe gari sassafe suka tashi, yasaka ta cikin ruwan dumi, sosai taji dadin jikinta, Hankalinta kwance tasaki jikinta dashi, saida taga yashiga wanka sannan tayi sauri ta shirya tafuto masa da kayan sakawa, yana futowa Shima ya shirya suka wuce part din mama hannunsa cikin Nata, ma'aikatan gidan Sai gaida su suke yi, har suka shiga part din mama hannunsa yana cikin Nata, a lokacin suna breakfast itada Hajja, Aisha de kunya ce tad'an kamata, Amma Shikuwa Shahaab ko ajikinsa, zama sukai Bayan sun gaida su, Hajja ta kalli Aisha tace"oh mesunan qawa jiya Kuma saina ji ki shiru kinyi luqus awajan mijinki, keda nake jiranki kizo mutafi" Mama tayi murmushi tace"ina zakuje?" Hajja tace"yo tacemin in dauketa mutafi gida, ita bazata zauna ba,kashe ta zaiyi" Cikin sauri Shahaab yayi qasa da Kansa, wannan zilala ta Hajja dame tayi kama?domin ya katse zancen yayi gyaran murya yace"mama zamuje muraka jabir Airport, daga Nan Kuma zamuje ayi mata passport" Mama tayi murmushi tace"to Allah yadawo daku lafiya" Babu musu yace"Amin" Ko gama cin abincin basuyi ba yakama hannunta suka tashi, yasan cewa idan Zaman nasu yayi tsawo to babu makawa Sai Hajja tasa yaji kunyar dabai ta6a jiba, suna tafiya gidansu Ummah sukaje, Bayan sun gaisa suka futo waje shida Abba, jabir ma yaja jakarsa yafuto, daga ita Sai Ummah ne yarage a gidan Ummah tace"jabir yakawo miki magani ko?" Tace"eh yakawo min,Amma banma dubashi ba, na menene Ummah?" Tace"ki hada da madara Kisha" Idonta ne yayi qwalqwal kamar zatayi kuka, cikin rawar murya tace"Ummah tsoro nakeji," tana fadar haka hawaye yazubo daga idonta Ummah ta zuba mata ido tana nazarin kalamanta, tasan Dama Sai ahankali, duk Wanda yaga Mahmud Wakili ai yasan cewa cikakken namiji ne Wanda ya amsa sunansa namiji, ajiyar zuciya tasauke tace"bakya shiga ruwan zafi ne?" Cikin sauri tace"yana hadamin" Ummah tace"tokiyi haquri mana, kicire tsoron abun aranki, muddin Zaki saka tsoro to kuwa kin dinga jin zafi kenan, Amma idan kikasa abun aranki Kuma kika cire tsoro to zakiji Dan sauqi, Kuma idan bakya shan maganin tayaya Zaki ji dadin jikinki harki samu wadatacciyar ni'ima? Banason shirme,saboda kin samu yana sonki ne shiyasa har kike gudun maganin, inda watace bazata qiba tunda ita tasan metake ji ajikinta, karki ga yana sonki kidinga hanashi haqqin sa, kija mijinki ajikinki daga wahalar ai babu mutuwa ko?kinga de babu abinda zaki fadawa matarsa, Amma soyaiya tasa yanzu kedin yake Gani a'idonsa, kicire tsoro kidinga bashi haqqin sa tunda har kika samu yana hada miki ruwan zafi to ai da sauqi, idan wani nema bazai hada miki ruwan zafin ba, kina Gani yanda ya karbi takardun babanku Wanda yadade dacire rai da samun aiki tun kafin a haifeki Amma gashi shi sama taka ya dauke shi yabashi office a lagos" Cikin sauri ta d'ago ta kalli Ummah, saboda batasan da wannan maganar ba, Ummah tace"sosai kuwa,ga gida yabamu, ga qaninki yana karatu, ga company yabaki, yanzu haka gidanmu na jigawa Abbanki yatura kudin damuka Dan sassamu an rushe shi Ana na cement, duk lokacin da mukaje ganin gida zamu zauna acikin kyakykyawan muhalli, to mutumin da yayi mana wannan karamcin menene ba zamuyi masa ba?,babu abinda zaki saka masa dashi Sai biyaiya ki Kuma bashi abinda yakeso, wuya ai bata kisa, kiyi hakuri kizama jajirtacciya awajan mijinki" Jikin Aisha yayi Sanyi kalau,itama saita ji tausayinsa ya kamata, haka suka futo daga gidan maganganun Ummah sunata mata yawo a qwaqwalwa, da'ita da Abba da jabir dakuma shi suka tafi Airport din, banda Ummah, a hanya taga Sai hira suke shida Abba kamar ba surukai ba, saida jirginsu jabir yatashi sannan suka dawo, suna ajiye Abba agida Kai tsaye wajan passport din suka wuce akayi mata sannan suka nufi gida, part din mama suka wuce, Aisha taji dadin zamansu a part din mama Amma haka yadinga zungurinta da hannu yana mata alama tatashi su tafi, hakan yasa cikin dabara ta cewa su mama zataje daki tayi bacci, tana tafiya Shima yatashi yabita.(😍) Har tsawon kwana biyar Shahaab bai nemi Aisha ba, Kuma tana lura dashi tasan yanaso, zuwa wannan lokacin har ta warke sosai babu abinda yake damunta yanzu,yanda yake kokarin kawarda Kansa akanta yasa tasake jin tausayin sa, yau wuni tayi tana shirya musu kayan su, kasancewar gobe zasu wuce, duk wani abubuwan da tasan zata nema Wanda ya danganci kayan mata saida tasaka su cikin Jakarta, har zuwa yanzu Kuma tunda tazo gidan bataga yafita wajan aiki ba, Sai jiya ne taji yana fadawa Ramadan ta waya cewa yad'auki hutu yanaso yadan huta kwana biyu, da daddare suna zaune suna kallo itace da kanta ta dinga tsokano shi, tasan tunda yayi mata wannan haqurin ai yayi kokari, shida yace bazai iya kwana uku ba, saida taji yafita a hayyacinsa sannan ta zame jikinta, kamar zaiyi kuka haka ya kalleta yace"bakyaso ko?" Tace"kaine de bakaso" Cikin sauri yace"nasan bakya so, banason takura miki ne shiyasa" Ahankali ta Girgiza masa kanta tace"ai haqqin ka ne,ko inaso ko banaso dole zan baka haqqinka, kayi yanda kakeso Dani, ainidin takace" ta qarasa maganar cikin faduwar gaba, kawai de daure wa takeyi, tasan zatasha wahala sosai, yanzu ma da zai ta6a qirjinta da zaiji yanda gabanta yake tsananin faduwa. Ajiyar zuciya yasauke yace"kin yarda inyi?Tome kike so nabaki?" Cikin tsananin mamaki ta kalleshi, tarasa gane meyasa yake mata haka, haka wancen Karon ma yake tambayar ta mezai bata? Yanzu danya kusanceta saiya bata wani abu? Cikin mamaki tace"kamarya?" Batare da tunanin komai ba yace"saboda abinda zaki Bani,kinsan wasu matan zasu fadi abinda suke so, ke mekikeso nabaki?" Yana fadar haka tad'auki haske, idan ta fahimci maganar sa yanaso yace mata munirat saita nemi wani abu awajansa sannan zata yarda ya kusance ta, kawai bazai futo fili yafada mata bane, Kuma shi ahakan yake haqurin zama da'ita Bayan yasan cewa abinda take neman kudin dashi haqqin sa ne, ajiyar zuciya ta sauke tace"kadena fadamin wannan maganar banajin dadi,duk lokacin dakake buqata ta kawai kazo, inde lafiya ta kalau zan barka kayi duk abinda kakeso, haqqinka nefa, kariga kabada sadaki to meyasa zan hanaka saboda abun duniya?" Shiru Shahaab yayi kamar ta doka masa sanda, tabbas yanzu ne yasan yayi aure, abaya munirat zalintarsa take yanda taso, Bai taba Bawa Aisha damar daukar kudinsa ba koda kuwa aqasan Dakin ya ajiye, Kuma bata taba dauka ba, Amma ita waccan shida Kansa zai ce mata ta bude ta d'auka, daga qarshe ga abunda yafaru, ajiyar zuciya yasauke tace"Allah yayi miki Albarka maamah,daga yau duk abinda kike so inde kinsan nawane Ina Nan Bana Nan to inde kina buqata ki dauka ko menene" Fuskarsa ta riqe da hannayenta biyu, cikin sauri tahade bakinsu waje daya, dama akusa yake, cikin sauri Shima yafara nuna mata yanda yayi kewarta, lokacin dazai shige ta runtse idonta tayi, lokaci daya numfashinta yake kokarin barin jikinta, Amma data tuno nasihar da Ummah tayi mata, saita saki jikinta, tabashi Dama yafara jin dadinsa, tana jinsa yana kuka yana sambatun sa cikin fitar hayyaci, Amma ita de babu wani dadi datake ji Sai wuya, Amma Kuma nayau din bai Kai na wancen Karon zafi ba, sannan Kuma Shima Kansa ogan ahankali yake tafiyar da'ita, yadade yana abu daya sannan yasamu nutsuwa, Bayan ya huta yafara kokarin daukar ta zasu shiga wanka, cikin sauri ta hanashi tataka da qafar ta suka shige toilet din, itace agaba yana Binta abaya hakane yasa ta dinga runtse idonta kadan kadan yanda de tasan bazai ganta ba bare yaga halin datake ciki,duk abinda take tana daurewa ne kawai saboda kaga yaga gazawarta. Washe gari jirginsu ya Lula qasar Dubai,a hotel suka sauka inda lokaci daya Aisha tazame masa yar qauye tuburan, Bayan sunyi wanka sun huta abinci sukaci suka kwanta bacci, washe gari suka fara fita yawo yana nuna mata waje daban daban, saida suka gaji da yawo sannan suka wuce yasai mata waya a Hiphone telecom kamar yanda yayi mata alqawari agida, daga Nan Kuma suka koma hotel, washe gari suka sake fita sune jirgin ruwa, sune wannan wajan wasa sune wannan, Aisha ta bude ido tayi kallo, ko a mafarki bata taba tunanin zuwa wata qasar waje ba, Amma yau gashi taje, tunda suka zo qasar kwanansu biyu ne yadaga mata qafa, Amma kullum da'irin Horan dayake bata, a rana saiya nemeta yakai sau hudu, tun tanaqi, harya saba mata da hakan kamar karatu tariga tasan kullum ne wannan abun, beyi dayawa ba shine zaiyi sau biyu, Sai yanzu ne Kuma take gaskata maganar Ummah datace idan batashan magungunan tayaya zata samu ni'ima ajikinta? Shiyasa kullum cikin shan maganin ni'ima take,uwa uba fruit, kullum wuni take tanacinsu, saida sukai wata daya adubai, sannan sukai shirin wucewa Saudia Kuma Sai akai dace Adede lokacin ake aikin Hajji,wannan dalilin ne yasa basu biya ta Qatar ba, zuwa wannan lokacin Aisha tasaba da buqatun Shahaab,Kuma har yanzun babu wani dadi datake ji, saide idan yana mata wasa ne takejin dadi sosai, anan take huce taqaicin ta, Shima daya fahimci haka saiyake 6ata lokaci yake mata wasan sosai, a Saudia kuwa sosai suka gudanar da ibadar su, acan dinma baya daga mata qafa, saide idan tana mp ne wannan Kam dole yake haqura da'ita, duk lokacin daya nemeta koda wasa bata hanashi, wani lokacin ma itace take kawo kanta, duk wani style najin dadi saida Shahaab ya Koya mata shi, sosai yake jin dadinsa shiyasa yasake yin qiba da haske, ita kanta Aishan Wanda ya ganta lokacin dazasu tafi, bazai ganetaba, tasake yin fari sosai har farin ma yayi yawa,suna gab da kammala aikin Hajji tafara jin yanayin kasala yana takura mata, ga yawan bacci dayake damunta lokaci zuwa lokaci, haka kawai saita dinga jin wani irin bacci me dadi, Amma Kuma saita danganta hakan da rashin aikin yi tunda bata aikin fari bare na baqi. Bayan sungama aikin Hajji Kai tsaye America suka wuce,sun dade a America saida sukai kusan wata biyu, a wannan lokacin Aisha tasake yin fari sosai, hips dinta yasake budewa, Amma kokad'an Shahaab bai lura da sauyawar taba, tsawon wannan watanni ukun kullum ne Sai Shahaab ya nemeta,wata irin kulawa yake bata yana sake lalla6ata saboda wani irin dadi dayaji ta qara na musamman tun Zuwansu qasar America, shiyasa kullum ne saiyasan yanda yayi ya tsokano ta yayi abunsa, babu ranar banza,abinda ta lura dashi shine tunda sukazo America Shahaab yakoma kamar wani wawa akanta, Sai abinda tace, musanman idan dare yayi har goyata yake haka kawai su dinga yawo acikin gidan dasuka sauka, Shikuwa shi yasan meyake ji, shiyasan irin dadin dayake ji aduk lokacin dasuka kasance cikin Raya Sunnah,shiyasa tagama mallakeshi,kuma yariga yasaba mata da hakan, tun batajin dadin komai harta dawo tana danji kadan kadan,suna shirin dawowa Nigeria taji duk abun Kuma yafita daga kanta, idan yanayi tanajin kamar tayi amai, Amma haka take daurewa duba da yanda shikuma kamar anqara masa wata jaraba ne a lokacin,saida suka cika wata uku cif sannan suka dawo Nigeria. Saukar dare sukai Basu samu Hajja a gidan ba, taje gidansu Ummah, mama ce kawai a gidan, mamaki ya kama mama ganin yanda gaba d'ayansu suka canza kamar ba hausawa ba, ta kalli Aisha sosai taganta ras babu alamun rashin lafiya bare susa ran Kota samo musu dan America(😍). Fatan alkhairi tayi musu acikin ranta sannan tasa aka gabatar musu da abinci,Aisha ta kalli abincin sannan ta kalli Mama tace"mama babu alale?" Mama tace"kiyi haquri takwara bansan ita kike so ba da kafin ku sauka angama hada miki" Shahaab yana jinsu baice musu uffan ba, saide cikin ransa yana mamakin Aisha, datake neman alale da wannan dare. Bayan sun gama cin abincin suka nufi part dinsu. Suna zuwa tazube a kujera cikeda gajiya tafara bacci, Shahaab kuwa kayaiyayin da sukazo dashi yafara Kai musu cikin daki,yana futowa yaga tana bacci, mamaki ya kamashi, wanne irin bacci ne wannan daga shigowar su kamar me cutar bacci? Tashinta yayi yace"tashi kiyi sallah mana" Cikin bacci tashige dakinta, saida tayi wanka tayi sallah, tana zaune tana azkar bacci yasake dauketa awajan, Dakin yashigo cikin shirin bacci, mamaki yasake kamashi baccin de?daukar ta yayi cimak yad'ora ta akan gadon sannan Shima yahau gadon ya kwanta tareda rungume ta, yasan baccin gajiya take, dole zata yi bacci Dama, but abinda tasaba bashi yau bata bashi ba, Kuma yanda yake jinsa yau akwai yar damuwa,yana buqatarta sosai, ahankali yafara yimata wasa cikin salon da dole saita tashi daga baccin, cikin baccin ta taji qamshin turaren sa Yacika mata hanci,lokaci daya taji amai yana kokarin taso mata, juyawa tayi tabashi baya taci gaba da baccin ta,can Kuma taji yafara shan nashanunta,haka kawai taji wani irin haushi ya kamata, kwata kwata taji batason abun, kokadan batason ya ra6eta, tashi tayi ta zauna, batace masa komai ba tafuto tabar masa d'akin tadawo falo, Nan ma biyo ta yayi yana tambayar ta "meyafaru" tace masa"bacci kawai nakeji karabu dani" Qin haqura yayi, yasaka hannu zai dauketa ta qwace jikinta tafice daga part din Kai tsaye tatafi Dakin mama ta kwanta, bayanta yabiyo saida yaga inda ta kwanta sannan yayi ajiyar zuciya yajuya yakoma part dinsu cikin sanyin jiki. Washe gari mama Sai ganin Aisha tayi abayanta tana bacci, daqyar tatashe ta tayi sallar asuba, tun kafin ma ta tambayeta ba'asin kwanan tana idarwa tafice Takoma part dinsu, Bai ce mata komai ba, Kuma bai nuna mata akan fuskar saba, saima murmushi Dayayi yace"me bacci" Itama murmushin tayi, sannan tayi masa Ina kwana,sannan ta shirya shi yayi shirin fita wajan aiki, bai dawo ba Sai dare, yauma hakan ce ta kasance kwata kwata Aisha taqi bashi hadin Kai, abinda yasake daure Masa Kai shine yanda take yawan bacci kamar wata yar maye, duk yanda yaso tabashi Dama yayi qi tayi, qarshe yauma wajan mama ta gudu ta kwana,Kuma tana idar da sallar asuba tasake komawa part dinsu, a kwana na ukun ma tana shirin kwanciya yashigo Dakin ya zauna abakin gadon yace"maamah magana nakeso muyi" Cikin rashin damuwa tace"to Uncle Ina jinka" "meyasa kike gudu nane kwana biyu, nayi Miki wani laifi ne?" Cikin sauri ta Girgiza masa Kai tace"banaso ne kawai,kaikuma saikaqi haqura ka nace dole saika yi" Yace"amma kina shiga haqqi na,bakida wata hujja dazaki kare kanki awajan ubangiji,nayi tunanin ma laifi nayi Miki, Amma haka kawai saboda mugunta Kuma kina sane kike hanani abinda nake so" Wannan kalmar daya fada ta mugunta tayi mata ciwo,lokaci daya tatuno ranar dasuka fara haduwa, dama fadane ya hadasu,ajiyar zuciya tasauke tace"nifa Uncle saide kace komai,Amma gaskiya bazan iya wannan abun ba,ni yanzun ma dazaka tashi kafita danaji dadi saboda wannan qamshin turaren Naka takuramin yake wallahi" Taqaici da haushi suka kama Shahaab, baisan me tataka ba datake fada masa kowacce irin magana, abu kadan Saitayi fishi, abu kadan saita kama yin fishi,maimakon tabashi haquri shine take fada masa maganar data so, Kallan ta yayi cikin 6acin rai yace"okay haka kikace?to yau sainayi abinda nakeso saimu ga tsakanin NI DAKE...Dan halak kafasa" Yana fadar haka yafara kokarin cire rigar jikinsa ta bacci, yana daga hannunsa sama da nufin cire rigar Aisha tayi wuf tafice daga d'akin,ta gudu wajan mama, taqaici yasake kamashi, me yarinyar Nan take nufi ne?ko wasu ne suke zigata? Aikuwa yau saide ayita taqare, rigar sa yamaida jikinsa,Shima yadoru abayanta, mama tana bacci batasan meyake faruwa ba Sai taji kamar magana tana tashi qasa-qasa, ahankali ta bude idonta Amma bata juyo ta Kalle su ba, cikin damuwa dakuma 6acin rai yasake yin qasa da muryarsa yace"kitashi mutafi nace" Aisha tayi shiru tarabu dashi, itama kanta batasan meyasa ba, Amma kwata kwata taji batason wannan abun yanzu, Shahaab yasake qasa da murya yace"wallahi zan daukeki" Cikin shagwa6a tace"ninacema banaso, Dan Allah karabu Dani kaje kayi baccinka" Hannun sa yasa yafara kokarin daukar ta, ita Kuma taqi, lokaci daya suka fara kokawa,(😂🙆🏻‍♀️). ita tana so ta qwace shikuma yanaso ya dauketa. Mama dataji abun nasu yana nema yakoma dambe saitatashi zaune, dama tunda suka dawo tarasa gane wannan zuwa da Aisha takeyi dakinta kullum da daddare, cikin damuwa tace"hasbunallahu wani'imal wakeel,hasbunallahu wani'imal wakeel!! yau nashiga aljanna nakasa futowa ni Aysha mezan Gani haka?,dambe?akan gadona?" Cikin sauri yacikata yakoma Gefe daya yana Sosa Kansa fuskar Nan tasa ta kumbura taf da 6acin rai,mama ta kalli agogo taga karfe d'aya saura, tace"me kuke a dakina?" Dama kamar jira yake, Cikin sauri yace"mama abinda yarinyar Nan take min kwana biyu banajin dadi,tunda muka dawo tazama muguwa batajin tausayina"(🙈🤭) Mutara zuwa anjima🏻 Shahaab littafin kudi ne,ki biya naira 300 kacal yafi ki karanta abunda akace ba'a yafe miki ba 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN tareda shedar biya ta wannan number 08033300034 Amnah El Yaqoub✍🏻 Mama tanajin abinda Shahaab yafad'a tad'auki haske,lokaci d'aya tagano inda matsalar ta dosa,kafin tace wani abu Aisha tace"mama nace masa banaso-banaso shikuma yadage nikuma babu inda zani" Tana fadar haka ta Fashe da Kuka. Cikin sauri ya nuna Aisha da hannu yace"mama kinajin abinda take fad'a ko?" Mama ta runtse idonta ta bude, ta kalli Shahaab tace masa"jeka zata taho,gobe Dasafe zamuyi magana" Babu musu yajuya yafice daga d'akin badon ransa yaso ba Mama ta juya ta kalli Aisha wadda ta d'ora kanta akan cinyoyinta tana kuka tace"Aisha" Cikin shashshekar kuka tace"na'am" Mama tace"meyasa kike gudunsa? Ko akwai abinda yake miki?" Kanta ta Girgiza sannan tace"ni babu abinda yamin, kawai de nace masa banaso ne, saikace tuwo kullum Adinga abu daya" Mama tace"Toya zakiyi?so kike mijinki yafara neman mata?kokuma so kike yayi miki kishiya?" Cikin sauri ta Girgiza kanta Mama taci gaba da cewa"to tunda bakya so kidinga kokari kina bashi abinda yakeso,ba dole ne ai saikin masa abinda yake soba, kefa mace ce, Kuma yarinya yar zamani, cikin dabara Zaki masa wasu dabarun ku rabu lafiya batareda anji kanku ba, ai akwai hanyoyin wasa Wanda Zaki gamsar da mijinki,shi namiji bashida kunya a wannan fagen,inde kikace Zaki hanashi wannan abun Tofa babu kwanciyar Hankali, inda yanada kunya bazai iya biyoki har cikin dakinaba,yanzu inda Zaki biye masa shi anan dinma Sai yayi abinda yaga Dama,Kuma babu maganar Wai Adinga abu daya saikace tuwo yanda kika saba masa dole haka Zaki cigaba,tun farko Dakin dorashi akan rashin yi koda yaushe to zai rage miki wasu abubuwan duk da yata6a aure abaya yariga yasaba Amma ai kowacce mace akwai yanayin ta, muddin kikace Zaki biyewa namiji ki saba masa da abu Tofa rana daya idan kikace ba zakiyi ba Tozaice baisan da wannan zancen ba, bare Kuma akan wannan harkar, haquri zakiyi kije kibawa mijinki haquri kada ki kwana cikin tsinuwar mala'iku, saiki San yanda zakiyi kimasa dabara ta yanda bazai miki abinda zai takura miki ba" Ahankali ta goge Hawayen idonta sannan tatashi tafice daga d'akin, Kai tsaye part din nasu ta nufa, tana shiga falon ta ganshi a zaune,da kallo yabita har tazo inda yake zaune ta tsugunna tace"kayi haquri" Kansa ya Girgiza kawai, sannan yatashi yashige dakinsa, itama tatashi tashige Nata Dakin, haka suka kwana kowa rai babu dadi. Washe gari da safe tun kafin tazo dakinsa yatashi ya shirya da Kansa, Bai jirataba yawuce wajan mama domin yin breakfast, itama saida tagama komai sannan tatafi, mama tana ganin Zuwansu kowa daban daban tasan cewa to ba'a shirya ba. Zama tayi akan kujera ta gaida mama, sannan ta kalleshi tace"Uncle Ina kwana" Batareda ya kalleta ba yace"lafiya" Kafin ta zuba abincin mama ta kalleta cikin murmushi tace"takwara kece kike jajen alale, gashi yau de nasa anyi miki ita" Cikin tsananin murna tace"Allah mama?Kai Amma naji dadi wallahi" Shahaab yadaga Kai ya kalleta, wato har murna take ma saboda alale, shi batayi murna da ganinsa ba, harara ya Wulla mata, sannan yaci gaba da juya spoon cikin cup tea din dake gabansa,Aisha kuwa bata kula dashi Bama taja alalen a gabanta ta bude cooler tana cewa"mama tunda muka dawo banga Hajja ba, Kuma banje gidanba,in anjima zanje kinji mama" Mama tace"gaki ga mijinki, ki tambaye shi mana" Juyawa tayi ta kalleshi tace"Uncle inaso inje gida" Batareda ya kalleta ba yace"bazaki ba" Sake Kallonsa tayi, taga ko daga Kai baiyi ya kalleta ba, bata sake ce masa komai ba kawai tafara zuba alale a flate Din gabanta, lokaci daya fuskarta ta sauya, mama ta kalleta tace"takwara lafiya?" Yatsina fuska tayi sannan yace"mama yanaga ansa qwai da ganye aciki? Nifa normal alale nakeso wadda ba'a saka mata komai ba,ita nakeso, sonake na ganta Ina saka mata yaji da manja inaci, Amma wannan Bana sonta, farin Mai aka saka mama, nikuma da manja nakeso" Mamaki yakama mama, duk yanda ta taqarqare ta tsaya tsayin daka wajan ganin yarinyar Nan anyi mata alale me kyau yanda ya kamata Amma tace bata mata ba? To Aisha kalau take kuwa?(🤔) Shahaab kuwa wani irin kallo yabita dashi, shide a saninsa haka ake alale, wacce alale ce take fada haka kamar ta Yan gidan yari? Mama tasaki ajiyar zuciya tace"kiyi hakuri takwara kici wannan din yanzu, itama zakiji dadinta, inyaso duk lokacin da kike son dayar saiki sasu suyi miki irin wadda kike so" Haka tasake kallon alalen ranta duk babu dadi tasaka spoon tafara ci,saide tanayin cokali biyar taji wani irin amai yataso mata, ta dora hannunta akan qirjinta tana so ta danne shi Dan kartayi, Amma Inaaaa, jitayi bazata iyaba, cikin sauri tatashi tsaye tayi kitchen da gudu. Cikin sauri ya d'ago Kansa yana kallanta, cikin tashin hankali ya manta da fishin dake tsakani yabi bayanta, mama ma tatashi tabisu, saida tagama yin aman tana riqe a hannunsa yana mata sannu, mama tace"sannu Aisha, Kai wannan abu banji dadinsa ba, kiyi hakuri nasa kinci abinda bakya so" Wanke fuskarta tayi sannan tace"babu komai mama" Shahaab dake riqe da kafadunta ya kalleta yace"bakya jin komai yanzu?" Saida ta zabga masa harara sannan tace"um"🙄 Tasaka hannu ta janye hannunsa daya riqe kafadunta dashi saboda wannan kusancin nasu yanasa wa tanajin qamshin turaren sa, Kuma batason jin qamshin, mama ta Kalle su tayi murmushi tafita daga kitchen din, itama Aisha tafice, Shahaab yariqe qugunsa ya furzar da iska daga bakinsa, sannan yayi ajiyar zuciya yana kallon kitchen din, zai iya cewa tun farkon Gina gidan Nan rabonsa da shigowa kitchen, Amma yau shine aciki ta dalilin yarinyar Nan Amma shi take harara, idan yakama yarinyar Nan bazai mata ta dadi ba. Juyowa yayi yafuto yakoma dinning din ya zauna, anan yaganta tana shan tea baqi, marar madara. Saida suka gama cin abincin sannan mama ta Kalle su tace"wannan rayuwar dakuka daukowa kanku babu inda zata kaiku, idan zaku daina wannan fishin ma Gara ku daina, idan Kuma so kuke mutane su mana dariya ne to shikkenan ga wajan Nan Sai kuyi tayi" Tana fadar haka tatashi ta basu wajan, bata zauna afalon Bama Kai tsaye d'akin ta ta wuce. Hawaye ne yazubo daga idon Aisha, ahankali ta ajiye cup din dake hannunta ta dora kanta akan table din tafashe da wani irin kuka, runtse Idonsa yayi sannan yabude, cikin 6acin rai yamiqe tsaye, yasaka hannu ya fuzgota, sannan yajata qiiii suka fice daga part din sukayi nasu, suna zuwa part dinsu yasaki hannunta sannan Yarufe qofar ya kalleta cikin 6acin rai yace"waike Dan Allah me aka miki ne? Me kike so? Nine yakamata nayi kuka bake ba, tunda ni kika Hana abinda nakeso Kuma nayi haquri naqyaleki" Cikin kuka tace"toba nabaka haquri ba" Yace"haqurin ki din banza,?cemiki akai haquri nakeso? Haka mace take Bawa mijinta haquri kinzo kin tsugunna agabana kamar me neman gafara, ni babu abinda zaki fadamin, jikinki ne de ko? To ai gashinan nabar miki abinki Sai kije kiyi abinda kikaga Dama dashi" Maimakon tabashi haquri, saikuwa ta juya zata shige dakinta(🤭) Dayaga da gaske de tafiyar zatayi, cikin sauri yasaka hannu ya fizgota tafada jikinsa, cikin sanyin murya dakuma sigar rad'a yace"wai tafiyar zakiyi?" Cikin kuka tace"bakaine kace natafi ba?" Yace"to Kuma ke bakisan wasa ba?,nace kije kiyi abinda kikaga Dama kenan ke bakisan wasa ba shine Zaki tafin?(😂) Dan qaramin bakinta taturo gaba sannan tafara kokarin raba jikinta da nasa, cikin damuwa yasake riqeta, yasake yin qasa da muryarsa yariqe fuskarta da hannayensa biyu yace"mekikeso?" Kai tsaye tace"karabu Dani" Yace"why?" Yatsina fuska tayi sannan tace"banason wannan qamshin dakake" Cikin mamaki yace"bafa turaren da bakya so din nasaka ba, wancen tunda kikace bakyaso bansake amfani dashi ba" Cikin damuwa tace"shima wannan din koma wanne ne de banaso" Cikin sauri yace"shine kawai abinda kike so?" Ta gyada masa Kai batareda tace komai ba,cikin sauri yasaka hannu yacire jacket din jikinsa yawullarta afalon, yacire ta cikin ma, sannan yacire wandon yayi qasa, singlet dinma yacire ta yayar, saiya kasance dagashi Sai gajeren wando,yasaka hannunsa yajata jikinsa ya rungume ta tsam Sai ajiyar zuciya yake, itama dataji babu qamshin turaren saita kwantar da kanta akan qirjin nasa tasake yin luf, sun dade Ahaka, shide Shahaab yana mamakin Aisha, tsakani da Allah ace mace batason qamshi saikace ba mace ba? Menene yasa ta sauya haka? Daukar ta yayi cak suka koma kan kujera, yazaunar da'ita akan kujera sannan yasaka hannu yacire gajeren wandon nasa, saiya dawo daga shi Sai Dan pant din sa dayake sakawa, ya zauna a kujerar ya dauketa yad'ora ta akan cinyarsa tareda kwantar mata da kanta akan qirjinsa yana shafa sumar kanta, cikin rad'a yace"mundena fada ko?" Daga masa Kai tayi, cikin jin dadi yace"kinyi alqawari?" Tasake daga masa Kai,jikinta yasake qamqamewa yana jin dadin yanda tudun qirjinta yake ta6ashi, cikin wata irin murya kamar Dan maye yace"ai mama ma tadena ganinmu muna fada koooooh" Yaja kooo din cikin Jan Hankali, nanma tasake gyara masa Kai,tareda dora hannunta akan nipples dinsa tana Dan shafawa, Lumshe Idonsa yayi, ahankali yace"kinsa kwana biyu Ina saka wannan abun" yafadi hakan yana dora dayan hannunta akan pant din jikinsa, ahankali itama tace"toka cireshi" Cikin shagwa6a yace"bakece kikasa nake sakawa ba, saide kicire"(🙈) Babu musu tafara Jan pant din, Shima yabata hadin Kai wajan tashi tsaye, tazare masa shi kuwa, sosai ta tsorata ganin halin dayake ciki, Shima ya gane hakan ganin yanda fuskarta tad'an sauya alamar tsoro, cikin daukan Hankali ya zauna sannan ya maida ta kan cinyarsa, cikin jin dadi tasake kwantar da kanta akan faffadan qirjinsa, cikin dabara ya Lumshe Idonsa sannan yafara rabata da kayan jikinta, Gefe daya Kuma yadaga kanta dake kan qirjinsa sannan ya manna mata bakinta akan nipples dinsa, tana ganin haka tasan cewa so yake ta tsotsa, bata so Hankalinsa yatashi yace zai kwanta da'ita, Amma data tuno shawarar da mama tabata, saita tsaya da nufin tayi masa wasa kawai zaifi, Dan haka cikin sauri ta kama kan nonon nasa tana tsotsa, cikin jin dadi yasaki wani irin qara marar sauti sosai, hannunta yakama yad'ora akan dayan, nanma babu musu tafara murza masa shi, lokaci daya Shahaab yarikice Sai maganganu yake mata marasa kan gado, kwata kwata ya manta da batun fita aiki, yana nasa aikin agida(🤭😲) Sosai Aisha tadage take masa wasa yanda ya kamata,saida taga yasamu nutsuwa sannan tabarshi, Amma anasa 6anbaren kokadan hakan bai gamsheshi ba,qarshe ma kuka yasa mata akan shide tabarshi yayi abinda yasaba, haka itama tasaka kukan tana bashi haquri, Amma inaaa, rabuwa yayi da'ita yafara yimata aiki anan kan kujerar, sosai yake jin dadinsa yanda ya kamata yayinda ita Kuma takejin amai yana taso mata, tana runtse ido da komai haka yayi, Amma Kuma itama taji dadin, wahalar da Tasha ce tafi jin dadin yawa, haka suka gama a lokacin tahada gumi jirgif ajikinta, rungume ta yayi yana goge mata gumin fuskarta, tareda kalamai masu dadi, saida ya huta sannan ya dauketa sukai cikin dakinsa, akan gadon ma sabon round yayi, saboda acikin kwana ukun Nan da baiyi ba, shiyasan meya Tara ajikinsa, sosai yake ihu najin dadi duk Yacika falon da Dakin nasa da ihu, Aisha taji ajikinta, danma yariga yasaba mata ne Amma duk da haka taji ajikinta, yana gamawa kuwa taji amai yataso mata, cikin sauri tatureshi daga kanta tayi toilet tana kwarara amai, kokadan babu qarfi ajikinsa, numfashi kawai yake maidawa Idonsa a Lumshe, yana jin yanda take zuba amai Amma yakasa tashi, saida tagama aman tas, sannan tadawo kan gadon tahaye ruwan cikinsa ta kwanta, babu musu yad'ora hannunsa abayanta yana Dan bubbuga mata Bayan alamun lallashi. Saida suka nutsu sosai sannan yace"sannu maaamah, Allah yayi miki Albarka, maaamah meyasa kika qara dadi kwana biyun Nan?bazaki San yanda nake jiba ne, Amma inajin dadinki sosai kamar nayi hauka wallahi,kiyi hakuri dazu nasaki kuka kinji, kiyafemin" Daga masa kanta tayi, yasaka hannu ya shafa kanta sannan yace"muyi wanka mutafi Asbiti ko, Naga tun dazu kina amai, muje a dubamin ke sosai" Cikin shagwa6a tace"uhm nifa kalau nake Uncle, banajin ciwon komai" Wuyanta yashafa yace"but jikinki da zafi maaamah" Cikin sauri tace"lafiyata kalau fa" Cikin sigar tsokana yace"kenan naci gaba daga inda na tsaya ko?" Cikin shagwa6a tafara birgima ajikinsa, cikin sauri ya riqeta yace"Maamah Zaki tada min tarzoma kibari Dan Allah" Murmushi tasaki sannan tasake rungume shi, saida suka gama firarsu sannan suka shige toilet sukai wanka, suna futowa Hajja takira wayar Aisha, dauka tayi cikin murna tace"Hajja" Hajja tace"mutanan qasar waje,bamuzo sannu da zuwa ba shiyasa muma baki kawo mana tsarabar yawon amarcin ba" Dariya tayi tace"yauwa Ashede kin gane, idan kikazo min saina baki" "to ai Gani a gidan, nazo tun dazu" Cikin sauri tace"to Gani nan zuwa" Kayanta tanema ta zura, bata shafa turare ba kawai humra ta shafa itama yar d'is, duk abinda take Shahaab yana kallon ta, tad'auki bra zata saka yayi saurin cewa "nahanaki saka abun Nan Amma bakyaji" Cikin shagwa6a tace"to Uncle Kuma yanzu Sai indinga yawo haka abu yanamin rawa?" Yace"ba hijabi kike sakawa ba?" Tace"ni banajin dadi wallahi,Nina Rasa meyasa ma yanzu Sai qaruwa suke" Yace"toba gashinan nanba,inda kina sakawa Kuma may be su ragu,saboda haka nide karki saka wata brezia kibarmin kayana Ahaka suyita qaruwa," Tace"to yanzu haka zan fita Uncle?" Yace"kokin saka saina biki nazauna aqarqashinki nacire miki ita Allah Bakinta ta turo gaba, tasan zai iya aikata wa, haka tacire brar tasaka rigarta doguwa, sannan ta saka hijab tafice daga d'akin, Shima shirya wa yayi cikin wata suit din, yabude jikinsa da turare yabi bayanta part din mama. Mama da Hajja suna zaune Aisha tashigo tafada jikin Hajja cikin murna, mama tana ganin Aisha ta sauya Kaya tasaki ajiyar zuciya a6oye, tana fatan ace yaran sun shirya, bata gama tunanin taba taga Shahaab din shima yashigo ya sauya shiga Sai wani farinciki yake, Nan da Nan ta fahimci komai, Sai Alokacin hankalin ta ya kwanta, yana zuwa ya qaraso kusa da Hajja Shima yana gaida ta, Aisha tana jin qamshin turaren tatureshi, cikin gudu tafada Dakin mama tana kwara amai. Shahaab ya runtse Idonsa yana fadin" innalillahi wa inna ilaihirraji'un wallahi na manta" Hajja tace"meka manta?" Cikin tashin hankali yabi Bayan Aisha yana fadin" Wai batason qamshin turare na" Bai jira amsar Hajja ba yashige d'akin mama,sosai yaga tana amai ta riqe cikinta da hannunta, yana Zuwa kuwa aman ya qaru sakamakon sake jin qamshin datayi, mama d Hajja suka shigo Dakin, mama tace"tunda batason qamshin kafita mana to" Cikin tsananin damuwa yajuyo yadawo falo Sai haushin Kansa yakeji, saida tagama aman sannan mama ta kamota suka dawo falon, zama tayi nesa da Shahaab Hajja tana mata sannu, mama ta kalleta tace"bakici abinci bafa yau, Amma sai amai kike kode duk alalen ne yasa?" Hajja tace"Aisha da batacin alale itace yau taci?" Mama tace"au bataci Dama?aikuwa tun ranar dasuka dawo take tambaya ta Wai ko zata samu alale? Nace mata wallahi babu, shine yau nasa suka mata, Kuma tanaci Sai amai, yanzu Kuma kinji Wai qamshin turaren sane bataso" Shahaab daya dorawa Kansa alhakin yin aman na Aisha, ya d'ago Kansa cikin damuwa yace"acan ma damuka je tayi wani aman" Mama ta kalli Hajja tace"kinji ai ko?" Sannan ta juya tasake kallon Aisha, wadda zazza6i yarufe ta jirgif tace"takwara Bari kici abinci muje Asbiti naji jikin naki ma da zafi sosai,mekikeso kici?me za'a kawo miki?" Mama ta jero mata wannan tambayar, Kai tsaye Aisha tace" d'ata zanci mama" Cikin sauri Shahaab da Hajja da'ita kanta maman, suka kalli Aisha, Hajja ta Girgiza kanta tace"kai, Anya yarinyar Nan kuwa ba ciki ne da'ita ba?" Gaban Shahaab yayi wata irin faduwa, cikin sauri ya kalli Hajja, mama ta kalleta da mamaki Tace"A a, to kode cikinne yasa ta take wannan za6en Abincin?" Hajja tace"haba kekuwa Aysha,yarinya tace batason qamshin turare Kuma ta kama tsirfa akan cin abinci ai dole ki lura sosai, Kuma uwa uba ga wannan aman datake, kiduba fa kigani yanda duk ta d'ashe tayi wani irin fari, ai daga Gani wannan ba farin Hankali bane,Kuma Aisha batacin alale,ciki ne yasa ta nema, dama Kuma ciki shikesa mace ta nemi abinda bata ta6a cibama arayuwarta,aini bangantaba tunda suka dawo Sai yau, Amma kana ganin yanayin ta aikaga na me ciki" Shahaab Kam qamewa yayi awajan a zaune, jiyake kamar a mafarki,Aisha da ciki? Ciki de Wanda yake Fata da burin samu?Kuma da gaske ne cikin ne? Mama tace"ai bamuga ta zama ba, Bari nakira Dr. Tazo ta dubata yanzu yanzu" Tafadi hakan tana Dialing number Dr. Shahaab de kallonsu yake yana ganin abun kamar almara, wata zuciyar tana gaskata maganar Hajja wata Kuma tana qarya tawa Dr.bata dauki lokaci ba tazo gidan, ta dudduba Aisha sannan ta dauki fitsarinta tatafi,Bayan tatafi gaba dayansu shiru sukai kowa da abunda yake saqawa a ransa, ita Kam Aisha tuni baccin data saba harya dauketa, Shahaab kam baisan Ina yakeba, ruwan Kansa yaqare yagaza yin tunanin komai, Dr. Tana dawowa gaba dayansu suka miqe tsaye kowa yana jira yaji abinda zata fada, cikin farinciki tabawa Shahaab wata takarda tana cewa"yalla6ai congrats, madam tana d'aukeda juna biyu na tsawon wata biyu" Mutara zuwa gobe🙏🏻 SHAHAAB littafin kudi ne, nera 300 ne kacal, idan kika karanta baki biyaba nabarki keda MAHALICCINKI 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN tareda shedar biya ta wannan number 08033300034 Amnah El Yaqoub Cikin tantama Shahaab yace"serious Dr.? But Haka ake fad'awa munirat daga baya Kuma a dawo acemin babu cikin, kin tabbatar da abinda kike fad'a Kuwa?" Cikin tsananin murna tace"sosai kuwa yalla6ai, haka bincike ya nuna" Hajja tace"Alhamdulillahi, Bari inje in fadawa Hadiza da mamuda"(😂) Mama tace"ina tunanin Gara suje India asake dubata dakyau, saboda anyi haka da munirat yakai sau nawa,tana fara jinya zatace ciki ne, Amma duk wajan likitocin da mukaje Sai suce babu komai,Ina tsoro itama Aishan kar daga baya su sake cewa ba cikin bane, shiyasa tun daga lokacin nadena yarda da maganar Doctors dinnan" Dr. Tayi murmushi tace"Hajiya mama inde kunje Indian Kuma binciken ku yayi iri daya da nawa, to zan dawo na kar6i Goron albishir dina" Shahaab yayi murmushi yace"nima nafi yarda da maganar mama,abaya Ansha Sakamin rai akan haihuwa Amma Kuma daga baya a dawo ace babu cikin,Nima Hankali na zaifi kwanciya akan muje Indian,idan kuwa abinda muke tunani yazama gaskiya to saiki fara shirin tafiya Umara" Hajja tasaki baki da hanci tana Kallan su d'aya bayan daya,duk saboda maganar cikin ake maganar fita qasar waje, ga Kuma Goron albishir na tafiya Umara,duk wannan budurin saboda ciki, sukam wanne irin haihuwa suke so haka?to wacce tace Aisha tanada ciki ma anbata kujerar Umara ita Kuma me cikin me ake tunanin bata?(🤔) Kallan Shahaab tayi ido cikin ido tace"dakata Shahaabu,Yaya Ina zaune nida ganowa Aisha tanada ciki likita da samun kujerar Umara?Hajjan Kuma fa?" Murmushi yasaki dimples dinsa suka futo yace"karki damu Hajja aike kyautar ki ta dabance, Babban matsayi zan baki na renon jikanki"(😄) Yana fadar haka babu kunya ya sunkuci Aisha dake bacci ya manna mata kiss a kumatu sannan yafice daga part din. Hajja da mama dakuma Dr. suka kwashe da dariya, Hajja tace"shaqiyin kawai, karfi da yaji ya maidani kakarsa" Dr. Tayi musu sallama tatafi, mama ta daga hannunta sama tana fadin"ya Allah, Allah na roqeka, Allah kasa wannan bincike yazama gaskiya, ya Allah ka nunamin 'ya'yan Shahaab kafin ka dauki raina" Tausayin ta yakama Hajja, cikin sanyin jiki Hajja tace"kiyi haquri mana Aysha,in Allah ya yarda saikin gaji da daukar ya ransa da hannun Nan naki, saide muyi musu fatan Allah yaqara hade kansu ya basu Zaman lafiya" Mama tace"Amin ya Allah" Haka sukaci gaba da zancen su cikin tsananin farinciki. Suna zuwa part dinsu ya kwantar da'ita akan gadon sa, ya sunkuya yazuba mata ido yana Kallan kyakykyawar fuskarta, ahankali yasaka hannunsa akan goshinta yafara shafawa har zuwa kan dogon hancinta, sannan yad'ora hannunsa akan lips dinta Wanda yagama shansu dazu yanda ya kamata, murmushi yasaki, yana fatan ace wannan aman datake cikinne yasa, hijabin yacire mata sannan yaja mata Bargo yarufe ta, shikuma ya zauna tareda daukar wayarsa yana dubawa anan yaci Karo da missed call din mutane bila adadin. Cikin nutsuwa yatashi yafice daga d'akin zuwa falo yana amsa waya, dayawa daga cikin wayar akan rashin zuwansa office ne kowa yana jiran zuwansa, shi Kuma Sai uzuri yake basu akan suyi hakuri saboda matarsa ce babu lafiya. Dakin yakoma ya zauna yana aikin gadinta, Amma duk yanda yaso tatashi akan lokaci hakan bai samu ba, dole Sai haquri yayi, yatashi yad'auki passport dinta da nasa yafita daga gida saboda yi musu shirin tafiya India. Sosai Tasha baccinta babu kama hannun yaro, ahankali take bude idonta harta gama bude shi duka, tayi miqa tareda dora hannunta akan cikinta jin yanda yake qugin yunwa, shafa cikin tasake yi yanzu ahakan ne Hajja da Dr. zasuce tanada ciki? Toshi cikin idan mace tana dashi ba girma yake yi ba? Girgiza kanta tayi alamun ba gaskiya bane, sannan tatashi tayi sallah, tashiga wanka da ruwa med'an d'umi, tafuto tabud'e bedside drower tad'auki paracetamol tad'auko madara cikin fridge dinsa Tasha maganin, sannan ta nufi part din mama. Mama tana ganin ta tace"sannu Aisha, kin tashi?" Kwanciya tayi akan cinyar Hajja sannan tace"natashi mama, ansiyo min d'atar?" Cikin sauri mama yace"Eh ansiyo" Ta qwalawa me aikinsu kira, Nan da Nan aka kawowa Aisha d'atar, tana ganin ta kuwa tatashi tafara ci kamar mayunwaciya,Hajja tace"bazaki nemi abinci ba Sai d'ata mesunan qawa?" Cikin jin dad'i tace"ai idan naci wannan dinma ya'isa,kinji dad'inta kuwa Hajja?" Hajja tace"ina zanji dad'inta nida baci nake ba?" Dariya suka saki Adede lokacin Shahaab yashigo falon,Bayan su mama sunyi masa sannu Aisha ma ta kalleshi tace"Uncle sannu da zuwa" Kallonta yayi yasaki murmushi yace"sarkin bacci Harkin tashi?" Murmushi tayi tace"natashi, dama inajin zazzabi ne yasani baccin, gashi yanzu banajin zazza6in sosai,Kuma mama ta siyomin d'atar kagani?" Ta qarasa maganar tana nuna masa d'atar hannunta Cikin jin dadi yakawo hannunsa zai dauki guda daya tareda fadin"ni ban'iya cin wannan abunba, Bari inci inji" Cikin sauri ta kaiwa plate din wawura tareda fadin"kaje mama tabaka mana,wannan dinfa Nima yamin kad'an" Zaro Idonsa yayi ya kalleta yace"yamiki kadan?" Hankalinta kwance tace"emana" Kallonsu mama yayi, yaga su dinma sun zuba mata ido ita suke kallo, Kallonsa ya maida Kan Aisha, suna hada ido da'ita yadan juya Kansa alamun tatashi su tafi, karaf akan idon Hajja, cikin sauri ta kawar da kanta Gefe, Aisha kuwa babu musu tad'auki plate dinta na d'ata ta cewa su mama "muntafi" Ta kalli Shahaab tace"Uncle tashi mutafi" Babu musu yamiqe yabi bayanta, Hajja tasaki salati tace"shikkenan, ya Koya mata, yanzu Aysha saboda rashin kunya kina zaune suruka take cewa mijin tashi mutafi? Kuma babu kunya ta kalli tsabar idonmu tace mana sun tafi? Lalle Aysha kinga rayuwa lokacin da Bana nan"(🤭😄) Mama tayi murmushi tace"ai ina kan Gani ma,jiya da matar taqi yarda har dakina yabiyota,bansan wacce irin fitina Yaron Nan yake wa yarinyar nanba, daga Gani ubansa yabiyo"😲🙊 Hajja tace"ikon Allah, Amma baki musu tatas ba dagashi har ita?,kika zuba ido kina kallonsu? Kamata yayi kuyi futo na futo dasu saboda gaba" Mama tace"mezan musu? Nadaiyi musu fada da safe,idan na daure mata gindi nace karta bashi nasan Ina fita tsaf zai nemeta adakin nawa, Kuma Nima haihuwar nakeso yaushe zan hanashi yayi?, shiyasa nabata haquri nace taje su daidaita kansu, Kuma kingani yanzu itace take cewa yatashi su tafi" Hajja tace"bakinsu daya fa,Ina Kallonsa shine yafara mata sign tatashi, shine ita Kuma data fishi rashin kunya bata wuce ba saida ta kalli tsabar idon surukar ta sannan tace yatashi su tafi, wato ita me Miji, wannan rashin kunya har Ina?" Mama tace"barsu suyi, lokacin sune, ke wayasan me kikai danaki angon" Nan da Nan Kuma Sai fuskar Hajja ta sauya zuwa farinciki(😄) Daga Nan Kuma saita daina fadan rashin kunyar Aisha tafara Bawa mama labarin soyaiyar ta da mahaifin Abbansu Aisha. Suna zuwa part din tafara cire masa kayan jikinsa takai shi yayi wanka, sannan yafuto ta shirya shi, tashiga kitchen dinsu tahada masa pancake tazuba masa Nutella akai, sannan takai masa tafara bashi, cikin jin dadi yace"maamah gobe fa zamu tafi India" Kallan sa tayi tace"Uncle nifa banda komai, kaima Naga ka yarda da maganar hajja da wannan likitan" Murmushi yayi yace"inaso Hankali na ya kwanta ne,maama idan ciki ne dake nikam Yaya zanyi da rayuwa ta?"😢 Tausayin sa ne ya kamata, cikin farinciki ta ajiye plate din hannunta, sannan ta rungume shi tana shafa bayansa ahankali, hannunsa yazura tagaban rigarta ya cafki nashanunta guda daya yafara matsawa tareda fadin"ina sonki maamah" Cikin jin dadi itama tasake rungume shi tace"ina sonka Uncle" Haka suka zauna tana rungume dashi shikuma yana mata aiki taciki, yayinda ita Kuma ta Lumshe idonta tana kar6ar saqon aikin nasa.(🙈) Washe gari suka tafi India, acikin jirgin ma tana kwance ajikinsa bacci takeyi, saida suka sauka sannan yayi qasa da Kansa yaja dogon hancinta yace"maamah munzo fa" Ahankali tatashi tana ajiyar zuciya irinna Wanda yasha bacci, ta kalleshi tace"har munzo Uncle" Yace"emana,wannan baccin fa yafara damuna, gaba daya ya hanani jin dadi tareda matata" Murmushi tayi ta lakuce masa hanci sannan ta matsa ta sakar masa kiss a kumatu tace"bagashi na tashi ba?" Murmushi yayi Shima sannan yakamo hannunta suka futo dayan hannunsa d'aukeda wata yar qaramar jaka dasuka taho da'ita. Kasancewar saukar dare sukayi basu fita ko'inaba, wanka sukai sukaci abinci sukai sallah, sannan suka kwanta, harta fara baccin Nata taji shi yana lalubeta, haka tayi haquri tabarshi yayi abunsa, Amma ta tabbatar yanda yake wannan kururuwar jin dadin dole Dakin dake kusa dasu zasu jiyo su.😲🙊 Suna gamawa zazza6i Sabo ya rufeta Sai karkarwar Sanyi take,ya dauketa suka shiga toilet yana fara yimata wanka tafara kwara amai Mai ban mamaki, so Sai take amai duk ta fita a hayyacinta har hakan ya tsorata Shahaab, daqyar suka gama wankan, suka dawo d'akin har zuwa lokacin karkarwa jikinta yake har idonta yayi jajir,jikinta yafara goge mata da ruwa har zazza6in yafara sauka, can Kuma bacci ya dauketa, Sai Alokacin yasaki ajiyar zuciya sannan yazuba mata ido yana Kallonta, a wannan dare Shahaab bai runtsa ba, yana zaune yana gadinta Sai gyangyadi dayake yana daga zaunan. Sassafe suka nufi Asbiti Bayan angama yimata gwaje gwajen komai suka bata gado aka daura mata ruwa, shikuma Dr. Yakira Shahaab zuwa office dinsa, Bayan sun zauna cikin farinciki yake sanar dashi matarsa tana d'aukeda cikin wata biyu. Cikin farinciki Shahaab yad'ora hannunsa akansa, ya hargitsa sumar Kansa tareda fadin"wayyo Allah na"😂 Sai yayi qasa yayi sujjada yana qara godewa Allah, sannan yadawo kan kujera ya zauna, Dr ya kalleshi da mamaki yana tambayar sa bai ta6a haihuwa bane? Kai tsaye yabashi labarin tsawon shekarun daya dauka yana neman haihuwar, daga qarshe yake fada masa yasake duba Aisha dakyau kode cikinne yasa kwata kwata batason sex, ga yawan bacci, sannan Kuma idan sunyi sex din tana amai. Murmushi Dr yayi yana yimasa qarin bayani akan duk alamomin cikin ne,duk lokacin datake baccin abarta tayi baccin ta, amai Kuma bazata daina ba saide in cikin ne ya danyi qwari, Amma zata rage yi idan sukayi kokari wajan bata magungunan dazai rubuta musu, maganar sex Kuma cikin ne bayaso, dole zai daga mata qafa zuwa Nan gaba kadan. Cikin farinciki Shahaab yabashi hannu suka sake gaisawa sannan yatashi yakoma Dakin da Aisha take, agefen gadon ya zauna yasaka hannunsa cikin Nata, tareda dora dayan hannun akan cikinta yana shafawa, kallon ta yake sosai kamar yau yafara ganin ta, yanzu shine yayiwa Aisha ciki? Kenan lafiyarsa kalau kamar yanda likitoci suka fada? Hawaye ne yazubo daga Idonsa, kamar zararre yafara magana shi kadai "zan zama uba, Aisha zata haifamin Dana na kaina, ya Allah na gode Maka" Sosai yake hawaye, yasake shafa cikin Nata sannan yace"kai,in namiji ne kasani, In mace ce kisani zamu fara fada daku, tunda kunzo min da bidi'ah bakwaso Daddynku yaji dumin mommy ko? To sainayi, rigimamman ciki kawai " Duk wannan maganganun dayake hawaye ne suke zuba daga Idonsa, cikin sauri yad'auki wayarsa yakira mama, Alokacin suna tareda Hajja, cikin rawar jiki ta dauki Kiran nasa Dama jira suke suji sakamako, yana jin ta d'auka yace"mama" Gaban mama yayanke yafadi tace"nashiga uku Shahaab meyafaru naji kana kuka? Meyasamu Aisha?" Cikin hawaye yace"mama Aisha tanada ciki, da gaske ne mama, mama yanzu shikkenan Nima lafiya ta kalau ko?ankusa adenamin Gorin haihuwa ko mama?" Itama kukan farinciki tasaki, tafara fadin"Alhamdulillah, Allah abun Godia Ina Aishan?" Kallan Aisha yayi datake bacci hannunta cikin nasa yace"gata Nan bacci take mama,mama na damu Aisha dayawa ashe cikinne baiso, Sai yanzu da Dr. Yake fadamin Nima na tabbatar dahakan" Mama data gane inda maganar tashi tasa gaba cikin farinciki tace"baiwar Allah kenan,ashe shiyasa take tahowa Nan,kanaji na ko Shahaab, kakula da'ita sosai karka bar wani abu yasamu yarinyar Nan, kakula sosai idan angama dubata saiku shirya kutaho" Murmushi yayi sannan ya goge Hawayen Idonsa yace"mama ko quda bazan Bari yata6a Aisha ba, babu abinda zai samu cikin Nan insha Allah" Yana fadar haka yakashe wayar, yakira Ramadan ya sanar dashi Aisha tasamu ciki, cikin wata irin qara Ramadan yace"what? Wai Dan Allah da gaske kake?" Cikin farinciki yace"da gaske Ramadan, yanzu haka muna India, munzo Asbiti,Ramadan ashe da Rabon Nima zanga gudan jini na kafin na mutu?" Ramadan yace"yanzu kagane matarka tada itace bata haihuwa kenan kokuma har yanzu kaida munirat Sai Allah?"🤔 Cikin 6acin rai Shahaab yace"ni Ina cikin farinciki karka 6ata min raina malam" Ramadan yayi murmushi yace"tuba nake oga,gaskiya duk lokacin da akai haihuwar Nan muna da Babban taro,Allah de yakaimu lokacin Kuma ya sauketa lafiya" Cikin farinciki yace"idan kace taro ma ai daya kenan,Amin ya Allah de, Allah yakaimu lokacin lafiya,Amma kanajin abinda Dr yace saide in haqura da'ita zuwa wani lokaci Wai cikin bayason abunnan"🙊 Ramadan ya tuntsire da dariya yace"inajin ustaz ko ustaziya zamu samu, Kai kaji wani fi'ili na ciki ko?" Shahaab yayi murmushi yace"wallahi kuwa, Toya zanyi" Fira sukaci gaba dayi cikin tsananin farinciki yana bashi labarin abubuwan datake masa Kala Kala duk Sai yanzu ne Shima Kansa ya tabbatar cikinne yasa ta hakan. (SHAHAAB littafin kudi ne, inde kika karanta batare kin biya ba, ban yafeba, nabarki keda ALLAH) ****** Hajja ta kalli Mama tace"cikinne ko?" Mama ta goge Hawayen idonta tace"shine wallahi, aikuwa Bari su dawo mukuma saimu fita wata qasar afara siyo kayaiyakin haihuwar" Hajja ta zaro ido(😳) Tace"nashiga uku,tun yanzu?" Mama tayi murmushi Tace"A a Gara muje,idan bamu fara siyowa yanzu ba yaushe zamu je?" Hajja tasaki dariya tace"kai, nikam zanga wannan haihuwa taku wanne irin so za'a yiwa abinda aka Haifa, Bari inkira iyayenta in fada musu" Tafadi hakan tana dannawa Ummah kira. Shahaab kuwa farinciki ma hanashi komai yayi, kawai wasa yake da hannunta yana tunanin Ina zai Sakata saboda farinciki? Da ruwan yaqare shine yacire mata, tayi bacci sosai, tana tashi ta ganshi a zaune yana zuba mata murmushi, addu'ar tashi daga bacci ta karanta idonta akansa,tace"Uncle karfe nawa kuwa, da alama na Dade Ina bacci kuma banyi sallah ba, inaso inyi sallah " Tafadi hakan tana qoqarin tashi, cikin jin dadi yace"Bari nakai ki toilet kiyi alwala" Cikin sauri Tace"A a zan iyafa, banajin zazza6in yanzu, kalau nake Jina" Yace"A a, banaso ki wahala, Baby na ya wahala, zan kaiki" Cikin mamaki tace"Baby Kuma?" Murmushi yayi sannan yace"sosai,Dr yace namiki ciki har cikin yayi wata biyu,ashe Nima zan iya yiwa mace ciki da gaske?"🤔😂 Fillon dake gefenta ta d'auka tafara dukansa dashi yana karewa yana dariya,cikin farinciki yariqe Fillon yace"to karya nayi? Nine namiki ciki, kema kin kusa zama uwa, kidinga Bawa babynmu nono,mudinga yimasa wasa, Shima yayi mana.... Saime kekuma kike so?" Cikin shagwa6a tace"Uncle..." Hannayenta yariqe yace"nagode Aisha,Allah yasaka da alkhairi, Allah ya saukeki lafiya,Aisha mezan baki a duniyar Nan Wanda zaisa kiji dadi?" Ahankali tace"zuciyarka Uncle" Idonsa ne yakawo ruwa, lokaci daya hawaye ya zubo daga Idonsa, Kallan ta yayi yace"nabaki, kin Riga kin sameta, har abada takice, babu Wanda zan yi fatan nasake Bawa Bayan ke" Cikin sauri ta rungume shi, tafara bubbuga bayansa alamun yayi shiru. Bayan kwana uku suka dawo Nigeria, afalon mama suka Yada Zango, Aisha Sai ciye ciye take itace rake, itace d'ata, saikuma alale irin wadda takeso, Shahaab kan yanzu komai tayi, tadena bashi mamaki, mama kuwa ta Rasa inda zata saka Aisha taji dadi, a ranar takira Hajiya zaliha take fada mata matar Shahaab tasamu ciki, saita shirya zasu fita siyo kayan Baby, acikin satin kuwa suka tafi China itada Hajja dakuma Hajiya Zaliha, saida sukai sati biyu sannan suka dawo niqi niqi da Kaya harda su keken Hawa na Yara.😲 Har zuwa sati ukun Nan Shahaab bai nemi Aisha ba, ita kanta tasan cewa ba qaramin so yake wa wannan cikin ba, inbanda ciki waye ya'isa yahana Shahaab wannan abun?🤔 Sosai ta Jinjina masa, kwata kwata ya kauracewa saka turare saboda ita, yadena kusantarta, bashida aikin komai sai Wanda zai sata farinciki, tsananin kulawar dayake bata ne yasa tasake jin soyaiyar sa tana sake shiga ranta. Yau satin su hudu da dawowa daga india, watan cikinta uku, daga Saman mararta kuwa ciki harya fara tasawa,tunda Shahaab yaga haka, yahana Kansa sukuni, bata Isa ta kwanta rub da ciki ba zai fara fada, murmushi kawai take tarabu dashi da gyara kwanciyar Tata. Yau da daddare Bayan sunyi shirin bacci ta kalleshi taga duk jikinsa yayi Sanyi, Idonsa yayi jajir kamar marar lafiya, Kallonsa tayi tace"Uncle lafiya?" Cikin wani irin yanayi na buqata ya kalleta yace"maamah....inashan wahala, natara dayawa maamah, ni wannan wasan Bana jin dadinsa kamar dayan" Ajiyar zuciya ta sauke tace"yanzu fa lafiya ta kalau Uncle, idan zakayi kazo kayi, ni banajin komai yanzu" Cikin kulawa ya kalleta yace"a a, kirufamin asiri maamah, Dr yace cikin ne bayaso, idan Kuma nayi a kazo aka samu matsala fa? Inason cikin Nan kamar raina maamah, banason abinda zaisa yasamu matsala ko yar kadan ce" Cikin tausayawa tace"to yanzu haka zamu zauna?" Yace"zan tambayi Dr tukunna, idan naji na gamsu da bayanin nasa Sai muyi" Tace"to Allah yasa mudace" Ta kwanta rub da ciki abun ta tafara bacci, Shikuwa yana zaune yana aikin tunani, yana juyowa ya ganta ta kwanta akan cikin, aikuwa da gabansa yafadi, cikin sauri yace"maamah!, maamah tashi mana, wacce irin kwanciya ce wannan?" Tashi tayi, ta gyara kwanciyar Tata, ta kwanta akan hannunta nadama, Sai a lokacin yasaki wata irin ajiyar zuciya, sannan ya matsa kusa da'ita Shima ya kwanta(😂) Cikin dare tana tsakar bacci taji shi yana fadin"maamah!" Ahankali ta bude idonta kadan tace"na'am Uncle" Yace"tashi ki gyara kwanciyar ki,kar Babyn Nan yasamu matsala tunda kika kwanta yanzu karfe biyu ko juyi bakiyi ba, gyara kwanciyar ki"(🙆🏻‍♀️) Babu musu ta sake juyawa ta kwanta akan hannunta na hagu tana mita acikin ranta, sunci gaba da bacci gab da Asuba yafarka ya Kalle ta sannan yace"maamah!" Tace"Um Uncle" Yace "tashi kidan gyara kwanciyar ki, maamah tun dazu fa Dana tasheki Ahaka kike" Runtse idonta tayi😖😖, sannan ta bude, ahankali tatashi zaune, tasaka hannunta ta kunna fitilar gefen gadon, sannan tace"Uncle" Yace"na'am" Akaro na biyu tasake cewa"Uncle" Yace"Na'am maamah" Akaro na uku tasake Kallonsa tace"Uncle" Yace"Na'am" Tace"dan girman Allah kabarni in runtsa, haba Dan Allah, tun Daren jiya kake min maganar kwanciyar Nan, na kifa ciki na kace a a, na kwanta hannun Dama, kace a a, na kwanta hannun hagu, kace a a, yanzu Yaya kake so inyi? So kake yanzu Kuma in kalli Saman Dakin? Saboda Allah tunda aka samu cikin Nan ka Hana kanka sukuni duk ka fita a hayyacinka kaduba kagani har Rama kafara Amma bazaka kwantar da Hankalinka ba?, haba Uncle"(😂🤣) Ajiyar zuciya yasauke yajata jikinsa ya rungume ta, sannan yace"toshikkenan yi haquri na nadena, shikkenan?" Daga masa Kai tayi, cikin lallashi yace"Allah ya saukeki lafiya maamah" Tace"Amin Uncle" Tasakar masa kiss akan lips dinsa, sannan sukaci gaba da baccin. Washe gari Bayan sungama breakfast ta kalleshi tace"Uncle Dan Allah inaso Inga Ummah ta, na Dade ban ganta ba, ita Kuma kasan ba zuwa zatayi ba" Hajja tace"toko nakira ta tazo taganki idan bayason ki fita?" Mama tace"har wani? Yanzun me suke? Su tashi suje mana" Shahaab ya kalleta yace"muje to, Amma muna zuwa zamu dawo gidanmu, banason mutane su dinga kallonki" Murmushi tayi, ta kama hannunsa suka futo compound din gidan, Hajja da mama suka Ta6e baki batare da sun tanka ba, mota ta nufa, suna zuwa yabude mata da Kansa tashiga, Shima yashiga sannan driver yataho da sauri yaja suka bar gidan. Suna zaune abaya, hannunsa yana cikin Nata, yad'ora dayan hannun akan cikinta, yad'ora bakinsa akan kunnan ta cikin rad'a yace"Ummah zataga jikanta yafara girma....." Murmushi tasaki, kafin tabashi amsa sukaji wani irin qara garammm anbigi motar su, motar data bigesu tasake tahowa tasake bugarsu, motar su tahadu dawani gida ta bigi bangon gidan, kasancewar basuyi Nisa da gida ba wannan qaran ne yasa sojojin dake gidansa futowa cikin sauri, tsananin tashin hankalin dasuka ganine yasa suka zuba a guje sukayi wajan motar su Shahaab wadda ta hautsina, wasu Kuma suka doru abayan motar data bigesu wadda ta juya da mahaukacin gudu, lokaci daya aka fara musayar wuta, kowa yana harbi, tun lokacin da'akabigi motar su kan Shahaab ya bugu da dayan gefen, yayinda Aisha Kuma tana daga 6angaren da motar tahadu da ginan, kanta yahadu da bango glass din windon yafashe,kasancewar batada nauyi, Kuma bata saka belt ba yasa tafado Qasan motar, cikinta yabugu da jikin kujera, lokaci daya ta runtse idonta, motar ce tafara hayaqi kamar wani abu yafashe aciki gaba daya Sai hayaqi yarufe motar, cikin sauri sojojin suka bude motar, aka futo da direban Wanda ko motsi ma ba yayi, cikin tashin hankali Shahaab yasaka hannu yadauko Aisha,Bai duba yanda hannunsa yafashe yake zubar da jini ba kawai Tata yake, futowa yayi da'ita waje Sai Alokacin yaga kanta yafashe yana zubar da jini, duk jini ya6ata mata gashinta, fuskarta yariqe yana jijjiga ta,tareda fadin"Aisha!, Aisha!! Aisha!!! Bude idonki ki kalleni " Amma kokadan Aisha batayi motsi ba, daya daga cikin sojojin ne yace"yalla6ai tana zubar da jini yakamata mutafi Asbiti abata taimakon gaggawa" Sai Alokacin ya zubawa jikinta ido anan yaga jini take zubarwa duk qafafunta sun 6aci,jini har qasa yake sauka, gabansa ne yayi mummunar faduwa,cikin tashin hankali ya furta "innalillahi wa inna ilaihirraji'un" kamar mahaukaci haka ya dauketa duk jini ya6ata jikinsa, cikin sauri aka wuce dasu Asbiti, suna zuwa wasu nurses guda biyu mata suka kar6i Aisha, likitan dazata dubata tana ganin yanda jini ya6ata jikinta tace"Subhanallahi wannan tasamu miscarriage ne?" Daya daga cikin nurse din tace"Dr. Bamu saniba yanzu de aka kawo ta" Yana jin haka ya Lumshe Idonsa hawaye me zafi ya silalo daga Idonsa, hannunsa biyu yasa yadafe goshinsa dashi, baisan lokacin daya fara shashshekar kuka ba, kokadan ya manta da ciwon dake hannunsa, sojojin dake tsatstsaye awajan duk jikinsu yayi Sanyi ganin yanda Mahmud Wakili yake kuka da Kansa, wasu sojoji ne guda biyu suka shigo cikin 6acin rai suka tsaya akansa daya daga cikin su yace"yalla6ai munyi nasarar samun Wanda suka aikata wannan laifin, Yanzu haka mun miqasu hannun hukuma, Kuma kafin mu kaisu ma saida muka motsa musu jikinsu, sun kuma tabbatar mana da cewa Hajiya Munirat ce ta turosu"(🙆🏻‍♀️) To.... ko Yaya zata kasance tsakanin Shahaab da munirat yanda yad'ora wa wannan ciki rai? 🤔 Ina labarin Mama da Hajja ne dasuka niqi hanya suka bar qasar sukaje suka siyo kayan Baby?🤔 Muhadu zuwa Anjima 🙏🏻 SHAHAAB LITTAFIN KUDI NE, IDAN KIKA KARANTA BAKI BIYABA NABARKI DA ALLAH BAN YAFEBA 300 NE KACAL 0164549488 Amina muhammad GTbank Mrs Usman ce✍ Page 23 Cikin sauri ya d'ago Kansa ya kalli sojan dayake masa wannan bayanin, lokaci d'aya yanemi kukan dayake yarasa, kafin yayi magana su Hajja da Mama dakuma Ummah da Abba suka shigo asbitin cikin alhini,Ummah tasamu waje ta zauna ta Lumshe idonta,addu'ah take acikin zuciyar ta akan Allah ya dubi wannan bayi nasa yasa kar wannan ciki yafita, Abba kuwa wajan Shahaab yaje ya zauna yana bashi haquri, Hajja da mama kuwa, kuka suke wiwi, mama Sai salati take tana fadin"inna lillahi wa inna ilaihirraji'un,shikkenan yanzu babu ciki yatafi,abinda muka qwallafa rai akansa ashe bamuda Rabon ganinsa" Hajja tace"wannan tsinannun mutane Allah ya kwashe musu Albarka, su Rasa wazasu kawowa Hari Sai wannan bayin Allah, yanzu shi ciki menene nasa daza'a hallakashi tun kafin yazo duniya" Ramadan yashigo asbitin a fujajan sakamakon labarin daya watsu agari, Shima anan yaji, saida yafara zuwa office din Yan Sanda yaji bayanin komai, sannan yataho asbitin, gaba daya yahada uban gumi baima lura da mutanan wajan ba yana zuwa yace wa Shahaab "Wai ita wannan yarinyar metakeji dashi ne? Yaza'ai ta nemi ta wulaqanta mu agari haka kawai saboda tana so ta huce haushi? Idan yarinyar mutane ta mutu tana tunanin za'a Barta ne?" Shahaab yadago Idonsa Dayayi jajir ya kalli Ramadan yace"wallahi tallahi illa daya idan maamah taji, itama munirat saita jishi" Cikin sauri mama ta kallesu yace"munirat Kuma?karka cemin itace ta turo su?" Ramadan yace"yaran sunyi magana sun tabbatar da cewa itace ta saka su,but a yanda sukai bayani kawai tasa suzo suyiwa Aisha illa ne,da alamun batasan cewa tanada ciki ba" Hajja ta dora hannun ta aka tace"laaaa ilaha-illallahu....mahammadurrasulullahi, s.a.w" Mama tace"Yanzu munirat Bayan kokarin kasheni datayi hakan bai mataba saita sa andauki haqqin yarinyar da bataji ba bata Gani ba? Aikuwa yau zamu raba raini tsakanin nida ita, yanda tasa cikin Aisha ya zube wallahi itama yau saita zube"(🙆🏻‍♀️) Tana fadar haka tamiqe da nufin fita, itama Hajja ta d'oru abayanta, likitan datake duba Aisha tafuto,Shahaab yana ganin ta yatashi tsaye, ahankali yace"Dr. Yaya jikin Nata?" Mama da Hajja cikin sauri suka fasa fita suma suka dawo wajan Dr, mama tace"likita cikin yagama zubewa ko?" Dr. Ta kalli Shahaab tace"jikinta da sauqi Alhamdulillah, saide tasamu rauni akanta, sannan Kuma ta zubar da jini da yawa, muna buqatar me irin jinin ta yazo mu dauka Sai aqara mata" Sai Alokacin yasaki ajiyar zuciya, Ummah kuwa har lokacin tayi shiru kawai addu'ah take acikin zuciyar ta,Dr. Ta dubi mama tace"cikinta yana Nan bai fitaba, saboda ankawo ta Asbiti akan lokaci, da andauki tsawon lokaci ba'a kawo taba, to da tuni yazube, yanzu de muna buqatar jinin" Ummah ta daga hannunta sama tana godewa Allah, Hawayen farinciki dakuma tausayin yartata yana tsiya ya daga idonta, Shahaab ya juya ya kalleta cikin sauri ya kauda kansa Gefe, matar tanada alkunya sosai, tunda suka shigo asbitin yaga bata cewa um bare um um, ya tabbatar duk yanda suke jin ciwo aransu basu kaita ba, tafi kowa jin ciwon abinda yasamu Aishan, Amma gata a zaune ta nutsu tana mata addu'ah, saiya sake jin Hankalinsa ya kwanta akan auren Aisha, koba komai tasamu tarbiya ta 6angare guda biyu, Hajja da Kuma mahaifiyar ta, kafin yagama wannan tunanin yaji Abba yana cewa"muje a dauki nawa agani ko zaiyi mata" Cikin sauri Shima Shahaab yace"muje Dr." Duka su ukun ne suka bita lab, aka dauki na Abba da Shahaab, dakuma Ramadan, Ana dubawa a kaga na Abba da Ramadan ne yayi daidai da Nata, na Shahaab baiyi ba,nasu aka dauka aka saka mata, sannan Shima Shahaab sukaje aka duba nashi hannun, inda yaji ciwo. Bai kwanta ba, Ana gama masa sukaje suka duba jikin driver Wanda yaji ciwo harda karaya a hannunsa, sun dade a d'akin sannan suka futo, kan kace me Asbiti Yacika kowa yana zuwa dubashi, banda masu kiransa awaya suna masa jaje kasancewar labari ya watsu ko'ina, ba'a basu damar ganin Aisha ba Sai dare,gaba dayansu d'akin suka shiga, Alokacin itama ta farka Shahaab yana gefenta yana bata tea marar madara kamar yanda ta buqata, ansaka mata bandeji a goshinta, mama tace"Takwara ga abinci kici saiki Sha magani ki kwanta ko?" Yatsina fuska tayi, sannan tace"mama banason cin abincin Nan" Shahaab yayi qasa da murya bakinsa gab da Nata yace"mekike so?" Kai tsaye tace"fruit zansha" Cikin sauri yatashi yadauko mata fruit din dake ajiye agefe, ya zauna yafara bata,Ummah da Abba suka hada ido sukai murmushi, Ummah tace"to Allah yasawaqe, Bari mutafi gida" Hajja tace"to saida safenku Hadiza, Allah yakiyaye hanya" Aisha ta kalleta tace"Ummah idan zakizo gobe kimin kwad'on zogale, Amma karki sa suger aciki, kawai kimin haka" Cikin sauri Shahaab yace"zogale Kuma?" Kallonsa tayi, tayi kalar shagwa6a da fuskarta batace masa komai ba, Girgiza Kansa kawai yayi, baice komai ba Ummah tayi murmushi tace" to zan kawo miki" , sannan suka fita, Ramadan Kuma yabisu abaya domin rakiya. Mama da Hajja ne suka zauna da Aisha, Shahaab da Ramadan kuwa basu tafi gida ba Sai wajan karfe goma Sha biyu saura, a hanya Ramadan ya kalleshi yace"yanzu menene abun yi? Yaya za'ai da mutanan Nan?" Shahaab yasaki ajiyar zuciya yace"zanyi musu waya su lallasa musu jiki sannan su kaisu gidan kurkuku su rufesu, ciki harda ita ogar tasu, inda ace cikin Nan yazube, wallahi saina makata a court" Ramadan yace"yanzun ma ai dole Sai an tura case din court,Amma yakamata kasanar ayi Maka tsakani kaida munirat, saboda yanzu da abun yazo da qaran kwana da tuni cikin da muke murna dashi yazube, sannan driver yamutu, kaga rayuka guda biyu ace a dauki haqqin su abun babu dadi, kawai ayi muku tsakani kaida ita" Shahaab yayi murmushi baice komai ba,shi kadai yasan me yagama shirya wa a ransa, haka suka qarasa gida Ramadan ya ajiyeshi, sannan yatafi gida, shi kadai ya kwana a gidan Bayan yayi wanka, Dasafe Ramadan yakai matarsa asbitin ta duba jikin Aisha, sannan yawuce gida yadauko Shahaab Wanda yake shirin futowa domin tafiya asbitin , Kai tsaye yace"muje wajan wadancen masu laifin" Babu musu Ramadan yajuya kan motar sa zuwa police station, suna zuwa mutanan wajan suka fara bashi girma Ana gaishe shi,Sarai yaga momy a zaune agefe itada yayun munirat su biyu, Sai share hawaye suke, Amma yayi mursisi yarabu dasu yayi kamar bai gansu ba,Kai tsaye d.p.o yawuce dasu zuwa office dinsa,Bayan sun gaisa dakuma jajanta abinda yafaru Shahaab yafuto dawasu takardu guda biyu daga cikin aljihunsa yabawa d.p.o sannan yace"kabawa munirat wannan takardun, sannan atura case din court, ayi musu hukunci daidai da abinda suka aikata, Badon Allah yakiyaye ba, da yanzu driver na, da matata dakuma abinda yake cikinta sun mutu" Cikin sauri d.p.o tace"Angama ranka yadade" Ramadan yasaka hannu a aljihunsa ya ajiyewa d.p.o damin kud'ad'e sannan suka futo daga office din. Ahanya Ramadan ya dubi Shahaab ysce"nayi tunanin zakace ayi muku tsakani kaida ita, sannan ayi musu duka gaba dayansu, Amma sainaga kace abata wasu takardu menene amfanin hakan?" Shahaab yayi murmushi yace" wannan takardun danace abata, tafi Dukan da zance ayi mata, wannan takardun danace abata Sai ta gwammaci ayi mata duka akan ta gansu, babu wani abu dazaka yiwa mace,macen ma wadda take sonka, irin ka saketa, munirat tayi min abubuwa qarshe nasaketa saboda idan nabarta agidana ma to na budewa fitina da tashin Hankali qofa,takardun danace abata Kuma results din maamah ne na samun cikinta, wannan ma kadai ya isheta" Ramadan yayi ajiyar zuciya yace"abun de babu dadi, Allah yasa mudace ya kiyaye gaba" Shahaab ya Lumshe Idonsa yace"Amin" Bayan tafiyarsu Shahaab , d.p.o yabawa wani kofur takardar da Shahaab yabashi yace"abawa waccen matar" Kofur yakar6a yawuce yabawa munirat da idonta ya qeqashe ko d'igon hawaye babu,taso ace taji labarin mutuwar Aisha, saboda ta kowanne ganni Gani take itace tayi mata katanga tsakanin ta da Shahaab, haqiqa taso ace ta mutu saita ga Ina zai Kai rawar jikin dayake akan ta, shikkenan yayi biyu babu,itan dayake qi yasake ta, Aishan dayake so tamutu, tana budewa taci Karo da result din cikin Aisha na farko Wanda akayi mata test a Nigeria, sannan ta duba dayar taga Wanda akayi mata test ne a India, ihu tasaka tana kururuwar kuka, tayi watsi da takardun, lokaci daya numfashinta yafara yin sama, tasa hannu ta dafe qirjinta, cikin sauri su momy suka qarasa suka dauki takardun domin ganin abinda yasa ta cikin wannan hali, suna Gani jikin momy yad'auki rawa,hakan yana nufin Shahaab de lafiyarsa kalau abun daga 'yarta ne, hawaye ne yazubo mata, cikin tashin hankali tafara roqon Yan sandan su taimaka su futo da munirat daga magarqama domin taga halin da yarta take ciki. (littafin kudi ne, idan kika karanta baki biyaba nabarki da ALLAH) ****** Zaune suke a d'akin da aka kwantar da Aisha, Shahaab yazuba mata ido yana kallon yanda take cin kwad'on zogale kamar marar gata, daya gaji da kallon ta saiya dauki wayarsa ya turawa Dr da sukaje wajan sa India saqo ta email dinsa dangane da matsalar cikin Aisha shin yanzun zai iya kusantar ta? Dr Kuma ya tabbatar masa zuwa yanzu Kam babu matsalar komai, Kuma yin hakan zai sake taimaka wa abinda yake cikinta yazama Mai lafiya da Kuma kuzari, idan bayayi dinma akwai matsala, jin wannan bayanin ne yasa Shahaab farinciki, yayi masa godia sannan sukai sallama ya maida wayarsa cikin aljihunsa. Satinta d'aya a Asbiti aka sallameta, duk wata kulawa data dace anbata, sosai jikinta yayi kyau saide fari data sake yi, tunda suka dawo gida Nan ma mama da Hajja basu Barta Takoma part dinta ba, saida tasake murmurewa sosai sannan Hankalinsu ya kwanta sukai maida ta part dinta, zuwa wannan lokacin an yanke wa su munirat hukunci inda aka tura su gidan kurkuku tsawon wasu watanni. Ranar da Aisha Takoma part dinta a ranar Shahaab yasake zama ango, domin kuwa tsawon lokacin Nan daya dauka baiyi ba saida ya fanshe shi, Kuma abinda yasake bashi qwarin gwiwa shine yanda yaga Aishan itama tanaso, a ranar basu zo part din mama ba, suna can manne da juna suna soyaiya kamar zasu cinye kansu. Washe gari suna zaune a dinning suna fara breakfast,Aisha ta miqe tana cewa"bari in sake shan tea dinnan naji yamin dadi sosai" Mama tace"bari inhada miki takwara, yi zamanki" Babu musu ta zauna, mama Kuma ta had'a mata tea din Wanda yake turiri sosai saboda zafi, Aisha tasa hannu zata kar6a Shahaab yayi wuf ya kar6e cup din yace"mama wannan ai yayi zafi dayawa" Hajja tace"to d'aga mata shi zakayi?Dan Allah kudena sangarta yarinyar Nan,kubarta ta dinga aiki da kanta saboda haihuwa ce a gabanta" Cikin damuwa Shahaab yace"ni ban hanata shaba, Amma wannan de yayi zafi dayawa idan kuma yaqona min Baby fa?"(🤭) Hajja ta tuntsire da dariya tace"idan batasha ruwan zafi ba, ai zatasha a wankan jego, zamu gauraya ne" Shahaab baice komai ba saida yaga tea din yadena turiri sannan yabawa Aisha, mama kuwa murmushi tayi tana jin dadin yanda Shahaab yake Bawa Aisha kulawa. Haka rayuwar tasu take tafiya cikin kwanciyar Hankali,idan Aisha tayi fada da Shahaab to akan cikin tane,bata Isa tadanyi gudu ba kokuma wani aikin saiya fara yimata fad'a yana masifa zata kashe masa Baby,hakan dayake mata saiya sake harzuqa ta tabiye masa su dinga fada, daga qarshe Hajja tayi mata fada da nasiha akan ta dinga yimasa uzuri akan cikin, abinda yadade shekara da shekaru ne yana nema yanzu Kuma yasamu, fadan Hajjan ne yasa take haquri dashi Ahaka har Cikin Yacika wata takwas, a Asbiti aka bata umarnin ta dinga yin tattaki saboda jikinta, cikin yafuto sosai ya girma duk Wanda ya ganta zaiyi tunanin haihuwar tazo yau ko gobe ne, Nan kuwa akwai sauran kusan wata daya, yau ma tagama Dan zazzagaya compound din Adede lokacin Shahaab yadawo daga wajan aiki, daga nesa ya hangota tana tafiya daqyar ga uban hips dinta yasake bajewa babu hijabi ajikinta wani mayafi tad'an yafa hannunta d'aukeda d'ata tanaci, Sai wata me aiki a gefenta tana riqe da wani plate Wanda yake d'aukeda d'ata dakuma kayan marmari, bata lura da zuwansa ba, Alokacin da aka bud'e masa mota yafuto harsun shige part din mama, Shima Kai tsaye part din maman yawuce yana zama a kujera ta kalleshi tace"Uncle sannu da zuwa" Yace"yawwa Maamah,Ina Baby na?" Idon mama ta Faka taga hankalinta baya kansu, sannan taja hannunsa tad'ora masa akan cikin tace"tun dazu yaketa motsi" Qasa yayi da muryarsa cikin rad'a yace"ko yanason jin d'umin Babansa?" Babu musu ta daga masa Kai, murmushi yayi sannan yajuya ya kalli Mama yace"mama, adena barin Maa-mah tana fita compound Dan Allah, baki saiya kamata, mutane Sai kallon ta suke itama Sai ciye ciye take agaban su" Aisha tanajin haka cikin shagwa6a ta turo Dan qaramin bakinta gaba,mama ta galla masa harara sannan ta maida Hankalinta kan kallon datake. Shima da yaga bata tanka masa ba, saiya futo da takardu daga cikin briefcase yabawa Aisha yace"kisa hannu a wannan takardun,Ana qoqarin daukar ma'aikatan dasuka dace a kamfanin ki, idan akwai Wanda kike so kisake d'auka saikiyi musu magana su kawo takardunsu Sai a tantance su agani". Kallonsa tayi tace"Uncle Dama inaso In fadama Dan Allah inason in koma makaranta kodan saboda aikin Nan, inaso Nima indinga zuwa office, Ina aiki kamar mata ma'aikata" Lokaci daya yanayin fuskarsa ya sauya, ya kalleta yace"tunanin da kike kenan?" Cikin sauri tace"emana, to tayaya zan riqe company Bayan ba karatu nayi ba? Ai dole in koma makaranta Uncle" Cikin daure fuska yace"wannan tunanin ki kenan,idan Zaki cire karatu aranki, toki cire, domin kuwa,ba-za-ki-yi ba" Yaqare maganar a rarrabe Wani irin kallo tayi masa, bata Tanka masa ba tatashi ta wuce dinning domin kuwa wata irin baqar yunwa takeji, mama ta kalli yanda Aisha take tafiya daqyar, ta juya ta kalli Shahaab tace"kaje Kaci abinci mana, kosai kagama fad'an karatun tukun?" Murmushi yayi yace"mama Dan Allah tayaya zan Barta tatafi wata makaranta?Kuma Babyn nawa waye zai dinga bashi kulawar data dace?tunda cikinta ya tsufa Hankali na atashe yake, fatana kawai tasauka lafiya,Amma ita maganar karatu ma take, Ni wallahi tausayi ma take Bani kwana biyun Nan daqyar takeyin komai, har yanzu bata cika shekara Ashirin ba, ko zata Iya haihuwar ma da kanta?" Mama ta ajiye wayar hannunta wadda take ta gwada Kiran layin Hajja Amma taqi shiga, ta kalli Shahaab tace"tayaya Kuwa zata Iya haihuwa tunda nauyin mijinta ma bata iya daukewa?"(😲🙈) Shahaab ya kalli Mama da sauri, cikin kunya yasosa qeyarsa, batare da yace komai ba sum sum yawuce dinning din Shima.(😂) Please kuyi hakuri da wannan bayawa, nagaji ne 🙏🏻 Shahaab littafin kudi ne, ki biya naira 300 ki karanta, idan kika karanta baki biyaba nabarki keda ALLAH 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN tareda shedar biya ta wannan number 08033300034 Mrs Usman ce✍🏻 Page 25 Zama yayi a dinning d'in yana kallonta qasa qasa,abinci takeci da hannunta dayan hannun Kuma wayarta take danna wa, ahankali yatashi tsaye yazare wayar hannunta, sannan ya zauna tareda ajiye wayar agabansa, Kallonsa tayi, tace"Uncle fati zan kirafa" Abincin yasake qara mata yana fadin"kici abincin tukunna" Batare datace komai ba tamaida Hankali wajan cin abincin, saida taci taqoshi, sannan tafara hamma, kallonta yayi, Adede lokacin itama ta kalleshi, cikin kulawa yace"bacci?" Tace"wallahi, bacci nakeji uncle, tunda natashi Dasafe ban sake yin bacci ba" Abincin sa yakeci cikin kulawa ya nuna mata dinning din yace"kwanta, Bari ingama Sai muje ki kwanta" Babu musu ta dora akan dinning din, har saida yagama cin abincin sannan ya kalleta yace"muje, ko bazaki iyaba na daukeki?" Murmushi tayi tace"zan'iya uncle" Hannunsa takama suka nufi wajan mama, yad'auki kayansa suka tafi, mama tabi bayansu da kallo tana murmushi, cikin ranta tana tunanin wayaga Shahaab da d'a?inajin da zai iya da jikinsa zai dawo da ciwon Aisha, ansan cewa dole a tausaya mata kasancewar ta yarinya qarama ga Kuma halin datake ciki, Amma itama lokacin data haife shi shekararta goma Sha takwas, ita haihuwa aita Allah ce, idan Allah ya sauketa lafiya abunda ake Fata kenan, Amma saka damuwa acikin rai duk ba nasa bane, addu'ah kawai itace mafita. Suna shiga part dinsu ya maida kofar ya rufe, yasaka hannu ya dauketa cimak, basu tsaya ko'inaba Sai dakinsa, akan gadon ya kwantar da'ita, sannan yafara rage kayan jikinsa, saida yacire komai yarage dagashi Sai boxer sannan ya kwanta tareda janyota yashigar da'ita cikin jikinsa, hannunsa ya dora akan cikinta, sannan yayi kissing din wuyanta yace"Cikin Nan tunda ya girma ya hanani rungume mata ta yanda ya kamata" Murmushi tayi tace"nan gaba kadan ma tsakanin mu zai dinga kwanciya" Murmushi yayi Shima yace"idan mace ce to wallahi bata isaba, idan namiji ne Shima wallahi bai isaba,babu Mai shiga tsakanina da matata Sai Allah" Murmushi tayi tana Lumshe idonta tace"me kakeso mu Haifa uncle?" Sake Sakata cikin jikinsa yayi sannan yace"ke mekikeso ki Haifa?" Idonta a Lumshe tace"mace...,inason in haifi 'ya mace insaka mata sunana, sannan Kuma ace tana Kama dakai, Mai dimple irin Naka, indinga yimata kwalliya, indinga yimata vedio, mudinga fita yawo, tazama babbar qawata" Cikin jin dadi yace"nide nafison ki haifamin namiji, saboda shine jigon gida, Kuma shine idan Allah ya rayashi zan'iya dorashi akan komai nawa, zai taimaka min akan komai Sa6anin mace, Amma Kuma a mahanga ta Hankali saide muce Allah yabamu mafi alkhairi ko?" Murmushi tayi tace"hakane, Allah yabamu mafi alkhairi" daga Nan ta Lumshe idonta, tanajin yanda yake kissing wuyanta, hannunsa Kuma yana cikin rigarta yana shafa cikinta. Sun dade suna bacci, bacci Mai cikeda nishadi dakuma jin dadi, shi bai farka ba itama haka, saida suka dauki lokaci sunayi sannan suka tashi, kayanta yacire mata, ya dauketa suka shige toilet, a toilet dinma sun dade acikin ruwa suna murzar jikin junansu kamar karsu rabu, sannan suka futo suka gabatar da sallah,basu je part din mama ba Sai dare, suna zuwa kuwa Aisha taga Hajja tazo, tsaya wa yayi yana waya daga Gefe, ita Kuma ta qarasa wajan su, Hajja ta kalleta tace"meciki" Murmushi tayi tace"Hajja Ina Ummah, meyasa Baku taho tare ba?" Hajja Tace"ina Hadiza Ina zuwa gidanki me sunan qawa?Nima yanzun zuwa nayi muna magana akan yajin da za'a miki" Shahaab daya qaraso falon ya zauna agefen Aisha yace"Hajja wanne irin yaji Kuma?" Kallan sa tayi tace" d'an yajin daddawa mana da akeyi, haihuwa tana tafe ai muma Gara mufara shiri,wannan yarinya Allah de ya saukeki lafiya" Ta qarasa maganar cikin alhini,Aisha ta harareta tace"ji Hajja,Dan Allah ni karkisa naji tsoro, mama kinga Hajja ko" ta qarasa maganar tana kallon mama Mama tayi dariya tace"rabu da'ita takwara, kalau Zaki haihu kinji,keda kike da likita atare dake, babu ruwanki da shan wahala" Shahaab yayi murmushi, zai iya yiwa wani komai Amma baya jin zai iya ta6ukawa Aisha wani abu, kwata kwata bashida qwarin gwiwa inde Aisha tana cikin tashin hankali, gaba daya rud'ewa yake yarasa meyake masa dad'i. Har qarfe Tara Hajja tana gidan, tana zaune suna Dan ta6a hira itada mama, tana Kuma Kiran mutanan Chamo suna ta magana akan shirye shiryen haihuwar Aishan, Sai wajan karfe goma sannan tatashi zata tafi mama tasa hannu tajata ta zauna tace"ai kinzo kenan,narasa me kike yi acan gidan idan kinje wallahi, ki zauna anan mana mudinga Dan zantukanmu" Hajja tace"ko? To ai can dinma Hadiza tana zaune ita kadai babu dadi, Kuma idan muka zauna din muna Dan ta6a hirar mutanan mu nacan" Shahaab yayi murmushi yace"kiyi zamanki kawai Hajja, itama ba mijinta yana Nan ba" Cikin sauri Aisha ta kalleshi tareda mintsi ninsa, murmushi yayi yana shafa wajan yace"yi haquri, ni bada wata manufar nafada ba" Mama tace"ai Gara dakika mintsine shin kozai tuna akan surukansa ake magana" Hajja tace"to Bari in zauna, idan na kwana biyu anan Sai inje can itama namata kwana biyu" Haka sukaci gaba da Zaman su afalon suna kallo suna hira, har shadaya na dare sannan suka koma nasu part din, acan dinma Bayan ta kwanta shi computer ya dauka yadan rage wasu ayyukan sannan shima ya kwanta. Haka mama ta dinga yaudarar Hajja ta hanata tafiya sukaci gaba da zamansu a gidan cikin kwanciyar hankali har cikin Aisha Yacika wata Tara cif, tun daga Nan Kuma hankalin kowa yadawo kanta, ma'aikatan gidan ma kowa ido yazuba mata yana jira yaga mezata Haifa, sunsan cewa uban gidan nasu Sai yafi kowa murna akan haka. Tun Ana tunanin haihuwar akan lokaci har suka daina, saida ta qara sati biyu, Alokacin ma basuyi tunanin haihuwar zata zo ba, itama Kuma kasancewar haihuwar ba sanin ta tayi ba, Sai hankalin ta bai kawo mata haihuwar ba, yau tunda safe yafita wajan aiki, Alokacin tana bacci bata tashi ba, tun shekaran jiya take danjin ciwon baya, saitayi tunanin ko yawan kwanciyar datake ne, ga mararta tana mata nauyi, babu Wanda ta fadawa wannan sauyin yanayin nata Baccin Nata yayi dadi sosai, kad'an kad'an mararta tana mata ciwo, tasa hannunta akan marar taci gaba da bacci, can bacci yayi Nisa taji wani irin ciwon Mara yataso mata, cikin azaba tafarka, yatsina fuskarta tayi, sannan ta sakko da qyar ta wuce toilet tafara fitsari, anan taci karo dawani irin ruwa yana zuba ajikinta,hakan yasa tacire kayanta tafara wanka, kafin tagama wankan taji marar Tata tasaki, ahankali tagama komai tafuto tayi sallah, sannan tasaka wata doguwar Riga me fadi ta nufi part din mama, ahankali take takawa ma'aikata Sai sannu suke mata, mamaki yasake kamata jin wannan ruwan yana sake bin jikinta, tana saka qafarta a part din mama, taji gaba daya qafafunta sun riqe, mararta ta d'aure dawani irin ciwo na fitar Hankali, cikin azaba ta tsugunna awajan tana runtse idonta, mama da Hajja suna zaune kwata kwata hankalin su baikai bakin qofar ba, Aisha kuwa idonta a runtse yake wani irin gumi ya tsatstsafo mata, jitayi wani irin abu yana neman rabata gida biyu, tsananin azabar dataji ne yasa tasaki wani irin qara tareda fadin"mama!!!" Azabure suka juya itada Hajja, suna ganin Aisha a tsugunne suka fita a guje sukayi kanta, Hajja tana duddubata ta kalli Mama tace"Aysha inajin haihuwar ce tazo" Mama da jikinta yakama rawa tace"eh gashinan Kam Naga kamar akan gwiwa take" Cikin sauri suka d'ago ta Hajja ta riqeta tana mata sannu, hawaye ne yafara bin fuskarta tana yarfe hannu, mama kuwa a guje tashige d'akin da suka adana kayan haihuwar ta Dauko wasu kayan, sannan tafara Kiran wayar Shahaab, yana d'auka tace"kana inane" Yace"ina office mama,meeting muke" Tace"to yarinyar Nan ce babu lafiya, Ina tunanin haihuwar ce tazo, gashinan Nan de zamu tafi asbi..." Kafin tagama magana taji ya kashe wayar, wayar ta kalla kawai ta jefata cikin Jakarta, Alokacin har Hajja sun qarasa gaban mota, gaba daya ma'aikatan gidan kowa mamaki ne ya kamashi ganin yanzu yanzu ta wuce ta gabansu Amma har naquda tatashi, suna shiga cikin mota driver yaja a guje suka fice daga gidan. Ko Nisa basu yiba suka hadu da Shahaab, yana ganin motar su ya tsaida su, yafuto daga motar dayake, yakoma cikin motar su mama, yashiga gaban motar sannan driver yaja, juyawa yayi ya kalleta kwata kwata ma bata cikin hayyacinta, mama da Hajja sun sata atsakiya Sai sannu suke mata, yayinda Hajja take goge mata Hawayen idon Nata, shikam Idonsa ne yayi zuru zuru kamar marar lafiya, baya cikakken minti daya, batareda ya juya ya sake kallon ta ba, suna zuwa asbitin aka kar6eta, Hajja tafara Kiran wayar Ummah da Abba zata sanar dasu, Shahaab ya zauna yad'ora Kansa akan hannayensa, abun duniya yataru yayi masa yawa, yayinda mama take zarya takasa tsayuwa haka Kuma takasa zama waje d'aya,suna jiyo yanda Aisha take kuka tana salati, har kusan awa daya bata haihu ba, ahankali yatashi yacire suit din jikinsa, yacire agogon hannunsa ya ajiye su anan, Kai tsaye yashige cikin d'akin, mama da Hajja suka bishi da kallo, yanayin da yaga Aisha yasa gabansa faduwa, ba kowa ne yafado masa Arai ba Sai mama, itama haka Tasha wahala kafin ta sameshi, kasancewar sunsan cewa Shima yasan aikin shiyasa babu Wanda ya hanashi, sun dauki tsawon lokaci Ana abu daya, sannan haihuwar tazo gadan gadan, shida Kansa ya qarata, sannan ya kar6i haihuwar ta da Kansa, shi Kansa yayi mamakin yanda yasamu wannan qwarin gwiwa, lokaci daya su Hajja sukaji kukan Baby Yacika falon, hawaye mama tafara, tana zubawa Allah kirari dakuma godia agareshi, acikin d'akin ma Shahaab yana ganin Babyn a hannunsa wani irin hawaye me dumi ya zubo daga Idonsa, nurse din dake gefensa tasa hannu ta kar6i Babyn sannan tace masa"yalla6ai congratulation, Baby boy ne" Hannu yasa ya goge Hawayen, sannan yafara cire safar hannunsa, yakoma ga Aisha yana kallon ta, wadda tuni baccin azaba yayi gaba da'ita, sauran nurse din Kuma suka fara gyara mata jikinta, saida aka gyara baby tsaf, aka saka masa kayan Sanyi farare masu mutuqar laushi, sannan suka Bawa Shahaab shi, nurse din tace"yalla6ai gashi,Bari mu qarasa gyara madam" Babu musu ya kar6i Yaron Wanda yakasa dauke Idonsa akansa, Yaron yana bala'in kama dashi sosai, babu abinda yabari nasa, fari ne tas 6ul6ul dashi kamar ba Aisha ce ta haifeshi ba. Yana futowa mama da Hajja da Kuma Ummah da Abba Wanda Zuwansu kenan sukayi Kansa, gaba dayansu kowa kokari yake ya kar6i Babyn, Hajja ce tayi nasarar kar6arsa, ahankali yasaka hannu yasake goge Hawayen Idonsa,yace"nagode mama" Mama tace"godia tame Kuma Mahmud?" Saida yasake goge Hawayen sannan yace"dakikasa nazama likita, duk da baki barni nayi aiki ba yau gashi dalilin karatuna na temaki matata" Murmushi tayi ta kalleshi Tace"to naji, yanzu de kayi shiru kuka Kuma ya qare Mahmud, saide ka godewa Allah bisa kyautar Dayayi ma" Cikin sauri Hajja tace"um um Aysha barshi ya koka, irin wannan Baturen d'a haka ai dole ubansa ya koka harda shashsheka..."(😂) Gaba dayansu dariya suka saka, Shahaab yayi mata wani irin kallo me cikeda harara, sannan ya goge Hawayen idon nasa, mama Tace"Ashe zaka iya kar6ar haihuwar? Yaya jikin nata to?" Ahankali yace"tana bacci, bansaniba Kota farka, nafuto zasuyi mata dinki" Hajja tace"oh wannan yarinya tana ganin dinkuna, gana Daren farko gana haihuwa" Shahaab yaji wata irin kunya ta kamashi kamar ya nutse awajan, kasancewar Ummah da Abba suna wajan, Sai akai sa'ah Adede lokacin aka kira wayarsa, cikin sauri ya matsa Gefe yafara wayar, daga office dinsu ne, sunyi tunanin zai dawo aci gaba da meeting din, Sai yafada musu labarin haihuwar, yakuma nemi excuse awajansu,Bayan Nan Kuma yakira Ramadan, yana dauka yace"Albishirinka" Ramadan yace"goro" Shahaab yace"Maamah tasauka,Nima nasamu Baby boy dina" Ramadan yace"Alhamdulillah, Allah abun Godia, kuna Ina yanzu?" Cikin farinciki yace"muna Asbiti" Ramadan ya kashe wayar, shikuma Shahaab yakoma wajan su Hajja, yana zuwa yaga Yaron yana hannun Ummah, Adede lokacin nurse ta futo tafada musu cewa sun maida ta Dakin hutu idan anjima zasu iya shiga su ganta. Zuwa yamma mutane sun cika asbitin, mutanan dayake meeting dasu, dakuma Wanda Ramadan ya faffadawa kowa kokari yake yazo yaga Yaron Mahmud Wakili, gaba dayansu suna cikin ke6antaccan Dakin da aka Kai Aisha, tana zaune kalau da'ita kamar ba'ita ce tagama kukan haihuwa ba, tea ne a hannunta tanasha Sai murmushi take, Shahaab ne yabude Dakin yashigo hannunsa d'aukeda Babyn, ya qarasa wajan ta ya zauna tareda ajiye mata Babyn yayi qasa da murya yace"kibashi nonon yasha" Harararsa tayi, babu Wanda yaji me yace mata,kawai de duk mutanan d'akin sunga yanda ta zuba masa wata irin harara me kama da kallon luv, Hajja tayi dariya tace"me sunan qawa yau an dandani ciwon haihuwa,ta gaba Kuma Sai yanbiyu insha Allah" Mama tace"haihuwa yaqin mata kenan, Allah de ya raya,yi sauri kigama shan tea din kibashi nono yasha" Da daddare aka sallamesu,acan gida ma falon mama cika yayi da mutane, mutanan Shahaab suna zuwa ganin baby, mutanan mama suna zuwa, Ummah ma bata koma gida ba, Sai wajan shabiyu saura sannan Abba yazo suka tafi, Alokacin kuwa Hajja tahada mata kunun kanwa tanasha, banda farfesun kaza da mama tahada mata da kanta, zuwa wannan lokacin Kam labari yagama ko'ina, shugaban EFCC Mahmud Wakili, yasamu qaruwa, har gajiya yayi da amsa kira, wasu daga bangaren kasuwancin sane, wasu Kuma daga office dinsu ne, banda turawa dayake mu'amula dasu Yan wata qasar kowa Sai ala sanya Alkhairi yake masa kasancewar sun San cewa ya dade bai samu haihuwar ba. Ramadan kuwa yakawo matarsa gidan itama anan take shirin kwana, a Dakin mama Aisha ta tare, anan suka kwana itada baby da Mama, su Hajja Kuma suka koma wasu dakunan, tunda akai haihuwar mutane suke sallama a gidan, wani ma zaiyi tunanin wani Dan qaramin biki ake, kullum cikin dora tukunya ake, Ana saukewa, hakan kuwa Sai yayiwa mama dadi, saboda inda babu mutanan da tuni Shahaab ya hanasu sakat, Dasafe kafin yatafi wajan aiki yana shigowa ya gansu itada Babyn, haka mama take kafawa ta tsare saiya tafi, sannan itama take barin Dakin, kulawa take Bawa Aisha yanda ya kamata, banda Hajiya zaliha datake mata Dan gyare gyare daga Gefe, abinci suke dura mata tanaci tana qoshi babu alamun yunwa atare da'ita, shiyasa danta yake samun wadataccan ruwan nono ko madarar ma ba'a bashi, kwanansu shida da haihuwa gida Yacika da mutane, mutanan jigawa duk sunzo ciki harda Walida, faty ma tabiyo ayarin kano itama tazo, gida yayi maqil ko lokacin auren ba'ayi wannan taron ba, Shima yana can ayyuka sunyi masa yawa saboda dinner dasuke shiryawa shida mutanan sa, kwata kwata yau din tun safe daya fita, Bai dawo gida ba Sai wajan Sha biyu na dare Alokacin anriga angama tsara komai, yana zuwa gidan yawuce part din mama, yaji dadin yanda baqin gidan sukai bacci, shiyasa Kansa tsaye yawuce Dakin mama, Adede lokacin mama zata shiga toilet,Hajja Kuma tabawa Aisha Yaron ta miqe itama zata tafi dakinsu ta kwanta,Adede lokacin shikuma yaturo kofar yashigo, mama ta kalleshi tace"Daga Ina kake da wannan Daren?" Zama yayi akan gadon yana gaida Hajja, sannan yace wa mama"ina taredasu Ramadan awaje ne,mungama shirye shiryen dinner ne,nagaji wallahi mama, babu abinci ne?" Mama tace"bari in futo daga toilet saina hadama wani abun" Ledar daya shigo da'ita yabawa Aisha yace"ga wannan" Cikin ladabi ta Kar6a Tace"to Angode" Sannan tafara budewa, leshi ne me launin baqi da golden, an dandatsa mata dinkin Riga da siket Mai kyau, Sai Babban mayafi da takalmi me tsini, dakuma wata sarqa babba, tana duba kayan tabawa Hajja tace"Hajja kingani" Hajja ma tafara daga kayan tana fadin"masha Allah, Amma kayan nan sunyi kyau sosai wallahi" Mama tafuto daga toilet taga kayan itama ta d'aga tace"sunyi kyau sosai, Allah yaqara budi" Tajuya ta kalli Aisha tace"saiki saka su goben, shi Dama wannan angon na Hajja nariga na ware masa kayan sa, anko zasuyi shida Hajjansa" Aisha tayi murmushi tana maida kayanta cikin ledar su, sarqar tasaka acikin gidanta, anan taci Karo da raceipt din sarqar, tana dubawa ta d'ago Kai ta kalleshi taga hankalin sa yana kan Yaron yana wasa da hannunsa, cikin tsananin mamaki tace"Uncle 20 million fa....meyasa ka siyo....?" Tana qarasa fadar hakan hawaye yazubo daga idonta, kallon ta yayi yasaki ajiyar zuciya sannan yace"menene Kuma abun kuka?" Mama ma tad'auki takardar tagani sannan tabawa Hajja itama tagani, Hajja tace"Shahaab wannan kudin ai yayi yawa, kudin sarqa kawai Ina zatakai wannan sarqar?" Mama tace"Aysha wacce irin magana kike haka? Wa gareshi Bayan ni idan ba itan ba? Yau idan na kwanta Dama Bayan ita da wannan Yaron da Allah ya basu wayake dasu a duniyar?saboda sufa yake neman kudin, idan yabata duka abinda ya mallaka ma ai be fadi ba" Hajja ma hawaye tafara, takasa cewa komai, Shahaab kuwa matsawa yayi kusa da Aisha cikin rad'a yace"kiyi shiru mana, idan Kuma kin renane to shikkenan kici gaba, nide bazan Dena siyo waba" Cikin sauri ta d'ago ta Kalle shi sannan ta murguda masa baki, murmushi yasaki, itama mama cikin murmushin tafice daga d'akin, tana fita aka dauke wuta, tadawo Dakin tana cewa"Mahmud Bani wayata akan gadon Nan, sun dauke wutar" Kafin Shahaab yayi magana Yaron yasaki wani irin kuka, Hajja tace"toshi Kuma me aka masa?" Aisha tace" bayason duhu, idan zamuyi bacci muna kashe wuta zai fara kuka" Shahaab yayi murmushi yabawa mama wayarta, sannan ya kunna fitilar wayarsa, Yaron yana ganin hasken wayar yayi shiru, Aisha ta kalli Hajja tace"kingani ko?" Tahunar gidan aka kunna lokaci daya haske ya gauraye ko'ina, Hajja tace" tabdi, kaikaji yaro da wani tsugudidi, awanan qasar tamu ne zakace bakason duhu? Yaya kake acikin uwar taka? Badan ma Allah yasa kafad'o cikin gidan Nan ba Ina zakaga hasken bare har kasaba dashi?" Shahaab yayi murmushi tareda daukan Yaron ya kalli Hajja yace"to yanzu de tunda yafad'o Nan din ba shikkenan ba?ai gashinan wuta tazo ko?" Yaqare maganar cikin sigar tambayar Yaron, mama ce tashigo takawo masa indomie wadda taci kayan hadi da Kuma nama ta ajiye masa, da gorar ruwa guda daya, babu musu ya ajiye yaron yafara cin abincin, Hajja ta musu saida safe tafita, mama kuma tad'auki sallaya ta shinfida acan gaban d'akin tatada sallah. Har yagama cin abincin mama bata idar ba, ya kalli Aisha data fara Bawa Yaron Nono, sannan yajuya ya kalli Mama yaga tana sujjada har yanzu, ahankali ya matsa kusa da'ita, cikin sand'a yazare bakin Yaron daga kan nonon dayake Sha yayi sauri yad'ora bakinsa akai yafara tsotsa, zaro ido tayi cikin sauri takai kallon ta wajan mama taga har yanzu bata dagoba. Kansa tafara janyewa daga qirjinta, Amma yaqi Dagowa saima Idonsa dataga yana Lumshe wa yana tsotsar nonon cikin wani irin Salo, mama tana Dagowa Aisha tacire bakin Shahaab daga kan nipple dinta, cirewar datayi batareda ya shirya ba shiyasa Sai hakan yabada wani irin sauti d'as, cikin sauri ta maida wa Yaron nonon sa, Shahaab kuwa Kallan ta yake da Idonsa dasuka qanqance, cikin rad'a yace"kadanfa nasha" Da idonta tayi masa nuni da mama, ahankali ya juyo ya kalleta, kwata kwata ya manta tana d'akin, cikin mutuwar jiki yad'auki wayarsa yafice daga d'akin Sai hada hanya yake, mama datayi sallama ta bishi da kallon mamaki, ko menene yasa shi a wannan yanayin? Domin kuwa itade Batasan aikin daya taya d'annasa ba(🙊) Washe gari Dasafe aka rad'awa yaro sunan kakansa(Ibrahim, wato Wakili) suna kiransa da Daddy, taro yayi taro mejego tashiga tafita, baqi ta gansu Kala Kala tun Ana mata bayanin mutanan har aka dawo aka Dena, da yamma suka shirya suka nufi wajan dinner, Daddy yana hannun Shahaab, yayinda dayan hannunsa yake riqeda Aisha wadda tayi mutuqar kyau kamar ba gobe, wajan dinner kuwa ya tsaru sosai, kafin kashiga wajan ma zakaga kofar dazata kaika cikin Dakin taron anyi mata ado dawani irin fulawa masu kyau, atsakiyar fulawar anrubuta DADDY, babu mutane sosai awajan, Amma Kuma duk Wanda kagani kasan cewa wani qusan ne acikin qasar, babu Wanda wajan bai hadaba daga ma'aikatan hukumar su, har ma'aikatan kamfanun nukansa, dakuma mutanan Arziqi dayake hulda dasu, saikuma turawa farar Fata Wanda suka zo daga qasashen qetare, Bayan anbude taro da addu'ah baban Baby yatashi yayi Dan jawabi cikin harshan turanci, Bayan yagama aka tafa masa, daga Nan aka Bawa mutane damar magana kowa yana kokarin tashi yaga yatayashi murna, Baby Daddy kuwa baya hannun Aisha, ita kanta bazatace ga wajan Wanda Yaron yake ba, tana zaune kusa da Shahaab Sai Fara'ah takeyi daidai misali, duk Wanda ya kalli kayan jikinta, dakuma sarqar wuyan ta, yasan cewa eh tabbas ta tabbata ita din matar Mahmud Wakili ce, photuna aka fara cikin aji babu wani tashin Hankali kowa yana zuwa ayi dashi, Ummah da Abba ma ba'a barsu abaya ba, suma sunje anyi pictures Kala Kala, saida aka nutsu kowa ya zauna masu cin abinci sunaci, can ta hango Walida da Faisal Yaron Hajiya zaliha suna Diban abinci kasancewar kowa da Kansa yake zuba abinda yakeso, Sai wani magana suke suna qus qus, Adede lokacin Kuma matar Ramadan takawo mata Daddy, kar6arsa tayi tafara jijjiga shi, Shahaab yadan sunkuya dede fuskarta yana tambayar ta"meyake sone?" Kallan fuskar Yaron tayi tace"yunwa yakeji Uncle,Kuma ban taho masa da madara ba" Cikin sauri yace"to yanzun meyake nufi? Meyake so?" Kallan sa tayi tasaki murmushi tace"nono" Kansa ya Girgiza, cikin sauri yace"karki bashi nono anan,bashi ruwa kawai" Murmushi tayi, ganin yanda ya wani rikice saboda tace Yaron yanason Nono, tace"nifa ba bashi zanyi ba" Yatsina fuska yayi yace"ai Gara mukoma gida hakama,kar yunwa ta kamashi" Cikin jin dadi Tace"to" Dama itama Zaman ya isheta, ahankali yatashi yanufi Ramadan, Wanda yake ta aikin kar6ar gift din da mutane suke zuwa musu dashi. Duk yanda yaso su tafi Alokacin hakan bai samu ba, saida suka qara wasu awannin, sannan taro yatashi cikin amince dakuma mutunta juna. Adaren Kam wanka kawai sukayi itada Baby, sukaci abinci suka kwanta, ko kyaututtukan da Daddyn Nata yasamu basu samu damar dubawa ba, Sai washe gari da safe sannan suka Gani itada Shahaab din,ita kanta tasan cewa tasamu alkhairi sosai a wannan haihuwa, bata da bakin da zata godewa wannan ahli saide ta saka musu da iya abinda zata Iya kawai. Haka sukaci gaba da bata kulawa har tayi arba'in, har zuwa wannan lokacin bata koma part din taba, tana d'akin mama,kulawa kuwa tana samu daidai gwargwado, tsaf saida mama tagama hadata, banda Hajja dakuma ummanta dasuke nasu qoqarin suma daga Gefe, tana samun kulawa yanda ya kamata, kayan gyaran datake amfani dasu ne yasa jikinta yasake yin mulmul kamar ka latsa jini yafuto, Daddy kuwa batasan wahalar saba, batada me raino haka Kuma batasan rainon saba, idan Hajja bata dauke Shiba, to yana hannun mama, idan mama bata dauke Shiba, to suma kansu ma'aikatan gidan sha'awar daukan Yaron suke, shiyasa tsakanin ta dashi saide in yana kuka ne, zata rungume shi tabashi nono yasha, saikuma wasa datake masa. Zuwa wannan lokacin mama takai Shahaab maqura, yayi haquri yayi haquri harya gaji, yana gama qirgawa yaga sunyi kwana arba'in, yafara murna Aisha zata dawo part dinta, Sai kuma mama ta bijiro masa da maganar ganin dangi, haka yayi shiru kamar ya rusa kuka, Badon yasoba suka shirya itada Hajja da maman, suka wuce Niger wajan dangin mahaifinsa, satinsu daya acan, suka wuce garinsu Hajja, acikin gidansu Aisha Wanda Abba ya gyara shi zua na cement suka sauka, sun zaga dangi sosai har kano sunje, nanma satinsu daya, sannan suka dawo Abuja, a ranar da suka dawo kuwa, mama ta rakata Dakin mijinta itada shirginta,Bayan tafiyar mama itama ba zama tayi ba, tashi tayi tasake wanka itada Daddy ta sauya musu Kaya, tasaka wata fingilar Riga wadda take baiyana komai mata a fili, sannan ta daure gashin kanta tad'auki Daddy suka dawo falo suna kallo, yana dawowa daga wajan aiki a tsatstsaye yaci abincin, yayiwa mama da Hajja sallama yagudu wajan matarsa, yana zuwa kuwa ya gansu afalo suna kallo, Daddy Kuma ta dorashi akan cikinta yanata wasansa,cikin farinciki yasa hannu yad'auki Yaron yana dagashi sama, Aisha ta daga Kai ta kalleshi tace"Sannu da zuwa Uncle" Zama yayi akan kujerar Shima, ya dauketa yad'ora ta akan cinyarsa, sannan yad'ora Daddy akan cinyarta, yahadasu ya rungume su a qirjinsa, cikin rad'a yace"sannunku da zuwa maamah,nayi kewarku sosai, kamar inyi kuka wallahi" Da niyya ta gyara zamanta akan cinyarsa cikin wani irin Salo Wanda tasan dole Sai yaji ajikinsa, sannan tasaka hannu tafara 6alle botir din gaban rigar sa tana cewa"muma ai munyi missed dinka,Musanman Daddy" Wani irin yarrr yaji ajikinsa, sakamakon yanda yaji tana murza mazaunanta akan cinyarsa, cikin sigar rad'a yace"da gaske?" Tace"sosai" Kissing din wuyanta yayi yace"to ita maman Daddyn batayi kewata ba kenan?" Murmushi tayi tace"maman Daddy Sai anshiga daga ciki sannan zata nunawa Abban Daddy yanda tayi kewarsa" Cikin sauri yatashi yadaukesu cak itada Daddyn, suka wuce dakinsa, tana ganin yanda Hankalinsa yatashi ta lalla6ashi tace"Uncle kayi wanka mana" Cikin sauri yace"to Amma yanzu zan futo" Yana fadar haka yashige toilet, tana ganin shigar shi tatashi tadauko wani tsumin ta tafara Sha, Daddy yana ganin tashin ta yafara kuka,ita kuwa tarabu dashi saida tagama shan tsumin ta sannan tadawo tadauke shi, Shima Kuma yayi zuciya yaqi yin shiru, batayi tsammani ba Sai ganin Shahaab tayi yafuto daga toilet din jikinsa duk kumfa, iya fuskarsa kawai ya wanke, cikin mamaki ta kalleshi, kafin tayi magana yace"maamah wanne irin rashin Imani ne wannan Zaki bar yaro yanata kuka shi kadai?kina d'aki yana d'aki Amma saboda rashin tsoron Allah kinbarshi yana kuka kan gari?" Bakinta ta turo gaba sannan tace"wankafa kake, Kuma inde kace kukan Daddy zaka biyewa saide in ba zakayi wankan ba,Yaya yakeso namasa?" Cikin sauri yakoma toilet din Sai jinsa tayi yana sakin ruwa ajikinsa (😂) A fujajan yafuto daga toilet din, ya nufesu, zama yayi akusa da'ita gaba daya fuskarsa damuwa ta bayyana qarara, daukan Yaron yayi yafara zagaya d'akin dashi, Amma mursisi yaro yaqi yin shiru, Dan qaramin tsaki yasaki yadawo ya zauna kusa da'ita sannan ya kalli Daddy yace"inaso inmori wannan lokacin kaikuma Naga alama gaba daya nema kake kasa abun yafita daga raina, Kuma wallahi daqyar nake bacci" Aisha ta kalleshi ta kawar da kanta, Dan dariya ce takeso ta kamata, saida ta danne dariyarta sannan Tace"to kawai ka haqura Uncle , tunda Daddy yana kuka ai abu bazai iyu ba" Cikin sauri yace"a a,ai ba za'ayi hakaba, Kar6e shi kifara sallamar sa tukunna,bashi yasha ko zaiyi shiru" Babu musu tasaka masa nono, Dafarko Qin kamawa yayi saida yagama kukan sannan daqyar yakama yafara Sha, Shahaab kuwa yazuba musu ido yana kallon su ya naniqe ajikinta kamar zai maida su ciki,ahankali Shima yafuto da d'ayan, yana shafa mata shi, Kallonsa tayi kafin tayi magana yad'ora bakinsa akai Shima yana Sha, saide yanda Shahaab yakesha ahankali yasa ta Lumshe idonta, tsawon lokaci suka dauka Ahaka, daqyar Aisha ta bude ldonta, taga Daddy harya fara bacci, sannan tasa hannu ta zare nonon daga bakinsa,Shima Shahaab ahankali ya d'ago Kansa ya kalleta, cikin shaqaqqiyar murya yace"maamah bai isheshi bafa, kinga ko kawar da Kansa baiyiba" Cikin wani irin yanayi tace"yanzu Uncle Daddyn ne zai kawar da Kansa?beyi fa wannan wayon ba" Cikin yanayi na sha'awa yace"haba?to tunda shi ya qoshi ni Bari insha Mai sauran ko?" Kafin tace wani abu yaci gaba da abinda yake. Mutara zuwa anjima 🙏🏻 SHAHAAB littafin kudi ne,300 ne kacal, kada ki karanta idan kinsan baki biyaba, idan Kuma kika karanta nabarki da ALLAH 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN tareda shedar biya ta wanna number 08033300034 Amina✍🏻 Page 22 Daqyar tasamu tasaka Daddy cikin gadonsa, sannan tad'ora hannunta akan lallausar sumar sa tana shafa wa, wani irin Salo yake mata Wanda yasa tafad'a kan gadon batareda ta shirya ba, babu musu Shima yabita, tsawon lokaci yana abu daya, ahankali wata iska me dadi ta buso ta window, labulaye suka fara kad'awa, daqyar yadago Kansa ya kalli window Adede lokacin aka fara wani irin ruwa Mai had'eda wata iska Mai dadi, ahankali yazare bakinsa daga kan nipples dinta, yatashi yarufe windows din dakin sannan yadawo yaci gaba da abinda yake, bakajin sautin komai Sai nishin Aisha, daqyar ta bude idonta ta kalleshi, cikin shagwa6a tace"Uncle zafi sukemin fa,karka shanyewa Daddy duka" Shiru yayi mata kamar baiji abinda tace ba, ahankali yayi mata wata irin zuqa Wanda hakan yasa Aisha tasaki wani irin ihu, sannan yahad'e bakinsu waje d'aya, Bai saurari yanda take kokarin cire rigar jikinta ba, kawai hannu yasa yayagata, a hauka ce yake mata komai,kamar wanda ya shekara baiyi ba, ita kanta Aishan itama a buqace take, saboda magungunan dasu mama suka dinga dura mata, wani irin qara suka saki atare lokacin dazai shigeta, cikin jin dadi yasaki wani irin nishi lokacin da yaji yashiga daqyar, ko minti uku baiyi ba yasakar mata wani irin kuka yana sake rirriqeta, yanda taga ya rikice ne yasa tafara kokarin rufe masa baki, cikin sauri ya qwace bakinsa Sai sambatu yake yi Wanda ta tabbatar da cewa shi Kansa baisan meyake ba, dadin da takeji ne yasa itama ta dinga taimaka masa domin kuwa zata Iya cewa tunda akai musu aure bata ta6ajin dadi kamar na yau dinba, batasan lokacin data fara masa kukan shagwa6a ba tana fada masa kalamai Wanda suka sa yasake jin qwarin gwiwar yimata salon dayake sake haukata ta,tun Aisha tana kukan shagwa6a dataji abun yafara fin qarfin ta saita fara kukan gaskiya, Amma shikuma Alokacin nema yake jinsa asama, Bai saurara mataba saida yaji yasamu cikakkiyar gamsuwa, ruwan da'ake kwarawa ne yasa alokacin daya saki wani irin ihu ba'aji Shiba, rungume ta yayi sosai ajikinsa, ahankali wani irin hawaye yana sake fita daga Idonsa, numfashi suke maidawa gaba d'ayansu, ahankali yakai Kallonsa kan gadon Daddy, anan yaga sun tashi Yaron saide Kuma baiyi kukaba kawai de wasansa yake yana daga qafafunsa sama, kallonta yayi yaga tana hawaye, murmushi yayi yad'ora bakinsa akan kumatunta ya share mata Hawayen da harshensa, sannan ya mirginota tadawo Kansa, yafara bubbuga bayanta alamun lallashi, cikin shagwa6a tace"kaga kasa Daddy na yatashi Kuma fa idan yafara kuka bazaka tayani lallashin saba" Cikin jin dadi yace"waya fada miki haka?nine ma zan lallashe shi, Kuma ai baya kukan ma, bakiga yabar babansa yaji dadinsa yanda ya kamata ba?" Cikin shagwa6a tace"uhm...uhm" Cikin sauri yace"menene?mekikeso?" Tace"bakai bane" Lumshe Idonsa yayi yace"kece de,duk kinsa nakasa riqe kaina, Allah yasonima ruwa ake" Murmushi tayi tace"toni menayi?" Sake rungume ta yayi yace" kece kikai komai ma kuwa,tunda kika shigo cikin rayuwata nadena iya saita kaina,kin sauya min rayuwa ta gaba daya, kin haska min duhun daya mamaye idanuwana, Ina sonki fiyeda kaina maamah, Bana fatan kasancewa da kowacce irin mace Bayan ke a duniyar Nan,kin sake min dadi fiyeda baya, Kuma kece kikasa nasakaki kukan saboda kalaman da kike fadamin sune sukasa naqara samun kuzari fiyeda lokacin Dana fara, maamah Dan Allah karki barni kinji...." Wani irin dadi ne yakama Aisha, bata ta6a tunanin haka ta kwarewa Shahaab dinba Sai yau, ita Kam Ina ita Ina rabuwa dashi?ahankali ta sauka daga Kansa, sannan tasaka hannayenta ta rungume shi, ta kalleshi cikin ido tace"tayaya kake tunanin zan iya rabuwa dakai?jin dadi na dakuma walwalata bazasu ta6a samuwa ba muddin Bana tare dakai, idan rayuwa bazata iyu batareda iska ba, to tabbas Aisha bazata iya rayuwa batareda Shahaab ba, Ina sonka Baby" Ta qarasa maganar cikin sigar rad'a, murmushi yayi yasaka hannunsa ya rungume ta, cikin shagwa6a yace"maamah..." Tanajin salon yanda Yakira sunan Nata, tasan cewa qari yake nema, cikin shagwa6a itama tace"Anjima kayi" Yace"sosai kamar na yanzu?" Tace" idan kanaso fin hakama" Cikin jin dadi yace"thank u maamah" Yasaka hannu ya daukata suka shige toilet, sabon wanka sukayi, sannan Aisha tasake gyara Dakin suka shirya suka dawo falo Daddy yana hannun Shahaab, ita Kuma ta wuce fridge tadauko chocolate tana Sha, kallo suke cikeda farinciki gaba dayansu, harda Daddy Wanda kawai hasken TV ya zubawa ido yana kallo. Ranar basu koma part din mama ba, itama batayi jajensu ba, tana can tareda Hajja,har dare Shahaab yana naniqe tareda Aisha, Bai daga mata qafa ko dayaba ranar. Washe gari takama weekend yana gida, Bayan sunyi wanka sun shirya part din mama suka nufa,Bayan sunci abinci Aisha ta nufi kitchen tad'auko ice-cream roba guda ta zauna tanasha, shikuma ya amsa waya yafita, Bai dawo gida ba Sai Bayan azahar, yana zuwa yaga mama tana cewa Aisha"sakashi a jikin ki yaji dumi sosai" Zama yayi yace"lafiya? Meyasame shi?" Kafin su bashi amsa Yaron yasaki atishawa, mama Tace"wallahi yanzu yanzu fa kawai Naga yanata atishawa kode kun kwana da esi a kunne ne?" Cikin sauri Aisha tace"mun kunna kam" Ran Shahaab ne yayi baqiqqirin yace"babu ruwan esi,yanzu haka sanyin da aka dinga dura masa ne" Yaqare maganar yana daukan Daddy yatashi yana jijjiga shi. Mama tace"sanyin me Kuma?" Cikin damuwa yace" mama dazu Ina shirin fita Ina kallonta da uwar robar ice-cream Sai Sha take ko tausayin Yaron Nan bataji, may be sanyin ya zuqo daga nononta"(🤭) Mama ta jijjiga Kai tareda sakin ajiyar zuciya, taga alama al'amarin Shahaab gaba yake yi akan Yaron Nan, inajin Nan gaba saiya Hana Aisha kyakykyawan motsi saboda Daddy. Aisha ta kalleshi tace"yanzu Uncle wannan Dan ice-cream din da Nasha shine zai saka shi mura? Bafa duka na shanye ba, Dan kadan Nasha ko mama?" Tajuya tana tambayar mama. Bai saurari abinda mama zatace ba yace"ungo taso ki goyashi, ai d'umin runguma yayi masa kadan, zoki goyashi idan yaji d'umin ki sosai may be yadena atishawar" Mama ta zuba masa ido tana kallon ikon Allah Kuma tanaso taga me uwar Dan zatayi (🤔😄) Cikin sauri Aisha tace"d'azu d'azu nagama goyashi, wallahi nagaji,ka kira me aiki ta goyashi" Cikin sauri ya kalleta, fuska daure yace"ki goyashi mana" Dan qaramin bakinta ta turo gaba sannan tatashi ta juya masa baya, yad'ora mata Yaron tagoyashi, sannan tafara jijjiga shi, Sai a lokacin yasaki wata irin ajiyar zuciya yanemi waje ya zauna, har zuwa lokacin mama bata ce musu komai ba, tana zaune tana ganin ikon Allah, Aisha kuwa daga gaji da tsaiwa saita nemi waje ta zauna, tana dora duwawunta akan kujera Daddy yasaki kuka, Sai atishawa, gaban Shahaab yafadi, cikin sauri ya kallesu, ganin yanda yake kallonta yasa tasake tashi tsaye, tana tashi Daddy yayi shiru, falon tafara zagayawa tana Dan jijjiga shi, cikin akasi inda ta cusa towel din goyon yafuto, aikuwa Daddy yayi baya zai fad'i (😲🙆🏻‍♀️) Ita de mama tana zaune, Amma batasan Yaya akai ba Sai ganin Shahaab tayi yayi wata irin super, Sai gashi agaban Aisha, Aisha tayi wata irin zabura ta tsorata, cikin tashin hankali yace"ki riqeshi dakyau mana,kinga kawo Shima, dama can ba qaunar goyon kikeba, kawo shi, Dan idan nabar miki Shima Zaki iya yarda shi, Kuma ko bemiki mita a ransa ba Nima sainayi" Mamaki yakama Aisha,Kallonsa tayi cikin 6acin rai tace"tayaya zan yarda d'ana aqasa uncle?Dan Allah kadinga saukaqewa kanka damuwa akan Daddy" Maimakon yabata amsa saiyace"waya sanima ko mintsininsa ake, yaro tun dazu daga kuka Sai atishawa" Kallonsa tayi da sauri ta Girgiza kanta ta nemi waje ta zauna ta dora qafarta daya Kan daya tareda d'aukan remote, Shima Yaron yafara jijjiga wa,da yaga jijjigawar ba zatayi ba saiya dorashi a bayansa yafara zagaye falon da Yaron, Hajja data idar da sallah tafuto daga d'aki taga Shahaab da goyon Daddy tace"yau kaine da rainon?" Cikin sauri yace"Hajja ruwan Sanyi ta dinga d'urawa Yaron Nan, gashinan Sanyi nema yake ya kamashi" Hajja tasa hannu ta kar6eshi tace"kawo shi mugani" Babu musu yabata shi, sannan yanemi waje ya zauna kusa da Aisha, mama tasaki ajiyar zuciya tayi murmushi ganin yanda suit din dake jikinsa harta fara tattarewa daga baya saboda wannan Dan goyon Dayayi, Sai wata zufa yake hadawa kamar wanda yayi tseren gudu(😂) Ganin ya zauna kusa da'ita ko kallo bai isheta ba yasa yasake jin wani irin haushi, yasaki qaramin tsaki nanma Aisha ko juyo wa batayi ba, yasaka hannu ya fizge remote din hannunta, Sai Alokacin ta kalleshi ta kawar da kanta itama tana Girgiza qafa alamun akusa take, Hajja kuwa da batasan wainar da mutanan falon suke Toya waba saita shige daki domin shafawa Daddy man kad'e ajikinsa. Haka rayuwar take tafiya yau dadi gobe babu dadi, Hankalinsu kwance suke rainon Daddy, idan kaga Shahaab da Aisha sun samu Sa6ani to akan Daddy ne, kokadan bayason abinda zai ta6a Yaron, mama kam idan yana wani abun saide ta zuba masa ido tana Kallonsa kawai, wani lokacin ko wankan Daddy ake haka zai zauna yadinga mita shide Adinga yimasa wankan Ahankali, haka suka dinga Haquri dashi har Daddy Yacika wata hudu, kwata kwata ba zakice Yaron watansa hudu ba saboda yana samun kulawa ga nono ga madara, uwa uba ga abincin Yara da'ake bashi, shiyasa suka fara zaunar dashi Kuma daram yake zama, Amma duk wani abu dayake gefensa inde hannunsa zaikai wajan, to yanzu zaiyi ajalinsa, kokadan hannunsa baya zama waje daya, idan Shahaab yadawo daga wajan aiki haka zai zauna akusa dashi yadinga yimasa hira kamar wani me Hankali, wasa kuwa idan yacire kayan jikinsa yadauke shi suka dinga wasa afalon saide Aisha ta jiyo sautin dariyar su, wani lokacin tayi musu vedio wataran Kuma ta dinga kallon su tanajin farinciki acikin ranta. Har zuwa lokacin Hajja tana gidan,idan sungaji da Zaman gidan itada mama haka zasuyiwa Shahaab magana yasa a fitar dasu wani wajan Sudan Sha iska su dawo, ahankali ahankali rayuwa take tafiya har Daddy yafara rarrafe, tunda yafara rarrafe mama ta Dena ajiye wayarta aqasa, idan tea aka kawo musu saide su riqe a hannun su, baya ta6a zama shi kadai, idan kuwa aka jishi shiru babu 6arna to yasamu wani abun ne yana lalata shi, shine zakaji shi shiru, gaba daya falon mama yazama kamar falon renon Yara uku saboda yanda aka baje masa kayan wasa, haka zai zauna daga shi Sai pampers yana wasansa afalon, suma masu aikin gidan inde sunzo falo Tofa Sai sunyi masa wasa zasu wuce, ganinsu dayake yau da gobe yasa baya musu qiwa, saide in baiga wani yashigo falon ba, yanzu zai fara daga hannu yana kuka alamun yanaso a dauke shi. Tunda Shahaab yatafi lagos Kwanansa biyu bai dawo ba, yau yana hanyar dawowa yakira Aisha yace tahada masa cake idan yazo zaici, gashi su mama basa Nan, Kuma tunda taji Yakirata yafada mata hakan tasan cewa to bayason na ma'aikatan gidan ne, ta kalli Daddy dayake wasa cikin motar wasan Yara, ta dauke shi ta goyashi suka shige kitchen tafara aikinta tana masa magana kamar wanda yake jinta, Shikuwa gwarancinsa yake ma yana saka hannunsa abaki, Bayan tagama hada komai tasaka butter da suger tana mixing tace"Daddy na d'an Albarka yau ai zaka barni in yiwa Abbanka cake ko?" Tadauko qwai tafasa taci gaba da mixing, Hankalinta yayi kan abinda take batayi aune ba taga Daddy yaja fulawar data ajiye ya kwaro musu ita kansu, lokaci daya ta tsorata tasaki qara saboda zubar fulawar kawai taji, shikuma qaran data saki ne yasa ya tsorata yasaki kuka Kuma ya qanqame bowl din yaqi saki, baqin ciki yakama Aisha(😖). Tunda yashigo kitchen din ya tsaya abakin qofar kitchen din yana kallonsu, sosai tayi masa kyau da goyon Daddy musanman da yaji tana masa magana kamar Dame Hankali take magana, ganin aikin da Daddy yayi mata yasa ya tuntsire da dariya yafara yimusu vedio, juyowa tayi ta kalleshi da fuskarta data cika da fulawa tafashe da Kuka, qaraso wa yayi kitchen din ya qwace bowl din hannun Daddy sannan ya kunce mata shi, kuka take sosai cikin kukan tace"kana ganin abinda yamin fa, ya 6are baki yanamin kuka kamar bashine yamin laifin ba" Cikin jin dadi ya janyo ta jikinsa ya rungumesu gaba daya, sannan yafara kad'e mata fulawar yana lallashin ta, daqyar yasamu tayi shiru sannan yace"ai nine nace amin cake din, to abarshi tunda Daddy yahana" Cikin shagwa6a ta kalleshi takai masa Dukan wasa a qirjinsa. Da daddare suna zaune a part dinsu suna kallo, Sanye take cikin rigar bacci tana kallon film din da ake haskawa, agefe daya Kuma waya take da faty tana sanar da'ita ansaka ranar bikin ta, shikuma Shahaab yana zauna aqasan kafet yana aiki a computer, yayinda Daddy yake Gefe yana wasa, saida tagama wayar sannan ta kalli Shahaab tace"Uncle ansaka ranar bikin faty fa, nanda wata shida" Hankalinsa yana kan aikin dayake yace"Allah yakaimu, Amma Ina tunanin zuwa lokacin Bama Nan ai, inaso muje umara gaba dayanmu, dasu Ummah dasu Hajja, daga Nan Kuma zamu je muga jabir" Cikin farinciki tace"Uncle Saudia zamu tafi gaba dayanmu?" Yace"insha Allah" Cikin jin dadi taje ta rungume shi tasakar masa kiss tace"wayyo Allah, Amma naji dadi uncle, mungode Allah yasaka da alkhairi yaqara budi" Cak ya dauketa yadorata akan cinyarsa yace"Amin, idan kinyi waya da qawar ki ta jigawa kifada mata Faisal yamin magana yanaso inje gidansu in nema masa aurenta" Fari tayi da idonta tace"wai Walida?" Kansa yadaga mata yana sake gyara mata gashin kanta, cikin jin dadi tace"zan fada mata, Bari inkirata ma yanzu" Tafadi haka tana qoqarin tashi daga kan cinyarsa, cikin sauri ya riqeta yace"Haba madam" Murmushi tasaki kafin tayi magana yafara waigawa falon yace"ina Yaron Nan yake ne?" Tashi tayi daga cinyarsa tace"inaga wasa yake" Shima tashi yayi yana nemansa, acan suka hangoshi yana rarrafe yana bin ball dinsa yanaso ya dauko ta, cikin sauri Shahaab yadauko shi suka dawo kan kujera suka zauna ya kalli Aisha yace"yazaki barshi yana rarrafe a tile maamah?" Tace"to Uncle akan cinyata zaiyi?na'isa in Hana Daddy rarrafe?tayaya ma zan San yatafi?" Goge wa Yaron qafa yakeyi, sannan yadora mata shi akan cinyarta yace"ki kula dashi karki sake barinsa yana rarrafe a tile please,Bari in Dauko takardu adaki" Aisha ta Girgiza kanta, Shima Daddy qoqarin zamewa yake zai sauka, babu musu kuwa ta sauke shi, wajan kallo yanufa ya zubawa TV ido yana kallo, itama Hankalinta yana kan kallon saijin ihun kukan Yaron tayi, cikin sauri ta nufeshi, Shahaab ma da yaji kukan yayi yawa cikin sauri yafuto daga d'akin hannunsa d'aukeda takardu yanufeta sannan ya karbi Daddy yace"me aka masa yake wannan uban kukan?" Cikin damuwa tace"ni wallahi ban lura ba, Sai kukan sa naji, speaker yaja tafado masa ahannunsa shine yake wannan kukan" Cikin sauri yaduba hannun yaga har yatsun sun danyi ja kasancewar sa fari, iska yadan hura masa a hannun sannan ya kalleta yace"maamah, kifadamin tsakaninki da Allah Anya ba cizon yaron Nan kikai ba?"(🤔😂) Cikin sauri ta d'ago ta Kalle shi tace"nashiga uku Uncle??" Cikin damuwa shima yace"maamah idan cizon nasa kikai ma Yaya zanyi dake?"yana fadar haka yajuya da Yaron suka shige daki, ita Kam murmushi ma tayi tabi bayansu Dakin, gaba dayansu su biyun suka hadu suka lallashi Yaron har bacci ya dauke shi sannan ne Kuma suka shirya😂 Rayuwa tana juyawa Izuwa yini, yini yana juyawa Izuwa kwana, kwana yakoma sati, sati yakoma wata har Daddy Yacika wata goma, Adede lokacin Kuma suka shirya gaba dayansu suka tafi Umara, Mama,Hajja,Ummah,Abba, Shahaab, Aisha, dakuma Daddy, satin su biyu a Saudia, Adede lokacin Kuma akai bikin faty,Walida Kuma ansaka rana wata uku masu zuwa itada Faisal Yaron Hajiya zaliha,kana ganinsu kasan family ne daya amsa sunan sa Family Kuma suke cikin kwanciyar Hankali da walwala, daga Saudia Australia suka wuce wajan Jabir, yayi murna sosai da ganinsu ya girma yasake zama saurayi, yana ganin Daddy ya dauke shi bacci ne kawai yake raba shi da Yaron, satinsu biyu a qasar, suka dawo Nigeria. Bayan sati daya Aisha da Shahaab suna zaune afalon su suna kallon Ball, gaba daya hankalin sa yana kan ball din da'ake bugawa, Aisha ma daba sanin Yan ball tayi ba tazuba ido tana Kallonsu har aka gama wasan, taga an nuno wani matashin saurayi da yaro ahannunsa dagashi har Yaron Sanye suke cikin kayan ball Sai mutane yakewa sign a takardar dasuke bashi, sosai yake Fara'ah dimples dinsa Sai lotsawa suke, Yaron hannunsa yadaga masa yana gudu da Yaron sosai alamun ball din dasuka buga tamasa dadi, Shahaab yayi murmushi yace"wannan Yaron bayaji" Aisha ta juya ta kalleshi tace"musulmi ne?" Murmushi yayi tace"sosai kuwa,d'an asalin Niger ne,Amma a Nigeria suke, family dinsa da kowa da kowa da matarsa duk suna kano,sunansa BIG BROTHER, but wasu suna kiransa BABBAN YAYA,ya'iya ball sosai" Aisha tayi ajiyar zuciya tace"um, ku kuka San Yan Ball Uncle" Juyawar dazatai taga Daddy yabude fos dinta yafuto da kudin ciki Yan Dari biyar biyar da dubu dubu gaba daya ya yaiyaga su, cikin 6acin rai ta daki Yaron tace"Daddy kudi kake yagawa haka?" Cikin sauri Shahaab ya kalleta, Jiyayi kamar shi ta daka,lokaci daya yafara huci yana Kai zuciyar sa nesa, jiyake kamar ya Fashe, daqyar ya'iya controlling kansa yace"maamah duka? Yanzu Harkin fara Dukan yaron Nan agabana maamah?" Cikin 6acin rai ta kalleshi tace"Uncle kudi fa yake yagawa, idan Bana dukansa bazai ta6a gane yayi laifi ko baiyi ba" Yace"to kudi Kuma saiki masa irin wannan Dukan? Ina laifin ma kisamu tsinken tsintsiyar laushi? Kidena masa irin wannan Dukan kinji nafada miki, idan kika sake Kuma zakiga abinda zai biyo baya" Haushi yakama Aisha,baqin ciki ne yasa batasan lokacin data sake kaiwa Yaron duka ba, Shahaab yana ganin haka yatashi tsaye, tana ganin yatashi tsaye takwasa a guje tayi dakinta, tana kokarin rufewa yayi nasarar shiga Dakin, akan gado suka zube, yajata jikinsa ya matse ta, dariya tafara tana kokarin qwatar kanta, tasan zata Iya shan wahala awajansa, inde akan Daddy ne, shiyasa tun kafin yayi mata wani abu takai hannunta tata6o masa inda tasan cewa dole yayi saranda, Shima anasa 6angaren hannunsa bibbiyu yad'ora akan nashanunta yana murza mata nipples d'in da qarfi, cikin muryarsa Mai cikeda buqata yace"meyasa bakya jine maaa-mahhhh" Yafadi sunan Nata a rarrabe, cikin kissa tafara zuba masa kukan shagwa6a, hakan ne yasake tunzurashi yaci gaba da aikata mata saqo, cikin tsananin azaba taji cikinta yayi wata irin murdawa, Nan da Nan tasaki kukan na gaske, cikin kuka tace"Uncle cikina, zan mutu Uncle" Idonsa a Lumshe suke, Amma yanda yaji tayi masa magana cikin serious, yasa yabude Idonsa yakai Kallonsa gareta, ganin halin datake ciki yasa cikin tashin hankali ya dauketa, yadawo falo yad'auki Daddy suka futo, Adede lokacin mama da Hajja suna compound din gidan suna zancen su, ganin yanda ya Dauko Aisha a hannu yasa suka iyo wajan sa cikin damuwa, mama tace"muje Asbiti kawai, ciwon ciki abun tsoro ne" Cikin sauri yace"ku zauna mama, Bari muje nakaita" Hajja Tace"A a, Zaman me zamuyi? Muje kawai" Babu musu suka dunguma zuwa Asbiti gaba dayansu, suna zuwa likita tabata taimakon gaggawa aka daura mata ruwa tareda allurai, Sai Alokacin tasamu bacci, gaba dayansu sunyi shiru suna mamakin wannan ciwon ciki na Aisha, cikin ikon Allah tafarka cikin qanqanin lokaci, Adede lokacin Kuma Likitan tadawo fuskarta d'aukeda murmushi ta kalli Shahaab tace"yalla6ai Yaron baba fa bayason guje-guje da tsalle-tsalle, congratulation madam tana d'aukeda juna biyu" Cikin sauri Aisha ta tatashi zaune, Shahaab kuwa wani irin farinciki ne ya kamashi yace"Dr da gaske?" Cikin farinciki tace"sosai yalla6ai" Hajja da mama ma cikin farinciki suka daga hannu suna yiwa Allah godia, bata dauki tsawon lokaci ba suka sallamesu suka dawo gida, suna zuwa gida ta wuce part dinsu, acan dinma dakinta ta wuce ta zauna abakin gado tafashe dawani irin kuka, tunda suka taho a hanya ya lura kawai sune suke budurinsu, Aisha bata cewa komai, kwata kwata ya lura batayi farinciki da samun cikin ba, lokaci daya jikinsa yayi Sanyi, shiyasa yanayin parking da yaga tafita daga motar yasan cewa akwai damuwa, su mama kuwa basu lura da sauyin yanayin taba, suma part dinsu suka wuce, ahankali ya kalli part dinsu yasaki ajiyar zuciya sannan yabi Bayan Aisha. Yana shiga kuwa, yaga bata falon, Kai tsaye dakinta yawuce, tun kafin yashiga Dakin ya tsinka yi muryar ta tana kuka, jikinsa ne yayi Sanyi kalau, yaja ya tsaya abakin kofar d'akin tareda harde hannunsa a qirjinsa yana kallonta, Sarai taji shigowar sa, Amma bata daga Kai ta kalleshi ba, asalima kukan ta taci gaba dayi, ajiyar zuciya yasauke yatako yaqaraso cikin Dakin ya zauna akusa da'ita yace"maamah" Tayi shiru bata amsa masaba, Kallan ta yayi yace"atunani na zakiyi murna ne da kyautar da Allah yayi mana maamah, bansaniba ko kin daina sonane shiyasa bakya son ki hada jini dani" Cikin kuka ta daga kanta tace"Daddy fa ko yayeshi banyi ba....kuma yanzu harna sake yin wani cikin" Idonsa ya Lumshe sannan yabude, yace" bazanga laifin ki ba idan kinyi watsi da kyautar da Allah yayi miki, saboda Sai wannan shekarar ne Zaki cika shekara goma Sha Tara, Amma ni shekaru na arba'in dawani abu, banda Ina cikin jin dadi dakuma yanayin jikina ke kanki kinsan cewa niba qaramin mutum bane maamah,kiduba kigani fa Sai yanzu ne nafara haihuwa, kafin ace yarana sun girma sun fara taimaka min nariga na tsufa, shekara ta goma Sha da aure ban haihu ba Sai yanzu ne Allah ya dubeni yabani Daddy, Kuma yanzu saboda butulci irin nawa Sai inqi wata kyautar Dayayi min?maamah ko Daddy bekai wata goma ba kika samu ciki zanyi murna da hakan,Amma idan zubarwa kike so kiyi Nima saina miki allurar, idan hakan zaisa kiyi farinciki, saide Kuma agaba idan Allah yahanamu haihuwar har abada, karkiyi kuka Dani, kiyi kuka da kanki" Hawayen idonta tashare tace"ni bazan zubar da ciki naba,Nasha wahala a haihuwar Daddy, Kuma ko shekara biyu beyi ba, gashi yanzu wata wahalar zan sake fuskanta" Janyota yayi jikinsa ya rungumeta sosai sannan yace"maamah haihuwa ta Allah ce,insha Allah, Allah zai saukeki lafiya, kiyi hakuri Dan girman Allah kidinga haifamin Yara wallahi inaso koda Yan biyu Zaki dinga haifamin" Cikin shagwa6a tace"Kuma ma idan na daki Daddy saika dinga min fada, ban Isa inyi masa wani abun ba saika dinga yin abu kamar zaka rufeni da duka, to ahakan ne zakace indinga haihuwa" Murmushi yasaki ganin ta sakko yanzu Kuma mita takeyi, cikin nutsuwa yace"inde akan Daddy ne na daina, wallahi na daina ki masa komai ma inde tarbiya Zaki bashi,Shima Wanda Zaki Haifa din nabaki Dama kihadasu kimusu tarbiya yanda ya kamata, shikkenan abinda kike so?" Dan qaramin bakinta ta turo gaba cikin shagwa6ar de tasake cewa" Kuma kullum kullum kadinga yin abu daya ba shiyasa ma nasamu cikin da wuri ba" Murmushi yasaki yace"maamah rigima...,maamah yin wannan abun ko rashin yinsa bashine yake kawo ciki ba,zan'iya yi sau daya ma kiga kin samu cikin" Yasake sassauta muryarsa cikin rad'a yace"ni yanzu ma dazaki Bani Dakin min hajji da umara" Cikin sauri takai masa Dukan wasa akan faffadan qirjinsa, cikin jin dadi yace"kinji maamah? Kinga Daddy yana wajan su Mama, kawai ma daga yau mu bar musu shi mukuma saimu raini cikin mu,Kuma yanzu ma nasan bazai dawo ba, kafin yadawo kinga saimu kwantar da qura" Murmushi tayi tana masa wata irin harara Mai kalar Kallan soyaiya, Shima wani irin shu'umin kallo yake jifanta dashi batareda yace komai ba, kawai dai cikin dabara yatura hannunsa cikin rigarta yakamo nashanunta yafara aika musu da kyakykyawan saqo, dadin dataji ne yasa tabashi hadin Kai, lokaci daya suka haukace, ta manta da batun ciki tabaje yana abinda yaso da'ita,irin dadin dayaji tayi lokacin data samu cikin Daddy yanzun ma shi yaji, ita kanta dadi taji sosai taji kamar zata suma,lokaci daya tafara sakar masa kukan dad'i, hakan ne yasa Shima ya haukace mata yafara wani irin sambatu kwata kwata baisan inda kansa yakeba, dagashi har ita sun manta basu rufe qofar Dakin ba, hakanne yabawa mama damar jiyo wani irin ihu da nishi tundaga falo kasancewar Daddy yana kuka ta taho domin ta kawo musu shi, tun kafin ta qaraso tsakiyar falon ta juya cikin sauri tana jiyo yanda Shahaab yake wani irin kuka kamar bashi ba, kamar 6arauniya haka taja Kofar falon ta rufe musu kamar tana tsoron zasuji shigowar ta, saida tafuto daga part din sannan tasaki ajiyar zuciya ta kalli Daddy dayake hannunta tace"megida,in zakayi shiru tun wuri to kayi shiru,iyayenka sunyi Nisa ba zasuji kiraba"(🙊🙈) SHAHAAB littafin kudi ne, 300 ne kacal idan kika karanta baki biyaba nabarki da MAHALICCINKI 0164549488 Amina muhammad GTbank Kokuma katin MTN tareda shedar biya ta wannan number 08033300034 Amnah El Yaqoub✍🏻 ASH-HAB page 26 Basu sararawa junansu ba saida suka dauki tsawon lokaci Mai yawa, Bayan komai yagama kammala babu Wanda yanemi Daddy acikinsu, wanka sukayi, Shahaab ya maida ta jikinsa yana sake nuna mata yanda yaji dadin baiyanar cikinta, dakuma alqawura iri iri akan yanda zai dinga basu kulawa daga ita har yaran dazata dinga Haifa masa. A 6angaren mama, itama bata sake nemansu ba, taga alama sabon amarci sukeji, saide a 6angaren daya tanajin kunyar kanta idan ta tuna da abunda kunnuwanta suka jiye Nata dazun. BAYAN SHEKARA DAYA Sosai yayi masifar kyau cikin manyan Kaya fari tas, babbar rigar ta kar6i jikinsa, Yayinda fatar jikinsa take wani irin sheqi alamun jin dadi atare dashi, turare ya fesa yasake gyara Zaman hular Kansa. Cikin jin dadi tayi ajiyar zuciya Bayan tagama qarewa mijin Nata kallo, a koda yaushe Gani take kamar tafi sauran mata sa'ah kasancewar ta tare dashi, tanajin alfahri wani lokacin saboda tunawa datake itadin matar MAHMUD WAKILI ce, cikin shekara d'ayan Nan tasake murmurewa jikinta ya murje, bata hada qiba sosai ba, Amma kokadan babu alamun Rama atare da'ita, leshi ne ajikinta dinkin doguwar Riga, batayi wani Daurin dankwali Mai wahala ba, Sai sarqar gold da zoben gold dasuke hannayenta, cikin yanayin roqon alfarma tace"Uncle Dan Allah, tunda ankusa fara bada admission Nima Atemaka min mana, in danyi karatun Nan" Cikin sauri ya kalleta, yayanta biyu, idan tafara karatu babu Wanda zaice tanada aure, yanzu nema girma da Dan Hankali suke sake shigar ta, yanda yakejinta a ransa baya tunanin zai iya barinta ta dinga cudanya tsakanin ta da wasu mazan, kafin yabata amsa Yaron dake kwance akan gadon yafara kuka, cikin sauri yasaka hannu ya tattare babbar rigar jikinsa, sannan yad'auki Yaron yana jijjiga shi, yasaka masa fida a bakinsa yana cewa"sorry sojana, kaida baka kuka, waya tabaka kake kuka? Ko saboda kaji mummynka zata gudu makaranta tabarmu ne, uhm?" Aisha tana jinsa tayi murmushi tace"Uncle zaka barni?" Cikin daure fuska ya kalleta yace"meyasa bazaki daina min wannan maganar bane?" Cikin nutsuwa tace"Uncle ilmi shine jigon rayuwa,kasancewa ta atare dakai inajina kamar ban Rasa komai ba, banida damuwar komai, Ina rayuwa ta yanda nakeso, Amma Kuma ta wani 6angaren nasan narasa wani abu guda daya shine ilmi, kabarni inyi karatu Nima ko kadan ne, Kaga FEENAH saida tayi masters dinta sannan ta auri AHMAD Bayan gwagwar mayar dayasha yana nemanta(DANA SANI). haka AMAL itama mijinta KARAM,shine yakaita har qasar waje domin ta qaro ilmi kasancewar sa Babban mutum Kuma Dan siyasa yasan cewa dole matarsa zatayi mu'amula da kowanne irin mutane,(BURINAH) IMAN bata auri ALIYU ba, saida ta kammala degree dinta na farko, sannan ta aure shi Kuma suka zauna lafiya (WAZAN ZABA?) sannan duk wahalar rayuwa da HANIFA Tasha, Bayan tayi aure HANIF shida Kansa ya maida ta makaranta(SHALELAN BABA) duk saboda suyi yaqi da jahilci. Haka BABY tana cikin karatun sauyin qaddara tasa ta auri MK, Shima daga baya saida ta qarasa karatun ta(NI DAKE) sannan duk girma irinna Familyn mazawaje,kaga yayansu mata basa dogon karatu, Amma NIHLA qaddara tasa saida tayi degree dinta a Abuja, sannan ta Auri ABBA, (DANGI 'DAYA) Haka ASIM, shida Kansa yake koyawa INSAAF, karatu, Kuma shine ya zabi abinda yakeso tayi(INSAAF) WAHEEDA Bayan Aurenta da NAUFAL tayi karatun ta a qasar waje (BABBAN YAYA). Meyasa nibazaka barni ba Uncle?" Ajiyar zuciya yasauke yace"saboda nabarki kiyi karatu duk kika min irin wannan dogon misalin?, to saiki qara da cewa MAHMUD WAKILI, EFCC CHIRMAN, shine kawai baibar matarsa AISHA MAHMUD, tayi karatu ba" Yana fadin haka yafice daga d'akin hannunsa d'aukeda junior,Mai sunan kakan Aisha wato mijin Hajja, Ismail,suna kiransa da junior. Qafafunta tafara bubbugawa aqasa cikin shagwa6a, sannan tasa hannu ta dauki wayarta da handbag dinta, tabiyo bayansa, basu zame ko'inaba Sai part din mama. Suna zuwa sukaga mama da Hajja suma sungama shirya wa, Kai tsaye wajan su yanufa ya ajiye musu Yaron, sannan yawuce zaici abinci, itama bayansa tabi, suka fara cin abincin. Daddy yana ganin junior yataho da gudu yadawo wajan Yaron yayi masa kiss a kumatunsa, Hajja ta kama baki ta kalli Mama tace"ikon Allah,wacce irin al'adace wannan? Kode awajan iyayen nasa yake Gani?" Mama ma da mamaki ya kamata tace"oho musu, jarabar uban kadai ma ai zatasa wataran yayiwa uwar agaban Yaron, anan zai Gani" Ta kalli Daddy tace"Daddy na karfa ka cijeshi" Juyowa yayi ya kalli Mama yace"Mama Baby ne?" Tace"eh" Yasake cewa"mama Baby ne?" Tace"eh Baby ne" Dariya yasaki yace"Baby nane" Mama tace"nikwa nasan Babynka ne, tunda uwarku daya ubanku daya" Hajja tayi dariya jin hirar mama da Daddy, tad'auki wayarta takira jummai, Bayan sun gaisa tace"to jummai gamunan zuwa, yanzu zamu dauko hanya kiyi mana kunun Aya Mai dadi de" Daga d'ayan bangaren jummai tace"to Hajja A'i, Allah yakawo ku lafiya" Hajja tace"Amin"sannnan tafara shirin kashe wayar, cikin sauri jummai tace"nikam Hajja A'i gulma ajali inba'ayi ba amutu, tun rannan kike cemin zakuzo nace ganin gida zaku zo ne kokuma wani abunne yataso?" Hajja tace"kai jummai da gulma kike, to zamu zo taro ne, mijin Mai sunan qawa zai bude gidan marayun daya gina" Cikin sauri jummai tace"oho, to, tona gane yanzu, to saikun zo, Bari naturo a siyomin kwatar aya, Sai ayi muku" Hajja ta kashe wayar, Adede lokacin su Aisha suka gama cin abincin, suna zuwa Aisha ta dauki Junior, suka futo gaba dayansu, motoci biyu suka yi, suka wuce Airport,acan suka hadu dasu Abba da Ummah, basu dade da zuwaba, jirginsu yatashi. Bayan sun sauka agarin ko zama basu yi ba, jummai tataho gidan, daga Nan manyan gari suma suka shishshiga mota sukai ayari gaba dayansu, suka wuce wajan taron, waje Yacika maqil da mutane, Gwamnatin Jihar ta basu hadin Kai yanda ya kamata, har akai taron bude gidan marayun lafiya, aka gama lafiya, su Aisha Kam gida suka iyo, Amma mazan duk suna can,kasancewar baqin da suka zazzo basu gama tafiya ba. Acikin gidansu Aisha Bayan kowa yayi wanka gaba dayansu bajewa sukai a Babban falon Hajja wadda aka qawata shi da kayan more rayuwa, yaji kujeru kamar ba'a cikin Garin CHAMO, gidan yake ba. Jummai ce tayi sallama takawo musu kunun ayar da Hajja tace ayi musu, mama Tasha Dan kadan ta ajiye, Aisha kuwa waya ce a hannunta tana turawa Shahaab saqo,Yayinda junior yake bacci akan kujera, Daddy kuwa daga shi Sai Dan qaramin wandon Yara tareda singlet yana wasa da ball a Dan qaramin tsakar gidan nasu, Hajja tad'auki kunun ayar Tasha, cikin sauri ta ajiye ta kalli jummai tace"jummai wannan aiba kunun Aya bane, kwata kwata babu gardin ayar abaki, wannan ai ruwan daurayar nawa kunun ayar ne, ni Dama tunda naji kince Zaki siyo kwatar Aya nasan cewa Sai ahankali" Jummai ta gyara zamanta sannan tacire mayafin kanta tace"ke kwantar da Hankalinki, na yanzun ne nake zunduma masa ruwa, Aida Ina murna kin Bani firji na kama kunun Aya inayi ka'in da na'in, Ina farinciki zan samu kudi, to wallahi inayi jikokina suke shanye wa, baifi in samu ribar nera talatin ba, itama talatin din inbawa Dan talla ita, nikam Aina Dena yima" Daddy yabugo ball tafado d'akin, yace"goooo, Hajja bugo" Hajja tace"inani Ina ball Daddy?" Jummai ta kalli daddy, sannan tajuya ta kalli Hajja tace" Hajja A'i gulma ajali....." Kafin ta qarasa mama tayi dariya tace" fadi maganar da kike so kawai jummai" Jummai tasake kallon Daddy, sannan ta kalli Hajja tace"shi wannan Yaron Jikan ki, zance ne kokuma Dan ki, bashine Yaron da Aisha ta Haifa ba?" Mama tayi murmushi tace" shine mana, Daddy ne" Jummai ta Jinjina Kai sannan ta kalli Daddy tace"kai yaka zonan" Babu musu Daddy yazo wajan ta, ta kalleshi tace"yaya sunanka?" Kai tsaye yace" Daddy" Tasake cewa "shekarar ka nawa?" Yace"hudu, biyar, shida" Jummai tajuya ta kalli su mama tace"kaiiii, wannan Yaron bashine Aisha ta Haifa ba, yaro shekara biyu yake wannan surutun mu idan anan ne ai Musanta shekarun nasa zamuyi, ai wannan saide muce yabawa shekara biyar baya" Adede lokacin Shahaab da Abba suka shigo,Shahaab yana jin abinda jummai tace yayi murmushi sannan ya tsugunna yana gaishe ta, cikin mutunta wa ta amsa tana sake tayaashi muryar bude gidan marayun da akai, cikin nutsuwa yatashi yawuce Dakin dasuka sauka, Shima Abba dakinsa yawuce Dama agajiye yake. Aisha tana ganin shigar sa daki ta wuce kitchen tadauko masa awarar qwai, da damammiyar fura ta wuce Dakin, tana zuwa kuwa ta ganshi a kwance alamun hutawa yake, zama tayi akusa dashi tace"Uncle tashi Kaci awara da fura" Babu musu yatashi, tafara bashi awarar abaki, yanaci yana hadawa da fura Mai Sanyi, saida ta tabbatar ya qoshi, sannan ta maida kayan kitchen tadawo Dakin Daddy yana biye abayanta Shahaab ya kalli Yaron yace"Daddy zonan" Yana zuwa yaja shi jikinsa cikin wayo yace"kanason sweet" Daddy yace"Eh inaso" Cikin sauri Shahaab yace"yawwa, to kaje Abba yabaka, yanacan da sweet dayawa awajansa, idan kagama Sha ka tsaya acan katayashi wasa, tun dazu yake nemanka"🙊😲 Cikin gudu daddy yafice daga d'akin, Aisha ta kalleshi, kafin tayi magana ya fuzgota jikinsa, hararar wasa tayi masa tafara nuna masa falo da hannunta, cikin tsananin buqata yace"to menene?" Tace" Uncle, kaji tsoron Allah kaji tsoron mutum ukun Nan, Hajja, mama, dakuma iya Jummai"(😂🤣) Idonsa a Lumshe, cikeda jaraba yace"idan bamuyi Bama bazasu daina mana surutu ba, kawai Gara muyi abunmu, munci abinci munsha ruwa, ba aikin komai zamuyi ba to menene yarage?" Ya qarasa maganar yana yi mata wani irin kallo Mai kashe jiki, kanta ta Girgiza tafara kokarin raba jikinta da nashi, sake rungume ta yayi cikin shagwa6a yace"nide kibani Abuna, ya kamata anemawa junior qanwa, dama kina cewa kinason Baby girl, toba saimu samo masa Baby girl yar jigawa ba?" Cikin shagwa6a tace" Uncle kaima fa kasan cewa bazaka iya control din kanka kayi shiru ba, sannan..... " Cikin sauri ya katse ta yace" tayaya zan'iya control din kaina a wannan yanayin? But tunda ke kina iya control din kanki, Saiki rufemin baki, OK?" Cikin shagwa6a ta kalleshi, saide kafin ta furta wani abu, yahade bakinsu waje daya. TAMMAT BIHAMDULLAH🙏 Anan nakawo qarshan littafina na Shahaab, idan akwai Wanda na 6atawa rai sanadin wannan rubutun to Ina roqonsa yayafe min saboda Dan Adam ajizine, abinda Naga yamin daidai ba lalle ne yayi wa kowa daidai ba, tun muna rubuta abu Mai amfani karkuma mu dawo muna rubuta shirme,duk lokacin danake rubuta labarin Shahaab inajin kamar karna tsaya saboda nikaina inajin dadin labarin, to Amma Kuma babu yanda zamuyi dole haka zamu dakata saboda kar Kuma tun muna marmarin labari mudawo muna shirme, a tunani na Gara a taqaita labari tunda dadinsa, ta yanda masoya zasu dinga jajensa. Masoyana Wanda suka nunamin soyaiya suka Sai littafi na banida bakin dazan muku godia,haqiqa kun nunamin soyaiya wasu soyaiyar dasuke min ce tasa suka Sai littafin fiyeda abunda nake saida shi,nasan soyaiyar dakuke min ne yasa hakan, Ina sake godia agareku, Ina fatan yanda muka hadu acikin wannan littafi Allah yasa muhadu a aljanna baki daya🤲🏻 Alhamdulillah duk shekara Ina rubuta novel guda biyu, wannan shekarar nayi BABBAN YAYA da SHAHAAB, Sai mun shiga wata shekarar Kuma in Allah ya Ara mana lokaci. Littafi na Kuma na kudi ne 300 ne ba free bane,idan kika karanta baki biyaba nabarki ALLAH ban yafeba 0164549488 Amina muhammad GTbank My number 08033300034 Amnah El Yaqoub ✍🏻