🌹GIDAN AUNTY 🌹 A heart touching love story Story & written By Aysha galadima ( mss Lee💕) 📚UK WRITERS (Unique kingdom writers)📚 Sabuwar marubuta masu tafiya da saban salo me kayatarwa. Littafina kirkirarran labarine banyi dan cin zarafin wani no ko wata ba, duk Wanda labarina ya zo daya da nashi yayi hakuri rashin sani ne. Yadda na fara littafinnnan a Sa’a Allah ya bani ikon kammalashi.. Bismillahir rahmanirrahim….. Paid book Book 1📕 Free page 1 TAHEE!!! TAHEE!!! “Naam oumma “ cewar wata yarinya wacce kallo daya zaka mata kasan bazata wuce 16 to 17 years ba, ta fito daga cikin wata kofa da kallo daya zaka mata kasan daga kitchen take, sabida flour da ya Dan bata mata jiki.” Har hanxu baki gama kwabin ba , kinsan abbanku ya kusan dawowa kuma kinsan inyazo ya taddaku haka ran mune zai baci duka ko!”kiyi hakuri oumma na kusa gamawa TAHEER nake jira ya taimakamun …”bata kammala magana ba sukaji anshigo falan ko sallama babu, Mai da hankalinsu sukayi kan kofa . Wata yarinyace itama da bazata wuce 15 to 16 ba a tsaye sai faman ya tsine take kamar wata babba, kura mata ido TAHEE tayi dan jiranjin mai zatace, dan tasan zuwan ameerah ba alkairi bane. Kamar kuwa ta shiga zuciyarta , “maryam dake da TAHEE wai Kuzo inji abba…, bata kammala maganar ta ba sabida saukar marukan da taji a waje maban banta. Kuka ta saki mai kara tana jiyowa. Karo taci da TAHEER da TAHEERA a tsaye sai faman huci suke saki, TAHEER ne ya soma magana “sau nawa zan fada miki duk lokacin da Kika kwaso rashin kuryarki ki dunga ajje ta a waje kafun ki tako mana daki, mahaifiyar Tamu kike dan baki da kunya “, kuka kawai ameerah take dan ba karamun zafin marin tajiba, dafe kuncinta tayi dagudu ta bar dakin . Kallansu oumma tayi cikin hade rai,”sau nawa zan ja muku kunne kudinga hakuri da mutanan gidan nan, ko so kuke kudinga ganin raina yana baci” , kamar hadin baki TAHEER da TAHEERA suka ruke kunnuwansu ,”oumma kiyi hakuri bazamu sake ba “, Daman ta San halinsu, dungure musu kai tayi, atare suka saki dariya dan dama sunsan ba fushi tayiba. Kamo hannayensu tayi tare da hadewa waje daya , TAHEE!! Naam oumma! TAHEERA ta amsa mata, maida kallanta tayi wajan taheer shima ta kira sunansa, amsa mata yayi shima yana kallanta. Numfashi oumma ta saki kafun ta soma magana cikin Sanyi , “ku kadai Allah ya bani, banaso kuna saurin fushinnan, inaso ko bayan raina kuzama masu kaunar juna kunji, ku zama masu hakuri da kawaici, Musamman Kai TAHEER , kafi saurin hawa”. Murmurmur taheer yayi tare da dan sosa keya, oumma kiyi hakuri, hararar wasa tasakar masa daman anan kafi kauri wajan bada hakuri. Kema taheera ki shiga taitayinki , hada ido Taheer da taheera sukai tare da hada baki , oumma kiyi hakuri bazamu sake ba . Girgiza kai oumma tayi kawai, basuyi wata wata ba suka rungumeta, hado kansu tayi su biyun ta rungume a jikinta. Suna cikin zamannan sukajiyo bugun kofa da karfin gaske , duk mimmikewa sukai tsaye, bakowa bane face abba sai faman huci yake bayansa kuma mamy ce hannunta rike dana Ameerah sai faman cika take . Baiyi wata wata ba ya tsinkawa oumma mari, Maryam sau nawa zan fada miki ki fita harkar yata,me yasa bakyajin magana, Tom bari kiji na fada miki na gaji da wannan halayen naki, ki tattara kayanki kije na SAKEKI. Kafun na dawo gidannan banaso naga fuskarki data yan iskan yayanki , sannan fuuu ya bar wajan. Shewa mamy ta saka toh maza maza azo abar mana gida tunda anzama bazawara, budar bakin ameerah sai cewa tayi da Yayan zawarawa sanin cewa ba mai tabata tunda uwarta na wajan , sai da mamy ta gama babatunta da zafesu tasss sannan takama hannun yarta sukabar wajan. Zubewa umma tayi a kasa zuciyarta na faman ta farfasa ga kuncin da zuciyarta ke mata, fashe wa kawai tayi da kuka, TAHEE ma zubewa tayi a kasa tana kuka sosai, TAHEER ne mai dauriyar cikinsu yake lallashinsu, abun yayi masa ciwo sosai, asaki mahaifiyarsu agaban idansu dan basu da gata. Abbu nayi kewarka , ALLAH YAJIKANKA ABBU!! Shima sai ya fashe da kuka , haka suka kwashi kusan minti 15 suna abu daya , ganin sunki daina kukan Yasa oumma tsayar da nata kukan, tashiga lallashinsu. Ganin sunyi shiru yasa ta mikewa, daki ta shiga ta tattaro musu Kayan sawarsu cikin jakunkunansu, sannan tasa taheer yasamo mata motar akurki dan kwashe mata kayansu, ba jimawa kuwa sai gasu, lokacin abba ya fita shiyasa mai akurkin ya shigo ya taimaka musu suka kwashe kayan.Mamy na labe ita da wata kawarta sai faman kwasan dariya suke , bayan sun gama kwashe komaine suka fito waje , oumma ta janyo kofar bangaransu Wanda ko cokali datasan natane bata bar musu shi ko daya ba. Awaje ta tarar da mamy ta fito sai habaici take tana kwasar dariya kawarta na tayata, sabida rashin tarbiyya har ameerah ce ke kiransu zawarawa da yayan zawara wa uwarta na biyemata. TAHEER da TAHEERA kuwa suna gefe sun cika bamm ji suke Idan suka kama ameerah ba abunda zai hanasu lallasata . Kamar oumma tasan abunda ke ransu takamo hannunsu suka fita , saida suka fita oumma ta fara tunanin ina zasu koma da zama. Ba yadda ta iya dole su koma BUNKURE da zama , Wanda ba tsoran komawa take ba , aah yadda rayuwar yayanta Zata koma , batasan abunda zai kuntata wa yayanta, ganin tsayuwar ba mai anfani bace yasata yiwa me motar magana , bawan Allah bunkure zaka Kai mu nawa zan baka, 7k zaki bayar. Haba bawan Allah kadan duba mana, shikenan ku kawo 6k , kallan TAHEE da TAHEERA tayi da su shiga , ko wannansu jiki a sanyaye yashiga inda abunda suka tsana shine zuwa bunkure yadda ake gallazamusu suda mahaifiyarsu, ba adau lokaci ba suka fara tafiya kowa yayi jigum ba meyiwa wani magana kowa da abunda Ke cin ransa. ASALINSU….. ➰➰➰➰➰➰➰➰➰➰ GARIN LAGOS Wasu dankara dan Karan Motocine kefaman zuga gudu akan titi, duk Wanda yazo wucewa sai ya tsaya motocinnan sun wuce tukunna sabida tanbarin da motocin ke Dauke dashi .Duk uban motocinnan basu tsaya a ko ina ba sai a NAHYAN HOSPITAL, one of the best hospital in Nigeria , ba karamun hospital bane da kallo daya zaka masa kasan ba karamun kudi aka kashewa asibitin ba , Kai tsaye wajan parking space suka nufa , cikin wani irin slow motocin suka tsaya , Wanda hakan ba karamun birge masu wucewa yayi ba . Bude motocin akai , wasu blacks American ne suka fito daga cikin motocin ko wannensu sanye da bakin suit da sunglasses,fuskarnan ba fara’a kwata kwata , yayin da hannunsu ke dauke da bindigogi. Daya daga cikinsu ,Wanda ya kasance kamar ogansu ne ya nufa wata black tinted Lamborghini sai faman sheki da daukar ido take.bude kofar motar yayi sai da aka dau kusan 40 seconds kafun ya zuro da kafarsa Guda daya , tubarkallah Masha Allah , wani irin takalmine a kafarsa kamar na sarauta, fatar kafarshi sai faman daukar ido take, wacce take fara kal cikin takalmin kafarsa, an dau kusan 2 minutes kafun mamallakin kafar fitowa. Oh my god , tubarkallah masha Allah , tabbas Allah madaukakin sarki yayi halitta anan, ba kowa bane face TAHNOON , one of the youngest billionaire kenan, daga tsohon president zayed Al_Nahyan, irin su ake kira one in thousand,dan guy din ya hadu tako ina ba Karya. Sanye yake cikin kuftan sai faman maiko da daukar ido take , wacce ta kasance blue colour , bakaramun kyau tayiwa surar jikin saba , wacce ta kasance kakkar fa, kallo daya zaka masa kasan yana motsajikin sa ,farine irin asalin fari mai shegen kyau da tsari, yana dauke da wasu irin sexy eyes fari tass dasu, kwayar idanshi ba Baka bace sannan ba brown bace ,wasu irin idanuwane dashi mai ladaftar da makaryaci, Wanda idanuwansa ba karamun tafiyar da yan mata yake ba, hancinshi dogone ba irin over dinnan ba, amma dogone da yayi matukar yiwa fuskarsa kyau , bakinshi dan madaidaicine Wanda ya kasance pink colour , yana da saje a fuskarsa wanda ya hade da gyaran fuskarsa. Kallo daya zaka masa kasan irin mutanan nanne da ake Kira half cast , ta ko ina gayen nan ya hadu, cikin taku da kasaita ya fara tafiya , Wanda da yawa mutane suke wa kallan girman kai, musamman in ya hadu da kasaitarsa da muskilanci , dan ba karamun miskili bane na bugawa a jarida, amma a hakan ba karamun tafiya yake da imanin mutane ba . Direct cikin premises din hospital ya nufa , duk inda ya wuce sai ma’aikata da majin yata sun gaishesa , daga musu hannu Kawai yake ,yayin da wadannan kattin ke binsu a baya , Daidai wata kofa naga sun nufa wacce ta kasance ta glass , kai tsaye wannan mutumin dazun ya bude masa kofa , lifter ce a wajan , shi kadai ya shiga wajen tare da wannan mutumin , yayin da Sauran suka tsaya . A flour 4 suka tsaya inda yakasance bakowa a wajan ( abun mamaki sai na tarar da wannan kartun sunja layi kamar masu jiran karban sadaqa😂), duk inda ya wuce sai sun Sara masa . Daidai wata kofa suka tsaya , anan ma wannan mutuminne ya bude masa kofa , tafiyar muntuna 2 biyune ya kaisu wata kofar , wata koface tsararriya a wajan me shegen kyau , direct cikin kofar suka shiga , babban office ne iya tsaruwa office dinnan ya tsaru, daga gefan hagunsa wasu dan ubansun cushion chairs ne masu shegen daukan ido ash colour , medium carpet din office din ma ash colour , daga gefan damansa kuma wani gadan duba marasa lapiya ne , daga inda kake kana iya hango table dinshi sai faman daukan ido yake ( irin na yan gayun nan😂), wajan sai faman daukar kamshi da sanyin freshener yake . Samun waje yayi kan daya daga cikin cushion chairs dinnan yayi tare da crossing legs, kallan mutuminnan yayi , cikin husky voice dinsa ya fara magana ,”zaki” shine Sunan da naji ya Kira mutuminnan Wanda in ba natsuwa kayi ba bazaka taba Jin mai have ba, “yes sir “Cewar zaki , “yaushene meeting dinnan”, “sauran few minutes sir “cewar zaki, jinjina masa kai kawai king Yayi tare da Mika masa wasu files karba zaki yayi tare da Sara masa tare da ficewa daga office din , duk wannan abun da yake fuskarshi kwata kwata ba annuri a ciki , ba a dau dogon lokaci ba daya daga cikin wayoyinsa ya fara ringing , sai da ta kusan katsewa sannan ya dauki wayar dake kusa dashi akan center table din gefenshi , UKTI shine sunan da ya bayyana akan screen din wayar , ajiyar nunfashi ya sauke ganin me kiran, dauka yayi cikin kamilalliyar muryarsa, “Assalamu alaikum”Shine abunda yace , ya dau sakanni kafun ya sake cewa komai, “masa’ul khair ukti( barka da Yamma yaya)”, bansan mai akace masaba amma ganin yadda ya natsu zai tabbatar maka da magana ce me mahimmanci suke tattaunawa,ya dau kusan 10 minutes yana wayar wacce ba abunda nakeji a ciki kasancewar cikin larabci yake maganar , baka Jin sautin muryarshi sai bakinsa dake motsawa, a haka zaki yazo ya tarar dashi , sannan suka dunguma zuwa inda aka kebanceshi dan yin meeting . Sun dau kusan 1 and half hours suna tattaunawa game da asibitin da kuma tsare tsaren da za a sake , basu sukabar NAHYAN HOSPITAL ba sai wajan karfe 5 na yamma, Kai tsaye NAHYAN ESTATE dake cikin BANANA ISLAND suka nufa . 🌹GIDAN AUNTY🌹 By mss Lee💕 👑 UK WRITERS 👑 https://chat.whatsapp.com/GOZ7a2miBjZ4vUjRXdRdrA 🫶 Dedicated dis page to my masoyiya ‘yar fillo ta zara’u our star lady ! I heart ❤️ you 🫶… PAID BOOK BOOK 1 📕 ……………..بسم اللهً الرحمنً الرحيم Free Page 2🦋 ➰➰➰➰➰➰➰➰➰➰➰ WACECE TAHEERA TAHEERA yarinyace yar kimanin shekara 17 da dan biyunta TAHEER Wanda suke tsananin kama kasancewarsu yan biyu. Mahaifinsu Malam Mohammad nada wadatarsa kafun yasamu karayar arziki ,yarasu shekaru biyar baya , Wanda a kazo har gida akwai wa kisan gilla, kisan da haryanxu ba’a san ko suwanene ba , yana da mata guda daya me suna maryam wato oummansu taheera , haifaffiyar buzuwace fara tass da ita daga kasar Niger , anan suka hadu da mahaifin su taheera, Wanda yazo kasuwanci kasar. Mahaifiyarsu marainiyace wacce iyayenta suka rasu bata da kowa sai yayanta Wanda tun lokacin baya daya fita da daddare ba’a karajin labarinsaba . Bakaramun wahala da gwagwarmaya suka shaba arayuwarsu , tun bayan rasuwar mahaifinsu taheera , kasancewar dangin babansu basu so ya auretaba, sun so ya auri yar dangi amma malam Muhammad ya nuna baya Santa maryam yakeso . Bakaramun wuya maryam Tasha ba a hannun dangin mijinta, babu me kaunarta sai KILISHI, wacce ta nuna mata so, ta tallafi yayanta har bayan mutuwar yayanta. Kilishi kanwace ga Malam Mohammad wacce suka hada baba dashi kasancewar shi kadai mahaifiyarsa ta haifa sai yan uwa . Ba karamun rawar gani ta taka arayuwarsu ba sabida irin yadda take temaka musu.Itace mace kwallinkwal da take fadar magana aji atake a wajan dalilin Auran wani hamshakin me kudi da take a Garin Lagos , shiyasa duk dangi akejin maganarta.Bayan shekara biyu da rasuwar Malam Mohammed, Malam bashari yanuna Yanasan auran maryam amma kememe maryam ta nuna bazata iya aure ta bar ‘ya’yanta ba , ba irin magiyar da Malam bashari beyiba har maganar tazo kunnen hajiya kilishi, sanin cewa bazata iya yiwa hajiya kilishi musu ba yasa ta Amince amma da Sharadin tafiya da yayanta. Wannan abu beyiwa Malam bashari dad’i ba amma haka yabar abun azuciyarsa. Hajiya kilishi ita ta dauki nauyin kome da kome na bikin maryam, tundaga kan kayan daki da sauransu, shiyasa ba karamun ganin girman matar takeji ba. Shiganta gidan bashari ba karamun wahala Tasha ba ita da yaranta, sabida tsangwaman da ake nuna wa ‘ya’yanta hatta abinci baya bawa ‘ya’yan maryam , ko ta tanbayeshi dalili kaitsaye ze ce mata sabida bashine ubansu ba. Wahalar dasu d’in da yake ne yasa maganar har taje kunnen kilishi Wanda takirashi tayi masa tatas harda i’kirarin zata kulleshi sannan ya saduda. Malam bashari yana da matarsa daya kafun ya auro maryam, asabe kenan wacce suke kira da mamy, mamy wata irin muguwar matace da batasan zaman lapiya , duk wani kulli kulli da tashin hankalin dake faruwa a gidan harda sa hannunta, da farko taso kullum su dunga danbe amma ganin maryam bata biye mata yasa ta canza taku take biyowa ta bayan malam bashari.yar ta d’aya Ameerah , yarinyace fitinanniya bata jin magana , ga rashin kunya a cikinta , Ameerah ta tsani y’ay’an maryam kasancewarsu farare tass kamar ka taba namansu ya fashe wani irin kyaune da su da baki baze musaltaba musamman tahee da take da asalin gashin buzaye har kugu, kasan cewar mahaifiyar su buzuwa mahaifinsu kuma bafulatani . Dalilin da yasa mamy da yarta suka dauki Karan tsana suka dora musu, dan ko ita mamin tasan maryam ta wuceta akomai amma sabida harsada da kyashi taki barinta, a haka har suka kwashe tsawan shekaru uku kafin yanxu rabuwarsu da Malam bashari. ➰➰➰➰➰➰➰➰➰➰ BANANA ISLAND unguwace ta wane da wane da ta amsa sunanta, a jere motocin suke tafiya , tun kafin ayi horn sojojin dake gadin first gate suka wangale musu kofa, tare da Sara musu, wata iriyar koface a wajan kallo daya zaka mata kasan ba Karamun makudan kudi aka kashe akanta ba, cikin kwarewa motocin suke tafiya harsukazo gate 2, nan din ma wani abun kallo ne , karamun titi ne a wajan sai kananan shukokin dasukayiwa wajan kwawanya, wajan bakaramun haduwa yayi ba , minti uku kacal yakaisu main gate din gidan inda yafi ko ina tsare sabida sojojin da ke ke waye da wajan .sanin Wanda yake cikin motar yasa ba bata lokaci aka wangale musu gate , wow !! Wow !! Wow !! Shine abunda bakina ke furtawa tunkan na karasa shiga nasan bakaramun gida bane wannan, dan filine a wajan me dauke da korayen shukoki inda yayi wa wajan kwawanyaw, babban estate ne me dauke da part part na musamman, duk inda ka kalla zaka ga alamun hakan sabida giftawar da masu aiki keyi lokaci lokacin cikin shigar uniform Dinsu . Kai tsaye wani babban glass building motocin nan suka nufa Wanda yakasance daban cikin buildings din , Daidai parking lot din building din motocinnan suka tsaya , ba bata lokaci duk suka fito daga motar, yanxun ma zaki ne ya bude masa kofa, sea da ya dau tsawan lokaci kafun ya fito gaba daya daga cikin motar, Sara masa sukayi a tare , ba Wanda ya kalla a cikinsu sai ma kara tsuke fuskarsa da yayi , a hankali ya fara tafiya cikin takunsa kamar bayasan taka kasa direct main door ya nufa , still zaki na biye dashi har cikin farlon da ya gama haduwa , direct wata kofa ya nufa , shi kuma zaki files din hannunsa ya ajje tare da ficewa gaba daya daga cikin building din. WANENE TAHNOON TAHNOON Wanda ake wa lakabi da KING , shalele kuma mafi soyuwa a wajan mahaifinsa , saurayine Matashi dan kimanin shekara 33 a duniya . Mutumne me matukar dukiya , kasaita da kuma miskilanci , bayasan raini ko kadan,baya shish shigi da shiga sabgar kowa , King babban muskiline Wanda da yawan mutane ke yiwa kallan girmankai, dan da wuya kaji yayi dogon magana da mutum, yawancin maganarsa da idone,king ya kammala karatunsa na likitanci a kasar turkey, a yanxu haka doctor ne shi babba daya karanci bangarori na lafiya, mutum ne shi me temako da sanin darajar mutane , amma in ba zama kayi dashi ba bazaka taba sanin hakan ba. King na da babban asibiti mai suna NAHYAN HOSPITAL, asibitine da yake temakawa marasa karfi duk da kasancewarsa asibitin kudi.wannan dalili yasa mutane ke ganin girmansa da kimarsa.Wanda duk Garin Lagos da ke wayanta zaka samu talakawa nazuwa Neman temako, Hakan yasa talakawa ke mugun sonsa da kaunarsa. Ko guri zaibi zakaga manya da yara na daga masa hannu tare dayi masa kirari, hakan yasa yayi suna sosai a fadin Nigeria dan ba Garin Lagos kawai yake temakawa ba , shiyasa da yawa masu kudi basa sanshi. Mahaifinsa zayed-al-nahyan babban dan siyasane Wanda har mukamun shugaban kasa ya ruke , kuma hamshakin me kudine dayayi Fuce a kasar Nigeria gabaki daya da ke wayanta. Alhaji zayed mutumne adali me temakon jama’arsa,shiyasa ake matukar girmamashi, Adalin shugaban kasane Wanda har yanxu mutane suke kwadayin ya kara shugabantarsu.tsohon shugaban kasa yana da mata biyu, matarsa ta farko Itace hajiya suhaima, hajiya suhaima balarabiyar dubaice daga ita sai yayanta da kanwarta iyayenta suka haifa, macace me matukar miskilanci da kawaici, ga tarin dukiya da Allah ya bata , ga ilimin addini Dana zamani. Hajiya suhaima yayanta 4, Babban d’anta sunanshi mohammed amma Allah yayi mishi rasuwa shekarun baya da suka wuce sai ‘yarta ta biyu samreen suna kiranta UKTI , tayi aure yanxu tana saudiya ita da mijinta, sai king da autarsu zoya. Matarsa ta biyu Itace hajiya kilishi , kamilalliyar mata wacce tasan ya kamata , macece me matukar wasa da yara , baruwanta Sabida kyautatawar ta yasa yawancin yayan gidan suna part dinta. Yar ta d’aya zulaiha wacce ta rasu tun tana yarinya. Suna rayuwane da familyn su cikin da Kaunar juna, tare da kakarsu dasuke kira Dada. Dada masifaffiyar matace gata da rigima ta bugawa a jarida, amma hakan besa ta wulakanta kowa ba , mutumce me temako da san jama’a, duk cikin jikokinta tafisan king duk da yawancin lokuta cikin rikici suke da ita , sai uncles Dinsu guda biyu uncle musaddiq da uncle salim, suma ko wannansu na rayuwa agidan tare da iyalinsa. Uncle musaddiq na da mata biyu hauwau wacce suke kira da mamy tana da ‘ya’ya 3 , kabeer , ihsan, sumayya sai matarsa ta biyu kubra ana ce mata momy tana da ‘ya’ya 2, haroon , firdausi(feedy). Uncle salim kuma matarsa daya mai suna amina ana ce mata aunty , basu da ‘ya ko daya sai ‘yar rikonta mai suna amrah, sabida duk dan data haifa baya dadewa suke mutuwa sai kanwarsu zarmeen wacce take aure a abuja da danta sha’aban. Cigaban labari… ➰➰➰➰➰➰➰➰ Sai gabanin yamma suka karaso bunkure , lokacin ba karamun jigata sukayi ba, daidai babban gida na kasa daya kasance kamar family house suka tsaya , nan yara suka fara taruwa , ga yan birni , ga yan birni Wanda labari har ya fara karadewa . Nan mutanan gidan suka fara leke dan ganin ko suwanene, mutanan da suka ganine yasa su fara kuss kuss ana tuntsurar dariya , duk wannan abun da ake taheer and taheera na gefe, itama oumma duk jikinta a sanyaye yake harta kammala biyan mai mota kudinsa bayan ya temaka musu ya sauke musu kayansu . Tun a soran gidan suka fara cin karo da kwano, ga Shara a wajan. Oumma ce tayi sallama yayin da taheer da taheera ke bayanta,gaishe da su oumma da su tahee sukai ganin babu raya yanxu agidan ma duk an aurar dasu sai wa ‘inda ba a rasa ba, cikin izgili da wulakanci suka fara amsa musu gaisuwar tasu, tare da habaice habaice kowa na fadar albarkacin bakinsa . Wata tsohuwa ce ta fito daga wani daki gashin kanta duk yayi furfura da kar take iya tafiya,”wa nake gani kamar maryama da bankadaddun ‘ya’yanta, me ya dawo daku kuma , ko da yake daman kun saba zuwa ba nosis (notice).”to Nide wallahi babu ruwa na ga dakin kucan ba Wanda yake shigarmuku sabida hajiya kilishi ta Hana, amma wallahi bazaki takurani ba,”wai ma tsaya uban me ya kawo ku wannan karan kuma “, sun ku yar da Kai oumma tayi dan kwata kwata ta kasa magana ma, taheer da taheera kuwa ko wannansu hade rai yayi, in akwai abunda suka tsana a zagar musu mahaifiya. Tabe baki kaka ta bawa tayi” oh ni ‘yasu kujimun muna furci daga tanbaya sai ki wani fara sum sum da kai sai kace wata muna fuka”.tun tsirewa mutanan gidan sukayi da dariya, yayinda ko wa ke tofa albarkacin bakinsa. Ganin abun nasu ba me karewa bane yasa oumma mikewa tare da nufar dakinta Wanda ya kasance na hajiya kilishi ne mallaka musu,dakine a ciki da falo harda d’an kewaye da aka d’anyi mashi daga waje.Balefi kusan duk cikin gidan babu inda ya kai nasu kuma kilishi ta Hana kowa kwace musu acewarta wata rana in suka zo zasu dunga zama a ciki. Shigarsu cikin ‘bangaren sai da suka d’auki tsawan lokaci suna gyaranshi dan ba karamun daud’a yayi ba, suna gamawa duk sallah sukai suka mimmi’ke ga yunwa sunaji amma ba daman cin abinci sabida sunsan ko zasu mutu mutanan gidan bazasu basu ko ruwan shaba. Haka suka zauna oumma da tahee suna daki d’aya yayinda taheer kuma yake shinfida a falo dakin. Cab cikin dare lokacin da kowa ke hutawa wani ba’kin haya’kine ke tashi kad’an kad’an kafun daga baya wannan bakin ya bace batt…, can dakinsu taheera kuwa wani abune kamar silver yake faman she’ki a jikin taheera yayin da fatarta ke d’auke da wannan silver d’in kamar na maciji, kafun wani lokaci ta rikid’e tare da dawowa katuwar macijiya, ko munti 2 batai ba jikinta ya kuma dawowa Daidai, sai nan ta kara dawowa wannan macijiyar, daidai gabanin asuba jikinta ya dawo daidai, kwata kwata babu alamaun wannan macijiyar. ➰➰➰➰➰➰➰➰➰➰➰ Comment and share ✍️ GIDAN AUNTY ❤️ (A heart touching love story) By Aysha Galadima ( mss Lee) 💖The talent troupe🔥 PAID BOOK BOOK 1📕 Bismillahirrahmanir rahim….. Free page 3 🦋 ➰➰➰➰➰➰➰➰ Wani kayataccen daki yashiga babban gaske me shegen kyau da tsaruwa , duk da kasancewar komai na part din da glass akayishi hakan be hana tsantsan kyauwun dakin boyuwa ba sai ma kara futo da ainahin kyan da yayi.Direct inda wardrobe din dakin yake ya nufa, daga jikin wardrobe din ya danna wani abu me kamar design , take wardrobe din dakin ya rabe biyu wasu manyan elevator guda biyu ne suka bayyana,na farko yashiga inda ya danna 3, direct floor 3 ya kaishi, wani katafaran falo ne awajan komai na cikin falon white colour ne hatta da labulayen dakin, ga wasu dan ubansun 2 set sofa masu shegen kyau a wajan suma white colour , daga kasanshi kuma wani lallausan farin carpet ne me shegen laushi, daga gefe a kwai standard glass da komai na cikinsa kana iya gani, iya haduwa falon ya hadu , baka jin komai na tashi sai sanyin ac da kamshin turare , a hankalii yake taka kafarsa kamar bayasan takawa, kai tsaye center table din falon ya nufa , remotes din dake center din falon ya danna, a hankali gefe daya na labulen ya fara budewa, tsarki ya tabbata ga Allah madaukakin sarki, wani kayataccen daki ne ya bayyana komai na cikin dakin white colour din hatta furnitures din dakin , babban gado ne a dakin me girman gaske sai shimfidarsa da ya kasance white and black,, daga gefe daya wani chair ne a wajan me shegen kyau shima white colour , iya tsaruwa dakin ya tsaru, direct toilet ya nufa ya dau kusan 30 minutes aciki kafun ya fito da white din jallabiya fara kal da ita , gaban mudubin dakin ya nufa wanda yake shake da mayuka mabanbanta da turaruka masu shegen kamshi,imperial majesty kawai ya fesa a jikinsa , take dakin yacika da kamshin turarensa , ba’ajin kamshin komai sai na imperial majesty daya cika dakin. Rawanin da larabawa ke daurawa ya daura akansa,inda ya futo cak a balaraben sa,ba karamun kyau kayan sukayi wa fatar saba , iya haduwa ya hadu , daga gefan fuskar sa kwantaccen bakin kashin kansa ne ya fito sai faman kyalli yake, bakin sajan bakinsa me shegen kyau ya futo da ainahin pink lips dinsa,rawanin sai ya kara futo da kyawawan idanuwansa masu zara zaran eye lashes ,tare da bakar gashin girarsa,iya kyau yayi kyau ba karamun na wasa ba, duk wanda ya kallesa sai yaso yasake kallansa, fatabarakallahu ahsanil kalikin shine abunda nake fada kawai a raina. Yanxu ma be zauna ba, wayoyinsa kawai ya dauka tare da ficewa a dakin baki daya.direct down stairs ya nufa yanxu ma ta elevator ya nufa, a kasa ya tarar da zaki, zaki na ganinsa ya sara masa tare da saukar da idansa dan ba karamun kyau uban gidan nasa yayiba , “tabbas ubangidan sa na da kyau , kyau da ake kira kyau” duk cikin zuciyar sa yake magana , cikinsauri kuma ya bude wa king motar da ya dauko kirar mercedez benz ganin ya karaso inda yake ,basu tsaya a ko ina ba sai babban masallacin dake unguwarsu,bayan idar da sallar magriba din ma basu bar masallacin ba sai bayan sallar isha’i, duk kallan da ake masa yanaji amma ko dako wa yaga masu kallan nasa beyiba sai ma kara tsuke fuska da yayi, ana idar da sallah zaki yaja motar tare da barin unguwar baki daya. ➰➰➰➰➰➰➰➰➰ Sallar asubane ya tayar da oumman nasu, tahee!! Tahee, “uhm” cewar tahee, oya a tashi lokacin sallah yayi, yanxu ma “uhm”ta karacewa kafun a hankali ta soma adduar tashi daga bacci,falo takoma tare da tashin taheer, ganin ya’ki motsawane yasa oumman mi’kewa “nasan sarai kana jina maxa ka tashi kafun ranka ya ‘baci”, murmushi yasaki tare dayin adduar tashi daga bacci, dama ya rigada ya tashi tun lokacin da oumma ta fara tashin taheera ya farka. mimmikewa sukai tare da dauro alwala kasancewar har gidan ana jin kiran sallah yasa su bin jam’i, bayan sun idarne ko wannan su yayi adduar safe da maraice kamar yadda suka saba a kullum,”oumma ina kwana”duk suka hada baki wajan gaishe da oumman tasu, murmushi oumma ta saki”fatan ‘yan biyu na sun tashi lapiya”, “lapiya lou” suka amsa mata.suna zaune sukaji sai faman buga musu kofa ake , tashi oumma tayi tare da bude kofar , ba kowa bace face kaka tabawa , daure da daurin kirji, gaishe da ita oumma tayi, tabe baki kaka tabawa tayi “ba gaisuwarkice ta kawoni ba, maza maza ki tashi kigyara tsakar gidan nan ga wanke wanke na jiranki, sannan kisaka tanbad’ad’d’un ‘ya’yanki su d’ebo mana ruwa,dan ba hutu kuka zoyiba”. “Insha Allahu zamuyi”cewar oumma, yanxun ma tabe baki kaka tabawa tayi”ke kika sani, kar Allah yasa kiyima”tana gama fada ta bar wajan , koma wa daki oumma tayi , yanda ta barsu a haka tazo ta samesu sabanin dazu yanxu ko wanne ya yi cidin cidin da fuska dan sarai sunji me kaka tabawa kecewa, murmushi oumma ta saki “kuyi hakuri yan biyun ummansu wata rana sai labari ai”,jikinsu ne yayi sanyi jin abinda oumma tace.kamo hannunta sukayi tare da sata a tsakiyarsu,”kiyi hakuri oumma ba wai fushi mukai ba , kawai bamasan abunda kaka tabawa da mutanan gidan nan suke miki”,shafa fuskar taheer dake magana oumma tayi,”bakomai taheer komai me wucewa ne bana so kuna sa abunda da suke mana a ranku, yanxu ku tashi kudebo musu ruwan da sukace kunji, ku kula sa hanya banda rigima”, “toh oumma “duk suka amsa mata , itama wajan ta biyosu tare da fara sharan tsakar gidan. Sun dau dogon lokaci suna d’ebo ruwan , lokacin har oumma ta kammala share tsakar gidan da ya dawo kamar bashine me tarkace ba. Tulun kayan wanke wanken suka hada ‘kuda sai faman bin kwanukan suke, sundau dogon lokaci suna wanke kwanukan , dadin su daya ma haduwa sukai su duka suka wanke dan ba karamun kwanuka aka bata ba ,gama wanke wankensu ba dadewa aka kawo markadan wake , zama tahee tayi ta buga wannan kullun, yayinda oumma ke hura jikakken ican da aka jika duk idanuwanta sunyi ja sabida yadda hayakin ya cika mata ido. Duk wannan abun da suke mutanan gidan sai faman kai kawo suke , ba wanda yace dasu ko sannu sai ma banzan kallan da ake binsu dashi da hantara.basu suka kammala ba sai wajan karfe shadaya,ragowar guntun dumamen tuwan jiya kaka ta bawa ta mikowa oumma,” kar alashemu ace bamu baku abinci ba ko akai mu duniya” cewar kaka tabawa ,kallan tuwan da baifi cin mutum daya ba oumma tayi, batace komai ba sai ma daki da ta nufa , anan ta samesu sai faman sauke nunfashin yunwa suke ,kwallace ta tarar mata , ganin suna kokarin mikewane yasata saurin goge idanuwanta kada suga rauninta, tuwan da ke hannunta ta ajje musu, cikin sauri suka mike tare da wanko hannayensu,har sun saka hannu zasu fara ci sai suka fasa tare da zubawa oumman tasu idanu,sarai ta fahimcesu amma ko motsawa batayi ba, langwabar da kai sukayi kamar wasu yara oumma suka kira sunanta , girgiza kai kawai oumma tayi tare da mikewa tare da zama a tsakiyarsu.taheer ne ya kutsuro tuwan tare da kallan oumman tasu “oumma haa” dariya duk suka saki ganin yadda ya bude bakin nasa , cikin kulawa yasa mata tuwan, itama taheera saka mata tayi a baki, hannu oumma ta saka itama ta fara basu a baki , duk da tuwan bashi da yawa amma haka ko wannansu yasamu yaci , cikin farin ciki da kaunar junansu. ➰➰➰➰➰➰➰➰➰➰➰ 10:20 pm motarsu ta danno kai cikin gidan , kamar ba dare ba har yanxu akwai hasken futullu da ya haska ko ina na gidan, daya daga cikin building din gidan zaki yayi parking , ya dau kusan 2 minutes zaune a cikin motar idanuwansa a lumshe kamar meyin bacci, a hankali ya zuro da kafarsa guda daya kafun a hankali ya juro da gaba dayar kafar tasa yana mikewa,cikin takunshi me kama da na izza ya fara tafiya tare da nufar kofar da zata sadashi da babban falon building din.Babban falo ne me kirgan gaske da ya cika da tsadaddun furnitures na alfarma , iya haduwa falon ya hadu ba abudna yake tashi sai daddadan kamshi da sanyin ac, ganin bata falon yasa ya juya da niyar komawa, foot steps dinta da ji ne yasashi tsayawa kafun ya juyo a hankali,murmushi ta sakar masa”son “ be amsa ba sai ma zuba mata kyawawan idanuwansa da yayi, sannu a hankali ta karaso wajan, sanye take cikin hijab hannunta dauke da tasbaha sai faman sakin murmushi take , sau da ta karaso inda yake kafun ya bude baki a hankali kamar wanda magana take wa wahala, cikin cool voice din shi me shegen dadi ya kira sunanta “Ammi,”hararar wasa ta jefa masa”sai yanxu ka tuna dani”lebensa ya motsa kamar me sanyin magana sai kuma ya fasa tare da dauke kansa, kamo hannunsa tayi tare da zaunar dashi kan daya daga cikin kujerun falon,”oya zauna ka ci abinci nasan yau kwata kwata ba abuncin kirki kaciba , na kusa yi maka aure kwanannan ko zaka shiga taitayinka”,bece komai sai hade fuska da yayi tare da kau da kansa, murmushi ta sakar masa “mai da wukar son wannan hade rai haka, nima wasa nake maka , ai samun wacce zata siyo zuciyar ka sai anshirya “a jiyar zuciyar da ko ammi dake kusa dashi bataji ba ya sauke tare da sassauto da fuskar tasa kadan . Abincin ta dakko masa da kanta tare da jerasu can center table din gabansa,zubawa tulun abincin data ajje a gabansa idanu yayi sai kace mutum goma zasu ci, bece komai ba sai idanuwansa da ya zuba mata ,sarai ta gane me yake nufi”duk suna part din dada tunda kai cin abinci cikin yan uwan naka ne bakaso”, lumshe fararan idanuwansa yayi, itama ammi bata kuma cewa komai ba sai abincin da ta zuba masa cikin hadaddan plate din da ta dakko, “oya haa” bude lumsassun idanuwansa yayi tare da kallanta, yanda tayinne yaso bashi dariya amma kwata kwata be yitanba, a hankali ya bude bakin nasa ta fara feeding din nasa , 7 spoon yayi tare da kawar da kansa,”son karkace mun kakoshi”lumshe mata ida nuwansa yayi, girgiza kai kawai ammi tayi tare da dakko masa hadaddan kunun ayar da tayi masa, sosai kuwa yasha kudin ayar bayan ya kammala shane ammi ta mike, “oya tuzuru aje a kwanta sea da safe”, bai ce mata komai ba sai mikewar da yayi , dariya amminta saki”bani na kar zoman ba rataya aka bani”inda sabo ta saba da halinsa na kinson yin magana tunda tasan halin kayanta,”Ammi sai da safe “ ya fada cikin husky voice dinsa, side hug tayi masa , Allah ya tashemu lapiya ka kwanta da wuri dan na san ka gaji, jinjina mata kai yayi alamar toh tare da ficewa. Har yanxu zaki na waje kikam kamar bushiya , inda ya barsa anan yazo ya samesa be ce masa komai ba , shima zakim bude masa kofar mota yayi, cikin takunsa na kullum ya nufi motar, haryasa kafa zai shiga sai kuma ya daga idanuwansa tare da kallan wani building sai kuma ya lunshesu tare da shiga cikin motar, daidai part dinshi zaki yayi parking yanxun ma shine ya bude masa kofa . “Sai da safe king”hannu king ya daga masa kabar bazai ce komai ba sai kuma ya bude baki a hankali “good night”. Murmushin jin dadi zaki ya saki be bar wajan ba har saida yaga shigewar king sannan shima ya barwajan. Direct yana shiga part din sama ya hau ta elevator , yana shiga dakin rawanin kasansa ya bayyana,kofar da zata sadashi da toilet ya nufa, ya dau mintuna a cikin toilet din kafun ya fito da wasu white pj mas masu laushi , imperial majesty ya fesa , dakin ya kara dauka da kamshin turaransa da ke kama daki,kan gadan sa ya nufa kai tsaye cikin luntsumeman gadansa, har ya kwanta sai kuma ya mike tare da dakko wasu magun guna .maganin hannunsa ya sha tare tare da bude bedside drawer. Har ya bude zai zubasu idanuwansa suka sauka kan wani hoto dan karami, daukan hotan yayi tare da zuba masa ido . Wasu matasan larabawane a jikin hoton sun rike hannun junansu, kana ganinsu kasan ba karamun kaunar junansu suke ba. Sauke ajiyar nunfashi yayi tare da mayar da magun gunan, shima hotan mayar dashi ma a daninsa yayi tare da danna wani remotes take futulun dakin suka dauke , wasu kaloli masu kyau da haske suka fara cika dakin me kama da dim lights , sannu a hankali bacci ya daukeshi. ➰➰➰➰➰➰➰➰➰➰ Comment and share 💖The talent troupe🔥 Writers of ….✍️ Duk karfin izzata Gidan Aunty Sarki sameer Jini daya Ya fita zakka….. 💖GIDAN AUNTY💖 ( A heart touching love story) By Aysha galadima ( mss Lee) 💖The talent troupe 🔥 PAID BOOK BOOK 1 📕 Bismillahirrahmanir rahim…… Free page 4 and 5🦋 Bugun kofar da akai da Karfine ya katsemusu hirarsu, TAHEER ne ya mike da Niyar bude kofar amma oumma ta tsayar dashi, “dawo taheer bari na bude” fita oummansu tayi suma mimmikewa sukai tare da bin bayanta. Yan gidan ne cike taf a wajan kowa sai faman zabga masu Harara suke , mazan gidan kuwa duk Wanda yaga taheera sai ya kara kallanta sai mafan satar kallanta suke sabamin matan dake harararta. “Munafukan Allah muna furcin me kuke kullawa, bayan kunsan akwai ayyuka a gabanku, shine dan muna furci da kinibibi kuka shige daki dake da ‘ya’yan ki masu kama da tattabaru” cewar wata da tafi kowa za’kewa a cikin su. Zuba wa sarautar Allah ido taheer da taheera sukai wai sune tattabaru hmm . Hakurin da suka ji oumma na bayarwa ne yasa suka maida hankalinsu kanta ,” kuyi hakuri Dije bansan akwai ragowar aiki ba shiyasa”. Matar da aka kira da dije ce ta Dallawa oumma harara “ kyaji da munafurcin ki, inba munafurciba ba me kuke kullawa a daki ko sallan karuwancin da kika saba kike koya musu” baki taheer ya bude daniyar yin magana amma kallan da yaga oumma tayi masane ya hanashi hakan , sun kuyar da kanshi yayi yana taunar lebensa. Wata daga cikin mutanan gidan ce ta soma magana itama “ kinsan dangin Matsiyata ba abunda suka iya sai tsiya in ba karuwanci take koya musu ba me suke yi a dakin”, nan da nan mutanan gidan suka fara musu gori da hantara , suna ci musu mutunci , kowa nagidan da abunda yake fada a kansu, kaka ta bawace kawai bata wajan . TAHEE da tunda aka fadi kalmar karuwanci idanuwanta Suka faru da ha waye ga wani irin ja da sukai, ba abunda ke mata yawa sai kalmar karuwanci ko magan ganun da mutanan gidan suke bata ji, wata gigitacciyar kara ta saki da ya firgita kowa dake wajan hatta taheer da ke kusa da ita, hannunta ya so kamawa amma ta hankadashi , daya bayan daya ta soma bin mutanan gidan da tun lokacin da ta saki ihu sukai shiru da kallo, ba Wanda ne tsure ba da irin kallan da take musu, ida nuwanta ne suka sauka a kan dije dake faman zare idanuwa , a guje tayi ganta , suna ganin hakan kowa na gidan ya Watse dan ba karamun firgitasu tayi ba daga mazan har matan. Wani murmushi taheer ya saki daman yasan za Arina, a zuciyarsa sai faman Allah shikara yake musu. Dije dake kokarin shiga daki tahee ta cafko, riko tayi mata ba na wasa ba , Innalillahi wa inna ilaihi rajiuna Dije take ta faman fadi , fuskar ta tuni ta jike da gumi sai faman zare ido take , jama’a ku kawo mun a gaji shikenan ni fatalwa ta kamani, kukai kawai Dije take majina duk ta bata mata fuska. Ita kanta oumma Dije ta bata dariya kuma ta bata tausayi dan Tasan kome zatayi yanxu TAHEE bazata hakura un tayi mata ta Karfi kuma rashin lapiyar tane zea tashi. Taheer ma dake gefe sai faman kunshe dariyarsa yayi ganin yadda Dije ke faman fadin fatalwa ta kamata. Kallan d tahee tayi mata ne ya sata kunshe bakinta “nayi shiru , Wlh nayi shiru” , tana gama fatar hakan ta rike bakinta gam hawaye na fita, Kwale idanuwan ta TAHEE tayi a kanta , take a wajan Dije ta saki futsari dariyar da taheer yake rikewane ta fito wajan dan ba karamun dariya ta basu ba. Baki TAHEE ta bude da nufin cizonta, lokaci daya kuma ta zube a wajan. Tana faduwa kuwa Dije ta arta a guje duk da kibarta a haka ta ke kudin tana tsine TAHEE a zuciyarta. Daukarta taheer yayi shi da oumma suka nufi daki da ita,” maza dakkomun maganinta “ cewar oumma , be dade ba ya fito dauke da roba a hannunta, ruwan adduar dake ciki oumma ta iba ta dan shash shafa mata a jikinta da fuskarta, nannauyar ajiyar zuciya ta saki , nun fashinanta na Daidai ta . Har yanxu akwai ragowar murmushi akan fuskar taheer , hararar sa oumma tayi” kasan Kai kadai ne zaka iya temakonta, me yasa baka temake taba kabarta a hannu tahee”, wani murmushin taheer ya saki” oumma kinsa konayi kokarin temakonta Nima hadawa zatai dani, ranta ya baci sosai ko nine naje wajan ba ragamun zatai ba “, jinjina Kai oumma tayi Alamar gamsuwa da maganarsa, wata ko daddiyar dari biyu ta dakko tare da mika masa” ungo maza jeka siyo mana kwaki da kyada nasan in ta tashi zata dan ji yunwa , nan yadda ka kalli kowa ba ko kace zaka musu wani abu nasan halin ka sarai, saura kace kaima zaka rama, in naji sabanin hakan ranka zai baci” jinjina mata kai yayi tare da amsa mata, dan tabbas ba hakura yayi ba amma yanxu ba yadda zeyi dadinshi daya tahee ta rama. Kasancewar basu da nida da me ka tin ba dadewa ya dawo , har lokacin tahee bata tashi daga baccin da take ba. Ajje Garin sukai sai da ta tashi sannan suka hada, har lokacin fuskarta a hade take , ba Wanda ya kulata a cikinsu har suka kammala cin abincin, maganin dazu oumma ta mikowa tahee , tana bata rai ta karbi maganin a haka ta shanyesa. Kiran sallar da ake ne ya sasu mikewa tare da dauro alwala, lokacin ta saki fuskarta kamar ba Itace tagama tsorata Dije ba, sallah suka kabbara tare da bin jam’i, bayan sun idan ne sukayi shafa’i da wuturi, sannan ko wannansu ya biya wa oumma haddar alqur’ani cikin natsuwa. Bayan sun kammala ne oumma ta kara musu arba’una Hadith da ahlari, sai da ta tabbatar sun gane sanna suka zauna suka fara hirarsu irin tasu sai faman tsokanar oumma suke kamar wata kakarsu. Ganin 11 tawuce ne yasa oumma ta umarcesu da suje su kwanta. ➰➰➰➰➰➰➰➰➰ Karfe 2 ya farka daga baccin da ya daukesa, a hankali ya fara karanta adduar tashi daga bacci cikin daddadar muryasa, sanna ya mike kamar bayasan taka kafafuwansa. Toilet ya nufa be dade ba yafito kyakkyawar fuskarsa dauke da ruwa da Alama alwala yayi, duk da kasancewar dare ne hakan be Hana takunsa na mazantaka canzawa ba, inda shinfidaddiyar farar daddumar take ya nufa tare da kabbara sallah cikin nutsuwarsa,ya dade yana nafilfilu sannan ya fara karatun alqur’ani mai girma a hankali cikin daddadar muryarsa ne ratsa zuciya kamar karya dena .sai da ya kammala suratul bakara gaba dayanta , sannan ya fara adduoi cikin harshen larabcin da ya zauna a bakinsa, ko wace harafi na futo wa . 4:2 shine abunda agogon wayarsa ya nuna masa, lumshe fararan idanuwansa yayi da suka fara canza kala tare da mikewa, inda system dinshi yake ya nufa , ya dade yana operating a kanta , kiran da ake na sallar asuba ne ya katse masa aikin da ya fara a system din nashi, ajjeta yayi gaba daya tare da gyara zamanshi kamar Wanda bazai tashi ba sai kuma ya mike tare da nufar hangar da zata sadashi da bathroom dinsa. Be dade ba ya fito cikin wasu kananan kaya white colour masu shegen kyau, damtsen hannunsa ya fito sosai , yayinda budaddiyar rigarsa me shape din v ya futo da kirjinsa kadan , sosai kayan sukai masa kyau , yalwataccen gashin Kansa masu sheki da san tsi sun kwanta luff tare da harneda da sajan fuskarsa, sosai kayan sukai wa kakkarfar surarsa kyau , ba abunda yake tashi sai kamshim imperial majesty . Masallaci suka nufa shida zaki bayan An idarne kamar kullum ya umarci zaki ya bawa liman kudi yayi Sadaka,kamar yadda ya umarceshin haka yayi liman sai faman addua yake masa. Direct gida suka koma bayan an idar da sallah , part din dake tsakiya zaki yayi parking , king kuma ya shiga part din. Zaune yake cikin fararan kaya , dattijon arziki kenan, uban marayu, fari shima amma ba kamar king ba, kana ganinsa kaga bafullatani dattijo. Ciki ciki king yayi sallama tare da nufar inda mutumin yake , amsa sallamar mutumin yayi tare da zuba masa kyawawan idanuwansa irin na king, kawar da Kai king yayi tare da zama a kasa wajan kafafuwan mutumin . Ya dau kusan 5 minutes zaune a wajan bece komai ba shima mutumin bai tanka masa ba har ynxu kuma bai dena kallan nasa ba. Dakyar ya iya bude bakin sa cikin daddadar muryasa kamar Wanda aka sa dole,” ina kwana abeey, ya karfin jiki”, nannauyar ajiyar zuciya ya sauke tare da amsa masa , lapiya son , jikina kuma nayi sauki ai, am getting much better now “. Dago da kaifafan idanuwansa yayi yana kallan mahaifin nasa , kawar da Kai abey yayi daga kallan king ya maida kan jaridar dake hannunsa . Sallamar da akaine ya Hana king magana , akan kujeran falan suka zauna, daya daga cikin sune ya fara magana” yaya barka da Safiya”, murmushi Abeey ya sakar masa “ katashi lapiya musaddiq”, amsa wa yayi da “lapiya Lou “, shima na kusa dashi gaishe shi yayi abeey ya amsa cikin kulawa. Kamar be san da mutane a falan ba,ya dau kusan mintuna yana juya yadda zai fara , kafun ya soma magana ciki ciki” ina.. kwana uncles “ daga haka be kara cewa komai ba, duk cikin su babu Wanda be san halinsa shiyasa basu damu ba Suka amsa masa cikin kulawa . Mikewa yayi tare da kallan abeey” take care” , jinjina masa kai abeey yayi, yana gama fadar hakan ya juya tare da barin part din, da kallo duk suka bishi suna kara jinjina miskilanci irin na king . Yana komawa part dinsa , Wanka yayi cikin tsada sun suit dinsa black colour da suka fito da ainayin kalar fatar jikinsa , black hair din sa da ya hade da sajensa sai faman daukan sheki suke , hannunsa sanye yake cikin diamond watches , har yanxu fuskarsa a hade take karamun pink lips dinsa ya kara turuwa sosai , sosai kayan sukai masa kyau danshi din kyakkyawa ne da baki bazai iya fassara wa ba , yanxu ma ta elevator ya sakko kasa, ko kallan dining din da aka cika da kayan breakfast bayiba, zaki ne ya bude masa kofar falan shima fuskarsa a hade take sosai . Wasu irin tsadaddun motocine jere a wajan sai faman kyalli suke , wata farar Mercedes’ benz aka bude masa , basu tsaya ko ina ba sai wani babban part dake cikin gidan. Cikin daya daga cikin kayataccen chairs din falon ya zauna , daddadan kamshin turarensa ya mamaye ko wana turare dake falon bakajin kamshin komai sai kamshin imperial majesty. Sanye take cikin wasu cotton din kaya masu laushi da sanshi, idanta sanye da farin glass sai faman mita take ita kadai, ganin wanda ke falon ne yasata tabe baki, “ nifa Adena zuwa ana takuramin, ina dalili Ance kayi aure kaki sai kazo ka tare min a daki da sassafe fisabilillah “, kara tsuke fuskarsa king yayi cikin daddadar muryarsa ya gaisheta “ Dada ina kwana , ya karfin jiki”, sallallami wacce aka kira da dada tayi , “yanxu fisabilillahi saraki zautacciya kamayar dani da har kakemun ya jiki!”to wallahi bari kaji, lapiyar da nake da ita ko ubanka baba tunanin yana da ita , bai kula taba Samm , dada kuwa sai faman mita take yace mata ya jiki,mikewa tayi tare da shiga wata kofa bata dade ba ta fito dauke da wani glass cup , ajje sa tayi a gabansa “maza maza ka shanye furar da kazo ka ka tattara ka Barmin daki”, ko kallan furar da ta ajje beyi ba sai da ya Mula dan Kansa sannan ya fara sipping din furar a hankali, furar tayi masa dadi sosai amma a zahiri sai ka dauka dole akai masa yasha,ko rabin cup din be shaba ya ajjeta “pray for me” , inma zagina Kayi kai da Allah “purey (pray ) din kawai naji,”Allah ya tsare ka dan Jikalle , Allah ya kawo auranka jibi jibi” tsuke fuskar sa yayi jin adduar ta ta karshe , diamond watches dinsa ya kalla tare da nufar hanyar fita daga falan Daidai lokacin da abeey da uncles dinsa ke kokarin shigowa,cikin tsokana uncle salim ya soma magana “wato kazo kacinyewa yar tsohuwarmu abinci kabarmu da kanzo ko”, duk murmushi suka saki yayinda fuskarsa take a haden ta har ynxu , wani murmushin abeey ya saki dan Sarai ya gane be san surutun da uncles din ke masa, uncle musaddiq ma sai faman dariyarsa yake ,sallama yayi musu tare da nufar part din mahaifiyarsa, bakowa a kantameman falon , direct dakin da yasan zai sameta ya nufa, knocking din kofar yayi, shiru ba’a amsa ba na kusan sakanni kafun ta bada izinin shigowa, cikin nutsuwarsa ya tura kofar dakin tana zaune cikin shigarta ta kullum, garage kyakkyawa irin asali da kyawun larabawa, doguwar jallabiya ce a jikinta red colour me shegen kyau da tsada , stone din jikin rigar sai faman kyalkyali yake, wata farar yarinyace a jikinta fara sol me kama da king kamar an tsaga kara, sallama yayi tare da karasa shigowa dakin, dagowa yarinyar tayi da sauri tare da nufarsa “AKHI!! ANA FI AINTIZARIK MUNDH ALBARIHA(yaya!! Tun jiya nake jiranka) ta karasa fada kamar zata saka kuka, lumshe mata idanunsa yayi tare da shafa fuskarsa da kyar ya furta “ana asf habibaty ( am sorry sweetheart), “hasanan akhi’usamihuk( okay brother , I forgive you). Zoya !! Matar dake saune ta fada , cikin kinkina ta amsa mata “naam ummey”, ala yumkinuk an tahyiah lam ‘udadhirk min dhalik( bazaki gaishesaba , ban ja miki kunne ba) cewar ummey, kamar zatai kuka tace “ana asf ummey( kiyi hakuri ummey), sannan ta mayar da hankalin ta Kansa “ana asf akhi, sabah alkhaiyr( am sorry brother , ina kwana), girgiza Kai Kawai yayi dan har ta fara sa masa ciwon kai. Cikin Yaren larabci ya gaishe da ummey, ba yabo ba fallasa ta amsa masa, bayan gaisuwa ba wanda ya kara magana sai zoya dake faman yi masa surutu, mikewa yayi tare da yi mata sallama , bin bayansa tayi da kallo har ya bar part din ka fun sauke nannauyar ajiyar zuciya. Tun daga entrance din falan ya fara jiyo hayaniya na tashi sama sama , yana shiga ya tarar dasu zazzaune a falon sai faman kwasan dariya suke, ammi na zaune tana kurban tea . Sallamar da yayine yasa falon yin shiru, kamar ba kowa aciki sai faman zare idanu suke , ganin sunyi shirune yasa ammi dago da idanuwanta, wanda ta ganine yasa ta sakin murmushi ,daman nasan za arina ta fada a zuciyarta, dukansu sak kowa sukai daga kan kujerar da suke , sai faman muzurai suke , cikin hada baki yan matan saka gaishesa” yaya king .. ina kwana”, kallan da yayi musune yasa hantar cikinsu kadawa, be amsa musu ba sai ma tanbayar da ya jefo musu, cikin husky voice dinsa “me ya hanaku zuwa makaranta”, ko waccensu tsure wa tayi suna kallan ammi ta gefan ido ko zata sa baki,ammi kuwa sharesu tayi, fingers din hannunsa ya daga musu “10 minutes only”, a guje ko waccensu ta bar part din dan sunsan ammi ce ta cecesu da bata wajan da Sunansu sorry. Suna barin part din ammi ta kalleshi, kaji da di daka tarwatsamun yaya , be amsa mata ba sai gaisuwar da yayi mata, itama bea dade ba yabar part din. Cikin wasu irin slow motocinnan suka fara fita, duk inda ya wuce sai kaga ana saramasa, suna hawa kan titi motocin suka fara gudu, sir ina zamu cewar zaki, ya dau mintu biyu kamar bazai tankaba sai kuma ya bude bakinsa” company “. ➰➰➰➰➰➰➰➰ Manage please abubuwane suka dan shamun kai.. Comment and share ✍️🫶 💖the talent troupe 🔥 Writers of …… Duk karfin izzata Gidan Aunty Sarki sameer Jini daya Ya fita zakka… 💖GIDAN AUNTY💖 By mss LEE 💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖 PAID BOOK BOOK 1📕 FREE PAGE 6 Yau ma da asuba suka tashi, bayan sun idar da sallah aikin gidan suka fara , TAHEER da TAHEERA suka debo ruwa kafin suyi wanke wanke, yau ko buga kofarsu da aka saba yi ba ayi ba, gidan tsit kamar ba kowa a ciki, suna kammala aikin nasu daki suka koma, wata tsohuwar 200 oumma ta basu “nasan kunajin yunwa, kuje Wajan abu me kosai kuce ta baku kosai”, Godiya sukai mata tare da nufar kofar da zata sadasu da waje , a hanya suka hadu da Dije zata shiga ban daki , tana ganin su tai saurin shigewa bayi tana tsine musu, basu bi ta kansu ba dan yunwa suke ji . Basu dadeba suka dawo, ganin oumma na karatun azkhar dinta yasa basu kuma cewa komai ba har saida ta kammala . Kosan tahee ta Mika mata tare da dakko musu wani plate din robber , juye kosan sukai a ciki tare da faracin abinsu, bayan sun kammala ruwa suka sha tare da yin hamdala, sai lokacin suka fara yar hirarsu, musamman taheer da taheera , oumma na sa baki lokaci zuwa lokaci. “Oumma” cewar tahee, amsa mata oumma tayi da “uhm” ko muma kosannan zamu kwadayi ko za a siya,Jim kadan oumma tayi kamar ne tunani abinda zatace sai kuma ta kalli tahee” banki ta taki ba auta, amma kinsani ko mun fara ba barinmu zasuyi muyi ba, kinmanta abunda ya faru kwanaki”, turo baki tahee tayi jin oumma tace mata auta” wai TAHEER ne fa auta amma kullum ni kike cewa auta”, kallan up and done TAHEER yayi mata “shikenan zo mu kwada tsaho , duk Wanda ya fi tsaho a cikin mu shine babba”, dariya duk suka saki dan sun sa da biyu ya fada mata wato dan ya fita tsaho. Daga waje suna jin yadda yan gidan ke musu habaici da zagin su musamman Dije da yarta. Da azahar ma haka suka sha kwaki da gyada cikin raha da kaunar junansu, bayan sallar isha’ine suka roki oumma zuwa dan dali, sai da oumma ta ja musu kunne sosai sannan ta barsu sukaje. Suna tafiya suna hirarsu Daidai sunxo shiga dandali tahee taji abu ya soketa, wajan ta taba Daidai inda shatin maciji ya fito a ciki dan kadan, TAHEER ne ya ankara da zanan macijin yayi sauri ya sa hannunsa a wajan, kamar kiftawar ido shatin ya bace bat. Hararar ta TAHEER yayi “me yasa ba kya kula , yanxu da wani ne yaga tanbarin macijin nan bani ba me kike tunani”, girgiza masa kai tahee tayi “bansan ya Akai ya fito ba sabida naji kamar wani abu ya tsirenii a wajan, ina tunanin akwia abunda yake faruwa a masarauta, dole muje mugani “daidai taheer ya bude baki da niyar yin magana yaji an bangajesu tahee har da faduwa kasa, kashi tayi a fusace da niyar bin bayansu amma TAHEER yayi azaman rike hannunta,” kasake ni, Raina ya baci”, kin sakinta taheer yayi sai ma wani abu me kama da na fito da ya dakko ya fara busawa , cikin kankanin lokaci tahee ta fara sauke ajiyar zuciya. “ ki dinga sassaita fushinki , banaso ranki yana baci , anjima zamuje daula”, gyada masa kai tahee tayi suka nufi wajan dandalin. Suna shiga aka fara gulmarsu ana zaginsu , iya kuluwa tahee ta kulu ganin yadda ake nunasu ana dariya, saurin damke mata hannu TAHEER yayi tare da girgiza mata kai suka kama hanyar komawa, jin muryar bintalo sukayi tana fadin “yanxu ma haka ana tunanin ba kawun mune ubansu ba , shiyasa ma ake nuna musu hantara ,kun manta uwarsu ba yar kasar nan bace kowa dai yasan halin buzaye da bun malamai “, saurin fusge hannunta tahee tayi, da nufar inda bintalo take , saukar marin da bintalo taji a fuskar tane yasa ta wuntsulo wa , tahee bata kyaletaba, ta kara tsinka mata wani marin, duk Wanda yayi kokarin binta sai tahee ta tsinka masa mari, taheer nagefe yana kallansu , sai faman sakin murmushin Mugunta yake, ganin tahee ta shako wuyan buntalo ne yasa shi nufar inda suke , yana zuwa da niyar rabasu shima ya samu nashi rabon dukan, kwata kwata tahee idanuwanta sun kulle, kara nufar su taheer yayi da niyar rabasu yanxun ma wani raban dukan ya samu, Daidai wajan kafadun ta ya samu ya daka da karfi, ko motsi bata karaba ta zube a kasa , bintalo ma sai faman zare ido take dan ba karamun shaka tahee tayi mata ba, duk kawayen ta da suka labe suka fito sai faman zugata suke akan abunda tahee tayi mata, ba Wanda ta kula a cikinsu sai kwallar bakin ciki da take, hanyar gida ta nufa kawayenta na taka mata baya , shima TAHEER kama tahee yayi suka nufi hanyar gidan. A soron gidan suka samu mutane shake a wajan, ga bintalo a gefe sai faman kuka take , kowa maida kallansa yayi kan su taheer dake shigowa, “muna fukan Allah har kun dawo,kenan toh wallahi bazata sabuba me yata tayimuku da zakuyi mata irin wannan bugun, ita uwar taku da yake tasan me kukai shiyasa ta makale a daki taki fitowa “cewar dije, kallanta TAHEER yayi kamar ma besan me ya faruba “aunty dije lapiya, ko Ance miki wani abune”, duk zuba masa ido suke bintalo kuwa tun bayan shigowarsu taji kamar abu ya shigar mata ido.hararar sa wata daga cikin kawayan Dije tayi” karya za ai maka kenan “, kallan ta TAHEER yayi sosai “ni bansan akan abinda kuke magana ba , in kuma akwai wani abun ai sai ta fada muji “,kallan bintalo dije tayi” maimaita abunda yayi miki ai ba karfin mu suka fi ba, ina daga masu kafane”,narnar bintalo tayi”inna daman ba abunda sukai mun, nice bansani ba na bangajesu suka fadi”, salati mutanan gidan suka fara , yayin da kawayen dijen suka fara binsu da kallo. Wani dan iskan murmushi TAHEER ya saki tare da nufar dakinsu da tahee duk wannan abun da ke faru oumma na daki na bacci batasan me ke faruwa va. ➰➰➰➰➰➰➰➰➰➰ Cikin wani hadaddan company motocinnan suka tsaya, daga saman company din ansa A_N_business enterprise’s, yanda aka rubuta sunan company din shi kansa abun kallo ne , komai na cikin company din da glass akayishi amma baka ganin komai da ke ciki saida su mutanan ciki su ganka. A Daidai wani parking space motocin sukai parking, zaki ne ya bode masa kofa, har yanxu lumshash shun idanuwansa a kulle suke, sai yanxu ne ya bude su a hankali, kafafuwansa ya fara zurowa kafun ya fito daga cikin motar gabaki d’aya,tunda ya shiga company’n ma’aikata ke ta faman miko gaisuwa,da hannu kawai ya ke amsawa bata re da yace komai ba Wanda sun Riga da sun saba da yanayin amsa gaisuwar sa . Daga inda zai hau lifter duk sauran bodyguard din suka tsaya ,shida zaki ne kawai a lifter din , Kai tsaye floor 4 dake last floor suka nufa,baka jin ko wace irin hayaniya a wajan komai tsit kakeji sai kamshin da sanyin ac dake tashi ta ko ina. Wata kofa zaki ya bude masa daga samanta an rubuta C.E.O TAHNOON cikin wani stylish way , ha daddan office ne ya bayyana me shegen kyau da tsaruwa iya kyau office din ya hadu kamar ba a shigarsa amma ko ina tsaf tsaf yake , daga cikin office din akwai wasu dan ubansu set din kujeru masu shegen kyau daga kan table din akwia wani dan karamin hotan samari su biyu masu dauke da harafin M&T,a kan daya daga cikin set din kujerun ya zauna, wasu briefcase zaki ya miko masa, be amsa ba illa “seat “ kawai daya ce cikin cool voice dinsa, cikin girmamawa zaki ya amsa da “ thank you boss” kafun ya samu waje ya zauna,rikitattun idanuwansa ya Dora kan zaki kafun a hankali ya furta “explain”. Gyara zaman shi sosai zaki yayi tare da soma bayani” boss duk wata sai an furar da makudan kudi daga a susun bankin company dinnan, batare da cikakken dalili ko sa hannu ba ,a cikin shekarar nan an rasa makudan kudade masu yawan gaske tacikin wani asusun banki da haryanxu ba a ganoshi ba”.sannan ya cigaba da yi Mishi bayanin abubuwan da ya shafi company din, kamar ba sai amsa ba tsahon munyi biyu kafin ya bude bakinsa” ina bukatar bayani game da futar kudinnan, sannan ta Wana bank ake fitar dasu”, jinjina masa kai zaki yayi “okay sir “ tare da nu far hanyar fita, “called zuhra” yaji saukar muryarsa, nan ma “okay “ kawai zaki yace masa. Dafe goshinsa yayi da ya fara sara masa sabida doguwar maganar da yayi, ko mintuna biyu cikakku ba ai ba akai knocking din kofar, shiru ba a amsa ba sanna ba a kara knocking ba kusan tsawan 3 minutes , kafun ya bude baki “come in”. Da Sauri aka bude kofar tare da shigowa ciki, tunda ta shigo ta zuba masa manyan ida nuwansa,be dago ba amma yaji yanda take binshi da kallo, ya tsani kallo amma duk da hakan be matsa daga inda yake ba , bata Ankara ba sai jin dakakkiyar muryarsa tayi “get out”, sosai jikin ta ya fara rawa sam hankali da nutsuwarta ya tafi akallon irin kyawun da yayi kamar kullum kara masa kyau ake , saukar marin da taji a fuskarta ne yasa ta shiga taitayin ta cikin rawar harshe ta furta “ am sorry boss” tare da nufar hanyar fita , sai faman tsine wa zuciyarta take akan gaggawanta dan ko zatai yawo tsirara king natane ( uhmm😟).ranshi ba karamun baci yayi ba amma a zahiri bazaka taba tantance Wana yanayi yake cigaba , system din gabansa ya dauka , ya dade yana anfani da ita ka fun ya ajje ta ya lumshe ido. Wutace keci sosai ta ko ina , da anyi kokarin kasheta karfin ta zai kara yawa, sosai wutar keci da wuta ga wasu bakin abubuwa dake yawa a wajan , gigitacciyar karar da aka sakine ya farkar Dashi daga baccin da ya fara . Launin idanuwansa harsun fara canzawa daga fari zuwa ja,gaba daya jijiyoyin wuyansa sun mike wata irin zufa ya fara , hannunsa na dama ya daga wani siririn diamond din abun hannune ya fito me dauke da harafin M&T, gaba daya zuciyarsa ba dadi, bazai taba mantawa da bakar ranar nan ba. Zaki ne yashigo office din ganin halin da king yake ciki ba karamun shiga tashin hankali yayi ba, wata drawer yayi saurin nufa cikin gaggawa ya dakko wata allura, da kyar ya samu yayi wa king a wuyansa,kafun a hankali nunfashin sa ya fara dawowa daidai, launin idan sa da ya kada ya fara dawowa Daidai. 5:30 sukabar company kai tsaye wani part yashiga acikin part dinsa, komai nacikin part din royals ne tunda ga kan kujerun falon da ya gaji da tsaruwa , be bata lokacin ba Kai tsaye bedroom din falon ya shin shima sosia dakin ya dahu iya haduwa. Ya dau kusan 10 minutes cikin toilet kafun ya fito sanye da white bathrobe kall dashi,jikakkiyar gashin kansa sai faman tsiyayar ruwa take. Wata kofa dake gefan Hagu ya shiga , ya dade a ciki kafin kamshin turaran sa ya kara de ko ina, a hankali yake fitowa daga cikin dakin , shigarsa ba karamin kyau tayi masa ba , yayi kyau sosai har ynxu fuskarsa a daure take . Masallaci suka dufa shi da zaki bayn an idarne suka dawo gida kai tsaye part din ammi ya nufa, ba kowa a part din,sai yalwataccen Hasken da ya cika falon, bin ko ina na falan yayi da rikitaccen idanuwansa, ringing din da wayarsa keyi ne ya katse masa, be dauki wayar ba har sai da ta kusa tsinkewa ,daga cikin wayar bata bari yace komai ba tace “part din granny now” , tana gama fadar hakan ta kashe wayanta. ******* Zazzaune ko wannansu yake a falon , ko wa ka gansa cikin farin ciki da annashuwa, daga gefe daya wasu yan matane su su hudu zAune a wajan sai faman hirarsu suke , daga Dayan side din ma wasu manyan mutane ne ke tattaunawa. A hankali kamshin turaransa Da baya boyuwa ya kara de ko ina na cikin falon, lokaci d’aya falan ya dauki shiru kowa hanyar shigowa ya zuba wa ido, a hankali yake taka kafarsa har ya shigo falon , fuskarsa kwata kwata ba alamun murmushi sai ma kara kadeta da yayi, sosai farin kayan jikinsa ya futo da tsantsan kyawunsa,motsa bakinsa yayi ciki ciki da yin sallama, a tare falon suka amsa dan ba wai sallamar sukaji ba ta motsin bakinsa suka gane. Zoyace ya taho da gudu da niyar rungumeshi, kallan da yayi matane yasata Jan burki “ana asf akhi( am sorry brother )kwalla harta fara tarar mata, lumshe idanuwansa yayi tare da bude mata hannusa guda daya , a guje ta karasa wajan sa tare da rike hannunsa” welcome back akhi , I missed you the whole day”, lumshe mata ida nuwansa yayi tare da budewa kasa kasa ya amsa mata “ me too”, direct inda mahaifinsa yake ya nufa, zazzaune ko wannansu yake cikin takaitaccen magana ya gaishesu, kowa amsa masa yayi sai faman binsa da kallo suke , abeey sai faman sakin murmushi yake . Hajiya Amina ( uwar gidan uncle musaddiq) wacce ake kira da mamy ce ta soma magana “ Kai dai king kayi wuyar gani, ba a ganinka Indai ba a part din dada ba ko na ammonia”, matar uncle Saleem ce ta Dora “ Aushe duk kanwar jace “. Murmushi ammi ta sakar musu “ Kude kawai kun fada ne”, mikewa king yayi tare da nufar wani sofa dake can gefe dasu, kallan dada zoya tayi, cikin tsokana ta kira sunan ta”dada”, harara dada ta wata a mata “kinibabbiya ba kiran Allah da annabi kikai mun ba, tunda kinga ubanki ai dole kikashen murya”,langwabar da Kai zoya tayi “Haba my dada nasan akhi na beci abinci ba , he need some coffee before eating”, tsaki dada taja “ ke kika sani kuma inma zagina kikai ba na hanaki yimun magana cikin yaran nasara ba, wani wai kamfin ( coffee)ke kika sanshi”,kowa na falon yadda dada ta kira coffee din sai da yaso basu dariya amma ba damar yi harta king maganar taso bashi dariya amma sai wani hade rai da ya kara.kallan akhi dake gefe zoya tayi, saurin daga mata hannu yayi alamun ba ruwansa ,maida kallan ta tayi kan ummey , itama dauke idanuwanta tayi daga kanta,mikewa ammi tayi nida ba a sako niba bari na bada coffee din, kulle idanuwanta zoya tayi tana dariya ,daya Daga cikin yan matan ne ta mike, kallanta ummey tayi amrah ina zuwa, cikin in ina wadda aka kira da amrah ta soma magana “dama zan taya ammi ne”jinjina mata kai ummey tayi , direct kitchen din dada ta nufa , basu dade ba suka fito daga kitchen din cikin yanga amrah ta ajje masa tray din abincin, “yaya king sannu da hutawa”, kamar wacce tayi magana da dutse yana zaune ko motsawa beyi ba ballantana tasa ran amsawa, zoya na gefensa a haka ammi ta fito da cup din coffee sai faman tiriri yake dayan kuma kayan tea ne a ciki da yaki bornviter , mika wa king coffee din tayi , lumshe mata ida nuwansa yayi , murmushi ta sakar masa kafun ta mikawa zoya tea dinta.beci abincin da aka kawo masa ba sai coffee dinsa da yake sipping a hankali yana gama sha ya mike tare da ce musu “good night “yana gama fada ya kama haryan fita . Cikin daga murya zoya ta soma magana “Laylat saeidat akhi, uhibuk( good night brother, love you)”,girgiza Kai kawai king yayi da barin part din. Sai a sannan yan matan suka tare da cigaba da hirarsu, dummy ce ta kalli amrah , Lalle amrah da raban kin kusa Shan Mari a wajan yaya king, Kinsan halinsa Sarai ba a burgeshi, cikin kasa kasa ihsan tace Garin masoya baya nisa kunsan yadda take mugun sonsa,murmushi amrah ta saki jin abinda ihsan tace “dadi na dake ihsan kin fisu fahimtar abu”ni kadai nasan yadda nake sanshi kumashidin mallakinane, dariyar mugunta firdausi ta saki , cikin kasa kasa da murya tace “mugani a kasa”, hararar ta amrah tayi dan Tasan itama san king take shiyasa basa shiri sosai , duk wannan magan ganun nasu cikin kasa kasa da murya sukai ba mejinsu, dago idanuwanta amrah tayi bata saukesu akan kowa ba sai nan auntyn ta , itama auntyn Tata daga mata hannu tayi alamun jinjina, firdausi ma maida hankalin tayi kan mahaifiyarta lokaci daya suka sakar wa juna murmushi duk wannan abun da suke ba Wanda ya lura dasu . (Uhmmmm 🤭😟) 💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖 Duk karfin izzata (star lady) Gidan aunty (mss Lee) Sarki sameer( xeemat love) Jini daya ( mss bbk) Ya fita zakka (maman sayyid) Comment and share 💖GIDAN AUNTY💖 ( A heart touching love story) By mss Lee 💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖 PAID BOOK BOOK 1 📕 Free page 7 🦋 Not edited Zaune Suke su biyu cikin wata katuwar masarauta me shegen kyau da daukan hankali, duk Wanda yazo wuce wa sai ya duka musu tare da gaishesu, TAHEER ne ya fito cikin wata kofa sanye da wasu kaya na alfarma masu tsananin kyau ba karamun kyau yayi a cikinsu ba , hannunsa dauke da wani siririn maciji fari tass dashi, Daidai inda tahee take ya nufa, zaune take cikin shigar alfarma na kayan sarauta , gefe da gefe masu yi mata fiffi tane ko wananne kawunanshi akasa, tanbarin macijin dake bayanta ya fito radau dashi, murmushi ta sakar masa ganin ya karaso inda take, shima murmushin ya sakar mata tare da Mika mata kyakkyawar farin macijin, mikewa tayi sosai tare da karban macijin, a daidai kan cinyarta ta dora macijin , shima macijin lumshe idanu yayi kamar mai jin bacci, kallan taheer tayi da mamaki dauke a fuskar ta,” kyauta ne na baki yau shekara 300 daidai da haihuwarki, zai debe miki kyewa “cewar taheer, tsananin farin cikine ya bayyana a kan fuskar tahee “ oh my god , nagode SIF” , jinjina mata kai kawai yayi , har ta bude baki zata sake magana sai wasu siraran hawaye suka zubomata”ka tuna lokacin da Nonna ta bani kyautar maciji kamar haka , amma sun kashe mun shi, sun kashe mun nonna , sun kashe mun susan”, shima girgiza mata kanshi ya shiga yi”Lola Raina yana baci duk lokacin da na turo wannan bakar ranar, kamar randa suka rabamu da nonna da susan Muma baza mu kyalesu ba,ga memaw nan ki rikeshi kamar yadda kika saba da susan, shima zaki soshi sosai”, yana gama fadar haka ya bar wajan , murmushin yake ta saki tana hadiye abunda ya tsaya mata a makogaro,kallan memaw din dake kan cin yarta tayi kafun ta kira sunan shi,”memaw”, bude idanuwansa yayi masu kalar baki tare da fara yawo a jikinta yana zagayeta , hakan ba karamin nishadi yasa taba, sai faman yawo suke , saida suka gaji dan kansu sannan suka tsaya har lokacin mucijin be dena yawo a jikinta ba.TAHEE!!TAHEE!!! A firgice ta farka daga baccin da take bakin ta dauke da adduar tashi daga bacci, kallan ta oumma tayi ganin yadda ta jike da zufa duk da kasan cewar akwai dan zafi zafin da ake ,”lapiyan ki kuwa”cewar oumma , saurin girgiza mata kai tahee tayi “ mafarki kawai nayi”, shafa kanta oumma tayi “ki kwantar da hankalinki mafarki ba gaskiya bane sannan ki dunga addua “nanma gyada mata kai kawai tayi,tunda umma ta fita a dakin kuma bata motsa ba mafarkin da tai na yi mata yawo aka“ NONNA,LOLA,SIF,SUSAN,MEMAW!? Sudin su wanene!? Maciji fa !?” Macijin da ta gani a mafarkine yashiga yawo a kwakwalwarta, amma sanin cewa mafarki ba gaskiya bane yasata share zancen tare da mikewa ganin oumma na kokarin shigowa dakin. Bayan sallar azahar kamar yadda suka saba bayan sun kammala ayyukansu, zama sukai suna hira , lokaci zuwa lokaci tahee sai ta dako ta kalli taheer har yanxu mafarkin da tayi yana mata yawo a ka , duk lokacin da tayi tunanin mafarkin sai taji wani abu kamar ya tabata, yanxu ma dago da fuskar ta tayi tana kallan taheer, hararar ta yayi ganin tun dazu sai faman binsa da kallo take kamar wata me aljanu “na canza miki ka manni ne kike faman bina da kallo fisabilillah”,cewar taheer yana hararar ta , murmushin da yafuto da dimples dinta ta saki”gani nai ka kara kyau kamar wani balarabe “ ta karasa maganar tare da kashe masa ido daya,yanxun ma wani hararar ya mata “dadin abun bake kadai ce me kyau ba, da nice mace ma kyan da zanyi sai nasaka maza kuka”, dariya duk suka saki, oumma ta girgiza kanta “Allah ya shiryeku “. ➰➰➰➰➰➰ A gajiye ya dawo gidan bayan mutane uku da yayi wa aiki a asibiti da kansa ,sai faman lumshe ido yake , amma a zahiri bazaka taba tunanin hakan ba , zaka dau ka yanayinsa ne haka , shaf shaf yayi wanka cikin armani white colour, sosai kayan sukai masa kyau , a maimakon gyara gashin da ya saba yan tajeshi kawai yayi ya zubo masa har bayansa, sosai yayi kyau a cikin shigarsa, wayoyinsa kawai ya dauka tare da nufar part din ammi, yau kwata kwata be sata a idanunsa ba amma a zahiri fuskarsa a hade take ba ko alamun yasan wani abu me kama da murmushi. Yana shiga part din ya tarar da su kowa da Riga da Wando sai faman rawa suke, amrah ce me koya musu yadda zasuyi step din rawar,kwata kwata basusan da shigowarsa ba , hatta kamshin turarensa da sukaji basu kawo komai a ransuba, dan kusan kullum da kamshin a cikin falon ammi. Folding din hannunsa yayi a kirji yana bin ko wannansu da kallo daya bayan daya ransa ba karamun baci yayi ba musamman irin shigarsu ko dan kwali babu, be tankamusu ba duk da yadda kan nasa ke Sara masa , sexy eyes dinsa dasuka fara canza kala daga launin fari zuwa ja ya zubamusu, ihsan ce ta fito sanye da hijab a jikinta hannunta dauke da cup sai faman tiriri yake, kallan su amrah tayi tare da girgiza kanta , “kunsan dai yaya king ya hana wannan raye rayen ko, Allah Inya dawo sai na fadamasa dan bazaku jajamun ba”, hararar ta summy tayi “ sannu kasa yanxun ma zaki iyazuwa, matsoraciyar banza kamar da gasken iya zuwa zakiyi”, girgiza kai firdausi tayi “Aah sumy Wana irin taje ta fada kinsan dai wallahi yaya king ya Kamamu ba karamun wuya zamusha ba musan man dressing dinmu, kuma kusan bama sawa sai in bayanan “, siririn tsaki amrah taja “matsalata da ku kun fiya tsoro wallahi, kafun ya dawo ba mun gama ba , ai baze san munyi ba , yanxu fa zamu gama step din rawar kafin ammi ta dawo”. Dukkansu yanajin abunda suke fadi , duk abunda suke yana ganinsu kwata kwata basu hankalta dashi ba, amrah ce ta kunna musu wata wakar, ta juya kenan a cikin salon rawar idanuwanta suka sauka a kanshi, sosai ta firgita , bakinta ne ya fara rawa kwata kwata ta rasa me zatace, kallanta summy tayi “ke kuma lapiya jikinki yake rawa”, girgiza mata kai kawai amrah take tama kasa magana ganin irin kallan tsanan da yake jifanta dashi “watan cin ubankune yayi”a zahiri kuwa yana yadda yake ko a fuskarsa bazaka gane yanayinsa ba duk da tsananin gajiyar dayayi. Ganin sai faman kallan waje taya amrah take jikinta na rasa yasa duk juyawa zuwa direction din,”Innalillahi wa’inna’ilaihi rajiun, shikenan mun kade har gay yan mu gashi ammi batanan “kowa da abunda yake sakawa a zuciyarsa , iya firgita sun firgita musamman ganin yadda launin idanunsa ya koma ,firdausi har da faduwa kasa tsabar rudewa,duk zubewa sukai akan gwiwowinsu ko waccen su sai matsar kwalla take,sosai suka rude musamman ganin irin kallan da yake bin kowannansu dashi, a hankali ya taka kafarsa tare da nufar sofa din dake left side dinsu , kwallar bakin ciki ihsan ta share dan duk su suka ja mata, ta ja musu Allah ya isa ba a dadi cikin zuciyarta, ba wacce ya kalla a cikin su sai ma wayar hannunsa da yake latsawa, cikin rawar murya me san sakin kuka ihsan tahe hannayanta “wallahi yaya zanyi bayani”, be Motsa da ga yanayin da yake ba balle su sa ran ze amsa mata, Kuka Kawai ihsan ta saki tana toshe bakinta karta kuma yin wani lefin, su amrah kuwa kowa sai faman zare ido yake fatansu Allah yasa be ji abunda suke tattaunawa. Kamar daga sama sukaji saukar maganarsa “ coffee “ da Sauri amrah ta tashi duk da acikin yanayin tsoran da take, dan iskan kallan da yayi mata ne yasa ba shiri ta koma tana zare idanu, ganin hakan yasa atsorace ihsan ta mike ganin be mata magana ba yasa ta nufar kitchen din cikin sauri, sai faman ajiyar zuciya take , duk tabi ta rikice ta rasa yadda zata hada masa coffee din , cikin sauri Sauri ta dakko wayanta dake aljihun Wandanta. Yanda ake yin coffee din tayi searching, cikin rudewa ta gama fito da abunda zata hada masa coffee din jikinta sai faman rawa yake . Cikin dan karamin tray ta fito da coffee din kusan na uku kenan tanayi kafun tayi wannan din, ganin su amrah na frog jump ne yasa kafarta rawa idanuwanta harsun cika da kwalla, coffee din ta ajiye masa tana komarin fara frog jump din ne abazata taji saukar muryarsa “ Leave” , nannauyar ajiyar zuciya ta dauke da harshi saida yajita “ nagode yaya king, na….” Hannunsa kawai ya daga mata ,cikin sauri ta bar wajan cikin gudu gudu, tunda Allah ya kubutar da ita. Sosai suke frog jump ko wacce fuskarta jaga jaga da majina , ga hawayen da suke yi, da zaran sunji kuka zai kwace musu zasuyi saurin toshe bakinsu gudun wani punishment’s din. Duk fadin falon ammi haka zuke zagayeshi ko wacce ta fita daga hayyacinta ba damar yin kuka a fili. Yana zaune sai faman operating wayar hannunsa yake se yanxune ya dauki coffe din da aka hada masa” kurba daya yayi amsa ya ajjesa. “Yaya dan girman Allah da manzan sa kayi hakuri”firdausi ce tayi maganar hawaye sai bin fuskarta yake, lumshe gajiyayyun idanuwansa yayi, tariga ta hadasa da abunda baze iya musu akai ba, “God save you”yafada cikin zuciyarsa “Leave “, baki summy ta bude Baki da niyar yin magana amma ya dakatar dasu ta hanyar dafe kansa , sun gane me yake nufi hakan yasa a guje ko waccen su ta bar part din Daidai lokacin da ammi ke shigowa, da kallo tabisu ganin babu Wanda ya kula da ita kafun ta karasa shiga falon. ➰➰➰➰➰➰ Karfe uku na dare ko ina yayi shiru kasan cewar ko wana bawa yana wutawa a irin wannan lokacin, wani macijine fari tas dashi ya fito cikin wani rani tare da kwanciya bayan tahee,cikin mafarkin da take tafara lalube lalube har hannun ta ya Kai…… Manage plx🥹 💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖 DUK KARFIN IZZATA (Star lady) GIDAN AUNTY( mss Lee) TAFITA ZAKKA ( maman sayyid ) JINI DAYA ( mrs bbk ) SARKI SAMEER (xeenat love ) 💖GIDAN AUNTY💖 ( A heart touching love story) By mss Lee 💖 💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖 PAID BOOK BOOK 1📕 Free page 8 🦋 Karfe uku na dare ko ina yayi shiru kasan cewar ko wana bawa yana wutawa a irin wannan lokacin , wani macijine tass dashi ya fito cikin wani rami tare da kwanciya a bayan tahee ,cikin mafarkin da take ta fara lalube lalube, har hannunta ya kai kan wannan siririn macijin, jin abu me laushi da san tsi besa ta bude idanuwan ba , sai faman shafashi ,a firgice ta farka daga baccin da take “mewam “ta furta cikin firgici, juyawar da zataine idanuwanta Suka sauka kan macijin , azabure ta Kwala ihu”oumma, oumma” ta fada a tsorace ganin duk ihun da tayi oumma bata motsaba, ja da baya ta fara ganin macijin na kokarin biyotan itama ,” Innalillahi me nayi maka kake biyoni, oumma ki temakamun”, duk ta firgice ganin macijin yayi Kuri da ido yana kallanta, ga oumma da ko motsawa batayi ba,kara nufota macijin yayi ta fara girgiza kai “ Dan Allah ba danni ba kayi hakuri , ni bansan me nayi maka kake bina ba, kayi hakuri dan Allah “ ta karasa fada tana fashewa da kuka, kamar daga sama taji saukar yar muryan dan yaro” ni ba abunda zan miki , kawai inaso na zauna wajanki “, waro manyan idanuwanta tayi kamar zasu fado kasa jin maciji na magana abunda bata taba jiba a rayuwarta,mintsinin kanta tayi dan tabbatarwa”kodai mafarki nake”, ta fara tanbayar zuciyarta,”Aah ba mafarki kikeba “ta kara jin saukan muryarsa , kara fashewa da kuka tayi fuskarta duk ta hada zufar wahala “ na rokeka koma wanene kai kayi hakuri ka kyaleni, ni ban muku komai ba”, be ce mata komai saima biyota da ya fara cikin tafiyar macijar, itama baya ta faraja tana girgiza masa , wani dan kwanan da ta gani tayi saurin dauka da niyar kwala masa , kamar wacce ta tuna wani abu sai ta tsaya tana kallansa”Mewam”a hankali ta fadi sunan, cikin sauri majicin ya karasa jikinta yana zagayeta , itama sai faman dariya take , duk wannan abun ba wanda ya farka daga baccinsa duk da tsananin ihun da ta kwala. Yau sun makara dukansu basu tashi sallar asuba da wuri ba, suna idar da sallah aikin gidan suka fara kafun mutanan gidan su fito,wanke wanke oumma ta fara su tahee na ebo mata ruwa , suna kammalawa tahee ta share tsakar gidan , sosia suka gyara gidan ganin yadda yayi Datti sosai kamar ba a gyarashi , Daidai lokacin da mutanan gidan ke futowa, daya daga cikin yayan gidan da suka zone tabi su da kallan kaskanci,”ke” ta fada tana nuna tahee , banza tahee tayi da ita kamar batasan da itaba,”bajini ina kirankiba ko sai na zageki zaki gane”, kallan tahee oumma tayi ba magana ake miki ba,dan karamun bakinta ta tura tana bin HAJJO da kallo, dan siririn tsaki hajjo ta saki”Aushe duk karyar banzace, ki jira ynxun ki mun wanki dan ba Hutu kuka zoyi mana gida ba”tana gama fadar hakan rai wuce warta, kande ma dake daki wuff ta fito”Nima yanxu zan gito miki da wankina “,da daidai da daidai mutanan gidan suka fara fitowa, kaka ta bawa da ke faman amma je ta karaso wajan , ke kuma uban me kike mana anan wajan ,muryar su hajjo taji”inna aiki muka sata , Kema in kina da wanki ki kawo tayi miki”,kaka ta bawace ta amsa mata “Aini baba rasa aikin sawa, yo inba aiki ba Menene anfanin katuwar budurwa haka har yanxu batai aureba”, da Sauri Dije ta fito hannun ta rike da mafici “ai inna kwara kiyi mata aure,ki duba ki gani ko bintalo da take 13 dududu saura mako uku bikinta”, dago da idanuwanta tahee tayi tana bin Dije da kallo sai kuma tayi saurin maidashi kan oumma da ta sun kuyar da Kai, zabura tayi da jin zancen inna” kuma kin kawo shawara me kyau dije, daman tanimu me guga ya dade yana santa,ubanta ne ya Hana yanxu kuma kin ga bayanan in yaso sai a hada Dana bintalo “, sosai mutanan gidan suka kwashe da dariya dan Sarai sunsan tahimu babban dan iskane a Garin ga shaye shaye da yake ,wuce wa oumma tayi daki batare da tace komai ba, taheer na tsaye duk ya hade ransa, dije kawai yake kalla yana girgiza kansa,kwallace ta tararwa tahee” ni zasuyiwa Auran dole , Auran ma da dan iska dan shaye shaye “ kawai sai ta fashe da kuka yan gidan kuwa sai faman shewa suke, tare da watsewa bayan uban tulun wankin da suka ajje mata, TAHEER ne yashiga lallashinta har tayi shiru sannan ya taimaka mata sukai wankin tare , duk jikinsu yayi sanyi musamman tahee dakanta ya fara ciwo. Suna gama wankin daki suka koma, oumma suka tarar tana gyara kayan sawansu”oumma “ tahee ta fada hawaye na kara zubomata, dakatar da ita oumma tayi tana daga mata hannu”bana san jin komai”tana gama fada ta dakko wa taheer ya mutsats tsiyar dariya biyar, ta lissa fa masa abunda zai siyo mata , karba yayi tare da fita daga dakin, itama tahee waje ta samu tare da juyawa tayi kwanciyarta, bunta da kallo oumma tayi tana kokarin share kwallar da take ta faman dannewa” ya Allah kai kadaine me iyawa ka kawo mana mafita “ ta fada a zuciyarta,itama taheen duk da yadda oumma ta share zancen tasan abun yana damun ta ne ba yadda zatayi ne , har taheer ya dawo daga aiken ko wannansu yayi jigum jigum, taliyar da oumma tasa ya siyo ma kasa cinta sukai saida oumma ta hade musu rai sannan suka tsast tsakura. ➰➰➰➰➰➰➰➰ Yau tun safe ba Wanda ya ganshi , hatta zaki bayan sun dawo daga masallaci be kara sanyashi acikin idanuwansa ba. Kwance yake kan kantamemen ‘kayataccen gadonsa, idanuwansa lumshe suke kamar mai yin bacci amma a zahiri ba baccin yake yiba, tsananin yanda kansa ke saramasa yasashi lumshe idanuwan, yunwa yake ji amma ba ze iya cewa a kawo masa a binci ba, a hankali ya bude kyawawan idanuwansa da sukayi matukar canza kala daga launin fari zuwa launin ja ja,idanuwansa ya maida kan agogon dakin kafun ya kara lumshe idanuwansa ya mike, sanye yake cikin wasu white kaya Riga da wando, wandon iya kwiwa , sosai kakkarfar jikinsa ya fito, inda coffee maker dinsa yake ya nufa, cikin kankanin lokaci ya hada coffee din , yana siffing a hankali bayan ya kammala Sha kai tsaye wani dan buttun ya dannan, take wata kofa dake jikin bango budewa da kanta, babban wajen Shaka tawa ne a wajan me girman gaske sosai , iya haduwa wajan ya haduwa , daga gefe daya wasu set din kujerane kawai a wajan sai wasu korayen flowers dasukayi wa wajan kawanya, sosai wajan ya hadu iya haduwa, inda take a cikin kejinta ya nufa,tana ganinsa ta fara bude fuka fikinta cikin muryan aku ta fara”gashinan yazo, gashinan yazo,king yajo “dan sakin fuskarsa da take a hade yayi tare da bude mata cage din , a guje kuwa ta fito tana zagayeshi kafun ta sauka a kan kafadunsa, shafa kanta yayi kadan kafun ya bude bakinsa” how’re you”, abun mamaki se ga tanan ta amsa masa, be kara cewa komai ba ya fito daga wajan .tabbas yasani a part from his family babu me damuwa dashi kamar zaki, wayar hannun sa ya dauka tare da danna wani number , seconds kadan aka amsa wayar sai da ya mula dan kansa sannan yasa wayan a kunnensa, sallamar zakice ta daki kunnensa, kamar baze ce komai sai kuma ya amsa, zaki zai kara magana yaji saukar muryar boss”am fine, you should rest too” yana gama fadar hakan ya kashe wayarsa. ***************************** ***************************** Zaune su amrah suke cikin wani kayataccen garden din da ya gaji da hanuwa, komai na wajan ya hadu sosai ba kadan ba ,ga sanyayyar iskar dake kadawa me shegen kamshi, sosai garden din ya hadu , amrah da ihsan suna zaune kan lilo be hade da flower gwanin ban sha’awa, sumayya da firdausi kuma suna zaune kan wasu kujeru, daga gefe daya yan aiki ne ke fan yi musu hidima, sosai suka cika gabansu da abubuwan ci kafun cikin isgilanci amrah tace musu subarwajan, suna barin wajan kuwa ihsan ta fara musu dariya, sosai take dariya musu tana binsu da kallo, dukan su sunsan dariyan me take shiysa suke binta da harara, sai data gama sannan ta kallesu “ wallahi yaya king halinsa saishi, ni Allah ne ya kubutar dani ,saura kadan na saki fitsari wallahi musamman yadda naga idanuwansa “, dukkansu dariya suka saki ,sumayyace ta kalleta “ Aini baku sani ba wallahi suma ne kawai banyi ba , dan ba karamun tsorata nayi da yanayinsa ba,zuciya tace kawai ke bum bum, amma duk da haka munci uban mu, Allah ne ya temakemu kuka tsaya a jan kunne be kada da tsitstsinka mana mariba”, yanxu ma duk dariya Suka saki tuno yadda yasasu tsallan kwani, ya tsine fuska Amrah tayi” ni kuma kunga ko a jikina dan my king ya samu wannan punishment din a Hakan ma ai na kalleshi da kyau “ dogon tsaki firdausi taja “shiyasa naga kin fi kowa rudewa ai , se shegen cika baki amma da kin gansa zaki fara ma kyarkyata” tana gama fadan haka ta tashi ta bar wajan, da harara Amrah ta bita" inma bakin cikin zan aura yaya king kike sai dai ki gama dan shi din nawa ne ni kadai”, babu Wanda ya Tanka mata tsakanin ihsan da sumayya sai binsu da kallo da sukai , inda sabo sun saba fada akan yaya king , kowa tace na tane sudai nasu ido kawai , daga nan suka canza hirar zuwa wata da ban suna yi suna dariya da Shan kayan da aka kawo musu har yamma suna wajan kafun su tashi kowa yayi part Dinsu. ➰➰➰➰➰➰➰➰➰➰ BUNKURE Dije ce rike da buta a hannu, yayinda take sanye da daurin kirji, daya daga cikin abubuwan da aka cika da ruwa ta nufa ganin ko wannansu cike taf da ruwa yasa cikin mugunta ta waiga ganin babu kowa a wajan duk sun shiga bacci yasa ta dauki a bu ta fasa daya daga cikin randar, take a Wajan ruwan ciki ya zube daman tafi ko wacce girma a ciki, d’ayar ta nufa da niyar fasa ta itama taji saukan Mari a fuskarta, ihu ta saka tare da sakin butar hannunta,wani kwakkwaran mari aka kuma yi mata , dafe kumatun nata tayi tana fashewa kuka, juya wa tayi dan ganin wanda ya marenta amma wayan bata ga kowa ba , a tsorace ta juya sai faman zare ido take , a hankali ta daga kafarta da niyar guduwa, sai Jinta tayi timmmmmmm a kasa ta fadi, wani a zababban kuka ta saki “ ku kuke ganin mu bamu muke ganinku ba , dan girman Allah kuyi hakuri”sai kawai ta kara fashe wa da kuka, jin shiru na wasu yan mintunan yasa ta mikewa da niyar guduwa , wasu kwararan maruka aka kara sakar maka , take a wajan ta suma fitsari na bi ta jikinta. ****** 💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖 DUK KARFIN IZZATA( star lady ) GIDAN AUNTY( mss Lee ) SARKI SAMEER( xeenat love) YA FITA ZAKKA (maman sayyid) JINI DAYA ( mss Bbk) ‎Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/GOZ7a2miBjZ4vUjRXdRdrA 💖💖GIDAN AUNTY 💖💖 ( A heart touching love story) By mss Lee 💖 💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖 PAID BOOK MAI SON AI MAI TALLAN KAYANSA YAMUN MAGANA TA WANNAN NUMBER 07041879581 BOOK 1 📕 Free page 9 🦋 ******** Suna zaune tun safe basu fito ba, oumma ta dafa musu ragowar taliyar jiya sukaji ana faman buga kofar da karfi kamar za a karya,” maryam bazaku fito bane kuna ji ina magana”, tsaya wa duk sukai daga cin abincin da suke jin muryar kaka tabawa, cikin damuwa oumma ta fito bayan ta yiwa su tahee kashedin karsu fito, a tsats tsaye tagansu ko wannan su , kaka ta bawa sai faman zaginsu take , “inna ina kwana”, bata bari ta karasa ba kaka ta bawa ta katseta“ban kwana ba , nace miki ban kwana ba , wallahi maryam kiji tsoran Allah , yanxu daman bakin cikin nace zan aurawa waccan yar taki me kama da aljanu tanimu shine zaku bi dare keda ban ka daddun ‘ya’yan ki ku fasa mun randa, kunsan tsawan shekarun randa ta da zaku tashi ku fasa mun” bata bari oumma tayi magana ba ta dora “ toh wallahi bari kiji,ko kina so ko ba kyaso aure kamar ya d’aurune dan ba fashi, itama munafukan da suka ‘ki futowa dani suke magana, ku fito ka aiki can kutashi kuyi, uban me ya hanaku yin aiki ma yau” sun kuyar da Kai oumma tayi kafun ta fara bata hakuri”kiyi hakuri inna, bamusan Wanda ya fasa miki randa ba” bata karasa ba Dije da bakin ta ya kun bura cikin haushi ta fara”toh karya za ai muku , in baku ba uwan wane ze fasa mata randa, yan bakinciki , shiyasa nace muku zuwan mutanen nan ba alkairi bane “ta kara sa da juyawa tana kallan mutanan gidan. “Hindu ce ta kalli inna ta bawa “ inna shiyasa ai jiya nace kawai kisa tanimu ya turo ba sai an jira bintalo ba, dan wannan bakin halin nasu ma waya sani ko sunbi wajan boka “ ta karasa tana hararar oumma da ta sun kuyar da Kai har ynxu fuskarta tana a yadda take. A daki kuwa jin yadda suke zagin oumman nasu yasa tahee fashe wa da kuka , sosai take kukan bakin ciki akan abunda suke musu, ita ba Auran ne ya dameta ba suje su aura mata duk Wanda suka ga dama amma bazata kuma lamunta da cin mutuncin da suke wa oumma ba, sosai shima taheer ransa ya baci. Kara fashewa da kuka tahee tayi jin kaka tabawa nacewa auwalu ya kirawo mata tanimu asa musu rana , sosai sukai musu tatas ko hakurin da oumma take bayarwa basu saurara ba suka bar wajan , Dije sai faman d’ingishi take dan tayi alwashin sai ta ruguza farin cikin su , dan tasan bokan da oumma ta ke bine yasa ayi mata haka (nace uhmmmmm Dije jikin ki be gaya miki ba kenan🤭). Farin macijin dake la’be tun dasu ya kurawa tahee ido ganin yadda take kuka shima sai launin idanuwansa suka canza daga baki zuwa ja ,sai ya silale ya fita baki d’aya daga dakin ganin oumma na kokarin shigowa. ➰➰➰➰➰➰➰➰ DADA zaune take cikin wasu lallausan kujera jikinta sanye da wasu fararan cotton din kaya , sosai kayan sukaiwa jikin tsufanta kyau,a center din gabanta wani dan madaidaicin glass jug ne cike da fura, sai faman tashi kamshin furar da yaji damu yake, kallan Aunty dake gefe a zauna tayi tare da gyara zamanta , inajinki Amina , cikin inda inda Hajiya Amina ta soma magana “ wai dada naga yan matan gidan duk sun tasa ne , shiyasa nake ganin me zai hana ayi Auran dangi, ko King ne a aura amsa amrah, naga kamar suna kyaunar junansu”, sosai dada ta zuba mata idanuwa kafun ta soma magana “amma dai haroon kike magana akai ko, ke yanxu Amina bazaki dena wannan halin naki ba , shi sadaukin Yaushe kike ganinsa har yace miki suna Kaunar juna”, kin kina ta soma tama kasa magana “ saurin da katar da ita dada tayi”bana san irin haka , inda shi sadaukin ne yace yanasan yar taki da babu abunda zai Hana Aki aura masa , amma tunda be fada ba kar nasake Jin wannan batu, zaki iya tafiya”, sosai ran hajiya Amina ya baci da magan maganun dada , dan tabbas tasan da hajiya kilishi ce ko uwar king din da babu abunda zai hana tayi naam da zancen, daman ta dad’e da sanin cewa dada ba kaunarsu take ba , amma fili sai ta saki murmushin nan nata “tuba nake dada , ban fada da wata manufa ba, na barki lapiya”, itama dadan jinjina mata kai tayi “akiyaye “,itama aunty mikewa tayi tana fadin “insha Allahu”, tare da kama hanyar fita daga falon, bin bayanta da kallo dada tayi kafun ta girgiza kanta tacigaba da sabgar gabanta. Kamshin da batayi tsammani bane ya cika mata hanci ,juyowa dada tayi domin tabbatarwa, shidin ne tsaye , fuskarsa kwata kwata ba annuri akai ,kallo daya dada tayi masa ta dauke kanta ,cikin kasan makoshi kamar bazai yi magana ba sai kuma ya bude bakinsa “Assalamu alaikum” dabadan hankalin ta na kansa ba da babu abunda zaisa taji sallamar tasa” Wa’alaykumussalm “ tabashi amsa itama ,ta kowa yayi ahankali tare da karaso wa inda take, a maimakon ya zauna a kujerar kusa da ita sai ya zauna akan kujerar da take , “barka da yamma dada”, ta bile baki dada tayi “sai yanxu ka bayyana kenan, Kai yanxu saraki da ban nemekaba da bazakazo ba kenan,kadai ji tsoran Allah “,amai makon ya bata amsa sai ya kwantar da kasan a kafadunta tare da dan kwa’be fuskarsa kadan,ture kafadarsa dada tayi tare da mikewa , cikin masifa ta soma magana “ kabari in kayi aure sai kawi wa matar ka haka , bani ba salan zawaran da sukeso su aureni su gudu sabida karyayyan kashi”,dan murmushi leben baki ya saki da ko dada dake kusa da shi bazata gane hakan ba, sosai yayi musamman da pink lips dinsa ya kara turuwa,harara dada ta sakar masa tare da ta’be baki “kajirani” tana gama fada ta mike da nufar kitchen dinta, bata dade ba ta fito dauke da wani dan karamun tray, cikin yanayinsa na rashin garaje ya mike tare da amsar dan karamin tray din da ta fito dashi, inda suke zaune suka koma sai a sannan dada ta karbi tray din, lafiyayyar tuwo ne da miyar kubewa d’anya da taji nama da Ganda , sai kifin da aka sa masa, sosai kamshin abincin yayi masa dadi amma sai ya dan kawar da kansa gefe, dungure masa kai dada tayi” toh d’an neman magana ni na yi da kaina”, sai a sannan ya jiyo fuska a sake amma kwata kwata babu murmushi akai,karban abinci yayi tare da fara ci bayan yayi Bismillah, sosai yaci tuwan dan ya dade beci abinci da yawa ba,tunda ya fara cin abincin dada take binsa da kallo, Itade tanasan jikan nan nata, maganar hajiya Amina ce ta fado mata arai, kamar zatai masa magana sai kuma ta fasa, tasan halinsa yanxu ze iya tsanar yarinyar ko yaje ya ‘bab’bala yar mutane. Ganin yadda take kallansa ne yasashi dage mata gira , waro idanuwanta dada tayi “yanxu ni sadauki kake dage wa gira daya , sai kace yar iska, toh maza maza tashi ka bar part dinnan, ga furar ka nan ma, ka ‘bacemun da gani” sallamar zoya ce ya katse dada , da sauri zoya ta karaso wajan king “akhi “,lumshe mata ido yayi tare da budewa”na’am ukhti”, dariya sosai ta saki jin ya kira ta da ukhti “akhii duk yau ban gankaba fa” ta fada tana marairaice fuska,kamar bashi ba , shima ya dan kwaikwayi muryarta “Nima duk yau ban ganki ba ukhti”, binsu da kallo kawai dada tayi tana tabe baki” da yake kin ga ubanki shine kika manta inda kikazo, toh ku tattara kubar min daki”marairaice fuska zoya tayi “Haba dadar mu”yanxun ma harararsu tayi “Oho dai “, king ne ce mata komai ba sai mikewa da sukai tare da daukan furarsu “sai mun kara dawowa dada”,ka tsesu dada tayi “bana bukata”, shima king din tabe baki kawai yayi suka bar part din, da kallo dada ta bisu tana sakin murmushi” kaidai ba me iya maka , zanga macen da zata iya hakuri da wannan baud’ad’d’an halin naka “. ➰➰➰➰➰➰➰➰➰➰ BUNKURE Kai tsaye macijin bai tsaya a ko ina ba sai cikin ban dakin gidan, Daidai kaka tabawa tana kama ruwa jitai kamar abu ya hau kanta, sai ta taba Wajan taji ba komai , sharewa tayi tare da cigaba da abunda take, dan karamin abu takumaji kamar yana yawo a jikinta, a sukwane tayi mike tana karka da jikinta, abun be dena yawo a jikinta ba sai ma kara yawa da yayi, ihu dada ta saki da nufar hanyar fita daga bayin, dan karamun halittar da ta ganin a kofar bayin yasata komawa ciki da sauri tana zare ido”nashiga uku” jitai wasu murya yan kanana suma suna cewa “na shiga uku”, amaimakon tayi salati sai ta fara “laha’ila, ni tabawa na shiga uku me nake gani” ta karasa maganar tana fashewa da kuka duk ta hada uban gumi, wata muryar daban sa’banin ta dazu itama” laha’ila ni tabawa na shiga uku ne nake gani” aka karasa maganar da fashewa da dariya, wani kukan kaka ta bawa tasaki ganin yadda halittar ta nufota Gadan gadan yasa kaka ta bawa sumewa take a wajan .macijin nanne ya bayyana tare da karasa wa inda take Daidai bakinta ya buga mata jelarsa, take a wajan bakin kaka tabawa ya kunbura, batt ya bace shima da barin ban dakin. Su tahee duk sun fito suna aikin su, yau kwata kwata ba annuri akan fuskokinsu, ruwa suka fara d’ebowa kafaun su fara aikin gidan , tana cikin aikin taji zuciyarta ta fara washewa daga cunkushewar da tayi a kirjinta, shima taheer hakan yaji, lokaci d’aya suka sake tare da cigaba da ayyukansu yadda suka saba, ganin haka yasa itama oumma zuciyarta yin sanyi ganin duk sun saki ransu, kusan awa daya suna aiki a tsakar gidan duk mutanan gidan sunshige ciki sabida ranar da ake me zafin gaske, ganin yadda ake kokarin bude bandaki yasa duk zubawa kofar ido, da kyar kaka ta bawa ta bude kofar sabida yadda bakinta ya kunbura sai faman din gishi take, binsu tayi da kallo ganin yadda suka tsare da idanuwa, bakin da ya kara kunbura ta bude daniyar zaginsu, zugin da taji ne yasa ra hadiye maganar tana matsar kwalla da bin gefensu ta wuce. Sosai dariya take so ta kwace musu ganin yadda ta wuce tana tsamin kashi, tana shigewa daki kuwa suka fara dariyarsu, TAHEER harda faduwa sabida dariya, itama oumman murmushi ta saki ganin yadda kaka ta bawa ta dawo kamar tsohuwar mahaukaciya, sosai suke dariyarsu, sai da suka gama dan kamsu sannan suka cigaba da aikinsu. **DIJE zaune take cikin dakinta da ya cika da uban shirgi ,sai faman tashin wari yake da d’oyi , ko ina na dakin yayi kaca kaca dashi ita kadai ce a dakin sai karamar nokia dinta dake hannunta , ta dad’e tana waya da kawarta jimmala kafun ta kashe tana dariyar mugunta, kamar jira ake kuwa tana kashe wayan aka tsinka mata mari, take a wajan tayi filinki sabida azabar marin da taji, bata dawo hayyacinta ba ta kara jin saukar wani marin a fuskar ta, kuka ta fashe da shi, sai faman waige waige take, ganin ba kowa a dakin yasa kudawa zuwan mata take a wajan, sosai ta kuma rud’ewa jin abu na yawo a jikinta,duk inda takai da tabawa sai taji ba awajan abun yake ba, sosai Dije ta rude sai faman marin kanta da take , tana marin tana kuka, ga majinan da ya cika fuskarta , sai faman tashin tsamin wari take… Comment and share 💖 THE TALENT TROUPE WRITERS 💖 💖LITTATTAFAN SUNE KAMAR HAKA💖 👇 💖DUK KARFIN IZZATA (star lady)💖 💖GIDAN AUNTY (mss Lee )💖 💖JINI DAYA ( MRS bbk )💖 💖YA FITA ZAKKA(maman sayyid)💖 💖SARKI SAMEER (xeenat love)💖 Mss LEE💖✍️ ‎Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/GOZ7a2miBjZ4vUjRXdRdrA 💖💖GIDAN AUNTY💖💖 ( A heart touching love story) Story &written By Mss Lee💖 💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖 PAID BOOK MAISAN AYI MASA TALLAN KAYANSA YAMUN MAGANA TA WANNAN NUMBER 07041879581 BOOK 1 📕 Free page 10 🦋 Shigowar bintalo dakin kamar wacce aka jefo ta ko sallama babu, yasa dije kamewa, komai sai ya tsaya mata, kallan kanta da dungayi ganin duk ta ya mutsa jikinta, kallan ta bintalo tayi rai a bace tana toshe hanci “Haba Dije , kazantar taki har takai kiyi kashi a jikinki, gaskiya kina bada ni , ji beki katuwar kawai sai wari kike faman yi , ga kashin ki me shegen d’oyi, ta karasa da hararanta. Dije ce ta soma magana “Haba bintalo , Kema kinsan haka kawai bazanyi kashi a jiki ba , lalurace ta sameni , ni kaina bansan ya akai hakan ta faru ba”, ta kare zance da zunbula hijabi, gudun kar yan gidan su ganta, tayi sauri tashige bayi bayan dan ruwan da ta dauka a buta. Su tahee ma ransu fess suka koma daki, bayan sun gama aikin su , haka suka yini a daki, lokaci zuwa lokacin tunanin dan iskan da akace za a aura mata yana fado mata arai. ******* A kwana a tashi ba wuya wajan Allah SWT, yau watan su tahee 1 da ‘yan kwanaki a bunkure, abubuwa da dama ya faru ciki harda maganar Auran tahee da tanimu da tayi mugun tsana. A yan kwanakinan ba karamun wuya suke shaba wajan mutanan gidan, musamman kaka tabawa da dije datayi mugun tsanar su, kullum da kalar ukubar da zasuyi musu, abu daya ne ke kwatarsu , duk lokacin da kaka ta bawa ta wahalar da su ranar bata iya baccin arziki sai safiya , a lokacin su tahee ke samun damar hutawa . Taheer ma yanxu ya koyi faci, Inya futa tun safe bashi ke dawowa ba sai 6 na yamma, a gida kuwa daga oumma sai tahee, yanxu ma kwance take kan cinyar oumma tana taje mata uban tilin gashin kanta da ya zubo har gadan bayanta da cikon da yake dashi, “oumma”cewar tahee,”naam aunty tahee”oumma ta amsa mata cikin zolaya , dariya tahee ta saka, “Allah oumma ni banasan wannan gashin kan nawa wani lokuta, kallifa ko tajeshi bana iyayi da kyau, “aikinsan hanyar iliya me aski, sai kije ya aske miki”, turo baki kawai tahee tayi dan tasan magana oumma ta fada mata. Suna zaune sukaji an banko kofar dakin , duk kallan kofar sukai lokaci daya , bintalo dake tsaye se faman cika take ta kalli tahee ba ko sallama , “toh matar mashayi sai kije angwan naki yazo”, tana gama fadar hakan ta banko musu kofa. Tsaki tahee taja tana kokarin kontawa oumma ta dakatar da ita “tashi kije”bata ce wa oumma komai ba ta zura hijabinta tare da ficewa waje. A tsaye ta ganshi cikin wasu yan iskan Riga da wando, sai faman tashin warin giya yake, saurin toshe hanci tahee tayi jin zata yi amai, ga bakikkirin bakar fuskarsa sai faman naso nake , cikin Maye ya zuba wa tahee jajan idanuwansa” ke dan uwarki , shine zan dunga kiranki kina kin zuwa, ke gaki yar iska ko” ya karasa yana tangal tangal kamar ze fado mata, matsala tahee tayi baya tana binsa n da kallan tsana “inka gama zan wuce dan banda lokacin dan iska”, wayo idanuwansa yayi cikin maye yana kifkifta kana nun inaduwansa” ke, ni kike cewa dan iska dan uwarki, toh bari na nuna miki iskanci, kafun na bada sadaki zan d’anaki nasan zakiyi ruwa” ya karasa tare da daga hannunsa zai tabata, saukar marin da yaji a fuskarsa ne yasa shi tangal tangal zai fadi, ganin yana ganin biyu biyu ne yasashi kara ware mummunar fuskarsa “ kutumar ubancan , ya na fara ganin garin yana juyawa ko an fara hazo ne “be kammala maganar tasaba tahee da idanuwanta suka juye ta kara tsinka masa mari” saurin dafe fuskar tasa yayi har yanxu bakin nashi be mutu ba” auzubillahi, ko an fara tafiya lahira ne ban sani ba” saukar marin da yaki a fuskarsa ne ya sashi zabura da fita “shikenan a fara sha hada , an fara mutuwa “, sai da ya bace wa ganin ta sannan idanuwan ta suka dawo Daidai ganin ba kowa a wajan yasata dage kafada da komawa cikin gida . Koda ta kowa cikin gidan oumma bata ce mata komai ma , itama tahee batace komai ba sai hirarsu da suka cigaba . ➰➰➰➰➰➰➰➰➰ LAGOS Tun d’azu ta kasa zama sai faman zirga zirga take , Aunty kawai take jira ta shigo, ta dade a tsaye kafun hajiya Amina ta shigo falon duk rai a bace , kallanta amrah tayi kafun ta sauke a jiyar zuciya, “Anda ce aunty!?” Ta tanbayeta da sigar tanbaya , bata kulataba sai da ta samu waje ta zauna “ amrah ban taba sanin matar nan makira bace sai yau, wai harni tsohuwar matar nan zata karya ta”, tass ta bawa amrah labarin abunda ya faru ta dora da cewa” wai ni amrah kina shafa kwallin tayar masa da sha’awan da Malam ya baki “ cikin kun burin fuska Amrah ta amsa mata “ ina shafawa aunty, gasky ya kamata a koma wajan Malamin dan bazan taba yadda wata ta same shi in ba ni ba, ni ko baze aureni ba inaso mujiyar da juna dan inasan na d’ad’and’ana zumarsa kona kashe sha’awar dake tasomun”jin jina mata kai kawai hajiya Amina tayi, itama amrah bata kuma cewa komai ba ta shige daki, da kallo aunty Amina ta bita “ ba ke ba ai amrah ko ninan da zan samu damar d’and’anasa so nake , musamman yadda yake da kakkarfar jikinta, ni kadai nasan dad’in da zansha “ duk cikin zuciyarta take wannan sa’ke sa’ken kafun ta nufi haryan dakin ta itama . *********** Ya dan Jima a hospital yau sabida wasu Mara lapiya a dake dake cikin wani mayuwacin hali, successfully kuwa akayi musu aiki, bayan ya dawo ne zaki ya kawo masa files din company, ba karamun barnan kudi akai ba, makudan millions sun ‘bata, batare da kwakkwaran daliliba,duk account din da kudin ke fita ta wajansu anne mesu anrasa, Wanda hakan ya bashi alamar tanbaya , tabbas ana fitar da kudi sannan dasa hannun wasu daga cikin companyn , amma tanbayar su wanene suke fitar dashi, daya daga cikin secret agent din companyn king yasa a nemo masa, tare da bashi Umarnin binciko masa komai daya danganci file din companyn,suna gama aikin da zasuyi sukai futar gaggawa shida zaki yau ko masu tsaro be fita dasu ba. ➰➰➰➰➰tunda ta tashi yau da fargaba ta tashi, ganin kullum mutanan gidan sai sunyi maganar aura mata dan iskan da suka ce, komai cikin sanyi take yinsa, “tahee”oumma ta kira sunanta “naam oumma”sosai oumma ke kallanta”meke damunkine yau”murmushin ya’ke tahee ta saki “babu komai oumma kawai yau da fargaba na tashi”, murmushin manya oumma ta saki” in Auran nan kikesa wa aranki kicireshi, ki dunga yawaita addua in alkairi ne, in kuma sharrine Allah ya nisan taki dashi”jin jina mata kai tahee tayi “insha Allahu oumma”. Bin bayan ta da kallo oumma tayi , abun na damunta sosai amma tana boye rauninta ne sabida kar tahee ta karaya, kullum adduar ta Allah ya zaba mata mafi alkairi. Shigowar tahee dakin ne yasa taheer sakin murmushi dan duk yaji zancensu,kara sakin wani murmushin yayi yana kamo hannun tahee din, be bari tayi magana ba ya dora da “nayi mafarki, nayi mafarki kinyi aure ,kin auri babban mutum da kowa yake san mallakarsa ba wancan dan iskanba, zakiyi rayuwa dasu sosai wasu zasu soki, wasu kuma zaki nuna miki ki”binsa da kallo kawai tayi duk da bata yadda da magan ganun saba amma hakan ya sanyaya mata zuciya . Karfe biyu na rana wasu manyan motocine suka shigo garin, kowa sai bin motar yake da kallo ana d’aga musu hannu, Daidai kofar gidansu tahee motocin nan sukai parking yara da manya kowa ya cika wajan , cikin gida kuwa har an kawo musu labari, da sauri kaka ta bawa ta shige daki tare da dakko wata farar Leda data cukurkude, bude ledar tayi tare da dakko tsinken turaran wuta, bayan ta kunna turaren wutarne ta koma ta dauko sabuwar tabarmarta ta shinfida a tsakar gidan , komai cikin sauri take yinsa . A hankali ta fito daga cikin bayan wata tinted prado,bayan uban damin kudin data bawa security su rabawa mutane , ba kowa bace face hajiya kilishi, a hankali cikin takun manyan mutane ta nufi cikin gidan fuskarta dauke da murmushi, yayinda biyu daga cikin security din suka fara fito da kayan motar suna shigar dasu cikin gidan . Tun daga kan matasan gidan har manya kowa tsugunnawa yake yana gaisheta, cikin sakin fuska take amsawa kowa harta karasa zama akan tabarmar da aka shinfida mata batare da ‘kyan ‘kyanin komai ba. Sosai sukai hirar Yaushe gamo ta bawa kowa tsarabarsa , duk wannan abun da ake su tahee basu sai me ke faruwa ba , sai hayaniyar da suke ji tana tashi sama sama,anan ne suke mata gulmar dawowar oumma da Sanar da tahee, sosai hajiya kilishi ranta ya baci akan rashin sanar da ita da basuyi ba , da Auran da suke san yiwa tahee, ranta ba karamun baci yayi har suka fara dana sanin fada mata , bata nuna musu komai ba sai fadan da tayi musu da Nasiha me ratsa jiki , sun dade suna tattaunawa kafin ta mike ta nufi dakin su tahee, kwankwasa kofa tayi , TAHEE dake tsaye rike da tsintsiya ta bude kofar , cikin waro ido da tsananin farin ciki ta furta “AUNTY” itama aunty tata murmushi ne kwance a fuskarta, budewa tahee hannuwa tayi da sauri kuwa tahee ta nufe ta , ta rungumeta sosai tayi farin ciki da ganin auntyn Tata har hakan ya kasa boyuwa, kallanta hajiya kilishi tayi ganin yadda ta kara ramewa ga bakin da tayi, batace mata komai ba sai girgiza kai kawai da tayi bayan tahee ta bata hanyar wucewa, sallar da hajiya kilishi tayi ne yasa ko wannansu kallan kofa, take ko wannansu ya saki murmushi, TAHEER ne ya tashi daga inda yake ya bawa aunty ta su waje , bayan sun gaisa sun dade suna hira kafun hajiya kilishi tayi wa oumma jajan abin da ya faru , kallan tahee hajiya kilishi tayi kafin ta kira sunanta” taheera “ tagowa tahee tayi tana amsa mata “na’am aunty” cikin dan hade rai hajiya kilishi ta soma magana” naji labarin kince kinaso kiyi aure har ankawo kudin ki , hakane “, fashewa da kuka tahee tayi tana girgiza kanta ni bana san shi aunty”ganin yadda take kuka ne yasa aunty tausaya mata itama tayi mata hakan ne sabida ta san asalin gaskiyar “shikenan share hawayen to” kamar yadda ta satan kuwa share hawayen tayi” yanxu zan baki za’bi zaki bini ko zaki auri tanimu” saurin dago da idanuwan ta tayi da zubawa auntyn tata, murmushi hajiya kilishi tayi tana mikewa “ kuyi shawara toh “, ganin yadda ta mike din zata basu waje oumma ta dakatar da ita “itama yar kice ai wata shawara zatayi , duk yadda kikayi ai Daidai ne”,Murmushin farin ciki hajiya kilishi tayi “nagode sosai yaya, Allah ya bar zumunci, nan da munti 30 zamu tafi “ tana gama fadar hakan ta bar dakin. Dan kallan oumma tahee tayi cikin damuwa tace “oumma kin yadda na tafi ya barku” yar harara oumma tayi mata kafun ta mike “ idan ba kyaso ki bita sai kitsaya ayi miki auren inyaso sai ki tare” tana gama fadar hakan ta shige dakin. Kallanta TAHEER yayi “ shawarar da oumma tayi miki shine alkairi a gareki dan mutanan nan bazasu kyaleki ba sai sun aura miki shegen mutumin can , me kama da biri “jinjina masa kai tayi cikin damuwar dake fuskar nan, ganin yadda ta damu yasashi fara janta da hira har ta sake. Suna zaune oumma tafi to tare da kallansu, sosai tayi wa tahee fada da nasiha akan ta rike mutuncin ta, ta zama me hakuri da kawaici a duk yadda ta sameta, sosai oumma tayi mata nasiha da nuna mata illar rashin yin azkar, har kuka tahee tayi ganin yadda oumma take Mata nasihan me ratsa jiki, ko wannansu dauriya yake, shima taheer ji yake kamar ya saki kuka amma ya dake tare da sakin murmushi, suna zaune a hakan hajiya kilishi ta dawo , kasan cewar tahee tayi wanka hijabinta kawai tasa tana sharar kwalla, TAHEER ya dauki jakar kayanta tare da fita dasu, oumma bata biyota rakiya ba gudun abinda ze je ya dawo . Cikin sanyin jiki tahee ta fito waje , tsatstsaye ta same mutanan yan gidan kowa sai faman harare Harare suke ba bakin magana , musamman Dije da har kwallar bakin ciki se datayi, bintalo ba sai faman zaginta take ganin ba a tafi da ita . Saida hajiya kilishi ta gama sallamarsu kafun ta kama hannun tahee ta shigar da ita mota, a haka motocin suka fara tafiya, tunda aka fara tafiya tahee tunani take , har aka karaso airport din bata sani ba sai da hajiya kilishi tayi mata magana , wata Hanya sukabi a cikin airport din da ya kaisu wani babban fili, wasu manyan jiragene awajan kusan guda uku, ko wanne da tanbarin AL_NAHYAN a jiki , daya daga cikin jiragen suka nufa jikin tahee sai faman rawa yake,Daidai bakin step din jirgin ta tsaya ta fara rarraba idanu, ruko hannunta hajiya kilishi tayi “karki damu ba abunda zai miki” saurin gyada mata kai tahee tayi zuciyarta sai faman bugawa take , ga hannun hajiya kilishi da ta rike gagam a haka suka shiga cikin jirgin, duk sauran bodyguard din Sara mata sukai tare da tsayawa a wajan jirgin…. Comment and share ✍️. 💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖 💖LITTAFAN SUNE KAMAR HAKA 💖 👇👇👇👇👇 💖DUK KARFIN IZZATA( star lady)💖 💖GIDAN AUNTY (mss Lee )💖 💖SARKI SAMEER (xeenat love )💖 💖YA FITA ZAKKA (maman sayyid)💖 💖JINI DAYA (mrs bbk)💖 Comment and share ✍️. Mss Lee 💖 ‎Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/GOZ7a2miBjZ4vUjRXdRdrA 💖💖GIDAN AUNTY💖💖 (A heart touching love story ) Story & written By Mss Lee 💖 💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖 PAID BOOK MAISO AYI MISHI TALLAN KAYANSA YAMUN MAGANA TA WANNAN NUMBER 07041879581 BOOK 1📕 Free page 11 🦋 Karfe 9:10 na dare jirginsu ya sauka a murtala muhammad international Airport (MMIA) dake Garin lagos, wasu dankara dan karan motocine sukazo daukarsu,da kyar tahee take daga kafarta jin yadda kanta ke sara mata, mintuna 35 ne suka kaisu AL_NAHYAN EATATE dake banana island ,tundaga kan Layin gidan kan tahee ke matukar sarawa ga wani irin tsananin bugu da zuciyarta kema ta,ko ina da yalwataccen haske kamar ba dare ba , ta ko ina sojojine ke Sara musu, sosai tahee ta rike hannun hijabinta gagam ganin irin sojojin dake gidan , sabida ydda zuciyarta ke bugawa sosai ta kulle idanuwanta , direct motocin part din hajiya kilishi suka nufa,sau biyu hajiya kilishi na kiran tahee amma bata masa ba , ana ukunne ta tabata sosai tahee ta ware idanuwanta, kallan ta hajiya kilishi tayi na yan sakanni kafun ta soma magana “ lapiyan ki kuwa “ gyada mata kai taheera tayi sai kuma ta bude bakinta” Kai na ne ke dan ciwo aunty “, cikin damuwa hajiya kilishi ta kamo hannunta ta futo da ita daga cikin motar”sannu kinji, nasan gajiya ce muje ciki kisha magani sai ki kwanta”nan ma gyada kanta tahee tayi batare da cewa komai ba,kafarta ta taka da soma tayifa sosai wani azababban zafi ke ratsa kafarta , kamar wacce ta dora kafarta a garwashi, ko wacce addua tazo bakinta yi take , nan da nan taji zafin ya tafi, haka suka karasa ciki tana bun hajiya kilishi a baya, dakin dake gefen star case ammi ta bude , “Bismillah tahee”, shiga ciki tahee tayi bakin dauke da Bismillah kamar ydda hajiya kilishi ta umarceta,”ga ban daki nan , zansa a kawo miki abinci da magani sai kishi ki kwanta”cewar hajiya kilishi,”na gode sosai aunty ,Allah ya saka da Alkairi”bata bari ta karasa ba ta katseta”Godiyar ta isa haka kisa mu ki huta”tana gama fadar haka ta bar dakin.itama toilet ta nufa tare da kama ruwa sannan tayo Alwala , tana fitowa ta tarar da jakar kayanta, hijab ta dauka tare da nufar inda dadduma take shinfide,sallolin da ake binta ta rama tana cikin addua ne aka kwankwasa kofar, Tashi tayi tare da budewa , wata budurwace ta shigo sanye da blue din Riga da dark blue din skeat ,”good day ma”cewar ta, murmushi kawai tahee tayi batare da ta amsa ba, abincin dake hannunta ta ajiye cikin center table din dake kusa da ita , cikin gurbatacciyar hausarta tace” madam tace na kawo miki abinci sannan kisha magani ki kwanta,”toh na gode”, jinjina mata kai budurwar tayi tare da furo mata kofa , abincin da aka kawo mata ta bude lafiyayyan abincine me rai da lapiya a ciki,sai kunun aya da aka sa mata cikin wani mini glass jug, daga gefen tray din wasu Kayan mar marine aciki, kadan ta tsakuri abincin “da oumma da taheer sunanan tare za muci abincin , nasan yanxu Suna can su kadai”, cewar tahee harta kammala cin abincin, kuskure bakinta tayi tare da watsa ruwa , sannan ta hau kan lapiyayyan gadon dakin ,lilliba tayi jin sanyi na ratsata ta ko ina , bata dade da kwanciya ba bacci ya dauke ta . ➰➰➰➰ A gajiye ya dawo gidan bayan zaki ya ajjesa, ko part din ammi be Jeba, Wanka kawai yayi tare da nufar down stairs , Kai tsaye kitchen din dake falon ya nufa, banban kitchen ne da ya gaji da haduwa komai na anfanin kitchen akwai shi a ciki,kitchen din sai faman daukan kyalli yake, coffee ya hada cikin coffee maker din kitchen din, kan daya daga cikin kujerun dining din kitchen din ya zauna, a hankali yake sipping coffee din dake hannunsa,bayan ya shanyene ya kara hada wani tare da barin kitchen din, stair case ya dau tare da nufar kofar hagunsa, taku kadan ya kai shi wasu kofofi guda uku, kofar tsakiya ya shiga , ya dau dogon lokaci a ciki kafun ya fito, stair case din da zai kaishi second floor ya hau, a hankali yake taka stairs din har ya karasa hawa saman, kan daya daga cikin kujerun falon ya zauna tare da fara operating din system dinsa, ya dade yana anfani da ita kafun ya kashe ta gaba daya , toilet ya nufa be dade ba ya fito tare da nufar faffadan gadonshi, remotes din fitulun part din ya kashe kafun ya kwanta cikin lallausan gadonsa, be dade da kwanciya ba bacci ya daukesa. Wutace sosai take ci, da anzuba mata ruwa Sai ta kara tashi kamar wacce ake hurata , ga hayaki da ya gauraye ko ina, daga cikin wutar kuwa hannu ake miko masa cikin azaba “Akhee habeeby!!Akhee habeeby!!”hannunsa ya Mika da niyar ya kamo Wanda yake cikin wutar… farkawa king yayi sai faman hada gumi yake bayan sanyin Acn da ya cika dakin, adduoi ya fara karantawa a hankali wata nutsuwa tazo masa ,wayarsa dake side din gadan sa ya kunna,4:30shine abunda agogon ya nuna masa, mikewa yayi tare da nufar toilet, wanka ya fara yi kafun yayo Alwala, ya dade yana nafila kafun ai kirin sallah, direct kasa ya nufa bayan ya idar da sallahn , sanye yake cikin white jallabiya , sosai farar jallabiyar tayiwa surar jikinsa kyau,gashin kansa sanye yke cikin bakin rawanin larabawa, sosai kyawun fuskarsa ya fito, musamman idanuwansa da suka kara haske sai kyalli suke duk da kasancewar fuskarsa a hade yake,a hanyar zuwa Masallaci suka hadu da abeey shima zasu tafi masallacin,a haka motocin su suk fita , a dawo wa ma tare suka dawo gidan,Kai tsaye part din dada suka nufa dukansu, ganin babu kowa a falon yasa su samun waje ko wannan su ya zauna. Mintuna kadan sai gashi ta fita sanye da hijabi a jikinta , ko wannansu gaishe da ita yayi , yayinda take amsawa fuskarta washe da fara’a, kankance ido king yayi” dada yau naga sai fara a kike ko an miki albishir da zuwa umarace”a hankali yayi maganar amma duk da haka sai da ta jisa, hararar sa dada tayi”A’ah gorin daurin aurenka aka kawomun”kara hade fuska king yayi tare da dauke idanuwansa daga kanta,tabule baki dada tayi “Kai dai Kasani mutum kullum cikin daure fuska ,kamar audiga ina dalili”, be tanka mata ba sai ma lumshe ida nuwansa da yayi, abeey kam murmushi kawai yayi, hira suka dada ta fara tare da su uncle musaddiq , abeey na sa musu baki lokaci zuwa lokaci na yana kallan king, ganin hirar tasu bame karewa bace yayi musu sallama tare da nufar part dinsa. Gym room dinsa ya nufa , tare da sa kayn motsa jiki , ya dade yana motsa jiki kafun ya futo duk ya hada zufa ,kwantaccen gashin kansa ya zubo masa har wajan idanuwansa,Wanka yayi tare da shirya cikin wani hadadden suit red colour, daddadan kamshin turaransa ya cika ko ina , gashin kansa ya sha gyada yayin da gefe guda na fuskar sa gashin ya futo harwajan idanuwansa,pink lips dinsa ya turo sosai , yayinda fuskarsa take a daure,sosai yayi kyau cikin shigarsa , sai ta kara futo da ainahin kalarsa ta larabawa,cikin takun sa ya bar part din , direct part din ummey ya nufa, har lokacin zoya bacci take , be dad’e ba ya bar part din tare da nufar part din ammi. Yana shiga falan ya tarar da ba kowa a ciki sai yan aikin dake gyara dinning , suna ganinsa ko wanne jikinsa ya dau rawa, cikin rawar murya suka gaishe shi,da hannu kawai yayi musu alama , suna ganin haka sukai saurin barin wajan, kan daya daga cikin 2 sitter din kujerun ya zauna tare da crossing legs dinsa. Cikin shigar material ammi ta fito daga kitchen , hannunta dauke da tray din abinci, cikin na tsuwarsa ya mike tare da nufar inda take da nufin sauke mata tray din, girgiza masa kai tayi “no son,abincin daughter ne”, kallan ta yayi na yan sakanni kafun ya bude bakinsa” me ya kawo su part dinnan da sassafe”,hararar sa ammi tayi “Kai me ya kawo ka da sassafe, Kai tsaye ya bata amsa “to see my happiness “murmushi ammi ta sakar masa tana kara jin kaunarsa a ranta ,”ba abincin su amrah bane, wannan na sister dinka ce , you will see her soon”bai ce mata komai ba sai lumshe mata ido da yayi, itama Kai tsaye dakin da tahee take ciki ta nufa, akan dadduma ta tarar da ita , mikewa tayi tare da karban tray din hannun Amin ta ajje mata a gefe” ina kwana aunty”kallanta sosai Ammon tayi “from today ki kirani da ammi not aunty” jinjina mata kai tahee tayi sai kuma ta bude baki”insha Allah ammi” dariyar jin dadi ammi tayi “kin tashi lapiya, hope ciwan kan ya sauka”, “eh ya dena ammi”cewar tahee, “toh Allah ya kara sauki, ga breakfast nan in kin gama sai ki fito falo karkiyi ta zama a daki ke kadai”, jin jina mata kai tahee tayi “toh ammi na gode “, fita ammi tayi daga cikin dakin, TAHEE kuma waje ta Samu ta zauna “ya Allahu har na fara kewar ku oumma na da taheer dina “. A falo kuwa har yanxu king na zaune ya lumshe idanuwansa “if not for ammi, who dare to keep him waiting”,lips dinsa na kasa ya fara tsotsa kwata kwata bazaka gane yanayinsaba, shafa gefan fuskarsa da akaine yasashi bude idanuwansa,ammi ya tarar a tsaye sai faman murmushi take saki, dauke kansa yayi daga kallanta,”sorry my son”, dago da idanuwansa yayi tare da kallanta “it’s okay , ammi am hungry “,am coming” kawai tace tare da komawa kitchen , hadadden breakfast dinsa da tayi masa shida tahee takawo masa , tsabar sarauta a baki take bashi,kadan yaci tare da Shan kunun ayan da yake matukar kauna,bayan ya kammala cin abincinsa ammi ta kallesa “son Yaushe zaka dawo gida”Kai tsaye ya bata amsa” it can be possible da yamma , kina bukatar wani abune “girgiza masa kai tayi “no son na tanbaya ne kawai”,mikewa yayi tare da pecking din goshinta “am going now”, take care shine abunda ammi tace masa , jinjina mata kai yayi tare da barin part din. A daki Kuwa tahee wanka tayi bayan ta kammala cin abincin da ammi ta kawo mata, hijab dinta ta saka tare da kwashe kwanukan ta fito falo, Daidai lokacin da yan matan gidan ke shigowa, kallan tara saura kwata amrah ta bita dashi”ke kuma daga ina”,murmushin yake tahee ta saki”ina kwananku “wani hararan amrah ta bita dashi “bashi na tanbayeki ba”.ihsan ce ta katse mata zancen ta” easy amrah , ki bita a hankali mana”, kallanta ihsan tayi cikin sake fuska”yan mata ya sunan ki”, amsa mata tayi da “TAHEERA “tana sun kuyar dakai, lokaci d’aya zuciyar firdausi da amrah ya buga, “wow gaskiya kina da suna me dadi gaki kyakkyawa”,Shigowar ammi ne ya katse ihsan, “ah ah yan matana yana ganku a tsaye “, sumayyace tai saurin bata amsa “bakomai ammi mun shigone sai mukaga bakuwarki shine muke dan gaisawa”murmushi ammi tayi “kun kyauta kuwa , ku samu waje ku zazzauna , Kema tahee zo ki zauna”, kallan ammi tahee tayi “dama ina san wanke wadan nan kayan ne”girgiza mata kai ammi tayi “basai kin wahalar da kankiba”, wani dan button ta danna sai ga yan aiki guda biyu sun fito, kallan daya daga cikinsu ammi tayi “asabe ga kwanukwanan a hannun tahee su zaki kai kitchen”, toh hajiya cewar wadda aka kira da asabe,kwanukan hannun tahee asabe ta karba “nagode “murmushi asabe ta sakar mata ,”oya zo ki zauna “cewar ammi, waje ta samu daga kasa zata zauna ammi ta dakatar da ita, “ga waje zauna akan kujera”,batai musu ba ta hau daya daga cikin kujerun, “toh yan matana wannan sunan ta taheera ana ce mata tahee, Kema tahee wadaddan yayyunkine, wannan ta farkon ta nuna sumayya, sunanta sumayya,sai ihsan a kusa da ita , sai amrah da kuma firdausi”yawu firdausi ta hadiye”ammi ko itace wacce Kikace zaki kawo mana “, gyada mata kai ammi tayi, “tahee zata cigaba da zama tare damu, Inaso ku zauna kamar yadda nasan ku, hope zaku karbeta”, murmushin yake amrah ta saki “insha Allahu ammi”a haka suka dan taba hira kuwa da abunda yake sa’kawa a ransa, TAHEE ma duk a takure take ganin irin kallan da amrah take binta dashi,dama dama ihsan da ke janta da hira, sumayya da firdausi ko kallanta basa yi. Zuciyarta tafarfasa take ba abunda take nanatawa sai “bazai yuba, it’s impossible “ tare da mikewa ….. Comment and share 💖 Alkalamin Mss Lee ✍️ 💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖 LITTATTAFAN SUNE KAMAR HAKA 👇👇👇👇👇 DUK KARFIN IZZATA (star lady ) GIDAN AUNTY ( mss Lee) JINI DAYA ( mrs bbk) YA FITA ZAKKA( maman sayyid ) SARKI SAMEER( xeenat love) Alkalamin Mss LEE✍️✍️✍️✍️ Ina Godiya masu commenting , I heart you all💖💖. ‎Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/GOZ7a2miBjZ4vUjRXdRdrA 💖💖GIDAN AUNTY💖💖 (A heart touching love story) Story & written By Mss Lee 💖 PAID BOOK MAISAN COMPLETE DIN GIDAN AUNTY YAMUN MAGANA TA WANNAN NUMBER 07041879581 BOOK 1 📕 Free page 12 🦋 Zuciyarta tafarfasa take babu abunda take nana tawa sai “bazai yiwu ba , it’s impossible “ tare da mikewa , kallanta ammi tayi “ah ah amrah ina zaki”cikin dan rawar murya ta amsa mata “dama ina da lectures naga lokaci yana tafiya inaso na shirya”jinjina kai ammi tayi alamar gamsuwa “All the best daughter”, murmushin yake amrah ta sakar mata “thank you ammi”, tana gama fadar hakan ta bar part din, cikin sauri ta nufi part din auntyn ta, cikin sauri take tafiya ko kula da auntyn ta dake falon batai tai shigewa dakinta, ganin hakan yasa hajiya ameena bin bayanta , a tsaye ta tarar da ita sai faman safa da marwa take , “lapiyar ki kuwa amrah kika shigo duk a rude ko har kingansa “, jijjiga mata kai amrah tayi sai faman zagaye take , kallanta hajiya amena tayi ,” kiyi mun ba yani mana”,aunty akwai matsala “ cewar amrah “kinsan jiya ammi tayi tafiya , yanxu baki gani ba da wata yarinya ta dawo , itama wai anan zata zauna “ta be baki hajiya Amina tayi “to sai me dan ta kawo wata yar kauye”girgiza mata kai amrah tayi “ah ah aunty bazaki gane bane , kinsan sharadin da boka ya sa mana , baki ga yarinyar bane , kyakkyawace sosai , gata a cike ta ko ina kamar wata babba, koni da na ganta sai da naji sha’awata ta motsa, balantana king da yake namiji, dole yaji wani abu aka ta, banasan kwata kwata king ya ganta , Kema kinsan dalilin da yasa nake zuwa part din ammi sabida kawai acan zan iya ganinsa” bata bari hajiya Amina tayi magana ba ta dora “ aunty ya kamata kiyi wani abu,dan wallahi duk Wanda yayi kokarin rabani dashi sai nayi azalinsa, hakuri ya fara kare wa duk lokacin da na gansa sai sha’awata ta motsa”, jin maganganun amrah ba karamun jijjiga hajiya Amina yayi ba “dole na kaiwa boka ziyara dan bazan taba bari dukiya ahalin nahyan ta su bucemun ba, yanxu ki kwantar da hankalin ki karyi abunda zai sa a zargeki, dan Nima ko zanyi yawo tsirara sai dukiyar nan ta dawo waje na “tana gama fadar hakan ta har dakin, waya amrah ta dakko tare da kiran wata number, ringing 2 aka daga wayar , bata jira cewarsava ta soma magana “ Ina bukatar ka kashe mun kishirwar data tasomun, zan fada maka inda zamu hadu”, tana gama fadar haka ta kashe wayarta, sai faman lumshe ido take tana Cizan yatsa. *****Apart din ammi duk yan matan sun koma part Dinsu, part din dada ammi ta nufa da tahee, sai faman bin ginin gidan take da kallo musamman wani dogon building din glass da ya burgeta , da wasu irin flowers me hade da pink colour , sosai flower din sukai mata kyau, falon dada suka shiga komai yana nan kamar yadda yake sai faman tashin kamshi yake kamar ba a amfani dashi,”Assalamu alaikum”cewar su ammi, itama dadan amsa wa tayi tana gyara farin glass din idanta, zama ammi tayi kan daya daga cikin kujerun falon, tahee kuwa samun waje tayi daga kasa kan carfet ta zauna, hakan da tayi ba karamun burge dada tayi ba amma bata ce komai ba. “Sannu da hutawa dada”, murmushi dada ta saki “Yauwa maman yara, a ina kika samo wannan kyakkyawar yarinyar”, murmushi ammi ta saki,”ina wuni “cewar tahee, amsawa dada tayi taba bin tahee da kallo, nutsuwar yarinyar ya birgeta,” dada wannan Itace yarinyar da nace miki inaso ta dawo waje na, na kawo miki itane ta gaisheki”,murmushin jin dadi dada ta saki “kin kyauta kuwa, yan mata ya sunanki” dada ta fada na mayar da hankali kan tahee, sun kuyar da Kai tahee tayi sunana Taheera , zaro ido dada tayi sai kuma ta tabe baki, yaran zamani kowa dai da irin nasa sunan , shi wancan bod’ararran ansa masa tahanuni (tahnoon), ke kuma ga naki salan sunan wai tahura (taheera), sun kuyar da Kai ammi tayi jin yadda ta kira sunan su, gashi ba halin dariya , dada kuwa bilhakki da gaske take ko dariya a fuskarta, kara kallan tahee tayi,”nikin ganni nan , wallahi iyayena sunan kwarai suka samun, ina dalili ai ku sunayan ku sai ku wallahi”,itama tahee dariya dada ta bata amma sai tai saurin gimshe kayarta amma murmushin yaki buya a fuskarta.”sannan ki saki jikinki nan ma gidan kune , ko me sikeso ki tanbaya za a miki kinji tahura “,sosai murmushin da take boyewa ya fito har dan gaf din hakorin ta fitowa “nagode sosai hajiya”dada bata bari ta karasa ba ta dakatar da ita”yau naji wani batu, dada zaki dunga cemun kamar sauran”,jinjina mata kai tahee tayi “nagode dada”sosai tayi wa dada adduar da har yar kwalla saida ta share “Allah yayi miki albarka “kasa kasa tahee ta amsa “ameen”ita de ammi sai binsu take da kallo tana sakin murmushi, kallanta dada tahee maman yara , gasky wannan ‘ya a kwai hankali, nasan a gajiye kuke , idan ta huta sai a gabatar mata da kowa na cikin a halin ta san yan uwanta, cikin girmamawa ammi ta amsa mata”mun gode sosai dada, Allah ya huta gajiya”, ameen aka wai dada tace mata kafin su kama hanyar fita da ga part din, bin bayansu da kallo dada tayi kafun ta saki wani murmushi akan fuskarta . ************ ILORIN babban waje ne katafaran gaske , me dauke da abubuwa mabanbanta a cikinsa , ba karamun makudan kudi aka kashe ba wajan gina falon, komai na cikin falon red colour ne tundaga kan carfet har zuwa kan labulayen dakin, hatta mutanan dake tsats tsaye ko wanne fuskarsa a rufe , matan sanye suke cikin jajayen kyalle iya gwiwa , yayinda mazan suka sanya dan karamun jan kyalle da ya bude al’aurarsu, magana suka fara cikin wani irin yare Mara dadin saturate, kasancewar falon babbane hakan yabasu daman Jan layi kowannansa dauke da glass cup ne Jan abu acikinsa, Yaren suka cigaba dayi , sunayi suna sunkiyar da kansu, wani hayakine ya cika falon , yayinda wata murya Mara dadin ji ta farara babbaka dariya, sannu a hankali ta koma ta jarirai, a haka karuwar muryar nan ta kuma karade ko ina da dariya , data gama sai kukan jarirai suma, an dau lokaci ana haka kafun hayakin ya dauke. Wata katuwar matace ta bayyana a falon , baka kirin da ita fuskarta dauke da wasu kananan kuraje ba kyan gani, durkusawa sukai baki dayansu tare da yi mata sujjada(wa’iyazubillah), sosai suka shiga yi mata kirari”shugaba me share mana hawayen mu, kece farin cikin kowa ne halitta , kece maganin kukanmu, kamar yadda kika saba share mana hawaye “, dariya Matar nan ta fara kafun lokaci daya ta hade ranta kamar ba yanxu ta gama dariya ba, cikin kakkausan murya ta soma magana “ lokaci yayi, lokaci yayi da zaku mallaki duniya, duniya takuce , mu kuma mune abun bautawanku, saura Kiris komai yazo karshe, tabbas aikin ku ya fara zuwa gangara “, kallan daya daga cikin mutanan falon tayi, “abar kauna”shine sunan da ta kira , wacce aka kira da abin kaunace ta fito tsakiya, “tuba nake me sharemun hawaye , tuba nake shugaban dudduniya”, shafa kanta wannan bakar matar tayi , “tabbas kaso mafi yawa na aikin nan yana hannunki,dole ki tabbatar jinin da kika dade kika kiwo ya kwaranya ga dodon tsafi , muna bukatar jinin kafun nan da mako biyu”kara sun kuyar da Kai Wadda aka kira da abar kauna tayi “Godiya muke abun bautarmu tabbas babu me share mana hawaye seke”kara hade fuskarta tayi tare da bin abar Kaunar ta da mayataccen kallo,Tashi tsaye abar kauna tayi , tare da rungumar bakar matar nan, matseta sosai matar tayi ajikinta tana shinshinar wuyan ta kafun lokaci daya su bace a falon ,sun kuyar dakai ragowar mutanan falon sukayi kafun ko wannansu ya buga cinyarsa sau uku,suna gama bugawa wani bakin hayaki ya cika falon, lokaci d’aya hayakin ya dauke, sabanin dazu, yanxu ba kowa a falon. ************* LAGOS zaune ammi take kan daya daga cikin sofa din falo, sosai taci ado cin ash din material sai faman walwali take , ga sanyanyan kamshi dake Tashi a jikinta, iya haduwa ammi ta hadu , har yanxu fuskarta dauke da murmushi akai kamar kullum, lokaci zuwa lokaci takan duba agogon wayarta , ganin 9:00 ta kusa yasa ta mike wa , hart fara taku zata bar Wanjan, daddadan kamshin turaran king ya cika falon, jiyowa tayi tana sakar masa murmushi, shima narkakkun ida nuwansa ya zuba mata yana binta da kallo, har ya karaso wajan, hannunsa guda daya yasa tare da kamo na ammi ya zaunar da ita, har lokacin be ce komai ba , kusan mintuna daya kafun ya ce mata”kinyi kyau” sosai hakwaranta ya fito waje jin abinda yace “kaima kayi kyau son , kamar Wanda ya dawo daga zance”, dan tabile bakinsa yayi tare da kawar da zancen,”coffee ammi” har ta bude baki da niyar bashi amsa wayar hannunta ta soma ringing, tana zaunan ta daga kusan mintuna biyu kafun ta kashe ,mikewa tayi tare da nufar kitchen , a tsaye ta tarar da tahee da asabe suna aiki, kallan asabe ammi tayi a hada coffee a kaiwa son , kinsan baya san jira , tana gama fadar hakan ta bar kitchen din, hannu asabe ta dora a ka “na shiga uku na lalace”sai kuma ta shafa kumatunta, tuni jikinta ya hau rawa, ita tahee dariya ma abun ya bata daga cewa takai coffee har da yar kwalla , bata ce Mata komai ba sai binta da kallo da take,girgiza kai kawai tayi atunanin tayi coffee din ne bata iya hadawa ba shiyasa duk ta zure haka “kawo kayan na hada miki”, sosai asabe ta shiga yi mata Godiya kamar zata zugunnata mata, kayan coffee din kuwa ta dakko mata , tare da nuna mata coffee maker din, bata san yadda ake anfani dashi ba, da temakon asabe ta hada coffee din da ko a ido sai ya burgeka, neman hanya guduwa asabe , tana ganin tahee ta kammala hadawa, tace mata bari taje ta dawo, TAHEE bata gane ba sai jinjina mata kai da tayi , kusan yan mintuna ganin coffee din na kokarin jin sanyi yasa ta dauka hankali kwance tare da nufar falon, agaban idan asabe dake bayan kofa sai faman hada zufa take, da sallamarta t shigo falon, Sam ta manta coffee ne a hannunta sabida dandanan kamshin da ya cika mata hanci, kanta a kasa sai faman murmushi take, jin tana kara kusanto kamshin da takejine yasata lumshe idanuwanta,sosai yanayin falon yayi mata dadi, da bugawa kadan kadan da zuciyarta ke mata, bata ankaraba taji ta taka abu, a firgice ta bude idanuwanta, tsabar firgita bata san lokacin da kofin coffee din ya subuce mata ba ,baya baya tayi zata fadi, sosai ta rintse idanuwanta dan ta sadakar faduwa zatai…. Comment and share 😎 Daga alkalamin Mss Lee 💖 💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖 💖DUK KARFIN IZZATA (star lady)💖 💖GIDAN AUNTY( mss Lee )💖 💖YA FITA ZAKKA( maman sayyid )💖 💖JINI DAYA (mrs bbk)💖 💖SARKI SAMEER( xeenat love )💖 ‎Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/GOZ7a2miBjZ4vUjRXdRdrA 💖💖💖GIDAN AUNTY 💖💖💖 ( a heart touching love story ) Story &written By Mss Lee 💖 💖💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖💖 PAID BOOK Dedicated this page to masoyiya and the talent troupe writers, masoyiya I heart ❤️ you Lodi Lodi. Book 1 💖 Free page 13🦋 Sosai ta rintse idanuwanta , tsawan yan sakanni jin bata fadi kasa ba kamar yadda tayi tunani, hakan ya bata damar fara bude idanuwanta a hankali cikin fargaba, akan fuskarsa dake hade sosai idanuwanta suka sauka , ta manta a yadda take sabida shagala da tayi da kallan kyawun fuskarsa, tsawar daya daka mata a lokaci daya da sakin gefen rigarta ne ya firgitata, ga kafarta dake mata zugi kadan kadan adalilin sakin ta da yayi ta fadi, a hankali ta saki wata yar karamar kara tana rike kafartata “are you mad” taji kausashshiyar muryarsa cikin dodan kunnanta, girgiza masa kai tashiga yi , sosai ta tsorata da yanayinsa ko kallansa ta kasa,ba karamin baci ransa yayi ba ganin yadda ta basa amsa “are you mute” takarajin saukar muryarsa, nan ma kai tashiga kokarin girgiza masa,wata gigitacciyar tsawar data sata mikewa ya daka mata , bata san lokacin da ta fara “kayi hakuri dan Allah “, ta karasa a hankali tana sun kuyar da kanta kasa , dan siririn tsakin da ko ita bata jisa ba yasaki tare da komawa inda ya tashi ,”clean this mess, and bring my coffee”, ya fada a takaice har ynxu fuskarsa ba a kanta yake ba, da sauri ta jinjina masa kai sai kuma tayi saurin bude baki “toh” tana gama fada ta koma kitchen, cikin kankanin lokaci ta gama hada coffee din da sai faman kamshi yake , cikin wani dan cup me shegen kyau , a hankali tayi sallama cikin rawar murya, kamar ba zai amsa ba kuma sai ya bude bakinsa a hankali”Wa’alaykumussalm “, ko ita da ke shigowa falan bana tunanin taji , cikin rawar hannu ta karasa inda yake , duk kamshin turaran sa ya cika mata kunne , so take kawai taga ta kebance, kusan mintuna daya bece komai va kuma be amsa coffee dinva, saida ta gaji dan kanta kafun tace “gashi”kamar me kokarin sakin kuka , nan din ba bai amsa ba saida ya mula dan kansa sannan ya saka fararan hannunsa ya dauka a hankali, wani sanyayyar ajiyar zuciya tahee ta sauke ganin ya karba , sai ta koma kitchen ta dakko abunda zata gyara inda ta bata , a hankali take yin komai duk da yadda zuciya da jikinta ke rawa,cikin kankanin lokaci ta gama gyara komai ta mayar kitchen . Tana shiga bata tarar da asabe ba aciki, tunani ta fara ta tafi daki ko tajira ya tafi, dan harga Allah shakkar fita take, ta dau kusan mintuna ashirin a kitchen ganin lokaci yaja atunaninta ya tafi zuwa yanxu, Daidai ta kai tsakiya falon sabida yadda tasawa ranta ya tafi sai jin muryarsa kawai tayi a fiske “coffee” daga nan be kara cewa komai ba.”Innalillahi “ shine abunda tahee ta fada cikin zuciyarta kafun a hankali ta nufi kitchen kamar wata muna fuka , wani coffee din Ta hado masa, yanxu cikin rawar murya ta bashi, kamar dazu sai da ya gaji dan kansa sannan ya karba, ta juya da niyar komawa ta kara jin saukar muryarsa “wait”,ji tai kamar ta fasa ihu a wajan, gashi tana tsoran ta tsugunna kartaje tai wani laifin , tsawan mintuna goma tana tsaye bece da ita komai ba ,cikin dan guntun tunanin da ta fada ta kara jin saukar muryarsa “coffee”, kukane kawai tahee bata saka ba a haka ta koma ta kara hada wani coffee din ta na kawo masa bata jira cewarsa ba ta arta a guje sai cikin dakinta. A hankali ya dago da kyawawan idanuwansa “ is she mad “ ya tanbayi kansa sai kuma ya tabe baki tare da jan siririn tsaki a haka yaci gaba da sipping coffee dinshi a hankali,kusan 11 na dare yana falon kafun ya nufi nashi part din. A Daidai gaban dressing mirror din dakin ta tsaya sai faman haki take, ita kadai ta san karfin halin da tayi kafun ta rugo a guje , sosai zuciyarta take harbawa ga wani irin kasala da take ji, “amma kyakkyawa ne”ta fada a ranta sai kuma ta ja dan tsaki, tare da hade rai “coffee”,”coffee”,coffee”,ko wanne shi oho, bata gama tunaninta ba fuskarta ta hango mata yadda fuskarsa yake a hade, yawun bakinta ta hadiye”nide nashiga uku” sai kuma ta tsaya kamar me tunani “wata kila bakone shima , naga bayajin Hausa gashi dan balarabe dashi”da wannan tunanin ta kwantar da hankalinta, watsa ruwa tayi tare da kwantawa, lokaci zuwa lokaci tunanin mutumin na fado mata a rai musamman yadda dan karamin bakinsa ke cewa “coffee”. ******* WASHE GARI Tahee na zaune kan lallausan medium carfet din dakin tana karanta azkar din ta aka kwankwasa kofa , bada izinin shiga tayi, a hankali asabe ta turo kofar bakinta Dauke da sallama sai faman kawar da Kai take gefe , TAHEE na kula da yanayin ta amma batace mata komai tunda itama Allah ya tseratar da ita .gaishe da asabe tayi, duk sai asabe ta tsargu ta kasa cewa komai har tazo fita sai ta Waiwayo kanta a kasa,”uhm dama hajiya ce tace idan kin kammala cin abincin ki same ta a falo”, toh kawai tahee tace mata kafun asabe ta bar dakin. Tana kammala cin abincin da aka kawo mata kamar yadda ammi ta umarcetan falo ta nufa, anan ta tarar da ammi na kallo a tv, ammi na ganin ta tamike “Yawwa daman ke nake jira , nasan kowa yana falan dada”, da karfi zuciyar tahee ta buga , tuno fuskarsa da tayi “nashiga uku , yanxu ya zanyi idan naganshi acan”, ammi ce ta katse Mata tunanin da ta fara ,”muje ko”murmushin yake tahee ta saki har ynxu zuciyarta bata dena bugawa ba ,a haka suka nufi part din dada kasancewar hijabi ne a jikinta. Zazzaune suke a falon dada , sai faman hiransu suke gwanin burgewa , shigowar su ammi ne yasa ko wannansu maida hankali kan har yar shigowa, amrah na ganin tahee take a wajan wani tsanarta ya darsu a ranta, ji take da za ta kashe mutum babu wannan da zata kashe face wannan maiyar. Cikin sanyin jiki ta gaishe da kowa na falon , ganin irin kallan da kowannansu ke binta dashi, sabanin ummey da abeey da fuskarsu ne dauke da murmushi, sai kuma dada dake faman washe hakwaranta. “Zonan kizauna kusa dani”cewar dada , a hankali tahee ta koma kusa da ita , nuna abeey dada tayi “kinga wannan , toh shine babban dana , kuma shine baban yaran gidan, daga yanxu Kema zaki dinga kiransa da abeey kamar sauran”, sai musaddiq da uncle Saleem da ta nuna, “ wannan kuma Itace babbar maman ku, ana kiranta da ummey, ga kuma matan kawunki musaddiq , ana kiran wannan ta farko mamy sai kuma momy gatanan, sai kuma ta karshen su da ake kira da aunty , ita matar kawunci salim ce, ga yan matan gidan kuma ,duk da nasan zuwanki zaki iya saninsu tunda kullum suna wajan maman yara, bayansu akwai babbar yayarsu dake aure a saudiya sunanta samareena (samreen😂) ana ce mata ukuti( ukhti)zaki ganta wataran,akwai maza guda biyu suna karatu a turai, sai sadauki” tana ambatar kalmar sadauki gaban tahee ya fadi , jitai dada na cewa “ zaki ganshi shima wata ran amma kiyi taka tsantsan , ah too in fada miki gaskiya, ga autar gidan kuma can” ta nuna zoya dake kwance kan cinyar ammi tana bacci,kadan tahee ta dago ta kalleta “amma kyakkyawace sosai “ ta fada a zuciyarta”Nima akwai yar autata da ban fada miki ba sunanta “zarmeen sai danta kwallin kwal wato mijina sha’aban “.kallan abeey da ummeey tayi “nasan ku ai duk kunsan da zuwan ta ko” eh dada duk suka bata amsa , har yanxu da Sauran guntun murmushi akan kumatun ummey,” toh sunan ta tahura” yalwataccen murmushi abeey ya saki “taheera dai ko dada”, gyada masa kai dada tayi “ au kai da kasan da sunan ma amma sai ka wahalar dani”, wani murmushi abeey ya kara saki batare da ya ce komai ba , kallan ta hajiya ameena tayi cikin sakin fuska” gata kuwa kyakkyawa da ita kamar ka sace”, sosai ran amrah ya baci da Jin kalaman auntyn tata, ranta ya baci sosai da irin yadda kowa ke karbarta, “Shegiya in ma asiri kikai musu nice zan karyashi “ ta karasa tare da binta da kallan tsana bata re da kowa ya lura da ita ba . ********* ************** Zaune take kan daya daga cikin daddiyar kujerar falon mahaifiyarta, tunda suka dawo daga falon dada take zaune a wajan hannun ta dauke da juice yayin da Dayan hannun nata ke dauke da wayarta sai faman latsawa take , sam hankalinta na kan abunda take a wayarta, jin taku a falon yasa ta saurin fita daga abunda take tare da sassaita nutsuwarta, hajiya hauwace ta shigo falan, tun zuwansu falon dada sai yanxu ne take dawo wa , cikin izza take taku har ta karaso kan daya daga cikin kujerun dake fuskanta sumayya. Murmushi sumayya ta saki, mamy daman ke ce , “nice mana akwai Wanda kike jiran zuwan sane “, tabe baki sumayya tayi ,”toh mamy daga tanbaya, tun dazu nake jiranki fa , amma daga zuwanki kina so ki bata mun fai “, washe baki hajiya hauwa tayi “Haba summy ta ne yayi zafi kinsa Nima wasa nake miki”, jinjina kai sumayya tayi” mamy baki kula da yar iskar yarinyar da aka kawo gidan nan ba , ki duba ki gani fa yanda kowa ke kaffa kaffa da ita ko mu da muke jininsu ba ai mana wannan abun ma , musamman dada da ke faman nanike mata, wallahi in bamuyi wasa ba sai dai mu zama yan kallo a gidan nan , se abunda yar iskar yarinyarcan ta fada sannan za’ai , kina kallanta kinsan ba haka taxo ba , akwia wata kullalliya a kasa , ni tsorona kartaje ta asircemun king, sabida kinga yawanci king acan yake wuni kuma mu ba mu isa shigaba in yana nan, gaskiya mamy ya kamata ki dauki matakin gaggawa, bazan taba bari cikar burina ya tafi a banza ba , inaso nayi suna, inasan duniya ta san da za mana , inasan mallakar king ko ta halin yayane mamy”kin Hana na nuna alamun ina san sa a fili har waccan banzar take tunanin auransa, dole mamy na mallakesa sannan dukiyar gidan nan mu ya kamata muji dadin ta ba wasu ba”, ta karashe maganar tare da kurawa mahaifiyar tata idanu, sauke nunfashi hajiya hauwau tayi kafun ta soma magana “tabbas Kinyi gaskiya Nima na dade ina halkanta da hakan , a sannu zanyi maganin kowa dan bazan taba bari dukiyar da na kwallafawa Raina zubucewa ba , aure kuwa kamar anyi shine “. Sallamar ihsan ce ta katse musu zancensu , bin ko wannensu tayi da kallo tare da girgiza kai, tasan halinsu Sarai , fatan ta Allah ya shirya mata su, ganin yadda take bunsu da kallo ne yasa mamy mikewa tare da hararar ta sama sama ,bata jira cewar ihsan din ba tai wuce warts daki, itama sumayyan tashi tayi tare da nufar nata dakin,ganin duk sun watse ne yasata kiran number wayar da tayi saving da my yaya, bugu biyu ya dauka.. 🫧🫧🫧🫧🫧🫧 Tunda ta dawo daga part din dada take safa da marwa , ita kadai tasan radadin bakin cikin da takeji, ta tsani yarinyar tsana mafi muni, ko ita lokacin da tazo ba a nuna mata kauna haka ba kamar yadda aka nuna wa waccan , “tabbas sai na lahantaki, lahanin da ko kyawun da akace kina dashi ze gushe, da kanki zaki bar gidan nan”, duk wannan zan tuttukan ita kadai amrah take yinxu kamar wata zautacciya, tunani ta fara me zatayi mata da zai kunsasa mata , ta dade tana tsaye a falon kafun ta saki wani shu’umin murmushi, kitchen Dinsu ta nufa, ba a dau dogon lokaci ba ta fito sai faman sakin murmushi take , direct part din ammi ta nufa dan tasan har yanxu su ammi Suna part din dada, ilaikuwa tana shiga bata tarar da kowa ba sai kamshin turare da sanyin Ac dake tashi, jin motsi a kitchen yasa ta kara sakin wani shi’umin murmushin, ta dau kusan mintuna biyu tsaye a wajan, jin alamun taku kamar za a fito daga kitchen din yasata zuba mangyadan da debo a kan hanyar da ta san dole koma wanene ta nan zai wuce . Taheee ce ta fito daga kitchen din hannunta dauke da bottle water tana sha dan ishirwane ya kaita kitchen din, bata san da mutum a falon ba , sai ji tayi an tura ta da karfin gaske, kafarta ta sulleba a cikin man da amrah ta zube, sosai ta saki gigitacciyar kara tare da tafiya Gadan gadan zata fada , ta rotan da taji anyi , a lokaci daya da gigitacciyar marukan da aka suke akan fuskar wanda bata sani ba ya kara girgitata, lokaci d’aya nunfashin ta ya dauke alamun ta suma . Share ✍️ Littafin gidan aunty na kudine , akan 300 kacal , da zaran na gama free pages dina Wanda suka biya ne kawai zasu dinga samun update , mai don gidan aunty zai iya biyan kudin ta wannan account din 7041879581 opay, Ayshatou galadima sai a turo sheda ta wannan number 07041879581. 💖💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖💖 ‎Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/GOZ7a2miBjZ4vUjRXdRdrA 💖💖GIDAN AUNTY💖💖 (a heart touching love story) Story &written By Mss Lee💖 💖💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖💖 PAID BOOK Nakusa kammala free pages dina,littafina na kudine akan 300 kacal, VIP 500, special 1000 mai bukatar cigaba da karantawa zai biya 300 ta wannan account din 7041879581 OPAY, AYSHATOU GALADIMA, sai a turo shaidar biya ta wnn number 07041879581. Wanda suke da bukatar a tallata musu kasuwancin su kuma zasu iya yimun magana ta wannan number 07041879581. BOOK 1 📕 بسم الله الرحمن الرحيم 💖💖…… Free page 14 🦋 Wani gigitaccen marin ya kuma saukewa akan amrah da tayi mutuwar tsaye , sosai marin ya shigeta nan take ta fashe da kuka,a matukar firgice ta daga idanuwanta, Wanda taganine yasa zuciyarta bugawa da zauri , fitsarine ke kokarin kwace mata da bata shiryaba, batai tunanin samun sa anan ba ko waninsa , kallan dake firgita Mara gaskiya ya bita dashi kafun ya mayar da idanuwansa kan tahee da kallo daya yayi mata ya dauke kansa da jan tsaki , kan daya daga cikin 3sitter din kujerun falon ya kwantar da ita, wani siririn tsakin ya kuma saki ganin dan karamin abinnan ya sumarda ita, da baya wajan kenan mutuwa zatai, ya kara Jan wani Siririn tsaki “spoiled rat” ya fada a kasan zuciyarsa. “Water “ ya fada cikin da kakkiyar muryarsa, cikin zabura amrah da jikinta ke faman rawa ta nufi kitchen da sauri ta dakko, zuciyarta sai faman tsinewa tahee yake ”nashiga ukuna Shegiya yar yarinya daga zuwan ta tasa ya mareni, nashiga ukuna, Allah yasa bega man da na zuba ba”, sai kuma ta zabura cikin sauri ta fito daga kitchen tare da kai masa ruwan sai faman sauke kai take zuciyarta na tsananta bugu, bai kalletaba sai ruwan da ya bude ya yattafawa tahee, a firgice ta tashi zata kara sakin wani karan,” if you dare”taji saukar muryarsa , kara rintse idanuwanta tayi zuciyar ta na tsananta gudu, siririn tsaki ya saki tare da matsawa can gefe,amrah na tsaye sai faman gumi take hadawa, cikin kausasshiyar muryarsa yace “apologize “daga nan be kara cewa komai ba kamar bashine yayi maganar va, wani irin kuka ne yazo wa amrah amma ta rikeshi, sosai zuciyarta ta kara tsanar tahee,”are you mad” bata bari ya karasa ba ta ce “kiyi hakuri” ta karasa cikin rawar murya sosai takejin ba’kin ciki a cikin zuciyarta ,”kneel and apologize with sympathy “ba yanda ta iya haka ta tsugunna ta shiga bawa tahee hakuri , sai lokacin tahee ta bude idanuwanta, sosai kwayar idanuwanta suka canza kala musamman bakin idan nata da ya fara dan washe wa kadan, gaban amrah ne ya fadi da Sauri ta sun kuyar da kan ta, “bakomai ya wuce “ tahee ta fada, ganin king na falon tace “nagode “ duk da kwata kwata basu yake kalla ba. Sallamar ammi ce ta katse tunanin amrah , ganin ammin yasata mikewa , Binsu da kallo ammi tayi tare da nufar tahee “lapiyan ki kuwa” sai kuma ta maida kallanta kan amrah”amrah “ ta kira sunan ta , in ina amrah ta soma , ammi bata kulata ba ta kara maida kallanta kan king” son”, lumshe mata idanuwansa yayi tare da bude wa akanta ba yabo ba fallasa, “me yafaru “ ta kara tanbayarsu, dan tabile bakinsa yayi kamar bazai ce komai sai kuma yayi magana a fisge “ I just come in, but I will come back later “yana gama fadar hakan bai jira cewarta ba ya juya , duk da kallo suka bi bayansa “ ko shine babban yayan su “zuciyar tahee tabuga sosai , musamman da taji ammi na kiransa da “son”, katse mata tunani ammi tayi “ba magana nake muku ba” amrah ce tayi saurin bude baki”daman ammi santsine ya kwasheta, sai yaya king ya temaka mata” ta karasa maganar cikin Dacin rai.kallanta ammi tayi cikin damuwa”hope bakiji ciwo ba “ gyada mata kai tahee tayi, sai a sannan amrah tayi wa ammi sallama ta bar part din, tagefan ido tahee ta bita da kallo tana cije baki, sannu ammi tayi mata kafun ta nufi dakin ta, itama tahee mikewa tayi tare da nufar dakinta. ➰➰➰➰➰➰➰➰➰ 🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧 BUNKURE Dije ce zaunce cikin wata bukka dake dauke da wasu irin tarkace , gefenta kuma bintalo ce sai faman bin wajan take da kallo duk da ba yau suka fara zuwa wajen ba, wani irin dariya aka brake dashi kafun wani hayaki ya cika wajan , kafun wani bakin mummunan mutumi ya bayyana a wajan, duk jikinsa tabo ne a jiki, ga wani irin wari dake tashi a jikinsa, kara bude bakinsa dake faman wari yayi yana faman sakin dariya , ko wannansu kasa sukai da Kai , duk da warin da yake , “Allah ya kara…. “ wata gigitacciyar tsawa ya daka mata, cikin wata murya Mara dadin sauraro ya soma magana “ hatta dai , kull din ki kisan yadda zaki dunga magana agaban shugaban ku “,sun kuyar da Kai Dije tayi” tuba muke boka , me biyawa kowa bukatunsa “, wata irin dariya ya barke da ita , kafun ya hade rai “ meke tafe da ku, ko da yake Munson me ke tafe daku, me kuke so ayi musu”, cikin jin dadi Dije tace so nake a batar dasu , itama wacca aka tafi da ita gidan daula a batar da ita ko a haukatata, sai yata bintalo takoma can da zama “, wata dariyar ya kuma yi kafun ya soma magana “bagamar a haukatar da yarinyarcan ba zaiyuba sai in har tana kusa daku, uwarta da dan uwanta kuma zaki iya kawar dasu cikin sauki idan kin bi sharadaina, a sannan ne kuma za a tura yar taki inda kikeso harta daukaka”, washe baki Dije da bintalo sukayi”Godiya muke boka” katseta yayi yana babbaka wannan mummunar dariyar tasa kafun wani dan karamun kulli ya fado a gabansu,” wannan zaki barbada musu a kofar dakinsu, da sun taka shikenan, amma kada ki kuskura wani ya taka basu ba , inba haka ba aikin ze ruguje, sharadi na biyu kuma dole ki bani yar taki na sadu da ita ,dan maniyinta kadai da aljani zai tabane zai zama cikar aikinkubayan hakan ba iya can din va, hatta maganarta sai andungaji akasin hakan kuwa rayuwarkuce zata kaskanta“, yana kammala maganar tasa ya babbake da dariya , tsuru Dije tayi tare da kallan bintalo dake faman zare ido”batare da wani dogon tunani va Dije tace “na amince”kara babbakewa yayi da dariya,cikin muryarshi da bashi da dadin sauraro yace” zaki iya tafiya, inna gama aikina sai ku tafi”, kallan Dije buntalo tayi kafun ta dauki maganin ya fita waje, yai saura daga bintalo sai wanan bokan da babu komai a jikinsa sai dan ganyen da ya rufe masa al’aurarsa. Cikin tsawa yace “mike” da sauri kuwa buntalo ta mike tana zare ido,”tube kayan ki , kizomun da baya da baya”, cikin sauri tsananin yadda ta tsorata da sauri ta cire kayanta , haihuwar uwarta, ta soma tahowa da baya da baya jikinta sai faman karkawa yake. Duwawunta ya zuba wa idanu sai faman hadiyar yawu yake yana sidar baki, cikin azama ya janyo hannunta ta fado kansa, wata kakkarfar ajiyar zuciya yasaki tare da sakin gurnani yana kara matseta a cikinsa, duk da warin da yake, ko motsi buntalo ta kasa sabida tsoran da taji, cikin azama ya juyar da ita ya Dane kanta, ba tare da wani abuba ya dage dan karamin ganyen jikinsa, take a Wajan bakakirin alaurarsa ta fito sai yawo take, bintalo kuwa harta fara hawaye, be tsaya wata jinkiriba ya shigeta da karfin gaske , tare da matseta a jikinsa yana sakin gurnani kamar wani mayun Wacin zaki……. ➰➰➰➰➰➰➰➰➰ 🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧 Yana barin part din ammin nasa hadadden gym dinsa ya nufa cikin kayan motsa jiki, sosai ya motsa jikinsa, ya dau dogon lokaci yana motsa jiki da abubuwa mabanbanta , kafun ya koma dakin sa ya watsa ruwa cikin shigarsa da tayi matukar yi masa kyau ya fito , sanye da blue din t_shirt da white jeans , sosai kakkarfar damshen hannunsa ya fito, kayan ba karamin yi masa kyau yayi ma , gashinn kansa sai faman kyalli yake, duk inda ya wuce sai kamshin imperial ya cika wajan, bai dau dogon lokaci ba yashiga cikin farar Lamborghini din da sai faman kyalli take da dauka ido take, cikin lokaci kankani, jerin motocin nan suka fita daga cikin gidan, sojojin wajan sai faman sawara motocin suke. Karfe 8:30 na dare amrah ce sanye da dan karamin towel da ko kwiwa be kara sa mata va, sai uban gashin attachment din dake yawo a bayanta. Waka ta saka tana tikar rawar ta , saida ta gaji dan kanta sannan ta kashe tana sauke ajiyar zuciya. Toilet ta nufa da nufin watsa ruwa ko dan kwali babu ajikinta, ta karasa kenan zata kunna fanfo, abinda ta gani ne ya firgitata tare da sakin gigitacciyr kara….. Comment and share ✍️ 💖💖💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖💖💖 Mss Lee 💖 Masu comment da masu yimun magana akan gidan aunty , ina matukar Godiya da jin dadi ✍️… ‎Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/GOZ7a2miBjZ4vUjRXdRdrA ‎ 💖💖GIDAN AUNTY💖💖 ( a heart touching love story) Story &written By Mss Lee 💖 💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖 PAID BOOK MAISAN GIDAN AUNTY DAGA FARKO HAR KARSHE YA TUNTUBENI TA WANNAN NUMBER 07041879581. MAI BUKATAR AYI MISHI TALLAH YA TUNTUBENI TA WANNAN NUMBER 07041879581 AKAN NAIRA 500 KACAL BOOK 1📕 بسم الله الرحمن الرحيم…….. Free page 15 🦋 Karfe 8:30 na dare, amrah ce sanye da d’an karamin towel da ko gwiwa bai karasa mata ba,sai uban gashin attachment din dake yawo a bayanta ,waka ta saka tana tikar rawarfa sai da ta gaji dan kanta sannan ta kashe tana sauke ajiyar zuciya. Toilet ta nufa da nufin watsa ruwa ko d’an kwali babu akanta, ta karasa kenan zata kunna fanfo, abinda ta ganine ya firgita ta tare da sakin gigitacciyar kara, a guje ta juya da niyar komawa , amma kafin ta karasa wajan komar wata irin mage ce ta fito ta wajan fara tass da ita, wata karan amrah ta saki, tuni ta fita a hayyacin ta sai faman ihun neman agaji take, dan karamun towel dinta ma tuni ya fadi a jikinta, saukar bulalar dataji a fatar jikintane yasata sakin razanannan kuka, sosai bulalar ta shigewa, bata gama shafa wajan ba ta karajin saukar wata bulalar, kuka kawai ta fashe da shi, ba tsaya ba aka dunga zulamata wannan bulalar, gadan gadan farar Magen nan tayo kanta, ganin haka yasa amrah sakin wani gigitaccen kara tana zube a kasa sumammiya. ******* Tana shiga daki ta fada kan gadanta sai faman murmushi take saki ita kadai, sosai take sakin murmushi idan ta tuno fuskarsa da irin yadda yake hade fuska, take fargaba da tsoransa ya kara shiga jikinta, musamman da taji ammi na kiransa da son.Lumshe idanuwanta tayi amma still shitake gani ,duk da tsananin tsoransa da ya dirar ma , amma sosai ya burgeta a iya ganin da tayi masa. Wanka ta tashi tayi kafun ta kwanta tana adduar bacci, mintuna kadan bacci ya dauketa. Sosai wasu irin halitta ke binta, yayinda tarike hannun wani da ba’a iya ganin fuskarsa, amma sai faman kareshi take daga cutar dashi dasuke kokarin yi, tun tu’ben da tayi ne yasa ta faduwa, shima Wanda tarikewa hannun ya tsaya har yanxu ba’a iya ganin fuskarsa, kafun suyi wani kwakkwaran motsi , wadannan halittun sun zagayesu sai tsalle suke saki , daya daga cikin sune yayi kanta yana zaro harshe , daidai yana kokarin cabkota wani irin girgiza ya karade ko ina, take a wajan wata katuwar farar macijiya ta bayyana a wajan, daga gefenta kuma wata farar kuliyace me shegen haske , sosai ta fito da farar farcinan, yayinda bakinta yake abune sai faman “meow meow “take cewa. Zabura wadannan halittun sukai kafun su fara Kai musu sara da faratansu, sosai macijin nan da Farar kuliya sukai musu jina jina lokaci daya suka bace batt ba aganinsu. A firgice tahee ta farka da ga mummunan mafarkin data fara duk jikinta yayi gumi sai faman zufa take hadawa, adduar neman tsari ta fara karantawa har taji nutsuwarta ta Daidai ta kafun ta mike tashiga bandaki, mintuna kadan tafito dauke da alwala, nafila tayi tare da adduoin da oumma ta koyasu hartaji ta kara samun nutsuwa kafun ta mike ta koma bacci. ➰➰➰➰➰➰➰➰➰➰ 🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧 BUNKURE Duk da tsananin yadda bintalo ke ihun ta hakan be sa yaji tausayintaba sai ma kulle mata baki da yayi da kazamin bakinsa me shegen wari, sosai yake zuba muguntarsa akanta, tsabar wahala kusan sumanta uku , azaba na sawa ta farfado, iya rashin imani saida yayi mata yayi mata kaca kaca ko dan yatsanta bata iya motsawa, se hawayen azaba dake digo mata ta ido, azuciya kuwa ta tsinewa Dije yafi a irga duk da kasancewar ta mahaifiyarta. Saida ya gama lalatarsa sannan ya bawa Dije da ke rabe damar Shigowa ya tafi da ita cikin hade rai, duk jikinta yayi sanyi ganin irin aika aikan da yayi wa bintalo, amma ko saudaya batayi nadamar hakan ba tunda burinta zai ciki, cikin razananniyar muryarsa me tsoratarwa ya daka musu tsawa akan su bace da ganinsa, ganin yadda bintalo ta kasa ko motsine yasasa babbaka dariya” ku sawa ranku aikinku kamar ya tabbatune” sai ga wata kwarya nan ta fado kasa da dan karamun ruwa a ciki jaa da shi, ruwan yasa dije ta dauka ta kwarawa bintalo a gabanta, cikin Karkarwa ta dauka tare da kwara mata, wani irin gigitacciyar azabar kara bintalo ta saki da ya firgita Dije , kara babbakewa da dariya yayi tare da hade ransa , kusan mintuna uku bintalo na kukan azabar nan kafun ta sauke nannauyar nunfashi tare da mikewa da kanta, ganin hakan yasa dijen sakin ajiyar zuciya a haka suka ajiyewa boka kudin da suka zo masa dashi tare da fita da baya baya har suka bar wajan, sai lokacin bintalo ke taku da dingishi dukda azabar da take ji ta ragu babu ita,amma gudun kar a asirinsu ya tonu basu koma gida ba sai wajan shadayan dare lokacin babu wuta, sannan babu me gane halin da suke ciki, zuciyar dije sai faman zillo take akai ta aiwatar da kudurinta kan oumma da suka shige mata hanci , ga wani tsanar su da ke kara ruruwa a Zuciyar ta. ************ Tunda ya tashi yau be fita ko ina ba sai bayan karfe goma na safe bayan motsajikinsa da yayi, Hakanan yau besan jin kowa a kusa dashi ga yunwa yana jin amma ya kasa motsa koda dan yatsar sane, coffee yake San sha dan haka ya mike cikin takun kasaitarsa kamar kullum, a hankali yake taku sanye Yake cikin black trouser da black singlet , sosai kakkarfar surar jikinta ta bayyana , farar fatar jikinsa sai sheki yake dauka, a hankali ya karasa inda coffee maker din yake, cikin yan mintuna ya gama hada coffee dinsa , a nutse ya zauna kan daya daga cikin sofa din wajen , sipping daya yayi wa coffee din tare da ajjesa, wani irin daci yaji coffee din nayi masa kamar zaisa amai, a hankali ya kara lumshe idanuwansa ko me ya tuna oho, sai gashi ya mike tare da nufar wani daki, ko cikakken minti ashirin beyi ba wani daddadan kamshi ya karade ko ina , a hankali kamshi ya kara kusan towa kafun mamallakin kamshin ya bayyana , sosai shigarsa tayi masa kyau , sanye yake cikin black suit sosai bakin suit din cikinsa ya fito da ainahin kalar farar Tatar’s a da sai sheki take , bakin nan kullum sai kara turuwa yake kamar mai shafa abu wajan, har yanxu fuskarsa a hade take amma sosai yayi kyau , ga diamond watche dinsa sai faman kyalli yake, wayace kare a kunnansa sai faman motsa baki yake ko abunda yake cewa ba aji, be tsaya a ko ina ba sai part din amminsa . A zaune ya sameta cikin shigar manyan mutane da ta saba , sosai tayi kyau cikin shigarta, kujerar da take zaune ya nufa tare da langwabar da Kai kadan, kallansa tayi tare da dauke kanta, bai ce komai ba sai hannunta da ya kamo ya dora a fuskarsa , a fusge ya furta “sorry ammi”, ajiyar zuciya ta sauke daman ba fushin take dashi ba ganin yaki zuwa haryanxu kuma tayi kewarsa ne yasa ta yi masa haka, a hankali ya furta “ina kwana ammi na “, murmushinta da baya boyuwa ta saki “ ka tashi lapiya son” lumshe mata ido yayi kawai batare da yace komai ba , ganin hakan yasan ammi tasan yan miskilancin ne a kusa, kadan suka taba hira yana amsawa kadan kadan,shafa gefan fuskarsa tayi” da alama wannan son din nawa ne ci komai ba” kara lumshe mata ido yayi tare da bude wa alamun amsa . Mikewa tayi “bari na dafa maka abinci ko” riko hannunta yayi tare da kallanta “ coffee” shine kadai abunda yace mata , jinjina masa kai tayi tare da nufar kitchen din, a tsaye ta samu tahee da asabe na aiki a kitchen , sosai tahee take jin dadin hakan sabida tana Kaunar taga ta iya abinci hala hala , ba tare da ta kalla taheen ba ta soma magana, “tahee hadawa son coffee kafun na kammala dafa masa abinci”, suman tsaye tahee tayi , zuciyar ta sai bugawa take gashi bata da dalilin musawa, kamar wacce zata saki kuka haka ta hada coffee din tare da fita falo , ko ina na falon mayataccen kamshin turaran da ke mata dadi ne ya cika wajan, Zuciyarta sai faman zillo take sabida tsoro, a hankali ta karasa inda yake bayan tayi sallama , cikin in ina ta soma magana “ina.. kwana”, kamar wacce tai da gunki ko motsi beba sai ma sarrafa wayarsa da yake cikin nutsuwa , kamar wacce zata saka kuka ta kara cewa “ina.. kwana”, yanxu ma be motsaba balantana tasa ran amsawar, siraran hawayene suka dan zubo mata kadan tare da sun kuyar da kai, kamar daga sama tayi saukar muryarsa “ fine” , wani murmushi ne ya subuce mata, sosai taji dadin amsawar dayayi, a hankali ya sa fararan dogon yatsunsa tare da dauka cup din, a hankali ya fara sipping, zuyawa tahee tayi da niyar komawa tazo daf da kitchen din ta tsinkayi muryarsa “ who permit you to leave”, sun kuyar da kai tayi tare da dawo wa ciki “ bakowa “ ta bashi amsa , tsawan mintuna goma tana a tsayen , kofin hannunsa ya ajje tare da kyara zama, another cup,”Tom “kawai tace masa tare da nufar kitchen din, har lokacin ammi na tsaye tana masa abinci da kanta, kallanta ammi tayi sai yanxu, sauke ajiyar zuciya tayi “wani cup din yace na hada masa”kallanta ammi tayi sai dai bata ce mata komai ba sai jinjina mata kai da tayi, wani cup din ta kara hadawa tare da nufar inda yake har yanxu zuciyarta bata bar bugawa ba, sallama tayi a falan kamar bazai amsa ba , sai ya amsa a hankali, batare da wani dalili ba lokaci daya taji kanta ya sara mata Daidai lokacin da zata mika masa coffee din, a maimakon ya sauka a hannunsa sai ya subuce ya zube a jikin hadaddan suit dinsa ……. (😳😳Tahee )…… Manage plx …. Masu comment ina Godiya sosai da sosai MASU BUKATAR COMPLETE DIN GIDAN AUNTY YAYI MUN MAGANA TA WANNAN NUMBER 07041879581 . MASU BUKATAR A TALLATA MUSU KASUWANCINSU SU TUNTUBENI TA WANNAN NUMBER 07041879581 AKAN NAIRA 500 KACAL. 💖💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖💖 DUK KARFIN IZZATA ( star lady ) GIDAN AUNTY (mss Lee ) JINI DAYA (mrs bbk) YA FITA ZAKKA( maman sayyid) BABY (mhiz innocent) 💖💖💖💖💖Mss Lee ✍️. ‎Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/JyvVuOvzYyF19np8UmFKV4 💖💖GIDAN AUNTY 💖💖 (a heart touching love story) Story & written By Mss Lee 💖 PAID BOOK LITTAFIN GIDAN AUNTY NA KUDI NE AKAN NAIRA 300KACAL , MAI SAN CIGABA DA KARANTAWA HAR KARSHE ZAI BIYA KUDINSA TA WANNAN ASUSUN : 7041879581 OPAY AYSHATOU GALADIMA , sai a turo da shaidar biya ta wannan number 07041879581. BOOK 1 📕 بسم الله الرحمن الرحيم ❤️❤️… Free page 16 🦋 Sosai tazaro idanuwanta waje tana faman girgiza kai,bata san lokacin da ta karasa kusa dashi tana kokarin goge masa ba , gigitacciyar tsawar da ya daka mata a lokaci daya da lafiyayyen marin da ya sauke mata ne yasata kara firgita, ga kanta da yake tsananin sara mata, lokaci d’aya taji juwa na dibarta “Dan Allah kayi hakuri” shine abunda bakinta ya iya furtawa, be kuma cewa komai ba sai mikewa da yayi kwasan wayoyinsa,Daidai lokacin da tahee take kokarin fadawa kan wani designer dake gefenta , taku daya yayi ya riko damtsen hannunta tare da Jefata kan daya daga cikin kujerun tare da sakin siririn tsaki, cikin bacin rai ya bar part din azahiri Kuma fuskarsa tananan a yadda take, baka isa fassara yanayinsaba ” me ya Hana ban karyataba “ ya fada a cikin zuciyarsa ransa na kara baci , dogon tsaki yaja iya kasan makoshi, hatta zaki daya bude masa kofa yayi mamakin ganin sa haka amma bashi da hurumin magana a haka har suka koma part dinsa. Tunda ya jefata kan kujerar da ya tashi har yanxu bata bar wajan ba , sosai taji kanta na sara mata, ta dau kusan minti biyar zaune a wajan tana addua, kafin lokaci daya ta nemi ciwan kan ta rasa gabaki daya, ajiyar zuciya ta sauke sai a lokacin kumatunta ke mata zafin marin dayayi mata , dafe wajan tayi tana sosawa “Mugu kawai” ta fada a zuciyarta tana turo dan karamin bakinta, amaimakon ta koma kitchen kai tsaye dakin ta ta nufa tare da fadawa kan gado tana sauke a jiyar zuciya har yanxu hannunta na kan kuma tunta. *******Ta dade kwance a ban dakin a sume, bugun ban dakin da ake da karfine ya farfado da ita, tayi mamakin ganinta kwance a kasa ga tsami da jikinta ke mata,kara bugun kofar da akaine yasata mikewa cikin din gishi, towel dinta dake Yashe a kasa ta dauka tare da daurawa, da Kyar take taka kafarta dake mata tsami, sai bin ko ina da kallo take, da kyar ta karasa jikin kofar, a tsaye ta sami aunty duk ta rude, tana ganinta ta saki ajiyar zuciya” me kikeyi acikin ban daki tun dazu, kinsan irin neman ki da nayi”, batasan lokacin da bakinta ya furta “bacci ne ya daukeni “,kallan ta aunty tayi tana sakin baki “bacci fa Kikace amrah “, gyada mata kai amrah tayi tana turo bakinta tare da rabata tawuce , binta kawai aunty tayi da kallo batare da tace komai ba tabar dakin. Samun waje amrah tayi kan gadonta tare da dakko wayarta dake ajje saman gadan, dogon tsaki ta saki sai a lokacin take tuno abunda tahee tayi mata,azabure ta mike tsaye “ ni amrah , nice yau nake bawa wata yar iska hakuri, ni amrah hmmm” girgiza kai tashigayi “ yau nice na kaskantar dakai na bawa wata shegiya hakuri, wallahi ko zanyi yawo tsirara sai na wulakanta ta sai na musgunawa rayuwarta sai tasan dani take magana “ ta kare zancen tana sakin kwallar bakin ciki… ******* Director part dinsa ya nufa sai faman taunar lips dinsa yake, be bi steps ba ta elevator ya hau , a second floor dinshi ya tsaya ko ina sai faman tashin kamshi yake da sanyin Ac musamman kamshin turaransa da ya kama ko ina na part din, rigar jikinsa ya cire kai tsaye faffadan zurar jikinsa ta fita fari tass dashi,sosai muscles dinsa da 6 spacks dinsa ya fito kallo daya zaka masa kasan ba karamin motsa jiki yake ba,kofar da take facing dinsa ya nufa, ya dau kusan mintuna 30 aciki kafun daddadan kamshi ya karade ko ina , sosai yayi kyau , a maimakon suit yanxu kananan kayane a jikinsa ,tun daga kan bakar jigar jikinsa tare da bakin wanda jikinsa , sosai yayi kyau cikin kayan , sumammiyar gashin kansa ya fito sosai yau ma kadan daga cikin yalwataccen gashin kansa ya fito har wajan idanunsa, sabida tsananin bacin rai pink lips dinsa ba karamin turuwa yayi ba sai faman tsuke fuskar yake, cikin takunsa na kasaita ya hau elevator tare da nufar 3rd floor, a maimakon hanyar da ya saba bi yanxu wata daban yabi,babban waje ne nashakatawa gata iska me dadin gaske dake huro wajan,kayataccen wajan shakatawa ne a wajan sosai wajan ya hadu,ga gefe d’aya dayake abude ko ruwan sama akai yana dan shigowa kadan kadan , akan daya daga cikin kujerun shakatawan yazauna ne kama da sararin samaniya, sosai yanayin wajan yasakashi cikin nutsuwa sai faman lumshe ido yake, daga gefensa ma wani cup ne me shegen kyau cikin sa wani lemone kamana da sararin samaniya shima.sai faman lumshe idanuwansa yake yana budewa, wayarsa dake ringing a hankali ya dauka batare da bata lokaci ba, Ahankali yake magana ko nakusa dashi ba Lalle yaji me yake cewa ba,sai lumshe kyawawan idanuwansa da yake faman yi. 🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧 Futowar da ammi zatayi a kitchen ne taga babu king babu tahee, tsayawa bin falon tayi da kallo kamar anan ne zata gansu,a tunaninta tahee ta koma daki ne shiyasa bata bita ba ta dauki wayar ta da niyar kiran king, tana kara wayan a kunnenta ta haye stair case din din falon.. A dan kwanciyar da tayi batasan lokacin da bacci ya dauketaba, wasu matasan yara tagani da akalla befi su bata shekaru uku ba, kyawawa dasu sai faman kuka suke , daga gefensu wani farin macijine shima tass dashi, kallan tahee dake gefe sukai sai suka kara fashewa da kuka , suna kuka suna biyota , cikin tsorata tahee ta fara jan baya, girgiza mata kai suka shigayi, cikin daddadan muryarsu “sun kashe mana farin cikin mu , sun cutar damu, bamuyi musu komai ba, laifin me mukai musu, nace laifin me mukai musu” suka karasa cikin data tsawa , firgita tahee tayi da yanayinsu, ganin sun tsaye ne yasa itama tsayawa,cikin rawar murya tahee ta fara magana “su..suwane ku, me nayi muku”, dariya suka saki tare da kara sakin wani saban kukan, “SIF,LOLA,”sai kuma farar magan ciki ta shafa can macijin nan” SUSAN”, tana gama fadar haka suka kara sakin kuka tare da bace bat kamar basu taba wanzuwa ba. A firgice tahee ta farka daga baccin da ya dauketa bakin ta dauke da addua , shafa wuyanta da ya dan rike tayi” me yasa nake yawan mafarkin masu sunannan,su wanene su”ganin babu me bata amsa yasata mikewa , kayan jikinta ta cire tare da shiga wanka , mintuna kadan tafito daga nan dakin, daya daga cikin abayoyin da ammi ta bata ta saka , gaban mudubin dake shake da kaya ta nufa,kurawa fuskarta ido tayi ganin irin sahirtaccen kyan da tayi a cikin kwanaki uku da tayi a cikin gidan , sanye take cikin red Egyptian abaya sai faman walwali stone din jiki ke dauka,asalin farin fatarta ta buzaye ta fito tass a jikinta, yayinda cikakken yalwataccen gashin kanta ya sauko har wajan kugunta, sosai bakin kwantaccen gashin goshinta ya kara kwantawa tare da dogon siririn hancinta , ba make up ne a fuskarta ba amma fadin haduwarta bata lokaci ne musamman dan karamin lips dinta da ya fito tass dashi kamar wacce ta saka janbaki,bakin kwalli ta saka da ya fito da farin kyawawan idanuwanta, sosai kwallin ya fito da asalin kwayar idanunta,cikakkiyar gashin girarta da dogayen eye lashes din idanuwanta su suka kara fito da ainahin kyawun fuskarta , ba ma a bociyar lip gloss bace shiyasa tabar dan karamun lebenta a haka, ribbon dinta ta dauka shima red colour tana kichiniyar daurashi, sosai ta jigata kafun ta daureshi sabida cikowarsa,mayafin abayarta ta dauka tare da yafashi saman kanta, red din takalmin ta ta saka , gaban mudubin ta kara komawa tare da karewa kanta kallo , murmushi ta sakar wa kanta tare da rufe fuska , “ ke din me kyau ce “kalmar da kullum taheer ke fada mata, murmushi kawai ta kara saki , tayi kewarsu sosai, hanyar fita daga dakin ta nufa bayan ta gama feshe jikinta da turaruka, Daidai lokacin da yan matan ke shigowa part din,amrah sai faman dingishi take haryanxu jikinta be dena tsami ba, sakin baki tayi ganin irin kyawun da tahee tayi, bama ita kadai ba hatta su ihsan duk sakin baki sukai suna binta da kallo, gaishe da su tayi babu Wanda ya amsa mata sai ihsan dake faman sakin murmushi, “tubarkallah Masha Allah , gaskiya ke kyakkyawa ce tahee”,sun kuyar da kai kawai tahee tayi tana wasa da yan yatsun hannunta, binta da kallo su sumayya sukai kowa yana hadiye abunda ke ransa, dogon tsaki amrah taja tare da karasa kan daya daga cikin kujerun falon, sosai take bakinci, dama ace Itace take da wannan kyawun, wani dogon tsaki ta kuma ja tare da daukar wayarta suma duk yan matan waje suka samu tare da zama ,ihsan ce ke kokarin magana ,jin sallamar zoya ne ya katse mata zancenta, inda Ihsan take ta nufa “aunty ihsan” rungumeta ihsan tayi “na’am my baby”kallan yarinyar da aka kira da baby tahee tayi , Itace dai yarinyar da ta gani tana bacci,”aunty ihsan wai ina da wata aunty tana ina “murmushi ihsan ta saki, “toh daman bazuwan kowa kikai ba sai na auntyn taki ko”dariya zoya tayi tana rufe fuskarta , itama murmushi ihsan din ta saki “oya kinganta” juya wa zoya tayi tare da kallan Wanda aka nuna mata, zaro fararan idanuwanta irin na king tayi, “aunty ihsan tana kyau, harta fini ma, amma yaya king dina ya fita” dariya ihsan ta saki kawai , sai alokacin tahee taga tsananin kamanninta da Wanda yake zuwa part Dinsu,murmushi kawai tahee ta sakar mata, itama murmushi zoyan ta saki “Aunt ya sunanki” taheera shine kadai abinda tahee tace,kara zaro ido zoya tayi “sunanki me dadi , ni kuma zoya yanxu Kema kinzama aunt dina kinji”girgiza mata kai tahee tayi sosai yarinyar tashiga ranta, duk wannan abun su sumayya na zaune suna kallan ikon Allah musamman amrah dake jin kamar ta samu wuka ta caccakawa tahee..shigowar ammi ne ya katsemata tunanin da ta shiga,”yaude yan mata na sai yanxu nake ganinku” ko wannansu murmushi ya saki sabanin sumayya da amrah da suka saki na yake “Aah ammi kinsan akwai school shiyasa “gyada musu kai ammi alamun gamsuwa kafin ta mike ,”yanxu dai ku Tashi ku kaiwa son abinci sai a dawo a yi hirar”, cikin firgita kowannansu ya zaro idanuwansa tare da furta YAYA KING….. Comment and share . 💖💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖💖 Duk karfin izzata Gidan Aunty Ya fita zakka Jini daya Sarki sameer Baby . MSS LEE💖.. ‎Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/JyvVuOvzYyF19np8UmFKV4 💖💖GIDAN AUNTY 💖💖 (a heart touching love story) Story & written By Mss Lee 💖 PAID BOOK littafin gidan aunty na kudine akan 300 kacal ne so har karshe zai biya ta wannan bank din 7041879581 opay Ayshatou Galadima , sai a turo shaidar biya ta wannan number 07041879581. Masu bukatar a tallata musu kasuwancin su , su tuntubeni cikin wannan number 07041879581. BOOK 1 📕 Free page 17🦋 Duk binsu da kallo ammi tayi ganin lokaci daya duk sun tsorata,suma duk sai sukai shiru ganin irin kallan da ammi ta bisu dashi, tahee da zoya ma duk tsayawa kallansu sukai, kamar daga sama cikin sauri amrah tace “zani ammi”jinjina mata kai ammi tayi tana sauke ajiyar zuciya, kafun ta karasa kitchen taji saukar muryar sumayya” Ammi nasan kayan sunyi yawa bari na temaka mata”ta karasa tare da dallawa amrah harara batare da ta bari ammi ta ganiba, ita tahee dariya suka bata ma, ko za a yankata aibazata je inda za a ballataba,jinjina mata kai ammi tayi tare da karasa shigewa cikin kitchen din, cikin sauri amrah ta jiyo tana kallanta,”mtswww na tsani shishshigi Wallahi “, kallan rainin wayo sumayya ta bita dashi, “zaki hanani taka ko ina na gidan mune”, dogon tsakin da firdausi taja ne ya katsesu “malamai kunbi kun ishemu inda gaske sansa kuke kuje kuce a aura muku shi mana kinbi kun cika mana kunne” tana gama fadar hakan ta mayar da headphone din kunnenta, ba Wanda ya kara cewa komai sai kallan banzan da suke bin junansu dashi , ihsan kam sharesu tayi tacigaba da game din da zoya ta sa musu , zuwa zaune kusan yan mintuna su asabe suka fito da kayan da za akai masa, har yan rigen rigen tashi ake tsakanin amrah da sumayya,amrah ce ta fara karasa tare da amsa kayan hannun asabe tana yatsina fuska,itama sumayya ragowar kayan ta dauka tana hararar amrah, Tashi tahee tayi da niyar komawa daki ammi ta tsayar da ita, “Kema daughter jirani na aikeki part din dada da na ummey”tana gama fadar hakan ta shige wani daki, mintuna kadan tafito dauke da wasu designers bag guda biyu, lokacin har su amrah sun bar part din, purple din ta nuna mata na dada ,red din kuma na ummey, mikewa zoya tayi “ammi zan bita”murmushi ammi ta sakar mata “toh daughter “kama hannun tahee zoya tayi, kowa na mamakin ganin lokaci daya ta sake da tahee, Kai tsaye part din dada suka fara zuwa Tun a hanya zoya Kezuba mata surutu falon yayi saura daga ihsan sai firdausi dake jin waka. Zaune dada take kasan lallausan carfet din falon ta, kamshin farfesun kayan cikin da akai mata sai faman tashin kamshi yake, cikin sallah tahee ta shigo falon tare da zoya,amsa sallamar dada tayi tana sakar masu murmushi” sai yanxu kika tuna dani tahura, ai nayi fushi “,sun kuyar da Kai tahee tayi cikin jin kunya” kiyi hakuri dada ba haka bane”, dan ta bile baki dada tayi “ gaskiya kam ki gyara, ko d’an hirar nan ki dunga zuwa kina tayani tunda su wadancan bankadaddun ba zuwa suke ba, sarakine kawai shima kullum cikin fada muke”, kallan ta zoya tayi”dada nifa , kinsan dai ina zuwa ko”,sakin baki dada tayi tana kallanta” kiji tsoran Allah, ni nayi mamakin ganin ki ma yau, ba dai kyau karya kinsani”, dariya zoya tayi tana rufe dan karamin bakinta, sakon da Ammi tabayar abata tahee ta mika mata “Allah sarki,kilishi ba dai mutunci ba ,duk gidan nan ita da hajiya suhaima ne masu kaunata sai sadauki”ta karasa zan Canta tana Shan farfesun ta, kallan tahee dake wasa da hannunta tayi”kinga zamu bata sai wani jin kunyata kike kamar wacce akace miki na zama sirikarki”, sosai dada da zoya suke janta hira tun bata sake ba har ta sake da su, sun dad’e suna hira kafin tahee tace zata kaiwa ummey sakonta,’kin barin ta dada tayi har saida taci farfesun da ta zuba musu zoya sai faman dariya take musu, da zata tafi ma sai da tayi wa dada alkawarin dawowa anjima sannan ta barta,tsakanin part din dada dana ummey ba nisa shiyasa basu dade ba suka karaso, sai bin ko ina tahee take da kallo ganin irin kyan da wajan yake dashi, zoya na gaba tahee na bayanta har suka shiga hadaddan kayataccen falon, sosai falon yake da girma da tsaruwa,ta ko ina kamshi ne ke tashi da sanyin Ac, ganin babu kowa a falon yasa tahee zama kan lallausan carfet din falon me shegen laushi da daukan ido, a guje zoya tashiga wata kofa kusan minti 5 sai gasu sunfi to ita da ummey dake sanye da black abaya sosai kyawun ta na larabawa ya bude shekarunta, wacce ta ganine yasata dan sakin murmushi, tare da zama kan daya daga cikin lallausan kujerun falon, gaishe da ita tahee tayi , yayinda ummey ta amsa mata cikin kulawa, haka kawai taji yarinyar ta kwanta mata arai sabida nutsuwarta, sakon ammi tahee na mika mata, wani murmushin ummey ta saki,”kice mata nagode sosai kuwa, bata gajiya “yadda ummey ta yabi ammin sai kaunar auntyn tata yakara shigarta sosai take santa,mikewa tayi daniyar tafiya ummey ta zaunar da ita “ ina kuma zaki, yanxu zamuyi lunch “ komawa tahee tayi ta zauna bazata iya yi Mata musuba sabida kunyarta da takeji, kallan ummey zoya tayi” ummey kingama a part din dada guduwa tasoyi “,girgiza mata kai ummey tayi cikin yaren larabci “bana hanaki surutu ba”, sun kuyar da Kai tayi”ana asf”ummey bata kulataba sai kallan tahee datayi “daughter taso muje muci abinci”ba yadda tahee ta iya dole ta mike ,tare suka nufa hadadden dining din dake falon,sosai wajan dinning ya hadu kasancewar wajanshi daban a cikin falon bayan antaka 3stairs, dakanta ummey tayi serving Dinsu , sosai kamshi girkin ya cika ko ina , nut spicy herb rice da Greek chicken kebab ummey ta zuba mata ,sai wani yan bowl masu shegen kyau da ta zuba mata salad da sauran dishes din, cikin glass cup kuwa strawberry milkshake ne aciki me shegen sanyi, sosai abincin ya birge tahee amma ta kasa moshi ,sai godiyar da tayi wa ummey kawai, itama ummey serving din su tayi ita da zoya, har sun fara cin abinci ganin sai wasa tahee take da spoon din hannunta ummey ta kalleta” daughter ya naga ba kyaci, ko abincin be miki bane”saurin girgiza mata kai tahee tayi “a’ah ummey yanxu zan faraci” ta fada tare da soma cin abincin a hankali , ummey batace komai dan Sarai ta gane kunyarta tahee takeji,suna cikin cin abincin kuwa daddad’an kamshin turaren da basuyi tsammani bane ya cika dodan hancinsu,da ma duk wani kamshi dake tashi a falon,kasa cigaba da cin abincin tahee tayi zuciyar ta sai faman bugu yake, naman da yake bakinta ma ta kasa taunawa sai faman tsotsanshin take, a hankali cikin daddadar muryashi yayi sallama , amsawa sukai baki daya banda tahee da ta kasa mosi, zoya sai kallansa take tanaso taje wajan sa amma ya Hana ta intanacin abinci,kan daya daga cikin kujerun falon ya zauna tare da crossing legs dinsa , binsa da Kallo ummey tayi , tayi kewarsa sosai da sosai amma a zahiri sai dauka hankalinta be kansa, cikin kasa kasa da murya zoya ta kalli ummey” ummey please ki cewa akhii yazo muci abinci , this once only please “kallan ta ummey tayi tare da dauke kanta,ganin hakan yasa zoya kara marairaicewa “please ummey”, girgiza Kai kawai ummey tayi har lokacin kuma tahee ta kasa ko kwakkwaran motsine, duk maganganin zoya yanajinta Sarai amma a zahiri sai ka dauka bayacikin falon,cikin larabci yaji saukar muryarta” taso muci abinci”,kamar bazai motsaba sai kuma ya tashi a hankali tare da nufar dining din ba tare da yace komai ba, Daidai inda yake shigowa tahee tana facing din sa, sarkewar da idanuwansu yayi te yasata shakewa da abincin da ke bakinta, sosai take tari dan ba hakaramun Shakewa tayi ba… *********Tun lokacin da suka baro part din ammi suke wa juna kallan kaskanci, daman ba shiri suke da junansu ba musamman da ya kasance suna san mutum d’aya , har suka karasa part dinsa ba Wanda yace wa kowa kala,duk da fargabar dake tattare dasu haka ko waccen su ta shiga falon dan bakantawa yar uwarta, bakowa a falon kasa ganin hakan yasa amrah nufar center kujerun tare da ajiye tray din hannunta, itama summy cikin gadara tanufi inda amrah ta ajje nata inama ta dora natan, ganin hakan yasa amrah saukar da na sumayya, itama sumayya sai abun ya bata haushi ta dan kwalar da na amrah, cikin kankanin lokacin suka fara ture turen abinci,a lokaci daya suka sa hannu tare da ture abinci junansu, take a wajan komai ya fadi kasa ya fashe Daidai lokacin da king ya fito daga wata kofa,bin ku waccen su yayi da rinannun idanuwansa , a part dinsa zasuyi masa wannan iskancin,kwata kwata basu ankara da shi a falon ba, amrah da tafi tsiwa ta tunkari sumayya , lokaci d’aya suka fara danbe da junansu, bece musu komai ba sai koma daki dayayi , cikin kankanin lokaci yafito hannunsa goye a bayansa sosai ransa ya baci, basu ankara ba sai saukar belt da sukaji, cikin bacin rai yake jibgarsu,”how dare you”, sosai suka firgita, sai faman hakuri suke bashi, sai da yasan sun daku sannan ya kyalesu, cikin nutsuwarsa ya zauna kan kujerar dake zaman mutum daya tare da crossing legs dinsa, ko wannansu zubewa yayi a kasa tare da yin kneeling, kowannansu na nadamar zuwa part din, kara had’e ransa yayi tare da kallan tulum abincin da suka bata,”it them all”, daga nan be kara cewa komai ba, sosai sumayya taji wani kukan na zuwan mata dan bata dade da cin abinci ba, amrah ma sai faman zare ido take hawaye na zubomata, belt din dake gefe ya dauka cikin sauri ko wannansu ya karasa inda suka zubar da amincin har da Wanda suka tattake, suna kuka suna tusa abiinci da suka zubar, ko wannansu ba yunwa sukejiba,sai tura tula abincin suke abaki,da Dinsu daya ko zuwa ne ya zube mutum zea iya tsugunnawa yasha sabida tsabtar wajan, saida suka cinye abincin tass ko wannansu na nishi sannan yasu suka gyara ko ina nafalon,yana zaune kan kujera saida ya tabbatar sun wahala sannan ya tashi ba tare da yace musu komai ba ya bar part din tare da nufar part din ummey. 🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧 🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧 BUNKURE Tun lokacin da suka dawo cikin dare Dije ke safa da marwa, sai tunanin yadda zata zuba wa su oumma magani abakin kofa take,ga bintalo dake kwance sai nishi take gabanta sai zafi yake mata,ta dade tsaye tana zagaye dakin kafun ta saki wani murmushin mugunta, samun waje tayi itama ta zauna ganin yadda bintalo ke ta faman nishi, ita kanta tasan da ita boka ya kusanta sai taji azaba balantana bintalo , amma duk da hakan bataji tayi danasanin yin hakan ba tunda Burinsu na daf da cika inyaso sai su koma wajan bokan ya basu abinda bintalo zayi anfani dashi takoma budurwarta.. Yau tunda sassafe Dije ta tashi ko alwala batayi ba bare tayi tunanin yin sallah , maganin da boka ya bata take faman jujjuyawa, kafin cikin sanda tafito daga cikin dakin su ta nufi nasu oumma , bakowa kuwa a wajan kasancewar Gari be dade da wayewa ba , kofar dakin su tahee tashiga bubbugawa sai da taji motsin an nufo kofar tayi saurin zuba maganin tare da komawa baya taheer ne ya bude kofar da niyar fitowa,jiyai an hankadashi ya koma baya ,ga wata yar iska da ta kara de wajan, ganin yana kokarin komawa Dije ta daka masa tsawa “ina kuke muna fukan Allah kufito”, ganin tana kokarin tara musu mutane ne yasasu fitowa taheer agaba oumma na biyedashi, ganin sun tsallaka garin maganin yasa dijen kyalkyalewa da dariya , binta sukai da kallo ganin irin dariyar da take kafun kuma ta yatsina fuska “inna tace ubanme kuke bakufito kunyi aikin da kuka saba ba, ga ruwa can babu kuje kudebo danshine aikinku”, tana gama maganar ta tabar Wajan sai faman sakin dariya take, duk binta da kallo sukai ganin irin dariyar da take kamar zautacciya, basu koma dakin ba suka fara ayyukansu cikin kankanin lokaci suka gama ,taheer ya tafi wajan garba mefaci da yake koyan gyara awajan sa , dakin yayi saura sai oumma ita kadai. 🦋🦋🦋🦋…… Ruwa oummey ta mika mata, ita da zoya sai faman sannu suke mata, amaimakon tarin ya lafa sai ya kara taso mata, tashi tayi cikin fitar hankali Sabida yadda ma’kogwaranta ya rike mata, a guje tayi hanyar barin wajan, kokarin dakatar da ita ummey tayi amma kwata kwata tafita hanyacinta, dausasan hannayensa yasa tare da janyota, kokarin fuskewa take haryanxu tarin yaki lafa mata , ganin hakan yasa oummey nufar daki da niyar dakko first aid box, hannu daya kawai yasa yana taffing din bayanta, yayinda yake hura mata iska a saman fuskarta, ya dau dogon lokaci yana hakan kafun ta fara sauke a jiyar zuciya nunfashin ta nadawo Daidai, ruwan da oummey tazuba mata ya nuna mata batare da ya kara kallan inda take ba, ruwan ta dauka tare da shanyewa tass tana sauke ajiyar zuciya Daidai lokacin da oummey ke dawowa wajan ganin tarin nata ya lafane yasata sauke ajiyar zuciya….,, Comment and share ✍️ LITTAFINA PAID BOOK NE AKAN 300 kacal , amma daga yau Tuesday zuwa ranar asabar duk Wanda zai biya 200 zai biya amaimakon 300 . Za’a biya kudin ta wannan asusun 7041879581 Opay, Ayshatou galadima sai a tura shaidar biya ta wannan number 07041879581. 💖💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖💖 _🦋Duk karfin izzata _🦋Gidan Aunty _🦋Sarki sameer _🦋Ya fita zakka _🦋Jini d’aya _🦋Baby MSS LEE💖💖✍️✍️ ‎Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/JyvVuOvzYyF19np8UmFKV4 💖💖GIDAN AUNTY💖💖 (a heart touching love story) Story &written By Mss Lee 💖 PAID BOOK PLX WAYANDA ZASU BIYA KUDINSU DAN ALLAH KUYI HAKURI ANSAMU KUSKURE BA OPAY BANE PALMPAY NE YANZU ZAN KARA RUBUTA MUKU DETAILS DIN 7041879581 Ayshatou galadima , palmpay . GIDAN AUNTY NA KUDINE AKAN 300KACAL ,ME BUKATAR SAMUN CIGABA HAR KARSHE ZAI BIYA KUDINSA TA WANNAN ASUSUN 7041879581 PalmPay Ayshatou galadima sai a turo da shaidar biya ta wannan number 07041879581. MASU SAN A TALLATA MUSU HAJARSU SUYI MUN MAGANA TA WANNAN NUMEBR 07041879581 BOOK 1 📕 Free page 18 🦋 Tunda yazauna akan daya daga cikin kujerun dining din bai kara motsawa ba har ummey tayi serving dinshi “thanks “ shine kadai abunda ya iya furtawa, ya dauka kusan mintuna 5 yana kallan abinci kafin ya dauki spoon din ya fara ci a hankali,tunda ya soma cin abincin tahee take satar kallansa ta kasan ido, duk abunda take yanaji aji kinsa ana kallansa,a bazata ya dago da kwayar idanunsa Daidai lokacin da tahee take dago da nata idanun, cikin sauri ta Dauke idanuwanta cikin yar yabar murya ta soma magana “Ummey nagode sosai,Allah ya kara arziki,bari na koma nasan ammi zata iya nemana” ta kare zancen nata tana sunkiyar dakai,”jinjina mata kai ummey tayi kafin ta mike “ am coming “kawai tace mata tare da barin wajan , har lokacin kan tahee na kasa ta kasa kwakkwaran motsi, ba’adau dogon lokaci ba ummey ta dawo da babbar Leda a hannunta, mikawa tahee ledar tayi” wannan naki ne daughter “,girgiza mata kai tahee tashiga yi, ta bude baki da niyar magana ummey ta dakatar da ita “I’m also your mom,karki karamin haka inna baki abu kinji”, cikin jin nauyinta tahee ta amsa mata tare da karbar ledar , sosai tayi wa ummey Godiya da addu’oi masu sanya zuciya tare da barin part din ,duk abun nan da suke king na zaune amma sam hankalinsa baya wajan sabida yadda yake jin wani irin turiri a jikinsa kamar ana hura masa huta,a hankali ya mike “I’m off “kawai yace batare da ya bari tace komai ba yabar part din, zoya sai faman tura karamin bakinta take yau be kulataba sosai , bin bayansa ummey tayi batare da tace komai ba, direct part dinsa ya koma cikin nutsuwarsa lokacin har an kara kyara wajan da su amrah suka bata,ko ina na falon sai tashin kamshi yake, cikin sassarfa ya shige wani daki, jijiyoyin kansa sun fito sunyi rudu rudu, sosai fuskarsa ta juye daga asalin farinta zuwa ja jawur, wani irin tururi ne yake taso masa kamar Wanda ake hurawa huta , gashin kansa da ya sha gyara ya fara batawa,tun yanayi a hankali har yazo ya fara fita hayyacinsa, gaban mudubin dakin ya karasa, a hankali ya fara fasa kayan gaban mudubin, duk abunda yaci kara dashi kawai ya ke dauka ya fasa , sosai ya farfasan kayan dakin, ganin hakan be masa ba yasashi dunkule hannunsa tare da bugashi da karfi akan madubin dakin, ji kake tasss madubin ya tarwatse gabaki Dayansa, kara yasaki tare da cigaba da buga hannunsa a jikin bango, sosai hannunsa ke Jini amma duk da hakan bai dena ba, wani show glass din da ya hango ya nufa Daidai lokacin da aka banko kofar da karfi, da sauri zaki ya karasa inda yake , hannunsa ya kai da niyar kama da king , be ankaraba yaji king yayi sama dashi tare da bugawa da kasa , sosai ya bugu a kafarsa amma duk da hakan bai hakura ba ganin inda yake nufane yasa zaki dakko wani allura a aljihunsa, a bazata ya tsirawa king a jijiyar hannunsa, juyo da rinannun idanunsa da suka matukar canza kala yayi tare da sauke su kan zaki, wata iriyar shaka yayi masa, sosai ya shakesa tare da bugasa da jikin bango, ko Karin kwacewa zaki yake daga Shakar da king yayi masa amma yakasa, ga idanuwansa da suka fara fito wa waje, cikin kankanin lokaci king ya fara sassauta rikon da yayi masa kafun a hankali ya fara lumshe idanuwansa da suka kada sukai ja sosai, ganin yana kokarin faduwa zaki yayi saurin taro hannunsa tare da kwantar dashi kan gadon, shafa wuyansa da king ya shake ya fara murzawa, saida nunfashin sa ya daidaita kafun ya fara gyara dakin , sosai ya gyara ko ina, wayanda suka faffashe ya waresu daban, ganin irin Jinin da king ke zubarwane yayi saurin futa daga dakin , cikin kankanin lokaci ya dawo dauke da first aid box a hannunsa, hannun king da ya ke futar da Jini yayi treating , yana matukar tausaya wa ogansa wannan yanayi da yake yawanshiga. *****A hankali tashiga falon dauke da sallama a bakinta, ammi dake zaune ne ta dago fuskarta da kyakkyawar murmushinta “daughter sai yanxu ake ganinki, karaso ciki mana kin tsaya kamar Mara gaskiya “karasa shigowa tahee tayi “ammi kiyi hakuri, su suka tsayar dani”, wani murmushin ta kara saki, “ai sunyi Daidai tunda bakya lekasu,nan gabama tattara miki kayanki zanyi ki koma can da kwata” ta karasa fada cikin zoyala, murmushi tahee ta saki da ya fito da ainahin gap teeth dinta dan siriri , ledar hannunta ta ajiyewa ammi, kallan ta ammi tayi tana san Karin bayani, cikin in ina ta fara magana “da..dama ummey ce ta bani banc….”katseta ammi tayi, shine kike dardar haka , “hope kin gode mata”jinjina mata kai tahee tayi, “good girl ,haka akeso anjima zan kara mata godiya , yanxu ki dauki kayan ki kaisu dakinki”dan murmushi tahee ta saki, “nagode sosai aunty” dan harara ammi kawai tayi mata ,harta juya zata tafi ammi ta tsayar da ita, tare da miko mata wayarta”nasan Kinyi kewar su yaya, gashinan ki kira ku gaisa “sosai farin cikin tahee ya kasa boyuwa har hakan yasa ammi farin ciki ganin ta cikin farin ciki, ta bude baki da niyar yi mata godiya ammi ta tsayar da ita”keje kiyi wayar ki, banasan wannan Yawan godiyar “tana gama fadar hakan ta nufi stair case , itama tahee murmushin jin dadi ta saki tare da nufar masaukinta da yanxu ya kasance kamar dakinta. 🫧🫧🫧🫧🫧 Tunda ta dawo daga bangaran king take kuka a daki, aunty sai faman lallashinta take akan ta fada mata abunda ke damun ta amma bata kulata ba sai faman kuka take, idanuwanta sunyi jajawur dasu, zabura tayi tare da mikewa , cikin kuna ta fara magana” Wallahi aunty na gaji, na gaji na fada miki hakurina ya kara gushewa , dole a auramun king ko yanaso ko bayaso, sannan a kawar mun da duk wanda yayi kokarin shiga gonata , bazan barsu ba, har ita yar iskar yarinyar can sai na kashe ta da hannuna, bama ita kadai ba , duk Wanda yayi kokarin kusantar inda yake bazan barsaba, aunty dole akoma Wayan boka , ko me za ai ma ayi inma dan dole zesa king yasoni yayi ni va damuwata bace”ta karasa maganar tare da sakin wani saban kukan,kallanta aunty tayi “ki kwantar da hankalinki yanxunnan zan kira yaya, aure kuwa kamar anyishine da kanki zaki dawo bawa mutanan gidan nan umarni bawaishi king kadai ba” ta na karasa zancenta ta bar dakin, wani lallausan murmushi amrah ta saki, “finally na zama mrs tahnoon, oh my god , bansan ya laushin faffadar kirjinka yake ba amma nasan ba karamun dadin kwanciya zanyi ba “ ta kare maganar tare da sakin dariya tana shiga bandaki…. 🫧🫧….. A bangaran sumayya kuwa bata shiga part din su direct ba sai da ta wanke fuskarta tare da sassaita fuskarta kamar ba abunda ya sameta, cikin takun yaukin ta , ta karasa shiga part Dinsu, kamar kuwa yadda tayi hasashe, ihsan da firdausi ne zaune a falo suka kallan wania series, kallansu sumayya tayi tana sakin murmushi da be kai zuciya ba, kallan ta firdausi tayi cikin tsokana “kaga matar yaya king bada kanki a sare, ina kika baro kishiyarki kuma yanxu “ jin maganarta ta karshene yasa sumayya Jan tsaki,”gatacan ta gudu sabida kar kuga shatin marukan fuskarta”ta karasa da sakin shegiyar dariya, binta sukai da kallo ganin irin shegiyar dariyar da take, ihsan dake kallanta ne ta dauke Kai tana sakin murmushi dan ta hango dan fashewar da bakinta yayi ga jikinta da ya dan ‘baci da abinci, basu kuma ce mata komai ba suka cigaba da kallan series dinsu hankali kwance. ➰➰➰➰➰➰➰➰➰ BUNKURE Tun dazu take safa da marwa tare da zirga zirga a tsakar gidan ko zataga oumma ta fito a haukace, amma har yanxu shiru,ga oumma sai faman aikin ta take hankali kwance ita da taheer da ya dawo tun dazu, ganin hakan yasa ta yafa mayafi tare da nufar gidan boka, “gafaran ku de, boka me share mana hawaye , abun alfaharinmu”wata mummunar dariya aka saki cikin wata kausashshiyar magana aka soma magana” shigo da baya da baya” kamar yadda aka umarceta kuwa hakan tayi sai faman kirari da take masa, cikin bukkar dake shegen wari da zarni. Yana zaune a Inda ya saba cikin Kazan tarsa, yana ganinta ya fara sakin dariya “nasan me ya kawoki ba sai kin maimaitaba, tun ba a je ko ina ba kun fara lallata aikin ku, kije ki dawo da yarinyar da kuka zo da ita kwanaki in ba haka ba kuna cikin tsaka me wuya, rayuwarki da ta yarki Zata mu nana tasu kuma ta daukaka” yana gama fadin haka ya kara babbaka dariya “kije , kije ki taho da yarinyarnan In ba haka ba aikinku na gab da lallacewa”da sauri Dije ta fito sai faman buga sauri taje jin zantikan boka, tana fita kuwa bokan nan ya kara babbakewa da dariya tare da sidar baki…. Comment and share ✍️ Kudin littafin dari uku ne kacal 300 me bukata zai biya kudinsa ta wannan asusun 7041879581 palmpay Ayshatou galadima sai a turo shaidar biya ta wannan number 07041879581. 💖💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖💖 Duk karfin izzata Gidan Aunty Ya fita zakka Jini daya Sarki sameer Baby . Mss Lee 💖✍️. ‎Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/GOZ7a2miBjZ4vUjRXdRdrA 💖💖GIDAN AUNTY💖💖 (a heart touching love story ) Story & written By Mss Lee 💖 PAID BOOK Duk me bukatar gidan aunty daga farko har karshe yamun magana ta wannan number 07041879581 ,bana da kira please . BOOK 1 بسم الله الرحمن الرحيم 💖💖……… Free Page 19 🦋 A hankali yake bude kyawawan idanuwansa da suka kada sukai ja, dafe goshinsa da ke tsananin sara masa yayi tare da mikewa zaune , bin dakin yake da kallo ta ko ina kafun ya dawo dashi kan hannunsa me ciwo, abubuwan da suka faru dazu ne suke dawo masa, sosai jijiyoyin kansa suka kara mikewa , ganin yana kokarin sawa kan sa wani ciwan kai ya mike tare da shiga toilet,ko kayan jikinsa be cire ba haka ya sakar wa kansu ruwan sanyi, sai faman sakin ajiyar zuciya yake, ya dade tsaye cikin ruwan kafun ya fito daga cikin toilet din , gashin kansa da ke faman d’igar da ruwa ya taba kafin yashiga wata door dake degensa , kusan awa daya da yan mintuna ya fito cikin sabuwar shigarsa, ash din Riga ce a jikinsa sai farin wandon da yasa, cikin sa sai faman tashin daddadan kamshin turaren sa yake, duk da yana yin da yake ciki ba karamin kyau yayi ba musamman gashin kansa da se faman kyalli yake , hatta ciwon hannunsa ya sake masa dressing kafin ya dauki wayoyinsa ya bar dakin , a kofar part din sa ya tarar da zaki sai faman kai kawo yake , Wanda ya ganine yasashi sakin ajiyar zuciya tun dazu yake tunanin ya koma ya duba sa amma yana shakkar shiga, ganin ya fito da kansa yasashi ajiyar zuciya , sau daya king ya kallesa tare da dauke kansa yana lumshe ido, wata hadaddiyar Ferrari la ferrari ya dakko sai faman kyalli take, ganin hakan yasa bodyguards dinsa matsowa, hannu daya kawai ya daga musu tare da nufar motar da zaki yayi Parking, cikin sauri daya daga cikin bodyguard dinnan ya bude masa kofar, bai ce komai ba sai shigewa dayayi, bayan ya kulle kofar sara masa sukai gabaki Dayan su kafun zaki ya tayar da motar tare da barin gidan gabaki daya , lokaci zuwa lokaci yakan dago idanuwansa ya kalli king da tun shigowarsa motar kansa yake a sunkuye kwata kwata ransa ba dadi , ya dago da niyar kara kallan sa yaci saukar muryarsa a bazata “ what happened “, ya gane me king ya ke nufi, be bata lokaci ba ya zayyane masa tun shigowarsa dakin har fitarsa saidai ya boye masa shakesan da yayi duk da yasan zai iya gane hakan.kara lumshe idanuwansa yayi sosai yake jin zuciyarsa wani irin amma a zahiri ko gezau bayayi har suka karasa katafaran asibitin Al_nahyan . ➰➰➰➰➰ Bata dau dogon lokaci ba , sai gata sun dawo ita da bintalo da sai faman ja mata Allah ya isa take a haka har suka kusa zuwa inda bukkar bokannan yake kafun tayi shiru, sai faman zare ido dake , dan ba karamun azaba Tasha ba a hannunsa, yana ganinsu ya fara babbaka dariya take da sudar baki kamar wani maye, jikinsa sai faman tashin wari yake .kara babbakewa da dariya yayi “kinsa mu duniya kamar yadda kuke so, burikanku zasu cika kamar yadda nayi muku alkawari, ayukanki da akai miki na baya bazasu taba fito wa fili ba hhhhhh” ya karasa tare da sakin sautin dariya Mara dadin ji,nannauyar ajiyar zuciya Dije ta sauke tana jin wani farincin na ratsata ta ko ina, bintalo na gefe jin ta take kowama zata iya takawa , sai faman washe baki take, kallansu bokan nan yayi tare da jefowa Dije wani magani, “ga wannan maganin kije ki zuba musu a duk inda kika san zasu taka, kada ki kuskura ki dawo nan wajen batare da kin cika aikin nan va,maza ki tafi”saurin daukar maganin Dije tayi sai faman Godiya take masa, tashi sukai da niyar tafiya ita da bintalo ya dakatar dasu”ke kadai zaki tafi, ita anan zaki barta sai kin dawo sai ku tafi a tare , Inba haka ba aikin da kuka fara zai karasa rugujewa da zarar kun isa wajan”, ko karin rike Mata hannu bintalo take bokannan ya daka masu tsawa” ku bace mun da gani “,hakuri Dije ta shiga bashi, bata tsaya sauraran bintalo ba tabar wajan ko tsoron halin da zata shiga batayi,tana fita bokan nan ya daka tsawa” zonan “ , jiki na rawa bintalo ta nufeshi, har kwalla ta fara tsoran ta karyace ze kuma tabata , bata karasa zancan nata ba taji razananniyar muryarsa” zauna anan “, inda ya nuna matane yasata sakin kuka , tsawar da ya daka matane yasa ba shiri ta zauna akan cinyarsa da ya bude,matseta yayi sosai a jikinsa yana shin shinarta, daga nan komai ya canza salo, sosai bintalo Tasha wuya a wajansa, ihu kawai take dan ji tayi azabar da taji yanxu yafi na wancan lokacin , kuka kawai take amma ko kezau bokannan beba sai da ya tabbatar ya biya bukatarsa sannan yayi jifa da ita har lokacin Dije bata dawo ba , ganin hakan yasa bintalo daukar hijabinta tare da rugawa a wuje sai a hanya tasaka hijabin sai faman tsine wa Dije take . 🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧 Zazzaune mutanan gida suke duka a falon dada , king ne kawai babu, zoya na gefan tahee yau sai faman hira take mata ita da ihsan , yan matan ma kowannansu na zazzaune a falon , amrah da sumayya sai faman harara juna suke batare da kowa ya hankalta dasu ba, musamman amrah da lokaci zuwa lokacin takan Kure tahee da kallo, ita kadai tasan abunda take rayawa akanta. Mikewa zoya tayi , aunty tahee please cakes dina zaki dakko mun kinji,jinjina mata kai tahee tayi tare da mikewa , kama hannunta zoya tayi suka soma tafiya, kallansu abeey yayi” yarana ina zuwa kuma “ sun kuyar da Kai tahee tayi “dama zoya tace zan dakko mata abune “, hararar zoya ummey tayi, kin kallanta zoya tayi tana buya bayan tahee, batace musu komai ba shima abeey da ammi murmushi kawai suke , su mamy kuwa kowannansu murmushin ya’ke yake saki, can dining su tahee suka nufa inda cakes din suke dayawa a ajje, kallanta tahee tayi “ wanne kikeso a ciki” wani me kalar chocolate ta nuna mata, daya daga cikin kankanin plate din tahee ta dauka tare da zuba mata chocolate cake din”, har tun juya da niyar komawa kuma sai tahee ta tsaya tare da komawa, cakes din ta zuba cikin kananun plates din tare da jerasu kan babban tray a haka harta karaso falon da suke zaune kowa sai binta yake da kallo, inda su dada suke zaune ta nufa tare da ajje musu tray din, babu Wanda be yi murmushi ba ganin abinda tayi, sosai ta burgesu musamman abeey da dada dake faman sakin murmushi, murmushin jin dadi uncel salim ya saki”mun gode sosai kuwa daughter , Allah yayi albarka “sosai kowa ya nuna jin dadin musamman dada da sai faman shi mata albarka take, abeey ne ya kalleta cikin zolaya yace “an kawo mana abun turawa daughter saura abunda sha”, murmushi ta saki tana sun kuyar da kanta , “tom bari na dakko muku” ta fada tana mikewa har lokacin zoya natare da ita kowa na mamakin sakewar da tayi da ita, murmushi amrah dake zaune tayi ganin ta kara komawa wajan dimming din, bata motsawa saida taga taheee ta futo da wani tray din cikin sa cups din glass ne sai juice din data dakko a kai tazo Daidai wjan da steps dinnan cikin Sauri amrah ta tashi da niyar wucewa sai ta bugar mata kafa batare da kowa ya lurasa sai aunty dake faman sakin murmushi ganin abinda amrah tayi,tray din hannun tahee ne ya fadi kafarsa sosai ta bugu jikin stairs din da kwalba ta fashe, mikewa kowa yayi ganin abinda ke faruwa, gadan Ganda kanta ya taho da niyar Dakar glass din, cikin sauri mutanan gidan suka nufeta , kara kawai tahee ta saki, Jin zata fada ga azaba da kafarta ke mata, ta sadakar faduwa kawai zatayi taji an riketa, sosai ta rike Wanda ya riketan, sai faman sakin kuka take, kafarta harta fara kumbura ga Jinin da yake fita a jikinta.. Ba yawa please . Comment and share. Mss Lee 💖✍️. ‎Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/GOZ7a2miBjZ4vUjRXdRdrA 💖💖GIDAN AUNTY 💖💖 (a heart touching love story) Story & written By Mss Lee 💖 PAID BOOK BOOK 1 Free page 20🦋 Ganin wanda ya riketan yasa ko wannansu sakin ajiyar zuciya sabanin amrah da aunty ta da suka fara farin ciki, hatta sumayya sai da ta tausaya mata duk da ba kaunarta take ba, dada sai faman sallallami take ganin Jinin da yake fita a kafar tata, ganin ta kasa taka kafar ne yasa ta daukar ta gaba dayanta tare da nufar 3 sitter din kujerun, har yanxu fuskarsa a hade ba ko digon dariya ga kuncin da zuciyar sa take tun dazu, hannu yasa da niyar zare kwalbar ta saki karan azaba tare da sakin wani saban kukan, inda kwalbar tashige ya kurawa ido, tabbas yasan in yace zai cire da karfi zai kara raunana mata ne , inda ya kunbura ya kalla da lumshash shun idanuwansa, a hankali ya kai hannunsa wajan tare da Mara matsawa a hankali, kara goce kafarta tayi jin wani saban azaba da take ji,kowa na cikin falon hankalinsa a tashe yake musamman ganin yadda kafar ta kunbura,”son kodai asibiti zamu wuce”cewar uncle musaddiq , lumshe idanuwansa yayi ,bai san takura da zata kaishi da yin magana , shurun da yayi ne yasa abeey kallansa” baka ce komai ba , in baza aje hospital ba sai a tafi clinic room ai ko ”, a fiske ya furta “no need abeey” kafun ya ciro wayarsa, wasu numbers ya danna tare da kaiwa kunnansa , bai jira anyi magana ba ya furta “ large first aid box” yana gama fadar hakan ya kashe wayar, dan gajeran murmushi ya saki , yasan tabbas akwia abunda yake damun gudan jininsa tun ba yau ba amma da muwar da ya gani yanxu ta nunka wacce ya saba gani, fatansa ya samu wacce zata gyara masa wannan murd’ad’d’en halin nasa. Kukan tahee ne ya fargar dashi tunanin da ya fada , kanta na cinyar ummey sai faman sannu suke mata,dada ma ganin ciwon kafarta na kokarin tashi yasata yin shiru, kara rintse idanuwansa yayi ganin tana kokarin sa masa ciwon kai, dabadan su abeey ba da ba abunda zai Hana be faffalla mata mari ba, ko cikakken munti biyar ba ai ba sai ga zaki da wani dogon first aid Box a hannunsa, king ya ajiyewa kafun ya gaishe da mutanan gidan, a hankali yake motsa hannunsa kafun ya bude first aid box din, abunda zaiyi anfani dasu kawai ya dauka tare da nufar kafarta, sosai take hawaye duk da ba a jin sautin kukan nata,kwalbar data shige mata kafa yake kokarin cirewa sabida zafi batasan lokacin da ta kama hannunsa ba tana rintse idanuwanta,fuskarta duk ta baci da hawaye , cikin sauri ya dago da idanuwansa jin shock din da yaji lokacin da hannunta ya taba fatarta, Sau daya ya kalleta tare da dauke kansa, be wani sha wani dogon wahala ba ya cire mata doguwar kwalbar ,bin kafarta data kunbura yayi da kallo kafun yayi mata dressing dinta,har yanxu akwai ragowar hawayen a fuskarta, kowa na falan sai faman sannu yake mata,sabanin aunty dake mata dan dole, amrah kuwa sai faman danasanin turatan dayi take ganin king ya tabata,a fakaice take goge kwallar ba’kin ciki, yana gama dressing din be jira cewar kowa ba ya far part din fuskarsa a had’e har yanxu. 🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧 Tunda Dije ta koma gida neman hanyar da zata kuma sawa su oumma maganin nan tayi, ganin kowa hankalinsa ba ya kanta tashige nan garansu sai faman ya tsine take kuwa, taci sa’a kuwa tunda ta shiga bataji motsin kowa ba harta sa kafa zata shiga ciki jin motsin ana taba ban daki yasata barbada maganin nan cikin sauri tare da barin wajan , Daidai taheer na fitowa daga ban daki, bin kofar da aka ‘bane yayi da kallo a tunaninsa oumma ce ,ganin babu Wanda yake shigo musu ban gare sai neman Futuna, kofar dakin nasu ya nufa,kamar Wanda aka rufewa baki ko sallama beyi ba yashiga dakin, jiyai kansa ya sara masa, duk dakin ya canza masa, waje ya samu ya zauna kamar Wanda aka tsira kuma ya mike, sosai yaji dakin ya fita aransa bazai iya zama ba, har ya taka kafarsa da niyar shiga inda oumma take sai kuma yayi saurin ja da baya jin kamar ya taka kaya, sosai yaji jikinsa ya daukan zafi , da yayi baya baya kuma sai yaji zafin na raguwa, da sauri ya fita daga dakin jin zafin na raguwa ne yasasa rugawa da gudu da barin gidan baki daya duk akan idan Dije da ta la’be a kan soro ganin yadda taheer ya fitone yasata sakin dariya, a zuciyar ta sai gode wa boka take . A daki kuwa kusan awan oumma d’aya sai faman zagaye take ganin har yanxu taheer be shigo ba, kofar toilet din ta nufa tare da kwankwasawa”taheer !! Taheer!! Taheer!!’ Ganin ta kirasa har sau uku be amsa ba yasata bude ban dakin, babu kowa a ciki sai ruwan dake nuna anyi anfani dashi, batayi tunanin komai ba ta koma ta zauna kusan yan mintuna ganin be dawo ba har lokacin yasa hankalin oumma ya fara tashi, hijabinta ta dauka da niyar lekasa, a tsakar gidan ta samu wasu daga yan gidan zazzaune kamar yadda yazama al’adarsu, Dije dake zaune har lokacin ne Tasaka shewa” za a tafi yawan tazubar Din da aka saba cikin dare” oumma bata kulataba tayi ficewarta dan tasan kota musu bayani ba saurara zasuyi ba, ganin hakan yasa yan tsakar gidan fara kuskus. Duk inda tasan zai iya zuwa taje har wajan da yake koyan faci taje amma bata tarar dashi ba , sosai hankalinta ya kara Tashi sanin da tai masa ba ya dare haka ko zeyi ma zai fada mata kafin yayi, bata koma gida ba taci gaba da duba shi duk inda taje sai tayi musu kwatancan sa ko sun gansa amma babu Wanda yace ya gansa, hankalinta ba karamun tashi ya karayi ba ganin har karfe Tara da yan mintuna ba taheer ba alamunsa, sosai ta bazama nemansa har tayi nisa sosai da gida, kuka oumma kawai take fatanta Allah ya tsare mata d’anta, tunanin ko ya koma gida yana nemanta shima yasata juyowa daniyar komawa gida, Daidai zata tsallaka titi wata had’ad’d’iyar bakar prado tai bal da ita, birki me Motar yaja cikin sauri tare da fitowa, shima na bayan motar be jira an bude masa ba ya bude da kansa cikin takun dattako ya karaso wajan, ganin yadda take zubar da Jini ga bakowa a wajan yasa ya kalli babban dansa dake gefensa, “khaleed kamata a sata a mota”,ba bata lokaci kuwa khaleed din da aka kira ya sata a mota ganin Jinin har yanxu be tsayaba yasa ba bata lokaci suka tada motar tare da barin Wajan batare da sun damu da sanin daga ina take ba, a Tunaninsa in ta samu lapiya sai tayi musu kwatance su dawo da ita. **ganin har karfe goma ta wuce ba taheer ba oumma yasa dije kara sakin wata dariyar mugun ta , bintalo ma dake zaginta ganin har lokacin nan basu dawoba yasa ta dena zagin nata sai faman washe hakwara suke burin su ya cika , a yan gidan kuwa babu Wanda ya damu da dawowarsu balantana suyi tunanin ko wani abune ya samesu , hajiya kaka tabawa kuwa tun safe tana daki sabida cikon kafarta da ya sata a gaba , duk abun nan da yake faruwa batasani ba , babu Wanda yayi tunanin sanar da ita, a ganinsu in oumma ta dawo daga barikinta sai tayi musu bayani.. 🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧 Tun da ta tashi daga bacci taji zuciyarta na faman tsinkewa ,burinta yau taji muryar su oumma dan sosai tayi kewarsu, kafarta da ta kara kumbura ta kalla kafun ta mike a hankali dakyar take taku har ta karasa ban daki, ta dau dogon lokaci a cikin bayin sabida ciwonta kafun ta fito daure da towel , komai cikin karfin hali take yinsa , pant din ta kawai ta saka tare da doguwar Riga batare da tasa bra a ciki ba,kadan ta shafa turarenta tare da komawa kan gadon, sosai kafarta ta kara kunbura dan basosai take takataba, kwankwasa kofar da akai ne yasata dago da fuskarta, ammi ce ta shigo dakin bayanta kuma asabe ce dauke da babban tray a hannunta, ya jiki tayi mata tare da ajje mata tray din abincin, cikin tausayawa ammi ta kalleta, “sannu daughter, ko asibiti zamu tafi ne” saurin girgiza mata kai tahee tayi, “ah ah ammi ba sai munje asibiti ba zai warke ai”, sosai ammi ta kalleta “Anya kuwa daughter kalli yadda kafarki ya kunbura, gaskiya asibiti zamu tafi “ta karasa tare mikewa , saurin kamo hannunta tahee tayi kwalla harta soma taran mata” Allah aunty da gaske nake miki ya dena , saura kadan kuma shima ba sai munje asibiti ba”, ta karasa kwallar na sakko mata, girgiza kai ammi tayi daman Tasan halinta da mugun tsoran asibiti, shiyasa bata kuma cewa komai ba ta gyada mata kanta”shikenan ga abincin kinan Kici kafin na kawo miki magani”, katuwar ajiyar zuciya tahee ta sauke tare da sakin mata guntun murmushi “insha Allahu aunty”, bata kuma ce mata komai ba ta kama hanya tare da barin dakin, ganin ta fita ne yasata mikewa a hankali tare da dakko abincin da aka kawo mata , sosai taci abinda sabida yunwar da takeji, ta dade zaune a Wajan har ta fidda ran shigowar ammi sai taji an bude kofar dakin, ammin ce kuwa ta shigo,har ta bude baki da niyar yin magana ya shigo dakin fuskarsa a hade taka ina kamshin turarasan yacika wajan,saurin sunkuyar da kanta kasa tayi tana hadiye abunda ya tarar mata a makoshi, lokaci d’aya taji wasu hawaye na tarar mata, kallansa ammi tayi “son duba mata kafar naga har yanxu kunburun be sace ba”, be motsa daga jinginar dayayi ba har yanxu , har ammi ta bude baki da niyar sake magana ya bude lumsassun idanuwansa tare da zubasu a kanta a hankali ya soma tafiya kafun ya karaso gaban gadon, bin kunburarriyar kafar yayi da kallo ganin tafi kunbura fiye da jiya kafun ya dauke idanuwansa ya maida kan ammi,a fiske ya furta “man zafi” cikin sauri ammi ta karasa gaban mirror din tare da miko masa man da ya tanbaya, TAHEE sai faman zare ido take, akan kujerar dake gefen gadon ya zauna, hannun doguwar rigarsa ya fara nannad’ewa tare da tsuke fuskarsa, ganin hakan yasa ta fara sakin kuka kasa kasa,a hankali ya daura hannunsa kan kafar tasa, Baisan lokacin da yayi saurin daukewa ba sabida shock din da yaji , kusan sakanni ya dauka kafun ya mayar da hannun nasa kan farar kafarta da yayi jajur Sabida kunbura,kuka tahee ta saka jin azabar da taji be kulataba sai ma rike kafar da yayi gam yana kara hade fuskar tasa, ganin yadda tahee take kukane yasa ammi saurin barin dakin dan tasan in tazauna zata iya hanashi matsa kafar bayan ita ta kirashi da kanta. Tsurawa kafar ido yayi kafun yasaki iska kadan ta bakinsa, a hankali ya soma matsa wajan da ya kunbura cikin kwarewa, kara tahee ta saki tare da kankame hannunsa, kafarta take san kwacewa amma ta kasa sabida yadda ya rike kafartata, wani kukan ta kara saki gabaki daya tafita daga hayyacinsa, be kulata ba sai ma kara matsa kafar da yayi yana shafa mata maganin, Daidai inda yafi kumbura ya dora hannunsa , wata karar tahee ta saki da iya Karfiinta na karshe ta ture hannunsa da ya kara fama ciwon, a maimakon ya saki hannun sai kujerar da yake zaune tayi baya yayinda tahee ta fado ta gaba, gaba d’ayansu suka fadi kasan, shi yana kasa ita kuma ta fado kansa, saurin rintse idanuwansa yayi tare da fusgar nunfashin dake kokarin kwace masa, kara lumshe idanuwansa yayi lokaci d’aya kuma ya ware idanuwansa jin saukar lips dinta akan nasa tare da saukar tsayayyun breast dinta a jikin sa adaidai lokacin da ake turo kofar dakin ……… (Tofaa 😂)….. Comment and share….. 07041879581…. MSS LEE 💖. ‎Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/GOZ7a2miBjZ4vUjRXdRdrA 💖💖GIDAN AUNTY💖💖 ( a heart touching love story) Story & written By Mss Lee 💖 PAID BOOK Littafin gidan aunty na kudine akan 300 kacal ,Sauran few pages na gama free pages dina , me bukatar ya karanta har karshe zai turo kudinsa ta wannan asusun 7041879581 palmpay Ayshatou galadima,sai a turo shaidar biya ta wannan number 07041879581. Nagode … BOOK 1 Free page 21 🦋 Ba kowa bace ta shigo dakin face amrah dake a zabure idanuwanta duk sun kunbura, a yadda ta gansu ne yasata fashewa da kuka tare da barin dakin cikin sauri, da Sauri ya bangaje tahee da batasan meke faruwa ba sabida yadda kafarta ke mata ciwo a kasa , har ya daga hannu da niyar tsinka mata mari sai kuma ya dungule hannu tare da rintse idanuwansa da suka kada sukai ja, kallo daya kawai yayi mata tare da ficewa a dakin ransa a bace , ko da ya fito falon be tarar da ammi ba hakan ya bashi damar fita daga part din gaba daya, ko part din ummey be karasa ba ya bar gidan . ****Da gudu amrah ta karasa part din aunty, bakowa a falon tai saurin shigewa daki, kuka ta fashe dashi sosai , kome ta gani sai tayi bal dashi, a haukace take fasa abunda taci karo dashi,”taheera “shine sunan da take nanatawa tana hawaye “wallahi sai na kashe ki,sai naga bayanki, shegiya tsinanniya ,wacece ke da zaki rungumeshi har dayi mishi kiss, wallahi sai na la’antaki bazan kara fadawa kowa bama da kaina zan kashe ki har lahira sannan na kashe banza”, bata karasa zancan nata ba aka tsitstsinka mata mari dama da hagu, a tsorace ta dago da idanuwanta a tunaninta aunty ce ta mare ta ganin ba kowa a dakin ta fara zazzare idanuwa, mafarkan da ta dungayi jiya da daddare ne ya fado mata a zuciya ,da kyar take iya hadiye abunda ke makoshinta, taku ta fara a hankali da niyar barin dakin,talewar da kafarta tayi ne yasa ba shiri ta bige kafar take da sakin azababban kuka, wani saukan marin da ta kuma jine yasa ba shiri ta mike tsaye ga azaba da kafarta kemata kamar wacce tayi targade.”ke “ taji wata razananniyar murya ta kirata,cikin rawar murya ta soma amsawa “naa…am, dan.. Allah kuyi… hakuri innayi muku lefi…”bata karasa maganar taba taji saukar bulala a bayanta,ihu ta soma “nashiga ukuna na lalace,dan Allah kuyi hakuri na tuba bazan sake ba “, kamar wayanda ake zugawa haka suka shiga laftarta saida suka ga ta daku sannan aka daka mata tsawa cikin muryar mata ,”ke, mike tsaye”azabure amrah ta mike fuskarta duk ta baci da majina ga kukan da Tasha “rufe mana baki”aka kara daka mata tsawa, hannayenta biyu tai saurin daurawa abakin mata sai faman waige waige take ga hawayen da ke zuba a fuskarta,”rawa zaki mana yanxun nan , duk rawar da muka saki,kuka kuskura kika fadi zaki gane kuranki, kinajina”, da sauri ta shiga daga kai har ynxu hannunta na kulle a bakinta,dariya muryoyin mace da na mijin suka saka kafun lokaci daya wajan yayi shiru,”maza yi mana rawar dan biri”ana gama fada mata haka aka jefo mata ayaba kuda d’aya, da sauri ta dauki ayabar ta fara tsalle kamar yadda dan biri keyi, fuskarta duk ta baci da hawaye ga guntun gashin ta da ya barbaje sai ta dawo kamar dan birin kuwa, tanayi tana kwantawa alokaci daya kuma tana kuka, sosai taji muryoyin nan guda biyu suna dariya kafin ta karajin wani sautin,”yi mana yadda mage take kuka”, kara fashewa da kuka amrah tayi kafun ta fara “meowwww meowww meowwww moewwww” ta nayi tana share fuskarta da ta baci, sosai suka wahalar da ita, iya rawan dabbobin kam har Wanda bata sansuva tayi rawarsu,ga kafarta dake tsananin yi mata ciwo kamar wacce ta goce a kashi. ********** kwance take kan lafiyanyan gadon dakin nata, hannu daya wayane a ciki yayin da Dayan hannun take rike da apple, waya take sai faman murmushi take saki ita kadai, turo kofar dakin da akai ne yasata dagowa,wacce ta ganine yasata mikewa zaune tare da kashe wayar, Momy kice kuma yau adakina, karasa shigowa wacce aka kira da momy tayi kafun ta samu waje ta zauna daga bakin gadon, “ko na komane”ta fada tana zubawa firdausi idanuwa, dan jinjina mata kai firdausi tayi tare da dage kafadun ta kadan,”akan wana dalili zan hanaki shigowa momy, naga yanxu bakya shigowane tun bayan tafiyar yaya haroon,ta bile baki kawai momy tayi kafun su canza hirar tasu zuwa wata,kallan ta firdausi tayi “amma momy ba kya tunanin waccan yarinyar da Gangan ta bige dan taga mutanan gidan suka tarai rayarta, kalli fa wai yau yaya king ne ya taba wata, ni ko hannunsa aka ce ya dora akan wata ai bazan yadda ba balantana wayancan shashashan da suke wahalar dakansu”,murmushi kawai momyn ta saki ba tare da tace komai ba dan Akan idanta amrah ta tura taheen, ganin momyn tata bata biye mata ba yasa share zancen suka fara zancan dan uwanta. 💖💖💖💖💖 Tunda ya bar gidan a guje zaki ya fara tuka Motan ganin yadda lokaci daya king din ya canza masa kamar wani zaki,a dake ya furta “my house “ya karasa maganar tasa tare lumshe idanuwansa, tafiya akai sosai me dan ta Zara daga banana island kafun suzo kofar wani hadadden building me shegen kyau, tundaga wajan gidan da glass akayi shi komai na cikin sa glass ne , cikin sauri sojojin dake bakin gate din suka wangale baban gate ganin me gayyane da kanshi ya zo, a Daidai parking lot zaki yayi parking inda sauran manyan motocin suke, yau be jira an bude mishi kofarba, yana fito wa ciki ya shiga cikin sassarfa, kofar dake kasa kawai ya bude ya shiga, sosai dakin da yashiga ya hadu, kayataccen falo ne a wajan babban gaske da yafi Wanda yashigo haduwa, Komai na cikinsa whites ne tunda ga kan labulayen dakin har kan lallausan carfet din dake shinfide fari tass dashi, ko ina nawajan tashin kamshi yake kamar ana anfani da shi kullum, kan daya daga cikin white sofa din ya zauna ko takalman kafarsa be cire ba, idanuwansa ya lumshe a hankali ,jijiyoyin kansa ne suka mike sosai , kyakkyawar farar fuskarsa tayi ja sosai, kara rintse idanuwansa yayi da karfin gaske ganin har yanxu yanajin tsayayyun breast dinta a jikinsa, sosai gashin jikinsa ya mike ,a zamube ya fara bal da duk abunda yaci karo dashi, zafi yake ji sosai a cikin Jikinsa,sosai gashin jikinsa ya kara tashi ji yake kamar tana jikin sa haryanzu, adduar ya fara cikin zuciyarsa, tsawan lokaci kafun wata nutsuwa ta fara saukar masa, sosai ya ke ajiyar zuciya ganin lokaci daya azababban zafin dake ratsashi ya tafi sai ma sanyi da yake danji a haka wani daddadan bacci ya dauke sa. *****har yanxu tana zaune a kasa tun lokacin da ya tunku data, kafarta hannunta rike da kafar tata, shigowar da akai ne yasata saurin dago da kanta?ganin su dada ne yasata sakin ajiyar zuciya, da sauri dada ta karaso inda take “me nake gani haka , tahura ya naganki a kasa duk zafin ciwon ne”, rasa me zatace mata tayi kawai sai ta gyada mata kai alamar a’ah, murmushi ta sakar mata a hankali kafun ta gaishe ta “ina kwana dada” girgiza kai dada tashiga yi “Allah sarki tahura,lapiya ta Lou, jiya da kyar nayi bacci sabida halin da kika shiga “wani murmushin ta kara saki kafun ta gaishe dasu abeey, shima cikin kulawa ya amsa mata tare da tanbayarta ya jikinta, sosai ta dan saki dasu Bayan ta gaisa da su uncle musaddiq da suka shigo daga baya, ganin sauran yan gidan ma suna zuwa yasa duk suka koma falon ammi,sosai kafarta tayi sauki dan tana dan takawa kadan kadan , afalon suka cigaba da hira har ummey ta shigo part din yau batare da zoya Suke ba sabida makarantar da tafi,a haka kowa na gidan ya shigo sabanin amrah , wunin ranar a part din ammi sukayi shi sosai suka nuna mata kulawa musamman ummey dake gefenta. 🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧 🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧 BUNKURE Da sassafe kaka ta bawa ta tashi yau kai tsaye dakin su oumma ta nufa , bubbuga kofar dakin ta shiga yi, jin shiru ba abude ba yasata kara bubbugawa “maryama kina ji ina kiranki shine zakimun uwarshegu ko, zaki nunamun ba’kin halin naku kenan ko, bazaki fito bane kina jina”, ganin yadda take faman buga kofar dakin su oumma ne yasa mutanan gidan fara taruwa,Dije dake labe tun lokacin da kaka tabawa ta fito yasata karasowa wajan,kallan kaka tabawa tayi tana kumshe dariyar dake cint kafun ta soma magana”inna ai maryama yanxu ta zama abinda ta zama “kallanta kaka tabawa tayi kamar ya bangane ba,”oh ai inna komai a filine , jiya agaban idanunmu tafita daga gidan nan , har kokarin zagin mu tai da muka yi kokarin tsayar da ita” sosai kaka taba ta kalleta “kina nufin tana yawan dare kenan”, tabe baki Dije tayi”ai kowa nanan sheda ne inna ki tanbayesu”, nan da nan yan gidan kowa ya fara tashi gulmar,babu me fadar alkairi akan oumma su taheer ganin yadda tafita tun jiya bata dawo ba, girgiza kai kawai kaka tabawa tayi rai a bace ta bar wajan” za tazo ta sameni ne duk gidan karuwanci da take zuwa”, da dad d’aya kowa ya fara watse wa ganin hakan yasa cikin sauri Dije ta shige dakin harda taka rawa, kallan ta bintalo tayi,”ya naga sai faman washe baki kike kamar wata tababbiya”a maimakon ta tsawa tar mata akan kalaman ta sai ta kuma kyalkyalewa da dariya, nan da nan ta kwashe duk abunda ya faru ta sanar wa bintalo, itama bintalon sosai tayi farinciki ganin burinta na Auran babban mutum zai cika ,wani shegen murmushi ta saki a zuciyar ta kuwa fadi take “lallai ma Dije baki da hankali,ai wallahi kafin nayi Auran nan sai na ci duniyata da tsinke yanda na fara jin dadin abinnan da boka Yayi mun ,wallahi yanxu na fara anjima ma sai na koma wajan sa dan ya mallake mun duk Wanda yace zai takuramun, ciki kuwa har dake dan ke kika koyamun”,duk wannan maganganun nata cikin zuciyar ta take kafun lokaci daya ta saki wata yar iskar dariya da ita kadai ta san ma’anarta. Comment and share LITTAFIN GIDAN AUNTY NA KUDINE AKAN 300 kacal zaku biya kudin ku ta wannan asusun 7041879581 palm pay ayshatou galadima , sai a turo shaidar biya ta wannan number 07041879581. Saura few pages na gama sakin free pages dina . MASU COMMENT INA GODIYA SOSAI DA SOSAI , I HEART ❤️ YOU ALL ✍️. MSS LEE 💖✍️ ‎Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/GOZ7a2miBjZ4vUjRXdRdrA 💖💖GIDAN AUNTY 💖💖 (a heart touching love story) Story & written By Mss Lee 💖 PAID BOOK NA KUSA KAMMALA FREE PAGES DINA Mesan KARANTA GIDAN AUNTY DAGA FARKO ZUWA KARSHE ZAI IYA BIYAN KUDINSA TA WANNAN ASUSUN 7041879581 palm pay ayshatou galadima sai a turo shaidar biya ta wanna number 07041879581 BOOK 1 Free page 22 and 23 🦋 A kwana a tashi ba wuya wajan Allah SWT, yau kusan sati biyu kenan da batan su oumma , Tsawan wannan lokaci babu Wanda ya damu da yasan inda suke ,hatta kaka ta bawa da ta share zancen, cikin wannan lokacin sosai bintalo ta fara bin maza ,ganin hankalin yan gidan su nasan komawa kanta ta koma wajan bokannan da mahaifiyarta Ke zuwa, gaba daya ta mallakesu ko dare zatayi babu me tanbayarta dalili, sosai ta baci da kazamin rayuwarnan, Dije kuwa kullum cikin farin ciki take idan bintalo ta Kawo mata kudi ko damuwa da inda ta ke samo kudin batayi,burinta ya cika tun lokacin da oumma tabar gidan,yanxu burinta ta kai bintalo can birni wajan da tahee take sannan itama tasa taheen ta shiga duniya. 🫧🫧🫧🫧🫧 A tsawan kwana kinnan sosai wata shakuwa me karfi tashiga tsakanin zoya da tahee, kullum in ta dawo daga makaranta zaki ganta wajan tahee tana fada mata abunda aka koya musu, yawancin lokuta suna part din ummey ko part din dada da yanxu take kulawa da ita sosai, ta bangaran yan gidan ma haka, momy tana sake mata sosai sabanin mamy da aunty,musamman aunty da ke nuna mata kyautata mata agaban yan gidan , abayansu kuma taita zaginta, ihsan da firdausi ma sosai suka sake mata a yan kwanakin nan, amrah da sumayya ne ko kallo basu isheta ba,ganin hakan yasa itama bata sake musu fuska. Cikin yan kwanakin nan sosai tayi kewar su oumma tanaso tacewa aunty ta kira mata su amma bata san ta yadda zata tanbaye taba. Yau ma tunda ta tashi da kewar su oumma ta tashi,so take kawai taji muryarsu sabida mummunan mafarkin da tayi a kansu, sai faman zagaye take a daki tana tunanin ta yadda zata tanbaye ammi , ganin bata da wata mafitane yasa ta mikewa tare da fitowa falo a hankali kamar Mara gaskiya, Daidai tana fito wa shi kuma yana shigowa ciki, kamewa tahee tayi wajan tare da rintse idanuwanta,yau sati biyu kenan rabanta da ta gansa, sosai ya kara yi mata kyau kamar kullum kara masa shi ake , a hankali tayi kokarin bude idanuwanta jin yadda zuciyarta ke bugawa da sauri sauri ga kamshin turaransa da ya cika mata hanci, da gyar ta karasa bude idanuwannanta, Ganin baya wajan kamar yadda tayi tunani yasata sakin ajiyar zuciya, ta juya daniyar komawa kenan idanuwanta suka sauka a kansa, kyawawan fararan idanuwanta ta zuba masa duk da yadda zuciyarta ke faman bugawa, sosai shigarsa tayi mata kyau musamman gyaran gashinsa da ya tubke sai faman kyalli yake ,sak ya fito a balaraben sa dan Inba Hausa yayi baza ka taba tunanin yasan Menene kalmar ba, wayace a hannunsa sai faman dannawa yake cikin kwanciyar hankali,fuskarsa kwata kwata ba annuri kamar Wanda yayi rashin lapiya ga kafar sa da yayi crossing lokaci zuwa lokaci yana motsata, a hankali ya motsa pink lips dinsa kamar me sanyin magana sai kuma ya fasa tare da datse lips din nasa,tunda ta Kafe shi da ido ko motsi batayi sam ta manta ma agaban watake, a hankali ya dago da idanuwansa karaf suka hade da nata,bata janye idanuwan ba sai ma sarkewa da idanuwansu sukai cikin na junansu , bata farga da shirmen da take ba sai jin saukar tsawar sa tayi, sosai ta razana juyawa tayi daniyar guduwa ta ji saukar muryarsa “if you dare “ya karasa kamar be san yin magana , cak tahee ta Tsaya kamar me shirin sakin kuka , ahankali take juyo da fuskarta da ta dukar sosai take jin kunyar abunda tayi ,zuciyarta sai faman bugawa take da sauri da sauri kamar wacce tayi gudu. Lokaci zuwa lokaci take dago da idanta ganin hankalinsa baya kanta cikin rawar murya ta soma magana “ ina wu..ni”, be amsa mata ba haryanxu idanuwansa na kan wayarsa, kara dukar dakai tayi tana wasa da kasan hijabin jikinta,”ina wuni” ta kara gaishesa cikin rawar murya, yanxun ma be amsa mata , ganin hakan itama ta shareshi tana dan turo dan mitsitsin bakinta, dauke gansa yayi daka kallan dan mitsitsin bakin da ta motsa kafin cikin kasa kasa da murya ya furta “coffee”,kara turo dan mitsitsin bakin nata tayi gaba kafin ta nufi hanyar kitchen din , cikin kan kanin lokaci ta kammala hada coffee din azuciyarta sai faman mitar Shan coffee din nasa take ,”coffee ,coffee”, kafun kuma ta sassaita nutsuwarta ta fito falon, a yadda ta barsa a haka tazo ta samesan yana zaune da kafarsa da yayi crossing, duk da yadda zuciyarta ke rawa hakan be sa nutsuwarta fito wa ba” gashi” ta mika masa tana dan russunawa, be fi sakon biyu ba yasaka hannunsa kan dan karamin tray din da ta miko masa, sipping ya fara a hankali,ta kasan ido tahee take satar kallansa “shi wannan kullum cikin Shan coffee ko abincin arziki be ci,nan gaba inaji sai coffee dinnan ya fito masa a jiki”, ita kadai take hirar ta a zuciya,kamar yasan me take tattaunawa ya dago da idanuwansa ,saurin sunkuyar dakanta kasa tayi, dan ta bile bakinsa yayi kafin ya soma magana” get me something to eat “,da sauri ta dago idanuwanta jin abinda yace , bata ce komai ba sai kitchen da ta nufa, a ba’kin gas ta tsaya tana karewa kitchen din kallo,tu nani ta fara me zata dora masa Mara sauki , ganin tana bata lokaci ne yasa ta nufar babbar freezer din kitchen, manyan tilapia fish ta dakko guda biyu , cikin kwarewa ta gyara kifin kafun ta feraye Irish potatoes dinta, bata dau dogon lokaci ba ta kammala hada grilled fish dinta ,da yaji sauce din Dankali sai faman tashin kamshi yake, kunun ayan da ta ga ammi ta jera a fridge ta dakko tare da zubawa cikin madaidai cin jug, cikin lokaci kankanin ta kammala hada abincin , kafin ta fito falo zuciyarta sai bugawa take, hanyanxun yana zaune a falon sabanin dazu yanzu ya dan jingida da jikin kujeran, sunkuyar da Kai tayi kasa,”ga abincin”, be ce mata komai ma sai gyara zamansa da yayi kafun ya bude plate din, sosai yadda aka kawata abincin ya burgeshi amma a zahiri sai ma tabe bakinsa da yayi, be kulata ba ya faraci a hankali , 3 spoon yayi kawai tare da Shan kunun ayar Daidai lokacin da ake shigowa part din da sallama , ammi ce ta fara shigowa bayanta kuma su amrah ne , duk tsayawa sukai cirko cirko a tsaye kafun ammi ta karaso falon cikin mamaki,”son Yaushe ka shigo”kamar bazea ce komai ba sai kuma ya bude baki “am looking for u”, murmushi ta sakar masa “sorry son ina tare da su ummey ne”, lumshe mata idanuwansa yayi, cikin rawar murya su amrah suka bude baki tare da gaishesa, ba Wanda ya amsawa a cikin su saima cigaba da tsakurar abincin da yayi kamar Wanda aka saka dole , kallan tahee dake tsaye ammi tayi, “daughter yanaganki a tsaye ke kuma , kisa mu waje ki zauna mana “ dan dago da kanta tayi kadan tare da satar kallansa ,be dena abunda yake ba hakan yasata sauke a jiyar zuciya kadan ,cikin rarrabewar murya ta furta “daman ina gyara dakine “, jinjina mata kai ammi tayi ba tare da tace komai ba ganin hakan tai saurin nufar dakin ta, da kallo su amrah suka bita dashi ko wannansu na mamakin ganinta a falon. 🫧🫧🫧🫧 KANO UMC ZHAHIR HOSPITAL Wata kyakkyawar yarinyace me matsakaicin kyau zaune kan daya daga cikin kujerun da aka ajje a cikin dakin asibitin, sosai ta zubawa Wanda ke kwance akan gadon ido, kafun ta fara share hawa yan da suka tarar mata a ido, cikin sanyin murya ta soma magana “Allah sarki ummu na ,Allah ya jikanki da rahma”, bata kammala zancan nata ba ta fashe da kuma me cikin rai, tana cikin kukan ne tashi alamun taba kofa , cikin sauri ta goge hawayen da suke zubo mata kafun ta kakalo murmushi a fuskarta, sallama nurse din tayi mata kafin maza wani matashin saurayi ya shigo dakin bayan sa kuma wani kamilllan dattijo ne , drip din da ya kare nurse din ta cire ,cikin girmamawa ta kalli dattijon nan, “insha Allahu ta kusa farkawa a ko Wana irin lokaci “,jinjina mata kai dattijon yayi kafun matashin saurayin gefensa yayi mata godiya, murmushi ta sakar masa tare da barin dakin bayan ta kwashe abin drip din data cire, kujerar da budurwarnan take Kai ta mike tare da sakar wa dattijon nan murmushi “Daddy ga waje ka zauna”, binta yayi da kallo kafun ya sakar mata murmushi shima “nagode daughter” cikin takun dattakon ya karasa tare da zama kan kujerar, kallanta matashin saurayin nayi tare da hararar ta cikin tsokana yace “daman nasan yanxu ba kya sona , harda dauke kai kamar ma bakisan dani ba”dariya matashiyar yarinyar tayi “sorry yaya khaleed , kaima kasan inayinka over “, wani hararar ya je famata “daga baya kenan”, yana gama fadar Haka suka karasa gaban gadon ,cikin tausaya wa yarinyar ta kalli mahaifin nata” daddy Yaushe zata farka” wani murmushin dattijon ya saki, kafun ya bude bakinsa yayi magana hannun ta ya soma motsawa kadan kadan,kafin a hankali ta fara bude idanuwanta ganin hasken da ya haska mata ido sosai ne yasata rintse idanuwan kafun ta kuma budewa hawaye na bin fuskarta, duk zuba mata ido sukai suna kallanta,”taheer!!taheera”, shine sunan da kawai take nana tawa , kallan matashiyar budurwar mahaifinta yayi kafun ya kira sunanta “zahra” cikin Sauri ta amsa da “na’am dady” kallan matar yayi kafun ya kalleta, “tai maka mata”, yanxun ma cikin sauri ta amsa “toh dady”, karasawa inda take tayi ganin ta na kokarin tashi zauna ne yasa ta temaka mata,tunda ta zauna bata ce komai ba sai bin yan dakin da tayi da kallo,duk abunda ya farune ya shiga dawo mata kai cikin sauri ta zabura “taheer “ shine sunan da ta fada tana kokarin sakkowa kasa, kallan ta mutuminnan yayi kafun ya dauke idanuwansa,cikin sanyin murya ya furta “kiyi hakuri kici abinci tukunna inyaso sai muyi magana “katsetsi oumma tayi tana fashewa da kuka “bazan iya ba, ina taheer dina yake , inaso na san halin da yake ciki, su wanene ku, me nake yi a nan wajan”, kallanta mutumin yayi kafun ya soma magana cikin kamilalliyar muryarsa “ kiyi hakuri ,mune wayanda muka kadeki sati biyu da suka wuce , sannan muka kawo ki asibiti sai yanxu Allah yasa kika farka”, waro idanuwa oumma tayi “sati biyu” ta fada cikin rawar murya “kuna nufin satina biyu a asibitin “gyada mata kai mutumin kawai yayi, fashewa da kuka oumma tayi “shikenan na rasashi “, ta kara fashewa da wani saban kukan, kallan ta mutuminnan yayi idan bazaki damu ba zaki iya sanar damu wacece ke , me ya fito dake cikin dare ,naji kina maganar sunan wani da alama wani makusancinki kike Nema “, girgiza kai oumma tayi har yanxu hawayen basu dena zubaba,”zan baku labari na, sannan ina rokon ku da kumayar dani inda kuka dakko ni sabida na nemo yarona”, jinjina mata kai dattijon yayi, yayinda mace da namijin suka samu waje suka zauna suma suna binta da kallo ganin yadda take kuka ,” sunana maryam ni haifaffiyar buzuwace, ‘ya’yana biyu taheer da taheera,mijina Allah yayi masa rasuwa…………..” tundaga farkon labarin ta zuwa karshe sai da oumma ta basu tare da dalilinta na fitowa waje,sosai zahra take kuka shima saurayin da aka kira da khaleed shima sai da ya goge kwalla a idanuwansa , sosai suka tausaya mata, gyaran murya mutuminnan yayi “tabbas labarinki abin a tausaya miki ne, Insha Allahu shima yaron naki zamu binciko miki shi da yar dar Allah, amma kafin nan zansa a baki sallama sai muce gidana gabaki daya in kin yadda damu, ni sunana Alhaji kabeer mai zamani, ga babban d’ana sunansa khaleed , sai autata sunanta zahra, mahaifiyarsu kuma Allah yayi mata rasuwa, ina fatan zaki amince”, shiru oumma tayi kamar me tunani ganin bata da wani zabine yasa ta amince musu ko ba komai zuciyarta ta kwanta da su”, sosai zahra dake sharan kwalla yin farin ciki har hakan ya bawa mahaifinta mamaki, ba a dau dogon lokaci ba aka rubuta musu sallama ganin wanda ya bada umarnin sallamar, cikin kankanin lokaci suka kama hanyar nasarawa G.R.A dake Garin kano. 🫧🫧🫧🫧🫧 Sosai ya ci abincin yanaci yana babbata fuskarsa, yan matan falon sai faman satar kallansa suke ta kasn ido ganin ammi na zaune a falon , kallo daya yayi musu duk suka mike , kallansu ammi tayi, “sai ina kuma “ cikin sauri suka hada baki “ammi daman zamu je wajan abeey ne “ kallan ammi kawai tayi tare da girgiza kai , suna gita ta kallesa tare da hararansa “ka kyauta da ka koresu” bai ce komai ba lumshe mata idanuwa da yayi tare da mike wa cikin takunsa ya zauna akan kujerar da take ,kansa ya dora akan kafadunta yana lumshe idanuwa, murmushi tasaki tare da zura hannunta cikin lallausan gashin kansa tana masa tausa a hankali “ka rage hade fuskarta nan son , kullum inasan ganinka cikin farinciki kamar yadda nasan ka a baya banasan rashin fara’arka” ta karashe zance cikin karyewar murya , saurin mikewa yayi tare da kamo hannunta,”am sorry ammi na” daga nan bai kara cewa komai ba sai mama tsa mata hannun da yake a hankali, ganin bayasan hirarne yasa ta dakko wani zancen daban, sun dau dogon lokaci suna hirar duk da rabin hirar ammi ce keyi kafin yayi mata sallama, direct part din ummey ya nufa , be wani jima a ciki ba sabida be saba zama ba yana gaisheta ya fito daga part din tare da nufar part dinsa. 🫧🫧🫧🫧🫧 YOLA “Aikin ku na kan gangara, baku da dogon lokaci wajan cikar ragowar burinku, watanni biyu ne sukai muku saura ku tabbata kun kawo jininsa,karkuyi saken da Jini biyu zasu hadu waje daya, kuna gab da tafka babban kuskure musamman idan Jini biyun nan suka kasance a waje daya “, a fusace take musu magana cikin bacin rai kafin ta dora “kun tabka babban kuskure kuyi kaggawar gyara abinda kuke kokarin batawa, baku da dogon lokaci kamar yadda kuka kawar da dan uwansa, shima ya zama muku dole Inba haka ba za kuyi kuka da kanku”tana kammala zan centa ta bace bat kamar bata taba wanzuwa ba. Ba Wanda bai razana da maganganun ta ba duk da kasancewar fuskokinsu a rufe yake babu alamar da za a gane mu su wanene, wani mutumine ya soma magana “tabbas yanxu ne ya kamata mu fara aiwatar da shirin mu, duniya ta muce dole mu mulki mutanan duniyar, dukiyar NAHYAN mallakinmuce dole mu karar da tsantsan su”…… Comment and share Mss Lee 💖💖 Masu comment ina Godiya….. ‎Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/GOZ7a2miBjZ4vUjRXdRdrA 💖💖GIDAN AUNTY 💖💖 ( a heart touching love story ) Story & written By Mss Lee 💖 PAID BOOK Mea bukatar complete din gidan aunty yayimun magana ta wannan number 07041879581 BOOK 1 Free page 24 and 25 🦋 “Tabbas yanxune ya kamata mu cika kudirin mu”,cewar d’aya daga cikin su me sanye da jajayan kaya a jikinta, gabaki d’ayan su maida hankalin su sukai kan daya daga cikinsu wacce take kishingide tun d’azu bata motsaba, tashi tsaye tayi tana kurban wani dan abu cikin wani Kofi me kayatarwa,duk da ba a iya ganin ko wacece cikin kausashshiyar murya ta soma magana rai a bace “bazan taba laminta ba , ginin da na soma tunda dad’ewa babu wani hamshakin daya isa ya rushe munshi”,duk hada baki suwai wajan cewa “tabbas maganar ki gaskiya ce abar kauna “,suka gamawa suka fara surutunsu cikin wani yare kafin su had’a kofunansu waje d’aya alamaun cheers . ****** KANO Kasantuwar akwai tazara tsakanin UMC da nasarawa hakan yasa saida suka danyi doguwar tafiya kafun su karaso Layin nasu, Kai tsaye daya daga cikin manyan gidajen dake Layin khaleed ya nufa,yayinda Alhaji kabeer yake zaune a dayan side din, zahra da oumma suna baya,tun bayan shigarta motar ta dukar dakanta kasa ,lokaci zuwa lokaci tana share hawayen da ke taran mata a ido, duk akan idon Alhaji kabeer da lokaci zuwa lokaci ya kan kalleta ta mudi bi, itama zahra nagefe ta zuba tagumi sosai take jin tausayin oumma da labarin ta, “ya kamannin taheer da taheeran suke “,tunda yan biyu ne zanzo naga kamanninsu nasan za’ayi kyawawa musamman yadda oummansu take da kyawu itama kamar wata balarabiya, tunanin da ke yi mata yawo akai kenan har su ka karaso gidan bata sani ba, horn khaleed yayi wani katan soja dake ganin gate din gidan ya bude tare da sara musu, babban gida ne Wanda ya hadu iya haduwa da kayan alatu komai na more rayuwa akwai a gidan, parking khaleed yayi a parking space,tare da futo wa ya bude wa mahaifinsa kofa,itama zahran futowa tayi har lokacin oumma kanta na sunkuye batasan an tsaya ba sai da zahra ta tabata,dago da kyawawan idanuwanta da suka sauya tayi tare da sakar wa zahra guntun murmushi,”nagode “,murmushi zahra tayi mata tare da bude mata kofar, fitowa oumma tayi tana bin katan gidan da kallo kafun ta sunkuyar da kanta ganin ta hada ido da Wanda yace mata sunansa Alhaji kabeer,murmushin manya Alhaji kabeer ya saki kafun yace “Bismillah “ya karasa da nufar inda zai sadashi da cikin gidan,”oumma Bismillah “ cewar khaleed da ke gefen ta ,saurin dago da idanuwanta tayi jin sunan da ya kirata da shi kafun ta soma tafiya cikin sanyin jiki zahra na binsu a baya, a cikin kyataccan falon gidan suka tsaya,sosai falon ya hadu iya haduwa, ba wani tarkacene aciki ba amma sosai ya hadu,kallan zahra Alhaji kabeer yayi “daughter kaita masauki ta dan huta” sosai zahra ta murmusa “to dady”kafun ta dauki magun mugun oumma ,kallan oumma tayi haryanxu da murmushin nan akan fuskarta” oumma bari na kaiki dakin da zaki hutu”,itama oumma dan murmushi ta sakarmata tana jinjina karamci irin na mutanan gidan duk da kallo daya zaka musu kasan masu arziki ne amma basu wulakanta taba. Wani dan corridor suka mi’ka kadan ya Kawosu wasu ‘kofofi dake kallan na junansu,kofar karshe zahra ta bude mata , babban d’a kine a wajan,gadone me fadi sai wardrobe ,komai na set d’in gado a kwai a dakin brown colour , murmushi zahra ta sakar mata “oumma Bismillah “ jinjina mata kai oumma tayi , a sanyaye ta furta “nagode”. 🫧🫧🫧🫧🫧🫧 Sanye take cikin maroon d’in abaya A shape,kayan sosai ya fito da shape din jikinta, cikakken gashin kanta ya fito sosai ta gefe gefen kanta da ya kwanta,kwance take kan 3 sitter din falon ammi tana bacci cikin kwanciyar hankali, zoya ce ta shigo falon itama cikin shigar ta sa’banin tahee ita kananan kayane a jikinta bink colour Riga da wando, kanta sanye da pink din hula itama gashin go shin ta sosai ya fito, gashin d’awisun da ta zo nunawa tahee take ta faman wasa dashi harta nufa hanyar dakin taheen sai kuma ta jiyo ganin ta kwance tana bacci, saurin rufe bakinta tayi tana dariya kasa kasa kafun ta salallabo a hankali ta nufi inda taheen take, gashin d’awisun ta dauka ta somayiwa tahee tafiyar tsutsa a tafin kafarta, motsa kafan kadan tahee tayi kafun ta gyara wanciyarta, kara sa mata gashin zoya tayi nan ma motsa kafar tata tayi a hankali tana ya mutsa fuska,ganin hakan yasa zoya cigaba da sa mata d’awisun, cikin sauri tahee ta farka har dan kwalinta na zamewa, sosai zoya ta fashe da dariya ganin yadda tahee ta ‘bata fuskarta, itama tahee ganin zoya yasa ta mike da niyar kamota,sauri kaucewa zoya tayi tana dariya, ganin hakan yasa tahee binta da sauri, gudu zoya ta sa tana dariya tare da komawa bayan kujera, ganin hakan yasa tahee binta da gudu har dankwalin kanta ya faduwa kasa, bata damu da faduwar da yayi ba ta cigaba da bin zoya da niyar kamota ,itama zoyan ta ki bari ta kamota sai zillewa take tana mata dariya, ganin hakan yasa tahee sakin duk karfin ta ta biyo zoya da ta nufi hanyar fita da gudu gashin kanta sai faman lilo yake a bayanta, karan da tayi da abune yasata yin baya baya kamar zata fadi , batasan lokacin da ta fado kansa ba,sai daddad’an kamshin da ya cika mata hanci , da sauri ta wayo idanuwanta waje “na shiga uku ni tahee, kullum sai kinyi lefi”, saurin sunkuyar da kanta kasa tayi tare da soma wasa da yan yatsunka, dai dai ta bude baki da niyar yin magana taji an capko dogon gashin kanta me shegen sanshi da daukar ido, tanbayar da ya jefo Matane yasata zare ido “ are you a non-Muslim da zakiyi Karin gashi a kanki” ya karasa zancen nasa da sauke idanuwanka kan gashin nata, sosai sukai masa dadin a tafin hannu musamman yadda suke kyalli amma a zahiri sai kara hade fuskarsa da yayi, “ni ban kara komai ba” ta fada muryarta na rawa rawa kamar me tsoran wani abu, kara damke kan nata yayi a hannunsa da karfi,sosai taji zafin yadda ya damki gashin nata ,bata san lokacin da dora hannunta kan nasa ba tana rintse idanuwanta, hawaye ne suka fara zubo mata cikin rawar murya ta soma magana “ka..kayi hakuri”, pink lips dinta dake motsawa a hankali ya zubawa idanuwa kusan minti daya ganin tana kokarin bude idanuwan yayi sauri hankad’a ta tafadi a kasa, amaimakon yashiga cikin falon sai ya bar falon gabaki daya, bin bayansa da kallo tahee tayi tana hararar iska ,”arrogant kawai “ta fada cikin sauri kafun ta toshe bakin ta gudun kar wani yaji, mikewa tayi a hankali “ke kuma zan kamakii, sabida kisan halin kayanki shiyasa kika gudu ni kuma aka Huce akai na thank god be ganki ba”ta karasa maganar tana sakin murmushi kasa kasa tare da shafa gashin kanta “wai gashin doki”wani murmushin ta saki tunano kalamansa, lokaci d’aya kuma duk fara’ar fuskarta ta dauke tuno oumma da taheer da tayi, yau kusan sati biyu basuyi waya ba, tunanin hakan yasa ta fara tunanin yadda zata yi Waja da su wajan ammi. 4:30 ammi ce ta shigo falon bakin ta dauke da sallama , har yanxu murmushin fuskarta be ‘boyuba, kallan tahee da ke zaune ita kadai tayi, “sorry daughter na barki ke kadai “, itama murmushi tahee ta sakar mata “sannu da zuwa ammi”saida ta zauna tukun na ta amsa mata, mikewa tahee tayi da nufar kitchen bata dade ba ta fito dauke da kara min tray, lemone a ciki masu sanyi gefe guda kuma kayan fruit ne cikin wa ni dan bwol, glass cup din dake kai tahee ta dauka da niyar zuba mata kunun ayar ammi tayi saurin Girgiza mata kai “no daughter ban dade da Shan ruwana ba , bani fruit din nasha “, bata ce komai ba ta ajje cup din tare da miko mata fruit din “nagode “shine abunda tace, murmushi tahee ta sakar mata batare da ta ce komai ba , kallan ta ammi tayi sau daya kafun ta dauki banana , sai da ta kammala cin bananar kafun ta dauki wayanta, dan danne danne tayi kafun ta dora wayan a kunne ,kusan sau uku tana hakan kafun ta kalli tahee, “yau 3 days ina gwada number yaya amma bata shiga, kiyi hakuri zan kara gwada zuwa anjima sai ku gaisa nasan kinyi kewarsu “sauke ajiyar zuciya tahee tayi lokaci daya jikinta yayi sanyi dan tunda tazo ammi take kyautata mata kamar yar cikin da ta haifa, kauda maganar tayi ta hanyar sa wata jiran, sun dade suna hiran su cikin raha lokaci zuwa lokaci ammi na kara wayarta a kunne , kiran sallahn magariba ne ya tayar dasu ,ita ta nufi sama tahee Kuma ta nufi dakin ta, tun jiya take jin wani iri kamar period dinta zaizo, koda tayo alwala sai da ta duba tukunna kafun ta fito, sallahr magariba tayi bata tashi a Wajan ba har saida tayi sallahr isha bayan karatun alkuranin datayi, yau akan daddumar bacci ya dauke ta lokacin da take karatun azkar dinta. Karfe 6:10am na safe tahee ta farka sabida ciwon maran da ta soma , sosai kafarta ta dama take mata ciwo, ban daki ta shiga domin gyara jikin ta ganin har yanxu period din be zo bane yasata yin sallah, kafarta sai faman ciwo take , asabe ce ta kwankwasa kofar daman shigo tahee ta bata sai faman yatsina fuska take, breakfast ta kawo mata yau ko hirar da suke batai ba bayan ta amsa tayi kwanciyar ta , fita asabe tayi bayan ta mata sallama tana mamakin ta, ganin ta fitane yasa tahee mikewa tare da nufar abincin, kadan tashi ta tashi aguje ta nufi ban daki, duk abunda taci saida ta amayo dashi, jikinta sosai yake mata ciwo, wanka tayi da kyar tare da saka dogon hijabi Sabida sanyin da ta keji,ko da ta fito falo bata tarar da kowa ba , ganin hakan yasa itama bata zauna ba ta nufi part din dada, tunda ta doshi hanyar zuciyar ta ke tsinkewa bata san dalilin hakan ba, ta dora kafar da niyar shiga kenan taji kukan ammi” BA’ASAN INDA SUKE BA ,DAGA ITA HAR TAHEER DIN ANNE MESU AN RASA ABUNKURE “ kalaman da suka shiga kunnanta kenan, bata san lokacin da ta kwalla kara da karfin gaske ba , kafarta da ke step na biyar ya gurde ta fado kasa Tim kanta ya bugu da jikin step din, sosai Jini ya barke mata akasan ta , kanta da ya buguma sosai yake zubar da jini , da gudun gaske sukayo kanta , tun lokacin da ta saki karar nan, ganin tahee Baje a kasan yasa hankulansu kara tashi kowa fatan da yake Allah yasa bataji me ake tattaunawa ba, wani saban kuka ammi ta saki, kaka ma ganin halin da tahee take yasata sakin nata kukan “shikenan ta faru ta kare”abunda dada ke fadan fada kenan , ummey da abeey sukai dauriyar dagowa, ganin yadda jikinta yasaki ne yasa dada sakin wani kukan” wai ina sadaukine ba bokan turai bane yazo ya dubamana amanar Allah”kallan abey dada tayi cikin fada fada ta soma magana me kuke jirane ku kira sadauki ya dubata duk kunbi kun tsare ta da itanuwa “ ta kara zancen nata da kallon su uncle salim da suka karaso suda iyalansu, sosai hankalin yan gidan ya tashi, “amma dada me zea hana a tafi asibiti kawai tunda nasan ba za a rasa king acan va” kwallar da ta zubo mata ta share maza zayed dauketa mu tafi asibitin kuma sai ku biyo bayan mu “da Sauri ammi ta mike ganin harsun nufi mota, baya ummey tashiga sai dada da tahee dake tsakiyarsu ba alamun rai , yayin da gaban motan kuma dr zayed ne da kansa zai tuka motar ammi na gefan sa, da gudun gaske suka bar gidan ganin haka yasa motoci biyu na sojoji bin bayansu, suma sauran yan gidan shiga mota sukai da bin bayansu sojoji ne take musu, aunty kawai aka bari datace ta zata taso amrah sai su taho tare, ba Wanda yace mata kala har suka taho asibitin. Koda su dada suka shigo asibitin da gudu sojojin nan suka zagayesu kowa duk Wanda yazo wucewa sai ya kallesu, kara dialing number king abey yayi akaro na ba adadi, yanxu ma kara kiran yayi not rechable Daidai lokacin da wasu manyan likitocin asibitin suka karaso da gadon daukar mara lapiya , inda take abeey ya nuna musu, daya daga cikin doctor dinne ya bude motar da niyar dakko ta, Daidai lokacin da motar king ta sharo da gudun gaske,Kai tsaye inda su abey suke zaki ya nufa, suna ganinsa suka sauke a jiyar zuciya yau da kanshi ya bude kofar ya fito tare da nufarsu,ganin su gabaki d’aya a wajan ne yasa ya maida hankali kan abeey” what happen “ ya fada a kasalance, kasa yi masa magana sukai sai bayan Botar da suke nuna masa , a hankali ya bude kofar wacce ya ganine yasa shi dan ja baya kafun cikin azama ya shige cikin kotar, ganin yadda jikinta ya baci da jinine yasashi rintse ido kafin ya dauke ka kamar yar baby a jikinsa , ko gadon da aka dakko be kalla ba ya nufa da ita ciki cikin sassafa, kowa na wajan binsa da kallo yayi amma ba bakin magana hatta ma’aikatan wajan kowa sai satar kallonsa suke, sau daya ya kalli doctor din gefansa , “doctor halima” yana gama fadar Hakan ya shige lifter tare da barin yan gidan , direct office dinsa ya nufa da ita duk jikinsa shima ya baci, cikin few minutes sai ga wata doctor mace tazo lokacin da yake mata dressing din ciwon kan nata, sau daya ya kalleta be ce mata komai ba ya dauki tahee yanxun ma cikin sassarfa ya nufi wani door da ita, itama ma doctor haliman cikin Sauri tabi bayansa bayan ta kirawo wasu nurse, duk ragowar likitoci tsayawa sukai suna tsoran shiga theatre din ganin be nemesu ba kowa ya koma gaban aikinshi, kusan hour daya da rabi ya fito daga cikin theater din, kallansa abeey yayi cikin damuwa “ yaya jikin nata “ duk zuba masa ido yan gidan sukai suna jiran amsarta sa “ sai ta farka tukunna” ya karashe zancan nasa da kallon ammi da yake jin kukanta har zuciya, muryar abeey ce ta Katse masa tunaninsa” zamu iya shiga” jin jina masa kai king Kawai yayi sabida ciwon kan da yake ji, wani baban daki aka kaisu inda aka kwantar da ita, sosai Wajan yake da girma kamar ba asibiti ba, kwance take kan gadon sanye da kayan marasa lapiya , kanta nannade da bandage sai drip din da aka sa mata, sosai fuskarta tayi fiyau da ita ga wani kyau data kara jikin ta kamar babu Jini a jiki, ko wannansu kallanta yake cikin tausaya wa hatta summy da bata santa saida ta zubar mata da hawaye, sun dade zaune a asibitin har wjan 2 na rana kafun abeey ya bada umarnin su koma gida yayi saura daga dada sai ummey saishi ,uncle Saleem da uncle musaddiq kuma suka tafi tare dasu, shima abeey office din king ya nufa cikin rashin sa’a ya tarar da office din a kulle, ganin ana kiraye Kirayen sallane Ysa abeey ya nufi masallaci koda aka idar da sallan be koma ciki ba sai da yayi la’asar. Koda ya koma cikin tashin hankali ya samesu ganin yadda tahee ta cire drip din hannunta sai kuka take , duk Wanda yayi yun kurin tabata sai ta buga masa wani abu, gabaki d’aya doctor din tsaya wa sukai suka su ammi kuka suka saka ganin halin da take ciki, zuyawa yayi da niyar kiran king sai gashi yashigo cikin wata shigar daban,bin dakin yayi da kallo ganin yadda ya baci, daya daga cikin nurse dince ta nufi tahee da niyar rigeta bayan ta ga Shigowar king , bata Ankara ba tahee ta buga mata abu ka , kara ta saki tana ja da baya , kuka tahee ta saka “karku tabani, su wanane ku, kumaini wajan dady na” sukenan kalaman da take, umarni king ya bawa doctors din su fice da ido kafun a hankali cikin takunsa ya nufi wajan gadon, cikin rufewar ido tahee ta dauki abu daniyar kwala masa sai kuma ta tsaya da kukan da take ta fara dariya kamar wata zautacciya, be ankara ba sai ji yayi ta rungumesa “daddy na “ shine kadai abunda tace tare da kudun dune king da ko motsi yakasa bayan rungumesan da tayi. Comment and share 😌✍️ Mss Lee 💖 ‎Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/GOZ7a2miBjZ4vUjRXdRdrA 💖💖GIDAN AUNTY💖💖 (a heart touching love story) Story & written By Mss Lee 💖 PAID BOOK MESAN COMPLETE DIN GIDAN AUNTY YAYI MUN MAGANA TA WANNAN NUMBER 07041879581. BOOK 1 LAST FREE PAGE Free Page 26 and 27 🦋 “Dady na “ ta kara kira sunansa idanuwanta na zubar da hawaye, salati dada ta saki “ Innalillahi wa inna ilaihi raji’una, Allahumma a jirni fi musu bati , tahura wanene kuma dady”, dada ta fada da nufar inda tahee take , wani kukan tahee ta saka “karku tabani bana so, ku dena ta bani su wanene ku”, gabaki d’aya su abeey kasa motsi sukai sai Innalillahi da suke maimaitawa tun dasu , ammi ko tsayuwa ta kasa sai waje ta samu ta zauna ta cigaba da kukan da yazo mata.nunfashi king ya saki yana kara hade rai tare da kokarin banbareta daga jikinsa, kamar wacce ake karawa karfi haka ta kara kudun duneshi tana sakin kuka, nunfashi king ya saki me zafi , besan lokacin da ya data mata tsawa ba, sosai ta razana da tsawar da ya daka mata, hatta abeey sai da suka kallesa, kuka tahee ta fashe dashi, cikin futar hayyaci tayi kofa da niyar fita,ko karin riketa abeey yake ,wata karar tasaki “banaso banaso banaso, shima dady bayasona ,Nima banasan kowa” ta kara fashewa da kuka , cikin ta da ya murya ne yasata sakin kara tana durkushewa, a wajan tare da sakin wani saban marayan kuka tana dafe cikinta,taki bari kowa ya ta’bata sai kuka take, lumshe idanuwansa king yayi kafun a hankali ya tako inda take, jada baya ta soma tana girgiza masa kai tare da sakin wani saban kukan, be dena bin nata ba har ta jin gida da jikin bangon, tsayawa dada tayi zani a hannu tana kallan ikon Allah ,tun bayan kuka data sa mata ta buya bayan ummey dake tsaye itama , a hankali ya tsugunna a wajan kansa har ya fara sara masa, gefe tayi da kanta tana cigaba da kukanta ga ciwon cikin dake nukur kusarta sai faman rike ciki take, “kalle ni” ya furta a hankali yana binta da idanuwa,dan mitsitsin bakinta ta tabule kamar me shirin yin kuka “shhhhhh” yace mata , shirun kuwa tayi har yanxu taki dago da kanta sai hawayen dake biyo fuskarta,” me akai miki kike kuka “ ya furta a fusge kamar bashi ba, bakin ta bude daniyar kuka ya kara dakatar da ita “bana san kuka” kukai kuwa gaya dena “basu ne ba suna ta bani nace kuma sudena banaso, Kai ma bakasona ka koreni” ta karasa maganar tata tana turo dan karamin bakin ta kamar wata yar yarinya “ Wannan yarinyar Anya ba aljana bace “ ya fada a zuciyarsa, amma sabida buguwar datayi aka yasa bece mata komai ba, “toh shikenan mun dena , suma bazasu ta baki ba”, da sauri ta kallesa tana share hawayen fuskar tata, “dady da gaske kake”,girgiza mata kai yayi kawai ba tare da yace mata komai ba, da sauri ta fada jikinsa tana kara dukun kune shi” dady banasan su na tabani kaji”,be ce komai ba sai lips dinsa da ya datse “ dady ! You killed me “ ya fada a zuciyar sa , ganin ta fara kuka kasa kasa ne yasa ya kalleta, be auneba ta fashe masa da kuka, “dady cikina, cikina” ta fada tana rike cikin nata, kasan cewar yasan dalilin ciwon cikin nata yasa be ce komai ba , ya dauketa tare da barin dakin a hannunsa kamar wata yar baby, bin bayansu da kallo su dada sukai, kafun ta sauke a jiyar zuciya, kallan su ummey tayi” mude mun shiga uku, yanxu kenan sadauki yazama Baban ta, ku kalla fa , wai bata san muba “ babu Wanda ya kulata harta gama surutun ta kowa da abunda yake sa’kawa a ransa. 🫧🫧🫧🫧🫧 Tunda aunty ta koma part din ta tsabar murna bata bata sanar wa da amrah da bata falon komai va, yayarta da ta haifi amrah ta kirawo, “yar uwa rabun jiki, Al bishirinki “ banji amsar da aka bata ba sai dariyar da aunty ta saka “uhmmm tsinanniyar can ai ta mutu, yanxu aikin mu zaizo cikin sauki daman “ gabaki d’aya yadda ta ga taheen sai da ta sanar wa yar uwar tata suna yi suna dariyar farin ciki , tana gama wayar tata takirawo aminiyarta, bata jira komai ba ta nufi dakinta cikin kasa kasa da murya ta sanar da ita Abunda ke faruwa,banji me akace mata ba Amma sosai ta nutsu tana saurarar kawar tata , wata dariyar mugunta aunty ta Saki “ bar shashashu , a tunaninsa ina yin duk wannan abun sabida su, Kema kinsan wacece ni , ina gama an fani dasu zan zubar dasu”, kara kyalkyalewa tayi da dariya, sun dan jima suna wayan kafun ta kashe kiran. ******* wayace kare a kunnan amrah , sosai ta nutsu tana sauraran abunda ake ce mata, fuskarta dauke da yalwataccen murmushi, ta dauki dogon lokaci taba wayan kafun ta kashe , dariya ta saki sosai saida tayi me Isarta sannan ta tsaya “ Lalle yarinya da dani zakice zaki taka, cikin sauki na gama dake saura aunty inma in ta kammala mun aikin” ta karashe zan can nata tana sakin dariyar mugunta harda rike ciki, ta dade a hakan sai ga aunty ta shigo itama dakin, duk abunda ya farun saida auntyn ta sanar da ita, nunawa tayi kamar batasan anyi ba, ta kara shiga cikin murna dan tabbatar da zancan mahaifiyarta, tsabar murna har wata kwarya kwaryan liyafa suka hadawa kansu ko tunanin su duba a asibiti ba sayi , duk a tunaninsu ta mutu. 🫧🫧🫧🫧 Direct office dinsa ya nufa da ita sai faman kuka take masa, baice komai ba sai ajjeta da yayi cikin wani bedroom me kamar daki komai nacikin daki akwai a ciki ga wasu na urori dake dakin kamar ba cikin asibiti ba, murkususun ta cigaba dayi tana kiran “dady !! Dady”, kallanta yayi yana lumshe idanuwansa da suka fara gajiya sabida ciwon kan da yake ,kafun ya karaso a hankali inda take, wasu injection ya hada tare da nufar inda take, tana ganin injection dinnan ta kara sakin wani saban kukan, tana girgiza masa kai “banaso , banaso” be kulata ba har ya karaso wajan , a guje ta mike duk da ciwon dake cinta ta saka kafa zata gudu, taku daya yayi ya rike damtsen hannunta, kuka ta saka masa tana kokarin kwace hannunta da ya rike , ganin allurar hannunsa yasa taci gaba da kokarin guduwan, sosai tasaka iya karfinta tana san kwace wa , kwakkwaran riko daya yayi mata tare da zaunar da ita kan gadon har lokacin kuka take, alkuran ya ajje abayansa tare da kallonta “na fasa to, yimun shiru”, kallan hannunsa tayi ganin babu alluran yasa lokaci d’aya kukan nata ya tafi, jingina tayi da jikinsa tana dan turo baki , be ce mata komai ba har kusan minti daya tana wasa da abun rigarta, allurar da taji ya tsira matane yasata sakin kara da niyar mikewa, sosai ya riketa kwakkwaran motsi ta kasa harsaida ya kammala allurar tasa, hade rai yayi sosai kamar bashi ba , cikin kausashshiyar murya ya firta “yi mun shiru” tsit kuwa kukan nata ya dauke sai karamin lips dinta da take turo masa , tsawan lokaci suna a haka lokaci zuwa lokaci yakan dago da idanuwansa , jim kadan ya kara dago da idanuwan nasa yaga ta fara bacci, ajiyar zuciya ya sauke kadan” am dead “ ya furta kawai kafun ya dakko wasu na ura, sosai yayi bincike akan ta bayan Wanda yayi mata lokacin dressing , nunfashi ya fesar ganin kiran abeey, be dau dogon lokaci ba ya dauki kiran ,”kana ina “shine kadai abunda abeey yace masa, “office “ king ya furta tare da lumshe idanuwansa kamar abeey na kallonsa, ko minti biyar cikakkiya abeey beyi ba ya shigo office din, inda tahee take kwance ya kalla tare da girgiza kansa, “me ya sameta” ya kara tanbayar king din” she lost her memory abeey” da sauri abeey ya kallesa tare da furta Innalillahi wa inna ilaihi rajiun, ganin hakan yasa king ya mike daga inda yake tare da nufar abeey din,” please abeey karka tayar min da hankali , kasan ba lapiya Kake dashi ba please abeey “, zuciyarsa abeey ya dafa tare da dafe kan sa, rikosa sosai king yayi duk da yanayin tashin hankalin da ya shiga amma a fuska ba alamun hakan, dago da idanuwansa abeey yayi da suka fara jaa alamun ciwon sa zai tashi,”kayi mun alkawari guda daya” kallansa king yayi da lumsassun idanuwansa, sosai abeey ya kara dafe zuciyarsa “KAMUN ALKAWARI ZAKA AURETA YAU DINNAN “. Comment and share ✍️ Mss Lee 💖 Alhamdulillah yau na kawo karshen free pages dina , mea san cigaba da gidan aunty zai turo kudin sa fa wnn asusun 7041879581 palm pay Ayshatou galadima , sai a turo shaidar biya ta wannan number 07041879581. Masu comment ina Godiya 💖🫶. 💖💖GIDAN AUNTY💖💖 ( a heart touching love story) Story & written By Mss Lee 💖 PAID BOOK MAISAN COMPLETE DIN GIDAN AUNTY YAYI MUN MAGANA TA WANNAN NUMBER 07041879581 BOOK 1 BONUS PAGE 28 and 29🦋 2 page ne na hade muku🫶. “IMPOSSIBLE “cewar king da idanuwansa suka fara canza launi,cikin bacin rai, be bari abeey ya kara magana ba cikin sarkewa,” how on earth abeey zakace na auri wannan yarinyar, as small as she is, yarinyar da in da Auran wuri nayi zan haifeta, please abeey mana I can’t marry her,never”, cikin sauri abeey ya kallesa ganin yadda idanuwansa suka fara canza kala ,yasan ransa ba karamun baci yayi ba Amma shima ba yadda zayyi tunda babu Wanda yake wucewa kaddarar sa,”bazaka iya aurantaba kake fadamun” abeey ya fada azafafe, “yes I can’t marry her ,and I will never “cikin bacin rai abeey ya mike tsaye, “shikenan kaje Kayi duk yadda kaga yayi maka tunda ban isa da Kai ba,yau ni ka kewa musu akan abunda na umarceka dashi, nagode sosai, Allah yajikan dan uwanka Muhammad nasan da yana raye da shine zaimun wannan alfarmar ya aureta”ya karasa a raunane , cikin sauri king ya dago da idanuwansa jin sunan da abeey yakira,”abeey” yakirawo sunansa a sanyaye, daga masa hannu abeey yayi “bana bukatar jin komai daga bakinka, kaje kayi duk yadda kakeso”, yana gama fadar hakan ya kama hanyar fita, jiri ne ya d’ebesa zai fadi cikin zafin nama king ya riko hannunsa tare da zaunar dashi, kara tashi abeey yayi wani jirin na kokarin ka yadda shi,”bana bukatar temakonka “, rintse idanuwansa king yayi, cikin sanyin murya ya furta “am sorry abeey, please ka zauna”be kulashiba sai ma kokarin tafiya da yayi “ Dan Allah “ king ya kara fada kamar Wanda nunfashinsa zai fita daga gangan jikinsa, kallansa abeey yayi duk da tsananin tausayinsa da yakeji a kasan zuciyarsa, azahiri kuwa hade ransa yayi shima, waje ya samu ya zauna , “am sorry abeey” king ya kara fada har yanxu idanuwansa na kasa,”ba fushi nake da kai ba,amma inaso ka tuna halin da amminka zata shiga, da me kake so taji da rashin ganeta da yarinyar bata yiba ko da rashin temakonta da zakayi,karka manta kai me temakon Al’umma ne, meyasa bazaka tausayawa rayuwar yarinyar nan ba ,sanadiyyar rashin mahaifiyarta da d’an uwanta tashiga wannan halin, kayi tunani inda nine..” be bari abeey ya karasa zancan nasa ba king ya soma magana” zan aureta amma da sharadi” da sauri abeey ya kallesa murmushi na kokarin su’buce masa,abunda bai taba tsanmanin jiba daga garesaba, bai kalli abeey ba yaci gaba”maganar yan uwanta zan sa a bincika,I will marry her just for her condition, idan memory dinta ya dawo zan saketa “ kallansa abeey yayi jin ya anbaci saki, amma be ce masa komai ba,yanxun ma be kalli abeey ba,”and it has to be a secret marriage,wannan ba aure bane temakone kawai data warke zan sauwake mata” yana gama fadar hakan ya kalli abeey, shima har yanxu abeey din shi yake kallo” na amince” abeey ya furta yana sauke ajiyar zuciya. Be kuma kallan abeey ba ya mike tare da shigewa toilet , da kallo abeey ya bishi yana girgixa kai, kafun ya mike tare da fita daga dakin, tunda ya shiga toilet ba abunda yayi sai jin gina kansa da yayi da kofar toilet din, sosai kansa yake sara masa,sink ya kunna,a hankali yake watsawa fuskarsa ruwa, ya dau godon lokaci a haka kafun ya fara sauke a jiyar zuciya, karar da ya Jine yasa shi bude idanuwansa da Sauri tare da barin toilet din, kwance take a inda ya barta , jikinta sai faman karkarwa yake, kara sakin wani karan tayi,”ze tura ta, ze turata “ shine abunda bakinta yake faman furtawa,a hankali ya karasa wajan tare da dora hannunsa kan goshinta, a matukar razane ta farka ,”Zee.. turata…. Zeee turata ,mugune shi” ta furta tana kokarin barin gadon, ganin yadda ta fita a hayyacin tane yasashi rike dan tsan hannunta, ture hannusan ta shiga kokarin yi, ganin ta kasa kwacewa ne yasata fashe cewa da kuka, “ze tureta “ ta kara furtawa, “shhhh” ya furta mata, bata kulawa ba sai kokarin kwacewa da take , tsawar da ya daka matane yasata hadiye kukan nata tana girgiza masa kai hawaye na futo wa daga idanuwanta,”zauna “ ya furta mata tare da sakinta, can nesa dashi ta zauna tana takurewa waje daya, yadda tayine yasa shi kallonta,”ya Allah “ ya furta kafun ya mike ahankali da nufar inda take, zama yayi daga gefen ta kadan , ganin tana kokarin ja da baya ne yasa shi kallanta “me ya faru”,lan gwabar masa da kai tayi tana turo baki, idanuwanta duk sun Tara kwalla, yadda tayi da fuskar ta tane yasa ya zuba mata idanuwa,kusan tsawan mintuna biyu yana kallan kyakkyawan fuskarta , ganin ta motsane ya sashi dauke idanuwansa,da sauri tahee ta kallesa “daddy na”ta karasa kwallar data tarar mata yana zubo mata, be ce Mata komai ba sai kallanta da yayi “mugune shi zai turata fa” zuwa lokacin harta fara shash sheka ,”it’s ok karkiyi kuka “ ya furta kamar wadda akasa dole , kara turo bakinta tayi gaba zata sake magana ya dakatar da ita,” yanxu zan tanbayeki, ki bani amsa kinji” gyada masa kai tayi kamar wata yarinyar, dafe goshinsa king yayi yana taunar le’be,” yaya sunan ki” ya furta a hankali,”shiru tayi kamar me tunani sai kuma ta washe fararan jerarrun hakoranta,”dady” ta furta tana tafa hannayenta, ya tsawa kallanta yayi “bani ba , sunanki na tanbayeki”, yanxun ma kara turo bakinta tayi,”sunana dady”,jinjina mata kai yayi batare da yace mata komai ba “dady”ya furta a kasan zuciyarsa,”I have a lot to do kafun na sake ki, I will try my best hankalinki ya dawo before I divorced you “, mikewa tsaye yayi ganin lokaci na tafiya, wasu magunguna ya dauka tare da allurai yasasu cikin wata bag kafun ya kalle ta,”Taso mu tafi” kamar jira take ,cikin sauri ta mike ta karaso inda yake , hannunsa ta rike gam kamar wacce za’a kwacewa ,be ce mata komai ba suka nufa barin office din, tunda taga sojojin dake ganin wajan jikinta ya fara rawa ta kara kankame hannunsa sai faman buya take a bayansa,zaki ne ya karaso wajan tare da sara masa, a guje ta juya daniyar guduwa cikin tsoro ganin kayan jikinsa,riko hannunta king yayi ganin ta tsorata da sojojin dake wajan, jakar hannunsa kawai ya mika wa zaki,kudun dune shi tayi tana kara buya a jikinsa,”Ya Allah” ya furta cikin zuciyarsa kafun ya fara tafiya da ita, dakin da su ammi suke ciki ya nufa, har yanxu suna a yadda ya barsu, kallo daya yayi musu tare da dauke kansa, ammin sa kawai take tunani ganin irin ramar da tayi lokaci d’aya,”tahura taho nan dada ce” dada ta fada tana miko mata hannu,kara boyewa tayi bayan king, matsowa dada tayi daniyar tabata, bata Ankara ba saiji tayi tahee ta fashe da kuka ,sallallami dada ta saka”Innalillahi wa inna ilaihi rajiun,ke yayi zafi “ dada ta fada tana sakin baki, duk kallanta su ummey sukai, itama ammin kokari take tayi magana amma ta kasa sabida yadda muryarta ta dushe, ummey ce tayi karfin halin magana”ya jikinta” kamar yadda ya fadawa abeey itama hakan ya fada mata “she lost her memory “ da sauri ta dago da idanuwanta tana fadan sunan Allah,kallanta dada tayi “yimun bayani naji yana mamori (memory)”, nunfashi ummey ta sauke kafun tayiwa dada bayani, itama dadan salati ta dauka , ammi ko jinsu batayi sai bin tahee da kallo da take, itama taheen tana bayan king tana binsu da ido ta rikesa gagam , shigowar abeey ne ya katse musu shirun su, da sallama ya shigo dakin fuskarsa dauke da yalwataccen murmushi, kallo daya yayi musu ya dauke kansa tare da kallan dada, “dada ya kamata mu goma gida ko, Inyaso sai a tattauna a can”, gyada masa kai dada tayi da Sauri”eh haka ya kamata,amma ita tahuran fa”, kallan king abeey yayi, shima king kallan yadda ta rike sa yayi kafun ya kallesu “zan taho muku da ita” abeey besan lokacin da murmushi ya subuce masa ba ,be ce komai ba ya kalli dada” dada tunda zai taho da ita kinga sai mu jira su a gida “ yanxun ma kai dada ta daga masa ,dukansu mikewa sukai tare da barin dakin,har lokacin tahee na tare da king,yana ganin sun shiga lifter ya juya tare da koma wa office dinsa,suna sauka premises ba bata lokaci suka shiga motocin da aka fito dasu, manyan sojoji na biye dasu, Kai tsaye hanyar da zata sadasu da gida suka nufa. 🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧 KANO Tana zaune cikin dakin da zahra ta bude mata har yanxu ,so take ta rama sallolin da ke kanta amma batajin zata iyayi da kayan jikinta, tana cikin wannan tunanin taji an kwankwasa kofa,”shigo “ ta furta a sanyaye, zahra ce ta shigo cikin dakin bakinta dauke da sallama,bayanta ma khaleed ne da manyan ledoji, ledojin suka ajje mata,ko wanne fuskarsa dauke da murmushi, “oumma gashi dady yace akawo miki”kwalla ne oumma taji yana san taran mata,”nagode sosai “ ta furta musu, ganin yanayin da take cikine yasa ba Wanda yayi magana,har zahra zata bude baki khaleed yayi saurin rike hannunta” oumma bari mu baki waje ki shirya”jinjina masa kai tayi tana ajiyar zuciya, kama hannun zahra yayi tare da barin dakin,tsawan mintuna biyar tana zaune a inda suka barta ganin lokaci na tafiya ne yasa ta mike ,daya daga cikin ledojin ta bude, manshafawane da yawa a ciki da turaruka,dayan ledar kuma abayoyine da hijab a ciki, harta sa zata hannu zata bude ledar karshe sai ta fasa tare da shiga ban daki, tsawan lokaci kafun ta fito daya daga cikin abayoyin ta saka tare da kabbara sallah ganin alkibla, ta dade tana sallolinta ,har amrah ta dawo dauke da babban tray a hannunta, bata fita a dakin ba sai ma jera wa oumma kayan tayi a cikin kwabar dakin,ganin ta idarne yasa zahra dakko abinci da ta shigo dashi tare da ajje mata “oumma ga abinci , maganinki kuma suna wajan dady” dan murmushi oumma ta sakar mata,”Tom nagode da kulawa”sosai zahra ta washe hakwaranta kafun tayi wa oumma sallama , bin ta da kallo oumma tayi tana jinjina karanci irin da su a wannan zamanin, kallan abincin da aka kawo mata tayi ,kwallan da take kokarin boyewa suka sauko, saurin goge su tayi tana istigfari aranta “Allah na tuba , Kai ka dai ne abun bautawa,Allah kaine mahaliccinmu sannan kafi kowa son bawanka, Allah na rokeka ka karesa a duk inda yake” sosai tashiga yi masa addua tare da tahee tsawan lokaci ,kafun ta tsakuri abincin da aka kawo mata, ji take kamar tana cin magani ,a haka taci kadan tare da ajjewa….. 🫧🫧🫧🫧 Tunda suka dawo gida babu Wanda ya kara tada maganar, Kai tsaye part din dada suka nufa baki d’ayansu, waya abeey ya dauka tare da kiran mutanan gidan, gabaki d’aya ya umarce ganin manyan gidan,a karshe ya jaddada musu kar yaron da yazo wajan,kowannansu amsawa yayi cikin kan kanin lokaci suka halarci babban falon dada. Lokacin da uncle Salem ya kira aunty suna zaune ita da amrah , sun hada dan karamin kwarya kwayar walima,ko wannansu inka duba fuskarsa zaka ganta dauke da farin ciki,musamman amrah da ta fi kowa farin cikin jin labarin mutuwar tahee, suna cikin wannan yanayin ne uncle saleem ya kira aunty, cikin sauri ta dauki wayar tana kashe murya cikin damuwa,”Muna falon dada kizo ke kadai”yana cewa hakan ya katse wayar tasa, aunty har da mikewa dan murya kasan cewar a speaker ta saka wayar, kamar wasu kawaye haka suka tafa ita da Amrah, jin yadda uncle saleem yayi magana cikin sanyi yasa suka kara yadda da mutuwar taheen, mayafinta dake kan kujera aunty ta dauka tare da yafawa, kallan amrah tayi tare da kashe mata ido daya bayan ta marairaice fuskarta gwanin tausayi kafin su saki dariyar keta aunty ta nufi hanyar barin part din tare da nufar part din dada. A zazzaune ta tarar dasu kowa yayi jigum dashi,itama karasawa tayi fuskarta cikin sanyi kamar ba itaba, ganin yadda ko wannansu yayi jigum dashi yasa ta bude baki da niyar yi musu ta aziya,gyara zama tayi sosai tana saita muryarta “Aushe abunda ya faru kenan ,Allah ya jikan…” bata karasa ganin yadda ko wannansu ya zuba mata idanuwa suna jirin jin me zatace, dada ce ta katse su ta hanyar kallan abeey,”ka Tara kowa ,ka Hana yara zuwa ko zaka fada mana dalilinka na yin hakan”, gyada mata kai abeey yayi kafun ya gyara zamansa,”kamar yadda kuka sani , d’aya daga cikin ahalin gidan nan kaddara ta fada mata da Hakan yayi sanadiyyar samun babban rauni a gareta amma duk da hakan muna godewa Allah da takaita,sannan inaso ko wannanku yaci gaba da tayata da addua kasan tuwar ta manta tunaninta wato ta rasa memory dinta”, tunda abeey Ya fara magana aunty take kallansa, jira take taji ya ambaci mutuwar tahee, amma shiru ganin kamar bata mutum bane kamar yadda sukai tunani yasa zuciyar aunty tashi,tana cikin wannan tunanin ne kunnuwanta suka jiyo mata kallan data kwantar mata da hankali na memory din da tahee ta rasa,"wannan ma abun jin dadin mune tunda ta rasa tunaninta” aunty ta fada cikin zuciyar ta,”a karshe ina mai farin cikin sanar daku cewa ,a yau dinnan rana me kamar ta yau an daura Auran tahnoon zayed al-nahyan tare da amaryarsa taheera mohammed” a zabure mutanan falon suka kallesa, aunty har wani kwarewar azaba tayi a makoshinta, Sam ta manta a inda take azabure ta furta “aure fa kace,Sam bazai yuba”gabaki d’aya falon kallonta sukai cikin mamaki,shima abeey kara hade ransa yayi”kamar ya kenan “ ya furta yana kallanta, sai lokacin ta gane katobarar da tayi ,cikin in ina ta soma magana “daman inaso nace kamar hakan yayi wuri”dauke kansa abeey yayi tare da kallan dada datayi shiru,”dada da fatan hakan be bata miki rai ba” jimmm kadan dada tayi cikin dattako ta jinjina masa”tabbas ka cika uba na gari amma bani zaka tanbaya ba ,iyayensa yakamata ka tanbaya”ta karashe zancenta da kallon su ummey, itama ummey bata amsa ba sallan ammi da tayi, girgiza Kai ammi tayi cikin sanyin jiki,”gaskiya baza ayiwa don Auran dole ba inde ba da amincewarsaba “ ta furta muryarta a sanyaye case dan murmushi abeey ya saki,” ya amince “da sauri kowa ya kalli abeey cikin mamaki, ya bude baki daniyar sake magana kenan, daddadan kamshin turaransa ya cika ko ina na dakin,kowa maida hankalinsa yayi kan kofar shigowa , a hankali yake taku, bayansa tahee ce dake faman rakubewa a gefansa,har ynxu kanta da bandage din da aka nade mata ciwonta, be kalli kowa na falon ba yasamu waje ya zauna kan daya daga cikin kujerun falon, itama taheen zama tayi a gefensa tana rike masa rigar jikinsa ganin irin kallan da yan gidan ke binta dashi,gyaran murya abeey yayi yana kallan king da ya ki dago da idanuwansa, cikin dakewa abeey ya kalle sa “ nasan kun gaji, ya kamata ku huta” ya karashe zancen nasa yana kallan king har yanxu , kin dago da idanuwansa king yayi sai sallamar da yayi musu yana mikewa,da sauri tahee ta mike tana kokarin binsa, da mamaki yake kallanta yana mamakin inda zata,be ce komai ba ya juya daniyar tafiya, taku biyu yayi itama ta soma binsa, kara jiyowa yayi yana kallanta, a dake ya furta “ina zaki”, langwabar masa da kai tayi”dady”,muryar abeey da yajine yakatse shi daga yin magana”ku tafi tare”abeey ya kara fada, taune lips dinsa king yayi tare da soma magana, ganin hakan yasa cikin sauri tahee tabi bayansa, tsabar mugun ta yau be shiga motar ba,a kafa ya soma tafiya ,itama bata gaji ba a haka take binsan, ganin kamar tana kokarin faduwane yasa zaki ya karaso da motar inda suke, baya king ya shiga, TAHEE na biye da shi sabanin dazu yanxu ta rike masa Riga ganin zaki na wajan, a Daidai part dinsa zaki yayi parking,Kai tsaye ciki suka shiga, be kalli inda take ba ya nufa daya daga cikin kofofin kasan , Daidai ya soma balle rigar jikinsa itama ta shigo dakin, da mamaki dauke kan fuskarsa ya kalleta “me kika shigo yi anan” da Sauri ta furta “ni tsoro nake ji”tana turo dan karamun bakinta,kamar bazai kula ba ya kalleta”zauna”,cikin sauri kuwa ta zauna ,wata kofar ya nufa dake gefensa”karki kuskura ki biyoni”gyada masa kai tayi tana turo dan karamun bakinta, yana shiga ko munti uku beyi ba ta mike “Allah ni sai na bika dady” ta karasa zancan nata tana tun karar kofar dakin,bazato ba tsammani ya ji an shigo dakin, da sauri ya juyo dan ganin wanda yayi wannan gangancin, itama ihu ta saki tana kokarin juyawa, san shine ya kwaceta tayi baya zata fadi ,cikin azama ya riko ta towel din jikinsa na kokarin kwancewa,gaba dayansu baya sukai zasu fadi ,Allah yaso akwai sofa daya a wajan suka fada kanta dukansu,shi yana kan sofa din itama tana kansa,hannunta ne ya sauka kan towel dinsa, manyan idanuwansa ya zaro waje yana kokarin tureta, itama kuma sai faman taba towel din take kafun ta kalle sa”dady Menene wannan abun”…….. ALHAMDULILLAH…….. Mu hadu a next page ,ina Godiya sosai masu comment,masu yimun ya jiki kuma nagode sosai Allah ya bar zumunci, Aunty sadeeya (mrs bbk), masoyiya (star lady) da gabaki d’aya team din the talent troupe writers inayinku over ,Allah ya bar zumunci💔💖💖💖🫶. MSS LEE💖 💖💖💖 GIDAN AUNTY 💖💖💖 (a heart touching love story) Story & written By Mss Lee 💖💖 💖💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖💖 MAISAN COMPLETE DIN GIDAN AUNTY YAYI MUN MAGANA TA WANNAN NUMBER: 07041879581 Paid book Page 30 🦋 Zaro manyan idanuwansa king yayi,ganin tana kokarin zame masa towel din kugunsa,tsawa yake so ya daka mata amma bakinsa ya kasa motsi Daidai lokacin da hannunta ya sauka kan mararsa, da Sauri ya Bige mata hannu yana kokarin mikewa,turo baki tahee tayi har yanxu bata dena kici niyar taba towel din ba,”Allah niii.. dady sai naga menene,inaso na gani”,da Sauri ya kalle ta na yan second,har ya rike hannunta da niyar tureta kome ya tuna sai ya fasa tare da sakin guntun murmushi iya haba,kallan ta yayi sosai kafun ya soma magana kamar Wanda aka saka dole,” kinaso kigani”,saurin daga masa kai tayi tana turo baki,”me zakiyi inkin gani”ya kara tanbayarta,yanxun ma turo baki takarayiii “Nidea dady inaso naga Menene a wajan “,lumshe idanuwansa yayi,yana kokarin sake magana ta kwance towel din jikin nasa, gigitacciyar kara ta saki tana kokarin tashi daga kansa ,ganin hakan yasa ya rike ta sosai ko motsin kirki ta kasa sai rawa da jikinta ya somayi,kallan yadda jikinta yake rawa yai ga saitin zuciyar ta dake faman sama da kasa,sosai tsoro ya bayyana a fuskarta da ta kulle gam, kara kallan yadda ta kulle ido yayi har hawaye sun fara fito wa,”bude idanuwanki “ ya furta Daidai fuskarta,”dadyyy” ta fadi sunan nasa a rarrabe,be amsa mata ba sai ma kara maimaita maganar da yayi”bude su yanxu kafun ranki ya baci”, jin hakan yasa tayi saurin bude idanuwan kwallar data tarar mata suna zubowa, kallan yanda hawayenta suke zuba yayi kafin ya soma magana “me akaimiki “girgiza masa kai tayi da sauri tana hadiye kukan ,lokaci d’aya tsoransa yashigeta,”kin zama kurma”da sauri ta bude bakinta “babu komai daddy” ta furta tana san sakin kuka” ba kyajin magana ko, oya kalli abunda kikace kinaso ki gani”ya fada yana kara tsareta da idanuwansa ,baki ta bude da niyar sakin kukan,” kika kuskura kikai mun kuka sai ranki ya baci”hannayenta biyu tasa tare da goge hawayen nata,”oya kalla ,tunda ke kika bude”, girgiza masa kai tashiga yi da sauri tana fashe wa da kuka “dady kayi hakuri bazan sake ba”,be kulata ba har ynxu”kinsan menene shi”, yanxun ma girgiza masa kai ta shiga yi, lips dinsa ya taune kafun ya funciki hannunta ya dora kan marar tasa, gigitacciyar kara taheee ta saki tare da fadowa jikinsa alamar ta suma,nauyayyiyar ajiyar zuciya ya sauke yana runtse idanuwansa,”you killed me,abeey duk kai ka jawomun” ya furta a hankali kafun ya nade towel din jikinsa, ya dau dogon lokaci zaune a inda yake ko motsin kirki yakasa kafun ya bude idanuwansa da suka gama rinewa,kallan inda take kwance yayi har yanxu tana suman, wata kofa yashiga a Wajan, cikin kankanin lokaci ya fito yana tsiyayar ruwa alamun Wanka yayi,kafun ya shirya a gaggauce,inda take ya nufa da hannu daya ya daga ta tare da sabawa kan kafadarsa,kofar ainahin bedroom din ya nufa tare da shinfideta akan lallausan gadon, bedside drowse din gadon ya bude tare da futo da wasu magunguna,guntun tsaki yaja kafun ya balli magungunan tare da balle murfin robar ruwan da ya dakko,bayan ya shanye maganin zama yayi Allan bed din yana rintse ido tsawan mintuna uku kafun ya bude, ruwan hannunsa ya zuba kadan a tafukan hannunsa kafun ya shafa mata shi a fuska,sau uku yana haka kafun taja wata doguwar ajiyar zuciya, ahankali ta fara bude idanuwanta kafun ta bud’esu gaba daya , azabure ta mike zaune idanuwanta ne suka sauka kan king dake zaune gefanta, Tara ta saki tana faman jada baya, sosai hawaye suka fara tarar mata, neman ta sauka take a kan gado tana girgiza masa kai,”dadyyy na dena kayi hakuri”tana gama fadar hakan ta sauka daga kan gadon zata gudu,taku daya yayi ya cafko hannunta,neman yi masa ihu take ya tsawatar mata ta hanyar cewa “yi mun shiru” shirun kuwa tayi tana sunkuyar da kai,kan gadon ya koma da ita kafun ya kalleta,”bakyajii ko” da Sauri ta girgiza masa kai “na dena dady” duk da tsananin tsoran da ya shige ta hakan be hana dan karamin bakinta turo kadan waje ba lokaci zuwa lokaci tana zabura gabanta na faduwa.cikin kakkausar murya ya soma magana “da yau idan aka hanakiii abu,kika kijiii ko ,kinsan me zan miki” girgiza masa kai tayi tana ware manyan idanuwanta,”ok zomuje wancan dakin se na nuna miki” da sauri ta langwabe kai “na dena kayi hakuri zan dunga jin magana”girgiza mata kai yayi”a’a zomuje na nuna miki” cikin tsoro ta kara kallansa “wallahi na dena”,uhmm kin kyauta, yana kammala maganar tasa ya nufi kofar fita, dan juyowa tare da d’age girarsa kadan,kika kuskura kika fito daga dakin nan hmmm… yana kammala magana ya fita daga dakin. ******* A firgice aunty ta koma part din ta , ko ganin hanya batayi sosai tana shiga falon ta tarar da ba amrah a falon, cikin sauri ta nufi dakin da amrah take ,tana shiga ta tarar da ita tana waya,ganin yadda aunty ta shigo cikin dakin ne yasa ta kashe wayar ,duk atunaninta mutuwar taheen ce ta komar da ita haka ,”aunty ya karin hakurin ku”, ta fada tana kyalkyalewa da dariya, cikin ba’kin ciki aunty ta kalleta “ubanki Kena ya karin hakurin “mikewa zaune amrah taji jin abunda aunty tace, waje ta samu ta zauna tare da fashe wa da kuka, tsaya kallanta amrah tayi,”wai ke aunty lapiya na ganki haka,mu da yau ta kasance ranar farin cikin mu”, bata kai karshen maganar ba ,aunty ta kudun Dino zagi ta dire mata,”ubanki ke da farincikin,dan ubanki da kinsan abun bakin cikin da naje na tarar bazaki mun wannan banxan zancen ba,toh bari na futo miki a mutun tunda bakya ganewa,ban taba sanin cewa sheguncan tsinannu bane se yn Andy, kamar ni zasu ha’inta”kamar ya aunty ban gane ba,cewar amrah ,wani dogon tsaki aunty ta karaja yanajin yadda zuciyar ta ke soyuwa da bakin ciki,”toh in baki sani ba yanxu ki sani,shegiyar yarinyarcan tana raye bayan tayi loosing memory dinta”,jin karshen zancan ta yasa amrah sakin ajiyar zuciya “aunty wannan me sauki ne tunda tayi loosing memory dinta ,kinga sai muyi anfani da wannan damar mu kasheta kawai”, a tsawa ce aunty ta tashi”ke dan ubanki me yasa kullum kwakwalwarki ta Kifi ce,to bari na fito miki dallah dallah, shegiyar yarinyarcan sun daura Mata aure da king, yanxu haka tana bangaransa “, kalmar an daura mata aure da king ne kawai ya shiga kunnanta, take a wajan ta yanke jiki ta fadi sumammiya, da sauri aunty ta nufi toilet,muntuna kadan tafito hannunta dauke da ruwa, watsawa amrah dake kwance tayi a wajan,tana farkawa tasaka kururuwa tana birgima kamar wacce aljanu suka shigeta,”bazata sa’buba wallahi bazan yadda ba , king nawane ni kadai ba wata shegiya da ta isa ta zama mallakinsa sai nii,wallahi sai naga bayanki, sai na kashe ki” itama aunty bata kulata ba sai ma barin dakin da tayi, sosai amrah ta haukace, sai faman fashe fashe take tana kururuwar bazata yadda ba ,tanayi tana kuka ,lokaci zuwa lokaci tana sakin dariya kamar me tabun hankali, da sauri ta nufi daya daga cikin a kwatunanta, tana budewa wasu magunguna ne a ciki, guda ukun cikinsu ta bude tare da kwankwadewa gabaki d’aya,lokaci d’aya ta bugu sai faman surutai take. ➰➰➰ A ‘ban garan mamy ma cikin futar hayyaci ta nufi ‘ban garanta,lokacin ihsan da sumayya suna zaune suna kallo, ganin yadda ta shigo ne yasa suka bita da kallo,”mamy lapiya naganki haka “cewar ihsan tana mikewa,bata kulataba sai ma zagaye falon da ta fara ,”shikenan aikin da muka dade munayi ya tashi a banza shegiyar yarinyar can na tsanekiii”, cikin hada baki suka kalleta”wace yarinya”yanxun ma bata kulasu ba, sumayya ce ta kulu cikin tabara tace”wai ke mamy ana ta miki magana sai wani faman ja mana rai kike”,girgiza kai mamy ta fara tana buga cinyarta, “shikenan ta faru ta kare, yanxu abunda zayed ya d’auke mu kenan,ya daurawa king aura ba tare da sanin muba” za bura sukai baki Dayan su musamman sumayya datafi kowa firgita,cikin rawar murya ta soma magana”wane..wane king din wai”dogon tsaki mamy taja,”Wana king kika sani, to bari na fada muku kuji ba sa kowa aka daura masa aure ba sai da wacce shegiyar taheera take kowa, ni zasu rai nawa hankali suce wai tayi loosing memory “,bushi bushi sumayya ta fara gani, take a wajan ta fada kan kujerar da ta tashi, d’age kafada ihsan tayi”toh mamy Menene aciki dan ya aureta inda da abincewarsa” bata karasa zancan taba taji saukan maruka dama da hagu” shegiya daman nasan ke ba Kaunar cigaban mu kike ba” ‘bace mun da gani,tana kammala zancanta ta kama hannun sumayya suka nufi up stairs,akabar ihsan da rike kumatu. 🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧 KANO Knocking din kofar dakin akai, “shigo “oumma ta bada umarnin shigowa ,khaleed ne ya shigo dakin cike da sallama,”oumma barka da hutawa” ya furta yana sakin murmushi,itama murmushi ta sakar masa,”barka khaleed”ta fada da sigar tabbatar wa, sosai ya washe hakwaransa, baki manta sunana ba oumma,Kai naji dadi” itama oumma murmushi ta sakar masa,”oumma hira na zo na tayaki kar abar mun ke ,ke kadai “yanxun ma murmushi ta sakar masa, yana cikin maganar sane zahra ta shigo dakin itama “Laa,yanxu yaya khaleed ahaka Allah yace ,shine ka gudo kabarni ni kadai wajan dadi”dariya khaleed ya saki”nasan halinki ai shiyasa nazo bude fadata “, da sauri zahra ta shigo ta itama ta zauna kusa da oumma,”oho dai nide bazan yadda ba”, kallan oumma tayi ,”oumma Aini zaki fi so ko”gyada mata kai oumma tayi ,da sauri khaleed ya kalleta,ni bakya sona kenan ko, girgiza masa kai tayi “Aah Kai ma ina sanka”, kama hannunta yayi “toh oumma zaki dauke Muma kamar taheer da taheera “, ya fada a raunane tunowa da mahaifiyarsu da sukayi, itama zahra kwallace ta tarar mata ,ganin yanayinsu yasa oumma sakin guntun murmushi”sosai ma kai kamar taheer kake a waje na ,itama kamar taheera ta take”sosai farin ciki ya bayyana a fuskarsu,suna cikin zaman nan ne dady ya zo wajan,kallansu yayi tare da girgiza kai”me kuke anan ku taso kuzo ku kwanta kun cika ta da surutu”dan turo baki zahra tayi” to dadi zan kwana a…”bata karasa ba dady ya kalleta”Ah ah fa, ku tazo maza” tashi sukai tare da kallan oumma cikin hada baki,”oumma sai da safe”, Allah ya tashemu lapiya ,suna gama fadar hakan suka wuce,shima dady kallanta yayi”sai da safe” be jira amsarta ba ya bar wajan. 💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖💖💖 Mss Lee 💖 💖💖GIDAN AUNTY💖💖 (a heart touching love story) Story & written By Mss Lee 💖 PAID BOOK 07041879581 Wattpad :Msslee22 TAKABBALALLAHU MINNA WA MINKUM , INA TAYA KOWA DA KOWA BARKA DA SALLAH DA FATAN ANYI SALLAH LAFIYA ,ALA MAIMAITA MANA AMEEEN. BOOK 1 Page 31🦋 Direct falon sa na kasa ya nufa, yana fitowa ya tarar da babban trolley din kaya ga kayan tray din abinci da aka jera musu, yar guntuwar paper din da ya gani akai ya bude,short Rubutun dake ciki ya bude tare da karantawa,yana gama karantawar trolley din kayan yaja tare da nufar dakin da ya batta, a takure ya sameta duk ta kudun dune waje d’aya,sai faman shashsheka take saki , kallanta yayi na yan second kafun ya karaso inda take ,be kulata ba ya nufi kan daya daga cikin sofa din dakin yana rintse idanuwansa kamar me jin bacci, tsawan lokaci yana a haka har yanxu kuma bata bude idanuwanta data kulle gam ba ga siraran hawayen da suke zubo mota.ciki ciki ya furta “me akayi miki” da sauri ta bude idanuwanta da suka canza kala zuwa jajawur,mikewa tayi da niyar nufar inda yake ya dakatar da ita,”zauna nan inda kike”ya kara sa zancan nasa yana tsuke fuska kansa har ya fara ciwo sabida yawan maganar datake sakashi,lan gwabar masa da kai tayi zata bude baki, kallan da yayi Matane yasa ta zauna tana tura baki,ya d’au kusan mintuna biyar a hakan kamar Wanda be san da zaman wata halittar ba ,kafun ya nuna komar dazu da yatsa,cikin kasa kasa da Murya ya soma magana “kaza mace ke sai Ance miki kiyi wanka”,yanxun ma turo masa dan karamin bakin ta kawai tayi,”toh ai bakayi mun ba”, kallan ta yayi da sauri yana so ya gane me take nufi,kafun ya tsuke fuska yana nuna kofar da zata sadata da wajan toilet din,”Kazama tashi kije kiji Wanka” gyad’a masa kai tayi har yanxu bakinta a ture ta fara kokarin tube rigar jikinta da sauri ya mike yana kallanta ,tare da jan rigar hannunta batare da ya rike taba,a haka harya karasa bakin kofar toilet din da ita,”mun tuna kadan na baki kiyi wanka ki fito sannan karki sawa fuskar ki ruwa “yana gama fadar Hakan ya bar wajan,rigar jikin nata ta bude nan da nan Santa santalan kafafuwanta suka fito cikin black tie din dake jikinta, vest din jikinta ta tube shima ,take fararan breast din ta suka fito sosai cikin black bra din dake jikinta,bra din ta kama da niyar cirewa kamar yadda ta cire sauran sai taji ta kasa, a ko karin cire war da zatayine manyan tsayayyun breast dinta suka fito waje da su har yanxu kuma ta kasa cire bra din, turo bakinta tayi tare da nufar kofar da ta ga king ya fita,yana zaune daga gefen bakin gadon ya jingina dashi , duk da yaji bud’ewar kofar da akai hakan be sa ya bude idanuwansa ba , da saurin ta ta karaso Inda yake “dady”,ta kira sunansa,shareta yayi har yanxu fuskarsa a rufe,”dady “ ta kara kiran sunansa, yanxun ma be amsa va sannan be motsaba kuma, ganin hakan yasa ta dauka yayi bacci kawai sai ta kama hannunsa guda daya ta dora kan kirjinta tana furta “dady ka cire mun” da mugun Sauri king ya bude idanuwansa sabida mugun shock din da ya ziyarceshi tundaga kan kafafunsa,cikin Sauri ya kulle idanuwansa yana kiran sunan Allah,kafun ya daka mata tsawa yana funcike hannunsa”barnan wajan “ya furta a kausashe,sosai ta firgita da tsawan da yayi mata ga kanta da yasoma mata ciwo, baki ta bude da niyar yi masa magana yanxun ma wata tsawar ya daka mata data fi ta dasu,har yanxu idanuwansa a kulle suke , ja da baya ta soma yi jikinta na dauka rawa kafun ta fashe da kuka tana dafa kannanta,”Kai na”,”kaina “ shine abunda take furtawa a hankali ya bude idanuwannasa kafun ya nufi inda take yana kawar da kansa gefe,kama hannunta yayi ta kwace zata gudun, saurin ruko hannun nata yayi “ya Allah” ya furta ,shi kansa yasan a wannan condition din nata be kamata ya dunga mata tsawa ba karya taba mata brain, yana cikin wannan tunanin ne yaji tana kokarin kwace hannunta ga kukan da take saki,be san lokacin da ya rungumeta ba gaba ki dayanta yana sauke ajiyar zuciya jin tsayayyun breast dinta a fatar cikinsa,har yanxu bata dena masa kukan ba,a hankali temperature din jikinta ya soma can zawa, ga wani zafi da jikinta ya fara cikin kan kanin lokaci, kan bed din ya karasa da ita ya na kawar da Kai , kafun ya ja mata blanket yana rufe kirjinta,sai a lokacin ya kalleta ,”Menene “ ya furta yana jin muryarsa kamar tana kokarin daukewa , hawaye na zuba a fuskar tata ta furta “Kai na “, taba kan nata yayi yana jin yadda kan nata yayi zafi sosai ,hannunsa ya mayar kan wuyan nata yanxun ma akwia zafin, be ce mata komai ba ya nufa inda ya ajje mata magungunanta,wasu allura ya dauka guda biyu ,saida ya hadasu sannan y nufa inda take , idanuwanta na sauka akan alluran nan ta soma kuka “ni banaso”ta furta tana kokarin me kewa, mayar da ita yayi ya zauna, wani kukan ta kara fashe masa dashi “ni bana so”gyada mata kai yayi yana ajje allurar “shikenan na fasa miki” gyada masa kai tayi tana sakin ajiyar zuciya, a hankali ya matso inda take har suna jin saukar nunfashin junansu, hannunta d’aya ya kama kafun ya rungumeta, ganin hakan yasa ta rikeshi so tie a blanket din da ya rufa mata yana zamewa,tsayayyun breast dinta akan rigar jikinsa,lumshe idanuwansa yayi yana kara matseta a jikin nasa ,kafun ya dakko allurar daya ajje , tie dinta yaja kasa kadan kafun ya fara mulmula mata wajan a hankali, lafewa tayi a jikinsa tana faman lumshe ido, sai saukar allura taji a jikinta , kuka ta fashe da shi tana kokarin kwacewa a jikinsa amma ya ki bata damar hakan sai da ya kammala allurar tasa, idanuwansa tuni sun kada daga launin farinsu,yana kammala allurar tasa murmula mata wajan ya shigayi, har yanxu bata dena kukan ba, ya dau dogon lokaci a haka ,kafun ya dena jin kukanta sai saukar nunfashi da ajiyar zuciya da take faman saki,dago da kanta yayi kadan yaga tayi bacci, girgiza kansa yayi tare da kwantar da ita kan gadon sosai, breast dinta da suka fito waje ya kurawa ido kusan tsawan minti daya kafun ya janye idanuwansa akanta, hock din bra din ya cire mata gabaki d’aya tare da ja mata blanket din har saman kirjinta,adduar kwanciya bacci yayi mata yana bin kyakkyawar fuskarta da tayi fiyau da ita da kallo na tsawan lokaci kafun ya bar wajan, muntuna kadan ya fito daga inda ya nufa fuskarsa ajike alamun alwala yayi, kabbara sallah yayi , ya dau dogon lokaci yana sallan kafun ya idar, ya soma karatun alqur’ani,shima ya dau tsahon lokaci yanayi kafun ya mike, kallan yadda take bacci peaceful yayi kafun ya nufi bed din, pillows uku ya jera a tsakaninsu kafun ya kwanta yana gyada bata blanket din, remote din lamps din ya dauka tare da kashewa, ya dau dogon lokaci a hakan yana tunanin ydda zai bullowa al’amarin a haka bacci shima ya daukesa batare da ya shirya masa ba. 🫧🫧🫧🫧🫧🫧 Tun bayan magungunan da ta sha,sosai suka birkita mata kwakwalwa sai faman surutai take, cikin sauri ta rarimi wayarta tare da kiran wani layi,bugu daya aka daga wayar,cikin maye ta soma magana “kana ina”banji ko me aka ce mata ba sai amsar da ta bayar cikin maye”kazo dakina yanxu ina jiranka” tana kammala maganarta ta jefar da wayar, wata kwalbar ta bude daban ta fara kwankwada, kusan tsahon mintuna 30 tana a haka kafun taji an bude kofar ,cikin maye batare da ta dago ba ta soma magana “me kika dawo kiyimun kuma bayan kin kasa tsinanamun komai,ki fita kawai ki bani waje”, ita kadai take surutanta ganin ba a kula ta ba ta dago a zuciye. Sanye yake cikin wasu bakaken kaya ,ba a ganin ko ina na fuskarsa hatta yan yatsin hannunsa akwai bakar safa akai,kulle kofar yayi taciki kafun ya fara takowa cikin dakin,Wanda ta ganine yasata sakin murmushi,cikin maye ta mike tare da nufarsa,tana zuwa daidai inda yake ya fesa mata wani abu a fuska, kansa tayi daniyar faduwa ya riketa tare da jefata kan gadon, be damu da yadda take a Mayan ba ya fara faffarka mata kayan jikinta,komai a zafafe yake yinsa, cike da mugunta ya fara yin sex da ita, ya dau kusan awanni hudu a kanta yana yin rough sex da ita kafun ya dakko wani Jan kalle,ya kwace maniyinta a jiki, saida ya tabbatar ya kwace sannan ya kafa bakinsa a wajan yana tsosa ,nan ma ya dau dogon lokaci yana yi kafun ya fita daga dakin ya barta a haka. 🫧🫧🫧 ➰➰➰➰➰ KANO kamar kullum yadda ta saba farkawa ta farka, gefenta ta kalla kamar tana jiran gefen yayi magana sabida yadda ta tsurama Wajan ido,ba Wanda ya fado Mata arai sai taheeran ta,duk da Tasan tana hannun Kwarai ko yau ta mutu tasan kilishi zata kular mata da ita,mikewa tayi tare da dauro alwala, sai da tayi nafila kafun ta kabbara sallah, bayan ta idar kamar yadda ta saba karatun alqur’ani ta fara da ka, ta dau dogon lokaci tana karatun kafun ta kammala ,har yanxu tana kan daddumar,kwankwasa kofar akai, cikin daga murya yadda za a jiyota ta bada damar shigowa,zahra da khaleed ne suka shigo dakin,ganin oumma zaune kan dadduma ne yasa suka karasa inda take “oumma ina kwana “ amsawa zahra tayi tana sakin mata murmushi,shima Khaleed gaishe ta yayi,ta amsa masa cikin kulawa, sun dau kusan mintuna ashirin a dakin suna Jan oumma da hira har ta sake musu itama tana amsa musu kafun suyi mata sallama akan zasu dawo . ➰➰➰➰ BUNKURE Tun bayan tsawan sati biyun da kaka ta bawa tayi batare da ta kara bi ta kan zancan su oumma ba ta soma Wasu irin mugayen mafarkai, sosai take mafarkan wani lokaci ma bata samun da Man yin bacci,abunda bata sani ba shine ba ita kadai bace take mugayan mafarkan kusan yawanci yan gidan basa bacci sabida mugayan mafarkan da suke musamman da wasu mucizai da suke kawo musu hari, daga rin Allah ya waye zasu manta da komai sai dare yayi sannan abun yake kara dawo musu . **** A bangaran Dije kuwa duk da irin mugayen mafarkan da suke hakan be hanasu sheke ayarsu ba ,liyafa ta cigaba yanxu kwata kwata mutanan gidan basa sa musu ido musamman yadda bintalo takoyi yawan dare, da yawan lokuta in tafita tun safe bata dawo sai dare wani lokacin ma sai washe gari, hakan baya damun Dije kwata kwata sabida yanda take mata barin kudi, yanxu har babbar waya bintalo ke rikewa ga manyan ledojin da take shigo dasu na kayan ciye ciye sosai ta fara samun kudi ka manyan matan da suke kara bude mata ido,kullum tana tare dasu,d’aya daga cikin matan da take bi me suna hajiya yasira sosai ta fara kwadaituwa da bintalo, shiyasa kullum cikin kashe mata kudi take tana neman hanyar da zata biyawa kanta bukata. 🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧 3:10am Kasa kasa ya fara jin shash shekar kuka cikin barcinsa,nutsuwa yayi dan jin daga ina shash shekar yake futowa,a hankali ya bude idanuwansa,sosai ta ke rungume a jikinsa pillows din da ya jera ma babu a wajan ta watsar,kara karfin kukan ta tayi sabida yadda cikin ta ya kara murdawa,”Nide kam na shiga uku,abeey duk kai kajawo mun” ya furta cikin ransa kafun ya kalleta ,fuskarta ta jike da hawaye ga zufar da take har yanxu idanuwanta a kulle suke,so yake ya banbareta a jikinsa amma se kara shigewa ciki take,a jiyar zuciya ya sauke a hankali yana taba goshinta,babu zafi ko kadan sai zufar da ta jikata,hannu daya yasa ya banbareta daga jikinsa kafin ya mike zaune, bed side lamp ya kunna guda daya yana ganin yadda ta kara kudun dunewa tana dafe cikinta,hannu ya kai da niyar ta bata ,sosai ta rike hannun nasa tana do rawa akan cikin nata,har yanxu kuma ta ki bude idanuwan, Daidai saitin fuskarta ya nufa tare da hura mata iskar bakinsa, ajiyar zuciya ta soma saukewa a hankali be dena ba ya cigaba da hura mata iskar,kamar me kokashin yin bacci sai ta kara fashewa da wani saban kukan sabida wani irin murdawa da cikin ta yayi mata ,bude idanuwanta tayi da sauri tana furta “dady” a hankali,kamar daga sama taci saukar muryarsa “me akai miki”, cikinta kawai take nuna masa ta ma kasa magana,kallanta yayi na tsawan sakanni kamar me nazari akanta ,kafun a hankali ya dora hannunsa kan farar fatar jikinsa,shock din da ya ziyarceshine yasashi lumshe ido ,a hankali yake shafa lallausan fatar cikin nata, itama taheen jin yadda yake shafa mata ciki yasa ta lumshe idanuwa,sosai ya cigaba da shafa mata a hankali har zuwa mararta , nannauyar ajiyar zuciya ta sauke tana kara lumshe idanuwa,bin idanuwanta yayi da kallo,ganin yadda take lumshe wa, ya dau dogon lokaci yana matsa mata cikin har wajan marar tata da yake jin dimi a wajan, sosai hakan yayi mata dadi bata san lokacin da ta fashe masa da kuka ba jin wani abu na tsarga mata a jiki , wajan cibiyarta da ya ta bane yasa ta motsawa tare da dago da fuskarta kama, daidai lokacin da fuskarta take dagowa a Daidai lokacin da ya kawo fuskarsa wajan , a bazata yaji saukan lips dinsa akan nata. Saurin kawar da kansa yayi daga saitin fuskar tata yana mikewa, be kara ko minti daya a dakin ba ya fita da sauri , lokacin da ya fita daga dakin itama tahee a haka wani daddad’an bacci ya kara daukarta har lokacin kuwa king be kara dawowa dakin ba. 🫧🫧🫧🫧🫧 💖💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖💖 💖💖GIDAN AUNTY💖💖 (a heart touching love story) Story & written By Mss Lee 💖 PAID BOOK MAI BUKATAR COMPLETE DIN GIDAN AUNTY YAMUN MAGANA TA WANNAN NUMBER 07041879581. BOOK 1 📕 Page 32💖 Sanye take cikin wasu baka’ken kaya ba’a ganin ko ina na fuskarta hatta kwayar idanuwanta ta kulle su da bakin glass,magana take da wani da shima ba a iya ganin fuskarsa cikin wani yare mara dadin ji, wata yar karamar leda ya mika mata ,cikin ta wani farin abune aciki,tana ganin abun da ya bata ta kyalkyale da dariya kafun ta soma magana “tabbas a wannan karan burin mu na daf da cika, tunda munyi nasarar juyawa yarinyar kwakwalwa,ta Hakane zamuyi anfani da ita muka she wancan tsinannan ,burinmu na cika sai mu dora mata lefi,tabbas wannan karan za a jubda Jini”,babbakewa da dariya mutumin yayi kafun ya soma magana,”tsawan shekaru na dauka ina jiran wannan lokacin, da dukiyar NAHYAN zata dawo hannuna,kina tunanin zanyi sake da wannan damar,basu kadai ba,duk Wanda yayi kokarin rutsemun ginin da na dade ina gidawa babu abunda zai hana muga bayinsa,kamar yadda muka ga bayan mohammad”lokaci d’aya suka babbake da dariya tare da zuya harshen su zuwa wani yare da baba ganewa. 🫧🫧🫧🫧🫧 Karfe 6:30am ya turo kofar dakin a hankali,tun futar dayi dazu be kara dawowa ba,a takure ya hangota kansaman gadon ta takure jikinta,ba a hango komai nata sai fuskar ta dake a ya mutse,a hankali ya fara taku tare da nufar bakin gadon ,gabaki d’aya dakin tashin kamshin imperial majesty yake,sosai kayan jikinsa sukai masa kyau,sanye yace cikin wani red suit me shegen kyau, fuskarsa sanye yake cikin wani bakin glass da baka iya hango kwayar idanuwansa,sosai glass yin yayi wa fuskarsa kyau musamman dan karamin pink lips dinsa da ya kara fito da ainahin sajan sa,gashin kasansa sai kyalli take kamar kullum kara mata yawa ake,kallan diamond watches dinsa yayi kafun ya mayar da kallansa kan fuskarta da take baccin ta har yanxu ,sabanin dazu yanxu harda dan turo dan karamin bakin ta duk da bacci take, guntun tsaki yaja kafun ya taba pillow da kanta yake,motsa fuskarta tayi tana kara cono bakinta gaba,wani tsakin ya kara ja yana dafe goshinsa da ke Sara masa, kara taba pillown yayi ganin bata motsa bane a hankali ya furta “ke”, nan ma bata motsan ba ,da dan karfi ya daki pillow din a bazata ta mike da niyar guduwa, dan karamin tsaki yaja yana furta “matsoraciya kawai “ cikin kasan makoshinsa,kafun ya kalleta,”baki iya sallah bane,komai sai an koya miki” ya furta yana kara tsuke fuskarsa , shiru kawai tayi tana faman rarraba ido kafun ta turo karamin bakinta, “dady” ya furta da shakakkiyar muryarta,kallan yadda tayi maganar yayi kafun ya furta “momy”shima yana harararta,dariya ta kyalkyale dashi,be bari ta kara magana ba ya furta je kiyo alwala, gyada masa kai kawai tayi,sosai ta gane kofar da zata kai ta toilet,baka kara cewa komai ba ta mike tsaye dukda kasan cewar bariga a jikinta haka ta mike ,tana nufar kofar, saurin kawar da kansa yayi da ka kallanta ,yana ganin ta shige kofar shima ya fita daga dakin. *****tun da ta shiga toilet din tsayawa kawai tayi tana bin ban dakin da kallo kafun ta dafe kanta da taji ya fara mata ciwon, sosai ta tsaya kallan bandakin ,cikin karan bani ta nufi wani glass dake kewaye da ban dakin, tsayawa tayi tana zubawa wajan idanu “toh shi dady yasan nan wani dakin ne shine zaice mun nazo”har ta juya daniyar komawa sea taji tana jin fitsari,kallan Inda zatayi futsarin ta fara dubawa,har ta tsugunna sai kuma ta tashi,kallan toilet tayi kamar me san tuno wani abu,kafun ta karasa wajan a hankali ,bakin tight dinta tacire jin ta fara yin futsarin,amai makon fitsarin kuma sai ga Jini, a firgice ta saki kara cikin razana ganin Jinin da tayi “dady ,dady” ta ke furtawa cikin birkicewa, cikin sauri ta nufi kofar fita daga ban dakin, Daidai ta taba hannun kofar toilet da niyar fita kanta ya sara mata,Kallan kafar tata tayi kafun kuma ta koma cikin bandakin,kamar tasan yadda ake anfani da kayan toilet din,sosai kuwa ta wanke jikinta har da zarcewa da yin Wanka da kayan wankan toilet din,kamar wacce ake controlling dinta, ban dakin sai faman tashin kamshi yake,komai a nutse take yi bayan ta kammala wankan harda gyara ban dakin duk da babu abunda tayi, fito wa tayi daga toilet din tana bin wajan da kallo, trolley din da king ya shigo da ita jiya ta tsaya bi da kallo, kafun ta karasa wajanta,budewa tayi a hankali tana bun jerarrun kayan dake cikin jakar,tsayawa kallansu tayi sosai kafun ta dakko wata doguwar riga baka sai digo digon ja dake jikinta, kara kallan jakan tayi,kafun ta sa hannu ta dauki wata jaka a ciki, bude cikin jakar tayi inners ne a cikin jakar sai pad shima,pant da bra ta dauka har zata kulle jakar sai kuma ta dauki pad din guda d’aya ,tare da Mayar da trolley din ta rufe kamar yadda ta ganta, a nutse ta saka pad dinta da pant, a wannan lokacin har bra dinta ta saka kafun ta kalli rigar dake gefenta,murmushi ta saki da har dimples dinta na dama da hagu na lobawa kafun ta saka rigar, bakaramun kyau rigar tayi wa jikinta ba musamman da ta kasance fara sai kayan suka haskata kasan tuwar kalan kayan ne ja da baki, hips dinta sosai ya fito cikin rigar jikinta ,yalwataccen gashin kanta da ya sakko har gadon bayanta me shegen cikowa ta kama da niyar tufkewa amma ta kasa,sosai ta fara kiciniyar yadda zata kamashi,ganin ta kasane yasa ta dakko gyalan kayanta daniyar barin dakin, taku d’aya biyu tayi kanta ya sara mata,tsayawa tayi tana bin inda take da kallo , tunani ta shigayi kafun ta turo dan karamin bakinta”to ni ya naganni a nan ba nashiga can ba” ta karasa zan can nata tana nuna kofar toilet ,sai kuma idanuwanta suka sauka kan kayan jikin ta , wayo manyan idanuwanta tayi tana bun jikinta da kallo, kafun ta kai hannu ta shafa kamar me tsoran shafawa, cikin Sauri ta dauke hannunta,”ko dady ne yamun wayo ,yasamun kayannan “ tunanin hakan yasa ta saki murmushi, cikin sauri ta karasa kofar fita daga dakin gashin kanta duk ya rufe mata fuska, bude komar datai ba wuya ta hango dadin nata na kokarin kai wani kyakkyawan cup bakinsa ,a guje ta nufi inda yake tana sakin gyalan hannunta,Daidai zai kai cup din bakinsa ta saki kara “dady”,dan juyo da idanuwansa yayi yana kokarin Shan coffee dinsa ta daka tsalle tare da bare kofin hannunsa,hawaye duk ya bata fuskarta cikin rawar murya ta furta “dady karkasha ,ansa guba “….. (Tofa😳). 🫧🫧🫧🫧🫧 ➰➰➰➰➰➰➰➰ AMRAH Karfe 4:30 ta farka tana ya mutse fuskarta , dafe goshinta tayi tana ware yan mitsi mitsin idanuwanta kafun ta waresu gabaki d’aya ,bin dakin ta farayi da kallo kafun ta motsa jikinta da niyar tashi, zafin da taji a kasantane yasata koma tare da bin jikinta da kallo,da kyar ta tashi zaune tana faman damshe bakinta sabida zafin da take ji a kasan ta, kallan yadda take babu kaya tayi kafun taja dogon tsaki tana mikewa tsaye ,kofar dakin ta sawa key kafun ta koma ta zauna,tana danasanin kiransa da tayi a waya ,”amma in kasan wata ai bata san wata ba” ta furta tare da nufar wardrobe dinta, wata fincinar riga ta dauka tare da sawa a jikin ta sai faman wale kafa take, kwalbar magungunan da tasha ta dauka tare da mayar dasu ma’ajiyarsu data boyesu,tunanin yadda zata kawar da tahee ta fara,ko tunanin gari be gama waye ba ,batayi ba ta dauki wayar ta tare da danna wata number ,kusan missed called uku har yanxu ba a daga ba ,wani dogon tsaki taja kafun ta kara kiran wayar, ringing biyu aka daga wayar,nishin da ta fara jiyowa cikin wayar ne yasata sakin tsaki dakashe wayar tata tana jefata kan gado duk tsikar jikinta ya tashi,sosai ta fara juyi saman gadon jarabarta na tashi, ga wani tsanan tahee dake kara ruruwa a cikin zuciyarta”a wannan karan da kaina zanje wajan boka ,bana bukatar te makon kowa” a haka ta cigaba da tunanin yadda Zata cika burinta batare da kowa ya farga da ita ba . 🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧 KANO “Assalamu alaikum “ zahra ta shigo dakin tana dukar da kai,amsa mata oumma tayi tana sakin mata murmushi,itama zahra murmushin ta saki tana kallan oumma,”oumma daman breakfast aka gama ke kadai muke jira yanxu “, kallanta oumma tayi kamar bazata ce komai ba sai ta mike ,daman sanye take cikin hijab dinta, zahra na ganin hakan ta saki a jiyar zujiya , ta dauka oumma bazata biyo taba kamar yadda Khaleed ya fada mata,da sauri ta bude kofar dakin tana nunawa oumma hanya har suka karaso babban falon, Khaleed na ganinta shima ya mike,kwalo zahra ta sakar masa tana mika masa hannu “yaya my gift”,dan hararar ta Khaleed yayi kije kafun ya soma magana “kije dakina ki dauka” tsalle ta daka har da juyi tana dariya,kallan oumma Khaleed yayi tare da hararar zahra”kin tsaya shiririta kirbar mana oumma a tsaye “ da Sauri zahra ta juya Wajan oumma “ kiyi hakuri oumma”, shima Khaleed kallanta yayi ,tare da nuna mata hanyar dining “oumma kiyi hakuri mun barki a tsaye “murmushi kawai ta sakar masa itama tana tuno su taheern dinta , basu kara cewa komai ba suka nufi dinning din gabaki d’aya ,har yar rigan rigan Wanda zaiyi serving din oumma ake ,saida suka gama cika mata gabanta da kayan abinci har saida ta dakatar dasu , a hankali zahra tayi serving din Khaleed shima kafin su fara cin abincin, har sun kusa kammalawa breakfast Dinsu sai ga dady yafito, da sauri zahra ta zaro ido tana mike wa “dadyy “ta furta da niyar nufar inda yake ,nuni yayi mata data koma ta zauna kafun ya karaso wajan shima ,cikin zoyala ya soma magana “wato har kun fara mantawa dani” dariya suka saki banda oumma data kura wa abincin gabanta ido, a hankali ta bude bakinta tare da gaishesa, kallo daya yayi mata tare da amsawa shima zama yayi zahra tayi serving dinsa,shine ya soma tashi tare da musu sallama , mikewa Khaleed yayi shima dady ya komar dashi”ku kammala cin abin cinki, akwai meeting din da zani, auta me kikeso na taho miki dashi”girgiza masa kai zahra tayi “any dady”gyada mata kai kawai yayi tare da barin wajan ,yana jiyo yadda take faman furta “ Allah ya tsare dady,love you more “girgiza kai yayi yana sakin murmushi kafun ya bar falon. Suma suna kammala cin abincin falo suka dawo, suka fara hira da oumma wannan karan sunki barinta ta koma har saida ta fara sake musu suna hira,sallah ne kawai ke tayar dasu da oumma ta idar dasu kara zuwa su dakko ta , ko gajiya da hiran basayi. 🫧🫧🫧🫧🫧 ➰➰➰➰➰➰➰ BUNKURE zaune Dije suke a daki ita da bintalo sai faman irgan kudi suke ,kallan Dije bintalo tayi cikin ya tsine,”wai ke dije wace Irin mutum ce me shegen san kudi,yanxu kudin ma bazaki barni na irgaba Haba ki canza Hali da wannan shegen san kudin naki”batare da dije ta damu da bakar maganar da bintalo ta saba fada mata ba ta wangale bakinta” Haba yar albarka ta ,Kema kinsan da kudin nan nake so ki koma gidan gayunnan “dan ta bile baki bintalo tayi kafun ta kammala irga kudinta tana mikewa,”ni yanxu bani da wannan lokaci,ki jira nagama cin duniyata sai ayi wannan maganar”ta karashe zancan ta tana jefawa Dije dubu biyar “ga wannan “ da Sauri Dije ta wawuri kudin tare da zurasu cikin zaninta,tsaki bintalo taja tana daukar wayar ta da ake kira,ganin me kiran ne yasa ta sakin murmushi “hajjaju barka da dare”daga daya ban garan banji me aka ceba sai dariyar da bintalo ta saki tana furta “baki da matsala hajjaju ganinan tafe”tana kammala zancanta ta kashe wayar tare da wawurar mayafinta tana barin dakin,ko damuwa da fadawa Dije inda zata bayi ba ta Sakai ta bar gidan. 🫧🫧🫧🫧🫧🫧 Tun bayan data Barar masa da coffee din hannunsa bai motsaba,kafun ya dago da idanuwansa a zuciye yana kallanta “how dare you”, kura masa ido tahee tayi tana kallansa har yanxu da sauran hawaye a fuskarta da gashin kanta ya rufe fuskar,daga hannu yayi da niyar tsinka mata mari a bazata yaji ta rungumesa tana sakin saban kuka,kasa motsi king yayi ba ‘a jin karar komai sai karar sautin kukan ta dake tashi,a hankali ta soma magana cikin shashsheka “dady karkasha kaji, suna so sukashe mu ni banaso ka mutu kaji”,yanxun kam ko kwakkwaran motsi king be yi ba ,tunani ya fara “Anya buguwar da yarinyar nan tayi be taba mata hankali ba”,’ban’bareta yayi daga jikinsa yana hade ransa,langwabar masa dakai tahee tayi tana tuna dan karamin bakinta, bin wajan da ta zubar da coffee din yayi kafin ya maida hankalinsa kanta,”me ke damunki “,girgiza masa kai Kawai tayi alamun itama bata sani ba ,sai alokacin idanuwansa ya sauka kan kayan jikinta, sosai kayan sukai mata kyau musamman dogon gashin da ya gani a kanta,duk da ne gama yadda da gashin kanta bane ,a hankali ya fara taku tare matso ta,ganin yanda ya hade fuskarsa yasa ta tsorata,tare da cuno bakinta, itama baya ta fara ja kamar yadda taga yana matsowa ,bata san lokacin da suka jingida da jikin bango ba,hannunsa daya king ya sa tare da dafe jikin bango ,sosai yayi mata runfa ko ganinta ba a yi sosai,dan sunkuyo da fuskarsa yayi dai dai kan tata…. Mss Lee 💖 07041879581 💖💖The talent troupe writers 💖💖 💖💖GIDAN AUNTY💖💖 (a heart touching love story) Story & written By Mss Lee 💖 PAID BOOK Mai bukatar complete din gidan aunty yayi mun magana ta wannan number 07041879581. MASOYIYA WANNAN PAGE DINKI NE 💖💖💖💖I heart you so much 💖. BARKAN KU DA SALLAH , hope anyi sallah lapiya, ina mika sakon jinjinawa ga al’ummar musulmai baki daya . 💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖 Kuma ban barku a baya ba … 💖💖masoyiya ta (duk karfin izzata ) Aunty sadiya (Jini daya ) Maman sayyid (ya fita zakka ) Auta( baby) Maman twins (sarki sameer ) Memerh (ubana ne ko kishiyata) Dukan ku ina Kaunar ku lodi lodi 💖🫶,Allah ya kara hada kawunanmu (Ameen) BOOK 1 📕 …….💖💖بسم الله الرحمن الرحيم Page 33 _34💖 Kawar da fuska tahee tayi tana faman turo dan mitsitsin baki, bin bakin nata da ta turo yayi da kallo kafun ya dauki karamin finger dinsa ya bige mata bakin,saurin Mayar da bakin tayi tare da saka tafukan hannunta idanuwanta har sun fara tara kwalla, kara kallanta yayi na yan sakanni kafin ya daga hannunsa kan fuskarta,a tunanin ta marin ta zai yi tayi saurin rintse idanuwanta,yana kai hannun nasa fuskarta, gashin kanta ya ke kokarin rufe mata ido ya bude tare da mayar dashi baya, batai aune ba sai ji tayi ya rige gashin gagam, karamar kara ta saki batare da ta sani ba ta rike hannunsa,kwallar da ta tarar mata na zubo mata ,kara rike kan nata yayi gam ,cikin sheshshekar kuka take furta “da.. da zafi”, sakin mata kan nata yayi yana hararar ta ,kamar Wanda aka sa dole ya furta “wayace ki barar mun da abu”, kwalla na zuba ta turo dan karamin bakin ta,”Nima ban sani ba “, kallan daya yayi mata ya jinjina kansa, be kara cewa komai ba ya bar wajan, saurin biyo shi tayi tana rike masa hannu,cikin narai da ido ta ke miko masa ribbon din ta,guntun tsaki ya ja kafun ya karbi ribbon din ,hannunsa yasa cikin lallausan gashin kanta,amaimakon ya Tufke mata gashin sai ya shiga ya mutsawa,sosai laushin gashin ya burgeshi, tsawan lokaci suna a hakan ,motsi tahee tayi tare da kallansa “ka fata” dauke kansa yayi daga kanta kamun ya kamar kan sumar kanta har yanxu yana mamakin yawan cikin gashin kanta,tattare gashin yayi waje daya kafun ya sa mata ribbon din, kallan jikinta yayi kafun ya mayar da kallansa kan kyakkyawar innocent face dinta, a hankali ya furta a ina Kika dakko kayan nan” girgiza masa kai tayi “Nima ban sani ba ,dady nayi kyau “girgiza mata kai yayi alamun a’ah,shagwabe masa fuskata tayi kamar wata karamar yarinya”dady"shareta yayi ganin tana ko karin bata masa lokaci kafun ya nuna mata veil dinta,shima mika masa tayi ,kamar Wanda ya kware kuwa haka ya nada mata shi ko wata macen albarka,dan siririn dantsen hannunta ya kama batare da yace komai ba yaja ta suka bar dakin, futar su ba dadewa wannan shayin da tahee ta zubar ya koma ba’ka’kirin dashi. *****har suka fito falo hannun sa na ruke da nata Daidai saitin one sitter yasaki hannun nata batare da ya kara kallan gefen inda take ba, waje ya samu kan daya daga cikin kujerun yana crossing legs din,karasowa wajan sa tayi tana shagwabe fuskarta,”dady yunwa nake ji”ta furta a hankali sabida yunwar da ta fara ji,kallan agogo yayi kafun ya mike tsaye Daidai lokacin da idanuwansa suka sauka kan babban tray din dake wajan dinning, karasa wa yayi hannu daya yasa tare da bude wani dan dogon plate ,lafiyayyen charcuterie,scratch pastas,and bread ne akai ,dan guntun murmushi yasaki sabida yasan babu me gigin aiko da abu part din sai ita,alama yayi wa tahee ta da karaso,da saurin ta kuwa ta karaso wajan ,nuna mata plate din yayi da hannu kawai batare da yace komai ba, kallan abincin tayi kafun fa kallesa shima,waje ya samu ya sauka kan kujerar dinning table din,ganin Hakan yasa itama ta zauna da sauri tana binsa da idanu,abincin da ya nuna mata ta tsaya kalla,kafin ta kallesa ganin hakan yasa ya dauki fork daya dare da saka abincin dan kadan abakinsa yana taunawa, itama taheen kamar yadda taga yayi hakan itama tayi,nuna mata yayi da ta karasa cin abincin yana ajje fork din, binshi tayi da kallo tana ajiye fork din itama kamar yadda taga yayi,kallan ta kawai yayi ba tare ya yace komai ba ya koma falon, turo dan mitsitsin bakin ta tayi tare da daukan plate din tana binsa da kallo,Daidai inda ya zauna kusa dashi ta zauna har tana gugan jikinsa,yanxun ma langwabar masa da kai tayi ,kin kulata yayi take a wajan ta fara hawaye tare da mikewa da niyar Mayar da abincin,hannunsa daya yasa ya dauki plate din tare da daukan scratch pasta din yayi tare da kai mata bakinta da sauri ta bude bakin yasaka mata,kara daukan wani spoon din yayi ta rufe bakinta tana kallansa,ya gane me take nufi a hankali ya kai spoon din bakinsa shima,murmushi ta sakar masa bin dimples dinsa sake lotsawa a hankali, finger dinta saka a wajan ,a bazata ya kalleta,wani murmushin ta kara sakar masa “dady na kafi kowa yau”, ta bude baki da niyar kara magana yasa mata abincin dake fork din abaki, be kara bari sunyi wata maganar ba har suka kammala cin abincin a tare ,duk Wanda yansu a lokacin sai yayi tunanin masoyaye da suka dade da fadawa soyayya, suna kammala ciki,magungunanta ya bata nan ma sai da suka sha daru kafun Tasha maganin. ➰➰➰➰➰➰➰➰ Zazzaune mutanan gidan suke a babban falon dada,tundaga kan abeey har zuwa kan su ihsan, zoyace kadai bata falan,da yawa daga cikin mutanan gidan babu Wanda ya karya kowa so yake yaji karin bayani akan zan tukan abeey musamman dayawa daga cikin zuciyoyin mutanan falon da take bugawa ,ummey da ammi na gefe suma a kan kujera ,sosai ammi ta fada sabida yar damuwar data sawa kanta akan rashin lapiyan tahee da kuma batan su oumma,gyaran murya abeey yayi “kamar yadda na fada zan sake maimaitawa” taheera matar king ce yanxu,kowa yasan rashin lapiyar da ya jarabceta, duk da haka kuma bazamu tauye mata hakkinta ba,kamar yadda ake yiwa ko wace amarya lefe itama haka za ‘ai mata ,sannan daga rana irin tayau taheera zata koma ban garan mijinta,shine me alhakin kula da rashin lapiyarta, ba shawarar kowa nake nemaba wannan umarni ne na zartar “, jinjina kai dada tayi cikin gamsuwa itama” kayi abun kai zayedu ,hakan ne ya kamata “sai kuma ta maida hankalinta kansu ummey “kuna da abun cewa ne “girgiza mata kai sukai kafun su hada baki “duk yadda kika yanke daidai ne dada”,suman zaune amrah da sumayya sukai jin zancen Auran na kara zama gaskiya , hatta su ihsan saida abun yazo musu a bazata,aunty kuwa kamar ta hadiyi zuciya haka take jinta. A hankali daddad’an kamshin turaran sa ya cika ko ina na falon, har yar Riga rigan dagowa ake, cikin takunsa da ke kara masa kyau ya soma takowa cikin falon,sosai shigarsa ta kara fito da ainahin kalarsa ,babu Wanda ya kalla cikin mutanan falon sai ma hade ransa da yayi duk da be dago ya kallesuba yasan shi suke kalla,tahee na bayansa tun Shigowar su falon ta ‘buya a bayansa sabida mutanan da ta gani,be hanataba har suka karaso cikin falon,kan daya daga cikin 2sitter din falon ya zauna ,itama tahee da sauri ta zauna kusa dashi tana buye fuskarta a jikinsa,abeey king ya gaisar tare da su dada,ta kasan ido yake bin amminsa da kallo ganin cikin kankanin lokaci ta rame,ga baki daya manyan falon ya gaishe dasu amma ba Wanda ya bari suka hada ido dashi musamman abeey, duk yan falon zuba musu ido sukai ganin kusan Anko sukayi,duk Wanda ya kallesu sai ya kara sabida irin haduwar da sukai musamman Jan colour din da yayi matching din shigarsu,mikewa dada tayi tana nufo su”tahura ta zonan kinji yar albarka”, girgiza kai tahee ta shiga yi,sosai ta damke hannun king, tana juya kai,zata saki kuka tsayawa kallonta dada tayi tana tabe baki dan kin samu ma zan kulaki aikuwa sai kinzo, kara nufota dada,aikuwa azabure tahee ta mike da niyar guduwa, cikin sauri king ya rike hannunta,kafin ya kalli dada ,cikin rawar murya ta furta “banaso “ gyada Mata kai yayi kafun ya zaunar da ita,itama dada ganin kallan da king yayi matane yasa ta tabe baki da komawa wajan zamanta, ba’kin cikin kamar ya kashe su amrah musamman da take tunanin wasan kwaikwayone kawai yarinyar take shiryawa,maganganun salma ne suka fado Mata arai,tabbas da wannan damar zatayi amfani wajan kawar da tahee,tunanin da take ne ya tsaya mata tare da wata muguwar shakewa ganin tahee ta dora kanta kan kafadun king tana rintse ido yayin da hannayensu ke sarke da na juna.Gabaki daya falon maida kallansu sukayi suna kallansu,musamman yadda taheen ta jingida dashi,shide abeey murmushi kawai ya ke saki. Be kara cewa komai ba ya mike tsaye ,kallan sa abeey yayi yana kokarin magana yaji sautin muryarsa kasa kasa”akwai abunda zanyi”be jira amsar abeey ba ya fara kokarin barin falon,”dady”tahee ta furta tana kara rike hannunsa gagam,kallan fuskarta yayi ganin alamun tsoro ya bayyana a fuskarta,bece komai ba ya kama hannunta shima suka bar dakin,gabaki d’aya falon binsa sukayi da kallo ciki da mamaki. 🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧 KANO Zaune oumma take kan sofa din kujeran falo, yayinda zahra take Kusa da ita, fruit din da take yan kawa ta miko wa oumma ,karba oumma tayi tana mata Godiya ,itama zahran slice din apple ta dauka ta kai bakin ta kafun ta soma taunawa, hira kawai take yiwa oumma tun bata biye mata yanxu har ta sake da ita sabida ta gane zahra tana da surutu kamar su tahee dinta,a dan zaman da tayi dasu babu abunda zata ce musu se addua sabida yanda suke kula da ita kamar sun Santa,kullum cikin yiwa ‘ya’yanta da dan uwanta km addua take a duk inda suke tare da fauwala wa Allah komai, ganin ta kara samun saukine ne ta fara tunanin barin gidan kuma tunda dama sabida lalularta ne sukai mata alfarmar zama ,tunda yanxu ta Riga ta samu sauki . 🫧🫧🫧🫧🫧 LAGOS Tunda suka bar part din dada,mota zaki ya bude masa suka shiga,har yanxu tahee na rike da hannunsa sabida ganin zaki da tayi ta kara tsorata musamman da ta gansa da kayan sojoji a jikinsa, fahimtar hakan yasa king be kwace hannunsa a cikin nata ba ,Kai tsaye umarni ya bada da su tafi asibiti,cikin kankanin lokaci suka isa cikin asibitin,saida ya mula da kansa sannan ya fito daga cikin motar da zaki ya bude masa hannunsa har yanxu rike da na tahee,ma’aikatan asibitin sai faman miko masa gaisuwa suke, ba Wanda ya kula aciki,duk Wanda ya gansa yau sai yayi mamakin ganin sa tare da mace abunda da ne taba faruwa ba,sosai ya hade ransa kamar kullum ta elevator yabi kamar kullum tun kafun a sauka daga kan elevator kan tahee ta fara juyawa,be ce mata komai ba sai rugumeta da yayi gudun karta fadi, har a aka sauka daga elevatorn yana rige da ita direct babban office dinsa ya nufa da ita cikin dakinsa, kwantar da ita yayi kan gadon ganin har yanxu da saurin tsoro Akan fuskanta,bata dau dogon lokaci ba kuwa bacci ya dauketa,kallan kyakkyawar fuskarta ya tsaya yi na tsawan mintuna biyu kafun ya fita daga dakin. 2:30 ya dawo dakin ganin haryanxu baccin take ya karasa inda take,hannunsa daya yasa tare da shafa fuskarta, cikin gigin bacci take furta”dady”,tsayawa kallan yanda take mutsu mutsu da bakin nata yayi kafun ya kawar da kansa gefe,a wannan be shafa fuskarta ba sai pillow din daya dan bubbuga kadan , a hankali ta fara bude lumshash shun idanuwanta kafun ta bude su baki daya akansa, lallausan murmushi ta kasar masa kafun ta furta “dady” a hankali,lumshe mata idanuwansa yayi kafun ya mika mata hannun, cikin sauri ta rike hannun nasa , mikar da ita yayi ba tare da yace mata komai ba ya nufi hanyar toilet da ita,alamu yayi mata data wanke fuskarta, da sauri kuwa ta wanke ,ruwan fuskar duk ya kwanta a gefen kanta,hannunsa yasa ahankali yana gyaramata veil din,yanxu ma be ce mata komai ba ya kama hannunta wani kofa suka nufa da ban cikin yan mintuna yasa akai mata scanning din kanta kafun su bar asibitin. Tunda suka kama hanyar asibitin ta koma baccinta har aka karaso cikin gidan,Daidai ban garan king zaki yayi parking,a hankali ya maida idanuwansa kanta ganin yadda take baccinta peacefully,har ya daga hannunsa da niyar tashinta ya fasa sai ma gyara mata gyalan ta da yayi kafun ya dauketa gabaki d’aya yana nufar cikin part din, saurin sunkuyar da kansa zaki yayi mamaki fal cikin ransa ga wani tsananin farin ciki da ya bayyana akan fuskarsa. Akan 3 sitter din falon ya kwantar da ita tare da nufar wani daki a sama,yana barin wajan ba dadewa ta farka,kallan falon tayi ganin ba kowa ta mike a zabure “dady”shine abunda ta ke furtawa tana jujjuyawa ko zata gansa, ta gane dakin da suka kwana cikin sauri ta nufi hanyar, bata karasa ba taci sallama saurin juyowa tayi azatanta king ne se ganin amrah tayi tana sakin mata murmushi,saurin ja da baya tayi tana Kallan yadda amrah ke sakar mata murmushi,wani shu’umin murmushin amrah ta kara saki tana karasa shigowa cikin falon,tray din hannunta ta ajiye tana bin falon da kallo sosoi bakin ciki ya kamata tunda take a gidan bata taba shigowa nan ba sai yau ta dalilin wacce ta tsana duk duniya,cikin Sauri sauri tasoma magana gudun kar king yazo ya sameta”amaryan mu ta dadynta, ga abincin kunan ke da dadyn ki kinyi ,karki barshi da yunwa “gyada mata kai tahee tayi har yanxu taki sakewa da amrahn,wani dan karamun abu amrah ta dakko tana mikawa tahee “to ungwa wannan dadynki yace na baki Ki shafa a jikinki,jin ta ambaci dady ne yasa da sauri tahee ta karasa tare da karban abun,da wayo da wayo amrah tasa ta shafa abun ajikin rigarta kafun ta bar part din da sauri zuciyarta na bugawa. Itama tahee batare da tunanin komai ba ta kama hanyar dakin da suka kwana tana jin jikinta na mata wani iri, zaune ta samesa sanye da Farar singlet da farin wando iya gwiwa a jikinsa, murdaddan jikinsa ya bayyana cikin kayan da yasa ,sosai kamanninsa ta larabawa ya kara fitowa a jikinsa musammman yanda gashin kanta ya kwanta a bayansa dalilin taje kan dayayi, da sauri ta taho da niyar rungumeshi ya dakatar da ita “jeki Wanka “ya furta a takaice Sabida bayasan dogon magana ,ma’ke masa kafada tayi “toh dady kazo muke muyi wanka kaji”Girgiza mata kai yayi “ni nayi”turo bakin ta tayi “toh dady kayimun wanda” yanxun ka girgiza mata kai yayi,”kinaso dodo ya kamaki” saurin girgiza masa kai tayi “Tohm jeki yi Wanka kizo kici abinci “gyada masa kai tayi tana turo baki kafun ta bar wajan, dafe goshinsa yayi yana girgiza kai kawai. Kamar dazu yanxun ma da kanta tayi wanka tare da dakko wasu guntayen kaya itama ta saka bayan ta gyara jikinta,kamar wacce batayi loosing memory ba haka ta zauna ta gyara jikinta ,ga wani kaikayi kaikayi da take ji,gun tuwar Riga kawai ta saka ko bra babu,shatun tsayayyun breast dinta suka fito ta cikin rigan , cikin dakin ta dawo sabanin dazu yanzu wani kyakkyawan kwaryace a gabansa cikinta fura ce sai faman maiko take alamun ta sha damu,da saurin ta tahee ta karaso inda yake be ankara ba sai ji yayi kawai ta fado jikinsa,guntun tsaki ya saki tare da tureta ta fado kasa,kwallace ta tarar mata a ido ta mike da niyar barin wajan ,hannunta da ya rike ne ya tsayar da ita ,batare da ya kalleta ba ya zaunar da ita gefensa tare da matsar mata da furan gabanta. Sosai Tasha furan kuwa,sai da ta gama sha ya dakko magungunan ta ,yanxun ma ba karamun damu suka sha ba sai da ya zare mata ido sannan ta tsaya tana matsalar kwalla. 🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧 AMRAH Tunda ta samu ta bar part din take farin ciki da sauri ta shige dakinta tare da kulle wa ko kan aunty dake mata magana bata biba,da sauri ta dauki wayar ta tare da dialing number salma,bugu biyu ta daga ,sosai amrah ta saki wata shegiyar dariya “Lalle kawata na yadda ke shedaniyace ,kinsan turaren da kika bani na yi nasarar bawa shegiyar yarinyarcan,in fada mi ban bar part dinnan ba saida na tabbatar ta shafa shi ,na san yanxu tana can ta fara hauka,so nake show din nan ya fara inga yadda shegiyar yarinyar zatayi”, sosai wacce ta kira take babbaka dariya ,bansan me ta fada mata ba sai dariyar da naga amrah ta saki tare da kashe wayar,wata number ta kira bugu biyu ta aka daga batare da ta damu wanda ta kira yayi magana ba ta soma magana “anjima ina bukatarka “tana kammala maganar ta taji an kashe wayar ba tare da an furta mata komai ba. Wata shegiyar dariya amrah ta saki farinciki fal ranta, fadawa kan gadon ta tayi tana sakin murmushi,jira take taji labarin zaucewar da tahee zatayi,bata damu da kiran sallahn da ake ba sai ma waya da ta dauka ta fara charting. 🫧🫧🫧🫧🫧🫧 9:30pm Tunda ya fita ya barta a dakin take cin abubuwan da ya barmata,tun tana ci da marmari har ta dena ,sai faman kallan kofa take kaikayin da take ji na kara yawa,yanxu ma hannu tasa tana sosa wa , duk inda ta sa hannu ta sosa sai taji wajan ya kara kaikayi musamman kan breast dinta zuwa cikinta,ajje abunda take ci tayi fara susar jikinta ,tun tanayi a hankali harta fara a haukace, cikin azabar da takeji ta fin cike yar karamar rigarta,tsayayyun breast dinta da suka fito waje duk sunfara yin ja Susar da take musu,kuka kawai ta fashe dashi tana cigaba da Susa jikinta, kamar a bazata king ya shigo dakin,binta yayi da kallo ganin yadda ta cire Riga tana kuka, a hankali ya karaso inda yake sabida baya da ta juya masa,hannu daya yasa tare da zuyo da ita,kallan yadda fuskarta ta baci da hawaye yayi,ga fatar breast dinta da wani wajan yayi ja,ko kallansa batayi sai susar da ta cigaba dayi a haukace kamar wacce ta fita a hayyacinta,kallanta yayi sosai “menene” jin saukar muryarsa sa akanta ysa ta dago fuskarta ganin shi dinne yasa da sauri ta fada jikinsa tana sakin kuka ,bayanta ya shafa a hankali yana runtse idanuwansa,kara za bura tayi da niyar barin wajan,riko ta yayi yana kara juyo da ita, kara kwace wa tayi da daga kamar ta alamar zata sa gudu,kara fincikota yayi jikinsa ,cikin fitar hayyaci tahee take so ta kwace jikinta ganin hakan yasa yasa hannu taya tare da riketa,sosai take kuka ,jin kaikayin na kara yawa ta fara sakar masa ihu ,jikinta har ya fara daukan zafi,kara rungumeta yayi a jikinsa,ganin tana kokarin sosa jikinta ne yasa yabi wajan da kallo,sosai ya waro idanuwansa ganin yadda breast dinta yayi ja alamun susa,cikin sauri ya furta” zafi yake miki”kanta kawai take daga masa,jin wani karfi yazo mata lokaci d’aya yasa ta kwace kanta,kara fisgota yayi jikinsa suka fada kan gadon baki daya ,shi yana kan gadon Ita kuma ta fado jikinsa,juyi d’aya kawai yayi ta koma kasansa,wani kukan ta kara saki tare da bude baki da niyar sakin ihu kawai ya hade bakinsu waje d’aya,sosai yake bata passionate French kiss abaki hannun sa d’aya kuma na kan breast dinta da yake shafawa a hankali har zuwa kan cibiyarta ,kafun ya kara sa hannu ya damki breast din da karfi ,launin idanuwansa na canzawa…… MASU COMMENT INA GODIYA SOSAI DA SOSAI🙌😍. Sannan ina kara baku hakuri da canza tsarin update da nayi,kamar yadda na fada zan dawo yin update ranar Monday,Tuesday,Wednesday and Friday 🥹✍️ MSS LEE 💖 💖💖GIDAN AUNTY💖💖 (a heart touching love story) Story & written By Mss Lee 💖 PAID BOOK mai bukatar gidan aunty complete yayi mun magana ta wannan number 07041879581. BOOK 1📕 Page 35-36 💖 A hankali yake bin jikinta yana shafawa a hankali, har yanxu bakinsa na cikin nata sosai yake bata passionate kiss a baki,ganin hakan be masa ba yasa shi saka hannu daya tare da tallafo kanta, tun lokacin da taji ya rufe mata baki idanuwanta a kulle suke musamman yadda taji yana shafa mata wajan da yake mata kaikayi ,runtse idanuwanta tayi da karfi nunfashinta na fita jin wani abu na tashi a jikinta,ko kari take ta tashi a jikinsa amma ya ki ba ta damar hakan sai ma kara rungumeta dayayi,sosai yake tsotsan bakinta idanuwansa a kulle,tun yanayi a hankali ya fara da zafi zafi, kuka tasakar masa jin yadda bakinta yake mata zafi ga breast dinta da yake matsawa sosai suke mata zafi,yana jin kukan nata har cikin kunnensa amma ya kasa barin nata,ji yake kamar sautin kukan nata ne yake kara tun zurashi,hannu tasa tana dan bugun kirjinshi cikin rawar murya take furta “dady ,dady”, ganin ya sakar mata bakin, be motsa da ga yanda yake ba sannan be bude idanuwansa ba ,ballantana tasaran samun amsa,a hankali kuma ya kwanta a gefenta tare da janyota jikinsa tana jin yadda take futar da sautin kukan nata a hankali,lumshe idanuwansa da suka rine kawai yayi tare da tapping din bayanta a hankali. ➰➰➰➰➰➰➰➰➰ AMRAH Haryanxu charting take ko tunanin yin sallolin da suka wuce ta batayi,ji tayi kafadarta na kaikayi, hannu ta sa da niyar susawa, sosai taji zafi susan da tayi har zata kara sharewa taji gefen cikinta shima na kaikayi,hannu tasa nan ma tana sosawa,ahankali jikinta ya soma mata kaikayi,tun tana sosawa cikin marmari har ta mike tsaye, karamar rigar da ke jikinta ta cire tare da cigaba da susan nata,wani zafin azaba taji cikin Sauri ta jefar da wayar hannunta tana cigaba da susar jikinta,tana cikin susar taji kamar an zaula Mata bulala a bayanta, da sauri ta kai hannu tana shafa wajan,bata an kara ba sai jin saukar wata bulalar tayi a jikinta,kara ta saki ga kaikayin da jikinta ke mata ga saukar dukan da take ji a jikinta lokaci daya ,kamar daga sama taji wata murya tana daka mata tsawa”keeeeee” da sauri amrah ta juyo tana zazzare idanuwa,wani saukar dukan ta kara ji a jikinta na azaba gashi har yanxu kaikayin be bar jikinta ba,kusan tsawan lokaci ana hakan kafun a tsaya ,fuskarta duk ta baci da hawaye da majina,gani tayi futulan dakin ya dauke gaba ki daya a tsorace ta mike tsaye tana faman kiran “aunty ,aunty kina ina”, saukar mari taji a fuskarta,wata gigitacciyar kara ta saki sabida azaban marin da taji,”dan Allah kuyi hakuri in na muku lefi,ku kuke ganin mu bamu muke ganin kuba” bata kammala maganar tata ba sabida saukar wani marin da taji a fuskarta, saurin dafe wajan tayi hawaye na zuba a idanuwanta, a firgice take taku ga kukan da ya rike mata makoshi,hanyar futa kawai take Nema a duhu duk da yadda take acikin halin tsoro, ji tayi an tale mata kafa bata Ankara ba kanta ya bugu da jikin gadon,kafarta ma ta daki gefen gado,karan azaba ta saki tana furta “Wayyo Allah ,nashiga uku “ tana cikin wannan kukan azabar wutar dakin ya dawo, sosai gefen bakin ta ya tashi ya kumbura lebenta, sosai mununta ya kara fitowa musamman yadda lebenta ya kunbura ya zama Kato ga azabar da kafarta take Mata, tana cikin wannan yanayin ne taji an turo kofar, da sauri ta dago idanuwanta tana furta “Aunty” ganin mutumin da har yau bata taba ganin fuskarsa ba a tsaye cikin shigarsa ta bakaken kaya,fuskarsa a kulle take kamar kullum , baka iya ganin komai na jikinsa, kulle kofar dakin yayi tare da fara takowa cikin dakin,ganin hakan yasa cikin sauri duk da radadin da take ji ta fara ta kawa baya, da Sauri kuma ta juya zata shiga ban daki,da mugun sauri mutuminnan ya cin mata tare da fusgota,beyi la a karayi da yadda taji rauni ba ya jefata kan gadon nata yana yowa kanta,kuka ta fashe masa dashi tare da nuna masa hanyar fita “ka fitan mun a daki,nice na kiraka toh ynxu bana bukata ka tafi ko kuma nayi maka ihu”,wata yar iskar dariya ya saki yana tafawa,be kulataba sai ma biyo ta da yayi gadan gadan ,a zabure ta mike zata kara guduwa ya cafkota ya jefa kan gadon ,hannu ya dauka tare da cinka mata mari, fashewa tayi da kuka tana faman bashi hakuri, be kulataba sai ma shinshinar wuyan ta da ya fara cikin mugunta ya damki kananun breast dinta yana matsawa kafun ya damki daya daga cikinsu yasa a baki,sosai yake tsotsan nipples din kamar wani mayun Waci dake jin yunwa, kara kaimi yayi wajan tsotsan nipples din nata cikin mugunta dayan hannunsa kuma na matsa dayan nipples din kafun ya mayar da hannun sa kan wandanta, hannu yasa ta cikin wandan nata yana shafa gabanta cikin mugunta ya zura 4 fingers a jiki yana wasa dasu da karfi,kuka ta fashe da shi tana Faman turesa, wani Gigitaccen marin ya kuma mata,kafun ya cire mata kayan jikinta, be da mu ba kawai ya Afkar mata da karfi karfi yake saduwa da ita yana gurnani,jin yadda ya dage ya buga mata gabanshi yasa take a Wajan ta suma, bai damu da yadda ta suman ma ya cigaba da aikin shi cike da mugunta , ya dau tsawan lokaci yana sheke a yarsa kafun ya Sauka a kanta yana cire condom din da ya saka, dogon tsaki ya ja tare da barin dakin ba tare da kallan ko inda take ba. 🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧 YOLA zazzaune suke cikin shigarsu ta kullum jajayan kaya, ko wannansu ya natsu cikin wata irin yare suke magana da alama muhimmiyar magana suke tattaunawa,sun dau kusan awa biyu suna tattaunawar kafun cikin lokaci daya su hada baki suna babbaka dariya tare da nufar wata doguwar kofa,sai da sukayi doguwar tafiya kafun suzo wani daki me bula bula, wasu Sangama sangama mutane suka sa su bude musu kofar kafun su ciga ciki,kusan mutane talatin ne a cikin dakin ko wannan su a kwance yake a galabaice ko motsun kirki basa iya wa sabida azabar yunwa da wahalar dasu da ake yi,bin mutanan dakin sukayi da kallo cikin izza kafun su sa a kawo musu wasu maza guda biyar, cikin kankanin lokaci kuwa aka fito da mazan nan ,ko wannansu a galabaice ko tsayuwa basayi sabida yadda suka galabaita. Daya daga cikin sune ya kalli na gefensa tare da nuna wasu maza su biyu,wannan sune wanda za’a tafi dasu yau ko,jinjina masa kai mutumin yayi kafun ya komar da kallan sa kan sauran mazan guda uku daya ya sunkuyar da kansa. Cikin daga murya ya furta “wadannan kuna tunanin zasuyi mana aikin kamar yadda ya kamata “duk tsayawa sukai daga maganar da suke kafun su zubawa mazan idanu,”wata matace ta furta”ku daga mun waccan yaran” cikin cika umarni daya daga cikin samudawan nan ya dago da fuskar Wanda akace din,fuskarsa duk tayi duhu ga idanuwansa da suke a kulle ,sosai matar ta kallesa kafun ta furta”wannan shine Wanda abar kauna ta sa a killace sa kafun a yi aiki dashi ko,” cikin jinjina kai suka amsa mata, cikin daka tsawa matar tace ya bude idanuwansa ,”cikin galabaita ya bude idanuwansa da suka kankance. Cikin san tabbatarwa na kurawa Wanda aka daka wa tsawan ido, take a wajan zuciyata ta buga tsabar firgici, bakowa bane face TAHEER duk jikinsa taban duka. 🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧 ➰➰➰➰➰➰➰➰➰➰ A kwana a tashi ba wuya wajan Allah,yau kwana biyar kenan da tahee tayi loosing memory dinta, acikin dan lokacin nan ne kuma tahee ta gama period dinta batare da kowa ya gane ba sai king amma shi kansa yana mamakin yadda take gyara jikinta,idan ya tanbayeta kuma sai ta daga masa hannu alamar itama bata wani ba, da yawan lokuta tana nanike da dadynta,tun yana shareta har ya fara dan sakar mata fuska. A ban garan mutanan gidan kuwa har yanxu tahee taki sake musu, dama dama dada da take yawan janta a jiki bayan ita babu wajan wanda take zuwa sai zoya da take zuwa part din dadan. A dan lokacin nan kuwa sosai tahee ta gane amrah,sau da dama tana yawan kokarin cutar da ita amma cikin amincin Allah har yanxu batayi nasara ba. A na cikin wannan yanayin abeey ya bada damar a fara hadawa tahee lefenta da duk wani abu da ake yiwa ya mace na auranta. Sanye yake cikin wasu fararan kananan kaya ko fuskarsa ba a iya gani sosai sakamakon p-cap din dake kansa black colour ,dukda fuskarsa bata fito wa sosai bakaramun kyau kayan sukai masa ba , gefensa tahee ce a tsaye sai faman turo masa dan karamun bakin ta take ,”ni de zan bika” dafe goshinsa yayi yana kallanta,”banasan nana ta magana ,”langwabar masa da kai tayi tana niyar sakar masa kuka, girgiza mata kai yayi yana lumshe mata idanuwa , a hankali ya dan ware mata hannunsa , da sauri kuwa ta fada jikinsa tana kudun dunesa… Masu comment ina Godiya SHIN WANENE WANNAN MUTUMIN DA YAKE SHIGOWA DAKIN AMRAH!?. WU WANNE MUTANAN YOLA !? ME YA KAWO TAHEER HANNUN MUGAYAN MUTANAN NAN!? WACECE ABAR KAUNA DA AKE YAWAN AMBATARTA!?. 💖💖💖 💖💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖💖💖 Duk karfin izzata(star lady ) Gidan aunty(mss Lee ) Sarki sameer( xeenat love) Dara taci gida ( maman sayyid ) Baby( mhiz innocent ) Jini daya ( mrs bbk) Ubanane ko kishiyarta ( meemarh) Mss LEE💖🤌. 💖💖GIDAN AUNTY💖💖 (a heart touching love story) Story & written By Mss Lee 💖 💖💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖💖 PAID BOOK MAI BUKATAR COMPLETE DIN GIDAN AUNTY YAYI MUN MAGANA TA WANNAN NUMBER 07041879581. BOOK 1📕 Page 37-38 💖 Maso da fuskarsa yayi Daidai kunnanta kafun ya furta “banda rashin ji” da sauri ta gyada masa kai ,dago da ita yayi daga jikinsa kafun yayi mata kallo d’aya ya dauke kansa,Jan hannunta yayi ya zaunar da ita kan kujera kafun ya dakko magungunan ta, tana ganin magungunan ta fara kunkuni duk yana kallanta,Ballan magungunan yayi ya bata, kamar zatai kuka haka ta sha magungunan Sabida kallan da yayi mata, allura ya fara hadawa ,tana ganin alluran ta fara bunburi idanuwanta duk sun cika da kwalla, kallanta yayi kafin yayi magana tayi saurin cewa “ni bana san Allura”,be ce mata komai ya rike hannunta , da sauri ta mike zata gudu ya rike hannun nata kafun ya hade ransa , narai narai tayi masa da ido har kwallar data tara sun fara sauka, ce mata komai ba har yanxu ya dakko allurar,kuka kawai tahee ta fashe masa dashi, duk da Hakan be kyaleta ba sai da yayi mata allurar.Ta dade tana kuka be ce mata komai ba har sai da tagaji dan kanta ta fara ajiyar zuciya a hankali ,kofa ya nuna mata kafun ya furta “jeki wanke fuskanki”, cikin turo baki ta mike tare da barin wajan , ba’a dau dogon lokaci ba ta dawo idanuwanta har sun fara canzawa zuwa red colour . Har yanxu be kulataba sai ma nufar kofar fita da yayi,itama cikin sauri ta biyo bayansa sai faman kunburi take. Direct part din dada suka nufa ,koda suka shiga ba kowa a falon sai su ihsan da basu dade da shigowa ba, ko wannan su shiga taitayinsu yayi musamman su amrah da ke binsa da mayataccen kallo kamar su hadi yeshi,har yar rige rigen gaishesa suke ,ba gaisuwar Wanda ya amsa acikinsu sai ma tanbayar da ya jefo musu cikin hade rai “ina da dada”har saurin hada baki suke wajan furta “sunje gaisuwa ne”, be kara cewa komai ba sai tahee da ya dan kalla ta kasan ido, har yanxu sai faman kunbure kunbure take , Taki yadda ta kalli kowa na cikin falon “ I will be back “ ya fada cikin kasa kasa da murya ,ko su da ke cikin falon babu Wanda ya jisa sai tahee data kara cuno baki, be kalli kowa na cikin falon ba ya fita ,ihsan ce ta kalli tahee tare da sakar mata murmushi,”kin tsaya a tsaye ,toh kizo ki zauna mana “ ko kallanta tahee batayi ba bare ta sa ran amsawa,kara maimaita maganar ihsan tayi, yanxun ma tahee bata kalleta ba sannan bata amsa mata maganar ba, cikin tsakanin jin haushi da tsantsan kishi amrah ta ja tsaki” aikin banza , kece ma kika tsaya kula wannan kaskantarciyar da bata da maraba da kazamar bola, ni naso ace ba iya kwakwalwar ce ta juyeba naso ace ta haukace shegiya dan gin mayu da alama ba haka kika bar muba,kuma wallahi ko ina so ko ba kyaso sea kin rabu da king danshi mallakinane,bata kammala zancan nata ba sumayya ta kalleta cikin jin haushin karshen zan centa wai malla kinta,dogon tsaki sumayya taja kafun ta furta “iska na wahalar da me kayan kara” tana kammala zancan ta tabar part din tana bin tahee da kallan tsana,ita dai har yanxu tahee tana tsaye kamar wacce aka dasa ,itama firdausi tashi tayi tabar part din batare da tace da kowa Uffan ba, falon yayi saura daga ihsan sai amrah da tahee ,tabe baki ihsan tayi kafun ta soma magana “ni bansan me ke damun ku ba wallahi tunda aure dai anriga an daura ai..” bata kammala zancan nata ba amrah ta zabura tana katseta cikin sauri,”tsaya tsaya, idan bazaki goyan mana baya ba ,bama bukatar bakinki a ciki” bude baki ihsan tayi da niyar yin magana taji wayarta na ringing , sunan mamy ne ya fito cikin wayar ,daga wa tayi tare da kara wayar a kunnanta,toh kawai tace kafun ta mike tsaye “zan dawo mamy na kira na “ tana gama fadar hakan ta bar wajan. Sosai wani farin ciki ya lullube amrah, ganin daga ita sai tahee,”dogon tsaki taja tare da mikewa tana bin tahee da wani matsiyacin kallo,kafun ta fara zagayeta tana tafa hannaye,TAHEE kuwa na tsayen ta har yanxu bata zauna ba sannan batayi wa kowa magana ba, bata ankaraba sai jin saukan mari tayi a fuskarta , da sauri ta dafe wajan da aka mare tan tare da dago fuskarta,amrah ce ta mare tan ,ta daga hannu da niyar kara marin nata tahee ta daddage ta tsinka mata marin itama, kara amrah ta saki sabida sosai taji zafin marin” ni kika Mara”,shareta tahee tayi tare da juyawa da niyar barin wajan , saurin fincuko tahee tayi baya,sosai kafarta daya ta bugu, itama taheen karar azaba ta saki cikin fitar hayyaci ta shake amrah,tare da gantsara mata cizo,sosai suka fara fada musamman tahee da idanuwanta suka rine,sosai take jibgar amrah kamar wacce aka aiko,suna cikin wannan rigimar king ya shigo falon ,da sauri ya daka musu tsawa,rabuwa sukai ko wannansu yana sauke nunfashi sabanin amrah dake sauke nunfashin wahala,”me ya faru” ya tanbayesu cikin daka tsawa,”mari na tayi” tahee ta furta tana nuna ban garan fuskar da amrah ta mareta ,cikin rawar murya amrah ta furta “karya take mun,rashin kunya ta zo tana mun dan nace ta zauna”, ganin irin kallan da king ya jefa mata,bude baki tahee ta yi da niyar magana ya daka mata tsawa,”bata hakuri” da sauri ta dago idanuwanta ,cikin rawan murya ta furta” mari na tayi fa”, Kallan da ya jefa mata ne yasa tayi shiru tana sauke idanuwanta, “kiyi hakuri” ta furta kawai tare da juyawa , hawayen da suka zubo mata ta share tare da soma tafiya cikin din gishi, dan kallanta yayi ganin tana dingishi har ta fice da ga falan kafun ya mayar da kallan sa yayi kan amrah dake faman sakin murmushin jin dadi,tana cikin dogon tunanin da ta fada taji saukar mari a fuskarta , sosai marin ya shigeta ,bata gama dawowa ba ya shako wuyan ta ,ganin hakan be masa ba yasa ya murde mata hannu da karfin gaske kamar me shirin karya hannun kafun ,kara amrah ta saki cikin azaba ta soma bashi hakuri,guntun tsaki yaja kafun yayi wulli da ita yana binta da kallan tsana kafun ya soma magana cikin kausashshiyar murya “daga yau ,idan kika kuskura hannunki ya kara taba ko gashinta ne ,hmm” ya karasa tare da jinjina kai kadan yana taunar lips, ko inda take be kalla ba yayi hanyar barin falon, amrah kuwa sabida azabar da takeji da bakin ciki yasa kukan da take ma ya dauke duka sai kukan zuciya da ta fara tana faman tsinewa tahee . Yana fita daga part din yaci karo dasu dadan suna kokarin shiga part din,TAHEE na rike da hannunta,sai hawayen da take sharewa, ganin king ya fito daga part dinta yasa tayi saurin kallansa “Yawwa kwanda da Allah yasa na ganka,ga tanan sai faman kuka take mun na mata tanbayar duniya tace mun faduwa tayi sai ka lallashi kayarka,dan bazan iya ba ,ka dauketa ku tafi”, ta kasan ido ya dan kalli taheen gefen fuskarta har ya danyi ja,kafun yace komai tahee tayi saurin cewa “ ni zan zauna a wajan ki” ba dada ba hatta king sai da ya dago idanuwansa ya kalleta ganin yadda ta hade ranta lokaci d’aya,”kikace me” dada ta tanbaya cikin mamaki ,sau da dama in dada tace tazauna bata zama shiyasa abun yayi mugun bata mamaki” zan zauna a wajanki” ta kara fada har yanxu bata kalli inda dadyn nata yake ba,washe baki dada tayi cikin farin ciki” oh Allah na ,yau de tahura zata yini dani ,Allah na gode ma “,ta karasa tana kamo hannun tahee sai faman zabga mata murmushi take, dan tabe baki king yayi ba tare da ya ce musu komai ba ya soma tafiya,kallansa dada tayi “Kai de bakin halinka yayi yawa,yanxu matar taka ma bazaka ce mata ka tafi ba tunda ni ka rainani “, dan tabe bakinsa yayi kadan kafun ya kalli yadda taheen take danyin dingishin kadan kadan,harta shige part din dada,har yanxu kuma bata kalli dadyn nata ba, mai da kallansa king yayi kan dada kafun yace “toh matata sai na dawo “ ya na kammala zancan nasa ya bar wajan, rike baki dada tayi tana bin bayansa da kallo kafun ta furta” shi wannan Auran dan iska ma ya Mayar dashi ,wacece matar tasa” ganin ba me bata amsa yasa tabi bayan tahuran itama. A kofar shiga taci karo da amrah, tana ganin ta ,ta kara hade ranta ,tare da shigewa cikin falon,itama amrah binta tayi da kallan tsana kafun ta wuce tana cizon yasa.kan doguwar 3sitter tahee ta kwanta tana buye fuskar tata kafun ta fashe da kuka kasa kasa, a haka dada ta shigo ta sameta, ganin yadda ta rufe fuskar tata yasa dada tayi tunanin bacci ne ya dauke ta”ke kuma tahura haka ake ai da kin wuce daki kinyi baccinki” tana kammala zan can ta tayi hanyar zuwa dakinta. Har yanxun tana kwancan tana kukanta har bacci ya dauketa a hakan . 🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧 YOLA Sosai ya jigata in ba kallan kurinla kayi masa ba ,ba Lalle ne ka gane saba, jikinsa duk ya saki sabida azabar wahalar da yasha, tsaki daya daga cikin mutanan ya saki kafun ya kalli Wanda ya dago da fuskar taheen,fatan dai kullum kuna basu hotan da ya kamata, cikin wata murmuya Mara dadi ya amsa mata,jinjina kai sukayi alamar gamsuwa kafun daya daga cikinsu ta furta ,a kara ninka musu hotan kamar yadda aka saba, ka tabbatar kana da ido a kansu ,duk Wanda yayi kokarin guduwa kuma ka harbe mun kansa ka ciro mun kwakwalwarsa,sosai matasan suka firgita da jin kalamanta, ko karfin motsa jikin su basu dashi balantana su rokesu,saukar bulala suka fara ji ,tun basa kokwarin guda har suka mike cikin a baza ,kafun a mayar dasu cikin kurkukun, kyalkyalewa da dariya mutanan sukai daya daga cikin mutanan ce ta furta “amma ni yarancan ya tayar mu da jikina ,dole na biya biyan bukatata kafun ya bar nan wajan,kara sakin wata yar iskar dariya sukai gaba ki dayan su , ta kusa da Itace ta kalleta ,”ni kuma ya zakiyi dani ,kinsan ke tawa ce ko” shafa mata fuska tayi kafun ta sakar mata kiss agaban mutanan,saurin rungume juna sukai kafun su bar wajan, haka ko wannan su ya rike hannun partner dinsa suka bar wajan. Cikin dakin da aka maidasu,cike yake da maza sosai aciki kowa ka kallesa a galabaice yake ,gashi ba daman yiwa juna magana, shima taheer yana rabe daga can gefe duk an tuttureshi,a boye yake share hawayan da yake zubo masa ,zuciyar sa fal tunanin oumman sa da tahee,kullum tunanin sa a Wana hali suke ciki yanxu.. ➰➰➰➰➰➰➰➰➰ KANO A cikin dan lokacin nan da tayi da mutanan gidan sosai suka saba musamman Khaleed da zahra, alhaji kabeer ne kawai bata haduwa dashi,har mamakin yadda su zahra suka sake da oumman yake amma har yanxu be ce mata komai ba akanta ko yayanta da suka bata . Bayan idar da sallanta sosai take yiwa yayanta addua musamman taheer da batasan halin da yake ciki ba , tana adduar tana share hawayen da suke zubo mata,sosai tunanin taheer dinta yake mata yawo a zuci ko a Wana hali d’anta yake ciki, ya zama dole ta koma bunkure ko ya dawo yana nemanta itama , wannan tunanin yasa ta mike sanye da hijab dinta duk da kasancewar bata da kudin motar da zata koma haka tafito falan , da sauri zahra ta mike tare da nufota “oumma sannu da fitowa, yanxu nake shirin zuwa wajanki, ga waje ki zauna kinji”dan girgiza Mata kai oumma tayi “zan koma bunkure ko zanga taheer “da Sauri zahra ta rike hannunta “To zan biki oumma “ girgiza mata kai oumma tayi , hawayene suka fara taruwa a idanuwan zahra “toh oumma ki zauna tare da mu dan Allah”, share mata hawayen da ta fara oumma tayi kafun ta furta “kiyi hakuri zahra” sosai zahra ta fashe mata da kuka gwanin ban tausayi dan ganin oumma take tamkar oummanta data rasa ,ganin yadda zahran take kuka yasa oumma kwata kwata bataji dadin abunda tace matan ba, suna tsaye a wajan shima Khaleed ya shigo falon, ganin yadda zahra tke kuka yasa ya karaso wajan ta yana tanbayarta ,fadawa jikinsa tayi sosai ta kara fashewa da kuka “yaya!! zata tafi ta barmu kace ta tafi dani kaji” ta karashe zancen nata da fashewa da wani saban kukan.shima kallonta Khaleed yayi” oumma dan Allah ki zauna damu, muna jinki kamar momma din mu da muka rasa” ga baki d’ayan su sun sakar wa oumma lakar jikinta,sosai tausayinsu ya kamata amma tasan ya zaman mata dole tunda ba a halinsu bace.”Assalamu Alaikum “ sallamar alhaji kabeer ta karade kunnuwansu, da gudu kuwa zahra ta nufeshi tana sakar masa kuka shima ,cikin matsanan damuwa ya kalleta ,”auta me akai miki” abunda ta fadawa Khaleed shi ta fadawa dadyn nata, share mata hawayen fuskarta yayi “shikenan dena kuka auta ,zomu karasa ciki”, murmushin jin dadi ta saki jin abinda yace mata,kama hannunta yayi suka shigo falan kafun ya kalli oumma shima,” oumma dan Allah ki zauna damu” ya furta yana kallan fuskarta ,ba zahra ba hatta Khaleed sai da ya murmusa ganin yadda dadyn nasu yayi,suma hade hannayensu sukayi kamar yadda dadyn nasu yayi, sun kuyar da Kai oumma tayi duk tana jinta a takure , fahimtar hakan yasa dady yace duk su zauna, samun waje sukai gabaki dayan su, cikin serous Tone dady ya soma magana,”na da anbincika mun garin naku kamar yadda kika bamu labari, har yanxu ba a ga taheer ba amma jami’ai suna kan bincikensu har yanxu”cikin sauri oumma ta share kwallar dataji tana kokarin zubo mata, cigaba da magana dady yayi”ko wana dan Adam da tashi kaddarar, sannan kisani Allah yana jarabtan salihan bayinsane domin ya duba imaninsu, tabbas duk musulmin Kwarai anaso ya yarda da kaddarar sa me kyau da mara kyau”sosai dady yayi musu Nasiha gabaki dayan su ,har yanxu kan oumma a sunkuye taye, kafun daga karshe ya dora da “muna neman Alfarmar ki zauna damu nida yarana kafun abinciko inda taheer yake ,gamu da kokan baranmu”,saurin buda baki zahra tayi harda tsugunnawa” Dan Allah kuma ko dan sabo dani” ta furta har ynxu muryanta na rawa,bude baki oumma tayi daniyar yi masa Godiya ya dakatar da ita”mudai ba godiyarki muke soba abincewarki muke jira” duk zuba mata ido sukai kowa yana jiran jin amsar ta,yadda suka zuba mata idanune yasa ta jinta duk a takure ,gashi ba damar tayi musu , musu”Dan Allah oumma” zahra kara fada ,gyada mata kai oumma tayi, da wani irin speed ta karaso wajan oumma tare da rungumeta ,lokaci d’aya tana sakin kuka da dariya, ganin yadda suka shiga farin cikine yasa zuciyar oumma raunana tabbas sunyi rashin uwa,shima dadyn sosai yaji tausayin yaransa ganin irin farin cikin da suka nuna,be kuma cewa komai ba ya tashi ya bar falon. 🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧 ➰➰➰➰➰➰➰➰➰ Tunda yashiga office dinsa time to time yake duba wayar hannunsa kamar me jiran abu,yadda take din gishine ya fado masa arai da lokacin da take furta”zan zauna a wajanki”tuno wa da hakan yasa ya dan taki tsaki sabida jin hau shin tunanin da ya fado masa, aikin gabansa ya cigaba dayi,lokaci zuwa lokaci ya na kara kallan time. 7:00pm bayan sun idar da sallahn magrib,sosai kafar tahee ta rike ga idanuwanta da suka kara ja kadan sabida kukan da Tasha, kallanta dada tayi “yanxu ke Sabida sakarci kafarki da wannan ciwon shine kikai shiru baki bari an duba miki ba” ita de tahee sai faman kuka take kasa kasa ganin yadda kafarta ke mata zafi,suna cikin haka abeey yashigo part din bayansa kuma ammi ce , ganin halin da tahee take cikine yasashi dubansu”dada ya akai haka ,da ansani tun lokacin da ta samu wannan ciwan an duba matashi,ciwo irin haka ai ba dadi” girgiza kai dada tayi”kaide kasan wannan ,Nima da muke tare da ita bansan da wannan ciwan ba ,nasan de tace mun ta fadi,mijinta kuma be fada mun ba” kamar ammi zatace wani abu sai tayi shiru kawai tana bin taheen da kallo, sallamar ummey ce ta katse musu zan canai, kara soma tayi ciki ganin yadda ko wannan su yayi cirko cirko, dai dai lokacin da su uncle salim suke shigowa falon, “Yawwa “ dada ta furta ,”yanxu kawai abunda za ai Akira likita ya duba ta,Kai saleem kirawo likita yanxu”, tsayar da ita abeey yayi ta hanyar furta”bari na kira mujinta yazo ya dubata dai “, kowa sai faman sannu yake mata, ganin lokacin sallah yayi ne yasa dada umartar kowa da yaje yayi sallah sai su dawo,itama taheen da kyar take tsayar da kafar tata sabida dan kunburin da tayi a hakan tayi sallahr tata cikin natsuwa kamar asalin tahee dinta, tana idar da sallan ta kwanta a wajan, anan bacci ya kara daukarta. Shigowa dada tayi hannunta dauke da fura ganin yadda take baccinta cikin kwanciyar hankali yasa dada kura Mata ido” ko dai cikine da ita” ta furta a ranta, kafun kuma ta kawar da zancan ta hanyar ajje mata furan a gefe tare da fita daga dakin. 🫧🫧🫧🫧🫧 9:30 motocin king suka danno kai cikin gidan , part dinshi yayi niyar zuwa sabida yanda ya gaji, tuno kiran da abeey ya masa ne yasa ya nufi part din dada, a hankali ya zuro da kafarsa kafun ya fito da gangan jikinsa gabaki d’aya tare da nufar part din, dada da abeey ya tarar a falan sai su uncle musaddiq da suke dan hira kasa kasa, dada na ganinsa ta jefa masa harara “ shanyar da ka shanya sun bushe saura babbaka” dauke idanuwansa yayi kanta tare da kallan abeey ,ganin yaki kallansa ne yasa jikinsa yin sanyi kadan kafun ya karaso cikin falon,ba tare da abeey ya kallesa ba ya furta “kaje ka duba lapiyar matarka”,cikin kasa kasa da murya ya furta “am sorry abeey” ko su uncle musaddiq basuji me yace ba se shi abeey din ,dago da idanuwansa yayi cikin dan rauni ya furta “ka kula da ita” jinjinawa abeey kai yayi cikin kwantar da murya ya furta “insha Allah” ,nauyayyar ajiyar zuciya abeey ya saki tare da sakin gun tun murmushi, king kai tsaye dakin dada ya shiga, kwance ya tarar da ita kan sallaya sai faman baccinta take hankali kwance, karasowa yayi cikin dakin tare da durkusowa kadan,sosai ya ke kallan fuskarta musamman dan wajan da yayi ja kadan,yadda ta turo bakinta ya kalla “cikin barcin ma” ya furta tare da dauke kansa,hannayensa yasa tare da daukarta kamar wata baby yana shirin fita daga dakin,dada ta shigo” iskancin kuma anan zaka fara” hade ransa yayi kafun ya kalleta” ko mu zauna anan dakin zefi “sakin baki dada tayi tana kallansa jin kalaman sa,”Nide babu ruwana, furar ta hura nazo dakko mata daman tunda yau taki cin abinci, yar hirar ma yau batayi ba”ta karara zan can nata tana dauko wata sabuwar furar cikin fridge ne dan girma,tana mika wa king ko dago da fuska ta kallesa takiyi wai ya fi karfinta, ta na mika masa tashi toilet shi kuma dan kallan taheen yayi jin ko abinci bataci ba kafun ya bar dakin, a falo ya tarar da oummey da ammey, kowa kallan mamaki ya bishi dashi ganin yadda ya dakko taheer,abeey kuwa sosai hakan yayi masa dadi,gaishe da su oummey Kwarai yayi tare da barin part din gabaki d’aya . ****** Direct wani daki ya shiga da ita dake kasan stairs komai nacikin dakin fari ne kal dashi ,sosai dakin ya hadu iya haduwa,kan lallausan gadan ya nufa tare da kwantar da ita ,sannan shima ya bar dakin,kusan tsawan lokaci kadan ya dawo sanye da wasu fararan phyjamas fari tas dashi me shegen laushi da san tsi , da alama Wanka yayi, kamshin imperial majesty ta ko ina ya cika dakin, inda take ya nufa hannunsa dauke da wani dan kwalbar dan karami,a hankali yake bin kyakkyawar fuskarta da kallo ganin yadda take ya mutsa ta,kafar data dan kunbura ya fara bi da kallo,kafun ya kai hannunsa a hankali kan kafar,kamar wacce aka sanarwa ta farka arazane tana sakin kara, Wanda ta gani ne yasa ta dan turo bakinta, tare da dauke idanuwanta tana share hawayan idanuwan,guduwa zatai akan gadon kafarta ta kara rikewa ,kallan ta danyi Ganin har yanxu taki kallansa,rike kafar tata da ta kumbura yayi gagam batare da yace komai ba, kara tahee ta saki,tana rike hannunsa da ya rike mata kafar,”da zafi ,ni banaso”ta karasa zancan nata da sakin wani marayan kuka, be ce mata komai sai hade ransa da ya karayi,kafar da ta kunbura yake matsawa a hankali tare da shafa man da ya dauko,duk da haka sosai take jin zafin,fuskarta duk ta baci da hawaye,”Banasan ka dady, I hate you” shine abunda take faman fada ganin ta kasa kwace kafarta da yake matsa mata,har dodan kunnansa yajiyo sautin I hate din you din data fada, be kyaleta ba sai da ya gama matsa kafarnan sosai,lokacin har kukan ya dauke sai sheshshekar da take faman saukewa,bece mata komai ba ya mike ya fita, be dade da dawowa ba ya shigo da wata kwarya ,mika mata furar dake ciki yayi,karba tayi idanuwanta na zubar da hawaye ta shanye furar daman yunwa take ji, magungunan ta ya mika mata,yanxun ma bata dago ba ta karbi maganin tasha,bayan ya hada allura yayi mata shima,da mamaki ya ke kallanta”fushi” ya furta kasan zuciyarsa , ganin yadda taki kulasane yasa shi dauke kansa cikin hade rai shima” wanka”yanxun ma batace komai ba ta mike tana dan gisawa kadan kadan,duk da ta gane ba wancan dakin bane haka ta nufa wata kofa ta shiga, kamar yadda wancan dakin yake haka wannan yake shiyasa batayi wahalar gane toilet ba, Wanka tayi cikin sabulan wankan toilet din masu shegen kamshi, kafin ta fito tana din gisawa a hankali,turo bakin ta tayi kadan tana bin wajan da kallo , cikin karanbani ta danna wani button,a hankali kuwa wajan ya fara budewa,wasu budaddun wardrobe suka bayyana , dan murmushi ta saki tana bin kayan wajan da kallo,wata white t-shirt ta dauka,sosai rigar tayi mata burgujeje har wajan qwiwarta,pant kawai ta saka tare da feshe jikinta da turare, sai wata hula da ta saka haryanxu gashin ta be shige jiki ba sai faman zamewa take, rigar data saka kuwa sosai yayi mata kyau kamar dan ita aka fita, juyawar da zatayi ne idanuwansu ya fada na juna, da Sauri ta d’auke idanuwanta tana juyawa,be ce mata komai ba ya fito daga dakin,kin fitowa tahee tayi daga wajan kusan tsawan lokaci saida ta ga hasken wajan ya d’auke duka kafun ta fito cikin sauri tana furta “dady” karo da tayi da abune yasa cikin tsoro ta fara shafa sa tana furta “dady”,uhmm kawai yace mata ,sosai ta damki rigar jikinsa kamar wacce akacewa za a kwace mata shi,soma taku yayi a hankali ganin duk taku dayan dazai yi sai tayi itama har suka karasa kan gadon, tana jin ta akan gadon ta kara lafewa a jikinsa, magana yake san furtawa amma bakinsa ya masa nauyi, ya dau dogon lokaci yana juya maganar tasa,”bai san lokacin da bakinsa ya furta “fushi kike “kara lafewa tayi ajikinsa ba tare da tace masa komai ba sai dan bakinta da ta turo masa,kamar wacce aka sa dole cikin muryar kuka ta furta”Itace ta mareni” kinaso na rama miki ya tanbayeta , da sauri ta daga masa kai kafun ta kara cewa “kuma taji mun ciwo” shima zamu rama,”kuma ka kara tabamun kafata, a hankali ya kai bakinsa Daidai kunnanta ka fun ya furta “yanxu Lefi nane ko” Kai ga jinjina masa,saman goshinta ya dan summata kadan kafun ya furta “shi yasa kikace kin tsaneni”turo masa dan karamin bakin ta sakeyi ,cikin wauta ta furta “ai yanxu ina sanka” tana karshen maganarta ya hade bakinsu waje d’aya…… ******** KUYI HAKURI DA RASHIN JINA KWANA BIYU DA BAKUYI BA. MSS LEE 💖 💖💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖💖 💖💖GIDAN AUNTY💖💖 (a heart touching love story) Story & written By Mss Lee 💖 PAID BOOK MAI BUKATAR COMPLETE DIN GIDAN AUNTY YAYI MUN MAGANA TA WANNAN NUMBER 07041879581. BOOK 1 Page 39-40💖 A hankali yake bata wani irin passionate kiss me tsayawa arai, ya dau dogon lokaci a haka kafun ya zare bakinsa cikin nata yana bin kyakkyawar fuskarta da kallo,rintse idanuwansa da suka fara kadawa yayi kafun ya furta “ what’s wrong with me”,cikin zuciyarsa ,be an karaba sai saukar lips dinta yaji cikin nasa,sosai itama take kissing din bakinsa kamar yadda yayi mata,tun lokacin da ta dora bakinta a kan nasa ya kasa motsi,sosai yake mamakinta gabaki d’aya ta kwance masa notukan kansa mamaki yake ta yadda ta iya wannan abun, a hankali ta zare bakinta cikin nasa tana bude idanuwanta,kyakkyawan murmushi ne ya bayyana kan kyakkyawar fuskarta da yasa dimples dinta lotsawa, bin dimples dinta yayi da kallo kafun ya sauke shi kan dan karamin bakinta da yayi jawur,”Nima na rama “ ta furta tana sakin dariyar da ya karawa fuskarta kyau da annuri,kamar wacce tayi wani babban abu harda yi masa kwalo ita a dole ta rama,yar karamar ajiyar zuciya ya sauke kafun ya gyara kwanciyarsa gefanta,ya dau kusan 3 minutes be ce komai ba kafun ya bude idanuwansa, a hankali ya furta” ko me akai miki se kin rama kenan ko”da sauri ta daga masa kai tana turo dan karamin bakinta ,kallan dan karamin bakin yayi kafun ya dauke idanuwansa “shiyasa dazu kikace a wajan dada zaki zauna kenan”, ya furta mata a hankali kamar Wanda aka sa dole, yanxu ma turo masa bakin tayi kafun ta furta “dady ta mareni fa kuma ta jimun ciwo”idanuwansa ya dan waro kadan” dagaske” ya furta, yanxu ma gyada masa kai tayi ,”oh shiyasa akace ba a sona kenan”, ya karasa zan can sa yana kauda kansa gefe,girgiza masa kai tayi cikin sauri ta furta” Aah ina sanka yanxu ai”,shareta yayi ba tare da ya tanka mata ba,matso da fuskarta tayi daidai tasa tare da furta “ina sanka fa dady”, juyar da fuskarsa ya karayi, itama kara matso da tatan tayi ita a dole sai ya kalleta, fahimtar hakan yasa king kara dauke fuskarsa, cikin murya kamar wacce zata saki kuka ta furta “Allah ina sanka dady”, yanxu ma shiru yayi mata Hakanan yau yake san yi mata magana,kuka ta fashe dashi ganin ya ki kulata, mikewa tayi zaune da niyar sauka daga kan gadon gabaki d’aya ,riko hannunta yayi ba tare da yace komai ba y jawo ta jikinsa , lafewa kuwa tayi tana faman sauke ajiyar zuciya kafun ta dan dago ta kallesa “ dady ina sanka kaji” ta furta har yanxu bata dena kukan ba ,amaimakon ya bata amsa sai ya furta “bana san kuka”, share hawayen ta farayi kafun ta kara lafewa a jikinsa tana faman yin shesh sheka kadan kadan, be san lokacin da ya kai hannunsa baya ba yana shafa mata a hankali, kusan tsawan lokaci ya dauka yana mata haka kafun ya fara jin saukar nunfashin ta akan kirjinsa alamar bacci ya dauketa,gyara mata kwanciyarta yayi kafun ya kashe musu hasken dakin gabaki d’aya sea wata dum light da ya bari blue colour, a hankali ya karanto musu adduar kwanciya bacci kafun shima wani baccin ya daukeshi. *********Wutace take tashi sosai a Wajan, duk ruwan da aka watsa mata sai wutar ta kara tashi kamar ana kara kunna ta,mika masa hannunsa yake yi ,a hankali yake furta “Akhie,Akhie”, so yake ya kwace jikinsa ya shiga cikin wutar ko xai ciro wanda yake ciki Amma sosai suka rikeshi,gabaki d’aya karfinsa yasa ya hankadasu suka fadi, da mugun gudun gaske ya nufa wutar kamar be san zafinta ba, wani irin tashi wutar tayi tare da tar watsewa a wajan,gabaki d’aya wajan ya dauki hayaki, a hankali yake furta “AKHIEE” kafun nunfashinsa ya dauke gabaki d’aya. Mutsu mutsu ya fara yi da kansa da ya gama jikewa da zufa kamar Ac bata wura cikin dakin,sosai ya matse tayi dake jikinsa ,da yayi sanadiyyar farkarwa sabida irin matsar da yayi mata, har yanxu fuskarsa a kulle take, a hankali yake furta “Akhie” cikin fusgar nunfashi kamar Wanda nunfashinsa ke neman daukewa. Kura masa ido tahee tayi kafunta furta” dady da zafi”, kara matsetan yayi a jikinsa kafun ya furta”Akhie “da dan karfi tare da ware idanuwansa dasukayi mugun kadawa sukai ja,saurin mikewa zaune yayi yana mayar da ajiyar zuciya a hankali a hankali,duk abunda ya faru ashekarun baya shine yasake dawo masa cikin kwakwalwarsa da kullum yake tunawa,dan siririn diamond chain din hannun sa da baya cirewa ya kalla me harafin M&T,sosai ya zubawa chain din ido kamar mesan tunawani abu, nunfashinsa ne ya fara yin kasa kasa kamar me shirin daukewa gabaki d’aya,a hankali kirjinsa yake sama da kasa kamar me kokarin kasa controlling din nunfashin nasa, TAHEE data tashi zauna ne ta matso kusa dashi kamar me shirin yin kuka “dady”,be kulata ba har yanxu nunfashinsa kuma be dena kokarin kwacewa ba jijiyoyin kansa sun fito rudu Rudu duk da ba’a gani sabida Duhun dakin,bata san ya akai ba sai gani kawai tayi ta rungumeshi a jikinta tare da dora kansa akan cinyoyinta, sosai ya matse cikinta kamar Wanda akacewa za a kwace masa ita, ahankali ta fara shafa masa bayansa kamar yadda taga yana yi mata,nunfashinsa ne ya fara daidaita kafun a hankali wani baccin ya daukeshi a yadda yaken, kokarin janyeshi tayi, amma ya kara riketa gagam,lumshe idanuwanta tayi tare da jingina da jin gadon itama a haka bacci ya dauketa. 🫧🫧🫧🫧🫧 Kiran sallar asuba na farko ne ya tayar dashi da kyar ya iya bude idanuwansa da sukayi masa nauyi, kallan yadda ya kwanta yayi kafun ya sauke idanuwansa a kanta ,sosai ta bashi tausayi, a hankali ya daga jikinsa daga kan nata ,yasan da kyar in wuyanta be mata ciwoba,gyara mata kwanciyar yayi kafun ya mike ya shiga wani door , be wani jimaba ya futo sanye da farar jallabiya tare da nadin larabawa, sosai kamanninsa ya kara fito wa na sak larabawan sai faman tashin kamshi yake kamar ba asubahi ba, a hankali yake yin komai ,mafarkin da yayi na kara dawo masa,ganin ana kokarin tada sallah ne yasashi fita a dakin gabaki d’aya. Be dade da fita ba tahee ta farka daga baccin ta,sosai wuyanta yake mata ciwo da cinyoyinta,dubawa tayi taga king bayanan turbune fuska tayi kamar yana kallanta kafun ta mike taje tayo alwala, tana cikin yin sallar yashigo dakin,kan gadon ya koma kamar Wanda akasa dole sai faman ya tsina fuska yake sabida yadda kansa yake tsananin sara masa,kafin ta tashi daga kan sallayar har wani baccin ya fara fisgarsa, a hankali ta fara taku ita a dole karta tasheshi taje ta kwanta itama a hankali,duk abunda take yana kallanta motsawane kawai baze iya va,be dade ba wani saban baccin ya daukesu gabaki d’aya. 9:45am tahee ta soma mitsi mitsi da idanuwanta kafun ta budesu gabaki d’aya,gefen da yake ta juya wayar taga babu kowa, da sauri ta mike tare da nufar hanyar fita, har ta saka hannunta da niyar bud’e kofar ta tuna gargadinsa “kada ki kuskura ki kara fitowa nan baki yi wanka ba,kaxama “,shagwabe bakinta tayi kafun taje tayi wankan shaf shaf ko munti 10 batayi ba kafun ta shirya cikin wasu riga da wando na pakistan masu taushi da santsi,gashin kanta da ya zubo mata kar gadan bayanta tayi kiciniyar daurawa ganin ta kasane yasata daukar ribbon din tare da nufar falo, ba kowa a falo sai kamshin daddadan kamshi da yake tashi ne cike da sanyayyar kamshin ac, kofar fita daga part din ta nufa hannunta dauke da ribbon dinta ga gashinta da ya dauko mata har wajan kwankwasanta sai faman sheki yake dauka,Daidai ta sa hannu zata bude kofar taji an turo kofar da karfi. Sanye take cikin wasu kananan kaya da basu dame jikinta sosai ba ,fuskarta Tasha uban makeup da bakin glass a idanta sai faman taunar cingum take, a yatsine take bin tahee da kallo irin kallon up and down dinnan, ta be bakinta tayi tare da kokarin shigowa ciki,wani irin kallo tahee ta jefa mata kafun ta furta”wacece ke”,daga hannu budurwar tayi tare da tsinkawa tahee mari a fuska”tanbayata kike wacece ni dan uwarki”. Tunda ta cinka mata marin tahee take dafe da kuncinta,kalmar uwarkice ta tsaya mata arai,itama batayi wata wata ba ta tsinkawa budurwar mari hagu da dama kafun ta dago idanuwanta a zuciye tana binta da kallo, cike da tsantsan mamaki budurwar take bin tahee da kallo itama hannunta dafe da kumatunta, dan ba kadan taji zafin marin ba”ni kika mara “ta furta kamar me shirin yin kuka ,banza tahee tayi da ita kafun ta juya tare da komawa ciki, tana cikin tafiyar taji anwani fusgota tare da hankadata, rufe idanuwanta tayi sosai ganin tana kokarin faduwa, a maimakon ta fadin sai taji an tarota,tare da saukan tagwayen maruka dafe kumatunta tayi ganin ba ita aka mara ba ,kafun ta bude idanuwan a tsorace,Wanda ta ganine yasata sakin ajiyar zuciya kafun ta kara rikeshi gagam. Suman tsaye budurwar nan tayi jin saukar marin da ba a taba mata shiba a duba,hawayene sosai suka cika mata idanuwa kafun ta dago da idanuwanta ta kallesa,sosai ya kara yi mata kyau fiye da kullum da take hasashensa acikin zuciyarta, kalllansa take kamar wacce tasami abun kallo kafun ta soma magana“yanxu king akan wannan shegiyar da take muku wasan kwaikwayo da rayuwa zaka sa hannu ka maran”, kamar wacce tayi magana da dutse haka ya mayar da ita a wajan,ribbon din hannun tahee ya karba itama bai ce mata komai ba ya tufke mata gashin kafin ya ja hannunta suka bar wajan. Sakin baki tayi tana kallan abunda yake wa yarinyar da taji lokaci d’aya ta tsana ,abunda ko a mafarki in aka fada mata bazata taba yadda dashi ba ,wai yau shine yake taba mace ba ita ,ganin sun juya ne yasata bin bayansu tda kallo ganin irin wulakancin da king yayi mata a gaban kaskantacciyar da takewa kallan me aiki”kamar ni, Basma isma’il yar governor guda aka mara agaban wannan kaskantacciyar”,da karfi ta furta”impossible gaskiya bazai taba yiwuwa ba, dole ma mom kisan yadda zakiyi ayi auran mu da king cikin kankanin lokaci kafun nan kuma sai na gyarawa shedaniyar can zama” tana kammala zancanta tabar wajan cike da bacin rai. Suna shiga daki ya saki hannunta kafun ya kalleta rai abace “ ba kyajin magana ko,kunnan kashine dake, baki isa a hanaki abuba” baki ta bude zatayi masa magana ya daga mata tsawar data firgitata har da ja baya kadan” shut up” ya kara daka mata tsawa “ daga yau in ina magana na kara gani kinsa mun baki, I will beat the hell in side you, stubborn girl” yana kammala zan cansa ya nufi kofa har zai futa ya dawo kallo d’aya yayi mata kafun ya furta “ idan na kuskura na kara ganin kafarki a waje zakiga abunda zai faru” ya karasa a zuciye tare da barin dakin. Sai a lokacin ta fashe da kuka ,gawani tsoran shi daya cika mata zuciya lokaci d’aya,sosai take yin kukan ga wuyanta dake mata ciwo ,a tsakar dakin ta kwanta har yanxu tana sakin kukan kamar wacce akace mata dadyn ta ne ya mutu, tafi tsawan mintuna 30 a kwance a wajan tun tanayin kukan da karfi har ya dena fitowa sai hawayen dake fito mata kadan kadan. Turo kofar dakin yayi hannunsa dauke da plate madaidaici, ajje plate din yayi a can center table din falon batare da ya kalletaba ya kara fita daga dakin, a hankali ta dago da kanta kan plate din da ya ajiye ,kafun ta kara sakin wani saban kukan muryarta har dushashewa take,gajiya da kwanciyar kasan tayi ta koma kan gado duk da tsananin yunwar da take ji, sanyi ta fara ji sosai shiyasa ta lulluba cikin bargon ko hangota ba a yi. *****Direct yana fita daga dakin part din dada ya nufa ,hayaniyar da ya fara ji tana tashine yasa shi fasa shiga part din tare da nufar part din abeey. A shingide ya samesa kamar kullum sanye da fararan kaya yana karatun jarida , a hankali king ya karaso cikin falon kafun ya samu waje ya zauna, ya dau kusan mintuna uku be yi magana ba, shima abeey beyi maganar ba sai binsa da kallo da yake yi,sosai yake jin tausayin sa, ba abune me sauki ba zama da wacce tayi loosing memory ba har bata yadda da kowa sai kai,muryar king ce ta dawo dashi cikin tunanin da ya fada” abeey ina kwana” wani yalwataccen murmushi abeey ya saki,tun lokacin da akai Auran sai yanxu king ya shigo falon ,ya sani sarai fushi yake dashi, cikin farin ciki ya furta”ka tashi lapiya son”jinjina masa kai king yayi, kafun ya mike da niyar tashi,kalaman abeey ne suka ratsa kun nuwansa” am sorry son” tada sauri ya girgiza masa kai “ stop apologizing please abeey,ni bakaimun komai ba”.girgiza masa kai abeey yayi “ah ah son, nasan haryanxu kana fushi akan Auran da mukayi mata”,be karasa zan can nasa ba king ya girgiza kansa “abeey Ka dena wannan tunanin ,bazan taba fushi akan farin cikin kaba “kalaman king sosai yayi wa abeey dadi,besan lokacin da ya saki murmushi ba tare da furta”Allah yayi maka albarka son”,lumshe ido king yayi kafun ya furta Ameen a hankali,ya dan jima a Wajan abeey suna tattaunawa kafun yayi wa abeey sallama,yana fito wa daga part din suka ci karo da sha’aban, dan waro idanuwansa yayi kadan kafun ya tabe bakinsa “finally the Parrot is here “ ya furta cikin zuciyarsa.kyakkyawan saurayine chocolate colour fuskarsa cike take da murmushi, Wanda ya gani ne yasashi kara sakin wani murmushin kafun ya furta “my gee”dan hararansa king yayi kafun suyi hugging din juna, sosai saurayin yake sakin murmushi bayan sun rabu,”nayi missing dinka gee kamar ba gobe “ta’be baki king yayi kafun ya furta “ina Mahma take” sakin baki saurayin yayi yana bin king da kallo” yanxu gee sabida baka da mutumci nagama ce maka nayi kewarka shine kake tanbayata mahma,toh baza’a fada ba”,dafe kai king yayi kafun ya furta “oh my god sha’aban kafara samun ciwon kai, wai mema ya kawo ka”dariyar keta Wanda aka kira da sha’aban din ya saki kafun ya furta “nazo ganin amarsune, tunda kayi aure babu goran gayyata “ gajeran tsaki king yaja kafun ya furta “I don’t have your time “yanxu ma dariya sha’aban yasaki”dole ka fadi haka mana king tunda ka angwance kalli wani kyallin amarci da kake”Naushi king ya kai masa a kirji yana kaucewa , a hankali ya furta “parrot”,daga hannu sama sha’aban yayi kafun ya furta accepted,girgiza kai king kawai yayi tare da kama hanyar part dinsa ganin ankusa yin sallar azahar,shima sha’aban part din abeey ya shiga yana furtawa king sai yazo cin abincin amarya. ➰➰➰➰➰ Yana shiga part din nasa yaga bata falo sam ya manta da zancan yace mata kada ta fito a dakin, a gogon hannunsa ya duba 1:10pm, dakin da suka kwana ya nufa kai tsaye sai alokacin ya tuno da abunda ya faru,dafe goshin sa yayi kafun ya furta “ya salam “ yana shiga cikin dakin,yana shiga dakin da plate din da ya ajje mata na abinci ya fara cin karo ,yana nan yanda ya ajjesa da alamu ma ko tabashi ba aiba, cikin dakin ya karaso yana bin dakin da kallo dan ganin ta inda zata bullo, a saman gadon dakin idanuwansa ya sauka, sosai ta takure waje daya kamar me jin sanyi, cikin sauri ya karasa kan gadon kafun ya yaye bedsheet din,da sauri ta tashi zaune a firgice da alamu bancin nata be yi wani nisaba, tana ganinsa ta kara ja baya da sauri kamar wacce taga wani abun tsoratarwar,”me ya Hana ki cin abinci “ ya furta yana binta da idanu, a hankali ta furta “na koshi dady”kamar wacce aka sa dole,karasowa kan gadon yayi kafun ya dora hannunsa kan forehead din ta,zafin da ya jine yasashi saurin kallanta,ganin tana kokarin lumshe ido,”open your eyes “da Sauri kuwa ta bude idanuwan nata har yanxu tsoran nasa be fita a ranta ba, fita yayi daga dakin ba jimawa ya dawo hannunsa dauke da wani mug me shegen kyau, tea ne a ciki mea dumi sai faman tashin kamshi yake,mika mata yayi ba tare da ya kalletanba “shanyesa duka “baki ta bude zatai magana ya bita da rikitattun idanuwansa,da sauri ta kar ba ta farasha saura kadan ta kware,saida ta kammala sha ya kyaleta ,ganin yadda take sun kuyar da kaine yasa ta bashi tausayi duk da yasan ba lefin ta bane , a gefan gadan ya zauna kafun ya janyota jikinsa yana rungumeta,kuka kawai tahee ta fashe masa dashi ,tapping din bayanta yayi a hankali kafun ya dagota “kayi hakuri dady” ta furta a marairaice ,dogon hancinta yaja yana dan dungure mata kai, dariya ta fashe dashi kafin ta kara rungumeshin. 🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧 YOLA bakaramun ukubar rayuwa su taheer suke fuskanta ba, gashi sau daya ake basu abinci a rana sai biredin da ake jefo musu kamar wasu kaji, mutanan cikin dakin har yan rige rigen dauka suke sabida bakar azabar da suke fuskanta. Suna kwance a inda aka killacesu a ka bude kofar dakin,kowannansu rarra kubewa yayi gudun kar a gansu, mutane biyar mutumin ranar nan ya zaro, ciki har da taheer , bugun su mutuminnan ya fara kamar Wanda aka kaiko, kafun ya samu wani d’aki me shegen duhu ya kullesu a ciki, ko wannansu ba me motsin arziki aciki shash shekar d’aya daga cikin suce ta cika musu kunne a hankali taheer ya bude idanuwansa da sukai masa nauyi kafun ya soma magana “me yasa kake kuka”kara fashewa da kukan saurayin yayi kafun ya furta “gida nake so na koma” daya daga cikin sune ya amsa masa a wahale shima “muma dukan mu muna so mu koma gida amma ba yanda zamuyi, ni so nake na samo hanyar da zan futa daga wajan nan,mutanan nan basu da imani ko kadan,bamuyi musu komai ba suke cin zalin mu,kamar yadda sukai wa sauran muma ina tunanin siyar damu zasuyi”be karasa zan can nasa ba yaji an banko kofar, saurin gimtse bakinsa yayi, wani gabjejene ya shigo dakin ,yanxu ma jibgarsu yayi cikin mugunta da rashin imani kafun ya jefo musu guess’s guda uku da pure water guda biyu ,kamar Wanda suka shekara basu ci abinci ba haka suka samu guntuwar gurasar nan sunaci ,kalaman saurayin can ne yake ta faman kai kawo a zuciyar taheer,sosai kwadayin samun mafitar ta yanda zasu gudu ya shiga ransa shima ,babu Wanda ya kara magana a cikin su sabida yadda ko wannansu yake jan nunfashin azaba. ➰➰➰➰➰➰➰➰ BUNKURE Acikin yan kwanakin nan sosai kaka ta bawa ta rame,duk lokacin da ta kwanta bacci mafarkin su oumma kawai take, tun abun baya tamun ta har ya soma damun ta,sosai ta shiga dana sanin abunda ta dinga yi musu alokacin baya , kusan kullum kenan yanxu sai ta leka dakinsu ko zata ga sun dawo, mutanan gidan ma ko wannansu ya fara shiga taitayinsa sabida wahalar baccin da suke samu cikin tare ,da yawa daga cikin su suka nutsu . A ban garan su Dije kuwa liyafa ce ta karu, yanxu kwata kwata bintalo bata kwana a gidan sai dai tazo da safe tayi abunda zatayi ta bar gidan , wani lokacin ma kayan ta kawai zata iya ta har gidan, har yanxu kuma babu me daga mata yatsa sabida duk ta bawa boka sunayensu . Dije kuwa ko a jikinta halin da bintalo ta jefa kanta ,tunda tana kawo mata kudi,burin ta daman ta samu kudi,yanxu har wata kawa tayi me suna hajjo aunty, hajjo aunty makirar matace ,burinta kawai ace tafi wani, sun hadu da dije ne a wani biki ,shikenan suka kulla alaka mai karfi kamar wacce suka yi shekaru da dama tare , yanxu ko wana sirri na Dije ,hajjo aunty ta san dashi, itace kuma me bata shawara,yanxu itama hajjo ta fara sawa Dije kwadayin yawo kamar yadda take,a tunaninta ai shine kadai hanyar da samun kudi kafun su tura bintalo can burniii. 🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧 ➰➰➰➰➰➰➰➰➰➰➰ LAGOS 8:30pm ya shigo cikin gidan , be nufi part din kowa ba sai na dada, babu kowa a cikin falon wani daki dake facing din na dada ya shiga,kamar yadda yayi hasashe kuwa tana kwance kan gado tana baccinta cikin kwanciyar hankali, kiss din da tayi masa a kumatu ne ya fado masa rai kafun ya kawar da zancen yana karasa shigowa cikin dakin , be jira komai ba dauketa kamar wanda ya dauki baby ya fito da ita, a maimakon ya fita daga part din dada wani corridor dake jiki ya nufa daga jikinsa wani dan adone a wajan ,adan wajan ya dan karkata kadan,take a Wajan jikin bangon ya tsaye wata kofa ta bayyana,shiga yayi ciki kafun ya kulle ta ciki, daga wajan kuwa kamar babu wata tsaga da ya taba yi a wajan, yar tafiya yayi kadan kafun ya bude daya daga cikin kofofi ukun da ke wajen, yanxun ma yar guntuwar tafiya yayi,kafun ya bude wata kofa,yana bude kofar kai tsaye bedroom din da suka kwana ne ya bayyana sai faman tashin kamshi dakin yake kamar kullum,kwantar da ita yayi kan bed din kafun ya warware mata veil din jikinta yana gyara mata kwanciyar . Sai da yayi Wanka kafun ya fito daga part din nasa , direct part din ammi ya nufa, koda ya isa part din ammi na kitchen sai faman aikace aikace suke,shigowar sa falon ne yasa ammey fito wa da yalwataccen murmushinta na kullum da ta saba, tana ganinshi ta bude masa hannayenta a hankali ya karasa wajan ta kafun yayi hugging dinta, cikin sanyayyar murya kamar bashi ba ya furta”nayi kewarki ammey “itama ammeyn cikin sanyin jiki ta furta “Nima nayi kewar ka sosai son,ya kake ya daughter na”gingina mata kai yayi kafun ya furta “all will be alright ammey,trust me zata ganeki soon” murmushi ammi ta saki tana ja masa hancinsa “ai na yadda da son dina ,shiyasa bani da wata damuwa”lumshe mata ido yayi yana budewa, kunun aya ta kawo masa tare da abinci, kunun ayan kawai ya sha sosai batare da yaci abinci ba,sun dau tsawan lokaci suna tare kafun yayi mata sai da safe. Koda ya fita daga part din ammey part din ummey ya nufa,ko da ya shiga part din itama tana kokarin fitowa ne , ganin shine yasa ta koma,bayan gaisuwa babu wani abu da ya kara shiga tsakaninsu,Mikewa yayi da niyar tafiya yaji saukar muryan ummeyn sa”ya jikin daughter “ajiyar zuciya ya sauke kafun ya furta “Alhmdllh “,ummey bata kara cewa komai ba tsawan 2 minutes kafun ta furta ,”gobe UMAIMA zatazo” harbawa zuciyar sa taji jin umaima zata zo amma a fili babu alamun hakan a fuskarsa sai “Allah ya kawo ta lapiya “ da ya furta yana barin part din…. 💖💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖💖 💖💖GIDAN AUNTY💖💖 (a heart touching love story) Story & written By Mss Lee 💖 PAID BOOK ME BUKATAR GIDAN AUNTY COMPLETE YA TUNTUBENI TA WANNAN NUMBER 07041879581. BOOK 1 📕 Page 41_42 💖 Karfe 11 na dare ya nufi part din dada ,lokacin ba kowa a cikin falon ko ina na wajan ya dau shiru, wani corridor ya nufa kusan tafiyar mintuna 2 kafun wasu kofofi su bayyana a wajan,kofar hagunsa yayi knocking ,kusan mintuna d’aya ba a amsa ba, kara knocking yayi nan ma shiru, juyawa yayi da niyar komawa wata kamilalliyar murya ta bashi izinin shigowa , a hankali ya tura kofar dakin ,babban falone a wajan me shegen kyau da haduwa,komai a cikin falon ya hadu iya haduwa, tsaye take cikin maroon din hijab dinta daya kara fito da kyawun fuskarta da alama sallah ta idar yanxu, murmushi ta sakar masa tana buda masa hannun,cikin takunsa na kullum ya karasa wajanta tare da rungumeta ba kowa bace face ZARMEEN wato kanwar abeey auta ga dada kuma .”mahma “ ya furta yana kallan kyakkyawar fuskarta,dungure masa kai tayi “babu wani mahma, se da ka ganni zakace mun wata mahma”, kunnuwansu ya rike “am sorry “dan tabe bakinta tayi “babu wani sorry da zan karba sai ka kawo mun daughter na ganta, tunda sai dai naji labarin auranka , ka kyauta son”, shiru yayi mata ba tare da yace mata komai ba” kama hannunsa tayi suka zauna kafun ta kallesa” yanxu son fadamun kana santa and ya kamanninta yake ” kallan aunty sa yayi na yan sakanni kalmar kana Santa na masa yawo arai “so!? Never, she’s too small for me”,ya furta cikin zuciyarsa ,kallansa aunty zarmeen tayi tana sakin murmushi” da alama dai ka fada santa da yawa tunda har ka kasa amsamun,gaskiya wannan daughter tawa ba karamun sa ‘a tayi ba and let’s go ,bari na nuna maka wani abu “ta kama hannunsa suna shiga wani daki , wasu designers din set din akwatunane acikin dakin milk colour masu shegen kyau, kallan mahma yayi alamaun karin bayani,murmushi mahma ta sakar masa “kayan legend daughter ne abeey yace a taho dasu sauran sai auntyn ka ta karaso gobe ,zauna se na bude maka” girgiza mata kai yayi “no need mahma” ta bude baki zatayi magana sha’aban yashigo dakin bakinsa dauke da sallama,tsayawa kallansu yayi kafin ya karaso cikin dakin “mahma yanxu kinga danki shine har kin fara mantawa dani” dan hararar sa tayi “ zaka shiga tsakanine “daga mata hannu yayi yana furta “toh mahma me kuke tattaunawa sannan wannan akwatunan na wanene “ budar bakin mama se cewa tayi “ka bari duk lokacin da ka kawo mun matarka kaima sai a dama dakai dan haka bamu waje “kyalkyalewa da dariya sha’aban yayi “Lalle Geee kana da farin Jini ,kowa kai yake so, basma ma sabida kai tazo gidannan Bawai gaishe da abeey ba kamar yanda ta fada, ga sauran yan matan gidan musamman wannan ne rawar kan”, wani shegen kallo king yabi sha’aban dashi kafun ya kalli mahma” good night mahma”murmushi mahma ta sakar masa “night too son”,kama hanyar fita yayi yana hararan sha’aban,cikin daga murya ya furta “ina gaishe da amarya”,Jan kunnansa mahma tayi,sai da ta bari king ya fita kafin ta furta “ka fita idona sha’aban”ouch ya furta yana kama hannun mahma din” mahma amma ba kya ganin king zai saki yarinyar nan d zaran ta dawo sense dinta,ko da ace yana santa mahma toh shi haryanzu ya kasa gane hakan,ya kamata kiyi wani abu akai”shiru tayi kamar me nasani kafun ta gyada masa kai “zan fara zuba masa ido tukunna” amma mahma basma fa kinsan ba dan kowa tazo gidan nan ba sai shi,gashi yana da mata”,gyada masa kai mahma tayi ,”wannan ba matsalata bane ,idan yace yana ra’ayin auranta fine, Inyace bayaso ai babu Wanda ya isa ya masa Auran dole ko” jinjina mata kai yayi alamar gamsuwa kafun su ci gaba da wata sabuwar hirar. ****tunda ya bar part din mahma zantukanta suke dawo masa ,”so!?? Din da tace shine abunda ya fi tsaya masa arai ga kayan lefe da suke shirin yi batare da sanin saba,yanxu shi yazaiyi ,dole yasan mafita tunkan abu ya kwabe masa Musamman idan small mom tazo gobe ,”ya Allah “ ya furta cikin ransa. Koda ya koma part dinsa be shiga dakin da take ba sabida hukuncin da ya Yankewa zuciyarsa dole ya nesan teta.hakan ce kuwa ta faru be shiga dakinta ba sai wani dakin sirrinsa da ya shiga , babu komai aciki sai na’urorin computers cike a wajan, d’aya daga cikin computers din ya nufa , a ciki ya hango yadda take bacci cikin kwanciyar hankali,abunda ya faru tun bayar fitansa ya duba, mamakine ya kara kamasa ya fuskanci duk lokacin da ya fita zai tarar an gyara ko ina , a tunaninsa masu aikine sai yau ya kara tabbatar da zarginsa , a nutse take yin sallarta,bayan ta idar karatun alkurani tayi cikin kira’a me dadi da natsuwa.mamakinsa be kare ba sai lokacin da ya ga ta gyara ko ina ,”Anya yarinyar nan ba aljana bace”. Kashe komai na wajan yayi tare da fita, lifter ya hau ya karasa 3rd floor dinsa , ko ina kamshin ac ne ke tashi kamar ba a amfani dashi, system dinsa ya dauka ,itama sosai yayi aiki akanta ya dade yana aiki akan system din har wajan karfe 3 na dare, har ya kwanta da niyar yin bacci kalaman mahma ya kara fado masa ransa “kana santa!?”, dogon tsaki yaja yana kokarin kawar da zancen amma ya ki barin sa , mikewa yayi tare da sakkowa dakin da take , har yanxu baccin ta take cikin kwanciyar hankali. Fuskarta ya zubawa idanuwansa, so innocent take baccinta kamar bata da damuwa, dan siririn gashinta da ya rufe mata ido ya sa dan yatsansa ya gyara mata kafun ya kara kallan kyakkyawan fuskarta,lips dinta da yayi ja sosai shine yafi daukan hankalinsa,daidaita fuskarsa yayi zuwa tata,sumbatan bakin nata yake kokarin yi ,kalmar “kana santa “ shine ya fado masa rai yayi saurin janye bakinsa kafun ya mike wajan gabaki d’aya yana rintse ido. Rana ta farko a rayuwarsa da ya kwanta akan sofa, sai faman rintse ido yake ko tunanin da yake ze bar zuciyarsa, ya dade yana kwance akan sofa din nan ,ganin kansa na sara masa ne yasa shi mikewa tare da komawa kan gadon, ko kallan inda take beyi a tunaninsa ko zai samu ya rintsa,abunda zuciyarsa ke kokarin kimtsa masa yake kokarin kaucewa,ganin yana kara wa kansa zafi ne yasa ya janyota jikinsa, a tare ko wannansu ya sauke a jiyar zuciya,a hankali kafin bacci ya d’auke shi. 🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧 YOLA 9:30pm Lokacin wani wahalallan bacci ne ya dauki mutanan dakin , TAHEER na gefe shima yana baccin wahalar, jiya yi kamar antabasa,a zabure ya mike yana kokarin kwace kansa, biyu daga Cikin mazajen da suke tare da sune suka rikeshi gagam bayan sun yi na saran bude kofar, idanuwansa kawai suka bar masa abude baya iya komai sai bin su da yake da kallo , komai suna yi ne cikin kulawa da taka tsantsan, sabida yadda gidan yake da wahalar futa amma duk da haka suka sha da kar, kamar sun san hanyar ko ina na wajan, sai da sukayi tafiya me Nisan gaske bayan sun fito dashi, wata mota da akai parking ne suka samu na sarar boyeshi a ciki kafun su juya da niyar tafiya, rike hannunsu yayi hawaye na zuba a cikin idanuwansa,a wahale ya furta “suwanene ku,me yasa kuka te makamun “, dayan guy din na kusa dashi ne ya kallesa amaimakon ya amsa masa tanbayarsa sai ya sakar masa yalwataccen murmushi”ka kula da kanka,wannan motar zata futar dakai daga Garin nan ,da zaran kafita kada ka sake ka kara waiwayota “ yana kammala zancan sa ya juya,kara rike hannun mutumin taheer yayi,”dan Allah ku fada mu suwanene ku”, dukansu murmushi suka sakar masa kafun Wanda ya rikewa hannun ya furta “SIF”,nagefansa kuma ya furta” LOLA”,basu kara bari ya furta wani abuba ,Wanda yace lola ya fesa masa wani farin abu a fuska take a Wajan bacci ya daukesa Daidai lokacin da motar nan ta soma tafiya, motar na barin wajan mutanan nan suka rikede tare da komawa macijansu. 🫧🫧🫧🫧🫧 ➰➰➰➰➰ Washe gari da wani irin ciwon kai ya tashi, da gyar yake bude idanuwansa da suka kada ,wani irin jiri jiri ne yaji yana kokarin kamasa, yana tashi itama tahee ta farka kamar wacce tasan lokacin tashinsa, a hankali ta fara karanto adduar tashi daga bacci duk a kunnansa,be kulataba har yaje ya shirya cikin wata ash din jallabiya ne shegen sanshi, kansa har yanxu da lemar ruwa alamun wanka yayi,yau ko masallaci be jeba anan cikin dakin yayi sallarsa,a haka tahee ta fito itama sai kunbura baki take ganin yaki kulata,cikin nutsuwa tahee ta kabbara sallar ta , komai cikin nutsuwa da bin ka’ida take yinsa, duk abunda take yana kallo amma haryanxu be motsa daga inda yake ba,tana idar da sallar ta soma karatun alkurani cikin wata kira’a me shegen dadi, lumshe idanuwansa yayi dan jin dadin karatun yake har cikin zuciyar sa,sosai ya kasa kunne yana sauraran karatun da take, ta dau dogon lokaci tana karatun kafun ta idar,a hankali ta nufi inda yake tare da dora kanta a saman cinyarsa,cikin sanyin murya ta furta “dady”yi yayi kamar be jitaba, ko motsawa beyi ba daga yadda yake,kara kiran sunansa tayi,amaimakon ya amsa mata se cewa yayi” baki iya gaisuwa ba”da sauri ta furta “dady ina kwana” banza yayi da ita kusan mintuna d’aya kafun ya bude rinannun idanuwansa da suka kada,kwata kwata besan dogan magana yau,”tashi ki zaune”ya furta ba tare da ya kalletaba,da sauri kuwa ta mike zaune” zan tanbayeki , ki amsa mun kawai “, be jira ta basa amsa ba ya fara tanbayarta game da karatun alquranin da ta fara karantawa , wanene ya koya mata",shiru tayi kamar me nazari kafun ta bude hannayenta biyu alamun itama bata sani, still tanbayar da yayi mata game da sallarta ,shima nan da hannunta ta nuna masa kafun ta furta “Nima ban sani ba”,tanbayoyi ya soma yi mata game da addininta, sosai kuwa take basa amsa ,shi kansa yayi mamakinta.a karo na farko daya furta “TAHEERA MOHAMMED”,be karasa kai zancen saba sabida yadda yaga tayi saurin dafe kanta,kallanta yayi kafun da kyar ya bude bakinsa “me ya faru” kanta kawai take nuna masa,shiru yayi yana binta da idanuwa tsawan mintuna daya kafun ya kara furta “taheera Mohammad “wannan karan kuka ta saka masa Sabida yadda taji kanta na mata zafi,tafukan hannayensa yasaka yana taba goshinta,babu zafi ko daya sai zufar da ta fara tsatstsafo mata,”ciwo yake miki” da sauri ta daga masa kanta, be ce mata komai ba sai mikar da ita da yayi tsaye ,direct kan bed din ya kwantar da ita, duk yadda take tsattsafo da gumi haka ta dage sai ta lulluba, be ce mata komai ba ya lullubetan,”karki bacci ina zuwa” ya furta mata a hankali,kanta kawai ta daga masa ,ya mike zai tafi kuma ta kara rike masa hannu,”dady kada ka tafi kaji”, lumshe mata eyes dinsa yayi “yanxu zan dawo” yana furta Hakan ya bar dakin , sunan da ya kira dazu take kokarin tunawa,ganin yadda kanta ya kara daukan zafine yasata rufe idanuwan nata, be jima ba ya dawo dauke da wani cup dan madaidaici, gefan fuskarta ya shafa , a firgice ta bude idanuwan ,Wanda ta ganine yasata binshi da idanuwa,mikar da ita zaune yayi kafun ya mika mata cup din hannunsa,”shanye ki ban kofin”,karban kofin tayi tare da kaishi Daidai bakinta, tana shakar kamshin sa tayi saurin janye bakinta, cikin marairaicewa tace “bana sha”kara hade ransa yayi kafin ya nuna mata cup din “kishanye kafun ran ki ya baci”kamar zatayi kuka tayi kurba d’aya ko hadiyeshi batayi ba ta fesoshi waje,sosai kuma ya batawa king farar rigar jikinsa,ta dago da niyar yi masa musu ganin yadda ya hade ransane yasata kara kafa kai cikin kofin, cikin sauri ta shanye abunda take ciki kafun ta mika masa kofin, ko minti d’aya batai ba ta mike daniyar barin wajan, hannunta na dama ya rike gagam tare da mayar da ita wajan da ta tashi,hannun ta fara kokarin kwace wa ,dayan hannun na toshe da bakinta, yana kula da ya na yinta sarai amma duk da hakan be sakar mata hannun ba sai ma janyota da yayi jikinsa,wani irin amaine yazo mata ba shiri ta fara kwarashi a jikinsa,lumshe idanuwansa yayi yana jin yadda take kwara bakikirin aman cikin fitar hayyaci,sai da ya bari ta gama kwarara aman kafun ya dagata a jikinsa gabaki dayanta ya nufi toilet da ita. ➰➰➰➰ Tunda suka watsa masa powder dinnan yake bacci cikin babbar motar da tayi kama da ta masu daukan kaya.tafiya ce me dogon zango tun suna tsayawa a hanya har suka dena ,cikin sharara gudu motar nan take tafiya har Garin Allah ya waye,har lokacin kuma taheer na cikin motar,cikin wani babban waje me cike da mutane suka tsayar da motar. Surutan mutanene ya farkar dashi,azabure ya bude idanuwansa ganin bakowa a Wajan sai tulun kaya yasashi fara rarraba idanuwansa,ga Duhun da ya toshe masa fuska baya gani, cikin fitar hayyaci ya fito daga cikin motar ba tare da kowa ya ankara dashi ba,cikin layi ya soma tafiya ,yana wuwwuce mutanan da ke babban wajan, ga tsakanin yunwar da ta haifar masa da jiri,ta fiya kawai yake baya kallan gabansa, gashi ko takalmi babu a kafarsa, Daidai wani babban titi ya soma ratsawa Kwata kwata baya ganin gabansa, motoci kuwa sai kauce masa suke, cikin sharara gudu wasu bakaken BMW suka shawo kwanar wajan ,ba tare da sun ankara dashi ba motar nan tayi sama dashi, ya fado ko motsi ba yayi, cikin sauri driver din motar ya fito,ganin baya motsine yasashi dora hannu aka ,”shikenan na zama gawa Nima”, tun kafin a tabbatar da mutuwar Wanda ya kade ya soma kuka, cikin Sauri wasu sojoji biyu suka fito daga cikin motar, cikin turanci suke tanbayar drivern yana basu amsa,a hankali aka bude bakar BMW din bayansu,da Sauri d’aya daga cikin sojan ya zo wajan kofar tare da sarawa na cikin motar, a hankali wata farar kafa ta zuro da kafarta,kafun ta fito da gangan jikin ta gabaki d’aya , fatabarakallahu ahsanin khalikin, kyakkyawa ce matar , gata fara sosai kana ganinta kaga cikakkiyar balarabiya , sanye take cikin jallabiya irin ta mata ash colour da ya rufe jikinta gabaki d’aya , a hankali ta soma ta ku sojojin nan suna take mata baya har ta karaso wajan da taheer yake a kwance,”ya salam “ta furta a hankali”kallansu tayi cikin bacin rai “me kuke jira ku sashi a car”cikin gaggawa kuwa daya daga cikin su ya dauki taheer zai sashi a motar su “on my car” ta kara firtawa,”mah” wani soja ya furta ,kallan da ta jefa masa ne yasashi sunkuyar da kai kafun ya shigar da taheer cikin motar ta,a guje suka bar wajan,Kai tsaye motocinnan basu tsaya a ko ina ba sai a cikin babban private hospital din cedarcrest hospital ltd dake sam mbakwe st ,ba bata lokaci a ka dauki taheer zuwa emergency. Wayar matar ne ya soma ringing cikin wakar larabci,dan guntun murmushi ta saki kafun ta dauki wayar cikin muryar larabci ta soma maganar da bana ganewa, bata dau dogon lokaciba ta kashe wayar.d’aya daga cikin sojojin ne ya nufeta ,cikin girmamawa ya furta “mah the flight is ready “,kamar bazata kulashiba sai kuma ta bude baki ta furta “cancel the flight “,sara mata kawai yayi kafun ya furta “yes mah”. Kusan 40 minutes kafun fitilar emergency din ta dauke , kofar na budewa suka fito da taheer da akai w bandage a jiki ga abun oxygen a fuskarsa,wasu kwallar ne suka tarar wa matar ganin irin halin da dan karamin yaron ya fada , wani babban likita ne yazo wajan,cikin girmamawa ya gaisheta ,kafun ya nemi alfarmar ganinta, bin bayansa tayi har zuwa office dinsa, cikin harshen turanci ya kara gaisheta kafun ya soma tanbayarta menene alakarta da mara lapiyan,budar bakinta kawai ta furta “SON”,da mamaki ya kalleta ,har ya bude baki da niyar cewa wani abu ta dakatar dashi “straight to the point plx “,nunfashi ya dauke kafun ya soma magana “saka makon wahalhalun da yashane yasa shi samun bad injury a jikinsa,and gashi ana barinsa da yunwa dole yana bukatar abinci masu gida jiki,alamu sun nuna ana azabar dashi ta hanyar duka dan duk jikinsa shatin duka ne ganyu da ta bata masa ciki, buguwar da yayi ba sosai bace ,wahalar da yashane yasashi suma a lokacin amma Alhamdulillah yanxu an tseratar dashi and a matsayin ki na mahaifiyarsa yana bukatar kulawarki sosai ta uwa”,gabaki d’aya taji bayanin nasa amma mamakinta ina iyayan yaran ganin babu me bata amsane yasa ta kalli doctor din,”zan iya ganinsa “,gyada mata kai yayi kafun ya furta why not,a tare suka nufa wani special daki da aka kwantar da taheer .kwance yake yana bacci ga nunfashinsa dake futa a hankali,bin sa ta farayi da kallo ganin irin raunukan da yaji,sosai duk Wanda yaga taheer sai ya tausaya masa,”kamar zai kai Yaushe kafin ya farka “zai iya farkawa daga anjima zuwa gobe da safe “,jinjina masa kai tayi,doctor din na fita ta bada umarni a kawo abinci masu rai da lapiya na Gina jiki, ba bata lokaci kuwa suka cika umarninta, har a kai sallar azahar tana zaune a dakin da taheer yake lokaci zuwa lokaci tana amsa waya. ➰➰➰➰➰ Tunda ya shiga toilet din yayi sauri cire rigar jikinsa da ta bata,kallan yadda take lumshe ido yayi kafun ya karasa wajan ta hasken toilet din ya kashe gabaki d’aya kafun cikin rintse ido yacire mata rigar jikinta da ta baci itama , duk da ya kashe hasken futulan hakan be hanashi rintse ido ba,sai da ya tabbatar ya cire mata komai na jikinta kafin ya kara daukar ta suka shiga wata glass din kofa dake cikin toilet din tare da turo kofar,ya dau kusan mintuna 40 a cikin toilet din kafun ya kunna hasken toilet din, sanye yake cikin bathrobe din Riga fari tass da ita ,itama taheen Itace sanye a jikinta, har yanxu tana rike a hannunsa ,wannan karan daukar baby yayi mata kafun su fito daga cikin toilet din, a Wajan shiryawa ma ya dau dogon lokaci a wajan kafun su shirya ,wannan karan ma saida ya kulle idanuwansa kafun ya sa mata kayan,turaransa na imperial majesty da babu me amfani dashi ya fesa mata,kallan yadda yake taje kansa da ya taru tayi kafun cikin kwabe fuska ta cire scarf din da ya dauka mata akai,yalwataccen gashin kanta ya fito fili, itama nuna masa nata kan tayi “dady nima “,kallan kan yayi kafin kamar Wanda aka umartan ya tasoma taje matan,yana yi yana lumshe ido, cikin kankanin lokaci suka shirya ,kama hannunta yayi suka nufi kalansa bayan ya dora mata mayafi akai ,cikin kulawa dan sanyin murya kamar bashi ba ya furta” me ke damunki yanxu “murmurmur tayi da ido kafun ta furta “yunwa nake ji”,dun gure mata hai yayi ta kyalkyale da dariya kafun ya kama hannunta suna barin part din. ****Daddadan kamshin turaran sune ya karade ko ina na cikin falon dada, gabaki d’aya mutanan gidan yau sun hallara a babban dinning din part din dada, kowa kofa ya zubawa ido ta ganin ta inda zai bullo ,kowa da abunda ke ransa musamman su basma da tasha makeup,itama mahma da sha’aban sai faman zuba ido suke ,abeey ba kallan kofar yake, a hankali yayi sallama cikin muryarsa fuskarsa kwata kwata ba annuri,gabaki d’aya mutanan falon hada baki sukai wajan amsawa,basma har kusan kwarewa tayi sabida yadda ta zuba masa ido ko kunyar a ganta bataji, amrah na gefe sai faman hararar ta take ganin halin basman da tun bau ta soma zuwa gidan ba. Mikewa basma tayi cikin washe baki ta furta “welcome yaya king”,bata karasa zancan nata ba ganin hannunta rike da na tahee data buya a bayansa, kallansu ta tsaya yi cikin bacin rai , dada data hango tahee ce ta furta “yau naji saban muna furci,Menene na buya Kuma tahura”, kallanta mahma tayi”mahma wai ina take ni har ynxu bangan taba ,son ku karaso mana kukai muke jira”, ba tare da ya kula kowa ba ya janyo tahee dake faman boye jikinta ,hannunta guda daya ya kama tare da nufar dinning da suke, zuba mata ido mahma tayi banda Masha Allah babu abunda take furtawa cikin zuciyarta,tabbas Allah yayi halitta a nan ,a fili kuwa Masha Allah din ta kara maimaitawa tana bin tahee da kallo,kowa na falan zubawa taheera ido sukai ,sosai yau tayi kyau kamar ba ita ba, hatta fatar jikinta sai data kara washewa,”ummey da ammey ma sai faman murmushi suke saki, wajan dining din suka karaso har yanxu hannunsa na rike da nata,bayan ya gaishe da kowa na falon itama haka tayi kamar yadda taga yayi,cikin danne abunda yake taso mata basma taja masa kujerar kusa da ita kafun ta saki wani murmushin “yaya king ga waje Bismillah “,kallan second biyu kawai yayi mata kafun ya karasa wajan,ga mamakinta sai gani tayi ya kara Jan kujerar baya,a tunaninta shine zai zauna sai gani kawai tayi ya dora tahee awajan,tare da jan kujerar kusa da ita shima ya zauna,wani shegen murmushin mugunta sha’aban yasaki saura kadan dariya ta kwace masa ganin reaction din basma da wasu daga cikin yan matan gidan, hakan da yayi kuwa sosai ya saka wasu daga cikin yan gidan farin ciki musamman abeey da mahma da sai faman sakin murmushi suke, mikewa mahma tayi cikin sakin fuskta “yau ni zanyi serving amare ,me zakuce” d’auke kansa yayi daga kallan mahma ba tare da yace komai ba,ganin yadda take Kallan tahee ne yasa tayi saurin rike rigar king tana kokarin buya ,kallanta yayi kafun ya kalli mahma, fahimtar hakanne yasa ya kalli mahma” no need mahma”hararar sa mahma tayi “dan kai bata jin yunwa sai ita akace maka bataji”shiru kawai yayi ba tare da yace komai ba,da kanta mahma tayi serving din kowa na falan, basma da amrah ji suke kamar sukaiwa tahee duka,ita kuma tana rike da hannun rigarsa har yanxu,ganin kowa sun fara cin abincine bandasu yasa abeey ya kallesa, Daidai lokacin da shima king din yake dago fuskarsa,saurin janye fuskarsa yayi daga ta abeey ,kafun ya kalli tahee,itama mahma kallan taheen tayi “kici abincinki mana ko bashi kike soba”nan ma shiru taheen tayi, tana kallan king kamar wacce zatayi kuka,ta gefan ido ya dan kalleta kafun yasaka hannunsa ya debo farfesun kayan cikin dake faman tashin kamshi, Daidai bakinsa ya kai kamar Wanda zai ci sai kuma ya nufi bakin tahee ,da Sauri kuwa ta bude bakin nata, ba basma dake falan ba ,kowa na cikin falon dakatawa yayi dacin abincin dasu,ba Wanda be bawa mamaki ba,sha’aban baisan lokacin da ya furta “wow “ da karfi ba, mahma ma bakadan ba tayi farin cikin abinda king yayi ummey da ammey duk sun kuyar da kansu sukai cikin jin kunya, aunty kuwa ji tayi gabaki d’aya abincin ya fita ranta,su uncle 𝖘𝖆𝖑𝖊𝖊𝖒 ma duk murmushi kawai suke saki, kara tsuke fuskarsa king yayi jin alamun idanuwa akansa, a hankali ya dunga bata farfesun har saida ya tabbatar ta koshi kafun yayi kokarin mikewa, riko ta hannunsa tahee tayi yanxu ma kamar wacce zatayi kuka, da ido yayi mata alamun Menene,farfesun da ya bata ta kalla, ya dauka bata koshi bane yasashi komawa ya zauna ,spoon din da ya ajje take kokarin dauka, fahimtar abunda take kokarin yi yashashi saurin dauke spoon din”Lalle baki da lapiya “ya furta cikin zuciyarsa,kafun ya dauki farfesun ya kai bakin ta, girgiza masa kai tayi ,ajje spoon din yayi yana kokarin tashi a karo na biyu ,ganin ta kallesa tare da kallan spoon din ne yasashi fahimtar abunda take kokarin to , komawa yayi shima ya zauna kafin ya soma Shan ragowar farfesun da ya bata,sha’aban na gefe sai faman sakin murmushin mugunta yake musamman yadda yaga fuskar basma da saura kadan ta fashe, abeey sosai yayi farin cikin daga nin wannan ranar,tabbas ya kara yadda ita kadaice zata canza masa son dinsa, ummey ma murmushi kawai ta saki tana godewa Allah, ammey kuwa kunya ce ta Hanata dagowa,lokacin dada bata falon, mahma sai faman washe baki take, har aka kammala cin abincin kafin akoma falon dada, king da sha’aban basu zauna a falon ba suka fita, mahma kuwa ta katse ta tsare har saida tahee ta saki jikinta da ita, dada har tana mata tsiya ganin tayi saurin sabawa da mahma, ana gama cin abincin basma ta dauki wayar ta kamar zata tashi sama ta nufi masaukin ta tana danna number mahaifiyarta, itama mahma kama hannun tahee tayi ta nufi part dinta da ita, acewarta tun yanxu zata farayi wa yarta gyaran jiki, suna shiga kuwa wani abu ta dakko Cikin wani boil dan karami , me hade da kwakwa da dabino sai madarar da aka saka a ciki, cikin da bara mahma ta sa tahee Tasha,itama da taji dadin abun duka kuwa ta shanye kayanta, tana kammala sha kuwa mahma ta kara mata wani abu me kamar zuba cikin spoon ,shima tass tahee ta shanye kayanta. Gabaki d’aya yinin ranar tahee na Wajan, anan tayi sallah ta kafe ta tsare,a iya zaman da sukayi ta fara fahimtar halin tahee din, har lokacin kuwa king be dawo part din ba, suna hospital dinshi shida sha’aban kasan cewarsa shima kwararran likita, tun a mota sha’aban yake wa king dariyar shakiyanci, banza king yayi dashi kamar be san yanayi ba, cikin neman bala’I sha’aban ya kallesa kafun ya furta “MY GEE , MR ROMEO NA JULIET “. Sorry 😞 for the late update 😞😞.. 💖💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖💖 Mss Lee 💖🙌 💖💖GIDAN AUNTY 💖💖 (a heart touching love story) Story & written By Mss Lee 💖 💖💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖💖 PAID BOOK Me bukatar complete din littafin gidan aunty ya tuntubeni ta wannan number 07041879581. BOOK 1📕 Page 43_44💖 Dan karamin duka king ya kai masa a kirji yana jan dogon tsaki,”matsalata da kai har yanxu you are not serous “, kallansa sosai sha’aban yayi kafun ya furta “wannan ba maganar serous bace Gee,idan baka san me yasa abincin da take so kaji”,gajeran tsaki king yaja ba tare da yace komai ba,dariyar shakiyanci sha’aban ya saki” toh shiknn tunda baka santa ai ga su basma sai ka hadasu ka aura “,wani banzan kallo king ya jefawa sha’aban,shima be damu ba sabida yasan halin king ,in a serous tone ya furta “ Gee karkayi wasa da damarka,ina guje maka ranar da yarinyar nan zata dawo sense dinta, ta gane baka santa,ka nutsu kafuskanci future dinka gee,I’m advising you as your brother and best friend in ka bari damar ka ta kwace maka shikenan ka rasa ta,kwanda ka rike matarka hannu bibbiyu,kafin muzo suna Muma Allah ya bamu matayan mutashi daga kauraye “ ya karasa maganarsa yana kashewa king ido cikin zolaya,kafun yayi saurin barin office din,kofar king yayi da kallo lokaci d’aya yaji zuciyarsa ta buga ,kalaman sha’aban na sake dawo masa,kallan da tayi masa dazu ne yafi komai tsaya masa arai, lumshe idanuwansa yayi yana tuno yadda idanuwanta suka tara kwalla, kokarin share zancen yayi amma lokacin da suke toilet ya kara fado masa arai musamman lokacin da ta fado jikin sa”Ya Allah “ ya furta afili ganin har yanxu tana masa gizo arai. ➰➰➰➰➰ 🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧 BASMA Tana shiga dakin ko zama batayi ba ta dauki wayarta,dialing number mom dinta kawai take a kagare, kusan 2 missed calls tayi mata bata daga ba ,amma duk da hakan bata hakura ba ta sake kiran wayar, a karo na uku, har ta kusa tsinkewa aka daga kiran, tana ganin mom dinta ta daga ta fashe mata da kuka ,cikin tashin hankali tacikin wayar ta soma magana“baby na waya taba minke “ sosai take kukan ko sauraran abinda mom din tata take cewa batayi,da gyar ta cikin wayar ta lallasheta kafun ta tanbayeta abunda ya faru, gabaki d’aya sai da ta zayyana mata tun zuwan ta part dinsa da marin da tahee ta yi mata,hatta abunda ya faru sai da basma ta fadawa mom din nata a shagwabe. Shiru momyn nata tayi kamar me nazari kafun ta soma yi mata maganar da banajin me take ce mata, sosai basma take sakin dariya ganin lokaci kankanin ta samo wa kanta mafita, har zata kashe wayar kuma sai ta kara karata a kunnanta “momy ina so nasan wacece ita, yanxu momy fa “ banji me aka ce mata ba sai kada kai da take kamar wata kadangaruwa,tana kashe wayar tata, ko mintuna talatin ba ayiba aka turo mata text din bayanan da take so,wata shegiyar dariya tasaki” zan ci uban kine,zakisan dani kike magana “,tana kammala zancan ta tabar dakin nata bayan ta dakko wani abu a cikin jakarta. 🫧🫧 A bangaran su tahee ma,tun bata sake wa mahma harta sake mata ,itama mahma lokaci d’aya taji wani san yarinyar yashiga ranta jinta take kamar ‘yar da ta haifa da cikinta,wasu turaruka masu shegen kamshi mahma ta fito dasu cikin wata yar kwalba me shegen girma,da kanta ta gyarawa tahee dogon gashinta kafun tayi mata dan ado da gashin,ba karamin kyau tahee tayi ba kamar ba ita ba,ba zata ba tsammani basma ta shigo dakin ,kallanta mahma tayi bayabo ba fallasa”baki iya sallama bane”bin tahee tayi da kallo kafun tayi sallamar,har yanxu idanuwanta na kan tahee dake Shan fura ,ji tayi kamar ta zabga mata mari ganin ko kallan inda take batai ba ga wani kyau data danyi kamar wacce aka bawa wani abu,ta gefan ido take kallan mahma dake zaune itama tana Shan furar ta kwata kwata hankalinsu ma baya kanta,idanuwanta basma ta tsayar kan tahee da gefan gashinta ke yawo a gadan bayanta,dan siririn scarf din data daura yana kokarin zamewa a kanta. Mikewa tahee tayi tana kallan mahma, “mahma bari naje wajan dada” gyada mata kai mahma tayi ,Nima ganinan zuwa ai, murmushi tahee ta sakar mata batare da ta kalli basma dake binta da kallan kurilla ba tabar part din, itama mahma tashi tayi ta nufi cikin bedroom dinta, wani bakin cikine ya kama basma ganin yadda suka shareta gabaki d’ayan su , a zuciye ta bi bayan tahee da ta nufi part din dada. Tana kokarin shiga part din basma tayi saurin Shan gabanta,”keee yar matsiyata” cewar basma,a hankali tahee ta dago da kanta dake faman sara mata kadan kadan tun dazu, batace mata komai ba tayi gefe zata wuce, wani irin shakota basma tayi tare da mai dota baya, dafe kanta tahee tayi jin yadda kanta ya fara sara mata”taheera kike kowa ,ke din ba sa’ar yi na bace ko uwarki maryam ba sa’ar yina bace balantana ubanki Muhammad dake kabari,tun wuri ki fita harkar mijina ,idan ba haka ba sai na karar da duk zuri’arki,shegiya me zubin karuwar”, tunda ta ambaci sunan taheera da maryam kan tahee da taji ya kara sara mata, saurin dafe kanta tayi jin yadda kanta ke juya mata, kwata kwata bata gane me basman take cewa ,abu take san tunawa amma ta kasa sabida yadda yake faman sara mata, shako wuyanta basma tayi cikin bacin rai ta kalleta ,”bari na fada miki abunda baki sani ba, king mallakinane ni kadai duk wannan haukar da kike ba sanki yake ba dan haka ki fita harkarsa,banza dangin matsiyata”,wani irin hankadata tahee tayi da yayi sanadin buguwar hannunta,a zuciye tahee ta dafe kanta hawayen da batasan na Menene ba ya fara zubo mata ,”taheera ,maryam ,Mohammad su ne abunda suke mata yawo cikin kwakwalwa “baya sankiiii kalmar da basma ta furta mata ne ya dawo kaikawo a zuciyarta,cikin futar hankali ta juya a guje tana hada gudu gudu sauri sauri harta bar part din dada ba tare da ta karasa shiga ba, har yanxu hannunta dafe da kanta, Daidai lokacin da motocin su king suka danno kai, tun daga nesa ya hangota dafe da kanta,kamar bazai bitaba ganin ta nufi part dinsa yasa ya nufi part din shima cikin takun nutsuwasa, tana shiga ta fara kwala masa kira,” Dady!!! Dady!!! Dady”,cikin bedroom din kasa ta koma tana cigaba da kara kiran “dady” ,ganin baya cikine yasata fitowa da sauri zata kara kiran dady ya shigo part din, da Sauri ta kara so Inda yake tana rike hannunsa fuskarta duk ta baci da hawaye, bin kyakkyawar fuskarta yayi da Kallo ganin yadda take hawaye “me akai miki” ya furta kalmar a fusge Yana lumshe idanuwansa,amaimakon ta amsa masa tanbayar da yayi mata sai ta kara rike tafikan hannunsa” Dady kana sona “da Sauri ya zuba mata idanuwansa ,”kana sona din da ta fada na Dakar masa zuciya ,ganin be amsa matan bane yasa ta kara furta “dady kana sona “har yanxu hawayan fuskarta be dena zuba ba,kokarin sassaita kansa yayi kafun ya kalleta “what’s wrong with you”, yanxu ma bata kulasaba sai ma kara daga muryarta da tayi “dady kana sona “, cikin kosawa da zancanta ya furta “bana sanki ok”,hannunsa da ta rike ta saki tana binsa da kallo kafun ta fara ja baya a hankali “baka sona, daman tace baka sona”, tana gama furta wannan kalaman ta juya a guje tana fashewa da kuka ,cikin zafin nama ya rikota ganin tana kokarin barin Wajan, ba tare da ta kallesaba tasaka hannayenta biyu ta ture shi daga cikin ta,kafun ta kalleshi haryanxu hawayen idanuwanta basu dena sauka ba, ido cikin ido ta kallesa kafun ta furta “Bana sanka”, tana gama fadar hakan ta juya a guje,kasa motsi king yayi sabida yadda kalamanta suka daki kirjinsa,lokaci d’aya yaji wani irin tashin hankali na taso masa da ya rasa na menene,dafe kansa yayi cikin sauri kafun yabi bayanta ganin tana kokarin barin part din, tahee kuwa Daidai ta saka kafarta zata fito kenan taji an hankadata da mugun karfi, cikin zafin nama king ya nufi inda take ganin tana kokarin faduwa,kafun ya riketa gabaki d’ayanta kanta ya bugu da jikin bangon wajan take a wajan Jini ya barke mata ta suma a wajan,kasa motsi yayi ganin yadda Jini ke fita daga kanta,sosai idanuwansa suka rine kalar abun tsoro,basma dake kokarin barin Wajan ya shago tare da bugata da jikin bango kamar ya samu kato haka ya dunga tsinka mata mari kafun ya kai mata wani irin muguwar Shaka ya kai mata kwata kwata baya kallan gabansa,kakari basma ta fara saki na azama kamar wacce nunfashinta zai dauke gabaki d’aya ,har yanxu kuma bashi da niyar sakin ta Daidai lokacin da sha’aban ya shigo falon , cikin sauri sha’aban ya karasa wajansu su yana kokarin banbareta amma abun ya ci tura ganin irin muguwar shakar da yayi mata ,zaki sha’aban ya kirawo da Kyar aka samu king ya saki basma da ta fadi itama take a wajan tana sakin haki ga gefan fuskarta da yayi bala’in kunbura,gabaki d’aya baya kallan gabansa kokarin kara shakota yake cikin daga murya sha’aban ya furta “she’s bleeding “,be karasa zancan nasaba ya sabi tahee da kanta ke faman bleeding yana kokarin wajan ,kafun cikin Sauri ya juyo inda basma take, itama da hannu d’aya ya fincikota tare da jefata wani daki dake kusa da wajan, turn print din hannunsa ya sa awajan take kofar dakin ta kulle,ya bar wajan cikin sauri, kafin ya fito daga part din nashi zaki ya ja motar a guje suka bar wajan.Tunda ya dora ta akan cinyarsa yake kallan fuskarta,”bana sanka “shine ya kara dawo masa,a hankali ya furta “please don’t do this now”ba tare da ko ita taheen da take sume zata jishiba, hannu d’aya yasa gabaki d’aya ya rungume a jikinsa kamar wacce akace za’a kwace masa ita,gabaki d’aya jikinsa ya baci da jiki dukda abun da yasa ya danne mata wajan,cikin saurin aka wangale babban gate din asibitin NAHYAN,ko gama parking zaki beyi ba ya bude kofar bayan ya lullube jikin tahee, tunda jami’an asibitin suka gansa suka fara sara masa , ba Wanda ya kula a cikinsu, ko cikakken muntuna biyar ba’ayiba manyan likitocin asibitin suka hallara a 3rd suna jiran umarni,doctor halima ya bawa umarnin tayi mata dressing ,kafun ya kalli wasu Likitoci mata gudu biyu” at the theatre “kawai ya furta masu,cikin sauri kuwa ko waccen su ta nufi wajan shiryawa,cikin kankanin lokaci shima ya canza zuwa kayan theatre din , gabaki d’aya likitocin mamakine ya ka masu ganin zaiyi theatre da mata zalla wannan karan abunda be taba faruwa, direct dakin theatre aka shiga da tahee bayan anyi mata dressing din. Sha’aban kuwa cikin sauri ya nufi part din dada,a zaune ya tarar dasu ummey zaune a falan suna hira ganin yadda yashigo ne yasasu mikewa,kallansa dada tayi”Kai kuma kamar Wanda aka jefo”!Be tsaya saurarar taba ya fara labarta musu abunda ya faru,gabaki dayan su sallallami suka saki ,hatta su abeey da ke kokarin shigowa part din,kasan tuwar kowannansu da gyale a jikinsu ba ‘bata lokaci abeey yasa a tayar da mota sai NAHYAN hospital ko takan basma da aka kulle ba Wanda yabi, sha’aban da abeey sai su uncle saleem suna baya ,suma su mahma Itace take tuki yau da kanta,daga ita sai dada sai kuma ummey suka nufi asibitin. ➰➰➰➰➰➰ ➰➰➰➰➰➰ 🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧 🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧 Karfe 8:50 na dare taheer ya soma motsa hannayensa lokacin matar tana kan dadduma bayan ta idar da sallarta, a hankali ya soma furta”zasu kashe mu, zasu kashe mu”ganin yana motsine yasa ta mike wa tare da nufo inda yake, a zabure ya bude idanuwansa yana kwalla kiran sunan “zasu kashe mu” kallan sa matar tayi kafun ta soma magana “kwantar da hankalinka ba Wanda zai kashe ka”, da Sauri taheer yaja baya yana kallanta, “Kema mayar dani zaki wajan nasu”, girgiza masa kai matar tayi “ba inda za akaika sannan babu me kara daukeka, su wanene zasu dauke ka sannan ina yan uwanka “, sai a lokacin taheer ya fashe da kuka tuno su oumma da yayi,batace masa komai ba sai data barshi yayi ku kansa iya yinsa kafun tayi serving dinsa abinci abinci da kanta, kamar mayun Wacin zaki haka yasoma cin abincin ganin yana kokarin shakewa ne ysa ta mika masa ruwa,yanxu ma cikin sauri yake shan ruwan, saida ta tabbatar ya koshi ya fara dawowa hankalinsa kafun ta kara yi masa tanbayar dazu,gabaki d’aya ya labar ta mata abunda ya faru tun lokacin da ya fito daga gidan nan wasu mutane suka tare masa hanya cikin wata bakin mota,yana kokarin barin wajan suka fesa masa abu, be kara tsintar kansa a ko ina ba sai gidan da aka dunga azaftar dasu. Share hawayen ta mayar tayi jin labarin da ya bata,Aushe dagaske hakan na faru ga yara kanana, kallansa tayi cikin tausaya kafun ta furta ,kanaso ka koma gida , cikin wata irin zabura ya girgiza kansa alamun ah ah , kallansa tayi cikin mamaki kafin ta kara tanbayarsa,naam kai ya girgiza mata cikin tashin hankali, fahimtar halin da ya shiga ne yasata mikewa da niyar kiran likita,da sauri ya riko hannunta ,”dan Allah ki dauke ni anan kullum dukanmu suke”wani saban tausayinsa ne ya kamata kafun ta sakar masa murmushi “karka damu babu Wanda zai kara tabamun kai,zan kirawo likita ya duba kane” gyada mata kai yayi har yanxu be dena jin tsoro ba,”karka damu yanxu zan dawo kaji”, Tom kawai yace mata itama bata kara cewa komai ba ta bar dakin. 🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧 🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧 Har suka karaso asibitin su king basu fito daga dakin theatre din ba, kasantuwar ansan ko suwanene yasa aka kaisu suma can 3rd floor din, gabaki d’aya hankalinsu a tashe yake ,tunanin ta ydda zasu sanar wa ammey kawai suke, suna cikin wannan tunaninne aka bude kofar theater din, gabaki dayansu kan tahee da kanta yake nannade suka nufa,dada harda yar kwanlanta,wani babban daki aka nufa da ita suna binsu a baya har lokacin ba Wanda yaga king a cikinsu,sha’aban ne ya kalli daya daga cikin doctors din kafun ya tanbayeta lokacin farkawarta, cikin jinjina wa ta furta “ba wani babban rauni ta samu ba, and all the necessary Dr yayi shi, zata iya farkawa nan da 2 hours time “, jinjina mata kai yayi amaimakon ya nufi dakin da aka kwantar da ita kai tsaye office din king ya nufa, koda ya shiga be tarar da kowa a falon ba, wata kofa ya nufa a cikin office din bayan yayi dan tafiya kadan ta kaishi wani kofar, yana budewa wani babban dakine a ciki nan ma be ga king ba sai motsin ruwa da yake dan ji, fita yayi daga dakin yana tare da komawa cikin office kusan 1hour har da mintuna 20 sai ga king ya fito cikin shigar fararar kaya,gabaki d’aya fuskarsa ba annuri,kallo d’aya yayi masa tare da dauke kansa ,kan d’aya daga cikin sofas din falon ya zauna har yanxu yanayin fuskarsa be sauyaba,wasu injection ya dauka har yanxu be kuka sha’aban dake zaune ba, ganin yana kokarin fita ne yasa sha’aban bin bayansa,Kai tsaye dakin da take suka nufa, ko da suka shiga dakin babu Wanda ya kalla a cikinsu kai tsaye inda take kwancan ya nufa har ya juya da niyar komawa yaga hannayenta na motsi, be san lokacin daya kama hannayenba yana kallan fuskarta, a hankali ta fara motsi da idanuwanta, kafun ta bude su tar sai kuma tayi saurin kara kulle idanuwan,tayi hakan kusan sau uku kafun ta bude su gabaki d’aya, abunda ya faru ne yashiga dawo mata daya bayan daya tundaga kan batan oumman ta, hannunta dataji an rike ta kalla,a hankali ta janye hannunta daga nasa kafun ta kalli ummey dake gefanta a hankali ta furta “UMMEY”, cikin tsananin farin ciki ummey ta kalleta,kin ganeni,jinjina mata kai tahee tayi,maida kallanta tayi kan abeey kafun ta furta abeey,wani yalwataccen murmushi ya saki me kayatarwa “ya jikin naki” cikin sanyin jiki ta furta Alhmdllh ,kallan dada tayi ta kira sunan ta itama ,wata irin kabbara dada tasa da yasa kowa ya kalleta, mahma tahee takirawo sunanta a hankali , murmushin jin dadi mahma ta saki ganin ta tuna da ita, gefenta ta kalla dan ganin ta inda zata bullo amma har yanxu bata ganta,”ammey ko”ummey ta tanbaya,saurin sunkuyar da kanta kasa tahee tayi kafun ta soma wasa da yan yatsunta Wanda aka sawa ruwa,murmushi yan dakin suka saki banda king dake binta da kallo ta kasan ido,Allurai ya hada guda uku yana kokarin yi mata su abeey suka fita daga dakin, itama dada mikewa tayi kafun suma su mahma suka bar dakin yayi saura daga king sai ita, wani irin sansa ne taji na taruwar mata a zuciya tuna yanda ya kula da ita lokacin da tayi rashin lapiya ,kalmar bana sanki da ya furta ne yasata hadiye duk fargabar da take ji a kansa, ko kallan inda yake batayi gigin kalla ba, a hankali ya matso inda yake kafun ya dakko injection dinnan,cikin kankanin lokaci yayi mata su wannan karan ko kokarin guduwa batayi ba ballantana tayi masa raki, sunkuyo da kansa yayi Daidai saitin fuskar,saurin dauke kanta tayi tana hade ranta dukda masifaffiyar tsoransa da take ji,Daidai saitin kunnanta ya furta “ya jikin ki”,tsikar jikintane ya tashi jin saukar muryarsa acikin dodan kun nata,ba tare da ta kalli inda yake ba ta furta “Alhmdllh “kalleni ya furta a hankali, kin kallansa tayi kamar yadda ya umar tan sai ma kara sunkuyar da kai da tayi,da dan zafi ya furta ba magana nake miki ba, da sauri ta dago da fuskarta amma har yanxu taki yadda su hada ido,ga wata masifaffiyar kunyarsa da take ji”Me kikeso”, ba tare da ta kallesa ba ta furta “babu”, yanxu ma kara sunkuyo da fuskarsa yayi “me Yasa babu” atsiwace ta dago tare da furta “sabida bana….” Be bari ta karasa zancan nata ba ya mata kiss abakin ,”Sabida bakya me”, kin dago da fuskarta tayi jin wani irin masifaffiyar kunyarsa da take ji,”batanbayarki nake ba”yanxun ma dago tayi tare da furta “sabida bana…”bata kai karshen zancan nata ba ya kara kai mata wani kiss din a karo na biyu, bai san jin abinda zuciyarsa zata bugane shiyasa ya kara tanbayarsa,ki amsa mun tanbayata,cikin dake wa kamar me shirin yin kuka ta furta “sabida bana sanka”, tana kai karashen zancan nata ya hade bakinshi da nata waje d’aya ,bata san lokacin da wani karfi yazo mata ba ta ture shi daga jikinta tana juya masa baya, shima be kara cewa komai ba ya bar dakin, fashewa da kuka tahee tayi tuno rayuwarta ta baya ko ina su oummanta suke oho,shima king wata sabuwar soyayyarsace take faman rura hutar zuciyarta amma tayi alkawarin ko zata mutu bazata taba nuna masa ba tunda yace baya santa. 💖💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖💖 Mss Lee 💖 💖💖GIDAN AUNTY 💖💖 (a heart touching love story) Story & written By Mss Lee 💖 💖💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖💖 DEDICATED THIS PAGE TO YOU MRS BBK (JINI DAYA),ALLAH YA BAKI LAPIYA 🙌❤️🌹. PAID BOOK me bukatar samun complete din gidan aunty yayi nun magana ta wannan number 07041879581. بسم الله الرحمن الرحيم 💖 BOOK 1📕 Page 45_46 💖 Shigowa dakin da akai ne yasa ta saurin share hawayenta ,Sabida kamshin turarensa daya cika mata hanci, da sauri sauri zuciyarta take bugawa ,har yanxu kuma ta ki yadda ta bude idanuwan nata,ta gefan ido ya dan kalleta,be ce mata komai ba sai wayarsa da ya dauka ya fita daga dakin, kara turo kofar da akai akaro na biyu ne yasata saurin dagowa kamar me shirin yin magana ,wacce ta gani ce yasa ta saurin sunkuyar da kanta kasa wata iriyar kunya na kamata,karasa shigowa ciki mahma tayi tana sakar mata murmushi,”daughter ya jikin naki”, cikin jin kunya ta amsa mata “da sauri”tana dan wasa da yatsun hannunta,wani murmushin mahma ta sakar mata”nasan kin gaji ko,abeey zai tanbaya king ko zamu koma gida ,Inyaso sai ki fi hutawa acan kinji”,yanxu ma wasa take da yan yatsun hannunta kafun ta amsa mata da “toh”,suna cikin wannan zaman ummey ta shigo dakin,kallan ta mahma tayi” Ta karaso kuwa” girgiza mata kai ummey tayi “tace zata zauna a Abuja zuwa jibi sai ta karaso” gyada mata kai mahma tayi “Allah ya kawo ta lapiya “, Ameen suka amsa gabaki dayansu kafun ummey ta kalli tahee da tunda ta sunkuyar da kanta taki dago dashi har yanxu “ah ah yau kuma ni ake jin kunya naga kin sunkuyar da kai”wata masifaffiyar kunyace ta kamata kamar ta tsaga kasa ta shige musamman yadda taji alamun idanuwansu na yawo a jikinta, ta bude baki da niyar yin magana abeey da sha’aban suke shigo dakin,”sannu daughter,ya jikin “ da Sauki ta amsa masa har yanxu kanta a duke,kallan su mahma abeey yayi “ yanxu za a sallame ta, in yaso se a cigaba da treatment dinta a gida”,mahma ce ta amsa masa da toh kafun ta tanbayeshi ina dada take,”nasaka saleem ya mayar da ita gida kunsan haryanxu ciwon kafar nata be gama sakin ta ba”, jinjina masa kai sukai cikin gamsuwa, kallansu abeey ya karayi “ya kamata mu koma gida yanxu ,dada tana bukatar hutu,nasan bazata taba hutawa ba in ba gani tayi mun dawo gida ba”,yanxu ma,mahma ce ta basa amsa amma akeey ai naga akwai ragowar ruwan da aka sa mata be kare ba”,gyada mata kai abeey yayi,”idan ya kare zasu dawo tare da mijinta”yana gama fadar hakan ya kama hanyar fita, tunda aka anbaci mijinta jijiyoyin jikinta suka tsaya ko kwakwa kwaran motsi ta kasa,mimmikewa su ummey sukai itama sallama tayi musu suka fita ita da mahma bayan ko wacce ta sakar mara peck a goshinta. Sha’aban ma sai yanzu ya samu damar yi mata yajiki” amaryar mu Allah ya kara sauki” yana gama fadar hakan ya bar dakin gabaki d’aya yayi saura se ita kadai a dakin, gwiwowinta ta hada waje daya tare da fashewa da wani saban kukan da batasan na Menene ba. A hankali ya turo kofar dakin da take, tsayawa kallan yadda ta hade gwiwa tana kuka yayi kusan minti d’aya yana tsaye a bakin kofar kafun ya tako cikin dakin,hannunsa daya yasa tare da shafa kanta, a zabure ta dago kanta har tana kokarin bige bandegin da aka sa mata akai,sosai ta tsorata da ganinsa dan batayi tunanin ganin kowa ba, suna hada ido dashi tayi saurin janye natan tana kokarin sunkuyar da kanta ya rige habar ta da hannu daya tare da dago da fuskar tata, kin kallansa tayi sai ma kokarin lumshe idanuwan datayi “ don’t you dare, bude idanuwanki”, sosai taji shakkarsa musamman da taji yayi mata magana kamar lokacin da ta barar masa da coffee dinsa a part din ammey,bude idanuwan nata tayi yanzu amma har yanxu taki yarda su hada ido dashi”kalleni” ya kara furtawa,ba musu kuwa ta dago ta kalleshi kafun tayi kasa da idanuwanta,”me akai miki kike kuka “, girgiza masa kai tayi alamun babu”amsa “ ya furta, cikin sanyin jiki tace masa “babu”, dan ta bile bakin sa yayi kafun ya saki fuskar tata, kallan ruwan da aka sa mata yayi ganin ya kare,hannu yakai tare da cire mata abun ruwan,dan kara ta saki kadan tana lumshe idanuwanta, kallanta yayi kadan ba tare da yace komai ba, scarf din kanta ya gyara mata tare da mayafin jikinta,”stand up” ba musu kuwa ta mike da niyar takawa,jirin da ya dibeta ne yasata saurin dafe jikin gadon ,kallanta yayi na yan second kafun ya miko mata hannunsa,bin farin zara zaran yan yatsun tayi da kallo,ga nails dinsa dake faman shining kamar Wanda aka sawa abu kararan kun bansa fari tas dasu kamar ba a anfani da hannun”kina batan lokaci”, be karasa zancan nasaba tayi saurin saka hannun nata , kallan yanda fuskarta ba walwala yayi kafun su soma tafiya a hankali, ta bayan hospital inda ba kowa suka nufa, tunda suka shiga mota babu Wanda ya kara cewa koda uffan ne, shi yana danna wayarsa ne ita kuma gabaki d’aya ta maida hankalinta kan titi dake tafiya, tunda suka shiga motar yake kula da yanda take takure jikinta,yanxu ma kara takure jikin nata tayi sabida yanda sanyin AC ke ratsa mata kashi da jijiya, bata Ankara ba sai ji tayi ya janyota jikinsa,ko kakarin mikewa ta sakeyi ya kara jungumeta a jikin nasa,Daidai saitin kun nanta ya rada mata “I will warm your body “, daga nan be kara cewa komai ba, itama jin sautin muryarsa a kunnanta yasa tsikar jikinta tashi,yanda ya rungumeta yasa bata da wani zabi bayan ta lafe a jikinsa tana shakar daddadan kamshin jikinsa,gyara mata kwanciya yayi kafun ya kara rufeta da faffadan kirjinsa, duk Wanda abun da ke faru zaki be sani ba sabida yanda labule ya raba tsakaninsu har aka karaso gida suna manne da juna musamman yanda sukai body contact suna jin dumin junansu. Direct part Dinsu zaki yayi parking,sai lokacin tahee ta ankara,da Sauri ta kwace jikinta tana hade ranta,ganin antsaya a part dinsa ne yasa tayi saurin kallansa, bece mata komai ba sai fita da yayi daga motar ya nufi cikin part din, tsayawa kallansa bayansa tayi cikin ta kaici ta rasa inama zata sa kanta, part din ammey ta zata wuce ko part dinsa ko na dada, itama fitowa tayi daga motar ,tsayawa tunanin inda zata nufa tayi ganin dare na karayi ne yasa tai shahada kawai ta nufa cikin part dinsa.tsayawa bin falon tayi da kallo ganin yadda kamshi ke faman tashi a ciki,sosai falan ya karayi mata kyau,duk abunda ya faru a falon yana kara dawo mata cikin kai,dubanta takai kan dinning tana tuna lokacin da yake bata abinci a baki, kwallar da ta fara fito matane yasa tayi saurin sharewa a fili ta furta “tunda baya sona banga anfanin tuna komai ba”ganin tsayuwar tata bame anfani bace yasa batare da wani dogon tunani ba ta nufi asalin dakin da ya fara kaita.tana shiga cikin dakin veil da scarf dinta ta cire, tana kokarin cire doguwar rigarta kenan ya fito daga wata kofa sanye da towel iya kugunsa, farar fatar jikinsa tafito shar sai kyalli take , karar da ta saki ne ya daga kar dashi daga goge kan nasa da yake, be kula da ita ba sai yanxu,ganin yanda ta juya masa bayane yasashi sakin wani dan iskan murmushi da be kai ko wuyansa ba kafun ya fara nufo inda take … ➰➰➰➰➰➰➰➰➰➰➰ 🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧 ➰➰➰➰➰➰➰ ABUJA CEDARCREST HOSPITAL LTD Tare suka dawo da doctor din, yana ganinsa ya saki murmushin nasara kafun ya soma yi masa tanbayoyi game da jikinsa yana amsawa,kallan Matar doctor yayi cikin girmamawa yace mata “congratulations mah, anyi nasara a aikin da akai masa ,sai dai bazamu iya sallamar saba sabida akwai maganin da zamu dorashi akai na tsawan 2 weeks ,and karayar kafarsama tana bukatar kulawa sosai”, shiru matar nan tayi kafun ta girgiza masa kai” ba matsala” tana gama fadar hakan tayi shiru da bakinta,cikin girmamawa doctor din ya kara gaisheta kafun ya bar dakin. Kallan taheer dake hawaye tayi kafin ta zauna akan kujerar dake gefansa ,”tafiya zakiyi kema ko, nasan dama sai sun biyo ni yanxu ma,mugayene su”,girgizamasa kai tayi cikin hausarta da bata gama kwarewa ba har yanxu” ba barin ka zanyi ba,kaji doctor yace za a Dora ka under medication,and your leg shima kaga be warkeba, zanyi tafiya ne kafun na dawo nasan sun gama baka medication dinka sai mutafi tare zansa a dunga kula da kai kaji”, kallan ta yayi kafin ya miko mata dan karamin yatsansa kamar yanda suka saba shida tahee”kin mun alkawari”murmushi ta sakar masa kafun ta rike masa hannun,”I promise you!” Yanxu tell me ya sunanka,”Taheer”, jinjina masa kai tayi, you have a nice name, ka kwanta ka huta zuwa gobe zan dawo ,ok” kamar yanda ta umarceshi kwantawa yayi yana binta sa kallo, gashin kansa ta shafa kafun tace masa good night” shima good night yace mata kafun ta bar dakin, wasu hawaye ya share ,”oumma !! Tahee, nasan kunyi kewata, Nima nayi kewar ku sosai”, tunda ya kwanta tunanin oummansa da tahee yake, yana turo yanda sukai rayuwar su cikin wahala bayan mutuwar mahaifinsu amma duk da hakan sun kaunace junansu sosai , a haka bacci ya dauke sa me cike da mafarkai kala kala “. 🫧🫧🫧🫧🫧🫧 🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧 Damshin kirjinsa da ya taba tane yasa ta kara sakin wata karar, a tsorace ta rufe idanuwanta zata bar wajan ya rike hannunta,a kausashe ya furta bude idanuwanki, ba musu kuwa ta bude idanuwan batare da ta kalle saba “ me yasa zaki mun ihu a kunne”, ba komai ta amsa masa,guntun tsaki ya saki iya mako gwaro “ kalleni ki bani amsa kafun ranki ya baci”, a hankali ta dago da kanta kafun tayi saurin kulle wa sabida arba da kakkarfan jikinsa da tayi,cikin rawar murya ta furta “bazan iya ba”, gira ya dage guda daya kafun ya furta me yasa , da sauri ta furta “ba..babu kaya ajikinka “,murmushine yake kokarin subuce masa a fuska amma ya dake batare da yyi murmushin ba,”naji bude idanuwanki “, kara girgiza masa kai tayi “ Allah bazan iya ba”, jinjina mata kai yayi “okay tunda bazaki iya ba, amma kin iya ganin abinda ke cikin towel ko”, bata san lokacin da tayi saurin toshe masa baki ba ,wani masifaffen kunyarsa na kara kamata tuno abunda bata mafarki kara gani ,kamar zatayi kuka ta furta “dan Allah kayi hakuri”,hannunta da ta dora akan bakin ya sumbata, da Sauri ta janye hannunta tana kokarin barin wajan, janyo ta jikinsa yayi kafun ya soma kokarin cire mata rigar jikinsa , hannun nasa tayi saurin rikewa tana zaro ido waje wasu kwalla ne yasoma taruwa a idanuwanta,kallanta yayi alamun menene, sun kuyar da kanta tayi kasa ganin taki maganane yasa ya kwace hannunsa da zai mayar kan rigarta, ringing din da wayarsa tayi ne yasa ya jiyo slowly kafin ya nufi d’aya daga ciki, kamar yanda yayi zato abeey ne yake kiransa ganin tana kokarin tsinkewa ne yasa yadaga wayan, a hankali yayi sallama , shima a bangaran abeey amsa masa sallamar tasa yayi yana kallan ammey da sai faman sakin murmushi take tun lokacin da taji warkewar tahee dukda taji zafin abunda basma tayi sai bata nuna ba,tasa abeey da yace king ya saki yarinyar tunda wacce aka jiwa raunin ta samu sauki,tanbayar me jiki abeey yayi,kallan bayanta yayi lokacin da take kokarin shigewa cikin kofar dressing room dinsa yayi ,kafun ya masa da “Alhmdllh “a takaice,”TAHNOON “ abeey ya kira sunan sa kai tsaye, dan waro eyes dinsa yayi jin yadda abeey ya kira ainahin sunansa yau ,”na’am abeey” ya amsa masa cikin yar kasalar da ya faraji “inaso ka saki yarinyarsan, hukuncin da kayi mata ma ya isa haka ba sai ka kulle taba”, da mamaki king yace “wace yarinya abeey”,basma “ abeey ya kara furtawa , shi sam ya manta ma da ya kulle wata ma , tuno abunda tayi dazun yasa ransa soma bashi” abeey “ dakatar dashi abeey yayi, “umarni na baka “ yana kammala zancansa ya kashe wayar, bin wayar king yayi da kallo kafun y zura hannunsa guda daya akan sumar kansa yana ya mutsata . Dakin dressing dinsa ya shiga ,ganin bata ciki ya gane ta shiga toilet ne , a nutse ya shirya cikin white din kaya me shegen laushi, sumar kansa kawai ya taje da ta kara yawa kafun ya feshe ilahirin jikinsa da daddadan turaransa me sanyaya zuciya , yana gama shiryawa ya fito daga dakin, dakin da ya kulle ta a ciki ya nufa bayan yasaka turn print dinsa, Ba’a ganin komai na dakin sabida yan da wajan yayi duhu sosai , light din dakin ya kunna,kwance ya hangota a sume kan carpet din dake cikin dakin , babu komai a ciki sai wasu cushions da aka kawata dakin sai ya zama kamar na hutawa , a hankali ya tako inda take ganin bata motsine yasashi nufar fridge din dakin, wani ruwa ya dauka me shegen sanyi da ya fara kankara yana zuwa inda take ya bude ruwan tare da zazzaga maga shi, a matukar firgice ta farka daga suman da tayi tana faman zare ido, ganin har yanxu ruwan be dena zuba bane yasata sakin kara cikin firgita, tsawar da ya daka matane yasata shiga taitayinta,a mugun tsorace take kallansa da bakinta daya kunbura, nuni da yayi mata tayi mishi shirune yasa tayi saurin kame bakinta hawaye na tsiyaya da sauri sauri a fuskarta,dan ran kwafowa yayi kallo daya yayi wa fuskarta ya dauke kansa, a kausashe ya soma magana “Daga yau, ko me kama dake na kara gani a kusa da matata, sai na la’antasa ballantana ke da ko matsayin dan kwalin kanta baki taka ba” yana kai karshen zan cansa ya nuna kofa da hannunsa ,”kafun na irga uku ki bace mun anan idan ba haka ba sai dai a sauki kasusuwanki “ be rufe bakinsa ba ta arta a guje dukda yadda kafarta da fuskarta tane zugi, ba ciwon da yaji matane ya fi bakanta mata ba, matarsa da ya kira shine ya fi komai tsaya mata a rai,koda ya Fito daga dakin,lifter ya hau direct ta kaishi hawa saman sa, koda yashiga ne shiga daki ba, dakin da ya taba shiga nan ya shiga ,me aku a ciki kallan sararin samaniya yayi ganin yadda stars suka fiffito ga duhu da Garin yayi, sosai yanayin yayi masa dadi, kan wasu chairs ya samu ya zauna yana kara bin stars din da kallo har wajan karshe shabiyu kafun ya sakko down stairs , dakin da take ya nufa, koda yashi a cikin bargo ya sameta duk ta takure jikinta, sanyin Ac din ya rage sosai kafin ya taba goshinta, temperature dinta ya fara dawowa normal, dan goshinta da akai wa dressing ya bi da kallo kafun ya gyara mata abun lullubar tata,alwala yayi tare da kabbara sallah kamar yadda ya saba, bayan ya idarma karatun alkurani me girma yayi kafin ya kashe light din dakin gabaki d’aya yana janyota jikinsa. ASUBA TA GARI …. 🫧🫧🫧🫧 🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧 ABUJA CEDARCREST HOSPITAL LTD Karfe 8:30am ta shigo dakin da yake , ganin ya rakube ne yasa jikinta yin sanyi, yana ganinta yayi saurin kokarin tashi, dakatar dashi tayi tare da karasowa inda yake,kallan abubuwan da tasa akawo masa tayi ganin babu abunda ya taba, “me yasa bakaci abunda nasa a kawo mata ba”, jiki a sanyaye ya furta na dauka bazaki dawo bane ,kwallar dataji tana kokarin zuwar mata tayi saurin hadiye kafun ta ja plate daya serving dinshi”me yasa kake tunanin zan tafi in barka, as I promise bazan tafi na barka ba , da zaran na dawo daga tafiya na zan zo na d’auke mubar musu ganin gabaki d’aya kaji “girgiza mata kai yayi tare da saurin bude bakinsa ta saka masa chicken din daga debo, da kanta ta dunga serving dinta, bayan ta gama shima ya karba ya bata,wata irin kaunarsa yaron ne taji ya shigar mata zuciya farat daya. A asibitin ta zauna har yamma tana tare dashi,sosai ya bata labarin su oumma da tahee har ta soma kwadayin san ganin su, taji dadin hirar tasu ko ba komai ya debe mata kewa , wata kafceciyar waya ta dakko a cikin Jakarta kafun ta mika masa,”idan na tafi zamu dinga yin waya da kai kaji”, zaro idanuwansa yayi hawaye na zubar masa “dagaske zamu dunga yin waya “ gyada masa kai tayi “kwarai ma kuwa”,kara mika masa wayar tayi ganin yayi shiru be karba bane ta kallesa”me yasa bazaka karba ba” oumma zata mun fada ita da taheer ,kallansa tayi tana nazarin kalamansa tabbas mahaifiyarsa ta bashi tarbiya “bakaso ka dunga gaisawa dani kenan”girgiza mata kai yayi “inaso” ok karba , hannu bibbiyu yasaka ya karba, hawaye na zubo masa ya dunga yi mata addua har saida ta tsayar dashi kafun ta nuna masa yanda ake anfani da wayar bayan ta fito masa da games da yawa a ciki. Ba ita tabar hospital din ba sai 9 bayan ta masa alkawarin dawowa gobe da safe suyi sallama. ➰➰➰➰➰➰ ➰➰➰➰➰➰➰➰ 8:30am tsaye tahee take gaban mirrorn dakin tana faman taje uban tulun gashinta ,gaban goshinta duk ya jike da ruwa har ya fara taba dressing din da akai mata,dan guntun tsaki ta saki lokacin da take kokarin tufke kan, kamar ta saki kuka haka take ji,ganin ta kasa sakawan ne yasa cikin haushi ta jefar da ribbon din, yana tsaye jingine jikin kofa , tun lokacin da ta fara taje kan ta ya shigo cikin dakin,ribbon din data yar dar ya je ya dauka haryanxu bata Ankara dashi ba saida taji ana ta ba mata gashin kai,baki ta bude daniyar kwala ihu ,”if you dare “ ya furta kalmar a fusge, kallansa tayi sosai ta mirror ganin shidin ne da gaske yasa ta sakin ajiyar zuciya da harshi dake kusa da ita sai da yaji, gashin kan nata ya tufke kafun ya kalli dressing din da yayi mata “wa yace ki sawa ciwan naki ruwa”, in ina ta soma ganin ya zuba mata rikitattun idanuwansa kwata kwata fuskarsa ba fara, sun kuyar da Kai kawai tayi tare da furta “ina wanka ne ya dan jike”, be ce mata komai ba ya juya da niyar barin wajan yaji saukar muryarta “ ina kwana”, dan waiwayo da fuskarsa yayi kadan ya kalleta batare da ya amsa gaisuwar tata ba” karki bata mun lokaci am waiting for u now”, yana kai karshen zancenta ya fice a dakin,hararar kofar da ya fita tayi cikin kwaikwayar muryarsa ta furta ,”karki bata mun lokaci am waiting for u now “, sai kace wani baba na , cikin sauri kuma ta dauki hijab dinta gudun karya zo ya sameta a dakin, a tsaye yya tarar dashi har ta fito be kalli inda take ba sai ma kofar fita da ya nufa,ganin hakan yasa itama ta tabe bakinta tare da nufar kofar,yana fitowa zaki ya sara masa har ya bude masa kofa king ya dan girgiza masa kai tare da miko masa hannu,tsaya wa tunanin me ze basa yayi sai ji yayi king yace masa “the key” waro idanuwa zaki yayi cikin suman tsaye jin ya anbaci key,idan zea iya ranshewa karshen ganin king ya tuka mota da kansa tun lokacin da yake zuwa hutu ne,”the key" ya kara anbata, da sauri kuwa zaki ya bashi key din cikin girmamawa,wani dan karamin file king ya mikawa zaki , ba tare da yace komai ba ,shima zaki jinjina masa kai kawai yayi tare da barin wajan, motar da aka fito da ita , shiga ciki yayi tare da tayar da ita,kallansa tayi ganin be ce mata komai ba ta rasa ya zatayi,batare da ya jiyo ba ya furta “kika kuskura na kara cewa wani abu rankine zai baci”, be kara kalmar tasaba tai shahada Kawai tare da shiga front seat din motar,Kai tsaye part din dada ya nufa yana gama tana binsa a baya kamar wata jaka,dada da su abeey kawai ya tarar a falon , tana ganin tahee ta soma washe baki “oh ni yau Allah ya kawo ni lokacin da zanga tahura batare da ta buya ba” sun kuyar da kai tayi kasa tare da gaishe ta , amsawa dada tayi tana godewa Allah, su abeey ta gaisar yanxu kafun ta gaishe da su uncle Saleem da suke mata ya jiki,Shigowar mahma falon ne yasa ta gaishe da ita tama , cikin kulawa take tanbayar ta ya jikinta ,king ma gaishe da iyayan nasa yayi daga nan be kara cewa uffan ba ,shi dai abeey lokaci zuwa lokaci yana sakin murmushi musamman kunyar yarinyar tana burgeshi. Ganin taki sakewa ne yasa mahma janta da hira , mikewa king yayi , kallansa abeey yayi “ina zakaje son” “ammey” ya furta wa abeey kallan tahee abeey yayi “ daughter tashi ki bishi kuje ,Allah yayi muku albarka baki daya “Ameen kowa ya ansa masa kafun subar part din, sosai take zumudin ganin aunty ta yanayin parking ta fito da Sauri ta manta ma tare da wa take, tsaye ammey take tana duba abincin kan dinning sai ji kawai tayi an rungumeta ,da Sauri ta juyo dan ganin wanene,”ammey nayi kewar ki”, tahee ta fada tana fashew da kuka,itama Ammeey hawayene ya fara zubo mata a tare suka kara rungume junansu suna yin kukan , ganin kukan nasu ba me karewa bane yasashi karasowa Inda suke hannu yasaka ya sharewa ammey hawayen nata,” tare da kallan tahee ,rikitattun idanuwansa ya sa mata be ce komai ba ya kama hannun ammey suka zauna a falo, yayi farincikin ganin wannan murmushin na ammey da ya dawo, abinci ta saka musu su duka ta hada tana bawa a baki , TAHEE kam kadan taci tace ta koshi kasantuwar king a wajan. Sun dade a part din ta kafun su nufi part din ummey, itama sosai tayi farin cikin zuwansu, zoya ma tana ganin tahee ta nufeta wai suje suyi wasa,cikin jin kunya ta saki murmushi tuno lokacin da suke wajan , hira sosai zoya ta dunga bata har saida king ya dakatar da ita, lumshe idanuwa tahee ta fara , tun shigowarta falon ta fara jin jiri jiri da wani abu kamar yana kiran sunan ta , daurewa kawai take , ynxu ma jirin da take ji ne yasa ta yin shiru, sun kara kusan mintuna 5 a part din kafun suyi mata sallama itama , tana fitowa daga part din taji wani d irin juwa ta kamata kamar wacca aka bangaja zata fadi kenan king ya rikota,itama cikin tsora ta rike hannunsa sosai kamata yayi suka shiga mota, ganin yadda take sauke ajiyar zuciya ne yasa shi taba goshinta,normal temperature dinta yake , part din mahma ya mayar da ita , zata fita ya rike hannunta ,”are you ok “ amsa masa tayi da ka kafun tace masa “eh”tana shiga ta tarar da sha’aban zai fita ,cikin girmamawa ta gaishewa, shima amsa mata yayi kafun yayi mata ya jiki , ganin kiran king yasa shi saurin yi musu sallama tare da barin part din. Hira suka fara duk da tahee tana nonnoke mata ,amma sai da tasa ta sake da ita, wani boil babba mahma ta miko mata tare da umartarta ta cinye komai da ke ci, ba musu ta karba kuwa ,loma daya tahee tayi kamar me shirin yin amai, cikin narai narai da ido ta kalli mahma, fahimtar haka yasa mahma hade ranta batare da ta bata damar yin korafi ba. 🫧 💖💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖💖 Mss Lee 💖 💖💖GIDAN AUNTY💖💖 ( a heart touching love story) Story & written By Mss Lee 💖 💖💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖💖 PAID BOOK MAIBUKAR COMPLETE DIN GIDAN AUNTY YA TUNTUBENI TA WANNAN NUMBER 07041879581. بسم الله الرحمن الرحيم 💖 BOOK 1📕 PAGE 47_48💖 Har kusan 3 na yamma tahee tana bangaran mahma kafun ta nufi bangaran ammeeyn ta acan ta yini sosai ammey take kula da ita, har tsawan wannan lokacin kuma bata ga yan matan gidan ba har ynxu kuma ba’ayi magana akan warkewarta ba. Yan zuma kunun ayar da ammey ta hada ta bata sai faman tashin kamshi yake, tana kammala sha dakinta ta nufa wanda tuni an gyara mata,bin dakin tayi da kallo ,dan murmushi kawai ta saki kafun ta dakko wani material purple me simple style, Wanka kawai tayi tare da kwantawa jin kanta ya dan fara sara mata,ribbon din kanta daya takura mata tacire, take a wajan dogon gashin kanta ya sakko har wajan kwankwasanta, shima mayafin material din jefar dashi tayi a kasa ta kwanta, ba dadewa kuwa bacci ya dauketa. 7:01 pm ammey ta shigo dakin sanye da hijab a jikinta, kan gadon da tahee take ta nufa ganin tana baccinta cikin kwanciyar hankali, shafa gefan fuskarta tayi kafun ta kira sunan ta a hankali “Tahee”, bata amsa ba sai da ammey ta kara kiran ta har sau biyu kafun ta motsa, a hankali ta fara ware idanuwanta kafun ta bude su gabaki d’aya ta sauke kan ammey, murmushi ta sakar mata, itama ammey martanin murmushin ta Mayar mata” oya a tashi a yi sallah, yanxu zan sa asabe ta kawo miki abinci,and idan an idar da sallahr isha’i zamuje part din abeey yana nemanmu”,a sanyaye ta amsa mata da toh ammey. Ammey na fita itama ta mike ganin lokaci na tafiya ,alwala tayi tare da kabbara sallah, ta idar kenan ta soma kukan da ya rike mata makoshi, sosai take kukan ,oummanta da taheer take yiwa addua da kyar ta tsayar da kukan da take tana sauke a jiyar zuciya, idanuwanta har sunji jajawur da su, tana zaune kan sallayar asabe ta kwan kwasa kofa , bata izinin shigowa tahee tayi , bayan tayi mata ya jiki sannan itama ta fita,bataci abincin da aka kawo mata ba sai da ta idar da sallar isha’i , shima dan tsakura kawai tayi sabida yanda ranta yake ba dadi, gudun kar ammey tai ta jiranta, ribbon dinta kawai ta saka tare da rolling din mayafin kayanta,turaren ta, ta saka dan kadan bame hawa kai ba tare da fitowa falo, kamar kuwa ta sani itama Ammeeyn ta shirya cikin ado na musamman cikin wata golden din Abaya ,tana ganin tahee ta sakar mata murmushi tare da furta “tabarakalla,daughter wannan kyau haka ko sarauniyar kyau albarka”murmushi kawai tahee tayi ,kama hannunta ammey tayi kasan tuwar basu da nisa da part din abeey yasa cikin dan kankanin lokaci suka karaso. Gabaki d’aya family din suna zaune a babban falon abeeey tun daga kan dada har zuwa kan zoya da tana ganin tahee taje ta rungumeta. Gabaki d’aya mutanan falon maida hankalinsu sukai kan tahee dake bayan ammey, hatta basma da fuskarta take a kumbure tana falon sai faman kakkare fuskarta take, dauke kanta tahee tayi daga kan basma kafun su karaso cikin falon, sai yanxu ta kula baya cikin dakin, wani ajiyar zuciya ta suke ganin bayanan, kamar yanda yan matan ke zaune kan shinfidadden carfet din falon,itama waje ta samu ta zauna a rabe. Bude taron abeey yayi da sallama ,kafun yayi gajeriyar addu’ar bude taro, bayan ya gamane ya cigaba da jawabinsa “ muna godewa Allah da ya kawo mu wannan rana ,kamar yadda kowannan ku ya sani d’aya daga cikin ku ta samu larura Wanda ya kawo ta rasa tunaninta har akai mata aure ,yanxu ma cikin kudurarsa Allah ya bata lapiya “, in a serous turn ya dora da “kowa yasan yar hatsaniyar da ta faru tsakanin ke basma(ya nunata) , da kuma abunda kikai wa tahee har yajawo mijinta ya miki hukuncin, daga yau inaso nasanar da kowa dake cikin falon nan, taheera Matar king ce , dole a matsayinku na kannansa ku girmamata a matsayin matar yayanku, sabanin hakan kuma zakuga bacin raina, hakan kuma ba yana nufin itama zata rainakuba, magana ta karshe da zan fada kuma shine tahee zata cigaba da zama a Wajan auntynta kamar da har zuwa bayan sati daya da za a mika ta dakin mijinta kamar yacce ake yiwa kowa ce budurwa, ninan uban tabe, komai da ake wa ‘ya nine nan zan mata shi ,wannan nauyinane “. Ba tahee da tayi suman zaune ba , gabaki d’aya yawancin mutanan falon sai da gaban su ya fadi, kowa da abunda yake cin ransa, amrah ma ihu ne kadai ba tai ba dan yanda ta toshe bakinta, ita kadai kawai take girgiza kai, sumayya kuwa mamy kawai ta kalla ta d’auke kanta,wasu zafafan hawayene suka fara sakko wa basma cikin idanuwanta, tayi mugun nadamar zuwa gidan tun farko da duk hakan bata faru va , da ta Sani a hostel tayi zamanta wajan friends dinta, wani tukwikwin bakin cikine ya tokare mata makoshi amma babu damar maganar, bata kammala zan can zucinta ba maganar abeey ta shiga dodan kunnanta da take jin tun da take a rayuwa bata tabajin bakin cikin da taji yau ba, “daga karshe inaso basma ki bawa tahee hakuri sabida raunin da kika ji mata,” sannan cikin girmamawa ya kalli dada “dada kina da abun cewa “Numfashi dada ta sauke bayan ta gama sauraran bayanan abeey “ Ni de babu abunda zance sai Jan kunne , duk wanda ta kara taba mana tahura wallahi ran kowa zai baci a cikin gidan nan, Kai ma zayedu shawaran dakayi shine daidai,Allah yayi maka albarka”, amsawa abeey yayi da Ameen kafun ya mai da hankalinsa kan ummey da abeey ko suma suna da abin fada,Babu Wanda yayi musu acikinsu sai albarkar da suka sa,murmushi yasaki tare da cewa kafun na sallami kowa inaso basma ta bawa wacce ta jiwa ciwo hakuri sannan karta kara gangancin yin abunda tayi dan kuskure ce. Wani kululun ba’kin cikine ya kama basma, kukan dake kokarin kwace matane tayi saurin hadiyeshi,kafun ta bude baki ta bawa tahee hakuri.ita tahee bata san ma meke faruwa ba Sabida dogon zangon tunanin data fada,nasan daita daga kanta kawai batare da ta kara fuskartar komai ba, bayan komai ya lafa abeey ya sallami kowa da kowa sannan ya umarci tahee ta tsaya ita kadai. Kamar yanda kuwa ya umartan gabaki d’aya kowanan su part din dada suka koma masu tattaunawa sunayi, su aunty ma ba damar ta fiya dole sea an bar part din dada tukunna, itama dada mikewa tayi tare da nufar part dinta ta jikin falon abeey acewarta zakaje ta Hutu, falon yayi saura daga abeey sai tahee da tunda aka watse kanta yake a kasa ko kwakkwaran motsi ta kasa.shima abeey din baice mata komai ba kusan mintuna biyu kafun ya fuskanceta “Nasan akwai abubuwa da yawa abakin ki daughter , sannan nasan kinsan ke yanxu matar aurece, ba wai munyi miki aure bane dan bama sanki ba, kaddarar kuce Allah ya hada duk da kowa yasan dalilin Auran naku, yanxu kuma Alhamdulillah kinsamu sauki shine daman abunda muke fata ,Amma duk da hakan bazamu tauye miki hakkin ki ba, idan kinsan zaki iya zama dashi a matsayin mijin ki shine fatan mu,amma idan bakya ra’ayi ni da kaina na miki alkawarin zansa ya sake ki, karki la’a Kari da murdaddun halin mijinki,indai zaki fuskance sa zaki gane mutum ne ne saukin kai , ba’ina fada miki haka bane dan kin so shi , kome kika yankewa kanki ni me goyan bayanki ne daughter “ ya karasa zancan nasa yana kallanta duk da akasan zuciyarsa fata yake Allah yasa ta amince da Auran ko zata dawo masa da ainahin king dinsa kamar da . Tunda ya fara zan tukansa wani irin masifaffiyar kunya ya kamata , sosai ta sunkuyar da kanta kasa tana wasa da yatsun hannunta, kalamansa sosai suka dakar mata zuciya , wacece ita da zata kujewa bukatunsu, bayan sun share mata hawaye a lokacin da take bukata , sun bata kula war da ko mahaifiyarta sai haka , lokaci d’aya kukan da bata shirya masa ba ya kwace mata, sosai take kukan ta , abeey kawai kallanta yayi ba tare da yace komai ba , saida yaga kukan bame karewa bane ya tsayar da ita tare da mika mata tissue,”kiyi hakuri daughter nasan bamuyi miki adalci ba, karki damu ki fadi kome ke ranki , kada ki dauke ni a wani matsayi daban ki dauke ni amatsayin mahaifinki kamar kowa “, cewar abeey, hawayen da suke faman rige rige akan fuskarta tayi saurin goge wa ,cikin wasa da yan yatsu ta soma magana “nagode sosai abeey Allah yasaka da alkairi,kun gamai mun komai a rayuwa ta, wacece ni da zan sabawa umarninku, ni me biyayyace a gareku, duk zabin da kuka yanke shi zanbi”, ta karasa zancan nata murya a karye haryanxu hawayen da suke zubar mata be tsaya ba, wani murmushi ne ya fito a saban fuskar abeey, azuciyar sai faman godiya yake wa Allah ,”Allah yayi miki albarka daughter ,yanda kika faranta mana kema Allah ya baki masu faranta miki,nasan har yanxu ciwan kanki ba warkewa yayi ba ya kamata kije ki huta”, jinjina masa kai tahee taji dan kanta harya fara mata ciwo kafun tace masa sai da safe tabar part din. Koda ta fito daga part din abeey wani jirine taji yana neman kayar da ita , ko kallan gabanta batayi kawai tafiya take, tana kaiwa part din Ammeey bedroom dinka ta nufa kaitsaye, kan gadon kawai ta fada tare da lullube jikinta da babban bargo, lokaci d’aya taji wani irin sayyi na shigarta ga AC da yake a kunne amma ta kasa tashi kashe, (wannan shi ake kira ga samu ga rashi), lokaci d’aya ta fashe da kuka ,kukan da batasan kukan me take yi ba , na farinciki take ko aka sinsa, mutanan gidan sun zamar mata kamar ahalin ta,wacece ita da zatayi musu , wani Saban kuka ne ya kwace mata musamman tuno da su oumma da tayi ,lokaci d’aya wani zazzafan zazzabi ya shigeta,kukan da take yi har ya dauke sai faman sauke ajiyar zuciya da take faman yi. 🫧🫧🫧🫧 Tunda suka nufi part din dada kowa da yadda zuciyar sa ke bugawa, mafi aka sarinsu tsayawar da abeey yace tayi ne yafi tsaya musu arai, ga maganar tarewarta da ya bullo dashi, a tunaninsu tunda ta samu lapiya sakinta king zaiyi ta kama gabanta amma sai abun yazo musu baibai, basma kam tana shigowa masaukinta ta wuce kamar wata zararriya, amrah ma tun tana danne abunda Ke ta soma mata har ta kasa ta bar part din cike da bakin ciki da zantuka mabanbanta da ita kadai ta barwa kanta sani. Su ummey ma part din mahma suka shiga sabida yanda ta kasa ta tsaye akan sai Anfara shirye shiryeki biki tunda sati d’aya ne dasu ba lokaci sosai,ita kadai sai zancen event din da yakamata ayi take yi tace a wannan karan ko king yana so ko bayaso sai anyi ko da dinner ce, sudai sai binta da ido suke , ganin sai faman lissafi take yi na abubuwan da ya kamata ace anyi wa amarya, ba ‘bata lokaci ta kirawo AMZY SALOON da kanta, kowa yasan amzy gwanace a fannin gyara amare musamman idan zaka kashe mata kuyi ydda ya kamata ,itama zata sa yaranta suyi maka gyara na musamman , da Yawan lokaci kuma batayi wa mutane da kanta sabida sai me kudi ne zai iya daukar ta, ta iya gyaran amarya na bugawa a jarida tun daga kan gyaran jiki har kan abubuwan da za’ a bawa amarya . Ganin babu lokaci ne yasa mahma kiranta , sannan ta mika mata makudan kudi acewarta ya hau jirgi tazo gobe , sosai kuwa amzy tayi mata godiya da alkawarin zata zo goben. Sun dade suna tattaunawa kafun ammey ta nufi part din ta , amma bata shiga dakin tahee ba Sabida umarnin da abeey ya bata , wanka ta sake yi kafun ta shirya cikin wasu leshi Masu shegen kyau kafun ta nufi part din abeey bayan ta janyo part dinta, itama ummey part dinta ta wuce kai tsaye , koda suka fito kuwa kowa ya tafi part dinsa. 2:43am ya shigo dakin da take hannunsa dauke da coffee yana sipping a hankali, wata yar karamar jaka da ya shigo dakin da ita ya ajiye kafun ya karaso gaban gadon da take, ganin yadda jikinta yake rawa ga busassun hawaye kwance akan fuskarta yasa shi tabe baki kadan , hannunsa daya ya dora akan goshinta da sauri ya cire hannun nasa yana dan zaro idanuwansa waje, yayi mamakin yanda kanta yayi Wanda zafin sosai,Acn dakin ya kashe gabaki d’aya kafun ya kamar da shi heater, gabaki d’aya dakin ya dau dimi, jakar da ya shigo da ita ya dauka , drugs ne a ciki sai allura guda biyu ,alluran ya hada kafun ya kai hannun kan duvet din ta ya dan yayeshi kadan, tun kafin ya janye hannunsa taka Jan duvet din ta lullube jikinta dashi sosai sabida yanda sanyi ya ratsa mata gabobin jikin nata, zama yayi a gefan gadon kafun yanxu ma ya kara yaye duvet din gabaki d’aya , da sauri ta farka daga baccin da ya dan fisketa,kwata kwata jikinta ba kwari, lokaci d’aya idanuwansu ya sarke cikin na juna a mugun tsorace ta zabura saura kadan ta fada daga kan gadon,hannunsa daya yasa tare da janyota jikinsa, kallan yanda fuskarta tayi so week yayi yana binta da wani kallo da shi kadai ya san ma’anarsa, ganin yanda yake kallanta yasa lokacin d’aya kukan da batasan namenene ya kwace mata, be ce mata komai ba sai kara binta da kallo da yayi na yan sakin ni,”Me akai miki” shiru tayi kukan da take tane meshi ta rasa ,yanda yayi maganar yasata jin wani irin a jikin ta da yasa ta dan zabura kadan,kara maimaita maganar tasa yayi ta sun kuyar da kanta kansa ta rasa abun cewa , goshinta ya kara tabawa har yanxu da zafi sosai ga rawa da jikinta keyi, coffeen da ya shigo dashi ya dauka tare da saitawa saitin bakin ta,kawar da Kai tayi dan kwata kwata bata jin yunwa ,”don’t waste my time” ya fada a kausashe yana binta da rikitattun idanuwansa , ba musu ta sanye ragowar coffee din ya zamar mata kamar magani, magungunanta ya bata ,suma da kyar ta shanyesu ganin yanda ya bata rai lokaci d’aya , allurar da ya dakko ne yasa ta girgiza masa kai, saura kadan ta kware da ragowar ruwan bakinta, hannunsa daya ya kai bayanta a bazata ya kwance madaurin rigarta, da sauri ta kama rigar wasu hawaye na zubar mata ganin ta ki sakin rigar ne ya sa ya dan daka mata tsawa kadan”saki rigar”,da sauri kuwa ta saki rigar gabaki d’aya ta sauko daidia kwankwasanta sabida yanda take a zaune, farar vest dintace ta bayyana da ya fito da shatin beast dinta da suka tsaya car dasu, kallo daya yayi musu tare da dauke kansa, allurar da ya dakko ne yasa zata fara yi masa kuka , a fisge kamar Wanda aka sa dole ya furta “karki sa ranki ya baci”, kuka ta fashe masa dashi “dan Allah kayi hakuri” ta furta muryar ta akarye ko fitowa batayi sosai , ganin kukan bana kare wa bane a bazata ya hade bakinsa da nata, waro manyan idanuwanta tayi akan sa fuskarsa,kamar yadda take bunsa da kallo shima kallan nata yake, lokaci d’aya ya janye bakinsa daga nata bayan ya kammala allurar da yake mata, wata kunyarsa ce ta kamata tayi saurin sun kuyar dakanta kasa, tana kokarin mayar da rigar jikinta ya rike jigar da jefa mata maya taccen kallonsa, sun kuyar da kanta kasa tayi zuciyarta na faman bugawa ,idanuwansa ne suka sauka akan breast dinta musamman yanda yake dagawa da sauka lokaci d’aya kuma ya janye idanuwansa akai, remote din light din dakin ya kashe ya bar dumb light din, a mugun tsorace ta kallesa , ta dauka fita zai yi daga dakin, janyota jikinsa da ya karayi ne yasa duk tsikar jikinta tashi,matsota da yayi jikinsa yaji hucin zafin jikinta har zai mike sai kuma ya fasa, rigar jikinta da ya fara cirewa ya karasa cirewa gabaki d’aya ,yayi saura daga vest din jikinta sai dan tights din ake jikinta,rungumota yayi jikinsa ba tare da yace mata komai ba, kokarin kwace jikin ta take sai faman mutsu mutsu take a kunne ya rada mata “stay still”, tsayawar tayi kamar yanda ya umarceta,kara rungumeta yayi a jikinsa lokaci d’aya suka saki ajiyar zuciya,zafin jikinta na ratsashi, a bangarantama dumin jikin sa da takeji yasa jikinta dena rawa da harshi kansa sai da yaji alamun hakan,kara matseta yayi a jikinsa ganin vest din jikinta na sukarsa yasa ya fisge vest din, tsayayyun breast dinta suka sauka akan kirjinsa, kara kannata yayi a jikin nasa jin saukar breast dinta,tun lokacin d’aya fincike mata vest din jikinta ta lumshe idanuwanta sabida kunyarsa da ya kamata duk da bata ganinsa,raba jikinsa yayi da nata kadan a tunaninta barin dakin zaiyi har ta fara sakin a jiyar zuciya, Rigar jikinsa ya cire ,kakkarfan jikinsa ya bayyana duk da ba’a iya ganin jikin nasa,janyota yayi jikinsa kai tsaye tsayayyun breast dinta suka sauka akan fatar jikinsa, wani irin shock ne ya dan ziyarcesu gabaki d’ayan su, kara rungumeta yayi kamar wacce ake shirin kwace masa ita,white duvet din da ya yaye ya janyo da hannu daya ya rufe su har fuska, jin yadda zuciyarta ke harbawa da sauri sauri ne yasashi dan sakin ajiyar zuciya “babu abunda zan miki” ya furta akasa kasalance,kafun ya kara da “zafin jikin ki zan saukar miki dashi”, yana kammala zancansa ya dago da Habarta da tayi saurin rintse ido, bakinsa ya saka cikin nata ,lokaci d’aya ya fara bata wani irin hot kiss me tsayawa a rai, tun yanayi a hankali har ya fara yi da zafinsa,ganin hakan be masa ba yasa shi mirginata tare yi mata runfa , bakinta kawai yake sumbata kamar Wanda ya samu sweet ,tsotsanshi yake kamar ya samu wani abu me dadi, cikin rawa rawa da hannunsa ya fara yasashi dora hannunta kan breast dinta, gabaki dayansu ajiyar zuciya suka Sauke lokaci d’aya , sarrafata mata kirji kawai yake kafun ya soma yawo da hannunsa a fatar jikinta har ya kawo kan ciniyarta, yanxu ma wani sabuwar ajiyar zuciya tahee ta sauke jin wani bakon al’amari na ziyartarta, shock dinta be kare ba sai lokacin da taji saukar hannunsa a kan marar ta yana shafawa, a mugun tsorace ta fara ture , tun tana tureshi a hankali har ta farayi da dankarfi murya a sarke ta fara kiran sunanshi da karfi ganin yana kokarin zura hannunsa cikin tight dinta, kuka ta fashe masa dashi tare da rike hannun nasa,dan dago da fuskarsa yayi ya kallesa kafun da dan karfi yaja breasts dinta yana matsatsu,kuka ta kara fashe masa dashi lokacin da taji dumin bakinsa akan breast dinta,kamar dan jariri mejin yunwa haka ya fara tsotsarsu, sosai yake shansu da zafi zafi kamar Wanda zai zuke abun ciki, ya dau kusan kin tuna goma abu daya , tun tana hawaye har ta dena Sabida radadin da taji breast dinta nayi duk lokacin da ya matsasu,kamar Wanda aka tsikara kuma yayi saurin takin kan nonon nata, da mugun sauri ya sauka kanta tare da juya mata baya, dafe goshinsa da ya sara masa yayi da cikinsa daya fara masa ciwo ,be kara kallan gefenta ba ya saka rigarsa tare da ja mata duvet din ya lullube mata jiki, har yazo zai fita kuma ya sake dawowa dan tapping bayanta yayi kadan kafun yayi mata peck a goshi,”good night “, ya furta murya a shake. ➰➰➰➰➰➰➰ ➰➰➰➰➰➰➰➰➰ 💖💖💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖💖💖 MSS LEE 💖✊ 💖💖GIDAN AUNTY💖💖 ( a heart touching love story ) Story & written By Mss Lee 💖 💖💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖💖 WANNAN PAGE DIN NA MAMAN SUDAIS NE 🙌❤️❤️. PAID BOOK MAI BUKATAR COMPLETE DIN GIDAN AUNTY YA TUNTUBENI TA WANNAN NUMBER 07041879581. BOOK 1 📕 Page 49_50💖 🫧🫧🫧 AMRAH Tana komawa part Dinsu ta fara sakin ihu, ihu take kamar wata zautacciya, data ga hakan be mata ba sai ta fara birgima a kasa tana kuka, sosai take kuka kamar wacce aka ce mata mahaifiyarta ta rasu, a haka aunty tazo ta tarar da ita , bata kulataba tayi shigewarta daki itama dan ita kadai tasan yanda ranta yake tafarfasa, “a wannan karan dole nayi wani abu”cewar aunty lokacin da take karasa shiga dakin ta. Wani saban bakin cikin ne ya kama amrah ganin yanda aunty ta shareta kamar bata san da wanzuwarta a wajan ba, itama a fusace ta shige dakinta, ko zama batayi ba ta dannawa mahaifiyarta kira , kusan missed called uku tayi mata babu Wanda ta daga a ciki,ihu amrah ta saki tana jefar da wayar tata a kasa baki d’aya, take a wajan wayar ta bada sautin kas_kas, a fusace ta juyo, juyawar da zatayi idanuwanta ya sauka a kan fuskarsa da take sanye da mask baki, sosai idanuwansa yayi jajur alamun bacin rai Tsanta kan fuskarsa, duk da tsoran da ya kamata ganinsa cikin tsiwa da bakin cikin dake ranta ta nuna masa kofa”me ya kawo ka dakina ka zo ka futar min a daki”, ba ta karasa zancanta ba ya fesa mata wani power a fuska ,take a wajan ta zube kasa, cikin Bacin rai ya daga ta dare da jefata kan gadon, ransa ba karamun baci yayi ba yau, sex yake da amrah kamar yasamu kayan wanki haka yake anfani da ita duk da kasancewar a bude take amma hakan sai da yayi mata kaca kaca cikin bacin rai, ya dade yana lalata da ita kafun ya sauka a kanta yana gyara mask dinsa dake kokarin cirewa,ko kallan inda take be kalla ba yabar dakin. 🫧🫧🫧🫧🫧🫧 🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧 WASHE GARI Kiran sallar asuba ne ya tayar da ita sai faman ya mutse fuska take , adduar tashi daga bacci tayi tana dafe goshinta,Kallan jikin ta tayi kafun ta tuno abunda ya faru tsakanin ta dashi, dan karamin bakinta ta turo tana hararan gefen da ya zauna kamar yana wajan “mutum duk yabi ya lallatsewa mutum jiki” ta karasa tana mike . Wanka tayi kafun ta dora alwala ,ko da ta fito doguwar Riga ta saka mara nauyi Sabida yan jikinta yake mata tsami musamman breast dinta dake mata zafi. Tana idar da sallah karatun alkurani ta zauna tanayi kafun tayi wa oumman ta da taheer addua, sannan da neman zabin Allah akan Auran da akai mata duk da tasan ita din ba tsararsa bace bazai taba karban taba, har yanxu jikinta da sauran zafin zazzabi, dogon hijab dinta tasaka ta fito falo fuskart duk tayi fayau da ita, bata tarar da kowa ba a falon , yunwar da ta faraji ne yasata nufar kitchen , tea kawai Tasha dan kadan ,shima tana kammala shansa taje ta amayar dashi, bata kara zama a falon ba ta koma dakinta tayi wanciyarta. 💖💖 A bangaran king tun da ya bar part din kai tsaye part dinsa ya koma ,idanuwansa duk sun canza daga launin fari zuwa jajawur,jijiyoyin goshinsa duk sun ya fito asaman kansa rudu rudu, cikin zafin nama ya nufi kitchen din sa, bai tsaya a ko ina ba sai wajan coffeee maker dinsa, kadan ya hada ya kai ba ki, tana kai wa kuma ya furzar dashi daga bakinsa ,rumtse idanuwansa yayi duka biyu yana nufar lifter dinsa , ko da ya isa 3rd floor , toilet din white room dinsa ya nufa , ruwan sanyi kawai ya sakar wa kansa hatta kayan jikinsa ba cire ba , ya dauka sama da hour 1 ruwa na dukansa, ganin mura na kokarin kamashi yasashi kashe ruwan, kayan bacci kawai yasaka ruwan kansa sai tsiyaya yake ,fresh water yauka Mara sanyi tare da dakko wasu magun guna dake bedside dinsa, Yana kammala shansu, karfin gudun Acn ya kara tare da kwantawa, tunda ya kwanta nunfashinsa sai faman seizing yake kamar zai fita daga gangan jikinsa, tunda ya runtse idanuwansa be bude ba sabida yanda jake jin kansa, ya dade a haka kafun bacci ya dauresa. Washe gari tunda ya tashi daga sallar asuba be koma ba, ransa a cunkushe yake yin komai , ko bayan da aka idar da sallah be nufi part din kowa ba ya koma part dinsa , kwata kwata babu digon murmushi akan kyakkyawar fuskarsa. 🫧🫧🫧🫧🫧 🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧 🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧 Karfe 12 da rabi ta farka daga baccin da ya dauketa, ganin yanda lokaci yaja ne yasa ta sake yin wani wankan ta shirya cikin doguwar rigar atanfa da ta fito da ainahin shape din jikinta, hakan nan taji sha’awar yin make up , powder kawai ta saka sai kwalli daya fito da fararan idanuwanta, lipstick ta dauka fari tasaka a dan karamin bakinta ,kafun ta daura dankwalinta daurin zahra buhari gashinta na sakko wa har gadon bayanta. Bin fuskarta tayi da kallo,”fatabarakallahu ahsanin khalikin”, iya kyau kyanta ya fito musamman yanda manyan kyawawan idanuwanta suke lumshewa ,idan ba sanin ta kayi ba sai ka dauka wata balarabiyace , kyanta na buzaye sosai ya fito da yawunta,ita kanta murmushi ta sakar wa kanta da ya sanya dimples dinta lotsawa,kamar wacce taga wani sai kuma ta saka duka hannayenta biyu tana kare fuskarta, kasa kasa take dariya ita kadai. Tana fitowa falo ta tarar da su ihsan su hudu, ihsan, firdausi,sumayya ,sai wata da ban da bata taba ganin taba . Ihsan na ganinta ta zaro idanuwanta waje dan batai tunanin kyaun taheen ya kai haka ba, kallanta kawai take sosai tayi mata kyau iya kyau hatta su sumayya da firdausi binta da kallo suke Musamman gashinta da ya zubo har gadan bayanta,bakuwar da suka zo da ita ma bin tahee tayi da kallo lokaci zuwa lokaci tana sakin murmushi,mamakinta ina suka samo wannan balarabiyar. A hankali tahee ta karaso cikin falon duk ta tsargu musamman yanda suke binta da kallan kurilla , murmushi ihsan ta sakar mata , amaryar yaya sannu da zuwa , wani iri tahee taji da ta kirata da wannan sunnan, dan guntun murmushi kawai ta saki tana gaishesu kafun ta gaishe da bakuwar itama, bayan gaisuwa kuma bata kara cewa komai ba tayi shiru da bakinta, lokaci zuwa lokaci suna sako ta a hiran da suke,daga uhmm sai eh ko aah ne amsarta. Sallamar mahma ne yasa suka maida hankulansu gabaki d’aya kanta, gaishe da ita tahee tayi , cikin kulawa kuwa mahma ta masa tana tsokanarta”wato har kin fara mantawa dani kenan ko”, dan sunkuyar da kanta kawai tahee tayi kasa tana wasa da yan yatsun hannunta, itama mahma bata kuma cewa komai sai waje da ta samu ta zauna cikin yan matanta, tana nuna bakuwar dake falon,” wannan sunan ta azeema, daga yau Itace zata dunga kula da abunda ya kamata kici , da gyaran da za ayi miki duk Itace zatayi miki,nasan baki santa ba,sannan inaso ki hada kayanki yanxun nan driver na Wajan part din nan ,zai kai miki kayanki part din da zaku zauna ayi muku gyaran jikin”, ta karasa zancanta tana nuna azeema itama” amzy wannan Itace amaryar tamu , please a gyaramun ita sosai da sosai”, murmushi amzy ta sakar mata ,”insha Allahu aunty baki da matsala za’a gyara miki ita sosai da sosai”, itama mahma murmushin ta saki “ nasan zaki iya ai “, ihsan ce ta kalli mahma ,”amma mahma har da mu za’ayi gyaran jikin ko”,kallansu tayi daya bayan daya kafun ta furta wanene yakeso ayi dashi,tunkan ta kai karshen zancenta ihsan ta daga hannunta, itama firdausi hannun ta ta daga acewarta bazata cutu ba ayi ba ita,sumayyace kawai bata daga hannun ba , ganin mahma na kokarin dauke kanta yasa ita ma ta daga hannunta, ranta duk ba dadi amma ya zatayi ta kara yadda dacewa king yayi mata nisa ,musamman ganin har yanxu yarinyar da take nunawa tsana ko saudaya bata taba daga mata yatsa da sunan rashin kunya ba,”Allah ya bani Nima nagari”ta fada kasan zuciyar ta dukda tsananin san king dake cikin ranta amma tayi alkawarin kokarin ciresa daga ranta itama . Murmushin farin ciki mahma ta saki,”toh amzy ga wasu yan matan kin samu , bayan su ma akwia karin guda biyu, duk zasu koma part din , Inya so sai ayi musu gyaran”,cikin gamsuwa ta furta Insha Allahu. Maida kallanta mahma tayi kan tahee da kanta ke durkushe tana wasa da yan yatsu, “oya daughter tashi kije ki hada kayan naki, nan da 30 minutes za’a kai miki can part din da zaku zauna,cikin sanyin jiki ta furta “toh “ kafun ta mike ta shiga cikin bedroom dinta,ta kulle kofa kenan tana jiyowa taci kara da faffadan kirjinsa,baki tabude zatayi ihu hannunsa d’aya kawai ya saka ya toshe mata baki tare da jinginar da ita jikin kofar,fuskarta yabi da kallo musamman dan karamin lips din ta dayasha lipstick sai maiko yakeyi, Zara zaran lashes din ta suke faman kadawa yabi da kallo, sosai ya kare mata kallo tunda ga kan kafafuwanta har zuwa tummy cikinta, kafun ya dauke idanuwansa akan kirjinta dake faman harbawa , hannunsa d’aya ya dora kan breast dinta, da sauri ta saki karamar kara tana ya mutse fuskarta tare da jan jikinta kadan baya, fuskar da ta ya mutse ya kalla kafun ya kara mayar da hannunsa kan kirjin nata, yanxu ma baya ta kara ja tare da saurin rike hannusa, kwalla har ta fara tarar mata,”me ya faru” ya furta a hankali,cikin rawar murya ta furta”za..fi,zafi nake ji agurin “, be ce mata komai ba ya matsa daga wajan da take , Daidai saitin mirror din dakin ya koma yana bin wjan harabar filin da kallo, itama sun kuyar da kanta kasa tayi tana dan satar kallansa sabida kyan da ta ga yayi mata ga fuskarsa da tayi fiyau kamar mara lapiya,a bazata taji saukar muryarsa ,”baki iya gaisuwa ba”, dan karamin bakinta ta turo kadan kafun ta furta “ina wuni”, banza yyi da ita batare da ya amsa ba ,kara gaishe sa tayi a karo na biyu shima be amsa matan ba sai takowa da yayi har inda take dan rankwafo da fuskarsa yayi Daidai kan tata, “kalleni “ ya furta mata , amaimakon ta kallesan sai ta kara dukar da kan nata kasa,a fusge ya furta”karki kuskura na kara maimaita wa” dan dago da kan nata tayi kamar me shirin turo masa baki, tana daga da fuskarta ya bata hot kiss da ya dauke sa kusan mintuna biyu yanayi,ita kam tahee kunya ce ta kamata ta rasa yanda zatayi, zare bakinsa yayi daga nata yana binta da kallo”from today , wannan shine gaisuwar da zaki dunga yi mun”, kin amsa masa tayi sai ma sunkuyar da kanta da ta sake yi,” zan kai wa mahma kaya “ ta furta Adan tsorace tana niyar juyawa, “And then “, ya furta nan ma shiru tayi masa ta kasa bashi amsa , “who am I to you “ ya furta yana kallanta,”yaya king “ ya furta batare da damuwar kallan da yake binta dashi ba sai ma dan daure fuskarta da tayi ,”apart from that “, ya kuma furtawa,da sauri ta juya zata bar wajan ya janyota jikinsa , “idan ina magana kina tafiya ranki zai baci , answer my question , who am I to you “, kukan da taji yana kokarin zuwammata ta rike tare da furta “yaya king “ shiru yayi yana kallan yanda ta dan daure fuskarta,”say something “, yanxun kam kukan da take kokarin rikewa ne ya subuce mata, hannayenta biyu hade masa waje d’aya batare da ta kallesaba ta furta “ na rokeka ka fita daga dakin nan , banasan ganin ka,kace ka tsaneni dady to Nima ka fitar mun daga dakin”, murmushine yaso subuce masa kalmar dady data ambata,matsowa kadan yayi kadan kafun ya furta “ni Yaushe nace miki na tsaneki “ dan turo bakin ta tayi sam ta manta a gaban wa take “rannan “, eyes dinsa ya dan zaro “ni karki mun sharri Yaushe na ce miki haka , gashi har kin fara bata kwalliyar taki” ya karashe yana daga mata ido daya . D’auke kanta tayi daga kansa tunanin yanda zata hada kayanta yake ganin hour dayan ta kusa cika ,”am going “ bata san lokacin data furta “Tom “ ba cikin sauri , da mamaki yake kallanta ganin ta bashi amsa lokaci d’aya, ganin kallan da yake binta da shine yasata saurin matsawa nesa dashi kafin ta furta “daman fuskata zan wake “tana kai karshen maganar nata tayi sauri ta shige ban daki daga inda yake yana jin karar lock din da ta saka ,dariya abun yaso bashi ma , bece komai ba ya nufi wajan wardrobe dinta, wasu kaya ya ware mata gefe guda kafin ya dannan wani designer frame nake dakin, take a wajan wardrobe din ta bude wata kofa ta bayyana awajan,yana shiga kofar ta rufe kansa kamar wata kofa bata taba wanzuwa Ba awajan. Ta dade a toilet din jin shiru yasa ta bude kofar a hankali tana Leko da kanta ,ganin babu kowa a dakin yasata sakin ajiyar zuciya,sai yanxu take mamakin yanda akai yazo cikin dakin ganin babu me bata amsa yasa ta janyo babba f trolley zata bude wardrobe din ta kenan taga wasu kaya an futo mata dasu ,dukda tasan ba Itace ta futo dasu ba, bata kawo tunanin komai ba ta saka kayan a cikin akwatin tare da daukan underwear’s dinta ta saka a ciki, cikin sauri sauri take komai ganin awa d’ayan da aka bata ya wuce , tana fitowa ta tarar da ba koma a falon sai asabe, asabe na ganin ta , ta nufota sai faman washe mata baki take tunda ta samu labarin ta zama mayar king yanxu, kadan ta dauka tare da kai wa zaki dake cikin mota suka bar wajan yayi saura sai tahee kawai, waje ta samu ta zauna a falo,yau kwata kwata bata ga auntyn taba gashi tana kunyar su ummey, gabaki d’aya yau ita kadai ta yini sai zoya da tazo mata itama ma bata dade ba ta tafi saboda islamiyya,hatta abincin da zataci daga part din mahma aka kawo mata wacce ta ka famata sharadin ko wajan part din karta kuma zuwa , kwata kwata batasan abunda yake faruwa ba acikin gidan. ➰➰➰➰➰➰➰➰➰➰ A part din dada Kuwa su ummey ne zaune cikin falon mahma, inda aka fito da wasu designers din akwatuna masu shegen kyau set uku,suna tattauna yanda za’ai wa tahee Jeren kayanta, bude kofar toilet din da akwai ne yasa mahma dakatar da maganar ta, a matukar firgice na zaro idanuwana , sanye take cikin doguwar abaya black colour , kwantaccen gashin kanta ya kwanta rup agefen fuskanta , ba kowa bace face matar da ta temakawa taheer ,har ta kaishi asibiti, murmushi ta zakarwa mahma ,cikin yaran larabci ta furta “dadi na dake mahma akwai saurin lissafi , Kalli su yaya ko wannen su ya tsaya kallanki “ ta karasa zancan nata tana zauna wa kan kujera , gabaki dayan su dariya suka saki ammey ce ta bata amsa “ shi yasa naga ai kina zuwa ko hutawa bakiyi ba kika dora ke da mahma bansan wann yafi zumudi ba”,dan girgiza kai matar tayi” Wlh yaya gashi ko amaryar tamu ban gani ba , yanxu so nake komai ya daidai ta “, tana kai karshen maganarta wayarta ta soma ringing , daga jikin wayar taga don ya bayyana , dan murmushi ta saki tare da daukar wayar tana barin wajan, su ummeey ma cigaba da tattauna wa sukayi ci gaba dayi. 9:30daidai mahma da kanta tazo ta dauki tahee ta kai ta saban part din da bashi da tazara sosai ,sai alokacin ta hadu da kanwar ummey da suke cewa small mom,sosai hajiya fatima ta yaba da hankalin tahee , tunda ta koma part din yarta take santin halin ta , duk da tace bazata zauna a gidan ba ,wani gida da ban zata zauna ,dagyar aka samu aka shawo kan small mom din dan har sai da dada ta saka baki a ciki. Wani babban daki dake upstairs aka nufa da tahee, suna shiga amzy ta miko mata wasu sababbin kaya marasa nauyi ta saka , karban kayan kuwa tayi ta saka , bakomai a cikin dakin sai babban gado da wasu abubuwan gyaran jiki da aka harhada, ba bata lokaci amzy da yaranta guda uku suka fara aikinsu cikin kware wa, wani ruwa ne babba aka sa tahee tashiga me shegen kamshi, da ya kare za a dakko wani , gabaki d’aya part din ya daure da kamshi me shegen daki duk da kasancewar ba yanxu su ihsan zasu dawo part din ba sai nan da kwana uku,sosai su amzy suka gyara fatar tahee da ita kanta sai dataji canji a cikinta, basu suka kyaletaba sai wajan karfe 2 na dare bayan sun kunna wani burner me shegen kamshi da dadin gaske . Ita dai tahee binsu kawai take da kallo ganin komai da suke cikin kwarewa, sosai gyaran ya burgeta amma kuma tana tausayinsu kasancewar tasan wanda ake yiwan ma ba santa yake ba ,tuno da hakan yasa ta fashewa da kuka sai da ta sha kukan ta dan kanta kafun bacci ya dauke ta. Washe gari ma bayan sallahr asuba su amzy basu zauna ba , wani gyara na musamman aka somayiwa tahee da ya banbanta da na jiya, tun abun na burgeta har ya fara bata takaici musamman towel din dake sata sawa shi kadai, har yamma kuma babu Wanda ta gani cikin family din sai abinci da ake aiko musu dashi, karfe 8 na dare mahma da small mom suka shigo dakin, ko wannansu sai yaga kyan da tayi yake yi ,gyaran da akayi a kwana daya mutum sai ya dauka wata biyu akai ana yi musamman duk yanda ka matso kusa da ita zakaji kamshi na ta shi ajikinta, hatta bakinta wani daddadan kamshin mint ne ke tashi, basu dade da zuwa ba suka tafi, bayan mahma ta bada umarnin kar abar kowa ya shigo dakin har sai lokacin da aka gama gyaran jikin, a tunaninta ammey ma zata zo sai taga sabanin hakan, harta kwanta bacci bata sanya ammeyn a idanuwanta ba . Arana ta biyu ma haka su amzy suka canza saban style din gyaran jikin,gawasu abubuwa da ake bata tana sha , hatta abinci ta dena ci sai fruit din da take sha kullum , da kayan da ake bata , sai wata kaza da kullum sai ta cita ,tana ci tana kuka haka suke sata cinye wa dole , yanxu ma su mahma da small mom ne kadai suka shigo part din, banda tubarkalla Masha Allah babu abunda bakinsu yake furtawa, suma yanxu ko munti goma basu yi ba sukabar part din, dan takaici har kuka tahee tayi , a haka bacci ya dauke ta. Arana ta ukun ma hakance ta faru kwata kwata basa bari ko kofar dakin ta nufa balanta ma tace zata dauki wani abun , ko me take so shi ake mata, cikin dan kankanin lokaci jikinta kuwa ya dumurmure sosai har wani santsi yake yi, suna cikin aikinsu suka fara jin hayaniya na tun karosu, kulle dakin da tahee take amzy tayi tare da nufarsu, ko wanne daki tasa aka bashi inda za a dunga musu gyaran jikin suma , duk yanda suka so ganin amarya abun yaci tura an hanasu hatta sumayya daukin ganin yanda tahee zata dawo take kawai a ranta. Duk yanda tahee taso abarsu su shiga an hanata ganin kowa , yau kwanan ta uku raban ta dashi ,sosai take kuka cikin dare ganin kullum soyayyar sa kara shiga cikin zuciyarta take . **** Akwana a tashi ba wuya wajan Allah SWT yau ta kama kwana biyar kenan ana yiwa tahee gyaran jiki , bayan kyaran jikin da take mata kuwa kunya ta cire sosai take koyawa tahee dabarun aure da yanda zata shawo kan mijinta, cikin kwana kinnan ta koya mata abubuwa da dama hatta tafiya sai da ta nunawa tahee kala kala , wasu abun ma kunya suke bata da amzy ta fada zata sunkuyar da kanta kasa,har yau kuma bata kara saka kowa na cikin gidan a ido ba sai yar hirarsu da take ji lokaci zuwa lokaci, suma sosai aka gyara su sai faman santin kyan da sukai sukeyi,ita de amzy sai faman dariya take musu musamman tunawa da kankat din da tayi, idan suka ganta sukuma wani irin santi zasuyi. Duk da amrah da basma sunsan abunda ke faruwa ,babu Wanda ya tako yazo inda ake gyaran, amrah na kwance tunda mutumin da yazo mata yaji mata rauni take jinya dan bakaramun rauni yaji mata ba ,kuma ta hana kowa sanin halin da take ciki sai Aunty da taji dadin abinda ya samu amrah. Kamar daga sama sai ga basma itama ta shigo cikin kananan kayanta da karamun trolley dinta,hakan da tayi sosai ya bawa kowa mamaki musamman yanda tasaka itama a gyara mata jikin nata. Washe gari kunshi akayiwa gabaki d’aya mutanan gidan har dada ba a bari a baya ba, kowa da kowa part din ya shigo, hatta su aunty duk kowa yazo banda basma da tayi karyar bata san kunshi .dadace kai batazo part din ba aka je har nata part din akai mata, duk da hakan kuma an hana kowa ganin amarya, a ranar akayi mata kunshi ja da baki da ya kara fito da kyaun siraran yan yatsunta, kunshi sai ya fito tar dashi kamar daurashi akai ,da yamma kuma akai mata gyaran kai,suma ata ban garan mutanan gidan kowa anmishi gyaran kan, ana kammala wa kuwa aka umarce kowa da ya koma part dinsa, saida aka tabbatar da bakowa ne sannan mahma da small mom suka nufi dakin da tahee take,suna shiga ko wannansu ya tsaya ,tsabar mamaki ko kwakkwaran motsi sun kasa sai bin tahee suke da kallo da amzy tasa tashirya cikin wani hadaddan lace kamar yaune Auran, iya kyau ta tahee tayi kyau,ko makiyi ya ganta sai ya yaba kyan da tayi, kwata kwata kasa magana sukai sai hannunta da mahma ta kama soka fito falo inda su ummey suke, suma sosai yaka da irin kyaun da tahee,kunyace ta kama tahee ko kwakkwaran motsi ta kasa balantana dagowa ta kallesu sai hannunta da take faman wasa dashi. Kafun goma gabaki dayan su kowa ya nufi part dinsa yayi saura daga mahma sai tahee , Zaunar da ita mahma tayi ,sosai tayi mata nasiha kamar yar cikinta ba abunda tahee take sai kuka ,karfe 12 tasa a kazo dau karsu kai tsaye part dinta aka nufa da ita batare da ta bari kowa ya gansu duk da kasancewar ba taro za’ayi ba kamar yanda abeey ya sake jaddada mata babu taran da za’ayi gobe za’a kai yarinya dakinta, duk da mahma tanbayeshi amma yace mata haka mijinta yace , jin hakan yasata kira wayar king amma kwata kwata ba yashiga ,kusan kwanaki biyar kenan ynxu bata sa shi a cikin idanuwanta ba , bama itama hatta mutanan gidan babu Wanda ya gansa, suna shiga part din dada wani daki ta nuna wa tahee akan taje tayi wanka ta Hutu , kamar tasan abunda take bukata kenan, duk da haduwar da dakin yayi hakan be sa ta tsaya kallan dakin ba sai ma toilet da ta nufa ,ta dade sosai a ciki kafun ta fito jikinta da white rub,kome ta taba kamshi yake tashi musamman dakin da ya cika da wani irin sanyi kamshi me cika zuciyar masoya, kwata kwata bata kallanta gabanta bayan. Tafi to daga toilet din, burin ta kawai ta kwanta ,Daidai tazo saitin gadon sai abu ya dan bigi takalmin kafar ta ,tayi baya zata fadi, hannu daya yasa ya janyota jikinsa suna fadawa saman gado ita a kansa…… 💖💖💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖💖💖 Mss LEE 💖💖 💖💖GIDAN AUNTY 💖💖 ( a heart touching love story) Story & written By Mss Lee 💖 💖💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖💖 Wannan page din nakune MAMAN SUDAIS,UMMUN SAEED, ISARATU917 . PAID BOOK MAI BUKATAR COMPLETE DIN GIDAN AUNTY YA TUNTUBENI TA WANNAN NUMBER 07041879581. BOOK 1📕 Page 51_52💖 Zaro idanuwanta tayi waje tana kallansa da mugun mamaki akan fuskarta, kokarin tashi take akansa amma ya ki bata damar Hakan bata Ankara ba sai ji tayi ya mirginata ta koma kasan sa , motsi ta somayi da bakinta ,kokarin magana take amma ta kasa sai kallan kofa da take , bin jikinta yake da kallo ganin wari irin kyau da ta kara yi masa , fuskarta ta ciro sai glowing yake ,tunda yake a rayuwarsa zai iya rantsewa bai taba tsayawa ya rike ko hannun mace ba , shi kansa mamakin irin kallan da yake mata yake ,kamar wani magnet haka ya kura wa fuskarta kallo, babu abunda ya fu birgeshi kamar yanda lips dinta suke faman rawa, ga kwayar idanuwanta da suka kara haske da sheki, hannunta d’aya ta daga zata turesa yayi saurin rike hannun sai yanxu idanunsa suka kai kan zanan dake hannunta, kokarin kwace hannun take ya kara rikewa,bin hannun yake da kallo kamar yau yata ba ganin hannun nata , a hankali ya dago da kallan su zuwa gare ta “ wanene yayi miki wannan abun”,bata gane me yake nufi ba shiyasa ta dan kallesa , kunshin dake hannunta ya nuna mata da ido, dan kawar da Kai tayi kafun ta furta “watace”, bece mata komai ba sai hannun da ya kara bi da kallo, bude tafin hannunta yayi guda d’aya tare da yi wa hannun kiss, saurin fusge hannunta tayi jin bakon lamari na ziyartarta tun daga kan dan yatsun kafarta,hannun kallanta yayi ganin ta hade ran ta ,tana bude hannun, kara rike hannnun yayi tare da zuba mata lumsassun idanuwansa,”Are you still angry” ya furta mata,bata bashi amsava sai ma cewa da tayi “ ni ka saukar mun ajiki”,bata kammala zancan nata ba ya kara kusan tota sosai, hakan da yayi kuwa shi yabawa damar bathrub dinta kara budewa,breast dinta daya gama shan gyara sosai suka kara girma,kallan ta yayi kafun ya mayar da kallansa kan breast din a karo na biyu, hannu daya yasaka ya fincike bathrub din, baki ta bude da niyar yin ihun ya hade bakinsu waje daya, wani irin kiss yake mata me wuyar fassara,sumbatarta kawai yake idanuwansa a kulle, hannunsa daya yakai kan breast din, jin laushin su kadai yakara zautar dashi, duka hannayensa biyu yasaka ya damki breast din nata,matsasu kawai yake da hannayensa biyu, fisge bakinta da ya fara yayi tayi tana kuka kasa kasa jin yanda bakinta da breast dinta ke zafi, saukar bakinshi akan breast dinta ne yasata sakin wani ajiyar zuciya me karfi, rintse idanuwanta da suka fara canza launi tayi, sakonsa sosai yake ziyartarta, kasa kasa ya somayi da hannunsa har ya dora akan mararta, zaro ido waje tahee tayi wani irin tsoro da fargaba na ziyartarta,ganin yana kokarin cire mata pant din jikinta ne yasata sakin kuka , a mugun rude ta fara basa hakuri” dan Allah yaya king kayi hakuri bazan sake ba,dan Allah”, be kulataba sai hannunsa da yake kokarin do rawa a kasan Marar ta ,cikin sauri ta riko hannunsa , tana langwabar da Kai , cikin muryar da bata san ta iya ba ta soma bashi hakuri”Dan Allah dady”, kallanta yayi jin dadyn data kara ambata,muryarsa a shake ya furta “meyasa” wani kukan takaicine ya kamata , tsoran ta ma kada wani yashigo dakin ya samesu a haka” ni banaso “ ta karasa da niyar sakin kuka, hannunsa ya dora abaki alamun ta yi mishi shiru, shirun kuwa tayi masa tana fiki fiki da idanuwanta,”ni inaso” ya bata amsa ,waro idanuwanta tahee tayi jin amsarsa,”Dan Allah kayi hakuri , mahma zata iya shigowa ko dada dan Allah kabar dakin nan”, jinjina mata kai yayi,”sune bakyaso su ganki, toh bari na baki ajiyar baby inyaso sai su gani da kyau”, fashewa kawai tayi da kuka ganin ta rasa abun cewa ma,dariyar da take kokarin fitowa ya hadiye tare da daure fuskarsa , girgiza masa kai tashiga yi kamar wata yarinya ,”dan Allah “ tsoro duk ya bayyana a fuskarta sai faman hada gumi take “ ba fushi kike da dadyn ba, shiyasa zan miki abunda zaki dena fushin”, girgiza Kai tashiga yi tunkan ya karasa zancansa “na dena fushi da kai Allah”, girgiza mata kai yayi “nan yardaba “ bata bari ya kai karshen zan can saba tace “Allah da gaske nake”, karamun dan ya tsansa ya mika mata friends, burun ta kawai ya bar dakin shiyasa tayi sauri sarke karamun dan yatsan, gajeran murmushi ya saki” mun zama friends tunda kin amince and duk abunda friend yake ayi dole ayi kinyarda “ nan cikin sauri ta gyada masa kai”na yadda “, kallanta kawai yayi batare da cewa komai ba “ba tafiya zakayi ba” tayi sauri fada tana dauka bathrub dinta, girgiza mata kai yayi “ah ah anan zan kwana” kamar wacce zata saki kuka ta furta kayi hakuri dan Allah mahma zata iya shigowa,”ok bari na kira ta sai na fada mata ba sai tazo ba kina wajena”ya karasa yana daukar wayar tasa, da wani irin mugun sauri takamo gabansa batasan lokacin da ta fincike wayar hannunsa ba, zaro idanuwansa yayi da mamaki kafun ya hade ransa lokaci d’aya ,tana ganin yanda ya hade ransa take a wajan wasu hawaye suka fara sakkomata, cikin yar rawar da hannunta ya soma ta miko masa wayar”kayi hakuri dan Allah”, be amsa mata ba sai zama da ya gyara, wani saban kukan ta fashe masa dashi” dan Allah kayi hakuri dady”, be ce mata komai sai hannunsa d’aya daya mika mata atunaninta wayar zai karba sai taga ya rike hannunta tare da kaishi saitin bakinsa ya sumbata” I like it so much “ ya fada tare da kara kai bakinsa kan hannunta da yasha maroon din kunshi ya sunbata.motsin da ta Jine yasata saurin hade hannayenta biyu “dan Allah dady ?gashinan mahma zata shigo ,please badan niba “da mamaki ya kalleta,lalle bata san wanene shi ba sunan kawai take ji, kara gyara zama sa yayi, ita kuma gabaki d’aya ta rude mikewa yayi tare da zuwa inda take Daidai lokacin da ake taba kofar dakin, da wani irin sauri ta janyosa bayan kofar tare da dora hannunta guda daya kan kirjinsa,he can’t believe it wai shi ne abayan kofa yau , bece mata komai ba sai hannunsa da ya saka cikin aljihu yana kallan ikon Allah. Basma ce ta bude kofar tana kallan tahee dake jikin kofar itama ,kokarin shigo dakin take amma tahee taki bata wannan damar, sakin baki tayi tana kallan yanda ta koma ko wata babbar albarka ,yar dariya basma ta saki duk da azuciyarta ba haka bane,”Lalle baki da hankali,da kika tsaya akai miki wannan abun da ko kyau be miki ba”, kallan tara saura kwata tahee tayi mata sam ta manta king na bayan kofa” ko ina da ja da kyan da nayi, ta karasa zancanta tana dan juyawa, karki damu wanda akayiwa dan shi ya yaba ya biya tukwuici kinga nana bukatar yabawar wasu “ta karasa zancan tana turo kofar ta tare da barin basma da sunan tsaye,sai alokacin idanuwanta suka sauka kansa , gira d’aya y dage mata da sauri kuwa ta juya masa baya wani kunya na kamata Allah yasa be jita ba, murmushi ya kasaki kadan da ko a la’b ‘bansa be fito wa ,cikin kunnnata ya rada “ na yaba amma ban bada tukuicin ba ai “ ya kara zancanta tare da daukar wani Siririn box me shegen walwali, ita dai har yanxu bata san meke faruwa ba dan taki yarda takallesa, wani dan siririn chain ya ciro a ciki meshegen walwali da daukar ido yasa mata a tsintsiyar hannunta , jikin chain din wani dan karamin adone da rubutu a cikinsa. "Ga tukwuicina”, ya karasa zan cansa da yi mata peck a kumatu,kasa motsi tayi saida taji karar rufe kofa alamar ya futa, wani irin ajiyar zuciya ta sauke fatanta Allah yasa karya hadu da kowa a hanya , chain din hannunta ta kura wa ido ganin yanda take ta faman walwali a hannunta har yanxu , sumbatar hannun tayi tana sakin murmushi ita kadai ,wani irin son king ne ke kara shiga zuciya da bargon ta , a wani ban garan kuma ta na tausayin kanta ne sanin cewa baya santa, kwallar da ta tarar mata ta goge , shaf shaf ta shirya jikinta cikin kayan bacci tare da kwantawa,bata dade ba bacci yau keta me cike da mafarkai daban daban. ✨✨✨✨✨ WASHE GARI Tunda ta tashi sallar asuba da wani irin tsoro da firgici ta tashi, ita kadai sai faman kuka take, jikinta har ya fara daukar zafin zazzzabi, tana idar da sallanta amzy ta shigo dakin cikin sallama bayan ta kuma mahma ce ko wannansu d’auke da tray a hannunsa, cikin sanyin jiki da kunyar da ya kamata ta gaishesu,gabaki d’aya amsa mata sukai cikin farin ciki ,trays din hannunsu suka ajje mata ,mahma na mikewa ta kalli amzy” amzy ga yata nan ki tabbatar kinyi abunda ya dace”, Insha Allahu cewar amzy tana sakin murmushi, fita mahma tayi ta barsu itama amzy abincin da aka kawo wa tahee tasata ci da kyar shima din tsakura tayi, bayan ta kammala cin abincin da kusan mintuna talatin amzy ta miko mata babban tray din gabanta, kaza ce a ciki jikinta duk Kantu sai wasu kayan fruit da wani abu da bansan ko menene ba ta sata sa ciki, kamar zatayi kuka kuwa hka ta zauna tana ci jikin ta duk ba dadi yau , da kyar ta cinyesu, tana kammala ci amzy ta sata yin wani wanka bayan Wanda tayi da turaruka da ya fi na baya kamshi,tana fitowa amzy ta shafe mata jikinta da wani abu sai glowing fatar jikinta keyi, bayan sun kammala ne amzy ta kara zaunar da ita , darasin yanda ake kula da miji ta fara mata da yadda zata kankaro wa kanta mutunci, sosai take mata darasi akan zaman aure da hakuri da juna, ta karasa zancanta dacewa “da yawa matan hausawa sun kasa ganewa , zama da miji bawai kawai auratayya da za kudunga yi bane aure, akwai kyauta tawa, akwia biyayya, akwia tsafta, uwa uba iri girki, kafin kiyi masa magana ki tabbata me dadi ce zata fito daga bakinki, idan kinga ransa yana abace kisaka kissarki ta mace ki shawo hankalinsa tare da kwantar masa da hankali, idan wani abun farin ciki ya samesa ki nuna masa kin fisa farinciki, idan na bakin ciki ne ma ki nuna masa rashin jin dadi, ki zama me kula da tsabtar ki da tsaftar mijinki, dan kina da yar aiki ba hakan ne ze baki dama ba kice bari ta wanke wa me gidan ki abu ba,komai dukiya da nasabarki ki kyautatawa mijinki, dan boxer din nan idan nacire dauka ki wanke masa cikin farin ciki( da yawa mutane abunda basa ganewa wanke wa miji boxer da singlet ba kazanta bace kamar yadda wasu ke dauka,wallahi ba karamun so , mutunci da kima yake karawa mace wayan mujinta ba, shiyasa hausawa ke cewa yare asirce miji suke yi kuma da yawa daga ciki ba haka bane tsantsan kulawa da mijine kawai,masu Shan maganin mata kuma ku kiyayi kanku wallahi ba kowana magani ne ake sha ba,idan kika yawaita shan maganin mata Wallahi duk ranar da baki shaba mijinki sai ya jiki wani irin, idan kinasan gyara kanki ina kika bar fruit masu daraja, ina kika bar dabino,kwakwa, da madara,abubuwa da ban daban , idan matsincin ne ki yawaita yin Tsarki da ruwan dumi wallahi ke da kanki zaki ji canji a jikinki, ina kukabar kanunfari!? Shima akwia abubuwa da mana da zakiyi wajan gyara jikin ki da abubuwa nagartattu basai kinje kin bata kanki ba ,please mata mu kula please yar kisisinar nan da rankwada da shagwaba a dungayi , dan honey 😂, darling dinnan please , karki yarda waidan kina da ‘ya’ya kice kin dena , da kun shiga daki maida kanki kamar yar baby😂, kar inji ana baban sani ko baban haruna, yan gidan aunty daku nake ,MAMAN SUDAIS kija musu kunne)sosai amzy ta cire kunya ta koyar da ita abubuwa da yawa, tsabar kunya kasa dago dakanta tahee tayi , ita kadai sai kuka take, amzy bata kulataba sai data bata kalubalan rayuwa, aure dan hakuri ne ,zomu zauna zo mu saba ba kullum ne ake kasancewa cikin farinciki ba. Ba ita ta kyaletaba sai wajan 2, bayan ta bata damar tayi sallah sannan aka kara sa mata wasu turarukan da zatayi Wanka dasu,TAHEE har yanxu bata dena kukan ba,tayi sallah tare da yin Wanka , wani Saban kukane ya kara zuwar mata , oummanta da taheer dinta duk sai da tayi musu addua sosai,uku daidai amzy tashigo dakin dauke da wata trolley me dan girma, wani brown din atanface me shegen kyau ba wani tarkacene a ciki ba simple dinki akayi amma sosai fadin yanda ya hadu bata lokaci ne, stone din jikin kayan sai faman walwali suke takalmi da da pose duk saida ta fito mata dashi da mayafinta, shiryawa tahee tayi cikin kayan bakaramun kyau sukai mata a jiki ba kamar a jikinta aka dinka su,sai da ta bari akai kiran sallar la’asar sannan tayi mata simple makeup mata hanayina, “fatabarakallahu ahsanin khalikin, Allah yayi halitta awajan nan ,sai da na furta Masha Allah, Masha Allah , Masha Allah, Iya kyau da haduwa ta hadu, tayi kyaun da yafi Akirata da zinariya , daya tamkar dubu ko makiyi ya ganta sai ya kara kallanta balantana masoyinta,abun hannun da king yasa mata sai faman kyalkyali yake , stones din jikin kayan ma sai ya kara kawata kwalliyarta, daura mata dan kwalin amzy tayi amma ta boye mata gashin kanta sai wanda suka kwanta a gangan goshinta, farar kyakkyawar fuskarta sosai ya fito cikin daurin bakinta sai faman sheki yake, takalmin da amzy ta dakko mata me dan tsini ne kadan,hatta da bracelets din daka saka mata masu walwaline,sai pose din data mika mata tana yafa mata mayafi, ita kanta amzy tana shiryata tana sakin murmushi me kayatarwa tabbas kyan da ake cewa akwai kyau tabbas akwai kyaun ,waje ta samu ta zaunar da ita akan gadon ka fun ta fita daga dakin, Daidai inda ta zauna din taji dan tudu a wajan , tana dubawa wayarsa ta jiya ta gani a wajan da Sauri ta saka ta cikin pose din gudun kar wani ya shigo dakin,amzy ce ta dawo dauke da kayan daukar hoto sosai ta ke dauka tahee ,zaman da tayi akan gadon sai ya kara kayata wajan kasantuwar bedsheet din gadon me design din brown ne , suna cikin saukar hoton mahma ta shigo ita da small mom, gabaki d’aya sakin baki sukai suna kallan ikon Allah,In banda tubarkalla Masha Allah babu abunda bakinsu ke furtawa, gabaki dayan su sun kasa kwakkwaran motsi, mahma ce tayi karfin furta “tubarkalla Masha Allah “ a fili, “daughter wannan kyan naki ya wuce akira ki da kyakkyawa sai dai shugaban kyawawa , har na rasa tsakanin keda mijin naki wanene ya fi kyau,”a maimakon su fito da amarya kamar yanda akace sai suka tsaya koda ta , gabaki dayan su photograper suka zama sai faman daukan ta hoto suke , saura kadan ta fashe da kuka, tun snap din da amzy tayi Mata tasaka a status dinta , cikin mintuna da basu fi goma ba sama da mutane dari sai da sukai mata magana harda Wanda basa kulata , HIS QUEEN shine kadai abunda ta rubuta a jiki amma zonaga comment, zata kara posting mahma ta hana ta sabida tasan in king yagani baruwanshi zaiyi maganintane, da sauri kuwa ta cire tana sakin dariya ko ba komai kusan mutane ashirin sun yi booking dinta acikin mintuna da be wuce goma ba, tabbas zuwan ta gidan alkairi ne,mikar da amarya suka tare da gyara mata mayafin kanta, abun hannunta ne ya sauka a kan hannun tahee , zaro idanuwa waje tayi tana sakin dariya “ Diamond heart love “, ta furta kasan zuciyarta, iya hasashenta ta kasa hasasho a dadin kudin sa Sabida yanda yake walwali zai tabbatar maka da asalin zallan diamond akayi shi. Har za’a sanar da fitowar amarya mahma ta hana acewarta angone zai fara ganin kwalliyar, gabaki d’aya fita sukai akabar small mom gudun kar Wanda ya shigo dakin, mahma kuwa kai tsaye part din king ta nufa, bin falon na shigayi da kallo dan gabaki d’aya an canza komai na cikin falon komai nacikin falon sabone, kallan sha’aban dake cikin shigar manyan kaya fara kaldasu tayi,”yana ina “ ta furta , fusgar da iskar bakinsa yayi” mahma tun dazu nake kiransa amma yaki jina yayi wuce warsa sama wai bacci zaiyi”, mahma batace komai ba sai wayar ta da ta dauka cikin dan baci bacin rai take kokarin dialing din number din sa, wani irin sahirtaccen kamshin turaransane ya daki hancinta, da sauri ta daga idanuwanta tana binsa da kallo, gabaki dayansu daga ita har sha’aban sakin baki sukai suna binsa da kallon kurulla, yayi bala’in kyaun da baki bazai iya kiyas ta kyan da yayi ba, sanye yake cikin wasu hadaddan ubansun shadda, light brown meshegen kyau da tsada kallo daya zaka mata kasan ba karamun kudi aka kashe mata ba, dinkin zamani ne ajikin rigar hatta babbar rigar dake jikinsa, kafarsa sanye take cikin wani half qucci dark brown kafarsa fara suwal sosai ta bayyana a cikin takalmin, fararan hannunsa ma sanye yake cikin diamond wuce me shegen tsada da zoben sa , dayan hannun kuma wasu siraran abun hannun diamond a jiki, dayan kusan kullum yana hannunsa Wanda ya fi kyallin cikine kawai yafi daukar idona, fuskarshi babu ko digon murmushi kawai amma ba kadan ta fito da zallan kyansa na larabawa ba, pink lips dinsa sosai ya turo ga gashinn idanuwansa da suka kara fito da fararan idanuwansa,hatta gashin kansa gyaran da ya sha nadaban ne sabida yanda hular kansa ta fito da adon gashinsa, a hankali yake taka stairs din sai ji yayi ana snapping dinsa , dago idan da zaiyi ba sha’aban kadai ba hatta mahma snapping dinsa take, tunda aka haifeshi zata iya rantsewa bata taba ganin kyawun da ta hango awajan saba kamar yau, dukda kasancewar sa kyakkyawa ne shi na karshen karshen, dan hararan sha’aban yayi yana kara tsuke fuskarsa kafun ya kalli mahma dake faman sakin murmushi”son na kasa ganewa da kai da ita wanene yafi wani haduwa,kamar hadin baki ,Anya bazan fara kishi ba “ ta karasa cikin Zolaya, dan kauna kansa yayi batare da yace komai ba, wani shegiyar dariyar iskanci sha’aban ya saka da har saida mahma da kai masa duka, hanyar fita king ya nufa kallansa mahma tayi ina zuwa,batare da ya kalleta ba ya furta “ office”, da sauri ta kallesa “office, wasa kake ko , dan wallahi yau duk wani miskilancin ka bazan dauka ba , yanxu maza ka wuce kai muke jira ka fito da amarya, nan da mintuna biyar nakeso a fito da ita inva haka ba ran kowa sai ya baci”ta karasa da nuna sha’aban “Kai ma wuce ka tafi wajan taron “ da sauri kuwa ya wuce yana dariyar dramarta da king, ganin tana kokarin juyawa yasashi riko hannunta, harara ta sakar masa zata wuce ya rungumeta “ am sorry, I will do everything to make you happy” wani murmushi ne ya subuce mata raba jikin ta tayi da nasa tana shafa gefan fuskarsa “ please kazo in not less than 5 minutes dan Allah “ lumshe mata ido yayi alamar toh, ta gane me yake nufi shiyasa ta juya ta far part din, amaimakon ya biyo bayansu sai ya shiga wani dakin da tahee ta taba zama dashima komai na ciki sai da aka canza masa, dan wani bottom ya danna da komai ganin ka bazaka san dashi ba, yana dannawa kuma wardrobe din wajan ta rabe biyu yana shiga ya kulle taci , ta wajan kuma wai ta dawo yanda take kamar babu wani makamancin abu a wajan, tafiya yayi me dan tazara kadan kafun ya iso wasu kofofi a wajn, kofar biyun karshe ya nufa, yana bude kofar abun mamaki sai gashi a part din dada, a bun frame din dake wajan ya taba take awajan kofar ta kulle ya dawo ainahin jikin bangon,yana dan jin hayaniyar mutanan gidan kadan kadan, dan tafiya yayi kadan batare da kowa ya gansa ba , kofar dakin da take ya kalla kusan second biyu kafun ya murda ya shiga dakin da sallama, sallamar sa daddadan kamshin sane ya ziyarceta da sauri ta daga manyan idanuwanta, take a wajan ya sauka cikin nasa idanuwan dake binta da wani irin kallon dashi kadai yasan ma’anarsu, yanda ya jingida da jikin bangon dakin ta kalla , itama a wannan karan ta kasa dauke kallanta daga garesa, cikin takun kasaita ya nufota da tun lokacin da ta kallesa bugawa zuciyarta ya tsananta, gefen inda take ya zauna tare da dora kanta akan kafadunsa” cikin rada rada ya furta fatabarakallahu ahsanin khalikin”,daga nan be kara cewa komai ba sai sauraran zuciyoyin su da suke yi na tsawan mintuna biyar itama tana lafe kwance kan kafadunsa, knocking kofar akai saudaya kafun suji saukar muryar Mahma” zaku iya fitowa yanxu” tana kammala zancanta , suka farajin takun takalmin ta alamar ta bar wajan, kusan mintuna biyu kafun ya mike tare da ita a cikinsa yana nufar kofar fita da ita da sauri ta kwace jikinta tana zaro masa ido , idanun cike da kalla harda dan turo karamin bakinta,kallan bakin yayi kafin ya kalleta “bakin nan da kike yawan turo Munsu xanyi maganinki and in baki dena ba yanxu ba gobe ba zan karbesu kamar yanda kika so” ai damugun sauri ta mayar da lips dinta tana sunkuyar da kanta, be kara bata damar magana ba ya janyota ajikinsa tare da tura dakin, sai da ya kara janyo gelenta kadan ya tabbatar ya rufe mata ciki kafun su karaso kofar da kowa ke zaune anzuba mata ido ana jiran fitowarsu, gefensu wasu matane guda hudu ko wanne da damin fulawa a hannunsa,suna jin alamun taba kofa aka kashe gabaki daya light din wajan sai ta wajan kofa da aka bari masu walwali,ana bude kofar zo kuga yadda zuciyoyin mutane ya dunga tsunkewa take a wajan aka fara musu watsin flowers masu kyau kafun wutar wajan ta dawo gabaki d’aya , gabaki d’aya mutanan wajan zuba musu ido sukai ga wata irin dum waka dake tashi kadan dan ,kowa ya rasa abun cewa basma da ke kokarin dago kai sai gashi tayi saurin maida kanta , amrah ma bakadan ba tayi nadamar zuwa wajan har idanuwanta suka sauka akansa, yanda ya rike ta sai ka dauka wayanda suka dade da shiga gogin soyayya bakaramun matching sukai ba , me daukar hoto sai faman taukansu yake , yanda take faman kashe idone alamun hasken ya mata yawa be san lokacin daya kwantar da Kanta kan kirjinsa ba ,gabaki d’aya mutanan falon kara sakin baki sukai suna kallan ikon Allah , Kai tsaye wajan dada suka nufa , tana ganinsu ta saki kuka me taba rai”oh ni yasu , Allah nagode maka adduar tsawan ran da nadungayi yau ta cika burina ya cika naganin Auran tahanuni, tunda Allah ya dauke ran mahmuda, Allah ka basu zaman lapiya me dorewa” ta karasa zancanta tana goge hawayanta, wani dan madaidaicin box dada ta dakko tare da daurawa tahee a tafukan hannunta”wannan kyauta ce na baki sabida yanda kike sani farin ciki tahura ta karki ji komai duk lokacin da ya bata miki rai ki sanar dani zanyi maganinsa” kuka tahee ta fashe dashi me rasa zuciya ko magana ta kasa yi,a hankali sautin kukanta ke tashi kadan kadan, daga wajan dada wajan ummey aka nufa dake share hawayan farinciki yau Allah ya nuna mata bikin d’anta da take mararin gani har cikin zuciyarta , itama nasihar tayi musu kafun ta bawa tahee kyautar diamonds set tundaga kan sarka , dan kunne , zobe da abun hannu bayanshi kuma ta bata kyautar manyan Lamborghini sababbin yayi gudu biyu ,guda gabaki d’aya aka saka afalon dukda dayawa mutanan wajan ba haka suka soba , da aka zo kan ammey kuwa kuka ta fashe dashi daya taba ran kowa ga tahee da take kuka kasa kasa itama , da kyar aka samu tayi shiru itama nasiha tayi musu kafun tayi musu kyautar diamond itama da babban mall dinta dake Lagos, kowa yaji dadin yanda ta hadasu musamman yanda ta raini king amatsayin d’anta tun yana karami,gabaki d’aya iyayan falon kowa kyautar da daga gold sai kyautar motoci da company da take samu , wannan abu shi ya kara bakatawa amrah da basma rai kowa yana ganin da ace babu tahee da shine zai samu wannan kyautar. Part din abeey aka suka nufa mahma na take musu baya, yanda ya gansu ba karamun farinciki yasa shiba daya kasa boyuwa akan fuskarsa, shima sosai yayi musu nasiha ne ratsa jiki akan zaman aure, yana kammala yi musu kuma ya basu kyaututttuka masu girman gaske , d’aya daga cikin jirgin NAHYAN sukutum ya mallakawa tahee,wani saban kuka tahee tasaka masu, kama hannunta mahma tayi batare da ta bari tace komai ba ta nufa da ita dakin da su ummey suke ciki daga ummey sea small mom, anyi anyi da ammey tazo taki zuwa acewarta sune iyayanta ai, sosai suka zaunar da ita sukai mata nasiha me ratsa jijiyoyin jiki da tsoka ko wannansu saida ya rungumeta tare da lallashinta kafun abar mahma ita kadai sai amzy da aka kara kira , wani wanka suka sata ta sake yi kafun su shirya ta cikin Wani Dan ubansun lace meshegen kyau red colour , shigarta ta ynxu harta taka wanda aka yi mata dazu kyau da haduwa, wani abu amzy ta bata Tasha kafun akara kyarata, suna kama gyarata kuwa aka dakko wata lapaya red itama aka nada mata a jiki( oh oh oh ni miss lee, ni kaina saida kyawun ta ya tafi dani). A bangaran king kuwa Suna fita abeey ya rungumeshi , yana sauke a jiyar zuciya ba “addua ta daya kullum naga auranka tun bayan rasuwar Mohammad, amma Allah baiyi ba sai yanxu , na rokeka ba danni badan na isa da kai ba , ka kula da maraicin yarinyar nan , tana bukatar kulawa ta musamman ko dan irin kaddarar rayuwar da ta fuskanci kanta a ciki, idan kamun hakan ka gama yi mun komai arayuwata, Allah yayi maka albarka yanda ka faranta mun Allah ya baka masu faranta maka kaima “, lumshe idanuwansa king yayi yanajin kalaman mahaifinsa har cikin zuciyarsa,har yanxu yana tuna kalaman nan” akhie , idan Allah yasa ban ga auranka ba inaso ka zama da happiness man , ranar auranka,duk matar da aka zaba maka ka karbeta hannu biyu kasota kamar yanda kake san mu”, kara lumshe idanuwansa yayi tuno Wannan kalaman daka wajan mutumin da har yau bazai taba mantawa dashi ba, besan lokacin da bakinsa ya furta “I promise you , I will always be what you wanted me to be”, kara rungumeshi abeey yayi tsam a jikinsa kafun ya raba jikinsu, dan Allah abeey king yayi “abeey ni baka bani kyautar jirgin ba ‘ai”, dan bugunshi abeey yayi “ Wanda kake dasu ya isheka, maza tashi kabar mun daki”, wani gajeran murmushi king ya saki da ya fito da zallan kyawun da Allah yayi masa ,ban taba ganin wanda ko be yi murmushi ba yana kyau balantana ya gwada koda motsa lips dinsa ne, sallama yayi wa abeey kafun ya bar part din, koda suka hadu da sha’aban sai faman tsiya yake masa, saida ya dawo masa asalin king dinsa kafin ya kyalesa. ✨✨✨✨ Karfe 8:20 pm mahma da small mom suka dauki tahee zuwa dakinta na aure bayan nasihohin da jan hankalin da akai mata,kasa mikewa tahee tayi daga zaunan da take sai faman kukar da take Durza da ya haifar mata da zazzabi, mikar da ita small mom tayi kafun su nufi motar da aka bude musu, ba ayarda kowa ya bisuba,suna zuwa Daidai part din akasa tahee ta fitowa da kafar dama bakin ta dauke da bismilla,har suka shigo part din komai sai sun sa tayi bismilla cike da addua suka shiga part din, basu tsaya a falo ba suka hau step da ita, wani door suka bude Babban falo ne meshegen kyau a wajan, shima basu tsaya a wajan ba kai tsaye daya daga cikin bedrooms din aka kaita, ba bata lokaci su mahma suka sata yin wani saban wanka, tare da shirya ta, saida suka zo tafiya ne tasakar musu wani saban kukan , jikinta sai faman rawa yake sabida zazzabin da ya kamata,da kyar suka samu sukayi mata dabara suka gudu. Ganin saura ita kai yasa ta kara fashewa da wani saban kukan. Kallan yanda take faman kuka yayi kafun ya karaso cikin dakin bakinsa dauke da sallama , kan gadon ya karasa tare da dagowa, jin an dagata yasa tayi saurin bude idanuwanta , kallan Wanda ya dagatan tayi kafun ta kara sunkuyar da kan nata tana fashewa da wani saban kukan, rungumeta yayi a jikinsa yana sauraran yanda take kukan,bayanta ya dan shafa kafun ya furta “it’s ok don’t cry”, a tsaye ya cigaba da shafa bayanta har saida ta daina kukan ta dawo ajiyar zuciya . Zaunar da ita yayi akan gadon kafin ya fita daga dakin ba dade wa ya dawo hannunsa dauke da karamun tray,farfesun kayan cikin dake cikin plate din ya mika mata , girgiza masa kai tayi alamun bata jin yuwa, shima dan girgiza mata kan yayi ganin tana kokarin yi masa musu yasa ya hade ransa , da sauri ta fara shan farfesun,daman yunwa take ji , be kyaleta ba saida Tasha fresh milk din da ya zuba mata, tana kammalawa ya bata magunguna Tasha , tana turo bakinta tashanye magun gunan,”we’re friends ai yanxu ko”, dan kanta ta daga masa kadan har yanxu taki yarda ta kallesa”ok since we’re friends , ai zaki te makamun ko” yanxu ma kanta daga masa, murmushin iya kan labba ya saki kafun ya mike “je kiyi alwala, turo masa bakinta tayi kafun ta furta “ni nayi salla” Nima nayi ai , ya bata amsa ganin zata kara magana ya katseta “banasan musu go and do what I asked you “ Tana shiga toilet ya ciro mata hijab shima ya fita , futowarta daga toilet din ta tarar da hijab din da ya fito mata dashi, sawa tayi Daidai lokacin da yashigo dakin,sallah ya ja su raka ‘a biyu , ya dade yana addua kafun ya dora tafukan hannunsa akanta yana addua, duk tanbayar da yayi mata game da addininta sosai take bashi amsa, suna kammala adduar ta kara turo bakinta, kallanta yayi kafun ya furta “na fita ko” da sauri ta daga masa kai, be ce mata komai ba kuwa yace mata saida safe ,kafun ya bar dakin. Wani ajiyar zuciya ta sauke , wardrobe ta bude ganin babu kayanta aciki sai wata karamar trolley , tana bude wasu kayan bacci ne a ciki dakyar ta iya daukan guda daya a ciki ta saka , tana sakawa ita kansa saida taji kunyar kayan da sauri ta haye kan gadon tana lulluba sabida sanyin da ya ratsa mata sassan jiki, da Kyar bacci barawo ya saceta tanayi tana farkawa gudun karya shigo dakin kafun bacci ya nauyi ya dauke ta sosai. Karfe 2am ya shigo dakin ganin ta takure waje daya ne yashi karasawa gaban kan,a gefenta ya kwanta a hankali gudun kar ta tashi daga baccin da take yi kamar a takure, goshinta ya taba yaji har yanxu zafin jikin ta be sauka ba, janyota yayi gabaki dayanta ya dora akan kirjinsa, wani ajiyar zuciya ta sauke me karfi da yasashi kallanta kadan, kara rungumeshi taji ajikinta kamar wacce akace za’a kwace mata shi, lullube jikinsu yayi da bargon yana jin yanda zafin jikinta ke ratsa sa,kallan innocent face dinta dake bacci cikin kwanciyar hankali yayi kafun ya furta “ stubborn girl na kusa yin maganinki “, yana kara rungumeta a jikinsa, ba dadewa shima bacci ya daukesa, baccin da zai iya cewa tun tsawan wasu shekarun baya beyi baccin da begaji dayinsaba kamar na yau. Kiran sallar asuba na farko ne ya farkar dashi, a hankali ya fara mutsu mutsu da idanuwansa kafun ya bude su gabaki d’aya akan kyakkyawar fuskarta ,zubawa fuskar idanuwansa yayi Kafun ya gyara mata kwanciyarta yana barin dakin. Kusan mintuna 30 da fitarsa itama ta soma mutsu mutsu kafun ta bude idanuwan gabaki d’aya, adduar tashi daga bacci tayi a bayyane ganin babu kowa a dakin yasa ta sakin ajiyar zuciya , Wanka tayi cikin simple doguwar Riga kafun ta tayar da sallar asuba , tana idarwa karatun alkurani ta yi , ta dauki kusan good 2 hours tana karatun har saida gari ya fara haske tukunna. Turo kofar dakin da akaine yasa ta Mayar da kallanta bakin kofar, zuba masa ido tayi ganin shirgarsa ta yau sak balarabensa , jallabiya ce a jikinsa white colour sai abun nadin larabawa red colour , harya karaso wajan bata sani ba sabida yanda ta zuba masa ido , sai da ya hura mata iska kadan kafun ta sauke ajiyar zuciya, cikin kunya ta sunkuyar da kanta,kafun ta furta “ina kwana”, ba amsa mata ba sai kallanta da yayi, kara maimaita gaisuwar tata tayi ,ynxu ma be kulata ba , sun kuyar da Kai tayi kasa ya daga da kanta, bakinsu ya hade waje d’aya kusan mintuna daya kafun ya zare bakinsa “ bakyajin magana kenan ko”girgiza masa kai tayi alamun Aah , waje ya samu ya zauna , dan turo masa bakinta tayi kadan “ina kwana “, har yanxu be amsa gaisuwar tata va, sai ma a wayarsa da ya dauka , tunowa da wacce take hannunta yasa taje ta dakko ta , binta da ido kawai yayi kafun ya dauke kansa, cikin girmamawa ta miko masa wayar be amsa ba sannan be kalletaba,”ga Wanka “ ta furta a sanyaye, kallanta yayi “Menene nawa “ wayanka ta basa amsa ,”it’s your” ya furta , da wani irin shock ta kallesa, batasan lokacin data rungumeshi ba,hannu d’aya yasaka ya tallabota gudun karta fadi” dady dagaske ta wace”, gira kawai ya dage mata,kara rungumeshi tayi lokaci d’aya wani kukan ya kara wace mata, dagasken gasken yanxu kukan take me taba zuciya , very tight king ya rungumeta a kunne ya rada mata “it’s ok” kafun ya dago da ita , kallan yanda hawayen suke zuba afuskarta yayi kafun ya harareta kadan”so kuke su mahma suzo suce miki na miki wani abun kenan ko”, girgixa masa kai tayi tana goge hawayan nata “nagode sosai Allah ya kara budi”ya ji dadin adduar da tayi masa sosai cikin zuciyarsa ya amsa da amin, a fili kuwa dan tabile baki yayi “we’re friends ai no need” jinjina masa kai tayi zata mike yakara gyara mata zama akan cinyarsa,yanda ake anfani da yawar ya nuna mata komai already daman anyi settling komai na cikin wayar, murmushin fuskarta kasa boyuwa yayi sosai ta nuna jin dadinta,ganin karfe takwas ta kallesa “dady me kake so kaci” Kai tsaye ya bata amsa da “you”,wara idanuwanta tayi “toh ni taya za a da fani” bece mata komai ba yakama hannunta suka fito falon sai ynxu ta ke kallan yanda komai na dakin yake a canje,janta yayi har wajan dining ganin abunci ajjjere ne tayi serving dinsa tare da kunun aya, kince yayi saida tasa hannu ta fara basa a baki, duk loma d’aya in yayi baya sakamar mata hannun sai ya tsotseshi,abun har kunya ya fara bata, sai da tayi feeding dinshi kafun shima yasoma bata dan dole take karba,suna kammala ci falo suka zauna tana zaune kan cinyarsa kallan gashin kansa take so take ta taba amma ta kasa, kamar yasan me take tunanin ya dauki hannun nata guda daya ya dora a saman kansa,murmushi ta saki tana kara tura hannayenta cikin gashin kansa me tsananin taushi da laushi, suna zaune ahakan sukaji an turo kofar da dan karfi, zaro idanuwa tayi waje tana kokarin sauka amma ya kara riketa ajikinsa sosai yana bin amrah da tashigo masa part kai tsaye da wani rin birkitaccen kallo daya firgitata, hatta karamin ture din hannunta saida ya fadi kasa tsabar firgita. 💖💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖💖 Mss Lee 💖 💖💖GIDAN AUNTY💖💖 ( a heart touching love story) Story & written By Mss Lee 💖 💖💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖💖 PAID BOOK MAI BUKATAR COMPLETE DIN GIDAN AUNTY YA TUNTUBENI TA WANNAN NUMBER 07041879581. BOOK 1📕 Page 53 _ 54💖 Da wani irin rikitaccen kallo ya bita dashi , hannunsa daya yasa ya rike kugun tahee da ta kasa motsi, a mugun fusace ya furta “are you mad “, jikin amrah rawa ya fara ganin yanda ya fusata , cikin rawar baki ta furta “dan Allah kayi hakuri yaya king, ca akai na kawo muku”, guntun tsaki king yaja yana dauke kansa daga kanta, wasu zafafan hawayene suka sakko mata,” clean that trash now”da sauri ta gyada masa tana furta “toh toh”, tattare kayan tayi waje daya Allah ya temaketa ma abun be bare ba dan a kulle yake sosai a cikin wata yar roba, tunda ya rike mata kugu ta kasa motsi sai ma shakuwar data kamata, mikewa tayi niyar yi ya kalleta, ganin haryanxu fuskarsa a hade take yasa ta furta “ru..ruwa zansha “, jinjina mata kai yayi yana kara rike kugun nata kafun ya kalli amrah da tayi nadamar zuwa wajan ya fi a irga,”jeki kawo ruwa yanxu”,da sauri amrah ta ajje tray din hannunta ta nufa fridge a tunaninta king ne zaisha harda daurayo cup dan ta bakantawa , sai taga sabanin hakan ,ruwan kawai ya karba ya balle murfin tare da kaishin saitin bakin tahee, a hankali take shan ruwan sai da ta sha sosai kafun ta dauke kanta,”baki iya gaisuwa ba “ ya furtawa amrah dake duke a kasa, da sauri ta furta “kayi hakuri , yaya king ina kwana”be amsa mata ba har tsawan mintuna biyu da ya shude kafun ya sake cewa “ni kadai kika gani “ da Sauri ta kara girgiza kai tana hadiye kukan da yake kokarin zuwan mata “ au… aun.. aunty ina kwana” dan kallanta tahee tayi kafun ta dauke kanta itama “lapiya Lou “ kawai tace mata,wani kululun bakin ciki ne ya kama amrah tana dannewa ne kawai dan ba yanda zatayi, cikin rawar murya ta furta “yaya king sai anjima, aunty sai anjima” mai gayyar ko motsawa beyi ba balantana tasa ran zai amsa ,kasa kasa take kallan tahee dan tasan tabbas da batayi mata sallama ba saukar mari zataji a kumatunta,Zata tafi ya tsayar da ita “wait”, yna nuna mata dinning “clean it up and ki gyara wajan”magana tahe tayi kokarin yi itama ya bita da kallansa , shiru tayi kawai tana sun kuyar da Kai,goge hawayan da suka zubo mata amrah tayi , shekara biyar kenan tunda tazo gidan bata ko daukan tsintsiya amma yau sai gashi tana bautawa wacce tafi tsana a duniya , kanta kawai take gyadawa, sai data wanke komai sannan ta gyara dinning su king na zaune a falo, kamar munafuka ta karaso inda suke tana satar kallan king “nagama” bece da ita komai ba sai dauka tahee da yayi kamar baby ya hau kan steps da ita.zubewa amrah tayi a Wajan tana sakin saban kukan da ya tsaya mata a makoshi”ni king zai wulakanta agaban wannan kaskantacciyar” birgima ta somayi akasa kamar wata yarinya jin Alamun kamar takun tafiya yasa tayi saurin barin part din bakin ciki da ta kaici fal ranta. Be sauke taba sai akan gadon dakin da suka kwana, kallan ta yayi kafun ya furta “me kikeso “,juyawa tayi kamar me tunani kafun tace “kayan sa wata nake nema”, hannunsa ya miko mata ba musu ta saka nata. Fitowa sukai daga cikin dakin sai bin ko ina take da kallo ganin duk ancanza komai data sani, steps suka fara takawa a hankali,kafun ya daga ta gabaki d’ayan ta ya karasa hawa steps din da ita, bata san lokacin da bakinta ya furta wow ba tana zaro idanuwanta, yanda komai yake a tsarane ya fi burgeta ,kamar ba akasar Nigeria ba ahaka wajan ya kawatu ina kawatuwa ta yanda ko baki bazai iya fusalta kyan wajan ba,”yayi miki kyau” yanxu ma gyada masa kanta tayi, bece mata komai ba ya jata cikin white room dinsa, nan ma sakin bakintayi tana kallan dakin musamman yanda dogayen labulen suke kawanye da dakin, remote ya ya danna take a wajan tabulen ya fara bude kansa,kara zaro idanuwanta tayi kafun ta karasa wajan balcony din, ganin yanda wajan shan iskar yake da shegen kyau shima komai nashi fari ne ,kamar karta motsa a Wajan jin yanda iska ke kadata,kallan glass din da yayi wa Wajan kwawanya tayi kafun ta dan Kai hannu kamar zata tava sai kuma cikin sauri ta dauke hannunta, jiyowar da zatayi ne sukai karo dashi,sunkuyar da kanta kasa tayi cikin jin kunya sam ta manta yana wajan,hannunta daya ya kama tare da dorawa kan glass din , cikin sauri ta zame jikinta daga nasa, bece mata komai ba ya kama hannunta suka nufi wata kofa dake cikin bedroom din, babu komai a ciki sai glass na kayan sawa shake a wajan masu shegen kyau hatta fitilar wajan ta banbanta da sauran,yana dannan wani bottom gabaki d’aya wardrobe din suka bude kayansa ne shake a wajan masu matukar tsada , daga ciki kuma akwai wasu kayan matan suma masu kyau, komai na cikin Wajan na mace da namiji ne hatta kayan sawar, gefe daya ma wasu takalma ne masu shegen kyau na mace sai kuma ta kalmansa masu shegen yawa suma , komai na bukata a kwai a dakin dan lissafa su bata lokaci ne , shima dakin sosai ya mata kyau amma ganin kayan mata a cikine yasa jikin ta yin sanyi daman ta san ba santa yake ba, wasu kayan sawa ya nufa doguwar abayace purple me shegen kyau , storn din jiki sai walwali suke dauka ,kayan ya mika mata kawai tare da ficewa daga cikin dakin, kallan kayan tayi kamar bazata saba sai kuma ta saka ,kallan yanda kayan yayi mata cif cif tayi kamar an aunata musamman in tayi motsi sai storn din suma sunyi motsi dakara , gashin kanta ta gyara kafun tayi rolling din mayafi, sosai farar fatarta tafito cikin abayar da ta saka , duk da tsananin kyan da tayi murnarta koma ciki tayi dan tasan baya bawa zaiyi ba dan baya santa. Kokarin cire wa ta farayi ya shigo cikin dakin sanye da kana nan kaya farare tas dasu, gashin kansa sai faman shining suke , bin jikinta yayi da kallo kafun ya karaso inda ta ke, dago da fuskarta yayi batare da yace komai ba ya soma bata wani hot kiss a kan labba, “Kinyi kyau”ya furta ta yanda bazata jiba tagadai ya dan motsa bakinsa. Kama hannunta yayi da kanshi ya fara nuna mata ko ina na cikin part din musamman wajan kucciyar sa da sukaje, wani irin farinciki da shauki ne ya kamata , duk maganar da zatayi itama kucciyar sai ta kwaikwayeta,bata san lokacin da ta ke dariya ba , be hanata ba saida ta gaji dan kanta kafun ya kaita dakin gym dinsa, nan sai bin wajan take da kallo kamar a mafarki, wajan swimming fool dinsa ya kaita ,kinshiga tayi wai batasan fadawa ruwa, murmushi kawai yayi ya kama hannunta da gyar tahee ta shiga wajan tana makale a bayansa take bun ko ina da kallo, gabaki daya 3rd floor da 2nd floor sai da suka zagashi, ita kadai sai faman sakin murmushi take. Tare suka sakko down stairs hannunsu sarke da na juna, kallanta yayi kafun ya rada mata “ am going out now “, cikin dan jin kunya ta furta “A dawo lapiya ,Allah ya bada abinda aka je nema”lumshe idanuwansa yayi sabida yanda yaji dadin adduar,gefen fuskarsa ya nuna mata alamar ta sumbaceshi, dan ware idanuwanta tayi akansa, shima kwaikwayr yanda tayi yayi ,kafun ya kara nuna mata , girgiza masa kai tayi alamun bazata iya ba, gyada Mata Kai yayi kamar ya hakura sai kuma ya janyota jikinsa”tunda bazaki iya ba , ni I can do it”, kokarin kwace kanta tayi ya kara matseta ta yanda bazata iya kwacewa ba,knocking din kofar akai tayi saurin kallansa ,”ana knocking” , hakan yayi ai sai su kalli yanda zanyi miki kiss din ai,dan turo masa baki tayi tare da marairaicewa, “dan Allah ka sakeni “, lumshe mata idanu yayi,”dan Allah “ ta kara karye masa murya a shagwabe , yanda tayi sai ya burgeshi kamar karta dena,wani knocking din aka sakeyi, batare da ya ankara ba ta sumbaceshi a kumatu, kasa motsiyayi sabida yanda kiss din tazo masa a bazata, da mugun sauri ta kwace kanta tagudu upstairs tana dariya kasa kasa. Kwafa kawai yayi yana bin stair case din da kallo kafun ya bude door din, zaki ne tsaye a bakin door din , yana ganin king cikin girmamawa ya gaishe shi kafin ya mika masa wasu file , jinjina masa kai king yayi yana karban files din amaimakon ya koma ciki sai ya fita shima . **** kan gadon ta ta fada tana sakin dariya kasa kasa, ita kadai tasan yan da take san bawan Allahn nan dan ya galadima ta komai arayuwa, ya kula da ita alokacin da take bukatar kulawa, ya zauna da ita alokacin da bata san wacece ita ba, indai ba butuluce itaba be kamata ta butulce masa ba , Ada tayi alkawari bazata taba nuna masa tana sansaba ,yanxun ma Hakane amma tayi alkawarin kula dashi iya iyawarta. Wani murmushine ya subuce mata musamman yanda ta hango face dinshi dazu bayn ta gudu, so take taje ta gaishe dasu ammey amma tasan hakan ba me yuwa bace kuma bata da number ammeyn balantana ta kira ta, wayar da ya bata ta dakko tana kare mata kallo, babbar wayace meshegen tsada dukda bazata iya kiyasta kudin taba. Snap tashiga ita kadai ta dinga daukar selfie, da Wanda tayi tana murmushi da Wanda take turo bakinta,da ka karshe ma gyalan tacire gashinn kanta y zubo, sosai tayi snap din ta, duk ciki babu na banza dan bakaramun kyau hotunan sukayi ba. Shaf shaf ta kara tsaf tace dakin , ta fito ta kara gyra floor 2 duk da yanda ya kasance kalkal dashi. Kamar ta gyara masa saman sai kuma taji tsoran hawa , hakura tayi da gyarawar Daidai zata sakko down stair ta hango wata yar karamar white farar takarda,dan karamin tsaki ta saki a fili ta furta “Allah ya shiryeni “ tana daukar paper har zata saka a trash bin dan karami dake wajan sai ta fasa tare da bude ta , Rubutun da tagani ne yasata jefar da takardar zuciyrta na tsananin bugu, kara kallan paper din tayi da kyau tana karanta ta , bata gasgata abunda yake ciki ba ta dan goge idanuwanta , d same kallarce a jiki” KILL YOUR HUSBAND” shine dai still a jikin paper din sai wani dan karamin zare ja da ya fado, a matukar rude taja baya in bata manta ba ta taba ganin zaren wata mata ta jefo mata tana dariya a cikin baccinta,yanxu ma kuma ta sake ganin zaren, Bismillah tayi ta dauke zaren tare da paper harzata yardar sai kuma ta fasa ,cikin dakinta ta koma , wani dan karamin locker da ba kowane zai kula da itaba tasaka paper da zaran a cikin tare da kullewa , har yanxu bata dena mamakin paper data gani ba musamman Rubutun ciki “KILL YOUR HUSBAND” ta kara nanata kalmar, tunani take so tayi Akan paper amma komai ya tsaya mata, ganin kanta na kokarin ciwo ne yasata ajje tunanin a gefe daya ta sakko down stairs din adai adai lokacin dasu zoya suke shigowa parlorn ita da su ihsan.da gudu zoya ta rungumeta ,itama rungumetan tayi ajikinta tana sakin mata dariya , kallan su ihsan tayi da suke shigo da trays a hannunsu, “bismalla “ta furta musu binta da kallo sumayya tayi dan batayi tsammanin jin haka daga gareta ba, zama kowannansu yayi kafun ta gaishesu tana sakin murmushi, suma gaishe tan sukai dan kwata kwata basu kawo tana da saukin kai hakaba , tunanin me zata kawo musu tayi kai tsaye tanufi kitchen , wasu manya robobine masu shen kyau da girma a gefe, dan bubbudesu tayi taga garane cike a ciki, Baban trays ta dakko ta zuzzuba musu aciki tundaga kan dublan, cincin , har abunda bata sani ba saida ta zuba musu ta kawo musu, still saidata koma ta dakko musu lemo da ruwa data gani shake a fridge, binta kawai suke da kallan, tana zama ta sakar ta sakar musu murmushinta da baya boyuwa”bismilla ku”, suma martanin murmushin suka mayar mata , sumayyace ta furta “mungode “, yaya fa” firdausi ta dan tanbaya,cikin dan jin nauyinsu ta furta “ya dan fita” , daga nan babu Wanda ya kara cewa komai sai zoya dake faman hira da tahee cikin wasa itama taheen tana bata amsa , su ihsan sai binsu da kallo suke dan sosai suke mamakin shakuwarsu,basu dade ba suka tashi zasu tafi kamar zatayi kuka,dan ko bakomai sun debe mata kyewa,kitchen ta koma tadakko wasu designers back masu kyau ta juye musu garan da ta zubo musu,kallan zoya tayi “amma zaki zauna ko”, zaro funny eyes dinta zoya tayi ,ummey nace karna zauna akwai islamiyya yau ,amma zan dawo gobe muyi game”, Tom shikenan kizo da wuri kinji,Jini jina mata kai tayi har bakin kofar falon ta rakosu tare da mika musu bags kin,suma cikin girmamawa suka karba ko ba komai ta karramasu,”ku gaishe da mutanan gidan “ta fada tana sakin musu murmushi, suma martanin murmushi sukai mata kafun su bar part din, ganin ana kiran sallah yasa ta koma sama tayi sallanta, bataci abincin da aka kawo ba sai gyara su da tayi a dinning har lokacin king be dawo ba. 🫧🫧🫧🫧🫧🫧 Karfe 4:30na yamma ta koma sama da niyar yin wani Wankan gani tayi kamar ana binta da sauri ta juya amma wayam babu kowa awajan , sharewa tayi tare da cigaba da tafiyar tata , tana shiga dakin Daidai zata nufi toilet ta karajin mutsu mutsu kamar na taku, da sauri ta kara juyawa Dan yanxu abun ya fara bata tsoro, bin bakin kofar ta farayi da kallo ko zata mebinta, wuff taci abu ya wuce ta gefen kunnanta, addua take so tayi amma bakin nata ya kasa motsi , karabi ta kunnan ta akai ta saki wata iriyar kara, launikan idanuwanta ne suka canza zuwa launin ja sosai mutsun nan yazo zai kara giftata, taku ta d’aya tayi ta shako wuyan abun ,take a wajan wata bakar kuliya ta bayyana bakakirin da ita hatta idanuwan Magen baki ne babu ko digon fari a ciki, mutsu mutsun kwace kanta tasoma yi amma ta kasa ,sai wani irin gurnani da take saki, sai ayanxu bakin tahee ya bude ta soma karanta adduoin da oumma ta koya mata,kara Magen ta somayi da karfi ,itama taheen kara sautin karatunta tayi tana makurewa Magen wuya,tana karatun tana lumshe idanuwa Sabida wata iriyar juwace take neman kada ita, daddagewa tayi tanaka Magen da kasa ,aikuwa tana buguwa ta saka wata iriyar kara kafun ta bace battt a dakin, tsugunnawa tayi tare da dafe kanta dake neman cirewa daga jikinta, wani irin kuka ta fashe dashi jin yanda kanta ke sarawa da karfi,ta dade a tsugunne dafe da kanta sai faman kuka take kamar wacce tasoma fita daga hayyacinta, turo kofar dakin yayi a hankali kafun yayi sallama , yanda ya ganta a tsugunne ne yashi karasawa wajan ta da dan sauri sauri, yana dagota ta fada jikinsa tare da fashewa da wani saban kukan har yanxu hannunta rike da kanta, kallanta yayi kafun ya furta “meke damunki” kasa yi mishi magana tayi sai kanta da take nuna masa, kallanta yayi kafun ya taba kan ,sosai yayi wani irin zafi na ban mamaki,cikin sarkewa ta furta “Kayi mun addua”, da sauri ya dauketa be zauna ako ina ba sai akan gadon , jingina yayi da jikin gadon tare ta dora ta akan cinyarsa yana kama kan,addu’oi ya fara tofa mata , ya dau kusan 20minutes yana tofa mata adduar , wata iriyar ajiyar zuciya ta sauke jin kan yadena yi mata ciwon kwata kwata,lafewa tayi ajikinsa tana shakar kamshin jikinsa me sanyaya zuciya ,kafun a hankali ya furta “me yafaru”, amaimakon ta bashi amsa sai cewa da tayi “ni yunwa nakeji”kallanta yayi da mamaki”bakici abincin da aka kawo miki ba”kanta ta daga masa alamun eh, dan Jim kadan yayi kafun ya dauketa gabaki d’aya ya sauko kasa da ita dakansa yayi serving dinta kafun ya bata a baki, sai da ya tabbatar ta koshi sannan ya kyaleta” ya kamata ki dunga cin abinci sosai sabida duk lokacin da ajiyata ta sauka bazan lamunta ba”, bata gane me yake nufi ba ta dai daga masa kanta kawai, wani irin murmushi ya saki yana lumshe mata idanuwa. Janyota jikinsa yayi kafun ya soma shinshinar wuyanta, da sauri tayi kokarin janjikinta amma ya hanata hakan,” Yaushe zaki bani abunda nake so” kallo na irin ban gane din nan ba tayi masa ,sarai yagane bata gane ba ,sai kara janyota dayayi jikinsa,”I want you here with you”, kasa motsi tayi jin yanda kamshin bakin sa na strawberry ke shiga cikin hancinta,”zanyi wanka, come and help your dad, daman kin taba mun alkawari zakiyi mun wanka ,to lokaci yayi zomuje oya”, waro masa idanuwanta tayi tama kasa magana ,hura mata iskar bakinsa yayi da Sauri ta lumshe tana sakin ajiyar zuciya,”kayi hakuri…”be bari ta karasa zancan ta ba ya hade bakinsu,sai da ya tsotse mata baki tas kafun ya janye bakinsa,kallan yanda ta soma hawaye yayi kafun ya dauke kansa,”it’s ok “ ya furta be kuma cewa komai ba ya haye sama,ganin yanda ya wuce din sai taji bataji dadin abunda tace masan ba, tsawan lokaci tana zauna tunani ta fara ta bishi ko karta bishi, daga karshe zabin zuciyarta tabi ta hau saman, tana shiga dakin taga wayam bayanan atunanin ta yana sauran dakin,d’aya bayn d’aya ta duba duk baya ciki,sai yanxu white room ya fado mata,da Sauri ta nufa saman tana bude kofa yana kokarin shiga dressing room dinsa da bathrobe a jikinsa blue colour , idanuwanta ta kulle ganin ba Kaya a jikinsa a hankali ta furta”kayi hakuri “bece mata uffan ba ya shige warsa, zubewa kasa tayi tare da fashewa da kuka ganin be kulataba, bude kofar da yayine yasata dagowa , hannu d’aya kawai ya mika mata bata san lokacin da ta karasa wajan sa ba , daga ta yayi gabaki dayanta be tsaya ya nufi toilet hanyar toilet da ita, da mugun sauri ta fara mutsu mutsun kwace kanta “bana so” yace mata a hankali be kara bata wani damar ba ya shige toilet da ita tare da turo kofa , kusan mintuna 30 kafun ya bude kofar yanxun ma dakko ta yayi amma ko sau daya bata dago da idanuwanta ta kallesa ba, sai ma kara Boye fuskar data keyi,dauke kansa yayi kamar be ga me take yi ba, yanxun ma duk mutsu mutsunta shine ya shiryata da kansa kafun ya nufi masallaci, yana fita tunanin abunda ya faru take kokarin tunawa ganin kanta na kokarin ciwo yasa ta kawar da zancen tare da kabbara sallah. ****karfe tara da rabi yashigo dakin ganin ta a kwance kamar me bacci yashi kashe mata light, shaf shaf yayi wanka ya kwanta a gefenshi duk tana jin motsinsa,ya gani yau shiyasa kawai ya janyota jikinsa ya rungume wani irin bugawa kirjinta ya somayi da sauri sauri,jin hakan yasashi sakin murmushi me dan sauri a bazata ya rada mata “don’t worry babu abunda zan miki ,inasan jin dumin matatane “,wani ajiyar zuciya ta sauke duk da ba yaune ta fara kwana dashiba amma wani irin tsoranshine ya shigeta a haka har bacci ya dauketa, shima gyara mata kwanciyar akan chest dinsa kafun wani bacci ya d’auke shi shima. 🫧🫧🫧🫧🫧🫧 WASHE GARI yau ma ana kiran sallar asuba ya farka yayi alwala batare da ya tayar da ita ba,itama ba dadewa ta farka ganin bayanan yasata sakin ajiyar zuciya ,shaf shaf tayi wanka tayi sallah ,tana idar wa ta fara gyaran gidan kamar me aljanu shaf shaf ta gyara floor 3 din duka sai wajan 8 ta dakko ganin ko ina kal kal yasa ta mamaki, down stairs ta sakko ta tarar da kulolin abinci , ajiyar zuciya ta sauke tare da dan kikkim tsa abunda beyi mata ba. Da sallama a bakinshi ya shigo part din, amsawa tayi tana binsa da kallo har ya karaso inda take”ina kwana”ta furta , dauke kansa yayi daga kanta ,ganin be amsa mata ba ysa ta kara furta “ina kwana dady”, yanxu ma be kulataba yayi kokarin wucewa ,batasan lokacin da ta kamo hannunsa ba , da karfi ta lumshe idanuwanta ta sumbaci kumatun ta, murmushin gefan fuska ya saki kafun ya furta “lapiya Lou “, dan karamin ajiyar zuciya ta sauke , shima kama hannunta yayi Kai tsaye suka nufi dinning, serving Dinsu tayi kowa a plate dinshi amma ya matsar da nashi plate din ya matso da natan,dan bude bakinsa yayi kadan kamar lokacin da bata da lapiya da tayi masa, abincin ta dakko a spoon zata bashi ya cire spoon din ya sa hannunta ganin hakan yasa ta fara bashi a baki da hannunta da ke wanke tas dasu kadan ya ci ya kawar da kansa kafun ya fara bata itama a baki , dan dole kuwa ta amsa , suna gama ci falo suka nufa be bata damar zama a ko ina ba sai akan cinyarsa da ya dorata,itama batayi musun hakan ba , gabaki dayan su shiru Sukai ba me magana a hankali ta furta “ naga angyara 2nd floor and kasn nan” kamar bazai bata amsa ba sai kuma ya furta “ su ihsan ne suke gyara anjima za a kawo miki me tayaki aiki “ yana gama zancan ta furta amma zan dungayin abinci ba sai na wahalar dasu ba” kallanta yayi da sign din Dagaske kike kafin ya dan harareta “you are not allowed to cooked sai kinyi 7 days dinki kamar kowa” bata kuma cewa komai ba kuma ,shima be sake ce mata komai ba . 12pm ya shirya ya fita ,kafun ya fitan sai da ya kira ihsan a waya akan suzo part dinsa ,da muryar su kuwa ta kashe wayar, dan kallanta yayi ganin yanda farinciki ya bayyana a fuskarta, dan dungure mata kai yayi kafun ya bar part din. Su ihsan ma ba dadewa sai gasu a part din su uku, ihsan ,sumayya, da firdausi,sai yar aikin da aka kawo mata me suna KULU,duk abunda tahee take so ta dunga yi ta fada mata,KULU sai washe baki take , babu wani aiki da zatayi yasa tahee sallamar ta, kafun ta tafi sai da ta zuba mata kayn Gara itama sai faman murna da adduoi take mata.da murna ta Tarbi su ihsan ,yauma sai da ta cika musu gabansu da kayan ciye ciye , sabanin jiya yau har da hira ta dunga Jansu ganin ynda suka sake mata, cikin kan kanin lokaci kuwa suka soma hirar su harda tafa hannu kamar basu ba , sun dade a part din dan kin barinsu su tafi tayi sai da sukayi sallar azahar, nan ma da kyar ta barsu har saida sukayi mata alkawarin dawowa gobe. Suna barin part din tazo wuce wa ta tarar da irin paper jiya da Sauri ta nufe ta, tana bude wa kalmar jiya ce a ciki “KILLED YOUR HUSBAND “, waigawa tayi ganin bamowa a wajan yasa ta nufi sama da sauri ta Adana ta da ta jiya, “Zan nemo ko ma wanene” ta furta a bayyane kafun tashiga toilets. ****** 10:30 suna kwance kan gado yana rungume da ita, zagaye hannunsa ya farayi a jikinta da Sauri ta rike hannusa tana girgiza masa kai,be kulataba ya cigaba da abunda yake,ganin mutsu mutsun nata yayi yawa yashashi rungumeta ajikinsa yana shinshinar wuyanta kafun ya saki wani ajiyar zuciya, tsoro da firgicine ya kamata ganin yanda yake faman sakin ajiyar zuciya , rigar jikinta yake kokarin cirewa tasaka masa kuka ,”ina jin tsoro, ka bari please “ ta fada murya a shake , shima cikin yanayi da muryarsa ta fara canzawa ya furta “ba abunda zan miki” kara girgiza masa kai tayi tana kokarin tashi” I promise “, daga nan be kara bata damar cewa komai ba ya hade bakinsu waje daya, kusan dogon lokaci ya dauka a haka kafun ya fara sakin wani ajiyar zuciya, gabaki dayanta ya daga ya shige toilets da ita , basu dau dogon lokaci Ba ya kara fito da ita a hannunsa sanye da wasu kayan, kwantar da ita yayi akan gadon kafin ya fita ya bar dakin, kusan Mintuna biyar da fitansa bacci ya dauketa,dawowa yayi hannunsa d’auke da wani medium din ruwan roba, wasu magani ya sha kafun. Ya kwanta a gefenta sai faman sakin ajiyar zuciya yakeyi, sai da ya bari baccinta yayi nisa kafun ya janyota jikinsa ya dade a haka kafun bacci ya daukeshi. Washe gari ma hakance ta faru su ihsan sun kara dawowa har lokacin babu kafar amrah ko basma, sosai sukai farincikin ganin juna ,hira sukai sosai wannan karan sumayyace ta roki alfarma KULU ta tafi su sai suyi aikin ,Sabida suna san zaga part din yayansu tun da basu taba shiga ba , haka kuwa akayi gabaki dayansu , su hudun suka gyara second floor da down stairs , 3rd floor ne kawai bata kaisu ba, sosai ko wannansu ya yaba tsaruwar part din sa, da kansu suka gyara part din suna yi suna hira sun dade a part din dan wannan karan kin barinsu su tafi tayi har saida mahma ta kira su awaya, gabaki daya wayar firdausi ta mikawa tahee tana dariya , gaishe da mahma tahee tayi acan ban garan ma cikin farin ciki mahma ta amsa mata tare da tanbayarta lafiyar ta , cikin jin nauyi ta ta amsa mata, janta da dan hira mahma tayi kafun ta umarci su sumayya su dawo, gabaki d’aya dariya suka sa mata ganin ynda tayi da face dinta, har bakin falon ta rakasu, abun mamaki tana shigowa palorn ta kara tarar da paper nan still Rubutun da ta saba gani a jiki ci ta gani “KILLED YOUR HUSBAND”,duk tunanin da zatayi ta kasa shiyasa yanxu ma ta kara adana paper kamar sauran. Da daddare ma hakan ce ta faru sam ta ki bari king ya tabata balantana yayi mata wani abun, sai da ya kara mata alkawarin bazea mata komai ba sannan ta barshi yaba ta. 🫧🫧🫧🫧 ➰➰➰➰➰➰ Akwana a tashi ba wuya wajan Allah SWT yau kwanan tahee biyar da kaita dakin mijinta, acikin kwanakin nan sosai wata iriyar shakuwa taban mamaki ta shiga tsakanin king da tahee , duk lokacin da zasuji abinci baya bari suci plate daban daban sai plate daya, komai tare sukeyi , hatta wanka wani lokaci sai yace tare zasuyi ,Da taji hakan take samunta gudu tabarshi saidai kawai ya girgiza kai yai wuce warsa, a cikin kwana kinnan KULU ta fara zuwa aikin, harsun fara sabawa da tahee, su ihsan ma kullum sea sunzo sun debe mata kewa sosai suka saba , amrah da basma ne har yau Ba sa zuwa part din, hatta su ammey suna waya a wayar su ihsan wani lokaci kuma awayar daya bata take kiransu.har zuwa wannan lokacin kuma ba abunda ya shiga tsakanin ta da king sai dan rage zafi da yake , ganin hakan yasa tun bata sakar masa jiki harta fara. Yanzuma tsaye take a gaban mudubi haka kawai tayi sha’awar saka kananun kaya yau, wani top din Riga ce ajikin ta blue colour sai wando da yar karamar rigar ciki white ita ma, tunanin turaren da zata saka tayi hakanan ta dakko wani turare da amzy ta bata tace ta kwada sawa yana da dadi, tana bude kwalbar gabaki d’aya dakin ya bade da kamshin turaran, a kokarin zuba wa a hannun turaren ya zubo mata a jiki, da Sauri ta fara goge wajan amma amaimakon kamshin ya ragu sai karuwa ma da yake, kafar futa daga dakin ta nufa , Daidai lokacin dayake saka hannunsa ta waje, ita kuma tana Jan kofar ta ciki, suna ja ko wannansu yayi karo da juna, ba abunda ya daki hancin king sai kamshin turaran da tahee ta bude , take a wajan wajan launin idanuwansa suka canza ga wani irin kasala da ya fara ji lokaci d’aya ,kallan shigar jikinta yayi na sakanni kafun ya d’auke idanuwansa , rumgumeshi tayi a jikinta tare da furta “sannu da zuwa”, yanxu ma bece mata komai ba sai gyada mata kai da yayi, shaf shaf Wanka yayi cikin pj mas farare tas masu dasu, furar da dada ta aiko musu dashi sukasha ko wannansu kafin ya kalli tahee ganin ta dena shan furan,” eat well nasan anjima zakiji yunwa” girgiza masa kai tayi “na koshi” be kyaleta ba sai da ya sata cin papper chicken me shegen dadi, suma kammala brush sukayi tare da hayewa kan gadon, a jikinsa ta kwanta kamar yanda ya sabar mata,lumshe idanuwansa yayi na wasu yan mintuna kafun ya sauke su akanta, dan dago habarta yayi tare da hade lips Dinsu waje daya , ahankali ya fara kissing dinta, a wannan kara sai ta fara bashi martanin kiss din,Hakan da tayi ba karamun zautar dashi yayi ba ya kara kaimi wajan yi mata french kiss dinsa, a hankali ya fara yawo da hannunsa a jikinta kafun ya dora hannunsa daya kan breast dinta, dan matsasu yayi kadan ta saki kara da sauke nunfashi,wasa ya fara yi da breast dinta tun yanayi a hankali har ya fara yi da sauri sauri, hannu d’aya ya saka ya fincike rigar jikinta gabaki d’aya , zaro idanuwa waje tari tare da kokarin kwace jiginta amma yaki bata damar hakan musamman yanda kamshin turaran jikinta ke kara zautar dashi, a hankali ya sakko da lips dinsa kan breast dinta, kisses yake basu ko ta ina kafun ya dora bakinsa kan daya daga cikin breast din, wani irin ajiyar zuciya ta fara saukewa jin dadi na ziyartarta ta ko ina ,sai kara bankaro masa su take,sosai ya tsotse breast din kafun ya fara bata kisses ta ko ina a jikinta, kara hade bakinsu yayi waje daya , tare da dora hannunsa akan mararta gabaki d’aya ya fice daga hankalinshi sarrafata kawai yake da zafi zafi, tun tana kokarin wacewa har ta soma sukansa, hannunsa d’aya yasaka cikin pant dinta, wani irin nishi ta sauke masa a kunne d’aya kara zautar dashi,ganin wandan yana takura masa ya dan taba bakinsa da nata , ya zare wandan gabaki d’aya , da wani irin karfi tahee ta soma tureshi tana kiran sunan da ganin be kulataba ne yasa ta fashe masa da kuka, bata san kukan da ta ke shi ke kara zautar dashi, romancing dinta ya somayi da zafi zafi sai faman sumbatu yake mata a kunne, da karfi ya funciki pant din jikinsa, dan yatsansa d’aya ya tura a wajan ya mantawa da Wanda yake tare, wani irin gigitacciyar kara tahee ta saki jin wata iriyar azaba da ta ziyarceta lokaci d’aya , kara tura finger dinsa da yayi ne yasata sakin wani gigitacciyar karar datafi ta dazu, dabazan sound proof bane bangon dakin da babu abunda zai hana wani yaji sautin karar, cigaba yayi da romancing dinta , kuka kawai take masa ganin ya ki barinta, wani irin karfine yazo mata ta hankadashi zata gudu ya fincikota jikinsa , da Sauri sauri ya fara cire kayan jikinsa,ganin abunda yake kokarin yi yasa tahee ta fara cizo da ya kushinsa ta ko ina amma ko kezau beyi ba sai ma bude kafafuwanta data harde waje daya yayi , a hankali ya kai fuskarsa kasanta yayinda hannunsa biyu suke kan breast dinta dake musu wani irin salo,hannunsa daya ya jura a wajan jin yanda abu ya zubo masa ne yasashi fara karkarwa , da sauri ta runtse idanuwanta tana sakin wani irin nishi,bude kafafuwanta yayi kafun ya zura kansa a wajan yana bata wani irin salo, wani irin jijjiga jikinta ya somayi kamar me shirin yin farfadiya , “DADY” ta furta da karfi murya a sarke tana damke bedsheet din gadon, ya dade yana wasa da ita kagun ya wara kafarta cikin futar hayyaci ya fara karanto adduar saduwa da iyali, tanajin hakan ta fara kiciniyar kwace kanta da sakin masa wani saban kukan, jin kukan ta kara zatar dashi take shiysa da mugun karfin shi ya ziyarceta yana sauke wani ajiyar zuciya, gigitacciyar kara tahee ta saka tana faman dukanshi, wani din azababban kuka take saki amma kwata kwata king be san tanayi ba , sai ma kara kaimi da yayi ,Da karfi take furta “wayyo Allah zai kasheni, Wayyo Dady zafi nakeji, oumma kizo ki temakeni zai kashe ni, TAHEER,abeey kuzo kuceceni zai kashe ni , mugune shi daman ba sona yake yi ba, bana sanka, surutai king ya fara kwata kwata ba a fuskarta ne yke cewa in banda kalmar I LOVE YOU din data fito bakinshi da kyar, sosai yake Jinsa a wata sabuwar duniyar da bai taba zuwa ba, yanda ya kara kusantar ta da karfine yasa tahee sakin wani wahalallan kara, take a Wajan ta dena motsi. ***** 💖💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖💖 Mss Lee 💖 💖💖GIDAN AUNTY 💖💖 ( a heart touching love story) Story & written By Mss Lee 💖 💖💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖💖 PAID BOOK 📕 07041879581 BOOK 1 📕 Page 55_56💖 Kwata kwata baya cikin hayyacinsa aikin gabansa kawai yake ko lura da suman da tayi beyi, azabar da ta ratsata ne yasake farfado da ita daga suman da tayi, tun tana kuka da karfinta har ta kasa saidai hawayen da suke zubo Mata a cikin idanuwanta,tsawan 2hours yana abu daya , kafun ya kankameta ajikinsa yana sauraran yanda kukan ta ke ratsa cikin zuciya,kara rungumeta yayi ajikinsa ,murya na Dan rawa rawa ya soma magana “am sorry, am so sorry, am really sorry Angel please ,thank you so very much,I love you,i love you, I love you, I love you so very much,ina sanki zawj ,please don’t leave me alone”, shi kadai yake surutan sa ,TAHEE kuwa kasa kasa take kukanta ko sauraran abunda yace cewa batayi ,abu daya ta sani bayasanta tunda yayi kokarin kasheta,itama batasansa yanxu, kusan mintuna talatin king yana aikin lallashi ,amma tahee bata jin me take cewa sabida yanda kasanta kemata zafi duk yanda ta motsa, wani irin zazzabi ne a jikinta sosai da yake ratsashi duk da shima jikin nasa zafin zazzabin ne a jikinsa, da kyar ya iya runkurawa zaune ,kallan kyakkyawar fuskarta data kunbura yayi kafun ya lumshe idanuwansa da yake budewa kadan,a hankali ya shafa fuskartata kafun ya sumbaci goshinta yana mikewa,kwata kwata jikinsa ba kwari da kyar yake iya taka kafafunsa,cikin kuzarin da yayi masa saura ya shiga toilet,Be jima sosai a toilet din ba ya fito daure da towel a jikinsa iya kugu, tundaga kan gashin kansa ruwane ke diga dis dis akan sa, yaye bedsheet din da ya lullubeta yayi, gaban shine yayi mugun faduwa Jinin da yagani sosai a wajan, har yanxu tana a yarda ya barta sai ajiyar zuciya ta ke saukewa,gaba d’ayanta ya dauketa ya nufi toilet da ita,tana jinsa ta kara runtse idanuwanta, be tsaya da ita ko ina ba sai cikin jacuzzi, wani irin razanannan kara ta saki tare da yunkurawa zata tashi, saurin mayar da ita yayi cikin ruwan, yanxun ma wani saban kuka ta fashe dashi tana tureshi,ganin dagaske kokawar mikewa take yayi saurin danneta cikin ruwan, yarfa hannayenta kawai take tana kuka ta kasa magana ma sabida yanda take jin ruwan zafin na ratsata, har cikin kwakwalwarsa yakejin kukanta, jiyake dama shine ciwon yake jikinsa, me kwatarsa a wajanta kuma sai Allah, ya dade yana gasa mata ciwon kafun yayi mata wankan da kansa ganin da kyar take motsa jikinta,a cikin white bathrobe ya sa mata kafin ya fito da ita daga toilet din, amaimakon ya maidata kan gadon sai ya zaunar da ita akan sofa, da kanshi ya d’auke bedsheet din da ya baci,ya canza wani kafun ya Mayar da ita kan gadon,haryanxu taki yarta ta bude idanuwanta,ganin yanda jikinta yake da zafin zazzabine yashashi kashe ac yasa mata heater kafun ya koma toilet din, ba dadewa ya dawo inda take, kokarin tabata yayi da mugun zabura ta firgita harta fama ciwonta,murya a shake ta furta “ni karka tabani, daman kace bakasona,kamayar dani wajan ammey na”,zuciyar king ce ta dan harba,yasan tabbas sai yasha daru da ita, kokarin kara tabata yayi takarasakar masa wani saban kukan,kallanta yayi for second kafun ya fice daga dakin, tana ganin fitarsa tayi kokarin zuwa kulla kofar amma takasa tashi, bacci ta soma ji amma sabida tsora takiyin bacci data fara gyangyadi zata farka a za bure a haka harwani wahalallan bacci ya dauketa me tattare da gajiya.duk abunda take yana kallanta tacikin camera din dayayi setting a wayarsa yanxu ganin tayi bacci ne yasashi nufar inda take a hankali ya gyara mata kwanciyar gudun karta tashi,so yake ya dubata ko yaji mata ciwo amma yana tsoro da ya taba cinyarta zata ya mutsa fuska ganin hakan ne yasashi kashe mata deem light kafun ya tayar da sallah, sosai yayi nafila yana yiwa Allah Godiya , shikadai yasan farin cikin da yashiga yau ,lokaci zuwa lokaci yana sakin murmushin da kafun aganshi za a dade, yana idar da sallan shima magani kawai yasha sabida zazzabin dake jikinsa, simple Riga Mara nauyin ya saka mata a hankali kafun ya rungumeta tsam tsam a jikinsa kamar za a kwace masa ita,yana kwanciya wani daddadan bacci ya daukeshi da ya dade beyi irinsa ba. 🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧 BUNKURE Liyafa ta cigaba ,sosai su Dije suke sharholiyarsu yanxu, ba ma bintalon ba yanxu hatta Dije yawanta take zuwa ita da kawarta da tayi yanxu kullum sune hanyar zuwa wajan bokaye, da sunji kina cikin yar matsala zasu rakaki wajan malami da sunan temako, yanxu kwata kwata bintalo bata gidan , ta debe kayanta ta koma wajan hajiyarta da zama acewarta kudi da gata zata samarwa kanta,hakan da tayi kuwa ko a jikin Dije dan itama harkar gabanta take yanxu, hatta su kaka ta bawa Dije ta sa an asirce mata su gabaki d’aya gidan komai sai abunda tace akeyi hatta abinci idan Angama dafawa sai ansanar da ita sannan zata zubawa kowa da kansa. Su kaka ta bawa an fara ganin rayuwa dan Dije babu Wanda take dagawa kafa a cikinsu. Yanxu zaune take hannunta dauke da wani fasasshen mudubi sai faman shafa powder take yayinda kawarta take zaune tana charting, sai faman kas kas kas cingum din bakinta yake , tanayi tana tabe baki kafun ta kalli Dije ,”Dije baby yakamata kiyi sauri fa kinsan alhazawan yanxu basa jira in ba so kike muyi a Saran kudin da zamu dan samu ba “, washe bakinta Dije tayi “yi hakuri kawar alkairi wai Nima yau ina kara saka hodarne yanda alhazawan suka ganni zasu kara rudewa”tana kai zancanta ta ajje Mirror din tare da mikewa sanye cikin yar a tanfarta da mayafin da ta yafa kamar yanda yan mata ke yafawa . Ba bata lokaci suka fito tsakar gida ganin yanda gidan yayi kaca kaca ne yasata fara kwalla kiran sunan mutanan gidan , da daddai da daddai suka fara fitowa , maida kallonta tayi kan kaka tabawa kafun ta balla mata harara “ saunawa zance muke banaso nazo naga waje yayi datti amma sabida ku kunnnan ku na dabbobine bakwajin magana , Kema tabawa dan yanxu baza a sanya din ba, wallahi kishiga taitayinki, yanxu ina Sauri kafun na dawo inaso naga ko ina kal kal sannan na bar magi guda uku aje ayi Miya , kada ku kuskura a tava sai nazo komia dadewa da Zanyi kuwa”,hakuri suka fara bata duk da yanda ta zazzagesu basu jiba sai faman hakuri suke bata, wani banzan tsaki taja tana binsu da matsiyacin ko kafin su bar gidan , kawarta hajjo aunty kuwa sai faman dariya take a cikin zuciyarta. ➰➰➰➰➰➰➰➰➰ YOLA Gabaki d’aya gidan ya rikice tun batan taheer kowa yashiga rudani sabida lokacin sadaukar dashi wajan bokan tsafi yayi, ko ina na gidan sai da aka bincika amma ba a ganshi ba, tsoro da firgicine ya kama ko wannan su musamman yanda suka fara zargin ko akwai me musu zagwan kasa, tun lokacin da aka sanarwa abar kauna batan taheer ta fara musu bala’in da ya girgizasu take a wajan tasa a ka yan ka mata samari biyar amma duk dahakan be yi mata ba , sako da lungu anduba a Garin YOLA da kewayanta amma ba a same saba, hatta kogan tsafin nasu ya kasa nuna masu inda yake, duk cikin su babu me kwanciyar hankali musamman wata 2 da bokanyarsu ta basu in ba haka ba za ‘a dau fansar rashin akan ahalinsu, wannan kalamai na bokanya ya razanasu,cikin rawar jiki suka sa aka fara musu bincike duk inda yake a kamosa a kashe shi . ➰➰➰➰➰➰ 🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧 WASHE GARI har makara yaso yayi da karya iya farkawa, yana motsawa itama ta fashe masa da kuka “ya salam” ya furta cikin kasan zuciyar sa,hannunta ya taba tayi saurin tune hannunsa tare da yunkurawa zata tashi, zafi taji sosia a kasanta da ya fi na jiya, wani saban kukan ta fashe masa dashi tana yarfa hannunta,”am sorry “ ya furta mata a hankali, wani kululun ba’kin cikine ya tokare mata makoshi “wai sorry “, bata kulashiba sai ma kokarin mikewar da ta sake kokarin yi a wannan karan fama ciwan tayi da yasata saurin rintse idanuwanta tana Jan baya, hannunta ya kama tayi saurin fusgewa bata san lokacin data bishi da wani kallo ba idanuwanta duk sun kunbura, ya bude baki zai yi magana yaji saukar muryata a dishe,”kamayar dani wajan ammey, bana sanka “, da Sauri ya kalleta yana jin yanda zuciyarsa ke harbawa da sauri sauri” please karki wahalar dani haka mana “, ya fada a zuciyar sa a fili kuwa dan peck yyi mata kafun ya furta “am so sorry wife”, sharesa tayi kamar bata jisaba sai ma wani saban kukan da ta fara raira masa kamar wacce ake wa wahayi, da sauri ya nufi toilet, be dade a ciki ba ya fito tare da daukanta kamar baby duk yanda take bugun kirjinsa ,direct cikin jakuzzi ya saka ta a hankali,kara ta saki da ta fi jiya tare da zabura da sauri ta mike cikin ruwan yayi saurin dawo da ita , batasan lokacin da wani karfi yazo mata ba ta soma kokawa dashi, ganin da gaske take ya sashi riketa da hannu daya , kuka ta fashe masa Dashi idanuwanta a kulle”daman kace baka sona ,shiyasa kakeso ka kashe ni, Nima bana sanka kamayar dani wajan oumma ta, oumma kinga yanaso yakashe miki ni tun ban kara ganin ki ba”tausayinta ne ya kamashi sosai ganin yanda take furta baya santa kuma bazata zauna dashi ba, Daidai kunnanta ya rada mata “am sorry “ kafun yacire tausayin sa a gefe ya gasata sosai duk yanda take kokarin gocewa, tare sukai wankan ynxu ma shiyayi mata , so yake ta kallesa amma takiyin haka sai ma daure fuskarta da tayi, simple Riga kawai yasaka mata wacce bazata takura mata ba, yazo zai mikar da ita ta boye hannun ,”zan iya da kaina”tana fadun hakan ta mike tsaye,duk da zafin da takeji in tayi tafiya amma taki bari ya temaka mata taku Hudu tayi tana kokarin faduwa ya rikewa kafun ya daga ta zuwa inda sallayar take,yana kula da yanda take tafiya, ga sallah ma da kyar take yi ,tanayi tana kuka, tana idar da sallah ta wanta a wajan ,da Sauri ya karasa Wajan ta bayan ya idar da sallah, ta bata yake so yayi Amma yana tsoran rigimarta, yanxu ma hannu yasa zai tabata ta fara masa masifa , bai taba sanin ta iya masifa ba sai yau, abun sai yaso bashi dariya da tausayi alokaci d’aya , tana masifan tana hawaye kuma taki yarda ta kallesa, be kulata ba ya daga ta gabaki dayanta ya mayar kan gadon ganin ta bazata iya tafiya ba. Be kuma ce mata komai ba ya fita daga dakin, kallan kofar tayi da manyan idanuwanta kafun ta d’auke tana share hawayenta,shigowarsa da tray a hannunsa ne ya ta d’auke idanuwanta daga kan kofar, da kanshi yayi serving dinta, ya kai bakinta tayi saurin dauke ba “bana ci” kawai tace masa zata koma , rike hannun yayi yanajin yanda kansa ke Sara masa kafun ya furta “Am so sorry please , kimu ko wana hukunci amma please kici abincin kisha magani “, kin kulashi tayi, yayi lallashin taki ji saida ya koma mata sak king dinsa ya hade rai kafun ta soma cin break fast din ,da kansa yake bata ganin yanda ya hade ransa kamar bashi ba . Tana kammala cin abincin mgani ya bata nan ma saida suka sha daru da ita kafun ta sha maganin, yana zaune a wajan bacci ya dauketa, ajiyar zuciya ya sauke kadan ganin bacci ya dauketa kafun ya dakko abubuwan bukatarsa,rigar jikinta yayi sama da ita ,sosai gabansa ya fadi ganin yanda ya ji mata ciwo , cikin kwarewa ya soma yi mata dinki, sai faman ya mutse fuska take ita kadai,kallan mitsitsin bakin ya kalla kafun ya lumshe idanuwansa “she’s killing me”,ya furta a fili, shima na bukatar hutawa shiyasa ba abunda ya tsaya yi Yakima gefenta ya kwanta yana rungumota. Basu suka farka ba sai 11:00, shima kukan tahee ne ya tayar dashi, wani gashin ya sake mata sai faman shagwaba take masa gabaki d’aya ta birkita sa da salon ta ,ba abunda yake ce mata sai “sai am sorry , I love you “, rigima sosai take masa amma duk da haka sorry yake ce mata . Azahar nayi ya kawo mata wani lunch din shima da kansa yke bata abinci da gyar ya samu ya lallasheta taci nan ma magani ya bata, dukda ta fara jin radadin ya ragu Ba kamar dazu ba, yana ganin wani bacci ya kuma Dauketa shaf shaf ya shirya ya fita fuskarsa sai faman shiining take ,shi kadai yake sakin murmushi musamman idan ya tuno abunda ya Wakana a tsakaninsu. Ga baki daya ranar Beje ko ina ba yana tare da tahee da sai faman rigima take, masa akan ita bazata zauna a wajansaba,kanshi ba karamun daukan zafi yayi ba. 💖💖💖THE TALENT TROUPE 💖💖💖 Mss Lee 💖 07041879581 Book 1 Page 57 Tana idar da sallar isha’i tasaka rigimar bazata kara kwana a dakin ba sai dai ya mayar da ita wajan ammey,yasan abunda take cewa ba mai yuwa bane dan bazai taba yadda ba shima , a hankali ya kama hannunta da take kokarin kwacewa fuskarta a hade ta ki yadda ta kallesa,”am sorry please,ki canzamun wani punishment din amma banda wannan please, I can’t “,kuka ta fashe masa dashi”ai daman ka fadamun bakasona shiyasa kayi kokarin kashe nii, ni dai Allah ka mayar dani”,kwantaccen gashin kansa ya dan shafa kansa har ya fara yi masa ciwo, shi kadan yasan yanda kukanta ke cakarsa har cikin zuciyarsa, har yanzu zazzabinsa be tafiva shima,”look at me”, ya furta a hankali,kin kallansa tayi sai ma kara kawar da kan da tayi, gyada kansa yayi kafun ya taba button din rigarsa “ok shikenan kamar Kari kikeso bari muyi round two”,ba karasa zancan saba tayi saurin rike hannunsa da yake kokarin cire rigar jikinsa,hawaye har sun fara cika mata ido,yanda tayin ne ya so bashi dariya amma ya danne gudun karya kara janyowa kansa wani saban rigimar,a fili kuwa dan tabile bakin sa yayi kadan yana d’auke idanuwansa shima ,marairaice masa fuska tayi ashagwabe ta furta “kace mun fa bazaka kara ba”,be kalletaba ya cigaba da kokarin cirewa “toh yanxu na fasa tunta bakyajin magana “, da sauri ta girgiza masa kai” Allah inajin magana , tsoro nakeji “, yanda ta karasa dinne ya bashi tausayi, kara rike hannunta yayi kafun ya goge mata hawayenta “idan wannan hawayen suka kara sauka toh zanshanye kayana”,da sauri ta goge hawayen nata,”ya ciwonki fa”, kawar da kanta tayi kafun tace masa “Ni lapiya ta kalau”, Tohm shikenan zamu iyayin wani kenan” cewar king ,ynxu ma kanta ta girgiza masa “Allah ban warke ba wajan da zafi,kuma kace mun ka dena fa”, rungumota yayi a jikinsa “ am really sorry zawj, nayi leafi Amin afuwa, kinji, am so sorry “a hankali ta gyada masa kai”banaso ka dena mun kaji”, murmushi ne ya subuce masa a fuska Ba tare da ya amsa mata ba sai dan shafa mata bayanta da yake.”zaki iya tafiya”, kanta ta daga masa alamar eh, mikewa yayi shi yana miko mata hannu “let’s eat something kar ki wanta haka”, a shagwabe ta turo masa bakinta “uhm uhm bana jin yunwa “, lumshe idanuwansa yayi kafun ya kalli bakin nata “ you’re making me to ad more “, ai be kai karshen zancen nasaba ta rufe bakinta ruf,dariya ta so bashi amma ya Waske, taku ta somayi a hankali duk da zafin ya ragu makamar dazu ba, duk yana kallan yanda take tafiyar , da te makonsa suka karasa falon, da kanshi ya ja mata kujera kafun ya soma serving dinta, kadan taci tace ta koshi, be kyaletaba saida ya tabbatar ta koshi sosai kafun su koma ya bata magani. wajan wanciyama sai da yasha rigimar bazata kwana a dakin ba, saida yace mata ba abunda zai mata sannan ta yadda ya kwanta a gefenta amma taki yarda ya tabata, shima din be tabata har saida yaga tayi bacci kafun ya rungumeta a jikinsa yana kashe gabaki d’aya dum light din. ➰➰➰➰➰➰➰ Zaune su amrah suke a falon Ammeey gabaki d’aya yan matan su ke su 5, ihsan, sumayya, firdausi,amrah da basma , kowa yana sabgar gabansa, su ihsan suna zaune kan carfet din Ammeey lokacin ta tafi part din data, suna shan fruit jifa jifa suna hira, amrah na kwance kan 3 sitter , basma kuma na zaune kan 1 sitter kafa daya kan daya yayinda take latsa babbar wayarta sai faman ya tsine take, cikin da rigar da sumayya take dannewa ta dan kallesu kafun ta kashewa su firdausi ido d’aya da dan karfi ta soma magana “ Nifa yau banga sis tahee ba, ko da mukaje part din ta kinga yaya king yace mana bacci take ,Anya kuwa su yaya bari dai nayi shiru,” kyalkyalewa da dariya sukayi jin iskancin da sumayya take wa su amrah dan sunsan halinta , itama firdausi dariyar take dannewa” uhm ke dai bari , a yan kwanakin nan da muke zuwa part din ai kinga baya hade mana rai kamar da yanxu fa har gaisuwar mu yake amsawa amma da dane ai bamu isaba,” wata dariyar suka kuma saki , ihsan sai satar kallansu basma take da suka cika fam , daga karshema basma mikewa tayi tare da barin part din ba tare da ta tanka musu ba, amrah kuwa harara ta dunga sakar musu, tayi alkawari kuwa sai ta haddasa musu wutar da bazasu iya kashewa ba,tunanin abunda zata musu take kafun ta dan saki murmushin mugunta tana barin wajan ba tare da tace musu uffan ba suma . Suna ganin ta bar wajan suka tafa gabaki dayan su , ihsance ta soma magana “wallahi bamu da mutumci, kun iya tsiya, ku kalli yanda fuskar su tayi kamar wanda aka fadawa mummunan abu”, itama firdausi dora tayi “ rabu da yan iska wai su soyayya , in banda ma iskanci irin nasu su kalli kamar yaya king suce wai sai sun aureshi ko da bala’I ai suma sun kwasowa dala da ganmu”, dan murmushi sumayya ta saki” Aah feedy, so sone fa, Kema kinsani duk Wanda ya kalli zubin yaya king ,ko baya sansa sai yaji wani abu aransa ,musamman idan aka samu marasa tsoran Allah, ko ni kunsani naso yaya king kamar raina tun bansan Menene so ba, har zuwan amrah muka fara samun sabani akan shi, amma yanxu na hakura dashi har abada Sabida yayi mana nisa nesa ba kusa ba , ku duba ku gani fa wa ya taba kawowa zai auri sister , duk da irin abunda mukayi mata bata kullacemuba lokacin da mukaje mata, gaskiya masu irin halin sister kadan ne”, jinjina kai sukayi gabaki d’ayansu kufun ihsan ta furta “ Allah sarki AKHII Allah ya jikanka da rahma, har na tuna lokacin da idan yaya king zai hukunta mu zai hana sa , ko uktiii ta hanashi, ban taba sani yana jin maganar su ba sai lokacin da mukai masa lefi akhiii moha ya bashi hakuri shi da ukhti, sai gashi kuwa beyi mana komai ba , da Yaya kabeer ne ko yaya haroon ina tunanin rugu rugu za suyi mana , duk da suma suna tsoran yaya king sosai kamar sunga mala’ika “,gabaki dayan su saida suka shiga jimamin mutuwar akhiiii kafun kuma su fara bada labarin laifikan da suke yake tema kar su da Wanda king yake Zanesu ukhti ke cecensa.” Ku naji fa Ance sun kusa dawowa suma duk da sun makale a turai sunki dawowa gida ,amma naji ance boss yace su dawo nan da one week kafun ransu ya baci” dariya suka sani kin yanda feedy ta kira king da boss, “itama ukhti fa taji anacewa zatazo tunda batazo bikin yaya king ba , ni har na matsu tazo dan nasan dole ko yayane sai anyi mana dinner indai taso kuma yaya king nasan zai amince ko sabo da ita ne”, gabaki dayan su kuwa jin hakan sai suka fara tsara yanda abun zai kasance duk da basu da tabbacin hakan, sunayi suna dariyar kansu musamman in suka tuno yanda king zai ci ubansu. ➰➰➰➰➰ ➰➰➰➰➰➰➰ PART DIN DADA Ga baki d’aya manyan iyaye ne zaune a falon dada , shiru ko wannansu yayi yana sauraran dada, saida ta kai aya kafun abeey cikin girmamawa ta amsa mata” dada Insha Allahu nan da sati d’aya zasu dawo kamar yanda kikai magana akai, sauran yaran ma insha Allahu zasuyi Auran lokaci ne kawai beyi ba”sallallami dada ta saki” zayeedu,lokaci ne kace beyi bafa , ko dai Bakuyi niyar aurar dazu yanxu ba, Ance zankada zankadan yaya haka babu aure , da alokacin mune ai sai ace baki akai musu , mu duk wacce tayi girman haka ai bazata auru ba, ni dai nagaji inasan ganin jikokina suna zagayeni, Allah ya ji kanka mahamuda Allah ya gafarta maka nasan da kana raye da tuni na fara ganin yan jikokina”, tana kai karshen zancenta ta fara goge hawayen da suke kokarin fitowa, gabaki d’aya sai da tasa jikin kowa na falon yayi sanyi musamman Wanda ta anbata da kowa bazai taba mantashi ba a cikin rayuwar sa, lallashinta suka fara gabi dayansu,kowa yana tofa albarkacin bakinsa. Allah sarki ummey tun lokacin da aka anbato moha jikinta yayi sanyi , addua ta fara masa cikin zuciyar ta , tana kokarin dannewa, amma duk yanda taso boyewan sai da abeey ya ganota, yayi shiru ne kawai bece komai ba dan shima abun yana taba masa zuciya har yanxu.sai da aka gama tattauna na tsawan lokaci kafun mahma ta kalli dada ,toh dada kingama anbato kowa zaiyi aure bamuji naki ba,wani babban salati kaka ta dauka tana kallan mahma da kananan idanuwanta “yanxu auta da yake kin mayar dani kakarkii ni zaki kalla kice na kara aure , toh Allah ya shiryeki dan nasan yanxu ina bude baki masu yan uwa zasu tarar miki” murmushi kowa ya saki dan kowa yasan da su uncle saleem yake , dukda haka kuwa sai da ya tanka,”wannan haqqun ne dada duk Wanda ya taba auta zamu shigar masa “, dan ta bile baki dada tayi tana mikewa tsaye “ daga kai har itan sai na Hana na ci muku mutunci sai naga me shigar muku, ni kunga tafiya ta bacci zanje nayi ma” gabaki dayansu seda fase sukai mata har ta bar part din kafin su dan tattauna gabaki dayan su, ana gamawa kuma kowa ya ya wuce part din da zashi. ➰➰➰➰➰➰ ➰➰➰➰➰➰➰ 🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧 🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧 Yau ya kasance Friday kamar kullum kiran sallah azubane ya tashesa, yanxun ma hakan ce ta faru a hankali ya bude fararan idanuwansa da suka kara yin haske dasu gwanin sha’awa, kallan yanda take rungume a jikinsa yayi, yana san mikewa amma bayasan tashinta, gudun kar lokacin sallah ya wuce shi yashi raba jikinta da nashi kadan yana gara mata kwanciyar tata, Dan ya mutsa fuskarta tayi bakinta ature,”stubborn , kina baccin ma bazaki hakura ba”. Wanka yayi jikin brown din jallabiya da ta kara haska kalar fatar jikinsa , gashin kansa a kwance kamar na larabawa ya nadawa rawanin irin nadin larabawa, duk da fuskarsa ba a sake take ba amma wani irin annuri da annashuwane akan fuskartasa da ya kara wa fuskar tsa kwarjini da haiba, gabaki d’aya kamshin turarensa ma imperial majesty ya cika ko ina, hatta tahee dake kwance lafe kan gadon tana shakar kamshin turaren har cikin ranta.tun motsa warsa ta farko ta farka itama amma taki motsawa , yanxu ma tunanin yanda zata tashi take yi , fatanta d’aya Allah karyace yau ma a dakin zaiyi sallah. Yana kallan motsinta tun dazu yasan ta farka , karasawa yayi inda take kafun ya sunkuyo kadan yayi pecking kumatunta, ai kuwa da sauri ta ware idanuwanta akansa , dan Jan hancinta yayi kadan kafun ya furta “morning “,ya karasa yana tayata mikewa zaune, a hankali ta zuro kafafuwanta kafun ta mike tsaye, tana mikewa kuma ai ta koma tana rintse idanuwanta, ganin hakan yasashi saurin kamata” let’s me help you “, girgiza masa kai tayi,”zan iya, gashican ana kiran sallah kar jam’i ya wuce ka”,ta karasa tana kara mikewa kafun ta soma tafiya a hankali duk da yanda take kokarin daidaita tafiyarta,kallan kafar yayi kafun ya furta “ I have to check it again”, yana ganin shigewarta toilet din ya bar dakin bayan dan jotting din da ya bar mata a cikin wat small paper da wayarta a gefe. A toilet kuwa daurewa tahee tayi ta gasa jikinta sosai kamar yanda taga yayi mata kafun tayi wanka da alwala, sosai taji dadin jikinta kuwa, wani pink material mara nauyi ta saka a jikinta tare da feshe ilahirin jikinta da daddad’an imperial majesty me shegen kamshi, a hankali take yin komai , har ta idar da sallah tayi karatunta kafun , a hankali ta sake mikewa ta koma kan gadon, yar paper din data ganine yafi Jan hankalinta,tana daga gawa taga wani hadaddan handwriting me shegen kyau” take care of your self , I love you “, shine abunda ke jikin paper , bata san lokacin da ta fara murmushi ba ita kadai, rike paper tayi a hannunta kafun ta kwanta baccin da take ji na fusgarta, tun tana Hana kanta bacci har yazo ya dauketa gabaki d’aya . ****Yana shigowa ya tarar da ita kwance lullube da bargo ga kamshin turaransa da ya cika dakin sosai, doso inda take yayi yana kara jin kamshin turaran na kara karfi alamar Itace ta saka , yana sunkuyowa kuwa ga daki hancinsa, kwanciyarta ya gyara mata kafun yayi mata peck a goshinta. A maimakon ya koma bacci system dinsa ya dauka ya fara operating, ya dade akai kafun ya je ya dakko coffe dinsa , har zai kai baki ya tuna lokacin da barar da shayin tana cewa da akwai guba aciki, kawar da coffee din yayi ba tare da yasha ba, kiran wayar sa da akai ne ya dauka ganin me kiran, a hankali yayi sallama, kafun ya dan saki murmushi jin abinda taci kin wayar kecewa, ukhtii ya kike, banji amsar data bashi ba , sai dan murmushin gefen fuska da yayi kadan, sun dade suna tattauna a wayar kafun ya ajje wayar ga ba d’aya , aikin da yake a cikin system dinsa ya cigaba dayi har wajan 11 , har lokacin kuwa tahee na bacci. 11 :30 am ta fara mutsi mutsi da ido kafun ta bude idanuwan gabaki d’aya cikin hasken dakin, a hankali ta mike zaune babu kowa a dakin sai system dinsa da daya daga cikin wayoyinsa da ke wajan. Mikewa tayi da niyar yin wani wankan da brush taga wayarsa na haske kamar ana kira, sharewa tayi kamar zata wuce taga ta karayi, cikin karan bani ta dauki wayar tasa da niyar kaimasa,message din da aka turo masa ne ya dan dauki hankalinta, bata san lokacin data fara karantawa ba “SWEETHEART NAJIKA SHIRU,BAYAN KACEMUN KAYI MISSING”. saura kadan wayar hannunta ta fadi cikin karo da message din da tayi, a Daidai lokacin da yake shigowa cikin dakin hannunsa dauke da plate. Mss Lee 💖 07041879581. 58 Kallo d’aya tayi masa ta dauke kanta, a Daidai lokacin da wani message din ya sake shigowa, dan kallan Rubutun da akasawa baby da yar love a jiki tayi kafun tayi saurin d’auke kanta , batasan lokacin da ta jefa wayar kan sofa ba tayi shigewarta , kallan fuskarta yayi yaga ta dauke kanta gabaki d’aya,mamakin abunda tayi yanxu yayi kafun shima yadan fuske ya zauna kan sofa din, wayar da ta jefa a wajan ya kalla daidai lokacin da saban message ya kara shigowa, kamar zai share sai kuma ya dauki wayar, eyes dinsa ya dan ware kadan kan screen din wayar yayi kafun yayi saurin kallan kofar da tashige, maida kallansa yayi kan wayartasa, messages din dazu yagani da private number, alamu ya nuna ankalli message din sai wanda aka turo na ukun “Baby”, ya nanata a kasan zuciyarsa kafun ya saka hannunsa d’aya cikin sumar gashin kansa,” oh my god ,kenan wannan message din ta gani yanxu”,duk da kasancewar private number ce amma sai da number ta fito kan wayarsa , lips dinsa na kasa kawai yake dan taunawa time to time, sosai wani bacin rai ya bayyana a kan fuskarsa, ransa ba karamun baci yayi ba a zafafe yayi dialing wani number , ringing biyu aka daga kiran kuwa, ko amsa gaisuwar da na wayar yake masa Beba sai ma umarni da ya bada cikin kausashashshiyar murya” na baka daga nan zuwa lokaci kadan ka binciko mun wata number yanxun, koma wanene akawomun ita ko shi immediately “ “, kitt ya kashe kiran batare da yace komai ba sai forwarding din number da yayi, wani irin huci yake futar wa shi kadai, bayasan binta ciki, shiyasa ya zauna ,yanaso kawai ya kalli fuskarta , yanda ta bar wajan kuma har yanxu yana jinsa, wani irin bugawa zuciyarsa take, tsawan lokaci yana jirin fitowarta , ganin bata da alamar fitowane yasashi nufar kofar shima. ****Aban garan tahee kuwa tana shiga ciki ta fashe da wani saban kuka me cin rai, kuka take sosai kamar wacce akace wani abu ya sameta, ita kanta bazata iyacewa ga dalilin kukan nata , sai wani abu da takeji ya tsaya mata a makoshi, a hankali ta furta “ Baby ko,har da wani sweetheart , sai yaje su karata ai, har da wani nayi missing dinka”, dan karamin tsaki taja cikin bacin rai ta goge hawayenta, launin idanuwanta har sun canza daga launin fari zuwa ja , Wanka tashiga shaf shaf ba dadewa ta fito fuskarta kwata kwata babu annuri, gefe d’aya na wajan wardrobe dinsu ta bude take a wajan kayan Sawarta suka fito reras dasu gwanin ban sha’awa , a hankali take takawa Sabida har yanxu ciwan ta be gama warkewa ba,shiryawa tayi cikin doguwar rigar abaya me milk colour me kamar bazar bazar , sosai abayar ta zauna mata ajiki duk da bata kamata ba, babu abunda ta shafa sai dan mai da lipstick a bakinta kadan, wani mountain din turare ta fesa a cikinta kadan, take wajan ya bade da kamshin turaran, cikakken lallausan gashin kanta da ya kara rinewa baki sak ta fara tajewa a hankali, har yanxu ranta ba dadi musamman I missed you din da ya fi komai tsaya mata a rai. Tana cikin taje kan ya shigo dakin amma ko saudaya bata dago ta kallesa sai ma cigaba da abunda take takeyi,a hankali ya tunkaro inda take, tana gani yazo daf da ita ta ajje coom din hannunta zata bar wajan, hannu d’aya yasa ya tsayar da ita, kin kallansa tayi sai ma kokarin kwace hannunta dake yi, “why all this please “, ya furta a hankali, a kufule ta kallesa cikin jin haushin maganarsa ta furta” your sweetheart is waiting for you, so please leave me alone ka tafi wajanta”, kallan dan karamin bakinta yayi,kafun wani dan murmushi ya subuce masa a saman labba, wani haushin ne ya kara kamata, tayi kokarin fusgar hannunta amma ta kasa, matso da fuskarsa yayi Daidai tata yana bin kyakkyawar fuskarta da kallo” toh ai gani a gaban ta, me yayi saura”, bata san lokacin da ta zuba mishi idanuwanta kafun tayi nasarar kwace hannunta, kara riko hannun ta yayi tare da rungumota jikinsa, turaren jikinta dake ta shin kamshi ya fara shinshina,a tsorace take kallansa duk da haushin sa da take ji,”kina kishinta ne “,kara kuluwa tayi da maganarsa a zuciye ta furta “akan me zan yi kishi,karshe sai ka dawo da ina kusa da kai ai sai kuyi karshen soyayya”, ita kanta bata san lokacin da bakinta ya furta hakan ba, a zafafe ya daka mata tsawa” are you mad , ni kike fada wa haka, are you on your senses,”sosai ta tsorata da yanayinsa, ganin yanda ya har zuko mata ne yasata fashewa da kuka, duk da yanda kukanta ke sukan zuciyarsa haka y daure bata re da yace mata komai ba ya bar wajan dakin gabaki d’aya , zubewa a kasa tahee tayi tana kara fashewa da wani kukan , kamar wacce aka tsikara kuwa ta mike tsaye tare da goge hawayenta, fuskarta tawanko tare da gyara fuskarta , mayafin abayar ta yana akanta a matsayin dan kwali bayan ta tufke kan da kyar, wani turaren ta kara fesawa kadan kafun ta bar dakin itama. Zaune ta samesa kan d’aya daga cikin sofa din dakin idanuwansa a lumshe, wuceshi tazoyi itama fuska ba fara’a taji saukar muryarsa “ come back here , dawo ki zauna “ ya karasa zancan cikin sanyi kamar bashi ba, wajan da ya nuna matan ta koma ta zauna, a hankali ya bude idanuwansa, kallan yanda fuskarta take ba walwala yayi kafun ya dan sun kuyar da kansa , abincin da ya zo mata dashi ya dan iba ya kai bakinta, ba musu kuwa ta bude bakin, a hankali ya soma bata a baki har saida yaga ta koshi tukunna ya kyaleta,”nagode “ kawai tace tana kokarin barin wajan ya kamo hannun ta cikin nasa” please stop it, zuciya ta ba dadi”dan sunkuyar da kanta tayi kasa ba tare da tace komai ba” I don’t like it, inason naga daughter dina tada ba wannan va,inasan wacce takewa daddy wasa , take masa hira,take rungumesa,inasan ganin wannan smile din na fuskarta,musamman idan zata kirani dady,I need the old you,zuciya ta ba dadi,anytime na bata miki rai , tell me , ki fada mun, kinji”, maganarsa ta dan sanyaya mata zuciya , kanta ta daga masa kawai , “are you jealous “,kin bashi amsa tayi sai kokarin mikewa datayi ya mayar da ita” tell me are you jealous “bakinta ta turo kadan kasa kasa ta furta harda wani cewa baby, murmushi ne ya bayyana a fuskarsa kafun ya dan ja hancinta kadan yana rungumeta,” my jealousy wife,Nima ban santa ba and karkisa hakan aranki,sabida ke kadai ce a zuciyar TAHNOON zayed al_nahyan”,kafun ya raba jikinsa da nata”you look so beautiful,har da wani kumatu kika kara sai kace ne yaya biyu a ciki”, kunyar maganarsa taji kafun ta dan kallesa ,”inaso naje na gaishe dasu Ammeey “, ta fada a marairaice, hancinta ya karaja kafun yayi mata peck din daya sa ta dan lumshe idanuwanta,”as you wishes, amma ba yanxu ba sai na dawo daga masallaci,okay”, gyada masa kai tayi kafun ta furta “Allah ya kaimu”, ciwan ki fa, saurin Tashi tayi daga cikinsa tana furta “ni lapiya ta kalau”. Wayar ta tadauka kafun ta dauki plate din da taci abinci, zaiyi magana tayi saurin tsayar dashi, “zan iya “,lumshe mata eyes dinsa yayi kawai Batare da yace komai ba, ganin hakan yasa tabar dakin cikin tahunta a hankali. ******* ********* Tana sakko wa kasa ta tarar da komai a gyara tsaf tsaf sai tashin kamshi yake falon, tazo zata gifta wajan kitchen kenan taga shigen paper din da take ganin, da sauri ta dauke paper din ta cukwi kwiyeta a hannunta kafun ta kai plate din kitchen , tana budewa sakon da ta saba gani ta gani a jikin paper yau ma, gabanta ne ya fadi yau, tsoranta kar wani abu ya samesa,da sauri ta yaga paper din ta saka a shara gudun kar yazo yaga takardar ,kwanukan da ta bata ta wanke da kanta,abinci take san girkawa ,amma ta rasa me zata dafa, pounded yam ne ya fado mata a rai da miyar efo riro, murmushi ta saki yalwatacce , tuno da abincin oummanta. Doya ta dakko manya guda uku, ta feraye tare ta dora a kan wuta, kafun ta fito da Ganda, nama, kifi da kuma kayan ciki, gyarawa ta farayi cikin kankanin lokaci ta gama gyarawasu ta dora namanta a wuta , Ganda ma haka bayan ta gyara bushashshen kifinta, Attaruhu tayi greating shima kafun ta fara yanka albasa, Daidai lokacin da su firdausi keyin sallama, daga kitchen din ta amsa musu ,amaimakon su zauna sai suka bita kitchen din suma, sakin baki sukai suna kallanta ganin yanda take yanka uban albasa,”sister me nake gani haka , amarya da yin girki”, cewar feedy, murmushi kawai ta sakar musu, aunty feedy sannunku da zuwa,amsa mata sukai gabaki d’ayansu, cikin zolaya ihsan tace “sister amma yaya baya nan ko shiyasa kike tikar aikin nan, kar ya dawo ya tarar da ke haka yasamu tsallan kwado”, dan waro ido tahee tayi kafun ta furta “gashinan a bayanku ai”, ba ihsan da akai wa maganar ba ,gabaki dayansu zuyawa sukai a tsorace,dariya suka bata ta dan dara “wasa nake muku yana sama” wata ajiyar zuciya suka sauke kafun su ajiye mayafansu ,”yanxu me zamu tayaki dashi dan wallahi banshirya yin tsallan kwado ba,tukunna ma me zaki dafa haka ne, ya Wuna ya fara tsinkewa fa inaso naci girkin amarya”,cewar ihsan ,murmushi kawai take “pounded yam da miyar efo riro,”zaro mata idanuwansu sukayi”Menene shi kuma “ wata sabuwar dariya ce ta kamata amma ta danne kafun ta furta “ynxu dai a ina za a samu alayyahu please “, tunani suka fara kafun summy tace bari nasa anemo, cikin kankanin lokaci tasa kuwa aka kawo alayyahun da yawa, ganin doyar ta dafu ne yasata tsane ruwan kafun ta juyeta a flask gudun karyasha iska, message ne ya shigo wayanta dan short” take care of your self, karki famamin ciwona please,ki kula , I love you “, tana ganin message din ta fara blushing ita kadai, hade baki sukai su uku kafun su furga “Awwwwwwwwwqqqn” kunyace ta kamata, ta fara dariya kasa kasa, doyar suka fara daka wa tunda sun hanata yi , kujeran dinning din ta zauna tana nuna musu ynda zasuyi,ita kuma tana ta yasu murmulawa da kyau, ana gamawa tahee ta fara hada miyar efo riro, take a wajan wani kamshi ya karade ko ina , su feedy sai faman santi suke tun kafun su dan dana abincin.miyar ba karamun kyau tayi ba musamman yanda komai ya fito aciki,ainahin miyar efo riro ta yarabawa tayi da taji ganda,nama ,kifi, da kayan ciki.wani hadaddan cooler me shegen kyau aka dakko mata tazuwa sakwara guda uku a ciki sai miyar da ta iba itama ta ware da ban, kafun ta sakasu su fito mata da wasu flasks masu shegen kyau,abeey ta fara zuwa ba , sai su dada da ummey da Ammeey,sai taga kuma bata kyauta ba in baka kaiwa su mamy ba suma, suma haka ta zuzzubamusu, tasa aka kai musu,abunda tayi ya farantawa su ihsan rai sai suka karajin wani girmanta da kimarta ya kara shigarsu,bayan ankai ko wana part a babban tray ta zuba musu nasu gabaki d’aya suka zauna kan carfet suna cii, suna hira kwanin nan sha’awa, suna gama ci kara gyara gidan sukayi sabida kiransu da ake tayi a cikin gida.har zasu tafi ta roki alfarmar su jirata ta shirya sai su tafi tare , kallan juna sukai kafin su gyada mata kai, a hankali ya’ke taku har ta kai sama, suna ganin wucewarta suka gudu, ihsan ce me cewa” ban shirya yin tsallan kwado ba da Shan mari”, suma gabaki dayan su dariya sukai dan sun san zasu sha drama in sun koma. Wanka tayi shaf shaf ta shirya cikin wani material blue colour me plazo din wando blue white colour ,mayafin ta ma dark blue ne tare da takalmin ta, shigar tayi mata kyau sosai, kadan ta dan fesa turaransa da ta gani, wayarta ta fara dubawa amma bata gantaba,tunanin inda ta barta tayi kafun ta sakko down stairs, bata tarar da kowannansu a falon ba, sakin baki tayi tana bin falon da kallo, girgiza kai kawai tayi kafun ta nufi kitchen , wayarta data ajiye lokacin da suke aiki ta dauka tana barin kitchen din. Bata dade da zama ba ya shigo cikin falon sanye da light blue din yadi me shegen laushi , kwantaccen gashin kansa ya kwanto masa , gashin kansa sa faman shining yake baki kirin da shi, fuskarsa kwata kwata ba walwala amma ba a hade take ba, gabaki d’aya falon ya saje da kamshin turarensa da na tahee, bata san da shigowarsa ba , sai faman game take cikin wayar, jitayi an fiske wayar, a firgice ta mike zata gudu ko kwallan Wanda ya kwace wayar batayi ba, rike hannunta yayi kafin ya furta “it’s me, nayi sallama har na shigo baki sani ba”, ajiyar zuciya ta sauke tana dafe saitin zuciyarta dan ta tsorata,”kayi hakuri ban kulaba”,Kai ya daga mata kafun ya dan ware mata hannunsa , ba musu kuwa tayi hugging dinsa kamar ynda ya bukata “am hungry “, ya furta a fusge,”ka farayin Wanka sai na kawo maka abincin,” ta fada a rarrabe gudun karya ga zakewarta, ido daya ya kashe mata , “yo muje kiyi mun”, ai da sauri tayi baya tana ware masa ido,murmushin da ya saka dimple dinsa lotsawa yayi , tsayawa kallan dimples din tayi kamar taje ta saka hannu a wjan haka takeji,” matsoraciya kawai”, yana kai karshen zancen maganarsa ya haye sama, itama shaf shaf ta fito masa da abincin da ta girma tare da lemo me sanyi, ta hau masa dashi sama , bai dade ba ya fito sanye da wasu kayan daban sai faman tashin kamshi yake ,zubawa sarautar Allah ido tayi ta kasa ganewa shigarsa ta ynxu da ta dazu waccece tafi kyau take a wajan kuma sai taji wani kishi ya daki zuciyarta” yanxu kamar ynda yake ganin kyansa haka matan waje ma zasu gani kenan”, kamar yasan me ke ranta ,sai saura “You’re the only mine and I’m the only yours,” murmushi tayi ba tare da tace komai ba duk da taji dadin maganarsa. Waje ya samu kan wani dan chair me zaman mutum biyu tayi serving dinsa , bin abincin yayi da kallo kafun ya kalleta alamar Menene wann,”pounded yam with efo riro”, abincin ya ravawa zanci kenan yau,Kai ta daga masa alamar eh , tana gama serving din ta mike da niyar barin wajan ya jawota jikinsa ya dorata kan cinyarsa tare da saka hannunta cikin abincin, batace komai ba ta soma bashi abaki, lumshe idanuwansa yayi jin yanda dadin abincin ya ratsa masa baki, be ce komai harta kara sa masa wani abakin, nan ma still be ce komai sai da yaci sau biyar kafun ya dan kalleta,”wanene yayi abincin nan”,a da rare ta Kallesa,”nice “, dan tabile bakinsa yayi kafun ya ya mutsa fuska kadan “shiyasa beyi dadi ba aushe “sakin baki tayi tana kallansa kafun ta mike daniyar kwashe kwanukan abincin ya Mayar da ita,”your cook is the most amazing part,I love the test so much,inaso wannan hannun ya dunga mun abinci”turo masa bakin tayi kafun kuma tayi saurin daukewa, ganin lokaci na tafiya yasa ta cigaba da bashi abincin,duk ci daya sai ya dan tsotsi yan ya tsunta kafun ya saki, har ta kammala bashi a baki. 🫧🫧🫧🫧🫧🫧 Karfe 6:54 aka kara kiraye kirayen kiran sallar maga riba, sallah tayi har yanxu kuma bata cire hijab din jikinta ba sai kallan agogo take yi ita kadai, shigowarsa cikin dakin ne yasa ta mikewa da sauri ,”sannu da zuwa”, lumshe mata idanuwa yayi alamar amsawa , ruwa ta kawo masa me sanyi yasha,tsawan lokaci tana jiran taji yace su tashi ya kaita part din su dada kamar yanda yai mata alkawari amma sai taji shiru. Duk motsinta yana ankare da ita sai ma gyara kwanciya da yayi, ganin hakan yasa ta yin saurin magana”Yaushe zaka kaini part din su dadan”ta karasa masa a maraice, eyes dinsa ya waro kadan “Yaushe nayi miki alkawarin zuwa part Dinsu, ni ba inda zani dan nagansu”,sakar baki tayi tana kallansa amma duk da hakan bata sadu daba”dazu fa ka fada hakan”, toh shiknn amma da sharadi daya kinyarda”, batare da jiran jin sharadin ba ta amsa da sauri “eh na amince”, kyataccen murmushi ya sakar mata da ya sata tsarguwa, ganin hakan ya fuske tare da dauke kansa, “let’s go amma ba dadewa zamuyi ba “, da sauri tabi bayansa kuwa ya rike mata hannu, suna fitowa waje zaki ya bude masa mota, a maimakon yashiga sai ya zaga ya bude mata kafun shi ya shiga, satar kallansa zaki ya dungayi abunda be taba gani va, Kai tsaye part din dada suka shiga, duk Wanda ya kallesu zaiga alamar kwanciyar hankali da natsuwa a tattare da su, musamman yanda sukai matching da juna, ganin irin kallan da suke binta da shine yasa ta jin kunyarsu, sakin baki aunty tayi tana bin tahee da kallo kamar ta mayar da ita kitchen , mommy da mamy kuwa murmushi suke sakar mata dan ko dazu sai da mamy ta kara cin sakwarar da aka kawo mata dan ba karamin dadi yayi mata, gaishe da gabaki d’aya falon tayi cikin jin kunya, suma cikin kulawa suke amsa mata gaisuwar ta tare da yi mata godiyar abincin da ta basu kowa sai yaba daddadan abincin ta yake , amrah tuni zuciyarta ta tsinke ganin yanda a dan kankanin lokaci tahee ta wani irin murmurewa, ko ita data dade a gidan jikinta bata shining kamar na tahee, basma bata falon. Lokacin, TAHEE kuwa ko ajinkin sai ma dan hararar su ihsan dake mata dariya kasa kasa tayi ,kafun su koma gefe suna hira sai faman tsokanar ta suke, king kuwa ko a jikinsa waje ya samu ya hade ransa kwata kwata babu bara ‘a amma duk motsinta yana ankare dashi,har karfe tara suna zaune a falon. Ganin basu da alamar mikewa mahma ta koresu part dinsu, suna komawa koma wajan shi ya nufa, ita second floor ta nufa shikuma ya wuce 3rd floor , Wanka tayi shaf shaf sabida bancin da take ji na neman fusgarta, cikin wani guntuwar rigar bacci da bata boye komai na jikinta ba ta saka , har da kulle kofar Sabida kar ya shigo, ba dadewa kuwa wani bacci me dadi ya dauketa. Tana cikin baccin ne taji kamar abu na yawo a jikinta,bata motsaba sai da taji abun na mata yawo a Daidai mararta, a mugun tsorace ta farka, cin Karo da kyakkyawar fuskarsa ta soma ja baya tana hadiye yawun da ya tsaya mata da kyar,a mugun tsorace ta furta”’me kakeyi anan bayan dare yayi”, bece mata komai Sabida yanda idanuwansa suka fara canza kala sai faman lumshesu yake, hannunta yake kokarin rikowa tayi saurin mikewa tsaye tana Jan baya, a mugun tsorace take kallansa ganin shima yana bin bayanta, kara ja da baya ta dunga yi shima yana biyota , bata san lokacin da ta karasa jikin bangoma shima a Daidai lokacin ya karaso inda take yayi mata runfa, cikin muryarsa da tayi mugun Dusha shewa ya furta “ i need you now”. ******* Barkanku da Shan ruwa da fatan ansha ruwa lapiya , Allah ya amsa mana ameen.💖 Mss Lee 💖 07041879581 59 Da Sauri ta fara girgiza masa kanta cikin tsoro , kallan gefe da gefensa tayi ko zata ga hanyar guduwa amma kwata kwata bata da wannan chance din.”I won’t hurt you “ ya kara furta mata cikin dashashshiyar muryarsa, yanxu kam ta kasa magana sai girgiza masa kai take yi kawai da kyar bakinta ya iya furta “ bana so, da zafi”, please ya kara furta mata yana kallanta “ ina jin tsoro” ta fada hawaye har ya fara sauka daga cikin idanuwanta Sabida tsoro, fuskarsa ya daidaita da na ta kafun a hankali ya daga hannunsa zuwa kugunta ,sama ya farayi da hannun nasa , da sauri tayi saurin ture hannunsa daga jikinta,tana kara girgiza masa kai” banaso ka deana tabani, inajin tsoro”, a hankali ya furta “shikenan tunda kinaso na mutu, batasan lokacin da ta danko rigar jikinsa ba , a rude ta furta “baka da lapiya dady”, shiru yayi mata bece komai ba sai eyes dinsa da sukai jajawur yake lumshewa,”baka da lapiya “ ta kara tanbayarsa,still shiru yayi mata ba tare da ya amsa ba, goshinsa ta taba taji zafi rau, ta zaro ido,”jikinka da zafi kasha magani bari naje na kawo mata abu kadanci “, kallanta yayi batare da ya bata hanyar da take Nema ba sai ma kara kusanto ta da yayi ya zamto basu da sauran gaf, gabaki d’aya ya kareta ba’a ganinta.tana kokarin yin magana kawai ya rike hannunta daya tare da dorashi kan mararsa, mutuwar tsaye tahee tayi,jin kamar abu ya zungureta ne yasa ta tsorata tayi sauri zata jan ye hannunta amma yaki bata damar hakan sai ma danna hannunta da yayi a wajan yana Runtse ido,” I need the help here”,rawa jikinta ya fara kamar mazari kafun tayi masa murmurmur da ido” toh ni bani da lapiya “, “kinaso na mutu, da Sauri ta girgiza masa kanta “, please this once kawai bazanji miki ciwo ba , I promised to be gentle “Hucin jikinsa ne ya ke kara tsoratata ga yanda take jin muryarsa kamar Wanda yake cikin ciwo”please “,ya rada mata a kunne, kuka ta fashe masa dashi, dan iska ya furzar kadan ya na ja baya”it’s ok “, juyawa yayi da niyar barin wajan tayi saurin riko rigarsa,dan kallanta yayi zaiyi magana ta furta” karkamun da zafi,ina jin tsoro”,bata kai karshen zancen nata ba ya hade bakinsu waje daya. Wani irin kiss yake mata kamar zaa kwace masa ita,ya dau kusan 2 minutes yana kissing dinta ganin tsayuwarsu be masa ba yasashi daga ta kamar baby har lokacin kuma be saki Ba kinta ba, kissing dinta ya’ke idanuwansa a kulle ya’ke sarrafata, jikinta sai rawa ya’ke musamman yanda take jin wani abu na ziyartarta a hankali ya soma cire mata kayan jikinta kafun ya ciga ba da sarrafata, rigar jikinsa ya cire hannunsa d’aya cikin breast dinta yana matsalawa a hankali, yana gama cire rigar jikinsa ya kashe fitular dakin gabaki d’aya sai dumm light da ya bari mara haske, tsawan lokaci yana sarrafata a hakan kusan mintuna 20,kafun taheee tasaki wani gigitaccen kara. Ina ganin hakan nayi saurin barin dakin sabida kallan da king ya jefamun🥺ko rahoto bangama dauka ba🥱. After 2hours, kwance take a jikinsa sai faman shashshekar kuka take, a hankali ya fara shafa bayanta alamun rarrashi,ya dau dogon lokaci yana shafa mata bayan ta, da kyar yayi bude bakinsa” thank you zawj,and am so sorry , kin hakura”, ya tanbayeta da sigar tanbaya , girgiza masa kai tayi har yanxu hawayen be dena sauka daga idanunta va,dan waro idanunsa yayi kafun ya saki murmushi “ ok fine , zomuje kirama “, bata san lokacin data zuba masa idanuwanda yake taso su hada ba amma taki barin hakan sai yanxu,dan bugunshi ta soma yi a hankali ya saki murmushi kan fuskarsa kafun ya kara rungumeta a jikinsa gabaki d’ayanta “ in my life, I never thought I will be happy again, na dauka baxan kara kasancewa cikin farin ciki ba, the moment I saw him fire na konashi amma na kasa yin komai akai , I feel very lost that moment, I want to hug someone very tight and cry ko abunda nakeji a zuciya ze ragu amma ban samu ba, it’s so painful , the moment I saw you, duk wani nauyin da zuciya take dashi ya fara raguwa, I love you from the first, I love you from the moment , ban taba yadda da hakan ba sai lokacin da kika yi loosing memory dinki, and I never feel scared kamar yanda naga kin fadi jini na zuba akanki ba, my heart feel broke that day, please don’t ever leave me alone , I can’t leave with out you”, ta kasa yadda da abubuwan da take ji, hawayene ke fita daga idanuwanta amma duk da haka bataso ta Tashi daga cikin gigin baccin nan, bata san akan wa ya fara magana ba amma har cikin zuciyarta tana jin yanda zuciyarta take mata daci,irin dacin da take kokarin boyewa na batar mahaifiyarta tasan shima yana jin irin wannan abun, take a wajan ta rungume shi ajikinta, har yanxu hawayen da take be tsaya ba” cry, cry, cry dady, I will always be with you, duk lokacin da kake so kayi kuka zan rungumeka, kayi kuka kaji” murmushine ya subuce masa jin kalamanta tare da kara rungumeta “I love you “ ya rada mata a kunne, lumshe idanuwan tayi ba tare da tace komai ba, bata ankara ba taji ya daga ta gabaki dayanta sama,zaro idanuwanta tayi waje tare da rike bedsheet din gagam ganin babu kaya a jikinta, dariya yasaki me sauki kafun ya nade har bedsheet din ya nufi toilets dasu. A tare sukai Wanka duk yanda taso kubucewa sai da ya toshe hanyar, sosai ya gasata sai faman raki da shagwaba take masa, koda suka kammala wankan ma shiya saka mata rigar da yakeso, kokarin Kare kirjinta take ya rada mata “na ga komai “kunya kalmar tasa ta bata tayi saurin rintse idanuwanta, sama yayi da ita suka kwanta a kan bed bayan ya canza musu bedsheet “ wannan kunyar zata cuce ni fa “, kirjinsa ta dan taka kadan tana boye fuskarta a jikinsa,kafun ya rungumeta a jikinsa suna shakar kamshin junansu. 🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧 WASHE GARI Karfe 4:15 tana zaune a falo tana game a cikin wayarta taga sabuwar number na kiranta, tunanin number wacece take ganin babu suna a ciki, kamar zata share sai kuma ta daga kiran tare da karata a kunnanta, ta bude baki da niyar yin sallama kenan taji wani irin murya mara dadin ji na babbaka dariya , da Sauri ta janye wayar a kunnanta ,tare da bin wayar da kallo ganin still kiran be katse ba. Maida wayar tayi kunnanta yanxun ma wata shegiyar dariya taji an barke dashi, har zata kashe kiran taji wata muryar wata mace na kiran sunanta “TAHEERA MOHAMMAD “, dan zaro ido tahee tayin jin mayar ta kira sunanta “wacece ke “ tahee ta kara tanbaya a tsorace , cikin daka tsawa matar ta dakatar da ita “ sanin ko wacece ni bashine me anfani ba, kine santa kanki da masoyina , duk lokacin da kika kuskura wani abu ya kara shiga tsakanin ki da masoyina sai na kashe ki, na kashe sa, sannan na kashe miki banzan dan uwanki da uwarku baki d’aya “, da Sauri tahee ta tashi tsaye cikin matukar rikicewa “ kinsan Inda oumma ta da dan uwanta suke !? Suna ina !? Wacece da zaki shigo rayuwa ta!?”, wata shu’umar dariya aka saki a cikin wayar kafun kitt kiran ya katse , da Sauri ta shiga call log da niyar kara kiran number taga private number ba ta yarda za ai ta kira matar, safa da marwa tahee ta fara a cikin falon gabaki d’aya ta rikice, so take tasan wacece matar nan, kuma wana masoyi take nufi, a ina ta san oumma da taheer , tanbayoyin da suke faran birkita mata kwakwalwa kenan amma bata da amsar tanbayarta, ganin kanta na kokarin ciwo ne yasata samun waje ta zauna tare da dafe goshinta,”Ya Allah meke shirin faruwa dani, ya Allah kafini sanin abunda ke buye da abunda ke fili,ya Allahu”, yar karamar iska ta furzar a bakinta kafun ta fara karanta adduar da tazo bakinta, cikin kankanin lokaci taji kamar ancire mata wani abu acikin zuciya . Door bell din da aka danna ne ya ja hankalinta ta mike tare da nufo kofar,”wanene ta tanbaya a hankali, jin ba a amsa ba kuma ba a bata amsa bane yasata bude kofar kadan, “babu kowa , kunnena be ji Daidai ba kenan”, hannu tasa zata kulle kofar taga basma tsaye a kanta sai faman sakin huci take,dan murmushi tahee tasakar mata,”kece, Bismillah “ dogon tsaki basma ta saki tana jifanta da mugun kallo,”WACECE ke da zaki bani izinin shigowa yar matsiyata” ta karasa tare da jan wani dogon tsaki, kallanta kawai tahee ta tsaya yi kafun ta saki wani murmushin da ita kadai ta san ma a nar kayanta, bata kuma tanka mata ba ta koma kan kujerar ta, tana game din ta ta bar basma tsaye a wajan, mamakine ya kamata basma ganin irin wulakanci da tahee tayi mata “Lalle yarinyarnan wuyanki ya isa yanka , ina tunanin sai na fara gyara miki zama “, ta karashe zancan wata da nufar inda tahee take da niyar tsinka mata mari, tana daga hannun nata tahee tarikeshi tare da yarfarwa tana binta da kallan tara saura kwata” kar ki kuskura kazamin hannunki ya kuma gigin taba mun fuska, na so mutum taki amma naga ke ba irin wacce ake mutun tawa bace , to kishiga hankalinki,taheee da kike gani ba kauwan lasabace”, ta karasa zan can nata tana danna wayar hannunta. Sakin baki basma tayi dan ita bata taba kawowa tahee na da bakin da zata mayar mata da magana ba sai yanxu, musamman yanda take kallanta ba tsoro ko dar a tattare da ita , rasa abun cewa tayi kawai ta juya ta bar part din, kusan mintuna goma aka kara knocking, a tunaninta basma ce ta bude “me…” bata kai karshen zancen ta ba tayi saurin rufe bakinta ganin wanda ke tsaye bakin door din, matsa mishi hanya tayi y shigo kafun a hankali ta furta sannu da zuwa , lumshe mata idanuwansa yayi ba tare da ya furta mata komai ba , “ you look beautiful “ya fada a hankali hannunsa daya na bayansa tun shigowarsa be Fito dashi ba , zufar daga gani a goshinsa ne yasata kama hannunsa , yayi saurin kara boye hannun da ya fara Jini kadan kadan ,da sauri ta kallesa tana so taga Menene a hannun da yake boyewa, “get me a hot coffe now , ok”, jinjina masa kai tayi , tare da nufar kitchen shi kuma ya wuce sama direct, harta dakko zata hada coffe din sai kuma zuciyarta taki Amin ta da kayn hada coffee di , a gaggauce ta hada tea me zafi a dan karamin tray, tana nufar kan step taga digon jini a kasa , bin digon Jinin tayi da kallo kafun ta kalli jikinta bataji ciwo ba ita, tunanin yanda ya dunga boye hannunsa ne ya fara mata a rai, cikin dingishin da take yi tayi saurin karasa hawa sama ,koda ta shiga a tsaye ta samesa hannunsa kare da waya da alama waya yake, ga hannunsa daya da tafun hannunsa yake a daure kamar Wanda aka yiwa dressing, bin hannun nasa take da kallo har ta karasa shigowa cikin dakin, nuni yayi mata da ta zuba masa kafun ya zauna a bakin gadon dakin, ba musu kuwa ta hada masa cikin dan madaidaicin cup, hannun da ya ji ciwo ya mika mata, kallan hannun ta tsaya yi ba tare da ta mika masan ba,shima be ce mata komai ba ya cigaba da wayarda yake a hankali, a maimakon ta kara basa a hannu sai ta kai masa cup din Daidai saitin bakinsa, hannun da ta miko ya rike tare da dorasa a cinyarsa, har lokacin wayar na kare a kunnansa, cikin rada rada ya furta “feed me”, ba musu ta fara bashi a hankali duk da yayi mamakin ganin ba coffee bane amma be ce komai va, kadan yasha tea din kafun ya dauke kasan “ok bari na bata”, ya fada yana mikawa taheee wayar, da ido tayi masa alamar wacece, shima da ido yyi mata nuni da be sani ba , karbar wayar tayi tare da karawa a kunnanta tare da yin sallama , daga cikin wayar ma wata zazzakar muryace ta amsa mata sallamar, da sauri ta dago tana binsa da kallo gabaki daya yanayinta y canza jin da mace yake waya,a hankali ta furta “ ina wuni” tana d’auke idanuwanta daga kansa, a dayan bangaran ma amsa mata akai cikin raha da murmushi tacikin wayar ta fara cewa “amarsu ta ango, gaskiya kinyi leafi babba , koda yake ba lefin ki bane lefin mijin kine da yana bari kina zumunci da kowa “, dan murmushi tayi kawai tahee tana satar kallansa kadan kadan, “nasan baki sanni ba ko, karki damu ba budurwarsa bace , Akhii bashi da budurwa sai mata daya kwallin kwal Insha Allah “, duk da bata san wacece ba amma lokaci d’aya taji kunyar matar ta kamata , murmushi ne sauti matar tayi kafun tace mika masa wayar, da sauri kuwa ta mika masa zata tashi ya riketa tare da saka wayar a handsfree,” akhiii naga alamar wannan amaryar taka kunya ce da ita kamar fulani, na kusa zuwa nigeria ai ,”kallan tahee data lumshe ido yayi kafun ya furta “tana jinki ai “, waro ido waje tahee tayi kafun ta dan bigi kirginsa “ouch” ya fada a hankali ,kitt yaji an kashe wayar, dariya ce ta kusa kufce masa dan yasan dalilin da yasa ta katse kiran.”she’s my ukhtii, nasan baki santa ba amma zaki ganta soon”, daman kana da yaya, daga mata kadai yayi “and also a brother “, suna ina “long story amma zan fada miki bayan zuba “, gingina masa kai tayi kafun ta kalli hannunsa , Menene a hannunka , kallan hannun yayi kafun ya furta “ouch , na fama ciwona “ bata san lokacin data kamo hannun ta fara hurawa ba, kallan yanda take hura hannun yayi kafun ya lumshe idanuwansa, light din dakin ne ya dauke duka zatayi magana wani irin haske me kala kala ya cika ko ina na wajan, kafun wani music da yake tashi me sanyi da ba a ji, a hankali haske ya fara karuwa da kanshi, zaunar da ita yayi akan gadon kafun ya tsugunna har kasa , waro idanuwanta tayi zata mike ya girgiza mata kai tare da dakko wani abu acikin da box dan karami, wani dan siririn diamond ring ya fito dashi kafun ya kalleta “ will you be my wife for ever “,kasa magana tahee tayi sai binsa da kallo da take , ta rasa wani irin farin ciki zatayi yau Itace king ya tsugunnawa a kasa yake so ta zama matar sa , rawa hannunta ya fara ta rasa wani irin tunani zatayi, har yanxu kuma yana tsugunne a kasan, kuka ta fashe masa dashi kawai kafun ta fada jikinsa tana cigaba da kukan, tapping bayanta yayi “I love you thousand of times , I love you thousand of years, you’re my heart, my soulmate, my happiness ,every moment I spend with you is my favorite, being in love with you is the best feeling,I hope to spend all my tomorrows chasing your perfect smile , just one message from you is enough to brighten my whole day, my lips are missing the taste of your lips ,my heart forgets how to beat every time you laughed,if loving you is madness , I don’t even want to be sane”, be karasa ba yaji saukar tattausan lips dinta a cikin nasa, gabaki d’aya notukan kansa ya kulle, wani irin dadi ne yake ratsa duka gangan jikinsa , yanda take kissing dinsa ne yafi komai tafiya da imaninsa, wani irin kiss take masa me tsayawa a rai, ta dau good 5 minutes tana zautar dashi kafun ta zare bakinta, gabaki d’aya wani irin. Kunyarsace ta kamasa ba, bata gama dawowa tunanin data fada ba ya kara hade bakinsu waje daya yayi shima tare da bata kyautar zazzafan kiss, cikin muryan kuka ta furta “thank you”, shhhhh yace mata , “don’t say anything please , lokacin sallah yayi will you help me , inaso nayi wanka”, ya karasa maganar tasa yana so su hada ido,jinjina masa kai tayi a hankali zata mike ya riko hannun ta d’aya tare da zura mata zoben diamond din” I love you sweetheart “, kulle fuskarta tayi cikin jin kunya tare da barin wajan, shima mikewar yayi yabiyo bayanta, lokacin da ta gama setting din komai na toilet din, tazo zata fita ya kulle kofar tare da maidata ciki “ tare zamuyi, I’m a baby now , ni kiyi mun wanka “, marairaice masa fuska tayi “na yi Wanka fa”kwaikwayar yanda tayi yayi shima “uhm uhm kinga bazan iya wanka da kai naba”, sakin baki tayi tana kallan ikon Allah kamar bashi ba , duk ynda taso ta kufce masa , sai da ya toshe hanyar, sai da ya gasa mata jikinta sosai dan dole sukayi wanka tare duk yanda take kare jikinta da gangan yake tabota da ta bude baki zatayi magana sai yace mata “naga komai ai”, ganin lokacin sallah na kokarin tafiya ne yasa cikin gaggawa yayi musu wankan tare da dakkota kamar wata baby, kaya kawai ya saka sai turare tare da nufar masallaci, itama sallar tayi har sai da ta jira isha’i , tana idar da sallah ta fashe da kuka ,ko a mafarki bata taba kawo Waranta zatayi farinciki ba , duk da bata cire rahama daga rahamar ubangijiba, kukan abu biyu take yi, Allah ya bata mijin da yake santa ba tare da yayi laa kari da wani na kasu na jikinta ba,ya kaunaceta, ya sota, ya taimaketa alokacin da take neman temaka,tabbas ta cika me sa’a , oummanta da taheenta kullum tana musu addua Allah ya bayyanasu, tasan bawa baya wucewa kaddararsa , har yanxu bata karaya ba wata rana zata gansu, gudun karya dawo ya ganta a hakane yasa tayi sauri ta wanke fuskarta tare da gyarata , light food ta hada masa , lafiyyayen Dankali tayi masa da yaji zogale da kifi gabaki d’aya part din ya kare da kamshin abincin. Yana dawowa kai tsaye kitchen ya nufa shima, a jikin kofa ya tsaya ganin tana gyara wajan da ta bata, ganin bata kula da zuwansa bane yasashi takowa a hankali ya rungumeta ta baya, zatayi ihu kenan ya rufe mata baki” matsoraciya kawai” ajiyar zuciya ta sauke “ka bani tsoro” sorry dear, me kike a kitchen kinsan ciwanki har yanxu be warke ba” kauda kanta tayi kafun ta furta “ni lapiya ta kalau”, murmushi ya saki me sauti kafun ya furta ,”shikenan ki shirya anjima zan baki baby” baya taja tare da fara yarfa hannunta daya “ban warke ba fa” uhm uhm kin ce mun fa lapiyar ki kalau, karamin bakinta ta turo masa kadan “ni wasa nake “, uhmm this your lips ko unmm “ ai be karasa ba tayi saurin barin kitchen , sai da tayi nesa dashi kafun ta furta “your food is ready “, uhmmm “my baby is on his way baby”, ya fada a zuciya tare da bin bayanta, tun kafun ta fara serving dinshi kamshin abincin ya cika masa hanci, da kanta ta bashi a baki kamar yanda ya bukata, sosai ya yaba da amincin sabida yanda yaji dadin girkin, yana ci yana sa mata albarka, saida ya kammala cin abincin kafin ya bata tukwicin dalleliyar prado sabuwa baka kiran me shegen kyau, farin cikin da take ciki ya kasa misaltuna , ta rasa me zatace, Godiya zata fara yi masa ya dakatar da ita ,bata gama shiga shock din motar ba sakamon papers din da ya bata, fara dubawa tayi amma bata fahimci komai ba sai kallansa da tayi, ware su yayi zuwa gida biyu, gabaki d’aya gift dinta da aka bata na biki ya nuna mata, tun daga kan takardun jirginta, da mall dinta , da gida da motocin da ta samu, suman zaune tahee tayi ta kasa kwakkwaran motsi kamar a mafarki” this one is for your studies , Monday zaki fara zuwa school insha Allah”……….. **** Ayi hakuri da mss lee kwana biyu 🥱🥹 GIDAN AUNTY Mss Lee 💖 07041879581 BOOK 1 Page 60💖 She was so speechless, gabaki d’aya ta kasa magana, ji take komai kamar a mafarki yake zuwar mata, bata san lokacin data rungumeshi ba tana sakin wani saban kuka me taba zuciya , ta rasa wani irin farinciki zatayi,sai kara rungumesa da tayi so very tight, murmushi ya saki yana hugging din ta back shima, a hankali ya fara shafa bayanta alamun rarrashi,”it’s ok , banasan wannan kukan please “,ya fada a hankali, duk da ta jishi hakan besa ta dena kukan ba sai ma kara masa karfi da tayi, ganin kukan ba me karewa bane ya hade bakinsu waje d’aya, bata hanashi kusan mintuna biyu kafin ya janye bakinta yana kallan yanda fuskarta ta baci da hawaye, tissue ya dauke ya fara goge mata hawayen amma duk da hakan ta kasa tsayar dashi,” i don’t like , stop it ok”, girgiza masa kai tayi a hankali zata bude baki ya dakatar da ita,”don’t even start it, banaso “, magana zata karayi ya girgiza mata kai tare da langwabar da Kai kadan “dady want to sleep”, murmushi ne ya subuce mata, ta saki dariya kadan,”Allah ya albarkaci rayuwanka, yasa ka fi haka,Allah ya cika maka burinka na duniya da lahira,Allah yasa ka gama da duniya lapiya , yanda ka sani farinciki Allah ya baka masu saka farin ciki fiye da haka “, batayi auneba sai ji tayi yayi sama da ita , da paper din hannunta,direct upstairs ya nufa da ita, be sauketa a ko ina ba sai akan wani bed me shegen kyau, daki ne babba a second floor sai faman tashin kamshi yake,takardun kuma ya sa mata cikin wani lock me anfani da turn print, “dare yayi, we have to sleep “, sai yanxu wani tsoro ya bayyana a fuskarta ganin zasu kwana waje daya , amma duk da hakan tana kokarin danneshi,dan tayi alkawari bazata taba hanashi a bunda yake so ba, ya na shiga toilet ta fashe da wani saban kukan farin ciki,dama oumma da taheer sunanan, nasan da sunfi kowa farin ciki da koma wata makaranta, cikin sauri kuma tayi istigfari tana goge idanuwanta gudun karya fito ya ganta tana kuka, ko da ya yafito kallo daya yayi mata yau dauke kansa, itama tashi tayi tashiga wankan, kayan da zata saka ta fara tunani tunda bata taba kwana a cikin dakin ba, tana fitowa taga wata red din Riga a ninke tare da yar karamar paper ,” wear it please “, tana daga rigan ta zaro ido waje sabida ganin ba ta inda jikinta zai rufu a cikin, rigar tayi shara shara da yawa sosai sai wani dan siririn pant, duba wardrobe din Wajan tayi taga duk manyan kayana ne a wajan babu ta yarda zata sasu yasata yin shahada ta saka kayan, ita kanta saida taji kunyar kanta sabida yanda jikinta yayi mugun fitowa,ganin bazata iya shiga cikin bedroom din ba ysa tayi zamanta a cikin dressing room din. A bangaran king kuwa tana shiga , ya dauki wayarsa da aka turo masa abu ta cikin email, abunda aka rubuto ya karanta kafun ya dauki wani number yayi kiranta, ringing 1 aka daga wayar kamar ana jiran tsammaninta tun tuni, bai amsa gaisuwar da na wayar yake masa ba sai ma tanbayar da ya jefo masa “ ansamo details din inda suke”, banji me akace masa ba tsawan mintuna biyar kafun ya furta “ duk inda suke a binciko su, few days kawai na baku”, yana kammala zan cansa ya kashe wayar, abun hannunsa dake yawo ya dan kalla, me harafin M and T, abunda suka faru tsawan shekarune suka shiga yawo a kansa, take a wajan wani masifaffen ciwon kai ya kamasa, ya dade yana addua kafun ciwon kan ya lafa masa a hankali, lokaci ya kalla ganin har yanxu bata fito bane yasa shi bin bayanta, a hankali ya tura kofar, tana zaune kan wata kujera bacci ya dauketa, kallan yanda rigar ta fito da ainahin jikinta yayi kafun ya saki wani murmushi me kayatarwa, sosai ya ke bin surar jikinta da wani irin mayataccen kallo, ganin abunda yake san dannewa yana kokarin ta somasa ne yasashi saurin kauda ido, tare da daukarta a hankali, a zabure ta ware idanuwanta , kafun tayi saurin kullesu ganin rigar dake jikinta tana kara kankame jikinta, bece mata komai ba har ya kwantar da ita kan fadon, da wani irin mugun sauri ta kashe Wutar dakin tayi saura lamp,dariya ce taso kamasa da har saida murmushi ya bayyana a fuskarsa duk da kasancewar da duhu, gefen gadon ya zauna tare da jawo ta jikinsa, kokarin zame jikin ta take sanyi amma ya kara kankame ta,”ouchhh” da sauri ya kalleta ganin yanda take runtse ido, duk da a duhu duke ,”ciwo na”, ta fada a hankali,”am sorry bari na duba wajan”, kafun ya kai karshen zancen sa ta dora hannayenta biyu akan bakinsa Dan bata bukatar jin karshen maganarsa,”ok am sorry ,bazan karayi ba sai wajan ya warke ,ok”, ya fada yana dora kanta akan kirjinsa, aziyar zuciya tahee ta fara sauke lokacin da yake shafa mata baya,” sleep tight, I love you “, ya fada yana kara rungumeta,”same “ ta fada a hankali duk da batayi tunanin zai jiba, “ I won’t force you!!!!!! But Inaso nasan soyayyar da kike mun”dan dagowa tayi ta kallesa kafun ta kara dora kanta akan kirzinsa batare da tace komai ba, shima be damu da tayi maganan ba shiyasa ya cigaba da shafa bayan ta,bata dau dogon lokaci ba wani daddadan bacci me shegen dadi ya dauketa, ajiyar zuciya king ya sauke yana kara gyara mata kwanciyarta “ I love you to the moon and back sweetheart “, ya fada tare da sunbatar goshinta,addua yayi musu kafin shima wani bacci me dadin gaske ya daukesa. 🫧🫧🫧🫧🫧🫧 After 5 days, wata iriyar soyayya king yake nunawa tahee me tsayawa arai, tun yan gidan basu fuskanta ba har kowa yagane irin soyayyar da yake mata, a tsakanin su abeeey da ummey kuwa baza ace ga Wanda yafi nuna farincikinsaba, ummey har da kuka dan ganin d’anta ya fara samun farincikin da ta dade take biri ya samu, ammey ma sosai take jin dadin ganin yanda son dinta ya fara dawowa kamar rayuwarsa ta da, dada kullum cikin sa masa addua take Allah ya kawo mata jikokinta nan kusa, duk lokacin da ta fada hakan kuwa sai dai ya kalleta amma har cikin zuciyar sa yanajin dadin adduar, a fili kuwa sai dai ya dauke mata kai, sau da dama saida tace munafurci dai babu kyau Allah yasa ba jaraka kake zuwa kana yiwa yarinya ba. A cikin yan kwanakin nan kuwa wata iriyar shakuwace ta shiga tsakanin ta dasu ihsan duk da kasancewar sun dan girmeta, amma hakan be hana su ki girmamata ba a matsayinta na matar yan su, sau da dama indai basu da lectures toh suna ban garantane, wani lokaci kuma a part din su dada suke zamansu, duk tsawan kwanakin nan bata ganin amrah da basma, duk da yawancin lokaci ta naji su ihsan na maganar zaman dakin da take yi yanxu musamman da taji motsun king ko me take bari take ta gudu inda bazai ganta ba,ta bangaran basma ma ta koma gidan wata aunt dinta acewarta zatayi mata kwana biyu ne itama, babu Wanda ya hanata, kwafa kwai tayi ita kadai Tasan abunda ke cikin ranta, a cikin kwana biyar din nan small mom da mahma kowa ya koma gida suma, gabaki d’aya family din babu Wanda beyi missing Dinsu ba, rigimar da zoya tasa akan zata bi small mom ne yasa itama aka tafi da ita, yanxu gidan ya rage saura su kadai. Yau ya kasance Saturday, Daidai da saura kwana biyu tahee ta fara zuwa makaranta. tana zaune kan 2 sitter cikin shigar kananan kayan da ya sabar mata, dan karamin plate din fruit ne a hannunta take yankawa ,lokaci zuwa lokaci tana sashi a bakinta, tun bayan tafiyar kulu take zaune akan 2 sitter din bayan bacci da ta dade tanayi akan, ringing din wayartane ya mayar da ita cikin dogon tunanin da ta fada, private number ne babu suna kwata kwata a jiki, gabantane yayi wani irin wawan faduwa, sabida mafarka da take yawanyi akan kiran, kamar karta daga sai kuma wani bangare na zuciyar ta ya bata goyan daga kiran, cikin sallama ta daga kiran , bata karasa sallamar tata ba sabida wani gigitacciyar karar da yasa tayi saurin cire wayar a kunnanta na yan sakanni kafun ta mayar da wayar a hankali, wani irin dariya mara dadin ji aka dauke dashi me ban tsoro kafun cikin hade rai taji an soma magana “Ba a mun taurin mai, duk Wanda yayi kokarin bujurewa umarnina ina kashe sa kamar sauran ne, kwanaki kadan na baki ki kashe mun mujin ki, dan jinin jikinsa mallakina ne ni kadai, idan kikai sabanin hakan kuwa ki tabbatar da samun gawarwakin mahaifiyarki da dan uwanki dan zan musu kisa irin kisan wulakanci ne , na turo miki sako ki duba “ kitt aka kashe wayar, TAHEE da ke zaune duk launin idanuwanta sun canza zuba launin ja me ban tsoro, wani irin tsikar jikintane taji yana tashi a jikin, cikin sauri ta bude private number din da babu suna ko daya a ciki,” KILLED YOUR HUSBAND “ wani irin gigitacciyar kara ta saki tare da jefar da wayar, gabaki d’aya launin idanuwanta sun canza zuwa launin ja, girgiza kai ta somayi kafun tayi ball da wani tanbuwal din glass me shegen kau, fashewar sa yayi Daidai lokacin da king ya bude kofar, da mugun sauri ya shigo falon,inda take ya nufa, cikin wata iriyar murya me amo ta dakatar dashi, “me nayi musu, me nayi musu,kaje ka kashe su dukansu bana san su mugayene,” da mamaki king yake kallanta ya rasa gane me take nufi shiyasa yayi yin kurin zuwa wajanta, wani gigitaccen ihu tahee ta saka, launukan idanuwanta na kara canza wa , cikin wata siririyar murya ta furta “ sun kashe mun NONNA,SUSAN, SUN KASHE MUN SIF DINA, Nima sun kashe ni , ka fada mun Menene laifin mu da suke san hallakamu “, kallo daya king yayi mata ya fahimci ba taheen sa bace, fuskarsa ya hade kicin kicin ba alamar fara’a yace kalleni”, amaimakon ta kallesan sai ta kuma dukar da kanta kasa, cikin gigitacciyar tsawa ya furta kalli cikin idona ynxu “, fashewa da kuka tayi tana girgiza kanta , ganin hakan yasashi yin taku daya, a mugun zabure tahee ta danki wukar da take ynxu apple da ita…. GIDAN AUNTY 07041879581 BOOK 1 Page 61 Tsayawa yayi a inda yake gabaki d’aya hankalinsa ya gama tashi ganin ta da wuka a hannunta, kalaman dazu take ta kara maimaitawa,gyada mata kai yayi shima “ ok zamu rama muma amma bani wukar nan tukunna”, kin bashi wukar tahee tayi saima fashewa da wani saban kukan tayi, jikinshi har rawa yake dan ya gane ba ita kadai ce ba, tsoransa karsu cutar da ita, sunan dazu da ta kira ne ya fado masa kafun ya kalli yanda take faman hada gumi duk da sanyin Ac dake fitowa, bayanta ya kalla kafun ya furta “NONNA”, da sauri ta juya tana sakin wukar hannunta, yana gani ta juya taku biyu yayi ya damki Dan tsan hannunta, kara ta sakar masa sai faman fusge fusge take ita kadai, wata iriyar gigitacciyar tsawa ya daka mata yana hade fuskarsa kamar bashi ba, “ki nutsu”, ya furta cikin kausashshiyar murya , nutsuwar kuwa tayi tana sun kunyar da kanta, “ ya sunanki “, shiru tayi tana kara sunkuyar dakanta, “karki bari na sake maimaita tawa “, cikin shashsheka ta furta “sunana LOLA”, dan kallanta yayi jin tayi magana da wata iriyar murya”wacece ke , me yasa kika shiga jikin mata ta”, yanxu ma shiru tayi masa, bece komai ba kafun a cikin dan daga murya yayi Bismillah, rawa jikinta ya fara ,” ah ah zanyi magana ka bari dan Allah “ ta fada cikin rikicewa, banza yayi mata kafun ya fara karatun alkuranin, yanxu kam ihu ta sa masa tana rokonsa karya konata, zaunar da ita yayi kan kujera har yanxu hannunsa na rike da nata kafun ya dakko wani bottle water da ke gefensa ya ajje mata a gabanta, da sauri ta saka hannu zata dauka ya matsar da ruwa nesa da ita “ ruwa , ruwa “ ta fara fada , “zakisha”, ya furta , bata jira ba ta amsa masa da Sauri” zan baki ruwa idan kin gama amsamun tanbayoyina, sabanin hakan kuma zan kona kine “, wacece ke, me yasa kika shiga jikin matata”, cikin wata iriyar murya ta fara kuka , “ ba cutar da ita nake ba, te makonta nake, suna san Kasheta ne kamar yanda suka kashe mun ahalina”shiru yayi na yan sakanni kafun cikin kausashshiyar murya ya furta “Menene hadinki da matata, sannan menene alakar ku da matata da zaki shiga jikinta”, ina bata kariyane kamar yanda Nima ta taba temakona a lokacin baya,ni ba muguwa bace, suna harin rayuwar tane”, su wanene” da mugun firgici ta kallesa , zasu kasheta kamar yanda suka kashe shi, bazan iya va”,wani irin rawa jikinta ya fara,”ruwa !!ruwa!!”, ruwan ya dakko kamar yanda ta bukata amma be bata ba,”banasan jin wannan tatsuniyar taki, kar na sake ganin ki a jikin matata, idan va haka ba zan konaki da ayoyin uban giji, ki gaggauta fita daga jikin matata yanxun nan”,kanta ta daga masa tana rike makoqwaranta, ruwan ya mika bata da mugun sauri ta fara sha, saida shanye duka kafin ta fara sakin ajiyar zuciya,”zan fita daga jikinta, Kai ma nagode da yanda kake kular mun da ita,nasan kana kula da ita amma ka nunkashi sabida kokarin kasheta da suke yi, ganin komai nasu ya fara lalacewa,ka kula da ita “, tana gama fadar hakan tahee tayi atshawa me karfin gaske,kafun ta sulale ta fado kan king da yayi saurin tarota, cikin zafin nama ya dauke tare da kaita cikin bedroom, kallan yanda take bacci peacefully yayi, kokarin kawar da tunanin yun kurin kashe masa mata da akace yake, iska ya furzar a hankali kafin ya furta “ it’s a lie”. System dinsa ya dauka bayan ya canza kayan jikin sa, ya jima yana operating a kanta,lokaci zuwa lokaci yana kara dubata duk da yana kusa da ita, kiran sallah la’asar ne ya tayar dashi, kan gadon ya karasa har yanxu bacci take peacefully abinta, goshinta ya danyi pecking kafun ya bar dakin. Mintuna 15 da futarsa ta fara motsa idanuwanta kafun ta budesu gabaki d’aya, mamakine ya kama ganin ta kwance akan gado, wayar da akayi mada da text message ne kawai ya fado kanta, duk yanda zata tuna zuwan ta kan gadon ta kasa, sakkowa tayi daga kan gadon bakinta dauke da addua, agogon dakin ta duba, 4 ta wuce da sauri tashiga toilet kafun ta fito ta kabbara sallah , tana Idarwa azkar dinta tayi kafun ta mike , kara kallan agogo tayi mamakinta har yanxu be dauke ba ganin be dawo gida ba, dan karamun bakinta ta turo waje kafun ta bar dakin, shima falon shiru alamar ba kowa a ciki,3rd floor ta hau nan ma shiru sai ac da kamshin turaran da ke buso dakin,dacin da bakinta ya somane yasata nufar fridge din data gani, tana budewa kuwa idanuwanta ya sauka kan kayayyakin ciye ciye dake shake a ciki, fiye da saurin fridge din, wani abun ma bata taba ganin saba, strawberry ice cream din data ganine yafi daukar hankali, janyoshi tayi tana sakin wani murmushin jin dadi, waje ta samu akan gado tana shan ice cream din, tana sha tana sakin dariya sabida yanda dadin ke ratsa mata kwakwalwa, idanuwanta ne suka sauka kan wata yar karamar roba dake kan bedside dinsa, ajje Ice creams din tayi tana janyo robar “ANTI DEPRESSANT” shine abunda aka rubuta jikin robar, har zata mayar sai kuma ta fara karanta abunda ke jikin robar, da wani irin shock ta mike tsaye, tana karanta abunda ke jikin robar, wasu hawayene suka fara sakko mata kawai ta fada kan gadon ta fashe da kuka , saida tayi me isarta kafun ta mike dauke da robar a hannunta, zata bar dakin kenan shikuma yana shigowa da sallama a bakinsa kasa kasa, cikin zuciyarta ta amsa sallamar tasa fuskarta kwata kwata ba fara’a, kallan yanda fuskarta ta dan tashi yayi kafun cikin sauri yayi yunkurun nufar inda take”what’s wrong with my baby”, hannunta d’aya ta nuna masa alamar ya dakata karo na farko a rayuwarta, da wani irin expression yake kallanta, be gama tunani ba ta dago robar drugs din dake hannunta, “ Menene wannan”, ta fada tana zuba masa idanuwanta da suka kara haske sabida kukan da tayi,wani irin harbawa zuciyarsa yayi” sam ya manta daya sha drugs din ya barshi a fili”, cikin dan daga murya kamar ba ita ba ta furta “ maganin Menene wannan kakesha “, kokarin matsota yake ta kara dakatar dashi” please calm down, am sorry I will explain”, bata san lokacin da ta buga robar a ‘kasaba maganin ciki ya zube” me yasa , me yasa , I thought Dagaske kake da kace kana sona, i though da gaske kake da kace kai dady nane, kana shan wancan pills din dukda kasan illar su, u’re a doctor, I thought ka d’auke ni a matsayin matarka, Aushe nayi kuskure ba haka bane, you’re taking this drugs to…. to…”, ta kasa karasa zancan nata sabida wani saban kukan da yake kokarin zuwan mata tana dannewa, wani irin shock ne ya dake shi, jin kukanta yake kamar ana kara cakarshi da maki a zuciya gabaki d’aya ya rikice , cikin sanyin murya ya furta “ please don’t be angry, I will explain “, manyan eyes dinta ta zuba masa hawaye na sauka akan idon nata” bana bukata” kawai ta furta tare da barin dakin, wani irin jirine yaji yana neman kayan dashi yayi saurin samun waje ya zauna , ga baki daya hannayensa ya tusa cikin gashin kansa yana ya mutsasu “ I’m in a big mess , she’s more angry than ever”, ya rasa Wana irin tunani zaiyi , bayaso koka d’an tayi fushi dashi dan bazan iya daukan fushinta ba, da sauri ya mike ya nufi bayanta, yana shiga ya tarar da bata cikin bedroom dinta, ragowar bedroom din second floor ya duba , shima duk bata ciki, muryar da ya fara ji sama sama a falon kasane yasashi nufar falon kai tsaye, TAHEE ce a falon tare da su sumayya da suka zo falon, wani irin ajiyar zuciya ya sauke yana binta da kallo , adaidai lokacin da ta daga idanuwanta itama, tana ganinshi ta d’auke idanuwanta fuskarta a dan hade kadan ta yanda su Ihsan bazasu gane ba.” Oh my god “ ya furta cikin zuciyarsa har yanxu ya masa dauke idanuwansa akanta, su firdausi na ganinshi suka kara gaishe ganin yanxu yana amsa musu gaisuwarsu bakamar daba, kanshi ya dan daga musu alamar amsawa dan kwata kwata ba shi yake bukata ba,so yake ya rungumeta, ya lallasheta ko zata dena fushi dashi, he want to feel her warm , he can’t take it”, satar kallansa ihsan tayi ganin yanda ya tsaya gabaki d’aya hankalinsa na kan tahee dake dannawa waya,murmushi ta saki kafun ta kalli tahee,” sister yau dai bari na cika miki alkawarin Pam cake din ki”, bata jira amsar tahee ba ta mike ta nufi kitchen, firdausi da sumayya ma duk sun ankara dashi dan haka da sauri suma suka mike “muma bari mu tayaki” dukansu basu jira jin amsar taba sukayi saurin guduwa , bece komai dan Hakan yake bukata, ganin ta tashi zata bi bayansu yayi saurin shan gabanta, hannunsa biyu yayi hade alamun pleading, dauke kanta tayi daga kansa zata wuce yayi saurin riko hannunta, fisge hannun tayi kafin ta furta “ don’t touch me again “, tana gama maganarta tayi upstairs, waje ya samu ya zauna kansa na sara masa, gabaki d’aya launin idanuwansa ya canza Sabida yanda yaji xuciyarsa na masa zafi, ya dau tsawan lokaci zaune a kan kujera kamar ya bita amma yana tsoro karta kara wani fushin, ganin lokacin sallah yayi ne yasashi barin part gabaki d’aya . Aban garan su ihsan kuwa suna shiga cikin kitchen din suka kulle kofar, kwai kwayar yanda suka ga king na kallan tahee suka fara, “wayaga Romeo and juliet “ cewar ihsan , dariya suka saki gabaki d’ayansu, kan kujerun dake kitchen suka zauna suna dasa saban hira , daman space suka basu kar king ya koresu, sun dade suna hira abunsu kafun su fito falo, ganin babu kowa ne yasasu sakin ajiyar zuciya , da Sauri ihsan tayi hanyar kofa ,kallanta sumayya tayi alamun karin bayani” kun manta pan cake mukace zamuyi mata, tana fitowa kara zaunar da mu zatayi , ni kuma ban shirya shan masga ba Wajan yaya”,ga baki daya basu yi wannan tunanin ba, gudun karta fito tazo ta samesu sukayi saurin barin part din. Tahee kuwa tana shiga daki wani saban kukan tayi kafun ta shiga ban daki, Wanka tayi ganin ana kiran sallah tayi alwalarta, ta kabbara sallah bata bar daddumar ta ba sai da akayi isha’i, wasu English wears ta saka masu daukar hankali blue colour , cikakken gashin kanta ya sakko har bayanta duk da hular da ta saka, wani irin masifaffen kyau tayi na musamman amma fuskarta har yanxu a cin kushe take, Fararan hannunta da yan yatsunta sun fito fes da masu musamman da kunshin hannunta ya kara fito da farinsu,Daddadan kamshin turaran princess ne ke tashi a cikin dakin ta ko ina, message din data gani akan wayarta ne ya sata sakin baki “ sorry sis karkizo kiga bamanan ummey ce ta kiramu”, ba kowa bane ya tura mata text din face ihsan, hararar wayar tayi kamar suna gabanta,kafin ta fito daga dakinta, karo suka ci da king da gaba daya yanayinsa ya canza, kallo daya tayi masa kafun ta d’auke kanta “ sannu da zuwa “ ta furta zata bar wajan, ya rungumota ta baya yana sakin ajiyar zuciya, cikin disashewar murya kamar mara lapiya ya furta “ I can’t take it any more , please am so sorry, bayanda Kike tunani bane,” raba jikinta tayi da nashi kafun ta furta “ your dinner is ready”, am not hungry, ya furta yana binta da kallo, bata kuma ce masa komai ba tayi wucewarta kan dining, apple ta dauka guda daya ita ma, ta wuce dakinta, zuciyar ta na raya mata ta kallesa amma ta danne, tana barin Wajan ya dafe kansa dake sara masa, tayi masa kyau sosai yau , and he don’t like her frowning face, cikin sanyin jiki ya nufa dakin shima , yana kallan yanda take shan apple dinta cikin kwanciyar hankali, bece mata komai ba yace toilet,ya dade a ciki bayan ruwan sanyin da ya sakar wa kansa, ganin zazzabin nasa na kara yawa ne yasashi kashe ruwan, shima wasu kayan bacci ya dauka white colour masu kauri sabida yanda yake jin sanyi, turare kawai ya fesa ya fito, yana fitowa yatarar da fitula aka she sai lamp din da aka dan kunna, sai tun zuciyarsa ya rike yana cije lips ,sallar da ya saba yake so yayi amma ya kasa sabida ynda yake jin jikinsa, a tunaninsa tayi bacci ne shiyasa ya na hawa bed din ya janyota jikinsa yana sakin ajiyar zuciya,kara rungumeta yayi kamar wacce za a kwace masa ita, tun lokacin da ya rungumeta ta bude idanuwanta ga zafin jikinsa dake ratsa nata jikin,tausayi ya bata kamar tayi magana sai kuma tayi shiru har bacci ya dauketa, “ am so very sorry “ yake fada a cikin zuciyar sa…. Mss Lee 💖 GIDAN AUNTY 07041879581 BOOK 1 Page 62 Kallan fuskarta dake bacci peacefully yayi kafun ya mayar dashi kan dan karamin bakin ta, lips din ta da sukai jajawur ya zubawa eyes dinsa kafun ya lumshe ido, kara rungumota yayi a jikinsa sabida sanyin da yaji yana ratsa shi, ya dau tsawan lokaci idanuwansa biyu ko alamun bacci bashi da niyar yi, har 2:30 idanuwansa biyu sai da bacci barawo yazo ya daukesa. Farkon kiran sallahr asuba ne ya tayar da ita, jinta rungume a jikinshine yasa ta dan motsa a hankali tare da zare jikinta cikin nasa. Kyakkyawar fuskarsa ta zuba wa ido, kafun ta saka tafun hannunta akan goshinsa, tazo zata dauke taji ya rike hannun nata yana bude idanuwansa, da Sauri ta kwace hannunta tashiga cikin toilet, kanshi ya dan girgiza kafun ya bar dakin shima. Tahee na fitowa simple doguwar jiya ta saka me warwar ash colour sosai kayn sukai mata kyau, tana idar da sallah gashin ta da ya ta kura mata ta soma tajewa bayan ta zauna kan stool din gaban mirror din,ta ciki taga shigowarsa dakin, a hankali ta amsa sallamarsa kafin ta jigaba da gyara kan nata, gaban stool din ya karaso shima, zata mike ya Mayar da ita tare da karbar Kum din hannunta batare da yace mata komai ba,a hankali ya gama taje mata kan nata kafun ya daureshi da ash ban din da yagani ,”ina kwana”, yaji saukar muryarta har cikin kunnansa, wani irin dadi ne ya zuyarcesa amaimakon ya amsa mata gaisuwar da tayi hannunta d’aya ya tare da juyo da stool din da take zaune akai, binsa kawai tahee take da kallo ganin kamar bashi da lapiya yau,bata Ankara sai ji tayi king yayi kneeling a gabanta, da wani irin mugun sauri ta sauka daga kan stool din itama zatayi kneeling ya hanata tare da mayar da ita kan stool din, kanshi kawai ya dora a cinyar tahee batare da yace mata komai ba, tunda ya dora kansa take jin zafin kansa na ratsa mata cinyoyi a hankali ta zura hannunta daya cikin gashin kanta ,”dady jikinka da zafi har yanxu, bari na hada maka breakfasts sai kasha magani, shiru be amsa mata ba ,sannan be dauke kanshi daga kan cinyartaba, sosai ta damu da hakan taga zazzabine a jikinsa ga sanyin Acn dakin da yawa kara mura ya kamasa,” dady please ka koma kan gado sai na kashe mata Acn karya saka mura” yanxu ma be amsa mata ba, gaban tane ya fadi tayi sauri saka hannunta a wajan hancinshi “da..dy,dady” ta kira sunansa murya a harde cikin rawa rawa , a hankali ya bude bakinsa kafun ya furta “am sorry please “, hawayenta da suka sauka akan tashi fuskarne yasashi saurin bude idanuwan, bata Ankara ba taji saukar bakinsa akan kumatunta, eyes dinta ta ware masa , cikin sanyi da rauni ta furta “ karka karashan maganin nan dady”, kansa ya daga mata” na dena tun da princess dina ta fushi dani,” ya furta mata a hankali har yanxu muryarsa bata gama daidaitaba, hannunta me zobe ta mika masa,tare da mike wa tsaye,”toh ka tashi mana”, ta fada tana dan turo masa bakin ta, hannun nashi ya mika mata ita a dole zata mikar dashi, tana rike hannun nasa ya janyota jikinsa suka kwanta kan lallausan cafet din wajan me shegen laushi,bakinsa ta tura masa yayi sauri kuwa ya cafkesu ya fara tsotsa, ganin hakan be masa ba ya juyata ta koma kasan sa bakinsa cikin nata, bakin take kokarin kwacewa amma ya ki bata damar Hakan saida ya tsotsa iya yinsa kafun ya janye bakinsa cikin nata da yake ji kamar karya dena shansu, bakin ta kara turowa tana kauda kai, bata ankaraba ta karaji ya bata wani passionate kiss a wajan, “nifa Allah ka bari” ta fada a shagwabe, “you’re making me to add more “ , girgiza masa kanta tayi “Nima kamun nauyi , hanjin cikina zasu iya fitowa fa”, hannunsa daya ya dora kan cikin nata yana shafawa batare da yace mata komai ba ya dauketa ya kwantar kan gado, zai sauka tayi saurin jiki hannunsa “ dady baka da lapiya fa, yanxu zan maka abinci sabida kasha magani”, lumshe mata ido yayi “ dont worry dear, I have important meeting, am sorry please “, kanta kawai ta daga masa tana sun kuyar da kanta” common ni bana san wannan kalan face din,”murmushi ta dan sakar masa tana boye fuskarta ,”oya let’s go , ya kamata matata ta dunga yi mun wanka fa”, ya karasa cikin zolaya, karamin pillow din dake hannunta ta buga masa “ ni kana sani jin kunya “, murmushi ya saki kawai tare da shiga dressing room. Tana ganin shigarsa tayi saurin sakkowa kasa , tunanin abunda zata hada masa me sauki ta fara, omelets ne ya fado ranta , cikin sauri ta soya masa shi, tare da coffee me zafi da ta hada masa daga saban abun coffeee dinta, bread ma tayi Toasting din shi, kafun ta koma dakin, a gaban Mirror ta tarar dashi yana taje gashin kansa da ya fara tsaho, wani blue din suit ne a jikinsa me kalar sararin samaniya, fadar irin kyau da haduwar da yayi bata baki ne ga wani irin daddadan kamshin turaran sa dake cika mata hanci, hakanan kawai sai taji wani kishi ya kamata , kenan yarda taga kyansa haka wasu zasu gani, har bata san lokacin daya karaso Wajan ba , sai tray din hannunta da taji ya dauka , a jiyar zuciya ta sauke tana bin bayansa “ kayi kyau sosai fa, kuma ni ..” kallanta yayi alamun ta karasa , itama kan kujerar ta zauna “kuma ke Menene “, kanta ta langwasar to ka gama breakfast dinka kasha magani,” sir maa, your wishes is my command my stubborn wife “, bakinta ta turo ganin coffe kawai ya ke sha , fuskantar hakan ysashi fara cikin omelet’s din ganin bata cine yasa shi kallanta” ni bazan sha coffe ba, kuma bazanci kwai ba,sabida ni bazanyi kiba ba”, kallanta yayi kafun ya furta “ you’re looking for my trouble ko”, dariya ta saki bata kuma ce masa komai ba har ya kammala cin abinci,” thank you, I enjoyed the food , but karki dafa komai , I don’t want you to stressed your self”, sakin baki tayi tana kallansa ganin yana kokarin saka suit din saman yasa ta temaka masa , bata san lokacin da ta furta “ suma mata haka zasu ga kyankya in ka fita , ni Allah ban yardaba”, sai kuma tayi saurin rufe bakin ta jin bara baraman da tayi, forehead dinta ya sumbata “ duk Wanda ya kalleni zan ce a harbeshi matata tace kar a kalleni”, murmushinta me kayatarwa ta sakar masa kafun tayi hugging dinsa “ Allah ya baka abunda kaje nema, Allah ya kare ka da kare warsa, Allah ya tsareka daga Sharrin ma sharrata ya dawo dakai lapiya”, so tie ya rungumeta “ thank you, take care of your self, love you” dariya ta saki kafin ta ce “me too” , hancinta ya dan dan gwale mata “you will explain me too din nan, kinsa na makara ko”, gwalo ta danyi masa tare da rakashi har falon kasa, zataje wajan kofa ya hanata,”take care “ ya furta tare da barin part din, ji tayi kamar an cire mata wani abu me nauyi Akan zuciyarta, shaf shaf ta gyara masa ban garansa , tare da naga ban gwaran, kulu na zuwa down stairs kawai ta gyara, ganin babu wani aikin tahee ta sallameta, taliya da manja take sha’awa shiyasa tayi taliyanta da yaji pepper sosai tana gama ci ta dauki wayarta dagata tayi haske alamar message ya shigo “ I LOVE YOU Angel “, murmushi tayi kafun ta bashi amsa da “ LOVE YOU TOO”, wani irin dadi ne taji ya kara kamata, cikin kan kanin lokaci tayi wani wankan kafun ta nufi part din su dada , sun dade suna hira abinci kafun ta shiga part din ummey da ammeey, hatta prt din su ihsan da su sumayya ko wanne sai da tashiga , sunji dadin zuwan nata kuwa, part din aunty ne da ta shiga har ta karaci zaman ta basu fito ba tun bayan fada mata da me aikin ta tayi tace gatanan zuwa, tana ganin lokaci ya ja ta koma part din dada anan suka ci gaba da hirarsu, dada na ganin 6 tayi ta Koreta acewarta mujinta ya kusa dawowa kuma gobe zata fara zuwa makaranta. Tana komawa part din ta , turaran wuta ta saka me shegen kamshi, kafin ta sake wani shirin cikin kananun kaya masu shegen kyau da suka fito da ainahin shape din jikinta, abinda zata dafa take tunani message din da ta gani a wayar ne ya dauke mata hankali , wasu irin kalaman soyayya me tsayawa mutum a rai ya turo mata, da ka karshe ya jaddada mata kartayi abinci, ganin hakan yasa ta dakko pop corn dinta , tana ci tana watching wani cartooon da akeyi, white paper din data hangone yasa tayi saurin dakkota, kamar yanda tayi tsammani kuwa, kalmar da aka saba fada mata shi aka kara fada mata yanxu ma , tayi alkawari ko Wanene yake ajjewa sai ta kamasa, door bell din da aka dan na sau daya ne ysa ta ajje popcorn dinta, ta karaso wajan door din, lekawa tayi kadan ta hangosa ta kashe mata ido d’aya , tana bude kofar yayi saurin shigowa, kafun yayi magana tayi masa wani fari da ido, cikin wani irin salo tayi masa Sannu da zuwa , kasa motsi yayi daga inda yake, ganin hakan yasa ta karbi ledojin hannunsa ta ajje masa, cikin wani irin saban taku daga canza ne daukan hankali, kamar rakumi kuwa haka ya dunga binta har tasa yayi wanka ta tayashi shiryawa, mamaki ne fal ransa surar jikinta sai faman fusgarsa yake yana kokarin sassaita kansa, ledojin ya bude mata , kayan ciye ciye sosai a ciki, tun daga kan pizza, burger , da shawarma sai ice creams da yawa da ice pops , ga uban chocolate da ke ciki kala kala, dayan ledar kuma, Kifi ne manta guda uku gasassu sai ledar kaji gasasshe shima , sakin baki tayi tana kallansa “ dady wannan abincin fa”, Kai tsaye ya bata amsa “it’s for my baby”, rungumeshi tayi da har saida yayi ajiyar zuciya sabida yanda boobs dinta suka taba masa kirji yayi kewar su sosai, kallanshi tayi kafun ta furta “ wanne zan zuba maka a ciki”, na koshi , ya bata amsa dan gabaki d’aya bashi da mood din cin abinci, so yake kawai ya kasance tare da ita , idanuwansa har sun fara sauya kala sabida duk motsi daya da zatayi sai jikinta ya dan motsa, bataci komai ba itama sai ice creams da ice pops din data iba ragowar duk ta sasu a cikin fridges din da yake shake da wasu kayan ciye ciyen, “ yayi sanyi da yawa , you have to eat dan yau zakiji yunwa “, kallan shi tayi da yace zata ji yunwa , bata gane abunda yake nufi ba shiyasa tace masa ta koshi ita, tana shan ice cream dinta tana lumshe idanuwa, lokaci zuwa lokaci tana bashi shima a baki, sai data gama ciye ciyen ta , tace masa zataje tayi brush , Tom kawai yace mata , tana shiga dakinta ya kashe light din kasan tare da barin dum din, TAHEE na cikin yin brush din ya shigo toilet din, ware idanuwa tayi sabida babu komai a jikinta sai karamin towel ganin shi da towel din ma yasa jikinta daukan rawa, zata fita ya hanata gabaki dayanta y dauketa, duk yanda taso ya ravu da ita be kyaletaba saida sukayi wankan tare , wajan sa kaya ma shine ya saka mata kayan da yake so duk da kasancewar komai na jikinta a bayyane yake cikin rigar.suna kwanciya ya kashe light tare da matso da ita jikinsa, jikinsa har ya fara rawa, bata hanashi yin abunda yake so ba, sai ma biye masa da tayi lokacin da yake sumbatarta bata san kara zautar dashi take ba, daga nan zani ya canza salo a zatanta iya romance zai tsaya sai dataji yana adduar saduwa da iyali,ya dade yana biya wa kansa bukata, wannan karan batayi masa rakin da ta saba ba, ta daure sosai ko shi saida yaga bajintarta, bayan komai ya lafa sun yi wanka ne tace masa yunwa takeji, kifin dazu yayi warming tare da feeding dinta a baki da kansa , ganin yanda take rike kwankwasone yasashi fara matsa mata wajan a hankali, a jiyar zuciya kuwa ta fara saukewa dan ba karamin dadin message din take jiba,da wuri ya sata tayi bacci sabida school dinta gobe . Shima da wurin ya kwanta rungume da ita. WASHE GARI Yau ya kasance Monday ,tun bayan sallar asuba tahee bata koma bacci ba , jinta take kamar a cikin sabuwar duniya , ganin yanda take farin ciki hakan yayiwa king dadi, yanxu ma duk yanda yayi da ita taci abinci taki ita ba tajin yunwa , da kyar taci abincin shima dan kadan, kayan uniform dinta take kalla ita kadai sai faman sakin murmushi take,shiryawa tayi cikin uniform din da ya kasance light blue din sararin samaniya sai wani dark blue din skirt shima , daga sama wani irin jacket ne da baya fito da jikin mutum shima dark blue, wani mini hijab ta dakko shima light blue ta saka tare da saka ta kalminta black colour , OMG sakin baki nayi kawai na zuba wa sarautar Allah ido, kyau iya kyau, fadar irin kyau da kayan sukayi mata bata baki ne,ko makiyi yaga kyan da tayi sai ya yaba mata , beret dinta dark blue ta dauka ganin ta kasa saka wa ne ta nufi dakinsa, ya na zaune d’auke da system ta shiga dakin, tundaga kan kafarta har zuwa kanta yake binta da kallo, wani irin masifaffen kyau me kayatarwa da tafiya da inajin mutum tayi, shikansa kasa d’auke idanuwansa yayi akanta , a gabanshi ta tsaya tana sakar masa murmushi “ dady nayi kyau”, more than kyau , amma am feeling jealous I can’t leave you ki fita haka , sakin baki tayi tana kallansa kafun ta dubi jikinta ganin babu ta inda jikinta ya fito, raurau tayi masa da ido amma ya dage bazata fita haka ba da kyar ya kyaleta shima sai dai kullum face masks a fuskarta, ta yarda da hakan shiyasa wani light blue din facemask ya baka mata kafun ya saka mata beret dinta,” u look more than beautiful, I love you “ murmushi ta sakar masa tana hugging dinshi, “ thank you sweetheart “, say it again “sweetheart “ ta kara maimaita masa, kokarin janyota yake tayi saurin yin baya tana dariya , lokaci ta nuna masa , bece mata komai ba ya bita dakinta, school back dinta da ta kasance black color ta Rataya aban gare d’aya , wata jaka ya mika mata me shegen kyau cikinsa cike yake da kayan kwadayi, “ all the best “, kallanshi tayi alamun bata gane ba kafun ta furta “ ba tare zamuje ba dady”, am sorry Zanzo wataran,I have to go somewhere, take care masu kula dake sunanan nothing will happen to you, and kar ki cire facemask din sai zaki ci abinci , in kin gama sai ki dakko wani a bag dinki kisaka,ok” murmushi ta saki tana daka masa hannu “okay”,suna fitowa wasu jerarrun motoci ta gani she kyalli suke dukansu ba kake, suna ganin king suka sara amsa tare da tahee itama , ita abun dariya ma ya so bata, wata matace ta karaso wajan me dan jiki da shigar suit a jikinta , ta tunana tahee harya “ this way ma’am “ , kallan king tayi ya jinjina mata kai, bye bye tayi masa kafin ta shiga cikin motar, wannan matar ce ta kulle mata motar kafun sukara sarawa king, zasu jira ya basu umarnin tafiya , a hankali motocin suka fara slow, TAHEE na motar tsakiya sauran motocin biyu muma duk bodyguard ne a cikinsu, 17 minutes ne ya kawosu wani kayataccen building JOLAS PRIVATE SCHOOL, abunda aka rubuta da wani irin design, suna zuwa bakin kofar bodyguard daya ne ya fita yayi wa masu tsaron magana kafun a wangale musu baba nan gate din makarantar ,” wow “ tahee take furtawa a kasan zuciyarta sabida haduwar makarantar tun kafin ta shiga, jefi jefi tana ganin wasu masu irin kayanta, tunda kasancewar private school ce da ba ko wana me arziki zai iya sa dansaba sai da motocin su tahee ya dauki hankali wasu daga makarantar, tafiyar mintuna biyu sukayi sukazo wani babban waje da yafi ko ina haduwa, ga wasu mutane kusan su 7 tsaye a wajan, ana tsayar da motar wannan Matar ta bude mata kofa ta sara mata,ga baki d’aya mutanan da zasuyi ‘ya da ita suka karaso wajan suna gaisheta , banbarakwai abun yayi mata musamman wani girma da suke bata, “ you’re highly welcome maah” suka fada tare da dakko wani rose red colour zasu mika mata wannan Matar ta karba saida ta duba ta sannan ta mayr musu suka bata, Godiya tayi musu kafin ta mikawa matar rose din….. Msss lee 💖 GIDAN AUNTY 07041879581 Mss Lee 💖 BOOK 1 Page 63 Suna shiga office din principal din aka kawo mata ruwa, ita abun nasu ma mamaki ya fara bata , cikin kulawa principal din me suna rose ta fara yi mata interview da kanta, itama tahee tana bata amsa cikin baiwar da Allah yayi mata, sosai madam rose tayi mamakin kwakwalwar tahee ganin yanda take amsa questions din kamar yanxun ake koya mata babu gargada, da farko tayi tunanin za a kai tahee ss1 sai da tayi mata interview taga kokarinta ya wuce wannan class din, harta ss 2 bazea yu Asataba , Number king madam rose ta kira har sau biyu kafun a na ukun taji an dauka , a tunaninta king ne sai da akayi magana ta gane bashi bane,” At the meeting “zaki ya bata amsa daman number sace bata king ba,ganin hakan yasa itama bata bin kiran ba ta jagoranci tahee zuwa class din da aka bata wato ss3 flora, lokacin da suka shiga gabaki d’aya hankalin yan ajin ya dawo kanta ,ganin madam rose a ajin, mikewa sukai gabaki dayansu cikin zallan turanci suka gaishe da madam rose , kafin mss Afia da take daukansu Mathematician ta gaishe da principal din itama,nuna mata tahee principal din tayi kasantuwar Itace class mistress din ajin,cikin ya ran turanci madam rose ta gabatar mata da tahee a matsayin new student kafun ta bar class din,kallanta mrs afia tayi tare da nuna mata wani kujera da ke 3rd seat alamun taje ta zauna, cikin girmamawa kuwa ta karasa ta zauna tare dayi wa wacce take wajan sallama tayi zamanta, maths din mss afia ta cigaba da yi musu, saida ta kammala kafun ta dan dawo baya sabida tahee ta fuskanta, ai kuwa gabaki d’aya ta gane maths din da a akai musu Sabida yanda take koyawa musu daki daki, saida aka kammala kafun ta kalli tahee cikin cikin yaran turanci” ko xaki gabatar mana da kanki”, a nurse tahee ta mike kafin cikin yaran turancin da maki aka sari da tayi sai da suka dauka ba bahaushiya bace sabida yanda ko wana word yake futa “My name is taheera Mohammed “, yan tanbayoyi mss afia tayi mata cikin nutsuwa ta bata amsa duk da yawan idanuwa da taji akanta,tana gamawa mss afia ta tafa mata kafun gabaki d’aya ragowar student din suma su ta fa mata, mss afia zaka fita kenan massager ya shiga da wasu books , kai tsaye desk din da tahee take mss afia ta Nuna mata, tana kai mata tayi Mata bayanin sauran subject din da zaa yi musu yau ne , ragowar books dinta yana wajan madam rose. Tunda mss afia ta bar class din gabaki d’aya ajin yayi shiru kowa har kar gabansa yake , tagen tahee ce ta dan kalleta kafun ta miko mata hannu “ I’m husna ma’aruf me gwanjo, nice meeting you”, itama mika mata hannu tahee tayi” nice meeting you too”, murmushin jin dadi husna ta saki kafin ta cigaba da duba books dinta itama, mintuna biyar tsakani sai ga wani teacher din ya shigo shima , chemistry ya rubuta cikin bold din rubutu, book din chemistry din tahee ta dakko da wani karamin book, abun da ya koya musu jiya ya fara tanbaya wasu daga cikin class din suna amsawa, musamman ta gefen ta da mafi akasari tafi bada amsa “ Good class rep” gabaki d’aya yan class din tafa mata sukai, TAHEE kuwa na tsuwa tayi tana sauraran bayanin topic din da yake musu me suna EVOLUTION OF ARTIFICIAL ORGANS, yana gamawa ya fara tanbayoyi ko yan class din sun gane, wasu na amsawa wasu kuma nayi masa tanbayoyi, saida ya kammala kafun husna ta mike a matsayin class rep din class din ta gabatar masa da new student din da aka kawo, shima tanbaya yayi wa tahee game da topic din yau, nan ma duk bayanin da yayi saida ta basa harda karin Wanda yayi musu, tafa mata yasa yan class din sukai kafun ya kalli husna cikin yaran turanci “ ki koya mata sauran karatun baya da akai” ok sir husna ta bashi amsa, yana fita tahee ta dan kalleta “ please ko zaki iya aramun note dinki”, mika mata husna tayi tare da mathematician din da aka gamai musu “ but lokacin break yayi , ki bari inkin koma gida zaki fi nutsu inyaso gobe sea na fara koya miki Wanda akayi na baya” duk da facemask din dake fuskar tahee hakan be hanata sakin murmushi ba “ thank you “, you welcome “ husna ta bata amsa ita ma, wasu daga cikin yan class din ne suka fara futa yayi saura mutane kadan, watace dake can bayan seat su uku suka taso cikin rangwada Daidai inda tahee book din tahee yake wata daka cikinsu ta saka mata kafa, book din ya fado, shewa suka saki kafun su bi tahee da husna da dirty look suna jan tsaki, “ am sorry please, haka halinsu yake basu da kunya sabida suna ganin suna da me tsaya musu”, gyada mata kai tahee tayi kafun ta dauki book dinta “ it’s ok “, messenger ne ya kara shigowa kafun ya mikawa tahee wani wasu card , yana fita husna tayi mata bayanin Wanda zata dunga karban abinci da kuma books ko wani abu da take so, ganin lokaci na tafiya ne yasa suka nufi cafeteria din kamar yanda husna ta jata , suna shiga cafterian matan dazu da wasu suka fara shewa suna nuna tahee, master card din abincinsu husna ta nuna , tanbayar abunda za a basu husna tahee, TAHEE bata karbi komai ba duk yanda husna tayi da ita, wani table aka nuna musu me zaman mutane biyar suka nufa, husna ce ta karbo musu abincin ta mikawa tahee nata, bata ci abincin ba ganin yanda mata da maza suke kwata kwata bata da sake wa, mrs afia ce ta shigo cafeterian gabaki d’aya student shiru sukai dan sun san halinta, inda tahee take ta nufa kafun ta nuna musu wani empty seat yadda tahee zatafi dadin sakewa , kamar kuwa ta sani wajan yafi Mata duk da bata ci komai na wajan ba, lokacin break na karewa suka koma class, da daddai da daddai teachers Suke shigowa class din, duk Wanda zai fita sai husna ta gabatar masa da new student din ajin har lokacin tashi yayi, gabaki d’aya tahee tayi week kamar ba ita ba har yanxu kuma bata cire face mask din fuskartaba, Ana tashi wasu dan kara dan karan motoci kuda uku ba’ka’ke suka shigo cikin harabar makarantar, Daidai inda tahee take motocin sukai parking, cikin taku Matar me suna stela ta bude mata kofa bayan books dinta da sauran abubuwa da ta dakko wa tahee, sallama sukayi da husna da itama aka zo daukarta. Tahee tana komawa gida wanka tahee da sallah kafun wani baccin wahala ya dauke ta, ba ita ta farka ba sai wajan karfe biyar, cikin sauri ta mike, Sallahr la’asar tayi kafun ta shiga kitchen har yanxu baccin fuskarta be saketa ba, cikin kankanin lokaci ta dafa musu abinci mara nauyi tare da kunun aya me shegen dadi, tana kammalawa gidan ta kara Kimtsawa kafun ta shiga wanka , har lokacin kuma baccin da take ji be sake taba, sallar magariba tayi kafun ta Jira ta isha’i shima tayi , tana Idarwa bacci ya dauketa akan daddumar. 8:50 king ya shigo part din ganin bata falon ya nufi dakinta, ganin yanda take bacci akan daddumane yasashi dan zaro ido kafun ya kara so inda take , gabaki dayanta ya dauketa ya mayar kan gadon, bude idanuwanta da suka jike da bacci tayi tana kallansa, dan hancinta yaja kadan “sleepyhead” , tashi zaune tahee tayi “ Yaushe ka dawo”, now ya bata amsa”sorry bansan bacci ya daukeni ba, sannu da zuwa, ya aiki”, ta jera masa duka tanbayoyin lokaci d’aya, “Alhamdulillah “ ya bata amsa a hade , kafun ta temaka masa yayi wanka shima ya shirya, abinci tahee ta zuba musu sukayi feeding juna kafun ya tanbayeta abunda aka koya masa, bayanin karatun ta shiga yi masa dukda shima yayi mamakin ss3 din da aka sata, question ya dunga yi mata tana bashi amsa shima, ya jinjina kwazanta sosai, book din husna ta dakko masa ya fara yi mata lession din baya da akayi cikin zallan gwarewa , be sha wahala ba wajan yi mata bayanin ganin tana saurin gane wa, hamma da yaga tanayi ne yashi ajje books din kafun ya dauketa gabaki d’aya suka koma daki, akan chest din shi tahee ta kwanta tana shakar daddadar kamshin turaren sa, a haka bacci barawo ya kwashesu gabaki d’aya . ***** Washe gari tueday da wuri tahee ta shirya ta nufi school bayan king yasata cin abincin dole, suna zuwa ba assembly shiyasa ajikin su ta nufa , lokacin itama husna tazo, ganin da sauran mintuna kafun a fara classes din husna ta fara koya mata previous karatun da aka yi na baya, suna cikin yi yan class din suka fara shigowa da d’ad’d’e da d’ad’d’e, wayan nan yan matan ne suka kara shigowa ynxu ma cikin isgili suka zo zasu yardar wa tahee book , husna ta tsawatar musu daman itama ba sa ga miciji da zuna, tsaki ta tsayen tayi kafin ta kalli ta gefen ta me suna kubra , “kubry let’s go”, tana fadar hakan tayi wucewarta , itama dayar suna salma ana kiranta salmyyy baby wucewa tayi tana Jan kwafa, guntun tsaki husna ta saki Daidai lokacin da teachers suka fara shigowa, yau ma lokacin break nayi husna ta kara koya mata wasu abubuwan kafin su nufi cafteria , a wnnan karan ba leafi ta dan taba abincin dukda yanda husna ta rikice da kyawun tahee duk da itama ba baya ba wajan kyau, da ta kalleta sai tace “ gaskiya friend ke kyakkyawa ce “ ba abunda tahee take ce mata saidai tayi dariya , suna kammalawa classes Dinsu suka nufa ganin lokaci yayi, suna shiga teacher din biology ta shigo class din, tana kammalawa wan teacher din ya shigo, haka teachers suka cigaba da shigowa har lokacin tashi. Yau ma da gajiya tahee ta koma gida , tanayin sallah cornflakes ta dama da yasha marada sosai , tana gama cinsa ta dakko ice cream ta sha har roba biyu kafin ta dakko wasu chocolate din suma masu shegen dadi, ko ina a gyare ya’ke sai faman tashin kamshi yake shiyasa 3rd floor din king kawai ta gyara kafun ta shiga wanka, sai yau ta tuna da wayarta, ganin ba charge ne ysa ta saka wayar a chargy, bayan sallah la’asar kitchen ta shiga ta girka musu abinci kafun ta shiga wanka , ana kiran magariba sallah tayi kafun tayi isha’i shima , tana idarwa kara shirya jikinta tayi duk da bata saka turare ba sai wani mara karfi da bazata jishi sosai ba da ta saka. Yana dawowa ta rungumeshi kamar ba ita ba , ganin yanda ya gaji ne yasa ta hada masa ruwan wanka, “ I can’t do it my self , I need my wife’s help”, duk da bashi da tabbacin zatayi abunda yace din, amma ga mamakinsa batayi masa musu ko kadan ba ta temaka masa yayi wankan sai wani kakkare fuskatake wai karya kalli fuskarta, sosai king yaji dadin hakan da tayi, suna kammala cin abincin karatunta da akayi mata ya kara koyamata. Suna shiga daki king ya kashe hasken dakin ya bar ita dum light , janyo tahee yayi jikinsa kafun ya hade bakinsu waje d’aya, bata hanashi ba itama ta fara maida masa da martani, wani irin susucewa king yayi sai faman gurnanin dadin yake saki, gabaki d’aya tahee ta zautar dashi da salon kiss dinta, cikin sauri ya fincike mata rigar jikinta kafin ya fara ya mutsata yanda ya keso, yanxun ma tahee bata hanasaba musamman wani dadi da ya fara ratsa mata kwakwalwa sai faman tura masa breast din ta take yana kara zaucewa, daga nan salo ya canza,wannan karan batayi wani rakiba duk da ta danji zafi amma dadin da takeji ya nunka zafin, king sai faman surutai yake mata yana shi mata albarka , wani abun duk bata gane me yake cewa, yana kara kusantar ta ta ya tanbayeta ko da dadi, cikin sauri tahee ta daga masa kai tana kara rungumosa jikinta. Bayan komai ya lafa king ya soma tsokanar ta , itama Kam ba bakin magana sai boye fuskarta da take a cikin kirjinsa. Washe gari me haka tahee ta cigaba da suka makarantarta kome aka koya mata in ta dawo king zai kara koya mata, yanxu har karatun alkurnani take basa musamman yanda suke tashi sallar tsakar dare, a kwanakin nan gabaki d’aya tahee bata samu damar shiga cikin gida ba sabida makaranta da take zuwa. Haka ranaku suka ci gaba da tafiya yau ya kasan ce satin tahee biyu da fara zuwa school , cikin yan kwanakin nan wata shakuwa ce ta shiga tsakanin ta da husna duk da har ynxu husna bata san tahee na da aure ba, A kullum kuma tahee sai wani haske da fresh da fatar jikin ta take, gabaki d’aya kirjinta ya kara cikowa, duk lokacin da king zai kusanceta sai ya tanbayeta ganin yanda breast dinga ke cikowa tana kara murmurewa, wani irin soyayya suke wa junansu kamar zasu hadiye zuna, duk lokacin da d’aya bayanan toh daya zai kira yaji lapiyar daya , Tsantsan kulawa suke nuna wa junansu, musamman yanxu king da baya jin kunyar nuna soyayyarsa a gaban kowa . Yau ta Kasance Friday, gabaki d’aya kowa na cikin family farin ciki ne dauke a fuskarsu , kowa Ka gani sai aikace ai kace yake, har wannan lokacin amrah bata yin gangancin haduwa da king sabida bugun mutuwar da yasa akai mata lokacin da zaki yakawo masa bayanin phone number din aka turo masa da text, ita kanta tayi na damar hakan sabida ga baki d’aya bata da sakewa yanxu ,kullum fargabar ta kar king ya ganta da warning din da yayi mata da babbar murya in ya kara ganinta. Karfe 3:02 su ihsan suka nufi airport dan dakko su kabeer da haroon, wasu matasan samari ne chocolate colour suma duk da basu da haske babu mummuna a cikin su, ko wannan su ya aske gashin kansa da ya tara sai kadan da suka bari, kowa yayi farin cikin ganin su ganin yanda suka canza kamar basu ba, babu Wanda be nuna farin cikinsa ba sai aunty dake yaken dole, kowa aka dawo gida hirar Yaushe gamo aka kara kafun kowa yaje ya huta kasan tuwar dakinsu daya suma flat Dinsu da abeey ya bude musu, duk Wanda hidimar da ake tahee bata sani ba tana daki tana baccinta, sai da taje part din su dada ake fada mata dawowarsu, miran king ta gani a wayarta , kunyar daukan kiran take a gaban su dada ga abeey da ya shigo shima, sai da safe kawai tayi musu duk da kunya da tabi ta cika mata ciki, tana zuwa part din su ta tarar dashi sanye da bakar singlet da wando fari, wajan shi ta karasa zata rungumeshi tayi saurin ja baya, kallanta yayi alamun Menene “ banasan kamshin turaran nan”, da sauri ya kalleta alamun ta maimaita Menene bataso, ta bude baki zatayi magana taji wani irin amai ya ta so mata, da sauri ta nufi toilet din kasa har tana hadawa da gudu, system din gabansa ya ajje cikin tashin hankali yabi bayan babyn tashi, sosai tayi amai da ya sata galabaita, saida ya tabbatar data gama dakanshi ya wanke mata jiki sai faman kare hancinta take, yana ganin hakan sauri ya wa tsa ruwa kafun ya canza kayan jikinsa, be shafa komai ba ya nufi inda take a kwance,dago da ita yayi ta kara komawa luuu zata kwanta “ No !! Noo please , stay still , meke damunki, Menene ya saki amai” bakinta ta turo masa Nima ban sani ba kawai bana san kamshin turaran da ka sane ,ina shaka naji ina jin amai, kuma ni dan wake zanci da yaji”, idanuwansa king ya zuba mata, abunda yake fado masa arai yane yake so ya gasgata, “are you serious “, kanta ta daga masa dan ita dan wake take so taci, da wani irin sauri king ya kankameta a jikinsa , ya rasa Wana irin farin ciki zai yi, gabaki d’aya ya susuce ko magana ya kasa bayan rungumeta da yayi a jikinsa, cikin rawar murya ya soma magana “ thank you so very much dear, Allah yayi miki albarka, ya faranta miki kamar yanda kika farantamun, ke din farin cikin rayuwa tace da bazan iya musaltawa ba, I love you! I love you !!! I love you , I will now be a father , OMG”, ya karasa maganar tasa yana dora hannunsa d’aya akan cikin ta , bata gane me yake nufi ba shiysa take bunsa da kallo, wani irin tsantsan kaunarta ta hango a kwayar idanuwansa, a hankali ya kwantar da kansa saman cinyarta, ji yake komai na dawo masa sabo kamar yanxu abun ya faru, daukar damshi damshin da taji ne yasa tayi saurin dago da fuskarsa, hawaye ta gani suna sakko masa akan fusga, yayi saurin kneeling a kasa tare da yiwa Allah sujjada, bazai iya musalta farincikin da yaji ba, “ dady” ta fada itama kamar zatayi kuka Ganin hawaye akan fuskarsa, murmushin dayasa hakwaransa fitowa yayi kafun ta furta “ thank you zawj, I will now be a father, baby na ta girma she will be a momma “ har yanxu bata gane ba , shiyasa ta kallesa da sigar tanbaya, “ you’re pregnant “ ya furta mata, da wani irin expression ta kallesa ganin tsantsan farin ciki shin fide a fuskarsa, bata san lokacin da wani kuka ya kwace mata ba, da Sauri ya riko hannunta yana lallashinta har saida tayi shiru “ please inasan cikina “ ya fada mata a raunace duk da besan dalilin yin kukan taba, tausayi ya bata sosai, Inba me yin butulciwa WACECE ita da zataki Jinin dadynta, saukar hannunsa da taji akan cikin natane yasa ta kankame hannun nasa kafun ta rungumeshi ajikinta “ I love you so very much hayaty “ ajiyar zuciyar da har ita sai da taji yayi kafun ya rada mata “ I can’t expressed how much you mean to me maman unborn “, dan dago da fuskarta tayi tana kallansa “Ni fa sunana baby ba maman unborn ba” hancinta ya ja mata kafun ya furta “ you’re not a baby now , yanxu kin zama maman baby”, shagwabe masa fuska tayi kamar zatayi kuka “ wato tun kafun kaga dan Ka fara nunamun banbanci “, are you jealous “ ya furta yana zaro idanuwansa, kin magana tayi ta tashi sai faman kunbure kunbure take, wani irin sanyi ne yaji ya mamaye masa ransa , yayi saurin rungumota” Haba ke soyayyarki da bance ai, kadan zamu sanwa baby, kinga ynxu kinzama babbyn baby ko”, ita sai yanxu abunda tayi ma yasata kunya tayi saurin boye fuskarta. Jin kansa yake kamar a mafarki “I’m gonna be a father, Alhamdulillah ya Allah, Alhamdulillah Ala ni’imatullah, Allah nagode maka,Allah ka albarkaci abinda ke cikin ta ka bata lapiya, Alhmdllh “ shine abunda king ke faman nanatawa aransa yana yiwa Allah tasbihi. GIDAN AUNTY Mss Lee 💖 07041879581 BOOK 1 Page 64 Not edited Gabaki d’aya ranar king farincikin da ya keci ya kasa boyuwa da kansa ya kara dubawa ya tabbatar da cikin , begama farin cikin ba tahee ta bijiro masa da yan wakenta, yace zai kira ayi mata tace shi take so yayi mata, sabida farin cikin ta yau king akaro na farko da zai girka abincin Inba coffee ba da kansa, komai da komai saida tahee ta futo masa dashi gabaki d’aya ya bata kitchen din da floor hatta lallausan gashin kansa saida yasan da zuwan king kitchen, yanayi yana nishi, ita dai tahee sai faman dariya take masa, wajan sa dan waken ma da ya sa daya zai ce mata zai hutu wai ya dauka da daddai da daddai ake dafa dan waken, ga wata uban kuka da ya cika a cikin dan waken , yayi gore shar dashi, yana kammalawa tace masa saura tumatun da albasa, tunda ya fara yanka albasa yake lumshe idanuwansa sabida yajinta, da ya tashi yanka ta , gida shida ya rabata , wai haka turawa suke cin albasa, batace masa komai ba ya soya ma ta dakko yajin ta, da kyar ta yarda ya zuba mata yajin ganin uban yajin da take kokarin tunawa, tana saka dan waken abakin ta zaro idanuwanta, kallanta yayi cikin damuwa zai janye plate din “ karki ya cutar mun dake bari ko order sai muyi”, duk da uban kukan da ya cika mata murmushi ta sakar masa kafun ta furta “ yayi dadi, shine kake mun wayo ka iya girki ko”, kallanta yayi haryanxu yana kokarin dauke plate din , kukan shagwaba ta saka masa gabaki d’aya ya susuce sai faman sannu yake mata, ko da zasu kwanta ma duk motsi daya in tayi sai ya tanbayeta me yake damunta, sosai ya shiga lallashinta har bacci ya dauketa. Kallan flat tummy dinta yai kafun ya kai bakinshi ya sumbata, harta tahee dake bacci sai da ta motsa, gyara mata kwanciyar yayi kafun yayo alwala, sosai yayi nafila ya nuna wa Allah godiyarsa. WASHE GARI Yau weekend , tunda tahee ta farka yake tarairayarta harta abinci shike bata da kansa, ita dai sai dai tayi masa dariya wani irin Kaunar cikin na kara shiga ranta, karfe 8:30 ya shiryata, duk yanda taso dojewa saida king yasa ta shirya, yau da kansa yayi driving dinta har zuwa asibitinsa, kowa mamakine ya kamasa ganin king na driving da kansa, abunda ya fi daukan hankali kowa yanda ya rike wa tahee hannu har zuwa office dinta, sai a lokacin ya cire mata facemask din daya sa mata a mota, dakanshi ya duba lapiyan cikin , kafun ayi mata scanning, cikin wata d’aya da kwana uku, yana ganin result din wani murmushi ne ya kamasa “ so am not that bad “ ya furta a cikin zuciyar, wani murmushin ya kuma saki, be dade a office din ba ya dauke sai faman shaqwaba take masa , yawo ya zaga da ita shima bayan ya saka facemask sosai yayi mata siyayya ko me yaga ya burgeshi zai dakko mata, naira tayi kuka tun tana ce masa sun isa har tayi shiru da bakinta. Suna gomawa gida ganin yanda take rike bayanta ne yasa yayi saurin rikota “ meke damunki” kanta ta dan girgiza masa “ babu komai “, kin tabbata ,murmushin jin dadi ta saki kafun ta furta “ na tabbata “, daukanta yayi gabaki d’ayanta , wani wanka suka karayi atare kafun ya matsa mata jikinta, hakan da yayi mata kuwa ba karamin dadi taji har bacci ya dauketa, rage Ac dakin yayi kafun ya saka mata me dumi, fuskar sa cike da annuri ya nufi part din abeey , jinsa yake kamar a wata duniyar, Daidai lokacin da ya shiga falon abeey shima a lokacin abeey ya fito daka wani kofa, kallan fuskar king da take d’auke da annashuwa yayi, kafun ya tanbayi ba asi king ya karasa ya rungeme abeey din ajinka, kamar a mafarki haka abeey yaji dan an dau tsawan lokaci king yayi masa haka , cikin sanyayyar murya king ya furta “ finally abeey, akhii dina zai dawo, I will get another moha” dago da fuskarsa abeeey yayi alamun bai gane ba, “ she’s pregnant “ king ya furta ko kunya babu, a bazata abeey yaji saukar magana kafun ya fara bin king da kallan tuhuma, dariyar da ya kara fito da kyansa yayi har dimples dinsa na lotsawa na duka sides din yayi, cikin karyayyar murya abeey ya furta “ finally my real king is back, Allah na gode maka da ka nuna mun ranar da king dina ya dawo yanda yake, I’m so very happy son, I will become a grandfather now, oh my god, Allah ya sauke ta lapiya , Allah ya bata lapiya “, sosai abeey yayi wa tahee addua wani irin farin ciki na cika zuciyar abeey, jiyar fitar da zaiyi ya fasa ma hakan ya koma ya zauna, number mahma yayi dialing, king na ganin haka yayi saurin barin part din. A part din dada ma yana shiga be dade ba ya fito duk yanda take tsokanarsa, yau kwata kwata be maida mata da martani ba gabaki d’aya hankalinsa na kan babyn sa da ya bari, part din ummey ya nufa, waya ya tarar da ita tanayi, be damuba gaisheka kawai yayi ya bar part din. Yana shiga part din ammey ya tarar da ita tana cin gasash shiyar kazar da taji kayan hadi, gaishe da ita yayi ganin yanda fuskarsa ta cika da annuri ne yasa ta kallesa da murmushi dauke a fuskarta, “ Son Anya wannan farinciki haka , ko dai akwai albishir me dadi”, gashin kansa ya taba a duniya in akwai me saurin gane yanayinsa abayan ammey yake , Daidai lokacin da take saka naman kazar abakinta tayi saukar muryarsa” she’s pregnant ammey”, wani irin kwarewa me shegen zafi ammey tayi a makogwaranta sai faman tari take, da Sauri king ya zuba mata ruwa ya bata , saida tarin ya lafa mata sosai kafun ta kallesa , “WACECE take da ciki son”, a hankali ya furta “your daughter “ , yanxu kam kwarewar da ammeey tayi ya fi Wanda tayi na farko sosai, dakyar tarin ya tsagaita mata, ta soma nunfashi a hankali, ganin yanayin da ta shiga ne yasa ya ajje mata naman da take ci ya gara shafa mata bayanta hartaji nunfashinta na daidaita, kallansa tayi murna sosai d’auke a fuskarta “ finally my son will be a father , and I will be a grandma , oh my god, congratulations son dina “ ta fada tana rungumeshi, shima rungumetan yayi yana kara jin wani irin farinciki na mamaye ransa, tanbayarsa wata nawa cikin ammey tayi, be damuba ya fada mata, wani irin farinciki yagani a fuskarta sosai harya so Bashi mamaki, har Ammeey ta fara lissafin siyayyar da za saka yi wa baby, shidai nasa murmushine , ya dan jima a part din ammey kafun ya bar part din, yana barin part din wani irin ball abbey tayi da plate din Kazan ta da ya sata bare wa, bata zauna a falon ba tanufi dakin ta cikin sauri. Yana fita ya hadu da kabeer da haroon, cikin ladabi suka gaishe da king, abunda ya basu mamaki ganin yanda ya amsa musu cikin sakewa ba tare da ya dauke fuska kamar yanda ya saba ba. Be kara wani minute din ba ya nufi part dinsa. Bin bayansa da kallo su haroon sukai, “bro kaga kuwa abunda nagani, yau yaya king ne ke amsa mana gaisuwa babu hade rai, “ cewar haroon, “ Nima dai abunda ya bani mamaki , amma in tayi tsami ai zamuji, Yaushe zamuje ganin amarya “, kallan baka da hankali haroon ya bishi dashi, “ da alama jikinka tsami yake , ka kwana biyu baka sha mari ba “, dariyar iskanci kabeer ya sakin kafun ya cewa haroon “ Yaushe zamuje part din ammey , yau tun safe ban ganta ba”, banza haroon yayi dashi yayi wucewarsa , shima kabeer din bin bayan haroon yayi suka cigaba da tafiya daman part din ummey zasu . 🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧 ABUJA MAITAMA Babban gida ne katan gaske da ya gaji da haduwa, babban gate din gidan aka bude lokacin da wata mota fara ta shiga cikin gidan ,Daidai parking space mamallakin motar yayi parting kafun ya bude motar, ba kowa bane ya fito face Khaleed dake sanye da bakin suit a jikinsa, wayace kare a fuskarsa da alama waya yake , direct inda entrance din gidan yake ya nufa , knocking biyu aka bude masa komar, karo yaci da zahra lokacin da take bude masa kofar, wayo idanuwa tayi kafun ta saki kara tana rungumeshi “ yaya Khaleed oyoyo, nayi missing dinka “ Daidai lokacin da yake gama wayar , banbareta yayi a jikinsa kafun ya dungure mata kanta “ ke har yanxu wai bazaki girma ba , daddy da oumma zance su aurar dake ko na fadawa Hajiya kin isa aure duk kin cika mana gida “, sakar baki zarah tayi tana kallansa , kafun tayi magana wata hamshakiyar mata ta fito daka wata kofa jikinta sanye da purple din material , sosai kayan suka haska kyakkyawar fatarta duk da ashekaru bazata wuce shakara 43 zuwa 44 ba , da sauri Khaleed ya karasa wajan ta kafun ya rungumeta, “ nayi kewarki oumma ,kullum sai nayi mafarkin abincin ki, da sauri na juya dan ganin wacce yake kira da oumma , sosai nayi mamakin ganin oumma ganin yanda hutu ya kwanta a jikinta ga wani irin masifaffen kyau da ta karayi sak buzuwa abunta, cikin nutsuwa ta sakar masa murmushin da dimple dinta sak irin na tahee lo’bawa “ Nima nayi kewar ka son, yanxu dai kaje kayi wanka kafun kaci abinci “, toh oumma ya fada tare da kallan zahra, da Sauri ta matso wajan “ oumma kinga ko , yaya Khaleed ya dawo yanxu kin dena sona daman yanxu dady kawai ke sona , hajiya ma ta dena sona “, hancinta oumma taja “ waya isa ya taba mun Autaras dina Kema kinsan wasa nake masa sabida ya dawo ne “, dariyar jin dadi kuwa zahra ta saki kafun su shiga kitchen ita da oumma, dakansu suka hada musu lunch, zahra ta nufi dinning tana shirya musu abincin, ita kuma oumma wani tray ta dauka ta nufi wata kofa , knocking din kofar tayi kafun a bata izinin shigowa , wata matace zaune akan wani lallausan carfet duk da manyanta ya gama fito wa a jikinta, murmushi ta sakar wa oumma “ sannu maryama , Allah yayi miki albarka , bakya gajiya da d’a wai niya “, murmushi oumma ta saki ba tare da tace mata komai, akan lallausan carfet din ta ajje mata abincin Daidai lokacin da Khaleed yake shigowa madaidaicin falo urn bakin shi d’auke da sallama, “ hajiya me rankarfe , kiyi aure mu huta” da kuwa wacce yakira da hajiya tayi masa , “ saidai kaine zakayi Auran dan jakar uba, aika dawo zamu dora , bari uban naka ya dawo da kai da waccen ya galalalliyar yazo yayi muku aure , Kai invaka da mata akwai wata yarinyar Dije yar kawar kawata ce da mukayi mutumci amma san yarinyar kamar zararriya, nasan Itace maganinka, ita kuma waccan yaga lalliyar a bata shu’aibu me wanki”, kamar mutumin arziki khaleed ya karaso inda take kafarta da ta mike ta fara yiwa tausa cikin kashe murya ya soma mata dadin baki “ Haba hajiyar mu me yayi zafi haka ,kinsan ba a shiga tsakanin mu dake ko, Indai mata ce zankawo miki ba da dadewa ba , kisha kuruminki”, ta bile baki tayi “oho maka “, kallan oumma dake faman sakin murmushi yayi,”oumma kisa baki mana “ dariya oumma ta saka tana mikewa “kunfi kusa Nidea ba ruwana , hajiya a huta lapiya “, itama hajiya murmushi ta sakar mata “ ala huta gajiya maryama,nagode “, kafun oumma ta fita daga parlourn. Tana fitowa ta tarar da dady da zarah,jakar da ya ajje ya dauka kafin tayi masa Sannu da zuwa , zarah na ganin oumma ta nufi part din hajiya itama , kallanta dady yayi, “Amarsu wannan kyau haka kamar yau ce aka shafa lapiya , kullum sai wani kara kyau kike kamar ba yarinya ba,” kunya kalaman dady suka bata , bata san lokacin da ta dara ba kafun tayi wuce warta part Dinsu, shima bin bayan nata yayi lokacin har ta hada masa ruwa tana kokarin fitowa “ Ah ah me kike nufi , yau fa amaryace zatayi mun wanka gaskiya inasan jin dumin matata nifa ba gwauro bane “Innalillahi oumma ta fara nanatawa aranta , yau taga abunda ya fi karfinta, dady kuwa ko ajikinsa yazo zai rike oumma kuwa tayi saurin Zillewa sai da taje bakin kofa kafun ta sakar masa wani murmushi da ya kusa kifar dashi “ kiyi wanka , bari naje na hada maka lunch dinka “ bata bari ya kuma cewa komai ba tayi ficewarta, dariyar dattako Alhaji kabeer yayi “ maryam badai kunya ba “, yana gama maganar zucin sa ya shige bandaki. FLASH BACK Abunda ya faru, tun lokacin da dady da su zarah suka nema alfarmar oumma ta zauna , gabaki d’aya tundaga lokacin wani irin shakuwa ce ta ban mamaki ta shiga tsakanin ta dasu zarah , duk da a yawancin lokuta gaisuwace take hada ta da dady, sati daya da faruwar haka dady ya yanko musu ticker zuwa abuja , inda yake rayuwa da mamansa, koda hajiya fatima taji labarin maryam itama sosai oumma tashiga ranta musamman yanda taga su zarah na kaunarta har hakan ya so bata mamaki.itama oumma gabaki d’aya ta fawwala lawa Allah lamuranta, a kullum ba ta gajiya wajan yiwa ya’yanta addua, har yanxu bata fidda Saran watarana zata gansu ba. Kwasam wata ranar litinin dady ya bijurowa hajiya cewar yanasan ya auri maryam sai su cigaba da kula dasu zarah kafun aga tahee da ya bata duk da haryanxu ana kan dubosa,itama hajiya sosai taji dadin maganar dakanta ta kira oumma akan auranta da dady yakeso yayi, rasa abun cewa oumma tayi ganin yanda dady yake satar kallanta yana jiran amsarta, a gefe guda ma hajiya na Rokan Allah kar maryam tace ah ah , wata iriyar kunyace ta kama oumma ganin yanda suke binta da kallo, a hankali ta furta “ Allah ya tabbatar da Alkairi”, ba hajiya ba hatta dady saida ya saki ajiyar zuciya, bakaramun dadi hajiya tajiba harda dan kukanta Aushe da raban zata kara ganin auren kabeerunta. A bangaran oumma kuwa har kuka sai da tayi ranar ganin yanda zarah da Khaleed suka nuna farincikinsu.wata iriyar soyayya dady yake nunawa oumma ko kunyar su Khaleed da hajiya bayayi, tun tana jin nauyin yadda yake nuna mata soyayya har ta soma bashi martani, sati biyu da hajiya taga abun nasa na musamman ne tasa aka daura musu aure da oumma . BACK TO STORY A dinning oumma tayi serving Dinsu abinci gabaki dayan su, ko wanne da annashuwa a kan fuskarsa,”yy khaleed har yanxu baka bani tsarabar bafa sai jamun rai kake”, kallanta yayi kafin ya kai wainar masa bakinsa, saida ya tabbatar ya cinye kafun ya soma magana , “ Na fasa , kin bi kin adda Beni kamar kin aikeni”, kamar zatayi kuka ta furta “shikenan “ ta mike da niyar tafiya, daga dady har oumma babu Wanda ya tanka musu, saida yagama cin abincin sa tsaf kafun ya zuba wani a plate , kallanshi oumma tayi alamun karin bayani” zan kaiwa autane, in tayi fushi dani ai babu zaman lapiya , yanxu sai tasa dady ya koreni”,gabaki d’aya dariya suka saki jin kalaman sa , yana barin wajan shima dady ya kalli oumma , “yanxu saura aikin lada , kin bawa kowa abinci a baki ban dani”, da Sauri oumma ta mike , dady yayi saurin rike hannunta , waigawa oumma tayi gudun kar wani ya gansu “ dan Allah kasakar mun hannuna kar wani yashigo”, shikenan zauna ki baki a baki , ba musu kuwa oumma ta fara bashi, befi spoon biyar ba ta gudu falourn hajiya . ( Soyayya bata tsufa, dady ka bani kunya 😂😂). 🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧 🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧 A tsaye ya tarar da ita tana gyara dakinsa , da Sauri ya karasa ya karbi towel dinta “ banaso ki bari” sakin baki tayi tana kallansa yau taga ikon Allah “ ka bani gyara fa nake “ a maimakon ya bata kamata yayi ya zaunar da ita kafun ya taba cikinta, “karna kara gani kinyi wani aikin , okay “lapiya ta fa kalau, shima amsa ya bata “ eh na sani ai , common me zakici” bata dade da Shan complex ba “ na koshi” me kika ci!? , itama amsa ta bashi da complex, girgiza mata kai yayi “ it’s not a food, zo muje kici wani abincin”, zanyi amai idan naci kabari anjima kaji,” be kuma ce mata komai ba sai cikinta da yake shafawa a hankali har yanxu jinsa yake kamar a mafarki, itama lafewa tayi a jikinsa sabida yanda take jin dadin yanda yake shafa mata cikin. Yinin ranar gabaki d’aya tare da tahee yayi shi, hatta abinci da kansa yake bata,ita kuma sai faman narke masa take. Da daddare ma lokacin da zasu kwanta sai faman shagwaba take masa hakan da take kuwa ba karamun zautar dashi yake ba musamman breast dinta da suka cika masa ido ga wani girma da yaga sun karayi masa, be san lokacin da ya fincike rigar jikinta ba ta ynda zai ga breast din da kyau. Ga baki d’aya ta birki ta masa tunanin, hatta lokacin da zai kusanceta jiyayi ta canza masa, kara susucewa king yayi gudun karya ji mata ciwo ne yasa yake binta a hankali sai faman surutai yake yi. GIDAN AUNTY MSS LEE 07041879581 BOOK 1 Page 65_66💖 Yau ya kama Monday, Tahee tana idar da Sallah ta d’an yi gyara gyare kafun king ya dawo, Tana kammalawa tashiga wanka ganin lokaci na tafiya, sosai tayi shirinta na zuwa makaranta Bayan uban Noddles din dataci duk da haka saidata dauki wasu chocolate da yawa a jakarta, kallan lokaci tayi yau ta kusa makara gashi be dawo ba.Mikewa tayi ta nufi dakinta wani wafer ta dakko guda biyu da chewing gum shima,tana sakko wa kasa shikuma yana shigowa falourn, Tsayawa kallanta yayi from head to toe kafun ya tanbayeta inda zata je da shigar uniform haka, sakin baki tahee tayi tana kallansa “ kaman ta yau Monday?”, girgiza mata kai yayi alamun ah’ah ,” Lokacin school fa yayi har na fara latti”,dauke kansa yayi kafun ya furta “ Babu inda zakije , you’re not feeling fine “ da Sauri ta karaso gabanta har yana saurin rikota “ Muna da text fa yau honey, please nifa lafiya ta kalau babu abunda yake damuna “ ta karasa zancanta cikin narai narai da ido, kallanta yayi kafun ya sakar mata peck a goshi “ you won’t go anyway banaso ki wahalar mun da Baby na”, ji tayi kamar ta saka ihu, tun ba aje ko ina ba ya fara fifita Babynsa akanta, Bata kuma kallansa ba ta juya zata tafi,” Ina zaki”, shiru tayi masa kafun a hankali ta furta “ zan cire kayana”, jakar hannunta ce ta fadi duk chocolate dinta suka fado kasa, kallan uban chocolate d’in ta dake cikin jakar yayi, wani hau shin ne ya kara kamata cikin Sauri ta fara kwashe ku ko kallan inda yake bata yi, da mamaki yake kallan yanda mood dinta ya canza , yazo zai yi mata magana tayi saurin hawa steps din dakinta.” Oh God “ king ya furta kafun ya nufi dakinta,akan gado yasameta tayi rubdaciki da Sauri ya karasa Wajan ta “ What’s wrong with you my Baby”, ya fada yana dago da ita, kwace jikinta tayi wani saban hawaye na kara zuwar mata zata kara komawa ya rikota a rikice “ No please! Meke damun ki ? , Cikin kine ?,Baby nane?” Duk shi kadai ya kara jefo mata tanbayoyin, wani karin ba’kin ciki ne ya kara kamata wato shi ta Babyn sa yake bata ita ba,cikin dan karfi karfi ta kara fusge hannunta zata koma kwance ya kara rikota , gabaki d’aya ya birkice ganin yaki sakin tane yasa ta saka masa wani saban kukan, runtse idanuwansa king yayi da tasan yanda yake jin kukanta a cikin zuciyar sa da bata soma ba , ji yake kamar ana Caka masa wutar karfe a cikin zuciyarsa, ganin ta’ki dena kukan ne yasa yayi hugging dinta” stop crying ,nayi lefi ko to am sorry”, a ‘kulle ta furta “Ni babu wani sorry! Yanxu ka dena sano komai Baby Baby Baby, Babynka kake so bani ba , Sabida Babyn ka hanani zuwa nayi text dina ni babu ruwana da kai “, ta karasa zata fashe masa da wani saban kukan , murmushi ne ya su’buce masa kafun a hankali ya d’ago face dinta yana share mata hawaye , taki kallansa sai faman kunbure kunbure take “ Shikenan nayi laifi! Am sorry! A dena wannan kukan , and kidena kishi da Babyn mu, ke kadai ce Baby na , shi kadan zamu san mushi kinji”, ka fada ta d’age masa alamun bata hakura ba, kunnensa biyu ya kama “ ohk tell me , me kikeso ! I promise zanyi but ki share wannan hawayen kafun na shanye kayana”, saurin goge hawayen tayi “Muna da test a school “ ta karasa a marairaice,”shiyasaki kuka?”,Bakinta Tadan turo masa “ ok jeki gyara face d’inki” da Sauri ta run kura zata tashi ya riketa “please be careful “, kanta kawai ta daga masa , cikin kankanin lokaci ta gyara face dinta ,”ki kula please cikin ki be yi kwari ba and banasan kisha sweet da yawa , and your lunch kici on time , take care of your self”, a bazata yaji saukar kiss akan Le’b’bensa,” You’re my hero ! I always cherish you “, ganin tana letti ne Yasa shi yin shiru yaga alama yau rigima take ji amma shi kadai yasan ya yake ji, yace zai yi driving dinta ta lallashi ya hakura ganin yana aiki tun dazu shima “, da kyar ta samu ya hakura shima still sai da ya kara mata motar sojoji guda daya , duk da ta hana su shiga cikin makarantar iya bakin kofa suke tsayawa , motar da take cike kawai suke shiga da ita,Mss Stella na gaba ita da driver, Allah ya temaketa tana shiga Teacher din da zai sauke su Civic education ya shigo, kafun ya fito wani Malamin ya shigo shima, a period na ukune suka test dinsu na Biology, saida aka fita break ne Husna ta kalleta “ yau basa ban ba kinyi letti , ai na dauka bazaki zo ba “, murmushi Tahee ta sakar mata “ Wallahi ba haka bane Husna ,Dan abune ya sha mun kai shiyasa “, itama murmushin Husna ta sakar mata “ Daman ke ai kullum ina da amsar maganar mutum, Ni kinga yanxu i’m hungry ! Let’s go and it some food kafin lokacin dawowa yayi “, gyada mata kai Tahee tayi kafun su fito daga class din , yawanci student basa compound, daddai kune zaki gansu a waje, da sauri stella ta fito daga mota zata nifo su, Tahee tayi saurin dakatar da ita batare da ta bari husna ta luraba, suna shiga cikin cafeteria aka kara binsu da kallo musamman Tahee dake sanye da facemask, Daga gefen su yan group din The untouchable ne wato yan class d’insu Tahee, salma ce ta kalli kubra kafun ta kalli Ruky , ta gefe d’aya ta nuna musu Tahee, gabaki d’ayan su shege suka sa da ya d’au kulan wasu daga cikin yan set din, Tahee da husna kuwa basu san sunayi ba gabaki d’aya harkar gabansu suke . Tashi Ruky tayi kafun ta nufi wani senior dinta da kana kallansa kaga tantiri gabaki d’aya kusan rabin wandanshi yayi asdawun ga wani irin ba’ki da lebensa yayi, dage gefensa ma wasu yara ne da suke da sak irin shigarsa, nuna masa Tahee Ruky tayi kafun ta koma seat dinta suna kara sakin wani shewar. Cikin tafiyar yan iska guy d’in ya nufi table din su Tahee , ragowar yan uwansa ma suka bi bayansa. Doughnuts din da aka zubawa musu ta fara bi da kallo gabaki d’aya sai taji ta kasa cin sa, a hankali ta daga gefan facemask d’inta Daidai baki tafara sipping ice cream dinta,kafun ta d’an d’ana sprinkles din gabanta. “Ke yan mata ji mana “ cewar Mata shin saurayin yana d’an d’age mata gira , ko kallan inda suke Tahee batayi ba sai ma face masks din fuskarta data gyara,”Ba dake nake ba” ya kara furtawa a zuciye , yanxun ma babu Wanda ya kula sai ma mikewa da sukai ganin lokcin break ya ‘kare , jinjina kansa guy d’in ya fara , ta’bashi na kusa dashi yayi “ Cool down TJ, Cool , kar ka hadamu kowa kallanka yake “ ‘Daga idanuwansa yayi gabaki d’aya yaga idanun ‘yan cafeteria d’in na kansa, dogon tsaki ya ja kafun ya fita daga Wajan , shikadai yasan me zaiyi wa Tahee. Tunda suka koma class ita da husna basu kuma fitowa ba sai da aka tashi, kamar kullum su stella Suna jiranta a inda tace musu. Tana koma wa gida ko uniform din jikinta bata cire ba bacci ya dauke , a haka King ya dawo ya tarar da ita, da Sauri ya kara sa inda take ,hijabin jikinta ya cire mata tare da daukar ta gabaki d’aya yayi sama da ita, yana kwantar da ita ta motsa kafun ta ware idanuwanta, da mamaki take kallansa “ Yaushe ka dawo “ ta fada cikin muryar bacci “now , are you okay” kanta ta daga masa ,”karfe nawa “ agogon hannunsa ya nuna mata 3:15,kamar zatayi kuka “sorry bari na dafa maka abinci,bansan bacci ya d’auke ni ba” binta yayi da lumshash shun idanuwansa “ kinci abinci?” Kanta ta girgiza masa “ Bana jin yunwa”, ganin yanda jikinta yayi weak yasa be ce mata komai ba y d’auke ya, kusan almost 30 minutes sai gashi sun fito cikin wasu kadan da ban da Alama wanka sukai, suna sakkowa down stairs suka ga tray akan center , Tahee na ganin kular taci wani yunwa ta kamata , fatan tsaki ne a ciki har da lashe baki kamar taga wani abu, “ what’s this “ king ya fada kamar yaga wani abun ‘kyank’kyami, batare da ta damu ba ta fada mashi sunan abun, spoon kawai ta dauka zata faraci yayi saurin janyewa , da Sauri ta kallesa kamar zatayi kuka “ ka bani abincina “ da wani irin kallo ya bita dashi dayasa tsigar jikinta tashi, cikin wani murya ya furta “ze bata miki ciki , bazakici wannan food ba ,let’s get another one”, kukan shagwaba ta sakar masa , da Sauri ya mayar mata da food din, spoon d’aya ta miko masa yayi saurin kauda kai, wani kukan take shidin yi ya bude bakinsa ta saka masa, cikin dan tabe baki ya cinye faten, wani spoon ta kara kai masa baki yayi saurin girgiza mata kai “ ci kayankii “, Narai narai tayi masa da ido,shima da wani irin kallo ya bita dashi “ok wat will I get in return “, ido d’aya kawai ta kashe masa, cikin shagwaba tasa shi cin abincin tun baya masa dadi har ya fara jin dadinsa, shima sosai yaci faten sai faman dariya take masa. Lokacin da Dada ta samu labarin cikin tahee har kuka sai da tayi sabida farinciki, da kanta ta shiga kitchen ta dafa wa Tahee fatee, sai faman masifa take ita kadai anbar yarinya me help tana fita makaranta, ita dai ummey sai Tausar Dada take ganin cikin har yanxu be fito ba, da kyar ta shawo kanta ita da magma da ta kira a waya , gabaki d’aya yinin ranar ammey bata fito ba sai su aunty da Suka shigo taya su ummey murna duk da cikin zuciyar aunty wani irin kululun bakin ciki ne cike a makoshinta. Lokacin da Amrah taji labarin cikin Tahee sau biyu tana suma kamar wata zautacciya haka ta dawo , gabaki d’aya ta bata cikin ‘Dakin, sai faman surutai take , ita bazata yadda ba .Su Ihsan ma da suka ji Labarin har da kida suka sa suka tashe abunsu. *****Ana idar da sallah isha’i ta saka masa rigimar zuwa part din Dada, ya lallasheta dan bayansan wannan fitar tata yanxu ma, yana ganin zata saka masa wata sabuwar rigima ya hade bakinsu waje d’aya , Bakin rigimar ya tsotse sarransa kafun yayi romancing dinta, yanda yake bi da ita har wani lumshe ido take dan wani irin dad’i da taji yana ratsata. Door bell d’in da aka Sanna ne ya tsayar dashi gabaki d’aya idanuwansa yan canza kala sai wani nunfarfashi da yake saukewa, singlet d’in jikinsa ya saka gabaki d’aya ji yake kamar babu wani abu da yake bukatar kamar kusantuwa da ita, ta door bell d’in yaga ihsan ri’ke da baban tray, karamun tsaki yaja kafun ya bude door din , gabaki d’aya ransa a had’e babu alamun fara, tunda ya bude ihsan ta sunkuyar da kanta kasa, shima be ce komai ba ya karbi Tray din hannunta, direct D’akin da take kwance ya nufa , a yanda ya bar ta a haka yazo ya sameta sai faman lumshe masa idanuwa take, yana zuwa inda take bata jira yayi magana ba ta had’e bakinsu waje d’aya , wani irin zaro idanuwansa king yayi, Gawani irin shock da yaji yana zuyartarsa, kwata kwata idanuwanta a rufe suke bata san ma me take yi ba, rigar jikinsa take kokarin cire masa, ganin hakan ya temaka mata wajan cire rigar, gabaki d’aya sun zauce musamman king da yaji wani irin dad’i na ratsashi, tana bukatar cikin abinci shiyasa ya dan raba jikinsa da nata kadan, wani irin kuma Tahee ta saka masa, wani irin yaaam take ji a jikinta abunda yake matane kawai take jin dad’insa , be auneba yaji ta dora hannunta akan mararsa, wani irin karan dad’i king ya saki kafun ya kara had’e bakinsu waje d’aya, cikin kankanin lokaci suka fita daga hayyacinsu, romancing d’inta yake kawai shima , yana shigar ta yaji wani irin masifaffen dad’i ya karad’e ko ina najikinsa, Sam ya manta da ciki a jikinta , aikin gabanshi kawai yake , ya dade yana saduwa da ita, zafin da ta fara jine yasa ta fara dukanshi, Sam be san tanayi har saida ya gamsu kafun yadawo ajiyar zuciya , lokacin gabaki d’aya Tahee ta dena kukan sai ajiyar zuciya da take saukewa , rungumeta yayi cikin lallashi batare daya ce mata komai ba ya fara shafa mata bayanta, da’kyar ya samu muryarsa ta fito” Allah yayi miki albarka wifey, thank you so very much, please don’t leave me , I can’t leave without you”, sosai taji dadin kalaman sa hannunta d’aya kawai tasaka ta rungumeshi sai da ko wannansu ya dawo Daidai kafun ya dauke ta gabaki d’aya sukai toilet, shi dakansa yayi mata wanka kafun ya canza bedsheet din gadon, abincin da ihsan ta kawo yayi serving dinta, da kanshi ya fara bata tuwan tana chi saida ya tabbatar ta koshi sannan ya ajje , ganin beci komai ba yasa itama ta fara feeding dinshi da kanta. *******Washe Gari ma da kyar ya batta taje school saida ta hada masa da shagwa’bar da yake matukar zauta masa tunani, Tunda taje school ta lura da Wanda husna take fad’a mata ‘yan untouchable sai wani Banzan kallo suke binta dashi, bata nuna tasan sunayi ba har lokacin break. Suna zuwa cafeteria wannan karan basu ci abinci a ciki ba , class suka dawo suka ci abincin su.Tj gabaki d’aya sai zuba idanuwa yake yaga ta inda zata ‘bullo, ganin be ganta bane yasashi washi wata kwafar , ai gobe ma ranace . Har aka kare weekend Husna bata bari Tahee ta had’a hanya da su Tj ba dan tasan basu da mutumci shiyasa take gudun abunda zai faru, itadai Tahee saidai tayi murmushi batare da tace komai ba. A bangaran su Tj da yan untouchable kuwa gabaki d’aya sun tamawa su Tahee jira suke Monday tayi kawai dan har meeting suka had’a ran Saturday akan abunda zasu yiwa Tahee. A bangaran ma’aurata ma wani iriyar soyayya suke zubawa me Tsayawa arai kusan kullum tarairarai junansu suke, Tahee har ta rage jin kunyarsa, duk abunda yake bu’kata zagewa take tayi masa , hakan yasa wani irin soyayya king yake mata da shi kansa bazai lissafa adadin taba. A cikin family ma wani irin kulawa su Dada suke bawa Tahee, Ummey ma ba’a barta a baya ba dan sosai suke kula da ita, mahma da small mom ma ba’a barsu a bayaba kusan kullum sai sun kira sun tanbayi ya jikinta, ihsan da su sumayya ma duk lokacin da suka dawo daga makaranta a part dinta suke yini yanxu kafun king ya dawo , shiyasa wata iriyar shakuwa ta kara shiga tsakaninsu, motsi d’aya zasu tanbayeta ko tana bukatar wani abu, abun har dariya yake bata. ➰➰➰➰➰➰➰➰➰ MONDAY Yau tunda ta tashi da d’an zazzabi ta Tashi kadan ga wata iriyar rigima da take ji da iya yau, hatta shi kansa gogan lalla’barta yake da kanshi, snacks dinta kawai ta iba a cikin school Bag dinta sai ice cream Guda biyu data d’iba, Tana zuwa school Daidai lokacin da husna tazo Sukai karatun da suka sabayi, mss hauwa daga ke daukarsu computer ta rabamusu test d’insu, gabaki d’aya saida ta fad’i score d’in kowa , gabaki d’aya Tahee ce overall sai husna dake class rep, hakan ya ‘kara ba’kantawa ‘yan the untouchable sabida gabaki d’ayansu babu Wanda ya tsinana abun arziki a cikinsu. Ana fitowa break su husna sunzo zasu fita Suka tare musu hanya, cikin wani banzan kallo Tahee ta kallesu daman ta gaji da halayensu, “ excuse me “ Kawai tace musu tare da ra’bawa zata wuce , Zukkyce tayi saurin tare hanyar, “ idan mun’ki matsawar ubanme zakiyi”, a kaikaice Tahee ta kallesu tare da jan tsaki tayi wucewarta, itama husna da wani banzan kallo ta kallesu tayi wucewarta. “Kutumar uba “ cewar kubry ,kallanta salmyyy tayi “ Gaskiya yarinyar nan ta rainamu,idanta san wata ai bata zan wata ba , yau zata gana kuranta “ tana gama fadar hakan suka wuce cafeteria su ukunsu, koda su Tahee suka karbi abincin su waje suka samu inda bakowa Suka ci abincin su, sunzo zasu koma Tj ya tare mata hanya, da wani banzan kallo itama Tahee ta bisa tare da ra’bawa zata wuce lokacin har an fara taruwa ganin TJ awajan, kara tare mata hanya Tj yayi akufe ta d’ago da manyan idanuwanta, bata kuma cewa komai ba ta juya Zata wuce, hannunsa ya d’aga da niyar ta ‘ba mata hijab ta daddage ta tsinka masa mari, ba ita da tai marin ba, gabaki d’aya kowa cikin firgici ya bita Dashi sabida sanin halin Tj da akai da kuma mahaifinsa da yake biyemasa ba’a masa komai a makarantar, wasu daga cikin student har sun fara tausayawa Tahee, Husna ma cikin d’an tausayawa ta kalli Tahee cikin rad’a rad’a ta furta “Tahee ki basa hakuri mu wuce kinji, karya ‘bata mana karatu, “ banza tayi da husna tahee kafun ta d’aga hannunta cikin alamun warning , “ daga yau sai yau, duk ranar da kazamun hannunta yayi kuskuren yin gangancin ta ‘bamun hijab, ba mariba ‘yan yatsun zan cire stupid kawai “, wani bacin raina ya kama Tj ganin yanda ya wulakanta a gaban mutanan da suke tsoransa ,su zukky ma kallan zaki sani suke binta Dashi ita kuma ko a jikinta.” Ni kika mara “, wani irin bombastic side eyes Tahee ta bishi dashi kafun ta furta “ an mara do your worse “, tana kammala zancanta taja hannun husna suka koma class , gabaki d’aya Husna ta shiga damuwa dan tasan su Tj bazasu ta’ba hakura da abunda Tahee tayi musu ba, su untouchable ba suna shigowa kallan Tahee Sukai alamun zaki sani , gabaki d’aya tana kallansu amma babu Wanda ta tanka sai ma maida hankali da tayi kan Topic d’in da ake musu har lokacin sallah yayi sukayi sallah. Yau wacce zatayi musu biochemistry bata zoba shiyasa yau suka tashi da wuri, suna fitowa daga class yawanci student basu tafi ba kowa jira yake yaga hukuncin da Tj zaiyi wa Tahee, su husna suna cikin tafiya sai ganin Tj Sukai da wasu boys a bayansa, hannu yasa a bazata ya dallawa husna mari, be sauke hannunsa ba itama ta d’aga nata hannun ta zuba masa mari, gabaki d’aya wajan shiru ya d’auka, a zuciye ya kalli mazan nan, “ inaso ko wace shegiya acikinsu ku ‘barkamun hijabin jikinsu, yau zasu gane wanene TJ a makarantar nan, gabaki d’aya sai naga wanene ubansu”, hannu ya d’aga zai taba hijab d’in Tahee wasu irin ratsats tsun motoci na bugawa a jarida suka shawo cikin makarantar da mugun gudun gaske , gabaki d’aya student din maida kallansu Sukan kan motocin da akalla zasu kai 8 ba’ka’ke kallo ga wata farar ratsatssiyar BMW a tsakiyarsu, cikin wani irin salo motocin nan sukayi parking , kafun kabaki d’aya mutanan cikin ba’ka’ken motar fitowa ko wannansu sanye da suit ba’ki’kirin ga wani Ba’kin glass da yake fuskarsu, ko wanne ka kalla fuskarsa sai ya kusa razanaka sabida yanda ko wannansu ya hade rai ga bindugogin da ke hannunsu, labari har ya kaiwa principal , hatta me makarantar sai da ya fito dan ganin wanene yazo fuskarsa sai faman had’a gumi yake,tsawan mintuna biyu kowa jira yake yaga wanene a cikin motar, hatta me makarantar yaja layi tare da malaman makarantar gabaki d’aya, zaki ne ya fito cikin shigar ba’ka’ken kaya fuskarsa Sam ba annuri, ya bud’ewa king kofa, cikin kwarjini king ya zuro kafarsa d’aya me sanye da farin wando far’kal dashi tare da ta kalmin kafarsa half shoe me shegen kyau sai faman daukar ido yake, tun kafin ya fito daga cikin motar gabaki d’aya da yawa sun fad’a san ganin ko wanene hatta yan untouchable da zukky harta fara tunanin tazana matarsa dukda bata gansa ba, cikin wani irin salo king ya fito daga cikin motar gabaki d’aya sakin baki student sukai ganin kyakkyawan balaraben da ko a kyawawa da wuya a tsamu me kyawunsa, sanye yake cikin white suit fari kal dashi ga gyaran gashin kansa na yau na musamman sabida tufkeshi da yayi kad’an akye yarsa daga gefe d’aya kuma ta fuskarsa lallausan gashin kansa ne da yazo har wajan idanunsa, lips dinsa gabaki d’aya yayi wani irin turuwa ,idanuwansa sanye yake cikin bakin glass gabaki d’aya babu fara’a akan fuskarsa. Da yawan daga cikin student sun fara sanshi kallansa da sukayi kawai hatta su zuky kowa yana fata dama mijintane , ne makarantar na ganinsa yayi saurin gaisheshi suma teachers d’in gaishesa Sukai cikin girmamawa, babu Wanda ya kalla a cikinsu sai matarsa da ta zuba masa idanu, a hankali ya soma ta kowa su zaki suna binsa a baya , be tsaya a ko ina ba sai a inda Tahee take, gabaki d’Aya mutanan kawanya sukai musu suka zagayesu ba a ganinsu , zaki kuma a zuciye ya dora bindigarsa kan Tj. ♾️♾️♾️♾️♾️♾️♾️♾️♾️ ♾️♾️♾️♾️♾️♾️♾️♾️♾️♾️♾️ YOLA GIDAN AUNTY 07041879581 Mss Lee BOOK 1 Page 67 💖 YOLA Wani irin kururuwane yake tashi a cikin falon, a haukace suka fara surutai cikin yaransu da bashi da dad’in ji ko sauraro,hayakin da suke bankawa suka ci gaba da bankawa cikin russunar da kai , sun dau dogon lokaci suna haka kafun wani irin ba’kin hayaki ya karad’e ko ina na cikin falourn, cikin wani Sauti mara dad’in ji aka soma magana , “ kunyi sake da damar ku, ayyukan da kuka dade kuna jiran cikar burinsa yana neman rugujewa cikin kankanin lokaci, samuwar jini a cikin jini tabbas yana nufin rugujewar ayyukanku baki d’aya hhhhhhh” aka karasa zancen cikin sakin wata iriyar dariya mara dad’in ji , gabaki d’ayansu zubewa sukai akan gwiwowinsu kafun su sunkuyar da kansu ‘kasa ,” tuba muke shugabanmu, tuba muke abun share musu hawaye , a nema mana mafita “, suke ta nanatawa gabaki d’ayansu, wata sabuwar dariya aka kara ‘narkewa dashi , a kausashe ta furta “ dama d’aya ce ta rage muku, kusalwantar da abunda ke cikinta , idan kukayi sake da damar jinin nan yazo duniya tabbas abunda ke ‘Boye zai fito fili” tana kammala zancenta ta ‘bace batare da ta basu damar sake yin wata maganar ba. Shiru sukai gabaki d’ayan su kowa yana tunanin mafita , a zuciye wacce ake wa la’kabi da Abar kauna ta mike ,” bazai sabuba, dole cikin nan ya zube idan ba haka ba gabaki d’ayansu sai na kashe su har lahira, bazai taba bari burina ya salwanta ba, bazai taba faruwa ginin da na fara tsawan shekaru ya rugeje ba dole nayi wani abu, wannan karan da kaina zanyi yakin, da kaina zan fuskanceta”, itama bata jira cewar suba ta ‘bace , gabaki dayan su sunji dadin kalamanta, shiyasa tana fita suka fara jinjina mata daman duk cikinsu tafi kowa hatsabibanci, tunda tace zatayi toh tabbas zatayi din kamar yarda tace . ♾️♾️♾️♾️♾️♾️♾️ ♾️♾️♾️♾️♾️ ♾️♾️♾️ ♾️ Kallansa tayi ganin yanda fuskarsa take a had’e, a hankali ta furta “ am sorry,sweetheart “, bece mata komai ba sai kyakkyawar fuskarta da ya cigaba da kallo kamar yasamu TV. Tunda zaki ya dora bindigarsa akan Tj, wani irin gudawa ya kwace wa Tj, sai wari da sutar da yake matsewa ce ta fito, ba shi da ka nuna wa bindigar ba, gabaki d’aya kusan Tsure wa yan makarantar sukai ganin abunda ya dauke musu kai kamar a film, kowa tanbayar da yake yiwa kansa meyasa balaraben can yaje wajan Tahee, suma su zuky wani irin gumine ya fara tsats tsako musu , tun ba’azo kansu ba jikinsu rawa yake . Saida ya gama kare mata kallo yadda yakeso kafun ya furta “ are you ok”, kanta ta d’aga masa kafin ta sakar masa murmushin da yake sanya ya masa zuciya , duk da ransa abace yake hakan be hana yaji bacin ransa kaso mafi yawa tafiya ba Amma duk da hakan be nuna mata ba, dauke kansa yayi kafin ya riko hannunta guda d’aya , gabaki d’aya wani irin mube musu hanya sojojin sukai kafun su sara masu, a hankali yake tafiya da ita hannunsa d’aya cikin nata,ba dalibai ba hatta malam suma sakin baki sukai ganin wani irin kyawu da sukai musu, ganin sun kusa karasa wa cikin motar ne yasa zaki bugawa Tj kan bindiga dayasa Jini fara zuvowa , wani irin kara Tj ya saki gabaki d’aya ya daburce, bude mata mota king yayi da kanshi, kafun ya zagaya inda Zaki ya bude masa yashiga, babu Wanda ya kalla acikin malaman har me makarantar da yake basa hakuri, tsoransama karya sa a kulle masa makaranta. Shima zaki cikin motar suka shiga kafun gabaki d’aya ragowar sojojin su tafi su tsaka motar king a tsakiya subar wajan, banda mota da aka bar sojoji guda biyar , suna ganin bace war motar king d’aya ya zabgawa TJ mari” kai dan iska ko”ya furta kafin ya umar ta akawo masa ragowar abokan Tj din, su musty har Anfara kuka tun ba aje ko ina ba, hatta yan untouchable sai da yasa aka kawo masa, be mari matan ba sai wankin ba daki yasaka sukai, kamar zasuyi Hauka haka suka wanke bandakin , tsabar mugunta babu ta kalmi yasa suka shiga haka suka saka kafafuwansu a ciki, gabaki d’aya toilet din makarantar yasa su wanke har su Tj din da yake tafiya a kwale sabida kashin da yayi a wando, duk da Anzo daukar su basu bari sun tafi ba sai da yasa su tsallan kwado da zaman kujera, tun student nanan har aka tafi aka barsu , yawanci student Allah shikara suke musu dan kowa ya san halinsu, saida sojojin nan suka tabbatar bazata moruba kafun su bar makarantar bayan wani horon punishment din da suka da aka yiwa su Tj , da Sauri kuwa me makarantar yayi na’am dan yasan wanene king, baya magana biyu, dama shima ya gaji da ba’kin halinsu da suke kokarin sawa a kulle masa ba shiri, da rarrafe su TJ suka soma tafiya sabida yanda kafarsu tayi tsami ko motsata basasan yi gabaki d’aya ko wannansu fuskarsa ta jike da hawaye, su musty sai faman tsinewa Tj da su Ruky suke. ****** Tunda suka shiga cikin mota be ce Mata komai ba sai hannunta guda d’aya da yake murzawa a hankali, d’an d’ago da idanuwanta tayi ta kallesa ganin ya dauke kansa yasata matsowa kusa dashi sosai, dan short din unique labulen da ya karesu ta gyara kafun ta danyi dage Daidai kunnansa “ My love “, ta furta cikin wani irin salo, lumshe idanuwansa yayi duk da wani irin abu da yaji ya taso masa amma sai da ya danne ya shareta, kara dagowa tayi akaro na biyu amaimakon tayi masa magana sai ta Dan ciji kunnansa kadan, da wani irin shock ya kalleta, ido daya ta kashe masa kafun ta dan marairaice masa fuska Daidai lokacin da zaki yayi parking . Door din mota ya bude mata, suka nufi part dinsu har yanxu hannunsa yana cikin nata. Har suka shiga cikin daki be ce mata komai ba , saida ya tabbatar tayi wanka , yasata cin abinci , duk yanda taso yi masa magana yaki bata damar hakan, ruko hannunsa tayi cikin nata “ Am sorry “, kallanta kawai yayi kafun ya lumshe mata ido har yanxu bece mata komai ba, ko karin tashi yake tayi saurin d’anewa kan cinyarsa “Am sorry babyna, ni banasan wannan shirun naka , kana so shima babyn mu yayi fushi?” Ta karasa tana dora hannunsa akan cikinta, lumshe idanuwansa yayi kafin ya kara rungumeta a jikinsa, “ you won’t be going to school for now , okay?” Tasan ransa zai baci daman, bata yi masa musu ba ta d’aga masa kai, food din tayi serving dinshi, dakanta tayi feeding baby dinta “ are you upset?” Cewar king , yalwataccen murmushi ta sakar masa kafun ta cusa hannunta kan lallausan gashin kansa tana wasa dashi” me yasa zanyi fishi da sweetheart d’ina?,Am not angry”, how are you feeling, do you need anything “, da Sauri ta daga masa kai alamar eh,” inasan choki choki, goruba, taura sai magarya”, kai ya jinjina mata “ zansa a duba miki a super market “, dariya ce ta kwace mata wai super market,pillow d’aya ta dauka ta buga masa zata gudu yayi saurin rukota, cakulkulu ya fara yi mata tana dariya “ no please na dena , na dena please “, tahee take fada , ganin tana kokarin kwarewa ne yasa ya lafa da iya mata cakulkulun, hira ta fara yi masa, yana sauraronta har lokacin sallahr la’asar yayi ya tafi masallaci. Karfe 8:40pm ihsan ta kawowa Tahee abinci wai inji ummey, duk yanda Tahee tayi da ita akan ta zauna ta’ki zama ta gudu,Sabida kwata kwata bataso king yazo ya tarar da ita a part din. Tana bud’ewa taga kafiyayyiyar masa da miyan Taushe da yaji man shanu,ya wunta ne ya tsinke shiyasa bata jira king ba ta dakko plate ta soma cin abin cinta. Sosai taji masan saida taji ta Ko shine ta ajje ragowar masan tana maida nunfashi, ta mike da nufin komawa kawai taji juwa na neman kada ita da Sauri ta koma ta zauna, sai da ta kara kusan mintuna 10 a zaune kafun ta mike da niyar ta shi,‘kulle war da cikinta yayine yasa ta sakin karar azaba kafun ta rike cikin nata tana ambatan sunan Allah,’kara kulle wa cikinta yayi da yafi na farko a zaba, “ya Allah cikina”, Nunfashinta ne yake kokarin futa daga jikinta sabida wani irin azaba da tajii a cikin ta , take a wajan Jini ya fara bin kafarta,’kara Tahee ta saka “Jini,jini,jini” ta kuma sakin gigitacciyar kara, banko ‘kofar da akai ne yasa ta d’ago kanta a wahala , Wanda ta ganine yasa ta fashewa ta kuka ta yanke jiki ta fadi, da wani irin masifaffen sauri king ya ‘karasa inda take be tsaya bata lokaci ba ya d’auketa kamar baby bayan ya lullu’be mata jikinta sai cikin motor , ga baki d’aya ya rud’e ,zaki zaiyi driving king ya hana tare da kar ‘bar mu motar, idanuwansa har sun fara canza wa a kausashe ya furta “ kar Wanda ya sani a cikin gida , duk Wanda yazo neman ta mun d’an fita ne “ yana kammala zan cansa ya ja motar cikin matsiyacin gudu sai asibitin NAHYAN. GIDAN AUNTY 07041879581 ( mss Lee 💖) Book 1 PAGE 68 Direct yana shiga cikin asibitin ta baya yayi parking, da Sauri ya daukota ganin yanda jinin da yake zuba a jikinta har yanxu be tsaya ba, office dinsa na sama ya hau kai tsaye bayan ya bada umarnin a kira masa Dr Maryam, tunda kafun ta karaso ya tsayar da jinin, tana zuwa be jira ta cewar ta ba suka fara aikin duba Tahee , gabaki d’aya fuskarsa tayi jawur jijiyoyin kansa sun tashi, cikin ikon Allah suka gano matsalar, tare da d’aure mata mahaifa sabida yanda wajan yayi rauni, saida ya tabbatar komai yayi settling kafun ya sauke a jiyar zuciya , test d’in da ya umarci Dr maryam tayi masa ne ta kawo masa , akan gadon sa dake cikin dakin office d’in take , a hankali ya kara murza hannunta cikin nashi kafun ya sauke idanuwansa kan kyakkyawar fuskarta da yi fayau da ita, hannunsa d’aya ya d’ora kan cikin ta yana shafawa a hankali , cikin ranshi kuma wani irin tafasa ransa yake, gabaki d’aya jijiyoyin kansa sun mike tsaye , launin idanuwansa sun sauya daga ainahin kalar su zuwa wani kalar launin ja daban, be san wanene yake gangancin ta’ba masa ciki ba , shikansa be san Wana irin hukunci zai yiwa Wanda yake ‘ko’karin salwantar masa da ciki,sunan Allah ya fara nanatawa aransa ganin yanda ransa yake ‘kara baci , yana dad’e a zaunan da yake yana karanto duk adduar da tazo masa rai kafun ya fara yiwa Tahee addua itama . Agogon hannunsa ya duba almost past 10, allurar baccin da yayi mata har yanxu be sake taba , Sabida ba ‘karamin jigata tayi ba , Sabida maganin da akai anfani dashi ba’karamun illane dashi ba da kai tsaye yake kisa, forehead d’inta ya sun bata “ am really sorry Angel “, kafun ya dakko phone d’inshi,a haroon ya kira a waya, cikin wata irin zabura haroon ta sakko daga kan gado ganin kiran King abunda bai ta’ba faruwa ba , safa da marwa ya fara gumi har ya fara tsatstsafo masa , yana d’aga kiran tunkan ya fara bawa king hakuri ya ji saukar muryarsa, “Number ihsan”, kittt ya kashe wayar tasa, tazo idanuwa haroon yayi, Allah yasa yarannan ba lefi sukai ba, gudun karya yi wani kuskuren yasa yayi saurin tura masa number ihsan ba ‘bata lokaci. Daidai lokacin da king ya kira number ihsan , a Daidai lokacin ne ta fito daga part d’in ammeey zata koma part d’insu, sabuwar number da ta ganine yasa ta share kiran kamar katta d’aga , sai wani zuciyar ya ce mata ta d’aga , tun kafin ayi magana zuciyarta ta soma dukan uku uku, “ where are you “, taji saukar muryar king, da mugun sauri ta cire wayar a kunnanta kafun ta mayar murya na rawa ta furta “ na fito ne zan koma part d’in mu “,shiru yayi kamar baze ce komai ba sai kuma taji saukar muryarsa “ wanene ya kawo mata abinci”, ta gane Tahee yake b Nufi shiyasa tayi saurin bashi amsa “ Ummey ce tace na kawo mata”, wani irin harbawa zuciyarsa yayi , besan lokacin da ya furta “ wacce ummeyn”itama amsa ta bashi da “ummeynka “ yanxu kam runtse idanuwansa yayi, me Hakan ke nufin ,”ummey, no”, kusan 2 minutes be ce komai ba ta d’auka ya kashe , itama har zata kashe cikin wata iriyar murya ya furta ,” kije ki bawa zaki kwanukan abincin, and ki gyara wajan, don’t said anything to anyone ko wanene , okay “, da Sauri ta furta “ insha Allahu yaya”,. Cikin sauri sauri ta nufi part d’insa zuciyar ta har ta fara bugawa itama , tana shiga ta tarar da uban Jinin da Tahee ta zubar, a mugun rud’e take bin wajan da kallo ga abincin da ummey ta bata . Da Sauri ta d’akko jakar zuba abinci ta had’a kayan abincin , Kafun ta kaiwa zaki dake waje , tana dawowa Jinin ta fara gyarawa kafun ta gyara falon, har yanxu zuciyarta be dena bugawa ba , fatan ta Allah yasa Tahee lapiya take. Saida ta tabbatar komai ya gyaru kafun ta kulle musu part d’in ta nufi nasu duk jikinta yayi sanyi. Duk wannan abun da yake faruwa babu Wanda ya sani a cikin gidan, zaki na kawo masa kayan abincin yasa akan bin cika masa su, tabbas kuwa a cikin su maganin yake , wani irin zazzafan zazza’bine ya fara kamata , gabaki d’aya ya rasa Wana irin tunanin zaiyi , yana ganin kiran Ukti amma ya kasa d’aukan kiran nata, sai bin Tahee yake da kallo ,har yanxu ya kasa gasgatawa, yana cikin tunanin da ya fad’a Tahee ta soma mutsu mutsu da ido, har ta ware kumburarrun idanuwanta kan kyakkyawar fuskarsa da ya du’kar ‘kasa “ sweetheart “ ta furta a hankali kamar me rad’a , da Sauri ya d’ago rinannun idanuwansa da suka canza kala, cikin sauri ya ‘karaso inda take “ are you okay “, shima ya furta mata kamar me rad’a , kanta kawai ta girgiza masa alamar eh, ahankali ya furta “ Am sorry “, rufe masa baki tayi da tafin hannunta “ Ni bakayi mun lefun komai ba , Babyn mu?” Ta tanbayeshi duk da shakkar tanbayar da tayi masa , kallanta yayi for second kafun ya furta “ he’s safe too” ajiyar zuciya ta sauke da har shi da yake kusa da ita sai da yaji,duk da bata da wani ‘karfi sosai a jikinta akan me hana ta kamo hannunsa ba tana shafa gefen fuskarsa “ wannan face d’in fa ta canza ba haka na santa ba “, rungumeta kawai king yayi a jikinsa ya kasa magana jiya ke kansa kamar zai tar watse, har sai da ya samu nutsuwar da yake bu’kata kafun ya raba jikinsu “ Sleep !! Okay “, da d’an mamaki Tahee ta kallesa tasan dai nan ba gidan su bane duk da ‘kamshin da ya karad’e ko ina na d’akin hakan be hana ta jin wari asibiti ba, “ bazan iya bacci ba , bana san warin asibitin nan kamar zan yi amai”, but har yanxu jikinki ba’kwari , “ Dagaske nake yanxu bana jin ciwon komai , inna cigaba da shakar warin asibitin zan iya amai fa “ ta fad’a tana ‘karasa turo masa ‘karamin bakinta , kansa kawai ya jinjina mata kafun ya temaka mata har zuwa cikin motar yana ri’ke da hannunta, saida ya tsaya a ocean basket yayi mata order d’in abunda zataci kafun su koma gida . Bai zaunar da ita a kasa ba da kansa ya d’auketa ta cikin lifter ya kai ta master bedroom dinsa , sai da ya tabbatar tayi wanka kafun ya fara bata abuncin da suka taho dashi, duk yanda take ce masa ta ‘koshi saida ya sata ci kafun ya bata wani magani ta sha , ba jimawa bacci ya d’auketa. Tunanin abunda ya faru yake har yanxu ya kafada fita daga cikin kansa , ga wani irin lafiyayyan ciwan kai da ya haifar masa , duk yanda ya so runtsawa abun gagara yayi sai wajan 2:40 kafun bacci ‘barawo ya sace shi. Ana kiran sallahr asuba ya farka , sabida tsananin yanda kansa yake ciwo bai je masallaci ba yau a gida yayi sallahn shi ganin Tahee na kokarin saka damuwa a ranta ne yasa shi cire komai ya mayar dashi gefe dan kansa ya fara kula da ita , tun daga kan abincin da zataci , da kanshi yake fita ya kar’bo mata order d’in duk abunda take so ko ya kira ihsan ta girka mata. Kwana biyu da rashin lapiyar ta jikinta har ya murmure ta dawo normal sai wani ci kowa da ta karayi na musamman , Tunda abunnan ya faru Tahee bata ta’ba kawo wa ranta cewa ummey ta mata abu ba , duk da tasan tana gama cin abinci cikinta ya fara mata ciwo , ga Tamar dar king your husband da take samu har yanxu, ta ‘bangaran king shima har yanxu be ce komai ba akai ba , amma ga baki d’aya mood d’insa ya sauya , wani irin miskilanci ne ya ‘kara shigarsa , Tahee ce kadai ke iya controlling kayanta . Karfe 3:02 biyu Tahee ta nufi part d’in dada ganin kwana biyu bata le’kasu ba kuma har yanxu basu san abunda ya faru ba, Tana shiga kuwa dada na damun fura, cikin washe baki ta karaso wajan dadan, “ Nazo a Daidai kenan , yau zansha furan dada “, murmushi dada ta sakar mata “ kamar kinsan kuwa ke nake damawa , wancan tanbad’ad’d’an mujin naki da ke kadai zaki iya naga sai faman shan kamshi yake kwana biyu, ko taya kuke rayuwa oho”, tana karasa zancanta ta mi’ka wa Tahee furar, in banda murmushi da Godiya ba abunda Tahee take wa dadar, sosai ta sha furarta har su ihsan suka shigo cikin falour suka cigaba da hira, kamar daga sama amrah ta shigo falon dadar, wayar hannunta da take dannawa ce ta su’buce mata bata san lokacin da bakinta ya furta “ Kutmar uba” da wani irin kallo dada ta kalleta ,” Wana irin shashan cine wannan sai kace nasara zaki magana ashariya “,gabaki d’aya amrah bata jin ta ban da kallan Tahee da take jikinta na tsanan ta rawar da yake , ko ta bun wayar ta batai ba ta ruga a guje tana d’ora hannu aka. Babu Wanda ya damu da halinta , inda samo kuma yaci ace sun saba, share zancanta sukai sukaci gaba da hira , a part d’in dada Tahee tayi sallar la’asar d’inta kafun ta wuce part d’in ummey. Kamar yadda ummey ta saba kar’barta yanxun ma hakance ta faru, gabaki d’aya saida ummey ta cika gaban Tahee da abubuwan ciye ciye, dukda tsananin kunyar da ummey ta sakata sai da ummey tasa ta saki jikinta sukai hirar su babu wani surukanci a ciki, kasan tuwan ummey balarabiyya shiyasa ta fuskanci Tahee sosai ta nuna mata dabarun zaman aure da yanda zata kula da cikinta , duk da kunyar ummey da taji hakan be hana ta share shawarwarin ummey da zasuyi mata anfani ba , da zata tafi sai da ummey ta hada mata kayan kwad’ayin datasa a kawo mata, tun kafin a kai mata part d’inta ta soma shan magarya tsabar kwad’ayi irin nata. Apart d’in ummey ma ta d’an jima , har ta yi hanyar part d’in ammey ganin ana kiran sallah yasa bata tsaya ba ta nufi part d’inta , sosai tayi missing ammeey kwana biyu kwata kwata bata ganin ta a part d’in dada , tana idar da sallahr ta shaf shaf ta dafa musu abinci mara nauyi, kafun ta ‘kara gyara jikinta , tana so ta shiga part d’in ammeey ganin lokaci ya ‘kurene yasa ta hakura da niyar gobe taje. A gajiye ya shigo gidan , Kai tsaye wanka ta tameka masa yayi kafun tayi serving Dinsu , abincin ma yau Asama suka ci kafun ta d’ebo magaryar ta cikin yar karamar roba tana sha , kallan ta ya tsayayi ta kashe masa ido d’aya “ magaryace fa , zakasha ?” Tayi tanbayar tana kallansa , gyad’a mata kai king yayi alamar eh, guda d’aya ta dakko masa zata saka masa abaki ya kawar da kansa gefe, hannunta biyu tasa ta kama fuskarsa zata saka masa magaryar ya kara dauke fuskarsa “ kace zaka shafa “ ta fad’a a shagwa’be , shima kansa ya d’aga mata alamar eh kafun ya nuna breast d’inta da ya fi komai tsone masa ido , “ wannan nake so” bata bari ya kara zancansa ba ta mi’ke zata gudu yayi saurin ri’kota , “ please baby “, marairaice masa tayi kamar zatayi kuka “ ban warke bafa kamanta “,d’an ‘karamin ya’ke kawai ya saki ba tare da yace mata komai ba , a kwana biyun nan Sam ta kasa gane kansa “ meke damunka “ girgiza mata kai yayi alamar bakomai , “ kamanta al’kawarin da Kayi mun, duk abunda yake damunka zaka fad’a mun, it’s a promise, kamanta ?”girgiza mata kai yayi alamar a’ah, gefen fuskarsa ta shafa cikin kwantar da hankali ta furta “ To fad’amun , Sabida ni nafisan my old king ba wannan da baya mun fara’a sosai ba “, ita kadai ta ke shawo kansa , kallanta yayi for second , besan ta yarda zai fad’a mata ba , “ please “ ta kara maimaita masa , a hankali ya furta “ Abincin da kika ci last was from ummey, and …” bata bari ya ‘karasa zancan saba sabida ta gano me yake ‘ko’karin cewa da mamaki ta kallesa “ I thought wannan magana ta wuce , me ya kawo zancan ummey a ciki , don’t even start it , I’m fine , our baby is fine , all this days damuwar da ka sawa kanka kenan? Why?”kallanta yayi ganin ranta na ‘ko’karin ‘baci “ it’s like that baby, karki fara wannan fushin please “, gefen fuskarsa ta shafa “ it’s okay , but ka cire wannan damuwar aranka , okay?”, kanshi ya d’aga mata alamar toh kafun ta furta haaa, hakan kuwa yayi kamar yanda tace, magaryar ta saka masa a baki tana sakin dariya , d’an kad’an ya tsotsi magar yar kafun ya cire ta cikin bakinsa “ wannan baby ya koya miki kwadayi da yawa , komai ke kina ci “, gwalo kamar tahee tayi masa , tana jingine a jikinsa shi kuma yana aiki a system, tunanin maganar sa ta d’azu ne ya fa d’o mata arai, da sauri ta kawar da zancan tana anbatan sunan Allah. Ganin ta soma gyangyad’ine yasashi ajje system d’insa , adduar da ya saba yi mata duk dare ta tsari yayi mata kafun bacci ya d’aukesu manne da juna . ♾️♾️♾️♾️♾️ ♾️♾️♾️♾️♾️♾️ ♾️♾️♾️♾️♾️♾️♾️ BUNKURE A cikin ‘yan kwana kin nan abubuwa da dama sun faru, a wannan lokacin sosai kaka ta bawa ta fara danasanin musgunawa su oumma da tayi arayuwa, kullum cikin ro’kar Allah take akan Allah yasake had’a ta dasu ko zasu yafe mata. Yanxu komai ya sauya agidan ganin irin rayuwar rashi da suka fara tsintar kansu a ciki. A ‘bangaran Dije kuwa kud’i takesamu, Sabida yara ‘yan matan da suke kaiwa karuwanci , sosai liyafa ta cigaba , har tsawan wannan lokaci bintalo bata ‘kara waiwayar gida ba , itama dijen yanxu kwata kwata bata damu da dawowarta ba . Kullum ‘yan gidan sai dai su zuba mata ido dan babu Wanda ya isa ya tanka mata .Gabaki d’ayansu sunyi nadamar abubuwan da sukayi wa oumma da su tahee , ganin yanda rayuwa take garasu, Dije kuwa sai saban wulakanci da ta ‘karo, ganin yanxu ita ke temaka musu, sai ta gama yi musu wulakanci san ranta kafun ta san musu abunda za su d’anci a bakinsu. ➰➰➰➰➰➰➰ Yau ta kama Thursday, har wajan karfe 9am na safe king na tare da babynsa sai faman shagwa’ba take sakar masa , yana fita d’an malele Tahee tayi , ta zauna ta shanye kayanta tass, kamar yan da tayi niya jiya , shiryawa taya cikin doguwar pink din Riga da bata kamata sosai ba , Hakanan yau ta d’auke dogon hijab abunda ta nufi part d’in ammeey, tana shiga taji wata iriyar hajijiya na kamata , cikin Sauri ta samu waje ta zauna , babu kowa a cikin falon har tsawan mintuna 10, ganin har yanxu ammeeyn bata fito bane yasa Tahee nufar ‘kofar d’akin ammey da niyar ‘kwan’kwasawa, kalaman da tajine ya matukar hautsina mata ‘ya ‘yan cikinta, gabaki d’aya ta rasa Wana irin tunanin zatayi, wata iriyar hajijiyace take kokarin kayar da ita tayi saurin dafe bango, wasu irin azababben hawaye ne suka fara sakkowa daga saman kuncinta , babu abunda ta ke nanatawa sai kalmar “Innalillahi wa ‘ inna ilaihi raji’un, Allahumma ajirni fi musi bati, wa akhlif li khairan minha “bakinta rawa ya fara , so take tace wani abu amma ta kasa ga wani irin masifaffen ciwan kai da ya sakko mata lokaci d’aya , cikin fitar hayyaci Tahee ta bar part d’in , Allah ya temaketa bata had’u da kowa ba , Tana shiga cikin part d’inta ta ‘kara tarar da abunda ya hautsina mata ciki, kallan kallo suka tsaya yiwa junansu, kafun a hankali cikin wani irin shu’umin murmushi Ammey ta kalli Tahee da tayi mutuwar tsaye , “ yarinya kenan, kinji abunda kunnuwanki be kamata suji ba yanxu ,amma duk da hakan kin rage mun aiki”cikin wata gigitacciyar tsawa Ammeey tace wa Tahee ta zauna, ita kanta Tahee bata san lokacin data zube ‘kasa ba tana bin Ammeey data had’e rai da kallo. Cikin wata iriyar murya me firgitarwa ammeey ta soma magana “ bazan tsaya kwana kwana ba , bari na fito miki a mutum yanda zaki fi saurin fahimta, abunda kunnuwanki suka ji miki hakane, nice na suba maganin zubar da ciki a cikin abincin da waccan munafukar ta kawo miki” da mugun zabure Tahee ta kalleta, bakinta har rawa yake wajan furta “ AUNTY”, akaro na biyu da ammey ta kara dakawa Tahee tsawa ,karki kuskura ki kara kirana da wannan sunan,har yanxu ke yarinyace , tsawan shekaru na dauka ina Gina masarauta ta , rana d’aya kice zaki rusamun ginin da na dade inayi, tabbas shi zai janyo a jalinki, kamar yanda ya janyo ajalin sauran.GIDAN AUNTY 07041879581 Mss Lee 💖 BOOK 1 Page 69 A rude Tahee ta dafe cikin ta , da wani irin shock take kallan Ammeey, kallo na tsantsan tsana , idan kowa yace zai ce Ammeey zata yi wannan abun bazata taba yadda ba sabida yadda ta nuna musu ‘kauna tun suna ‘kanana , bata gama shiga Rudu ba sai da taji muryar Ammeey ,” zaki yi tunanin ina sanku ko, toh babu Wanda na tsana a duniya kamar ku, sau dadama da na fara gina masarauta ta kune kuke ruguzamun, shiyasa nayi al’kawarin ruguza duk Wanda yayi ‘kokarin ta’bamun masarauta, bama ke ba koma wanene yayi gigin shiga gonata sai na kawar dashi. Ada nayi tunanin ‘kyaleki amma sam sai naga kin fu kowa za’kewa a cikin su wanda shine babban kuskuren da nayi na shigo dake cikin a halin nan,azato na baki da wayo,Aushe sam ba hakan bane , bana kawo ki gidan nan dan ki zauna cikinsu bane , na kawo kine dan ki ‘karasa aikin da na fara , na kawo kine ki kashe mun tahnoon , Wanda kike i’kirarun mijin ki a yanxu “. Cikin rud’ewa Tahee ta soma binta da idanuwa, gabaki d’aya jikinta rawa yake , jin maganganun ammeey take kamar a mafarki ko a cikin wani film da ba gaskiya ba ,”Ni na kashe mijina , bazai yuwa ba , mijina fa , kisa “, abunda Tahee take faman nanawa a cikin ranta . Ta sowa Ammey tayi daga kan kujerarta fuskarta babu ko alamun fara’a, Daidai inda Tahee take a zaune ta tsugunna itama tana bin fuskar Tahee da wani shu’umin murmushi,hannunta d’aya ta d’aga zata ta’bata Tahee tayi saurin bige mata hannu hawaye na sakkowa daga cikin idanuwanta, a zuciye Ammeey ta janyo kanta ba imani ta tsinkawa Tahee mari , cikin ‘kunar rai ta cigaba da magana “ idan kikai kuskuran musa mun abunda zansaki to ki tabbata yanda na kashe mahaifinki haka zan kashe mahaifiyarki da d’an uwanki, sannan na dawo kanki Keda abunda ke cikin ki da dole sai ya fita ko kina so ko ba’kyaso dan King nawane ni kadai, bazan ta’ba yadda wata taso abunda na dad’e inaso ba “. A zuciye Tahee take kallanta zuciyarta harwani tafarfasan ba’kin ciki take , cikin kunar rai ta d’aga hannunta da suke faman yi rawa tana nuna Ammeey, murya a sha’ke Tahee ta soma magana “ kece kika kashe mana Abbu dama, kece kika sa ayiwa Abbu yankan rago, duk tsawan wannan lokacin da sa hannunki a ‘batan Oumma da Taheer ?me mukai miki ?lefin me iyayena sukai miki da zaki sakamusu ta wannan hanyar?”mi’kewa tsaye Ammey tayi batare da ta damu da amsawa Tahee amso shin taba ,Wani ruwa da ta gani akan center din kujeran ta d’auta,cikin sakin murmushi ta soma magana “bani da lokacin amsa miki wannan tanbayoyin naki,amma kamar yadda nasha Alwashi , duk wanda yayi gigin tarwatsamun burukana toh kamar ya tarwatsa rayuwarsane, kamar yadda na salwartar da ran ubanki, na tarwatsa ahalinki, sannan na kashe miki d’an uwan mijin ki, na raba tsakanin uwa da d’a , bani da wani sai na cikar burukana da yayi saura yanxu kuma kece mukullun Karshen cikar burina , zan baki d’an kwanaki biyu , ki salwartar da abunda yace cikin ki sannan da ki kashe mijinki, idan ba haka ba ki fidda rai da kara ganin ahalinki har Abadah,”Tana kai karshen zancanta Ammey ta bar d’akin tana sakin wani shu’umin murmushi . “Innalillahi wa ‘inna ilaihi raji’un, Allahumma ajirni fi musibati wa aklifni karyan minha, Ya Allah kaga baiwarnan taka, Allah kai ne Wanda kace mu rokeka, Allah kaga wannan baiwa taka , Allah ka nuna ikonka akan bauwarka,” ta karasa zancanta tana sakin wani kukan bakin ciki, kukan da ta dad’e batayi irinsa ba , ace maka shin ka yana kusa da kai Wanda ka Amin ta dashi ka basa yadda yazamo shine makashinka, “Innalillahi wa ‘inna ilaihi raji’un “,gabaki d’aya Tahee ta rasa Wana irin tunani zatayi sabida yanda komai na tunaninta ya tsaya mata , ji take komai da yake faruwa kamar a mafarki ne ba a zahiri ba , Wacce ta nuna masu so Itace maka shin mahaifinta , wani irin tsantsan tsanace taji tana yiwa Ammey da ya kore duk san da take mata , ga wani zazzafan zazzabi daya rufeta lokaci guda , da kyar idanuwanta suke buduwata , a hankali ta lallaba ta nufi dakinta ko kallan gabanta batayi sosai , bata tsaya a ko ina ba sai kan gadonta, lokaci d’aya zazzabi da ciwon kai ya rufar mata daya sa wani irin bacci mara dadi ya d’auketa me cike da mafarkai. ***** 2:30pm ta farka daga baccin daya kwasheta tana karanto adduar da tazo bakinta , lokaci d’aya abunda ya faru d’azu ya shiga dawo mata cikin kwakwalwarta, tabbas d’an Adam butulune, sallahr azahar ta gabatar tana mika ka Allah kukan ta tare da adduar neman tsari daga Sharrin Ammeey da masu hali irin nata , a hankali kuma wasu zafafan hawaye suka shiga sakko mata cikin kwayar idanuwanta tuno irin yankan ragon da akai wa abbunsu, gashi bata san Wana hali oummanta suke ciki ba , a d’aya ‘bangaran kuma tana tsoran halin da mijinta zai shiga idan yasan wacece ta kashe masa d’an uwa , macen da ya d’auketa kamar mahaifiyarsa, macen da tafi mahaifiyarsa kusanci dashi , rana d’aya ya fuskanci Itace makiyarsa , “Innalillahi wa inna ilaihi raji’un “,Na barki da Allah shi kadai yasan yanda zaiyi dake cewar Tahee tana goge hawayen fuskarta , a d’ayan ‘bangare na zuciyarta kuma ta sha alwashin sai ta tonawa Ammey a siri ko ta halin ‘ka’ka . Bata jin yunwa shiga bata yi abinci ba , sai ma addu’oi da ta du’kufa yi na Kariya a gareta da abunda yake cikinta . Yinin ranar gaba’ki d’aya cikin ‘kunar rai tayi shi , sai ma kokarin sassaita fuskarta da tayi gudun kar ya dawo yaga mood d’inta ya canza. ✨✨✨✨ Karfe 8:40pm king ya shigo part d’insa lokacin har Tahee ta kammala komai na ta ,ta saka wasu kayan bacci masu matu’kar d’aukar hankalin, gabaki d’aya kayan jikinta ana ganin surar jikinta,cikin wani irin salo ta karasa Wajansa tare da hugging d’insa , shi kansa king saida yayi ajiyar zuciya ga idanuwansa da ya fara canza kala zuwa kalar ja musamman yanda cikakkun breast d’inta suka ta’ba masa kirji, medium size jug d’in hannunsa yayi saurin dam’kewa , d’an d’age Tahee tayi kafun ta sakar masa peck a kumatunsa , cikin disashewar murya ya furta “ welcome back baby “, be amsa mata ba sai ma face d’inta da ya bi da kallo,” me yasa face d’inki tayi Jaa, are you okay ?” Saurin kawar da kanta gefe tayi tana kara saisaita face dinta , cikin yar shagwaba ta furta “ bakaine ka’ki dawowa ba , kuma babynka suna so su ganta , yaufa kamanta da mu gabaki d’aya ta ‘karasa kamar zata saka masa kukan shagwa’ba,”oh my god, zaki kasheni da wnnan salad naki ,okay dadyn baby yayi lefi ayi masa hakuri and anjima zamu gaisa da baby ai ko ?” Ya karasa yana kashe mata ido d’aya , kawar da zancan tayi ta hanyar karban karamin jug din hannunsa “ Menene wannan ?”, kallan jug d’in yayi kafun ya furta “ kunun aya Ammey tayi mun”, yana kai karshen maganarsa jug d’in na subucewa ya fad’i tass, gabaki d’aya ya tarwatse sai yar kwalbar da ta saukar wa Tahee a ‘kafa, kuka ta fashe masa dashi, cikin rud’ewa ya d’auketa yayi bedroom dinsa da ita , atunaninsa kwalbar data caketane amma ita sam ba haka bane , kukan bakin ciki ne yazo mata ganin saban Salan iskanci Ammey wato ta basu kunun aya su mutu. #MANAGE PLEASE 🙏 GIDAN AUNTY 07041879581 MSS LEE 💖 BOOK 1 Page 70 Lallashinta yayi har tayi shiru bayan ya gama dressing din kwalbar da ya shigar mata kafa, wayansa ya dauka da niyar kiran Ammeey tayi saurin dakatar dashi ,bata san lokacin da bakinta ya furta me zaka mata, d’an kallanta yayi shima na ‘yan second kafun ya furta yaja hancinta kad’an “ wani kunun ayar zansa a kawo mana”, ita kanta bata san lokacin da take wani abun ba “ No kabari gobe zanyi maka wani kajiii babyn? Ynxu bari na fara temaka maka kayi wanka sai kaji abinci ,okay? Kanshi ya d’aga mata alamar toh kafun ya kuma cewa “ but bari na saka a kawo mana wani kunun aya , Kema ai naga kina san kunun Ammeey” no kaji ka fara yin wanka already na hada maka another juice please ni yunwa mukeji nida babyn ka fa “,cikin ya ta’ba kafun ya saki wani ajiyar zuciya “ toh ayiwa dady hakuri yanxu zakuci abinci” yana kai karshen maganar sa yashi ya nufi kofar da zata sadashi da ban dakinsu, ajiyar zuciya Tahee ta sauke cikin zuciyar ta kuwa cewa take “ Allah ya tsare na karacin abincin shaid’aniyar iblisarcan, Wanda naci a baya ma a rashin sani ne , muguwa me kama da kwarkwata, ta Allah ba taki ba “, gudun karya sakko ya tarar da abun kunun yasa tayi saurin fita daga d’akin, Daidai inda kunun ayar yake ta nufa , a bun mamaki amaimakon ta samu kunun ayar sai wani ‘bakin ruwa da ta samu, addua ta soma yi cikin xuciyarta, kafun taje ta dakko Mopper ma gabaki d’aya ruwan kunun ayar ya kuma komawa ba’ki , karfin adduarta ta soma tun tana yi a zuci haka ta cigaba dayii ita kanta bazatace ga adduar da take karantawa ba, da Bismillah ta fara goge ba’kin ruwan harta kammala, tare da kunna karatun alkurani yanda bazai damesu ba , tana cikin Kimtsa falon ya sakko ‘kasa shima cikin shigar kayan bacci blue colour masu Taushin gaske , serving Dinsu abincin tayi atare suke feeding din junansu har suka kammala , a kan 3sitter ya zauna ita kuma ta kwanta akan cinyarsa tana wasa da sajanshi “ babyn” ta kira sunansa a hankali kamar me rad’a , kallanta yayi alamar na’am duk da ne bud’e baki yayi magana ba “ wacece Ammey a wajan ka “ wani lallausan murmushi ne ya bayyana akan fuskarsa da ya kara kawata kyawun fuskarsa har hakan yaso bata mamaki, mi’kar da ita yayi zaune tare da kamo hannunta Suka nufi d’akinsa ta lipter , zaunar da ita yayi akan sofa kafun ya bar d’akin , mintuna kad’an kuma ya dawo hannunsa d’auke da wani karamin white box’s,budewa yayi take a wajan wasu hotunan Suka bayyana duk da darewarsu amma babu abunda ya samesu,” sorry laifina ne da har yanxu baki gama sanin Tarihin mijinki ba,nasan kinsan full name dina , amma still zan kara fad’a TAHNOON ZAYED AL_NAHYAN, mumu 4 ummey ta haifa Akheee moha shine babba Allah ya masa rasuwa ,sai ukhtiii next tomorrow itama zaki ganta , sai ni sai kuma auta zoya , tun ina ‘karami na nake ‘bangaran Ammey sabida yanda take nunamun soyayya da wata shakuwa ta musamman komai ta samu ni zata fara bawa kafin ta bawa kowa na gidan har hakan ya kara sha’kuwa a tsakaninmu, soyayyar da take munne yasa sau da dama mutane sai su dunga d’aukar cewa ita tahaifeni sabida wani irin shakuwa da yake tsakanina da ita, part d’in ammeey na dawo cikin abinci, komai nawa a part din Ammeey nakeyinsa, hatta kwana a part d’in ammeey nake yi har lokacin tafiyata waje karatu, acan turkey na kammala karatun likitancina, har na kammala at time moment…” sai kuma yayi shiru yana runtsu idanuwansa , itama kallansa tayi sabida wani irin tausayinsa da ya mamayeta, tabbas ba karamin cutar dashi Ammeey tayi ba , hannunta d’aya ya dam’ke cikin nasa ,” At That moment, mukayi accident da Akhi , and at the same time motar da muke ciki ta kama da wuta , duk yanda nayi kokarin cecensa na kasa , ina jin zafin hakan every single day idan na tuna na kasa cetan best brother , I can’t save him, na kasa cetansa , agaban idona wuta ta ‘konashi” ya karasa zancansa kamar nunfashinsa zai d’auke , rungumeshi Tahee tayi tana fashewa da wani irin kukan tausayinsa , tabbas idan Ammeey zata iya ‘kona mutum da ransa toh tabbas zata iya yin kome tace ,a zuciyar ta kuwa fad’i take “Ammey kin cuci rayuwar mu, kin rusa mana farincikin , tana zan iya sanar Dashi kece kika kashe masa d’an uwa, kika rabasa da mahaifiyarsa”, shafa bayanta yake a hankali cikin rad’a rad’a ya furta “ banasan kukan nan naki idan ba so kike Nima nayi ba , duminki kawai nakeso,zuciyata ba dad’i inasan farin cikin matata “, ya karasa kalmar matata Tahee ta had’e bakinsu waje d’aya, duk yanda taso tsayar da hawayen fuskarta ta kasa , wani irin deep French kiss take basa, gabaki d’aya ta mantar dashi abunda ke damunsa, light din dakin king ya kashe kafun yaja bargo ya lullu’besu sabida sanyin da yake busosu….. After 2 hours kwance take a jikinsa gabaki d’aya taki yarda su hada ido, “ a ina kika samo wannan karatun, I like it please kunyarnan ta tafi haka tana cutana fa “bugun kirjinsa tayi a hankali amma dukda haka saida yace ouuuush, yana kara rungumeta a jikinsa , lumshe idanuwanta tayi kamar me jin bacci Amma sam ba baccin take ba , tunanin yadda zata tona wa Ammey asiri kawai take a cikin ranta, tana cikin tunanin bacci ya d’auketa, forehead d’inta ya sumbata kafun ya ‘kara rungumeta a jikinsa, abubuwanda Suka faru tsawan shekarune suka dawo yawo akansa, babu inda ya fi tsaya masa arai kamar mutuwar d’an uwansa, ganin yanda jijiyoyinkansa suke ‘ko’karin ta shine yasa ya soma adduar tsari cikin zuciyarsa , ya d’ad’d’e yana addua kafun yayi nafila akan rokan Allah ya sassauta masa abun da yake ransa kafun shima ya kwanta yana kara rungumota a jikinsa. ******** ✨✨✨✨✨ WASHE GARI king yana tafiya masallaci itama Tahee ta Tashi tayi sallarta, bacci take ji sosai shiyasa ta koma zata kwanta, a side d’in hagun da king ya fi kwanciya a gefen ta kwanta , hannunta d’aya ta zura ta karka shin pillow sa yanda zataji dad’in kwanciya sai taji abu kamar yana tokararta, gyara kwanciyar ta tayi yanda zata fi jin dad’in baccin nata amma still tanaji kamar abu na sukarta, ni’kewa zaune tahee tayi tare da yunkurin canza pillows din, hannunta ne ya sauka akan tsakiyar pillow d’in hannunta , da Sauri ta janye hannunta tana karantar addua, wajan ta kara ta’bawa amma still tanajin kamar akwai abu a wajan, cikin rashin tsoro ta kara kai hannunta wajan still har yanxu tana jin abinda takeji, rigar pillow d’in ta yi saurin zazzagewa kafun ta kara taba wajan, still dai abun na Wajan, cikin Sauri ta dauki pillow d’in ta nufi d’akin ta dashi, reza ta fara nema cikin sa’a kuwa ta samota, bakin pillown ta farka duka kafun ta zazzage abinda yake ciki, ‘karamar kwabace ba’ka ta bayyana a cikin abin cushion d’in, bakinta d’auke da Bismillah ta bud’e kwalbar, wani haya’kine ya fito daga cikin kwalbar ba’ki’kirin da shi ,Addua Tahee ta fara da ‘karfi cikin ‘kan’kanin lokacin kuwa haya’kin ya bace gabaki d’aya . A Daidai lokacin da wannan kwalbar ta fad’o a daidai lokacin kan king yayi mugun sara masa , ga wani jiri jiri da ya soma d’aukarsa, part d’in ammey zaishi amma ya fasa ya nufi nashi part d’in, yana shiga cikin falon sa ya fad’i kasaaaaa.. #MANAGE GIDAN AUNTY 07041879581 MSS LEE 💖 MAI BUKATAR KARANTA GIDAN AUNTY HAR KARSHE YA TUNTUBENI TA NUMBER TA . BOOK 1 Not edited Page 71-72 🔚 Tunanin abunda ta gani cikin pillow ne ya fi komai d’aga mata hankali, yanxu gabaki d’aya hankalinta ya karkata kanshi, so take tasan ko yana lapiya , wayarta ta soma dubawa ganin batanan ne yasa tayi saurin barin d’akin har zata hau sama sai ta fasa ta sakko kasa , Wanda ta gani akasanne ya bata mamaki bata yadda da hakan ba shiyasa ta ‘kara matsowa dan tabbatarwa kanta ,tabbas ,”shine” ta kara nanawata, da Sauri ta karasa inda yake , a hankali ta kai hannunta kan goshinsa , sanyi goshinsa yayi hankali a tashe ta soma jijjigashi, kuka ta fara ganin abun kamar a mafarki gashi ko motsi ya kasa yi , gabaki d’aya ta rasa abunyi, ruwan da ta gani tayi saurin ‘balle murfin tare da yayya famasa ruwan amma gabaki d’aya kamar ba mutum take yayyafawa ba , rud’ewa ta karayi ga wani irin murd’awa dataji cikinta ya soma yi mata , salati kawai ta soma hannunta d’aya dafe da mararta yayin da d’aya hannun nata yake kan fuskarsa, kuka kawai Tahee take da iya ‘karfinta ganin ko motsi bayayi,rubutun da dada ta batane ya fado ranta da Sauri ta mi’ke duk da tsananin murd’awa da cikinta yake mata , fridge d’inta na sama ta hau cikin Sauri sauri gudu gudu , tana bud’ewa Kuwa ta ganshi, da Sauri ta dauko ko kallan gabanta bata yi, Daidai inda yake ta nufa , cikin Sauri ta ‘balle murfin robar ta soma yayyafa masa kafun ta bud’e bakinsa ta saka masa ruwan kad’an, tari ya fara sosai wani ba’kin ruwa ya fara fitowa daga bakinsa, adduar da oumma ta koya mata ta soma kafun ta fara tofamasa, gabaki d’aya fuskarsa tayi zufa duk da sanyin Ac dake ratsa ko ina na falon, ruwan adduar ta kara saka masa ,yanxu ma tarine ya sarkesa jijiyoyin kansa gabaki d’aya sun fito waje, ta d’au kusan 20 minutes tana masa addua kafin ya soma ajiyar zuciya , gyara masa kwanciya tayi yanda zai ji dadin sakewa . Tsawan lokaci Tahee ta d’auka tana bin kyakkyawar fuskarsa da kallo, a zuciyarta kuwa addua take faman yi masa , dabarace ta fad’o mata, babbar plasma Tvn ta ta kunna tayi connecting, suratul Bakara ta kunna ta saka volume dadda zata dunga ji daka kitchen, kafun ta kulle kofar shigowa part d’in gabaki d’aya , cikin d’auri ta shiga kitchen dan ta Sama musu abunda zasu ci, chips tayi masa tare da pepper chicken , sai omelette din da ta kara yi masa , amaimakon ta had’a coffee yau hakanan zuciyarta bata yadda da kayan coffe din ba shiyasa ta d’ona ruwan tea me cike da kayan kamshi,Lokacin data duba a gogo almost 10:30 tayi , a dinning ta jera musu breakfast d’in kafun ta dawo inda yake , fuskarsa ta soma shafawa a hankali, kusan tsawan 2 minutes kafun ya d’an saki a jiyar zuciya, idanuwansa da sukai masa nauyi ya bud’e a hankali bakinsa d’auke da addua, zuba mata narkakkun eyes d’insa yayi itama shidin ta ke kallo, temaka masa yayi ya zauna kafun ya kalli inda yake da mamaki, kokarin tuna abunda ya faru yake amma ya kasa ,” me yasa na ke kwance anan” ya furta cikin sanyin murya , kallansa Tahee tayi na ‘yan sakanni kafun ta furta “ ka gajine shiyasa bacci ya d’auke ka , ynxu ka tashi kayi Wanka sai muci breakfast “, a gogon hannunsa ya kalla ganin lokaci yayi saurin mikewa tsaye tare da ita a jikinsa, dining din ya nufa dakansa yayi serving abincin a plate, jinsa yake kamar an cire masa abu me nauyi a kirjinsa ga bakinsa kwata kwata ba appetite din abinci,batare da yace mata komai nan ya soma bata abincin abaki har saida ya tabbatar ya isheta, zata bashi yayi saurin kawar da kansa gefe , “ I lost my appetite, and inaso nayi wanka “, kamar zatayi kuka ta kallesa “ ko na dafa maka wani abunne “ murmushi ya sakar mata sosai da ya dad’e beyi kamar saba “ don’t worry bari na fara wanka , okay ?”, a sanyaye ta furta “okay”, wayarsa ya mika mata kafun ya furta “ used it “, tana kar’ba ya juya ya nufi upstairs,kallan wayar tayi na ‘yan seconds hakanan yau take dan taga abun cikin wayar, da pin ajiki abun mamaki tana saka hannunta pin d’in ya bud’e take a wajan hotan ta ya bayyana lokacin da take part d’in Ammey, da Sauri ta shiga photos gabaki d’aya babu hotunansa a ciki sai hotunanta da ita kanta bata san lokacin da aka d’auke ta ba, wasu hotunan bacci take aka d’auketa , hatta lokacin da ta Samu matsalar kai, da ta fara shigowa part d’insa akwai hotunan a ciki, hawaye ne ya fara tarar mata a ido tayi saurin sharesu, soyayyar mijinta na kara shiga cikin zuciyarta , a hankali ta cigaba da kallan hotunan ita kadai tana murmushi. ******** *********** A cikin part d’in Ammey kuwa a zuciye ta fasa wani babban glass d’in jug, gabaki d’aya idanuwanta sun canza Sabida bala’in da yake cinta , sai faman zagaye inda aka kawatashi kamar wajan iska take ko tsoran a ganta bata yi, daga gefe d’aya wannan mutumin da yake yawan zuwa d’akin amrah shima zaune, dukda ba a ganin fuskarsa a yadda idanuwansa sukai ja mutum zai gane yana cikin tsan tsan tashin hankali da bacin rai, a fusace Ammey ta jiyo kan mutumin, “kace mun kasaka kwalbar ban inda ya dace Garin ya akai komai zai lalace lokacin da burinmu yake gab da cika, bazan d’auki a sara ba , bazan d’auka ba , na dad’e da tsara rayuwata , babu Wanda ya isa yace zai lalatamin,zan kashe sa , sannan na kashe duk Wanda yayi run’kurin ruguzamun shiri, kamar ydda nayi rantsuwa da dodo , bazan sa’ba ba dole burina ya cika ,yau ba sai gobe ba zan fara aikina dole na basa babbar kyauta da zai ‘kara ruguza farincikin sa har abadah”, ta karasa zancanta tana sakin wani d’an iskan dariya , taso wa mutuminnan yayi daga zaunan da yake , inda Ammey take ya nufa tare da kamo hannunta d’aya yana shin shinar wuyanta, tsaki Ammey taja tana turesa , a zuciya ta furta “ wannan ba lokacin da ya dace bane , raina a bace yake karka kara batamin, kaje wajan waccan karuwar yarinyar tukunna me zubin arha banza da kasaba latsawa, komai ina sane dashi”, da karfi ya matse hannunta guda d’aya , cikin wata kausash shiyar murya ya furta “ ke baki isa ki hanani jikin kiba sabida ked’in mallakina ne , dole na kashe mijinki dan naga alama yana kokarin shigar mun hanci da kudun duni, yanxu zan barki sabida raina a ‘bace yake , akan duk da haka yau zan kawar da aikina akan d’an talikin can, sannan karki manta dole ki fara aikin boka yanxu, bazan taba yadda jinin da ke cikin waccen shed’aniyar ya fito duniya ba , zuwan shi duniya kamar ruguzama shirin da muka dad’e munayi ne ,inaso a salwantar Dashi cikin ‘kan’kanin lokaci, dan wannan karan bana bu’katar kuskure , kafun na koma kan yan iskan yarancan da suka dawo, suma rayuwar su tana cikin gangara “, ‘karar fad’uwar glass sukaji da Sauri suka juya dan ganin ko wanene, babu kowa a wajan da Sauri Ammey ta nufi inda glass d’in ya fashe , nan ma babu kowa a wajan sai glass d’in sai kuma labulen da aka d’an bud’e da alamun mutum ya tsaya a wajan, cikin tashin hankali Ammey ta ‘kara dubawa babu wa kowa a wajan gabaki d’aya , a’bangaran mutumin kuma yana jin fashewar abu ya d’auki wani Jan zobe ya saka a hannunsa tare da soma karanta wasu abubuwa marada a dad’in ji take a Wajan ya ‘bace gabaki d’aya. Da Sauri Ammey ta shiga cikin falon ta nan ma ba kowa a jan, cikin bacin rai ta d’auki wani d’an karamin aban kifi fari tas Dashi ta buga a kasa tare da caka masa ‘karamin wu’ka ko tsaran azo Atarar da ita bata yi, a kausashe ta soma magana “ inaso a kasheta , sannan aka she mun abunda ke cikinta , sanadin hakan inaso zuciyar mujinta ya buga” sai kuma ta fara ‘kyal’kyalewa da dariya tare da nufar d’akin ta na sa azuciyarta tana ayyana duk Wanda yayi gangancin saurarar magan maganinsu na d’azu to ya kawo kansa Halaka dan sai ta kashe koma wanene “. ✨✨✨✨✨✨ Apart d’in Tahee kuwa har yanxu karatun Alkuranin da ta saka bata kashe ba sai ma ‘kara volume da tayi da Zata hau sama , Hakanan take jin ranta babu dad’i lokaci zuwa lokaci sai ta ta’ba cikinta ,intatuna halin da mijinta yake ciki sai kuma taji zuciyarta na bugawa haka kurum, dakin da yake ta shiga lokacin harya shirya cikin shigar’kananan kaya da kullum yake futo da ‘kyansa da kwarjininsa, ‘kura masa ido Tahee tayi hakanan take ji bata so ta dena kallansa , har ya ‘karaso inda take bata sani ba sai daddad’ar iskar bakinsa me ‘kanshin mint da ya hura mata a fuska,nunfashi ta sauke tare da ajiyar zuciya “ wannan kallan fa ,kamar kina missing d’ina”, bata san lokacin da hawaye suka fara sakko mata a ido ba da ita kanta bata san na Menene ba , cikin tashin hankali ya ri’keta a rud’e ya soma tanbayarta “ me ya faru?, me kikosa?, baki da lapiya ? Cikin ki? Baby…..”, bai ‘karasa ba ta had’e bakinsu waje d’aya , sosai take kissing dinsa kamar me jinyunwar haka , kokarin raba bakinsu yake ta kara had’e lips dinta cikin nashi yau da kanta take basa hot kisses d’in da yake neman zautar dashi,be hanata ba sai ma ‘kara gyara mata tsayuwar ta yayi, tana sakin bakinsa ta soma sunbatar face d’insa ta ko ina, kafun ta rungumeshi tana sakin wani saban kukan,” ya ilahiiiiiiii, please banasan kukan nan yana ta’bamun zuciya please kiyi shiru karki d’agan hankali”, gyada masa kai tayi kafun ta soma share hawayen , kallanta yayi sosai kafun ya furta “ me yasa ki kuka “ ajiyar zuciya Tahee ta sauke , kafun ta bud’e bakinta da yayi mata nauyi “ Nima ban sani ba , kawai banaso ka fita ne yau” murmushi ya saki me d’au sauki yana jan hancinta,” am sorry kinji akwai operation d’in da zanyi wa wani a zuciya , but zan i promise insha Allah zan dawo dawuri,okay ?”, kamar zatayi kuka ta d’aga masa kai ,”oya smile “ ya fad’a yana kara sakar mata wani murmushin, a hankali ta murmusa dukda har zuciyar batajin dad’i sam, “please kaci abinci kafun ka fita “,d’an risina mata yayi kafun ya furta “ duk yadda madam tace “, bata san lokacin da murmushi ya su’buce mata ba sai da ta murmusa, har sukaje wajan dinning hannunsu na sar’ke da na juna , da kanta tayi feeding d’insa a baki har lokaci kuma bata dena binsa da kallo ba , wayarshi da ya bata d’azu ta mika masa , kiss yayi mata a kumatu ka fun ya d’auki main wayarsa dake kan dinning d’in , ko a bakin kofar fita daga falon nasu ‘kin sakinsa tayi har hakan yaso bashi dariya da Alama yau rigima takeji, da ya juya zai fita sai ta ri’kosa ko tace “ zawj amma babu Wanda zaiyi operation din sai kai “, hannunta biyu ya kama kafun ya mayar da ita cikin falon ya dur’kusawa, “ zan dawo ba da dad’ewa ba , yau naga alama rigima kikejii, take care of you and my baby, I love you “, a sanyaye ta furta “ I love you too, kafun ta soma masa adduar data saba yi masa idan zai fita “ har zuciyarsa yaji dad’in adduar da tayi masa haka kurum yaji kamar ya fasa fitar shima sabida kewarsa da yaji ya soma yi lokaci guda Amma ba damar hakan sabida operation d’in da zaiyi. A kan kujerar da ya zaunar da ita anan ta kwanta, ita kad’ai ta dungajin kad’aici na damunta , Addu’ar neman tsari ta soma yi a cikin zuciyarta tare da yiwa mijin ta adduar dawowa gida lapiya,tana zaune akan kujerar wani wahalallan bacci mara dad’i ya d’auke ta . ✨✨✨✨ 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 ABUJA A ‘bangaran zarah da khaleed wata irin soyayya suke wa oumma , duk Wanda ya gansu tare da oumma babu me cewa ba Itace ta haifesu ba , sosai Hutu da kwanciyar hankali ya bayyana a jikin oumma ta zama babbar hamsha’kiyar mace , a yanxu Dady ya bud’e mata babban super market da ya zama mallakinta komai na ciki a ‘kasar waje ake kawo mata musamman da dady ya had’a ta da wata matar abokinsa da take zaune a London ita da yaranta, a tsakaninsu sosai Amin ta ya shiga tsakaninsu har ya zam to sun zama ‘kawaye sosai duk da har yanxu hajiya madina bata taba zuwa nigeria sun had’u ba saida ko kaya za a kawo akwai Wanda take sawa ya kawowa oumma da ynxu ake wa la’kabi da Hajiya maryam. A yanxu ma shirye shiryen tafiya BUNKURE suke da dady yace zasu kai wa ziyara kafun su wuce saudiya, da farko oumma ta so ‘kin zuwa amma dady ya zaunar da ita tare da yi mata nasiha akan tawakkali da hakuri, duk da yasan macece me hakuri da juriya dan ko shi saida ne. Gabaki d’aya gidan tare zasuje hatta hajiya da itama tace da ita za ‘ayi tafiyar , A kano zasu fara sauka ta jirgi kafun su bi ta mota zuwa BUNKURE . Sanye zahra take cikin shigar doguwar Abaya pink colour tare da small fashion bag d’inta fara da shoe din ‘kafarta me d’an tsini shima white colour , tayi rolling da mayafin abayar da ya kasance shima pink colour , babbar wayar ‘kirar iPhone 13 promo max d’inta ita bayn kwabar pink colour ne me d’antan barin barbie, sosai kayan sukai mata kyau, dukda ba wani makeup ne a fuskartaba amma sosai tayi kyau, d’ayan hannunta kuma janye yake cikin medium size trolley bag d’inta. Khaleed ne ya fito shima cikin shigar ‘kananan Kaya d’aya hannunsa shima janye da trolleys guda biyu bayansa hajiya ce itama taci uban adonta na tsofaffi har da ba’kin glass a idanunta. Oumma da dady ne suka fito suma sosai shigarsu ta ‘kayatar, dady sanye yake cikin wani Boyel d’in manyan kaya blue colour da suka ‘karawa fuskarsa dattako da annuri, oumma kuma sanye take cikin wani tsadajjen material pink colour sai adansa flowers me blue da yake jiki, ta kalmin kafarta da Jakarta sai ya kasance blue colour yayin da mayafinta ya kasan ce pink colour , ita kadai sai walwali take , duk inda ta motsa sarkar wuyanta da stone Suma sai sun ‘kada,kallan juna zahra da khaleed sukai , kafin zahra ta karasa wajansa tana masa rad’a a kunne, shima khaleed kamar ‘karamin yaro yayi mata rad’a a kunne suka ‘kyal’kyale da dariya, cikin had’a baki suka furta “ Oumma Wlh kunyi matching sosai 100%”, sun kuyar da Kai oumma tayi cikin jin kunya ganin hajiya a falon tarasa Yaushe zarah zata dena ‘barin bakin nan nata , itama hajiya da ta fuskanci oumma taji kunyar maganar zarah sai tayi shiru batare da tace komai ba , Dady kuwa kanshi kawai ya girgiza aranshi yana tunanin lokacin da zahra zatayi hankali. Basu ‘bata lokaci ba suka d’au hanyar NNAMDI AZIKIWE INTERNATIONAL AIRPORT, cikin sa’a da suka je Airport d’in ma basu zauna ba jirginsu ya tashi zuwa Garin Kano Ta dabo. Hour 1 d’aya da mintuna 10 ne ya kawo su Garin Kano , kai tsaye manyan motocin da suke jiran su a Airport d’in aminu Kano Suka shiga , Dadyn da zahra sai khaleed motar su d’aya , oumma kuma ta zauna tare da hajiya, a maimakon su nufi Gidan su na G.R.A kai tsaye hanyar da zata kaisu Bunkure suka nufa , gabaki d’aya oumma sai ta kasa sakewa tuna abubuwan da sukai mata,fahimtar hakan yasa hajiya cikin dattako ta rike mata hannu” karki damu babu abunda zai faru sai Alkairi”, gyada mata kai oumma tayi, mamakin yanda suke bin hanyar tayi wani wajan duk angyarashi ba kamar daba , lokacin da aka shigo layinsu saida gabanta ya fad’i ga Taheer d’inta da ya fad’o mata arai, tun daga layin shiga unguwarsu aka soma bin motocin su da kallo, wasu rayan na bin motar har aka zo bakin kofar gidan su , labari har ya kai cikin gidan cewa ga mutanan Birni sunzo da manyan Mota.mazan cikine kawai suka fito dan sosai rayuwa ta canza musu, suma su kawu sule shida rabi’u kowa yayi jugum jugum Suna jiran abinda zai faru, Dan duk atunaninsu anzo kama d’aya daga cikin sune, su Dady ne suka fara fitowa , tsakanin Rabi’u da kawu sule har yar rigen du’kawa sukai wajan gaishe da Dady, da fara’a a fuskarsa ya amsa musu, su oumma ne suka fito daga mota suma , gabaki d’aya babu Wanda ya gane oumma a cikinsu , kamar yanda suka gaishe da Dady haka suka gaishe da su oumma kafin cike da fargaba kawu sule ya furta “ Allah yasa ba kamamu kukazo yi ba Dan girman Allah kuyi hakuri”, kallan mamaki oumma ta bishi dashi, abunda bata ta’ba gani ba kenan wai magana cikin salama , cikin sakin fuska dady ya furta “ ko zamu iya shiga daga ciki”, d’an shiru sukayi kafun Rabi’u ya furta “ bari na yiwa yan gidan magana “, tun kafin dady ya amsa masa har yashiga gida , cikin ‘kan’kanin lokaci kuma ya dawo” Bismillanku “, su oumma ne suka soma yin gaba kafun su khaleed suka bi bayansu, suna shiga suka tarar da anshin fid’a musu doguwar tabarmar da gaba d’aya ta fita a hayyacinta duk ta zare , bin gidan oumma tayi da kallo gabaki d’aya ya canza mata yanxu babu wannan ‘kazantar, batare da wani ‘kyan ‘kyami ba suka zauna nan tabarmar, ragowar yan gidan kuwa gabaki d’ayansu cun kushewa sukai waje guda a ‘kasa kowa ka gani abun tausayi ba kamar suba, da d’ad’d’ai da d’ad’d’ai suka soma gaishe da su oumma har lokacin kuma babu Wanda ya gane ta a cikinsu, kaka ta bawa ce ta fito cikin d’akinta sai faman d’ingisa ‘kafa take, kallan Oumma ta tsaya yi kamar zatayi Magana kuma ta fasa itama zata tsugunna Oumma tai saurin ru’kota, a hankali oumma ta furta “ kaka tabawa”, itama kaka tabawa cikin dafe ‘kirji tayi saurin furta “Maryama”, gabaki d’aya ‘yan gidan kallan kallo suka fara a tsakaninsu suna tunanin wace maryama ake nufi,murmushi me ciwo oumma ta saki kafun ta furta “Na’am “, ai ba shiri kaka tabawa ta fashe da kuka tana neman yafi yar oumma , abinda bata ta’ba tsammani ba , ‘ko’karin dur‘kusawa take duk da ciwon da ‘kafarta take mata amma oumma ta hanata hakan batare da ‘kyan’kyamiba oumma ta rungumeta a cikinta, suma ‘yan gidan sai alokacin suka gane wacece, gabaki d’ayansu ko wannensu neman yafi yar oumma yake ita dai babu abunda take yai sai murmushi, ta lura Dije da Bintalo basa cikinsu amma bata ce komai ba , saida komai ya lafa kaka tabawa ta soma basu ha’kuri akan basu da abunda zasu basu, sukuwa sai murmushi kawai suke sakarmusu, ‘kara neman yafi yar oumma kaka tabawa tayi kafun ta soma labarta mata irin neman ta da suka dungayi da neman Taheer da har yanxu basu ganshi ba, sannan da irin cin zalin da Dije take gana musu, cikin kuka taka tabawa ta ‘karasa da “ maryama nasan Alhakin kine yake bibiyar mu, na ro’ke’ke da Girman Allah, ki yafe mana , mun gane kuskuren mu”, itama oumma cikin kuka take furta “ Na yafe muku gabaki d’ayanku ,” itama a ta ‘kaice ta basu labarin barowarta gida da Auran ta, abunda yafi baba oumma mamaki yanda suka nuna tsananin farincikinsu babu Hassada, nasiha sosai dady yayi musu da jan hakali cikin hikima da dattako, koda ya kammala hajiya itama sai data ‘kara yi musu nasihar su so junansu da hakuri da juna”, Tashi khaleed yayi, ba dad’ewa aka soma shigo da manyan kayan Aminci tun daga kan shinkafa, makaroni da mai da manja har dasu Dankali da doya da kwai sai da aka ajjemusu, sosai akai musu siyayya hatta oumma siyayyar taso bata tsoro, cikin kuka kaka tabawa ta soma yi musu Godiya da addua , daman tun safe babu abinda suka ci, Dije ta tattara komai na anfanin gidan ta siyar Dashi, hatta gidan tayi ‘ka’karin siyarwa Allah be bata sa’a ba , ta ibi wasu kayanta a cewar ta zata shiga yawan samo kud’i, har lokacin kuwa Bintalo ba a ‘kara ganin ta acikin unguwar ba. Gabaki d’ayansu saida Dady yabi ya rarraba musu kud’i akan su ja jari, wasu dubu hamsin wasu talatin, kaka tabawa kuwa dubu d’ari ya bata cif cif . Babu Wanda baiyi nadamar abunda yayi wa oumma ba gashi a sanadinta, mijinta ya temaka musu, itama oumma tsarabar da tayi niyar basu tasa aka rabasu, Atampopi mazan kuma shadda, hatta hajiya kaka sai data bawa kaka tabawa tsarabar kujerar makka , so kaga farin ciki wajan mutanan gidan kamar su akai wa albishir, itama oumma sosai taji dad’in canzawarsu ko ba komai an zama ‘yan uwa yanxu, ko da zasu tafi har bakin ‘kofa suka rakosu suna yi musu addua , ba ‘karamin dad’i oumma taji ba harda hawayenta da zasu rabu, aranta kuma tana Adduar Allah yasa shima Taheer yana cikin ‘Koshin lapiya a duk inda yake, basu d’au dogon lokaci ba suka kama hanyar komawa Kano dan gobe da sassafe jirgin su zai tashi zuwa ‘kasa me tsarki. ✨✨✨✨✨✨✨ 1:29pm Tahee ta farka a firgice sabida mummunan mafarkin da tayi, da Sauri ta janyo wayarta tare da dialing number d’insa amma abun mamaki switched up ake ce Mata abun da bai ta’ba faruwa ba , ‘kara dialing number tasa tayi the same abinda ake ce mata kenan, ajiyar zuciya ta sauke data Tuna cewa zai may be ko yana cikin theatre har yanxu, ganin lokacin sallah na tafiya ne yasata mi’kewa ta nufi d’akinta. Tana idar da sallah wanka tayi cikin material d’in me rawa black colour , ganin babu Wanda ya shigo part d’in harsu ihsan yasa ta saka wayarta kawai a aljihun kayanta , tare da rolling d’in mayafinta da niyyar zuwa part d’in Dada. Lokaci d’aya gabanta ya yanke ya fad’i, ga wata irin iska data soma ratsa mata zuciya kamar ana cire mata wani sassa na jiki, hannunta dafe da zuciyarta ,gabaki d’aya yau ta rasa me ke damunta lokaci zuwa lokaci Babynta na fado mata arai ganin haryanxu be kira taba . A ‘bangaran king kuwa a hanyar dawowansa Gida ,lokacin da yake driving dan yau shikad’ai yafita dan dakansa yake driving yau, hatta zaki yau be fita dashi ba ,Daidai Lokacin da ya yanki kwanar Area d’in babban titin da zata sadashi da banana Island wata babbar trolley data ‘bullo tayo kansa gadan gadan, ‘ko’karin Jan burki yayi amma sai burkin ya kwace take a Wajan babbar trolley d’in tayi sama da motar da King yake ciki tare da fad’owa duk ta rugurguje. Driver ciki na ganin hakan yayi saurin d’aga wayar sa dake ringing kafun ya furta “Angama sir “ sai kuma yayi saurin Jan trolley d’in da gudu ganin a ‘ko’karin tsayar dashi. Wasu matasa biyu da akai abun kan idan su ne sukayi saurin ‘karasowa inda motar king take kafun su kira jami’an ‘yan sanda ,ganin yadda motar ta lotse , wani card da d’aya daga cikin samarin ya ganine ya d’auka kafin yayi dialing number , Daidai lokacin dasu Abeey suke zaune a falon dada kiran matashin ya shigo wayarsa , haka kawai zuciyarsa ta tsinke kamar ba zai d’aga ba sai kuma ya d’auka , tun kafin yayi magana Matashin saurayin ya sanar dashi Accident d’in king duk da be tabbatar da alakarsu ba , “ babu abunda Abeey ya ke furtawa face Innalillahi wa inna ilaihi raji’un, cikin gaggawa ya bada umarnin akaishi NAHYAN hospital ko sauraran su dada dake tanbayar me ya faru be yi ba , cikin tashin hankali suka nufi asibitin lokacin har manyan likitocin asibitin sun shiga da shi Emergency Room, tsaro sosai Abeey ya sa a saka a cikin asibitin gabaki d’aya , dai dai lokacin da uncle musaddiq da uncle saleem suka karaso cikin tashin hankali suma , sun fi 2 hours tsaye a bakin emergency room har lokacin kuma likitocin da suka shiga basu fito ba sai abubuwan da nurse ke ta faman d’akkowa. Umarni ya bama uncle saleem da yaje ya d’akko su Dada amma kar a fada musu condition d’in da king yake ciki sai sunzo. Hakan kuwa akayi yana zuwa ya tarar dasu ashirye hakanan komai ummey asanyaye take yinsa , ga wata iska da take ratsata kamar lokacin data rasa Moha d’inta ,ga baki d’aya da mutanan gidan aka tafi ban da tafi dake fama da fad’uwan gaba lokacin. Suna shiga asibitin saura kadan jiri ya kwashe ummey, Ammey kuwa sai faman murmushi take saki a fakaice da mutum ya kalleta kuma zaiga Tsantsan tashin hankali akan fuskarta . Lokacin da suka samu labarin accident gabaki d’aya mutuwar tsaye sukai, ummey kam yau ta kasa daurewa tazo zata fad’i Abbey yayi saurin ri’ke ta hakan kuwa ba karamin bacin rai ya saka Ammey, gabaki d’aya ita sai ta nuna tafi shiga zamuwa Dan har faduwa kasa saidatayi gabaki d’aya kowa hankalinsa ya tashi, ganin babu Tahee a cikinsune Dada ta bata umarnin Mamy Matar uncle musaddiq suje su d’akkota, Aunty kam yau itama ta shiga damuwa ko ba komai ba shi ta tsana ba Tahee ta tsana, yan matan gidan ma kowa sai faman kuka take a cikinsu . ****A ‘bangaran Tahee jitayi gabaki d’aya zaman gidan ya isheta babu abunda takeso kamar tajita a waje ,da Sauri ta zabura cikin Sauri ta nufi hanyar fita daga part d’inta , babu inda take kalla sai hanya duk da duhu ya farayi, abun mamaki har tazo gate d’in farko babu security Sabida lokacin sallah yayi, a gate na biyu ne yake da tsaro amma duk cikin su babu Wanda ya hanata fita harta fice daga gidan mutane biyu ne sukayi run’kurin tsayar da ita amma babu Wanda ta kula a ciki, tana ganin ta Fita daga gidan kuma lokaci guda ta saka gudu , gudu kawai take abunta ita kanta batasan hanyar da take biba. Su mamy na zuwa suka samu wannan mummunar labari, gabaki d’aya an duba gidan bata ciki, har layin gidan kwata kwata babu Tahee babu alamarta , Gabaki d’aya bincike aka soma , lokacin da d’aya daga cikin masu tsaran ya fad’awa zaki abunda sukayi take a Wajan ya dakatar dasu daga aiki gabaki d’ayansu mutane kusan goma sannan yasaka wasu tsaran da suka fi wanda ya bari, sosai a ka shiga binciki. Su mamy na barin hospital d’in wani doctor Armeen ya fito daga cikin ER sai faman had’a gumi yake , ba Wanda be san Abeey ba shiyasa dakansa yayi wa abeey jagora zuwa office d’insu, cikin girmamawa ya soma bawa Abeey hakuri kafun ya sanar dashi King ya shiga COMA, alokacin kuma Mamy take sanar dashi neman Tahee da akai aka rasa, gabaki d’aya kuma sai kowa ya ‘kara har gitsewa musamman ummey da Ammey da suka yanke jiki suka fad’i lokaci guda, dada ma kuka kawai ta saka babu abunda take cewa sai Innalillahi wa inna ilaihi raji’un, cikin gaggawa Abeey yasa a binciki duk inda take anemota kafun ya sanar wa da commissioner da kansa akan abincika masa duk inda take anemo ta cikin gaggawa , shima gabaki d’aya ya shiga damuwa , yana tsoran halin da King zaishiga idan yasamu labarin ‘bacewar matarsa ****** SHIN KING YANA TASHI DAGA COMA? GA TAHEE DA TAKE DA CIKI TABAR GIDA KO INA ZATAJE? SHIN ZASU KARA GANINTA ? INA TAHEER ? INA DIJE DA BINTALO? WANENE MUTUMIN DA YAKE MAGANA DA AMMEY? WANENE YAJI ZANCANSU LOKACIN DA SUKE TATTAUNAWA? SHIN SU OUMMA ZASU KARA HADUWA KUWA ? INA YAYAN OUMMA DA AKACE YA BAR GIDA? Alhamdulillah anan na kawo karshen littafin GIDAN AUNTY BOOK 1 . Ina rokan Allah kamar ydda na fara littafin nan a sa’a ya bani ikon kammala shi. ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH…