An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels Compiled by Umar Dalha Copied by Princess Aysha Muhammad 💖💝BATUUL 💖💝 1 By phartiemarhk All Thanks to Allah (SWT) for granting me d chance,ability , previledge and knowledge to write this story. I dedicate this book to *KHALEESAT HAIDAR* (Maijidda) ,you have been an amazing writer,you make time for it everyday. You have set realistic goals,embraced the ecstacy of writing. You followed your heart not the market and fame. You don't just Start stories,you finish them,you dream big. You learn the rules,follow the rules and break them because rules are meant to be broken😅.Constructive, Criticism,Solicit,Accept and Manage. Put your ego in your back pocket and sit on it. Writing is à Journey, not à destination. Enjoy the scenery and give back to the writing community. WRITE SCARED. Remember you are the master of inspiration, not its Slave. Set your stories Free. Send them into the world . DON'T SLACK ON THE HARD STUFF. *PHARTIEMARHK* LOVES ❤💝You😘 Sanye take da Abaya baqa da yasha aiki da Swarovski stones ta yafo qaramin gyalen abayar ba tareda da wrapping dinshi ba kafarta sanye da slippers din vinci shima baqi mai Swarovski Stones din à jiki .Siririyace sannan ba doguwa ba tana da shape mai kyau irin wanda ake kira figure 8 bata da haske kuma bata da duhu sosai, Irin dai mutanen da ake kira chocolate color ne ko kuma wankan tarwada, dan karamin fuskar ta zagaye yake da dan karamin baki, yayinda Dogon hancinta ya dace da mazaunin sa, Idan tai murmushi kuwa dimlpe dinta yake lotsawa ya Kara hasken annurin fuskar, idanun ta kuwa haka suke tamkar farin wata wajen haske yoh masu iya magana sukace Ga Wata 🌙👈 ga Zara 😀,hooo me kr2 Idan nace zan tsaya zayyano kyawun fuskar ta toh Lalle za'a dade ban gama ba, domin dai BATUUL mai kyau ce. riqe take da iPhone dinta à hannun hagu yayinda dayan hannun take riqe da karamin yaro da bai wuce shekara uku ba, tafiya takeyi à hankali kuma cike da natsuwa sannan ga hadari da ya rufe ko ina, ruwa ko yaushe kan iya saukowa sai iska mai dadi dake kadawa à hankali à filin Idin Ramat square dake Maiduguri ,ta juyo sannan ta kalli yaron dake riqe da Hannunta sannan tace Babich kaga kasa su Mama Sun tafi Sun barmu ko ai shikenan in muka rasa sallah yaron yayi dariyarshi mai kyau yace ai zamuyi sallah har in roqi Allah ya bani irin CLS din Yaa Ahmad tace to kaga muyi sauri sai mu yi sallahn yaron ya dubeta sannan yace yaa Baatul ai kece bakya yin sauri inata Jan hannunki tace toh shikenan zanyi saurin muje mu samesu haka suka karasa har wajen Sallahn daga gefen mata suka samu har an shimfida musu abun sallah sannan suka zauna wata farar mata mai kyau da baza ta wuce shekaru 35 zuwa 38 ba tana riqe da jariri ta juyo ta dubesu tace a ina kuka sami hulan ? Baatul tace Aunty a mota ya bari matar da aka kira da Aunty tace ai ke kika biye mishi da kin barshi yayi sallah babu hula tunda da gangan ya cire, Batuul tayi murmushi tace Aunty ai da yanxu bamajin Khuduban nan da akeyi Aunty tace hakane Baatul ta juya ta kalli wata yarinya da bata wuce sa'arta ba tace Fa'iza kin dauko min jakata da nace ki fito min da ita dan inaso inyi sadaka in an idar da sallah yarinyar da aka kira da Fa'iza tace ehh yaa Baatul na dauko gashi nan ma ta dauko wata jakar Hermès mai ruwan toka da kana gani kasan an kashe naira ta mikowa Baatul ta amsa tayi murmushi sannan tace na gode Fa'iza haka suka zauna shiru suna sauraron khuduba har aka gama aka tada sallah Baatul ta dubi Fa'iza tace tunda ba kya sallah ki karbi Aabid à hannun Aunty tace toh Yaa Baatul ta sa hannu ta karbi jaririn daketa wasa sannan ta dan koma gefe su kuma sukayi kabbara suka nutsu dan su nuna godiyarsu ga Allah (swt) da yasa suka gama Azumi lafiya har yasa suka ga sallah. Ahaka suke Zauna bayan idar da sallah har Imam ya gama hudubar bayan sallah da wa'azi da tunatarwa , nan Dubban jama'ar da suka hallaci sallar suka fara kokarin kama gabansu. 💖💝BATUUL💖💝 3 Dedicated to *KHALLESAT HAYDAR* Tuki yake cike da nutsuwa da kwanciyar hankali kan titin Kashim Ibrahim Road ba a jin komai sai karar AC dake busa iska mai kanshi da dadi har suka karasa masallacin suna ta fadin (Allahu Akbar Allahu Akbar Laillaha illalah Allahu Akbar kabira wal hamdulillahi kasira wa subhanallahi bukratan wa asilaah wa sallalahu ala nabiyina Muhammad wa ala alihi wa sahbihi wa sallama tasliman kabira) Abinda suke ta maimaitawa har suka isa masallacin kenan suka samu waje suka yi parking sannan ya fito ya budewa Abui kofa Farida ma ta bude ta fito ta miko mishi Sallaya daga bayan mota sannan ta kalli Abui tace bari in karasa side na mata Abui yace okay mamana Bayan idar da sallah ne Aunty ta dauko jakarta ta ciro rafar yan dari biyar sabbi fil ta mikawa Batuul tace gashi ki bayar sadaka ai baba ya baki naki ko ? Batuul tace ehh sannan Aunty ta sake cewa Ni zamu Je mota dasu dasu Yusra dan Aabid ya fara jin yunwa in kin gama ki samemu tace toh Aunty ta karbi kudin ta saka à jaka tace sai nazo su kuma suka tafi ....Hajiya Allah yasa anyi à sa'a Allah yasa muna da rabon ganin badi Hajiya à taimaka Fisabilillahi Batuul ce ta karasa inda mutanen nan da Almajirai suke a zaune ta ciro kudi daga jakarta na bandir din dari biyar da na dari biyu ta fara rabawa bayin Allah dake wajen su kuma suna ta yi mata addua tana cikin rabawa ne wani iska mai hade da ruwa ya fara saukowa take ba tare da shiri ba ta zube musu kudin dake hannunta ta juya zata bar wajen kenan taji tayi karo da mutum, ta dago kanta da iska ke kokarin cire gyalen da sauri tana fadin Hey am sorry, bata samu karashe maganar ba sabida yadda taga mutumin ya tsaya yana kallonta dogo ne sosai dan sai da ta mikar da kanta sosai kamin ta karashe ganin tsawonsa , kyakyawa ne sannan ba fari bane baqi ne amma baqin shi mai haske ne, yana da side burns sannan yana da dogon hanci da mitstitsin baki dake zagaye da millionnaires belt duk da akwai hula akanshi sai da ta hango gashin kanshi kanannadadde da hulan bai rufe ba haka ma gashin gira da lashes dinshi bakake ne, cikin seconds da basu fi uku ta gama kare mishi kallo tayi sauri ta saukar da kanta kasa dan hawaye taf ya cika idonta, bugun zuciyanta ya karu kamar zai fito ya bude baki kenan zaiyi mata magana cikin sauri ta matsa baya daga wajen bata tsaya yin komai ba ta juya cikin sauri sauri da dan gudu ta karasa inda tayi parking BMW 8 séries ta bude ta shiga ta jefa jakanta baya , tana zama tayi ajiyar zuciya Aunty ta juyo ta dubeta tace lafiya kike ajiyar zuciya ? Tace Aunty ruwan nan da nayi escaping bai jikani bane ya sani yin ajiyan zuciya Aunty tace toh ni yanxu karbi key mu tafi gida Yusra ta Ce min yunwa takeji, ga Aabid ma na rigima Batuul ta juya bayan motar ta kalli wacce aka kira da Yusra tace ba sai da nace kici abinci ba kamin mu fito ba kika ki wai ke sai kin dawo Batuul ta juyo ta dubi Aunty tace Janet fa har binta ta riqayi da abincin kamin ta saka mata kaya taqi shine yanxu zata cewa mutane wai tana jin yunwa bata ce komai ba Yusran sai zumburo baki da tayi Batuul din ta sake ce mata ki bude jakana akwai TWIX ki dauko kuci ke da Hafix (Babich) ki bawa Fa'iza ma sannan ta juya ta dauki tissue à gaban motar ta goge fuskanta da ya jike da ruwa, ta bude pidgin din motar ta dauko orbit mai flavor din pepper mint ta jefa à baki sannan ta gyara gyalen ta daura shi kamar dankwali sannan tayi igniting motar ta tada suka tafi Tunda ta bar wajen yake tsaye yana kallonta har ta shiga motar suka tafi bai dena kallon wajen ba sai da yaji an taba shi ta baya ya juyo ya ga Wanda ya tabashi Ya kalli Wanda ya tabashin tare da Sakin Fuska yace Massa ya akayi shehu ya bari ka bar wajen shi kuma ban ga ka saka rawani ba Massan yace Man bari kawai ai bazan iya zama ayi hawan Durba dani ba yanxu haka ma gudowa nayi yace kai mey kake yi anan kai kadai bayan naga Abui ma suna tare da Shehu yace yeah abu nazo yi amma banyi bama sai nan gaba Massa yace okay muje sai da ya sake juyawa tare da ajiyar zuciya kamin yabi inda hanyan da Batuul tabi kamin su tafi 💖💝BATUUL💖💝 2 Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Agogon batman din dake manne jikin bango ne yayi ticking 6:30 da rabi dai dai na safe tare da yin sauti, Tashi yayi tare mikewa daga kan lallausan katafaren gadon da yake kwance kai, yana mai karanto adduar tashi daga bacci (Alhamdulillahillazi ahyana ba a dama amatana wa illaihin nushur sannan ya kara dayiwa Annabi (SAW) salati, ya tashi ya juya ya kalli agogon da ya farkar dashi daga bacci yaga har 6:40 tayi, yayi sauri ya karasa toilet din dake manne à dakinshi cikin hanzari yayi sauri yayi brush yayi wanka sannan ya fito daga toilet din daure da towel da kuma wani towel din a hannunshi yana goge fuskarshi da ita har ya karaso gaban wani babban mirror da mutum kan kalli kanshi gaba daya tun daga kai har kafa ya karasa goge kanshi kenan zai shafa mai yaji karar wayarshi na ringing da har yayi kaman bazai dauki wayarba sai kuma ya juya ya karasa inda wayar take, yana ganin mai kiran da sauri yayi maza ya dauka tare da zama sannan ya risina kamar mai Kiran na gabanshi, zama yayi kamin ya kara wayar a kunnanshi tare da cewa Hello Ammah *nda wattu*(ina kwana) daga daya bangaren aka amsa da *kêlewa sêlai* (Lafia Alhamdulillah) sannan aka sake ce mishi Abu ka shirya ne yace à ah Amma saura kadan yanzu zan shirya in fito tace yawwa Dan Shehu yace bana karfe takwas za ayi sallah kuma kasan kaine zaka tafi da Abui ya ce *yo dai kêrma lukin*( toh gani nan fitowa yanzu ) ya katse wayar ya ajiye Closet din kayanshi ya bude sannan ya dauko wani sky blue din shadda mai kyau da tsada ya saka ya dauko cuff links dinshi na Mandarina duck sannan ya sanya su a hannayen rigartasa tare da dauko hular Rawaram blue mai dan ratsin black brown ya seta ta a kanshi kamar da kan akayi hular ta zauna d'as agogon shi na Fendi ya makala à hannunshi na dama sannan ya dauki Turaren Tom Ford da Rasasi dake gaban mirror dinshi yafesasu à jikinshi kamin ya koma gaban coffee table ya dauki key din motar dake ajiye akai da kuma wayarsa sannan ya sako takalminshi baqi na Haven ya fito daga dakin tare da kallon agogon hannun shi yaga bakwai daidai Saukowa yake daga kan benen cikin kwanciyar hankali da natsuwa har ya karasa sauka ya isa wani kaftareren parlour da girmanshi ya dauki set din kujeru uku, karasowa yayi cikin parlour ya isa wajen wani dattijon mutum mai dan haske yana sanye da kaya na alfarma , sanye yake da farin glass à idonshi, hannunshi kuma riqe yake da remote ya saka tashar Iqra yana kallon yadda musulmai ke nuna farin ciki ga ubangijinsu, gabanshi kuma glass table ne dauke da flask din tea an zuba Kadan a *finjal* ( karamin transparent kofi na shayi) Ya karasa tare da zama dab da kafan dattijon tare da Ce mishi Abui *nda wattu* (ina kwana) *Bara ngêmêriaa* (Barka da Sallah) Bara *Ngêmêriro* ABUTTURAB (barka dai ABUTTURAB) ka tashi lafiya yace Alhamdulillah Abui sannan yace mishi Jiya na tura Abubakar yace maka an sanar da ganin watan sallah daga *SHEHURI* (palace din sarkin Borno) yace min ka rufe kofa kuma wayoyinka ma duk a kashe yace ehh Abui na gajine jiyan shiyasa na shiga da wuri kauyukan da mukaje kai zakka ne hanyoyinsu babu kyau amma Massa ya kirani ya fadamin that babanshi yace anga wata gobe sallah kuma nasan shehu da kanshi zai qira ya sanar da kai shiyasa ban sauko na fada ba yace ehh tun jiya shehu ya kirani yace okay bari in shiga inga Ammah dan tun safe ta kirani wai ka shirya kana ta jirana yayi murmushinsu na manya yace ai Ammah tun karfe biyar da ta tashi bata koma ba sai da tashi kowa har masu aiki tun karfe biyar suka tashi suna ta hidima yace ai Ammah akwai kokari sannan ya tashi ya sauka daga kan matakala da basu fi biyar ba yabi wata hanya har ya isa kitchen tare da sallama wata mata mai dan madaidaicin jiki kyakyawa fara ta juyo ta dubeshi tare da amsa sallamanshi tace Abu kowa ya tashi à gidannan kai baka tashi ba kuma bana karfe takwas za ayi sallah Abui tun dazu ya shirya yana jiranka, yayi murmushi tareda karasawa wajenta y'a rungume matar tareda da sumbatar goshinta yace mata Ammah barka da Sallah tayi murmushi kamar ba ita ke fada ba yanxu *Baaranêm* Abu (Barka Abu) suna tsaye a haka wani saurayin yaro fari kyakyawa dogo amma bai kai Abu girma ba ya shigo tare da gyaran murya yace Ammah muna nan fa ta juyo tace Babana har ka shirya ne ya karaso tare da daukan Apple dake cikin basket à kan kitchen Island din ya dan bata rai yace Ammah an manta da damu ana kula da Babban da ya dace ace yana gidanshi yanxu, Abu y'a juyo ya harareshi yace ai sai ka kaini gidan nawa Ammah tace ai gaskiya Sadiq ya fada Abu ya girgiza kai ya fita Ammah ta dubi Sadiq tace muje kuyi breakfast mu tafi masallaci Sun fito kenan sun karasa dining area mai dauke da round dinning table mai adon royal gold, kan dinning table din dauke yake da abinci na alfarma irin su *ndalayi*, *kisre* (sinasir) *kêmoniye*(farfesun kayan ciki) *ngaji*(burabusko) miyar kubewa, yakuwa, peppered chicken sai kunun gyada. zagaye table din yake da kujeru guda sha biyu sunja kujerun zasu zauna kenan wata yarinya fara kyakyawa da baza ta wuce 16 yrs ba ta fito à guje tana fadin Ammah wanne zan sa........bata karasa maganar ba tayi shiru tareda da riqe baqi tace ooops Yaa Abu ina kwana ya dubeta yace kin tashi lafiya tace ehhh Alhamdulillah ta juya ta kalli mamansu tace Ammi Yaa Abu ba ya tafi Umara ba ? Sadiq ya juyo yana dariya yace bai tafi kuma da shi zaki tafi masallaci tace amma lokacin da mukayi waya da ina school ai kace ya tafi, Sadiq ya sake murmushi yace toh ya fasa tace toh ta sake duban Ammanta tace Amma *ndaso yikêkin* ? (wanne zan saka ?) Ammah tace mata ki saka blue din tace toh ta juyo ta dubi Yaa Abu tace da Abui zaku tafi masallaci ? Kanshi à duke yana danna waya ba tare da ya dago ba yace mata ehhh Ammah da Sadiq basuce komai ba sai tsayawa da sukayi suna kallonta dan suji dalinlinta na tambaya amma bata ce musu komai ba ta koma jikinta a sanye tana fara tafiya taji yace Farida tace naam Yaa Abu yace mata saura ki tsaya kwalliya ki bata min lokaci ba tare da cewa komai ba ta juya taci gaba da tafiya har taje daki sannaan ta zauna akan makeken gadon dake dakinta ta fara yiwa kanta magana tana cewa Yaa Abun nan kullum wai sai da Abui zai tafi dan yasan kullum Abui nake bi shine kuma yace shima dashi zaije kuma ya dinga hana mutane magana wai shi bayason surutu, Ni nan gaba zan dena bin Abui ina bin Ammah Ammah ce ta kira daya daga cikin masu aikin gidan tace Fanne ba a kawo shayin Abu ba da sauri mai aikin taje dauko flask din ta ajiye ta juya ita kuma Ammah ta tafi bawa mijinta abincinshi , ya dauki flask din tare da zubawa a cup yana kurba kadan kadan kanshin shayin ne ya sani matsawa baya saboda in naci gaba da shaqa toh sai nace musu su zubamin, kanshi ne da ya hada na lemon grass, na'na',citta, kanumfari da cardamom seeds da mint leaves. Bayan ya gama shan shayin ne ya dauki saucer ya Saka kisre guda daya da miyar kubewa danya da yaji naman kaji à ciki. Ahankali ya dinga ci har ya gama sannan ya miqe ya yaje wajen hand wash basin din dake dinning area din, ya wanke hannunshi ya tsane da towel sannan ya bude fridge ya dauki robar ruwan faro, ya juyo ya tambayi sadiq bayan ya kurbi ruwan Sadiq wane masallaci zakuje da Ammah ? Yace filin polo zamuje kasan bata cika Son zuwa Ramat square dinnan ba yace Toh ni zan wuce bari inje inga ko Abui ya gama sai mu tafi Allah ya kaiku lafiya sai kun dawo ya sake cewa Sadiq kayi tuqi à hankali dont play rough with my life on road Sadiq yayi dariya yace she is mine too y'a karasa falon ya tarar Abui ya gama cin abinci har ya miqe yana saka babbar rigarshi Ammah kuma na fesa mishi turare sannan ta gyara mishi hula Abu yayi murmushi yana son yanda suke kula da junansu dukda Sun tsufa. Abui ne ya juyo ya kalleshi yawwa Abutturab muje lokaci ya kusa kurewa sai kuma ya tuna ashe sarkin rigimar tasa ba ta fito ba ya bude baki kenan zaiyi magana sai gata ta fito da murmushinta mai kyau ta saka riga da skirt din super yellow mai shudin flower ta saka hijab shima blue hannunta riqe da jakar cardio baqa ta karaso taje ta rungume babanta sannan ta tambayeshi Abui *shawangêna*(nayi kyau)? Yace mata sosai mamana kinyi kyau muje ko ? Tace okay su ukun suka fita su kaje inda motar take pake Abu ya budewa baban nasu mazaunin dake gefen driver farida kuma ta shiga baya. kamin su fita Ammah ma suka fito ita da Sadiq tana sanye da laffaya green and red suka nufi GLK din dake pake à wajen parking mota, sai da suka shiga suka tada suka fita tukunna Abu ma yabi bayansu, su sukayi hagu ta su Sadiq kuma tayi dama. 💖💝BATUUL💖💝 4 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* A gaban gate din wani mansion ta tsai da motar tare da yin horn, masu gadine su biyu suka fito cikin hanzari suka bude musu gate din suna yi musu sannu da zuwa, karasawa tayi cikin gidan har ta isa inda ake parking, kamin ta tsaida motan Yusra tayi sauri ta bude kofan ta fita Hafix ma ya bita a baya, cikin hadin baki Aunty da Batuul suka ambaci "Inna lillahi wa inna illaihi rajiun"Fa'iza ta fito itama a guje ta bi bayansu tana fadin bakuji ciwo bako su kuma suna ta kyalkyala dariya Yusra tana fadin ai na rigaka shima Hafix yana ya rigata, suna karasawa bakin wani sliding door mai girma na glass suka tsaya dan baza su iya danna kararrawar ba yayi musu nisa sai Fa'iza ce da ta karaso ta danna musu kararrrawar suka tsaya jiran à bude musu kofar, à dannawa na biyu ne aka bude musu kofa daidai lokacin Aunty da Batuul suka karaso suka Shiga ciki, parlour ne mara tarkace amma yana da kyau, wallpaper ne baqi mai flowers fari da grey zagaye da dakin , daga tsakiya akwai farin kujera mai L shape da throw pillows akai ,karamin round Table daga gaban kujeran, office chair daga gefe sai Babban TV da ya kusa cinye bango dan girmanshi à manne da bangon. Kanshine mai dadi na sandal wood ke fitowa daga parlour hade da iskan Ac mai dadi da sanyi ,bayan sun karasa daga ciki sun wuce wani bene mai rails silver suka isa wani dinning area shima créam ne da Brown mai dauke da dogon dining Table da kwanuka na alfarma sai chandelier daga tsakiya Bayan sun shiga sun zauna ne yarinyar da ta bude musu kofa tace "sannunku da zuwa Aunty " cikin hausar ta da ba dai dai ba " Aunty tace mata sannu Janet, Su Ahmad Sun fita ne naga motan da suka fita dashi à parke " "Janet tace à ah Aunty sun dawo tun dazu Sun hau dakinsune, su da babane dukkansu Sun dawo shima ya tafi sama" " Batuul ce ta juyo bayan ta ajiye wayar da take dannawa tace Tabawa fa ko har yanxu aiki take ba à samu tayi wanka ba, Janet tace à ah Aunty taje dakine zatayi wanka, tace okay Tafiya sukeyi suna ta gaisawa da dimbin jama'ar da suka halarci sallah Massa ya dubi Abutturab ''Man yaushe zaku koma Abuja ne ? Abutturab ya furzar da iska daga bakinshi sannan yace " Yeah i want to leave in the next four days dan inada appointment da Minister amma nasan su Abui sai next week cuz su sai Sun gama sallah anan. I cant wait that long" "Massa yace okay nima sai next week din zan shigo ", suna tafiya har suka iso inda su Abui suke, Abui ne ya Juyo ya dubesu tare da cewa mutumin da suke tsaye tare, "ai gasu nan ma", mutumin ne ya fadada murmushinshi tare da fadin "Masha Allah" ya miqa musu hannu suka gaisa, yacewa Abui "Its been long i met them , almost 19 yrs nasan bazasu tunani bama, anyway ya kuke ? Ana karatu ko kuma an gama ? Ko kuma aure za Ayine ya fadi maganar tare da dariya ? " , take fuskan Abuturrab ya canza dan baya so ana mishi maganan aure in Abui na kusa , yanxun nan zai tada maganar har sai ya dinga magiya taré da bashi hakuri Abui ne ya bawa mutumin ansa tare da fadin "ai aure kam sunqi shi, Shi Aliyu(Abutturab) architect ne dan yanxu ma yana da contact da minister Abuja, Mustapha(Massa) kuma Doctor ne tunda yayi karatu à Germany sukayi retaining dinshi, but munaso ya dawo dan baza mu barshi cikin turawa ba", mutumin yace "gaskiya kam, Allah ya taimaka. " *Alai*(Alhaji) Ahmad Kyaree zan wuce yanxu dan nasan su Madam suna jira, tare mukazo dasu kuma ga ruwan da akeyi, zan kawosu before ku koma in sha Allah " , Abui yace okay à gaidamin su, ace musu muma muna nan zuwa. Tunda mutumin ya fara magana Abutturab bai dago kanshi ba har sai da mutumin ya fara maganan aure, a snn ne ya dago kanshi ya k'arewa mutumin kallo har yaso gano inda ya sanshi amma ya kasa, sai cewa Abui yayi bayan mutumin ya karasa barin wajen, " Abui is he an old friend"? "Yeah à good one too inji Abui ", tare da basu labarin tare da ce musu su tafi kamin ruwan ya kara yawa " Ta miqe kenan tana cewa Aunty zata haura dakinta tayi wanka ta canxa kaya dan Sun jike ta hango Babanta na saukowa daga bene, da gudu taje ta rungumeshi, "tace Baa yanxu nakeso inje wajenka, ya d'an janyeta daga jikinshi yana tambayarta "Batuul ya kayanki à jike" ? "Tace Baa ai anyi ruwa à waje ku tun dazu kuka dawo ko ? Ya sake ce mata "Batuul yanxu sallahn Allah shine kika saka baqin kayan nan kikaje har masallaci dashi ? Batuul ta danyi kasa da ido ta zumburo karamin bakinta kamin tace "Baa sabone fa kuma designer ne na Hauté Èlan kai ka siyomin mafa " , yace mata "toh naji maza Je ki cire su kar kiyi mura, tayi murmushi tace yanxu zan dawo ai, ta haura sama shi kuma ya karasa saukowa kasa . Har ta wuce wani daki à sama sai kuma ta dawo daga baya, cikin sand'a ta bude kofar dakin, a hankali take turawa, sai da ya fara karane ta bude shi gaba daya tana fadin Taraan, yara ne maza a dakin su biyar, kowa da game controller a hannunshi suna ta ihu,typical dakine na maza da akayi littering gwangwanaye drinks, kayansu da suka cire daga k'asa, gadajen à hargitse sai plates din abinci da spoons.Yan manyan guda biyu da baza su wuce 13-15 yrs ba sanye suke da wandunan shadda sai fararen vest à jikinsu hannunsu kuma maqale da agogo, sai mai bi musu shi kuma sanye yake da complète kaftan dinshi brown harda hula akanshi ya tsaya akan sofa yana ihun ni zanyi winning, dayan kuma sanye yake da three quarter da T-shirt shima yana riqe da game controller, karamin cikinsu ne snn duk yafisu haske yana daga gefe riqe da Ipad à hannunshi yana ta aikin dannawa, Suna ganinta suka yadda abubuwan dake hannunsu, Manya ukun na ihun Aunty ta dawo kanana biyun kuma suna cewa Mama ta dawo, a guje suka fito kowa na rige rigen ya riga dan uwanshi fita daga dakin, Da sauri Baatul ta matsa daga bakin kofa dan kar su bigeta tana ta dariya ta juya ta bar kofar dakin ta karasa nata dakin ta murda kofan ta shiga. 💖💝BATUUL💖💝 5 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Tana shiga daki ta nufi inda towels dinta ke rataye, ta janyo daya sannan ta cire kayan jikinta da suka jiqe, ta daura towel din a kirjinta, ta nufi toilet din dake dakin nata, bayan minti goma ta fito tana kanshin shower gel da sabulun Makari,da towel a jikinta daya kuma a daure a kanta kamar turban, gashin goshinta ya kwanta lub lub, fuskanta ya kara haske da kyau, ta karaso gaban mirror dake cike da turararruka da yan kayan kwalliya da na shafa , ta jawo stool din mirror ta zauna sannan ta dauko man Makari, a hankali ta riqa shafa man kamar baza ta gama ba, bayan ta gama ne ta karasa gaban closet din kayanta, ta bude ta dauko peplum blouse da skirt din atamfa baqi mai pattern din purple ta saka à jikinta, kayan ba karamin kyau yayiwa jikinta ba, komawa gaban madubin tayi ta shafa powder a fuskarta sannan ta saka kwalli a idonta, ta shafa nude lipstick a bakinta , ta bude costume box dinta dake kan madubin daga gefe ta dauko dankunne da sarka silver masu duwatsu a jiki, sai abun hannu da zobe shima silver, sannan ta fesa turare, ta kalli kanta a madubin tare da murmushi sannan ta koma ta zauna a kan gadonta tare da d'aukan wayanta, bayan ta d'an daddana wayan ne ta kara à kunne tare da fadin "Hello Riri, shine kikace min a Ramat Square zakuyi sallah, kuma bakije ba, Daga daya bangare aka amsa ana dariya tare da fadin "Yo babe nan naje mana, i wanted calling you inji inda kike sai sai da na duba wayana naga ban fito dashi ba, You know anytime Yaa Abu na gida toh komai nawa doesnt seems to be ryt" "Batuul tace babu wani Yaa Abu, anytime kika samu matsala sai kice shine, toh duk ranar da zan ganshi sai na fada mishi "Riri tayi dariya,tace mata dan baki sanshi bane ai, koh face dinshi idan kika gani zakiga ko smiling bayayi, brows dinshi kullum a hade, bayayiwa mutane ma magana wai surutu na saka mishi ciwon kai, kuma ko bashi zaiyi ba wai baza ayi a kusa dashi ba, "Batuul tace all these apart, ni zanzo yau dan Baa yace nan da kwana hudu zamu koma dan yana da aiki sosai kuma gobe da jibi zamuje wajen su Yayya da sauran Family "Riri tace yawwa bae of earth,daman ina ta tunanin yadda zan ganki, I missed you soo much wlhy, kizo yanxu i have have So many things for you alone, Batuul tayi dariya tace "You are not serious, ai sai na fadawa Baba tukunna, sai yayi approving zuwana "Riri ce ta marairaice murya hade da cewa nasan Baba zai barki sai dai in kece bakison zuwa, pls kizo, am bored over here, kuma kinsan Yaa Abun in yana nan ba a yawo " "Batuul ce ta cemata ni ba ruwana and i told you zan fada mishi whenever i meet him" "Ai bazaki iya ba nasanki, I wish zaki zo yana nan shima yaga wanda ya fishi rashin magana,ai mantawa ma nayi halinku daya nake fada miki "Ni dai yanxu a bar maganan, yanxu zanje in fadawa su Aunty zanzo wajenki , "Aii sai kinxo" sannan suka katse wayan, tashi tayi ta jona wayan a caji ta juya ta fito daga dakin, har ta karaso kasa, ta sauka daga benen ta jiyo muryoyin yan gidan a dinning suna cin abinci, karasowa tayi wajensu, Mahir na ganinta yace Yaa Batuul kinyi kyau, Hafix ma yabishi yace kinyi kyau, tayi murmushi tace musu nagode, kuyi shiru ku gama cin abinci, kujera itama taja ta zauna a gefen Baba daga hagu, Baba ne ya ce mata "kinga kayan nan yayi miki kyau amma ba kiyi ta saka baqin kaya ba a kowane occasion", Aunty ce tace ai Y'ar kauye ce," ta juyo ta dubi Baba tai raurau da ido, yana ganin haka ya yace "À ah Mamana ba y'ar kauye bace, ai kayan nayi mata kyau" ko ? ya tambayeta ,murmushi tayi sannan ta dauki plate, ta janyo wani babban tray da aka rufe da foil paper ta bude,Danderu ne na kaza yana ta tiriri da kanshin kayan yaji, kadan ta saka à plate din sannan ta sake janyo wani food flask din ta dauki masa daya a ciki tare da miyar masa, a hankali ta riqa ci ba tare da cewa komai ba har suka gama Sun gama cin abincin ne suka tashi suka koma palo, Fa'iza da Janet ne suka zo suka gyara dinning din tare da kara turaren wuta à duka electric burners din gidan Sai da kowa ya zauna ya nutsu sannan ta dubi Baba tace "Baa inason inje wajen Farida tunda gobe da jibi we Will ne busy, "Okay what time zakije ? Cewa tayi "ko yanxu tunda naga its already after 12" " Tunda su Baa Liman(Driver)suna hutu sai Ahmad ya kaiki dan ya fiki iya driving kuma bana Son kina driving ke kadai especially a Maiduguri da ba a bin régulations din driving " "Okay Baa nagode, " Aunty dai bata ce komai tunda Baba ya yadda shikenan. Tashi tayi ta k'ara haurawa sama ta dauko jakarta ta channel purple shima irin kayan da karamin gyale shima purple amma light, ta kara duba fuskanta a mirror sannan ta sauko Tana saukowa taga Ahmad riqe da key din mota a hannunshi yana jiranta, karasowa tayi ta ce wa su Baba zasu tafi, " yayi musu sai sun dawo sannan yace mata idan ta gama sai ta kira a zo a dauketa, tace toh", Tacewa Aunty sai Sun dawo, Aunty tace mata ki gaishe da Ammah kice mata nima zanzo ko bayan mun koma Abuja ne, Toh tace sannan suka fita suka nufi inda akayi parking motocin gidan suka shiga wata Audi fara sol, Ahmad ne ya tambayeta anguwan da zasu bayan yayiwa mai gadi horn kamin yazo ya bude mishi kofan, ce mishi tayi Old GRA ne in munje zan nuna maka hanya, Ya juyo yace mata "Yaa Batuul Allah kwatancanki akwai wahala yanxu sai mu kai two hours muna neman wajen da baifi muje a 20 mins ba " "Tace toh ka bani inyi driving" baice mata komai ba yaja motan suka bar gidan bayan mai gadin yayi musu a dawo lafiya Tafiyan minti goma sha biyar suka isa gidansu Farida a old GRA ,Horn yayi aka bude musu gate suka shiga, suna shiga gidan bugun zuciyanta ya karu, ambaton Allah ta riqa yi har sai da taji ya dan ragu sannan ta bude motan ta fito daga ciki tare da yiwa Ahmad sai anjima akan in ta gama zata kirashi Farida na Jin tsayuwar mota ta fito daga cikin gida a guje tazo ta rungume Batuul ta na ihun i missed you so much babe, "Batuul ce tace mata sakeni kar ki ballani Baba ya hanani zuwa nan gaba" Dariya tayi sannan tace nasan Baba bazai hanaki zuwa sai dai in ke zaki min halin naki ki qi zuwa, Batuul batace komai ba har suka karasa ciki ,tacewa Farida Ammah da Abui da Sadiq fa ? "Ammah da Sadiq basu dawo ba inaga Sun tsaya wajen Ayyi, Abui yana Shehuri, Nida Yaa Abu ne a gida kawai shima yana sama, Batuul tace "okay", sama suka haura suka isa dakin Faridan, suna shiga ta cire gyalenta ta ajiye a akan gadon ta juya inda fridge din dakin yake zata dauki Fanta, tana budewa taga babu Fanta à fridge din, "kinsan zanzo shine baki saka Fanta a Fridge dinki bako, sai tarin bakaken drinks da kika ajiyewa mutane(coke),ni na sauka fridge din kasa in dauko, batajira jin abinda Farida zata ce mata ba ta sauka ta isa dinning area ta bude standing fridge din zata dauki Fanta taji wata Murya cikin sanyi an Ce "Farida kawomin bottle water daya", bugun zuciyantane ya k'ara tsananta, Bata juyo ba kuma batayi magana ba har sai da ya k'ara maimaita maganar amma yaji shiru, ransa ne ya b'aci ya taso yaga abinda takeyi da har ya hanata amsa mishi, yana zuwa ya fizgota da k'arfi da har saida ta fada kirjinshi kamin yayi sauri ya janyeta 💖💝BATUUL💖💝 6 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* tsayawa yayi ya na kallonta ita kuma kanta à kasa, ba a Jin komai sai bugun zuciyanta da ya kara tsananta, riqon da yayi mata ne da kuma bugun zuciyanta yasa hawaye taruwa à idonta, kiciniyar kwace kanta ta fara yi daga wajenshi amma yaki saketa, Dumi yaji a hannunshi ya juya yabi hannun nashi da kallo, hawayen da ya gani ne yasa shi sakinta a hankali ya juya mata baya, juyowa ya sakeyi zai yi mata magana yaga bata wajen, Parlour ya koma zauna yabi stairs din da ta hau da kallo, lokaci daya ya shiga kwada ma Farida qira, A bakin kofa ta kusa cin karo da Farida, Farida tace "kinga abinda nake gaya maki, I Wonder why he is calling me yanxu" bata karashe maganan ba ta ta riqe Baatul tana tambayarta "Why are you sore ? Mey ya sameki kuma idonki ya canja , kamin ta bata answer ta sukaji ya sake kwada ma Farida kira, bata jira cewan Batuul ba ta sauka kasa tace "Gani Yaa Abu" a nutse yace "Who is she ? I mean that lady, doesnt she talk ko kuma gaisuwa ne bata iya ba ? A zuciyanta cewa tayi "Innalillahi wa inna illaihi rajiun, Yaa Abun nan komai ba a yi mishi daidai, in nayi magana yace na cika surutu, yanxu kuma Batuul bata yi magana ba zaiyi fada" Tana cikin tunanin taji yace "am i not asking you ?" "No Yaa Abu bata jin dadi ne shiyasa bata gaisheka ba, Ce mata ya sakeyi "daga ina take"? "Batuul cefa kawata tun muna Centagon wacce ka kaini gidansu a Maitama last year da ka dawo har kace bazan kwana ba", Hannu ya daga mata alaman ya isa, "ki miqomin ruwa a fridge", a kan center Table din gabanshi ta ajiye ta juya ta bar falon D'aki ta nufa, tana shiga ta tarar da Batuul à tsaye tana riqe da jaka da gyalenta a hannu, "Zan tafi gida" "Ban gane zaki tafi ba saboda mey" Farida ta tambaya , Yaa Abu yayi miki fada ne dan nasanshi da yiwa mutane fada, "Ni baiyi min komai ba kawai zan tafi ne" "In kinje toh mey zaki cewa Aunty ya dawo dake bayan kince har dare zaki kai " kuma in Ammah ta dawo mey zan fada mata ? That kinzo har kin koma ? If Yaa Abune baza mu sake bin hanyan da yake ba nima haka yake min "Toh naji bazan tafi ba amma baza muje inda yake ba " Farida ta kyalkyale da dariya tace, "Keh da kika ce zaki fada mishi ina gulman shi yanxu kuma ke da kanki zaki qi bin hanyan da yake " "Ni ki rabu dani, kuma ai ni babu abinda yayi min kuma zan fada mishi din ai", haka suka ci gaba da hira har Batuul ta manta da Abutturab na gidan Yana zaune a palo bayan ya kurbi ruwan da Farida ta miqo mishi, tunani yayi na lokacin da Baatul ta bigeshi a masallaci da yadda tace mishi sorry har yanxu da ta zo gidansu yaga hawaye a idonta, hawayen da ya tuna ne ya sashi ajiye ruwan yana fadin "Damn it" à hankali, "does shi always cry"? Yana cikin tunanin yaji an bude kofan palon , Ammah ce tare da Sadiq a bayanta suka shigo suna hira, ciki suka karaso suka zauna a palon, Abu ne yayi musu sannu da zuwa, Ammah ce tace "baku tsaya anyi hawa bane da ku "? "Ehh naso mu zauna sai kuma na fasa amma Abui yana can" , "Muma munje mun duba Ayyi ne, sannan ta kwalawa Fanne kira,cikin hanzari Fanne ta karaso tacewa Ammah "sannu da zuwa,Gani" "kije ki duba min Farida kice mata mun dawo, sama Fanne ta haura ta fadawa Farida sakon da aka bata sannan ta fita, Farida tacewa Batuul "muje ki gaida Ammah nasan baza ta hawo palon sama ba shiyasa ta sa a fadamin" "Ni sai kinje kin duba in Yaa Abu baya palo tukunna zanzo" "Farida tace you are kidding me,taso mu tafi ai in Ammah tana nan bazai yi komai ba" Hannun ta Farida ta jawo suka sauko k'asa, lokaci daya ta d'ago kanta suka hada ido hudu dashi, ta dauke nata da sauri ta karaso cikin falon ba tare da ta kallesa ba suka iso gun Ammah, Farida da gudu ta karasa gun Ammah tana fadin "shine Ammah kuka qi dawowa da wuri inata jiran ku, Ammah bata yi mata magana sai Batuul da ta cewa " A ah Batuul yaushe kikazo, su Aunty na lafiya ? Ashe kunxo, Aunty da mukayi waya tace mayb baza ku zo ba dan Baba na aiki, anyi sallah lafiya ? Batuul da murmushi a fuskanta ta k'arasa wajen Ammah ta zauna daga k'asa sannan tace Alhamdulillah, ta tambayeta ta karfin jiki, "Alhamdulillah Batuul, kun gama karatu lafiya ? Next two weeks zakuyi graduation dinku ko ? Da "Eh" ta amsawa Ammah, Ammah tace "Allah yasa kuyi a sa'a, suka amsa da Amin dukkansu, Sadiq ne ya cewa Batuul "Wane school kikayi applying admission ne , ko har yanxu oxford din zakije ya k'arasa maganan yana dariya, Batuul tace " ban sani ba ko Baba nan yake nema min but if ban samu ba may Baze ko Nile zai kaini dan bayason inyi nisa, Sadiq yace "ai dama oxford makaranta masu ilimine ko da yake ai kema kina da ilimi you can do it", tayi murmushi tace kai Yaa sadiq" Abutturab na zaune yana kallon TV amma duk hankalinshi yana kansu, tunani yake yaushe ma suka santa and everything about her,wai har Sadiq ma yasan makarantar da take son zuwa, tab'e baki yayi ya ci gaba da kallonshi, Ammah ce ta tashi ta hau sama, yan matan ma suka bita, da ido ya bi bayanta har saidai suka shige ciki 7:20 na dare duka y'an gidan na kan dinning suna dinner,Abutturab ne kadai baya nan Ammah ce ta tacewa Batuul "kwana zakiyi amma ko" Batuul tace "a ah Amma zan tafi yau, yanxu ma Ahmad nake kira baya picking, shi zaizo daukana Ammah tace , "No ai ba sai kin kirashi ba , gasu Sadiq sai su mayar dake bari a gama dinner, Toh kawai tace dan batason yiwa Ammah musu Abui ne yace "su tafi da Abutturab dan yanxu zamu fita da Sadiq", mik'ewa yayi yacewa Batuul in taje gida ta gaida Baba, tace mishi yayi ta trying number dinshi its not going" Ta amsawa Abui da "Toh" sannan ya ciro rafar kud'i daga aljihunshi yace ga Barka da sallahn ta nan,tayi godiya. Saukowa yayi daga stairs sanye da grey sweats da farin shirt hannunshi rik'e da key din mota, Ammah ce ta tareshi tana tambayanshi inda zashi,yace mata shehuri zashi, Ammah tace mishi "zakayi droping Batuul a gida , shi ya manta da yarinyar ma saida Ammah ta ambaci sunanta , cewa Ammah yayi "Sadiq fa baya nan ne, "tace sun fita da Abui, iska ya fitar daga bakin shu snn yacewa Ammah " a kirata mu tafi, am in a hurry, Fanne Ammah ta kwadawa kira tace taje ta kira mata Batuul ace ta fito su tafi, fitowa tayi bayan Fanne ta fada musu sakon Ammah, wannan karon babu gwagwaro a kanta sai gyalen kawai ta yafa,tana saukowa Ammah ta tambayeta ta shirya ? Tace "ehh" Toh ga Abu nan zai kaiki gida" Ido ta wara ta dubi inda Abun ke zaune yana jiranta 💖💝BATUUL💖💝 7 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* A hankali take tafiya sabida yadda bugun zuciyanta ke k'aruwa, tana zuwa bakin k'ofa ta juyo ta kalli Farida da pleading eyes ko zata rakata amma sai taga tana d'aga mata hannu da wide smile a fuskanta, Ammah ta sake juyawa ta duba taga ko tana wajen, itama hannu ta d'aga mata tare da mata murmushi, horn dinshi ta sake ji da k'arfi , murda kofan tayi ta fita daga palon har ta k'arasa wajen da motocin gidan ke pake, rasa wanne motan yake ciki tayi sai da taga ya dallo hasken motan daidai inda take tsaye tukunna ta k'arasa amma bata bud'e ba, tsayawa ta sakeyi tana contemplating gaba zata shiga ko baya ? Ranshi ne yayi mugun b'aci ya sake danno mata horn din da k'arfi, kofan dake gaba na gefen driver ta bud'e ta zauna ba tare da tace mishi uffan ba, tada motar yayi sai da sukaje gaban gate kamin mai gadi ya bud'e mishi gate bayan yayi mishi horn ne ya jeho mata tambaya ba tare da ya dubi inda take ba yace "wane anguwane", a hankali cikin sanyin magana tace mishi "Lagos street", tambayanta ya sakeyi " Which side of Lagos street? , "In munje area din zan nuna maka" Baisan Lokacin da ya juyo ya watso mata wani irin kallo ba, a ranshi fadi yake "Is she kidding me, muje zata nunamin, bata san ma hanyan gidansu ba kenan" bai ce mata komai ba ya fita daga gate din gidan ya d'au hanyan anguwan da ta fada mishi, tafiya sukeyi babu wanda ke cewa kowa komai sai k'ira'ar Juhanny dake karanta suratul Qasas da k'arar air conditioner, gaba daya hankalinshi na kan tukin da yake , Batuul kam skirt din jikinta ta riqe da k'arfi har hannunta na yin gumi saboda kwata kwata she is not comfortable, Allah Allah take su k'arasa gida, wani hanyan Lagos street din yabi wanda bata tab'a bi ba har suka isa, suna zuwa ya sake tambayanta " Ta ina gidan yake" juyawa tayi tabi window motar da kallo taga bata san wajen ba, a hankali tace mishi " ba nan bane fa" , wani kallon ya sake watso mata wanda yayi saurin sata sadda kai k'asa , tare da gangarawa gefen titi ya tsaida motan, dago kanta tayi taga ita yake kallo yana jira ta k'ara yi mishi bayanin ina ne idan ba nan ba, ce mishi tayi "Ni ban taba ganin nan ba a anguwanmu, mu koma gidanku sai in nuna maka daga farko inda hanyan gidanmu yake ko kuma in qira Ahmad sai ya d'aukeni a can" sai da ya bari ta gama magana bai ce mata komai ba sannan ya tada motan yaci gaba da tafiya, tsaki yayi tare da duba agogo yaga k'arfe takwas 8 daidai, Sun kusa minti talatin suna yawon neman hanyan gidan basu samu ba, ita dai babu abinda takeyi sai addu'a gashi tana ta k'iran number Ahmda baya d'auka, sai da ya gaji da yawon neman tukunna ya sake tambayanta "For God's sake tell me where your house is" cikin kakkausar murya yayi mata maganan, take jikin ya fara b'ari hawayen dake mak'ale ya k'arasa gangarowa, shiru tayi ta kasa ce mishi komai, magana ya sake yi " Are you this dumb naji Sadiq na cewa kina da ilimi", tsaki ya sake ja yace mata "okay tell me right now cuz you have wasted my time alot", ce mishi tayi "Nifa ban gane hanyan nan da ka bi ba, ba ta hanyan nan muke bi ba mu in zamu....., bai bari ta karasa magana da ta keyi ba yace mata "GET OUT" da k'arfi, kai ta d'ago ta kalleshi dan ta k'ara tabbatarwa da gaske yake, ce mata ya sake yi "I SAID GET OUT", kasa yin komai tayi a lokacin saida ya mik'a hannunshi ya bud'e mata k'ofan sannan ya k'ara ce mata "OUT" ko ledan da Ammah ta bata bata tsaya dauka ba ta bud'e motan ta fita, tana fita ya fizgi motan kaman wanda zai tashi sama A wajen Batuul ta tsaya ba tare da tasan abun yi ba, ga tsoro da ya cika ta, tsoro ma takeji tayi motsi dan gani take wani abun zai kama ta, kuka ta saka a hankali tana k'iran Baba, wayanta ta ciro ko xata ga mis cal din Ahmad amma taga bbu, takaici yasa ta ki kiransa kuma mayar da wayar cikin jaka, tsugunawa tayi a wajen ta kifa kanta a cinya ta ci gaba da kuka dan ita bata ma san inane nan ya kawota ba, gashi anguwan babu commercial vehicles bare tace zata hau d'aya ya kaita gida, shirun da anguwan yayi ne yasa ta d'ago kanta ta sake dubawa ko zata samu mafita, da taga babu yadda zatayi ne ta yanke shawaran kawai ta tashi tayi ta tafiya ko zata samu yadda zatayi, Tunda ya bar wajen hankalinshi yake kanta, tuk'i yake cike da damuwa, "yama za ayi mutum yace baisan hanyan gidansu ba idan ba rainin wayo ba"? Tambayar da ya yiwa kanshi kenan tare da jan tsaki, Tunawa da yayi da fuskanta da yadda hawayen ke gangarowa daga idonta ne yasashi saurin taka brake da k'arfi, mutane ne ke ta yi mishi horn amma bai kulasu ba, parkin gefen titi yyi, lkci daya yace "ta ci sa'ar nasan darajar human" wayanshi ya d'auko ya lalubo number Farida ya k'ira, tana d'auka yace "ke inane anguwansu k'awarki", ce mishi tayi "lah Yaa Abu har yanxu baku k'arasaba" a tsawace yace "Tell me what i asked you and dont question me" ce mishi tayi "Lagos street ne behind Leventis, Yaa Abu wani abune ya faru" bai jira ta k'ara magana ba ya katse wayan, yana ajiye wayan ya juya motan hanyan da ya bar Batuul a wajen, yana isa inda ya bar ta ya duba yaga bata nan sai d'an kwalinta da bata san ya fad'i ba a kasa gun, fitowa yyi ya dauka ya jefa bayan motanshi, a hankali ya dinga bin hanyan, daga can ya hango ta tana tafiya tana share hawayen dake zubowa a idonta, karasawa yayi inda take yayi mata horn, bata juyo ba sai ci gaba da tayi da tafiya da sauri, wani horn din ya sake mata amma bata juyo ba sai ma sauri da ta k'ara sabida tsoro, gabanta yaje ya tsaya da motan, bude mata k'ofa yayi yace mata "GET IN," ko kallonshi bata yi ba taci gaba da tafiya, fitowa shima yayi daga motan yabi bayanta dan ranshi ya soma b'aci, yana isa wajenta ya kama hannunta ya jawota har wajen da yake, fixge hannunta tayi da karfi tace "dole ne sae na shiga motar ka malam" bata ankara ba sae ji tayi sa ka ta cikin motar, yyi banging kofar snn ya zaga ya shiga ya tada motan ya bar wajen, kuka ta dinga yi a motar uwa wata karamar yarinya, kara gudunsa yyi had'e da dukan steering wheel din motan yace "Damn it" sae kace warce ya sato, a ranshi fadi yake "Duk su Ammah ne suka jawo masa yana xaman xaman sa" gnin har lkcn bata fasa kukan da take ba yasa ya bude pidgin din motar ya dauko handkerchief ya miko mata, kin karb'a tayi, wani haushi ya kuma kama sa ya mayar da handki din, wani gida suka kusa wucewa tayi sauri tace mishi ga gidanmu nan, brake ya taka yayi horn a gate din yana jira a bud'e, bata jira an bud'e ba ta fita da sauri ta shige gidansu, bin ta da kallo yyi cike da bacin rae, yafi minti goma a k'ofar gidan ba tare da ya tafi ba, idonshi ya fad'a kan ledan dake ajiye, d'auka yayi ya fito yayi sallama da mai gadin ya mik'a mishi yace mishi na Batuul ne, k'iran sunanta da yayi ne ya sashi jin wani iri ya juya ya koma mota ya tada ya tafi. 💖💝BATUUL💖💝 8 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Tana shiga gida hanyan garden tayi ta wanke fuskanta da kyau dan kar a ce tayi kuka, da sallama ta shigo palon, ba kowa sai Aunty da Aabid a hannunta tana bashi madara, karasawa tayi cikin palon zata hau bene bayan ta cewa Aunty ta dawo taji Aunty tace "Batuul zo nan, mey ya sami idonki ya canja kala, kuka kikayi" da sauri ta ce " a ah Aunty kaina ne yake ciwo tun da naje, nace zan dawo ma Ammah tace in bari sai da yamma a dawo dani, tana gama maganan ta hau stairs da gudu, da ido Aunty ta bita ba wai dan ta yadda da abunda ta fada din ba, tana kaiwa last stair case din taji sallaman mai gadinsu ya shigo da leda wai a bawa Batuul inji mutumin da ya kawota, Aunty ce tace ya ajiye, yana ajiyewa ya tafi abunshi, Batuul kam tsayawa tayi tana kallonshi har saida ya ajiye ya fita tukunna ta tab'e bakinta ta tafi , dan ita ta ma manta gaba daya da batun abunda Ammah ta bata, dakin k'annenta ta bud'e ta lek'a dan a cike take da Ahmad da yaqi picking call dinta kuma bai k'irata ba bare yazo d'aukanta , tana budewa taga dak'in ba kowa, an tattarashi tsaf sai k'anshi da sanyi yake yi kamar ba shine a hargitse ba d'azu, rufewa tayi ranta a b'ace dan taso ta sameshi ya fad'a mata dalilinshi na qin d'aukan wayan, ďakinta ta k'arasa ta bude, tana shiga ta tarar dashi kamar yadda ta fita ta bari sai d'an gyara da aka sakeyi, kayan jikinta ta cire ta shiga toilet, bath tub ta shiga ta cika shi da ruwan dumi, tana shiga ta dinga kukan da bata san dalilin yinshi ba, sai da tayi mai isanta sannan ta fito daga daga cikin bath tub din ta nufi sink tayi alwala,fitowa tayi daga toilet din, gaban mirror taje ta shafa mai, ta fesa turare masu sanyin k'anshi, da ta gama ta k'arasa gaban closet dinta ta bud'e ta dauko kayan bacci, gown ne na sponge bob iya gwiwa ta saka, ta saka hula blue sannan ta shimfid'a sallaya ta hau ta tada Sallah Isha, tana idarwa ta hau makeken gadonta ta kwanta, remote din AC ta d'auka ta k'ure to the highest volume, duvet dinta ta janyo ta rufe duka jikinta dashi, wayanta taji yana ringing, kamar baza ta d'auka ba ta janyo shi da k'afa ta k'ara a kunnenta , a hankali ta amsa da "Hello" daga d'aya bangaren aka amsa da "sweetheart i was worried about you, inata trying number ki it wasnt going,kun isa gida lafiya", a hankali Batuul tace Farida ina gida, jin muryan Batuul yayi k'asa ya sata tambayanta "Batuul are you okay", a hankali Batuul ta ce " yeah am okay" Ya Ammah, kice mata na gode....", katseta Farida tayi ta ce mata "Yaa Abu ya k'irani wai in fada mishi inda gidanku yake , Baatul tace mata " eh ina ta yi mishi describing ne bai gane ba shine nace ya k'iraki ya tambayeki amma ai tun dazu mukaxo, har ma na kwanta, ce mata ta sakeyi "bari in barki sai da safe tunda har kin kwanta" jikin ta sanyaye ta ajiye wayan dan tasan ba lafiya bestyn ta take ba saboda ko zatayiwa ko shiru bata yiwa Farida, tasan mayb wani abun ya haďa ta da Yaa Abu Tuki yake yana tsaki kwata kwata fitar da yayi niyyan ma fasa ta yayi, wayanshi ne yayi ringing, duba mai kiran yayi sannan ya jona wayan da speaker motan kamin ya d'auka, yana ďauka yace " said yanxu kika ga daman k'irana kenan" , daga daya bangaren cewa akayi cikin siririyar murya da kanaji kasan an lank'washeta " Bae kaima kasan ba da gangan naqi kiranka ba, kasan muna ta ibada ne kuma muna tare da family so...." bai bari ta k'arashe maganan ba ya katseta da cewa " Yasu Mummy, yaushe ne dawowanku" , "su Mum na lafiya, next week zamudawo ai zakazo d'aukanmu ko, i even have something for you, ďazu mun fita dasu Mum munje bin Dawood naga wani turare ance shi ne latest of d month,na siyamaka dan har su prince Hamdan ma shi ne nasu for this month, bai bari ta karasa maganan ba ya ce mata " okay yanxu ina driving ne , i will get back to you when i reach home", a sanyaye tace "Aii bae take care" ta katse wayan, kullum sukayi waya sai yayi mata hali, amma babu komai ai Mum dinta tace mata indai ta aureshi komai zaiyi normal, said yadda tayi dashi, shima har yazo ya fita sonshi,ayyanawa tayi a ranta ai tunda tana da kyauzatayi anything possible ya sota fiye da komai, tunanin hakan ne ya sata wani daria mai sauti , y'an dakin hotel din ne suka juyo suna tambayanta mey take yiwa wannan dariyan, murmushi ta sakeyi ta ce musu "Tunanin yadda zanyi da Abutturab nakeyi da yadda zai so ni in munyi aure" ta tab'a matar dake gefenta tace "Yaa zee wlhy ina sonshi, baza ki gane bane, wacce aka k'ira da Yaa zee dince ta ture mata hannu daga jikinta tace "rabu dani dallah, anyi anyi ki rabu da yaron nan kink'i, ni banga ma wani abu da yake dashi ba in banda tsawo da ya ďebo kamar isha da girman kai kaman wani basarake, ga manyan mutane nan na sonki amma kin nacewa k'aramin yaro da ya baki y'an shekaru, in banda wulak'antaki babu abinda yakeyi, dubi fa ko yanxu da kika k'irashi ce miki yayi sai yanxu kika ga daman k'iranshi, shi mesa bazai kirakin ba ďan rainin wayo kawai" taja tsaki ta ci gaba da danna wayarta, yarinyar ta sake cewa "Yaa Zee baza ki gane bane, da kinsan wahalan da nasha kamin ya fara kulani ,ke da kanki zakice inci gaba da hak'uri saboda in inyi fulfilling dream dina in aureshi , kuma ai ina sonshi, tun first day dina a school nake bin shi yana shuning dina har na samu yana kulani yanxu ai bazanyi missing wannan opportunity ba, yanxu kawai jira nake muyi aure komai zaiyi daidai yadda muke so , Yaa Zee tace mata" ke kika sani, Ni ki rabani da labarin wannan sarkin tsawon naki," taci gaba da abinda take, tashi yarinyar tayi ta fita daga ďakin tana dariya Aunty ce ta tura Fa'iza ta duba mata ko Batuul idonta biyu, da taje sai da ta lek'a ,hasken da ta ganine ya sata shiga , a hankali tace mata, "Yaa Batuul Aunty tana qiranki, bata tashi ba tacewa Fa'iza "gani nan zuwa" Fa'iza na fita ta tashi tabi bayanta after ta duba fuskanta a mirror taga ya ďan zama normal , tana sauk'a k'asa taga duka yan gidan a palo kowa ya baje ledoji a gabanshi sai hira sukeyi suna dariya, Baba ne ya fara hangota yayi mata alama da tazo wajenshi, kusa dashi taje ta zauna , Ahmad ne ya kalleta ta doka mata harara, dariya yayi ya ďauke kanshi yaci gaba da abinda yakeyi, Baba ne yace mata "Da zamuje mu ďaukeki da muka fita dan Ahmad ya ce min ya bar wayanshi a gida, sai da mukayi waya da Aunty ta ce mana kun dawo , a hankali tace mishi "Ehh Baa, inata kiran shi baya picking shine kawai Ammah tace a dawo dani, tun dazu ma na dawo", tashi tayi ta koma wajen Aunty tace mata "Aunty gani", "kinci abinci ne da kika shiga kika kwanta, kuma da kikace kanki na ciwo wane maganin kikasha", kamar zatayi kuka tacewa Aunty "Naci abinci har na sha panadol, bacci nakeson yi yanxu", da ta tashi tafiya ne Aunty ta nuna mata ledan da mai gadi ya shigo dashi yace nata ne, Faiza tacewa ta hawo mata dashi ta k'arasa sama ta kwanta, binta kawai Aunty tayi da kallo dan ta san duk bacin ranta baya nunawa amma yau wani abun ya sameta, Yana xuwa gida, ta back door ya shiga dan baya son had'uwa da kowa saboda ranshi ya gama b'aci, ďakinshi ya nufa ya buďe ya shige, toilet ya shiga ya watsa ruwa yayi alwala ya fito, pjs dinsa ya saka sannan ya shimfiďa abun sallah ya hau ,dan yaso yayi a shehuri idan yaje amma saboda yarinyar nan bai samu yayi ba sai yanxu wajen after 9, tada sallahn yayi , bayan ya idar ya gama azkar ďinshi ya hau gadonshi tare da janyo Mac book dinshi yana duba aikin da zaiyi nan da kwana huďu, yana gamawa ya kashe wutan ďakin ya kwanta 💖💝BATUUL💖💝 9 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* K'arfe biyar 5:00 daidai adhan din sallah Asuba ya fara dai dai lokacin Abutturab ya farka daga bacci, addu'ar tashi daga bacci yayi, k'afafuwanshi ya sauk'ar daga kan gadon a hankali, tashi yayi ya isa inda comfy fararen towels dinsa ke rataye yayi, guda ďaya ya janyo, kayan baccin dake jikinshi ya cire sannan ya ďaura towel din ya shiga toilet, brush yayi ya watsa ruwa sannnan ya haďa da alwala ya fito, closet ďinshi ya buďe ya ciro farar jallabiya ya saka bayan ya goge ruwan jikinshi da towel, gaban mirror ya koma ya fesa turaren jéan pául Gaultiér ya k'ara da Hugo sai Arabian oud ya shafa, abin sallah ya shimfiďa yayi nafilfili, bayan ya idar ya karanta suratul Mu'minun cikin murya mai daďi, tashi yayi ya fita masallacin dake manne a jikin gidan daga waje, yana k'arasa yayi raka'atul fajr sannan ya zauna jiran Ladan ya tada sallah su fara, k'arfe 5:40 ladan ya tayar suka fara sallah, suna idar da sallah bayan y'an azkar suka fito daga masallacin, Abui da Sadiq ya hango ya k'arasa inda suke, "Nda wattu" yacewa Abui tare da mik'a mishi hannu, Abui ne ya amsa mishi da kélewa sélai, Sadiq ne shima ya mik'o wa Abutturab hannu suka gaisa, suna tafiya Abui ya k'ira sunan Abutturab, "yaushe ne tafiyanka" Abutturab ya amsa da "Na so in tafi on monday but naga i have things to cover before meeting dina da minister on tuesday, so i have decided to leave tomorrow monday", Abui yace "okay sai kayi rescheduling flight dinka to gobe, kuma ka fad'awa Ammah dan bata sani ba, mu sai next week dawwanmu inaga" yace "okay Abui" sannan suka k'arasa cikin gida kowa yayi ďakinshi Hasken ranar da ya hudo window ďakinta ne ya sata buďe idonta a hankali, ranan da ta gani ne ya sa ta wara y'an madaidaitan idonta ta dubi agogon dake kan bed side drawer taga 6:30, da tsalle ta tashi daga kan gadon, gashinta mai tsayi da shek'i da ya baje tana bacci ta kama ta haďe su in a messy bun, toilet ta shiga ta kuskure bakinta da Listerine mouth wash tayi maza tayi alwala ta fito, sallah ta tada , bayan ta idar tayi azkar ta fito daga d'akinta ta bud'e ďakinsu Ahmad, fridge din ďakinsu ta buďe ta ďauko ruwan sanyi ta shiga kwara musu, a firgice kowannensu ya tashi suna mitsitsika ido, Sa'eed ne yace mata "haba Yaa Batuul yanxu kuma mey mukayi kika tashemu da ruwan sanyi", dukkansu ransu a b'ace suna kallonta suna jiran suji mey sukayi da ta katse musu bacci, "Y'an rainin wayo kunga ban fito sallah ba shine babu wanda yayi knocking min k'ofa, ai tunda baku ganni nazo gaida Baa ba sai kuzo ku dubani, amma kowanne da yaje masallaci dawowa yayi yaci gaba da baccinshi, sai yanxu nayi sallah asuba, yan rainin wayo kawai, Khalil ne yace " toh mu mun san baki tashi bane, kuma ai Aunty ma munsan zata tasheki" Harara ta watsa mishi, Ahmad kam ko uffan baice ba dan ya san harda haushin jiya yasa ta zuwa da watsa musu ruwan sanyi suna bacci, Mus'ab ma baice komai ba, tana faďan dalilinta na watsa musu ruwa yaja bargonshi ya kwanta dan inda sabo sun saba da masifanta, saida ta gama faďanta sannan ta juya tare da banko musu k'ofa ta fita, k'asa ta sauko taga babu kowa ta koma d'akinta 11:00 ta sauko cikin abayar Al layl tayi kyau sosai, fuskanta ba komai sai kwalli da ta saka, duk y'an gidan na parlour, Su Ahmad ne suka bita da kallo ransu a b'acen abinda tayi musu ďazu,itama palon taje bayan ta gaida Baba da Aunty ta sami waje ta zauna, Baba ne yace mata "Batuul tafiyanmu gobe ne dan haka yau zakuje ku gaida su Yayya da kowa da kowa, meeting dina tuesday so dole mu tafi gobe, kuma kinga graduation ďinki saura two weeks, sai ki fara shirye shirye ko" tace "yo Baa", Aunty ce tace mata "kan naki ya dena ciwon", ita ta manta ma gaba ďaya da tayi ciwon kan k'arya, tunowa tayi da abinda ya sata yin k'arya, ďan k'aramin tsaki tayi daga ciki, a ranta tace wannan mugu ne dagaske shiyasa Farida bata sonshi tafi son Sadiq, da sauri tacewa Aunty, " eh da nayi bacci na tashi ya dena", "sai kije kici abinci ki fito mu tafi dan muna da wajen zuwa dayawa a yau" toh tace sannan ta nufi dinning ta bubbuďe food flaskses da kwanunkan dake kan dinning ďin, plate ta ďauka ta saka pancake guda da ďaya da strawberry syrup sannan ta ďauki Fanta ta zauna ta ci a hankali har ta gama ta dawo palon tace ta gama, Aunty ce tacewa yaran toh ku tashi mu tafi Baa Liman na jiranmu shi zai kaimu, dukkansu sukayiwa Baba sallama suka fita, wata range rover 2011 suka dosa dukkansu, Baa Liman ne ya buďe kofan driver ya shiga, motan duk ya hargitse da surutu kowa yana faďin ga wak'an da yakeso a sa, daga k'arshe ne Batuul tace a saka musu wak'okin Wael Jassar, ana sawa duk suka fara bin wak'okin shi na farko a album din 7aareg damohom, motar cike da hayaniya ba a jin abinda wani ke faďi har suka isa gaban wani gate sukayi horn, mai gadi ne ya buďe musu su ka shiga, basu bari an gama parking ba suka buďe k'ofofin motar suka fito, da gudu suka shiga gidan suna faďin *yayya ishena*, *yayya ishena* Yayya munzo, Yayya munzo)da kanuri, wani ďaki suka buďe suka shiga, ďan madaidacin parlour ne mai kyau sai k'anshi turaren wuta yake da sanyi, suna shiga suka nufi wajen wata tsohuwa fara sol, dukda ta tsufa amma kyanta na nan, anyi mata kitson gaba da ya zubo daga gefe, na bayan kuma ta tufke shi, murmushi tsohuwar tayi ta rungeme yaran, Batuul na shigowa taje wajenta ta ture yaran daga jikin tsohuwar tare da cewa "Ku ďaga min takwara kar ku ballamin ita, tunda kuma bana yiwa takwarorinku haka, rungume tsohuwar tayi sannan tace mata Yayya *tussuna nya rukéi*, (na daďe ban ganki ba, nayi missing ďinki), Yayya tace mata " *nda rui sha, jirem géi*(dubeta kamar dagaske ban yadda ba), Aunty ce ta k'araso ďakin ta zauna sannan suka gaisa da Yayya, cikin girmamawa suka gaisa sannan yayya ta k'ira daya daga cikin masu aikinta, "ki kawo musu abinci da kayan sha ki jera a kan dinning,cikin kanuri ta faďi maganan don bata jin Hausa, sunajin abinda yayya ta faďa kowa ya fara faďan choice dinshi na abinda zaici, duk saida aka kawo musu abinda sukace sunaso aka jera musu, a gidan suka wuni har dare k'arfe goman dare Baba ya iso gidan yayya shima, bayan sun gaisa da yayya sun ďan tab'a hira yace su tashi su tafi dan gobe flight dinsu eleven ne,tsaraba dayawa yayya ta haďa musu ta saka masu aikinta su kai musu mota, bayan kowa ya gama shirinshi zasu fita daga ďakin yayya ta k'ira Baba ckin ďakinta, zama tayi a kan gado shi kuma ya zauna a k'asa kanshi a duke, magana ta fara kamar haka "Batuul tace min ta gama sashen karatun nan nata amma zataci gaba, kuma har waje naji tana cewa zata, toh ni bance kar taci gaba ba amma ban yadda har waje ba, in kuma har wajen zaka fita da ita toh lallai saida mijinta , haba wane karatu ne haka da tunda aka haifi mutum yakeyinshi bai k'are ba, yarinya shekara sha shida zata shiga na bakwai amma babu abinda takeyi sai boko, toh inma uwarta ke zugaku da kai da Batuul ďin ni bazan ďauka ba, bazan yadda yarinya tayi ta girma babu aure ba, ai uwartata ma abinda ya sa na k'i ta kenan lokacin aurenku wai tana boko, toh mutane da dama ma ai sunyi bokon a gidan mazajensu, dan haka Batuul baza ta ci gaba ba sai tayi aure", duk maganan nan da tayi cikin kanuri tayishi, tunda ta fara magana Baba bai ďago ba sai da ta gama, a sanyaye ya ďago kanshi yace mata "In sha Allah yadda kikeso za ayi Yayya, nima ďin bana son fitanta waje karatu babu muharrami, dan haka zan duba yadda za ayi", Yayya tace "yawwa gara a duba , Allah yayi muku albarka, toh yaushe ne tafiyan naku gobe" yace "11" tace Allah ya kaimu ya kiyaye hanya sannan ta fito yana biye da ita a baya har suka k'araso parking lot, yaran nata tsokananta har Babansu ya tayar da motan tana ďaga musu hannu har suka fita daga gate ďin 💖💝BATUUL💖💝 10 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Sweat pant blue ke Jikinshi da riga bak'a yana dadanna Macbook dinshi, tea ne a flask daga gefenshi idan yayi aikin sai ya ďan sha kaďan, wayanshi ne yayi k'ara ya ďauka yaga Amma keh k'iranshi, rusuna yayi yace "Hello Ammah", daga ďaya bangaren Ammah ce ta amsa da " ina falon sama, kazo maza ina jiranka", tunani ya fara yi akan dalilin wannan k'ira da take mishi dan tun daga muryanta ya san ba lafiya ba, maganan Ammah ya sakeji tana cewa "banji ka amsa ba", da sauri yace "Ammah ina zuwa" ya katse wayar, matsar da Macbook ďin yayi gefe ya tashi ya fita daga ďakin, hanyar falon sama yabi har ya isa, yana zuwa yaga Abui da Ammah a zaune tare a kujera ďaya, k'arasawa yayi ya nemi waje ya zauna akan tattausan rug ďin dake shimfiďe , a kusa da Abui dab ya zauna daga k'asa, kanshi dake duk'e ya ďago ya gaida su a tare, Abui ne ya fara amsa mishi sannan Ammah, bayan y'an seconds Abui yayi gyaran murya tare da k'iran sunan shi, "Abutturab magana zamuyi dakai kamar kullum akan dai maganan kayi aure ne, mun gaji da zaman ka haka", Ammah ce tayi sauri ta karashe maganan da cewa "bazan yadda da tafiyanka waje babu mata ba, wane aiki ne zakaje ka k'ara banda wanda kayi musu ba, yanxu Abui ke cemin gobe zaka tafi ,kuma kana gama aikin ne zasu tura ka waje, toh ni bazan yadda ba, kayi aurenka in yaso kaje kayi shekara goma a can banida damuwa", Abui ne ya tareta da cewa "a ah ba shekara goma ba dai, abi komai a hankali, yanxu kai Abutturab kamin ka gama contract dinnan har su turaku waje muna so ka fiddo da mata ayi muku aure, mutuncinka ma zaifi k'aruwa a idon mutane, within two weeks kayi mana introducing wacce kake so, inma babu wacce kuka daidaita zamu samo maka a family, ga cousins ďinka ko a cikinsu ka duba, in akwai wacce tayi maka fine, in kuma babu sai ka nemo da kanka, Ammah ce tace "ai ni Nafison ma mu nemo mishin dan da alamun bashida niyya", Abui yace "Aure is a life time journey, he should chose his own choice dan kada a samu matsala, Allah yayi maka albarka", baice komai ba har saida su Ammah suka gama maganan da zasuyi sannan ya ďago kanshi yace musu "In sha Allah zainyi Ammah, but inaso a ďan k'aramin lokaci, two weeks ďinnan yayi min kaďan, a k'aramin ko da one month ne, in sha Allah by then i will be done with duk abunda zanyi, sai ayi introduction ďin" Ammah ce ta sake ce mishi "Aliyu ban yadda ba, two weeks ďinnan da na faďa shi kenan, tukunna ma y'ar gidan waye kake cewa za ayi introduction ďin da ita", sunanshi da yaji ta k'ira ne yasashi saurin ďago kanshi, don ya daďe baiji ta k'irashi ko da Abutturab ba amma yau gaba ďaya Aliyu ta ambata, a hankali yace "y'ar gidan perm sect ce Engr Abba Muhammad Jidda", Abui ne yace "Masha Allah, ai Engr abokina ne, mutumin kirki ne sosai, ba komai kaje in mun koma Abuja sai kuyi magana da yarinyar akan zaka turo, tashi kaje Allah ya maka albarka" Amin yace sannan yayi musu godiya ya tafi, Ammah dai bata so haďin nan da ďanta ya samo ba, dukda tana y'ar Tchad amma bata so ďanta ya auri shuwa, amma haka dai ta hak'ura ba dan tana so ba, gara yayi auren da ya zauna babu mata, ci gaba sukayi da hiran Abutturab ďin da sauran y'ay'ansu bayan ya tafi Suna isa gida bayan sun shiga ciki dukkansu suka zube a palon, Baba ne da ya shigo daga k'arshe yace kowa ya shiga ya kwanta gobe flight ďinsu sha ďaya ne dan haka kowa ya shirya da wuri, mik'ewa kowa yayi ya tafi makwancinshi ya shirya yin bacci, Batuul na shiga ďaki ta cire kayan dake jikinta ta ďaura towel zata shiga toilet, fridge ďinta ta buďe zata sha Fanta taga ya k'are, wayanta dake ajiye gaban mirror ta ďauka ta nufi kan gado ta zauna sannan tayi dialing number Janet, tana ďauka tace "Janet ki kawo min fanta ďakina , na fridge ďina ya k'are, "Janet ta amsa da to anti za a kawo miki wani abu dinne bayan Fanta", Batuul tace No i dont need anything else, am okay" sannan ta katse wayan ta ajiye ta shiga toilet, warm shower bath tayi ta fito daga toilet ďin, tana fitowa akayi knocking k'ofar ďakinta karasawa tayi ta buďe, Janet ce ta shigo da square serving tray na ceramic ďauke da Fanta akai, akan table ďin ďakin ta ajiye ta juya zata fita Batuul ta k'ira sunanta "Janet ku shirya da wuri gobe zamu koma,ki faďawa Fa'iza da Aunty Tabawa, karku sake delaying ďinmu kamar lokacin da zamu zo, "Toh anti zan fada musu", "kuma ba sai kunyi breakfast dayawa ba,amma kije wajen Aunty ta faďa miki abinda za ayi goben", da toh ta amsa sannan ta fita, tana fita Baatul ta shirya cikin kayan baccinta na Lulu kitty purple, ta haďe gashinta cikin hula dark purple ta gama shafe shafenta ta hau kan gado, Laptop dinta na Apple ta ďauko ta ďanyi danne dannenta sannan ta kashe ta mayar kan side drawer, wayanta ta ciro a caji, kamar dama jira ake ta ďauki wayan ya fara ringing, ganin mai k'iran ya sa wani wide smile shimfiďuwa a fuskanta, dimple ďinta sai da suka lob'a deeply, wayan ta saka a kunnenta tare da tsuke fuska kamar ba ita ke murmushi ba yanxu ta Kuma yi shiru taqi magana, daga ďaya bangaren aka ce "shikenan since you wont talk, i will end d call, da sauri tace "Affaaannn" da k'arfi ta k'ira sunan har tana jiyo dariyanshi daga ďaya b'angaren, "woh lady so kike ki min bursting ear drums ko ko ya", sake k'iran shi tayi da Affanu, "ta yaya ma akayi kika zama friend ďita ya faďa yana dariya", "I know you love me" Batuul ta faďa mishi, ce mata yayi "waya faďa miki i love you, ai d moment you left for airport na manta da momeries and friendship ďinmu", "face ďinta tayi kalan tausayi dashi ta zumb'uro baki kamar yana ganinta tace mishi "ka manta dani, nayi fushi ma tunda ka manta ni" murya ta fara yi kamar zatayi kuka, da sauri ya fara ce mata "No no no Lulu, kar kiyi kuka mana, i didnt mean to hurt, kema ai kinsan you are my potential treasure, ai nima sai ki sani kukan" ya faďa muryanshi na rawa, kyalkyalewa ta kuma yi da dariya, ce mata yayi "dariya ma na baki ko, am offended shikenan ma goodnight", da sauri ta tare shi, "wait wait pls, dagaske dariya ka bani how you reacted, so you care, intersting", dukkansu biyu a tare suka sa dariya, ce mata ya sakeyi "Amish you dearest", a hankali itama tace mishi "Amishd you too", "so when y'all coming back", Affan ya tambaya, "Gobe ina Abuja by now", da sauri Affan ya tambayeta "Dagske Lulu gobe zaku dawo, baby na fa", dariya Batuul tasa sannan tace "masu baby, toh ba gobe zata dawo ba sai nextweek, hope kana kula min da ita da kyau, jiya ma i was with her, ce mata Affan yayi "i got to call her now in roqeta su dawo before next week dan i cant wait that long" Da dariya Batuul tace mishi "Aii best friend, good night", da haka suka katse k'iran, suna gamawa tayi adduan bacci ta shafe jikinta dashi, taje ta shafe duka k'annenta har way'anda ke kwana a ďakin Aunty, sannan ta tofe duka angles ďin gidan , ta kashe bedside Lamp ďinta ta kwanta Bayan ya koma ďakinshi ne yaji komai baya mishi daďi, key ďin mota ya ďauka ya fita shehuri ba tare da ya cewa komai ba, kai tsaye dogarai suke buďe mishi k'ofa dan sanin matsayinshi da sukayi a fada, chamber Massa ya wuce kai tsaye ya shiga, Massa ya tadda kwance a makeken gadonshi na sarauta yana waya kuma da alama yana jin daďin wayan da yake, waje Abutturab ya nema ya zauna akan ďaya daga cikin royal chairs ďin ďakin, ganin wayan da Massa keyi bazai k'are bane ya sashi tashi ya fizge wayan ya katse, "dan wulak'anci na kai minti goma ina ďakin nan, amma kakeyi kamar ba kasan ina nan ba ka zauna kana ta waya kana k'yalkyala dariya, ni banga ma abin yiwa dariya ba a waya da budurwa,mtsewww", tsayawa Massa yayi yana kallonshi har sai da ya gama yace mishi "mik'o min wayata in ka gama" mik'a mishi wayan yayi ya nemi waje akan gadon ya zauna ya dafe kanshi, ganin da Massa yayi abokinshi ba wasa yakeyi ba yasa shi zama kusa da shi dan ya san ba komai ke sashi damuwa ba, komai girman abu yana danne zuciyanshi, dafashi yayi yace "Man whats wrong, you dont look yourself, you seem to be upset, hope dai lafiya, tell me whats wrong am dead worried right now", ajiyar zuciya yayi yace "Su Abui ne suka ce that sun bani two weeks i should introduce to them the girl i would marry , ko kuma su nema min da kansu, wai bazan tafi project ďina ba mata ba" kuma you know i have no one at hand da zance musu gata am ready to marry, cikin jimamin abinda ke shirin faruwa da abokinshi yace "Man toh baga Ajiddeh ba, you guys go along well dan naga babu wacce ke samun attention ďinka kamar ita kuma ma she is beautiful and everything" wani kallo Abutturab ya watsa wa Massa, "wa yace maka dan kyanta nake kulata, yeah i know there is this ounce of affection i have towards her but bai kai har ince zan aureta ba, su Abui should understand su k'aramin lokaci, i need time, bana son yin mata biyu, so kaga i should be given time dan in samu right choice ďina" k'arashe maganan yayi tare da nannauyan ajiyan zuciya" Massa ne yace mishi kawai kayi introducing Ajiddeh tunda tana sonka you can make her all you like, zatayi duk abinda kake so, Ko Shehu bazaiyi siding damu ba saboda shima damuwanshi kenan a kanmu, sai dai ma ya ce a k'ara dani, Man kawai muyi addu'an abinda yafi alheri", cigaba sukayi da hirar neman mafita daga k'arshe kawai suka yanke shawaran ya auri Ajiddeh tunda ita kaďai ce option ďin dan basu san wacce su Abui ďin zasu zab'a mishin ba, k'arfe goman dare ya mik'e yace da Massa zai koma dan yana da flight gobe by 11:00, sun fito waje Massa na rakashi inda yayi parking mota Massa ke tambayanshi, "Man ya akayi ne baka zo ba jiya inata jiranka", tambayan ne ya sashi tunawa da duk abinda ya faru tsakaninshi da Batuul, ďan k'aramin tsaki yayi daga ciki yacewa Massa "gajiya nayi", dariya Massa yayi yana ďan tab'a kafadarshi yace "ango tun bakayi auren ba har ka fara gajiya, toh in kayi auren kuma bazamu na ganinka ba kenan", Abutturab bai ce mishi komai ba ya buďe motarshi ya shige tare da ce mishi "sai munyi waya, ni zan wuce", Allah ya tsare hanya Massa yaayiwa Abutturab sannan sukayi sallama Bayan sallah asuba babu wanda ya koma bacci, kowa shirin tafiya ya farayi, sai hayaniya akeyi a gidan, kowa ya tashi a gidan banda k'ananan k'arshe, Janet ce tayi knocking k'ofan, bayan an mata izinin shigowa ta shigo ďakin, tarar da Aunty da Batuul a ďakin tayi,Batuul na shiryawa Aunty kayanta da zata tafi dasu a cikin jaka, Aunty ce tace mata yarannan fa har yanxu basu tashi ba Janet, maza je ki k'irawo Fa'iza kuzo kuyi musu wanka dan 8 ya wuce, da toh ta amsawa Aunty sannan ta fita k'irawo Fa'iza dan suyi aikin da aka sasu, ďaya nayin wankan ďaya kuma na shafa musu mai da sa musu kaya, Batuul na gamawa tacewa Aunty "zanje in shirya sannan ta fita daga ďakin Aunty ta isa d'akinta, wanka tayi sannan ta fito ta shirya cikin atampa exclusive green da pattern ďin yellow da bak'i, ďinkin yayi mata kyau sosai, skirt ne with peplum blouse mai three quarter hannu, ba a sa komai a jikin rigar ba sai patterns ďin atamfar aka yi mata aiki dashi, ďan kunne kawai ta saka bata sa sark'a ba, agogon gucci ta ďauka ta mak'ala a hannunta, babu wani kwalliya da tayi sai kwalli kawai da ta saka a idonta, duk da ba tsayine da ita ba, bata saka takalmi mai tudu sai slippers din versace baqi da ta saka, luggage ďin kayanta ta jawo ta ajiye bakin k'ofa sannan ta ďauko k'aramin bak'in gyale ta ajiye a kafaďarta, fitowa tayi ta sauko k'asa taga kowa ya shirya cikin kayan alfarma suna breakfast, shiyasa ma bata fara saka abaya ba dan tasan Baba sai yayi mata maganan abayar, k'arasawa tayi itama ta janyo kujera ta zauna , Aunty da Baba ta gaida a tare suka amsa mata sannan duka k'annenta suka gaisheta suma, Bismillah tayi ta fara cin abincin itama, a nutse suka gama breakfast ,tara da rabi dai dai aka fara fita da kayansu, manyan mazan kowa da hand luggage ďinshi a hannu, na Aunty, Batuul dasu Hafix kuma yana hannun su Janet, Baba ne shima ya sauk'o daga bene rik'e da nashi, Batuul na hango shi da sauri taje ta karb'a ta k'arasa dashi k'asa ta bawa driver su fita dashi, Kanta ya shafa Yace ya gode , Baba na k'arasowa duk suka tashi suka fita suka nufi inda motocin gidan ke pake, Baa Liman ne da Sunday driver zasu kaisu airport, Batuul da Ahmad, Sa'eed, Khalil, Mus'ab mota ďaya suka shiga while Baba, Aunty, Yusra, Mahir, Hafix da Aabid na mota ďaya, sai da sukayi addu'an fita daga gida da ayatul kursiyu kamin drivers ďin su fita daga gidan Hanyan Maiduguri international airport suka bi, goma da rabi suka isa, ana shiga cikin airport ďin heartbeat ďin Batuul ya k'aru idonta ya fara tara hawaye, addu'a ta soma har taji ya ďan ragu, bayan sun shiga har ciki sun sauk'a ta isa wajen Aunty ta ce mata, "Aunty tunda muka zo Maiduguri heartbeat ďina baya running at a normal pace, yanxu ma muna shigowa airport naji ya k'aru sosai", Aunty ce ta dube ta tuna da ranan da ta dawo idanunta sunyi ja, ce mata tayi "baki da gaskiya shi yasa yak'e karuwa, dariya sosai Batuul tayi sannan tace "kai Aunty, wane rashin gaskiya zanyi har heartbeat ďina ya rik'a karuwa, ni dai babu abinda nayi", ta juya ta tafi, binta Aunty tayi da ido dan itama ta tab'a shiga yanayi irin na Batuul na k'aruwan bugun zuciya, murmushi tayi ta girgiza kai sannan ta tattara kan yaran sukayi departures waiting room suna jira a k'ira su in jirgi ya shirya 💖💝BATUUL💖💝 10 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Sweat pant blue ke Jikinshi da riga bak'a yana dadanna Macbook dinshi, tea ne a flask daga gefenshi idan yayi aikin sai ya ďan sha kaďan, wayanshi ne yayi k'ara ya ďauka yaga Amma keh k'iranshi, rusuna yayi yace "Hello Ammah", daga ďaya bangaren Ammah ce ta amsa da " ina falon sama, kazo maza ina jiranka", tunani ya fara yi akan dalilin wannan k'ira da take mishi dan tun daga muryanta ya san ba lafiya ba, maganan Ammah ya sakeji tana cewa "banji ka amsa ba", da sauri yace "Ammah ina zuwa" ya katse wayar, matsar da Macbook ďin yayi gefe ya tashi ya fita daga ďakin, hanyar falon sama yabi har ya isa, yana zuwa yaga Abui da Ammah a zaune tare a kujera ďaya, k'arasawa yayi ya nemi waje ya zauna akan tattausan rug ďin dake shimfiďe , a kusa da Abui dab ya zauna daga k'asa, kanshi dake duk'e ya ďago ya gaida su a tare, Abui ne ya fara amsa mishi sannan Ammah, bayan y'an seconds Abui yayi gyaran murya tare da k'iran sunan shi, "Abutturab magana zamuyi dakai kamar kullum akan dai maganan kayi aure ne, mun gaji da zaman ka haka", Ammah ce tayi sauri ta karashe maganan da cewa "bazan yadda da tafiyanka waje babu mata ba, wane aiki ne zakaje ka k'ara banda wanda kayi musu ba, yanxu Abui ke cemin gobe zaka tafi ,kuma kana gama aikin ne zasu tura ka waje, toh ni bazan yadda ba, kayi aurenka in yaso kaje kayi shekara goma a can banida damuwa", Abui ne ya tareta da cewa "a ah ba shekara goma ba dai, abi komai a hankali, yanxu kai Abutturab kamin ka gama contract dinnan har su turaku waje muna so ka fiddo da mata ayi muku aure, mutuncinka ma zaifi k'aruwa a idon mutane, within two weeks kayi mana introducing wacce kake so, inma babu wacce kuka daidaita zamu samo maka a family, ga cousins ďinka ko a cikinsu ka duba, in akwai wacce tayi maka fine, in kuma babu sai ka nemo da kanka, Ammah ce tace "ai ni Nafison ma mu nemo mishin dan da alamun bashida niyya", Abui yace "Aure is a life time journey, he should chose his own choice dan kada a samu matsala, Allah yayi maka albarka", baice komai ba har saida su Ammah suka gama maganan da zasuyi sannan ya ďago kanshi yace musu "In sha Allah zainyi Ammah, but inaso a ďan k'aramin lokaci, two weeks ďinnan yayi min kaďan, a k'aramin ko da one month ne, in sha Allah by then i will be done with duk abunda zanyi, sai ayi introduction ďin" Ammah ce ta sake ce mishi "Aliyu ban yadda ba, two weeks ďinnan da na faďa shi kenan, tukunna ma y'ar gidan waye kake cewa za ayi introduction ďin da ita", sunanshi da yaji ta k'ira ne yasashi saurin ďago kanshi, don ya daďe baiji ta k'irashi ko da Abutturab ba amma yau gaba ďaya Aliyu ta ambata, a hankali yace "y'ar gidan perm sect ce Engr Abba Muhammad Jidda", Abui ne yace "Masha Allah, ai Engr abokina ne, mutumin kirki ne sosai, ba komai kaje in mun koma Abuja sai kuyi magana da yarinyar akan zaka turo, tashi kaje Allah ya maka albarka" Amin yace sannan yayi musu godiya ya tafi, Ammah dai bata so haďin nan da ďanta ya samo ba, dukda tana y'ar Tchad amma bata so ďanta ya auri shuwa, amma haka dai ta hak'ura ba dan tana so ba, gara yayi auren da ya zauna babu mata, ci gaba sukayi da hiran Abutturab ďin da sauran y'ay'ansu bayan ya tafi Suna isa gida bayan sun shiga ciki dukkansu suka zube a palon, Baba ne da ya shigo daga k'arshe yace kowa ya shiga ya kwanta gobe flight ďinsu sha ďaya ne dan haka kowa ya shirya da wuri, mik'ewa kowa yayi ya tafi makwancinshi ya shirya yin bacci, Batuul na shiga ďaki ta cire kayan dake jikinta ta ďaura towel zata shiga toilet, fridge ďinta ta buďe zata sha Fanta taga ya k'are, wayanta dake ajiye gaban mirror ta ďauka ta nufi kan gado ta zauna sannan tayi dialing number Janet, tana ďauka tace "Janet ki kawo min fanta ďakina , na fridge ďina ya k'are, "Janet ta amsa da to anti za a kawo miki wani abu dinne bayan Fanta", Batuul tace No i dont need anything else, am okay" sannan ta katse wayan ta ajiye ta shiga toilet, warm shower bath tayi ta fito daga toilet ďin, tana fitowa akayi knocking k'ofar ďakinta karasawa tayi ta buďe, Janet ce ta shigo da square serving tray na ceramic ďauke da Fanta akai, akan table ďin ďakin ta ajiye ta juya zata fita Batuul ta k'ira sunanta "Janet ku shirya da wuri gobe zamu koma,ki faďawa Fa'iza da Aunty Tabawa, karku sake delaying ďinmu kamar lokacin da zamu zo, "Toh anti zan fada musu", "kuma ba sai kunyi breakfast dayawa ba,amma kije wajen Aunty ta faďa miki abinda za ayi goben", da toh ta amsa sannan ta fita, tana fita Baatul ta shirya cikin kayan baccinta na Lulu kitty purple, ta haďe gashinta cikin hula dark purple ta gama shafe shafenta ta hau kan gado, Laptop dinta na Apple ta ďauko ta ďanyi danne dannenta sannan ta kashe ta mayar kan side drawer, wayanta ta ciro a caji, kamar dama jira ake ta ďauki wayan ya fara ringing, ganin mai k'iran ya sa wani wide smile shimfiďuwa a fuskanta, dimple ďinta sai da suka lob'a deeply, wayan ta saka a kunnenta tare da tsuke fuska kamar ba ita ke murmushi ba yanxu ta Kuma yi shiru taqi magana, daga ďaya bangaren aka ce "shikenan since you wont talk, i will end d call, da sauri tace "Affaaannn" da k'arfi ta k'ira sunan har tana jiyo dariyanshi daga ďaya b'angaren, "woh lady so kike ki min bursting ear drums ko ko ya", sake k'iran shi tayi da Affanu, "ta yaya ma akayi kika zama friend ďita ya faďa yana dariya", "I know you love me" Batuul ta faďa mishi, ce mata yayi "waya faďa miki i love you, ai d moment you left for airport na manta da momeries and friendship ďinmu", "face ďinta tayi kalan tausayi dashi ta zumb'uro baki kamar yana ganinta tace mishi "ka manta dani, nayi fushi ma tunda ka manta ni" murya ta fara yi kamar zatayi kuka, da sauri ya fara ce mata "No no no Lulu, kar kiyi kuka mana, i didnt mean to hurt, kema ai kinsan you are my potential treasure, ai nima sai ki sani kukan" ya faďa muryanshi na rawa, kyalkyalewa ta kuma yi da dariya, ce mata yayi "dariya ma na baki ko, am offended shikenan ma goodnight", da sauri ta tare shi, "wait wait pls, dagaske dariya ka bani how you reacted, so you care, intersting", dukkansu biyu a tare suka sa dariya, ce mata ya sakeyi "Amish you dearest", a hankali itama tace mishi "Amishd you too", "so when y'all coming back", Affan ya tambaya, "Gobe ina Abuja by now", da sauri Affan ya tambayeta "Dagske Lulu gobe zaku dawo, baby na fa", dariya Batuul tasa sannan tace "masu baby, toh ba gobe zata dawo ba sai nextweek, hope kana kula min da ita da kyau, jiya ma i was with her, ce mata Affan yayi "i got to call her now in roqeta su dawo before next week dan i cant wait that long" Da dariya Batuul tace mishi "Aii best friend, good night", da haka suka katse k'iran, suna gamawa tayi adduan bacci ta shafe jikinta dashi, taje ta shafe duka k'annenta har way'anda ke kwana a ďakin Aunty, sannan ta tofe duka angles ďin gidan , ta kashe bedside Lamp ďinta ta kwanta Bayan ya koma ďakinshi ne yaji komai baya mishi daďi, key ďin mota ya ďauka ya fita shehuri ba tare da ya cewa komai ba, kai tsaye dogarai suke buďe mishi k'ofa dan sanin matsayinshi da sukayi a fada, chamber Massa ya wuce kai tsaye ya shiga, Massa ya tadda kwance a makeken gadonshi na sarauta yana waya kuma da alama yana jin daďin wayan da yake, waje Abutturab ya nema ya zauna akan ďaya daga cikin royal chairs ďin ďakin, ganin wayan da Massa keyi bazai k'are bane ya sashi tashi ya fizge wayan ya katse, "dan wulak'anci na kai minti goma ina ďakin nan, amma kakeyi kamar ba kasan ina nan ba ka zauna kana ta waya kana k'yalkyala dariya, ni banga ma abin yiwa dariya ba a waya da budurwa,mtsewww", tsayawa Massa yayi yana kallonshi har sai da ya gama yace mishi "mik'o min wayata in ka gama" mik'a mishi wayan yayi ya nemi waje akan gadon ya zauna ya dafe kanshi, ganin da Massa yayi abokinshi ba wasa yakeyi ba yasa shi zama kusa da shi dan ya san ba komai ke sashi damuwa ba, komai girman abu yana danne zuciyanshi, dafashi yayi yace "Man whats wrong, you dont look yourself, you seem to be upset, hope dai lafiya, tell me whats wrong am dead worried right now", ajiyar zuciya yayi yace "Su Abui ne suka ce that sun bani two weeks i should introduce to them the girl i would marry , ko kuma su nema min da kansu, wai bazan tafi project ďina ba mata ba" kuma you know i have no one at hand da zance musu gata am ready to marry, cikin jimamin abinda ke shirin faruwa da abokinshi yace "Man toh baga Ajiddeh ba, you guys go along well dan naga babu wacce ke samun attention ďinka kamar ita kuma ma she is beautiful and everything" wani kallo Abutturab ya watsa wa Massa, "wa yace maka dan kyanta nake kulata, yeah i know there is this ounce of affection i have towards her but bai kai har ince zan aureta ba, su Abui should understand su k'aramin lokaci, i need time, bana son yin mata biyu, so kaga i should be given time dan in samu right choice ďina" k'arashe maganan yayi tare da nannauyan ajiyan zuciya" Massa ne yace mishi kawai kayi introducing Ajiddeh tunda tana sonka you can make her all you like, zatayi duk abinda kake so, Ko Shehu bazaiyi siding damu ba saboda shima damuwanshi kenan a kanmu, sai dai ma ya ce a k'ara dani, Man kawai muyi addu'an abinda yafi alheri", cigaba sukayi da hirar neman mafita daga k'arshe kawai suka yanke shawaran ya auri Ajiddeh tunda ita kaďai ce option ďin dan basu san wacce su Abui ďin zasu zab'a mishin ba, k'arfe goman dare ya mik'e yace da Massa zai koma dan yana da flight gobe by 11:00, sun fito waje Massa na rakashi inda yayi parking mota Massa ke tambayanshi, "Man ya akayi ne baka zo ba jiya inata jiranka", tambayan ne ya sashi tunawa da duk abinda ya faru tsakaninshi da Batuul, ďan k'aramin tsaki yayi daga ciki yacewa Massa "gajiya nayi", dariya Massa yayi yana ďan tab'a kafadarshi yace "ango tun bakayi auren ba har ka fara gajiya, toh in kayi auren kuma bazamu na ganinka ba kenan", Abutturab bai ce mishi komai ba ya buďe motarshi ya shige tare da ce mishi "sai munyi waya, ni zan wuce", Allah ya tsare hanya Massa yaayiwa Abutturab sannan sukayi sallama Bayan sallah asuba babu wanda ya koma bacci, kowa shirin tafiya ya farayi, sai hayaniya akeyi a gidan, kowa ya tashi a gidan banda k'ananan k'arshe, Janet ce tayi knocking k'ofan, bayan an mata izinin shigowa ta shigo ďakin, tarar da Aunty da Batuul a ďakin tayi,Batuul na shiryawa Aunty kayanta da zata tafi dasu a cikin jaka, Aunty ce tace mata yarannan fa har yanxu basu tashi ba Janet, maza je ki k'irawo Fa'iza kuzo kuyi musu wanka dan 8 ya wuce, da toh ta amsawa Aunty sannan ta fita k'irawo Fa'iza dan suyi aikin da aka sasu, ďaya nayin wankan ďaya kuma na shafa musu mai da sa musu kaya, Batuul na gamawa tacewa Aunty "zanje in shirya sannan ta fita daga ďakin Aunty ta isa d'akinta, wanka tayi sannan ta fito ta shirya cikin atampa exclusive green da pattern ďin yellow da bak'i, ďinkin yayi mata kyau sosai, skirt ne with peplum blouse mai three quarter hannu, ba a sa komai a jikin rigar ba sai patterns ďin atamfar aka yi mata aiki dashi, ďan kunne kawai ta saka bata sa sark'a ba, agogon gucci ta ďauka ta mak'ala a hannunta, babu wani kwalliya da tayi sai kwalli kawai da ta saka a idonta, duk da ba tsayine da ita ba, bata saka takalmi mai tudu sai slippers din versace baqi da ta saka, luggage ďin kayanta ta jawo ta ajiye bakin k'ofa sannan ta ďauko k'aramin bak'in gyale ta ajiye a kafaďarta, fitowa tayi ta sauko k'asa taga kowa ya shirya cikin kayan alfarma suna breakfast, shiyasa ma bata fara saka abaya ba dan tasan Baba sai yayi mata maganan abayar, k'arasawa tayi itama ta janyo kujera ta zauna , Aunty da Baba ta gaida a tare suka amsa mata sannan duka k'annenta suka gaisheta suma, Bismillah tayi ta fara cin abincin itama, a nutse suka gama breakfast ,tara da rabi dai dai aka fara fita da kayansu, manyan mazan kowa da hand luggage ďinshi a hannu, na Aunty, Batuul dasu Hafix kuma yana hannun su Janet, Baba ne shima ya sauk'o daga bene rik'e da nashi, Batuul na hango shi da sauri taje ta karb'a ta k'arasa dashi k'asa ta bawa driver su fita dashi, Kanta ya shafa Yace ya gode , Baba na k'arasowa duk suka tashi suka fita suka nufi inda motocin gidan ke pake, Baa Liman ne da Sunday driver zasu kaisu airport, Batuul da Ahmad, Sa'eed, Khalil, Mus'ab mota ďaya suka shiga while Baba, Aunty, Yusra, Mahir, Hafix da Aabid na mota ďaya, sai da sukayi addu'an fita daga gida da ayatul kursiyu kamin drivers ďin su fita daga gidan Hanyan Maiduguri international airport suka bi, goma da rabi suka isa, ana shiga cikin airport ďin heartbeat ďin Batuul ya k'aru idonta ya fara tara hawaye, addu'a ta soma har taji ya ďan ragu, bayan sun shiga har ciki sun sauk'a ta isa wajen Aunty ta ce mata, "Aunty tunda muka zo Maiduguri heartbeat ďina baya running at a normal pace, yanxu ma muna shigowa airport naji ya k'aru sosai", Aunty ce ta dube ta tuna da ranan da ta dawo idanunta sunyi ja, ce mata tayi "baki da gaskiya shi yasa yak'e karuwa, dariya sosai Batuul tayi sannan tace "kai Aunty, wane rashin gaskiya zanyi har heartbeat ďina ya rik'a karuwa, ni dai babu abinda nayi", ta juya ta tafi, binta Aunty tayi da ido dan itama ta tab'a shiga yanayi irin na Batuul na k'aruwan bugun zuciya, murmushi tayi ta girgiza kai sannan ta tattara kan yaran sukayi departures waiting room suna jira a k'ira su in jirgi ya shirya 💖💝BATUUL💖💝 11 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Suna zaune suna jiran jin announcement ďin departure su, Mahir yacewa Aunty zai sha smoothie, sauran yaran naji yace zai sha suma duka sukace zasu sha, Aunty ganin dukkansu na son sha kuma ba wai suna son bane dagaske kawai dan sunji ďaya daga cikinsu yace zai sha ne dan kawai suje yawo yasa faďin cewa za su sha Aunty cewa Batuul, "Batuul jeki da Fa'iza ku kawo musu , bazan iya da yawon yaran nan a cikin airport ďinnan ba , yanxu sai in nemi wani in rasa, Murmushi Batuul tayi sannan ta mik'e ita da Fa'iza suka karb'i kuďin a hannun Aunty suka tafi, suna tafiya yaran na ihun faďan shi ice cream yake so wani kuma yace milk shake yakeso, bata kula kowanne daga cikinsu ba tayi tafiyar ta, mutanen dake zazzaune sai kallonsu sukeyi ,suna tafiya suna ďan hira da Fa'iza har suk'a k'arasa eatery ďin dake airport ďin, order ďin smoothie ta bayar ta zauna jiran a gama packaging su tafi, ana gamawa aka mik'o musu Fa'iza ta karb'a, suna juyowa zasu tafi taji bugun zuciyanta ya sake k'aruwa, saurin tafiyanta ta rage tana Hasbunallahu wa ni'imal Wakeel, juyowa Fa'iza tayi ta dubi Batuul tace "Yaa Batuul lafiya ,naga kina tafiya a hankali, Ce mata tayi "Lafiya Fa'iza, muyi sauri mu k'arasa" Suna cikin tafiya daga gefe ta hango Abui da wani mutum a tsaye, bata ga fuskanshi ba dan ya juya bayanshi, Abui ke facing ďinsu sai bayan mutumin kawai take gani, Hasbunallahu wa ni'imal wakeel ta sake sabida yadda bugun zuciyanta ya k'aru, da sauri ta k'arasa inda ake zaman jiran , a ranta tana cewa in sun koma gida zata faďawa Aunty dagaske bugun zuciyan nata ya k'aru, suna zuwa suk'a mimmik'awa kowa abinda yace yana so suka koma wajensu suka zauna, basu fi minti biyar da zama ba akayi announcing passengers ďin Maiduguri to Abuja su fara boarding yanxu jirgi zai tashi, mik'ewa sukayi suka isa inda jirgin Med View ke tsaye suka hau matakalar suka shiga ciki, a first class suka sami waje suka zazzauna, Batuul ce k'arshen shigowa, duk seats ďin sun cika sai last two seats ďin k'arshe ne da daga shi sai economy class babu kowa a wajen ta k'arasa ta zauna, tana zama ta cire wayarta daga cikin jaka da ear piece sannan ta saka jakar daga sama inda ake ajiye luggages, wayarta tasa a flight mode ta jona ear piece ďin da wayan ta mak'ala a kunnenta, a hankali ta jinginar da kanta a kujerar tare da lumshe idanuwanta, heart beat ďinta ne ya k'ara k'aruwa kamar zai fito daga ciki, seat belt din jikinta tayi unfasten snn ta shiga karanto addu'a a hnkli a xuciyarta tana dan jujjuya kanta, ji tayi kmr mutum na tsaye kanta don wani dad'da'dan kamshi ne ya bugi hancinta, duk da hka ba ta buďe idonta ba sai da ta gama addu'ar da take snn ta bude idonta a hnkli, wani mugun faduwa gabanta yyi ganin Wanda ke tsaye kanta idonsa a kanta ko kiftawa baya yi, dauke kai yyi da sauri fuskar nn tasa a daure yace "Excuse me" sae a snn ta lura da handbag dinta da ke ajiye kan seat din dake gefenta, daukewa tayi ta mayar cinyarta snn ya xauna, mamaki ne ya cika ta ba kadan ba, mikewa tayi ta ajiye handbag dinta xata fita duk da bbu takamaiman abinda xata je yi amma ya ki bata hanya, ita kuma taki cewa ya matsa mata, komawa tayi ta xauna ranta yyi mugun baci, to wae shi wnn guy din me yake daukan kansa, me ma yasa zai zo kusa dani ya zauna at d first place, ko ina ne sae mun hadu, su Farida ma basu dawo ba shine shi zai tafi ya barsu, ko mey zaije yi shi kaďai oho" ďan k'aramin tsaki taja ta kawar da kanta tana kallon waje ta window, tsakin da taja ne ya sashi kallonta, lokaci ďaya yyi kwafa ya dauke kansa da yaga hankalinta baya wajen, announcement aka shiga yi nacewa " passengers on board should pls fasten their seat belts, Med view flight is about to take off" fasten din seat belt dinsa yyi ganin bata da niyar yin hkn ita yasa ya juya yana kallonta, a lumshe ya ga idonta snn ga earpiece a kunnenta, da farko dan tsaki ya ja ya kawar da kansa, amma ganin few minute ya rage flight yyi take off yasa ya dan buga hannun seat dinta, ko kadan batuul bata ma san yana yi ba don kure Karatun da take saurara tayi, ya kuma buga handle din seat dinta da karfi nn ma bae ga alamar tasan yana yi ba, jin announcement din da ake yasa yyi saurin jawo seat belt din ya shiga kkrin fasten din mata, Batuul kam kawae jin hannun mutum tayi jikinta, ta bude ido da sauri tare da cire earpiece din kunnenta tace "What...." Shiru tayi ganin har ya gama sa mata ya dauke kai, lkci daya ya lumshe ido kamar mai bacci, takaici ne ya isheta bata san lkcn da ta furta "Hw dare yhu!" Bude ido yyi da sauri ya xuba mata manyan idonsa yana kallonta, murya can kasa yace "fuck does words of urs!" hawaye ne ya cika idonta, lkci daya ta rufe fuskarta da mayafin jikinta, dauke kai yyi ba tare da ko dar ba, bayan yan mintuna Batuul ta bude fuskarta suka hada ido, hawaye ya gani fuskarta, lkci daya jikinsa ya dan yi sanyi don ya tsani kukan mace, a hnkli ya furta "Damn her, ita kenan kullum hawaye, ko meh nayi mata oho," kusan a zuciyanshi ya faďi haka, handkerchief ďinshi dake aljihun jeans ďinshi ya ďauko ya mik'a mata ba tare da ya kalleta ba fuska daure, k'in karb'a tayi, haushi ne ya kamashi ya maida handkerchief ďinshi ya ruk'o kafaďanta da k'arfi, "clean that face, bana son sake ganin hawayen nan, don bbu abinda nayi maki I only helped yhu, ko kuma you leave this seat immediately" saketa yayi dan k'aruwa hawayen sukayi, ya ja dogon tsaki ya ďauke idonshi daga wajenta, sake juyowa yayi bayan y'an mintuna yaga har lkcn hawayen take, da kanshi ya ďauki handkerchief ďin ya fixgota ya shiga goge mata hawayen , ture hannunshi tayi daga fuskanta tace mishi "malam ka rabu dani da hawaye na, ai fuskana ne kuma hawayena ne, let me be plss" ta juyar da kanta tana kallon gajimare da sauri , magana zaiyi mata kenan hostess ďin jirgin ta tsaya a daidai kujeran da suke, plate holder ďin seats ďin nasu ta jawo ta ďora musu ruwa akai a ďan k'aramin disposable cup, hak'oranta ta washe ta gyara murya tana yiwa Abutturab magana, "Sir what would you like to have", bai ďago kanshi ba yace mata "Get me coffee", okay tace sannan ta dubi Batuul tace mata "Ma'am what would you like to have", k'in juyowa Batuul tayi, sake tambayanta matar tayi sannan ta juyo tace mata, "am okay, i need nothing" murmushi matar tayi sannan ta wuce" wayanta ta ďauko dake mak'ale a pocket ďin seat ďin gabansu ta sake mak'ala ear piece ďin a kunnenta taci gaba da jin karatun qur'anin da takeji ďazu, hostess ďince ta dawo da coffee ta ajiye mishi ta juya. k'arfe 12:10 daidai jirginsu yayi landing a filin jirgin Nnamdi azikiwe international airport dake Abuja, jirgi na tsayawa Batuul ta tashi zata fita daga seat ďin da sauri fuskar nn tata a daure, k'in matsawa yayi ta fita har saida mutanen dake can economy class suka gama fita na first class ďin ma sun k'are, ita dae bata ce mishi komai ba har ya gama zaman mulkinshi ya mik'e cikin isa, ko gama barin wajen be yi ba ta bangajesa ta fice ta ďauko jakanta, sae da ya gama bari ta dauki jakarta snn ya fixgo ta yace "Are yhu blind" buge hannunsa tayi ta fita da gudu, tana fita taga y'an gidansu a waje ďaya, Aunty ce tace mata "mey kika tsaya yi ke baki fito ba sai yanxu", cewa Aunty tayi "bana so inzo fita ina jiran mutane shiyasa na jira kowa ya gama fita", Abutturab ne ya k'araso inda yake fuskarshi a sake kamar ba shi ke ďaure fuska ba ďaxu a cikin jirgi, Hannu ya mik'awa Baba tare da ce mishi "Baba ya gajiyan jirgi", murmushi Baba yayi yace mishi "Alhamdulillah Aliyu, mun godewa Allah mun iso lafiya" juyawa yayi ya dubi Aunty ya ďan sunkuyar da kanshi tare da gaisheta, itama amsa mishi tayi cikin sakin fuska, hannu ya mik'awa duka k'annen Batuul suka gaggaisa, Aabid ne kawai bai gaisa dashi ba sai kanshi da ya shafa tare da murmushin da ya bayyana dimple ďinshi yace mishi da "Hello champ" dariya sosai Aabid ya saka kamar yasan abinda aka faďa mishi, tsayawa Batuul tayi tana kallonshi da mmki a ranta take cewa "Yaushe yasan su Baba kuma" shi kam ko kallon inda take bae yi ba, tab'e baki tayi ta juyar da kanta, suna tsaye motoci suka k'araso inda suke, Baba ne yacewa Abutturab "toh Aliyu sai kaje ka huta ko gobe za a fara aiki" da murmushi ya amsawa Baba da "In sha Allah", sai da ya jira sun shiga motocinsu sannan ya shiga nashi shima da aka zo ďaukanshi dashi, hanyan Gwarimpa su Batuul sukayi, motar su Abutturab kuma tabi hanyar Asokoro. 💖💝BATUUL💖💝 12 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* , Thank you sister, you are one in earth, you are truly an inspiration, Thank you soo much for being there for me, we love you❤ A hanya Baba ke tambayan Batuul abubuwan da take buk'ata na graduation ďinta, ce mishi tayi "Baa dama kayan graduation ne ,prom da zamuyi a ranan da yamma sai walima shi kuma inada kayanshi", kallonta Baba yakeyi har ta gama sannan yace mata "Sai kuje ko Dubai ne ku duba tunda babu time kuma shi kaďai kuke da visanshi, sai ki siyosu a can", murmushi tayi tace "Baa ai nayi magana ma da designer ďita har na gama faďa mata yadda nakeson kayana, next wek ma tace zata gama", tambayanta Baba ya sakeyi "are you sure babu matsala Mamana zaki samu yadda kikeso", kai ta gyaďa tace ehh Baa In sha Allah", murmushi yayi ya shafa kanta yace, "Allah ya miki albarka" daďin addu'an ne ya sata saurin jnfrr da "Amin", hira suketayi suna tafia, k'arfe biyu daidai suka isa gaban wani gate saboda nisan tafiyar dake tsakanin airport ďin da cikin gari ga hold ups hornsukayi, gidan exactly irin gidan da suka baro ne a Maiduguri, sai dai wannan cream paint ne da brown gate wancan kuma farin paint ne da black gate, masu gadi ne guda biyo suka taso suka buďe musu, a lokaci ďaya suka ce musu sannu da zuwa tare da yi musu ya hanya, cikin sakin fuska suka amsa musu da Alhamdulillah Friday da Jonathan driver ya k'arasa ciki dasu wajen parking, firfitowa sukayi daga motocin suka nufi cikin gida, shima cikin iri ďaya ne da wancan abinda kawai ya banbantashi da wancan shi cream and brown live wallpapers ne manne a bangon, sai wani large human size family picture daga gefe manne da bango, k'arasawa kowa yayi cikin gidan ya samu waje ya zauna a falon, Baba ne kaďai ya haura sama,khalil ne yace "Home sweet Home" Ahmad ne yace mishi "ai nan ba home bane, dole zamu koma maiduguri saboda Abuja ba garinmu bane", "but still this is where we live" inji kalil, tsakaninsu suke ta hiransu abunsu, Mus'ab ne ya tashi zaije ya kunna Tv, Aunty tayi maza tace mishi "koma ka kashe TVn nan ku wuce kuje kuyi alwala kuzo muyi salla" komawa yayi ya kashe TVn duk suka tashi suka tafi sama yin alwala, basu fi minti biyar ba suka sake sauk'owa bayan sunyi alwalan, Baba ne yajasu Sallah dukkansu kasancewar an idar a masallacin gidan, suna idarwa sukayi y'an addu'oinsu suka shafa, hannu suka mimmik'awa junansu har Baba da Aunty suna cewa *Baa nda dubdo, Auntu nda dubdo*, (Baba ina wuni Aunty ina wuni), "Wassalatu wassalamu ala Rasulillah" Al'adan gidan kenan indai sukayi sallah sai sun gaida junansu , suna gamawa wata mata siririya da baza ta wuce 25 yrs ba ta shigo falon ta k'ofan kicin , sanye take da kayan kuku tana rik'e da wani food flask mai kyau zatayi hanyan dinning su Yusra ne suka hangota suka ruga wajenta da gudu suna faďin "Aunty Esther mun dawo, ashe kina nan shine baki fito ba, mey kike dafawa, jawosu tayi jikinta tace muje kuga abinda na dafa in baiyi muku ba sai ku faďa min wanda kukeso, murna suka sa suna jin daďi, sai da tazo ta gaida Baba da Aunty sannan taja yaran suka tafi, Baba ma mik'ewa yayi yace yana da aiki gobe sosai yanxu zai fita, tare suka ce mishi "Baa adawo lafiya, Allah ya bada sa'a" , Amin ya amsa musu da sannan ya fita, Mik'ewa Batuul tayi ta k'ira janet tace ta hawo mata da jakanta, ana kawo jakan ta ciro Macbook ďinta ta kunna, skype ta shiga ta duba ko Farida na online, da taga bata nan ne ta ďau waya ta k'irata, tana amsa tace kixo skype sannan ta katse wayan dan tasan in Farida ta fara magana ba yanxu zata gama ba, connecting tayi da Farida, tana ganin Batuul ta mik'e cikin sauri ta zauna, cewa tayi "babe i missed you soo much, ji nakeyi kamar Nigeria gaba ďaya kuka bari ba Maiduguri, i just cant wait to be back, katseta Batuul tayi tana dariya tace "Riri you can talk for Africa, tun ďazu fa kike magana , har na tausayawa Affan", dariya Farida ma tayi tace " He loves me, babu yadda zaiyi, infact he enjoys surutuna and not only Africa, the whole planet", dariya suka sa dukkansu biyun a tare sannan Farida tace "Ya hanya, what time kuka isa", "Hanya Alhamdulillah , tun 12 but sai 2:00 muka isa gida" sunanta ta k'ira tace "Farida Yaa Abun ku yau ya dawoDawo Abuja ko" dan ita gani take ba shi bane, da sauri Farida ta amsa da "Ehh, kinji yadda gidan yayi daďi, dama so nake ya tafi, naji ance ma country ďin gaba ďaya zai bari, ni daďi nakeji, kinga ko yau da ya tafi har na samu na fita" Batuul ce tace nifa babu ruwana kullum kiyi ta gulmanshi, nidai babu ruwa", tsaki Farida taja tace "ai idan ka nuna kana tsoronshi ya fi baka wahala, ni yazo yayi aure ma ya tafi" dariya Batuul tayi tace "zaki sani, nifa about grads na k'iraki, gown zan saka , kefa" ta tambayi Farida , "Ni wando zan saka" inji Farida, "wane wando kuma sai kace su Hamra, its either gown or skirt, am not wearing any trouser" dariya maganan ya bawa Farida tace "woh calm down lady , am just kidding, yadda kikace haka zamuyi, but a ina zamuyi ordering", "dont worry about that, just send me irin wanda kikeso zan bayar ayi mana" inji Batuul, "aii zan tura miki details ďin duka " da haka sukayi sallama, suna gama wayan Batuul ta cire kayanta ta shige toilet ta watsa ruwa ta fito, wani doguwan riga ta saka mra nayi bayan ta shafa mai, ta ďan fesa turare Abutturab na isa gida ya shige ciki yasa key ya buďe dan babu kowa, ďakinshi ya nufa yana shiga ya zauna akan gado, tunanin aikin dake gabanshi yayi, mik'ewa yayi ya shiga toilet ya watsa ruwa yayi alwala ya fito, kaya ya canja amma basu kai waďanda ya cire nauyi ba, sallah ya tada, uana idarwa bayan addu'oin da yayi ya mik'e ya sauk'a k'asa, kitchen ya nufa ya fara neman abinda zaici dan ko breakfast baiyi ba, coffeee ya haďa ya zauna a kujerun island ďin kitchen ďin ya fara sha, sai da ya gama juye saurin a wani ďan madaidaicin flask ya koma sama dashi, wani ďaki daban ya nufa na glass, komai na ďakin farine da glass, sanyi ke fitowa daga ciki, yana shiga ya isa wajen wani drawing board ya zauna a kan kujeran dake gaban board ďin, kayan aikin architects ne a ďakin irinsu irregular curves, french curves, desktop ďin apple, daga gefa akwai wani table akai an ďaura su set squares, CAD,pencils da sauransu, wayanshi ya ciro ya k'ira layin Amma, tana ďauka yace mata "Ammah ina wuni" da lafiya ta amsa sannan ta tambayeshi ya hanya, "Alhamdulillah ya amsa mata da sannan yace sun isa lafiya" tambaya yayi ko Abui na gida tace ehh, mik'awa Abui wayan tayi sannan shima suka gaisa, addu'a yayi mishi akan aikin da zai fara sannan Ammah ta karb'i cewa Ammah yayi "Ammah ki faďawa masu aikin dake BQ na dawo suzo su dafa min wani abu am hungry", cike da damuwa tace "Abu saida nace kayi breakfast kace ba yanxu ba gashi 2:30 yanxu, kuma kasan condition ďinka,zance suyi maza su shigo suyi maka " sannan ya katse wayan bayan yayi godiya, gaban desktop ďin ya koma ya fara danne danne, wayanshi ne yayi k'ara, ganin mai k'iran ya ďan saki tsaki sannan yayi recieving tare da sawa a kunnenshi, daga ďaya bangaren aka fara magana "Hello baby, ranan i called you kace min in ka koma gida you will call me amma baka k'ira ba", shiru yayi baice komai ba har saida ta gamana sannan yace mata "ya kk", cikin yanga da karairaya murya tace mishi "lafiya inata missing ďinka amma kai babu ruwanka dani, ko da kace zaka k'irani inata jira naji shiru", ce mata yayi "yeah i was busy shiyasa, Yasu Mum" bata ji daďin amsan da ya bata ba amma ya ta iya tunda tana aonshi haka zata hak'ura , ce mishi tayi "su mum lafiyansu rannan ma tace in garish ska", "ina amsawa, in kun dawo zamuyi discussing wani issue, i dont want to take long, so in kun dawo sai muyi magana", tunanin maganan da zasuyi ďin ta tsaya yi a ranta, tana ta addu'an Allah yasa maganan aurensu ne dan ta daďe ta nuna mishi ya fito ya ncewa ba yanxu ba, shirun da yaji yayi yawa ne ya sashi tambayanta "kina jina" da sauri ta katse tunanin tace mishi "Eh ina ji, amma baby wane magana ne baza muyi ba sai na dawo, ai waya ma ya isa" katseta yayi da cewa "nace sai kin dawo ba awaya zanyi maganar ba" jiki a sanyaye tace "okay sai mun dawo" ta katse wayan, sai da ya gama wayan ya koma wajen CAD ďin yana daddanawa Batuul na saukowa ta nufi palo inda Aunty ke zaune, kusa da Aunty taje ta zauna sannan tace mata "Aunty sannu da hutawa", "yawwa sannu Batuul", magana ta gani a bakin Batuul dan taga yadda take ta fidgeting da zoben dake hannun ta, tace mata "Menene Kinxo kin sani gaba kin kasa mgana", a hankali Batuul ta buďe bakinta zatayi magana sai kuma ta fasa, da Aunty taga Batuul ďin tak'i magana ne tace toh Allah ya kyauta ta juyar da kanta taci gaba da kallon Tv, can da Batuul taga shirun bazai fissheta ba tace "Aunty dama inason ki faďawa Baba in munyi grads bayan result ďinmu ya fito ya kaini LONDON UNIVERSITY OF ECONOMICS, dgaske i promise zanyi karatu har in fito da first class" da mamaki Aunty ta waigo ta dubeta, tasan dai Batuul da Baba tare suke komai sai dai taji daga baya amma ya akayi yau take tambayanta, ce mata Aunty tayi "ban gane inyiwa Baba magana ba, kinyi magana ne yace bazai kaiki ba", cikin marairaicewar fuska Batuul tace tun ina school yace min wai inyi hak'uri da wajen nan duk inda nakeso a Nigeria zai kaini amma banda abroad", kallonta Aunty tayi sannan tace toh tunda yace baya son waje ai sai ki hak'ura, meye sai nayi mishi magana, its his decision i cant change" hawaye ne ya fara gangarowa idon Batuul tace "Aunty in kinyi magana zai yadda ni nafison wannan university", mamakine ya sake lullub'e Aunty, tasan Batuul bata yiwa maganan Baba musu amma yau harda hawaye, hawayen ne yasa ce mata "tashi kije, zamuyi magana", da murna Batuul ta tashi tana addu'a Allah yasa ya yadda, kitchen ta nufa taje tayi waffles da syrup ďin vanilla ta dawo dinning ta ci Masu aikin gidan ne wata dattijuwa daga cikinsu ta hawo sama ďakinda yake taje , knocking tayi daga bakin k'ofa, baice ta shigo ba dan baya yadda kowa ya shigar mishi wannan ďakin, tashi yayi da kanshi ya duba yaga ko waye ke nemanshi, yana buďewa yaga tsohuwar, da sauri yace mata "Bawa ashe kece ai da kin shigo baki tsaya knocking ba" ce mishi tayi a ah babana ai nasan aiki kake shiyasa na k'wank'wansa, dama zance maka na gama yi maka abincin ne", da toh ya amsa mata sannan yace ai ban san kina gida ba da na k'ira na ce miki ina dawowa", ce mishi tayi "ai babu komai , yanxu ma Hajiyace ta k'irani take ce min ka dawo kana neman abinci shine na shigo na samo maka wani abun, a kawo nan ne ko a bari a dinning"," a ah Bawa ba sai an kawoshi nan ba zan sauk'a inci" toh tace sannan ta sauk'a ta koma k'asa 💖💝BATUUL💖💝 13 By phartiemarhk Sai da ya gama aikin da yakeyi ya sauk'o yaci abincin, bai wani ci dayawa ba ya tashi ya shiga toilet ďin dake k'asa yayi alwala ya fita masallaci dan lokacin 3:50, da ya idar ya dawo gida, tunda ya shiga yaci gaba da aikinshi sai kuma sallah ke tadashi, bai kwanta ba sai after 12, yana kwanciya bacci ya kwashe shi, washegari 6 ya tashi bayan yayi sallah asuba yayi wanka, jeans blue ya saka da farar rigar max n spencer sannan ya ďaura blue Tuxedo ta giorgio Armani daga sama, kayan ba k'aramin kyau suka mishi ba kasancewanshi dogo, agogon ciélo ya mak'ala sannan ya fesa turaren karenbkelly da vesace eros, k'arfe bakwai daidai ya gama shirinshi ya fita, CLS golden ya buďe ya shiga ya fita daga gidan, office ya wuce, a nan yaci gaba da aiki har sai da minister yayi mishi waya suka tafi sighting area da zasu yi constructing, shi ya bada shawaran contractors ďin da ya kamata ayi aiki dasu, shi kuma yayi musu designing plan ďin yadda wajen ya kamata ya zama, satinshi ďaya yana aiki babu hutu, a ranar satin ne su Ajiddeh suka dawo, yana office 12:00 yaga k'iranta da number ta ta Nigeria, gaba ďaya ma ya manta da yau zasu dawo kuma yace mata zai ďaukota in sun dawo, tsaki ya ďan ja kamin yayi recieving call, kamin yayi magana ta riga shi da murna tayi mishi magana "Hello Baby mun dawo, we just landed, yanxu ma kai nake jira, bazan bi su Mum ba ni", sai da ta gama yace "olryt gani nan zuwa", key ya ďauka yayi magana da PA ďinsa akan duk wanda yazo neman shi ya tashi for d day sai gobe, cikin girmamawa ta amsa da "Okay sir, sai ka dawo", yana fita yayi hanyan airport, awa ďaya da rabi ya isa, side ďin international arrivals yabi, waya ya ďauko zai k'irata kenan yaji an sa ihu daga bayanshi "Baby am here" ko bai juyo ba yasan Ajiddeh ce, da gudu ta taho ta rungumeshi kamar za a k'wace mata shi, "i missed you soo so much baby" peck tayi mishi a kumatu sannan ta ďan sassauta rik'on da ta mishi ta ďan kwanta a kafaďanshi, shi mamakin halin Ajiddeh ne ya hanashi magana, duk y'an gidansu na wajen har Dad da Mum ďinta amma babu ruwanta haka tazo ta mak'aleshi, janyeta yayi daga jikinshi yayi mata magana a hankali "sweetheart baki ganin akwai jama'a a nan besides gasu Mum nan " zumb'uro baki tayi tace "ai dama nasan bakayi missing ďina ba, komai nayi is not right to you, wata ďaya we didnt meet, i was just happy, kuma su Mum ai sun san ina sonka ne" bai sake ce mata komai ba dan yasan she wont understand, k'arasawa yayi inda suke ya ďan risina ya mik'awa Dad hannu, gaisawa sukayi ya juya ya gaida Mum, da murmushi ta amsa sannan , juyawa yayi ya gaida Yaa xee, a dak'ile ta amsa mishi, bai bi ta kanta ba ya cewa Dad muje, Mum ce tayi saurin ce mishi "No ai drivers sunzo da su zamu tafi, sai dai kai ku tafi da Ajiddeh", cewa yayi okay, sai da ya bari suka isa inda driver yake sannan sukayi inda motanshi ke pake, unlock button ďin jikin key ya danna ya buďe, k'ofar ta buďe ta shiga shima ya shiga ta ďaya bangaren ya tada suka tafi, hanyar Wuse II yabi da ita, kalonshi tayi tace "baby kace zamuyi discussing wani issue in muka dawo", ta tsaya tana duban shi tana jira taji amsa da zai bata, sai da ya ďebi wajen 30 seconds tukunna yace mata "Yeah , inaso ne in turo gidanku batun aurenmu, i dont want to take long so ki faďawa su Mum", har ya gama magana ita dai ji take kamar a mafarki take, shirun da yaji yayi yawa yasa ya dubeta ya ga kallonshi take yace mata "you there", da sauri ta girgiza kanta tayi hugging ďinshi a cikin motar, sai da ta sake shi tace, "Aliyu i cant believe my ears, you just said zaka tura gidanmu though bamuyi grand proposal ďinmu ba but its okay, am super excited, I love you soo much baby, ai yau ma zan faďawa Mum, sai ta faďawa Dad" peck ta k'ara mishi sannan ta zauna da kyau tana ta jero mishi abubuwan da zasuyi na bikin Batuul kam tana can gida tana shirin grads ďinsu, da kuma murnan yau Farida zata dawo, dukkansu biyun kaya iri ďaya tayi musu ďinki ne kawai ya bambantasu, har takalma iri ďaya sukayi, taso taga Farida yau amma babu time, kawai driver ta tura ya kaiwa Farida nata kayan, a washegarin graduation ďin taje saloon aka wanke mata gashinta, sai da ta gama ta k'ira driver yazo ya ďauketa, tana shigowa gida taga kowa a palo, k'arasa tayi ciki ta cire gyalen abayar jikinta ta zauna a kan kujera, su Ahmad ne suka fara cemata" inyeh su graduate, shikenan daga gobe kin tashi daga pupil", dariya tayi musu tace "as in, yanxu sai university, ku ku tsaya ma tukunna, ticket tara aka bani a school that means mutanen gidan nan tara ne zasu" ihun kowa shi zaije suka farayi, dariya tayi musu tace "ai sai dai kawai wasu su hak'ura dan bazai ishe mu ba, we are eleven and nine tickets ake badawa, so excluding Aabid still mutum ďaya bashida ticket, and i want you all there", da taga babu wani da is willing to hak'urane ta ciro wayarta tayi dialling Farida, tana ďauka tace " Riri kinsan meye, i have only 9 tickets mu kuma we are ten, kuma i didnt invite kowa ma, so if akwai extra inaso for one of us", cewa Farida tayi "dama ni am not inviting kowa, zan bawa Yaa Abu 3, sai Abui, Ammah da Sadiq, kinga inama da extra 2, "Yawwa babe, na aika Baa liman da kayanki sunyi daidai ko" inji Batuul, "sosai ma wlhy , thank you soo much", katse ta Batuul tayi tace " I hear you, who are you thanking", dariya Farida tayi tace sorry i gat to go Ammah na k'irana we will talk later, bye" da haka suka katse wayan, cewa y'an gidan Batuul tayi ai ta samu ticket ďin mutum ďaya duk daďi sukaji suka ci gaba da hiransu, k'arfe tara ta tashi ta hau sama Da murmushi a fuskanta ta buďe ido, k'iran asuban fari ne ya sata tunawa da yau wace rana ce, a hankali ta tashi daga kan gadonta ta shiga toilet, wanka tayi da brush sannan tayi alwala ra fito, nafilfili tayi, ta godewa Allah da ya nuna mata ranar gama makarantan ta lafiya, Addu'a sosai tayiwa iyayenta da al'ummar musulmai, da ta gama tayi karatun k'urani, tana gamawa aka tada sallah ta tashi tayi, koma tayi kan gado bayan ta idar da sallah amma ba bacci take ba, itama bata san tak'amaimai abunda zatayi ba dan murna, wayanta ta jawo ta k'ira Affan, yana ďauka tace "cousin of life" a hankali ya amsa mata kamar mai jin bacci, "Hello best friend what is it kika tadani da sassafe haka", ido ta wara tace "Affan dont tell me you are still on bed sleeping , its our day fa yau, our graduation day", ce mata ya sakeyi "Batuul saifa 9 o'clock and its still 7, i have two more hours to do everything", ce mishi tayi "ai yanzu zan k'ira Maa ince mata ko tashi sallah bakayi ba, Affan get out of that bed and get ready", katse wayan tayi batajira mey zai ce ba, haka ta k'ira Farida ma, ita ma hira sukayi tayi dan ta kasa bacci itama, sai da takwas yayi suka katse sukaje shiryawa, ďakin su Ahmad taje ta tashesu tace kowa ya shirya kar su b'ata mata lokaci, Janet ce tazo tace mata wata mata tazo nemanta, cewa janet tayi ta hawo da matar ďakinta, ita kuma ta juya ta tafi, tana ďaki sukayi knocking tace su shigo, wata mata ce fara siririya da murmushi a fuskanta suka shigo, wani ďan madaidaicin akwati a hannunta ta ajiye, sai da ta zauna sannan suka gaisa da Batuul, matar ce tacewa Batuul yanxu zamu fara ko dan kince 9 ne event ďin naku ko, da ehh Batuul da amsa mata sannan tace "Light nude make up zakiyi min, ko foundation bana so a sa min, just my brows then liner, i just want everything nude" murmushi matar tayi tace mata "Na gane but brows ďinki are full, ko za a ďanyi carving", a ah Batuul tace sannan suka fara, takwas da ashirin da bakwai suka gama, ba k'aramin kyau Batuul tayi ba, matar ce ta ciro mata kayanta a closet ďinta da takalmi da duk abinda zata buk'ata, matar ce ta taimaka mata ta saka kayan, dogon gown ne bak'i, mai buďaďďan k'asa, wani gold plated pendant da chain ďinshi matar ta saka mata a wuya na montinè da agogonshi sai pin earing da matching bracelet ďin sarkan, cashmere scarf bak'i mai golden crystals ta ďaura mata akai kamar turban, ga front hair ďinta da ya fito ya kwanta lub lub sai ya k'ara mata kyau, wani murmushi ta saka da taga kanta a mirror, ba k'aramin kyau tayi ba , takalmin karen kelly heel bak'i ta saka, a hankali take takawa har ta fito daga ďakin ta sauk'a k'asa, sai da Aunty tace Masha Allah da ta ganta , duk da Batuul bak'a ce bata kai sauran y'an gidan haske ba amma ta fisu kyau, Baba ne yace "Mamana kinyi kyau" da murmushinta mai kyau tace "nagode Baa", break fast sukayi dukkansu sunsa kaya sunyi kyau, matar da tayi mata makeup ďince ta sauk'o ta mik'o mata clutch bag ďinta shima golden shima na karen sannan tayi musu sallama, k'arfe tara da rabi suka isa international conference center inda venue graduation ďin yake, tun daga waje manyan motoci ke a pake, k'arasawa sukayi ciki, decoration ďin wajen yayi kyau kalan graduation gown ďinsu ne purple and blue, sai da suka shiga ta saka graduation gown ďinta da hula, side ďin da aka tanadawa graduants ďin tabi, kujeranta ta nufa seat number twelve, Affan ne daga hagunta sai na Farida daga gefen Affan, tambaynshi tayi Farida bata k'araso ba, bai bata ansa ba ,Affan ne ya dubeta bayan ta zauna, mitsitsika idonshi yayi sannan yace "sorry this is my best friend's seat, can you kindly move to the next seat", dariya tayi ta ďan dugure mishi kai tace "Allah ya shiryaka Affan, in best friend ďin taka tazo sai in tashi", dariya shima ya saka yace "Besty you look gorgeous, i mean i cant say how much beautiful you look, am gonna miss you", ya fara share hawayen k'arya, dariya ma ya bata tace mishi "Farida fa, she isnt here....."bata k'arasa maganan ba ta ciro wayanta kenan zata k'irata taji bugun zuciyanta ya k'aru, a zuciyanta tace "No no, not today, let me be happy its my day" sannan ta fara ambaton Innalillahi wa inna illaihi rajiun, tana cikin addu'a taga Farida tazo kusa da Affan ta zauna, da harara tabi Farida da ido, Affan ne ya kare Farida da hannunshi yacewa Batuul "wannan kallo haka ai sai ta ji tsoro, babe ya akayi kikayi latti, i was waiting for you here all alone", ajiyan zuciya Batuul tayi tace "baza ku gane waye Yaa Abu ba, wai fa girlfriend ďinshi ce mukaje ďauka shine take b'ata mana lokaci tana ta wani abu kamar yarinya,ni shima nake tausayi ansa aurensu nan da three weeks, ya mayi ya bar mana gida mu samu mu huta", dariya Affan yasa yace mata "babe you are too much", lets concentrate on what we are here for, suka maida hankali kan speech ďin da VP ďinsu keyi, ita dai Batuul kawai tayi shiru ne amma bugun zuciyanta k'aruwa yayi dan har hawaye ya fara taruwa a idonta 💖💝BATUUL💖💝 14 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Shiru hall ďin yayi ana sauraron speech ďin da VP keyi, da ta gama ne sauran members ďin High table ďin suma suka karb'i mic suna yiwa graduating students ďin Nasiha game da rayuwansu da kuma wanda zasu fara a university, sai da aka gama speech ne aka fara presenting su drama, deabate da wasu abubuwan, ana gamawa aka fara k'iran graduating students su karb'i certificates ďinsu,Batuul ce number Twelve, Mc na cewa Fatima Kashim Goni , hall ďin ne ya cika da ihu bayan Batuul ta mik'e, juniors ďinta ne ke ihun dan kirkinta da kuma taimako kowa ya santa a school ďin, hatta malamai sai da sukayi , ihun da aka sane ya sa Abutturab mamakin wacece wannan da ta samu applause haka, a hankali ta sauk'a daga kujeran da take ta k'arasa ta karb'i certificate ďinta daga hannun Vice President, a hankali tace mishi " Thank you Sir" sannan ta amsa bayan y'an hotuna da aka ďaukesu dashi ta koma inda sauran ke tsaye, haka aka ci gaba da k'iran sunayensu har sai da aka k'ira 67 students sannan aka yi musu standing ovation tareda tafa musu, a kan stage ďin kowannensu ya cire graduation cap ďinshi suka sa ihu sannan suka watsa su tare da faďin we made it,kowa kujeranshi ya koma bayan ovation ďin da akayi musu, lokacin ne aka fara presenting prizes, Best in further Physics goes to Affan Abba gana, tafi aka sa mishi, bai dawo ya zauna ba ya sakeji ance shine best in TD, haka ya sake karb'an building and cinstruction sai chemistry, Farida Ahmad Kyari aka k'ira best in Mathematics da Further Maths, sai Hamra Imam Imam best in biology, Maryam Ibrahim Tsoho best in Agric Abdul Azeez Abidemi ne best in Accounting and commerce, Sai da aka gama k'iran sunayensu aka ce best in Economics goes to Fatima Kashim Goni, tashi tayi taje ta karb'a da smile a fuskanta, bata k'arasa wajen zamanta ba aka sake cewa itace best in IRS, Government,Geography, English sai Arabic marketing da Food and Nutrition, tasowa akayi ana tayata dan baza ta iya ďauka ba, haka aka ci gaba da bata prizes har na neatest, punctual da most obedient, Dj ne ya kunna mata wakan stand up for the champion dan tafi k'owa karb'an prizes a wajen, Abutturab na daga zaune tunani ya fara wacece Fatiman nan, koma wacece Masha Allah tayi k'ok'ari, sai da ya sake ambaton sunan ne ya tuna da Kashim Goni ai Minister ne, lokacin ya tuna da ai Batuul ce, kwata kwata bai ganeta ba dan wani kyau tayi da tsawo saboda heel ďin dake k'afanta, Sadiq dake zaune gefenshine ya tab'a shi yace "Yaa Abu yarinyar nan is Genius, ga wani kyau da tayi bari mu fita sai na tambayeta yadda akayi tayi tsawo"ya faďa yana dariya, Abutturab bai kulashi ba illa wayarshi da ya ci gaba da dannawa, haka aka ci gaba da ocasion daga k'arshe aka rufe da addu'a, tun suna ciki suka fara selfie har suka fito waje, Kowa wajen family members ďinshi ya wuce, Baba Batuul ta fara rungumewa shi kuma yace mata "Mamana Allah yasa Albarka, Allah ya taimaka yasa kufi haka", daďi ya sata cewa Amin da sauri, wajen Aunty ta koma, da murmushin murna a fuskanta ta shafa kan Batuul tace "Sannun Batuul Allah yayi miki albarka, Allah yasa afi haka", Hotuna sukayi tayi dama sunxo da photo graphers ďinsu , duk y'an gidan sai da tabisu sukayi hotuna ďaya bayan ďaya sannan sukayi na Family, Affan ma sai da yazo dasu Maa sukayi hotuna, Farida ce tazo a guje tana k'iran sunan Batuul, ganin su Aunty yasa ta gaishesu, sukayi congratulating ďinta, cewa Batuul tayi kixo Ammah nata jiranki tun ďazu muyi pictures, taqi ayi wai sai kinxo, murmushi Batuul tayi tace "toh muje nima yanxu nake tunanin zuwa , tacewa Aunty zataje ta dawo, Aunty ce tace suma gasu nan zuwa wajen su Ammah ďin bari su gama gaisawa da mutane, suna juyawa zasu tafi ta rik'e hannun Farida da k'arfi, kallonta Farida tayi tace lafiya "I dont know y, but these days i use to feel restless kuma heart beat ďina na increasing", Farida da damuwa a fuskanta tace "Dont worry kiyi addu'a, we will talk about it later", k'arasawa wajen su Ammah sukayi, y'an gidansu Farida ne a wajen sai sai wata farar yarinya daga gefen Abu, sai wani da bata sani ba, bata kalli gefen da Abu yake ba ta je wajen Ammah ta rungemta," janyeta Ammah tayi ta dubeta tace "useki Bitti, Masha Allah, Allah bariki", murmushi tayi ta tace "Amin Ammah", juya wajen Abui tayi shima ya shafa kanta yayi mata addu'a, Juyawa tayi ta dubi Sadiq da Massa da suke a tare tace Yaa Sadie "ina wun", smirking yayi yace "Batuul wannan tsayi da kika k'ara ai har nima kin fini, ban ma ganeki ba, ni kai har yanxu banma yadda ke bace", da murmushinta mai kyau tace "Yaa Sadiq u are just too much, kome na saka ai bazan fika tsayi ba", yace mata "gashinan kin kamo hanya", dariya tasa sannan yace mata "congrats Batuul, we are proud of you, keep it up", murmushi tasa sannan tace "Thank you Yaa Sadiq", mutumin dake tsaye da Sadiq tacewa "ina wuni", da murmushi yace "Lafiya kalau, congratulations, kinyi k'ok'ari sosai, Allah ya bada sa'a", duk da bata san ko waye shi ba amma addu'an da yayi mata yasa ya burgeta, da murmushi tace "Nagode In sha Allah", Abutturab na daga gefe shida Ajiddeh sai zuba take mishi, Ammah ce tace bakayi congratulating Batuul ba, Idonshi ya sauk'e k'asa yace "ai mun haďu nayi congratulating ďinta" dan shi har yanxu ya kasa yadda Batuul ce, da mamaki Batuul ta ďago ta dubeshi duk da yadda zuciyanta ke bugawa dan tasan bai yi congratulating ďinta ba amma yacewa Ammah wai yayi, tana ďaga kanta suka haďa ido, sauri tayi ta ďauke nata dan brown hazel eyes ďinshi na sata taji wani iri, matar dake gefenshi fara siririya tacewa "ina wuni", kamar baza ta amsa ba har saida suka haďa ido da Ammah ne tace lafiya a dak'ile, duk da bata san Batuul ba, bata tab'a ganinta ba amma sai da taji bata sonta, Ammah ce tace toh tunda kun gaisa sai ayi pictures, photo grapher ne yazo ya fara arranging yadda zasu tsaya, da Batuul na daga gefen Abui ita da Farida, cewa Batuul yayi ta dawo gefen Abutturab, Ajiddeh kuma ta koma daga gefen su Sadiq, ba dan taso akayi wannan canjin ba haka ta koma daga gefen su Sadiq, itako Batuul kamar bata ji shiba ta tsaya a inda take har sai da ya sake cewa "young madam ki dawo nan, ya nuna mata gefen Abutturab, a hankali take tafiya har tazo inda yake nuna mata ďin , rigarta ta kama daga k'asa tana cikwikuyewa, tsayawa tayi amma gaba ďauanta ji take kamar a kan k'aya take tsaye, tsayawan da tayi gefenshi ne ya sashi jin wani iri, so yake a gama hoton nan gaba ďaya ya bar wajen dan gaba ďayanshi wani iri yakeji, sai da mai hoto yayi clicking wajen talatin sannan ya tsaya, Ammah ce tace Abutturab ya tsaya suyi daga shi sai Batuul, ďago kanta tayi ta dubeshi taga shima ita yake kallo, maza tayi ta ďauke kanta ta k'ara damke riganta da k'arfi har hannunta na gumi, hawaye ne ke shirin fitowa daga idonta dan gaba ďaya a tsorace take, tsayuwa suka dukkansu biyun dan babu yadda suka iya, mai hoton ne yace Abutturab ya ďan matsa kusa da Batuul, matsawa yayi dan so yake aka gama wannan photo session ďin da ta sasu yi, tana ganin ya matso itama ta mata da baya, ysayawa yayi ranshi a b'ace yana kallonta, hannunta ya kama ya jawota har saida ta kusa faďawa jikinshi, ido ta wara ta bishi dashi taga bama ya kallonta, su Ammah ta juya ta gani taga hankalinsu ma baya kansu, wannan farar matar ce kawai taga ta k'ura musu ido tana kallonsu, da Batuul ta kalleta ne ta bita da harara, kanta ta ďauke daga duban matar ta tsaya har pg ya gama snapping ďinsu, yana gamwa su Aunty suka iso, bayan sun gaggaisa aka sake sabon photo session, Ajiddeh kam k'in shiga tayi wai flash ďin na reflecting idonta yana sa mata ciwon kai, suna gamawa Batuul da Farida sukace zasuje suyi pictures da friends ďinsu, Affan suka fara haďuwa da a garden ďin school ďin yana ganinsu ya cewa Batuul "Best friend i will miss, i dont know how i will start over without you, you have been there for me through good and bad times all these six years..." bai k'arasa maganan ba kukan da take ta mak'alewa tun safe ya fito, da gudu taje tayi mishi bear hug tace "Affan i will miss you more, how you always make me laugh, how you make me waffles every week end night, kuma har yanxu ban koya ba, Affan muje Uk tare kaji sai kaci gaba da koyamin,i will miss everything about you", tana buďe idonta dake rufe zata janye daga rik'on da yayi mata taga Abutturab a tsaye daga gefe ya zubo mata hazel like eyes ďinshi yana hararanta, kamar ma waya yakeyi amma ya kasa ci gaba da wayan sai tsayawa da yayi yana kallon inda suke, idonta ta ďauke taci gaba da magananta tace "zan faďawa Maa ma kar a kaika cyprus a bari muje Uk tare" Farida da ta tsaya daga gefe tana share hawaye dan sun bata tausayi duk da itama tana tausayin kanta na rabuwa da masoyinta amma tasan shak'uwan Affan da Batuul daban ne, ce musu tayi "you guyz there, kun tsaya kuna ta kuka and you are making me an emotional fool here, wont anyone give me a hug", hannayensu suka buďe mata taje itama ta rungumesu, Affan ne yayi k'arfin hali dan shima sun kusa sashi kukan yace musu "its okay, am always the man, just give a call and i will be there right away", murmushi sukayi a tare suka ce mishi "The man", haka sukaci gaba da hiransu sannan suka gyara fuskokinsu suka je inda sauran abokanensu suke sukayi hotuna, K'arfe 1:30 kowa yayi shirin watsewa, Farida ce tacewa Batuul "muje gidanmu sai daga nan mu tafi prom ďin daga nan it will be easier ko", Shiru Batuul tayi sannan tace " okay muje mu faďawa su Aunty sai su turomin kayana gidanku, wajen Aunty Batuul taje ta faďa mata komai sannan tace okay kuje sai Baa Liman yazo miki da kayanki, mota su Aunty suka ahiga suka tafi , wajen dasu Ammah suke suka k'arasa taga su Ammah ma basa nan daga Abutturab sai wannan farar matar ta zauna daga gaban mota tana ta kumbure kumbure, hango su yayi yabi Farida da harara yace "ina kika tsaya inata k'iran wayanki bakya recieving", ce mishi tayi Yaa Abu a silent wayan yake, banji bane" Batuul ce a ranta addu'a take Allah yasa ba dashi zasu tafi ba, da ta sani da kawai su Aunty tabi in yaso daga baya a kawota, da taga Farida ta buďe k'ofan baya ta shiga ne yasa itama ta buďe ta shiga, tana zama ďaga kan da zatayi suka haďa ido da Abutturab, harara ya sakar mata tayi saurin ďauke kanta sannan yaja mota suka fita daga wajen 💖💝BATUUL💖💝 15 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Sau biyu idonsu na haďuwa ta rear mirror da Batuul tana saurin ďaukewa, daga k'arshe komawa tayi gefe owners corner yadda baza ta na kallonshi ba, ita da tasan shi zata bi ma baza ta bari y'an gidansu su tafi ba, ga wannan heart beat ďin da yaqi barinta kamar heart na shirin fitowa, gaba ďaya ma ita she is not comfortable, Ajiddeh ya duba yaga tana ta fushi, rage volume ďin music yayi sannan ya kallota a hankali yace "Babe meye ne kike ta b'ata rai", zumb'uro bakinta ta sakeyi ta juyar da kanta ga kallon window, bai sake bi ta kanta ba yaci gaba da tuk'in shi cikin kwanciyar hankali har suka isa wuse II, gaban wani tangamemen gate ya tsaya yayi horn, mai gadi ne ya buďe mishi ya sa kai ya shiga, yana shiga ya nemi waje yayi parking, Ajiddeh ce ta fito daga motan shima ya bita suka fita a tare, zagayawa yayi ta b'angarenta yayi mata magana, "wai fushin mey kike yi ne haka, tun a wajen event ďin naga kina ta b'ata rai bayan kuma lafiya muka fito", ce mishi tayi yarinyar nan wacece, meye haďinka da ita da har za a ce kuyi snapping picture daga kai har ita sannan taqi bin motar gidansu sai naku", juyawa yayi ya dubi motar ya kalli Batuul dake danna waya kanta sunkuye, side view ďinta ake gani da lashes ďinta da suka kwanta, kallon da taga yana yiwa Batuul ne ya sata cewa "Aliyu da kai fa nake magana", juyowa yayi yace mata "she is my cousin", kallon mamaki ta bishi dashi dan tasan almost duka cousin ďinshi, beside ai taga yarinyar y'ar minister ce kuma bai tab'a ce mata minister ďan uwansu bane, cikin rashin yadda tace "Aliyu baka tab'a ce min a cousins ďinka akwai yarinyar nan ba, ni gaba ďaya naji bana sonta" ce mata yayi "well there is a first time for everything, yau kin santa", shi da kanshi mamakin kanshi yayi, why did he lie, mey sa yace Batuul cousin ďinshi ce bayan ba haka abun yake ba, ce mishi ta sake "Fine naji, but duk cousins ďinka i like her least, infact i dislike her", da mamaki ya dubet yace "contro, ki tuna da wanda kike magana, i told you she is my family and you are telling it to my face that you dont like her, kar ki manta we are getting married next three weeks, you cant just disregard duk wanda kika ga dama", ranshi da ta gani ya b'aci ne sosai yasa tace "Baby am sorry, i dunno, am just pessimistic about her, i have this negative feelingl, haushi ta bashi yace mata "naji am going, we will talk later", tunda ya shiga mota take tsaye a wajen, tasan halinshi baya son wasa, bare in ranshi ya b'aci, yanxun ma haka tasan sai tayi dagaske zata shawo kanshi, yadda ya figi motan ne kamar mai shirin tashi sama ya fita daga gate ďin gidan, ya tsorata su Batuul ba kaďan ba, maza maza ta jawo seat belt zata saka kenan suka haďa ido, wani kallo ya sakar mata tayi saurin sauk'e kanta a sanyaye, a ranta faďi tayi "kai ka sani, haka kawai kayi ta b'ata rai kana b'atawa kanka rai, ai matar ma da zata aureka ina tausayamata", Farida ce ta matso kusa da Batuul tace cikin raďa "yaje ta b'ata mishi rai shine zaizo ya sauk'e a kanmu, ai kaďan ma ya gani sai ya aureta, dan da gani wannan babu abinda ta iya sai kwalliya, mu dai kar yaje ya zubar da mu", murmushi Batuul tayi tace "kai Farida ke dai , nidai babu ruwana", a wani brake sukaji yaja a gefen titi, tare suka ďago suka dubeshi dan suga abinda ya faru dan su suna ma ce hatsari akayi, ganin da sukayi lafiya yasa su ajiyar zuciya, cikin dakewar murya yace "ďaya ta dawo gaba", a tare suka ďago suka dubi junansu, Farida ce tayi saurin cewa "Batuul kije gaba", a razane Batuul ta kalli Farida, a ranta cewa tayi "Farida are you sick, ya za ayi kice inje gba", ce mata tayi " No am okay here ke kije", cewa Farida tayi kinga ni am by d road, kuma highway ne its risky in buďe k'ofa.....", bai bari ta k'atasa magana ba yayi magana cikin tsawa yace "kuna b'ata min lokaci, ďaya ta dawo gaba, ba driver ďinku bane ni", buďe k'ofan Batuul tayi ta koma front seat dan ta tsani ihu, tana shiga ya figi motar da k'arfi, sauk'e kanta tayi ta sa a tsakanin cinyoyinta dan k'amshin turarenshi ya isheta ta bugun da zuciyarta keyi, kallon ta yayi ta gefen ido yaga ko she is fine sannan ya k'arasa dasu gida K'arfe uku saura suka isa gida , Suna shiga gida bayan yayi parking suka buďe k'ofofin suka fita, har sunje bakin corridor taji yana cewa "keh", tsayawa tayi taqi juyowa dan tasan sunanta ba keh ba kuma tasan yassn sunanta, saida taji yace waye zai rufe miki k'ofa sannan ta tuna ashe bata rufe mishi k'ofa ba, komawa tayi taje ta tura k'ofan sannan ta dawo ta shiga, A falo ta tarar da Ammah da Sadiq, Ammah ce tace "Batuul kuda zakuyi shirin fita mey kuka tsaya yi, ai da kunyi sauri kun dawo yunda kuna da abun yi", Farida ce tayi maza tace "Ai Yaa Abu ne ya tsayar damu sai da muka kai Ajiddeh gidansu ya tsaya suna ta hir.....", bata k'arasa ba ya shigo da sallama, Ammah akwai yacewa sannu da hutawa yabi Farida da harara ya wuce ďakinshi, basu zauna a falo ba suka haura sama dan basuyi azahar ba, Farida ce ta fara shiga toilet bayan ta cire kayan jikinta tayi wanka tayi alwala ta fito, tunani Batuul ta zauna yi na mesa ma ta yadda da idea Farida na zuwa gidansu bayan akwai wannan masifaffen, bata san lokacin da Farida ta fito ba sai ji tayi ta tab'ata, a ďan tsorace ta juyk tace "hell you scared me", dariya Farida tayi tace "sarkin tsoro, tunanin mey kikeyi", mik'ewa tayi daga kan gado ta fara cire kayanta itama zata shiga toilet da murmushinta na tsokana tacewa Farida "My charming prince", da gudu Farida ta janyota suka zauna a kan gadon a tare tace "Omg, i have been waiting for this moment, bari in k'ira Affan in faďa mishi, tell me about him dan Allah, dogone, fari ne, is he handsome, shekarunshi nawa, ďan inane", dariya Batuul tasa bata barta ta k'atasa tambayoyinta ba tace "I live for you Riri", mik'ewa tayi zata tafi , tayi sauri ta sake janyota tace "Batuul dagaske nake ki faďamin waye shi, finally mun same shi", ce mata Batuul tayi "wasa fa nake miki Farida, ai in zai zo you will b first to know tun ban zauna tunaninshi ba", tsaki Farida taja ta saketa tace "ke dai positive vibe killer ce Allah, ni ban sani ba ko 18 birthday ďinki kike jira kiyi legalizing boyfriend ba", "You still love me", sannan ta shige toilet da murmushi a fuskanta, tana fitowa ta tarar da Farida tana Sallah, itama doguwar riga mara nauyi tasa ta saka hijab ta tada sallah, basu fito ba sai da suka jira aka k'ira la'asar sukayi suka fito, ďan kwali kawai ta ďaura, shima bai rufe duka gashinta ba, irin square scarf ďinnan tayi triangle dashi , dinning suka nufa zasu ci abinci dan rabonsu da abinci tun breakfast, tafiya kawai Batuul takeyi amma ta gaji da bugun zuciyan nan nata dake k'aruwa all the time, addu'a kawai tayi ta ci gaba da tafiya, suna isa dinning suka ga Yaa Abu a kan kujera yana cin abinci hankalinshi kwance, wani irin kallo ya bita dashi ganin gashinta da ya kwanta a kafaďunta har sai da taji wani iri ,kujera Farida ta ja ta zauna, Batuul juyawa tayi zata koma sama dan baza ta iya zama inda yake taci abinci ba ga gashinta da yake a buďe, Ammah ce ta fito daga kitchen ta ganta a tsaye, ce mata tayi "Zauna mana bitti kici abinci, kujeran dake facing Abutturab ta nuna mata, jiki a sanyaye taja kujeran ta zauna, kasa tab'a komai tayi sai da Ammah ta sake mata magana, plate ďaya ta ďauka ta jawo food flask ďaya taga pasta ne a ciki, mayarwa tayi ta ďauko wani, duk abin nan da takeyi in ta ďaga idonta sai sunyi ido huďu dashi, ďayan ne da ta ďauka taga shinkafa a ciki, kaďanta ďiba ta zuba a plate ta janyo bowl ďin salad shima ta ďan saka kaďan, a hankali take ci dan a takure take, hannunta na hagu ta ďago zata mayar da gashinta dake buďe, tana ďaga ido idanunsu suka sake locking, bugun zuciyantane ya k'aru da k'arfi har saida hawaye ya taru a idonta, hawayen da ya gani yana shirin zubowa ya sashi yin tsaki ya mik'e, ido Farida ta bishi dashi tana tab'e baki a ranta tace "masifaffe ko mey aka mishi kuma yanxu yana cin abinci ma sai yayi faďa", Batuul ta duba taga kanta a sunkuye, bata yi tunanin komai ba dan tasan haka cin abinci Batuul yake a hankali, k'ok'artawa Batuul tayi ta mayar da hawayen sannan tayi ajiyan zuciya ta fara cin abincinta K'arfe 6:30 mai shiryasu for prom tazo, sama suka hau da ita ďakin Farida, tunawa sukayi da ba a kawo kayan Batuul ba, ďakin Ammah taje ta faďa mata ta sameta tana waya, sai da ta jira ta gama waya sannan tace mata "Ammah har yanxu fa ba a kawo kayan Batuul ba kuma tana ta k'iran wayan Aunty not reachable", da damuwa a fuskanta ta tashi tace "toh muje in duba in Sadiq na nan ya kaita ta ďauko ke kuma sai ayi miki kamin su dawo ko" wayan Sadiq ta k'ira yace mata baya gida, driver kuma sun fita da Abui, k'asa suka sauk'o , Abutturab ta gani a palo da remote a hannunshi yana kallon Fast8 a MNET, wajenshi ta k'araso tace "Abu, zaka kai Batuul gida ta ďauko abu, tayi mantuwa ne", tsayawa processing wacece Batuul yayi dan yasan babu Batuul a gidan, sai da tace mishi "kana jina", ce mata Yayi "k'awar Farida ko, Ammah babu wanda zai kaita ne, ina drivers ďin gidannan, ni yanxu ma nake shirin fita", ce mishi tayi "ai sai ka kaita ka dawo sai ka wuce inda zaka ďin", ba dan ranshi yaso ba yace a ce mata ta fito, Farida ce ta koma sama a guje tace mata ta fito za a kaita su ďauko, cikin hanzari ta tashi ta ďauki hijab ta saka suka sauk'o k'asa a tare, Ammah ce tace mata "Bitti maza kije ku dawo da sauri", da toh ta amsa mata ba tare da tasan waye mai kaitan ba, parking space taje taga babu alamun motan da akwai mutum, horn taji daga gefe, anyi wining glass ďin ďayan side ďin k'asa, wajen wannan motan ta k'arasa , tana ganin Abutturab ne a ciki tace "innalillahi wa inna illaihi rajiun" a fili, "Yaa Abu da kai zamu tafi", mamakin salatin da tayi ya tsaya yi kamar na taga wani mugun abu, bai ce mata komai ba ya sa hannu ya buďe mata k'ofa , jiki a sanyaye ta shiga ta zauna, tun kamin ya tada motan yace mata "inane gidan", ce mishi tayi Gwarinpa, Tai Solarin crescent", bai ce komai ba ya tada suka fita daga gidan suka ďau hanyan Gwarinpa 💖💝BATUUL💖💝 16 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Suna shiga Tai solarin crescent gidansu ne na uku by the right, maza tayi ta nuna mishi dan sun kusa wucewa, dan tsaki ya ja ya danna horn aka buďe musu suka shiga lokacin 6:50, fitowa tayi daga motan ba tare da tace mishi komai ba, shima fitowa ya bi ta da kallo yace "Dake ni drivern ki ne shi sa c'mon sense din ki bae nuna maki ki bude baki kiyi godiya ba koh" bae jira cewarta ba ya nufi masallacin dake jikin gidan don yin sallahn magriba, tsaki batuul ta ja ta kama hanyar shiga gida a xuciyarta tana cewa ae ba ni nace ka maido ni ba dae, shi kam yana zuwa bakin gate ya haďu da k'annen Batuul sun idar da sallah xa su shigo gida, gaisheshi sukayi ya amsa musu da smile a fuskarsa ya k'arasa masallaci, Batuul na shiga ta wuce ďakin Aunty, a kan sallaya ta tarar da ita tana sallah, jiranta tayi sai da ta idar tayi azkars ďinta sannan ta juya ta dubi Batuul, ce mata tayi " tun ďazu fa Batuul na aiki Baa Liman ya kai miki kayan shine ya fita ya dawo nace yaje yace shi ya manta ma sam da aiken, kuma Baba na nemanshi a office, yanxu nake jiran Ahmad ya shigo ya kai miki wllh, cewa Aunty tayi "Ammah ce tace a kawoni dan har mai make up tazo" mik'ewa tayi tace bari inje in ďauki kayan, Aunty ce tace mata mu sauk'a k'asa ai kayan ma suna can ba a hawo dasu sama ba , k'asa suka sauk'a suka k'arasa parlour, akwati ne mai kyau purple da bak'i na victoria's secret ajiye daga gefe, akwatin ta k'arasa ta ďauka sannan suka fito waje tare da Aunty, "Batuul banda rawan kai a wajen don Allah ki kama kanki, event ďin dare in banda ma na gama makarantane da bazan bari kije ba, kuma duk inda 10:30 tayi ku dawo gida keda Faridan, ku kula da kanku", "In sha Allah Aunty zamu kiyaye" a tare suka fito compound ďin gidan da Anty, daga gefen gidan k'ark'ashin wani rumfa na bunu mai kyau da hasken wuta ya haska da farin florescent suka hango su Ahmad suna tennis, tsayawa Batuul tayi taga mutumin dake tare da k'annen nata ya rungume hannayensa yana kallon ynda suke buga tennis din with interest murmushi dauke fuskarsa, bata tab'a ganinshi yana murmushi ba sai yau, mamaki ne ya sata tsayawa dan tana ce ma ya tafi, Aunty ce tace "ba Abutturab bane wannan ko shi ya kawoki dama", juyawa tayi ta dubi Aunty tace "Eh shi ya kawoni" Anty tace "Batuul shine kika barshi a waje ko ruwa ba a kawo mishi ba, ke kam wace irin yarinya ce", cewa tayi "Aunty ban san zai tsaya ya mai dani ba", ganin Aunty da yayi ne yasa shi k'arasowa wajensu, a nutse yace "Aunty ina wuni", da murmushi ta amsa da "lafiya Abutturab, ya gida, mun saka aiki ko, ai bansan kana waje ba da an kawo maka ruwa", murmushi yayi yace "a ah Aunty ba komai, ai ba aiki bane, kuma inaga bata san bn tafi ba," ya k'arashe maganan yana kallon Batuul, k'in ďago kanta tayi sai da ya dena kallonta ta ďago, Aunty ce tace "toh maza kuje Batuul karki b'ata mishi lokaci, Allah ya kiyaye", tafiya sukayi suka isa inda motar ke pake bayan yyi ma Anty sallama, buďewa tayi ta saka akwatin nata daga baya bayan ya buďe da controller hannunshi sannan ta koma gidan gaba ta shiga shima ya shiga ya tada suka tafi, dan tsaki ya ja can kasa a xuciyarta yace " Was i even suppose to wait for her" haushin kansa ya ji ssae, ko da yake wasan da kanninta ke yi ya tsaya kallo, yyi assuring kansa, babu wanda ya cewa kowa komai sai wak'an dake playing. K'arfe 7:20 suka isa gidansu Farida, sauk'a tayi bayan yayi pakin ta zagaya ta ďauko akwatin ta, tunawa da abinda yace mata daxu yasa ta hade rae tace "Na gode" ko kallonta bae yi ba ta ja akwatin ta ta yi gaba, yadda take jan akwatin ya gani kamar ta ďauki wani abun mai girma, ďauke kanshi yayi tare da jan tsaki har yazo ya wuceta ya shiga cikin gida, bayan shiganshi da minti biyu ta shigo janye da akwatin, mai aikinsu Farida, Fanne ce ta k'araso inda take ta karb'i akwatin tace mata "sannu", da mrmushi ďauke a fuskanta tace "yawwa Fanne na gode", sannan suka hau sama, ďakin Farida suka shiga suka sami Farida an mata kwalliya tayi kyau sosai, blue English gown ta saka da black accessories, tayi kyau ba kaďan ba kasancewarta fara, "Masha Allah kinyi kyau Riri" inji Batuul, murmushi tayi haďe da batting lashes ďinta tace "yeah i know", bata bi ta kanta ba ta wuce toilet tana dariyan ansa da Faridan ta bata, ruwa ta watsa sharp sharp, ta fito tana tsane ruwan jikinta da towel, mai ta shafa da sauri tazo ta zauna a gaban mai makeup ďin, kayanta ta fara taimaka mata ta saka, red fench floral gown, sannan ta fara mata make up, red matte lipstick ta shafa mata, sosai Batuul tayi kyau, sai da ta gama da fuska sannan ta saka mata accessories ďinta silver sai red agogo, gashinta ta gyara mata ya kwanto daga gefe, k'asan yayi curls, ba kaďan ba Batuul tayi kyau, k'arfe takwas da sha huďu suka fito daga ďakin sukayi ďakin Ammah, tana ganinsu tace "Masha Allah kunyi kyau", a kunyace Batuul ta amsa tace "mun gode", k'asa suka sauk'o suna jiran mai kaisu yazo, Abutturab ne ya sauk'o daga stairs har ya canja kayan dake jikinsa ya saka ralph lauren shirt da blue sweats, k'afanshi sanye da slippers ďin Fenty, hanyan waje yabi zai fita ba tare da ya kalli palon ba rike da makullin motarsa, mabuďi k'ofan ya buďe zai fita yaji Amma na cewa "Abuu, don Allah ga su Farida nan zaka ajiyesu a Tulip bistro, tunda kai ma fita xaka yi, 8 ma ya kamata su tafi amma yanxu har 8:30, kuma bana so suyi driving da kansu, dare yayi", bai juyo ba saida yaji ta gama, shi bai ma san mey zai cewa Ammah ba, amma ransa yyi mugun baci, wato dae ysu shi ya xama drivern wa ennan yaran, cewa kawai yayi "toh" snn ya sa kai ya fita kmr xae tashi sama, tashi sukayi suka bi bayanshi, har bakin k'ofa Ammah ta rakasu tace musu kar suyi dare kamar yadda Aunty ta faďawa Batuul, hasken dake filin gidan ne ya haska Batuul, sai ya k'arawa accessories ďin jikinta glitters, ďago kanshi yayi zai duba ko sun fito idanunshi suka sauk'a kan Batuul, tsayawa yayi yana kallonta da gashinta da yasha gyara sosai iska na swaying ďinshi, yadda take tafiya yake kallo a hankali kamar baza ta k'araso inda motar take ba, wani takaici ya turnuke shi ya danna horn da karfi, Farida ce ta fara zuwa, shiga motan tayi ta zauna a gidan baya, ganin babu yadda Batuul ta iyane yasa ta shiga gaba dan ďazu ma ce musu yayi shi ba driver ďinsu bane, k'anshin turaren Batuul ya nuna mishi cewa ta iso, ya dubesu su biyun ya daka masu tsawa yace "ina kuke tunanin zan kaiku haka da gashi a buďe kmr wasu mahaukata, ku fice min a mota kuje ku rufe kanku kuma kar wacce ta b'ata min lokaci, it seems kuna wasa da ni ne yau, duk gidan nn a rasa Wanda xae dinga yawo da ku a mota sae ni", Farida ce ta b'ata rai tace Yaa Abu toh Ammah ma bata ce komai bafa, kuma ma ai baza mu daďe ba", harara ya jefa mata ta mirror ba shiri ta bude mota ta fita da sauri, Batuul dai batace komai ba dan ranta ya gama b'aci saura kaďan tayi kuka , ta buďe k'ofa zata fita ita ma Farida tace "bari in dauko mana" hkn yasa ta koma ta xauna, kafin farida ta dawo Abuturrab ya ja tsaki fiye da sau goma, ita dae Batuul kanta na kasa sae wasa take da xoben hannunta, Farida na dawowa ta mi'kawa Batuul k'aramin jan gyale ita kuma bak'i, suna yafawa yaja motar suka tafi, hanyan Tulip suka bi, sai da ya tsayar da motan ya ce musu "duk iskancin da xa kuyi ku tabbatar by ten kun gama" Farida ta dan turo baki ta amsa mishi da "okay" suka fita daga motan suka shiga Cikin hall ďin event ďin, wajen ya haďu sosai kowane table kujerun mutum biyu ne da sunayensu a jikin kujerun, Runtown ne akan stage yake wak'anshi na Mad over you, anata ihu, Affan da Farida kujeransu ďaya , kujeran Batuul ne kawai ita kaďai, sai kuma na waďanda suka je wajen rawa, suna zaune ana ta yin abubuwa har aka iso lokacin bada award, Batuul ce ta cinye cutest da most classy, Farida most beautiful, Affan kuma Ladies Man, bayan an gama raba sauran awards ďin ne mutane suka hau wajen rawa. Gidansu Massa Abutturab yaje, sai da ya fara shiga cikin gida , Maman Massa ya tarar zagaye da mutane a falonta da ma'aikatan gidan, gaishe shi suka farayi tun daga bakin k'ofa, k'arasa yayi ya tsuguna dab da k'afanta yace mata "Yaa Mera nda dubdo"(ina wuni Yaa Mera), kanshi ta shafa tace "Baanyi wushe" (lafiya Babana), ya shirye shiye", shi ya manta ma gaba ďaya da aurenshi nan da sati uku, sai da ya tuno shirye shiryen mey take nufi sannan yace "Alhamdulillah Yaa", "Masha Allah" tace sannan ya mik'e yace "bari in duba Massa Yaa", tace "toh Babana, sai ka fito", mik'ewa yayi ya tafi chamber Massa, tura k'ofar ďakin yayi ya shiga tare da sallama, su biyu ya gani a zaune suna playing game a tv, tsakin sallamar shi da basu amsa ba yayi, inda socket ďin ďakin yake ya wuce directly ya kashe, tsayawa sukayi suna kallonshi da mamakin yaushe ya shigo, Massa ne yace mishi "Man final tournament fa muke bugawa ka kashe", bai ce mishi komai ba sai da ya samu waje a kan gado ya zauna sannan yace "sai kace yara kun rik'e controller kuna ta game, nayi sallama babu wanda yayi responding a cikinku" ya sake jan k'aramin tsaki, a tare mazan Massa da ďayan suka dubi juna suka sa dariya, dubansu yayi yaga dariyan mey sukeyi sannan yace musu "abin yi ne baku da" ya ciro wayanshi daga Aljihu, ďayan ne ya koma daga gefen Abutturab yace mishi "ai gaskiya ka faďa, mu yara ne sosai ma, kai da zaka zama ango next few weeks ai kam ka zama babba", harara Abutturab ya jefa mishi yace " kuyi mana kuma auren, kun zauna kuna abun yara har ana yin sallama bakwa ji", Massa ne ya dubi wanda ke gefen Abutturab yace mishi "Abba faďa mishi ai jira muke manya su fara yi sai mu bisu a baya", dariya ma suka bashi yace "Ku kuka sani, mu munyi gaba", haka suka ci gaba da hira suna tsokananshi, sai 10:30 ya tuna da su Farida, mik'ewa yayi cikin hanzari yace "shit", binshi sukayi da ido suna so ya gaya musu abunda ya faru, kallonsu yayi yaga duk shi suke kallo , ce musu yayi "wlhy su Farida na kai wajen prom kuma nace by ten ya kamata in je na manta", Massa ne yayi maza yace "yawwa i wanted to ask you that girl, k'awar Farida ce ko, she is damn pretty, she is so densed, she is ....." , bai k'arasa ba Abutturab yace mishi "Hey meye hakan, k'awar Farida ce fa, yarinya ce fa kake cewa she is so densed, yarinyar da bata fi sixteen yrs ba", da ido suka bishi ganin bai tab'a shiga maganan y'an matansu ba, fita yayi daga ďakin bai ce musu komai ba A Tulip bistro yaje yayi parking, wayanshi ya ďauko yayi dialing number Farida ba a ďauka ba, sai da ya k'ira wajen sau goma ba a ďauka ba, buďe k'ofan motan yayi ya fita daga ciki ya shiga cikin hall ďin, fuska a tamke ya shiga hall ďin ya tarar ana ta hayaniya, Farida ya hango a kan stage ita da wasu friends ďinsu suna zazzaune a zagaye sunyi round suna playing truth or dare, rasa ya zai yi ya k'irata yayi dan ko yayi ihu ma baza taji ba, Batuul ya hango daga gefe ta zaune ita kaďai a kan kujera da awards a kan table ďin da take tana danna waya, deciding yayi kawai yaje yayi mata magana ta k'ira Farida su tafi, inda take ya k'arasa ya sunkuyo daidai kunnenta zai yi mata magana dan yasan ba lallai taji ba in ya tsaya yi mata maganan kuma bayason su b'ata mishi lokaci,k'anshin turaren da taji ne ya sata saurin ďagowa , heart beat ďinta ya k'aru, waigowa tayi da sauri suka kusa cin karo, zata mik'e ya sa hannu ya maida ta, tsayawa tayi tana kallonshi a tsorace, shima fuskanta ya tsaya kallo yadda lights ďin ke haska stones ďin jikinta sai ya k'ara mata kyau, lkci daya kuma ya hade rae, hannunta ta motsa alamar ya sake mata, sake mata hannunta yayi yace mata "Go and call your friend , ina jiranku a waje", juyawa yayi ya fita daga hall ďin, mik'ewa tayi bayan ya fita jiki a sanyaye ta isa inda Farida take tace mata "Yaa Abu na jiranmu a waje", fita Batuul tayi bayan tayi sallama da mutane ta isa inda motar ke pake, shiga tayi ta zauna daga baya, ta ďago idonta kenan zata ce mishi Farida na fitowa suka haďa ido huďu ta mirror, maza tayi ta ďauke nata tace mishi "tana fitowa" a hankali, Tare da Affan Farida suka fito kamar ka su rabu, sallama sukayi ta shige gaba dan horn ďin da Abu ya danna, direct gida ya wuce dasu, suna shiga gida suka wuce ďakin Ammah suka ga tayi bacci, a hankali suka jawo mata k'ofan suka wuce nasu, kayan jikinsu suka cire sukayi wanka, sukayi sallah isha, bayan sun ďanyi hiran event ďin yau suka kwanta bacci THREE WEEKS LATER A firgice Batuul ta tashi daga baccin da take tana ambaton sunan Allah..... 💖💝BATUUL💖💝 17 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* THREE WEEKS LATER A firgice Batuul ta tashi daga baccin da take tana ambaton sunan Allah(a uzu bikalimatillahi tammat, min sharri ma khalaq, bismillahi llazi la ya dduru ma'as mihi shay'un fil ard wa la fis sama'i wa huwal aliyul azim), zama tayi akan gadonta, gumin da ya tsatsaffo a fuskanta ta sa hannu ta goge, mamakin irin mafarkin da tayi yau tayi, tasan mafarkanta na tsoro basa wuce macizai amma na yau daban ne, mik'ewa tayi tabi hanyan toilet ta shiga, ruwa ta watsa tare alwala ta fito, hijab ďinta ta ďauka ta saka sannan ta shimfiďa abun sallah ta hau ta fara nafilfili, bayan ta idar sosai tayi addu'a Allah ya kare ta daga sharrin abun ji da na gani sannan ta ďauko Quraninta daga kan bedside drawer ta karanta, sai da ta gama karanta suratul Anbiya' da Hajj sannan ta duba agogo taga k'arfe biyar, zama tayi a kan abin sallah ta ci gaba da addu'o inta har aka tada sallah a masallaci ta mik'e tayi raka'ataynil fajr ,tayi sallah asuba, tana idarwa tayi azkars ďinta na safe sannan ta mik'e ta cire dogon hijab ďin dake jikinta ta ninke shi tare da abun sallah ta maidasu inda ta ďaukosu, gadonta ta koma ta kwanta, sai da tayi addu'a dan ta tsorata ďazu sosai sannan ta ja bargon ta rufe jikinta dashi ta kwanta, bata tashi ba sai sha biyu saura, ta mik'e taje tayi wanka ta saka wani riga da skirt k'arami mai kyau bata ďaura ďank kwalin kayan ba sai hula kawaj da ta saka a kanta, k'asa ta sauk'o bayan ta gama shafa mai, babu kowa a gidan, a ranta tace mayb mazan sun tafi ball ko tennis ďinsu na jaraba, Aunty da Yusra kuma na gidan biki, sai da taci abinci sannan ta koma palo ta ďau remote ta canja favorite tashar ta star plus, mik'ewa tayi ta koma sama dubo wayanta, missed calls uku ta gani, ďaya na Aunty biyu na Farida, Aunty ta fara k'ira, tana ďauka tace "Hello Batuul, mun fito kina bacci, ki shirya a kawoki gidan bikin , Farida ma na ta tambayanki", sai da Aunty ta gama tace "Aunty kaina ke ciwo tun da na tashi, bana son zuwa saboda hayaniya", da damu Aunty ta ce mata "kinsha magani Batuul", "eh", tace sannan ta ce mata "ki kula da kanki sai mun dawo, zan k'ira su Janet a waya in faďa musu suna dubaki sannan suka katse wayan", suna gamawa tayi dialing number Farida, Farida na ďauka tace "wane irin bacci kikeyi haka har na k'ira twice bakiyi picking ba", ce mata tayi "wayan fa yana ďaki ni kuma ina k'asa, toh meye ma na k'irana da sassafe , ke da ake hidima a gidanku", "ai hidiman ne ya sani k'iranki, wlhy gidan ya cika da mutane , babu daďi, am coming over to your place", kamin Batuul ta sake magana ta katse wayan, A Protea hotel dake asokoro suke zaune, vip apartment suka kamawa abokanansu da suka zo ďaurin aure, hira suke ana ta tsokanan ango, bai ce musu komai, kanshi ya dafa ya rik'e da k'arfi dan wani ciwo yake mishi sosai kamar zai rabe, wayanshi ya ďaga ya k'irawo Massa dake cikin sauran abokan nasu, ďagowa Massa yayi yaga mesa yake k'iranshi bayan suna zaune a tare, ganin ya rik'e kanshi ne ya sashi tashi ya isa wajenshi, tambayanshi yayi bayan ya rik'e hannunshi da ya rik'e kan nashi dashi "Aliyu lafiya naga ka rik'e kanka, meke damunka", a hankali yace mishi ka kaini gida kaina na ciwo", tare da mikvewa yayi hanyan k'ofa, binshi Massa yayi a baya yace "toh ai gidanku ma da hayaniya, muje in munga doctor sai mu wuce gidanmu ka kwanta, stress ne yayi maka yawa", sai da suka je bakin k'ofa Abba ya ce ina "ina kuma angon zai tafi, tun ďazu yake b'ata rai yayi shiru yana ta tunani, saura fa kaďan ka k'ara hak'uri mun kawo maka ita", sauran ne suka sa dariya suka ci gaba da shak'iyancinsu, Massa ne ya dubesu yace "am sorry dan Allah zamuje mu dawo, Abba call me if ana needing wani abu", lokacin har Abutturab ya fita shima ya bishi a baya, sai da suka biya Nizamiye hospital aka duba shi aka yi mishi prescribing drugs sannan suka ďau hanyan gida, a hanya Massa yace mishi "Man i told you stress ne ke damunka, these days tunaninka ya cika yawa, mey ke damunka", Abutturab ne yace mishi "kafi kowa sanin auren nan is a compromise, yes i like her but myself being married is just out of it", Massa bai ce mishi komai dan likita yace ya huta sosai so baya son ya dameshi dayawa, concentrating yayi a tuk'inshi har suka isa gida, a parlour chamber Massa ďin ya kwanta a ďaya daga cikin dogayen kujerun, Massa ne ya mik'o mishi maganin yasha ya sake kwanciya, tambayanshi yayi "in faďawa su Ammah baka ji daďi bane ko kuma ya za ayi", hannu ya ďaga mishi alaman a ah sannan yace mishi "yanxu Ammah zata tada hankalinta a kan ďan wannan abun, i will get better before event ďin yau", ya sake juyawa ya kwanta ďaya bangaren nashi, wutan ďakin Massa ya rage mishi yace sannan ya fita Batuul bata fi minti talatin da waya da Farida ba sai gata a gidan, mik'ewa tayi daga kwancen da take ta ce mata "woh Farida , you can be in planet Mars ke ďinnan, yaushe mukayi waya dake da har zakice min kin iso", dariya Farida tasa tace "toh ai ni ďin kenan", zuwa tayi ta zube a kan kujera tace, "kinga gidanmu kuwa, ba ni akewa aure ba amma nafi masu aure wahala, hatta ďakina ya zama ba nawa ba, gaba ďaya gidan ya zama wani iri, jiya ma sai a wajen Abui na kwana, bazan iya ba, ga y'an Ndjamena nan da sa mutane aiki kamar babu y'an aiki a gidan", dariya maganan ya bawa Batuul tace "Lazy you, toh dama ai hakane if ana biki a gidanku sai kayi hak'uri, baki da k'anne da anyi suna a gidanku tun lokacin zaki gane yadda abun yake, lokacin sunan Aabid fa har cubicle ďin toilet ďina sai da aka fasa, bare naku biki, bikin ma na first child ďin gidanku ai sai hankali", ce mata Farida tayi "as in baza ki gane ba, toh aiken kuma na meye, ni ďaurin auren nan da zasu tafi maiduguri ma ya fi min komai daďi, su tafi gidan ya kima normal", "ai ba matan bane zasu ďaurin aure, maza ne zasuje a ďaura su dawo" inji Batuul, baki ta zumb'uro tace "ni dama auren Yaa Sadiq ne ma da sauk'i, amma Yaa Abu fa, ga matar ma ba shiri nake da ita, tayi ta wani girman mutum babu komai sai tsayi da fari, kina ganin duk tsayin Yaa Abu fa da kaďan ya fita, ni ďazu ma kamar naji Ammah na cewa wai a dawo da boxes ďin lefen da aka kai mata tunda sunce sunyi kaďan, 40 boxes fa wai sai an k'ara musu ya zama sixty, shine Ammah ma tacewa su Aunty Amna da suka kai su dawo dashi", girgiza kai Batuul tayi tace mata "ke dai kullum Yaa Abu, toh yanxu dai zai bar muku gidan", da sauri Farida ta mik'e daga zaunen da take tace "Ai ni daďin da nakeji ma bayan auren da sati ďaya zasu wuce UK, life will be better, babu sa ido", dariya Batuul tayi ta ďan dungure mata kai tace "ni tashi muje muyi alwala muyi sallah" Wayan Farida ne yayi k'ara , dubawa tayi taga Ammah ke k'iranta, amsawa tayi tare da cewa "Hello Ammah", katseta tayi tare da cewa "Farida kina inane tun ďazu ina nemanki, ina kika shiga", "muna tare da Batuul ne, gidansu nazo", ce mata tayi "ke da waye kikaje gidansu Batuul ďin", a hankali tace "Baa Alai nasa ya kawoni", "toh yanxu zan turoshi zaizo ya ďaukeki ya kuje gidan Yaa Mera, zaki karb'o min sak'o", inji Ammah, da sauri tace "toh" dan murnan ba a yimata faďan fitan da tayi ba a sani ba, ta katse wayan, juyawa tayi ta dubi Batuul taga tana kallonta tana murmushi, ce mata tayi murmushin mey kike min haka, "ashe Ammah bata sani ba kika fito, da tayi miki faďa sosai ai", murguďa mata baki tayi tace "yanxu ma aikena tayi, ni a gama wannan auren mu huta, ki shirya muje mu karb'o sak'on", Batuul ce ta dube ta tace mata "in shirya muje ina?, ke ni babu inda zan fita yau, kije ki dawo", marairaicewa Farida tayi tace "haba mana, you know i love you, you love me too, muje tare kinji, i will get you pack of twix da Raffaello pls", dariya ma ta bawa Batuul tace "Noooo, dagaske babu inda zan fita, beside Aunty ma bata gida bare in tambayeta", Farida bata cewa Batuul komai ba ta shiga dialing number Aunty da wayan dake hannunta, Aunty na ďaukan wayan tace "Hello Farida ya akayi", cewa Aunty tayi, "Aunty muna tare da Batuul ne Ammah ta k'irani ta aikeni, nace ta rakani wai tace baza taje ba saboda bakya gida, Aunty kiyi hak'uri muje, gidan Yaa Mera ne, bana so in tafi ni kaďai", dariya Farida ta bawa Aunty tace mata "kice nace ta rakaki, wani ihu Farida tasa tace "Nagode Aunty, yanxu zamuje mu dawo, ta katse wayan, tsayawa Batuul tayi tana dubanta, ya zatayi da Farida ne a rayuwa, k'in kulata tayi ta tashi ta hau sama ta ďau wayanta ta bugawa Aunty, tana ďauka tace "Aunty kunyi waya da Farida yanxu ko", Aunty ce tace mata "ehh yanxu ta k'irani, ki rakata Batuul kuje ku dawo", toh kawai Batuul tace ta katse wayan, Farida ce ta biyo ta ďakin tace "zamuje ko Batuul", hararan wasan tabita dashi, tana dariya tazo ta zauna a gefenta tace "ai nasan you cant do without me", suna zaune har Baa Alai yazo yace mata ya iso su fito su tafi, mik'ewa sukayi, k'aramin bak'in gyale kawai Batuul ta ďauka ta yafa akan hulan dake kanta da wayanta, suka fita, Batuul ce ta shiga gba Farida ta zauna daga baya, har cikin gidan ya shigar dasu yayi parking suka fito su biyun, suna fita Batuul ta rik'ewa Farida hannu tace "Farida ya fara", kallonta Farida tayi tace "mene ďin ya fara?", "heart beat ďina mana, its increasing, am telling you ppl, its becoming serious", ce mata Farida tayi "sorry anjima sai mu faďawa Aunty", bata amsa mata ba dan ita kaďai tasan abunda take ji, tafiya sukayi mai ďan nisa tukunna suka isa cikin gidan, har ďakin Yaa mera suka isa, tana ganinsu tayi murmushi tace har kunzo, "wannan ba Batuul ba", da mamaki Batuul tace "ehh nice" dan batasan matar ba, matar ce tace mata "Masha Allah kin girma, tun kina 2yrs rabona dake, mamanki na gidan biki ko", da ehh Batuul ta amsa mata sannan Farida tace "Yaa Ammah ce ta aikomu wai muz...." bata k'arasa ba tace mata "ehh kuje da Ya bawa ta nuna miki inda ake aikin kiga ko sun gama" ta haďa ta da Baiwa ďaya suka tafi, Batuul na zaune tare da Yaa mera tana tambayanta abubuwa har makaranta, tace mata sunyi graduating yanxu university zasu shiga, wayanta take ta dannawa tana sawa a kunne sai ta cire, Batuul ta duba tace mata "Batuul", a hankali ta ďago daga wasan da take da zoben hannunta ta dubi yaa mera tace "na'am", "chamber ďin Massa zakije ki duba min shi inata k'iranshi baya ďauka, intercom ďinshi ma baya ďauka kuma ya shigo ďazu, ki ce mishi ina k'iranshi", bata sa komai a ranta ba ta mik'e tace "ta ina ďakin yake", kwatance tayi mata "tace in kin fita ki mik'e sai kin wuce dorms uku, chamber yana by the left", ta amsa da toh ta fita, a hankali take tafiya har ta isa ďakin, knocking tayi taji ba a buďe ba, a hankali ta tura k'ofan ďakin taga babu haske, sai ďan dim light daga ciki, kai ta sa ta shiga cikin ďakin, k'anshin da taji ne ya sata jin kamar zuciyanta zai faďo dan bugawa, tsayawa tayi a spot ďin da take ta kasa gaba ta kasa baya 💖💝BATUUL💖💝 18 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Tsayawa tayi tana juye juye in zata bi, kawai deciding tayi da ta fara sallama ko zai jiyota inma a ciki yake, sallama tayi ta yi taji ba ba a amsa ba, lalube ta fara ko zata switch ďin ďakin har ta gama lalubenta bata ga komai ba, deciding tayi toh ta k'ira sunanshi ko zai amsa, "Massa" ,shiru tayi tana jira taji ko za a amsa amma taji shiru, sau uku tana k'iran sunan taji ba a amsa ba kawai ta juya zata fita ta ga kamar mutum na kwance a kan seater, k'arasawa tayi wajen seater ta tsaya ta tabbatar mutum ne kwance a kai, broad figure ďinshi na kwance peacefully amma bata ganin fuskanahi dan ya juya mata baya, sake k'iran sunan tayi taji bai amsa ba, deciding tayi ta tab'a shi tunda baccin nashi ya kai har haka nauyi, hannu ta sa a goshinshi taji wani ďumi da laushi, maza tayi zata ďauke hannunta taji wani hannu mai laushi da faďi a kan nata, wani abu ne taji gaba ďaya yabi jikinta ga heartbeat ďin ya fara aikin nashi kamar mai shirin fitowa, idonta ya cika da hawaye tab saura k'iris ya zubo, tsayawa tayi still a wajen ta kasa ko da k'wak'waren numfashi, juyowa yayi ya jawota ta kusa faďawa kanshi tayi hanzari ta dafa kujerar, wayanshi ya ďauko daga gefenshi, flash light ya kunna ya haska yaga ko wacece, idonta ta rintse da ya haska flash light ďin a fuskanta, hawayen da ya taru a idon ne ya silalo ta ido ďaya, tsayawa yayi yana kallon cute face ďinta , k'aramin lips ďinta idonshi ya sauk'a akai, yadda hawayen ya gangaro har kan cute lips ďin yabi da ido, ita dai tana tsaye ta kasa motsi, idon ma bata buďe shi ba dan bata san ma ko waye bane, tashi yayi daga kwancen da yake ya zauna har lokacin bai sake mata hannu ba, sai da ya zauna ya fara mamakin, ya akayi tazo gidannan, kuma mey ma ya kawota har ďakin nan, k'ara janyo hannunta yayi , a lokacin ta buďe idonta, wara idon tayi ganin wanda ke rik'e da hannunta a gabanta, ihu ta buďe baki zata kurma yayi maza ya toshe bakinta, ce mata yayi "shut up, and tell me y you are here" tare da fixgo ta ta k'arasa gabanshi, sai da yaga kyarman da jikinta keyi ya ragu sannan ya sake mata baki da hannu, mik'ewa yayi ya isa wani waje ya kunna wutan ďakin, gaba ďayanta ya duba tun daga kai har k'asa sannan ya koma ya zauna a kujerar da ya tashi, tambayanta ya sakeyi, "mey kike yi a ďakin nan har kika zo kina tab'a ni", kasa magana tayi dan gaba ďaya ta tsorata da ganinshi, tsawa ya daka mata "yace ba magana nake miki ba kinyi shiru kina kallo na, sai da ta tuna da sunan wacce ta aikotan sannan jiki a sanyaye tace mishi "Yaa mera ce tace in zo nan chamber in k'ira mata Massa, i didnt know inace kaine Massa, kuma ďakin ne da duhu shine nace bari in tashe shi, kayi hak'uri", gaba ďaya ta gama tsorata da ganinshi, juyawa tayi zata tafi yayi maza ypa fixgota, ce mata yayi "tab'a min fuskan kuma na meye", "innalillahi wa inna illaihi rajiun ta ambata a zuciyanta, ba ta faďa mishi tashin Massan zatayi bane kuma da duhu ita bata san ma fuska bane, cikin dakewa tace "ďakin ne da duhu, ban san fuskan ka bane" ta warce hannunta daga ruk'on da yayi mata tayi ta fita daga ďakin a guje, sunanta ya k'ira amma ko sauraronshi bata yi ba tayi tafiyarta, ranshi ne yayi mugun b'acin k'in amsawa da tayi, tashi yayi ya shiga toilet dake bedroom zaiyi wanka Sai da ta iso k'ofar ďakin sannan ta tsaya ta daidaita numfashinta, ganin ta samu nutsuwa ya sata tura k'ofan ďakin a hankali, da sallama ta shiga ta zauna sannan tace "Yaa Mera , Massan baya nan" kamar kar ta faďa mata taga Abu sai kuma tace "amma naga Yaa Abu a ďakin yana bacci", jin ance Abutturab na ďakin yasa ta cewa "ohh shi yana gida, toh dama ai dan shi nake neman Massan, yau zasuyi wushe wushen ko?", ta tambayi Batuul, ďago kai Batuul tayi tana dubawa ko wani ake tambaya, da ta ga babu kowa a ďakin sai ita ya tabbatar mata da ita Yaa Mera ke magana, " No, ni ban sani ba fa Yaa, bansan mey zasuyi yau ba, sai dai in Farida ta shigo mu tambayeta" inji Batuul, Yaa Mera ce ta sake cewa "ai tunda ma yana gidan bari in k'irashi yazo in ganshi muyi magana dashi", mamakin matar takeyi kamar ba sarauniya ba, babu ruwanta, ita ko bayi ma bata ajiyewa kusa da ita gata da fara'a, ga kyau, kammansu ďaya da Ammah, Abutturab ďinma dasu yayi kama, hasken sune kawai bai ďauko ba sai yayi duhun Abui, su Farida da Sadiq ne sukayi kama da Abui amma suka ďauko hasken Ammah, tana zaune tana ta zancen zuci Farida ta shigo da plate ďin kisre da miyar kuka da yaji kaji, gefen Batuul taje ta zauna ta cewa Yaa Mera "Yaa sun iya kisren sosai, kamar fa da engine sukeyi , ya burgeni yadda sukeyi shiyasa ma na ďebo kaďan, Batuul ci kiji", Yaa Mera ce tace "shiyasa mamanku tace sai anan za ayi, yanxu ma daga nan za a kwasa akai gidansu matar Abun", ido Farida ta wara tace "Yaa drums dayawa fa akayi, kuma duka za a kai musu, wannan matar ta Yaa Abu suna yi bada wasa ba", dariya ta bawa Yaa Mera tace mata "al'adanmu kenan Farida, haka mukeyi in zamu aurar da yara", cewa Farida tayi "lallai, su suka sani", taci gaba da cin abincinta, lura tayi da Batuul bata ci tace "meye kika sani gaba, kici mana", harara Batuul tabita dashi tayi magana a hankali yadda Yaa Mera baza taji ba "ce miki nayi inajin yunwa, ki gama mu tafi ni", Yaa Mera ce ta ďagi taga Batuul ďin bata cin kisren, ce mata tayi "Batuul bitti, beri bei" (Batuul y'ata, kici abinci), a hankali ta amsa da "toh", sannan ma matso tasa hannu a cikin plate ďin Yana fitowa daga toilet ďin bayan yayi wanka da alwalar la'asar, wayanshi ya ďaga ya k'ira Massa, yana ďagawa yace mishi " Kana inane", Massa ne ya amsa da "muna tare dasu Imran a Protea, ya kan naka, yayi sauk'i", ce mishi yayi "Yeah sosai, ina jiranka kazo ka ďaukeni", sannan ya katse k'iran, kaya ya saka cikin sabbin kayanshi da suke gidan da ya ďinka na biki, bayan ya gama ne yayi sallah la'asar, yana idarwa wayarshi tayi k'ara, ďauka yayi yasa a kunne, "salamu alaikum, Yaa Mera nda dubdo", ehh ina gida, toh bari in sauk'o sannan ya katse wayan", sosai yayi kyau da kaftan ďin da ya saka, ya ďaura hula akanshi sannan ya fita, side ďin Yaa Mera yayi, da shiga ya samu waje ya zauna ya sake gaisheta, Farida ma gaisheshi tayi , bayan ya amsa ne Yaa Mera ta dubeshi tace "yau ne wushe wushen naku ko", kai ya gyaďa tare da amsa mata da "ehh", ce mishi tayi "wane time za ayi?", "k'arfe bakwai ne zuwa sha ďaya", "toh yanxu kace musu su shiryata k'arfe biyar, anan za ayi mata kéla tul kamin ku wuce wajen wushe wushen, zamu tura musu mota, daga nan zamu kaita wajen, har kaya zamu bata ta saka, mun gama magana da mamanka", cewa yayi "okay Yaa, In sha Allah zan faďa mata, sai ta faďa a gidan nasu" , sallama yayi da ita ya mik'e kenan zai yi hanyan waje yaga an buďe wani k'ofa, k'ofan yabi da kallo, Batuul ce ta fito daga ciki hannunta rik'e da hand napkin tana gogewa, ta cire gyalen dake yafe akanta ďazu sai hular kawai, idonta dake kan abinda ke hannunta ta ďago suka yi ido huďu, wani irin abu taji gaba ďayanta, shima tsayawa yayi kallonta, idonta ta ďauke daga kanshi shima yayi k'wafa ya fita daga ďakin k'iran Massa ne ya shigo wayanshi, recieving yayi yace mishi "ka iso ne?, toh gani nan fitowa", motar da Massa ke ciki yaje ya buďe ya zauna , Massa ne ya tambayeshi "ya jikin dai Man, wannan rashin lafiyan ai sai ya bari a kwanakin nan ba, kai da kake shirin zama ango da dai ya isa wani wajen, yayi wrong timing gashi da yake ka fishi k'wari kayi fighting ďinshi", kallon Massa yayi da ďan murmushi a fuskanshi ya girgiza kai yaci gaba da danna wayarsa, "Hello", yace bayan ya an ďauki wayar da ya buga ďin, amsa akayi da "Hello baby, am missing you over here, ya gajiya dan ni gaba ďaya na gaji so nake kawai a ďaura auren nan mu tafi mu huta dan ba k'aramar gajiya nakeji ba a jikina, yanxu ma a ďaki nake ni kaďai wai za a min gyara....", yasan idan ya barta taci gaba da magana sai ya manta dalilin da yasa ya k'irata, katseta yayi yace "gajiya Alhamdulillah, ki faďawa su Mum za ayi miki kéla tul before a tafi wushe wushen a gidan Aunty ďina, kuma kayan wushe wushen ma daga can zaki sa, zan aiko mota by 5, you should be ready", ce mishi tayi "Aliyu gaskiya waďannan abubuwan naku na al'ada na gaji dasu, tunfa last week ake ta yi, kuma kayan ma mum ta riga da tasa an siyomin a turkey, ni gaskiya a bar wannan ďin kawai, ai anyi sauran, kuma ma its too late yaushe zan faďa musu su shirya", ranshi ne ya fara b'aci, cikin dakewa yace "wani shiri zakuyi, ce miki nayi zan aiko mota ki taho ke kaďai, kuma in kin faďawa mum ďin nasan ba hanaki zatayi ba", tsaki yaja dan ranshi daďa baci yayi yace "in na aiko da motar kar kizo" ya kashe wayan , Massa ne ya dubeshi yaga ranshi ya b'aci yace "lafiya naga kana tsaki", tsakin ya kuma ja yace mishi "yarinyar nan , tun last few days nayi observing that duk abinda na faďa sai ta canja, ce mata fa nayi yanxu zan turo driver a kaita gidab Yaa, take cemin ita baza taje ba", bai ci gaba ba Massa ya dafa kafadmďanshi yace mishi "Man its okay, zata dena in sha Allah", da haka suka canja hira, hotel ďin sukaje yaga abokananshi dayawa sun sake k'aruwa, sai da ya ďan huta yake tambayan Massa, "gobe what time za a tafi ďaurin auren Maiduguri", "sunce flight ďin goben k'arfe huďu ne , so muna da time da in mutane suka k'aru za a yi musu booking tunda da yamma ne", "okay" kawai yace mishi suka shiga cikin abokanan Ganin ya katse wayan ne ta tsaya ta k'urawa wayan ido kamar wanda sukayi wayan dashi ďin zai fito, Mesa Aliyu yake min hakane take tambayar kanta, jibi nefa ďaurin aurensu amma kawai dan ta faďi magana ya katse mata waya harda cewa in ya turo motar kar tazo, ai gaskiya ta faďa tun kwananki suke ta yi musu abubuwa wai al'ada, shi kuma kawai sai ya ďau fushi, a ranta take cewa "dan yaga inasonshi ne yake wasu abubuwan", k'wafa tayi ta cewa mai yi mata gyaran jikin zata je ta dawo, matar tace mata babu komai sai kin dawo, fita tayi daga ďakin, tun daga bakin k'ofa gidan cike yake da y'an uwa d abokan arziki, matane kyawawa, farare da gashi kowa taci kwalliya an zuba gwalagwalai, ďaďďaya zaka bak'i a gidan nan, tana tafiya mutane na ta gaisheta wasu ta gaishesu cikin yarensu shuwa, wani ďaki ta buďe ta shiga, ďakin babba ne mai kyan gaske, babu mutane a ciki sosai, daga Mum , sai wata mata da zatayi sa'ar Mum sai Yaa zee, k'arasawa tayi ta zauana daga gefen mom, matar kawai tace wa "Jainaba inta afe", matar ce tace mata "afe selai Ajiddeh, ya shirye shirye, da gajiya", tace gashinan fa na gaji sosai, ina su Attutu, Abba Mahammad da Adum", ce mata tayi "suna gida bamuzo tare ba anjima za a kawosu", juyawa tayi ta dubi mum da ke jiranta ta gama ta faďa mata dalilinta na fitiwa ana mata gyaran jiki, ce mata tayi "Mum yanxu Aliyu ya k'irani wai zai turo a ďaukeni k'arfe biyar a kaini gidan k'anwar mamanshi, wai akwai wani abu da zasu yi min daga can zamu wuce wajen wushe wushen, kuma ma wai kayan da zan saka ma su zasu bani", cikin ďaga murya Mum ta fara magana "nifa Abun nan nasu Hajiya Bilqees ya isheni, wace al'adarsu ce bamu gani ba fara bikin nan, ni sanin da nayiwa Hajiya Bilqees ma ba kanuriya bace amma gaba ďaya dan tana auren kanuri ta canja gaba ďaya, a ina ake wani kéla tul a Ndjamena, kuma da suke cewa su zasu baki kayan kisa ai ganin kasawarsu ne yasa muka ce zamuyi miki , ko ďari mukace muna so ai yaci a kawo miki, kinfi k'arfin akwatuna arba'in, ba dan Babanku yace a bari ba kuma zai sab'awa duk wanda ya tada maganan wlhy da sai an maida musu tunda dama cewa tayi a dawo dashi in muka k'i karb'a", Yaa zee ce tace "Mum ai ita tabi ta liqewa yaron kamar babu wani namiji a duniya sai shi, ni gaba ďayanshi bai min, sai girman kai da uake dashi kamar mutumin da", matar da aka k'ira da Jainaba ce tace "toh ku yanxu menene na tada jijiyoyin wuya, ai damu suke zancen , ku bari kawai a gama bikin zasu shigo hannu, tayi yadda yace ďin, anjima in ya turo driver kije, tashi kije a gama miki gyaran kamin lokacin yayi", da haka ta mik'e ta koma ďakin, tana zama ta k'irashi, ansawa yayi shiru yana jiran yaji mai zata ce mai zata ce mishi, cewa tayi "Hello baby, toh mey na kashe wayan, in ka shirya ka turo motan na faďwa su Mum sunce inje", ce mata yayi "okay yayi kyau, by five zaizo", ya katse wayan K'arfe shida na yamma Aunty ta dawo gida lokacin har Batuul sundawo, a palo ta zauna ta k'irawo wayan Batuul tace mata ta dawo, sauk'owa tayi mata sannu da zuwa, zama tayi daga gefenta tace "Aunty ya gidan bikin", ce mata tayi "lafiya Batuul, masha Allah , gobe zasuje Maiduguri ďaurin aure, har Baba ma zaije, amma shi sai ranan ďaurin auren, jibi kenan", baki Batuul ta tab'e tace Allah ya basu zaman lafiya", "Amin" tace sannan tace mata tace "yaushe kuka dawo ne", "tun three thirty suka sauk'eni a gida ita kuma Farida ta wuce gida", ta sake cewa "Aunty maganan admission ďin nawa kunyi da Baban, time yana wucewa", Aunty ce tace "ni na manta ma Batuul amma yau zamuyi maganan in sha Allah , Allah dai yasa kar in manta, "Amin ta amsa da sannan suka mik'e a tare sukaje yin sallah dan an fara k'ira, Batuul na ďaki bayan ta idar da sallah ta zauna tana game a Macbook ďinta, Yusra ce ta shigo tace mata "Yaa Batuul, Mama tana k'iranki tana ďakinta", cemata tayi "kice ina zuwa", ta juya ta fita, tana fita ta ďauke Macbook ďin akan cinyarta ta mayar gefe, mik'ewa tayi tabi bayan Yusra, da sallama ta shiga ta tarar Aunty tana duba abu a closet ďin kayanta, k'arasawa tayi cikin ďakin tare da sallama ta zauna aka makeken gadon ďakin, cewa tayi "Aunty gani", sai da gama dubo kayan da take nema sannan tace wa Batuul "kije ki shirya zamu tafi wushe wushen Aliyu, k'arfe 8 zamu fita, kije maza ki shirya", da sauri Batuul ta ďago kanta tana kallon Aunty, ganin Aunty ko noticing kallon da take mata ma batayi ba yasa ta cewa "Aunty wushe wushe kuma, nifa bazan je ba , tun ďazu ma na faďawa Farida, kuma ma ban shirya bafa", ba tare da Aunty ta kalleta ba tace "ki tashi kije shirya, jama'a sai tambayana ina kike akeyi, wasu ma cewa suke ni ke hanaki fitowa bayan halinki ne na k'in jama'a yake hanaki shiga taro, ki tashi kije ki shirya" tana faďa mata tana warware laffayan da ta ďauko, baki Batuul ta zumb'uro ranta a b'ace ta mik'e ta fita, ďakinta ta isa ta zauna akan gado gaba ďaya ranta a dagule, toh ita wane kaya ma zata sa , bayan angon ma ba son mutane yake ba shine za ace wani sai anje bikinshi, mik'ewa tayi ta shiga toilet ta watsa ruwa ta fito, zama tayi shafe jikinta da mai sannan ta isa closet ďin kayanta ta ciro abaya ďaya a hanga na Al layl mai kyau da purple crystals a jiki ta sa, gashinta ta taje ta k'ara parking ďinshi sannan ta shafa powder ta saka kwalli a idonta da chappete a bakinta, turarenta masu k'anshi ta fesa ta sauk'o k'asa tana jiran Aunty, Aunty na sauk'o zata cewa ďaya daga cikin masu aikin ya k'ira mata Batuul ta ganta zaune a palo, ce mata tayi "Batuul bana son iskanci, kina jina, ince kije ki shirya shine zakije ki wani sako min doguwar bak'ar riga, dama naga ranki bai so ba shiyasa dole ki b'ata min rai ko?, toh ki wuce kije ki canza su kuma karki b'ata min lokaci, mik'ewa Batuul tayi tace "Aunty bansan kayan da zan saka bane", "duk kayanki kice min kin rasa na sawa, ba wushe wushe bane, ai kina da dongashua da zaki saka, ki wuce kije ki canja ki dena b'ata min lokaci", rafiya tayi ta haura sama ,kaya ta canja ta saka shadda duck mai blue da bak'i, ďinkin riga robe da straight skirt, ta ďauko k'aramin jan gyale ta yafa, ta saka sark'a da ďan kunne suma ja da abun hannunsu, shoe Rack ďinta ta nufa ta ďauki slippers ďinta louis vuitton mai ja da bak'i ta saka, tayi kyau sosai har ta fi da, sauk'owa tayi, Aunty batace mata komai ba tayi hanyan waje, Batuul ma ta bita a baya, mota Aunty ta buďe ta shiga, Batuul ma ta shiga gidan gaba, Fa'iza da ke rike da Aabid suka zauna a baya itada Yusra, Aunty ke tuk'a motan suka ďau hanyan inda za ayi event ďin, parking sukayi a wajen parking ďin motoci , suna fitowa daga mota, sautin kiďa ke tashi a wajen, tana fitowa daga mota wata rolls royce ta danno kanta wajen, daidai fuskan Batuul motan ya haska, tsayawa tayi mai motan ya gama iskancinshi na haske mata ido sai ta tafi dan bata gani, su Aunty har sunyi gaba sun barta, k'ofan motan aka buďe, iska ne ya buso mata k'anshi turaren, kanta ta ďago dan tasan mai turaren, kashen wutan motar akayi tana ďaga ido, fuskan Abutturab idonta ya sauk'a akai, ba kaďan ba yayi kyau, kaftan sky blue ya saka, yayi kyau sosai, shades ďin ray ban ne mak'ale a idonshi, gani tayi yana tahowa hanyanta, tsayawa tayi ta kasa motsi sai bugun da zuciya ya fara Aunty(Mama) haka k'annen Batuul ke k'iranta 💖💝BATUUL💖💝 19 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Ganin yana nufota ne tayi maza ra rik'e rigan cikinta, ray ban glass ďin dake fuskanshi ya cire , ido huďu sukayi da Batuul, kasa ďauke idonta tayi daga kallonshi shima hakan bai ďauke nashi ba, sai da ya iso har inda take sannan ya tsaya, idonta ta ďauke daga kallonshi shi kuma yaci gaba da kallon nata, a hankali ta sake rik'on da tayiwa riganta, ya buďe baki kenan zaiyi mata magana ta juya a guje ta bar wajen, ranshi ne yayi bala'in b'aci ya daka mata tsawa, " *Batuul*", ko juyowa batayi ba taci gaba da gudunta, sosai ranshi ya b'aci, ba sau ďaya ba yanxu tana mishi irin haka sai yana mata magana ta gudu, tunawa yayi da ranan da ya fara ganinta ranan idi, haka ya buďe baki kenan zai ce mata ta gyara gyalen kanta, gashinta na a waje tak'i ko da tsayawa jin mey zai ce mata ta gudu, ko ďazu ma haka tayi mishi ta gudu daga ďakin yana k'wala mata k'ira, inda tabi ya kafawa ido yana daga tsaye, ji yayi an dafashi ta baya, Massa ne ya zagayo gabanshi yace mishi "Yanxu amarya ta k'irani wai suna ciki tun ďazu, sun jiramu bamu zo shine suka shiga", juyowa yayi ya dubi Massan sannan yace "toh mu shiga", shi da tawagar sauran abokanshi da kana ganinsu kasan dagaske suke suja k'arasa ciki, fili ne babba zagaye da canopies sai kujeru daga ciki biyu aka kasa wajen, side ďin amarya da gefensu, k'awayenta da dangi, sun sha ankon atamfa maroon, sunyi kyau sosai kasancewarsu farare, ďayan side ďin dangin ango ne suma da ankonsu na irin kayan da Batuul ta saka, daga gefe side ďin amarya ne da ango anyi musu rumfan fulawa da kujeru biyu, mutanene cike a wajen wasu na zaune wasu na kai kawo, Kamal da Mansur ne daga tsakiya rik'e da mic suna ta rero wak'a, ganin ango da abokansa sun shigo ya sa mawak'an k'ara kaimin wak'arsu, k'anshin turaren wuta ke tashi ta ko wane angle,tuni wajen ya kaure da hayaniya, k'awayen amarya aka fara k'ira suyi rawa da danginta, sun shiga sun tattaka rawa sosai sannan aka k'ira Family ďin ango, Batuul na zaune ita da Farida duk ranta a b'ace, gaba ďaya bata so Aunty ta sata zuwa wajen nan ba, ta k'agara ayi abinda za ayi ita ta koma gida, k'iran y'an uwan angi ne ya sa Farida mik'ewa zata shiga wajen rawa tare da janyo hannun Batuul, warce hannunta tayi daga rik'on da Farida tayi mata tace "mey haka kike jana, mey zan tashi inyi miki", "rawa mana baki ji an k'iramu bane, ai ni komin rashin shirinmu da Yaa Abu sai nayi rawa, ba namu bama munyi bare na gida", ta faďa tana dariya, "A dawo lafiya", inji Batuul ta sunkuyar da kanta taci gaba da dannan wayanta, Farida ganin dagaske Batuul take ya sata juyawa ta shiga filin rawa, rawa sosai su Farida sukayi da sauran family, sai da suka gama lokacin aka k'ira ango da amarya su fito suyi rawa, mik'ewa sukayi a tare shi da Ajiddeh, sosai tayi kyau, bak'in lace ta saka da blue laffaya, anyi mata kéla yaskè(kitson gaba) da aka bi akayi mishi ado da gold sai ya k'ara mata kyau, ko ina a jikinta gold ne , har anklet sai da ta saka na gold da nose ring, hannayensu mak'ale cikin na juna suka tasi suka isa filin rawar, mutane ne suka shigo ana ta yi musu lik'i, abokan ango dollars, Euros suke zubawa amarya, sau ďaya Batuul ta ďago kanta ta kallesu ta mayar, wayanta ne taga yana ringing, Aunty ke k'iranta, jutawa tayi ta dubi inda Aunty ke zaune taga tana mata alama da tazo da hannu, tashi tayi ta isa inda Aunty ke zaune, sai da ta zauna a empty kujeran dake gefen Aunty sannan tace "Aunty gani", jakanta ta ďauko sannan ta ciro bandir ďin 1000 sabbi dal ta mik'awa Batuul, da ido Batuul tabi kuďin tana jira taji na meye na "Kije kiyiwa ango da amarya lik'i, ni bana son tashi saboda da Aabidĺ, Batuul gaba ďaya bata yi zaton abinda Aunty zata sata yi ba kenan, ranta ya b'aci amma ba tayi musu ba dan bata son b'atawa Aunty rai kamar ďazu, kuďin ta ansa sannan ta mik'e Kamar mai shirin yin kuka rai b'ace ta isa inda suke, y'an dubu dubun nan ta rik'a cirowa tana yiwa amarya lik'i dashi, wani mugun harara Ajiddeh tabi Batuul da, daga k'arshe ma barin wajen tayi ta koma daga gefe wajen danginta, Batuul bata sanma tana yi ba, kuďin da yake hannunta tabi da ido, ko rabi bata lik'a ba, juyawa tayi ta dubi Abutturab taga idonshi na kanta, sauri tayi ta ďauke nata idon, Aunty ta sake waigawa ta duba a inda take zaune taga tana kallon wajensu, babu daman ta bar wajen, kawai kuďin ta fara zara tana yiwa Abutturab lik'i da, ido ya kafa mata yana kallon yadda tayi kicin kicin da fuska tana b'ata rai, Massa ne ya hango Batuul tana yiwa Abutturab lik'i, zuwa yayi inda take ya fara mata ruwan dollars a kanta, gaba ďaya sauran abokan ango ma hankalinsu kan Batuul, lik'i suka dinga yi mata kamar itace amaryar, ba k'aramin haushi Ajiddeh taji ba, ji take kamar ta shak'e yarinyar nan ta huta, gaba ďaya bata sonta , hankalinta sam bai ďauki Batuul ba, wani irin b'ata fuska Abutturab ya rik'a yi ganin yadda abokansa ke yiwa Batuul lik'i bayan ga amaryar basu yi mata ba, niyya yayi yaje yace su dena wannan shirmen, A guje Batuul ta sake kuďin hannunta a jikin Abutturab ta fice daga filin dan ta tsorata sosai da yadda dukkansu ke mata lik'i ita da bama rawa tayi ba, wajen zamanta ta k'arasa ta zauna, tana zama Massa ya bita shima ya zauna a kujerar Farida dake gefen nata, wani irin murmushi yayi mata yace "Fatima ko", kai ta gyaďa mishi ba tare da ta ďago ta dubeshi ba, k'anshin turarenshi duk ya cikata har yana neman sa mata murya, juyawa tayi ta dubi inda Aunty take taga hankalinta baya ma wajensu, ita masu rawa take kallo, "masha Allah", yace sannan yace "ranan grads ďinku i wanted talking to you sai kuma ban samu chance ba, you know kin burgeni, ni ban tab'a sanin Su Baba nada yarinya babba haka ba sai ranan graduation ďin da naji sunanki, kin tab'a sanin Aunty ce ta yayemu ni da Aliyu, ina zaki sani ai ba a haifeki bama lokacin", ďagowa tayi ta dubeshi , toh ita mey ruwanta da Aunty ta yayesu, ina ruwanta ma in a gidansu aka haifeshi shi da Aliyun, juyar da kanta zatayi taga idon Abutturab a kansu rai a b'ace, ďauke idonta tayi taci gaba da wasa da awarwaron hannunta, "Cutie, it seems your mind is totally not here, mayb you should share your contact with me, sai muyi magana anjima, nima ďin yanxu am busy", dariya ne ya kusan kufce mata na sunan da ya k'irata dashi wai cutie, da har zata bashi number ta na da sai kuma ta tuna ai zai iya tambayan Farida ma ta bashi, deciding tayi da ta bashi natan , ai ba lallai ne in ya k'ira ta ďauka ba, karanto mishi tayi numbers ďin ya rubuta a wayanshi, mik'ewa yayi tareda kai hannun zai shafi fuskanta rayi maza ta matsa da baya, idon Abutturab akansu duk abunda sukeyi yana kallonsu sai ma harara da yake binsu da, tashi yayi zai fita daga filin ranshi b'ace, Massa ne ya hango shi zai fita yayi maza ya cewa Batuul "Aii cutie we will talk later", yayi maza yabi bayan Abutturab yaji lafiya zai fita ana cikin event, daga waje ya tarar da shi wajen da sukayi parking motoci, zuwa yayi yacewa Abutturab"Ya ka fito ka bar amaryarka a ciki, ana ta event, wato halinka ko a ina sai ka nun.....", bai k'arasa ba ya katse shi da "Mustapha what is wrong with you, for Gods kaga abinda kuka dinga yi a wajen nan, duk kun wani juya kuna yiwa yarinya lik'i bayan amaryar ma baku yi mata wanda kukayiwa yarinyan nan ba, kuma da ta bar wajen ka wani bita a baya , wannan ai neman raini ne a wajen yara, mey zaka nema a wajen Batuul yarinya k'arama, k'annenmu nefa, y'ar Aunty ce inma baka sani ba toh ka sani, k'anwar kace", kasake Massa yayi yana kallonshi, wannan faďa da yake yi kuma na meye haka, ce mishi yayi "toh menene in k'anwata ce ko kuma y'ar Aunty ce, ai nan nema zanyi yadda nakeso ko akwai inda aka hanani nemanta, kuma right from day one na faďa muku ni k'aramar yarinya zan aura, manyan mata wannan sai ku, kuma Batuul is d right choice for me saboda abinda ya fara min tarbiya shi yayi mata tarbiya dan haka ana gama bikinka zan kai nawa maganan gaba sai dai in itace tace bata sona" ya faďa yana maida numfashi, wani irin kallo Abutturab ya bishi dashi ya rasa mey zai ce mishi, tsaki yaja ya koma cikin wajen Massa ya bishi a baya Yana barin wajenta ta sauk'e ajiyar zuciya, ďazu a wajen lik'in nan taji an k'irashi da Massa, da ma shine, tab'e baki tayi a ranta tace toh wannan ne prince , ai surutunshi yayi yawa, dama Abutturab ďin ne prince zai fi dan shi yafi ji da kai, ku kuka sani dai, dama sune take ganin pictures ďinsu a album ďin gidansu suna yara , baki ta tab'e tace ku kuka sani dai, Mik'ewa tayi daga indactake zaune ta isa wajen Aunty, marairaicewa tayi kamar zatayi kuka tace "Aunty, ciwon kan ďazun fa ya dawo, insaso in je gida", dubanta Aunty tayi sannan tace "baki sha magani bane ďazu", da sauri ta kaďa kai, "nasha, mayb effect ďinshi ne ya sakeni, inaso in sake shan wani", Aunty bata sake cewa komai ba ta ďaga waya ta k'ira Ahmad, yana amsawa tace "ga Batuul nan zaka kaita gida, kanta na ciwo", bayan ta katse wayan ta cewa Batuul "ki tashi ku tafi, Allah ya sauwak'a, in kuma zaki iya ku bi ta asibiti Dr zaka ya dubaki", cewa tayi "toh Aunty bari muga idan na sha na yau ďin bai yi ba sai mu tafi gobe ya dubani", da haka ta mik'e tayi hanyan waje, a bakin k'ofa tazo zata fita shi kuma zai shigo suka kusa bugewa, matsawa tayi da sauri kar ya bugeta dan taga ranshi duk a b'ace, tsayawa yayi kallonta har sai da ta wuce, Massa ne da ya ganta ya fara smiling, "Cutie ia zuwa", sunan da yaji ya k'irata dashine yasa shi saurin juyowa, tsayawa yayi yaji mey zatace, a hankali kamar mai raďa ta ce mishi "kaina ne yake ciwo za a mayar dani gida", baiji mai tace ba, haushi ya sake turnuk'e shi yaja tsaki ya shiga ciki, tsakinshine ya jawo hankalinsu suka dubeshi, su sunace ma ya tafi, da damuwa Massa ya dubeta "let me drop you mana", "No brother na yana jirana shi zai kaini, nagode" tace ta juya ta bar wajen bata sake ce mishi komai ba, a mota ta tarar da Ahmad yana jiranta, buďewa tayi ta shiga ta zauna, with concern yace mata "sannu Yaa Batuul", ta amsa da "yawwa muje", dan so take ta bar area nan gaba ďaya, rage Ac motar yayi sanan ya tada suka tafi A kujera ya tarar da Ajiddeh ta cika tayi fam, yana zama ta dubeshi tace "Aliyu dama wushe wushen naku kenan, muzo a wulak'anta mu", tunda ta fara magana bai ce mata komai ba sai da yaji ta ambaci wulak'anci, katseta yayi tareda da tambayanta "wulak'anci mey aka yi muku", "ehh mana wulak'anci mana , dubi fa yadda abokanka da yan uwanka suka dinga yiwa bak'ar yarinyar nan lik'i kamar itace amaryar, da kunsan ita kuke son yiwa lik'in kaje ka aureni, ai da an aura maka ita sai kuji daďin yi mata lik'in da kyau, wani kallo ya bita dashi da ya sata haďiye magananta da sauri, "mey ke damun kankine wai, wa yace miki ana faďa min ko wane irin magana, ba ni ba ko mutum dake kusa dani bana yadda a faďa mishi magana anyhow bare ni da kaina, da kike cewa a aura min ita ai da naso tare za a haďa min dake akai min ku ko kuma in fasa nakin in aureta, sai ki rik'a yin magana kamar yarinya, jibi ne ďaurin aurenmu inma zaki gyara tun wuri ki gyara dan bazan yi tolerating shit ďinnan a gidana ba, you have change", ya faďa yana mai kallon agogon hannunshi, duk maganan da sukeyi a hankali suke yin shi kamar masu yiwa junansu hiran soyayya Batuul na isa gida ta hau sama, wipes ta ďauka ta goge abinda ke fuskanta sannan ta shiga tayi wanka tayo alwalar isha ta hau abin sallah, tana idarwa ta cire hijabin jikinta ta ninke shi ta ajiye a gefe, ko hula bata ďaura akanta ba ta sauk'o k'asa dinning dan yunwa takeji, kwanukan wajen ta shiga buďewa, plate ta jawo ta ďebi white rice da stew sai potato salad, ďakinta ta tafi da abincin sannan ta zauna taci a a nutse, tana gamawa ta buďe fridge ďinta ta ďauki ruwa tasha, sai da ta gama abubuwan da zatayi tahau gado ta yi addua ta kwanta, bacci nebmai nauyiya ďauketa, can cikin bacci wajen k'arfe goma sha ďaya ta jiyo murya kaman na Farida, a hankali ta buďe idonta taga Farida tsaue kanta da wannan wide smile ďin nata tana kallonta, ta kunna hasken wutan, Aunty ce ta shigo ďaki tana tambayan Farida "tayi bacci ko, watak'ila kan ne ya ďan saketa", ganin Batuul ta farka ne ya sata cewa "ya kan Batuul, yayi sauk'i", a hankali tana goge ido tace "ehh Aunty yayi sauk'i nasha analgesic ", da Masha Allah ta ta amsa sannan tace mata "Allah ya k'ara lafiya" tayi musu sai da safe ta fita, kallon Farida Batuul ta tsaya yi, "You didnt tell me you were coming over", baki Farida ta buďe da mamaki tace "toh ko in koma ne, wannan tambaya haka da ake jeho min", bata cewa mata komai ba taja bargonta ta rufe kanta ta kashe wutan daga gefen gadonta, Dariya Farida tayi bata ce mata komai ba sai da taje tayi wanka tayi sallah ta canja kayan bacci, wutan ďakin ta sake kunnuwa tayi tsalle ta hau gadon, Mik'ewa Batuul tayi ta dubi Farida tace mata "meye matsalanki wai", tashi Farida tayi daga kwance da take tace "my problem is i love you so much", tsaki Batuul taja zata koma ta kwanta ta farida ta janyota "kinsan na faďa miki dama gida ya isheni, wait ma, keh da na barki kina yiwa ango lik'i sai nemanki nayi na rasa, Allah kinga yadda kika yi kyau a wajen kamar kece amaryar sai lik'i ake miki , ko amarya ma ba ayi mata ba, Yaa Massa ne ya fara miki ai ko sunace kece amarya har Pounds an zuba miki, mehn i enjoyed that part", "Allah Farida ke ko, yanxu dan wannan kika tada ni, Allah ya shiryaki", wayanta ta jawo ta k'ira Affan, yana ďagawa kamin yace komai tace "Bestfriend com and carry your girl, tun ďazu take damuna ta hanani bacci", ce mata yayi "bata wayan, mik'awa Farida yayi, zama tayi tana jira ta gama wayan, amma har bayan minti talatin basu gama ba, da taga basu da ranan gamawa ne ta jawo bargonta ta kwanta Copied By YAYA HAYAT (admin Hayat hausa novels Hausa novels and fashion Cool novel, makeup and kitchen1⃣ AND Cool novel, makeup and kitchen2⃣) WHATSAPP NO: +2349030159301 💖💝BATUUL💖💝 20 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Bayan Aunty ta duba Batuul, ďakinta ta koma ta tabbatar su Yusra sunyi bacci, addua tayi musu ta tofesu dashi gaba ďaya jikinsu sannan ta tofa a duka angles ďin gidan, toilet ta shiga tayi wanka sannan ta fito tayi sallah, sai da ta idar ta gama addu'o'inta sannan ta mik'e ta cire doguwar rigar dake jikinta, ninkesu tayi sannan ta ďauko kayan baccinta doguwar riga har k'asa, yellow silk mai flaps biyu ta saka, turare ta shafe jikinta dasu sannan ta nemi hula ta saka a kanta, k'asa ta sauk'o ta k'arasa kicin ta tsiyayo fresh orange juice a cup ta ďaura a kan k'aramin serving tray ta haura sama, da sallama ta shiga ďakin Baba, yana zaune a kan gado da farar jallabiya idonshi da glasses yana rik'e da ipad, da alama aiki yake, ďagowa yayi ya kalleta cike da Kulawa sannan ya amsa sallamarta,har ta k'araso ciki, a bakin gadon ta zauna sannan ta ajiye juice ďin a kan bed side drawer, dubanshi tayi itama da kulawa tace "uncle sannu da hutawa, ya dare", bai ďago daga kallon da yakewa ipad ďin ba ya ansa da "Alhamdulillah", sai da ya amsa sannan ya ajiye ipad ďin a gefe ya juyo ya dubeta yace "Ya gidan biki", cike da natsuwa Aunty ta amsa da Alhamdulillah, amaryar tashi ma mai kyau, Allah ya basu zaman lafiya", Amin Baba ya amsa da sannan yace "nima ďin sai jibi zan tafi , ďaurin auren 11 ne, by nine zanbi flight sai mu dawo a ranan", "Allah ya kaiku lafiya, ya dawo daku lafiya, su kuma Allah ya basu zaman lafiya", a tare suka amsa da "Amin", a hankali ta sake cewa "uncle", bayan ta mik'a mishi cup ďin juice, kurb'a yayi kaďan sannan ya juyo bayan ya ajiye cup ďin yace "Maryam, ya akayi ne", a hankali ta ďago ta dubeshi kamar bata son magana tace, "uncle dama karatun Batuul ne, kwanaki da sukayi graduation tace min inyi magana da kai akan karatunta, wai in baka hak'uri ka barta ta fita waje, dama kunyi magana ne da ita kace baka son zuwan nata waje?", cewa yayi "Allasarki mamana, eh munyi maganan da ita na ce mata tayi hak'uri da wajen nan , ta zab'i duk inda takeso a nan Nigeria zan kaita, "toh uncle mey zai hana a kaitane tunda munsan Batuul mun san hankalinta, am sure zata kula da kanta da mutuncinta, baza mu samu matsala ba in sha Allah", glass ďin dake idonshi ya cire ya dubi Aunty sannan yace "Maryam, nafi kowa son ganin na bawa Batuul abinda takeso a duniyan nan, amma bazai yiwu ba, wannan zuwan da mukayi Maiduguri sallah Yayya ce min tayi indai Batuul zata fita waje karatu toh sai da miji, ni kuma ban shirya yiwa Batuul aure ba, tayi k'arama da yin aure shiyasa nace gara in nemo mata makarantanta a nan gida tunda ita Yayyan cewa ma tayi ko a gidan ne sai an mata aure, toh yanxu bakinta nake son rufewa in bar Batuul a gida tayi karatunta dan ta dage sai anyi mata aure", kallo kawai Aunty ke binshi dashi, cewa tayi "aure kuma uncle, nawa Batuul ďin take da za a fara mata zancen aure, ko 17 fa bata cika ba uncle, yaushe za a fara sata a lissafin aure, tayi zamanta a gida tayi karatunta, zan bata hak'uri tayi a gida, in yaso sai taje ko da msc ďinta ne a waje, by then zan yadda da aurenta", sai da tagama Baba yace "Allah ya tabbatar mana da alheri , ya zab'a mata abinda yafi alheri", ta amsa da "Amin", mik'ewa tayi ta ďauke cup ďin da Baba yasha juice ďinshi da ta kai k'asa ta dawo sama ta kashe musu wuta suka kwanta, tunanin maganan da suka gama yi da Baba ta rik'a yi, addu'a tayi daga k'arshe ta shafa ta kwanta ta barwa Allah komai A k'ofar gidansu Ajiddeh ya tsayar da motan ba tare da ya shiga ba, enveloles guda biyu manya ya mik'o mata, sai da ta karb'a sannan yace mata "Wannan tickets ne na masu zuwa ďaurin aure, mun riga da munyi chattering plane ďin, in bai isa ba gobe before 1 ki sanar dani dan 3 zamu tafi, ki faďawa Su Mum an gama readying komai har na sauk'an baki, kuma a ranan zamu juyo bayan an ďaura aure, daďi taji sosai , burinta na auren Aliyu Ahmad Kyari ya kusa cika, bata tab'a jin tana son mutum kamar shi ba , tsayawa tayi tana kallonshi kamar a mafarki, hure mata fuska yayi ya ďaga mata gira yana tambayanta ya akayi, rungumeshi kawai tayi ta shige jikinshi gabs ďaya, bayanta ya ďan bubbuga sannan ya janyeta, hannunta ya rik'e yana kallon lallen dake hannunta, "yayi kyau yace mata", da murmushi tace mishi "thank you baby, tun ďazu nake jira kace nayi kyau amma baka faďa min ba", kallonta yayi gaba ďayanta tayi kyau dagasken dan baima lura ba ďazu, gefen fuskanta ya shafa sannan yace "ai keh mai kyauce", wani daďi ne ya kamata ta rasa mey ma zata ce mishi, ce mata yayi "ni zan wuce gida yanxu , kuyi mana addua, zamu wuce gobe mu dawo saturday, so sai mun dawo kenan, kamar kar ya tafi ta rik'a ji, har wani ďan hawaye ne ya taru a idonta, buďe k'ofan tayi ta fita, sai da ta shige kamin ya ja motarsa yayi gaba, kamar ba su sukayi faďa ba ďazu, sha biyu saura ya isa gida, hayaniya ne ko ta ina kamar dare bai yi ba , ko ina kunne yake da haske, ďakinshi yaje yabi ta wata hanya da zata sada shi da ďakin Ammah saboda yawan jama'ar dake gidan, tura k'ofan yayi tare da sallama ya shiga, tana zaune da wasu manyan kwalaye a gabanta Sadiq na daga gefenta tana mishi bayanin wani abu, waje ya samu daga kusa da ita ya zauna kamar zai shige mata jiki, juyowa tayi ta dubeshi tace "Abu kaine da daren nan", kai ya gyaďa tare da cewa "nine Ammah , nazo ne muyi sallama tun yanxu dan gobe ba lallai mu samu time ba", Sadiq ne ya sake wane murmushi mai haďe da dariya yace "Yayanmu ango, daga gobe kuma ka zama posession ďin Hauwa", murmushi ya tare da girgiza kai yacewa Sadiq "you will never change" jujjuyawa yayi ya duba ďakin can ya juyo ya dubi Ammah yace mata "Ammah ina Farida ne", ce mishi tayi "Ai Farida tun da rana ta gudu gidansu Batuul, mita take ta yi min wai ana b'ata mata ďaki da toilet ita baza ta zauna ba, shine ta tafi wajen Batuul", sunan Batuul ne da Ammah ta ambata ya sashi tunata, kaďa kanshi yayi yace " Faridan Abui, ai da ta faďa wa Abui cewa zaiyi tazo ďakinshi", Sadiq yace "Riri akwai case", Abutturab ne ya sake matsowa kusa da Ammah, hannunta ya rik'e yace "Ammah gobe zamu tafi Maiduguri ďaurin aure, a yi mana addua Allah ya kaimu ya dawo da mu lafiya", kallonshi tayi na y'an dak'ik'u sannan ta shafa kanshi tace "Allah yayi maka albarka Abu, Allah ya tabbatar muku da alherin rayuwanku, ya baku zaman lafiya, ya azurtaku da zuriya ďayyiba, Babana you are taking a great step a rayuwanka, amana zasu baka ita, ka rik'e ta tsakani da Allah, in tayi laifi ka nuna mata tayi ba daidai ba, in yayi girma ka hukuntata daidai da laifin da tayi, ka zama mai yi mata adalci a koda yaushe, hankalin mace ba irin naku bane, kayi hak'uri da duk abinda zaka fuskanta , Allah yayi muku albarka", ji yayi duniyar tayi mishi wani iri, kamar an ďaura mishi wani abun mai nauyi, ajiyar zuciya ya sauk'e sannan yace "in sha Allah Ammah, Allah ya k'ara muku nisan kwana" shafa kanshi ta sake yi tace "Amin Babana", Sadiq dake zaune a gefe ne ya ciro handkerchief daga aljihunshi yana goge hawayen k'arya yace "wannan emotional moment ďin naku can melt a mountain, har kuka zaku sani", Ammah ce tace "saura kaima, ai kana hanya", dariya yayi tare da nuna kanshi da yatsanshi yace "Ammah ai ni yarone tukunna, mun bar manya sai sun gama tukunna" ya k'arashe maganan yana murmushi, ce musu tayi "in kunje gobe Yaa Mera ta sa a shirya komai da zaku buk'ata a shehuri na abinci, accomodation dama kun gama shiryawa ai ko" kai suka gyaďa mata a tare suka amsa da "ehh", tace "toh shikenan Allah ya kaiku lafiya ya dawo daku lafiya, Allah ya taimaka, ku tashi kuje ku kwanta yanxu dare yayi kuma kuna da abun yi", mik'ewa sukayi dukkansu biyu suka rungumeta tare da sumbatar goshinta sannan sukayi mata sallama suka fita Washegari k'arfe huďu jirginsu ya isa Maiduguri, motocine masu yawa suka zo taransu, samari ne gaba ďaya a airport ďin, sai da Abutturab, Massa, Sadiq da Abba suka tabbatar kowa ya isa masaukinsa sannan suka sukavbar airport ďin suma, gida yaje ya tarar da Abui zaune tare da mutane a palon gidansu, gaishesu yayi ya zo kusa da Abui sukayi magana ya haura sama, wanka yayi ya canja kaya ya fito , sake zuwa yayi suka yi magana da Abui sannan ya fita daga falon, mai gadi ya k'ira yace mishi ya ďan goge mishi mota zai fita dashi yanxu ya mik'a mishi key, zama yayi k'ark'ashin wani bishiya ya danna wayanshi har aka gama wankin aka dawo mishi da key, mik'ewa yayi ya karb'a sannan ya isa inda motar take ya buďe ya shige, rear mirror shi ya seta zai juya kenan idonshi ya hango mishi wani abu, hannu ya mik'a daga baya ya ďauko abun da ya gani, tsayawa yayu ya kafawa ďan kwalin dake hannunshi ido kamar mai karanta wani abu, ranan da ya fara ganin Batuul ya tuna, ya ganta a masallaci, sai kuma da Ammah tace ya maida Batuul gida, ranshi ne ya b'aci kamar ranan akayi abun, k'ofa ya buďe zai yar da ďankwalin ko me ya tuna kuma sai ya fasa ya mayar cikin safe keep ďin motar, tadawa yayi ya fita daga gidan, Muna guest inn yaje , buďe mishi k'ofa akayi ya shiga inda aka sauk'i abokanshi yaje , yana shiga yaga kowannensu har sun canja kaya, wasu na sallah wasu na cin abinci, alwala shima ya shiga yayi ya jagorance waďanda basuyi ba sallah , abinci ya ďebo bayan sun idar da sallah dan baici komai ba tun safe, yana cin abinci suna hira da abokananshi har ya gama suna ta hira Mik'a Batuul tayi daga kan gadonta, gaba ďaya jikinta baya mata daďi, tashi tayi taje tayi wanka ta dawo, agogo ta duba taga k'arfe ďayan rana, hannu tasa ta tada Farida, "ki tashi Riri, rana tayi", da kyar ta samu ta tada Farida, tashi tayi ta zauna akan gado tacewa Batuul "Nifa ban koma na kwanta ba tun asuba sai eleven shine kika tada ni", Batuul bata ce mata komai ba ta tashi taje saka kayanta, doguwar rigar atamfa ta saka, fita tayi daga ďakin ta tarar da Aunty a palon sama, gaida Aunty tayi sannan ta zauna kusa da ita ta jawo remote tana canja channel, Aunty ce ta tambayeta "Faridan fa, ya akayi kika fito kika barta", cewa tayi "wanka takeyi na fito na barta" tunowa tayi da mafarkin da tayi jiya, Juyawa tayi ta dubi Aunty ta cemata "Aunty jiya da safe da ina bacci nayi mafarki, wai ina kwance a wani falo babba akan gado, akwai rami a falon, wata farar mata ni banga face ďinta ba tazo tana tura gadon cikin ramin, wai sai ga wani mutum yazo yana tare gadon, shinefa wai da mutumin ya turani na bar kusa da ramin shi sai ya faďa ciki, amma ya samu ya rik'e wani k'arfe daga ciki yana mik'omin hannunshi in fito dashi, kuma har sunana ya sani, da farko Batuul yake ta cewa, daga baya ne ya fara cewa Fatima, shine na sauk'o daga gadon na rik'e mishi hannu ya fito dani, bayan ya fito ina ta so ya sakeni yak'i, sai kuma ga matar ta sake yowa kanmu, shine lokacin na tashi", saida Aunty ta gama sauraronta sannan tace mata "bakiyi addu' bane kamin ki kwanta" ta tambayeta, "nayi addu'a da zan kwanta, da na tashi ma jikina yana ta b'ari, duk jikina gumi, sai da nayi wanka nayi nafila tukunna na ďanji dama dama kuma da na tashi da safe zan faďa miki naga kun fita", "Allah ya rufa asiri, kina yawaita addua kullum ba sai kin kusa kwanciya ba, kuma next time in kinyi mummunan mafarki kar kina faďa, kinji", "toh" ta amsa da, Farida ce ta k'araso palon , wajen da Aabid ke kwance yana wasa ta k'arasa , zama tayi ta ďaukeshi tare da gaida Aunty, ansa mata da sannan ta tashi ta tafi Washegari asabar, ranar ďaurin aure, tunda yaje ďakin da ya sauk'a na hotel ďin bai kwanta ba, salloli da addu'a yayi sosai na Allah ya tabbatar musu da duk alheran dake cikin auren nan ya kawar musu da sharran dake ciki kuma sannan yayiwa iyayensu addua , tashi yayi ya shiga toilet bayan ya gama, wanka yayi ya fito yaje ďakin da sauran abokan nashi suke ya tada su suje masallaci suyi sallan asuba, duk ďakunan da ya san abokanshi da mutanen da sukazo ďaurin aure sun sauk'a sai da yabi ya tada su, wasu ya samesu idonsu biyu wasu kuma suna bacci, sai da ya gama ya wuce masallaci, bai shigo ba sai takwas, yana shigowa ya k'ara watsa ruwa, Massa ne ya shigo bayan ya fito daga wanka sanye da bathrobe fari, ko sallama bai yi ba ya fara "ango ango ka sha k'amshi", murmushi Abutturab yayi yace "nasan zanyi aure someday or the other but never thit would be this close, kamar ba ni zanyi auren ba nakeji", gefenshi ya dawo ya zauna ya dafa mishi kafaďa yace "There is time for everything bro, Allah ya sanya muku alheri" sannan ya mik'e ya fice daga ďakin, closet ďin ďakin Abutturab ya bude, kayane a jere iri iri, sai da ya saka under garmenta ďinshi sannan ya ďauko wata farar shadda , ďinkin dogon kaftan ne na zamani yayi kyau, sawa yayi tare da ďauko hula fari da blue da cuff links ďin kayan, agogon Hublot ya mak'ala bayan ya saka hulan, a cikin closet ďin ya ciro turarukanshi masu k'anshi ya fesa su , sai da ya gama tukunna ya ďauko bak'in takalmi daga k'asan closet ďin ya saka, juyowa yayi ya dubi mirror yayi kyau sosai, wayanshi ne ya ringing, sai da ya zauna ya ďauki wayan "salamu alaikum, Abui nda wattu", Abui ne ya amsa da "kelewa Alhadulillah, kuntashi lafiya", "Alhamdulillah Abui", "dama ina so ne in faďa maka ku shirya da wuri kai da abokanka, dan goma saura yanxu, kuyi hanzari kuzo kar a b'ata lokaci", a nutse ya amsa sannan suka katse wayan, Ammah ya k'ira bayan sun gaisa tayi mishi addu'a, Su Massa ne suka shigo su dayawa kowa ya sha gayu, Su Massa har da saka babbar riga kaman shinene ango, tun daga hotel ne photographers suka fara covering , na gida can ma sunayi, fitowa sukayi suka nufi inda motocinsu suke suka shishiga, motocine manyan gaske, su Benz, BMW, Audi, Range Rover...., convoy sukayi har wajen ďaurin aure, tun daga waje yake gaisawa da mutane har suka isa filin dake wajen gidansu Ajiddeh, k'arfe sha ďaya limami yayi announcing an ďaura auren Aliyu da Ajiddeh akan sadaki sisin gwal talatin.💖💝BATUUL💖💝 21 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* K'iran Ajiddeh ne ya fara shigowa wayanshi, kin dagawa yyi da farko don ya rasa gne haushinta yake ji ko akasin hka, ansawa yayi daga karshe tare da yi mata sallama can kasa "salamu alaiki zawjati", wani irin murna takeji kamar ta ganta a gabanshi, ta saki wani murmushi cikin muryarta me ddin sauraro tace "baby an ďaura, am officially yours now", murmushi kawae yayi hade da girgiza kai yana mamakin Ajiddeh ko kaďan bata jin nauyinshi ko kunya, cikin sanyin murya yace"In sha Allah forever" zata sake magana kenan wasu mutane suka zo yi mishi murna, ce mata yayi "hold on wife, zamuyi magana anjima, am busy over here", da murnan sunayen da ya k'irata yau ta katse wayan, daman mum ta faďa mata in ya aureta sai ya sota fiye da komai, gashi nan tun yau ta fara gani, gaisawa yayi da mutanen dake gabanshi, jama'a sai k'aruwa sukeyi suna mishi murna tare da yi mishi fatan alheri a rayuwan aurenshi, walima suka wuce daga wajen ďaurin auren a state hotel, k'arfe ďaya suka gama walimarsu suka wuce airport daga nan, a airport sukayi azahar gaba ďayannsu, 1:45 sukayi boarding plane, k'arfe uku dai dai sukayi landing a Nnamdi azikiwe international airport dake Abuja, basu isa gida ba sai biyar saura, a gajiye ya shiga bayan an gama kai mutane masaukinsu, Bayan su Batuul sun gama cin abinci, wajen k'arfe uku Aunty ta ce su shirya suje gidan Ammah, ita yau baza ta samu zuwa ba, in sunje gaisheta, sai sun haďu a dinner, dan gudun magana Batuul ko attempting saka abaya ma batayi ba, wani peplum blouse da skirt na atamfa ta saka, ta samu k'aramin pearl pendant ďinta da stud masu kyau suma ta saka, ta ďauki k'aramin mayafi ta yana a kanta, Addua take a gama bikin nan ko zata huta da yawon nn ita kam, Baa Liman suka sa ya kaisu, k'arfe huďu suka isa gidan, gidan a cike yake da mutane kowa nata hidima, gaishesu suka rik'a yu har suka isa ďakin Ammah, basu sameta ba a ďakin ba, ďakin Farida sukaje , da sauri Farida ta janyo k'ofar dan kamar ba ďakinta ba, side ďin Abui ta jawo hannun Batuul sukayi tana cewa Batuul "ni in zanyi aure baza a zauna a gida ba, dubi fa gidan kamar ba shi ba kuma fa masu aiki na ta gyara amma kamar basayi", "dama haka taro yake, sai an kwana biyu zakiga gidan ya koma daidai", suna isa side ďin Abui Farida ta murďa k'ofan ta shiga, Ammah ta tarar ita da Aunty Amna suna zaune a ďakin bak'i na side ďin Abui tana yi mata bayanin wani abu, ga robobi nan manya manya a gabansu cike da kaji da snacks, k'arasawa sukayi daga ciki, Farida ce ta fara gaida Ammah da Aunty Amna, sai Batuul, bayan ta amsa gaisuwan ne tacewa Batuul "Bitti sai yau na ganki tunda aka fara bikin nan, lafiya bakya zuwa", kai ta sunkuyar sannan tace mata "Ammah ina zuwa, shekaran jiya ma naje wushe wushe", " toh yayi , madallah, ďazu tela ma ya kawo kayanku na dinner na sa a ďinka muku, sai kuyi shiri anjima kuje kunji", toh kawai Batuul tace amma ba wai dan ta saka zuwan a ranta ba, suna zaune su Ammah kuma nata bayanin yadda za a kai kayan nan gidan amarya, mik'ewa Farida tayi ta fita, shigowa tayi ita da wata yarinya ďauke da plates a hannayensu na abinci, ajiyewa tayi ta zauna yarinyar kuma ta fita, cewa Batuul tayi ta taso suci abinci, mik'ewa Batuul tayi tazo kusa da ita ta zauna, ďan kwalin dake kanta ta cire ta ajiye daga gefen gadon sannan suka fara cin abinci, sallama akayi a k'ofa, Sadiq ne ya shigo ďakin , sai da ya gaida Ammah da Aunty Amna sannan ya zauna, Ammah ce ta dubeshi tace "kun dawo Sadiq, ya hanya, anyi lafiya babu matsala dai ko", kai ya girgiza tare da cewa "Alhamdulillah Ammah kunyi k'ok'ari mutane kamar turo su akayi a wajen ďaurin auren nan, komai ya tafi lafiya", cewa tayi "Alhamdulillah , dama haka nake son ji, Allah ya sanya Alheri, Allah ya basu zaman lafiya" dukkansu suka amsa da Amin, Farida ce tace "Yaa Sadiq shikenan yanxu Yaa Abu zai bar zama a gidanmu, shikenan daga shi sai kai, gidanmu zai zama daga Abui sai Ammah sai ni, zanyi abinda nakeso", dariya ma ta bashi yace mata "zama gadin gidan zakiyi ashe, ai nima sai kin rigani barin gidan nan, waye ma zai barki ki zauna, next year kema by now munje maiduguri har mun dawo", b'ata rai tayi tare da zumb'uro baki tace "Ammah kin ga Yaa Sadiq ko", kamar ba ita ta fara hiran ba, "Sadiq ka dena damun ta tana cin abinci", dariya yayi ya mike yace "Ammah bari inje in dawo", tace "okay sai ka dawo", Batuul ji tayi sun birgeta, inama tana da yaya itama, amma irin Sadiq ba irin Yaa Abu ba dashi bama a ganin dariyanshi, Sadiq na fita yayi hanyan su ya haďu da ango, tsaidashi yayi yace "Abui ya shigo gidane naganka a side ďinshi, ce mishi yayi "No Ammah na ciki, daga wajenta nake, yace "okay let me get to her", k'ofan falon Abui ya buďe, yana saka k'afa Batuul dake ciki taji gaba ďaya ta zama restless, bugun zuciyan ta ya fara, a hankali ta rik'a tauna abincin dake bakinta, k'ofar ďakin da suke ya tura ya shigo, cak komai ya tsayawa Batuul dan batayi expecting ďinshi ba at this time, k'anshin turarenshi ya cika ko ina na ďakin, da sallama ya k'araso ďakin yana kare ma mutanan ciki kallo snn ya zauna a gefen gado, Gaisheda Ammah dake ta binsa da kallo yayi ta amsa tana masa sannu da xuwa, sannan ya gaida Aunty Amna da ta dage sae tsokananshi take, Farida ce ta gaisheshi ba tare da ta kallesa ba, ba yabo ba fallasa ya amsa mata, sau ďaya ya kalli inda Batuul take ya ďauke kanshi, ita dai bata ce mishi komai ba gashi nan dab da ita ya zauna, xame hannunta tayi daga plate ďin ta cewa Farida ta k'oshi, Abuturrab na kallon Ammah yace "Ammah béri manyin, (Ammah inason abinci) banyi breakfast ba yau throughout bare inci lunch ga yamma tayi", Aunty Amna ce tace "wannan duk ďokin zama angon ne ya hanaka cin abinci" tana dariya tayi maganar, bai ce mata komai ba sae murmushin da yyi dan ya saba da tsokanar Aunty Amna, shi bai tab'a haďuwa da Aunty ďinshi mai tsokana kamar ita ba, Ammah ce ta dubi inda su Farida ke cin abinci ta lura da Batuul bata cin abincin, tambayanta tayi "bitti ya akayine bakya cin abincin", murmushi Batuul ta k'irk'ira tace "Na k'oshi Ammah", ce mata tayi "Bitti ďauko wa Abu abincinshi a palo, yana nan na shirya akan tray xa ki gani", a sanyaye ta mik'e tare da cewa toh, inda ta ajiye ďankwalinta ta duba zata ďauka taga akai ya zauna, bata ce mishi komai ba tayi hanyan palo, binta yayi da kallo har ta b'ace sannan ya ďauke idonshi tare da tabe baki a ranshi yace batason rufe kanta, dan yasha ganin gashinta on several occasion, mik'ewa Ammah da Aunty Amna sukayi suka fita dan sun gama abinda zasuyi, turowa kawai zasuyi a zo a ďauki kayan, inda Farida take zaune ya duba yaga tana ta faman dambe da k'ashi, ďauke kanshi yyi daga kallonta tare da jan tsaki, can ya sake dubanta gnin bata ma san yana yi ba sae fama da k'ashin take bayan ga nama me yawa a plate din yasa ya xabga mata harara yace "ke in baza ki ci abinci nan ba tashi ki fita, kin zauna kina ta kokuwa da k'ashi ko ina zaki kai na cikin plate ďin" zumb'uro baki tayi tareda kinkiman plate ďin abincinta tayi waje a ranta tana faďin "ohh masifaffe, mutum ran aurenshi ma sai yayi masifa ko ina ruwanshi da k'ashin da nake ci oho", ta fice abinta ya bi ta da harara. Bayan few minutes Batuul ta shigo ďakin kinkime da babban tray, saura kaďan ta sake tray ďin don wani irin faďuwa gabanta yayi ganin shi kaďai ne a ďakin, kanshi ya ďago ya ganta tsaye, ďauke kai yayi yaci gaba da abinda yakeyi a wayarsa, ganin ta fara gajiya da tsayuwan ne ya sata k'arasawa jiki a sanyaye ta shigo, a gabanshi ta sunkuya ta ajiye tray ďin , shi kuma gashin kanta da tayi parking in a messy bun yake kallo, yadda sukayi curls wasu na lilo ya zubawa ido, ďagowa tayi daga tsugunnen ta mik'e tsaye, tsayawa tayi a kanshi tana so tace yana zaune a kan ďankwalinta zata ďauka amma ta kasa bude baki, binta yayi da kallo yace "wa zai zuba min abincin kin wani ajiye kin nemi waje kin tsaya kina kallona, C'mon sense din ki bae baki cewar ba dungure min abincin xaki yi ki mike ba", bata kulashi ba sae wani hade rae da tayi ta tsuguna ta ďauki plate da serving spoon kanta a kasa tace mishi "mey zan zuba maka", ba tare da ya kalleta ba a takaice yace "anything", gima ta zuba mishi a plate ďin, daga gefe ta saka mishi scrambled potato mai cheese sai kémoniye a wani saucer, kallonta kawae yake har ta dago kai tana kallonsa tace " Ya isa?" Bae tanka ta ba sae sunkuyawa da yayi ya ďauki abincin ya fara ci a hnkli, ďagowa yayi da kanshi ya ganta tsaye tana fidgeting yatsunta kamar zatayi magana, kallonta shima ya tsaya yi sae dae fuskarsa a daure, sunkuyar da kanta tayi da sauri, shi kam bae fasa kallonta ba sae a nn ya kuma lura da yarintar ta, k'aramace ssae ya faďa a ranshi, a fili kuma cikin dakewar murya yace mata "get me a bottle of water", ba musu taje ďauko mishi ya bita da kallo har ta bude fridge ta dauko ruwan, kan ta juyo ya maxa ya sunkuyar da kansa, ta karaso ta mik'a mishi, hannu yasa zai karb'a taji hannunshi cikin nata, maza tayi ta sake ruwan ya faďi a k'asa, kallonta yayi tare da jan ďan k'aramin tsaki ya ďauki ruwanshi, ganin ta kasa mishi maganan ďankwalinta ne ya sata kawai ta fita haka, juyawan da tayi zata bar wajen kawai ta bige tumbler dake wajen , a take suka tarwatse a wajen, ba karamin rikicewa tayi ba ta daga k'afa da sauri zata matsa daga wajen ta tak'a ďaya daga cikin broken glass ďin, wani k'ara ta saki ta tsuguna a wajen, wani mugun kallo yake jefa mata kmr xae maketa, ita ko duk ta tsorata ta saka kuka, ganin jini a kafar ne ya sashi ajiye abincin hannunsa a gefe da sauri ya mike, tunawa da yayi lokacin da yake k'arami suna London, Aunty na koya mishi homework ďinshi ya ďauki blade ya yanke hannunshi dashi, rudewa tayi sosai har idonta sai da yacika da hawaye tayi mishi treating hannun, har sai da ya warke tukunna ta fara barinshi yana yin abu da kanshi, karasawa yyi inda take ya tsugunna dab da ita har tana iya jiyo numfashinshi a fuskanta, ga k'anshin turarenshi ita yayi mata yawa, hannunshi yasa zai janyo k'afarta tayi maza ta janye, tsaki yayi tare da janyo k'afan yana dubawa, glass ďin da ya mak'ale a k'afan ya sa hannu ya cire, wani ihu tasa tare da k'ank'ame shi, shiru yayi yaji yadda heartbeat ďinta ke bugawa da k'arfe, idonta ta buďe da taji zafin ya ďanyin sauk'i, da sauri ta sakeshi ta matsa baya ganinta kwance a jikinshi, tashi yayi ya koma gefen gadon ya zauna, yunk'urin tashi tayi itama zata tafi ta kasa, wani k'ara ta sake sawa, tasowa yayi ya dawo gabanta ya mik'a mata hannun alamun ta rik'e ya mik'ar da ita, nok'e hannayenta tayi, haushi ne ya sashi sunkuyowa ya ďauketa cak sae jin ta tayi jikinsa, ta wara ido ganin abinda yayi, k'ok'arin sauk'a ta farayi daga hannunshi, hade rae yyi ssae ya xuba mata idonshi masu kama da na masu jin bacci, hawaye ne makale idonta suna shirin zubowa, ce mata yayi "stay still, ciwo kikaji bazaki iya tafiya ba, am helping, ki tsaya in gama or ki sha mari ynxun nn, ina wasa da ke ne" yana hararanta ya kare mgnr, shiru tayi ta dena k'ok'arin sauk'an da take sae dae ba karamin faduwa gabanta yake ba, toilet ďin ďakin ya shiga da ita ya ajiyeta a bakin bathtub, shower ya janyo ya kunna ruwa yana zubawa a wajen tare da sa hannu yana wanke jinin da ya fara bushewa a wajen, rintse ido tayi ta dafa sa sabida zafin da wajen keyi, sai da ya gama ya sake ďaukanta cak ya fito da ita ďakin, a kan kujera ya kwantar da ita , ďakin Abui ya shiga ya ďauko first aid kit, dab da k'afanta ya zauna ya kamo k'afan ya shiga gogewa da spirit da cotton wool, ido ta rintse tsabar azaba ta rik'e hannunshi da sauri, sae kuma ta sake kuka, hannunta da ta rik'eshi dashi yabi da ido, ďauke hannun yayi daga jikinshi yaci gaba da abinda yakeyi, zafin ne yayi yawa tace mishi "Yaa Abu dan Allah ya isa haka, akwai zafi", dubanta yayi yaga hawaye take ssae ,ce mata yayi "clean your face and close your eyes, it wont hurt, beside raki ne yyi maki yawa", hakan tayi ta rik'e mishi riga har sai da ya gama dressing ciwon , tashi yayi daga wajen ya gyara mata k'afan ta kwanta comfortably, juyawa yayi zai fita tace mishi "Yaa Abu don Allah ka kira min farida", tsayawa yayi cak ba tare da ya juyo ba jin ta k'ira sunanshi sai da yaji abinda take buk'ata, ba tare da ya juyo ba yace "Anki" fita zaiyi daga ďakin kenan Farida ta shigo tana ihun "Batuul mey kika tsaya yi tun ďazu ina jiranki kizo kiga kayan da akayi mana, its f**ki....." bata k'arasa ba tayi maza ta rik'e baki ganin Yaa Abu a tsaye, dariya ne kawae Batuul bata yi ba ganin yadda ta haďiye maganan, a sanyaye ta k'arasa wajen Batuul tace "mey ya sameki, ya akayi kika ji ciwo har haka daga fitana" "Shut ur filthy mouth nd clean up this mess kafin in dawo" yana kai wa nn ya sa kai ya fita, da harara ta bisa snn ta dube Batuul tace "shi ya ji miki ciwon ko, ai nasani, kuma in yaga mutum yaji ciwo yafi kowa damuwa, garin yaya", kai Batuhl ta girgiza tace mata "Ba shine fa ya ji min ciwo ba, nice na fasa tumbler da na ajiye, dama ance everybody will b d first victim of his own corruption, gashi nan ni ya fara ji wa ciwo", tausaya mata Farida tayi tace "sannu", tambayanta Batuul tayi "mey kike faďa ne da kika shigo har da su f**king" ta k'arashe maganan tana mata dariya, "kayanmu ne na dinner, yayi kyau sosai, both d material and d style sunyi kyau sosai, sai ma mun saka tukunna", ce mata tayi "Dinner sai ku, ni yanxu ina naga k'afan zuwa dinner" a ranta kuwa hamdala tayi ta samu rusheshen excuse da xata bada dan dama bata son zuwa, a hnkli Farida tace "toh nima bazanje ba tunda bazaki ba", ido Batuul ta wara ta buďe baki tace "kinsan mey kike faďa , dan bazanje ba kema bazaki ba, ai sai in sa Ammah ta turaki dole, bare da ita ma za a ai dole kije", dariya Farida tasa tace "I wont miss it for the world wasa ma nakeyi, zanje kema kuma zakije yarinya", kamin ta bata amsa Ammah ta shigo ďakin, ganin Batuul a kwance yasata hanzarin k'arasowa inda suke, tambayanta ta shiga yi yadda akayi taji ciwo, faďa mata gaba ďaya, sai da ta gama tace mata "Toh yanxu ina Abutturab ďin, shine dan bak'in hali ya fita ya barki ke kaďai Kuma bai zo ya sanar dani kinji ciwo ba", "yanxun nan ya fita Ammah", Batuul ta faďa mata, taimaka mata sukayi ta tashi, har toilet sukaje da Farida tayi alwala ta fito, kaďan kaďan take ďingisawa, side ďin Ammah suka koma sukayi sallah suka fara shirin zuwa dinner dan Ammah tace babu abinda zai hanata zuwa, har da dan hawayenta don ba hka ta so ba. 💖💝BATUUL💖💝 22 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Shiri suka hau yi bayan sunyi isha da magariba, ďakin Ammah suka zauna suna dudduba kayan, lace ne purple mai ďan ratsi ratsin grey mai kyau, ďinkin ya amshsu soaai, iri ďaya akayi musu, sai da suka gama Ammah ta dubi Batuul "Bitti kunyi kyau, amma babu sark'a da ďan kunnefa, ke Farida ya baki bata ba, sai ki saka keh kaďai", hararan Batuul Farida tayi sannan tacewa Ammah "Ammah kiga jewellery box ďin mafa a gabanta yake, nace ta zab'i wanda zata saka tak'i wai baza ta saka ba", Ammah cewa tayi "A ah Batuul bazai yiwu ba, ina aka tab'a gaye babu ďankunne", mik'ewa tayi ta buďe closet ďinta ta fiddo wani ďan akwati k'arami mai kyau kmar chest box na katako, sai da ta zauna ta buďeshi ta fiddo wasu set ďin y'an kunne da sark'a masu kyau da abun hannu da zobe na azurfa harda agogonshi ta mik'awa Batuul, "ungo maza saka wannan", a kunyace Batuul ta karb'a ta saka, kamar wasu diamond ta saka haka ya dinga haske sabida tsabar kyan da yayi, sai da ta saka Ammah ta dubeta tace "Masha Allah ko kefa", wasu matane suka shigo dukkansu sunyi shiga ta alfarma cikin kayansu masu kyau, harda Aunty Amna a cikinsu, zuwa tayi kusa da Ammah sannan tace mata "Ammah motocin sunxo sunce a shirya a fito, tace toh sai kije ku fara tafiya, ni Sadiq ne zai kaini ku tafi tukunna", Farida ce ta fara fita, motan farko tabi, Batuul dake ďingisawa kamin taje motocin sun k'are, dawowa tayi tacewa Ammah babu motocin suntafi, a ranta tana murna Allah yasa babu wanda zai dawo, "ba damuwa, bari in Sadiq yazo sai mu tafi tare", tace "toh", ta hau gado ta kwanta, Takwas da kwata Sadiq ya k'ira Ammah uace mata ya iso, yana jiranta, wasu y'an matane sunsha kyau suma zasu wajen dinner suka ce mishi, tafiya zaiyi yace ehh amma Ammah yazo ďauka, suka ce mishi tunda ita kaďai ce bari su shiga dan har yanxu motocin suke jira su dawo, gaba ďaya bayan sunyi occupying saura seat ďin gaba kawai, tare da Batuul Ammah suka sauk'o, rik'e da hannunta a hankali suka taho sabida ciwon da taji, sai da suka zo Ammah taga mota a cike, ce mishi tayi "Sadiq ya akayi haka, ina Batuul ďin zata zauna", "Ammah bansan da Batuul ba shiyasa na ďaukesu", "Shikenan kuje da Batuul ďin , bari in k'ira Alai yazo in ya sauk'e mutanen da ya kai ya dawo ya ďaukeni, Bitti shiga kuje", Batuul dai na tsaye tana ta addu'an Allah yasa ma kar a samu space ďin, cewa Ammah tayi "a ah Amma, ke ki fara tafita ni sai a sa driver ya kaini ko Ahmad ne sai in k'ira ya kaini", bata rufe bakinta ba Ammah ta hango Abutturab yana tahowa, cikin tafiyarsa ta kasaita ya nufo inda suke yana gyara hulan kanshi, k'amshin turarenshi gaba ďaya ya baza wajen, baima lura dasu a wajen ba, sai da ya k'araso yaji muryan Ammah ya ďago ya dubi inda suke, ce mishi tayi "yawwa Abu ka shiryako", yace "ehh Ammah yanxu zan wuce sunata jirana" ce mishi tayi "toh ga Batuul nan ka tafi da ita, bana son barinta ita kaďai a gida ni zamu tafi tare da sadiq", Batuul da kanta ke sunkuye a k'asa tana wasa da abin hannun da Ammah ta bata ďazu tayi saurin ďagowa ta dubeshi jin abinda Ammah tace, ido huďu sukayi ya daka mata harara tare da ďauke idonshi daga dubanta, marairaicewa yyi yace "Ammah sai fa naje hotel mun haďu dasu Massa da sauran friends ďina tukunna mu biya in ďauka Ajiddeh, tabi Sadiq kawae, ke sai mu tafi tare", Ammah tace "ka ji ka. ina ni ina wannan yawon da ka lissafa, gara dai itan, kuje da ita kawae, kuma ai Ajiddeh ba duka motar zata cinye ba da kake cewa zaka ďauko ta, iyaka ta zauna a gaba, Batuul ďin ta zauna a baya", wani irin b'acin rai yaji gaba ďaya ranshi, wai mesa Ammah ke son haďa shine da yarinyar nan ko da yaushe, a tak'aice yace "muje", snn ya juya ya nufi wajen motarsa, Ammah ta cewa Batuul dake tsaye a wajen ta rasa mey ke mata daďi "Bitti kuje kinji", a hankali ta fara ďingisa k'afarta ta isa wajen motar, wani tsaki yaja ganin yadda take tafiya kamar mai tausayin k'asa, sabuwar lambo ce bak'a k'irin mai tint glass, buďe gidan gaba tayi ta zauna , yadda ya fizgi motan ne ya tsorata ta tayi saurin sa hannunta ďaya a jikin k'ofa ďaya a wajen hand brake tana neman wani abinda zata rik'e, jin hannunta tayi kan nashi, da sauri ta janye nata hannun ta dafa gaban motar, sai da suka fita tukunna Ammah ma ta shiga na Sadiq suka fita Gudu yakeyi akan titi kamar shi ya shimfiďa, tsabar tsoro har wani zazzabi ne taji yana son kamata, sanyi takeji sosai, hannu ta saka ta rage Ac dake aiki a motar, ganin ta rage Ac ne ya sashi juyowa ya dubeta yace "hw dare yhu! inamiki wasa ne zaki tab'a min mota, ko dan kin ganki a ciki" wayanshi ne yayi ringing ya duba yaga mai k'iranshi, bai ďauka ba har ya tsinke, haka ya dinga ringing wayan baya ďauka , daga k'arshe ma ya sata a silent, ita dai bata ce mishi komai ba, tunda abunda ke daminta ma ya isheta, ganin ya juyar da kanshi bai k'ara magana ba ta ďan kwantar da seat ďin motar ta ďanyi relaxing tare da lumshe ido dan kanta ya ďan fara ciwo , a hankali ya juyo ya dubeta yaga yadda ta jingina amma a takure, fuskanta ya kalla, idonshi ya sauk'a kan ďan k'aramin bakinta da aka sa mata purple ombre lipstick, kyabe baki yyi tare da ďauke idonshi daga kallonta yaci gaba da tuk'in shi, can ya sake juyowa ya dubeta, lashes ďinta da suka kwanto fuskarta ya kalla this time around, kamar zatayi magana ta ďan motsa bakinta, bin bakin yayi da ido, buďe idonta tayi taga idonshi akanta, da sauri ta mik'e ta gyara zamanta, shi kuma yyi saurin ďauke idonshi yayi ya mayar kan titi tare da jan tsaki, haushin kanshi yaji da ya tsaya kallonta har ta buďe ido ta ganshi, kuma fa ba wae tayi masa kyau bne, gyara zamanta tayi ta janyo kujeran, ta jingina kanta a glass ďin window tana kallon waje, a k'ofan hotel ďin yaja yayi horn aka buďe mishi ya sa kai ciki, motoci dayawa ya tarar na abokanshi suna jiranshi, duk sun shirya sunyi kyau, sauk'e glass ďin motar yayi tareda fitowa waje, inda suke ya isa, Massa ne ya fara tareshi "Kai fa wulak'ancinka dayawa Aliyu, ya zayi kazo ka bar mutane suna ta jiranka, kainefa da kanka kace babu african time 8 dot muna wajen , ana ta k'iran wayanka ma baka ďauka, har matar taka ma baka ďaukan wayanta tana ta damuna, har na rasa k'aryar da zan shirya mata ma ta yadda daga k'arshe", duk maganan nan da yakeyi Abutturab baice mishi komai ba, idon Massa ne ya faďa kan motar da Abutturab yayi parking , ce mishi yayi "Man ba cutie bace a motan can, mey takeyi a motan ka kuma", ba tare da ya kalleshi ba yace satota nayi zanje in saida ta, ya k'arasa wajen sauran abokan yana mik'a musu hannu, sai da suka gama gaisawa yace musu "kuyi hak'uri na b'ata muku lokaci, something came up, muje ko", kowa motarshi yaje ya buďe ya shiga, photographers na ta ďaukansu hotuna da video, bin Abutturab Massa yayi wajen motanshi yace "na tambayeka ya akayi ka taho da cutie kai da zakaje ďauko matarka ku wuce, ina zaka da ita, a hasale Abuturrab yace "bakaji bane, nace maka saidata zanyi" ya k'arasa wajen motansa, massa yace "Man i aint joking, am damn serious", yaje ya tsaya dab da widown da Batuul ke zaune yace "cutie", da hanzari ta ďago ta dubeshi, ce mata yayi "fito in kaiki a motana, tare zamu tafi", juyawa tayi ta kalli Abu, wani mugun harara da ya kada hanjin cikinta ya sakar mata, lkci daya ya dauke kanshi kamar bai san abinda suke faďa ba, da kyar ta iya bude baki tace " yaa Abu Bari in bi Yaa Massa tunda kaima zakaje....." tana k'ok'arin buďe k'ofa, cikin dakewa yace "come on get back, da kinsan da Massan kika tsaya sai da kika biyoni, kai kuma ka bari in na maidata kaje ka ďaukota ka kaita koma ina zaku, just follown Ammah's instruction" yana kai wa nn ya tada motarshi yaja ya bar sa wajen, tsayawa Massa yayi yabi motar da ido, toh mey Abutturab ďinnan ke nufine akan Batuul, haka rannan a wajen wushe wushe ya hanashi sakat, yau kuma ya hanata binshi, yasan kuma ba sonta yake ba, ina! dama ai babu batun so, kafaďa ya ďaga yayi hanyar motanshi, koma dai menene zaiji bayan bikin, shima convoy ďin motocin da akayi yabi a baya Allah Allah ta rik'ayi su isa inda zasu ta rabu dashi, gashi ya wani hade rae wane hadarin kaji, ko kwakkwaran motsi ta kasa a motar, mistakenly idan ta kallesa kuma ya xabga mata harara, gate ďin gidansu Ajiddeh ya shiga dan a buďe yake kasancewar ana biki, wasu motocin sun samu sun shigo, wasu kuma na daga waje, parking yayi, y'an mata ne dayawa duk sunsha kwalliya sunyi kyau, wata ce daga cikinsu ta iso inda motan Abu yake, tace "ango muna ta jira har amarya ta gaji da jira", a takaice yace "Ae gashi nazo ďaukanta, kuyi mata magana, ko kuma bari in k'irata ta fito", harara tabi Batuul da ganinta a gaban Motan Abutturab, sae kuma tayi dariya tace "No bari inje in fito da ita dan nima yanxun daga wajenta nake", ta juya ta tafi, Massa ne ya fito yacewa sauran y'an matan suzo su shiga motocin kamin amaryar ta fito, a hankali take takowa, tun daga nesa ake ganin kyan da tayi, kayanta sai walwali suke saboda hasken dake wajen, tana k'arasowa wajen motan ta tsaya tabi abinda take kallo cikin motan da ido, buďewa yayi ya fito tare da cewa Batuul "get back" a hnkli ta buďe k'ofan motar tayi ta fito, wani irin Kallo Ajiddeh tabi Batuul dashi baki bude, Batuul bata ma san tanayi ba ta buďe gidan baya ta shige, zagayowa yayi ta gabanta yace "wifey" yana kallonta tare da buďe mata k'ofan, wani irin kallo ta sakar mishi tace "Aliyu mey haka?, wane sabon wulak'anci ne kuma wannan, ya zaka zo ďaukana zamu tafi dinner sai kazo da wata, motan nan fa musamman mukayi order saboda in shiga ranan nan shine ka ďauko wata a ciki", shiru yyi yana kallonta sanin gskya ta fada, hannunta ya kamo ya wara mata manyan idonsa yace "c'mon its your happy day, meye dan wata ta shiga, Batuul cefa ba kowa ba, my cousin sis bbu motar da xata shiga ne shi sa Ammah tace in daukota nima ba a son raina ba coz ke naso ki fara shiga motar", a fusace tace "ai nasha faďa maka ni bana son yarinyar nan, wlhy hankalina baya kwanciya duk inda na ganta, kuma ya xaka yrda ta biyoka bayan ga motoci da drivers a gida", Iska ya furzar daga bakinshi a fusace yace mata "get in, in kuma baxa ki shiga ba ki koma gida" yana kai wa nn ya zaga mazauninshi ya zauna, sai da taga dama tana cika tana batsewa sannan ta shige motan, yana fita sauran motocin suka bi bayanshi , a conference hall akayi dinner, suna shiga mutane duk sun hallara, shi da kanshi ya fito ya buďe mata k'ofa ta fito tana ta b'ata rai tana cin magani, Aunty Amna ta fito ta samesu tace k'annen ango ne zasu shigo da amarya, tsayawa Ajiddeh tayi tana jiran taga su waye k'annen Aliyun da zasu shigo da ita, a hankali Batuul ta fara ďingisa k'afarta zata shiga hall ďin, Aunty Amna ce ta tsaida ita, Batuul tsaya ku shiga da amarya, Farida na fitowa, tana gama rufe bakinta Farida ta fito, su suka tsaya a gaban amarya kaďan , Batuul a hannun hagu, Farida daga hannun dama, sai Abutturab daga gefen Farida, kiďa ne ke tashi a hall ďin kowa yy kyau ssae, sae da suka shigo hall din Batuul tayi tuntub'e don dama ďingisa kafan takeyi, kan ta kai kasa Abutturab yayi maza ya rik'ota, shiru hall ďin yayi kowa idonshi da hankalinshi yayi kansu duk da basu karaso ciki ba gaba daya don da yawa sunyi xaton amaryar ce ya rike, xame jikinta tayi daga rikon da yyi mata ta karashe durkusawa wajen tana runtse ido hade da yarfe hannu, yana gnin hka shi ma ya bita ya durkusa da sauri yana kallon kafar yace "What?" Hawaye cike idonta tace "Na buge ciwona" Anty Amna ce ta taho da sauri don gnin abinda ya faru, Farida ta xaro ido tana kallon ikon Allah, Ajiddeh kam still tayi a wajen xuciyarta na bugawa da karfi. 💖💝BATUUL💖💝 23 By Phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Tunda ya rik'eta masu hotuna ke ta ďaukansu hotuna dan sun zata amaryarce, Ammah dake zaune can gaba tana hango lokacin da suka shigo har lokacin da Batuul ta bige ciwonta, a ranta taji inama Batuul ďanta ya aura, dan tana son yarinyar, tunanin cewa matar mutum kabarinsa da tayi ne ya sata kawar da zancen tayi musu addua zaman lafiya, Aunty amna ce ta k'araso da sauri ta rik'e k'afan Batuul ďin, babu abinda Batuul ke yi sai yarfe hannu, hawaye na ta zubowa ďaya na bin ďaya, ďagowa Abuturrab yayi ya dubeta yaga yadda hawayen ke zuba, ya hade rae yace "cmon shut up, mey aka yi miki kike ta wani kuka kamar yanxu kikaji ciwon, clean those tears ynxun nn", ya faďa yana kallon idonta, sauri tayi ta kawar da nata idon daga dubanshi, Aunty Amna ba tare da ďago ta dubeshi ba tana rik'e da k'afan tace "kai fa mugune Abuu, yarinyar tazo yi muku abin kirki taji ciwo shine zaka fara mata faďa, akan wane dalili, ka rabu da ita ka kama matar ka ku shiga ciki", Farida ce tace "Aunty Amna mu maidata gida mana in baza ta iya tafiya ba", shi dai bai tafi ba kuma bai ce komai ba yana tsaye a kansu, Sai da Aunty Amna ta ďago ta dubeshi sannan ta sake ce mishi "Abu kama matarka ku shiga ciki mana, zan kula da Batuul," sai da ya sake kallon fuskanta dake ta ambaliyan hawaye tukunna ya ja ďan k'aramin tsaki ya juya ya dubi Ajiddeh, tana nan a tsaye kamar ta kurma ihu dan takaici sae wani xufa take, hannunta ya rik'e sannan yace mata "wife muje ko", wani k'ululun bak'in ciki ne ya sake kamata, duk b'ata mata lokacin da yayi bai gani ba bare ya bata hak'uri shine ya wani rik'e mata hannu wai suje, ji tayi a wajen kamar tace ta fasa dinner amma sanin halinshi zai iya cewa ta tafi kawai ya sa ta bishi kmr Wanda aka xare ma laka, tana tunanin yadda zatayi da wannan yarinyar da yake ikirarin cousin ďinshi ce, dan tana sonshi kuma bata son ganin kowace mace ta rab'eshi ko da y'ar uwarshi ce, kae da ba dan in ta kasheta dole sae an hukuntata da gwara kawae ta daba mata wuka ta huta, da tunanin nn a ranta suka k'arasa MC na ta koďa su a wajen nan, sae dae Sam fuskarta bbu annuri xufa kawae take yi, Ammah ce ta k'ira wayan Farida dan duk hankalinta na kansu tace mata su shigo da Batuul ďin ciki, haka kuwa akayi , Aunty Amna da Farida su suka taimaka mata ta mik'e suka shiga hall, daga gaba wajen su Ammah ta zauna, Aunty na daga gefenta, tunda ta amsa gaisuwanta bata sake ce mata komai ba , bare ta tambayeta yadda akayi taji ciwon, MC ne ya fara magana da k'iran mai buďe taron addua, Aunty ya k'ira, she wasnt expecting it amma tunda aka k'ira ta tasan girmamata sukayi, tashi tayi taje tayi musu addu'a tare da fatan samun zaman lafiya da xuri'a dayyaba, data gama aka bi ta addua, daga nan aka k'ira abokin ango da k'awar amarya suzo su faďi biography ďin couple ďin, Massa ne ya fitowa Abutturab, ita kuma Ajiddeh k'awarta da taje k'iranta da Abutturab yazo ďaukanta ce ta fito, suna gamawa aka fara sauran events ďin, sai da akazo yanka cake ne aka k'ira iyayen amarya da ango, Ammah cewa tayi baza taje ba , Aunty da Yaa Mera suje kawai, haka kuwa akayi, daga nan aka fara rawa, ita dai Batuul tana nn inda take zaune, sai dai in daga ido taga idon Abutturab a kanta, da sun haďa ido kuma ya zabga mata harara, haka ma Ajiddeh da in ta maka mata wani hararan sae ka rantse kace idanuwanta xasu zaxxago, Batuul kam sae dae ta tabe baki a xuciyarta tace kwa ji da shi daga ke har mijin naki, daga yau ma ba lallai ku kuma ganina ba bare ku harare ni" ko lik'in ma kin tashi tayi ta musu, a haka dai har a gama dinner lafiya aka tashi komawa gida, Inda su Aunty sukayi parking nan Batuul ta ďingisa k'afarta taje ba tare da kowa ya ganta ba tun kamin mutane su fara fitowa a hall ďin, jiran Fitowan Aunty tayi daga hall ďin, sai da mutane suka fara watsewa tukunna Aunty ta fito, ganin Batuul zaune ita kaďai da mamaki ta k'araso tace mata "Batuul mey kikeyi a nan?"mik'ewa tayi tare da k'arasowa inda Aunty ke tsaye tace "gida zan bi ki muje", sai da Aunty tabita da kallo sannan tace mata "ban gane gida zaki bini ba, da ni kika zo dama ko kuma can ďin da kika baro ba gida bane", kmr xata yi kuma tace "Aunty ni kawai....", bata bari ta k'arasa ba ta katseta da cewa "kije ciki motoci na tafiya yanxu, na faďawa Baba ma can zaki kwana, tunda ke ba a abun arxiki dake sae na tsiya", jiki a sanyaye idonta duk ya cika da k'walla ta juya zata tafi, Aunty ce ta dakatar da ita da cewa "Batuul", tsayawa tayi for some seconds tukunna ta juyi tana k'ok'arin maida hawayen dake shirin zubo mata a fuska, juyowa tayi ta dubi Aunty tana jiran jin mey zata ce mata, cewa tayi "Batuul mey ke damunki, ya akayi kika ji ciwo", hawayen da ta ke ta k'ok'arin dannewa ne ya zubo , takowa Aunty tayi tazo gabanta ta rik'e ta tareda tambayanta "Batuul lafiya kike kuka, meye ya sameki, kinyi shiru ki faďa min, ciwon da kikaji ne?", kai ta girgiza, "toh meye" Aunty ta sake tambayanta, a hankali ta amsa da "babu", "Ban yadda babu ba, babu ne ya saki zuwa da cemin zaki gida ko kuma babu ne ya saki yin kuka", ita dai Batuul ta kasa cewa komai dan batasan ma mey ke sata kukan ba, cewa tayi "kawai inason komawa gida ne dan gidan da hayaniya ba zan iya bacci ba", ta k'arashe maganan tana share hawayen fuskanta, ba dan Aunty ta yadda da maganan ta ba tace mata "toh yanxu idan na koma da ke mey zaki cewa Ammah ya maida ki gida, ki bari tunda bikin ma ya k'are gobe sai ki dawo gida kinji" ta faďa mata tare da ďan dafa kanta, kai kawai ta gyaďa a sanyaye , "keh da wa kika zo ne ma", ajiyar zuciya tayi tace tare da Yaa Abu mukazo", Aunty batace komai ba tace mata "toh yanxu ki koma ciki, su Ammah ma yanxu zasu tafi, kiyi maza ku tafi, gobe sai Ki dawo gida ki huta abun ki", toh kawai tace, Baa Liman ne yazo inda motar ke pake yace "Hajiya zamu jira wani ne", tace mishi "a ah Baa Liman, yanxu zamu tafi", sai da safe Batuul tayiwa Aunty a sanyaye ta yi hanyan hall ďin, sai da ta jira taga Batuul ta shiga snn ta shiga mota suka tafi Ammah ta hango ita dasu Aunty Amna sai y'an tsirarun k'awayen amarya da y'an uwanta, inda Ammah take ta k'arasa , Ammah na ganinta ta mik'e tace "Batuul ina kikaje, inace kun tafi da Farida , yanxu na k'irata a waya tace baku tafi tare ba, daga ina kike", cewa tayi "Ammah hayaniya ne yayi yawa a hall ďin shine na ďan fita waje", ajiyar zuciya ta sauk'e tace "toh, da har munji tsoro kowa aka tambaya sai yace bakwa tare, sae Amnah tace kila kin bi mamanku, ga Abun ma can na tsai dashi nace sai ya maidaki ko kuma in an ji kina gida su wuce, mu sai munyi ensuring everyone is safe home zamu tafi", gyaďa kai kawai tayi dan yanxu ta yadda shiga motar Abutturab ďinnan qaddarar tace, Ammah ce tayi mishi alama da yazo, k'arasowa yayi giranshi na sama da k'asa a haďe, harara yabita dashi sannan yace wa Ammah gashi nan, "ku tafi toh tunda tazo, kayi maza kaje ka sauk'e y'ar mutane ta gaji", a tak'aice yace toh ya juya, ko ba a faďa mata ba tasan binshi ya kamata tayi, a baya ta bishi shi da matar tashi dake wani yatsine yatsine har wajen mota, shi ya buďewa Ajiddeh front seat ta zauna, shi kuma ya zagaya ya shiga side ďinshi, itako back seat ta zauna kanta a kasa, a nutse yake tuk'in hannunshi cikin na Ajiddeh yana yi mata magana k'asa k'asa tana ta shan k'anshi, da suka isa gidansu Ajiddeh ma fita sukayi suka barta a motan sai da sukayi wajen minti talatin a waje tukunna ya rungumeta kmr baxa su rabu ba daga k'arshe ya shigo dan da alama aikin lallashi yake ta yi, yana shiga motan sae da ya bari ya fita daga compound din gidan snn ya juya yana kallon Batuul fuskarsa daure yace "waye driver ki, c'mon kin dawo gaba ko sae na sauke ki a titi", ita dai bata ce mishi komai ba ta buďe k'ofa ta dawo gaba, sai da ya kama hanya ssae tukunna ya fara magana ba tare da ya kalleta ba "keh wato ni na zama driver ďinki ynxu ko, duk yadda za ayi sai kin samu yadda kika yi Ammah ta haďani dake koh, kin wuce kin tafi yawon ki kin ďagawa mutane hankali ana ta nemanki, inama kika fita kika tafi in d first place?" kinsa matan aure zama a waje duk da sunan jiranki, tunda ya fara magana bata ko kalli inda yake ba, shiru tayi bata kulashi ba, tsawa ya daka mata tare da cewa "ba tambayanki nayi ba, ina kikaje?" hawayen da tayi ta mayarwa ne ya zubo mata, kuka ta saka da karfi kamar wacce aka daka ta kifa kanta akan gwiwanta tana rerawa, sosai take kukan kamar ran ta zai fita, juyawa yyi yana kallonta, a fusace yace "wato ba a isa yi miki faďa ba shine zaki fashe min da kuka kmr wata yarinya, shut that mouth ynxu", kamar k'ara mata kukan akeyi taci gaba da kukanta kamar bata ji shi ba har da shessheka, tsaida motar yayi xuciyarsa na tafasa yace "fita min a motata", ko kallonsa bata yi ba tana ta aikin kukanta, da tsawa ya sake ce mata "i said get out,", ďago kanta tayi tareda share hawayenta ta dubi cikin idonshi tace "babu inda zanje, ka mayar dani wajen Ammah kace mata baza ka kaini ba mana", mamaki ne ya sashi sakin baki yana kallonta, dama tana magana haka, ranshi ne yaji b'aci, buďe k'ofa yayi ya fita ya zagaya ta inda kofarta take, buďe nata k'ofan yayi ya ce mata "out", tana zaune kamar bata jin abinda yake faďa, fixgota yayi ya fitar da ita daga motan da karfi ya juya ya koma nashi side ďin ya tada motan ya tafi, tana ganin tafiyarshi ta nemi waje ta zauna tana kuka ssae, iska ne ya fara kaďawa mai k'arfi tare sa walk'iya, ďankwalin dake kanta ta warware ta yafa a kanta tana hawaye, tana nn zaune aka fara yayyafi, duk'unk'une wa tayi waje daya dan sanyi yayi mata yawa ga tsoro don bbu alamar mutum wajen, ruwane sosai ya sauk'o kamar da bakin k'warya amma ko niyyan tashi ba tayi ba sae hade kanta da tayi da gwiwa tana kuka a hnkli, ruwan da ya ganine ya sashi parkin, snn juyar da kan motan a hnkli, cikin 'yan mintuna dawo wajen da take sbda gudun da yyi, fitowa yayi daga cikin motar ya isa inda take har lkcn yace "tashi mu tafi", kamr bataji shi ba ta ďauke kanta, sai rawar sanyi take, da taji zai isheta ne ta tashi tayi hanya daban da sauri jin ya biyota yasa ta saka gudu, binta yayi da hanxari ya fixgota, jiri ne taji yana ďibanta dan sanyin ya mata yawa, tangaďi ta fara zata faďi yayi sauri ya tarota jikinshi, mutsu mutsu ta shiga yi xata kwace kanta bugun xuciyanta ya tsananta, kin saketa yyi ruwa na dukansu, cak ya ďauketa daga karshe ya kaita cikin motan yayi mata baya da seat ďin ya kwantar da ita fuskarsa dab da nata har tana iya jiyo numfashinsa cikin kaushin murya yace " Idan kika kuskura kika fito xaki sha mamaki na" kasa motsi tayi daga gurin xuciyarta kmr xae fito don tsoro kamshin turarensa duk yabi ya isheta ga fuskarsa dake dab da nata har lkcn, da kyar take jan numfashi tsabar wani rawan sanyi da take, yafi minti uku yaki daga kallonta duk da ynda yaga jikinta ke rawa ssae, daga karshe ya mike ya rufe motar. Xagawa yyi maxauninsa ya Shiga, maimakon ya ja motar sae ya kasa, ya fi minti uku daga karshe ya juya yana kallonta yace "Batuul!",ya ji shiru bbu amsa, sau uku yana k'iranta yaga bata ko motsi, kafaďanta ya kama tare da jijjigata yana k'iran sunanta amma ko motsi bata yi, janyota yayi jikinshi da sauri ya kwantar tare da bubbuga mata baya, ko ba a gaya masa ba yasan she is unconscious ne, hnklinsa ya tashi ba kadan ba, all possible ways da yasan xae yi ta farfaďo yyi amma shiru, kawai yayi deciding da ya bata mouth to mouth respiratory aid, ďan kwalin da ta yafa a kanta ya cire, gashinta da ya kwanta lufluf yabi da ido, sunkuyo da kanshi yayi dai dai fuskanta tare da rintse ido yana k'ok'onton yayi ne ko kar yayi, but dats the only alternative, sai da ya kawo bakinshi daidai da nata idonsa na kan lips dinta hannunsa daya na kanta ta jawo wani dogon numfashi amma bata buďe ido ba, wani irin ajiyar zuciya ya sauk'e tare da komawa baya seat ďinshi ya zauna yana kallonta, sai da yaga ta fara motsa hannun tukunna ya lullubeta da dankwalin kanta bayan ya kashe Acn motar ya tayar ya jasu sukayi gida, suna isa gida yyi pakin ya fito ya ďauko ta a hannunshi kamar wata y'ar baby yana kallon fuskarta, mutanen gidan da sukazo biki waďanda basuyi bacci ba duk suka bishi da ido, bai bi ta kallon da suke mishi ba ya haura sama ya shiga da ita ďakin Ammah tare da sallama, Ammah na ganinshi ďauke da Batuul ta mik'e tsaye a rude tace "Aliyu mey hka, mey ya sami y'ar mutane ni Bilkisu, daga ina ku ke", bai ce komai ba sai da yaje ya shimfiďar da ita kan gado , ya kashe AC ďakin tukunna ya juyo wajen Ammah da damuwa a fuskarsa. 💝BATUUL💖💝 33 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Da sallama ta shiga ďakin taga bata nan amma akwatinta da jakanta na daga gefe, sai glasses ďinta dake ajiye kan mirror, zama tayi tana jiranta dan da alama toilet ta shiga, tana nan zaune ta fito tana goge ruwa a hannnunta da ďan k'aramin napkin, da gudu Batuul ta tashi taje ta rungumeta tana faďin, " *Yayya nyi kammo isi min gullèma, biya ngaima amme nya sorin*, Yayya ke kullum baki cewa zaki zo sai dai kawai a ganki kin faďo", Sai da janyeta daga jikinta tukunna tace " *dai fandoro letè chingya nyairo gullukin, kèrma dè fato tadanyi yero kadiko, fanuwa na*?, ku bari ranan da na tashi zuwa gidajenku sai in sanar daku amma yanxu gidan ďana nazo, babu izinin wanda zan jira kuna jina", dariya Batuul tasa tace "duk mey yayi zafi haka Yayya, namun ma in kin tashi zaki iya zuwa kai tsaye ba sai ki nemi izinin kowa ba", ta karashe maganan tana kallon Yayya da ta k'ura mata ido tana ta kallon ta, kai ta ďaga tareda da ďage girarta ďaya tace " *Yaaa kèrma dè ai yo do, wa shimmin rumin dè nyimai nya nèm shawan kongèna ro nonema*, Yanxu kuma menene kika zubamin ido kina kallona haka, kinsan ai ko a yarintarki baki kaini kyau ba, sai ma dai rashin tsayi da kikasa na biyoki da" tsaki taja tace " *ndu nyiro nyiro nyi shawasè gullono, u awo wallimin dè dai rukkin, rui futu ngam nèma dè, biya dai montindo jarawai adè na kwalluwa*, waye yace miki kina da kyan da har zan tsaya kallo, ja'ira ni wannan rama da kuma bak'in da kikeyi nake gani, wannan jaraba ta makaranta da bata k'arewa, gashi duk ya lalataki", rai Batuul ta haďe tace "kin fara ko, ni kinga ma ďakina zan koma", sanin da Batuul tayi sarai akan maganar da zasu shiga nan ne ya sata cewa zata bar mata wajen, cikin ďaga murya tace " *lenèmiya wande waltim yisimi, fuskam yaame yedai a, aima ba kènza gèi ya, nyai sammaso bannazèna, afuno gèi awo gade mananuwin a ba, kamme nyairo kanuri manaja shiro afunon mananuwin, Baan do dè gèrenge yishin ai, shima nyairo sèkèlima fayin ai*, in kin tafi karki dawo, da fuskanki kamar na uwarki, babu komai sai hanci da gashi da kika kwaso, duk ta fama b'ataku, inba Hausa ba babu abunda kuka iya, ana yi muku kanuri kuna maidawa mutumin magana da Hausa, ai ina nan ina jiran dawowan Baban naku, in shi ya koya muku duk zanji", ta gama faďa harda kalmashe k'afa, dariya abun ya bawa Batuul ta girgiza kai ta fita, D'akinta ta koma taje tayi wanka ta saka gown mara nauyi ta fito kitchen taya su Aunty aiki, k'arfe biyar da rabi suka gama aikin da zasuyi suka jera a dinning, K'arfe shida su Ahmad suka dawo daga Islamiyya, lokacin Baba ma ya dawo a tare suka shigo, sai da kowa yayi sallah tukunna suka sauk'o cin abinci, Aunty ce tacewa Batuul taje ta sauk'o da Yayya suyi dinner, ba b'ata lokaci ta haura sama suka sauk'o a tare, cup ďin ruwan da Baba ya ďauka zaisha ya maida ganin Yayya na sauk'owa daga bene, da mamakin ganinta ya mik'e ya isa inda take ya rik'o hannunta suka iso dinning ďin, sai da ta zauna tukunna ya fara gaidata, yace "Yaa baki cemin kina zuwa ba, kuma ko jiya saida mukayi waya dake fa", yaran ta duba sannan tace "toh garin naku wani nisane dashi, ko sae na nemi ixinin ka kafin in xo gidan ka," da sauri yace "A'a wllh ba hka ba yayya nayi mamaki ne kawae" ta dan kyabe baki tace 'a jiyan bayan mun gama magana da ka sanar dani abinda ke faruwa naga gara kawai inzo ayi ta ta kare, nasa Hamza yayi min booking jirgi na taho yau kawae", duk abin nan Aunty bata ďago ta kallesu ba sai da taji Yayya na cewa Baba ya sanar da ita abinda ake ciki tukunna ta ďago ta kalli Baba, cigaba da serving abincin tayi ganin yaqi kallo direction ďinta jikinta a sanyaye. K'iran Yaa Mera ne ya shigo wayan Ammah, farida dake xaune gefenta ta dauki wayar ta mika mata, Ammah ta daga tare da sallama, gaisawa suka yi snn Yaa Mera tace, "ashe Babana ya shigo gari, ďazun nan kawai na ganshi ya shigo wllh", Ammah tace "ehh ya kai sati yanxu ashe bae je gaida ki ba" Yaa Mera tace "Wllh kuwa sae daxu ya shigo min" Ammah tace "Ikon Allah, amma bae kyauta ba, nima dae ina nn shigowa Yaa akwae wata magana da xamu tattauna, ko xuwa gobe da safe in'sha Allah xan shigo" Yaa Mera tace "Toh sae kin xo" da hka suka yi sallama Ammah ta ajiye wayar tana kallon farida, hawaye taga idonta tana kkrin gogewa kadda Ammahn ta gani, da mamaki Ammah tace "Ya aka yi farida? Ya haka?" Shiru farida tayi tana share idonta, ganin ynda Ammah ta kafe ta da ido yasa a hnkli tace "Ammah why Batuul?" Ammah tace "Ban gane ba" wasu hawayen suka kuma xubo mata tana girgixa kai tace "Ammah Ya Abuu fa ba shiri suke da Batuul ba, ga kuma matarsa masifaffiya muguwa, Batuul baxa ta iya masu ba cutar ta kawae xa su yi tayi gashi ba kowa gare ta can ba, don Allah ku canxa shawara ko cikin family can Maiduguri ki samu dai dai Ajiddehn a aura masa" tsaki Ammah tayi tare da maka mata harara tace "Toh naki yin hkan, da Batuul kadae xuciyata ta Aminta a hada Aliyu, uwar me Jiddahn xata yi mata wanda Allah bae mata ba, shi kuma Abuturrab din idan aka aura masa ita yyi gunduwa gunduwa da ita ya maido mana," mikewa farida tayi har lkcn tana hawaye ta fita daga dakin. Xaune ta ga Abuturrab dakinta ya rike kai da dukkan alama ita yake jira, yana ganinta kuwa ya mike da sauri ya karasa ya kamo hannunta suka xauna gefen gado yace "In tambaye ki farida, wae wnn kawar taki or wat ever ita tace tana son aurena?" Shi kansa jin tambayar yyi wani banbarakwae a baki don yasan Batuul baxa ta taba cewa tana sonsa ba, he is just confuse, farida ta girgixa kai tace "I don't think Batuul tasan da xancen ma, don daxu ta kirani tana ban hkurin xuwan da bata yi yau ba," ya fuzar da iska yace "Do me a favour little sis, don Allah ki xiga ta a kan kar ta amince nasan dae in har tace bata so baxa a mata dole ba" farida tace "Shknn I will try my best, but ni baxan mata magana kai tsaye ba sae in ita ta kawo xancen don ga dukkan alama bata san abinda ke faruwa ba ma" mikewa yyi rai ba ddi ya fice daga dakin. Batuul na xaune dakin Anty duk hankalinta ya tashi ganin ynda uwar tata ke hawaye gashi ta ki gaya mata abinda ya faru, ae bata san lkcn da ita ma ta saka kukan ba tana durkushe kusa da Anty, da kyar Anty tayi controlling kanta ta shiga lallashinta sae dae ta k'asa gaya mata dalilin kukan nata don bata san ynda 'yar tata xata dauki xancen aurenta da Abuturrab ba, bude kofar dakin aka yi Ahmad ya shigo da sallama sae dae ganin ynda Batuul ke kuka hankalinsa ya tashi ssae don xuwa lkcn Anty ta daina nata kukan, hankali tashe ya shiga tambayar Anty abinda ya faru, Anty tace "kanta ke ciwo wae shine take kuka, ya aka yi Ahmad?" Ahmad ya durkusa kusa da Batuul yana mata sannu, sae da Anty ta kuma tambayarsa ya aka yi snn yace "Yayya ce tace in kira ta, kuma gashi kanta na ciwo bari kawae inje ince she's not okay" har ya mike Anty ta dakatar da shi tace "A'a bari xata je, ae ta sha magani" tayi hkn ne gudun wani maganan don har ynzu xuciyarta bae yi sanyin abinda yayya tayi mata daxu ba daga tace ita Batuul baxa ta auri mai mata ba in ma aurar da ita ake son yi gwara ta fito da saurayinta kawae, nn fa Yayya ta dinga xaxxaga mata ta inda take shiga ba nn take fita ba, mikewa Anty tayi daga karshe ta bar mata falon, shine tun lkcn take kuka a daki har Batuul ta shigo ta sameta. Kallon Batuul tayi tace "Tashi ki je Batuul" ba musu Batuul ta mike tana share hawayenta ta fita. Yayya na kishingide tana cin Apple, Baba na xaune daga gefenta ya tankwashe kafa suna magana da kanuri, k'arasowa cikin dakin Batuul tayi sae dae bata da walwala don tasan Yayya ce ta bata ma Anty rae ko bata fada mata ba, Xama tayi dan nesa da su tace "Ga ni Yayya" Yayya ta tabe baki ta mike xaune da kanuri tace "Wato har uwar taki ta xuge ki shine xaki wani shigo ma mutane ko sallama bbu, kin wani hade rae koh" Baba dae bae ce komai ba kansa na kasa, Yayya ta ci gaba da cewa "Toh auren Aliyu dae bbu fashi wllh, yaro d'an arxiki mai asali gaba da baya, waye bae san kakansa ba a Maiduguri?" Xumbur Batuul ta mike xuciyarta na wani mugun bugun da bae taba yi ba har wani rawa jikinta ya shiga yi tana kallon Kakar tata tace "Ban gane ba Yayya" da kanuri Yayya tace "Ohh ke da duk baki san abin da ake ciki ba, toh ae shirye shiryen bikin ki ake da Aliyu jikan Kyari, wato d'an wajen Ahmad" Batuul ta xaro ido cikin kidemewa tace "Ni Yayya?" Ae bata jira cewar Yayya ba ta fice da gudu daga dakin ta nufi dakin Anty, Har lkcn Anty na xaune ta xuba tagumi, ta xube jikin uwar tata cikin rawan Murya tace "Anty ban gane abinda Yayya take gaya min ba ynxu," K'asa cewa komae Anty tayi tana kallonta, hkn yasa Batuul ta fashe da wani matsanancin kuka tace "Wayyo Na shiga uku Anty, wae Ya Abuu ake cewa xan aura, ni ban gane ba" Rungume ta Anty tayi sae dae she's lost of words. Bayan Magrib Abuturrab na xaune daki abun duniya ya ishesa duk ya rasa tunanin da xae yi farida ta shigo tace "Ya Abuu Ammah na kiranka" mikewa yyi yace "kin yi abinda nace maki farida?" Farida tace "Ya Abuu bata fa ce min komai ba har ynxu, meaning she is still unaware, ni kuma baxa ta soma jin komai a bakina ba ka bari..." ficewa yyi daga dakin ba tare da ya tsaya jin sauran xancen nata ba, dakin Ammah ya shiga ya sameta tana waya, ya xauna har ta gama snn yace "Gani Ammah" Ammah tace "Dama cewa xanyi ka shirya kaje can gidansu Batuul ka gaida Yayya, ta shigo tun da rana" rasa me xae ce da ita yyi don bae son bacin ranta, da kyar yace "Toh Ammah" daga hka ya mike ya fita hankali tashe yasan shknn wani ikon Allah kawae xae hana a manna masa Batuul, wae for God's sake me suke son yyi da 'yar yarinyar nn?? Ya ma xae fara tunkarar Ajiddeh da wnn xancen, da kyar ya iya shiryawa ya dauki makullin motarsa ya fita daga gidan. 💖💝BATUUL💖💝 34 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Kuka sosai Batuul ke yi kanta kife jikin Anty dake hawayen ita ma, ďagowa tayi daga karshe jin Anty ta ki cewa komae cikin rawan murya tace "Aunty mesa za a min aure nida ke karatu, mesa Yayya ta matsu inyi aure har tasa Baba ya yadda zaimin ynxu, Aunty dan Allah ki tashi muje ki faďa musu banason yin aure, idan basu yrda ba to su canxa min wani mijin ba ya Abuu ba, don Allah Aunty ki tashi mu tafi nasan in kika faďawa Baba zai yadda", ganin Aunty ta ki tashi yasa Batuul mik'ewa har lkcn tana kuka tana faďin "Nasan in na faďawa Baba zai yadda, kullum duk abinda nace mishi yana min, wannan ma zanje in bashi hak'urin ince mishi karatu xanyi...." cikin hanzari Aunty ta mik'e ta tareta ganin tayo baya zata faďi, ta fada kanta, sabon kuka Aunty ta fashe da ta shiga girgiza ta ganin jikinta duk ya saki idonta lumshe, sunanta ta shiga k'ira tana cewa "Batuul, Batuul ki tashi kinji, babu wanda zai miki auren nan, wasa sukeyi miki dama, ki tashi yanxu zanje in samu Baba da Yayya ince suyi hak'uri, kiyi hak'uri ki tashi kinji Batuul, babu mai sake saki kuka, ki tashi muje tare Batuul", Batuul kam ko motsi batayi sai dai har lkcn hawaye na tsiyaya daga idanunta, wani ihun Aunty ta sake sawa tana jijjiga ta, buďe k'ofan ďakin akayi su Ahmad suka shigo jin ihun Anty, cirko cirko suka tsaya ganin kan Aunty kife jikin Batuul tana ta Kuka, da k'yar ya iya yin k'arfin hali ya ja k'afanshi ya k'arasa inda su Aunty suke, tsugunawa yayi dab da Batuul ya rik'o hannunta, ďayan hannun kuma ya ďaga Aunty, cikin sanyi yace "Aunty ciwon kan nata ne har yanxu", kasa bashi amsa tayi sai hawayen dake ta zuba daga idonta, juyawa yayi ya dubi sauran k'annen nashi da har lkcn sun kasa motsi suna nan inda suke sai hawayen da suma suka fara har y'an k'ananan yace "kuje ku k'ira Baba, yana ďakin Yayya", ya juya yaci gaba da murza hannun Batuul yana ďan jijjigata, ba a fi minti biyu ba da fitansu Baba ya shigo ďakin yana tambayan tana ina, ganinta kwance jikin Aunty ya kasa magana, sosai jikinshi yayi sanyi, yasan duk yadda akayi kan maganan auren nan da taji ne ya dameta, Bai sake cewa komai ba sai da ya sunkuya ya ďauketa cak sannan yacewa Ahmad, "ďauko key mu tafi asibiti", a bakin k'ofar ďakin suka ci karo da Yayya tana tambayar "meye ya faru wai, inata magana ja'iran yara kun qi kulani kun zuba min idanuwanku kamar na mujiya", ido ta wara ganin Batuul hannun Baba tasa ihu tana cewa na shiga uku ni Zara'u, mey zan gani haka, meye hakan wai kunyi min shiru, mey ya sameta, baza kuyi min magana ku faďamin mey ya samu Batuul ďin ba", babu wanda ya kulata a dakin, gaban Aunty ta k'araso tace "Maryam bafa nason wulak'anci, mey kuka yiwa Batuul ďin ina tambayanku kika min shiru, mayafi Aunty ta ďauka ta yafa tabi bayan su Baba ko kallon inda Yayya take batayi ba, tasan indai ta buďi baki toh kowa bazai ji da daďi ba dan ranta yayi k'ololuwar b'aci, hanyan Nizamiye hospital Ahmad yabi dan nan ne family hospital ďinsu, har lokacin bata farfaďo ba, suna zuwa cikin gaggawa aka karb'eta akayi emergency da ita, har lokacin babu abinda Aunty take sai kuka da addu'a Allah ya bawa y'arta lafiya, Abuturrab kam xaga gari yyi ya koma gida Karfe tara saura ya shige daki yyi kwanciyarsa. Washegari kamar yadda Ammah tayi alk'awari, k'arfe biyu ta shirya tayi gidan Yaa Mera, da driver ta tafi dan so take ya jirata su koma, a falo ta tarar da ita zaune ta mik'e k'afa dogaranta mata biyu na mata tausa, sallama tayi ta sa kai cikin ďakin, da fara'a ya Mera ta tashi ta yiwa y'an matan alaman su wuce, kansu a k'asa suka gaida Ammah sukayi waje, waje ta samu daga palon ta zauna tace "Maryam wannan gidan naki da tafiya yake, dubi duk na gaji", murmushi tayi tace "kai Yaya, ai babu wani tafiya kawai dai kin daďe ne baki zo ba", biyu ďaga cikin y'an matan da suka fitane suka shigo ďauke da manya tray ďauke da fruits, abinci, sai nama iri iri, direwa sukayi suka koma daga waje, Yaa Merace ta fara magana "jiya kawai sai ga Babana, nayi mamakin ganinshi, shine yake cemin wai yayi sati ma", ruwan dake kan tray ta ďauko ta ajiye gefenta sannan tace "ai yanxu ma zuwan nan dan shi nayi, auren Mustapha nan da sati biyu kenan ko, toh inaso a haďa ayi da na Abutturab, dan matar nan tasa bazan zauna in zuba mata ido su cutar min da ďa ya zama mara amfani ba", ido Yaa Mera ta wara tace "Yaya aure Babana zai k'arayi, yaushe? kuma wa zai aura?", kai ta girgiza tace "Maryam auren ne kawai zai min maganin halin nan da yake ciki, yaro gaba ďaya ya zama bashiba, shine nayi magana da Babanshi ya nema mishi auren Batuul, so nake ma a haďa da na Massa tunda saura sati biyu, in yaso sai ya koma bakin aikinshi da ita, dan yarinyar na da nutsuwa, kamar jinina nake jinta", kallonta Yaa Mera ta tsaya yi tace "Yaya badai Batuul ďin Maryam ba?", kai ta kaďa tace "k'warai kuwa ita", tace "toh Yaya ai na Massan ma jiya Babanshi ke cemin wai sun ďan ďaga, sun k'ara wata ďaya dan Mamar yarinyar bata jin daďi, yanxu haka an fita da ita waje, Amma Yaya baku tunanin ko Batuul nada wanda takeso, ko kunyi magana da iyayenta sunce bata da kowa, dan kar azo a shiga hakkin yarinya", Ammah zatayi magana kenan wayanta ya shiga ringing, ďauka tayi taga Farida ke k'iranta, recieving tayi tasa a kunnenta tace "Farida ya akayi", cikin shesheka tace "Ammah Batuul", cikeda da damuwa jin ta ambaci Batuul kuma tana kuka tace " Batuul kuma, mey ya sameta", cewa tayi "Ammah tana kwance a asibiti bata da lafiya, tun jiya she is still unconscious tun.....", Ammah bata bari ta k'arasa ba tace "Farida, kina jina, kije ki samu Abu kice mishi maza ya tashi ku tafi asibitin tare, nima yanxu zan wuce daga nan", maida kukan nata tayi tace "toh Ammah", suna gama waya ta mik'e tace "Maryam kinji, Batuul din ma ba lafiya tana kwance asibiti, yanxu gunta zani in duba ta", bakin k'ofa Yaa Mera ta rakota tayi mata sallama tace Allah ya bawa Batuul ďin lafiya ta gaisar mata da Anty, itama zasu zo dubata idan mijinta ya dawo, da haka sukayi sallama akan zasuyi waya. Hijabi kawai Farida ta ďaura kan top da wandon dake jikinta tayi ďakin Abutturab, knocking tayi taji bai amsa mata ba, buďewa kawai tayi ta sa kai, wani sanyi ne ya kaďa har cikin jikinta duk da hijabin dake jikinta, kai ta ďaga ta dubi Acn ďakin nashi taga yana lowest temperature, k'arasawa tayi daga ciki ta ďau remote ďin ta kashe Acn gabaki ďayanshi, yana kwance kan gadonshi rigingine ya ďaura hannunshi kan goshinshi idanunshi lumshe kamar mai bacci, a hankali ta k'araso cikin ďakin ta zauna daga bakin gadon, sunanshi ta shiga k'ira taji bai amsa mata ba, sarae tasan kuma idonsa biyu, ce mishi tayi "Yaa Abu Ammah cefa tace inzo in faďa maka ka shirya mu tafi asibiti", jin ta ambaci asibiti ya sashi buďe idonshi dake lumshe ya zuba mata su, bai tashi ba yace "waye ba lfya?", a hankali tace "Batuul ce bata ji daďi tun jiya, shine.....", wani tsawa ya daka mata, "tashi ki fita", a gigice ta mik'e sai da taje bakin k'ofa ta juyo tace mishi "Yaa Abu Ammah cefa ta aikoni", wani harara yabita dashi, ba shiri ta saki k'ofan tayi waje, tana fita ta k'ira Ammah ta faďa mata yadda sukayi da Abutturab, ran Ammah ba k'aramin b'aci yayi ba ta katse wayan ta shiga neman numbershi, jin wayanshi na k'ara ya janyo wayan, ganin mai k'iran yasashi saurin tashi zaune yayi recieving, yana ďagawa Ammah ta fara magana "Abu kana jina, bana son shashanci, in aiko yarinyar ta faďa maka sak'ona shine zaka korata, toh yayi maka kyau, ina kan hanyan zuwa asibitin, ka tabbata kamin in isa kana can", tana kaiwa nan ta katse wayan, ji yayi gaba ďaya kanshi na sara mishi, mesa Ammah baza tayi understanding ďina bane, mik'ewa yayi ya ďauki key ďin mota ya sauk'o k'asa rae ba ddi, a palo ya tarar da Farida zaune tana ta jimamin rashin lafiyar k'awarta, tana ganinshi ta mik'e, harara yabita dashi ya fita waje a fusacd, yana tafiya tabi bayanshi a ranta tana tausayin halin da k'awarta zata shiga in ta auri masifaffen nan, sai da ya shiga motar tukunna itama ta shige, bayan ya fita daga gidan ne ya tambayeta asibitin ba tareda ya ďago ya kalleta ba, faďa mishi sunan asibitin tayi daga nan ya ďau hanya. Suna isa asibitin da gudu Farida ta buďe ta fice, bata damu da hararan da yake binta dashi ba tayi wucewar ta ciki, k'in fitowa yayi daga motan har sai da Farida ta dawo tace mishi Ammah tace ya shigo, tana gaba yana biye da ita suka isa har ďakin da aka kwantar da Batuul, a VIP ward aka kwantar da ita, Su Aunty da Ammah na daga palon yayi sallama ya shigo kanshi a k'asa, durk'usawa yayi ya gaida Aunty, fuskanta babu yabo ba fallasa ta amsa mishi sannan yayi mata ya mai jiki tace mishi "Alhamdulillahi taji sauk'i", daga nan bai sake cewa komai ba sai hararar da Ammah ke jifanshi dashi da sun haďa ido, juyawa yayi zai fita Ammah tace "ka shiga ka gantan ne da ka juya zaka fita", juyowa yayi yana kallon Aunty yace "i tot ba a shigane dan naganku zaune a nan", murmushin karfin hali tayi tace zaka iya shiga , bacci take", ta nuna mishi k'ofan ďakin, a hankali yake ďaga k'afanshi har ya isa bakin k'ofar ďakin, hannu yasa zai murďa kenan wata nurse ta buďe k'ofan zata fita, hanya ya bata ta wuce tukunna yasa kai cikin ďakin, xaune ya ganta tana hawaye cotton wool a hannunta alamar allura nurse din ta mata, Yayya na xaune d'aga gefenta tana mata sannu, suna hada ido da shi gabanta yyi mugun faduwa ta gyara zip din skirt dinta da sauri, sunkuyar da kai yyi ya karaso ciki kmr bae son taka kasa, Yayya ta washe baki ganinsa tace "A'ah sannu da xuwa mai gida," gaisheta yyi murmushi dauke fuskarsa don ba laifi sun d'an saba, ta amsa da fara'a tace "Ehh ynxu da taku ce ta kawo ka ae na ganka, tun jiya na iso ban ga keyar ka ba sae ynxu da kishiyata ba lfya koh" murmushi kawae yake yace "Jiya ae na xo aka ce min kina bacci" ta yo waje da ido tace "Kai Haba, halan wnn yar bakin cikin ce tace maka hka" ta fadi ta na nuna Batuul da kanta ke kasa har lkcn gabanta na faduwa don ko kallonsa bata son yi, Abuturrab yace "Ae kam ita tace min kina bacci" Yayya tace " kaji bakin ciki kiri kiri, toh ko taki ko taso dae ni ce ta farko ita ta uku, bbu ynda xata yi" daga hka ta mike tace "bari dae in baku waje kadda inyi rashin hnkli" duk da Mood din Abuu sae da ta basa dariya, ya bi ta da kallo har ta fita, snn ya hade rae ya juyo yana kallon Batuul, hawaye ne ke sakko mata, ya kusa second talatin yana kallonta, kafin ya karasa gadon ya ja kujera ya xauna bbu yabo bbu fallasa yace "I knw by now kina da masaniyan abinda ke shirin faruwa koh?" K'in cewa komae tayi sae hawayen da take ssae, cikin rashin damuwa da shirun da tayi yace "Wato ke kika ce masu ni kike so knn koh?" Da sauri ta d'ago kai tace "Allah ya kyauta! ko kuma kai kace kana sona ba!" Ido ya kafa mata cike da mamakinta, ita kanta tayi Mamakin furucin nata don unexpectedly taji ya fito bakinta, ya mike tsaye yana mata wani irin kallo yace "Kinsan Allah kika kuskura kika yrda suka makala min ke, kin dauko hanyar tarwatsa farin cikin ki ne, ni ina da mata kuma ina sonta, infact ko bani da mata ma ni me xanyi da ke? Kawae daukan magana ne wnn, wllh tun wuri kice masu ke kina da wanda kike so, kar ki yrda a soma kai xancen nn da nisa idan ba hka ba...." Kuka ssae take har da shessheka tana kallonsa, hkn yasa ya kasa karasawa ya koma ya xauna xuciyarsa na masa xafi, can ya kalleta yace "Dama ki daina wnn silly tears din mu sama ma kanmu mafita ynxu, kina da saurayi ko baki da?" Wani kallo tayi masa ta dauke kai ya mike a fusace xae yi magana Ammah da farida suka shigo dakin. Sunkuyar da kai Batuul tayi, Ammah ta Karaso tana kallon Abuu da ya shiga shafa kai daga tsayen da yake, Ammah tace "Kukan me kike bitti?" Da sauri yace "shine nima nake tambayarta taki bani amsa tun daxu" Farida ta kallesa ta gefen ido ta tabe baki sanin karya yake ta xauna gefen kawartata da damuwa tace "Sannu Dear, I was so worried da Ahmad yace baki da lfya" Ammah ta xauna kujerar da Abuu ya tashi tana kallon Batuul tace "Sannu Bitti, ya jikin?" A hnkli tace "Da sauki ynxu" Ammah ta galla ma Abuu harara tace "A garin ku hka ake xuwa duba mara lfya empty handed?" Shiru yyi bae ce komae ba, ya rasa me yasa Ammah ke yi masa hka shi kam, gefen Farida ya karasa yana kallon Batuul yace "Me kike son in siyo maki?" Farida ta amshe tace "Fruits, Shawarma, Chill yoghurt da gasasshen kaza will do" harara ya maka mata rae a bace ya juya ya fice daga ward din, ko da ya dawo Ammah sun tafi da farida dake son xuwa yi ma Bestien nata girki ta dawo asibitin, Yayya ma Ahmad ya maida ta gida, Anty kadae ce ward din sa Batuul gaba tana cin abinci, don tun jiya rabonta da abinci, kansa a kasa ya karaso ward din, ledan hannunsa ya ajiye kan table din dake gefen gadon bayan ya kuma gaida Anty, Anty tayi masa gdya ta dauke abincin gaban Batuul sanin ba ci xata yi ba ta rufe, ta tattara komae a basket tace "Bari in je gida ynxu in dawo Abuturrab" yace "Toh sae kin dawo Anty" 💖💝BATUUL💖💝 35 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Aunty na fita ya jawo kujera ya zauna kusa da gadon yana kallonta, ita kam kanta a k'asa yake, dan ji tayi kamar ta bita su tafi, har ji take ďakin na suffocating ďinta, tabe baki yyi ya mik'e ya isa wajen da ya ajiye ledan da ya shigo da ya ďau wani bowl da Batuul ta wanke a hannu ciki da zata ci abinci ya zuba apple, grapes sai pomegranate a ciki ya bude table water dake wajen ya juye ciki ya nufi toilet, tana zaune ya fito ya zuba fruits din kan plate ya dawo ya zauna kan kujerar da ya tashi ya fara b'are pomegranate yana shan abin shi, Batuul kam kin ďagowa tayi ta kalleshi bare tasan abinda yake, cikin nutsuwa ya shiga maimaita mata maganan ďazu ya kara da cewa "yhu beta pretend yhu are nt recovering, ki kuma gaya ma likita auren dole xa a maki, I bet he will find a solution" ko kadan Batuul bata san mey yake cewa ba dan ji tayi abincin da taci yana son dawo mata tsabar tashin xuciya, ranshi ne yayi mugun b'aci ganin ynda tayi banxa da shi tak'i cewa komai, a fusace ya tashi ranshi a haďe, cikin tsawa yace mata "keh kurma ce ina miki magana kin wani min shiru kina jina, are yhu stupid", ko ďagowa batayi ba bare ta nuna mishi tasan abinda yake faďi, ranshi ne ya daďa b'aci yace "Kehh!" k'ala bata ce mishi ba, jin amae na shirin taho mata yasa ta tuge drip ďin hannun ta ta yunk'ura xata sauka daga gadon yyi saurin rik'eta yana mata mugun kallo yace "ina zaki?", hawaye ne ya shiga zuba daga idonta tana girgiza mishi kai alaman ya saketa amma yaqi, sai ma daďa rik'eta da yayi da k'arfi don mamaki reaction din nata ya bashi to ko dae ba ita kadae take ba, bai ankara ba kawai yaji ta kwararo mishi amai a jiki. Aunty na komawa gida tasa aka kawo mata Aabid dake wajen Fa'izah ta bashi abinci, dan rabonta dashi tun jiya da Batuul ta zama unconscious, tana gama bashi ta mik'ashi ta shiga yin wanka, fitowanta kenan daga toilet taga Baba zaune akan gado, har ta ďan tsorata, ganin shine ta k'arasa fitowa daga toilet ďin, dubanshi tayi taga ita yake bi da ido, ce mishi kawai tayi "Uncle sannu da zuwa", snn tayi gaban mirror, kwaso mayukan da zata shafa tayi ta dawo bakin gadon itama ta zauna, Kallonta yayi yadda takeyin abu kamar bata san yana ďakin ba, hannunta ya rik'o tare da cewa "Maryam", bata ďago ta kalleshi ba tace "Na'am", yace "ya jikin Batuul ďin, waye a wajenta", k'ok'arin maida hawayen dake shirin zubo mata tayi a hankali tace "Abu na wajenta, wanka nazo inyi in kai mata kayan da zata canja itama", matsowa yayi kusa da Aunty ya jawota jikinshi, hawayen da take ta k'ok'arin maidawa ne ya shiga zubowa, kuka sosai ta shiga yi mishi, patting bayanta ya shiga yi , bai hanata ba har sai da ta ďan tsagaita dan kanta tukunna ya ďago tareda da k'iran sunanta, ajiyar zuciya tayi tace "ina jinka", yace "Maryam yanxu akan nace zanyi wa Batuul aure shine kika bi kika ďagawa kanki hankali?" yayi tambayar yana kallonta, ganin tak'i magana sai hawayen dake zuba daga idanunta yasa yace "auren nan da zatayi kamata yayi kifi kowa murna, wannan yaron ďanki ne, kinfi kowa sanin waye shi, ke da kanki kinsan babu wanda Batuul zata aura hankalinmu ya kwanta da yafi Aliyu, da bakin ki kin yabi nutsuwarshi, toh sai yanxu dan zai auri y'arki shine kike qi, wani hali garesa da har baki son ba shi 'yar ki? Naga dae auren nan ko ba yanxu ba dole ta yishi, toh meye amfanin a barshi nan gaban bayan yin hakan shine gatan da zamu iya yi mata, kuma shine rufin asirinta da namu baki ďaya, inma karatunta kikeji, da kaina zan sa a nemo mata admission a can inda zatayi auren, babu abinda zai tauye mata karatun ta, kiyi hak'uri kiyi mata addu'a Allah ya bata zaman lafiya da kwanciyar hankali a duk inda zata tsinci kanta", jikinta ne yayi sanyi har yanxu hawayen na ci gaba da zubowa ta shiga gogewa cikin sheshek'a tace "Uncle Batuul k'arama ce fa, batasan meye aure ba bare abinda ke cikinshi, kuma fa mai mata zaku aura mata, abin ai zai yi mata yawa, kai da kanka kasan yadda Batuul ke da rauni, haka zataje a cutar da ita tunda ita ba wani wayo gareta ba", murmushi yayi tareda ďagota yace "yanxu naji dalilinki na k'in auren, bakiso y'arki ta auri mai mata saboda kema ke kaďaice gidanki ko, nima ďin ai zan k'ara", da sauri ta ďago tana kallonshi ya sake jawota jikinshi yana murmushi yace " Be optimistic Maryam, in kika nuna tsoron kishiya y'ar taki kuma tayi yaya, addu'a zakiyi musu Allah ya haďa kansu ya basu zaman lafiya, shi kuma Allah ya bashi ikon rik'esu da amana, sannan Batuul fa University take, tana second year ďinta, kinga ba yarinya bace, she is matured enough, she can decide what is wrong and right, tasan abinda zai cutar da ita da wanda zai amfaneta, mubita da Addu'a Allah yasa hakan ne mafi alkhairi", ya faďa yana goge mata hawayenta, da haka Baba ya rarrashi Aunty har ta hak'ura da zancen auren, tace Allah sa hkn shine mafi alkhairi. Su Ammah na isa gida tayi summoning chefs guda biyu, mace ďaya dattijuwa sai ďayar budurwa, order ta shiga basu na abinda takeso a dafawa Batuul kuma kar su ďau lokaci, waya ta ďauka ta k'ira Farida data haura sama, ba jimawa ta sauk'o, Ammah tace mata "je ki ďauko min computer yanxu kizo kimin ordering wasu abubuwa, babu b'ata lokaci Farida ta haura sama bata jima ta sauk'o rik'e da Macbook ďinta ta ďaurashi kan table ďin dake gaban Ammah sannan ta samu waje daga k'asa wajen k'afan Ammah ta zauna ta buďe system ďin tana k'ok'arin jonawa da internet, sai da ta gama taga yayi connecting to internet ta ďago tace "Ammah mey zakiyi ordering, Jumia za a shiga ko konga ko kuma universal shopping zakiyi? ta dubi Ammah tana dariya, zama Ammah ta gyara tace mata kayan lefen Abu nakeson haďawa, lokaci ya k'ure bazan samu aje a haďo kayan ba, shiyasa zanyi ordering komai", da sauri farida ta kalleta tace "Ammah wai auren nan dagaske kukeyi sai anyi, rashin lafiyan nan mafa da take nasan lbrn da taji ne ya sata" harara Ammah ta maka mata tace "sannun gyatuma, ai fimu son Batuul ďin kikayi, in baza kiyi abinda na saki ba tashi ki bani waje in Sadiq yazo anjima in sashi yayi min, xancen banxa kai", jiki a sanyaye tace "zanyi Ammah,mey za a duba miki yanxu, tace "customised designer akwatuna nakeso kimin order, wanda babu wani da za a sake yiwa irinshi sai ita", murmushi Farida tayi ta shiga surfing sai gashi ba b'ata lokaci tace "Ammah gasu nan da hotunansu, wai akwai na Macs n spencer, sai D&G, LV, Mandarina Duck, Versace, paclane, cartier, ralph Lauren da BOSS, Ammah suna da yawa mafa", sai da Ammah ta karb'i Laptop ďin ta ga pictures ďin tace "ki zab'i ten best kiyimin ordern su, kije credit card ďina yana kan shelf a ďakina ki dawo ki gama", Farida na fita Ammah ta ďau waya ta k'ira Aunty Amna dake Paris, sai da ya kusa katsewa ta ďauka, Ammah ce tace mata "keh kullum sai waya ya kusa katsewa kike ďauka, watarana har ya katse ma ba a samunki", tace "Ammah wayan ne tana hannunsu Nawwal basa barina dashi, yanxu ma ita ta kawo min a guje", Ammah tace "toh yanxu duk bama wannan ba, turaruka nakeso ki siya ki turomin da English Golds, Diamonds, Inner wears, vanity sets sai English wears, sai perfumes, shoes, da nighties sai bags" da sauri Aunty Amna tace "Ammah ba dai auren Sadiq bane ya tashi ban sani ba, yaushe za ayi, wace ma matar", ta tambaya with so much excitement sounding vry surprised, Ammah tace "A'ah ba shi bane", Aunty Amna tace "toh waye za a siyawa kayan nan haka da naji kaman lefe", ta faďa excitement ďinta na komawa ciki jin ba Sadiq ne zaiyi aure ba, cewa Ammah tayi "Aliyu ne zai k'ara aure", da mamaki Aunty Amna tace "aure kuma Ammah, yaushe yyi aure har yake son kara wani, wace matar da zai aura ďin, kardai Abu ya zama mai son aure aure fa", cewa Ammah tayi "Amna auren Aliyu na farko ba amfani ne dashi ba", tas Ammah ta gama gayawa Aunty Amna yadda auren Abutturab ďin na farko yake da dalilin da yasa take son ya k'ara auren, jiki a sanyaye jin abunda Ammah ta faďa mata tace "Ammah ni inace ma ni kaďai ya share baya nema, ashe har gidan ma hakane, toh Allah ya rufa asiri, wacece matar da xae auran yanxu", Ammah tace "Batuul", da sauri Aunty Amna ta karb'e tace "Batuul dai, Batuul ďaya da na sani?", Ammah tace "k'warai kuwa ita", guďa Aunty Amna ta sa tace "Ammah dama yarinyar nan nada hankali, sosai nakeson yarinyar tana birgeni, Toh Allah ya tabbatar da alheri, yaushe ne bikin, idan yara na hutu sai muzo kawai gaba daya" Ammah tace "ai next week kenan ďaurin auren, biki ko daga baya ne sai ayi", da mamaki Aunty Amna tace "Laah Amma, everything so fast, toh shikenan, zan duba sauran, amma Ammah perfumes ďin bazai yiwu su biyo plane ba, kuma in za ayi shipping zasuyi taking time, so akwai wani abokin Babansu Nawal yana da perfume shop a Aminu Kano crescent, yayi sabon order recently, so kawai zan mishi magana ya kawo har gida, inma container zaki duba, that will be better sai ku zab'a mata, amma sauran yanxu zan shiga in dudduba", Ammah tace "toh shikenan Amnah, zan turo miki kuďin sai kiyi siyayyan, yanxu zansa Farida ta turo miki sizes da details ďinta tunda k'awartace tasan komai", da haka sukayi sallama, suna gamawa ta shiga k'iran mai gold ďinta dake Dubai, yana ďagawa shima ta bashi order ďin Gold har na wajen 50 mil zai turo mata samples in ta zab'i waďanda take so sai a sakosu a jirgi a turo, shima da haka suka rabu, Farida ganin Ammah dagaske take kuma tasan kayan da k'awatar tafi so tace "Ammah a saka mata abaya a ciki, tana sonsu sosai", Ammah tace sai ki dubo mata suma online shima ki mata ordering ko set 30 ne", sai da ta tabbata ta gama order komai har atampopi daga London tasa aka turo mata su sai laces da lappayu daga switzerland, sai da tabbata ta gama tukunna ta tashi taje tayi sallah. Har ta gama aman bai saketa ba yana nan rik'e da ita duk ta wanke su gaba daya, murya can kasa yace " Srry!" Kkrin sauka ta shiga yi yaki sakinta, a hka wata nurse ta shigo ta samesu, da sauri ta karaso bakin gadon tana cewa "Wat happened?" Sae a snn Abuturrab ya sake ta, nurse din ta shiga yi mata sannu, shi kam unbutton din shirt din jikinsa ya shiga yi ya nufi toilet, nurse din ta shiga cire mata rigar jikinta ganin tana da vest a ciki, da sauri ta rike rigar taki barin ta cire mata, nurse din tace "Haba! you've messed the blouse, ki cire sae in baki wani abun ki lulluba da shi kafin a kawo maki kaya" bbu ynda Batuul ta iya hka nurse din ta taimaka mata ta cire rigar jikinta, ta sakko daga kan gadon, nurse din tace bari ta kawo mata wani abu ta rufe jikinta, Cleaners ta fara kira su je su gyara wajen su canxa bedsheet, Batuul na tsaye duk ta kagu nurse din ta dawo ta rufe jikinta kafin ya fito, ae ko sae gashi ya fito da singlet rike da shirt dinsa da ya wanke, suna hada ido ta juya masa baya da sauri ta ji kmr ta nutse wajen, dai dai nn nurse din ta dawo rike da hijab cleaners biyu na biye da ita, daya rike da xanin gado daya kuma na rike da bucket da mopper sae Freshner, da sauri ta karasa ta karbe hijab din tasa, ficewa yyi daga ward din bayan ya dauki makullin motarsa da wayarsa, ko minti biyar bae yi da fita ba Anty ta shigo rike da kayan Batuul a leda. Ammah ta bi sa da kallo bayan ta amsa gaisuwarsa ganin ya nufi stairs tace "Meye hkn Abuu?" Ba tare da ya kalleta ba yace "Amai tayi min" daga hka ya haura sama, farida ta saka dariya sanin ynda Amai ke bala'in irritating yayan nata sae gashi an masa a jiki, Ammah tace "Allah sarki, Allah dae ya bata lfya". Da daddare yana kwance kiran Ajiddeh ya shigo wayarsa, ya dde yana kallon wayar kafin ya d'aga ganin ya kusa katsewa. 💖💝BATUUL💖💝 36 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Yana ďaukan wayan ya hau ta da bala'i, "wai ba nace miki zaki iya tafiyar ki bane, wat are yhu still waiting for, in kuma ke da amaryar za a kai sai inji", kashe murya tayi cikin salo tace mishi "Babe na wuce fa tun ranan da kace min in koma, naga ko sau ďaya baka nemeni ba shiyasa na k'iraka yanxu tunda ni ina sonka ya na iya da halinka", kallon screen din wayar yyi, sae a snn ya lura da international Number ma ta kirasa, jin yayi shiru bai ce mata komai bane yasa taci gaba da cewa "Babe am missing you, wai yaushe zaka dawo ne, am so lonely without you here", d'an ajiyar xuciya ya sauke yace "soon, i gat things to do over hear, i will be back immediately when am done dear", ssae taji ddin abinda yace mata, cikin muryar shagwaba tace "Aii baby, i will be waiting, take care of yourself, i will also do that for you, bari in barka ka huta", da haka ta katse k'iran tayi wani murmushi a ranta tace zaka shigo hannu ne vry soon, baza ma ka samu k'afar zuwa Nigeria bama nan gaba bare har kaje kaqi dawowa har ka mance ni na kwanaki, wani irin dariya ta saki da ta tuna irin tanadin da takeyi a kanshi, shi kam lumshe ido yayi bayan sun gama wayan, aman da Batuul tayi mishi ne ďazu scene ďin ke dawo mishi kamar yanxu abin ke faruwa da yadda yaji jikinta yayi zafi lokacin da ya rik'eta, buďe idanunshi yayi ya mik'e ya nufi toilet yin alwalan sallar Isha don bai ma jin yau zai iya fita masallaci, yana fitowa daga toilet ďin Farida ta turo k'ofar ďakin, harara ya watsa mata yace "sallama ne baki iya ba ko knocking da zaki shigo min ďaki kai tsaye", dariyan dake cikinta ta mayar dan tun lokacin da taji Batuul tayi mishi amai da ta tuna take k'yalk'yalar dariya, tasan halinshi na k'in amai, maida dariyar tayi da sauri ganin yana k'ok'arin tada sallah tayi maza tace "Yaa Abu", bai amsa bama bare ya juyo ya dubeta, sake k'iran sunanshi tayi tace "Yaa Abu", tayi shiru ba tare da tace mishi wani abun kuma ba, wani mugun kallo ya jefeta dashi yace mata "fita min a ďaki", da sauri ta juya zata fita, ta tsaya daga wajen k'ofa ta lek'o kanta tace "Ammah ke nemanka fa", tana kaiwa nan ta fice da sauri tana dariya, sai da ya idar da sallah tukunna ya fito, a ďakinta ya tarar da ita Farida na daga gefenta, harara ya sakar mata ganin ta kafa mishi ido, daga gefe ya zauna yace "Ammah gani", dubanshi tayi tace "sae yanxu kayi niyyan zuwa kenan, toh abinci zaka kaiwa Batuul a asibiti, maza kuje tun ďazu aka gama na tura a k'ira ka baka ga daman xuwa ba", ido ya rintse tun da yaji inda zashi har sai da yaji tayi shiru tukunna ya buďe yana kallonta yace "Ammah ba driver na nn ba, wllh kai na sarawa yakeyi, ko Sadiq sai ya kaita in ma drivern bae nn kinji Ammah na", Ammah tace "bakaji inda nace zaka bane, in kaje kace su baka magani a can ďin, tashi kaje kar ku b'ata lokaci", mik'ewa yayi jiki a sanyaye ya koma ďauko key ďin mota, shi baisan mesa Ammah ke yi masa hka kan yarinyar nan ba, k'wafa yayi tunawa da yayi da aman da ta mishi daxu ya ďau key ya fito, a wajen parking ya tarar da Farida da masu aikinsu su biyu rik'e da basket ďin abinci, daga jikin makullin ya buďe musu k'ofa suka saka kayan daga baya shi kuma ya shige gaba hka ma Farida, sai harararta yake, itadai bata ce mishi komai ba har suka fita gidan, k'ira'ar Shuraim kadae ke tashi a motar. Bayan nurse da cleaners ďin sun fita Aunty ta taimaka mata tayi wanka ta saka kayanta mara nauyi da ta kawo mata, tea Aunty ta haďa mata tasha ta kwanta, tana kwanciya bacci ya dauketa, gyara mata kwanciyanta Aunty tayi ta gyara mata bargon sannan ta jawo kujera ta zauna gaban gadon ta zubawa y'ar tata ido tana tausayin halin da zata shiga, turo k'ofar ďakin akayi, Yayya ta shigo Ahmad a bayanta, ganin waďanda suka shigo ďakin yasa Aunty ta ďauke dubanta daga kallon k'ofar, k'arasawa cikin ďakin sukayi, daga gefen Batuul Ahmad ya tsaya zuciyarshi fal da tausayin y'ar uwarshi, rashin lafiyan kwana ďaya har ta rame, Aunty ya duba yace "Aunty yaushe sukace zasuyi discharging ďinta?", ya faďa yana ďan tab'a goshinta yaji temperature ta, Aunty tace "Yanxu doctor ya shigo ya duba ta, ta samu tayi amai, amma baice min yaushe zai sallametan ba", da jimami Ahmad ya sake cewa Aunty "Aunty wai mey ke damunta, meye doctor yace muku na damunta all of a sudden", caraf Yayya dake tsaye bakin window tana k'ok'arin ďaga labule kamar an sata ta karb'e maganan da cewa "mey ko zai sameta, daga na ce mata za a haďa aurenta da yaron nan yaron kirki Abutturab shine fa ta tada hankalinta har da rashin lafiya, ko xuga ta uwar tayi oho", jin abunda Yayya ke faďi ya dubi Aunty da mamaki yace "Aunty aure kuma, wai hakane dagaske?", "Au k'arya zanyi maka, toh tambayi uwar taka da bata k'arya sai ta faďa maka gaskiyan zancen, kuma ko nayi rantsuwa baxan yi kaffara va, ita ke daďa ingiza ta har aka kwantar da ita asibiti", Ahmad da ranshi ya fara b'aci jin tana aibata Aunty yace "Keh Yayya nifa bake na tambaya ba", "ehh ai nima ďin nasan ba ni ka tambaya ba, amsa ce na baka don nasan ba baka xa suyi ba", Aunty dae ko kallon inda suke bata yi ba dan ita tunaninta daban takeyi, Ahmad yyi tsaki yace "kinga zo mu koma, dama Baba cewa yayi in kawoki ki ganta mu koma, toh tunda ba ma dubatan zakiyi ba kizo mu wuce, dan ni in na tafi sai dai ki nemi mai dawo dake", masifa ta shiga yi ganin yayi hanyan k'ofa yana cewa Aunty zai tafi, Allah ya bawa Batuul lafiya, binshi tayi a baya tana ta zazzaga mishi ruwan bala'i har tana cewa sai tasa an karb'e motar ya dena tuk'awa tunda wulak'anci ne abun, suna fita Aunty ta tashi ta gyara windown da Yayya ta buďe, wayan Batuul da ta taho mata dashi ďazu ne ya fara ringing, mik'ewa tayi ta ďauki wayan, ganin mai k'iran yasa ta maida ta ajiye. Sai dare Batuul ta tashi lokacin har an idar da sallah magrib, da taimakon Aunty taje tayi alwala tayi Sallah, Ce mata Aunty tayi bari in shiga office ďin doctor, tun ďazu yake nemana kina bacci shiyasa ban fita ba, Aunty na fita wayanta dake ajiye gefenta yayi ringing, da kamar baza ta ďaga ba ganin mai k'iran yasa ta ďauka lokacin har ya kusa katsewa, a hankali murya can k'asa tace "Hello", wani irin ajiyar zuciya ya saki jin muryanta, shima murya kaman ta mai damuwa yace "Habibty dont do this to me again kinji, i was so worried abt you, tun jiya nake k'ira you werent picking, do you know how this affected me", shiru tayi tana saurarenshi idonta ya cicciko da hawaye tana tuna abinda Yayya ta faďa mata jiya, jin tayi shiru ta kasa magana yasa yace mata "you there", kasa mishi magana tayi sai kukan da ta fashe mishi da, har cikin ranshi yake jin kukan nata, kiďimewa yayi ya shiga tambayanta "Fatima mey ke damunki, ki daina kuka and tell me whats wrong with you, you are making me distressed, kina inane i will come right away...", da k'yar ta samu ta saita kukan nata tace mishi "Na'am", cikin shesheka, with so much concern yace mata "Its okay stop crying and tell me whats wrong with you kinji", har muryanshi na rawa, murya can k'asa tace mishi "I was sick", mik'ewa yayi tsaye daga zaunen da yake yayi hanyan ďakin Mummynshi, tambayanta ya shiga yi "mey ke damunki Fatima, kuma kina inane", a hankali tace mishi " Nima ban san mey ke damuna ba, I was admitted a asibiti tun jiya", ce mata yayi "Its okay, you will get better soon kinji, i will b on my way right away, take care of yourself", har ya katse wayan sai ya tuna ashe baima tambayeta wane asibiti bane, sake kira yayi ta faďa mishi asibitin da aka kwantar da ita, da haka ya katse k'iran ya karasa ďakin Mummy, zaune ya tarar da ita akan abin Sallah, zama yayi daga bakin gadonta yana jira ta gama azkar ďinta tukunna ta juyo ta dubeshi tace "Babana dama kana gida baka fita ba, ya akayi naga duk ka zama wani iri, what is it", ce mata yayi "Mummy Batuul, i mean Fatima ba lafiya, yanxu haka tana asibiti a kwance, Mum ki shirya muje mu duba ta kinji Mum", kallonshi take yadda ya rikice yana mata magana, bata tab'a ganinshi ya damu akan wata mace kamar haka ba, kanshi ta shafa tace "jeka canja kaya ka ďauko key kazo mu tafi", da hanzari ya mik'e ya fita, girgiza kai tayi tana addu'an Allah yasa son Batuul ya zame mishi alheri ta cire Rigar sallah dake jikinta ta shirya tafiya asibitin da ďanta. Batuul na gama waya zata ajiye taga an turo k'ofar ďakin, a zatonta Aunty ce ta shigo, Farida ta gani bakin kofar rik'e da Basket a hannunta, Murmushi ta saki tana kallonta, ba shiri murmushin dake fuskanta ya bace ganin wanda ke tsaye bayan Farida, sunkuyar da kai tayi da sauri, farida ta karaso ta xauna gefenta murmushi dauke fuskarta har lkcn tace "Waow Besty, I can see yhu are getting much beta ynxu, ga abinci na kawo maki, ur favourite!" Batuul tayi murmushi sae dae bata ce komae ba don ita ko kadan bata ji ddin dawowan Abuturrab ba, karasowa cikin ward din yyi ya ja kujera ya xauna fuskarsa a daure, farida ta sauka daga gadon ta nufi basket din abincin don dibar mata farfesun da tayi mata, Batuul ta kalleta tace "Don't wrry dear, am okay ynxu, bn dde da cin abinci ba, ltr sae in ci, hope yhu are spending d nyt here?" Farida ta wara ido tace "Y not love, ae da shirin kwana dama na xo" wani harara Abuturrab ya watsa mata yace "Ki gama abinda xa kiyi mu tafi, dnt waste my tym" Bata fuska farida tayi tace "but Ya Abuu Ammah fa ce tace in kwana wllh" mikewa yyi kmr xae maketa yace "Tafi mota ki jira ni" kuka ta saki, ganin ya yo kanta ta fice da sauri daga dakin, juyawa yyi yana kallon Batuul ya galla mata harara yace "C'mon sense din ki bae baki cewar hakurin filthy abinda kika min a jiki daxu ya kamata ki ban ba" ganin taki kallon inda yake bare ya sa ran amsa yasa ya karasa inda take yana mata wani irin kallo, bude kofar dakin aka yi Anty ta shigo, da sauri ya koma baya, Anty ta karaso cikin dakin ya juya kai a kasa ya gaisheta, amsawa tayi d'aga hka ta nufi inda wayarta yake ajiye ta dauka ta fita, Batuul ta dauki wayar ta da ya soma ring a gefenta ta dauka ganin me kiranta, "Hello love gani a hospital din ban san ward din da ku ke ba" satan kallon Abuturrab tayi ta ga idonsa kyar a kanta, ta sunkuyar da kai tare da dauke kai, a hnkli ta gaya masa ward nmbrn da take, snn ta katse wayar ta ajiye, shi kam har lkcn bae bar kallonta ba xuciyarsa na tafasa ganin ynda ta ki ko da kallon inda yake, Anty ce ta kuma dawowa dakin da mamaki take kallonsa tace "ga kujera Abuturrab, ya da tsayuwa" murmushi ya kirkira yace "Tafiya xan yi Anty" Batuul ta kalli Anty a hnkli tace "Anty Abubakar ya xo wae yana waje, na gaya masa ward nmbr" kallonta Anty tayi xata yi magana aka tura kofar dakin, kansa a k'asa ya shigo da sallama mum dinsa na biye da shi a baya, da fara'a Anty tace "A'ah sannun ku da xuwa" Kallon Abubakar kawae Abuturrab ke yi ko kiftawa bae yi, Anty ta ajiye ma mum dinsa kujera ta xauna tana kallon Batuul tace "Sannu Fateema, ashe baki ji ddi ba" Batuul da kanta ke k'asa ta dan yi murmushi cike da jin kunya tace "Ina yini Mama" Matar ta fa'da'da murmushin fuskarta tace "Lfya lau Batuul ya jikin?" A hnkli tace "Da sauki" tace "Allah ya sauwake" har k'asa Abubakar ya kai ya gaida Anty ta amsa murmushi dauke fuskarta tana tambayarsa ya aiki, yace "Alhmdllh Mumy" mikewa yyi yana kallon Abuturrab dake kallonsa har lkcn ya mika masa hannu, Abuturrab ya sunkuyar da kai suka yi musabaha, snn Abubakar ya juya yana kallon Batuul sae dae taki kallon inda yake, sae a snn Abuturrab ya ga daman gaida Mahaifiyar Abubakar ta amsa da fara'a, Mikewa Mumy tayi daga karshe ta nufi gun Batuul ta ajiye mata ledan hannunta tace "Toh fateema Allah ya kara lfya kin ji" Batuul tace "Ameen ngd Mumy" Mumyn ta kalli Anty tace " Hajiya ni xan koma Allah ya sauwake" Anty tayi mata gdya ssae, Abubakar yace "Momy ki jira ni gani fitowa ynxu" dariya Mahaifiyar tasa tayi tace "Dama ae xan jira ka" d'aga hka Anty ta rakata suka fita ward din, Batuul ta sace kallon Abuturrab ta ga kallonta yake, ga Abubakar da duk ya kagu ya fita ya basu waje da Habibtyn sa. 💖💝BATUUL💖💝 25 By Phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Tsayawa yayi ya zubawa fuskanta lumshashen idonshi, babu komai fuskanta daga dogon hanci sai lashes ďinta da suka kwanto a fuskan da ďan k'aramin baki, ya kai minti biyu yana kallon fuskanta ya ma rasa me yake kallo a fuskar, daga k'arshe ya dan ja tsaki ya tada motar sukayi gida, Batuul kam tunda ta kwantar da kanta bata ďago ba, parking yayi da suka isa gida ya kashe motar, jin an tsaida motan ya sata buďe idonta a hankali ta dubi side ďin da yake, maza tayi ta ďauke idonta don kallonta yake, buďe k'ofa tayi zata fita yace mata "wa zai ďaukar miki maganin", bata kulashi ba ta dawo ta ďauki ledan magani tayi gaba abinta, ďakin Ammah ta nufa, a hankali ta tura k'ofan ďakin tasa kai, babu kowa a ďakin sai k'anshi dake tasowa ta kowane angle, shiga tayi ta zauna kan gado tare da jinginar da kanta a jikin gado ta lumshe idonta, numfashi take sauk'ewa kamar wacce tayi wani babban aikin, buďe k'ofan ďakin yayi shima ya shigo, babu kowa sai Batuul jingine a gado, k'irjinta na heaving, a zuciyanshi yace "she is lazy, kamar wacce ta ďauko gari" tabe baki yyi yaja k'ofan ya rufe, falon sama ya tsaya zai k'ira Sadiq ya tambaye shi inda Ammah take, yana ciro wayan ya hango Ammah ita da ďaya daga cikin masu aikin gidan ďauke da babban tray suna hawowa sama, sai da suka hawo tukunna ya k'arasa wajen ta yace "Ammah mun dawo", ba tare da kalleshi ba tace "mey suka duba sukace ya sameta", ta faďa tare da tura k'ofar ďakin, sam shi baya jin daďin yadda Ammah ke yi mishi akan yarinyar nn, binta yayi shima jiki a sanyaye ya shiga ďakin, trayn hannunta yarinyar ta ajiye ta juya ta fita, sai da ta fita tukunna ya zauna ďan nesa da Ammah yace "pneumonia ne sukace yana son kamata, sunce ta guji anything cold sai ta rage yawan wasa da ruwa da shan abun sanyu", katseshi tayi da "wane irin ta rage wasa da ruwa, ai dama ba yi takeyi ba, kuma da k'yar aka samu ta rabu da wannan pneumonia tun tana k'arama yake wahalar da ita, sai da aka samu yarinya ta huta zaka sa ya dawo mata, ai da baka sata shiga ruwa ba da babu abinda zai sameta", a hankali yace "Ammah nace kiyi hak'uri fa, bazai sake faruwa in sha Allah, kiyi hak'uri", tana kwance bata buďe ido ba tana jiyo duk abinda yake faďa, wani ďan k'aramin murmushi tayi dan taji daďin yadda yake yiwa Ammah, ashe akwai waďanda yake jin maganarsu, "ai dama aikin kenan , da kayi abu ka fara bani hak'uri, k'arfe nawa zakuje gaisuwan iyayen?", sakin murmushi yayi dan ya gano cewa ta hak'ura tunda ta fara wani zancen, ce mata yayi "bayan azahar zamu je, sai dare kuma aje a ďaukota", "Allah ya kaimu , Su Aunty Amna sai suje su ďaukota, ba sai kun shiga gidan naka ba ai tunda kwana huďu kawai zakuyi ku wuce, tayi zamanta kawai a nan a side ďinka, kar a bata mata gida, duk ranan da kuka tashi dawowa gidanku ya zamana sabo", yace "hakan ma yayi Ammah, inaso inci abinci" ya faďa mata kamar wani k'aramin yaro, tray ďin ta nuna mishi tace "dama Batuul na sa akawowa, amma yana da yawa zaka iya ci a ciki, Ammah ce ta mik'e ta isa inda Batuul take ta tasheta taci abinci, har kan gadon ta bita da abincin, ta ansa, kasa cin abincin tayi da hankalinta sam yaki kwanciya, shiko ko kallon inda take ma bai yi ba sai abincin shi yake ci suna ta hira da Ammah, a hankali ta ďan tsatsakuri abincin ta tace ta k'oshi, mik'ewa yayi ya yiwa Ammah sallama akan zaije ya shirya suje gidansu Ajiddeh. Wayan hannunta ta k'urawa ido xuciyarta na bugawa da karfi ga wani mugun bacin rw da ya baibayeta, gumi yana ta tsatsafo mata, mesa takejin faďuwan gaba ne duk lokacin da taji sunan Batuul ko ta ganta, yanxu akan yarinyar nan Aliyu ya katse min waya harda yi min tsawa, danshi taji a fuskanta tana kai hannun taga hawaye a fuskanta, rai a b'ace ta mik'e ba tare da tasan mey zatayi ba, ďakin Mum ta nufa hawayen wani na bin wani, mata ne sun kai takwas a ďakin wasu kwance wasu kuma na cin abinci suna hira, ba sallama ta shiga ďakin tafaďa jikin Mum, kuka ta saka kamar wacce aka daka, a firgice Mum ta ďagota tana kallon jikinta taga ko da akwai abinda ya sameta, da taga jikinta lafiya ta tambayeta "meye ya faru haka, mey ya sameki, ko Aliyun ne wani abu ya sameshi", kasa magana tayi sai ci gaba da kukanta takeyi, Yaa zee sake gefe taja tsaki tace "waye kuwa in bashi ba, ai ďan wulakancin nan nema ko baku tambaya ba", tambayanta kowa ya shiga yi amma ta kasa basu amsa, sai da ta gaji dan kanta Mum na rik'e da ita ta ďago tace "Mum kefa kikace idan mukayi aure zai soni fiyeda koma..." bata k'arasa ba Mum ta tareta da cewa "toh meye ya faru yanxu", cikin sheshek'a tace "Mum katse min waya yayi harda min tsawa wai ya kai k'anwar shi asibiti, kuma ba k'anwarshi bace, ni bana son yarinyar nan, duk randa na ganta sai zuciyana ya rik'a faďi, har gumi nakeyi, ko a wajen dinner kuna ganin yanda ya rikice wai dan ta ji ciwo, mum na tsaneta wllh", sai da ta gama tukunna Mum ta mik'ar da ita tace mata "mey na yin kuka toh, ba wannan bak'ar yarinyar bace dai y'ar Maryam, mey zaiyi da ita yana da farar mata kamar ki, ko kuma kin tab'a ganin wanda aka yiwa kishiya duk zuri'armu, ai mun fi k'arfin kishiya, duk jarabar mutum sai dai ya rabu damu rabuwar kuma sai ya ďanďani kuďarsa amma ba dai yace zai shigo da wata matar muna ciki ba, kuma ke ďinnan da kike gani auren mutu ka raba, bare azo zancen kishiya, ki share hawayenki babu abinda zai faru dake", Yaa zee ce ta turo baki tace "Ammah nifa yaron nan bai kwanta min ba, ya rik'a wani huhhura hanci yana kallon mutane ďai ďaya, ni mugun haushinsa ma nake ji", juyowa Ajiddeh tayi cikin rashin kunya tace "ai ni dama bance mijina ya birgeki ba, kinje kin kaso aurenki kin kasa zama a ďakin miji shine zaki dameni da mijina bai birgeki ba, toh ni a haka nake sonshi kuma babu ruwanki dashi, a fusace Yaa zee ta mik'e tayo kan Ajiddeh kamar zata daketa tana faďin "da wa kike, maimaita abinda kika faďa yanxu inji in baki da hankali", Mum ce tareta da cewa "Mey kukeyi hakan wai, kuda zaku haďu ku rufawa kanku asiri kunkama kuna faďa, keh zainab babu ruwanki da mijinta, kema Ajiddeh babu ruwanki da ita" taja tsaki, Jainaba dake gefe itace ta taso ta ďago Ajiddeh tace "ke yanxu kukan na meye kikeyi haka, akan dan ya ďauki yarinyar ya kaita asibiti koko dan taji ciwo ne ya taimka mata kike kuka, share hawayenta tayi tace "Jainaba tun randa na fara ganin yarinyar kawai naji bana sonta, gashi mamarshi sai tayi ta haďashi da ita, haka ranan graduation ďinsu tace wani wai su biyu su tsaya ayi musu hoto, wlhy da na gansu tare sai da zuciyana ya kusa harbawa ga wani gumi da nakeyi kamar nayiwa sarki k'arya duk da sanyin da akeyi, ko jiya da zamuje dinner da ita yazo wai babu motoci a gidan sun k'are duk yawan motocin gidansu amma sai da ta haďoshi da ita, haka ma da aka tashi ta tafi yawonta sai da akayi ta nemanta duk sunbi sun ďagawa kansu hankali, ni wlhy bana sonta", sai da tayi shiru Janaba tace "toh meye alak'arshi da ita?", "ni ban sani ba, kullum ce min yakeyi wai cousin ďinshi ce, ban san ta ina ta zama cousin ďin tashi ba, ko a wajen wannan wushe wushen nasu kunga yadda abokanshi suka tsaya yi mata liki kamar itace amaryar, ni in bata dena shiga harkata ba Allah illatata ma zanyi", Mum ce tace "Ai ba wani alak'a na jini bane a tsakaninsu, abotace kawai a tsaksninsu na iyaye tun suna yara", kai Janaba ta girgiza tace "toh ita mamartasa mesa take son haďashi da ita kullum, ko tana son shi ne ya aureta", ďagowa tayi ta dubi Janaiba da idonta suka rine tace "babu wani, mey zaiyi da ita, kawai dai iko take nuna mishi na ita ta haifeshi dole yayi abinda takeso, kuma ni bata tab'a nuna bata sona ba", "toh ki kwantar da hankalinki, babu abinda zai sami aurenki indai muna raye, ku da zaku bar k'asar ma gaba ďaya, ki kwantar da hnklin ki kinji", kai ta gyaďa kawai ba tare da tace komai ba, haka suka ci gaba da hiran babu namijin da ya isa yi musu kishiya ko da ta wasa ce, da yadda za ayi da duk wani wanda yayi gigin cewa zai yi dashi da wacce zai auran. Convoy ďin motoci sukayi shida abokanshi bayan sallar azahar har gidansu Ajiddeh, daga waje suka tsaya ya k'ira wayanta, shi yama manta da ďazu ya b'ata mata rai, a dak'ile ta amsa wayan har yanxu ranta a b'ace, ce mata yayi "ki faďawa su Mum gamu nan mun iso, zamu shigo yanxu", tsaki taja tace "meye toh sai ka k'irani ne, ko gidan bak'onka ne", cire wayar yayi daga kunnenshi ya duba ya tabbatar da wacce yake magana, mayarwa yayi ya k'ara wayar a kunnenshi yace "Ajiddeh kinsan da wanda kike waya kuwa", "na sani mana , wanda ya daka min tsawa ya katse min waya akan wata Batuul....", ji tayi an warce wayan daga bayanta anyi sallama cikin natsuwa, Janaiba ce ta anshe wayan tace mishi "Aliyu har kun iso ne", bai nuna mata kamar sunyi komai da Ajiddeh ba yace "ehh muna bakin gate", tace "toh bari a zo a shigo daku", k'wafa yayi bayan sun gama wayan a ranshi yana zanyi maganin ki, bakinki bazai sake min tsaki ba, shi ba dan Ammah ma tasa shi zuwa ba wlhy da bazai zo ba, dan ya gaji da bikinma gaba ďaya, bayan y'an mintuna aka zo aka yi musu jagora, a guest room aka sauk'esu , duk matan suna parlourn lokacin, cikin girmamawa suka gama gaishesu sannan suka sa aka shigo musu da akwatuna dozen , suka ajiye musu bandir ďin dubu d'ai d'ai sabbi guda biyar, sannan suka yi musu sallama suka tafi akan anjima zasu zo ďaukan amarya, daga nan sukayi hanyan gidansu Abutturab ďin zasu gaida su Ammah, kai tsaye side ďin Ammah yayi dasu har sama, Batuul na kwance a palon sama tana kallon e tv, bata zata ba taji sallama, gashinta a buďe, da hanzari tamik'e daga kan kujerar, kamin ta tashi ta rufe kanta har sun shigo, idonshi ne ya faďa akanta , ido huďu sukayi, lumshesu yayi kamar mai jin bacci tare da galla mats hararara, juyawa tayi zata bar falon Massa ya tareta "haba cutie, sai kiyi ta wani b'uya, inata nemanki ina kika shiga ne", a tak'aice tace mishi "ina nan mana, kaine baka ganni ba", taci gaba da tafiya Massa na biye da ita, waje Abutturab ya bawa sauran abokan nashi suka zauna shi kuma yaje ya cewa su Ammah sun iso, a bakin k'ofar ďakin ya tarar da Massa ya juya zai dawo, bai kulashi ba ya buďe ďakin ya shiga, a gaban madubi ya tarar da ita, cikin dakewa yace "ki dena zamawa mutane a gida kai a buďe kina k'ira musu aljanu, kullum za a ganki kai babu ďan kwali", idanunta ta juya dan tasan masiface kawai yakeji da ita tak'i kulashi, ai ko juya idanun da tayi yasashi fixgota har ta kusa faďawa jikinshi tukunna tayi maintaining balance ďinta ta tsaya, duk da haka tana jiyo numfashinshi a fuskanta, "did you just roll your eyes, I mean ni kika harara?", yana tambayanta fuskarsa daure, tsoro ne ya sa ta kasa ansa mishi, kiciniyar k'wace kanta ta farayi daga rik'on da yayi mata idonta taf da hawaye, janyota yayi jikinshi ta faďa k'irjinshi, shiru tayi a jikinshi tana jiyo bugun zuciyanshi, sun kai kusan minti biyu a haka babu wanda ya motsa daga k'arshe ta samu ta k'wace kanta ta gudu ta shige toilet ta rufe, binta yayi da ido ya kai minti uku tsaye daga baya ya juya yyi kwafa ya fice daga ďakin, a palo ya tarar da su Yaa Mera, Aunty, Ammah, Aunty Amna da sauran Aunties ďinsu a zaune suna gaggaisawa, bayan sun gama gaisawa sukayi musu sallama suka tafi, su Ammah sukayi musu fatan komawa gidajensu lafiya, suka haďa musu guzuri dayawa. Da daddare akaje ďauko amarya, kuka sosai tayi kamin su fito kamar ba ita ke ďaukin ayi auren ba, sosai babanta ya zaunar da ita yayi mata faďa, wa'azi da Nasiha sannan suka tafi, a side ďin Ammah aka sauk'eta ita da y'an uwanta bayan su Ammah sun gama masu fatan alheri sukace akaita side ďin Abutturab, can dare wajen k'arfe goma ya raka abokanshi ya shigo ya tarar da Batuul da Affan zaune sun rakoshi yazo yi musu sallama dan yaje gida wajen Aunty tace mishi ai tana gidansu Farida, shima faďa Aunty tayi mishi kan in yaje school yayi abinda ya kaishi ya maida hankali ya kula da ibadunshi don gobe zai wuce, sunsha kuka sosai, bear hug tayi mishi tace zata koma ciki dan baza ta iya ganin tafiyanshi ba, Farida taje ďauko mishi wani abu, Abutturab ne ya shigo ganin su tare ya bisu da harara, komawa tayi daga ciki zata wuce ta corridor taji an fixgota, baki ta buďe zata saka ihu ya toshe mata baki da ďayan hannunshi, jikinta a sake yake dan bata da k'arfin yin kokawa dashi, dab da ita yake numfashinshi na bugun fuskarta, idonta da ya cika da hawaye yayi ja yake gani, lumshe idon tayi ba tare da ta buďe ba hawayen dake tare suka zubo, jikinshine yaji yayi sanyi , baya son ganin hawayen mace, sassauta rik'on da yayi mata yayi yace "wane moron ďinne ya biyoki har cikin gida kike hugging ďinshi, kasa yi mishi magana tayi dan tasan in ta buďe bakinta to kukane, janyota ya sakeyi yace "ba tambayanki nake ba, waye shi nace",a hankali ta buďe baki zata yi mishi magana ta kasa, sulalewa tayi a k'asa ta shiga rusa kuka, binta yayi ya kamota jikinshi, "mey aka miki kike kuka kuma yanxu, salon ki kuma hada ni da Ammah koh", ya faďa tareda ďagota yana hararanta, cikin sark'ewar murya tace "Affan , he is going", kallonta yayi sannan yace "who is he nace?", a hankali tace "my bestfriend, cousin, everything", dubanta ya sakeyi sannan ya saketa daga rik'on, jin ya sake ta ta ruga ciki a guje tana share hawaye, kusan kwana sukayi itada Farida suna jin tafiyar Affan, kamar ance musu bazai dawo ba. Ana gobe Abutturab da matarshi zasu tafi Batuul ta koma gida dan Ammah tace sai ta warke zata tafi, ko sau ďaya basu tab'a magana da Batuul ba, in ta shigo wajen Ammah iyakanta tabi Batuul da harara, itakam Batuul ďauke idonta takeyi tace kya ji dashi, ranan da ta koma gida Aunty take faďa mata Baba ya samo mata admission a Nile, tayi hak'uri da London university of economics ďin, bata faďa mata dalili ba, ranta baiso ba amma tayi addu'an Allah yasa hakan ne yafi alkhairi, a ranan da daddare yazo yiwa su Aunty sallama shida matarshi, sai da suka fara zuwa gidansu Ajiddeh tukunna sukayi gidan su Massa, haka sukayi ta yawo, wajen sha ďaya sukaje gidansu Batuul, tana kwance a parlour ita kaďai tana kallo taji bell na ringing, da mamakin waye mai buga k'ofa war haka ta tashi taje ta buďe, manyan idanunshi na masu kama da mai bacci ya watso mata, da sauri ta ďauke nata idon dan wani iri takeji ganin idonshi, matsawa tayi ta basu hanya suka shiga ciki, Ajiddeh bata sanma nan bane gidansu Batuul sai da taga Abutturab ďin ya matsa ta hango Batuul, tsaki taja itama ta shigo, hanyan sama tayi zata hau taji ya biyota a baya, sai da ta hau sama yana biye da ita tukunna ta tsaya, a dake ya ce mata "Aunty fa, i want to meet her", bata ce komai ba tayi hanyan ďakin Aunty, tafiyan a hankali yake kallo daga baya har ta shige ďakin, ya sauk'o k'asa, ďakinta ta wuce bayan Aunty ta sauk'a, samun kanta tayi da tsayuwa a bakin window tana jiran taga tafiyansu, ta daďe sosai tukunna taga sun fito, sai da taga tafiyan nasu tukunna ta faďa kan gadonta, bata murna kuma bata farin ciki, ta rasa gane meke damunta, washegari karfe tara jirginsu ya ďaga suka tafi UK. Alhamdulillah, a nn xan dakatar da rubuta littafin *Batuul* har xuwa bayan Ramadan idan Allah ya Kai mu da rae da lfya. Duk Wanda na bata ma knowingly nd otherwise, ya yafe min ni ma na yafe masa from the bottom of my heart, Allah Ubangiji ya karbi ibadunmu a wnn wata mai girma, ya sa mu cikin 'yantattun bayinsa don son ma'aiki S.A.W. Ramadan Kareem fanz. Urz *Phartiemarhk* 💖💝BATUUL💖💝 24 By Phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* "Wai ba magana nake maka bane Abu, mey ya sami Batuul ďin", Ammah ta fada tare da k'arasawa gadon da ya shimfiďar da Batuul ďin, jikinta ta tab'a taji yayi zafi rau, ďankwalin dake kanta ta cire mata shima taji shi a jik'e, a fusace ta juyo ta dubeshi tace "tun kamin raina ya gama b'aci ka faďa min abinda ya sami Batuul Aliyu", da damuwa a fuskanshi ya ďan dubi Batuul ďin da Ammah ke k'ok'arin cire mata jik'ak'k'en kayan dake jikinta tana kuma sauraran amsarsa, da kmr baxae ce komae ba don yasan ko ya buda baki gskya xae gaya ma Ammah don shi baya karya, gnin kallon da take jifansa da shi yasa yace "Ammah nifa banyi mata komai ba, muna tafiyane a mota ta rik'a min kuka ba gaira ba dalili, ni kuma i couldn't endure it nace mata ta fita min a mota, taki fita kawae na kamata na fitar da ita, nayi tafiyata, gnin ruwa yasa na koma na ďaukota muka dawo", baki sake Ammah ta tsaya tana kallonshi da mmki, rae a 6ace tace "hankalinka ďaya kuwa Abuturrab?, ka ma san mey kake faďa min? tsakiyar dare ka cewa y'ar mutane ta fita maka a mota, don rashin kunya kuma ka bude baki kke min tsari? mesa baka dawomin da ita kace baza ka ďauketa ba Aliyu, yanxu da wani abun ya sameta mey kakeso in cewa Maryam?, wato baza ka dena wannan bakin halin naka bako Abu, a haka mukayi maka auren aka baka amanar y'ar mutane da wnn halin xaka rike masu 'ya, maimakon da kaga tana kukan ka tambayeta kaji mey key damunta shine zaka koreta tsakar daren nn don rashin imani, Allah ya rufa maka asiri da wannan mugun hali naka, ni y'ar mutane da aka aura maka ma nake tausayawa", jikinsa yyi sanyi ssae don ko kadan bae son 6acin ran Ammartasa, har kasa ya durkusa kansa a kasa cikin sanyin murya yace "kiyi hkuri don Allah Ammah, ba mugun hali bane, kullum haka naga take kuka babu dalili kmr wata yarinya karama, plss ki yafe", katseshi Ammah tayi a fusace "rufe min baki, waye baisan Batuul yarinyar arziki bace, magana ma bata isheta ba kukan mey zatayi maka, ko a ina kke ganinta, in ma tayi kukan ina ruwanka da ita, nace ina ruwanka? Toh wlhy ka fita idona in rufe, wannan halin naka tun wuri kayi watsi dashi dan ba na arziki bane", ganin ran Ammah ba karamin bacewa yyi ba yasa ya marairaice mata kmr wani karamin yaro yace "Ammah nace fa kiyi hak'uri, don Allah kar kiyi fushi da ji, wllh hkn bazai sake faruwa ba in sha Allah, plss Ammah na" bnxa tayi masa na wajen minti biyu, shi dae har lkcn yana durkushe inda yake, juyowa tayi tace "nidai na faďa maka kuma ka tabbata gobe da sassafe ka shigo kunje asibiti , bazanyi taking risk ďinnan ba , zakaje ka halaka y'ar mutane sbda wani banxan hujja taka, in kai baka da hankali ni ina dashi", atishawan da Batuul tayi ne ya maida hankalinsu kanta, Da sauri Ammah ta zauna ta dagota ta zaunar da ita tare da ce mata "sannu bitti, ina ke maki ciwo", a hankali ta buďe idanuwanta tayi scanning ďakin, akan Abutturab ta sauk'e idonta, shima ita ya zubawa manyan idanuwanshi kamar mai shirin bacci har lkcn bae mike daga durkushen da yyi ba, baka tantance fushi yake ko akasin sa, maza tayi ta kawar da idonta daga kanshi ta cewa Ammah "sanyi nakeji", cikin hanzari Ammah ta mik'e tare da cemata "tashi bitti ki cire kayan nan jik'ak'k'u, ki canjasu kinji", k'ok'arin cire mata rigan jikinta ta fara, cikin jin kunya ta rike rigan tace "Ammah tulukin"(Ammah zan cire da kaina), sake mata tayi tana jiran ta cire taga kuma bata da alamun cirewa, ďagowa tayi ta dubeta tace "bitti cire mana, sanyin kar yayi miki yawa", ďago kai Batuul tayi ta dubi inda Abuturrab yake, idonshi kyam a kanta, sunkuyar da kai tayi, Ammah ce ta dubi inda Batuul ďin tabi da ido ta ganshi a durkushe ta hade rae tace "Mey kuma ka tsaya ka sata a gaba kana kallo, kaje kuma da sassafe kazo kai kaita asibiti", murmushin da bae shirya ba yyi a sanyaye ya mike yace "Sai da safe Ammah" snn ya juya , da yaje bakin k'ofa sai da ya kuma juyowa sukayi ido huďu da Batuul ta ďauke idonta da sauri ya juya ya fice, yana fita Ammah ta dubeta tace "Bitti, tashi muje kiyi wanka ki canja kaya, ni bansanma ina yarinyar nan ta karkaďa ba, ita taimaka mata ta cire kayan jikinta da sarkan da komai ta kaita toilet, ta haďa mata ruwan wanka mai zafi tukunna ta fito, Ammah na fita ta tub'e kayan dake jikinta ta shiga bathtub ta zauna a ciki, ta kai minti ashirin a ciki sai da taji ruwan ya fara hucewa tukunna ta fitodaga ciki, da bathrobe ďin da yayi mata yawa ajikinta ta fito, Ammah ta tarar ita da Farida har ta canza zuwa kayan baccinta zaune suna hira, Farida na ganinta ta mik'e cikin sauri ta isa wajen Batuul, rik'eta tayi tareda da zaunar da ita akan gadon a hankali tana kallonta kamar wacce aka ce mata Batuul zata karye in tayi k'wak'waran motsi, sai da ta tabbatar Batuul ta zauna tukunna tace "yanxu Ammah ke faďa min abinda ya faru, ni bansan baki tafi ba ai, na nemi ki a hall ďin ban ganki ba, daga baya Yaa Massa yazo yana tambayana ina kike, wai tare zaku tafi shi zai maidaki, toh i thought ma har ya dawo dake gida sai daga baya Ammah ke tambayana wai muna tare, sorry Sweetheart, bs nasha faďa miki Yaa Abun nan mugu bane kina k'in yadda gashi nan ai yana so ya illata mana keh, yanxu ai kya yarda, ni matarshi ma nafi tausayawa, ko da shike ma bana tausayinta tunda ita ta gani zata ita, tayi ta yiwa mutane kallon....", Ammah ce ta tareta da cewa "toh meye na maganan y'ar mutane zaki sa gabanta yayi ta faďuwa babu gaira babu dalili, bana son hiran mutane, ki dai yi na yayan naki tunda shi ya jawowa kansa da bak'in halin nan nashi", a marairaice Farida ta juyo ta dubi Ammah tace "Ammah dagaske nefa, sai waďanda taga dama take kulawa, a gidan nan daga Yaa Abu sai Sadiq take kulawa kamar su kaďai ne mutane", "toh keh meye naki a ciki, dama Abun ne dolenta a gidan ai, tunda shi tana kulashi ai an wuce komai, ke dai ina faďa miki babu ruwanki da ita", baki Farida ta zumb'uro tare da cewa "toh Ammah in sha Allah", Batuul dai bata ce musu komai ba, tana nan zaune tana ta tunanin abinda ya sameta yau, tunani tayi da yanxu wani abun ya sameta mey zai dawo yace ya sameta, wata zuciyar tace mayb yayi k'aryan shi bai ganki ba mana, ai gaskiyan Farida ne da take ce mishi mugu, Ammah ce ta katse mata tunaninta da cewa "Bitti shafa mai ki saka kaya ki kwanta kinji", ta mik'a mata mai da wasu rigunan bacci masu kyau riga da wando milk da brown masu kauri, sai da ta shafa man ta saka kaya tukunna tasa aka kawo mata abinci da magani tasha bayan taci abincin, Ammah ce tace su tafi wajen Abui su kwana dan nan ďin zaiyi musu hayaniya, hakan kuwa akayi, Farida ce ta taimakawa Batuul suka isa har side ďinshi, ko ina duhu an kashe wuta sai ďan hasken tv dake haskawa da alama Abui na ciki bai yi bacci ba, wani ďaki Farida ta shigar da Batuul tace mata ta kwanta zataje dubo Abui taga ko bai yi bacci ba, in yayi bacci zata kaso mishi tv ta dawo, tana fita Batuul ta jawo bargo ta rufe jikkinta dashi tayi kwanciyarta, Yana isa ďakinshi ya zauna a coffee chair ďin ďakin, kanshi ya dafa ya kai wajen minti 5 a haka tukunna ya mik'e daga k'arshe tare da jan tsaki ya cire jik'ak'k'en kayan jikinshi ya ďaura towel ya shige toilet, sai da yayi wanka tukunna ya ďaura da alwala yazo ya sa kaya tukunna yayi sallah, bayan ya gama addu'o'inshi ya hau ya kwanta, kasa baccin yayi, tunanin yakeyi daga gobe fah Shida Ajiddeh har sai mutuwa ce zata rabasu coz shi saki baya daga tsarinsa, ya rasa gane farin ciki yake ko bakin ciki, toh ya ma akayi na aureta ko tun can dama ina sontane, mik'ewa yayi cak daga kan gadon kamar wanda aka tsikara, kasa bawa kanshi ansa yayi kuma yasan babu mai bashi wannan ansa, yanxu komai nashi sai da Ajiddeh hatta gadon da zai kwana, shine komai nata yanxu a rayuwa, responsibility ďinta gaba ďaya ya dawo kanshi, he has to protect her with all his life kamar yadda zai yi protecting nashi, zuwa ya farayi yana kaiwa da komowa a tsakar ďakin, idonshi ne ya sauk'a akan hannunshi, glitters ďin jikin kayan Batuul ya gani da suka mak'ale mishi a jiki, duk da yayi wanka amma baisa sun bar jikinshi ba, zama yayi daga bakin gado yana bin duk inda glitters ďin yabi, tunowa yayi da ranar da ya fara ganinta har ixuwa yau ďinnan da yazo ya kwantar da ita kan gado, ranshi ne yaji yana mishi duk babu daďi, duk sanda ya ganta sai yaji zuciyarshi na yi mishi double flip, gashi Ammah kullum sai ta haďashi da ita har ya kai ga yau Ammah tayi fushi dashi duk a kanta, iska ya furzar daga bakinshi tare da cea damn it ya daki gadon da yake zaune a kai da k'arfi, yanxu gobe ma tace sai na kaita asibiti, da damu wa fuskarshi yace Allah ya kaimu. Abui da kanshi ya shigo ya tada su Batuul suyi sallah asuba tukunna ya wuce masallaci, a can ya haďu da Abutturab suka gaisa bayan an idar da sallah, ce mishi yayi ya sameshi idan gari ya waye ya amsa da toh kowa yayi side ďinshi, Su Batuul kuwa na yin sallah suka koma bacci, k'arfe 8 yayi side ďin Ammah dan ta shaida mishi yazo da safe ya kai Batuul asibiti a duba ta, yana shiga ya tarar da Ammah zaune itada wata y'ar uwar Abui, sai ya samu waje ya zauna tukunna ya gaishesu, babu yabo babu fallasa ta amsa mishi , sai kuma yayi shiru jikinsa yyi sanyi kalau, da dae yaga shirun yayi yawa yace "Ammah nazo muje asibitin", sai da ta gama abunda takeyi ta juyo ta dubeshi bbu yabo ba fallasa still tace kaje tana side ďin Abui, ka turota ta shirya ku tafi", "toh" kawai yace ya mik'e ya fita, yana fita matar ta dubi Ammah tace mata " Yaa Bilki ya naga kamar kina fushi da angon namu ne", ta tambayi Ammah, sanin halin matar Ammah tace mata "babu wani fushi, ai safiyace, bawai an gama watsakewa ba", kai matar ta gyaďa tace "gaskiyane, amma jiya kamar naga ya shigo da yarinyar nan da taji ciwo wajen dinner ďauke a hannunshi yana kallon fuskarta", surutun ne ya ishi Ammah tace mata "ni ban ganshi ba", sanin sarai Ammah tasan abinda take son sani ya sata ce mata "yanxu ki ďan jira Sadiq ya na shigowa zan tura shi ya karb'o" yana tafiya yana zancen zuci , mamakin irin yadda Ammah ta ďaukaka yarinyar yakeyi, toh wai meye ma da yarinyar da har xa ayi fushi sbda ita, wani dogon tsaki ya ja rae a bace ya isa side ďin Abui, ďakin da yasan zasu kwana ciki ya nufa ya tsaya daga bakin k'ofa, knocking yayi da farko yaji shiru, sake knocking yayi tare da tura k'ofan ďakin, a hankali Batuul ta mik'e tare da atishawa, idonshi ne ya faďa a kanta, hulan dake kanta ne ya faďi, sai gashinta da ya barbaje yabi bayanta, idonta ta kai bakin k'ofa dan ganin mai knocking ďin, da sauri ta mik'e ta wara idonta ganinshi a tsaye a bakin k'ofa, tada Farida ta shiga yi, a fusace Farida ta mik'e tana gungunin "yanxu kuma meye zaki tada ni", k'ofan ta nuna mata amma ta kasa cewa komai, yana tsaye sanye da farar jallabiya, tashi tayi da sauri itama ta zauna, tace "lahh" saukowa tayi daga gadon ta k'araso gabanshi da ladabi tace mishi "Ina kwana Yaa Abu", a takaice ya amsa mata da "lafiya", tsayawa tayi tana kallonshi taji mey zai ce ya kawosa, ce mata yayi "kice waccan ta fito mu tafi asibitin ina jiranta", juyawa tayi ta dubi Batuul sannan ta dubeshi tace "Yaa Abu da sassa...."harara ya bita dashi har bata samu k'arasa maganan ba tace "toh" ta rufe k'ofan ta koma ciki, a kan gadon ta tarar da Batuul tana zaune abinta, tana hangosu amma bata jin mey suke cewa, ce mata tayi "wai ki shirya ku tafi asibitin", "ni mey aka ce mishi yana damuna toh, ni lafiyata k'alau", Farida ce ta koma cikin bargo tace "kije ki faďa mishi mana, faďa min bazai yi miki wani amfani ba" ta juya ta kwanta abinta, Mikewa Batuul tayi tare da tsaki ta fice daga ďakin, yana daga parlour sama a zaune yaga tazo ta wuce tayi hanyar ďakin Ammah da kayan baccin da yayi mata yawa, sai yawo takeyi a ciki, shiga ďakin tayi ta gaida Ammah da matar dake zaune bata san ko wacece ba, "Bitti ya jikinki inji Ammah", da ďan murmushi ta amsa da "naji sauk'i Alhamdulillah", "Masha Allah ki shiga kiyi wanka ki fito ya kaiki a dubaki kinji, kar da akwai wani abun bamu sani ba", ba dan bata son musu da Ammah ba da tace mata batason zuwa, amma babu yadda ta iya, matar dake zaune duba sukayi ido huďu, ďauke idonta tayi dan wani harara ta sakar mata, ita bata ma santa ba, mik'ewa tayi ta shige toilet tayi wanka ta fito, ta saka babban hijab zata fita Ammah ta dakatar da ita tace mata "ina zuwa bitti", tace "ďakin Farida zanje in ďauko kayanta ďaya in saka mutafi", buďe wardrobe ďina akwai wasu kayan nata a ciki har da sabbi ki ďau ďaya ki saka", ta amsa da toh, matar nan sai bin Batuul take da ido, duk inda tayi akan idonta, duk tasa Batuul ďin tsarguwa, sai da ta ciro kayan ta koma toilet ta sakasu dan baza ta iya sawa ba a gabansu, abaya ce ta saka very simple, sai dai tsayin ya ďanyi mata yawa kasancewar Farida ta fita tsayi, ko mai bata shafa ba bare a samu ta taje kanta, chappette kawai ta shafa a lips ďinta da body spray da ta fesa tacewa Ammah ta shirya, ce mata tayi "toh kuje bitti Allah ya kara lafiya, yana jiranki", tayi mata sallama ta fita, a parlour ta tarar dashi yana zaune yana rik'e da remote, tsayawa tayi ba tare da cewa komai ba, ďagowa yayi ya dubeta yaga ta tsaya mishi a kai, tsaki yaja tare da mik'ewa a ranshi yana faďin shikenan yarinyar nan ta gama rainashi, dan ko gaisheshi ma batayi ba, kuma duk Ammah ce ta ja masa, a baya ta bishi har suka isa inda motar ke pake, wata infinity brown mai tint taga ya nufa, itama shi ďin tayi, sai da ya buďe tukunna itama ta buďe ta shiga, sai da ta zauna tukunna ya kunna yaja suka tafi, suna cikin tafiya turarenshi yayi mata yawa ta fara atishawa, tunda ta fara bai juyo ya kalleta ba sai da tayi na uku, juyowa yayi ya dubeta with irritation, ďauke kanshi yayi daga dubanta, yana juyawa ta sake jero biyu, rae a bace yace "kiyi using handkerchief mana, you cant b spreading it anywhere", bata ko kalleshi ba ta sake jero biyu, k'wafa yayi tare da kashe Ac motar yasan ko ba komai shi yayi contributing wa atishawan, yana kashewa kuwa ta rage yi continously sai dai jefi jefi, a gate ďin Nizamiye hospital dake Life camp yayi horn aka buďe mishi ya shiga, reception ya tsaya zai yi mata folder, ce mishi tayi "inada folder na anan", juyowa yayi ya dubeta a yatsine yace "sai ki faďa mana number", number ta faďawa matar dake tsaye gun, a cikin computer ta binciko tace mata "Fatima Kashim Goni ko", kai ra gyaďa mata, matar ce ta fito tayi directing ďinsu har office ďin wani consultant farar fata, ko turancin kirki baya ji dan yanda ya amsa musu ba da turanci mai kyau ya amsa musu ba, k'arasa sukayi ciki matar kuma ta koma, kujera Abutturab ya jawo ya zauna itako Batuul tsayawa tayi bata zauna ba, likitan ne ya dubeta yace "beautiful lady come and seat down, relax and dont stress yourself" ya faďa cikin turancinshi da babu daďi yana nuna mata kujera, Abutturab ne ya juya ya dubeta tare da watsa mata harara, ďauke kanta tayi ta jawo kujera ta zauna, tana zama ya juya ga Abu yace mishi "couple?", ko kadan bae xaci tambayar, yaji tambayar wani iri, ya ďaga kanshi ya sace kallonta, itako kanta a k'asa kamar bataji mey yace ba, samun kansa yyi da gyada masa kai kawae snn ya mik'a mishi hannu suka gaisa sannan ya fara mishi bayanin abinda ya kawosu, sai da ya gama mutumin yace musu pneumonia ke son kamata, ta guji duk wani abu mai sanyi sanyi sannan yayi musu prescribing drugs, mik'ewa yayi suka sake gaisawa da likitan sannan suka fita sukayi hanyan pharmacy dake asibitin, da pos yayi amfani ya biya duka kuďin magana sannan sukayi mota dan su koma gida, a hanya wayarsa ya fara ruri, ya dauki wayar hnklinsa na kan tukin da yake ya duba me kiran nasa ya ga Ajiddeh ce, tsaki yyi ya mayar da wayar ya ajiye, gnin tana ta kira yasa ya kuma jan wani tsakin ya daga tare da yin shiru, daga can bangaren cikin tsiririyar murya tace "Gud morning hubbyna baka tashi bane" a takaice yace "Na tashi, hw was ur nyt" cike da shagwaba tace "Au ka tashi Shine ka ki kirana sweetheart" kamar baxae ce komae ba can yace "Kinga driving nake Wife, we will tok later" ta dan wara ido cike da jin ddin sunan da ya kirata da tace "Driving kuma da sassafe angona ina ka tafi" kaguwan da yyi ta kyalesa yasa yace "Na kai sister hospital bata da lfya" dan yatsine fuska tayi tace "Sistern ka? Yhu mean farida or Who?" Xae yi magana Batuul ta fara tari tana covering bakinta da hannunta lkci daya ta daura fuskarta kan kafarta tana ci gaba da tarin ba kakkautawa, juyawa yyi yana kallonta, gnin sosae take tarin yasa ya gangara gefen titi ya tsaya, ko kadan bae lura har lkcn waya na kare kunnansa ba kuma Ajiddeh bata fasa Hello din da take yi ba jin shiru, sosae Batuul ke tarin har da kkrin amae, bae san lkcn da ya ajiye wayar hannunsa ya dagota yana kallon idonta da yyi ja ssae har lkcn ta toshe bakinta da hannunta, da kyar ya bude baki yace "Sorry" ta kauda kanta tana kkrin bude motar, ya jawota yace "Ina xaki C'mon" bakinta take nuna masa, hkn yasa ya gne me zata yi ya bude lock din motar ya fita ya xaga ya bude mata, fitowa tayi daga motar tana layi ta nufi wani gutter ta tofar da mucus din bakinta snn ta juyo tana rike da kanta dake mugun tsara mata, tana shiga motar ya rufe snn ya xaga ya shiga motar ya xauna dai dai lkcn da wayarsa ke katsewa dubawa yyi yaga miscals din Ajiddeh har uku, ya ja tsaki xae ajiye sae ga kiran ya kuma shigowa, dagawa yyi tace "Wani wlknci ne wnn Aliyu, y will b treating me like this for God sake, don ka ga na damu da kai" Cikin tsawa yace "Hold it plss kar ki bata min rae da sassafen nn, baki ji me nace maki bane, or are yhu deaf can't yhu hear her coughing" Shiru tayi xuciyarta na tafarfasa, amma gnin ransa ya baci yasa ta marairace murya tace "To Wacce kanwartaka? Baka gaya min wacece ba" a takaice yace "Batuul, we will tok ltr" yana kai wa nn ya katse wayar ya ajiye, snn ya tada motar tare da juyawa yana kallon Batuul da ta jinginar da kanta jikin kujera idonta a lumshe. 💖💝BATUUL 💖💝 29 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Dawowa yayi yabi stairs ďin da kallo, da sauri ya ďauke idonshi daga wajen dan bazai iya kallon Ammah ba , falon k'asa tazo ta zauna ba tare da ta kalli inda Abutturab yake ba, jikinshi ne ya k'ara yin sanyi har sai da Sadiq ya lura dafa kafaďanshi yace mishi "it will be okay, just pray and be optimistic, a hankali ya ďaga k'afanshi kamar k'afan na mishi ciwo, har cikin falon shima ya k'arasa, ya samu waje a k'asa ya zauna ďan nesa da Ammah, cikin sanyin murya yace mata "Ammah ina wuni " ba tareda ta kalleshi ba a tak'aice tace "lafiya" daga hka yyi shiru don ya rasa abun cewa, Abui ne ya shigo daga waje, da sauri Abutturab ya mike ya isa wajen Abui, cikeda girmamawa yace "Abui barka da gajiya, sannu da dawowa gida " , kallon mamaki Abui ya shiga yi masa daga sama xuwa k'asa snn a takaice yace "sannu na gode , ashe ka shigo gari " inji Abui yana me dubansa har lkcn, Kai Abutturab ya gyaďa tareda cewa "Ehhh Abui, ďazu na shigo " , yace "madallah toh yayi kyau " , bai sake bi ta kanshi ba yayi hanyan stairs, Ammah ce ta tashi tabi bayanshi suka haura tare tana mishi sannu da dawowa gida, Juayawa yayi ya dubi Sadiq a sanyaye , kai Sadiq ya girgiza mishi alamar assuringly, kamar yasa ihu haka ya rik'a ji a wajen, idonshi ne yaji yana kawo hawaye, tambayan kanshi ya fara "mesa na zama haka ne? , akwae randa su Ammah xa su ki murnan ganina bayan tsawon watanni, yana cikin tunanin yaji wayanshi na ringing, hawayen dake idonshi yayi maza ya goge ya ciro wayar daga aljihu, sunan da yayiwa Ajiddeh saving ya gani a screen ďin, sai da ya kusa katsewa tukunna yayi receiving yasa a kunne, Sadiq kam juyawa yayi ya bar wajen, jiki a sanyaye yace "Hello" , "Aliyu wai meye haka ne, har yanxu baka fito ba wai , tun ďazu fa nake zaman jiranka, daga cewa kaje gidanku yanxu zaka dawo shine zaka zauna ka shanya ni, ni da ina nan ma Wllh bazan bari ka tafi ba, kuma Hotel ďin kake son naje ni kaďai?" wani irin tsawa da ya daka mata ne ya sata yin shiru ba shiri, gaba ďaya jikinta sai da ya ďau rawa har gumi sai da ya tsatsaffo mata a goshinta , "bana son rashin hankali kina Jina ko, kin manta inda nace miki zanje ne, gidan iyayena naje kuma da kike cewa ke kaďai zaki kwana a hotel yau kika fara kwana a hotel ke kaďai ne , kuma ba dawowa zanyi ba so kar ki koma hotel ďinnan ki wuce gidanku ki kwana a can" gaba ďaya ta tsorata dashi, a hankali ta buďi baki tace "toh sai da safe" , wani iska mai zafi ya furzar daga bakinshi ya maida wayar aljihu, ďakin shi ya nufa, tsaf ďakin yake kamar yadda ya tafi ya barshi , babu abunda aka canja sai ďan k'uran da yayi, sai da yayi karkaďe k'uran tukunna yayi wanka ya kwanta, gaba ďaya bacci ya k'aurace mishi, sai yanxu abubuwan da yayi suka fara tariyo mishi, sai yanxu yake sake ganin rashin kyautuwar abinda yayi wa iyayensa, kusan kwana yayi yana tunani, ganin babu abunda tunani zai mishi ne yasa ya mik'e yaje ya ďauro alwala ya fara Nafila, haka ya kwana yana addu'a yana rok'on Allah ya huci zuciyar su Ammah, yana zaune kan sallaya har aka k'ira sallah asuba, Tashi yayi ya tafi masallaci, a nan ya haďu da Sadiq da Abui, tunda Abui ya amsa gaisuwan shi bai sake ce mishi komai ba, ba K'aramin tashi hankalinshi ya daďa yi ba, babu abunda yak'i irin ganin b'acin ran iyayenshi, Sadiq ne yaci gaba da kwantar mishi da hankali har suka shiga gida kowa yayi ďakinshi, zaman jiran gari ya waye yayi yaje ya samu Ammah, yasan in Ammah ta hak'ura toh Abui bashi da matsala, bakwai saura ya kasa hak'ura ya tashi yayi ďakin Ammah, yasan bata bacci war haka, yafi minti uku tsaye bakin k'ofar ďaki ya kasa shiga, a hankali yayi knocking k'ofar ďakin, muryan Ammah yaji tace bismillah, a hankali ya tura k'ofar ďakin ya shigo, Ammah na zaune daga bakin gado casbah a hannunta, da sallama ya shigo kanshi a k'asa ya zauna dab da k'afanta , cikin sanyin murya yace "Ammah Nda wattu" sai da ta ďauki seconds ba tare da kallon inda yake ba ta amsa mishi da "Lafiya" hankalinshi ne ya sake tashi yasan Ammah ba K'aramin fushi tayi ba , ko da wasa bata so tayiwa mutum kanuri yayi mata hausa, amma gashi yau ita da kanta tayi mishi hausa, shiru yayi ya rasa mey zaice can da yaga shirun baya zuwa ko ina yace "Ammah Dan Allah kuyi hakuri, wlhy ban san meye ya yazo kaina ba , Ina sha Allah bazan sakeyi ba, ku yafe min pls " cikin kanuri yyi mata maganar, duk maganan da yakeyi ko sau ďaya bata juyo ta dubeshi, jiki a sanyaye ya sake matsawa kusa da k'afanta yace "Ammah fishinki na ďaga mun hankali fiyeda komai, nayi alk'awarin hakan bazai sake faruwa, kuyi hakuri ku yafe min, fishinku a kaina na Janyo min fishin ubangijina, Am so sorry Ammah " , Hannunta yaje ya rik'a cikin nashi cikin sark'e war murya yace "Ammah kiyi min aikin gafara ko zan samu kwanciyar hankali, Ammah nasan na b'ata muku ......" , bata bari ya k'arasa ba ta Janye hannunta daga rik'on da yayiwa hannunta tace mishi " hakurin mey kake bani wai, ni nace maka kayi min laifi ne, I thought you did what you think is right ko, then you should let me be ka dena damuna da hakuri, bance kayi min komai ba", kanshi ya kifa a cin y'anta ya fashe da kuka yana girgiza kai, ya kai 1min kwance kai bata ďaga shi ba, tausayin dan nata ya cikata don tasan of course ba yin kansa bne, ta sa hannu a hankali ta ďauke kanshi daga cinyarta tace "you can go, am okay bakayi min komai ba , rasa mey ya ke mishi daďi yayi ya dubeta da idonshi da suka rine sukayi ja yace 'Ammah pls forgive me, am promising you it won't happen again, Ni gaba ďaya garin ma bazan sake bari ba, I will resign daga aiki a can, you should forgive me Ammah " ce mishi tayi "Aliyu tashi kaje, bana so kazo kana damuna kaji , you should leave " , kallonta yayi zai sake magana tace " I said leave", jiki ba k'wari ya mik'e ya fita, da ido tabi bayanshi cike da tausayin ďan nata, waje ya fita daga ďakin kanshi na Sara mishi, ďakinshi ya koma ya kwanta ya runtse ido hawaye na bin kun cin shi, wayar ya Janyo yayi receiving saboda K'aran da take, a kunnenshi ya saka tareda yin shiru, Ajiddeh ce tayi magana daga ďaya b'angaren tace "Aliyu har yanxu baza ka dawo ba , yaufa zamu wuce, kuma ma....." katseta yayi yace "Look here free me, in baza ki iya zama ba toh ni kinga rabu dani, you should just go back am busy over here, xa ki iya tafiyar ki" ya katse wayan, hankalinta yafi na kullum tashi, shikenan ta shiga uku ta dinga nanatawa ta faďa kan kujera, baya fitowa daga ďakin sai in zai zo bawa Ammah da Abui hakuri amma duk da haka babu progress, hka yyi ta neman fuskar iyayen nasa amma bae samu ba, Farida da Sadiq ne ke shigowa wajenshi suna tausanshi tareda bashi baki, ranan kwana uku da yaje ya samu Abui, a ranan Abba ya nuna masa komae ya wuce ya hak'ura, murna fal cikin ransa ya fita tareda yiwa Abui alk'awarin hakan bazai sake faruwa ba, Ammah kam har yanxu tak'i hakuri tana nan kan bakanta A ranan da ya cika kwana huďu a gida, da yamma ya fito falo ganin babu kowa kuma he is bored of zama a ďakinshi shi daya, ďaya daga cikin dogayen kujerun falon yaje ya kwanta a kai tareda lumshe ido kamar mai Jin bacci, Batuul ce ta shigo gidan ďauke da royal Food flask mai shegen kyau sai kuma leda a ďaya hannun Aunty ta aikota, mutum ta gani kwance kan kujera duk tunaninta Sadiq ne, da yake suna dan ďasawa dashi cikin sanďa ta tako tazo inda kujerar take , daidai fuskanshi ta tsuguna tare da yin k'ara, mik'ewa yayi xaune da sauri don har ya fara bacci rike da remote a hannu, ya juya don ganin wane isasshen ne hka , sai da hanjin cikinta suka kaďa ta xaro ido a tsorace don she wasn't expecting him ko kaďan, da sauri ta koma baya Dan gaba ďaya ta gama tsorata da ganinsa, kallonta yayi tsaya yi ko kyaftawa baya yi, juyawa tayi zata bar wajen da sauri ya daka mata tsawa yace "Dawo nan " , tsorata ta sakeyi ba kaďan ba ta sake ledan dake hannunta dama tun farko ta ajiye food flask ďin ta haura sama a guje ta shige ďakin Ammah, Ammah na ganinta ta shigo a guje ta mik'e tace "Subhanallah bitti, ke da waye haka? Wa ke binki " , ba shiri ta k'irk'iri murmushi tace "Ammah ba komai" tare da k'ara faďaďa murmushinta, komawa Ammah tayi ta zauna tace "Bitti sak'on fa" , tace "yana falo Ammah, bari in taje in ďauko , bata k'arasa rufe bakinta ba ya shigo da Sallama rik'e da ledan a hannunshi, sai da ya ajiye tukunna ya sami waje ya zauna, shi da kanshi ya rasa mey ya hanashi komawa Dan yasan ba magana Ammah zata yi mishi ba, itama Ammah duk da ta fara tausaya mishi ta kuma ajiye fushinta kansa gaba daya ganin yanda ya rame har ya ďan k'ara duhu kuma tasan ba yin kanshi bane amma sam bata nunawa, Ammah tace "Bitti bakiga Yayanki ba" , pretending tayi tareda murmushi tace "ai mun gaisa a falo" , Mik'e wa tayi tace "Ammah zan tafi, Aunty tace kar in zauna muna da aiki, Dan taxi ma nazo da, motana ya samu problem kuma su Ahmad basa gida, Baa Alai da Baba kuma sun tafi Kaduna" , ta gyara gyalen kanta bayan ta gama maganan, Ammah ce tace "Taxi kuma, No baza ki koma a taxi ba, bari ďaya daga cikin drivers ďinnan yazo ya kaiki " ta Janyo intercom zatayi waya ďaya ya maida Batuul gida, Abutturab ne cikin sanyin murya kamar mara gaskiya yace "Ammah drivers ďinfa ďaya yana office tareda Baba, ďayan kuma na aikeshi, bata kalleshi ba tace "bari in k'ira miki Sadiq ya kaiki kinji , nasan baiyi nisa ba" ta ďauki wayanta zata k'ira Sadiq Abutturab ya mike yace "Ammah zan kai tace tunda ina nan " , a firgice Batuul ta kalleshi ta gefen ido, ďaure fuska Ammah tayi tace "Allah ya kiyaye, kuma daga nan ka tabbata ka shiga ka gaida Aunty "toh" yace ya juya yana yiwa Batuul wani irin kallo ya fita zuwa ďakinsa ďauko makulli, Batuul na ganin haka ta mik'e tareda k'irk'iro murmushi tayiwa Ammah sallama tace zata jira shi a k'asa ta fice a ďakin cikin sauri, da gudu ta sauk'o daga sama ta fita gidan gaba ďaya, waige waige takeyi tana sauri har ta iso bakin titi, tana zuwa ta samu taxi ta shige ta faďa mishi inda zai kaita, Ammah kam tun bayan fitan Batuul tayi tagumi tayi shiru zuciyarta na raya mata dama tun farko Batuul suka aurawa Abu da yanxu basu shiga bak'in cikin nan da suke ciki ba, wata zuciyar ce tace mata ai yanxu ma ba b'aci yayi ba, still zasu iya hadasu, a haka ma sai su k'ara k'arfin bond ďin dake tsakanin family, ji tayi zuciyarta tayi Na'am da zancen, take wani murmushi ya shimfiďu fuskarta, ta samu kanta cikin farin cikin da ta daďe bata ji irinshi ba, zama tayi kawai tana jiran Abui ta faďa masa wannan [truncated by WhatsApp] 💖💝BATUUL💖💝 30 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR** Yana fitowa daga ďakinshi bayan ya ďauko makullin ya dawo ďakin Amma, dubanshi tayi tace mishi "baku tafi ba wai, mey kake jira", cewa yayi "Eh ita nazo k'ira ta fito mu tafi", ďauke Idonta tayi daga kallonshi tace mishi "tana palo k'asa ae tana jiranka", juyawa yayi ya fita daga ďakin jin abinda Ammah ta faďa mishi, sakkowa falon yyi, yyi murmushi ganin bata nn ya fita compound, nan ma sai da ya dudduba bai ganta ba, masu gadi yaje ya samu ya tambayesu suka ce mishi ai ta wuce, bai sake ce musu komai ba ya koma wajen motarsa ya hau ya bar gidan, hanyan gidansu ya ďauka , dai dai tana isa ta sauk'a zata bawa driver taxi kuďi shima yayi parking motarsa gaban gate ďin gidansu saboda yayi beating traffic ďin cikin gari, su ko sai da suka bi ta ciki, gaba ďaya hankalinta ya gama tashi ganin motarsa, kasa tsayawa tayi ta karb'i canjinta tayi maza ta nufi cikin gida, yana ganin haka shima ya buďe motanshi ya fito cikin sauri yabi bayanta, dai dai k'ofan palo ya cimmata tareda da fizgota, gaba ďaya ta gama tsorata dashi har kyarma jikinta yakeyi, kuka ta fashe mishi da, rintse idonshi yayi ganin ta fara mishi kuka a ranshi yana cewa "she will neva change",lkci daya ya buďe ido ya hade rae tare da k'ara janyota har jikinsu na tab'a juna, yana mata mugun kallo ya fara mata magana "wato rainin nan naki yana nan har ynxu ko?, yaushe na zama sa'an wasanki, I mean yaushe na fara miki wasa da zaki min kara a kai ki gudu, kuma kukan da kikeyi sai ki faďa min na meye, wato ke har yanxu baza ki canja ba ko?", shiru tayi tana saurarenshi har tana jiyo heartbeat ďinshi, sai da taji yayi shiru tukunna ba tareda da ta ďago kanta ba ta fixge jikinta daga rik'on da yayi mata ta shige palo da sauri, inda tayi yabi da ido, da kamar zai koma sai kuma ya fasa ya tura k'ofan palon, dai dai nan Aunty ta fito daga kitchen, da mamaki a fuskanta ta buďe baki tace "Lalala, wa nake gani kamar Abutturab", murmushi yayi tareda sunkuyar da kai k'asa ya k'arasa shigowa cikin palon,sai da ya zauna tukunna ya gaisheta, ta amsa da fara'a ta shigo falon ta xauna tana tambayarsa yaushe ya shigo gari, hira sosai sukayi da Aunty , Janet Aunty ta k'ira tace ta k'ira mata Batuul, dawowa tayi tace tana zuwa, sai da ta canja kaya ta saka straight skirt baqi da peplum blouse peach, ta sauk'o, kanta da ta taje take tattarewa ta sauk'o ba tare da sanin yana gidan ba, turus ta tsaya ganin mutum zaune yana hira da Aunty a gidansu, ita a zatonta ya wuce tun ďazu, ta hade rae a hankali ta karaso wajen Aunty tace "Na'am Aunty, Janet tace min kina k'irana", cewa Aunty tayi "Ehhh, kitchen nakeso ki shiga kiyi Assisting su Esther ku k'arasa mana abinci, mik'ewa tayi daga hannun kujeran da take tayi hanyan kitchen, ya bi ta da kallo, Aunty ce tace mata "Batuul ya haka, bakya ganin Yayanki ne zaune baki gaidashi ba" juyowa tayi tace "Aunty mun gaisa, shi ya dawo dani gida ma fa", ta faďa ba tareda ta bari sun haďa ido ba ta juya ta ci gaba da tafiyanta, har ta shige kitchen bae daina kallonta ba, a gidan ya zauna har akayi sallahn magriba sukaje suka dawo, suna ta hira shida k'annenta dan yana da son yara, Batuul kam duk aikin da takeyi ranta a b'ace yake , kwata kwata she is not comfortable don da ta fito kitchen sae sun hada ido, dama ga wannan masifan heartbeat ďin nata da ya fara dawowa bayan tsawon lokaci, gaba ďaya ya sata ta sake takura, k'ara b'ata rai tayi ta fito tana jera abincin da suka girka a dinning, suna haďa ido ya sakar mata harara, ďauke kanta tayi bata sake kallon inda yake ba, tana gamawa ta haura sama bata sake sauk'owa ba har ya bar gidan bayan Aunty ta tilasta shi cin abinci har tana ce mishi ko dai sabawa da yayi ne da girkin Ajiddeh yasa baya jin daďin wani abincin sai nata, murumushi yayi a ranshi dan shi baisan ma ya taste đin abincin Ajiddeh yake ba dan ba iyawa tayi ba, haka ya hak'ura ya zauna yaci dan babu yadda ya iya, bazai iya yiwa Aunty musu ba Bayan anyi sallahn Isha Abui ya shigo gida, dama Ammah duk ta matsu ya dawo ta faďa mishi abinda ke ranta, bayan ya dawo saida ya sauk'o palon k'asa tukunna Ammah ta kawo mishi abincinshi har palon, sai da tayi serving ďinshi yana ci tukunna ta fara magana, shima dama ya lura da magana a bakinta, cewa tayi "Abul Aliyu", ďagowa yayi bayan ya cinye spoon ďin abinci da ya saka a bakinshi yace "Na'am Umm Aliyu", ya tsaya yana kallonta yana jiran yaji mey zatace, sai da tyi ajiyan zuciya tukunna tace "dama wani shawara nayi đazu akan yaran nan namu, kuma ina ganin its beneficial to both families, mey zai hana mu nemawa Abutturab auren yarinyan nan Batuul, yarinyar nutsatsiyace sosai kuma gidan da ta fito nan aka fara yiwa Abutturab tarbiya, a gidan ya fara koyon komai na rayuwanshi, kuma ko babu komai in suna tare a can , toh nasan lallai zata na watching moves ďinshi dan tana da lura da sanin ya kamata, xa kuma tana nuna masa what's right nd wrong, gata kuma da hankali, kaga inma shi ya tafi yaqi dawowa toh ita ba yadda zatayi tayi ta zama babu ganin gida dole sai ta dawo, toh ,kaga a haka zai biyota su dawo ko dan kunyanmu", tunda ta fara magana ya maida spoon ďin abincin cikin plate ďin, murmushi ďauke a fuskanshi yace "Masha Allah, wannan ai abin farin ciki ne sosai kuma nima zanfi kowa murnan ganin wannan al'amari ya faru, kamar Farida haka nake jin Batuul a raina, gobe in Allah ya kaimu zanje in tuntub'i mahaifinta akan zancen muji in babu matsala ko kuma da akwai wanda takeso ", Ammah tace"Abul Aliyu in sun yadda ma kawai a ďaura auren su tafi in yaso daga baya ayi biki , sai taci gaba da karatunta a can,", yace "okay duk zanyi trying inji, Allah dai ya taimaka" haka dai sukayi ta zancen haďa Abutturab da Batuul aure har Ammah na cewa ai da tun farko ma sunyi tunanin nan da duk yanxu basa cikin matsala Washe gari ranan juma'a bayan an idar da Sallah a masallaci Abui ya haďu da Baba, bayan sun gaisa Baba yace "Alhaji mu dai bama tab'a haďuwa dan kanmu sai dai ko masallaci ko kuma meeting",dariya Abui yayi yace "rayuwan kenan Alhaji, in mukace zamu zauna gida abin bazai yi kyau ba, da shike ma yanxu girma yazo, mun kusa sauk'a mu huta ai", duk su biyun suka sa dariya, Abui ne yacewa Baba " *Alai wa office lan gèrezain, dai fatoro iske kèla kwamnyen* , Alai ana jirana office yanxu, amma anjima zanzo gida, there is this issue i want to discuss with you", da haka sukayi sallama, da yamma wajen k'arfe biyar Abui na tashi daga office yayi gidansu Batuul ko gida bai je ba, lokacin Baba na gida saboda its a short day duk sun tashi aiki da wuri, fitowan Batuul kenan daga backyard đin gidansu, tayi mamakin ganin Abui a gidansu, har k'asa taje ta tsuguna ta gaisheshi sannan ta tashi da taje tayi serving ďinsu drinks da snacks, bayan ta ajiye zata mik'e Abui yake tamabayanta ya makaranta, tace Alhmdllh, nn yayi ta sa mata albarka har sai da taji kunyanshi sosai , bayan ta tafine Abui ya fara magana , sai da ya gama baynin abinda ya kawoshi tukunna Baba ya fa'da'da murmushin fuskarsa yace "Alai nidai b'angarena babu matsala dan babu abinda zaka nema matsawar inada iko akan abun in hanaka, kuma ma ai Abutturab yaron kirki ne sosai, dama dai akwai wani yaro da naga ya fara zuwa wajenta tun wancan watan amma bansan ko sunyi maganan aure ba, kuma tunda ga na gida da aka san halinshi ai yafi da a bawa na waje da ba'a san halinshi ba, dan ma dai naga yaron nada hankali amma zamu bashi hak'uri, yanzu dai ni zanje inyi shawara da y'an uwana da manya na sai mu san abin yi dan Yayya ma ta matsa tafi kowa son a aurar da Batuul sai gashi Allah ya taimakeni akai", godiya sosai Abui yayiwa Baba daga nan suka shiga hirar politics da matsalolin dake damun Nigeria. Batuul na kwance kan gado wajen k'arfe 8 na dare bayan tayi sallah isha, kayan bacci ne jikinta dogon wando da y'ar riga, kan gadon duk ta baje takaddu sai Macbook ďinta daga gefe, chocolate bowl ta janyo ta ďau twix ďaya ta b'are ta jefa a bakinta tukunna taci gaba da duba takaddan, tana ci taji wayanta na ringing, tashi tayi ta ciro wayan daga caji, Recieving tayi tareda komawa kan gadon ta kwanta, kamin tayi magana daga ďaya b'angaren akayi sallama tareda da faďin "Ranki ya daďe Habibty, i cant imagine life without you", murmushi tayi har ana jiyo sautin daga ďaya b'angaren tace "tareda naka, you can live normally mana tunda ai da can ma baka sanni ba and you were living", dariya yasa yace "that was then, amma ai yanzu tunda na sanki, life is gonna be hard without you, promise you wont leave me", ji tayi gaba ďaya ya gama bata tausayi, ita tasan ba sonshi takeba but tana respecting ďinshi sosai, avoiding promise ďin da yace tayi mishi tayi tace "Ya jikin Mummy, ta k'ara samun sauk'i ko?", da sauri ya tareta yace "Ba kinqi zuwa in kaiki wajenta ba, kullum sai ta tambayeni yaushe zan kawo mata kene, har banaso tana tambayana dan bansan mey zance mata ya hanaki zuwa ba", kai ta girgiza kamar yana gabanta tace "No fa ba naqi zuwa bane, we have time , kuma i dont think its right muje gidanku tun yanzu , i will come when its time", tambayanta yayi mey takeyi dan yaga mind đinta is not with him, tace mishi assignment takeyi, da haka ya barta tace they will talk ltr Bayan Abui ya tafi, Aunty ce ta sauk'o k'asa ta sami Baba zaune yana kallon CNN channel, daga gefenshi ta samu waje ta Zauna tayi mishi sannu da gajiya tareda ajiye. abinda ke hannunta, volume ya rage ya juyo ya dubeta ya faďa mata yadda sukayi da Abui, ita gaba ďaya bata expecting haka, ta k'asa daina kallon mai gidan nata, hankalinta ba k'aramin tashi yayi ba jin xancen Baba kuma tasan babu yadda za ayi yaqi bawa Abutturab Batuul tunda har gida Babanshi yazo nema mishi aurenta, ajiyan zuciya tayi cike da damuwa tace "Uncle Batuul ďin kuma, shi da yayi aure ko shekara bai wuce ba, ai sai ya bari ko matar tasa in ta haihu ne sai ya fara zancen k'arin aure amma ba daga aure ya bijiro da sabo ba", ta faďa tana jiran jin mey Baba zaice, cewa yayi "indai zai kula dasu duka biyu ai bamu da matsala, kuma ai ba sanin matsalarshi mukayi ba na son k'ara aure, kuma ma dai yaron nan ďanki ne, kinfi kowa sanin halinshi, ya kamata kifi kowa murnan kasancewar wannan al'amari, kinsan ko shekaran jiya kina zaune kina ji sai da Yayya ta k'irani akan Batuul, toh yanxu mafitar addu'an da nayi na samu, nasan Aliyu yaron kirki ne zai kula da Batuul in sha Allah", ido kawai Aunty ta zubawa Baba yana magana hankalinta na dađa tashi, Batuul tayi yarinya da auren mai mata, barema irin su Ajiddeh, cutan Batuul kawai za ayi indai ta zauna a gidan nan a matsayin matar Abutturab, dan tasan yadda familyn Ajiddeh suke akan kishiya, mik'ewa kawai tayi ba tareda ta sake cewa komai ba ta haura sama don bata jin xata amince da wnn batun at all, idonta ya kaďa har ya canja kala. 💖💝BATUUL 💖💝 28 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Tana fita ta wuce gidansu daga hotel din, cike gidan yake da mutane da suka zo biki, wucewa takeyi tana ta daga kai ita a dole matar mai kuďi, matan dake zaune sai gaidata suke wasu kuma suyi gulmarta, ďakin da tasan zata samu Mum straight ta wuce, ba ko sallama ta saka kai cikin ďakin, Mummy na ganinta ta taso cike da murna ta rungumeta tana faďin "Yar albarka baki min waya kince kun iso ba " ta fadi tana K'arewa Ajiddeh kallo ganin yadda ta canja lokaci kaďan, ga wani kyau da ta k'ara dama can Masha Allah, Hannunta ta jawo bayan ta saketa daga rungumar da tayi mata taja hannunta suka shiga bedroom, Junaiba dake zaune ce ta bisu cikin ďakin, a tsakiya suka sa Ajiddeh, Mummy ce ta fara ce mata "Ajiddeh kinga yadda kika canja , lalalala Masha Allah, kin zama matar manya, duk komai yana tafiya yadda muka shirya ko? , Jainaba ce tayi maza ta karb'e maganan da cewa " Mummy ai ko baki tambaya ba gashi kin gani, yarinya zata cuci kanta, ana so a ayi miki abin kirki a taimakeki kina ke mijinki, kefa kina sonshi, toh da mun barki haka da yanxu duk ba haka bane, yanxu faďa mana muji inda matsala mu san yadda zamu b'ullowa matsalar mu magance ta" , tunda suke surutun su bata ce komai ba sai danna waya da take tayi , sai da ta gama ta ďago tana kaďa hannu tace "Mummy ai Aliyu sai abinda nace, tun farkon aurenmu da ya fara min masifa kullum ni k'azama ce, na faye son jiki, bbu abinda na iya, gashi da bak'in halin jaraba sam ba a zama ayi hira dashi , amma tun bayan nayi muku complain ďinnnan da kukace in turo kuďi , everything have been fine since then, kuma sam baya tambayan mutum mey zakayi da kuďi komi yawansu bayarwa yakeyi shiyasa bamu samu matsala ba, maganan da nakeyi muku yanxu haka Mummy tunda mukayi aure sau ďaya yaje gida, waya kam dama babu magana, ai na gaya muku wannan watan sun turo k'anwarshi tazo, itama ďin dai bata daďe ba Nasa ya maidata , wannan zuwan ma da zamuyi ban yadda mun zauna a gidanmu ba saboda Kar ma susan da zuwanmu " "Jainaba ce tace "ai hakan ma yayi daidai da kikayi, toh ya akayi da wancan abinda nace miki na abincin shi ne, wannan na naman, tunda cewa kikayi ba kya girki, ko kinyi bayaci" , dariya tasa tace "Jainaba kenan, ai in yasan wata baisan wata ba, shi yake dafawa kanshi abinci ko kuma ya siyo, toh watarana yakan ajiye na dare da safe yayi warming yaci, ni dama bana bi ta kanshi, kuma dama ba iya dafawa nayi ba, sai dai kullum in rik'a ordering don of recent ya sallami cook din gidan" , Mik'e wa tayi tana dariya tace "Mummy ,Jainaba, ku bari mu dawo daga dinner in mun nutsu zan faďa muku duk yadda ake ciki, ni sam ban maje naga Amarya ba, tunda aka saka ranan nan ya ďaga mun hankali wai sai nayiwa Ufa magana ayi bikin aurenta a gidannan saboda bata sn y'an uwan mijinta su rainata " , Mummy ce tace "ai da gaskiyarta, Ina zata yadda da raini, gara da ta bar gidansu tazo nan ďin ayi komai a gama, ko ba komai itama tana da y'an uwanta masu akwai " Da haka suka fita daga ďakin, Mummy da Jainaba suka tsaya daga falo Ajiddeh taje side ďin da Amarya da k'awayenta suke. Babu abinda ke tashi a wajen nan sai sautin kiďa, Hall ne mai girma da aka yiwa ado sosai na gani na faďa dan da gani kasan yaci Naira, Tun daga mota Abutturab yake k'iran number Ajiddeh amma bata receiving, fitowa yayi daga cikin motan yayi heading cikin hall, mata ne tare da maza kowa yana displaying talent ďinshi na rawa, Ajiddeh ya hango daga cikin y'an rawa sai kaďa waist takeyi, ranshi ba K'aramin b'aci yayi ba ganinta cikin maza tana rawa ga wasu shegun kaya da ta saka duk bayan ta a buďe, ji yakeyi kamar yaje ya fincikota amma babu hali, waje yaje ya samu ya zauna daga gefe yana jiran lokacin da zata gama, sai da suka gama tik'a rawansu tukunna bayan Dj ya k'are suka bar filin rawar, tana juyowa idonta ya sauk'a kan Abutturab, haďe rai tayi kamar ba ita ke dariya ba yanxu, k'arasowa tayi inda yake zaune ta tsaya mishi a ka k'erere tana ďan karkaďa k'afa, ďagowa yayi ya dubeta tare da cewa mata "Babe har kun gama rawan ne? " wani Harara ta sakar mishi tace "Kai fa ka cika wulak'anci, tun ďazu muyi da kai zaka zo shine sai yanxu ka wani ďebo k'afa kazo, y'an uwana sai tambaya sukeyi ina kake, kowa yazo da mijin shi sai ni kaďai ce babu mijina, ni tun farkon nasan wulakantani kaso yi dama bada son ranka muka zo ba....." katse mata maganan yayi tareda kamo hannunta ya zauna da ita kan kujeran dake kallon nashi, magana ya fara yace "Babe c'mon, tun ďazu fa nake wajen nan ina k'iran wayanki baki ďauka, da na shigo kuma na ganki you guys were busy dancing" , a ranshi yana son yi mata maganan cewa ita matar aurece, bai kamata tana irin wannan shigar ba har tana Cuďanya da maza, amma bazai iya ba, kawar da zancen yayi yaci gaba da cewa "so bana so in dameki shiyasa na bari sai kin gama tukunna sai ki ......" bai k'arasa ba yaga ta warce hannunta daga rik'on da yayi mata ta bishi da harara ta juya daga wajen ta nufi tsakiyar hall ďin Jin an ambaci cewa y'an uwan Amarya suzo ayi hoto da ita, wani irin bak'in ciki yaji a ranshi wai shi Ajiddeh ke yiwa abubuwan nan da takeyi haka "toh meye ke damuna ne? " ya tambayi kanshi, inda tabi shima yabi da ido ya ganta ita da sauran y'an uwanta maza sun sata a tsakiya cameras nata haskasu sai washe baki takeyi yana cikin tunani yaji an da dafashi daga baya, a ďan firgice ya juya yaga ko waye, kanshi ne yaji yayi dammm tare da zaro ido ganin mutumin da yake expecting gani least a wajen, zagayowa yayi ya zauna daga ďayan kujeran murmushi ďauke a fuskanshi yace "Ashe kana gari, Well i can see you are surprised to see me here ko bro? , bai bashi ansan tambayan da yayi mishi ba sai ma jifanshi da yayi da nashi tambayan shima "What brought you here Sadiq? Mey kazo yi?" Shima bai bashi amsa ba sai ce mishi da yayi "Answer me first bro, ni na fara tambayanka kuma your question is irrelevant, yaushe ka shigo Nigeria, ko da shike dama ance mana kana shigowa mune dai bama ganin ka " ďagowa yayi da sauri ya dubi Sadiq Jin abinda Sadiq ďin yake faďi , cikin rashin Jin daďin abinda Sadiq ya faďa mishi yace "ance muku ina zuwa Nigeria? Su waye ke faďa muku cewar ina zuwa" murmushin takaici Sadiq ya saki yace "Allah sarki these doesn't matter now, Ni auren Abokina Muhsin nazo, shine angon, so banma jima da shigowa ba, but tunda na shigo na ganka wani xuciyar ke cemin ba kai bane, I thought ma gizo kake yimin ba kai bane cus I wasn't expecting you " , sai da yayi shiru tukunna Abutturab yace mishi "Ai Amaryar k'anwar Ajiddeh ce, so shine muka zo Dan kusan Ajiddeh ce tayi sponsoring biki saboda mamar yarinyar ai ta rasu" kai Sadiq ya kaďa yace "Ohhh , that's nice then, toh yau ďin zakaje gidane ko kuwa zaka koma ba tare da kaje ka gaida Ammah ba " jikinshi ne yaji ya daďa sanyi Jin an ambaci sunan Ammah, ba tare da ya yadda sun haďa ido da Sadiq ba yace "toh shikenan bari in faďawa Ajiddeh zamuje yanxu, k'ar inje kuma bata sani ba hankalinta ya tashi " , da tausayin ďan uwan shi a ranshi yace "gaskiya hakan ma yayi kyau, kaga kar tazo tana ta nema ai babu daďi" , yace "Ehhh shine yanxu zan k'irata, naga ma she is so busy yau ďinnan" , yaci gaba da dialling ďin number ta, da k'yar aka samu ta ďauki wayan bayan ya k'ira kamar sau bakwai , tana ďauka tace mishi "baby wai meye haka, baka ganin am busy ne ? Kasan fa ni nayi komai na auren nan kuma na daďe ban haďu da y'an uwana ba ai sai ka barni in huta, da ka k'ira kaji ban ďauka ba ae sai ka hak'ura, amma ka ta wani k'irana sai kace ladan a masallachi" , sai da ta gama ya kwantar da murya yace "sorry Babe, something came , zanje wajen su Ammah ne in duba su, ya daďe da na gansu, I will go briefly and come back " , batasan lokacin da ta mik'e daga zaunen da take ba, gumi ne taji gaba ďaya ya fara tsatsaffo mata, Ce mishi "Aliyu ba muyi haka dakai ba, mu da zamu koma gobe mey zakaje yi, toh ni dai bana son zuwanka, kuma baxa kaje ba " , samun kanshi yayi da katse wayarta, har sai da yayi mamakin kanshi shima, mik'e wa yayi ya cewa Sadiq "muje ko? " kallon mamaki yabi Abutturab dashi wai wannan shine yayanshi da yake takawa maza ma birki amma yau shine da kanshi mace ke mishi tsawa har yana ji a waya, ji yayi hawaye na son zubo mishi yayi maza ya maidasu yace "Yaa Abu muje" , ya shige gaba Abutturab na binshi daga baya, Wani ihu ta saka tare da fashewa da kuka, hankalin su Mummy yayi kanta a tashe, tambayanta suka shiga yi lafiya take ta ihu haka amma tak'i magana, Yaa Zee ce tace mata " a k'ira miki mijin nakine ko wani abin ne ya sami mijinki", wani irin kallo ta Watso mata tace "Da wani abun ne ya same shi ai duk mai sauk'ine akan abinda yake shirin faruwa" taci gaba da kurma ihunta, su Mummy ganin tana Janyo hankalin mutane kansu tayi maza tasa su tafi da ita gida, har suka isa gida tana kuka suko sun sata gaba suna kallonta suna jiran Jin meye ke damunta, sai da tayi shiru tukunna tace " Mummy Aliyu ya tafi gidansu, duk k'ok'arina na kar yaje sai da yaje kuma gashi malamin nan sai da yace indai nayi mishi toh ko kar in yadda ya haďu da ďan gidansu ko ďaya in ba haka ba Babban Al'amarine zai biyo baya, Mummy ni ban san meye Al'amarin ba amma duk yadda akayi ba mai kyau bane, gashi kuma ya tafi, Mummy ya tafi na shiga uku, bige mata baki Mummy tayi tace "akan wannan abin kika ďagawa kanki hankali, mu inane bamu shiga, ai in yasan wata baisan wata ba, ki kwantar da hankalin ki ba gobe zaku koma ba, toh babu abunda zai sameku daga ke har shi ďin " a haka dai suka ci gaba da bata hak'uri da baki har suka samu tayi shiru amma ba Dan hankalinta ya kwanta ba, Dan gaba ďayansu basu san waye Aliyu ba, ita tasan yadda ta wahala a hannunshi farkon aurensu , tasan idan asirin nan ya karye toh nata ya k'are Tafiya sukeyi babu wanda yace da wani komai, Abutturab ne ya ďago ya dubi Sadiq yace "Farida ma last month taje wajena ai, amma kai ko sau ďaya baka nemana ko? " wani siririn dariya Sadiq yayi, yasan yayanshi is feeling guilty of himself shiyasa baisanma mey zaice ba, Sadiq yace "No Yaa Abu, abubuwa ne sukayi min yawa, ga hidiman Ammah, Abui da kuma na wasu shiyasa, amma in kuka koma har can zanzo , In shaa Allah" , jikin Abu ne ya kuma yin sanyi yace "Allah ya yadda " a ranshi yana tunanin mey zai fara cewa su Ammah, sai yanxu yake sake ganin rashin kyautuwar abinda yayi, a haka suka isa gida suna hira jefi jefi, a k'ofar gida Sadiq ya tsai da motar tare da yiwa masu gadin horn, da sauri saurinsu suka taso suka buďe, ba K'aramin mamaki sukayi ba ganin Abutturab, da sauri suka faďaďa fara'arsu suna "Alhaji K'arami sannu da zuwa , an sha hanya to ya iyali , fitowa yayi daga motan ya mik'a musu hannu suka gaisa , sai murnan dawowanshi suke dan yana da kyauta sosai duk rashin dariyarsa, wucewa Sadiq yayi tukunna Abutturab yabi bayanshi, a hankali yasa kai cikin falon har wani faďuwa gabanshi yakeyi, Farida ce ta fito daga kitchen da tray a hannun ta, to abin ka da jini batasan lokacin data ajiye trayn ba tazo da gudu ta rungume shi ba, har da hawaye a idonta bayan ta sassauta rik'on da tayi mishi ta kalleshi tace "Yaa Abu ashe za kazo, Dan Allah kana zuwa gun mu kaji" Janyota ya sakeyi jikinshi yace zan rik'a zuwa kullum kinji Autan Abui" Dariya tasa ta goge guntun hawayen dake idonta tace "yawwa Yaa Abu, gidanmu babu daďi da baka nan, gaba ďaya abinda yayi mata da taje wajenshi last month ya rik'a tunawa, sae yaji bai kyauta ba, duk rashin shirin su da Farida amma cikin k'annenshi yafi sonta, haka itama tafi sonshi, masifanshi ne kawai bataso, juyawa tayi tace "bari in kira Ammah ya Abuu tana daki" k'asa cewa komae yyi sae bin ta da kallo da yyi, dai dai nn Ammah ta shiga sakkowa daga stairs. 💖💝BATUUL 💖💝 27 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* K'arfe biyar suka sauk'o k'asa ita da Farida zatayi wa Ammah sallama ta wuce , a kitchen suka tarar da Ammah ita da wasu y'an aiki tana masu magana, ganin Batuul da shirin tafiya tace "Bitti ba dai tafiya bako, ko Baa Alai din yazo ne, in baizoba ki bari anjima ko Sadiq ne ya mayarda dake", murmushi Batuul tayi tare tareda da girgiza kai tace "Ammah da kaina nazo, kuma Aunty tace in dena zama a waje har six, shine nakeso in koma gida kamin shida " tace "toh shikenan yayi kyau bitti, yanxu driving din yayi kyau sosai ko" tace "Ehhh Ammah muna trying", tace yayi kyau toh, Allah ya taimaka,muje parlour bari in hau sama in dawo " haks suka koma daga parlour suna jiran Ammah , suna zaune ta sauk'o rike da Babban farin leda a hannun ta, a tare suka mik'e suka isketa, Batuul ta mik'awa ledan tace "gashi bitti, useki kinji, nagode sosai, ga wannan kinji nakine", gaba ďaya sai taji wani irin da yadda Ammah ke mata magana, hawayene ya taru a idonta, kamar tayi laifi haka ta rik'a ji', maza tayi ta maida hawayen dake shirin zubo mata ta karb'i ledan daga hannun Ammah, jiki a sanyaye tace "nagode Ammah" , "Babu komai Bitti, ki rik'a zuwa akai akai kinji, ki gaida Aunty in kin koma da sauran yaran kinji" kasa motsawa tayi daga wajen har sai da taga Ammah ta haura bene tukunna ta juya a sanyaye tayi waje dama Farida ta dade da fita, a cikin mota ta tarar da Farida zaune ta k'ure wak'ar Ed sheeran ta shape of you a motar tana ta rawa, sau uku tana k'iran sunanta bata ji ba, har sai da ta zauna tukunna tace "Dadin abin ke da Affan ďin duk halinku ďaya da ya wahala sosai " juya ido tayi tace "ai inma ba ďaya ba haka zai hak'ura dani, babu yadda ya iya" tana ďaga gira ta k'arashe maganan, Sai da Batuul ta tada mota tukunna tace "Alhamdulillahi ma da halin naku ya zamo ďaya", dariya Farida tasa ta fita a motan tace 'toh ni dai ban shiga school this week , sai next week, Yauwa I forgot to tell you, Guess? Ta tambayi Batuul tareda daga mata gira ďaya, "kinsan I always get it wrong when I guess, so just tell me, time is going" Farida tace "toh naji, Mrs, Yaa Massa is getting married, ďazu Ammah ke faďamin wai da na tafi, y'ar Sultan ďin Sokoto zai aura wai sunanta Rahama" sai da ta gama Batuul tace "Allah sarki Yaa Massa, ashe......" , bata gama faďan abinda zatace ba Farida ta katse ta "wani irin Allah sarki, ke da kika k'ishi kememe kice baki sonshi shine harda wani tausayinshi, shima ďin nei dai ya barki , ai da nice shi Allah straight away Baba zanje in samu, sai dai kawai kiji ance an ďaura miki aure, wai shi tunda baki sonshi zai hak'ura da azo ayi abinda za azo ana magana daga baya , ni haushi ma yake bani , he was very lenient on you ke kuma kikayi ta gwara shi ,muna nan dai muna jiran Jin wanda zaki aura, Kai Allah yasa ma Baba ya badake Sadaka tunda ke kowa bai yi miki ba" Dariya maganan ya bawa Batuul tace " toh muguwa haba dai sadaka, that is not happening , not with me, ni kinga tafiya zanyi before Aunty ta faramin waya" , dariya Farida ma tasa tace "zaki sanine bari mu gaji dake Kiga ikon Allah " Sai da tayi reverse tukunna ta cewa Farida "Dan Allah turomin number shi Yaa Massa inyi congratulating ďinshi dan tun lokacin da yake ta damuna nayi deleting sai kuma number shi ta Germany shi kuma bazai yi Amfani ba", juyawa Farida tayi tana komawa ciki tace "fadi gaskiya dai Dan yanxu yana da matarshi , Dariya sukayi a tare kowannensu na dariya Batuul tayi sallama da Farida ta koma gida. Daidai ana k'iran magrib ta isa, A cikin gida da taje parking taga kamar motan ďazun nan ne pake, sanin babu yadda za ayi yazo gidansu kawai ta tab'e baki ta shige cikin gida, Aunty na alwala Batuul ta shigo da Sallama tace "Aunty na dawo ", Aunty tayi mata sannu da zuwa, ta juya zata koma ďakinta Aunty ta tsayar da ita ta hanyan cewa "in kin idar da Sallah kinada bako , ji tayi k'irjinta ya bada sauti Dam! Ita?, bako kuma? , toh shi waye ?, ita dai babu wanda yace mata zaizo wajen ta ko a y'an ajinsu , maza maza hankalinta ya tuna da motar dan ta gani pake , toh in shine bakon ni ina na sanshi ta ďan ja siririn tsaki, da sauri tace "Aunty ba wajena yazo ba, ni ban sanshi ba, "matsar min daga k'ofan toilet in wuce ni, waje na yazo tunda nice Batuul " marairaicewa tayi tana girgiza kai tace "Aunty dagaske fa ni ban sanshi ba ", bayan Aunty ta saka hijab zata tada Sallah tace mata "toh naji baki sanshi ba, wuce kije kiyi Sallah", jiki a sanyaye ta fita tayi ďakinta, tana tafiya tana ta sak'e sak'e a ranta "toh shi wannan mutumin what does he want with from me, ni ban sanshi bama gaba ďaya inba da na ganshi ba ďazu a traffic, am not even sure ko shi ďin ne bama" Alwala tayi ta tada Sallah, tana idarwa ta tub'e kayan jikinta ta shiga wanka, wani dogon riga mara nauyi ta kuma maidawa mai hula purple, ta ďan fesa turarenta mai sanyin k'anshi, kamin ta sauk'o Mahir ya shigo yace "Yaa Batuul Mama tace kizo", K'aramin gyale ta yafa bak'i tace "muje toh " tare suka isa ďakin Aunty dashi , da sallama ta shiga tace "Na'am Aunty" , ďagowa tayi ta dubeta tace "kije Guest room, bak'on naki na can na faďawa su Janet su kai mishi drinks kuma bana son gardama" tsayawa tayi bayan Aunty ta gama ta kasa tafiya, dubanta ta sakeyi tace "baza ki wuce ba, mutum na jiranki tun ďazu " kamar mai shirin kuka tace "Aunty Allah ban sanshi ba, maybe ma mistake ne bama ni yake nema ba", Hararan da Aunty ta sakar mata ne ya sata yin shiru ta juya zata tafi, tafi minti uku tsaye bakin k'ofan ďakin ta kasa shiga daga k'arshe dai ta ďaga labulen tare da sallama tasa kai ciki, bata ďago kai ko sau ďaya taga mutumin dake zaune ba, kujeran dake nesa dashi taje ta zauna tareda da sadda kanta k'asa, shiru ďakin yayi babu wanda yayi magana, tunda ta shigo ya k'ura mata ido yake kallonta, ita bata ma San yanayi ba, ji tayi ya k'ira sunanta daga inda yake zaune "Batuul ", bata amsa ba kuma bata ďago ba sai ma mamakin da take na yaushe yasan sunanta, Sai da ya k'ira a karo na biyu tukunna ta amsa ba tare da ta kalleshin ba, murmushi ta bashi ta k'ara burgeshi dan komai na Batuul na burgeshi, from d very first time he set his eyes on her , cikin nutsuwa ya fara mata magana "Well it seems you are not ready to respond, okay then ni....." , ďagowa tayi ta kalleshi , mutumin nan ne na ďazu a traffic kuwa "Hasbunallahu Wa ni'imal wakil ", dama haka yake, k'yak'yawa ne sosai ba kaďan ba , kuma fari ne sosai. .....", katse mata tunani yayi ta hanyan ci gaba da maganan shi " Ni sunana Abdallah , I know baki sanni ba but though may be you have seen me once, that is ďazu kenan if you could remember, I can't deny the fact that am in love with you, shiyasa I did all possible things to get to you today, Am praying and hoping that babu wanda ya rigani, ita gaba ďaya mutumin nan ya sata Jin wani iri , da k'yar ta samu ta ďago tace mishi "okay i will think about it " ta mik'e, gabanta yazo ya tsaya yace "toh tsaya mana, kamar wacce ake Kora, in kika tafi a ina zaki sameni in kinyi tunanin, kinga yanxu ki bani number ki, then anjima sai we will talk Dan naga you are not comfortable " Da sauri ta kaďa mishi kanta har sai da ta saka shi yin murmushi, a lokacin ta karanto mishi ta juya ta tafi, da ido ya bita a ranshi yana faďin "Alhamdulillahi yayi mata, yau zai faďawa Mummy wannan great News ďin dai ta daďe tana jira" , Murna fal ranshi shima ya fita daga ďakin Ranta b'ace ta shigo cikin gida, ignoring kowa tayi zata haura sama Aunty tace "zo nan Batuul" , dawowa tayi ta zauna daga gefe kanta a k'asa, "kikace baki sanshi ba, ya akayi yasan sunanki, har parlour ya shigo ya sameni yace min Batuul yake nema " , "Aunty nima ban san ya akayi yasan sunana ba , ni ban sanshi ba " ido Aunty ta k'ura mata da taga taqi magana tace mata "tashi kije" ranta gaba ďaya a dagule, ta rasa mey ya hanata cewa mutumin bata sonshi, ko dan ta ganshi matured ne not like the other guys da suke binta, alwala sallah Isha tayi ta tada Sallah, tana idarwa ta kwanta, tunanin abubuwan da suka faru a yau ta rik'a yi, abinda ke damun Ammah ne ya dawo mata, mesa Yaa Abu zaiyi haka, shi ko tsoron hakkinsu baya ji gashi har yasa Ammah a damuwa matar da take very jovial and authoritative ta zama very silent just because of Abu, tsaki taja tareda juyawa ďayan gefenta, dama can mugu ne shi ita ta dade da sanin haka, haka taci gaba da tunane tunanenta har bacci ya ďauketa, cikin bacci taji kamar wayarta na ringing , tashi tayi ta zauna ta duba screen ďin wayar, sai sabuwar number ta gani, har ya katse bata ďauka ba sai da aka sake k'iranta , ďagawa tayi bayan tare da tace komai ba, daga ďaya b'angaren taji ance " salamu alaiki Noor " cire wayan tayi daga kunnenta ta sakr duba number, cikin muryan bacci tace "ba Noor bace, it's a wrong number " zata ajiye wayan taji ya sake cewa "toh ai ke ďin Haske ce shiyasa na saka miki suna Noor " , cikin kosawa da surutun da yake mata tace "who are you " , murmushi yayi daga cikin wayan har tana jiyowa yace "It's Abdallah, tunda kin kasa ganewa let me tell you, well as it is, nakasa bacci because of tunanin ki na kasa bacci " ita dai bata ce komai ba sai shiru da tayi tana sauraronshi, "baza kiyi min magana inji muryan ki mai dadi ba Noor " a hankali tace "bacci nakeji yanxu bazan iya doguwar magana ba, am sorry you should call me tomorrow " , murmushi ya sakeyi yace "Alright Noor, it's okay kiyi bacci but gobe zan kiraki kuma zakiyi min magana but for now you should go to bed , okay? " a hankali ta amsa mishi da "toh" , yace mata "good night sleep tight" ya katse wayan, mamaki ta rik'a yi mesa shi wannan mutumin baya bata haushi kamar sauran mazan dake cewa suna sonta, ganin babu mai bata amsa yasa ta kwanta ta koma bacci B.A flight ne ya iso Nigeria K'arfe 6 na yamma, cikin mutanen dake fito fitowa daga ciki harda Abutturab da matarsa Ajiddeh, tafiya suke cike da nutsuwa, sunyi kyau sosai, kanta kwance yake kafaďanshi gashin nan da yasha gyara an barshi iska sai kaďawa yake , wani mutum ne yazo cikin hanzari ya karb'i Jakar dake hannun Abutturab yace "Sir this way please, the car is parked down there" bayan mutumin nan suka bi har wajen motar da zata kaisu, bayan ya buďe musu sun shiga sun zauna ne Ajiddeh tace "Babe, bana so muje gidanmu saboda y'an sa ido, kar aje ana cewa mun shigo gari, we should lodge in a hotel, kuma ma tunda babu wanda yasan muna hanya sai y'an gidanmu Mum da Yaa Zee kaga it will take time before a gyaggyara kuma ma ai ba daďewa zamuyi ba ana gama bikin nan zamu koma, so we should stay in the Hotel " gefen fuskanta ya shafa yace " alright then, hakan ma zaifi" Hotel ďin dai suke so su sauk'a suka faďawa mai tukin motar, ba b'ata lokaci ya juya yayi hanyan Hotel ďin da aka faďa mishi , suna isa bayan sun kama ďaki tayi ordering abinci taci tayi wanka tasa aka turo mata driver daga gidansu, Ce mishi tayi ya tashi su tafi yace mata "No he is exhausted, bazai iya zuwa ba , amma zaije dinner " ganin kaman ranta ya fara b'aci yayi maza ya taso ya rungumeta tare da mata peck yace "baby na gaji ne yanxu; I can't come but anjima zanzo dinner da za ayi I promise, kuma zan baki what you asked for " sai a sannan ta sake fuska tace "toh zaka K'aramin akan na da" yace "yeah , everything for you " juyawa tayi ta fita daga ďakin, da ido ya bita a ranshi yasan something is not right but ya kasa ganewa ko menene, ya rasa gane mesa baya iya yiwa Ajiddeh faďa akan abubuwan da takeyi , yanxu ko kayan jikinta ma bai kamata tana matar aure ta rik'a fita babu ďan kwali ba amma bazai iya ce mata komai ba, kan gadon ya koma ya zauna tareda da dare kanshi Dan mugun Sara mishi ya fara. 💖💝BATUUL 💖💝 26 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* A YEAR AFTER K'aran Alarm ne ya cika dakin gaba ďaya, kwance take tana bacci har sai da K'aran ya kusa katsewa tukunna taja tsaki, ta Janyo wayar da k'afarta, ko kallon fuskar wayar bata yi ba ta saka hannu ta katse karan tukunna ta maida wayan, duk abin nan da tayi bata bude ido ba, sai da ta mike ta zauna daga bakin gadon tukunna ta buďe idonta a hankali wayar ta sake ďauka taga 7:09, tafi minti biyar a zaune daga bisani ta mik'e tana fadin "mutum da kanshi zai saka abinda zai dameshi", gashinta ta tattare ta haďe su waje ďaya, ta isa inda bathrobe dinta ke rataye ta cire kayan baccin dake jikinta ta saka bathrobe din ta shige toilet, sai da tayi brush tukunna tayi wanka, gaban mirror ta zauna bayan ta fito daga wanka ta shafe duk jikinta da mai,ta fesa body spray tukunna ta je saka kaya, closet dinta ta buďe ta ciro wata coffee abaya mai Babban hannu da adon milk daga jiki, sai da ta saka kayanta tukunna tayi inda jakunkunanta ke rataye ta jawo d'aya daga ciki ta zuba tarkacenta a ciki sannan ta yafa gyalen abayar a kanta sannan taje ta saka slippers din Laura Ahman shima milk, har ta fita ta tuna da key ď in mota da wayarta ta koma cikin hanzari ta ďauko lokacin 8am daidai, k'asa ta sauk'o babu kowa a gidan shiru, ta tasan kowa ya tafi makaranta, Aunty da Baba kuma mayb suna bacci, ta nufi dinning area, sai da ta bubbuďe duk kwanun dake dinning din tukunna ta ďauki soviet ta ďauki sandwich ďaya a cikin wani transparent bowl, ta ďauki disposable cup ta tsiyayi fresh orange juice a juice dispenser, har ta zauna zata fara ci taga time zai k'ure maza ta mik'e ta yi hanyan waje , sai da ta taje dab bakin k'ofa zata fita Taji muryan Aunty a zaune a parlour tana ce mata "sannu Batuul , kin kyauta , cin abinci a waje ko ? Nasha fada miki banaso babu kyau shine kika wani ďauki sandwich a paper kamar wacce ta rok'o toh yayi miki daidai", sai da Aunty ta gama maganan da takeyi tukunna ta juyo da murmushi a fuskanta ta dubi Aunty tana k'arasowa cikin parlour ta ce "Aunty Nda wattu, nifa banma San kin tashi ba, Ina kwana" ta sake maimaitawa bayan ta zauna kusa da Aunty, Da lafiya Aunty ta amsa mata sannan tace "Batuul ba kya Jin magana ko" Da sauri Batuul ta girgiza kai tace "Aunty ba haka bane fa, har na zauna zanci naga time ya kusa k'urewa zanyi latti shinefa zanje mota dashi , bama a layi zanci ba fa" ta gama maganan tana sadda kanta k'asa dan tasan Aunty ta hanata, Sai da Aunty ta dubi hannunta taga ma abinda ta ďauka din tukunna tace "mota ba layi bane ko ? Ai cikin gidane, kuma waye ya hanaki tashi da wuri har kika kusa lattin ke da ba sllh kike ba bare ace baccin asuba kika koma kika makara, kin wani ďauko Sandwich ďaya kamar wacce ta rok'o" ganin faďan baya k'arewa kawai ta fara cin Sandwich ď in tana tunkud'awa, haka ta gama ci tana kurb'an juice ď in har ta gama, mik'e wa tayi zataje ta ajiye sauran juice da ta rage, dama tunda ta fara cin abincin Aunty bata kalleta ba sai da ta gama ta mike tukunna ta dubeta tace "sauran Juice din kuma fa? wa kika ragewa" marairaicewa tayi tare da da juyowa tace "Aunty na koshine zanje in ajiye", "Da kinsan bazaki iya shanyewa ba kika ďebo dayawa, dawo ki zauna ki shanyewa shi", haka ta dawo ta zauna ta shanye a ranta tana addu'a Allah yasa bata yi latti ba, bayan ta gama shanyewa a dustbin ta jefa cup din da tissue ta dawo tace "Aunty zan tafi" ďagowa tayi ta kalli Batuul tace "A dawo lafiya, Allah ya bada sa'a" ta amsa da Amin ta wuce, har taje bakin k'ofa Aunty ta sake k'iranta "Batuul", juyowa tayi tare da cewa "Na'am Aunty", "What time zaki gama lectures" Aunty ta tambayeta, "10:30 zan gama, class ďaya dani yau, by 11am zan dawo", "okay in kin gama inaso kije ki gaida Ammah, jiya munyi waya tana tambayana ke, so ki wuce daga can sai ki dawo da yamma" toh kawai tace ta fita, Parking area ta nufa taga ďaya daga cikin masu aikin gidan na goge motar, farar BMW, k'arasawa tayi wajen motan tana laluben makulli daga cikin jakan, ďagowa tayi bayan ta samu makullin ta amsa gaisuwan da mai aikin ke mata "Yauwa Friday sannu da aiki" ta danna button din motar, kamar jira yake dama tana dannawa ya buďe mata, sai da ta shiga ta zauna tukunna ta ciro ďari biyar ta mik'a mika mishi, murna ya dinga yi yana mata godiya, murmushi kawai tayi ta jawo motar ta ta tafi, a bakin gate ma sai da ta mik'awa masu gadin ďari biyar biyar tukunna ta fita daga gidan, a wajen wani traffic ta tsaya tana jira a basu hannu su wuce, wani super tint AMG ce ta tsaya daga gefenta nata, bata kalli motar ba saima wayarta da ta ďauko daga ďayan kujeran zata duba time, jiya tayi kamar ana kallon ta ta gefe, a hankali ta juya ta dubi gefenta, k'irjinta ne taji yayi dam , wani mugun faďuwa gabanta yayi, sosai ta tsorata da mutumin dake cikin motar dan wani irin kallo ya tsaya yana yi mata, sunan Allah ta shiga jerowa tare da fatan traffic ď in ya basu daman wucewa ta wuce, bata sake k'ok'arin kallon gefen ba, a haka traffic ď in yayi signalling ďinsu da su wuce, a guje ta figi motar kamar mai shirin tashi, Sai da tayi nisa sosai tukunna ta ďago ta rear mirror ta duba ko mutumin na binta a baya amma bata ga alaman motanshi ba, wani ajiyan zuciya tayi tare da faďin Alhamdulillah a fili, 8:34 daidai ta isa school, dpt dinsu taje tayi parking sannan ta fito tayi hanyan class ďinsu, a tare da lecturer ďinsu dai dai suka iso, ta k'ofan baya ta shiga ta samu waje ta zauna , nutsuwa kowa yayi a ajin har malaminsu ya fara lecture, 10:30 dai dai ya gama ya fita suma suka mik'e suka fito, sai da ta ďan gaggaisa da y'an ajinsu da ta sani tukunna tayi hanyan motan ta , bata tsaya yin komai ba ta shige ta wuce abinta, hanyan gidansu Farida tabi, a hanya tana driving tana tambayana k'iran number Farida tasan duk yadda akayi dai ta tashi daga bacci yanzu dan can gari yanxu 2 biyu tayi, sau biyu tana k'ira bata ďauka ba, cikin minti 18 ta isa, har cikin gida ta shiga tayi parking , da sallama ta shiga parlour babu kowa a ciki sai kanshi da yake tashi, hanyan stairs tabi zata hau sama wata mai aiki ta fito daga kitchen ta gaisheta sannan ta tambayeta Ammah na gida, Ce mata tayi ehh tana sama, godiya tayi mata ta k'arasa hawa Saman, a hankali ta buďe k'ofan ďakin Ammah tare da sallama, su biyu ta tarar a zaune, da gudu Farida ta taso ta rungume Batuul tana ce mata "dullop head I missed you, you didn't tell me zakizo" murmushi Batuul tayi tace "ai yanzun ma ba wajenki nazo ba" bata rai Farida tayi tace "Really? well am not hurt, nasan zaki dawo ki nemenin nima" ido Batuul ta juya tare da mata gwalo tace "not in this life" Ammah na daga zaune tayi murmushi ta girgiza kai, gaban Ammah Batuul taje ta zauna tace mata "Nda dubdo Ammah" , "Lafiya kalau Bitti, ya gida ya Aunty, ya kuma karatu, ana dai yi lafiya ko'? kai ta gyaďa mata tare da cewa "Alhamdulillah Ammah , duk lafiya " dubanta Ammah tayi tace "kin buya Bitti, sam ba a ganinki ko kuma makaranta ne? " Da sauri ta sadda kanta k'asa dan tasan bata kyauta ba, rabonta da gidan ta kai wata biyar, kuma kullum suna haďuwa da Farida a school, jiki a sanyaye ta girgiza kai tace " Ammah, zan rika zuwa yanxu" Ammah tace "toh yayi kyau, ai Faridan ma ďazu da asuba suka iso, ni yanxu zan shiga in kwanta dan yau ban samu nayi bacci ba tunda Farida ta iso ta isheni da surutu" ta faďa tare da mik'e wa zata kwanta , da ido Batuul ta bita ganin yadda maganan Ammah yayi sanyi gashi har ta ďan rame, ganin zata juyo ne ya sata tayi maza ta ďauke idonta daga duban ta, Ce musu ta sakeyi " Farida in kun sauk'a ki turomin Yaa Bawa" tare suka amsa da toh dukkansu biyun, tana shigewa Batuul ta Janyo hannun Farida tana tambayanta "Ke da muka turaki Uk kiyi wata ďaya shine ko sati ďaya baki cika ba kika dawo " Suna fita suka haďu da Yaa Bawa ta tattaro kaya zatayi k'asa suka ce mata Ammah na nemanta sannan suka shige ďakin Farida "Batuul ce ta sake tambayanta "wai meye inata magana kinyi min shiru" tsaki Farida taja tace "ai ni da dan ta nice wlhy ko kwana ďaya banyi a kasar nn, dama can ba so nake ba Ammah ta sani dole inje, wlhy saura kaďan in mutu dan baqin ciki, dama sai da kika tayi min dariyan mugunta har da wani rakani airport bakiga ko waya banyi nace miki zan dawo ba, ni nan gaba ko meye za a bani ba zanje gidan ya Abuu ba, toh meye ma yayi zafi, ni dai ban k'ara zuwa, gidan Yaa Abu bai yi ba, shi zafin kai matarsa y'ar duniya mara mutunci, gaba ďaya ta gama da Yaa Abu, Dan tausayi ma yake bani " tsaya Batuul tayi tana kallonta har sai da tayi shiru tukunna tace "tun ďazu kike surutu, tell me exactly what happened da kika dawo before time " tsaki Farida taja tace "kina son spoiling mood ďina ko, toh tunda baki ganeba, gidan ne babu daďi, tunda nayi stepping k'afa na a cikin gidan maganan arziki bai tab'a haďani da Ajiddeh ba, kai tun lokacin da na shigo gidan tana hakimce a parlour ita da wasu y'an uwanta ko k'awayenta ne oho taqi amsamin sallama ban sake bi ta kanta ba, shima Yaa Abun da ya dawo gida da yamma naje zan fara mishi complain cewa yayi wai shi fa baya son K'ananan maganganu , wai haka matar tashi take I shud let her be, ni nake dafawa kaina abinci, shima ďin sae dae Cook suyi ya ci, gara ma da naje ne take ďan sani in dafa mishi wani abun, kuma baya iya ce mata komai duk iskancin da takeyi, daga ta ganni zata fara wani shan magani tana habaice habaice, har da cewa rannan wai aikin banza, ai mun riga da mun makara daga ni har iyayena tunda har muka bari ta aureshi, toh shine shekaran jiya da naga iskancin nata kaďan ne da ta saka Ammah jiya na tashi na bita har ďaki bayan y'an iskan y'an uwan nata sun tafi nace wlhy in ta kuma faďin wani abu akan iyaye na sai na lakaďa mata dukan tsiya, kuma in daki banza babu mai ce min komai, da yake k'aramar y'ar iska ce bata ce min komai ba...." Ido Batuul ta wara ta riko hannun Farida tace "Dan Allah dagaske kike, duka fa kikace zakiyi mata har ďakinta kuma, ta girmemu fa sosai farida" hannunta ta Janye tace "Ni ina ruwana da girman ta, ai bata rike ba, y'ar rainin hankali ai da ta sake faďin wani abun wlhy da sai ta raina kanta, sai na kusa illatata, Dan ko banida karfi sai na samu wani abin na bigeta dashi, shine fa bayan Yaa Abu ya dawo, yana shigowa ta fashe da kukan munafurci wai yau wuni nayi ina zaginta har dasu dungure mata kai, dukana kadae ne bae yi ba in gaya maki, shine fa yayi maza yayi min booking flight na dawo yau, har ce min yayi fa wai hutun ya isa haka in koma dama shi bai nemeni ba bare inzo ina tayarwa matarsa hankali, Dan bakin ciki ma ko tsayawa banyi na mishi explaining komai ba na juya naje haďa kayana, a parlour ma na kwana shi kuma ya jata sukayi sama , da asuba ya sauk'o ya tulo min kuďi masu Uban yawa kamar su aka ce mishi nazo nema, ya haďani da John Driver ďinshi ya kawoni airport, da ya rakani bakin k'ofa nidai sai da na mishi magana nace mishi wlhy Hakkin su Ammah bazai barshi ba, tunda yayi aure sau ďaya ya tab'a zuwa ya dubasu waya kam ba a xancen sa don baya kira, kuma fa ba wai baya shigowa Nigeria ba, yana shigowa Dan ko randa naje a jiyan shi ya dawo, sai da naga jikinshi yayi sanyi tukunna na fita na bar mishi gidanshi, yau da asuba muka k'araso, kinji yadda akayi na dawo banyi wata ďaya ba, tagumi Batuul tayi tana kallonta cike da tausayin Ammah, shi yasa duk bata da sukuni knn ta ga ta rame, gskya ya Abuu bae kyauta ba. Hi Everyone out there reading Batuul , EID MUBARAK, Allah yasa Ibadunmu karbabbune, so sorry for the late post, alot of things came up so I couldn't write but daga yanxu har a gama Batuul In Shaa Allah baza s samu matsala ba though nasan am a lazy writer in (Sister KHALEESAT's voice 😁), but then I will try and be updating you everyday In Shaa Allah, A small Sallah gift from Phartiemarhk to you guys, Luv you [truncated by WhatsApp] 💖💝BATUUL💖💝 31 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Washe gari da asuba Batuul na xaune kan darduma ta idar da sllh Anty ta shigo dakin tace mata in gari ya gama waye ta sameta a bedroom dinta, hakan kuwa akayi wajen takwas ďin safe taje tayi knocking k'ofan Aunty, sai da taji an bata izini tukunna ta shiga, Aunty na kwance kan gado ganin Batuul ya sata mik'ewa dan dama ba bacci takeyi ba, tun daren jiya bayan sun gama magana da baba ta kasa samun nutsuwa, daga gaban dressing mirror Batuul ta tsaya ta kasa k'arasawa ganin yanayin Aunty kamar wani abun na damunta, alama tayi mata da ta zauna tukunna ta samu waje daga k'asa ta zauna tareda gaisheta, magana Aunty ta fara yi mata kamar haka "Batuul ke kika cewa Baba kina son aure" da sauri Batuul ta ďago kanta jin abunda Aunty ta faďa gabanta na faduwa, lkci daya idonta ya cicciko da hawaye ta ma rasa mey zata cewa Aunty, sai da Aunty ta sake magana tace tambayanki nake Batuul kika min shiru", hawayen dake idonta har ya fara gangarowa ta shiga girgiza kai cikin sheshek'a tace "Aunty wlhy Allah ban tab'a irin maganan da Baba ba, ni bansan wa ya faďa mishi ba, ni da nake son inyi karatu", taci gaba da goge hawayen dake kwaranya a idonta, da tausayi Aunty ta dubeta dan dama tasan babu yadda za ayi Batuul tace tana son aure, dama so take ta ga ko Batuul ďin na da ra'ayin aure sai ayi mata amma ba da mai mata ba, ae kam sam baza ta yadda da wannan batun ba, baxata yrda a cutar mata 'ya ba, Aunty ta sauke ajiyar xuciya tace "rantsuwan kuma na meye,ni bance kimin kuka ba, tambayanki kawai nayi, tashi kije kici gaba da abinda kike yi Allah shi miki albarka," kasa mik'ewa Batuul tayi daga zaunen da take sai da Aunty ta sake ce mata "Tashi kije shikenan", hak'uri ta shiga bawa Aunty tana kwalla tace "dan Allah kiyi hkuri Anty amma ni bn ce ina son aure ba" tausayinta Aunty taji tace ta tashi ba komai, in ta shirya tafiya school ta sameta tukunna, da kyar ta samu ta tashi ta fita daga ďakin dan har kanta ya fara sarawa. Zaune yake a garden din gidan da yamma misalin biyar da wani abu yana kallon tsuntsayen dake ta shawagi abunsu a sama, dan yanxu bashida aiki sai na xama da tunani, wayarsa ne ya soma ringing, ya dauki wayar ganin mai k'iransa yasashi recieving da sauri cike da Mamakin kiran, daga daya bangaren Ammah tace "Ina neman ka ynxu" d'aga hka ta katse wayar, mikewa yyi da sauri ya nufi cikin gidan duk da bae san kiran da take masa ba amma ya ji ddin kiran Mahaifiyar tasa, har ya manta rabon da su yi magana ta waya da ita, bedroom dinta ya nufa da sallama ya tura kofar yaga bata ciki, dai dai nn farida ta fito daga dakinta ya juya yana kallonta yace "Ammah fa?" Tace "Tana bangaren Abui ae," a hnkli ya rufo kofar ya nufi bangaren Abui, sae dae duk jikinsa yyi sanyi ya rasa dalili, da sallama ya shiga falon kansa a k'asa ya xauna kan lallausan carpet din dake malale tsakiyar falon ya gaida iyayen nasa, Abui ne ya amsa, daga hka ya sunkuyar da kai yana jiran jin kiran da iyayen nasa suka masa, Ammah ce ta fara magana kamar hka "Aliyu kana jina koh" d'ago kai yyi yana kallonta sanin a serious issues take kiran sunansa kan tsaye, yace "Ina ji Ammah" in a serious tone tace "Aliyu a gskya mu kam bamu ga amfanin auren nn naka da kayi ba, Sam bashi da amfani, mun tilasta ka kayi aure ne don mu samu kwanciyar hankali kai ma hka, sae dae we were mistaken don tun da kayi auren nn hankalinmu ke tashe, baka yi sa'ar mata ba Abuu, da mun san abinda xae je ya dawo knn da bamu yi Na'am da yarinyar ba, kwata kwata bata san darajan iyayenka ba sae nata, don hka ni da mahaifinka mun yanke shawarar kara maka aure" d'ago kai yyi cikin rikicewa yace "Aure kuma Ammah?" Ta hade rae tace "Kwarae kuwa aure" marairaice wa yyi yace "Ammah ko shekara guda knn fa....." Tsawa ta daka masa tace "Ko ka wata guda ne, meye amfanin yarinyar da take neman rabaka da iyayenka da 'yan uwanka, kai har kana da bakin yi mana musu Aliyu, toh wllh ka guji bacin raina, 'yar mutunci da tasan darajanmu da xa kuma ta dinga nuna maka muhimmancin 'yan uwanka xa mu aura maka," ya share xufar da ke keto masa kmr xae yi kuka yace "Ammah wllh ina son Ajiddeh kuma ni bni da ra'ayin hada mata biyu, ku tausaya...." Wani tsawan da ya fi na da Ammah ta daka masa cikin fushi tace "Shknn Abuu, ni xan hakura in bar ma Ajiddeh kai sae ka maida ta uwarka, d'a na Aliyu da na sani a da baya min musu, jikinsa na rawa yake daukar duk abinda nace, ni kam wnn ba Aliyu na bne nasani...." Hawaye ne ke sakko mata sosae, jikinsa yyi sanyi ya dawo kusa da ita ya rike kafafuwanta cikin rawar murya yace "Haba Ammah, ni din bnxa xa ki xubar ma hawayenki, bani da amfani in har xa ki dinga xubar min da hawaye, kiyi hkuri ki rufa min asiri amma, hawayen ki masifa ne a gare ni, wllh na amince da kome kika ce, Aliyun ki ne ni ba a canxa maki ba wllh" duk ya rikice ba kadan ba yana rike da kafarta, kallonsu kawae Abui yake bae ce komae ba, Ammah taji ddin hkn ta shafa kansa cikin sanyin murya tace "Allah maka albarka" dagowa yyi da sauri ya daura hannunsa kan cinyarta yace "Nagode Ammah na" bata kuma cewa komae ba ya koma ya xauna ya langwabar da kai yana kallonta yace "To wace matar kika xaba min Ammah" kallonsa tayi bbu yabo bbu fallasa tace "Ba wata bace facce 'yar uwarka Bitti" xaro ido yyi ya koma baya da sauri yace "Batuul???" Ta hade rae tace "ita fa" innalillahi wa inna ilaihi raji'un, abinda ya dinga maimaitawa knn yana kallon Ammah da ke ta hararansa tana karkada kafa. A bangaren Ajiddeh kuwa tun ranan da sukayi waya bata sake k'iranshi ba saima ďagawa su Mummy hankali da tayi akan abinda ke shirin faruwa tsakaninta da Abutturab, su Mummy ganin abin na nema zama matsala ne dan ta dena kula kowa ita fa sai ansan yadda za ayi mijinta ya zama kamar yadda yake a da, Jainaba ce ta kawo shawaran su ziyarci sabon bokan da taji ance yana aiki kamar da bakin wuk'a amma fa ba a k'asar nan yake ba, yana can Tchad, a ranan sukayi shiri akan gobe zasu tafi, da daddare Mummy da kanta take sanarwa Daddy akan zasuyi tafiya gobe, da ya tambayeta inda zasu tace mishi ai kakar su Ajiddeh zasuje gaidawa sabida tun kamin aure rabonta da ita kuma ba lafiya bane da ita, da mamaki yake tambayan Mum akan dama Ajiddeh bata koma ba tun bayan bikin dan shi sam baisan ma tana gida ba, Mummy ce tace mishi "ehhh wai mijinta take jira akwai abinda yakeyi a nan ďin", cewa yayi "kuna dawowa ta koma wajenshi, in ta zauna a nan ďin amfanin mey take mana, taje can gidan nashi su zauna idan kun dawo", toh kawai Mummy tace ,cheque yayi musu signing yace su rubuta amount ďin da zasu buk'ata tunda ziyara zasu, basu sanar dashi ma cewa da mota za a yi tafiyar ba, washegari k'arfe shida suka ďau hanyan Maiduguri daga nan zasu shiga Tchad ta can, tafiya sosai sukayi bayan sun isa Tchad kamin su isa k'auyen da bokan yake, da k'yar suka samu sukaje inda yake, wata bukka ce da gani ta daďe ko ina duhu sai wani đan haske dake fitowa daga windon bukkar, da zuwansu yace musu yasan abinda ke tafe dasu duk ya sai dai akwai abinda har yanxu ya kasa ganowa, shima baisan meye bane amma abin babba ne, kuma nan gaba yake shirin faruwa, har saida yace musu duk laifinsu ne da tun farko kamin bikin sun nemeshi da duk matsalan babu, hankalinsu ne ya k'ara tashi gaba ďayansu babu ma irin Ajiddeh suka shiga bashi hak'uri kamar sun mishi laifi, zata iya yin komai in dai akan Abutturab ne, gaban bokan ta sake matsawa tace "naji ranka shi daďe, amma tunda al'amarin bai faruba yanxu, ni ayi min abinda zai manta da kowa kuma bazai sake waiwayen gida ba, sannan daga baya sai mu san yadda zamu b'ullowa abun dake shirin faruwan", kai ya kaďa bayan ya gama jin batunta yace " hakan ma yayi", tashi yayi ya shiga wani ďaki daga cikin bukkar ya fito rik'e da wani k'warya, sai da ya zauna ya zauna ya mik'o mata wani kuttu yace "ga wannan nan zaki samu tsohuwar bak'ar tsamiya, da hannunki zaki jik'ata, sai ki ajiyeshi a waje mai danshi da sanyi, kada ki bari rana ya tab'ashi, shi kuma wannan", ya mik'o mata wata bushashiyar fata yace "garin maganine a ciki, tunda dama yace kiyi tafiyarki toh aikin zai zo ma da sauk'i, wannan garin a k'ofar gidanki zaki barbaďa, sai kuma wajen kwanciyanshi nanma zaki barbaďa, Kinga yadda wannan tsamiyar keda tsami da duhu, haka zai rik'a ji duk lokacin da ya tuna gida, sanyin nan kuma da kika ajiye a wajan, duk lokacin da ya ganki ko ya tuna dake haka zai rik'a ji, g'arin nan kuma da zaki barbaďa, yadda iska zai kwasa ya tafi dashi wajen ya shafu haka zai shafe babin gidansu a k'wak'walwarshi", duk maganan har suka gama da yarensu sukeyi, wani irin murna Ajiddeh takeji har cikin ranta shikenan zata samu yadda takeso, kuďi masu yawa suka zube mishi tareda mishi alk'awarin dawowa bayan kwana biyu, suna fita Ajiddeh ta dubi su Mummy ta ce "Mum, gobe zan koma, inada Visa ticket kawai zan siya shima online zanyi dan bansan lokacin da zai koma ďin ba, gara inje tun wuri in gama abunda zanyi", Mummy ce tace "toh shikenan, duk yadda akayi sai ki faďa mana a waya, Allah dai ya taimakemu ya bamu sa'a, a daren suka ďau hanyan birnin Tchad, murna fal cikin Ajiddeh. Batuul na gama shirin makaranta tazo yiwa Aunty sallama zata wuce, bayan ta gaidata ne tace "Aunty yau in na tashi daga school zanje gidansu Farida", dagowa Anty ta da sauri tana kallonta tace, "mey zakije yi a gidan?", da mamaki Batuul ta dubi Aunty dan bata tab'a hanata zuwa ba, asalima ita ke sata zuwa ko bata son zuwa, cewa tayi "wajen Farida zanje, nace mata zanzo jiya banje ba shine zani yau" a takaice Anty tace "No ki bar zuwan , some other time kya je, ki dawo gida in kin gama lectures kawae", jiki a sanyaye Batuul tace "toh Aunty na tafi", "Allah ya dawo dake lafiya", a hka ta fita dakin, tana fita k'iran Abdallah ya shigo wayanta, sai da ya kusa katsewa tukunna ta ďauka, a hankali tace "Hello", wani k'ayataccen murmushi ya saki yace "Habibty hope ba tada ki nayi ba, naji voice ďinki so low", ce mishi tayi "No am okay, yanxu ma school zanshiga, tun ďazu na tashi", yace "okay okay durlyn, i will meet you there cux nayi missing cute face ďinki", ce mishi tayi "toh, sai kazo", ta shige mota ta wuce school. 💖💝BATUUL💖💝 32 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Gaba ďaya ji yayi kanshi yayi mishi nauyi, idonshi ya canja kala ya zama ja har wani gumi ne ya tsatsafo mishi a goshinshi, ya girgiza kai yana ci shiga gaba da ambaton innalillahi wa inna illaihir raji'un, sai da yaji bugun zuciyanshi ya ďan daidaita tukunna ka kalli Ammah dake hararansa har lkcn ya marairaice murya yace "Ammah ki min rai ki aura min wata daban amma ba Batuul ba, yarinya ce fa karama, kuma kila ma baxa ta rasa saurayin da take so.....," wani irin kallo Ammah ke mishi, hkn yasa ya sunkuyar da kai ya kasa k'arasa maganar, Ammah tace "ko ma dae jaririya ce, ita din muka yi niyyan hada ka da, don nasan xata fi mana babban macen da ka aura, in kuma nuna mana xaka yi ba mu isa ba bismillah, ae dama ka saba daga sanda kayi aure" Runtse ido yyi a hnkli yace "Wane ni Ammah, in'sha Allah yanda ku ka ce hkn xa ayi." jin ya faďi haka yasa Ammah sakin fuska ta juya ta kalli Abui tace "dama nasan ďana zaimin biyayya, tashi kaje, Allah shi maka albarka, bbu 6ata lkci xa ayi komae don ka koma bakin aikin ka", shafa kanshi tayi tace " Allah maka albarka" da k'yar ya samu ya mik'e daga tsugunen da yake, yayi musu sallama ya fita daga falon, abubuwa ne suka mishi yawa a kanshi, shi ta ina zai fara sanarda Ajiddeh ma aure iyayensa xa su masa, kuma ma matar ba wata bace illa Batuul, yarinyar da bata wuce sha takwas ba tsabar a ja masa raini, me zaiyi da Batuul yarinyar cikinsa? shi if he can clearly remember ma ai Massa ke sonta tun kamin ya bar gari, tunawa da yayi da Massa ne ya sashi saurin ciro wayarshi daga cikin aljihu ya lalubo number shi Massan, dialing biyu ya ďaga, "dama ana jinka a gari", abunda Massa ya fara faďa kenan, share tambayar da Massa ke mishi yayi yace "Kana inane?, inaso mu haďu", ya tsaya jin mey Massan zaice mishi, cewa yayi na fita yanxu bana gida but i will b back in an hour", yace "Aii then, zanje gida yanxu before ka dawo zan shiga in gaida Yaa Mera, sai ka dawo ďin, i need to discuss some issue with you", da haka suka katse wayan, suna gamawa ya murďa k'ofan ďakinshi ya shiga ya ďauko key ďin mota ya fito waje, direct hanyan gidansu Massa ya ďauka, cikin y'an minutes ya isa gidan yayi parking bayan an buďe mishi gate ya shiga, Side ďin Yaa Mera yayi, tayi mamakin ganinshi, dan rabonshi da gidan tun aurenshi da Ajiddeh da yazo yi mata sallama, mamaki shimfiďe fuskanta tace "Wata sabon gani Babana kaine a gidan nan yau, ashe ka shigo gari", k'arasowa yayi gabanta ya zauna yace " *Yaa Nda dubdo, aaah u' bèlan amma tusen gèi*, "ina wuni Yaa, ehhh na shigo amma banma daďe ba", ya k'arashe maganan da murmushi a fuskanshi, hira sukayi sosai da Yaa har tana ce mishi matarshi dai ba 'a ganinta, har sun manta kamanninta,suna nan zaune Massa ya shigo da sallama, tun daga can ya tsaya k'are ma Abutturab dake gaban Yaa Mera kallo, ba makawa Abu ne sai dai ya ďan rame, ko meye dalili oho yaci gaba da shigowa abunshi cikin ďakin, hannu ya mik'awa Abutturab tareda cewa "Man an dena ganinka, rabona dakai fa tunda naje wajenka kamin kazo gida, that is two months after your wedding, i tot baza ka shigo bama sai aure na ai", Yaa Mera ce tace "Abunda na gama faďa mishi kenan, nace gashi matar bata haihu ba bare mu muje can suna tunda su sunqi su zo gunmu", sauk'ar da kanshi yayi k'asa dan shima abin nan da yayi na damunshi, gashi nan har yana son zame mishi matsala, Massa ne yasa dariya yace "Kaji ko, ashe su Yaa zaman jiran jikansu suke, sai kayi k'ok'ari ku samo musu kai da Ajiddeh, kaga sai suji daďin bin naku can garinku mai daďi da baku son bari", wani kallo ya sakarwa Massa da ya sashi k'ara yin dariya yace "toh ba gaskiya bane", mik'ewa Yaa Mera tayi ta shige daga ciki su kuma suka wuce chamber ďin Massa, suna shiga ďakin ya zauna a ďaya daga cikin kujerun ďakin tareda mik'e k'afafuwanshi, Massa ya dubeshi yana buďe fridge zai ďauko ruwa yace "wai gajiya kayi ne haka na ganka so slow, ko kuma duk cikin canjawan da kayi ne", wani irin glare ya wurgawa Massa ya tashi daga kwancen da yake ya zauna, k'arasowa Kujeran Massan yayi shima ya zauna tareda mik'awa Abutturab ruwa, karb'a yayi bayan yasha ya rufe ya ajiye bottle ďin daga gefenshi ya fara msgana kamar haka "Musty, kwanankin baya lokacin biki na kamar naga you showed interest akan yarinyar nan, har yanxu kuna tare ne?", yayi tambayar yana kallonshi, gaba ďaya kan Massa ya ďaure dan shi baisan ma wace yarinyar yake tambaya ba, cewa yayi "wacce yarinyar wai, dan ni ban gane wacce kake nufi ba", ce mishi yayi yarinyar nan k'arama mana, yarinyar Aunty", tsaki Massa yaja yace "kaji ka da wani zance, Aunty ďaya muke da mai k'aramar yarinya, specify inji", shiru yayi ya kasa furta sunan nata, da k'yar ya iya buďe bakinshi yace "Batuul", "ohhh dama wai Batuul kake nufi kake ta wannan abin, wait!, dont tell me bakasan zancen aurena ba", da mamaki Abutturab ya dubeshi yace "kayi aurene?", kai ya girgiza yace "No banyi ba but nan da two weeks za ayi", kan Abutturab ne ya ďaure, yaushe Massa zaiyi aure har bai sani ba, kuma wa zai aura inba Batuul ba, yes ba Batuul bace tunda har su Ammah sukace ya aureta, da sauri ya juya ya dubi Massan da ya zuba mishi ido ganin yadda yake abu kamar ba shi ba yace "Tell me wacece zaka aura inba Batuul ba, kuma ya akayi haka bayan at that time kace min sonta kakeyi", murmushi Massa yayi yace "Toh kai duk mey ya kawo zancen nan, kai da kace mey zanyi da yarinyar tayi k'arama shiyasa na rabu da ita", kai Abutturab ya girgiza yace "c'mon jokes apart, ba wasa nake ba, mesa ka rabu da ita kuma wa zaka aura?", Massa ne yace "Rahama mana zan aura, y'ar Sultan, Batuul tun lokacin ta nuna bata sona shiyasa ma ban kai abun wajensu Ammah ba, but naso in aureta, she will make a good wi.....", wani tsaki Abutturab yaja yace "hold it, okay?", gaba ďaya ranshi ya b'ace, sai da ya ďan nutsu tukunna yace "Mustapha am in a problem, kuma babu mai iya fiddani sai kai, kasan auren nan da nayi shekara kenan, kuma su Ammah suna ganin shine ya hanani zuwa inda suke, and ni inason Ajiddeh, like banima da ra'ayin mata biyu, i cant cope, toh ďazu su Ammah suka tareni da zancen sai na k'ara aure, da nace suyi hak'uri, amma ganin ransu ya b'aci yasa nace na yadda, toh shine da na tambayesu wa suke so in aura, dan ni i have no one in mind shine sukace min wai Batuul", yadda ya k'ira sunan nata kamar ba daga bakinshi sunan ya fito ba yayi maza ya ďauke idonshi daga kan Massa , dariya Massa yasa harda kyakyatawa ya kwanta akan kujeran, sai da ya gaji dan kanshi ya gama dariyan tukunna ya mik'e ya zauna, Abutturab ko kallonshi baiyi ba har ya gama dariyanshi, sai da yayi shiru tukunna yace mishi "ka maidani ďan iska ma ko, inyi maka serious magana shine kake dariya", ya k'ara tamke fuska ya tashi zai bar ďakin, da sauri Massa ya sha gabanshi yace "No baza muyi haka ba, mu koma ka faďamin how am i of help dan ni gaba ďaya zancen ne yazo min a bazata, kaga kuma tunda bazanyi kuka ba ai sai inyi dariya", ya faďa yana k'ara smiling, wani siririn tsaki yaja ya koma ya zauna a kujerar da ya tashi, sai da dukkansu biyu suka zauna Massa yace "ina jinka, mey kakeso inyi maka?", shiru yayi ya kasa magana dan baisan ya Massa zai ďauki zancen ba barema da yace aurenshi nan da sati biyu, iska ya furzar daga bakinshi sannan yace "Inaso kaje kacewa su Ammah kai ke son Batuul, zaka aureta", a razane ya juyo jin abinda Abun ya faďi yace "Are you really okay, duk yadda akayi Ajiddeh har brain ďinka ta tab'a, toh in naje nace musu inasonta sai inyi yaya da ita bayan inada mata", kai ya girgiza yace mishi "ai dama kana sonta, kuma kasha faďamin kai baza ka zauna da mata ďaya ba, and as crowned prince kaga zaka k'ara wata, kaga tunda sooner or later zakayi, y not do it now", kai ya girgiza yace "No way, thats not happening with me, bazanje inyi abunda ban shirya yinshi ba besides ai Batuul ďin na faďa maka da kanta tace min bata sona, kaga there is no way zan auri yarinyar da bata sona", kai shima ďin ya girgiza yace "Musty you are not understanding the whole thing, am telling you......", katseshi Massa yayi yace "hold on, kai mesa baza ka auri Batuul ďin ba, she is perfect, beautiful, simple, religious, mey kuma zaka nema bayan wannan, like menene aibun Batuul, ni wlhy da zata soni zan aureta but ta riga da tace min bata sona, so i will b living with that intuition a cikin kaina shiyasa bazan nemeta ba, kuma tunda har su Ammah ne suka nema maka auren nan i bet its for everyones welfare, they have seen the best in her, kuma ni nasan they have a genuine reason for all this, Batuul is your sister, you can tell others who she is, kafi kowa sanin asalinta", kanshi ya sauk'e k'asa ya rasa ya za ayi ya fahimtar da Massa akan bazai iya auren yarinyar nan ba, yafi minti ďaya kanshi na dafe kan hannunshi tukunna ya ďago a fusace har idonshi ya canja launi yace "Na faďa maka bazan iya aurenta ba", sai kuma ya sassauta murya jin ihun da yayi yace "Mustapha i cant marry her, like i cant withstand her for a day, bare kuma har aure da yake for eternity, i just cant, i dont know but there is this effect she have on me anytime nake tareda ita and am never comfortable with what i feel", ya k'arashe maganan yana mai sauk'e idonshi daga kallon Massa, Ajiyar zuciya Massa yayi ya dafa Kafaďan Abu yace "okay calm down, kasan mey za ayi yanzu, ka kwantar da hankalinka, addu'a kawai zakayi akan lamarin nan, zamuyi magana daga baya, kuma kada ka nunawa su Ammah baka so dan ransu zai b'aci", shima Abun ajiyar zuciya yayi yayi patting hannun Massa dake kafaďanshi yace "In sha Allah zanyi", da haka suka canja zancen suka shiga na wajen aiki da bayan rabuwa, duk da Abuturrab Sam hankalinsa bae jikinsa. Bayan Batuul ta dawo daga makaranta gida ta dawo kamar yadda Aunty ta ce mata, da sallama ta shigo taga babu kowa a palo, kitchen ta shiga taga Aunty dasu Esther na aiki, k'arasawa tayi ta gaida Aunty tayiwa sauran sannu da aiki duk suma suka mata sannu da dawowa, jikinta ne yayi sanyi ganin yanayin da Aunty ta amsa mata gaisuwan, hawaye ne ya fara taruwa a idonta don ita a tunaninta tun maganan ďazu da safen nan ya ke b'atawa Aunty rai, maza tayi ta fita daga kitchen ďin dan tasan kuka zata fara gashi akwai masu aikinsu a gun, anjima zataje har ďaki ta sake bata hak'uri akan maganan duk da dai batasan mey ya fara kawo zancen aure ba, sama ta haura bayan ta fito daga kitchen ďin, hanyan ďakin k'annenta tabi, buďe k'ofan tayi ta shiga , ta ga dukkansu shirin Islamiyya sukeyi, wasu na saka uniform wasu sun gama, shiga tayi ta samu waje ta zauna daga ďaya daga cikin gadajen ďakin, ita da kanta batasan mey ya shigo da ita ba, Khalil yace "Yaa Batuul wannan takwarar taki tazo", ya faďa yana b'ata rai, Mus'ab ne yayi maza ya karb'e maganan tareda zumb'uro baki yace, "mtsew ni Allah kullum bana son zuwanta", hararanshi Batuul tayi tace "bana son rashin hankali, Mamar Baba cefa kake cewa bakason zuwanta, ita da gidan ďanta", Ahmad dake fesa turarene yace "ehh mana ai gaskiya suka faďa, abu duk randa tazo sai tasa ran Aunty ya b'aci, ni bana ganin amfanin zuwan nata, gara mu mu rik'a zuwa wajen nata mu kaďai,ni da tace bata son Abuja ma daďi naji, kuma fa kamar sunanki naji tana k'ira tana ta faďa, ai Aunty ce tace mu hau sama shiyasa banji mey suka faďa ba", tsawa Batuul tayi musu tace "bafa na son iskanci, waye yace muku ita take b'atawa Aunty rai, wato dukkanku gulma kuke koya ko", Sa'eed da dama tun can shi bamai magana bane yace musu "ku shirya mu tafi dan Allah, its getting late", ya ďauki wayanshi kan mirror ďinsu ya saka a aljihu ya fita, Su Yusra ne suka shigo ďakin su sun gama shiryawa sukace Yaa Ahmad mun gama shiryawa fa, inji Aunty mu k'ira ka mu tafi kar muyi latti, dukkansu fita sukayi daga ďakin bayan sun gama shiryawa sukayi mata sai sun dawo, jiki a sanyaye tace "okay sai kun dawo, kuyi karatu sosai kunji ko, in kun dawo zan baku chocolate", ta faďawa su Mahir da ďan dariyan yakenta, suna fita ta tashi itama tabi bayansu tayi hanyan ďakin da tasan zata tarar da kakarta da k'annenta ke cewa tazo, tasan duk gaskiya suke faďi, duk yadda akayi ma itace tasa ran Aunty b'aci, batasan meyesa bata sonta ba, tunda tasanta, tasan kakarta bata tab'a son Aunty ba duk da kyautatawan da Aunty keyi mata dan Aunty tasha yiwa Yayya abun kirki tun suna Maiduguri harda suka dawo Abuja ma kuma ba tareda sanin Baba ba, amma bata tab'a appreciating ba, zuwanta bakin k'ofar ďakin ne yasa ta kawar da tunanin da take ta murďa k'ofan ďakin. 💖💝BATUUL💖💝 37 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Daga gaban gadon Abdallah ya tsaya a tunaninsa Abuturrab xae basu waje sae ya ga otherwise, don kujera gogan ya ja yyi xaman sa yana facing dinsu, Abubakar na ganin hka ya xauna gefenta ya shiga mata magana murya can k'asa da damuwa, Batuul ta k'asa ďago kai ta kalleshi, sake matsowa yayi kusa da ita yace "Habibty tok to me mana, mey doctor yace na damunki", a hankali kamar bata son aji mey take faďi tana wasa da fingers dinta tace "nima ban sani ba, but i think doctor ya faďawa su Aunty, ni ban sani ba", ta k'arasa maganan tare da ďago kanta, ido hudu suka yi da Abutturab dake kallonta ko kiftawa bae yi, ya watsa mata wani irin kallon da ya sata saurin sadda kai, haka Abdallah yaci gaba da yi mata tambayoyi da yi mata sannu da damuwa, bata cewa komai daga "um", sai "um um", banging k'ofa suka ji suka juya, Batuul ta sauke ajiyar xuciya ganin shi ne ya fita, juyowa Abdallah yayi yace "Habibty who is he? your uncle", girgiza kai tayi tace mishi "brother ďin Farida ne", juyawa yayi ya sake kallon k'ofan sannan ya mik'e tsaye yace " Shknn Habibty i will b going, Mum na mota tana jirana get well soon, i will b back tomorrow in'sha Allah", yayi mata wani lallausan murmushi da itama maida mishi, daga haka ya fita yana waigen ta, a bakin k'ofa ya tarar da Abutturab na waya, tsayawa yayi ya gama wayan su yi sallama, ganin ya kusa minti biyar tsaye kuma ya ki k'are wayar yasa ya ďaga mishi hannu ya wuce, Abuturrab na ganin ya wuce ya katse wayan ya tura k'ofar ďakin, hawayen dake idonta take gogewa da tissue, tsayawa yayi yana kallonta daga bakin k'ofa, snn ya shigi tare da tura k'ofan ya rufr, jin k'aran k'ofan ne ya sata ďagowa da sauri, duk da rashin k'arfin jikinta hkn bai hanata mik'ewa cikin sauri tayi hanyan toilet ba, da gudu taje zata buďe k'ofan, taji ya fixgota, tsayawa tayi a wajen ta kasa motsi gabanta na faduwa, ya juyo da ita yana kallon yadda ta rintse ido hawaye na zubowa, fuskanta ya tsura ma ido da ďan k'aramin lips ďinta da ya koma ja, hannunshi ya ďaura kan kafaďunta ya matso da ita gabanshi yana kallonta da kyau yace "waye shi?" Kin cewa komae tayi har lkcn idonta a runtse, ya daga kafada yace "As if i care, kina jina dama Aunty na shigowa ki ce mata kin warke a maidaki gida kuma ke kina da wanda kike so, nasan wannan da yazo ya saki gaba yana miki surutu kmr radio saurayinki ne, toh dama kice musu shi kikeso kuma keh shi zaki aura, is dat clear?", sai da taji yayi shiru har lokacin tana hawaye ta buďe ido a hnkli tace "kai mey zai hana ka faďa musu, kaima ai kasan su kuma zaka iya samun su ka faďa musu kace kana da matarka basai an sani aurenka ba dan ni bbu abinda xanyi da mai mata, sabon jini dama ai sai sabo, mey ma zanyi da......", ganin yadda ya zuba mata lumsassun idanunshi yasa ta maida sauran maganan tana gogewa hawayen dake fuskanta, bin fuskanta yayi da kallo har idonshi ya sauk'a kan k'irjinta dake ta heaving, dariya abun ya bashi amma ya dake, yasan duk maganan da tayi a tsorace take, saketa yayi yana mata wani irin kallo yace "Really?, Fine then, zamu haďu ne tun da bakiji abinda na faďa miki ba, ki yadda ayi auren, xagi gane mai mata kuma tsohon jini kika aura yarinya", yana kaiwa nan ya juya ya fita daga ďakin, a nan wajen ta tsuguna ta sa kuka kamar wacce aka aikowa lbrn mutuwa, a nan Aunty ta shigo ta sameta, da gudu Aunty tazo ta ďagata tana tambayanta mey ya sameta, kasa magana tayi sai kukan da take tayi, Anty ta maida ta kan gado ta rungumeta hankali tashe tana lallashin ta, a nan tayi bacci jikin Aunty. 11 o'clock bayan doctor ya dubata yayi discharging ďinsu akan zai na zuwa har gida yayi mata alluranta da suka rage sannan yace a guji duk wani abu da zai rik'a b'ata mata rai kuma kar a rik'a faďa mata maganan da bata expecting har ya rik'a shocking ďinta tana zama unconscious, Baba ne yayi magana yace zasu kiyaye, da haka suka yiwa doctor sallama, suna komawa gida tace ita baza taje ďakinta ba a ďakin Aunty zata zauna, wanka tayi bayan ta shiga ďakin sannan ta kwanta, ba ita ta tashi ba sai k'arfe biyu, tayi alwala ta tada Sallah, tana idarwa Aunty ta shigo rik'e da tray a hannunta, ajiyewa tayi ta zubawa Batuul abinci sannan tace mata ta sauk'o taci, da kyar taci kaďan tace ta koshi, Da yamma wajen k'arfe biyar tana zaune tana kallon E.tv Aunty na haďa kayan Aabid Baba ya shigo ďakin, kan gadon da Batuul ke zaune ya zauna, tashi tayi zata sauk'a ta gaisheshi yace mata "Yaanyi" (Mamata), ďagowa tayi ta kalleshi da idonta da ya fara kawo ruwa, hannu yasa ya goge mata hawayen ya matso da ita jikinshi ya fara mata magana kamar haka "Ya jikin ki Batuul", jiki a sanyaye ta amsa mishi da "Alhamdulillah Baa, yayi sauk'i, na warke yanxu", yace "Masha Allah, har yanzu kinason zuwa Uk kiyi karatun?, ya tambayeta yana kallonta, ďagowa tayi ta dubeshi dan ta tabbatar da abinda taji yana faďa mata, ganin dagaske yake da sauri ta shiga gyaďa kai ta daďa rungume shi, tasan dama babu wani aure da za ayi mata kawai Yayyace ta faďa, ce mishi tayi "ehh Baa inaso" murmushi ďauke fuskanta, murmushin yayi shima yana shafa kanta yace "toh zan samo miki admission sai kije kiyi karatunki kinji ko, ai zakiyi karatu sosai ko?", kanta ta gyaďa har lkcn murmushi shimfiďe fuskanta har yafi nada, cewa tayi "Baba toh yaushe ne za ayi, ko sai na gama semester ďinnan sai inyi transfer", ta tambayeshi tana jiran jin mey zaice, Aunty dake aikinta tana jinsu ta saki dariyan takaici dan tasan so kawai Baba yake ya shawo kan Batuul dan yasan tana son karatu sosai, zata iya hak'ura da komai dan tayi achieving dream ďinta, Babane yace "very soon Mamata, amma kinsan mey nakeso dake", kai ta girgiza mishi yace "yawwa, kinga dama bana son zaman hostel, ko", nanma kai ta gyaďa, yace "toh kinga sai kiyi zamanki tareda Yayanki, nasan sosai zai kula dake", kanta ne yaďaure ta fara tunanin wane Yayan kuma, ce mata yayi "nasan tunanin wane yayen kike, Abutturab nake nufi", wara ido tayi ta kalli Baba tana girgiza kai tace "Baa toh zan zauna inyi a gida na fasa wllh, bana son zuwa," hawaye cike idonta ta kare maganar "k'ara janyo ta yayi jikinshi ya goge mata hawayen dake zuba a idonta yace "ki kwantar da hankalinki kinji Batuul, nasan anytime you will be proud of whatever decision i made, nasan Aliyu tun yana k'arami, nasan abunda zai iya da wanda bazai iya ba, ki kwantar da hankalinki kinji, kuma auren da Yayya ta faďa miki gaskiya ne", sosai ta shiga kuka harda sheshshek'a" muryarta na rawa tace "Baba nifa yarinya ce, just last month na cika 18, kayi hak'uri in na girma sai kayi min ko da waye ma kaji Baa", dariya maganan nata ya bashi yace "Batuul akwai Babba ne da k'arami a bautar ubangiji, babu, toh kinga ina laifin tun kina k'arama ki fara bautawa ubangijinki, kinga ladanki nema zai k'aru, ga kuma ladan da zaki samu na yi mana biyayya, ko ba kya so", ya tambayeta yana kallon fuskanta dake ta ambaliyan hawaye, kasa cewa komai tayi, ci gaba yayi da mata magana yace "toh mamata y dont you start it early and be rewarded abundantly, tunda at any point zakiyishi its better you do it now, and am assuring you Abu will b d best husband we will ever recommend for you, Nida Babanshi have been good friends for over 30yrs, har gida yazo ya sameni ya nemawa Aliyu aurenki, duk mutumin da yaso jininka har yaso haďa zuriya dakai yafi k'arfin wulak'anci, kinga ba daďi ince musu a'a, sosai yake ganina da mutunci, friendship ďinmu da muka gina based on trust yafi k'arfin ya nemi abu a wajena in hanashi", jikinta ne yayi sanyi sosai, ďagota yayi yana kallon fuskanta yace "Ko in koma ince musu kince bakya so", a hankali ta girgiza kanta alamar a'a, yace "yawwa Mamana Allah ya miki albarka, yanxu ki share hawayenki ki rok'i Allah ya tabbatar miki da duk alherin dake cikin bikin nan", haka ya dinga bata baki yana kwantar mata da hankali har yasa Batuul ta hak'ura, sai da aka k'ira magrib tukunna ya fita daga ďakin ya tafi yin Sallah. Washegari misalin goma na safe Abuturrab na kwance falo kan 3sitter abun duniya ya taru yyi masa yawa ganin ynda Ammah ta dage sae Shirye shiryen aurensa take ba ji ba gani, Ammah ce ta shigo falon ya mike xaune ganinta, da fada ta fara magana tace "anya kuwa Abuturrab kana son gamawa da mu lfya, tun jiya ina bin ka ka je gida ka duba yarinya an sallamesu ka ki xuwa?" Sakkowa k'asa yyi da sauri yace "Don Allah kiyi hkuri Ammah, ynxu nake son shiryawa in tafi wllh" bae jira cewarta ba ya mike ya nufi stairs, cikin mintunan da basu wuce goma ba ya sakko sanye da kananun kaya yana rike da makullin mota, cikin falon ya karasa yana kallon Ammah yace "Xan tafi Ammah" ta d'an sake fuska tace "Toh Allah ya tsare, kuma saura ka je masu empty handed, don nasan ba kai ya isheka ba" murmushin karfin hali yyi ya fita daga falon, parkin space ya nufa ya dauki motar da xae dauka ya bar gidan rae ba ddi. A waje ya bar motarsa ya fito ya shiga gidan, har xae danna bell ya fasa ya murda kofar a hnkli ya ji sa a bude, turawa yyi ya shiga falon da sallama, bbu kowa falon sae kamshi me ddi dake tashi da sanyin Ac, da alama duk yaran gidan sun tafi makaranta, ya karasa cikin falon ya xauna kan kujera, motsin da yake ji a kitchen ya sa shi sanin da mutum, ba a dau lkci ba ta fito rike da bowl din fruit salad da alamar lkcn ta hada ganin ynda taje jujjuya shi, sanye take da d'an mini skirt da top, ta bar gashinta in a messy bun s, cak ta tsaya tana kallonsa gabanta yyi mugun faduwa, shima kallonta yake daga sama xuwa k'asa, mikewa ta ga yyi, bata tsaya wani tunani ba ta nufi sama da gudu, yyi kwafa ya koma ya xauna, ya kusa awa daya xaune falon masu aikin gidan sae kai komansu sake bae ce su kira masa kowa ba, Anty ce ta sakko don shiga kitchen ta daura girkin rana da masu aiki ganin sha biyu ya kusa, da mamaki take kallonsa tace "A'a Abuturrab, yaushe ka xo" ya sunkuyar da kai yace "Ban jima ba Anty, ina yini" tace "Lfya lau, maimakon ka aika su fa'ixa su kira mu" murmushi kawae yyi bae ce komae ba, Anty ta nufi kitchen fa'ixa na biye da ita a baya, sae da suka shiga kitchen din snn tace "Tafi ki kira Batuul" juyawa tayi ta fita daga kitchen din. Batuul na kwance dakin Anty sae dae ban da faduwa bbu abinda xuciyarta ke yi, da ta tuna maganganun baba sae ta ji hawaye ya sakko mata, ynxu shknn hka tana ji tana gani xa a aura mata Ya Abuu, fa'ixa ce tayi knocking, ta share hawayen fuskarta tayi mata ixinin shigowa, fa'ixa ta ba ta sakon Anty snn ta fita, mikewa xaune tayi jiki a sanyaye. 💖💝BATUUL💖💝 38 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Jiki a sanyaye ta mik'e ta fito daga ďakin ta sakko downstairs, ganinshi zaune a palo yasa ta jin daďin kimonon da ta ďaura kan kayan dake jikinta, ďauke kanta tayi kamar bata ganshi ba tayi hanyan kitchen, da ido ya bita har ta shige tukunna ya ďauke idonshi daga wajen, tana shiga tace "Na'am Aunty, gani", tray da aka cika da snacks iri iri sai drinks da ruwa Aunty ta nuna mata tace mata "ďauki ki kaiwa Abuu", da sauri ta ďago zuciyanta sai faďuwa yake tana kallon Aunty dake ta aikinta tace "Aunty ni kuma", ba tareda da ta juyo ta kalleta ba tace "ehhh ďauki ki kai mishi tun ďazu yake zaune ban sani ba kuma babu wanda ya faďa min", zuciyanta duk babu daďi har idonta ya fara hawaye ta matsa gaban Island ďin ta kinkimi trayn tayi waje, tunda ta fito yake kallonta har ta iso palon, ďan nesa dashi ta ajiye mishi trayn fuskarta daure ta juya tayi tafiyarta, murmushi yyi ya ci gaba da kallon tv da yake, kitchen ďin ta koma ta tsaya bata cewa kowa komai ba ta hau kan deep freezer ta zauna, juyowa Aunty tayi zata cewa Janet ta mik'o mata abu a Fridge taga Batuul zaune kan Fridge, kallonta Aunty ta tsaya yi da mamaki tace "Batuul meye hakan, mey kika dawo yi kika barshi shi kaďai a palon", kanta ta girgiza tana kallon Aunty tace "Aunty toh ai abinci zai ci kuma ma nifa.....", bata k'arasa ba ganin kallon da Aunty keyi mata ta sauko tace "kiyi hak'uri zanje", ta juya jiki a sanyaye ta fita daga kitchen din, da k'yar take ďaga k'afanta har ta isa palon, yana nan inda ta barshi yana kallonn Discovery channel, sau ďaya ya ďaga kai ya kalleta ta sadda kai k'asa tana ta fidgeting yatsunta, ya ďauke kai yaci gaba da kallonshi har ta k'araso ta zauna can nesa dashi, lokaci lokaci yake satan kallonta ita ma hka, sai da programm ďin ya k'are tukunna ya dubeta, ta sadda kai k'asa tana wasa da yatsunta, sauk'a yayi daga kujeran ya janyo trayn yana kallonta murya can kasa yace "Baki faďa musu sak'ona ba knn har ynxu koh?" Kin cewa komae tayi kuma bata d'ago kanta ba, kallonta ya tsaya yi, ta dan sata kallonsa jin shirun yyi yawa, suka hada ido ta dauke kai da sauri, kallon hanyar kitchen yyi kafin yyi kwafa ya dauki glass cup ya bude lemon kwalin dake kan trayn da ta ajiye masa ya tsiyaya ya mayar ya rufe, ba tare da ya kalleta ba yana girgixa kai cikin sanyayyan muryarsa yace "Ni tausayin rayuwar ki da nake yasa ki ka ga ina maki kashedin kar ki yrda su makala min ke, yhu are too young to start facing challenges or rather I shud put it as problem, ni ina da matata kuma muna son junan mu like! har kika kuskura aka yi auren nn u will only end up shattering ur life, it's still not late for yhu...." Bata Bari ya kai karshe ba ta xamo kasa da sauri hawaye na bin kuncinta xuciyarta na tafasa tace "Kai wae me xae hanaka yin magana sae ni? Naga kai ma xaka iya gaya masu baka son auren ae koh?" Yyi wani murmushin da ta kasa fassara nufin shi yace "Ni baxan iya yi ma iyayena musu ba, ina ganin darajan su shi yasa kika ga har ynxu ban musa masu ba" wani mugun kallo ta shiga yi masa har lkcn tana hawaye ssae tace "Kai ne kasan darajar iyaye ni ban sani ba koh, toh kmr ynda baxa ka iya masu musu ba nima baxan iya ba, sae dae idan an makala maka ni ku kashe ni kai da matarka" tana kai wa nn ta mike tana kuka ssae ta haura sama da gudu, bin ta da kallo yyi yana murmushi, kafin ya fara shan drink din hannunsa, cake kawae ya dan ci ya mike yace ma Janet da ta fito daga kitchen ta ce ma Anty xae koma, fitowa Anty tayi bayan Janet ta bata sakon shi, tayi Mamakin rashin ganin Batuul a falon sae dae bata nuna ba tace "Har xaka tafi Abuturrab" Yace "Eh Anty, it's almost time for sallat ne" tace "Toh shknn, Allah ya tsare" fita yyi daga falon, ita kuma ta nufi sama don xuwa jin dalilin kin jin maganarta da Batuul tayi rai a bace, dakinta ta sameta kwance tana kuka har da sheshsheka, Anty ta tsaya daga bakin kofa tana kallonta tace "Meye hkn Batuul?" Mikewa xaune tayi da sauri ta kuma fashewa da kuka tace "Don Allah Anty ku rufa min asiri a fasa auren nn wllh bana son ya Abuu shi ma baya sona ..." Harara Anty ta galla mata tace "Wnn kuma sae ki jira idan babanku ya dawo ki sanar da shi" tana kai wa nn ga juya ta fice daga dakin. Aunty na shigowa daki taji wayanta na ringing, kamin tayi picking taga har ya katse, ďauka tayi ta duba taga wa ya k'ira, missed calls biyu ta gani duk Ammah ce ta k'ira, zama tayi daga bakin gado zata k'ira kenan wayan ya fara ringing, Ammah ďince ke k'ira, ďagawa tayi tare da yi mata sallama, bayan sun gaisa Ammah ke tambayan Aunty "Maryam ya shirye shirye", murmushi Aunty tace "Alhamdulillah Ammah", ita har yanxu mamaki take na zata aurar da Batuul nan da y'an kwanaki, Ammah ce ta katse mata tunani da cewa "dama kayan Batuul ne nakeso a tambayar min ita inda akwai abunda take buk'ata dan Aliyu ya tambayeta tace ita bata son komai, toh ni ba yarda nayi dashi ba shine nakeso a bincika min sannan gyaran jiki zan turo a kawota gida sai ayi mata duk abinda ya kamata", shiru Aunty tayi har sai da Ammah ta kai aya tukunna tayi ajiyan zuciya tace "Toh Ammah zan tambaya miki ita, sai dai gyaran kamar zai fi tayi a gida nake gani ba sai taje can ďinba ai hidima zaiyi yawa, har nayi magana mai gyara gobe zata zo daga Ndjamena", cewa Amma tayi "toh shikenan hakanma yayi", da haka suka gama wayan, zaman tunani Aunty ta yi dan ita bata da wani shiri ma da zatayi na bikin, ko y'an uwanta ma bata faďa musu, waya ta sake ďauka tana k'iransu ďaya bayan ďaya duk ta sanar dasu auren Batuul, sai mamaki sukeyi ganin abun yazo da wuri. Bayan Abuturrab ya koma gida da daddare Abui ya k'irashi har siďe ďinshi, daga palo ya tarar dashi kishigiďe yana kallon News, da sallama ya shiga ya zauna k'asa sannan ya gaidashi, gyaran murya yayi sannan ya k'ira sunanshi, "Aliyu", a hankali ya ďago dan gaba daya jinshi yayi wani iri dan Abui baya k'iran shi da sunanshi, yace "Aliyu na nema maka auren Batuul bawai dan na isa inyi maka abinda nakeso ba, bawai kuma dan bana sonka ba sai dan inason ci gabanka, yarinyar nan amana zan baka, ba iyayenta kaďai bane suka baka amanarta, har ni amananta zan baka, ka rik'eta kamar yadda zata zauna a gun iyayenta, in ka cuceta toh ka cuci amanar mu, yarinyace ita sannan mace, she is so naive and weak sai kayi hak'uri da ita, sannan bawai dan an haďaka da ita ka fifita matarka da kakeso kanta ba, kayi k'ok'arin adalci tsakaninsu sai kaga Allah yasa komai yazo maka da sauk'i, Aliyu ban yadda da saki ko yaji a tsarin zaman aurenka inba maishi ya sab'awa shari'a ba da bama fatan faruwanshi, ka kula da ita kamar yadda zaka kula da Farida, bana son ka zama silar rugujewar abotan da yake kulle tun kamin zuwanka duniya, kaji tsoron Allah a duk inda ka tsinci kanka, In sha Allah aurenka da Batuul alheri ne", k'asa ďagowa yayi dan wani nauyi kanshi yayi mishi, ji yayi kamar abu aka ďaura mishi a kan, Abui ne ya sake k'iran sunanshi, da k'yar ya ďago ya iya cewa "Na'am Abui", wani chest box ya ďauko daga gefenshi ya mik'o mishi yace "ga wannan shine Sadakin Fatima, shi za a mik'awa Waliyyin Batuul as Sadaki, sannan a can zataci gaba da karatunta, kayi supporting ďinta in every way to the best of your ability tunda tana karatunta muka nema maka aurenta, Allah yayi muku albarka", wasu makullai guda biyu ya mika masa yace "wannan na motane bayan an ďaura muku aure sai ka bata, wannan kuma gidana na farko dake Mississipi street na bata shi halal", da sauri ya ďago ya kalli Abui da mamaki, shi ya rasa gane wane irin so suke yiwa Batuul dashi da Ammah, ko aurenshi na fari basuyi wannan abin haka ba, da k'yar ya iya buďe baki yace "In sha Allah Abui, zanyi yanda kace,", yace "yawwa, ka gama arranging gidan da zata zauna na nan da can ko kuma haďasu zakayi waje ďaya", kai ya gyaďa tareda cewa "Yeah a can dai tare zasu zauna amma a nan Asokoro nacewa Mum zata zauna", Abui yace hakan ma yayi kyau, Nasa Mustapha da Sadiq suyi duk necessary arrangement ďin ďaurin auren, Allah ya tabbatar muku da alheri ya taya ka riko, Allah yayi muku albarka", jiki a sanyaye ya mik'e yayi wa Abui sallama ya fita. Har gida Abui yasa sukaje shida Baba da Uncle ďin Abutturab da yaji lbrn Abdallah ke neman sonta suka samu iyayen Abdallah suka bashi hak'uri, Basu nuna komai ba suka ce dama wani ai baya auren matar wani, dama can Allah yayi ba matarsa bace, suka musu add'uan Allah ya bawa Batuul da Abutturab zaman lafiya, kuma sukace zasu bawa Abdallah hak'uri su bashi baki, da haka sukayi musu godiya suka tafi. Ranar asabar k'arfe goma aka ďaura auren Aliyu Ahmad Kyaree da Fatima Kashim Goni akan sadaki sisin gwal 60, a k'ofar gidan kakanta dake Goni Mukhtar street a Maiduguri, tana kwance ďakin Aunty babu abunda takeyi sai rawar sanyi, Yayya ce ta shigo tana cewa "Keh Batuul fito ai an ďaura, tashi daga kan gadon nan tun jiya kike kai, maza fito a ida miki kitson da kike ta gudu tun jiya", kan gado ta hau ta yaye mata bargon, hawaye ta gani idonta, sai rawar sanyi take, hannu tasa zata ďagota taji jikinta zafi, ba shiri ta janye hannunta, Farida ce ta turo k'ofan ta shigo janye da wani akwati, ganin Yayya kan gadon yasa ta tambayan mey ya faru, da gudu ta k'araso ganin yadda Batuul ďin take yasa ta fita a guje taje ta k'ira Aunty, a rikice Aunty ta shigo, da kanta tayi k'ok'arin ďago Batuul sannan ta nemi key ta mik'awa Farida tace suje dan su Ahmad na Maiduguri ďaurin aure kuma batasan ma ina driver ďinsu yake ba, mutanen dake gidan ne suka tashi ganin yanayin jikin Batuul suna tambayan mey ya faru, babu wanda ya iya basu amsa dan Yayya da kanta ma kuka take tana k'iran sunan Batuul ďin, ikon Allah ne kawai ya kaisu asibitin dan gaba ďayanta Faridan ta rikice, suna isa asibitin aka taso aka karb'i Batuul akayi emergency da ita, Yayya duk ta ishi mutane da kuka wiwi a asibitin, Anty kam xama tayi reception ta jinginar da kanta jikin kujera, da ganinta kasan hankalinta a tashe yake, farida ce tayi karfin halin kiransu Ammah ta sanar da su halin da ake ciki, kan kace me sae ga Ammah da Anty Amnah sun taho asibitin, sae bayan kusan minti talatin likita da nurse uku suka fito daga emergency ward, likitan ya bukaci Anty ta bi sa office sanin da yyi ita ce Mahaifiyar Batuul, jiki a sanyaye Anty ta shiga office din likitan, likitan ya dauki farin gilashinsa ya sa yana kallonta yace "Gskya Madam 'yar ki na cikin wani yanayi, a daina daga mata hankali don Allah, dab take da kamuwa da hawan jini" hawaye cike idon Anty tace "Ya jikin nata Dr?" Yace "Da sauki, ta samu bacci ynxu, sae dae meyasa baxa ku tuhumeta ku ji damuwar ta ba Hajiya?" Anty ta share hawayen idonta tace "Xa muyi hkn Dr, mun gode," yace "Gud!" Tace "xan iya shiga in ganta Dr?" Yace "Xa ki iya, amma kada a tada ta" mikewa tayi ta kuma yi masa gdya ta fita, bacci me nauyi ta tarar Batuul na yi an sa mata drip, su Ammah ma duk suka shiga suka dubata, ganin bacci take duk hankalinsu ya kwanta, sae a snn suka iya barin asibitin, Farida ta maida Yayya ma gida don sae gyangyadi take a asibitin, Anty bata kira baba ta sanar da shi halin da ake ciki ba sanin suna Maiduguri har lkcn, Karfe sha biyu kiransa ya shigo wayarta ta daga, nn yake gaya mata sun sauka Abuja lfya, sae a snn ta sanar da shi halin da Batuul ke ciki, hankalinsa ya tashi ssae, ya sanar ma Abui daga airport suka nufo asibitin. Karfe daya saura Abuturrab ya shigo gida duk a gajiye ga damuwa da yyi masa yawa bae san ynda xae yi da Ajiddeh ba idan ta ji xancen auren nn, sa'arsa daya bbu wanda ya sani cikin 'yan uwanta, tun da aka daura auren gabansa ke faduwa ya ji kmr an daura masa abu me nauyi ne a kai, part din Abui ya nufa direct don Avoidin mutane dake cike gidan, ko minti biyar bae yi da kwanciya ba Ammah ta shigo, ya mike xaune ya gaisheta yace "Mun dawo Ammah" murmushi tayi ta xauna gefensa tace "Toh Allah ya taya ka riko babana, sae dae fa Batuul din na asibiti ya kamata ka je dubata ynxu duk da nasan yhu are tired" yace "Asibiti kuma Ammah, me ya sameta?" Ammah tace "Kai dae ka je ka dubata, Allah dae ya bata lfya" a hnkli yace "Toh," Ammah ta mike, yace "Ammah ki ce Sadeeq ya kawo min makullin mota" fridge ta nufa ta bude ta dauko chill yoghurt ta mika masa tace "Gashi ka sha Abuu, nasan baka ci komae ba yau" karba yyi yace "Nagode Ammah" ta juya ta fita tana cewa bari in dauko maka makullin, ajiye yoghurt din yyi don bae jin xae iya sha. Driving kawae yake amma gaba daya hankalinsa baya jikinsa, a hka ya iso asibitin, Ahmad ya hadu da a haraban asibitin, Ahmad ya gaishesa da ladabi snn ya kai sa har ward din da Batuul take, Wata Sistern Anty ce xaune ward din, don Anty ita ta koma gida sbda baki, har lkcn Batuul bacci take, Abuturrab ya gaida Anty Hafsat, ta amsa masa da fara'a tana tsokanansa don sun saba, murmushi kawae yake kansa a kasa, har dae ta tashi ta tace masa tana xuwa ta fita, Ahmad ta bi bayanta. Ya dde tsaye yana kallonta snn ya ja kujera ya xauna, ya kusa minti talatin xaune ya ga tana juye juye, ya kafa mata ido ko kiftawa bae yi, a raxane ta mike xaune ta bude ido tana kwala wa Anty kira tana kkrin sauka daga kan gadon, ya Mike da sauri ya riketa, hkn bae hanata ci gaba da kiran antyn da take ba tana kuka xata sauko, ko kadan bata lura da wanda ke rike da ita ba don idonta rufe yake, rungumeta yyi jikinsa, lkci daya ta daina fixge fixgen da take tayi lamo jikinsa tana sauke ajiyar xuciya, lumshe ido yyi yaki budewa. 💖💝BATUUL💖💝 39 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Sunfi minti biyar a haka, har lokacin idonshi lumshe, hannu ya sa yana kwantar da dogon gashin kanta da aka kitse rabi aka bar rabi, k'amshin turaren da ya cikata ne yasa ta tunanin inda tasan turaren, a hankali ta buďe ido tana k'ok'arin janyewa daga jikinshi, saketa yayi ya ďan matsa da baya, idonta cike da hawaye ta juya tana k'arewa ďakin da take kallo, ganin shi kaďai ne ďakin yasa ta matsa can k'arshen gadon ta fashe da wani matsanancin kuka, sosai take kuka tana k'iran Aunty, tsayawa yayi yana kallonta, can ya k'arasa inda take ya haďe rai yace "Wai kukan mey kike yi ma mutane hka, baki ga inda kike bane or did yhu want to worsen yhu condition, tunda na dawo nake sintirin asibiti, am even wondering anya ke ba sicker bace, da ko tawa ta sameni" ko kallonsa bata yi ba ta shiga kkrin sauk'a daga saman gadon zata fita daga ďakin tana kuka, yayi maza ya fixgota, baya tayi zata faďi yasa hannu ya taro ta ya maido ta k'irjinshi, ďago kanta yayi har lkcn tana kuka yace "Allah zan mareki in baki nutsu ba, mey ke damunki da zaki rik'a abu kamar yarinya, are yhu okay!" kai ta girgiza mishi ta ďago rinannun idanunta ta sauk'e kan kyakyawan fuskanshi cikin sheshek'an kuka tace "Yaa Abuu wai an ďaura ko, tunda baka sona bana son ka dan Allah ka taimakamin kacewa su Baba su barni a nan inyi zamana, in kayimin haka nima Zan yadda da duk wani condition ďinka ko na meye ne, ko kuma zanyi zamana ba tareda da kowa ya sani ba sai ka saken......", bai bari ta k'arasa maganan ba ya k'ara k'arfin rik'on da yayi mata ya daka mata tsawa yana mata mugun kallo yace "Da alama baki da hankali, sae ynxu kika san da hka, C'mon wuce kije ki kwanta", ssae ta tsorata ganin yanayinshi, tana hawaye ta juya tayi kan gadon, sai da ta koma ta kwanta tukunna ya juya ya danna bell ďin k'iran doctor. A gida can Ammah ta haďa kayan lefen Batuul Babban mota guda, su Aunty Amna da sauran Aunties ďinsu matane suka kai, su bakwai suka haďu sukaje, da mutunci aka karb'esu can gidansu Batuul ďin, abinci kala kala aka shiga serving ďinsu, kowa ya ya6a ganin yawa da kyan kayan da Batuul ta samu, Basuci abubuwan da aka kawo musun ba sai juye musu Aunty tasa akayi, tukuicin 1million ta bawa Sisters ďin Baba su basu, k'in karb'a sukayi har sai da Yayya ta saka baki tukunna suka karb'a sukayi godiya suka koma. A can asibiti kuwa nurse ce ta shigo da saurinta jin bell ďin yayi ringing, ganinshi tayi tsaye daga gefen gadon ya nuna mata gadon yace "call her doctor immediately" da sauri ta fita suka shigo tareda da doctor da stethoscope rataye wuyanshi da wani ďan board haka a hannunshi, nurse ďin kuma rik'e da wani k'aramin silver tray da allura akai, yana zuwa ya saka stethoscope ďinnan a kunnenshi yana ďan gwada gudun pulse ďinta, alama yayiwa nurse ďin ta mik'o mishi alluran zai yi mata , ba shiri ta mik'e tana kuka, sosai ta bawa likitan wahala da Aunty Hafsat dake k'ok'arin rik'eta itama, yana tsaye jikin bango yana ganin shure shuren da take tayi, ganin taqi tsayawa ne yasa shi matsowa gaban gadon ba tare da yyi wani tunani ba ya kwanto da ita jikinshi, cikin raďa yace mata "I will slap you idan baki tsaya kin dena bawa mutane wahala ba", lamo tayi jikinshi gabanta na faduwa, har sai sai da aka tsikara mata alluran ta daďa k'ank'ameshi ssae tana hawaye, bai ďagata daga jikinshi ba bayan likitan yayi mata allura itama dae kasa tashi tayi don duk bata da karfi, a nan jikin nashi bacci ya ďauketa ya shimfiďar da ita ya dubi Aunty Hafsat dake ta kallonsu da sha'awa don sae ka rantse masoya ne, yace zaije gida ya dawo. Sai yamma Aunty tazo tare da Baba, a kan gado suka tarar da ita tana bacci, daga bakin gadon Baba ya tsaya yana kallonta, sosai ya tausaya mata ganin yadda ta rame ta k'ara haske, hannu ya ďaura kan goshinta ya tottofa mata addu'a, snn ya ja kujera ya zauna bayan ya gama ya kalli Aunty yace "Yaushe sukace zasu tafi da ita?", Aunty tace "D'azu dai da suka zo basu ce komai ba toh inaga sai gobe", Aunty Hafsat ce tace "Uncle a barta mana in ta warke sai su tafi da ita, amma yanxu ai bata jin daďi", sai da ya gama jin abinda Aunty Hafsat tace yace "A'ah Hafsat, in kuma yana da abin yi a can fa?, in dae xa a sallameta ko xuwa gobe kawae su tafi ta warke a can din", tashi yayi ya fita yacewa Aunty zai je wajen doctor ya tambayeshi yaushe za a sallametan, ita Aunty bata cewa komai sai ido da ta bishi da, tausayin Batuul sosai takeji a cikin ranta, Babane ya dawo yace musu gobe doctor yace za a sallameta, a nan ya tafi ya bar Aunty da Aunty Hafsat, yana fita Aunty ta dubi Aunty Hafsat tace "Hafsat wlhy tausayin Batuul nake, ban tab'a kawowa zatayi aure so soon ba, sannan kuma ma mai mata, Batuul yarinya ce amma sun k'asa fahimtar abinda nake nufi" Aunty Hafsat ta girgiza kai da damuwa tace "Yaa Maryam ko ni yanxu jimamin abin nakeyi, danma dai naga Aliyun nada hankali da nutsuwa sosai, ko ďazu shi ya taimaka akayi mata allura da k'yar", Aunty tace "dama nifa bata Aliyu nake ba, nafi kowa sanin Aliyu tunda rainona ne, matarshi nake jiyewa Batuul, familyn su basuda daďi akan kishiya, bare Batuul da take yarinya, bata ma san meye kishiyar ba", ajiyar Zuciya Aunty Hafsat tayi tace "Yaa Maryam addu'a kawai zamu tayata yi, itama a sata ta dage da yin addu'a, duk abunda zatayi ta kasance shine a bakinta, kuma ai can zata ci gaba da karatu ko?", kai Aunty ta gyaďa tace "Ehhh haka Babanta yace, har admission ďin wai ya nemata a can, yace gidan nasu ma da makarantar babu nisa, makarantar na Houghton street, gidan kuma na ST GEORGE'S, kinga da kanta ma ta rik'a zuwa", Aunty Hafsat tace "yawwa hakanma yafi kinga zata rage damuwa sosai in tana zuwa school, baza ma tana zaman gidan ba bare su ishi junansu har su samu misunderstanding, Allah dai ya basu zaman lafiya", Aunty tace "Amin ya Allah, sosai zansa ana yiwa Batuul addu'a , duk sati a rik'a mata sauk'an Qur'ani", Aunty Hafsat tace "Allah ya dai ya rufa asiri Yaa Maryam, Allah ya karemu daga sharrin duk mugun abu naji ko na gani", daga nan suka ci gaba da hirarrakinsu. Sai dare Abutturab ya dawo tare da Ammah, Ammah ce ta fara shigowa yana biye bayanta, Batuul na cin abinci lokacin Aunty Hafsat na kishingiďe kan sofa dake can angle, tana ganinsu ta mik'e ta zauna suka gaggaisa, Ammah tana tambayanta ya mai jiki, Kan gadon ta zauna ta jawo Batuul jikinta tace "Bitti ya jiki, kina samun sauk'i dai ko", kai Batuul ta gyaďa dan wani kunyan Ammah takeji yau, Abutturab dake tsaye Ammah ta kalla tace "kai baka yi mata ya jikine ka tsaya kana kallonmu", kallon Batuul yayi a takaice yace "ya jiki" hararanshi tayi ta ďauke kanta cike da jin haushin alluran da ya rik'eta yasa akayi mata daxu, mamakin hararanshi da tayi yayi ya girgixa kai ya ďauke idonshi daga kanta, sunfi minti talatin wajen Ammah sai nan nan take da Batuul ta rasa ina zata sa Batuul ďin, shi dai kujera yaja ya zauna lokaci lokaci yake ďaga kai yana kallonsu, suna haďa ido take hararanshi, daga baya dariya ma abun ya fara bashi, mik'ewa Ammah tayi tace "Bitti zamu tafi kinji, Allah ya k'ara lafiya, Aunty Hafsat ta fita rakata shi ya tsaya daga baya, kallonta ya tsaya yi amma taqi ďagowa ta kalleshi, gabanta ya matso yace "kin gama harare hararen mara kunya, irin na fara sake maki fuska a tunanin ki ko, Gud! yhu had beta stop decievin ur self coz am still the Abuturrab yhu knw!," bata ďago ba dan mugun bugawa zuciyanta yake, ya dago kanta yana mata mugun kallo yace "Baki ji na ne?" Kuka ta saki kmr jaririya tana kallonsa, ya koma baya da sauri yana kallonta da mamaki, ya buda manyan idonsa yace "Na maki wani abun ne? Daga magana?" Kin cewa komae tayi sae kukan da take, mamaki ya sa shi k'asa cewa komae, can ya sauke ajiyar xuciya ya runtse ido yana shafa kansa murya can kasa ba tare da ya shirya fadin hkn ba yace "ohkk srry!" Lkci daya ya bude ido jin abinda bakinsa ya furta, D'ago kai tayi tana kallonsa ya maka mata harara ya nufi kofa da sauri, ta bi sa da kallo har ya fita kafin ta tabe baki tana share hawayen fuskarta, lkci daya jikinta yyi sanyi qalau tunawa da tayi ynxu fa ita matar Abuturrab ce, tafiya fa xae yi da ita ya raba ta da iyayenta da 'yan uwanta ya kai ta garin da bata san kowa ba, ta fashe da matsanancin kuka ta fada kan gadon tana tausayin rayuwarta. Washegari tunda aka sallameta bayan taji ranan za a wuceta da ita take kuka kmr ranta xae fita, duk ta fita hayyacinta, k'arfe takwas aka zo ďaukanta, lokacin Aunty ta bata wani lace blue mai kyau da tsada ta saka, ta bata wani laffaya shi kuma Golden, ta saka mata costumes ďin gwal, Batuul dai babu abinda take sai kuka, duk da ba wani kwalliya tayi ba tayi kyau sosai, wajen Baba aka fara kai ta yayi mata Nasiha sosai, rungumeshi tayi sosai tana rusa kuka, da k'yar ta sakeshi, k'annenta ma kukan sukayi tayi ganinta tana kuka, Ahmad, Sa'eed da Khalil ne kawai basuyi kuka ba amma suma jikinsu yayi sanyi, Aunty kam kasa mata magana tayi dan ji takeyi itama zatayi kukan idan ta bude baki, kanta kawai ta shafa cikin sanyin tace "Allah ya miki albarka, ya kare ki a duk inda kike", daga nan ta juya tayi ďaki, Sistern Baba ce ta kai ta har mota, suka shishshiga convoy ďin motocin dake waje akayi gidan Ammah da ita. 💖💝BATUUL💖💝 40 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Suna isa bayan an shishiga dasu gidan Aunty Hafsat ta d'ago Batuul dake ta faman razga kuka, sauran Aunties ďin Aunty da suka taho tare suma suka fiffito daga motocin, Aunty Amnah ce ta fito ta tarbesu da fara'arta, babu abinda Batuul takeyi sai kuka kmr xata shide tana rungume jikin Aunty Hafsat, k'anshin turaren wutane kala kala ke tashi ta kowane angle ďin babban palon, ga wani sanyi dake bugasu, babu abinda matan palon suke sai guďa, sama akayi da Batuul zuwa ďakin Ammah, Farida na biye bayansu ta rasa farin ciki take taya Bestyn nata ko kuma bakin ciki take da auran Yayanta, A kan lallausan rug ďin dake ďakin Ammah Aunty Hafsat ta zaunar da ita, ďagota Aunty Amnah tayi ta maidata kan gadon tace "A ah baza ta zauna a k'asa ba", Aunty Hafsat dai batace komai ba sai murmushin da tayi, haka akayi ta shigowa gaida amarya amma fir taqi buďe fuskanta sai faman zubda hawayen da take, saida duk suka gama suka fita tukunna Ammah ta shigo ďakin, hannu tasa ta sake janyo gyalen yadda baza a gane ba, Ammah na k'arasowa ta zauna daga gefen Batuul, mayafin dake kan Batuul Ammah ta ďaga tana kallon fuskan Batuul da ke hawaye, "Masha Allah", abinda Ammah ta fara faďi kenan gani yadda Batuul tayi kyau sosai, matso da ita gefenta tayi tace "Bitti kukan har yanxu, toh kiyi hak'uri kinji, ai nanma gidane, karki damu kinji, ki kwantar da hankalinki", ita dai Batuul taki cewa komai sai hawayenta da ya daďu, mik'ewa Ammah tayi tasa Aunty Amna su kawo musu abinci tace tana zuwa itama ta fita. Yana kwance rigingine ďakin Massa idonshi lumshe kamar mai bacci, Massa ne ya shigo ďakin yana waya ganinshi kwance yasa ya katse wayan ya zauna daga arm ďin kujerar ya ďan tab'ashi, a hankali ya buďe idanunshi dake lumshe ya sauk'esu kan Massa yana jiran jin mey zaice, mik'ewa yayi ya zauna ganin Massa ya ki cewa komae yace "wai meye kake kallona haka ne, is this your first time seeing me", murmushi Massa yayi yace "ango irinka ne ni ban tab'a gani ba, yau za a kai maka amarya shine kazo ka kwanta min a ďaki, da ni nake ango yau ai da tun rana zan tafi, da kanku ma zaku kaini in na isheku", ďan tsaki Abutturab yaja zai koma ya kwanta Massa yasa hannu ya rik'oshi yace "Man what are you doing wai, tun ďazu kazo ka kwanta, kai ko marmarin ďauko amaryar taka ma bakayi, dukda nasan ba kai zaka ďaukota ba ai sai kaje ka dubata koh", wani irin kallo ya sakar mishi yace "ni ba sai ka tsaya yimin surutu ba pls, just tell me you need privacy, i should excuse you", ya koma ya kwanta, baki Massa ya buďe zai yi magana yaji wayanshi na ringing, tashi yayi yaje ya ďauko, ganin Ammah ke k'iran yasashi amsawa a risine, a nutse yace "Ammah Nda dubdo, ya gajiya", ta amsa mishi da "Lafiya Massa, kana tare da Abu ne", juyawa yayi yana kallon Abun da ya mik'e da sauri tun sanda yaji Massa ya ambaci Ammah, ce mata yayi "Ehh Ammah, gashi nan muna tare", tace mik'a mishi wayan", "Toh kawai yace ya isa inda Abutturab yake ya mik'a mishi wayan, ansa yayi yasa a kunnenshi a hankali yace "Ammah Nda dubdo", bata ansa gaisuwan da yayi mata ba tace "Shine har da kashe waya tsabar raini ko Abu, Yayi maka kyau ai, bakaje ka ďauko matarka ba dan ka nuna mana kai ka isa ko, toh Abui yasa anje an ďaukonta hkn kuma bae sa ka xo gaida wa enda suka kawo tan ba yayi maka kyau, kayi abunda kaga dama Abu", bai samu yace komai ba tana kaiwa nan ta katse k'iran, kanshi ya dafa tareda cewa "Shit not again, wlhy bana son Ammah na fushi dani akan yarinyar nan", wayanshi ya janyo dake gefenshi a kujera a sanyaye tareda da ďaukan key ya shiga neman layin Ammah, ringing yakeyi amma taqi ďagawa, mik'ewa yayi yacewa Massa da ya kafeshi da ido yace "Am going", bayanshi Massa yabi yace "Mu tafi tare", tare suka fita Abu na tuk'a motar, tunda suka shiga gidan matan dake cike falon suk'e tsokananshi, Farida ya gani na sauk'owa kan stairs, tsaidata yayi ya tambayeta "Ammah fa" ce mishi tayi "tana side ďin Abui", daga nan bai tsaya jin komai ba ya juya yayi side ďin Abui, Ammah kawai ya gani tana k'ok'arin rufe wani akwati, k'arasawa yayi har wajenta yace "Ammah kiyi hak'uri kinji, bansan kina nemana ba, wayan na silent ne, I was having a slight headache shine na tafi gun Massa in huta", ya k'arasa magana tareda da yi mata side hug, ji tayi baza ta iya ci gaba da yi mishi fushin ba, juyowa tayi itama ta kalleshi tace "Abu mesa kullum sai kasa ni yin magana", kai ya girgixa da sauri yace "In sha Allah Ammah bazan sake saki magana ba", tace "Allah yasa, kaje ku gaisa da y'an uwanta da sukazo tare da ita, wannan akwatunan ma nasune zansa a fidda musu inda motocin ke pake", yace "Toh" ya juya ya fita, a palo ya tarar dasu Aunty Hafsat har sun sauk'o k'asa, a nan ya gaggaisa dasu cikin jin kunya, Aunty Amna sai tsokanarshi take, shi dai baya cewa komai sai murmushi da yakeyi kanshi a k'asa, da haka sukayi sallama suka wuce, su Aunty Amna suka rakosu har wajen motocinsu, sukayi Godiya suka bar gidan. Su Aunty Hafsat na tafiya Farida ta shigo ďakin ta hau kan gadon da Batuul ke zaune, mayafin kan nata ta yaye, jikinta ne yayi sanyi ganin yadda Batuul ke hawaye babu k'ak'k'autawa, janyota tayi jikinta itama ta fara hawayen tace "Batuul you are making me emotional, kiyi hak'uri ki bar kukan nan haka dan Allah kinji, everything happens for a reason, it was destined to happen kuma In sha Allah its for d best, ni nasan ko ba komai Ammah will b there for you always kinji, as it is kuma, Yaa Abu is not that bad, just that baison raini and baya sakewa da mutane but bayan haka he is a very nice person at heart, nasan he will take care of you, kiyi hak'uri ki bar kukan nan kinj, kar ya sa miki ciwon kai, kinga Ammah ma in ta shigo taga har yanxu kina kukan nan baza taji daďi ba", ta gama maganan tana sharewa Batuul hawayen da yaqi ya dena zuba daga idanunta, da kyar Farida ta samu tasata tayi shiru, Ammah ce ta shigo ganin Batuul zaune a inda take bata motsa ba tace "Bitti baki tashi kin canja kaya ba tun ďazu, maza tashi shiga kiyi wanka, ai kayan nan sun miki nauyi", kanta a k'asa dan wani kunyan Ammah takeji kwana biyun nan, Ammah ta dubi Farida tace "taimaka mata ta shiga tayi wanka", ita kuma Ammah ta juya wardrobe ďinta ta cirowa Batuul kayan baccin da zata saka, tana ajiyewa ta fita. Sai wajen k'arfe goma ya shigo cikin gidan, kai tsaye ďakin Ammah ya nufa, sallama yyi can kasa ya tura kofar dakin ya shiga kansa a kasa, Ammah na waya daga xaune gefen gado, Batuul kuma na xaune kasan lallausan rug din dakin ita da farida da ta sata gaba ta ci abinci, gabanta ya fadi ba kadan ba ganinsa tayi saurin d'aga mayafin dake kan kafadarta ta mayar kanta ta rufe har fuskarta da shi, shi kam Karasowa cikin dakin yyi ya ja stool din gaban mirror ya xauna, Farida ta gaishesa ya amsa ba tare da ya kalli inda suke ba, Batuul ta shiga jujjuya spoon din hannunta cikin shinkafa da miyan gabanta, a hnkli Farida tace " Ki ci mana besty, ko in dibar maki sinasir din ne?" Batuul ta girgixa mata kai kawae, Ammah ta juya tana kallon Abuturrab bayan ta gama wayar da take, ya sauka kasa ya gaisheta, tace "Sae ynxu Abuu" dan shafa kansa yyi yace "Muna tare da Massa ne Ammah" Ammah tace "ina massan?" Yace "Bae dde da tafiya ba" Ammah tace "Toh ka ci abinci kuwa?" Bata jira cewarsa ba ta juya tana kallon Batuul tace "Bitti kin gama cin abincin?" Farida tace "Taki ci Ammah" dawowa kusa da su Ammah tayi tace "sbda me Bitti? Nan fa ba bakon waje bne ki ci abinci" sunkuyar da kai Batuul tayi, Ammah tace "Maxa ki ci Kinji" mikewa Ammah tayi tace "Bari in je gun su Amnah ina xuwa" d'aga hka ta nufi kofa Abuturrab ya bi ta da kallo ganin ko ta kansa ba ta kuma bi ba, girgixa kai yyi cike da takaici, Farida xata mike Batuul ta riko ta da sauri murya can kasa kmr xata yi kuka tace "Plss kar ki tafi farida" tausayin ta ne ya cika ta, ta juya tana kallon Abu ta ga hararanta yake yi, a hnkli tace "ynxu xan dawo Batuul waya ta xan dauko" a sanyaye Batuul tace "Promise?" Farida ta gyada mata kai snn ta mike ta fice daga dakin. Mikewa yyi ya dawo gefen gado ya xauna kusa da inda take xaune a kasa, girgixa kai yyi yana wani irin murmushi yace "Happy for yhu an makala min ke, ba dae kince kin ji kin gani xa ki iya ba koh?" Banxa tayi masa gabanta na faduwa hawaye na bin kuncinta, yace "Toh wae ma wa kike rufe ma fuska ma tukun?" Nan ma dae bata tanka sa ba, ransa ne ya fara baci yace "Kehh!" Still taki cewa komae, sakkowa kasa yyi ya dawo gabanta yana facing dinta a fusace yace "How dare yhu ina maki magana kike kyaleni?" Kmr jira take ta fashe da kuka ssae ta shiga rerawa, bude baki yyi yana kallonta cike da mamaki, can ya runtse ido yace "Na maki wani abun ne?" Kukanta kawae take bata ce komae ba ya bude idanuwansa yace "Ohhk Allah ya baki hkuri" mikewa yyi ya koma inda yake ya xauna, ya kusa minti goma xaune bata bar kukan da take ba shi kam sae kallonta yake sae dae fa xuciyarsa tafasa yake, gashi yana shakkar kuma ce mata komae don yasan sae kwanan gidan ya gagaresa daren, don kanta tayi shiru daga karshe, abincin gabanta ya kalla xae yi magana Ammah ta shigo, karasowa gun Batuul tayi tace "Kin cinye abincin Bitti" a hnkli Batuul tace "Na koshi" Abuturrab yace "Ammah ban fa ci abinci ba duk yau" daukan plate din gaban Batuul tayi ta mika masa tace "gashi ka kara a nn kar a xubar bata wani ci ba" kallonta yake da mamaki, kafin ya sa hannu a hnkli ya karba, ya mike yace "Sae da safe Ammah" Ammah tace "da wuri hka," yace "Na gaji ne da yawa" Ammah tace "Toh Allah ya tashe mu lfya" tana fadin hka ne tana kallonsa ta ga ko xae yi ma Batuul sae da safe, ae ko tuni ya fahimci hkn, kusa da Batuul ya tafi ya dan duka yace "Sae da safe" ba karamin mamaki Batuul tayi ba, ta dago kanta dake cikin mayafi tana kallonsa, murya can kasa tace "Allah ya tashe mu lfya" ita ma tayi hkn ne sanin Ammah na jiran jin abinda xata ce ne, ssae Ammah taji ddin hkn a xuciyarta tace "Alhmdllh, tunda sun fara fahimtar juna" Abuturrab ya kuma yi ma Ammah sae da safe snn ya fice daga dakin rike da plate din abincin da Batuul ta rage. Tun k'arfe biyar Batuul ta tashi dan dama ba isasshen bacci tayi ba, sai kuka da tayi ta yi cikin dare, tana jin k'iran Sallah ta sauk'o daga kan gadon, kayan baccin dake jikinta ta cire ta ďaura towel, sai da tayi brush, tayi wanka tukunna tukunna ta tayi alwala, tana fitowa tasaka bak'ar abayar da ta gani cikin akwatin da Ammah tace nata ne da zatayi sallah jiya, ta saka Hijab tayi raka'atainil fajr sannan ta tada Farida tukunna tayi Sallahn asuba, bata koma ta kwanta ba har k'arfe bakwai, akwatin ta jawo ta shiga dubawa ko da kayan shafa a ciki, ganin akwai yasa ta shafa mai ta saka ta ďan fesa turare, kwalli kawaita saka a idonta sannan ta ďauko wani lace purple daga cikin kayan akwatin dan duk ya fisu simple, duk a sanyaye take bata da wani kuxari, ďinkine mai kyau riga da skirt amma yayi kyau sosai, daidai yayi mata kamar dama can a jikinta aka ďinka kayan, ta saka silver jewellery, komawa tayi kan gadon ta zauna tana tunanin y'an gidansu, wayanta ta shiga nema, tunawa tayi bata ma zo dashi ba can ta baroshi gida, idonta har ya cicciko da hawaye, zama tayi kan gadon tana ta tunane tunane, daga yau shikenan zata bar gaban iyayenta ta koma zama da wani mutum daban da ba sabawa ma tayi dashi ba, ba shiri ta shiga kuka sosai, sai da tayi mai isanta dan kanta tayi shiru dan bata ma bari Farida taji ba, haka tayi ta zama shiru ita kaďai, k'arfe tara Ammah ta turo k'ofan ďakin itama har tayi wanka ta saka atamfanta mai kyau, ganin Ammah ce ta shiga gyara ďankwalinta kanta, a hankali ta gaida Ammah, da fara'a Ammah ta amsa mata tace "Bitti har kin tashi", kai kawai ta gyaďa ta kasa ďagowa, Farida ce ta fito toilet ďaure da towel, Ammah ta tace "Bitti sauk'o kiyi breakfast kinji, Farida in ta gama tazo daga baya", kasa motsawa tayi a inda take, Farida ce ta dubeta tayi murmushi tacewa Ammah "Ammah yanxu zan gama shiryawa zamu sauk'o tare", Ammah tace "Toh karki b'ata mata lokaci", daga haka ta fita, a tare suka sakko falon da Farida bayan ta gama shiryawa sae dae ta dan rufe fuskarta da mayafin jikinta, har dinning farida ta kai ta tana rike da hannunta, Ammah da Anty Amnah na xaune sae Sadeeq da Abuturrab dake rike da cup din tea yana sha a hnkli, tun da suke saukowa daga stairs yake kallonsu har suka karaso dinning din, Sadeeq yyi murmushi yace " Ina kwana Anty Amarya" dariya duk suka yi bnda Abuturrab dake ta shan tean sa, Anty Amnah tace "Toh ku xauna mana kin bar ta a tsaye Farida" kujerar dake gefen Abuturrab Farida ta ja mata tace "Xauna Batuul" Batuul bata so hka ba sae dae bbu ynda ta iya don idansu Ammah na kansu ta xauna a hnkli kan kujeran, kamshin turarensa me ddi duk ya cika ta, farida kuma ta xauna daga gefen Sadeeq.💖💝BATUUL💖💝 41 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Kanta a k'asa ta kasa ďagowa, bata tab'a jinta takure a gidansu Farida ba irin yau, hawaye ne ya fara taruwa idonta tana k'ok'arin maidawa, Ammah ce tace "Bitti ya haka, kici abinci mana", Murmushi Sadiq yayi yace "Toh ai Yaa Abun ne bai bata ba shi ya zauna abinshi sai ci yake kuma ba haka akeyi ba", gaba ďaya kunya ya kamata su Farida sai dariya sukeyi, shikam Abu sau ďaya ya kalleta ya ďauke kanshi yaci gaba da shan shayin shi, Aunty Amna ce tace "Batuul ďauki spoon ďinki kici a cikin nashi plate ďin da ya ďiba kinji, rabu dashi inyaso shi ya ďebi wani", kallon Aunty Amna yayi da tayi kamar batasan yana kallonta ba, Ammah tace "Farida zuba mata tunda ita kunya takeji taqi sakin jikinta",tashi Farida tayi tazo daga gefen Battul ta ďauki serving spoon tace wa Batuul "Bestfrnd what would you like to have, i will be at your service", tana murmushi ta kare maganan, juyawa tayi suka haďa ido da Abutturab dake shan tea yana kallonta, harara ya watsa mata tayi saurin ďauke kanta tana zumb'uro baki a ranta tace masifaffe, ta juya ta sake lek'a fuskan Batuul dake k'asa, kaman yadda waitresses sukeyi tace "Ma'am just say anything and i will serve you", Sadiq ne ya harareta yace "Kin tsaya surutu yaushe zata faďa miki abinda zataci, kawai ki zuba mata komai", shima zumb'uro mishi bakin tayi ta ďauke kanta ta janyo plate ta shiga zubawa Batuul abinci, sai da ta zuba mata duk abincin dake kan dinning ďinnan, plate ďin soup ďin kayan cikin kawai ta iya jawowa gabanta ta saka spoon a ciki, a hankali take ďiba tana kaiwa baki, kanta ta ďago shima a lokacin zai ajiye cup ďin hannunshi, wani irin kallo yayi mata ya mik'e ya bar wajen, hanyan stair case yabi ya haura sama, da ido su Aunty Amnah suka bishi ganin bai ci wani abin kirki ba ya mik'e yayi tafiyarsa, Ammah kam ko ta kansa bata bi ba, yana barin wajen ta sauk'e ajiyan zuciya, abincinta ta shiga ci tana haďa soup ďin da soyayyen dankali a hnkli, kaďan taci ta janye hannunta daga ciki, sai da kowa ya gama tukunna suka koma sama. Wajen sha ďaya Ammah ta shigo ta gansu a ďakin Faridah suna kwance kan gadon Farida suna kallon wani abu a system sai dariya sukeyi, ta daďe tsaye tana kallon yadda Batuul ta sake, sosai hakan yayi mata daďi, basu lura da tana ďakin ba sai da sukaji ta k'ira sunan Farida, da sauri Batuul ta mik'e tana gyara ďankwalin kanta kamar ita aka k'ira, murmushi Ammah tayi tacewa Farida "Ki shirya kije Baa Liman na jiranki zakije gidan Yaa Mera ku kai mata sak'o", kai ta gyaďa tace "Toh Ammah", ta juya ta kalli Batuul da tayi shiru tace "Ki shirya mu tafi", Ammah da har ta juya zata tafi ta juyo tace "A ah, ke nace kije, bance zaki tafi da ita ba, banda ita a yawo yanxu, duk fitan da zatayi yanxu sai da sanin mijinta", da sauri Batuul ta ďago idanunta da suka fara kawo ruwa jin abinda Ammah tace, taci gaba da cewa "Bitti tashi muje kamin ta dawo, muje in k'arasa harhaďa miki abubuwan da nasan zaki buk'ata kamin anjima ku tashi tafiya kuma babu time", zuciyantane ya shiga bugawa jin abunda Ammah tace, yau kuma zasu tafi, ina ďin wai zasu tafi da har za ayi mata shirin abinda zata buk'ata, gaba ďaya kanta ya gama ďaurewa, gabanta ya shiga faduwa, Allah yasa ba can kasar Ammah ke nufi ba, jiki a sanyaye ta tashi tabi bayan Ammah sukayi waje Farida kuma ta sa mayafinta tayi waje, har suka isa ďakin Ammah Batuul sak'e sak'e takeyi a ranta, sai da Ammah tace mata ta zauna tukunna ta samu guri ta zauna k'asan carpet ďin, ďagota Ammah tayi ta zaunar kan gadon, sai sissinne kai take wai ita kunya, wasu manyan kwalaye Ammah ta nufa tacewa Batuul "Bitti kinga wannan ma nakine, ďazu Aunty tasa aka kawo miki shi, turarrukan wutanki ne da na shafawa, in kinje kullum ki riqa amfani dasu, ya zama kullum ďakinki akwai shi, kinga dai yadda Mamanki takeyi ko, ko gidanku aka shiga sai an fito ana k'anshi, toh haka zaki rik'ayi kema kin ji, zakije inda bakisan kowa ba Bitti, ki dage da addu'a, duk abinda Abu zai yi miki kar kice zaki faďawa su Aunty, nima matsayin Aunty nake in har yayi miki abunda ba daďi kar kiji komai ki k'irani ki faďamin, ni da kaina zan sab'a mishi", take idon Batuul ya fara zubda hawaye hankalinta ya tashi ba kadan ba, Ammah taci gaba "Kinga in kun koma bake kaďai bace, ki bata girmanta a matsayinta na wacce ta girmeki, babu ruwanki da shiga harkarta, babu ruwanki da duk wani abu da zakiga tanayi indai ba ta haďa dake bane, ki zauna da ita tsakani da Allah, kinga zaman aure ne yasaki barin gaban iyayenki har wata k'asa, kiyi hak'uri ki zauna sannan ki kula da ibadunki, ki kula da kanki sosai kinji, Allah yayi miki albarka" sosai Batuul ta shiga kuka kamar anyi mata wani abun, da k'yar Ammah ta rarrasheta ta bata baki tayi shiru, Ammah dake cicciro kwalaban turaren cikin kwali tana yiwa Batuul bayanin duk yadda suke, ta dubi Batuul tace "Bitti tashi je ki k'iramin Yayanku yazo ayi packaging kwalayen nan", jiki a sanyaye take kallon Ammah tace "Ammah bansan ina yake ba", Ammah tace ai bazai wuce ďakinshi ba, kije can yana ďakin kice yazo ina nemanshi yanxu", kamar bata son mik'ewa a hankali ta tashi jiki ba kwari ta dauki mayafinta, har ta fara tafiya ta juyo tace "Ammah inane ďakin nashi yake?", Ammah tace "ďakin k'arshe by your left", jiki a sanyaye ta juya ta fita daga dakin, tafi minti biyar bakin k'ofar ďakin tukunna ta shiga knocking a hankali kamar bata so aji gabanta na faduwa, bayan 'yan mintuna taji ya murda kofar ta koma baya da sauri, shi kam tsayawa kallonta yyi da mamaki don yyi tunanin farida ce hkn yasa ya taso ya ji dalilin knocking maimakon sallama, hade rai yyi ya juya ya koma cikin dakin, a hnkli ta bi bayansa ta shiga dakin ta tsaya daga bakin kofar kanta a kasa tace " Ammah na kiran ka" mikewa taga yyi, tana ganin hka ta juya da sauri xata fita daga dakin yyi hanxarin rikota ya juyar da ita yana mata wani irin kallo, kin bari su hada ido tayi, yyi wani murmushin yace "Tunda kika yrda aka hada mu dama akwae sharadodin da xan lissafo maki kafin mu bar kasar nn, nd yhu have to abide to them ol idan kina son kwanciyar hankalin ki da xaman lfyan ki, it's vry well knwn to yhu dat ni bana son ki, yea bana sonki sure, we 2 were neva on gud terms ryt frm d start! Duk da hkn baki yi making any effort ba wajen preventing parent dinmu frm hooking us up, rather yhu encouraged them ta hanyar amince masu dari bisa dari, So...." Wani matsanancin kuka ta fashe da ta durkushe wajen ta shiga rerawa, komawa baya yyi yana kallonta, lkci daya hankalinsa ya tashi, kofan da ke bude ya kalla ya karasa da sauri ya rufe, snn ta dawo ya durkushe gabanta shi ma yana kallonta yace "Na maki wani abun ne?" Kuka take ssae, kukan bakin ciki da kukan tausayin kanta, ji take kmr Allah ya dauki ranta ta huta kawae, ko bae fada ba tasan karshen farin cikinta ne a duniya ya xo, a dan rikice yace "Talk to me mana, me na maki kike kuka, why kike son hada ni da mahaifiyata ne wae, daga magana sae kuka," kin dagowa tayi bare yasa ran amsa, sae kukan da take har da sheshsheka, ji yyi an bude kofar dakin Ammah, ae bae san lkcin da ya jawota jikinsa ya rungumeta ba, wani dad'da'dan sanyin kamshin da ya bugi hancinsa ya sa shi runtse ido da sauri, ita kanta sae da ta tsorata ta kasa ci gaba da kukan da take gabanta na faduwa, sun kusa minti biyar a hka, cikin sanyin murya idonsa lumshe har lkcn kmr me rada yace "Am... am.. I mean am srry!" A hnkli ya kuma cewa "Am srry" sae kuma ya bude idanuwansa ya daura kan gashin kanta dake fitar da wani fitinannen kamshi don gyalenta ya xame, d'ago kai tayi suna hada ido ya saketa ya mike da sauri, da kyar ita ma ta mike kanta a kasa xata fita ya fixgota ya wani hade rae kmr ba shi ba yace "clean those tearz" sunkuyar da kai tayi, ya ciro handki a aljihunsa ya dago kanta ya shiga goge hawayen fuskarta, yana mayar da handki din aljihunsa ta juya ta fice ya bi bayanta, ko da suka koma dakin Ammah bata ciki, Batuul taje can karshen gado ta xauna bayan ta daura mayafinta a kai, stool ya ja ya xauna shi ma ya fiddo wayarsa yana dannawa, lkci lkci yake satan kallonta ita ma hka, da sun hada ido kuma ya jefa mata harara, a hka Ammah ta shigo ta samesu, xama Ammah tayi yace "Gani Ammah" Ammah tace "Eh dama wa en can kwalayen xa ayi packaging kadda lkci ya kure ko ya kaga" kansa a kasa yace "Toh Ammah bari in kira sadiq," ya mike ya fita daga dakin, Ammah ta juya ta kalli Batuul, da sauri ta sunkuyar da kai cike da kunya don gani take kmr Ammah xata ji kamshin turarensa a jikinta. Da yamma Ammah tasa Batuul ta sake shiryawa cikin wani kayan, atampa exclusive ta saka mai kyau, kayan yayi mata kyau sosai har ta gaji, k'asa suka sauk'o lokacin Abutturab shima yana k'asa yana jiranta, shima yayi kyau sosai cikin kaftan ďinshi fari da hularshi Rawaram, tunda take sauk'owa yake kallonta har sai da ta k'araso tazo kusa dashi tukunna ya ďauke idonshi daga kanta, Ammah ce tace "ku fara zuwa gidan Yaa Mera daga nan ku wuce gidansu", "Toh kawai yace ya juya yana jira ta fara fita, ganin batada niyyan motsi yayi ďan siririn tsaki ya fita, a hankali take ďaga k'afa tabi bayanshi, sai da ya buďe motar ya shiga ya zauna tukunna itama ta buďe ta shiga, babu wanda yace da wani uffan har suka isa gidan Yaa Mera, sosai taji daďin ganinsu, Nasiha tayi musu sosai tasa aka cika musu gabansu da abinci iri iri, suna zaune Massa ya shigo shima yayi ta tsokanan Batuul da ta kasa cewa komai, basu wuce awa ďaya ba suka yiwa su Yaa Mera sallama, itama tayi musu addu'a suka wuce, sai da ya ďau hanyan gidansu tukunna ya fara magana ba tare da ya kalleta ba "ki dena yiwa mutane wannan shirun naki, sai anyi miki magana kiyi kamar bakya jin abinda ake faďi idan aka tambayi dalili ki saka ma mutane kukan munafurci" kamar batasan mey yake cewa ba taci gaba da kallon window ta waje, jin tak'i cewa komai yayi k'wafa yaci gaba da tuk'inshi, suna zuwa gaban gate ďin gidansu, hannu tasa zata buďe k'ofan ta fita kamin masu gadi su buďesu musu gate, kamar yasan abinda take shirin yi ya danna lock ďin motar, murďawa tayi taji yaqi buďuwa, rau rau tayi da ido tana kallonshi, har idonta ya fara hawaye , mamakinta ya tsayayi yace "da akayi miki mey ďin zaki fara hawaye kuma", ďauke kanta tayi tare da ďan murguďa bakinta ta ďanyi murmuring wani abu sae dae fa duk ganinsu da tayi a kofar gidansu ne yasa ta samu wnn livern, kallonta yayi yace "Did you say anything", daidai lokacin aka buďe gate ďin yayi k'wafa ya ďauke kanshi daga dubanta ya sa kai cikin gidan, kin buďewa yayi bayan yayi parking har saida ta juyo ta kalleshi, yace "clean those tears , baza ki shiga gidannan da hawaye ba", ba shiri ta shiga share hawayen dake idonta, sai da ta goge ta juyo tana dubanshi ganin yaki budewa har lkcn a hnkli tace " na goge", daga gefenshi ya danna lock ďin, da sauri ta buďe motar ta fita a guje, murmushi yayi ya fito daga cikin motar, da gudu ta shiga palon gidansu tana k'walawa y'an gidansu k'ira a jere, Aunty Hafsat da ta fito daga kitchen ta fara haďuwa da, da mamaki Aunty Hafsat tace "A ah Batuul daga ina haka kika shigo kina ihu", tafiya taji kan stairs, juyawa tayi taga Aunty ke sauk'owa, da gudu tayi wajen Aunty ta rungumeta, tana jinta jikin Aunty ta fashe kuka, murmushin k'arfin hali Aunty tayi dan itama kwana ďaya da tayi bata gidan tayi kewarta sosai, ďagota tayi tana kallon fuskanta tace "Kukan na meye kuma Batuul", sake komawa tayi ta kwanta jikin Aunty taci gaba da kukan da takeyi, da sallama ya shigo falon, ďagowa tayi daga jikin Aunty tana kallon Aunty tace "Aunty su Mahir fa", Aunty tace "Ai yau babu wanda yaje Islamiyya cikinsu, Hafiz kam kuka ya dingayi wai sai an kaishi inda kike", hawayen dake idonta ne ya k'arasa gangarowa jin abinda Aunty tace, da gudu ta k'arasa hawa sama tayi ďakinsu, buďewa tayi tagansu kamar kullum ďakin yadda yake suna kallon ball, da gudu ta shige ta rungumosu, sai da suka sake juna Yusra tace "Yaa Batuul wai inji Baba zaki tafi Uk yau zamu daďe bamu ganki ba dagaskene?", ji tayi kamar zata fasa ihu tayi murmushi tace "a ah bazan daďe ba, ai zaku rakani airport ko", da sauri suka shiga gyaďa kai, ta kalli manyan da sukayi kamar basu san tana ďakin ba tace "y'an rainin wayo dama nasan jira kuke in bar gidan shiyasa kun ganni yanxu ma baku damu ba", dariya sukayi suka juyo sukace "penalty za a buga shiyasa", duk suka taso suka dawo kan gadon da take, zama tayi suna ta hira da k'annenta har saida Aunty ta tura a k'irata, kitchen ta samu Aunty, anty ta dubeta tace "Batuul wa yace miki haka akeyi, ya zaki tafi ki barshi shi kaďai ko ruwa baki bashi ba", baki ta zumb'uro tace "Aunty toh ba su Janet zasu bashi ba", Kai Aunty ta girgiza tasan akwai aiki sosai gaban Batuul dan ba wayone ya gama isanta ba gashi lokacinsu is limited, amma ba komai ko ta wayane zatayi mata magana, kai ta girgiza ta juya ta ďauko tray ta jera abubuwa tace "ďauki ki kai mishi", baki ta zumb'uro ta kinkimi trayn tayi palo dashi dungure masa tayi a kasa ba tare da ta kallesa ba, ya bi ta da kallo har ta haura sama yyi murmushi, sai magrib lokacin suna shirin tafiya Baba ya dawo, shima ganinshi ta shiga sabon kuka, da k'yar ya samu tayi shiru, Abu kam suna haďa ido yake sakar mata harara, cewa Baba tayi sam sai k'annenta sun rakata airport, da farko da yaqi dan sai sun koma gidan Ammah zasu wuce, amma ganin yadda take kuka yasa driver ya kaisu, sai a lokacin Aunty taji baza ta iya jurewa ba itama taja Batuul sukayi ďaki, sunfi minti talatin har saida Baba ya shigo yace ya isa haka ta fito su tafi, kuka takeyi sosai har ta shiga cikin motar, bai ce mata komai ba shima ya shiga, motar su Ahmad na daga gaba nasu na baya sukayi gidan Ammah. [8/22, 14:39] Umar Dalha: 💖💝BATUUL💖💝 42 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Kanta ta kifa tsakanin cinyoyinta ta dinga rusa kuka, shi dai bai ce mata komai ba sai kallonta da yake ta gefen ido yaga if she's fine, sai da suka shiga cikin gida bayan yayi parking ya juyo ya dubeta ganin batada niyyan tashi ya sa ya bude motar ya fito ya wuce gun motar k'annenta, sai da k'annenta suka fito suka nufi motar Abuturrab tukunna ta shiga goge hawayen dake fuskanta, dan murmushi tayi masu ta sauk'o daga cikin motar tana kallonsu tace "mu shiga mana", ba musu sukayi gaba, yana daga gefe yana kallonsu, yaran masu kyau duk sun fita haske, juyawa tayi ta dubi inda yake tsaye yasa hannu ďaya cikin aljihu, wani kallo ya shiga yi mata, ďauke kanta tayi daga dubanshi tabi bayansu, ita ta buďe musu k'ofa sai da suka gama shiga itama ta shiga da sallama, da murna Farida dake zaune tare da Ammah ta mik'e tana k'ok'arin ďaukan Hafiz, waje suka samu suka zazzauna daga k'asan rug ďin palon, da fara'a Ammah ta shiga ce musu "Ahmad ku tashi ku zauna kan kujera mana", babu abinda sukeyi sai murmushi, ta dubi Batuul tace "Bitti ce musu su hau kujera mana su tashi daga k'asan nan", kallonsu kawai Batuul tayi ta kasa musu magana, ganin sunqi tashi Ammah ta mik'awa Yusra, Mahir da Hafiz hannu alamun suzo wajenta, Yusrace kaďai taje dan ita tana da saurin sabo, Janet Farida tashiga k'walawa k'ira, babu b'ata lokaci ta fito tace "Aunty gani nazo", ta dubeta tace "kawo musu ruwa", ba b'ata lokaci ta juya ta tafi kawo musu ruwa, Ammah zatayi magana kenan ya turo k'ofa ya shigo yana tafiyarshi ta k'asaita, palon ya k'araso ya zauna, Ammah ta dubeshi tace " tare da su xa ku airport knn", Batuul da kanta ke k'asa taqi ďagowa yake kallo kamin ya kalli Ammah yace "Ehhh kuka tayi ta musu kamar yarinya wai tanaso su rakata", Ammah tayi dariya tace "Babu wani yarinta, ai gaskiyanta da tace su rakota su yi bankwana", baice komai ba sae tab'e baki da yyi ya mik'e yana kallon Ammah yace "Ammah Sadiq ďin ya fito ne, saura thirty minutes tafiyan namu", Ammah tace "Ai yanxun nan ya shiga wanka", daga jin haka ya wuce, Ammah ma tashi tayi tace "Bitti muje ki shirya kar lokaci ya k'ure kinji", ba musu ta mik'e amma har lokacin ta kasa yadda wai itace za a rakata airport zata bar garinsu dan tayi aure zataje zama da wani, take idonta ya fara kawo ruwa, jiki a sanyaye ta bi bayan Ammah, tana shiga bath tub ta dinga kuka dan kanta ta mik'e ta fito bayan ta kusa minti goma a ciki, wasu kaya ta gani Ammah ta ajiye mata kan gado, Lace maroon ne mai green designs da jewellery ďinsu na gwal, ba b'ata lokaci ta ďauka ta sakasu cikin rashin kuxari, riga da skirt ne, kayan sun mata kyau sosai, a bakin gado ta zauna bayan ta gama y'an shafe shafenta ta shiga tunanin irin rayuwar da xata yi ynxu. D'akin Abuu Ammah ta shiga bayan Batuul ta shige toilet, har ya canja kaya lokacin yana zipping wani akwati, ganin Ammah da yayi ďakinshi ne ya sashi barin abinda yake cikin hanzari ya k'araso inda take, bata ce mishi komai ba har ta k'arasa shigowa tukunna ta zauna daga bakin gadon, rabon da Ammah ta shiga ďakinshi har ya manta, jiki a sanyaye ya bita ya zauna daga k'asa, ce mata yayi "Ammah ai da kin k'irani nazo ba sai kinzo da kanki ba" har ta buďe baki zata fara mishi magana ta fasa tace "in ka gama ka sameni a ďaki toh", daga haka ta mik'e tayi waje, ajiyar zuciya ya sauk'e dan yasan da magana bakin Ammah, koh minti biyu batayi ba da fita shima ya fita yabi bayanta, zaune ta tadda Batuul bakin gado har lkcn, ganin Ammah ta shigo yasa ta sauk'e kanta k'asa zata sauk'a k'an rug ďin Ammah tace mata tayi zamanta, kin zama tayi kan gadon ta sauk'o k'asa, da sallama ya shigo ďakin shima ya zauna kan stool ďin mirror, Ammah na kallonshi ta fara magana "Abuu ga amanan Batuul nan na baka da hannuna", da sauri Batuul ta ďago jin abunda Ammah tace, jiki a sanyaye ta sauk'e kanta dan har idonta ya fara tara ruwa, Ammah taci gaba tana kallon yadda ya sauk'e idonshi k'asa tace "tunda kayi aure kasa k'afa ka fita daga garin nan hankalina bai kwanta ba, ni bansan tsakaninka da matarka ba amma mu dai kam babu abin alheri da tayi mana, ni da kaina na sa aka nemo maka auren Batuul dan tun kamin aurenka da Ajiddeh Batuul naso ka aura amma Allah bai yi ba sai yanxu, ko sau ďaya ban yadda kasa hawaye zuba daga idon Batuul ba, ban yadda ko da wasa matarka ta wulak'anta min ita ba, yadda take zab'inka haka nima Batuul take zab'ina sannan amana na baka ita kamar yadda iyayenta suka aminta dakai suka baka y'arsu, ka kula da ita fiyeda yadda xa ka kula da kanka, sannan makarantarta ba denawa zatayi ba, an sama mata admission a can, ka taimaka mata da dukkan k'arfinka har sai ta kamalla dan tana karatunta muka nema maka aurenta, Allah ya tayaka rik'o ya baka ikon yin adalci tsakaninsu", ta juya tana kallon da Batuul da ta jik'a gyalenta da hawaye a lokacin tace "Bitti ga yayanki nan xa ku tafi, na faďa miki duk abinda zaiyi miki mara daďi, don't hesitate in zama ta farko da zaki faďawa, ki zama mai respecting ďinshi kinji, he will be your guide In sha Allah, tsakanin ki da matarsa girmamawa, ki goge hawayenki kinji, kuma duk lokacin da kike son dawowa ki faďa mishi zai dawo dake kina yin kwana biyu kinji", Sadiq ne ya turo k'ofan tareda sallama, da murmushi a fuskanshi ya dubi Abu yace "ba dai kun fasa tafiya ba yau", Abuu ya dubeshi fuskanshi babu walwala yace "We are coming", Ammah ta dubi Batuul ta ďagota tace "Bitti share hawayenki ki tashi kuje, Allah yayi muku albarka, ya baku xuri'a dayyaba", da k'yar Batuul ta iya mik'ewa tana gyara gyalen dake kanta har wani shidewa take don kuka, Sadiq sai tsokananta yake sae dae shi ma xuciyarsa fal yake da tausayinta, suna sauk'a k'asa suka tarar da Massa shima yazo, gaba ďayansu suna zaune palon sun gama shanye drinks ďin da aka kawo musu, Ammah tace "jeka Abui ya shigo yanxu kuje kuyi sallama dashi, tare sukaje sukayiwa Abui sallama yana gaba tana biye da shi a baya, Abui ya sake musu Nasiha tareda yi musu Allah ya kiyaye hanya, mota uku suka yi suka nufi airport. Tunda suka ďau hanyan airport take kuka ba k'akk'autawa dan tasan farin cikinta ragagge ne tunda har ta yadda tabi Abu wani garin da babu kowa nata, tausayin kanta take sosai tana kuka, sai da tabi y'an uwanta ďaya bayan ďaya tayi hugging ďinsu tana kuka su din ma kukan suke, har ta iso kan Farida dake kukan itama ta rungumeta, da k'yar suka sake juna don itama kukan da take ya hanata yin magana, ta kasa yin komai sai gyaďa kanta da takeyi, cikin hanzari ta sake Farida xata bi Sadiq da ya kasa ci gaba da kallon emotional scene din ya juya xae bar wajen, Abuturrab ya fixgota jikinshi, sosai ta shiga yin kukan kmr ana tunxura ta, dai dai saitin kunnenta ya sunkuyo a hnkli yace "control, its a public place baza mu tafi kina kuka kamar wacce na sato ba", kwanciya tayi jikinshi tayi lamo tana ajiyar xuciya, yana jin yadda heartbeat ďinta ke up and down, hannunshi ďaya ya ďaura bayanta, ďayan kuma yayiwa su Sadiq alamun suja su Ahmad su tafi, hakan kuwa akayi, takai minti biyar kwance jikinshi, can da ta tsagaita kukan ta fara dawowa normal ta ďago kanta, jinta jikinshi yasa ta kallon fuskanshi taga shima ita yake kallo, da sauri ta matsa baya ta juya bayanta ganin ko su Farida na nan, taga wayam babu kowa wajen, kallonshi tayi da idonta da yacicciko tace "Yaa Abu dan Allah mu koma kar mu tafi plss", wani irin kallo ya bita dashi yaja akwatin dake gabanshi yace "When you are done ina ciki", babu yadda ta iya haka tabi bayanshi a sanyaye tana share hawayen dake sakko mata, a departures waiting room ya xauna yana jiran jin announcement din departure'n su sanin few minutes ya rage, ya juya yana kallonta ganin a tsaye take, a hnkli ta xauna nesa da shi kanta a kasa, tabe baki yyi ya kauda kai, bayan kusan minti takwas akayi announcing cewar passengers din Abuja to UK su fara boarding ynxu jirgi xae tashi, mikewa yyi yana kallonta, wasu sabbin hawayen ne ke sauko mata duk jikinta yyi sanyi ta kasa tashi, har ya fara tafiya yana jan trolley dinsa ya tsaya, juyawa yyi yana kallonta ganinta xaune yasa ya dawo yana kallonta bbu yabo bbu fallasa yace " Ko in daga ki ne" a hnkli ta mike tana rufe bakinta da mayafi kar ta saki ihun da taji na shirin fitowa, sauke idonsa yyi daga kallonta ta kama hannunta ya shiga tafiya tana binsa har suka isa inda jirgin British Airline (B.A) yake tsaye, yana rike da hannunta suka shiga jirgin, a first class ya samar masu empty seats, a hnkli ta xauna ta jinginar da kanta jikin kujerar tare da lumshe ido, ya saka trolleyn hannunsa daga sama inda ake ajiye luggages, snn shi ma ya xauna, announcement aka shiga yi na cewa "Passengers on board shud pls fasten their seat belts, British Airline flight is about taking off" Abuturrab yyi fasten din seat belt dinsa yana kallonta, gani yyi ko motsi bata yi ba, ranan da suka yi boarding same plane daga Maiduguri xuwa Abuja ya tuna, yyi shiru yana kallonta, a hnkli ya kai hannunsa ya mata fasten din belt din da kansa, ta bude rinannun idonta tana kallonsa, lkci daya ya hade rai, da sauri ta sunkuyar da kanta, wayarsa ya fiddo ya maida shi flight mode ya jona earpiece ya sa a kunne ya lumshe ido, jirginsu na tashi ta fashe da wani kukan tausayin rayuwarta, bude ido yyi yana kallonta sae dae bae ce komae ba, tayi mai isarta bayan wani lkci tayi shiru ta kwantar da kai jikin kujeranta lkci daya bacci ya dauketa, sae a snn ya cire earpiece din kunnensa ya rike kansa dake sara masa xuciyarsa a dagule, from Where is he going to start this long explanation to his Ajiddeh, just ta ina xae fara ce mata iyayensa ne suka makala masa Batuul, ya xata dauki xancen, will shi even believe him, tunanin hkn ya sa ciwon kansa ya tsananta, jinginar da Batuul tayi jikinsa tana bacci ya dawo da shi duniyar tunanin da ya tafi, juyawa yyi yana kallonta ya ga bacci ssae take, ya fuzar da iska tare da lumshe ido ya jawota jikinsa don gyara mata kwanciya, muryar wata hostess din jirgin ya sa shi bude idonsa, tana tsaye dai dai kujeran da suke plate holder din seats dinsu ta jawo ta dora ruwa a kai a karamin disposable cup, murmushi dauke fuskarta tace "Sir what would yhu like to have?" Yace "Just coffee" kallon Batuul tayi xata yi magana yace "She's OK" juyawa tayi ba a dau lkci ba ta dawo da cup din coffee ya karba yace "Thank you" d'an bow din masa tayi tana murmushi tace "Yhu are welcome Sir" daga hka ta juya ta bar wajen. Karfe sha biyu saura na dare Batuul ta bude idonta ganinta jikinsa yasa ta kallesa, idonsa lumshe yake alamar ya fara bacci, a hnkli ta xame jikinta ta xauna da kyau, ta shiga rera kuka tunawa da tayi shknn fa ta rabu da Anty, bude ido yyi yana kallonta, ya gyara xamansa a fusace yace "God! What again? Ke wae baki gajiya da kuka ne, am tired of this pls, aiki kawae su Ammah suka hada ni da I knw" jin ta kara sautin kukan yasa ba tare da yyi wani tunani ba ya jawo ta jikinsa murya can kasa yace "are yhu hungry" kin cewa komae tayi, ya watsa mata wani kallo yace "Kina jina dae koh?" Girgixa masa kai tayi, ya hade rai yace "Gud! Go back to sleep ynxun nn" rufe idonta tayi, tayi lamo jikinsa sae dae yana jin ynda xuciyarta ke bugawa. Har asuba daga ita har shi basu rintsa ba, da ta bude ido xae tambayeta ko tana jin yunwa ta girgixa kai ta kuma rufe idon, Karfe bakwae na safiyar washegari jirgin British Airline ya sauka airport a UK, nn fa Abuturrab ya ji duniyar gaba daya tayi masa xafi, da ya tuna Ajiddeh sae gabansa ya fadi ba kadan ba, da kyar ya mike yana kallon Batuul da idanuwanta suka rine ssae, hade rae yyi lkci daya ta mike kanta a kasa, ya fiddo trolley dinsa ya shiga tafiya, bin bayansa tayi hawaye cike idonta har suka sauko daga jirgin, duk da ta sha xuwa kasashen turawa da Baba har ma da Anty Hafsat yau komawa tayi kmr bakauyiya a haraban airport din, don sae shishshige masa take, ba komae kuma ya janyo hkn ba sae don duk a tsorace take, ba kuma wae turawan suka bata tsoro ba sae don tunawa da tayi da Ajiddeh [8/22, 14:41] Umar Dalha: 💖💝BATUUL💖💝 43 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Amma na ganin tafiyarsu ta koma cikin gida itama tana jimamin rashin Batuul da zatayi, ďakin Abui ta wuce ta sameshi zaune yana kallo da glass idonshi, daga gefenshi ta zauna tace "Barka da zama Abui", yace "Yawwa Ammah, naga har kin fara missing yaran naki", murmushi tayi mishi tace "Ai ni tausayin yarinyar nan ke cikani, sosai nake tausayinta danma dai tana da nutsuwa", juyawa tayi ta kalli Abui with full attention tace "Abui amma hankalina gaba ďaya yaqi kwanciya, matar Abu nake jiyewa Batuul dashi kanshi Abun, ko wancan karan ni nasan Abu ba yin kanshi bane zaman da yayi ba tareda dawowa gida ba har na shekara ďaya", with full concentration Abui yake kallonta har saida tayi shiru yace "Ehhh shiyasa this time da mukaje Maiduguri kamin a ďaura aurenshi sosai nasa aka mishi addu'a, sauk'an Alqur'ani kuma kullum sai anyi har yau ďinnan Allah ya rabasu da sharrin masharranta", wani ajiyar zuciya Ammah ta sauk'e tace "Alhamdulillah", ta gyara zamanta tana fuskanta Abui tace "Nima tun lokacin da Ashiekh yace a dage da addu'a ban daina ba, yanxu naga komai ya fara daidaita, dan banga alamun abinda akayi mishin har yanxu yana jikinshi ba, sai dai mu sake dagewa Allah ya sake rufa asiri, wannan karan har Batuul ďin sai da na sa ana yiwa sauk'an Qur'ani da addu'a, daga baya ma zan sake tura mata maganin kariya dan yanxu lokaci ya k'ure shiyasa ban basu ba" Abui yace "Allah ya sake karewa, tare suka amsa da "Amin", mik'ewa tayi tana kallon Abui tace "Abui abincin fa baka ci ba gashi har takwas ya wuce", murmushi ďauke fuskanshi yayi mata alama da tazo ta zauna gefenshi, ba musu ta dawo ta zauna gefenshi tana kallonshi yace "naga kina ta hidiman yaranki bakizo bani abinci ba shiyasa nima banci ba", murmushi tayi dan tasan tsokanarta yake ta ďan kalleshi tace "Toh su ba yara bane, kai ai kullum inayi maka kuma daga yau su tafiya zasuyi", k'ok'arin tashi take daga wajen tana cewa "Abui bari in kawo maka tea toh tunda baza kaci abincin ba", jawota yayi jikinshi yace "No am okay, kiyi zamanki nima bana jin yunwa, i ate late in d evening shiyasa banci abincin ba, kuma tea ďinma i dont feel like taking it", batace komai ba ta sake shigewa jikinshi daga nan sukaci gaba da hiransu, Har suka fito daga terminal ďin bata dena kuka ba, shidai bai ce mata komai ba dan kukanta ya ishesa, tafiya yake tana biye dashi sai shishige mishi take har lkcn abun har yaso bashi dariya, Taxi ya tarar bayan sun fito yace mishi "GEORGE'S street", driver da kanshi ya fito zai buďe musu k'ofa yace "No its okay you can sit back", gidan baya ya buďe mata ta shiga sannan ya zagaya ya buďe ya shiga shima, babu abinda zuciyan Batuul yake sai faďuwa, hawayen da take ta k'ok'arin mayarwa yaqi tsayawa sai ma daďa zubowa yake, sau ďaya ya kalleta ya ďauke kanshi, har sukayi nisa bata dena kukan ba, ranshi ya gama b'aci sosai, juyowa yayi yana kallon yadda take ta sheshek'a kuka, hannu yasa ya kama kafaďunta yace "Behave! Kinaji na ko, tun farko i gave you option, da kin buďi baki kince bakyaso am sure babu mai miki dole, but kikayi kunnen k'ashi shine yanxu zaki dameni da kuka", jajayen idanunta da suka rine ta ďago ta kalleshi taga shima idonshi akanta yake, hannunshi dake kafaďunta ta ture taja da baya tana goge hawayen fuskarta, kallonta ya tsaya yi da mamaki daga baya yayi k'wafa ya juya jin wayarshi na k'ara, iska ya ďan furzar daga bakinshi ganin mai k'iranshi, recieving yayi tare da sawa a kunnenshi a hnkli yace "Babe am back", wani irin k'ara tasa da har ya sashi cirewa daga kunnenshi tukunna ya mayar yace "Hae chill ba sai kinzo ba ina hanyan dawowa ko David ban faďawa muna hanya ba", da mamaki a ranta tace suna hanya kuma, shi da waye? oho ko ma dai waye shi ya sani, abunda ta shirya mishin in yaso duk munafikin da ya biyoshi shi ya sani ya faďa musu, da sauri ta kawar da tunanin tace "Baby ai da ka faďamin da ko breakfast nayi maka, but ban tashi ba ina bacci har yanxu, babe kazo min da Domino's pepperoni Pizza da Cold stone Ice cream tunda akwai a hanya dashi nakeson yin breakfast", kai ya girgiza yana mamakin halin Ajiddeh, ko yaushe ma ta iya girkin da har zata ce wai da ya faďa mata tayi mishi breakfast, ya sauke ajiyar xuciya yace "Fine naji, mun kusa isowa gida you should get up from your slumber and get ready", yana iya jiyo murnar da takeyi tace "Right away baby", da haka ya katse k'iran, suna gama wayan ta dirk'o daga kan gadon, straight away garden ta wuce da ďan bingel ďin rigar bacci dake jikinta taje duba kuttun data ajiye, ganin yana nan very safe ta dawo bakin palo dan tun ranan da ta dawo zuba abin ba ayi shara a gidan ba sai bayan ta aiwatar da abinda tayi niyya, sai da tabbata komai daidai ta koma cikin gida tayi wanka ta sako wata y'ar crop top da bum short, sosai ta gyara dogon gashinta ta baďe jikinta da turare ta koma ta kwanta, Batuul kam banda bugu babu abinda zuciyarta keyi, haďuwarta da Ajiddeh ba wani mai yawa bane tasan babu abin arzikin da ya taba haďata da ita in banda hararta da takeyi kullum in sun hadu, maganganun da Ammah tayi mata ne suka dinga dawo mata kai, Ammah tace mata kar ta yadda su rainata, yes hakane baza ta yadda su rainata ba, toh ita inama ruwanta da ita ne, ba sai ta kulata bane bama zata rainata, ďan tsaki taja ba tare da ta san tayi hkn ba, juyowa yayi yana kallonta jin tsakin da tayi, ganin za a wuce Domino's yasa shi cewa driver ya tsaya, parking driver yayi ya fita ya shiga Domino's bayan 10 mins ya fito rik'e da kwalaye a hannunshi na pizza da ledan Ice cream, kanta na daga jikin window tana ta kalle kallenta ta ďago tana kallonshi, wani irin relief yaji ganin idonta ba hawaye, shiga yayi ya zauna driver ya tada motar suka tafi, tafiyar 8mins suka isa anguwansu, gini ne uniformly masu kyau duk iri ďaya da red bricks, bambancin wani da wani kawai motocin dake pake ko kuma yadda flowers ďin ke jere, bin ko ina da kallo ta rik'ayi zuciyanta na ci gaba da bugawa, har compound ďin driver yayi parking, tsayawa yayi yana kallonta bayan ya fito daga motan ganin taqi fitowa yace "you can come out, ba motata bace", ďauke kanta tayi a sanyaye ta fito, ta bi bayan shi, murďa k'ofan palon yayi ya shiga da sallama yana kalle kalle, kan vanity table ďin palon ya ajiye boxes ďin hannunshi, Batuul ta kasa Karasowa cikin falon, Ajiddeh ce ta sauk'o a guje daga kan bene tazo rungume shi da murna tare da lumshe ido, shima ya rungume ta ssae, sam bata lura da Batuul dake bakin kofa ba, cikin muryar shagwaba tace "Babe shine ka daďe a Nigeria ina ta jiranka, ka kawomin pizzan?", idonta ne ya faďa kan vanity table ďin ta juya zata ďauko kwalin cike da murna, cak ta tsaya ganin Batuul a bakin kofa, lkci daya komai ya tsaya mata, zuciyanta ne ya shiga bugawa da sauri da sauri tana kallon Batuul da itama ke kallonta duk a mugun tsorace take hkn bae nuna a fuskarta ba, dawowa tayi da baya tana kallon Abu, idonta ya cicciko ruwa tana kallon idonshi ta fara mishi magana da kyar, "Aliyu who is she?", this d time he dreaded dama, runtse ido yyi ya kamo hannunta zai jawota jikinshi ganin yadda jikinta ke b'ari, ta wani warce hannunta da karfi daga rik'on da yayi mata cikin rawan murya tace "wannan wane irin jaraba ne Aliyu, watan ka ďaya can kana tare dasu shine zaka dawo ma baza a bari ka dawo kai kaďai ba sai an haďaka da wata, watanma a rasa da wacce za a haďaka sai wannan mai kama da y'an ethopian ragowar yunwa", sosai ran Batuul ya sosu jin abinda Ajiddeh ke kiranta da, lkci daya hawaye ya kawo idonta ta sunkuyar da kanta, shima Abu ranshi ya b'aci jin maganganunta amma baison nunawa gaban Batuul dan ya gama cika mata bakin yana son matarsa, kuma bai son ta rainata, iska ya fitar daga bakinshi ya birkita lallausan gashin kansa yace "calm down babe, kinsan she is my cousin, and.. and... Babe karatu fa tazo yi nothin else, babanta ne baison tayi zaman hostel shiyasa yakeso ta zauna gun mu", da mamaki Batuul ta ďago kanta jin abinda yace, shi kansa bai san lkcn da yyi formulatin karyan ba lkci daya kmr da can ya tsara, ajiyar zuciya ta sauk'e ba tare da ta shirya ba, sae dae duk da hka xuciyarta bae bar tafasa ba don ita har ga Allah ta tsani Batuul with passion, ita kanta bata san dalilin k'in ta da take ba, janyewa tayi daga jikinshi tana k'arewa Batuul kallo tana yamutse fuska ganin yadda jikin Batuul ke kyalli saboda gyaran da yasha, tasan hasken Batuul bai kai haka kyau ba, gashi sai wani kyalli takeyi kamar amarya, nn hankalinta ya kuma tashi tace "toh in suna son karatunta waje sai an kawota gidana ne xata yi, nasan duk salon sa ido ne aka haďoka da ita babu wani karatu, sai kace wanda nake yankan namanshi inaci baza a bar mutum ya huta ba, toh wlhy sai dai ko ni ko ita a gidannan dan bazan yadda da harkar munafikai ba", ta fadi hkn tana masa wani matsiyacin kallo tana girgixa kafa, da mamaki ya tsaya yana kallonta, wai shi Ajiddeh ke yiwa shirmen nan a gaban yarinya don ta rainasa, kallon Batuul yayi da itama ta tsaya jin abunda Ajiddeh ke cewa, karasawa yyi fuskarsa daure ya kama hannunta yayi hanyan staircase da ita, mutuwan tsaye Ajiddeh tayi ganin abinda yyi, a tsorace take kallon Abutturab ko shi ďinne dan tasan ko da safe sai da ta sake duba magungunan da tayi mishi taga kuma komai daidai yake, toh ya akayi ya iya tsallake maganarta har yaja hannun wannan shegiyar da yake ikirarin k'anwarsa ce su bar ta tsaye, wasu hawayene masu ďumi shiga bin kuncinta ta bisu da kallo, Batuul kam ta kasa cewa komai sai binshi da takeyi a baya gabanta na faduwa, wani ďaki taga ya buďe suka shiga, kallonta yayi yace "Sit right here" ya juya yaja k'ofar ya fita, juyawa tayi tana k'arewa ďakin kallo, ďan madaidaicine mai kyau komai na ciki grey and white, ďaya daga cikin sofan ďakin taje ta zauna dan ita batasan ko ďakin waye nan ya kawota ba, yana fita daga ďakin k'asa ya dawo inda Ajiddeh ke tsaye ta kasa gaskata abinda take gani da idonta, ganinshi yana nufota ya sa zuciyarta yin sanyi dan tasan bokan nan yayi assuring ďinta komai zaiyi daidai, sae dae hkn bae hanata tsuke fuska tana hawaye ba, magana ya fara yi mata yace "Ajiddeh mey ke damunki wai kike abinda kika gama yi yanxu kamar wata yarinya", murmushin takaici ta saki tasan dole ma ai asirin nan ya kamashi, idonta cike da bala'i tace "dole mana kace mey ke damuna, kaje an gama munafirce min kai shine zakazo kana tambayata mey ke damuna", yasan ya fara losing control dan ranshi ya fara b'aci amma bayason biye mata suyi faďa after a long time, matsowa yayi gabanta yana kallon idonta yace "control and hear me out ki dena wannan haukan da kikeyi, its not what you are thinking uhhn?", harzuk'a ta sakeyi dan yanxu ta fara tsorata maganin nan bai kamashi ba knn, rai b'ace tace "Lallai Aliyu, hauka ko" tayi ďan dariya mai sauti tace "ai kuwa yanxu zakaga hauka in baka fita da tsinanniyan nn ba daga gidana wllh", ranshi yaji yayi mugun b'aci cikin tsawa yace mata "Keeeh", idonta na zubar da hawaye tana kallonshi tace "meye zakayi min kuma bayan wanda ka riga da kayi, ni nasan munafikan dake gidane suka haďoka da wannan mai kama da karuw.....", bata samu k'arasa maganan dake bakinta ba ya daka mata wani irin tsawa tareda da damk'ota ya shaketa yana huci, turata yyi lkci daya idonsa ya kada, Batuul dake ďaki tana ta kalle kallenta ta zauna a takure sosai ta tsorata jin k'aran a falo, jiki na b'ari ta buďe k'ofa don ganin ihun mey taji, sauk'owa tayi tana kallonsu, bnda rusa kuka bbu abinda Ajiddeh ke yi, juyawa yyi yana kallon Batuul a tsawace yace "C'mon get back before i get there ynxu", sosai Batuul ta tsorata ganin yanayinshi, sae dae bata nuna ba ta juya a hnkli ta koma sama tana share hawayen dake son xubowa daga idonta ta koma ďakin ta rufoshi. [8/22, 14:44] Umar Dalha: 💖💝BATUUL💖💝 44 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Juyawa Abuturrab yyi ya haura sama a fusace ya shige bedroom dinsa, tsaki yyi ganin hw untidy the room is, wae kuma mace ce ke rayuwa ciki, toilet ya nufa ya wanke baki ya dauro alwala ya fito ya tada sllh, ya jima xaune kan darduma yana mamakin hali na Ajiddeh, hw wil she b insulting his family into his face kuma ya dinga tolerating hka, tsaki yyi a xuciyarsa yace na san maganin ki, mikewa yyi ya shiga toilet don yin wanka, cikin kananun kaya ya shirya bayan ya fito, ya cire bedsheet din kan gadon, ya shimfida sabo, bae tsaya gyarawa ba yyi kwanciyarsa tare da lumshe ido, lkci daya ya bude ido ya mike xaune tuno Batuul da yyi, sauka yyi daga kan gadon ya fita daga dakin ya nufi wanda ya kai ta, tura kofar yyi ya shiga, xaune ya sameta can karshen gadon dakin, ta jingina jikin gadon, kana ganin idonta kasan kuka ta gama, ya wani hade rae yace "Wato ni kike jira in xo in maki sllhn in maki wanka koh, are yhu okay?" A d'an tsawace ya kare maganan yana mata mugun kallo, mikewa tayi da sauri gabanta na faduwa ta fara waige waigen inda xata ga kofar toilet, taji yace "Over there" juyawa tayi tana kallon inda ya nuna mata snn ta karasa ta bude kofar ta shiga, vry neat toilet din me hade da bathroom, sae dae da gani kasan ba a amfani da shi, ba laifi yana da girma ssae, ta dde tsaye toilet din ganin bbu toothpaste bbu toothbrush, bbu sabulu da sponge, a hnkli ta juya a sanyaye ta tura kofan ta fito, dai dai lkcn da shima ya shigo dakin, kallo daya yyi mata ya dauke kai, sabon brush, da toothpaste ya ajiye mata gefen gado, da sabulai da shower gel, sae wani sponge me laushi, da brand new white towel duk lkci daya ya dire su snn ya juya ya fice, karasawa gadon tayi ta dauki wanda xata yi amfani da ta koma bayin, wanka tayi gaba daya bayan ta wanke baki, snn ta dauro alwala ta fito, ta dde xaune kan darduma hawaye na bin kuncinta tana rokon Allah ya yyi mata katanga tsakanin ta da Ajiddeh don har ga Allah tsoronta take ita dae, ko kadan bata ji haushin matsayin da Abuturrab ya bata a gidan ba gaban matar tasa na cewa ita cousin dinsa ce da ta xo karatu kawae, share hawayen idonta tayi tayi murmushi don ita ma ya saman mata saukin bala'in matar tasa, bude kofar dakin taji anyi ta d'aga kai da sauri tana kallonsa, fuska daure yace "ki sakko ki sama ma kanki abun kari" ganin yana tsaye har lkcn yasa ta Mike da sauri ta nufi kofar da dogon farin hijab din jikinta, juyawa yyi ta bi bayansa, a tare suka sauko downstairs sae dae duk a tsorace take, gabanta yyi mugun faduwa ganin Ajiddeh xaune har lkcn a falon idon nan nata duk ya kumbura alaman ba karamin kuka ta ci ba, ko kallon inda take bae yi ba ya nufi kitchen, Batuul kam kanta a kasa take bin bayansa kmr munafuka, Ajiddeh ta bi ta da wani mugun kallo cike da tsana, suna shiga kitchen din duk ya nuna mata food stuffs ba tare da ya kalleta ba yace "Sae kiyi duk abinda kike so," daga hka ya dauki mug ya hada Coffee don akwae ruwan xafi a E.kettle ya fice daga kitchen din, bin sa tayi da kallo a tsorace, kaddae tafiya xae yi ya bar ta daga ita sae Ajiddeh a falon ta xo ta risketa, tunanin hkn ya daga mata hnkli ssae, ta kasa motsi inda take, shi kam yana haurawa sama Ajiddeh ta bi sa da kallo hawaye na bin kuncinta, ita tasan tana son Aliyu tsakaninta da Allah ta rasa ynda xata yi ya xama sae abinda tace masa, ynxu duk kudin da ta kashe asirin nn bae yi tasiri kansa ba lallai da sake dole ta kira mummy ynxu ba da dde wa ba, kallon kofar kitchen din tayi xuciyarta na tafarfasa sae dae tana tsoron shiga ta riske Batuul don tasan Abuturrab xae iya yi mata komae ynda ransa ya baci, mikewa tayi rai bbu ddi ta haura sama tana tunanin mafita don ita kam wllh shegiyar baxata xauna mata a gida ba da sunan karatu ta dinga mata leken asiri, kofar dakinsa ta tura a hnkli ta shiga, kwance ta samesa idonsa lumshe, ta karasa kan gadon ta kwanta faffadan kirjinsa ta saki kukan kissa tace "Don ka ga ina son ka Aliyu shi yasa kke walakantani hka koh, ni bni na daura ma kai na sonka ba Allah ne ya daura min, kuma da xan iya da tuni na cire na huta...." Ta fashe da wani matsanancin kuka, d'ago kanta yyi yana kallon fuskarta da ya wanke da hawaye, ya sauke ajiyar xuciya ya rungume ta yace "Y xa ki dinga fadin bad things about my relative Ajiddeh, ni kuma ba hka nake ma naki ba, yhu are the cause of every fight btwn us, bakya daraja family na Jiddah," shiru tayi tana sauke ajiyar xuciya, a hnkli ya shiga shafa dogon gashin kanta dake ta kamshi, cikin sanyin murya yace "Yhu knw I love yhu babe, yhu are d cause of everything, Batuul will only b here for sometime, snn yarinyar bata da damuwa, nd of course she wil b of help to yhu ke da ba kya son aiki, idan kika sake mata xa ki ji ddin xama da ita, she's a Nyc gal" jin Ajiddeh bata ce komae ba yasa ya d'ago kanta yana kallonta, cikin shagwababbiyar murya tace "Toh shekara nawa ne karatun nata?" Yace "Ban sani ba babe, ni ban ma san me take karanta ba, dad dinta yace yana son ta xauna gun mu tayi karatunta kin ga baxan iya ce masa A'a ba, ni ma kuma burden aka daura min ynxu don dole wani abun na makaranta ni xan mata, don hka ba ke kadae abun nn ya shafa ba har ni babe" shagwabewa ta kuma yi ta shige jikinsa tace "Toh shine xaka nemi tijara ni gabanta babe, har kana....." Bae bari ta kai karshe ba ya hade bakinsa da nata, nn fa suka lula wata duniyar, ya shiga gwada ma Ajiddehn ynda yyi kewarta ita ma hka duk ta rikita shi. Karfe sha biyu saura ta farka daga bacci, ta xame jikinta a hnkli daga nasa don bata son ta tada shi ta nufi bathroom, wanka tayi ta fito ta shirya cikin wasu sheggun kaya irin wanda ta saba sa wa, ta fito dakin ta sauko falo, pizzan dake ajiye har lkcn ta nufa. Batuul kam tsayawa tayi tana k'arewa kitchen ďin kallo, kitchen ne mai girman gaske da yasha kayayyakin aiki sai dai da gani babu maintenance, tafi minti goma tsaye kitchen ďin ko xata ji Ajiddeh ta shigo amma shiru, hkn yasa hnklinta ya kwanta sae dae kuma ta rasa mey zata dafa, ga kitchen ďin duk yayi k'ura, batayi gigin gyarawa ba ta ďauko noodle k'waya ďaya ta buďe fridge nanma taga sausage,babu b'ata lokaci ta ďauko dafa haďaďďen noodles, standing fridge ďin dake kitchen ta buďe ta ďauko ruwa ta fito, ajiyar zuciya ta sauk'e ganin Ajiddehn ta bar falon, da sauri ta haura sama, duk ďakuna a jere suke iri ďaya ta rasa wanne ne ma ta fito daga ciki, hannu tasa zata buďe wanda ke baya ta tuna ai da zai sata bata ga an wuce ko wane ďakin ba, that means na farkon ne, a hankali ta murďa ta shiga turawa, takai seconds uku kamin tasa kai cikin ďakin, ajiya zuciya ta sauk'e ganin batayi mistake ďin ďaki ba, shiga tayi ta zauna ta fara cin abincinta, rabonta da abinci tun kamin su bar gida sai yanxu da take ci, ko a jirgi ma k'in ci tayi, sai a lokacin idonta ya kai kan ďan medium fridge a ďakin, frame ta gani daga samanshi mai kyau manne a jikin bango, hoton Abutturab ta gani da uniform ďin aviation a jikinshi tsaye gaban wani jet yana dariya, yayi kyau a hoton duk da tasan ya ďan jima dan taga girmanshi bai kai yanxu ba, hoton ta k'urawa ido dan bata saba ganin dariyanshi ba, d only time she could rememeber ranan da ya dawo da ita gida ranan da zasuyi prom yaga su Ahmad na tennis, that was d only day taga murmushinshi dan ko ran aurenshi bata ga yana dariya, ďan tsaki taja, toh ita meye nata ma da dariyanshi ynxu matsalarta Ajiddeh, juyawa tayi tana duba ko da wani frame ďin, ganin babu wani ta jawo abincinta da ya ďan huce ta faraci dan dama ba mai cin abinci mai zafi bace, a hankali take ci har ta gama tasha ruwa ta ďau plate ďin ta ajiye kan fridge ďin dan ita tsoron fita take kar taje ta haďu da Ajiddeh, dawowa tayi kan gadon ta kwanta, sai yanxu take jin gajiyar dake jikinta, tunanin rayuwarta ta shiga yi a gidan, da haka har bacci ya ďauketa nan kan gadon. Daukan Pizzan Ajiddeh tayi ta dawo palon ta zauna tareda ciro wayanta dake aljihun wandon dake jikinta, ranta gaba ďaya a dagule yake dan tsakaninta da Allah batason Batuul da gaba ďaya zamanta kusa da mijinta, sai da ta ďauki slice ďin pizza ďaya ta faraci tukunna ta fara neman layin mummy dan a san yadda za ayi, wannan aikin nasu bai ci ba, ringing biyu mummy ta ďaga, mummy ce ta fara magana da "ya dawon?", cikin b'acin rai Ajiddeh tace "Mummy ya dawo, babu abinda ya faru yadda muka tsara, sai ma wani masifan dake son bibiyata yanxu", cikin hanzari mummy ta katseta da cewa "ban ganeba, kina nufin asirin bai yi tasiri ba kome?, kuma masifar mey naji kina k'irawa kanki", kuka ne ya sub'ucewa Ajiddeh tace "Mummy babu wani aiki da bokan nan na Jainaba ya iya, duk k'arya yayi mana ya karb'e mana kuďi dan yanxu haka wata matsalar ce kan ta da", Mummy tace "kece dai kikaje kikayi shirme bakibi abinda malamin yace ba, ko ba munyi dake in ya dawo ke da kanki zakije tarbarsa ba dan ki tabbata yabi takan abun", cikin sheshek'a tace "Mummy ni nace miki nasan zai dawo nema, ina kwance ya k'irani wai sun dawo kuma sai na tabbata duk komai dai", Mummy tace "toh naji, yanxu kuma matsalar mey naji kina cewa na bibiyarki, tace "Mummy sun haďoshi da wannan y'ar iskar mai kama da refugees ďin Ethopia, ni tun farko ai sai da nace muku bana sonta, gashi yanxu wai a gidana zata zauna", Mummy tace "ban gane ba, wai wace yarinyace kike surutu haka akanta", tace "Mum ko ba yarinyar nan ba Batuul, dan munafirci irin nasu da baya k'arewa shine suka haďoshi da ita wai karatu zatayi, kuma a rasa inda zata zauna sai a gida na", Katseta tayi da cewa "nifa ban gane wa kike magana ba akai har yanxu Ajiddeh, wacece ita", tace "Mum wannan yarinyar da yazo da ita a motar da zamu dinner, bayan nan a wajen dinner ta kusa faďi har ya rikota, toh ita fa", mummy tace "ohhh jaraba, toh wannan duk ba matsala bane, su suka sani, mu yanxu tashi muke, indai muka samu mukayi tasiri akanshi ai mun gama da kowa da kowa, wulak'anci kaďai ya isheta har sai ta nemi hostel ko kuma ta koma gidan ubanta karatun, kuma ai suma da nasu gidan a can da sun sata zama ai", Ajiddeh tace "Toh mummy ni yanxu ya zanyi dashi, ni bazan iya da bak'in halin nan nashi ba, ko ďazu inace abu yayi na kama mishi hauka ashe babu abinda yayi toh da naga a hankalinshi yake shine fa na sauk'o, wlhy bakin rai nashi daban yake, i cant take it", Mummy tayi ajiyar zuciya tace "zai bari kizo Nigeria?", kai ta girgiza kamar Mum ďin na gabanta tace "Mummy wlhy ko giyar wake yake sha bazai barni ba, dan ni da kaina nasha faďa mishi ban son zuwa, ko wancan bikin da mukazo nasan da abinda na shuka shiyasa, amma da cikin nutsuwarshi yake da babu inda zamu tunda da bakina na nuna mishi bana son zuwa", Mum tace toh shikenan yanzu zamuyi magana da Jainaba sai muji yadda za ayi, duk yadda akayi zakiji a waya", tace "toh Mummy ki gaida Dad", da haka suka katse k'iran D'aya saura ya buďe idonshi, ganin Ajiddeh bata nan yasan tana ďakinta, tashi yayi ya dafa kanshi tare da sauke ajiyar xuciya at last dae ya shawo kanta ya kuma san ta hakura, mikewa yyi ya faďa toilet ya sakarwa kanshi shower yayi wanka yayi alwala, sai da ya fito ya canja kaya zuwa English wears, k'arfe 1:15 ya gani lokacin, yasan by now ya fara jin yunwa, ďan tsaki yaja tunawa da yayi Ajiddeh ba iya abinci tayi ba, yanxu dole yadawo gidan da xae riqa fita yana nemawa kanshi abinci, tunawa ya sakeyi Batuul na gidan, wani xuciyar yace mishi ai sai ta riqa dafa muku, wani kuma yace mishi yarinyar nan ce zatayi maka girki, baka shirya cin abinci ba knn, ďan tsaki yaja dan itama yanxu wata liability ce, fitowa yayi ya buďe ďakin Ajiddeh don sata tayi sallah dan in ba faďa mata akayi ba toh ba yi zatayi ba akan kari, ganin bata nan ya fito yayi hanyan ďakin da ya ajiye Batuul, kan gado ya sameta kwance tana bacci ta k'udundune waje ďaya a cikin bargo. [8/22, 14:46] Umar Dalha: 💖💝BATUUL💖💝 45 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* K'arasawa yayi bakin gadon yasa hannu zai yaye bargon yaga small figure ďinta na bacci peacefully a ďan takure, kitson da aka yi mata ya rufe rabin fuskanta, d'an tabe baki yyi ya bugi gefen gadon da nufin t'ada ta amma ko motsi bata yi ba, cire bargon yyi lkci daya ta mike xaune da sauri ta shiga komawa baya ganinsa, tsaki yyi yace "Kin ma yi breakfast din kusa?" Kai ta gyada ba tare da ta kallesa ba, yace "Gud, sae ki tashi kiyi sllh ki kara komawa kitchen ki sama ma kanki lunch, don matata bata girki!" Jin bata ce komae ba ya duka kusa da ita har tana iya jiyo numfashin sa da kamshin turarensa da ya cika ta, cikin kaushin murya yace "Hope am clear?" Kai ta gyada masa tana kkrin mayar da hawayen idonta, ya juya ya fice daga dakin. Kwance ya tadda Ajiddeh parlour, kwalin pizza duka uku a buďe an ďan tab'a kowanne, sai apple a hannunta yana kallon Tv, daga gefenta ya zauna ya kamo hannunta yana kallonta yace "shine kika gudo kika barni koh babe", ba tareda ta kalleshi ba don ita kam Batuul ta tsaya mata a rai tace "ai bacci ka keyi shi yasa na dawo nn" murmushi yyi ganin ynda ta basa amsan ya mik'e yace "tashi kiyi sallah toh", dauke kai tayi kawae, kwalin da tayi littering yabi da ido ya kaďa kai ya koma sama, yana idar da sallah ya koma gaban desktop ďin dake ďakinshi, buďewa yayi yana dudduba sak'onnin da aka turo mishi, yawanci daga office ne sai na k'arshen ne ya gani daga Sadiq, sai da ya gama buďe na office ďin tukunna ya buďe wanda Sadiq ďin ya turo mishi, tsayawa yayi ya gama karanta abinda yake ciki tukunna yayiwa sauran reply sannan ya kashe ya ďauki wayanshi ya shiga neman layin Sadiq, Sadiq na ďauka yace "Yo bro, kun isa lafiya", Abu yace "Sallama kenan", kai Sadiq ya sosa kamar yana gabanshi yayi sallama, Abu ya amsa yace "Yeah naga ka turomin abu ta email, Sadiq yace "Ehh Abui ne yace in turo maka, acceptance letter Batuul into London University of Economics ba?", Abu yace "tun yaushe aka nema mata admission ďin, like everything is so fast kuma tana da wannan k'ok'arin ne na karatu a can ne ma?", dariya Sadiq yasa yace "Yaa Abu dont estimate Batuul, yarinyar nada kok'ari sosai, ai sai da akayi issuing transcript ďinta suka bata admission toh kaga they are satisfied with her perfomance", yace "Fine naji, sai anjima ka gaida gida", Sadiq yace "Okay bro, a gaidamin Batuul da sis Ajiddeh", yace "zasuji", daga nan ya katse k'iran, duk da yana son jin muryar Ammah bae kirata ba don bae son ta d'aga masa hankali da xancen Batuul. Kan abin sallah ta zauna tayi jigum bayan ta idar da sallah, akwatinta da wayarta ke ciki ta hango daga gefe, bata san ma ko yaushe aka shigo dashi ba, da murna ta tashi ta isa ta buďe akwatin, wayarta dake ciki ta ciro ta kunna, ganin layin dake ciki yasa jikinta yin sanyi ta koma bakin gadon ta zauna, yanxu sai ta sayi sabon layi kenan, ďan tsaki tayi ta jefa wayan kan gado, tana missing gida, tana son tayi magana da Aunty da kowa ma, hawaye ne ya fara gangarowa daga idonta, tunanin roaming ne ya faďo mata, da hanzari ta mik'e tana dariya ta ďauko wayar daga kan gado, babu b'ata lokaci tayi roaming, da murmushi a fuskanta ta shiga dialing Aunty, kamar jira akeyi aka ďauki wayan, da murna tace "Hello Aunty ina kwana", ajiyar zuciya Aunty ta sauk'e daga ďaya b'angaren har Batuul na jiyowa tace "Lafiya Batuul, halan yanxu kika tashi daga bacci naji kina kwana", dariya Batuul tayi tana goge hawayen idonta tace "A ah Aunty, garin ne kamar safiya shiyasa nace kwana, yanxu nayi azahar ma", Aunty tace, "yayi kyau Batuul, tun ďazu ma muke trying number ki baya shiga, Su Mahir sai damuna suke a k'ira musu ke", kukan dake shirin fitowa ta maida jin abinda Aunty ta faďa mata tace "Allah sarki Aunty suna ina, a basu mu gaisa", Aunty tace "sunyi bacci Batuul tun ďazu, sai dai gobe in basu ku gaisa", kai ta kaďa kamar Aunty na ganinta, Aunty tace mata "Batuul kun isa lafiya babu matsala ko, ina y'ar uwar taki", wani iri taji maganan Aunty, wai har itama cewa take Ajiddeh y'ar uwartace, dan batasan mey ya gama faruwa bane bama yau da safe, sai da Aunty ta sake maimaita tambayan jin tayi shiru, a hankali tace "Aunty tana lafiya, ai tana ďakinta", Aunty tace "yayi kyau Batuul, in kin huta zamuyi waya kinji, inason muyi magana", Batuul tace "Toh Aunty, Baba fa, yana gida?", Aunty tace gashi nan Batuul, tayi rau rau da ido tace "Aunty shine baice zaiyi magana dani ba", Aunty tayi dariya tace "ai gashi nan faďa mishi da kanki", kamar zatayi kuka bayan Aunty ta mik'awa Baba wayan tace "HellO Baa, nda dubdo", da murmushin shi na manya yace "Mamana nda dubdo, ya sabon waje", a hankali tace "Baa Alhamdulillah", yace "Masha Allah Batuul, Allah yayi miki albarka, ki kula da ibadunki, ki girmama na gaba dake kinji, babu ruwanki da tsokana ko tadawa mijinki hankali, ki zama mai biyayya kuma kiyi ta hkuri kinji, Allah ya taimaka", tana kuka da k'yar ta iya buďe baki tace "In sha Allah Baa, nagode", da haka suka katse k'iran, kuka sosai ta sa bayan sun gama wayan, shikenan rayuwanta ya canja kenan, ta dde xaune ganin yunwa ya dameta don har uku na rana yyi yasa ta mike a hnkli da Hijab jikinta ta tura kofan dakin ta fito, downstairs ta nufa a xuciyarta tana addu'an Allah yasa Ajiddeh bata nn, xaune ta sameta falon tana kallo tana cin sauran pizzan ta, duk irin faduwar da gabanta yyi hkn bae sa ta koma ba, cikin natsuwa ta tako har cikin falon ta kalleta a hnkli tana ci gaba da tafiya tace "Ina yini Anty?" Wani matsiyacin kallo Ajiddeh ta bi ta da shi har ta shiga kitchen din, snn ta mike, sae da ta fara kallon stairs snn ta bi ta cikin kitchen dib, Batuul na tsaye tsoro ya cikata don xuciyarta ya bata sae ta biyota, lallai tayi gangancin sakkowa Ajiddeh na falo, daga bakin kofa ta tsaya tana kallonta tana murmushin rainin hankali tace "Ke a tunanin ki kin samu gun xama a gidana koh? To yhu are mistaken yarinya, don sae kin gwammace da baki shigo gidana da sunan xama kiyi karatu ba, banda kinibibi, gulma, da munafurci irin na iyayen ki sun san basu da halin kama maki hostel me xae kai su karambanin turo ki UK karatu, shine xa a wani xo a daura ma miji na nauyi da wahala to wllh kun yi kadan, duk uban da ma ya kawo wnn shawarar zae saketa ne, don sae sai kin gwammace da titi kike kwana kan gidana, makwadaita kawae" Ae Batuul bata san lkcn da ta fashe da kuka jin xagi da cin fuskar da Ajiddeh ke ma iyayenta, ita din ba mai son fada bace bare ta mayar mata da martani, durkushewa gurin tayi ta dinga kukan takaici da tausayin rayuwarta, ran Ajiddeh yyi fari don har da murmushinta, ta cigaba daga inda ta tsaya. Abuturrab kam na daki kan system wayarsa ta hau kara, dauka yyi ganin Ammah yasa shi saurin d'agawa da sallama, Ammah tace "Abu kun isa lafiya, shine ba kira?" Yyi k'asa da kai yace "Kiyi hkuri Amnah ynxu nake da niyar kiran ki, gajiya ne yasa hka", Ammah tace "Shknn Babana, ina Ajiddehn, kun sameta lafiya", yace "Alhamdulillah Ammah she is doing good", tace "toh Abu, bazan gaji da yi maka Nasiha ba, ka kula dasu ka zauna tsakaninka da Allah dasu, Allah zai tayaka rik'on indai niyyanka is pure, sannan Fatima yarinyace k'arama, hankali bai gama game ta ba, in ka cuceta akan matarka, toh Allah sai yayi mata sakayya, kaji tsoron Allah Abu, kuma makaranta Abui yasa Sadiq ya turo maka, in ka duba kaje kayi mata necessary abubuwan da duk ya kamata" sai da yaji tayi shiru tukunna yace "In sha Allah Ammah nagode, Allah ya k'ara nisan kwana", ta amsa da "Amin, Allah yayi muku albarka, bata wayan inyi magana da ita", yace "Ammah tana ďakinta, sai dai in kai mata", tace kai mata ina jira", yace " Toh xan kira ki" daga hka ya katse wayar ya fita yayi hanyan ďakinta, ganin bata ciki yasa ya sakko falo, tsayawa yyi daga stairs hango Ajiddeh da yyi tsaye kofar kitchen din don yasan ba arxiki ya kai ta ba, Karasowa yyi Ajiddeh na hango sa tayi tsit daga cin fuskar da take ma Batuul cike da faduwar gaba, shiga kitchen din yyi yana kallon Batuul dake durkushe har lkcn a kitchen din tana kuka, Ajiddeh ta juya ta bar bakin kofar da sauri ya bi ta da kallo, murmushi yyi yana kallon Batuul dake kuka kmr xata shide yace "Yhu see! Kinga abinda nake guje maki knn, kika rufe ido kika ce sae ni, don hka yhu have to endure duk me xa ki fuskanta daga matata tunda kika ce kin ji kin gani...." kallonshi tayi da idonta da yyi jajir ta mike da kyar ta fice daga kitchen din hawaye na bin kuncinta, murmushi ya shiga yi yana jujjuya wayar hannunsa, wayar ya fara ring, sae a snn ya tuna abinda ya sakko da shi, xaro ido yyi ya bar kitchen din da sayri ya hau sama ya nufi dakinta, kwance ya sameta tana kuka ssae, ya karasa gadon ya xauna yana kallonta yace "Wae kukan me kike ma mutane hka daga an gaya maki gskya" kin cewa komae tayi, ya kalli wayar hannunsa jin ya katse, yasan Ammah ba hakura xata yi ba, sake bugowa tayi, ya ajiye wayar ya dago Batuul ya daura hannu kan kafadarta ya runtse ido yace "Alryt! Kiyi hkuri" ko kallonsa bata yi ba kuma bata daina kukan da take ba, a tsawace yace "Nace kiyi hkuri" ae sae ta kuma fashewa da kuka, rungumeta yyi ba tare da yyi wani tunani ba, yana patting bayanta a hnkli kmr me rada yace "Am.. am srry" ita kanta ta rasa dalilin da yasa ta tsaida kukan nata sae ajiyar xuciya da take saukewa, tana jikinsa ya jawo wayar da har ya katse, sae ga shi Ammah ta kuma kira, d'agawa Ammah tayi cikin fada tace "Walakanci ne hka Abuu?" Yace "Kiyi hkuri Ammah tana bayi ne, gata" kara wayar yyi a kunnenta yana rungume da ita, jin muryan Ammah yasa hawaye sake gangarowa a hnkli cikin sanyin murya tace "Ammah ina wuni", Ammah tace "Lafiya lau Bitti, ya gajiya, duk gajiyan ne naji muryar ki hka", kallon fuskarta Abuturrab ke yi kawae, tana sharen hawayenta tace "Alhamdulillah Ammah, babu gajiya ya su Abui da Farida", Ammah tace "suna lafiya Bitti, babu dai matsala ko", kai ta ďaga tana kallon Abu da suna haďa ido ya kuma mannata jikinsa, jiki a sanyaye tace "Ehh Ammah babu komai", Ammah tace "haka nake son ji dama, kiyi hak'uri sosai kinji Bitti, sai kiga komai yazo miki da sauk'i, makarantarki ma soon zaki fara zuwa kinji, ki manta da komai kiyi abunda ya kaiki, as i told you, don't hesitate in telling me your problems kinji, koh na meye", kai ta gyaďa kamar Ammahn na ganinta hawaye na xubo mata tace "Toh Ammah zanyi nagode", tace "Yawwa Bitti", daga haka ta mik'awa Abu wayan, ji tayi yace "Yeah gobe Monday zamuje a gama processing komai, sai Anjima Ammah mun gode", ita kam Batuul bata ďago ta kalleshi ba sae kkrin janye jikinta daga nasa da ta shiga yi amma ya ki saketa, cikin kakkausar murya yace "Wae ma kukan mey kike yi ma mutane daga an fada maki gskya,", sake fashe mishi tayi da sabon kukan takaici, lumshe ido yyi yana murmushi, lkci daya ya bude ido ya dafa kafaďunta yace "okay naga alamar kina son hada ni da Ammah ne, today shud b the last time da xa ki min kuka a gidana, its not going to b good for you idan na sake ganin kin yi hka, ba gidan ku bne nn, tunda kika zab'i aurena yhu have to endure everything yhu will come across" Shiru Batuul tayi tana saurarensa, duk taji yace ita ta xabi aurensa sae ranta ya baci, ido yabi fuskanta dake jik'e da hawaye, ďan k'aramin lips ďinta ya koma ja, yace "clean your face and hear me out", a hankali tasa hannnu tana goge hawayen, sai da ta gama yace "nasan dai kinsan zancen komawanki makaranta, gobe zakije a fara komai, it doesnt mean komawanki makaranta zaisa kiyi min yawo a gida ba, am not tolerating that, sannan babu ruwanki da matata inba girmamawa ba i cant take duk wani raini da zakiyi mata, ban yadda ki rainata ba, sannan ban yadda da tarkacen k'awaye ba, not in my house, abinda ya kaiki shi zakiyi ki dawo, inma zakiyi toh ya tsaya daga can makaranta, in kuma baki yadda da all i said ba, try me and see what will happen", har sai da taji yayi shiru tukunna ta janye daga rikon da yyi ma kafadunta tace "ai dama nasan you are always against my happiness, you snatched it all away from me, kuma da kake cewa kar in raina matarka ai nima duk sunanmu ďaya da ita, am also your wife kammar yadda kace an lik'a maka ni, and as it is, zan ďauki komai daga wajenka but not from her ka ja mata kunne bbu ruwanta da ni, kar ta kuma involving iyayena a abunta yawo kuma ba halina bane, k'awaye kuma, nobody can live in isolation, ba kowa na sani ba,", cikin k'arfin hali tayi duka wannan maganganun dan idonta rufe tayi duka wannan maganan, chest ďinta sai heaving yake, tsaf ya gama kalleta yana kallon yadda zuciyanta ke bugawa, dariya ta kusa bashi, a hankali ta buďe idonta, cikin hanzari ta tashi zata gudu dan sai yanzu maganganun da tayi suke dawo mata, hannu yasa ya fincikota jikinshi, a tsorace tace "Ni ja kyaleni xan hada ja da Ammah" sake janyota yayi jikinshi daidai kunnenta ya sunkuyo yace "fine if thats what you actually said, just try me and see", jin sauk'ar numfashinshi a wuyanta yasa duk tsigar jikinta tashi, kan gadon ya jefata ya juya xae fita daga ďakin, daidai bakin k'ofa yana fitowa suka ci karo da Ajiddeh ta shiga masa wani kallo, bai ce mata komai ba yayi tafiyarshi, da ido tabi k'ofan ďakin sannan tabi bayanshi da ido, hankali tashe tayi hanyan ďakinshi itama, ae ko baxa ta yi tolerating wnn ba. [8/22, 14:46] Umar Dalha: 💖💝BATUUL💖💝 46 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* A hargitse ta tura k'ofan ďakin, yana kwance kan gado ya lumshe ido kamar ba shine ya shigo yanxun ba, dai dai kanshi tazo ta tsaya tana huci, ranta b'ace har wani gumi takeyi ta shiga yi masa magana, "Aliyu nifa bazan yadda da wannan abinda kuka tsira ba, wlhy ni bazan yadda da zamanta ba a cikin gidan nan, inma kai baza ka iya faďawa iyayenta baka son zamanta gidanka ba sai ka kama mata hostel ďin da kanka kawae, amma ba dai tayi ta zama min a gida ba dan dama nasan munafirci ya kawota", sai da yaji tayi shiru tukunna ya buďe lumsassun idanunshi dake rikitata yace "tunda gidanki ne sai ki koreta", ido ta wara tana kallonshi hawaye na bin kuncinta, cikin rashin damuwa da hawayen nata yaci gaba da cewa "tsabar rashin hankali da rashin sanin ciwon kai shine ki kaje kika tsareta a kitchen kina gaya mata maganganu koh, toh duk kika yrda ta raina ki baxa ki ji da dadi ba kuma bbu ruwana baxan kuma ce mata don me ba ", hankalinta ne ya k'ara tashi wai yau ita Abu ke k'ira mara hankali akan wata can y'ar iskar, wlhy Allah sai tasan yadda tayi da Batuul, sai ta wulak'anta ta fiyeda tunaninta, k'wafa tayi ta juya a fusace ta banko mishi k'ofar ďakin a xuciyarta tana cewa xaka rashin hankali kuwa, tabe baki yyi ya sake lumshe idanunshi ya gyara kwanciya yana shak'ar k'amshin Batuul da ya mannne mishi a kaya da yayi hugging ďinta. Tana fita ďakin tayi hanyan ďakin Batuul a fusace kamar wacce zata tashi sama, kai tsaye ta tura k'ofar ďakin da Batuul ke ciki, tana zaune kan gadon a takure ta haďe kanta da guiwa, bata ďago kanta taga ko waye ba dan tasan shine ya dawo, ji tayi ance "tashi ki fita dan ubanki tunda ba ubanki ya gina min gidan ba", a tsorace Batuul ta ďago tana kallonta da mamaki shimfiďe a fuskanta, gani tayi tana k'ara shigowa ďakin, da sauri Batuul ta mik'e tana kallonta, inda akwatinan ta ke ajiye Ajiddeh ta nufa ta ďauka tana watsarwa, a tsorace Batuul ta tsaya tana kallonta, hawaye ya taru a idonta, ita wane irin masifa ne wannan yake tunkarota ko kwana daya bata yi ba, hawayen dake k'ok'arin zubo mata ta maida ta sauk'o daga kan gadon tana ganin yadda Ajiddeh ke watsar da kayan tayi hanyan waje, wai wannan ma fa dan bata san matarsa bace ita, hanyan waje tayi zata fita daga ďakin, hannu Ajiddeh tasa ta rik'ota tana cewa "ga y'ar iska na miki magana koh, toh dan ubanki kisan inda dare yayi miki dan gidana ba gidan ajiye y'an iska karuwai bane", ido Batuul ta rintse jin abunda Ajiddeh ta kirata dashi, zata iya rantsewa gaba ďaya rayuwanta bata tab'a jin an ambaci wannan word ďin a gidansu ba wai sai yau gashi ita ake k'ira da word ďin, hawayen dake idontane ya shiga gangarowa, hannunta tasa ta goge fuskanta, tasa hannu ta murďa k'ofan zata fita, wani irin force taji Ajiddeh ta tunkuďata dashi , ido ta rintse tana k'iran sunan Allah lkci daya ta fasa ihu tana jiran jinta a k'asa, amma ta ji akasin hka don jikin mutum ta faďa baya tayi zata faďi yayi hanzarin rikota ya rungumeta, shigewa jikinshi tayi tana boye fuskanta a kirjinsa, sai a lkcn ta fashe da kuka jikinta na rawa tsabar tsorata da tayi, kuka sosai ta shigayi tana cewa "Yaa Abu dan Allah ka maidani gida, dan Allah inaso inga Aunty, hannu yasa ya daďa haďe jikinsu dan yasan tsorata tayi ba da wasa ba, neman kukan da takeyi tayi ta rasa jin kanta faffaďan k'irjinshi, sai da yaga ta fara nutsuwa sannan ya saketa yana kallon fuskanta da hawaye ya gama wankewa, saketa yayi ya matsar da ita gefe ya zaunar da ita kan kujeran dake tsakanin ďakunan biyu, mutuwar tsaye Ajiddeh tayi ganin Aliyu ya kare Batuul, sam ba haka taso ba, taso koda Batuul bata mutu ba ta nakasa ta in yaso iyayenta suzo su ďauketa amma wannan jarababben ya taimakota, juyowa yayi ya shigo ďakin yanayinshi da ta gani ne ya sata tsorata, baice mata komai ba yasa hannu ya rik'o hannayenta tana binshi a baya kamar wata doluwa yayi ďakinshi da ita, kallonsu Batuul tayi hawaye cike idonta, ita dama tasan abin tausayi zata zama a gidan nan, duk abin nan da matarsa tayi baice mata komai ba sai ma rikota da yayi su tafi abunsu, kuka sosai ta kifa kanta kan cinyarta tanayi, sai sunan Aunty take k'ira da Baba, yana shiga ďakinshi da ita ya sake mata hannu, magana ta fara mishi cike da masifa "wllh Aliyu yarinyar nan ta barmin gidana dan....." bai bari ta k'arasa maganan ba ya wanka mata mari lafiyayyu guda biyu, a gigice ta ďago kanta da idonta da ya rine yayi ja tana kallonshi, wani shegen murmushi ta saki tana hawaye tace "koh baka dakeni ba nasan karuwarka ce ko daga yadda ka rik'eta a jikinka, ni za a yiwa bariki a wani ce karatu tazo yi, munafiki kawai azzalumi, Kuma wlhy kaji na rantse sai na illatata, mugu kawai.....", wani irin fixga da yayi mata yasa ta kasa k'arasa maganan da takeyi, idonshi ya sake yin jaa, yana kallonta yace "ai ke gidan na ubankine koh, dan bakida hankali kashe y'ar mutane zakiyi xa ki hankaďata hka, kinsan zaki iya barin gidan nan ita ta zauna, jahila kawai wacce bata aiki da hankalinta, kika sake min shirmen nan a gidana sai na b'ata miki yadda baki zato ba, mahaukaciya jahila", yana kai wa nn ya jefar da ita ya fice daga ďakin, inda ya barta kan kujeran nan ya dawo ya sameta sai kuka takeyi, ce mata yayi "kukan mey kike ma mutane ke kuma har ynxu", bata ďago ta dubeshi sai kukan da ta ci gaba dayi, cikin tsawa ranshi b'ace yace "ba magana nake yi miki ba", rinannun idanunta ta ďago ta kalleshi cikin sanyi hawaye nata zuba tace "Yaa Abu dan girman Allah da Annabinshi ka mayar dani wajen Aunty", hararanta yayi ya kamo hannunta, komawa tayi baya da sauri ta janye hannunta, tsayawa yayi yana kallonta yace "you thought all i was telling is lie huh, gashi nan kin fara gani tun ba aje ko ina ba, its just your first day and you have already faced soo much, sai da na faďa miki babu ruwanki da ita, mesa kika nemi magananta", haushi ne ya cikata ta tsananta kukanta tabi ta gefenshi zata shige ďakin yayi saurin rik'ota, wayantane taji yana ringing, fixge hannunta tayi tayi ďakin, bayanta yabi a hanzarce, hannu yasa ya rigata ďaukan wayan yana kallon mai k'iran, Affan ya gani rubuce in bold da hrt emoji daga gaban, kin bata yayi har sai da wayan ta katse, batare da ya kalleta ba ya jefa wayan kan gado, tsayawa tayi tana kallonshi , Juyawa yayi yana k'arewa ďakin kallo yadda kayanta ke zube a k'asa, ce mata yayi "da kika zauna kina yiwa mutane kuka waye zai tattare miki kayan da aka zubar garin neman faďanki, kinsan baki da k'arfi kika nemi tsokananta", bata ce mishi komai ba ta nemi waje ta zauna daga bakin gadon tare da janyo wayarta, dubawa tayi taga wa ya k'irata, ganin Affan ne ya sata ajiyan Zuciya, cikin kakkausar murya yace mata "ba magana nake yi miki ba, waye zai tattara miki kayan", zumb'uro bakinta tayi ta juya tana gyara zamanta kan gadon tace "Ai ba ni na zubar ba, suna zamansu ta shigo ta watsar, a k'irata ta gyara mana", da mamaki ya ke kallon yadda take mishi magana, matsowa yayi gaban gadon, da sauri ta shige cikin bargon tana cewa "nikam in ka tab'ani zan faďawa Ammah", ce mata yayi "tashi ki tattare kayanki", ba musu ta yaye bargon ta taso ta shiga kwashe kayan, juyawa yayi zai fita daga ďakin, har yaje bakin k'ofa ya juyo yace "kin nemi abinda zaki cin ko kuma baki gama jan maganan ba", ganin batace mishi komai ba ya fita daga ďakin ya barta anan Tana zaune ďakin har k'arfe 8 ďin dare, ga yunwa da ya addabeta, tsoron fita takeyi dan batason ko sake kallon Ajiddeh tayi, ta rasa mey zatayi kuďin wayarta ma ya k'are da ta k'ira ko su Aunty taji daďi, Affan ďinma da ya k'ira ďazu yaki k'ira har yanxu, tashi tayi ta shiga toilet tayi wanka tayi alwala ta tada sallah isha, sai da ta idar ta gama addu'anta tasha kuka ta tashi ta hau gado ta kwanta bayan ta kashe wutan, ta gwammace ta kwanta da yunwa da ta fito su haďu da Ajiddeh, jin an murďa k'ofan ďakin yasa ta k'ara tsorata, a hankali ta sauk'o daga kan gadon zata shige toilet taga haske ya gauraye duka ďakin, tsayawa tayi a tsakiyan ďakin ta kasa motsi, k'arasowa yayi cikin ďakin ya ajiye mata daya ledan dake hannunshi yace "in kin gama tsayuwan naki ga abinci ki ďauka kici, you get ready gobe by 11 zan kaiki school and mind you kina rufe k'ofar ďakinki da makulli", wani irin ajiyar zuciya ta sauk'e jin shine, bata juyo ba har ya gama maganan da zaiyi sai ji tayi an juyo da ita, "kina jina ina magana kika min shiru, na fara wasa da ke koh", a hankali tace "Ai naji", saketa yayi ya juya ya fita daga ďakin tare da kashe mata wuta. Dakin Ajiddeh ya nufa rike da wani ledan ya murda kofar ya shiga, xaune ya sameta can karshen gadonta idon nn nata ya kumbura tsabar kuka, ya ajiye ledan hannunsa tare da sauke ajiyar xuciya ya nufeta, tana ganin hka ta mike da sauri xata bar wajen yyi hanxarin rikota tare da hade ta da jikinsa, ta fashe da kuka tana dukan kirjinsa tace " let me be Aliyu, ka kyaleni, 1st thing tomorrow morning am leaving yhur goddam house, with or without my divorce prove, bna auren kuma, ae ba kai kadai bne namiji a duniya, sae ka xauna da 'yar uwar taka....." Ya runtse ido yace "Stop this Jiddah, yhu pushed me into behaving the way I did, meyasa baki saurarata ne wae, na gaya maki Batuul is only here for sometime, karatu ta xo yi tana gamawa xata koma Nigeria, I love yhu Jiddah bana son duk abinda xae bata maki rai, had it been we are not this close da iyayen Batuul da baxan yrda da xaman ta gu na ba coz it's also a burden to me, plss nd plss Ajiddeh kiyi hkuri ki bar ta tayi karatun ta, her being here is nt for ever, if yhu love me do me this one favour pls babe," tsuke fuska tayi ta kauda kai, ya marairaice yace "Plss babe!" Kuka ta fashe da tace "Shine xaka mareni Aliyu" ya kuma rungumeta yace "Ohh! Am srry babe sharrin shaidan ne plss, idan kuma baki hakura ba ki rama" shiru tayi bata ce komae ba, kissing wuyanta ya shiga yi a hnkli yace "Say something mana babe" lumshe ido tayi don kiss din Aliyu na rikitata, cikin sarkewar murya tace "Naji" bae daina abinda yake mata ba yace "kin amince ta xauna gidan ki har ta gama karatun?" Runtse ido tayi tace "Yeaa!" Yace "Promise!" Da kyar tace "I do love" Kiss din bakinta ya shiga yi passionately tana mayar masa da martani, kan kace me sae ga su kan gado. [8/22, 14:47] Umar Dalha: 💖💝BATUUL💖💝 47 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Yana fita Batuul ta sauk'e ajiyar zuciya ta dawo kan gadon ta zauna, wayarta ta ďauka ta haska ledan da ya ajiye mata taga tambarin Mc donalds a jiki, ďan tsaki taja dan bata cika son abincin Mc donalds ba, amma tunda yunwa takeji babu yadda ta iya haka zataci, janyo ledar tayi ta shiga buďewa, kwalin chips ne a ciki sai chicken wings da dip in sauce, sai wani cup da aka sa strawberry shake da ruwa da pine apple drink, kaďan taci chips ďin, shake ďin kawai tasha da ďan yawa ta tashi ta ajiye sauran da bataci ba kan fridge, toilet ta koma tayi brush ta fito ta kwanta, tafi awa a kwance amma bacci ya k'auracewa idonta, hawaye ne ya fara zirara a idonta, she have never been this lonely gaba ďaya rayuwanta, dukda ba mai son surutu bace tafi son zama ita kaďai amma na yau ya dameta, ko ba komai a gida tana jin motsin y'an uwanta, amma yau hakan ma ya gagareta, tunanin gidane ya sata fashewa da kuka, wayanta ta janyo tana ganin hotunansu da shirmen da sukeyi, tanayi tana kuka wani kuma tayi dariya, tana nan zaune har k'arfe uku, yadda taga rana haka taga dare, gara ma da rana ta ďan samu ta rintsa, amma yanxu baccin ma ya k'aurace mata, tashi tayi taje tayo alwala, sai da tayi nafilfili tukunna tayi karatun Qur'ani a wayanta, tana nan zaune kan abin Sallah har asuba, tana idar da sllh taji wani irin bacci na fizgarta, nan kan abin Sallah ta gyara tayi kwanciyarta, tana kwanciya bacci ya kwasheta, cikin baccinta kamar a mafarki taji k'aran buďe k'ofarta, a ďan tsorace ta tashi ta zuba mishi lumsassun idanunta , k'arsowa yayi cikin ďakin yana binta da kallo, sai da ya shigo tsakiyar ďakin ya tsaya yace "wane irin bacci kikeyi anata knocking baki buďe ba", juyawa tayi ta duba inda ta ajiye makullin ďakin taga yana nan, k'ofan ta sake kallo taga shima da makulli mak'ale a jiki, cikin tsawa yace mata "ba magana nake miki ba, ko bakiji lokacin da nace miki ki shirya zan kaiki school bane kika kwanta kina bacci", sai lokacin ta lura da kayan jikinshi taga har ya shirya zuwa farin shirt mai stripes ďin bak'i da bak'in wando, windown ďakin ta duba taga har rana na fitowa ta kalleshi taga ita yake kallo har lkcn, ta ďauke idonta tace "ai bacci ne ya ďaukeni bansan safiya tayi ba", ta faďa tana zumb'uro baki, k'wafa yayi yana kallonta yace "get ready and come down in the next 15mins", daga haka ya juya ya fita daga ďakin, tab'e bakinta tayi a ranta tace masifaffe, daga haka ta cire dogon hijabin dake jikinta da rigar baccin ta shiga wanaka, ko minti biyar batayi ba ta fito daga toilet ďin bayan tayi brush, akwatinan kayanta ta buďe ta shafa mai ta ciro wata doguwar riga blue mai dogon hannu ta saka, chappette kawai ta shafa a lips ďinta ta taje gashin kanta sannan fesa turarukanta masu dadi'n k'anshi ta shafa, a hankali take sauk'owa daga stairs ďin har ta k'araso cikin palon, yana zaune kan ďaya daga kujerun palon, Ajiddeh na jikinshi sanye da wasu shegun kayan bacci da ya bayyana duk jikinta, ita ta fara hango Batuul, wani irin harara ta sakar mata kamar idonta zai zazzago ta k'ara shigewa jikin Abu dake k'ok'arin canja channel, cikin raďa tace mishi "baby i dont want you to leave", tana yi tana kissing wuyanshi, shima janyota yayi yace mata "dont you worry, i will b back for you, kinga school zan kaita ta fara processing", ita kam Batuul ko kallon inda suke batayi ba tazo ta wuce su zata fita waje, sai a lokacin ya ganta, da ido ya bita har ta fita daga palon sannan ya mik'e yana kallon Ajiddeh yace "Baby ki kula da kanki", ya manna mata kiss a bakinta, hade rae tayi tace " Babe ko gaisheni fa bata yi ba ta wuce" yace "ni din ma ae bata gaishe ni ba, kyaleni da ita" daga hka yayi waje, a bakin k'ofan palon ya tarar da ita tana tsaye, yace "Go back nd greet my wife" daga kai tayi tana kallonsa, ya hade rae yace "Do dat fast my frnd" juyawa tayi a hnkli ta koma falon, tsakiyar falon ta tsaya ba tare da ta kalli Ajiddeh ba tace "Ina kwana" a sanyaye tayi gaisuwan, Ajiddeh ta wurga mata hararan tsana tace "Da ban kwana ba kya gan ni, munafuka 'yan maula" Juyawa Batuul tayi ta bar falon ta fita waje, har lkcn yana tsaye inda ta bar shi, ba tare da ya kalleta ba yayi wucewar shi garage ďin gidan, tana nan tsaye ya fito da wata dank'areriyar Benz, a hankali take k'arasowa inda motar take ta buďe gidan gaba ta shiga, k'anshin turarenshi ne ya cikata, juyar da kanta tayi tana kallon wajen glass, bai ce mata komai ba yaja motar ya ďau hanyar makarantan, tafiyan minti goma suka isa k'ofar makaranta sae a snn ya juya ya kalleta yace "yhu look for wat to take for breakfast a sch din," ko kallonsa bata yi ba wani irin farin ciki ya ziyarceta ganinta a k'ofar university da kullum take mafarkin zuwa tayi karatu, batasan lokacin da murmushi ya sub'uce mata ba tana kallon yadda students kowa na aikin gabanshi, jin sautin murmushinta da yasa gefen kumatunta lotsawa ya bayyana dimple ďinta ya sashi juyowa yana kallon yadda take murna, yau ne rana ta farko da ya fara kallonta tana dariya haka, driving yake amma gaba ďaya hankalinshi na wajenta har ya iso gaban wani building yayi parking motarshi, sai a lokacin ta juyo da murmushinta ta kalleshi taga shima ita yake kallo, hararanta yayi ya buďe motar ya fito, ita dai bata fito ba dan baice mata ba, har ya fara tafiya yaga bata fito ba tana cikin motar a zaune, rai b'ace zagayo ya buďe mata k'ofan yana mata mugun kallo yace "zaman mey kikeyi da baki fito ba", baki ta zumb'uro ta sa k'afanta a waje, ita batada lokacinshi dan ji tayi duk bak'in cikinta ya yaye, k'wafa yayi ya juya yaci gaba da tafiya, biyoshi tayi a baya har lokacin da murmushi fuskanta, har sukazo k'ofan shiga wani office sannan ya juyo yana kallonta rai a haďe, haďe dariyanta tayi ganin yadda yayi kicin kicin da fuska sannan ya tura k'ofan ya shige, a sanyaye itama ta shiga a ranta tace masifaffe kawai, nidai yau is my happy day banida time ďin kowa ta shige cikin office ďin itama, Office ďin ta k'arewa kallo, an manna hotunansu su Adam smith, Alfred Marshal, David Ricardo, J.S mills da sauran manyan economists ďin duniya, wani bature ne zaune kan kujera a office ďin, da gani shekarunshi zasu kai 60, dogo sannan yana da jiki, hannu ya mik'awa Abu yace "Mr Kyaree you are welcome", baki ta kyab'e jin har sunanshi ya sani, juyowa yayi yana kallon Batuul yace "You can sit down madam", yayi mata nuni da kujeran gefen Abu, kallon Abu tayi taga shima kallonta yake da lumsassun idanuwanshi, kujeran ta jawo ta zauna, tana zaune suka gama maganganun da zasuyi, mutumin ya ďago yana kallonta yace "Mrs Fatima are you single?", question ďinne ya zo mata bazata, ta ďago tana kallon Abu dake danna wayarsa, a hankali ta ďauke kanta ta kalli mutumin da taga sunanshi Stephen xata yi magana ta ji Abuturrab yace "No! She's nt, she's married" kallonsa tayi sae kuma ta sunkuyar da kai, mutumin yyi murmushi yace "Dat's Gud, yhu are welcome to London University of Economics Mrs Fatima kashim Goni" murmushi Batuul tayi jin ynda yyi pronouncing sunan nata, nan Mr Stephen ya shiga yi mata bayanin abubuwan da ya kamata, shi dae Abuturrab danna wayarsa kawae yake, sun kusa minti ashirin office din bayan ta cike wasu forms din da ya bata ta kuma yi signing kafin ya dauko ID dinta na makarantar ya bata, ya kuma yi mata maraba snn ya mika mata timetable da wasu textbuks har uku yyi directing dinta zuwa dept dinta, godiya tayi masa tana murmushi, Abuturrab ya mike ya kuma yi masa godiya mutumin ya basa hannu snn suka fita office din, bin bayansa kawae take farin ciki shimfide fuskarta, da alama ya san kan makarantar sosae ganin ynda yake tafiya with courage abunsa kuma short cut yake bi, xaro ido tayi da ta tuna ae shi ma makarantar yyi if she remembered rightly, ko kadan bata damu da ynda ya hade rae ba farin cikin da take ji a lkcn baxae ma bari ta damu da hkn ba, jefi jefi tana ganin bakaken fata kmr su suna wucewa, har gaban dept din ya kai ta, wata baturiya ce ke tafiya rungume da litattafenta, ya karasa inda take yace "Excuse me Ma'am!" D'an kallonsa tayi tace "Pardon?" Yace "Just a minute or two" Tambayarta ya shiga yi da harshen turanci ko a Dept din nn take, ta masa nodding tace "Yea!" Murmushi yyi yace "Dat's gud Ma'am, am handing my sister over to yhu, assist her for today, yhu know! she's new in here" Baturiyar da baxata wuce shekaru 18 ba tayi murmushi tana kallon Batuul tace "She's welcome, she will really like it in here, from Africa I guess!" Yace "Yea! Exactly Africa! Africa Nigeria." Karasawa gun Batuul dake kallonsu tayi ta kamo hannunta tare da shaking dinta tace "Welcm frnd, yhu will really enjoy it in here, I am Samantha Brown, yhu" Batuul tayi murmushi tace "Am Fateema kashim" k'asa pronouncing din sunan yarinyar tayi Batuul tayi dariya, yarinyar ta bude deep green eyez dinta tace "your looks are more like dat of Britney Smears a pop artiste, just dat yhu are a dark, I will cal yhu Britney! Nyc meeting yhu Britney" kallon Batuul dake dariya bakin rai Abuturrab yyi, sae ta basa dariya don bae taba ganinta cikin farin ciki haka ba, murmushi yyi yana kallon Samantha yace "Dat's a gud start! I will take my leave now Miss Samantha, it's nyc meeting yhu for the first time" hannu tayi masa stretching ya karba tace "Nyc meeting yhu too Mr..." Yana murmushi yace "Aliyu Ahmad" murmushin ita ma tayi tana nodding ta sake hannunsa, karban timetable din hannun Batuul yyi yana dubawa, snn ya mika mata, ya ciro 20 pound sterling hade da wayarsa d'aya ya mika mata yace "Driver xae kira ki anjima" risinawa tayi ta karba kanta a kasa tace "Nagode" bae tanka ta ba, ya ma Samantha waving ya juya ya bar su wajen. Karfe biyar saura suna xaune ita da Samantha da wata Linda sae 'yar uwarta yar Nigeria Aisha, ba karamin farin cikin haduwa da Aisha tayi ba ko ba komae ta samu 'Yar uwa a makarantar, sae dae ita a hostel take, fitowarsu lecture knn suna ta hiransu ita kuma tana duba textbuk din hannunta, wani guy ne ya karaso inda suke yana kallonsu yace "Hi" duk suka amsa bnda Batuul da bata dago ba, xauna wa yyi daga gefenta yana kallonta yace "Assalamu alaikum!" D'agowa tayi da sauri tana kallonsa, sae a snn ta ga bahaushe ne me kyau, sunkuyar da kai tayi ta amsa masa sallamarsa, da harshen hausa yace "Ya lecture 'yar uwa" tace "Alhmdllh tnxx" ya d'an yi murmushi jin ynda ta amsa masa yace "Am Shaheed Mukhtar by name, yhu?" Wayarta ne ya shiga ring ta mike tana kallon screen din tace "Srry Shaheed, I will be on my way ynxu" kallon Aisha dake ta kallonsu tayi tace "Plss ki d'an rakani outside gate, driver ya xo dauka na" bata jira cewar Aisha ba ta shiga yi ma su Samantha sallama, daga nn tayi gaba da sauri Aisha ta bi bayanta, binta da kallo Shaheed yyi yana murmushi, sae da suka yi nisa Aisha tace "me yasa xa ki yi masa hka Fatima, kinsan waye Shaheed kuwa, a vry popular guy a makarantar nn, he's so intelligent, course din mu daya, nd he is in his final year, ni na yi mamakin ganinsa wllh, don bin sa 'yan mata ke yi ba shi ke bin su ba" Batuul tayi murmushi tace "Gskya ne" tana ganin motar Abuturrab ta gane ta juya tana kallon Aisha tace "Toh sae gobe idan Allah ya kai mu, thnk for ur company frnd" murmushi Aisha ta mata ta gyada mata kai, Batuul ta juya ta nufi motar, duk a xaton ta driver ne, har xata bude baya sae kuma ta fasa ta bude gaba, ido hudu suka yi da shi, ta sunkuyar da kanta, yace "Baki ga daman d'aga call din ba knn" shiga motar tayi ta rufe ya tada motar suka bar wajen, a hnkli tace "Ina yini?" Ba tare da ya kalleta ba yace "Lfya lau" sae da suka kusa gida yace "Ya lecture" kmr an tilasta sa tambayar don can ciki yyi ta, ta kallesa tace "Alhmdllh" yana gama parking ta bude motar ta fita, sae dae bata yi gigin tafiya ba ta jira har ya fito, sae da ya shiga gaba ta bi bayansa, Ajiddeh na kwance falo ta kure Ac tana kallo sanye da kananun kaya as usual, a hnkli Batuul tace "Ina yini" Ajiddeh ta d'an saci kallon Abuturrab, ganin kallonta yake yasa tace "Lfya lau" sama Batuul ta nufa, ajiye wayarsa dake hannunta da long notes din da ta siya a makaranta tayi ta kwanta tare da lumshe ido, ta kusa minti goma kwance snn ta mike ta cire watch din hannunta da jewelry ta cire doguwar rigar jikinta xata shiga bayi tayi wanka, bude kofar dakin taji anyi ta juya a rikice suka yi ido huda da shi, xaro ido tayi ta durkushe wajen, ya dauke kai ya juya da sauri ya fice daga dakin. [8/22, 14:47] Umar Dalha: 💖💝BATUUL💖💝 48 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Yana fita ta mike da sauri ta rufe k'ofar ďakin, har lokacin jikinta b'ari yake, she wasnt expecting anyone, komawa tayi ta zauna daga bakin gadon hannunta zagaye a k'irjinta duk kunya ya isheta, tafi minti biyu a haka daga baya ta mik'e ta faďa toilet, ta daďe cikin bath tub ďin kamin ta fito, a hankali ta lek'o kanta dan tsoro takeji kamar zataga wani a ďakin, ganin babu kowa yasa ta k'arasowa cikin ďakin, akwatinta na kayan shafa dake gefe ta cicciro waďanda take buk'ata ta shafa ta maidasu cikin akwatin, gown ďin atamfa holland bak'a mai manyan patterns ďin ja da purple ta saka, bata ďaura ďankwalin ba , comb ta ciro daga cikin kayanta ta dawo gaban mirror ta shiga taje gashinta, sai da ta gama ta haďeshi in a bun, tunanin shirya kayanta dake cikin akwati a closet ďin ďakin tayi, bbu b'ata lokaci ta tashi ta buďe closet ďin, tana buďewa taga electric burner a ciki, sai da ta karkaďe k'uran wajen tukunna ta shiga jera kayayyakinta a ciki, sosai ta shiga gyaran ďakin, har bedsheet ta canja wanda ta gani a cikin closet ďin ďakin, cikin lokaci kaďan ta gama gyaran ďakin ta kunna burner ta saka sandal woods, babu abinda ďakin keyi sai k'anshi, sai da taga ďakin ya koma yadda takeso sannan tayi ajiyar zuciya , faďawa tayi kan gadon tana maida numfashi, idonta ne ya faďa kan wayarshi da ya bata dake ajiye kan bed side drawer, hannu tasa ta dauko wayar, ta d'an tabe baki ta shiga gallery duk hotunan Ajiddeh ne wayar wasu da shigar mutunci wasu kuma bbu kyan gani, k'an wani hotonsa da yyi shi kadae yana xaune office ta tsaya tana kare ma kallo, yyi mugun kyau sanye da suit blue da fadin shirt daga ciki, murmushin sa me rikita Ajiddeh yyi a hoton Lol, Batuul tayi tsaki hade da tabe baki ta wuce hoton, wani hoton ta kuma gani yana sanye da farin 3qtr da farar polo, ainahin kyansa ne ya fito a hoton, ita kanta ta san yyi kyau amma hkn bae hanata kyabe baki ba, ajiye wayar tayi ta juya abun ta ta rufe ido kmr me shirin bacci. Abuturrab na fita daga ďakin dama dakinsa ya wuce, direct toilet ya shiga yayi wanka, tsakin da baisan dalili ba ya riqayi har ya fito daga toilet ďin, sweatpant grey da farar shirt ya saka, zama yayi gaban system ďinshi yana dudduba abubuwan da zaiyi, bayan wajen thirty minutes ya mik'e tare da jan ďan siririn tsaki ya fita daga ďakin dan ya fara jin yunwa, ko coffee ne zuwa zaiyi ya haďa kamin ya samarwa kanshi abinda zaici, tunda ya fito daga ďakinshi yakejin wani k'anshi mai daďi, lumshe ido yayi yana shak'ar k'anshin, sauk'a yayi k'asa yayi hanyan kitchen, Ajiddeh na kwance nan inda ya barta ta tasa bowl ďin Tacos a gaba tanaci, ďauke kanshi yayi cike da haushinta ya wuce cikin kitchen, coffee maker ya nufa ya haďa sannan ya fito, sama ya koma yayi hanyan ďakin Batuul don ce mata ta fito ta samawa kanta abinda zataci, tun kamin ya kai ga shiga ďakin yakejin k'anshin nan na daďa k'aruwa, a aljihunshi ya fiddo makulli ya buďe ďakin ya shiga, a figice ta mike daga kwancen da take dan tasan saida ta rufe k'ofarta kamin ta kwanta, lumshe ido yayi ya bude ya shiga bin ďakin da kallo ganin yadda ta gyara shi yayi kyau, abinda dakinsa bae samu daga Ajiddeh ba, tashi tayi daga kwancen da take ta zauna tana kallonshi, kyab'e baki yayi ya k'arasa shigowa cikin ďakin, gashin kanta da yasha gyara yabi da kallo, ita kam wasa ta shigayi da zoben hannunta zuciyanta na bugawa taqi ďagowa ta kalleshi, kyab'e bakinshi ya kuma yi ya ďauke idonshi daga kallonta yana daďa bin ďakin da kallo yace "abincin da zakici sai ance ki fito ki nemawa kanki?, ko dan ki samu na fađa wa Ammah cewa bana baki abinci", bata ce mishi komai ba kuma bata ďago ta kalleshi ba, sipping coffee ďin dake hannunshi yayi yace mata "in kin gama zaman sai ki sauk'o ki nemawa kanki abinci don baki taho da Cook daga Nigeria ba", daga nan ya juya har xae fita ya dawo ganin wayarsa gefensa ya dauka, gabanta ne ya fadi tunawa da tayi a gallery take, kunna wayar yyi ya ga hotonsa, kallonta yyi yace "Ohh hotona ma kike kallo knn," dariya yyi yace "Lallai kina da wahala yarinya, xa ki iya kishi da matata?" Ji tayi kmr ta rusa ihu don takaici sae dae bata iya ta ce masa komae ba, yyi murmushi yace "Ae kam da kin gamu da aiki" daga hka ya fita daga ďakin, bayanshi ta bi da kallo tareda da fadawa kan gado tana kukan takaici. Ji tayi wayanta na ringing, ta duba taga Aunty ke k'iranta, da sauri ta goge hawayenta cike da murna ta ďaga ta gaida Aunty tace "Aunty har na fara zuwa school yau, Aunty sai kinga makaranta, i couldnt believe it sai da na ganni a lecture hall, da i thought i will never get d chance to study there, but God has other plans, am just happy tun ďazu", Aunty tayi murmushi daga ďaya b'angaren tace "Ai dama every disappointment is a blessing in disguise, kinga you were sad abt getting married, but God knows best, sai kinyi aure zaki samu kiyi fulfilling dream ďinki", ajiyar zuciya Batuul ta sauk'e tunawa da tayi auren da tayi ne yayi silar zuwanta makaranta, jiki a sanyaye tace "Aunty its so nice, Nagode", Aunty tayi dariya tace "godiya kuma, Allah zaki godewa ai", tace "Ai nagode mishi sosai shima, saura Baba shima zance mishi nagode", Aunty tayi dariya tace "toh shikenan, kayanki sun iso?", da mamaki tace "Aunty wane kaya?", Aunty tace "kayayyakinki mana da kuma su turaren wuta", tace "A'ah Aunty, ni kawai wanda nazo dashine, sai turaren wutanma ďan kaďan ne", Aunty tace mata "toh shikenan, in sun iso Abu zai kawo miki, sai ki gayamin", tace "toh", hira sukayi da Aunty daga nan sukayi sallama, tana ajiye wayar aka bude kofa, mikewa tayi da sauri sanin shi ne ya dawo, wani mugun kallo yake mata daga bakin kofar ta sunkuyar da kai a hankali tace "Anty ce ta kira ni" juyawa yyi ya bar kofar ta bi bayansa da sauri, downstairs ya sakko tana biye da shi a baya, xama yyi gefen Ajiddeh yana kallonta yace "Kin yi sllh babe?" Xata basa amsa idonta ya kai kan Batuul dan zaro ido tayi kafin ta mike cikin fada ta fara magana "Aliyu meye hka xata wani sakko mani falo da kwalliya hka kmr gidan mijinta? Ohh dama ita ce ta cika min gida da turare hka?" Kallon Batuul da ta k'asa ci gaba da tafiya Abuturrab yyi don shi bae ga wani kwalliya da tayi ba banda kaya da ta sa, xae yi magana Ajiddeh ta ci gaba da masifarta "Toh gskya baxan yi tolerating haka ba, cin arxiki ta xo yi gida na don hka ta bi ni a hankali, daga yau ni kar ta sake sa min turare a gida kuma kar ta kuma sakko min falon miji bbu hijab, idan ba hka ba gskya xa a ga bala'i" murmushi Abuturrab yyi ya ajiye cup din coffesn hannunsa ya kalli Batuul dake tsaye har lkcn a tsawace yace "Baxa ki bar wajen nn ba" juyawa tayi a d'an tsorace xata koma sama, yace "C'mon kin wuce kin yi abinda xa ki yi ko sae na xo kan ki" kitchen din ta nufa hawaye cike idonta, rasa abinda xata girka tayi gashi tana tsoron kar ya shigo ya ganta tsaye, bude deep freezer tayi ta ga kayan miya kala kala da nama, deciding kawae tayi ta soya Irish, tayi sauce kadan, cikin mintunan da basu wuce ashirin ba ta hada abincin ta kashe gas, kan kace me tuni kamshin d'an sauce din da tayi da hanta ya bade gidan, Ajiddeh sae wani yatsine fuska take tana kyabe baki, Abuturrab ya juya ya kalleta yace "What's that?" Tsaki tayi bata ce komae ba, ya mike ya nufi kitchen din, goge goge ya sameta tana yi ga abincin ta ajiye gefe, juyawa tayi tana kallonsa, kmr baxae ce komae ba sae kuma yace "Iyakar girkin knn?" A hnkli tace "Um!" Tabe baki yyi har xae fita sae kuma ya karaso cikin kitchen din, plate ya dauka ba tare da ya kalleta ba ya nufi inda ta ajiye abincin ta bi sa da kallo, kadan ya dibi Irish din da sauce a gefe, ya daga kai suka hada ido, sauke idonta kasa tayi tace "ya ishe ka hka?" Juyawa yyi yace "Yea!" Snn ya fice, hade rae Ajiddeh tayi tana kallonsa har ya xauna gefenta tace "Haba babe, wnn ae xub da girma ne, maimakon ka fita ka siya ko ka aiki driver" yace "koh? In xa ki ci ki sa hannu mu ci" tsaki tayi ta dauki remote, fork ya dauka ya fara cin abincin, he was so surprise at the taste of the food, bae taba tunanin Batuul ta iya girki hka ba, lumshe ido yyi yana cin abincin, amma sbda bae son ta rainasa bae cinye potatoe din ba duk da bae ishe shi ba ya ajiye, dai dai nn Batuul ta fito bayan ta gama tsaftace kitchen din rike da plate din abincin ta, bata yi gigin kallon inda suke ba ta haura sama. Abuturrab na gama kallon program din da yake kallo ya mike ya haura sama ya bar Ajiddeh nn falon, har xae shiga dakinsa sae kuma ya nufi na Batuul, ya kusa minti biyar tsaye don bae ma san me xae kai sa dakin ba, bude kofar dakin aka yi ya koma baya da sauri duk ya daburce, kallonsa take da mamaki, ba tare da yyi wani tunani ba ya samu kansa da cewa "Tnx!" Sae kuma ya juya da sauri ya nufi dakinsa, bin sa da kallo tayi sae kuma ta kyabe baki ta sauka downstairs, dai dai lkcn da Ajiddeh ta duka ta dauki plate din potatoe'n da Abuturrab ya rage xata d'an d'ana taji taste din girkin da ya cika ma mutane gida, sae a idon Batuul, sake plate din tayi duk da har ta kai daya baki, duk ta daburce. [8/22, 14:47] Umar Dalha: 💖💝BATUUL💖💝 49 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Sunkuyar da kai Batuul tayi ta karasa sakkowa, Ajiddeh ta ji kmr ta nutse wajen don kunya, mikewa tayi tana yatsine yatsinen borin kunya ta nufi kitchen da sauri, hannu ta wanke da bakinta a sink ta shiga kakarin amai, Batuul bata san lkcn da dariya ya subuce mata ba, ta juya da sauri ta koma sama ta dinga tuntsirar dariya a corridor, bude kofa Abuturrab yyi yana kallonta da mamaki, xae yi magana sae ga Ajiddeh kmr xata tashi sama, ganin dariya Batuul take ya sa ta tsaya daga stairs tana huci, Abuturrab ya kalleta ya kalli Batuul da ta k'asa daina dariya ganin ynda Ajiddeh ke huci, a fusace Ajiddeh tayi kanta ae bata san lkcn da dariyar ta koma ciki ba tayi bayan Abuturrab a tsorace tana kiran Anty, ya hade rae yace "meye hka wae?" Lamo Batuul tayi bayansa, a fusace Ajiddeh tace "Honey ni fa take ma dariya hka kmr sa'arta fa?" Juyawa yyi yana kallon Batuul yace "kina da hankali kuwa? Dariyar me kike mata?" Batuul ta turo baki tace "Ni ba da ita nake ba fa" wani kallo ya shiga mata ya fixgo ta daga bayansa yace "ki fadi Dariyar me kike idan ba hka ba I wil slap yhu" sunkuyar da kai tayi don wani dariyar taji na taho mata, ya daka mata tsawa yace "Baxa ki yi magana ba" a hnkli tace "Kaga abincin da ka rage fa naga tana ci a falo kuma tana gani na sae ta shige kitchen ta fara amae...." Bata karasa ba ta shige bayansa ta dinga dariya har da kyakyatawa, dariyar shi ma ya fara yi yana kallon Ajiddeh da ke kikkifta ido, ganin irin dariyar da suke ya fusatar da Ajiddeh tayi bayansa da gudu xata fixgo Batuul, tura Batuul yyi bedroom dinsa da sauri shi ma ya shiga ya rufe, ae tsit kke jin Batuul don ta tsorata ssae, shi kam bae fasa dariyar da yake ba, Ajiddeh kam dakinta tayi hawayen takaici na bin kuncinta tana da ta sanin kallon potatoe'n, kallon Batuul Abuturrab yyi bayan ya gama dariyarsa ya hade rae yace "Xaki yi spelling Doom yau, ba dae dariya kike mata ba" kmr xata yi kuka tace "Wllh ni ban sani ba... Sharrin shaidan ne" sae ga hawaye na bin kuncinta, wani sabon dariyar Abuturrab ya shiga yi, Batuul ta durkushe wajen a sanyaye tana kallonsa don ita har ga Allah tsoron Ajiddeh take, ya shafa kansa yace "Ki tashi mu je ki bata hkuri idan ba hka ba ta kora ki daga gidanta yau" mikewa tayi tace "Toh" ya mike shi ma ya nufi kofa tana biye da shi a baya, yana bude kofan ya juya da sauri yace "Gata nan" a guje Batuul ta juya xata bar wajen cikin rashin sani ta take dogon gown din jikinta, ji kake tim a k'asa ta fadi, wani kara ta saki ta fashe da kuka tana kiran Anty, ya durkusa da sauri ya d'ago ta yana kallon kafarta yace "Ohh sorry!" Kuka take tana yarfe hannu don ji tayi duk jikinta na mata ciwo, ae fa nn ya rikice yana dube duben ko ta ji ciwo, gefen gado ya xaunar da ita yace "Yhu c, me ya kai ki sa kayan da ya fi ki tsayi" kukan ta kawae take bata ce komae ba idonta a runtse, ya galla mata harara yace "Ina ke maki ciwo?" Kneel dinta ta nuna masa, ya daga gown din jikinta idonsa ya sauka kan smooth fresh long leg dinta, k'asa dauke idonsa daga cinyarta yyi don har cinya ya kai rigan, ita kam jin ya daga mata riga kuma bae ce komae ba yasa ta bude ido, da sauri ta janye kafarta daga gabansa ta sauke riganta, ji yyi kmr ya nutse don kunya amma da yake gogagge ne, wayancewa yyi ya mata mugun kallo yace "Don kin samu ina tofa maki addu'a" sae kuma ya mike yace "Idan kin ga dama ki tashi mu je ki bata hkuri" a hnkli ta mike ganin ya fara tafiya ta bi bayansa, suna isa kofa ya juya yaga dingishi take, yace "Meye hka?" Kmr xata yi kuka tace "Ciwo yake min" fixgo hannunta yyi suka koma dakin ya xaunar da ita gefen gado snn ya nufi gaban mirror ya dauko man xafi ya dawo, ya wani hade rae shi a dole Lol, nan dae ya daga mata rigar kuma ya bude man ya diba, ya fara shafa mata a gwiwan, runtse ido tayi jin xafi ta dafa kafadarsa tana kiransa, kallonta kawae yake har ya gama snn ya mike ta bude idonta, ganin ya nufi kofa ta mike ita ma ta bi bayansa da sauri, a hnkli ya murda kofar Ajiddeh Batuul na boye bayansa, xaune ya sameta ta cika tayi fam tana girgixa kafa, yace "Babe!" Wani wawan kallo ta jefa masa, ya gintse dariyarsa ya juya yana kallon Batuul don yasan bata san tare suke ba, a hnkli yace "Baxa ki bata hakurin ba" Batuul kmr xata yi kuka tace "Don Allah Anty kiyi hkuri ni ba da ke nake dariya ba fa" mikewa Ajiddeh tayi da sauri tace "Ohh biyo ni daki kika yi don kin isa?" Batuul tace "A'a kiyi hkuri ni ban san xa ki ji haushin dariyar ba" Ajiddeh tace "Ae sae kin gaya min me kike ma dariya xa ki kwana gidan nn yau" shiru Batuul tayi, hkn yasa Abuturrab ya fara dariyar da yake gintsewa yace "Ta fa baki hakuri Anty" Ajiddeh ta fashe da kuka tace "Aliyu ni na gaji da wnn walakancin naka, na gaji" dariya kawae yake yace "Babe ita fa ba potatoe'n da kika ci ya bata dariya ba, aman da kika tafi kitchen kike yi shi ya sa ta dariya, ko ba hka ba Batuul" a hnkli Batuul tace "Ehh!" Ajiddeh ta kuma rushewa da kuka kmr an aiko mata da sakon mutuwa, me Abuturrab zae yi bn da dariya, dariyar da bae taba yi ba a rayuwarsa, ita kanta Batuul hadiye dariyan take tana lekan Ajiddeh. [8/22, 14:47] Umar Dalha: 💖💝BATUUL💖💝 50 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Had'iye dariyarshi yayi ganin kukan da Ajiddeh keyi kamar wacce aka daka ya juyo yana kallon Batuul da tayi saurin gintse dariyarta ta sunkuyar da kai, hannunta ya kamo ya dawo da ita gaban gadon Ajiddeh ya hade rai yace "sake bata hakurin", a hankali Batuul tace "kiyi hak'uri" jajayen Idonta da suka rine ta dago tana mata wani mugun kallo, kallon Batuul yayi yace mata "Get out", kamar munafika ta fice daga d'akin, tana fita ya dawo bakin gadon ya zauna tareda janyo Ajiddeh jikinshi, kukan ta sake fashewa da, bayanta ya shiga bubbugawa yace "Hey babe, tace fa ba dake take ba, beside meye Na zuwa da yin amai bayan har ta ganki kinci, ai cemata zakiyi ta zubo miki ma tunda gidanki ne" ya k'arashe maganan yana murmushi, d'ago kanta tayi tana hararansa da rinannun idanuwanta a fusace tace "toh kai dariyar da kake yi ta me? Memakon kayi mata fad'an abinda tayi shine ka biye mata kuna min dariya don walakanci koh", har lokacin yana murmushi yace "its okay yanxu ai na sata baki hakuri, i will deal with her next time she tries anything stupid thing" d'ago kanta tayi ta sake kallonshi , kai ya kad'a mata yace "i mean it wife, kin ma yi sllhn kuwa" shirun da yaji tayi yasashi gane batayi ba, yace Mata "tashi kije kiyi sllh, I will b back right away" daga haka ya mik'e ya fita Batuul na fita ta wuce d'akinta, kan gado ta fad'a taci gaba da dariya, sai da tayi mai isarta tukunna ta gyara kwanciyarta kan gadon, nan bacci ya d'auketa, bata dad'e da kwanciya ba taji k'iran sllhn wayarta Na bugawa, a kasalance ta tashi dan ba isanta baccin yayi ba sannan baccin bayan la'asar ne, da k'yar ta mik'e ta kashe, ta Shiga toilet tayi alwala, abun sllh ta shimfida ta hau kai, bayan minti biyar ta tashi tayi sllh magrib, nan ta zauna har akayi Isha tayi, daga nan ta mik'e tayi shirin Kwanciya, wanka tayi ta fito ta saka kayan baccinta riga da dogon wando, snn ta koma kan gadon ta kwanta bayan ta rufe k'ofar d'akin, tafi awa d'aya kwance baccin yaqi xuwa mata, babu abinda takeyi sai tsaki, tashi tayi ta janyo system d'inta, in to the bad lands ta kunna zataci gaba da kallo, tura k'ofan d'akin akayi, a tsorace ta d'ago kanta ganin waye , mamaki ne ya kamata dan tasan ta rufe k'ofarta, toh mesa zai wani ce ta dinga rufe k'ofarta bayan yasan he have access to it, d'an murgud'a baki tayi ta sunkuyar da kanta taci gaba da kallo, shigowa yayi ba tareda yyi bother ya kunna wutan d'akin ba, a bakin gadon ya tsaya, yace "Abinci kike jira a siyo maki da baki sakko neman dinner ba, or are yhu afraid of my wife" zumb'uro baki tayi cikin duhun ganin baya ganinta, a ranta tace shi wannan mutumin ina ruwanshi ne da cin abinci na, jin tayi shiru yasa ranshi ya b'aci, a tsawace yace "ba magana nake maki ba", tsorata tayi ba tare da ta shirya ba ta rufe system din ta mike ta yi kneel kan gadon bata ce komae ba, fixgota yyi tayi 'yar kara ya dago ta da sauri tun kan ta kai kasa, tsayar da ita yy gabansa ya ciro wayanshi a aljihu ya haska fuskanta, a hankali tace "bana jin yunwa" d'an k'aramin bakinta dake motsawa yabi da ido, hka kawae gabansa ya shiga faduwa yana kallonta, ita kanta faduwa gabanta ke yi a lkcn, duk kamshin turarensa ya cika ta, kashe wutan wayar yyi ta juya a hnkli xata bar wajen ya fixgota ta fado kansa, runtse ido tayi a tsorace tace "Ya Abuu ni bna jin yunwaa" D'ago kanta yyi amma taki bude idonta, kallon lips dinta kawae yake cikin duhun ko kiftawa bae yi, murda kofar dakin aka yi, ya tura ta da sauri ya koma baya, ita kam rawa jikinta ya dau yi, da sauri ta haye kan gado, ya kunna fitilar wayarsa, Ajiddeh ce ta shigo ta tsaya tana kallonsa tace "Wae me kke a nn Babe?" Tana masa tambayar tana kallon Batuul da tayi kmr me bacci, Abuturrab ya juya yana kallon Ajiddeh yace "Erm dama amma ce ta kira wae a bata shine na shigo naga tana bacci" hade rai tayi tace "Toh ita bata da waya ne da sae kai xa ace ka bata" ficewa yyi daga dakin ba tare da ya tanka ta ba, sae dae tunawa da yyi ba mutunci gare ta ba yasa ya tsaya daga bakin kofa yace "Mu je" tsaki tayi ta fito daga dakin. Batuul ta sauke ajiyar xuciya ta mike ta rufe kofarta da key ta dawo ta kwanta. Washegari Batuul na gaban mirror xaune tana shafa lotion don fitowarta daga wanka knn, taji ana bude kofar dakin, turo baki tayi ta jawo hijab da sauri ta sa, yana shigowa yyi mata kallo daya yace "Daga yau, duk safiya kika tashi kafin kiyi shirin sch ki sakko ki tsaftace gidan gaba daya, snn breakfast da dinner ke za ki dinga yi ba kuma wa cikin ki kadae ba, is dat clear?" Shiru tayi tana kallonsa a hnkli tace "Idan ina da lecture da sassafe fa?" Ya galla mata harara yace "Sae ki tashi da asuba!" Juyawa yyi ya fice, ji tayi kmr ta fara kuka, yaushe ne xata tsaya hada breakfast a gidansu tana da lecture da safe, a sanyaye ta mike ta ciro doguwar riga na kanti pink da adon blue ta sa ta fito, bbu kowa falon ta nufi kitchen, breakfast ta hada cikin kankanin lkci na fried Irish da soyayyan kwae sae ruwan Lipton, ta jerasu kan dinning, ta koma kitchen din ta wanke utensils din da ta bata ta gyara kitchen din ta fito, falo ta shiga nan ma duk ta share tayi mopping ko ina, falon ya dawo yana kyalli, dakinta ta koma, ta kuma shiryawa tayi rolling kanta da plain mayafin kayan jikinta blue, ta shafa chappette a lips dinta ta feshe jikinta da turare, ta fiddo flat shoe dinta ta sa, sannan ta dauki jakarta bayan ta sa wayarta a ciki ta fito falo, har lkcn bbu kowa falon, kallon agogo tayi taga har tara ya kusa, duk taji kmr ta rusa kuka to ta ina xata fara ce masa xata tafi suna dakinsu, ta kusa minti goma tsaye falon wata xuciyar tace kawae tayi wucewarta da kafa tunda bbu nisa sosai, amma ta kasa aikata hakan sbda tsoronsa, hawaye na ya cika idonta sanin da wuya ta samu 1st lecture, tara dai dai ta koma sama ta shige dakinta ta fada kan gado ta dinga rusa kuka kmr yarinyar, tara da minti sha biyar Abuturrab ya fito har xae sauka downstairs sae kuma ya nufi dakinta, har lkcn tana kwance tana kuka, ya karasa cikin dakin ya tsaya daga bakin gadon yana kallonta da mamaki yace "Me ya faru" kauda kanta tayi taki basa amsa, yace "Ke kina da hnkli kuwa ina maki magana kina kauda kai" wani sabon kukan ta fara, ba tare da yyi wani tunani ba ya xauna gefen gadon ya d'agota yana kallonta da mamaki yace "What's that, what happen?" Still taki cewa komai bata kuma fasa kukan ba, ya dafa kafadunta yace "Talk to me mana, an maki wani abu ne wae?" Ganin ynda ya tsare ta da ido yasa ta shiga girgixa masa kai sae dae bata ce komae ba, jawota jikinsa yyi ya dago kanta ya hade rai yace "Idan baki bude baki kin min magana ba I will slap yhu" ta sauke idonta kasa wani sabon hawayen ya xubo idonta a hnkli tace "Am late, nayi missing 1st lecture" kallonta ya tsaya yi ko kifta wa bae yi, ya dake yace "What made yhu late?" Shiru tayi bata ce komae ba, yace "Yhu are not deaf fa, ansa me now" a hnkli tace "ko ba kai bne!" Bude idonsa yyi yace "Ni?" Kauda kanta tayi ya juyo da ita da sauri ya hade rae yace "daki daya muka kwana da xan sa ki latti? Ohh har kin kirkiro wani karyar da xa ki ma Ammah ki hada ni da ita koh, wae yhu are late! Did yhu sleep in my room ne xaki ce yhu are late or tunda kika tashi yau kin tsinana mu da wani abu ne a gidan nn, No of course u are just busy sleeping" sake kauda kanta tayi ita ma ta hade rae, ya juyo da kanta yace "Kika sake dauke min kai I will slap yhu wllh" rufe ido tayi da sauri, yyi shiru yana kallonta, sauke idonsa yyi kan lips dinta, hka kawae gabansa ya shiga faduwa, ita kanta Batuul faduwa gabanta ya shiga yi idonta rufe, without thinking twice kawae ya samu kansa da kai lips dinsa nata, a tsorace ta bude ido jin soft lips dinsa a nata, dai dai lkcn da suka ji an bude kofa, mikewa yyi da sauri ya k'asa kallonta, ya nufi kofa, suka kusan cin karo da Ajiddeh bakin kofar xata shigo, ae da sauri ya tsotse tsarabar chappette din da ya yo a lips dinsa, ta wani hade rai tace "Wae me kke dakin nn tun daxu Aliyu?" Daburcewa yyi da farko sae kuma ya wayance daga baya yace "Erm naga lkci ya wuce bata fito ba shi yasa na shiga in ga abinda take, nd nd.. I found her crying" Ajiddeh tace "Gskya idan kana son xaman lfya Aliyu ka daina shigowa dakin nn, bana so, idan tana bukatan abu ne ta jira idan muna falo ta sauko ta same mu" barin ta yyi a nn yyi ficewarsa, ta juya tana kallon Batuul ta galla mata hararan tsana tace "Munafuka kawae, 'yan maula" daga hka tayi ficewarta, ko kadan Batuul bata san me Ajiddeh ta gama cewa ba don har lkcn gabanta bae bar faduwa ba ji take kmr lips dinsa na nata har lkcn. Ta kusa minti sha biyar xaune sae gashi ya dawo, daga bakin kofa ya tsaya ba tare da ya kalleta ba yace "Idan kin ga dama ki fito driver ya kai ki sch" daga hka ya fice, mikewa tayi a sanyaye ta dauki jakarta ta d'an gyara fuskarta kuma snn ta fito. [8/22, 14:47] Umar Dalha: 💖💝BATUUL💖💝 51 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* A dinning d'in ta ganshi zaune yayi serving kanshi breakfast din da ta yi yana ci, Ajiddeh na daga gefenshi tana ta kumbure kumbure, tana ganin Batuul ta watso mata wani mugun harara, ko kallonta Batuul batayi ba ta karaso cikin falon ba tare da tace musu komai ba ta wuce, har ta kai bakin kofa idon shi na akanta, sai da yaga fitanta snn ya maido da hankalinshi kan Ajiddeh da ta zuba mishi ido rai a b'ace tana kallon yadda yake kallon Batuul, yasan driver bazai tafi ba sai ya jirashi ya fito dan yana son bata wayanshi in ta tashi a k'ira a d'auketa kuma ya bata kud'i, yi yayi kamar bai San kallon da take mishi ba yace "so you ain't eating har yanzu, kilan zaki dafa ne ko kuma sai na tafi zaki faraci ta shigo ta ganki kinaci kije kina amai koh", ya karashe maganan yana murmushi, sake hade rai tayi tace "kaga nifa wulakancinka ne banaso Aliyu, koh jiya a gabanta ka dinga min dariya, ko ta rainani ai kai ka jamin, bare ma bata isa tayi hkn a gidana ba", bai ce mata komai ba yaci gaba da cin abincinsa yana murmushi, sai had'iyar miyau take tana kallon yadda yake cin abincin, duk yadda akayi abincin nada dadi ganin yadda yake ci sannan ga k'anshi duk ya gama bad'e ta a gun, kallonshi tayi rai a b'ace tace "magana fa nayi maka amma kaqi kulani sai tunkud'a abinci kakeyi kamar wanda bai tab'a ci ba", kallonta yayi da idanunwanshi dake piercing zuciyarta yace "ko kin taba dafa irin wannan ne a gidannan da kike cewa inaci kamar ban tab'a ba", baki ta turo tace "nifa duk ba wannan ba, ai abinci ga ka gashi, baby ni abinda na tambaya tun jiya, I urgently need it, gashi har ka shirya bakace komai ba fa", cike da shagwaba ta kare maganar, shi kam har ta gama maganan bai ce mata komai ba, da alama santin chips d'in Batuul yasashi kasa magana, ran Ajiddeh ne ya fara b'aci, tashi tayi a fusace zata tafi ya riko hannunta da sauri, ya dawo da ita ya zaunar kan dinning chair din, kallonta yayi da murmushi a fuskanshi yace "keh bakisan in mutum na cin abinci bai son damuwa ba, da kinci abincin kema nasan all your worries will b cleared away" wani irin kallo ta mishi yace mata "tunda bakici je d'auko min cheque d'ina a sama", da murna ta mike ta haura sama, bata jima ba ta sauko rike da cheque book dinshi a hannunta, har saida ya gama cin abincin tukunna ya janyo ya rubuta mata amount din da take bukata, murna ta dinga yi kamar mey, har bakin kofa ta rakoshi tareda yi mishi peck a kumatu sannan yayi mata sallama ya tafi. Inda Batuul taga driver na tsaye nan ta nufa, da kanshi yazo ya bud'e mata k'ofa tareda ce mata "Morning Ma'am" kai ta gyad'a mishi ta shiga ta zauna ba tareda ta iya ce mishi komai ba, ganin bai tada motar ba yasa tace mishi "am getting late, let's get going" babu musu ya tada ya d'au hanya, har suka isa school ranta b'ace yake, tasan ta riga da tayi missing first lecture, har gaban department dinsu ya kaita, kamin ya fito ya bude mata kofa ta bude ta fito, wucewa tayi lecture hall ta tadda ana lecture , shiga tayi ta zauna ba tareda ta cewa Kowa komai ba, Aisha dake gaba sai kallonta takeyi haka ma Samantha, sai da ta zauna tukunna suka juyo suka ci gaba da sauraren lecturer, batafi 45mins da shiga ba lecturer ya gama ya fita, a tare Samantha da Aisha suka yo wajenta, Aisha ce ta fara ce mata "don't tell me har kin fara latti daga farawa", kamin tayi magana Samantha ta karb'e da cewa "Hey love you were late today, and you missed almost two lectures today, you okay?" , hawayen da take ta kokarin maidawa ne ya shiga zubomata, a tsorace su Samantha ke kallonta ganin yadda take hawaye, janyota Aisha tayi ta rungume, Samantha ce tayi mata alama da ta jata suyi waje, sai da sukaje inda babu mutane tukunna suka zaunar da ita, kuka sosai ta shiga, babu abunda sukeyi sai rarrashinta, har suka gaji suka rabu da ita, sai da tayi mai isarta tukunna tayi shiru dan kanta, hawayenta tashiga gogewa da hannu sannan ta dubesu tace "what were we thought, I mean d topic", Aisha dan haushi ko kallonta batayi ba, Samantha ce tana kallonta tace "It seems you are hungry, let's go and get something to eat, am also famished" kallon Aisha tayi taga ta had'e rai, jiki a sanyaye tace "Aisha cikina ke ciwo", cikin sanyi Aisha tace "toh Fatima koh baki d'aukemu komai ba ai kinsan bazamu cutar dake ba, ciwon ciki dai ko clinic ai sai muje a baki magani, amma kinzo late we were worried sannan kuma kiyita kuka kiki bamu ansa", Samantha dai baki ta bud'e tana kallonsu, sai da taji sunyi shiru sannan ta dubi Aisha tace "She said what, what's d problem?", a takaice Aisha tace "stomach ache", ido Samantha ta xaro tace "then?, we should be in the clinic, let's rush her", kai Batuul dake zaune ta girgiza tana kallon yadda Samantha ta rud'e tace "I will b fine dear, you shouldn't worry, it usually does, I will take my medication when am back home", da rashin gamsuwan abinda ta fad'a musu Aisha ta girgiza kai tace "Fatima bafa cutar dake zamuyi ba, nanfa kika zauna kina kuka amma kice wani wai you are okay, how does that even makes sense", ta k'arashe maganan ranta b'ace, a hankali Batuul ta kamo hannunta ta zaunar gefenta tace "dagaske nake ya daina, kinga Kuma inada magani na a gida, ba lallai school clinic suyi min prescribing irinshi ba" sai yanxu Aisha ta yadda ta fad'awa Samantha yadda sukayi, littafin dake hannun Samantha Batuul ta ansa tana Kallo tace "Did I miss so much", Kai Samantha ta girgiza tace "you got no worry, I will explain everything", giranta d'aya Batuul ta d'aga, Samantha na kallonta ta fashe da dariya tace "yeah you gat my back" tanayi tana kad'a kai, dariya su dukan suka sa, Samantha tace " SHIT!,But girl you scared me, you shouldn't cry again when am there, I have this terrible phobia of tear, it doesn't even have a name", dariya ta basu, Batuul tace, "not in my weirdest dream, its not happening again I promise" ta k'arashe maganan tareda mik'ewa dan taga duk jikinsu yayi sanyi, sai da ta mik'e ta fara tafiya tukunna ta juyo ta dubesu tace "who is joining me for a cup of frapuccino", a tare suka mik'e suka biyota, suna isa wajen taji cikinta ya k'ulle, a hankali ta fara d'aga k'afarta ba tare da ta bari sun gane, har suka samu waje suka zauna cikin bai barta ba, k'aryan da tayiwa su Aisha ne ya dawo mata, dama ance babu kyau k'aryan ciwo, d'an k'aramin tsaki taja dan tasan period d'inta can come anytime tunda har cikinta ya fara ciwo, waiter dake aiki a wajen ne ya iso wajensu, ya tambayasu abunda xa a kawo musu, Samantha tace "Serve me caramel", juyawa yayi ya kalli Aisha yace "Ma'am what would you like to have?" , kallonshi tayi tace "Hazel nut sugar free and and chicken lasagne", daga haka ya juya yana kallon Batuul da taketa tunani hankalinta ma baya wajen, sai da Aisha ta d'an tab'ota tukunna ta d'ago tana kallonsu, tambayanta yayi itama me take so, tunda har cikinta ya fara ciwo in tasha abu mai zak'i wahala ne zai k'aru mata gashi batada magani, ita pad d'inma bata dashi, tunanin hakan yasa ta hawaye da tayi k'ok'arin maidawa, jiki a sanyaye tace mishi "peppermint sugar free", da haka ya tafi yaje kawo musu, baifi minti biyar da tafia ba ya dawo riqe da tray, ajiyewa kowa abinda yayi ordering yayi sannan ya bar wajen, sai da suka kusa gamawa kanta a k'asa taji anyi musu sallama, bata d'ago ta Kali mai sallaman ba amma tasan namiji from his voice, kujeran dake gefenta taga yaja ya zauna, ji tayi yana cewa "This isn't fair, you girls enjoying without an invitation?", Samantha ce tace "Hey lemme order one for you, ta juya zata k'ira waiter, hannu ya d'aga mata alamar surrender yace "Hey No Thank you, am okay", kallonshi Aisha tayi da mamaki ganin baya tab'a kula matan dake binshi ma amma yanzu shi da kanshi yake zuwa inda suke, a hankali Aisha tace "You sure?", kai ya gyad'a mata tareda da yi mata murmushin shi mai kyau, kallon Batuul yayi yace "Sai dai in wannan da bata magana xata bani nata, I will gladly take it", Batuul batasan ma sunayi ba dan hankalinta ma baya kansu, kud'in frapuccino da zata biya ma bata dashi a yanzu haka da take zaune, tunaninta sam bai kawo bata da kud'i ba har sai da ta tuna ba da jakan jiya ta fito ba kuma yau bai bata kud'i ba, d'an tab'a table d'in yayi yace "y'ar uwa tunanin mey kikeyi, you are too young for that", sai a lokacin ta d'ago ta kalleshi da murmushinshi mai kyau a fuskanshi, ajiyar zuciya tayi tace "Ba tunani nakeyi ba", tsareta yayi da ido yace "okay tell me what we just said", shiru tayi ta d'auke kanta, murmushi yayi yace "you see you can't say, ki dena its not good for you at such a tender age", batace mishi komai ba itadai, dan tama manta da sunanshi ko jiya da ya fad'a musu, alama yayiwa waiter yaxo, ce mishi yayi ya bashi bill d'insu, shi ya biya musu duka kud'in abunda sukaci, duk da suna ya bari bai sauraresu ba, Samantha ce ta mik'e tace "okay Mr Shaheed, we got class now, hope to see you ltr, and thank you for all" murmushi yayi mata kawai yana kallon Batuul dake Zaune, ciwon cikinta na dad'a k'aruwa, a hankali ta mik'e tana kallonshi taga shima ita yake kallo suka had'a ido, maza tayi ta d'auke idonta tace mishi "mun gode" murmushin sa na nan fuskanshi har lkcn yace "its okay", daga haka suka mishi Sallama suka wuce, bayansu yabi da kallo har sai da ya dena kallonsu ya juya tareda murmushi, suna tafiya Samantha tace "He is such a gentle man, am already crushing babes", Aisha kawai ta biye mata Batuul kam shiru tayi tana jin abinda ke damunta har suka isa class Abuturrab na fitowa ya shiga Duddubawa ko zai ga motar driver amma wayam, da mamaki ya ciro waya ya k'irashi, yana d'agawa yace "I didn't say you should leave, where are you guys", a daburce driver yace "Sir Ma'am insisted we should leave, and am by d office now, av already dropped her", rai a b'ace ya katse k'iran ba tare da ya jira driver ya k'arasa magana ba, he wanted giving her money, kuma inma ta gama lecture ya za ayi tasan anzo d'aukanta, d'an tsaki yaja ya fad'a motarsa, awa biyu sukayi suka fito daga class d'in, gumi sosai takeyi tsabar azaban ciwo amma ta daure dan bataso su Aisha su sani, Aisha ce ta fara yi musu sallama ta wuce yau da yayarta zasu tafi, bayan minti kamar Sha biyar Samantha ma ta wuce, sai lokacin tayi tunanin bata fad'awa driver ya dawo lokacin ya d'auketa ba ya fad'o mata, waje ta nema ta zauna ta kifa kanta kan gwiwa ta fashe da kuka, sunan Aunty kawai take k'ira, ita Yanzu ya zatayi ga ciwon ciki da zai hanata takawa ta tafi da k'afa tunda ba nisa sosai, gashi bata da kud'i bare tayi karambanin hawa Bus ko Taxi tunda ba lallai ma ta gane ba, kuma batada number Yaa Abu bare ta k'irashi tace ta gama lectures azo a d'auketa, to in ma tana da shi iya kiransa xata yi, kuka sosai takeyi kamar wacce ake zanewa, tafi awa d'aya zaune a wajen, kamar daga sama taga mota yaja ya tsaya gabanta, a hankali ta d'ago rinannun idanuwanta dai dai lokacin da ya fito daga motan, tsayawa yyi ya hade rae yana kallonta, sunkuyar da kai tayi ta mike a hnkli tana jan kafa ta xaga xuwa seat din gaba, tana shiga motar shi ma ya shiga ya rufe, ya juya yana kallonta fuskarsa daure sae dae fa har da borin kunyan daxu da safe yace "How dare yhu xan ba driver na order ki sa ya ketare? Kin yi employing driver ne garin nn?" D'ago kai tayi tana kallonsa, sae a snn ya lura da idonta da yyi ja, kana ganinta kasan kuka tayi, d'an kyabe baki yyi ya tada motar ya ja ya nufi gida, jinginar da kanta tayi jikin kujeran motar ta lumshe ido tana jin ynda ciwon cikinta ke karuwa ba kadan ba, yana gama parking a garage ya bude motar ya fita ba tare da ya bi ta kanta ba, da kyar ta bude motar ta fito, bata jira ya kulle motar ba ta nufi cikin gida, bin ta yyi da kallo yana mamakin halinta, komai kuka kmr wata 'yar goye, tsaki yyi ya rufe motar ya nufi cikin gidan shi ma. Bbu kowa falon Batuul ta haura sama da sauri ta shige dakinta ta sa key ta fada kan gado ta cusa kanta cikin pillow ta dinga rusa kuka kamar ranta zae fita, juye juye ta shiga yi ta sauko k'asa ganin kwanciyar ma ya gagareta, kan kace me duk ta fita hayyacinta. Abuturrab kam bedroom dinsa ya shiga, ya nufi toilet yyi wanka, xaune ya samu Ajiddeh dakin da ya fito, ta mike tace "Babe wllh na mance ban gaya maka ba, lotions dina sun kare, gashi akwae wani turare don nake son siya, xan kuma sake kayan make up" wani kallo ya shiga mata yace "Wae ke wace irin mace ce Ajiddeh, how on earth mijin ki xae dawo daga aiki bbu sannu da xuwa, baki bari ya huta ba, baki kawo masa ko ruwa ba ki xo kina masa lissafe lissafen banxa, to bani da kudin siyan komae ynxu" sakin baki Ajiddeh tayi tana kallonsa, sae kuma ta ja tsaki tana hararansa cike da fitina tace "Toh idan ban maka lissafe lissafe ba Aliyu wa xan ma, ko ina da su xan xo ince maka bbu, ubana xan kira ince yyi min bayan kana da halin min" kayansa ya sa ya fice daga dakin ya bar ta nan tsaye, downstairs ya sauka ya kwanta dogon kujera ya lumshe ido, to ita kuma wancan kukan me take a sch, tsaki yyi ya mike xaune ya jinginar da kansa jikin kujera, shi kam kawae wahala aka hadasa da, mikewa yyi ya koma sama ya nufi dakin Batuul, kwance ya sameta kasan dakin tana juye juye tana kuka, tsayawa kallonta yyi da mamaki, shi dae ya shiga uku, karasawa dakin yyi ya durkusa gabanta ya dagota yana kallonta yace "Wae ke kina da hankali kuwa?" Kuka take tana yarfe hannu tana neman kwace kanta daga rikon da yyi mata, jawota yyi jikinsa don xuwa ynxu ta d'aga masa hankali yace "Wae wats wrong with yhu, me ya faru ki gaya min? Talk to me plss, What happen" rufe fuskarta tayi jikinsa tana kuka, ya dago kanta yana kallonta yace "Fateema!" Da kyar tace "Cikina ke man ciwo" yace "Ciki kuma? What did yhu eat at sch" girgixa masa kai tayi ta runtse ido tace "Nothing!" Sae kuma ta fashe da kuka, duk ta rikitasa yace "Wait yana maki haka a gida ne, wani irin magani ake siya maki?" Boye fuskarta tayi jikinsa taki cewa komae sae kuka don ita kadae tasan axaban da take ji, murda kofar dakin aka yi, ae da sauri ya turata ya mike ya koma baya, Ajiddeh ta shigo ta tsaya daga bakin kofar fuskar nan nata daure tana kallonsu, kame kame ya shiga yi yace "Kinga babe wae cikinta ke ciwo kuma taki fadin cause din, nd nd... Wat are we going to do to her then, ko mu tafi clinic?" Ajiddeh ta yatsine fuska tace "Cikinta ke ciwo ko kuma tana Al'ada?" Kallon Ajiddeh ya tsaya yi kafin ya juya ya kalli Batuul da tayi k'asa da kai tana hawaye, Ajiddeh ta watsa mata harara tace "Ko ba jini bane?" Ae Batuul k'asa dagowa tayi, Ajiddeh ta ja tsaki ta fice daga dakin, kallonta Abuturrab ya tsaya yi, [truncated by WhatsApp] [8/22, 14:47] Umar Dalha: 💖💝BATUUL💖💝 52 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* K'arasowa yayi gabanta ya d'agota yana kallon yadda gumi yasa front hair d'inta kwanciya, sae kuma ya hade rae yace "dama haka yake yi miki can gida" jin taki cewa komae ya jawota jikinsa, ya rasa dalilin da yasa tausayinta ke shigansa hka, ko don amanarta Ammah ta basa ne yasa hakan, k'asa yyi da murya yace "Tambayan ki nake, talk to me" sake shigewa tayi jikinshi tana riqe cikinta, kuka ta shiga yi mishi tana ta mutsu mutsu, gaba daya ta rikitashi da kukanta, kokarin tashi takeyi daga jikinshi ganin amai na shirin zuwa mata, ya riketa yana kallon fuskanta da ya gama jikewa da hawaye yace "kina da magani ne" kai ta shiga girgiza mishi, wani karfi taji yazo mata ta janye jikinta daga rikon da yayi mata xata mike ya rikota yace "ina zakije", yana mata mugun kallo dan ranshi ya fara b'aci, bakinta ta toshe tana girgiza mishi kai, ce mata yayi "amai zakiyi", kai ta gyad'a mishi sauran hawayen idonta na k'arasa zubowa, k'arasawa yayi da ita toilet d'in, tun kan su shiga ta shiga kwarara amai nan bakin kofar, har ta gama yana riqe da ita, da k'yar ta samu ta miqe, jiri ne taji yana kwasanta ta sulale k'asa a wajen, binta yayi ya kamota jikinshi tare da miqar da ita, babu abinda takeyi sai hawaye, d'ago kanta yayi yana kallonta yace "are you done", kai ta gyad'a mishi ta maida kanta ta kwanatar jikinshi dan rashin k'arfi, ji takeyi kamar zata fad'i in ba a riqeta ba, gaban sink ya dawo da ita har lokacin tana jikinshi, sai maida numfashi takeyi, tap din sink din ya kunna, ya sata wanke baki da fuskanta, har ta gama. Idonta na rufe, bata ankara ba sai ji taji ya sunkuceta a hannunshi, ta bud'e ido da sauri tana kallonshi, harara ya sakar mata ya wani hade rae, maza tayi ta rintse ido har saida taji ya sauk'e ta kan gado tukunna ta budesu a hankali, bayanshi kawai ta iya gani har ya kai bakin k'ofa, rintse ido tayi hawayen azabar take ji yaci gaba da zubowa, pad d'in da zatayi amfani da ma ita batasan ina zata samu ba tukunna, kuma tunda har tayi amai, ya kusa zuwa kenan, yana fita d'akinshi ya wuce, zaune kan gado ya tadda Ajiddeh, da alama waya ta gama, bai bi ta kanta ba ya wuce ya d'au keyn motan shi yayi hanyan fita, a guje ta diro daga kan gadon ta sha gabanshi tace "yaushe ka dawo ne da har zaka kuma fita Aliyu, kuma ina zakaje da yamman nan hka", bae tanka ta ba ya bi gefenta ya fita, ganin yayi hanyan d'akin Batuul yasa ta k'ara hasala ta sha gabansa tsabar masifa har idonta ya kankance tace "Aliyu ba dai gun wannan yarinyar zaka ba, wannan ai iskanci ne, period dinne takewa iskancin nan kamar yau ta farashi, ko kuma sabon salon karuwancin nata ne hakan", wani mugun kallo ya bita dashi ya sa hannu ya matsar da ita gefe ya ci gaba da tafiyarsa, biyoshi tayi a baya tana ta mishi surutun da baima san mey take fad'a ba, k'ofan d'akin Batuul ya tura ya shiga, tana kwance kan gadon nan inda ya barta, k'arasawa yayi bakin gadon daga tsayen da yake yace "zaki iya tashi?", a hankali ta bud'e lumsassun idonta ta kalleshi, hade rae yyi ya sake nanata mata tambayan, k'ok'arin tashi ta shiga yi, da k'yar ta samu ta mik'e xaune, hijab dinta dake gefe ya mik'o mata ta saka, Ajiddeh dake bakin k'ofa baki ta sake tana kallonshi tana huci, da k'yar Batuul ta mik'e yana kallonta yace "can you walk?", a hankali ta gyad'a masa kai, ita ta fara wucewa gaba yana binta a baya, ja tayi ta tsaya ganin Ajiddeh bakin k'ofa, a d'an tsawace yace "muje mana", a hankali ta juyo idonta yayi raurau tana kallonshi, hannu yasa ya rik'ota, har bakin k'ofar ya isa da ita, wani mugun kallo yayi wa Ajiddeh cikin kakkausar murya yace "give me way", ganin yanayin da yayi magana ya sata tsorata, bata tsaya musu ba ta matsa daga bakin k'ofa, tana yi ma Batuul wani mugun kallo da yasata saurin d'auke kanta, a hankali yake tafiya tana biye dashi har suka isa bakin stair case, ji tayi cikinta yayi wani irin kullewa, ae bata san lkcn da ta sulale ta zube wajen ba tace "Ya salam" ya salam d'in da ta ambata ne ya sashi juyowa da sauri durkusawa gabanta yyi ya shiga tamabayanta baza ta iya tafiya bane, a wahalce ta gyad'a mishi Kai, hannu yasa ya d'auketa cak, Ajiddeh dake tsaye a bakin k'ofa, a tsorace take kallonsu, sosai zuciyanta yake bugu kamar zai fito, idonta har ya cicciko, har cikin mota ya sakata sannan ya zaga shima ya shiga ya tada suka bar gidan, driving yakeyi lokaci lokaci yake juyowa yaganta tana ta murk'ususu, wayanshi ya d'auka ya sanar da doctorn shi gasu nan zuwa, har suka isa asibitin idonta rufe yake tana hawaye, shi ya taimaka mata ta fito, tana riqe jikinshi suka isa cikin asibitin, direct office d'in consultant d'inshi ya wuce da ita, sai da ta zauna shima ya zauna, bayan sun gaisa ya juya yana kallon Batuul yace "Hello young lady , what's d problem", shiru tayi ta kasa ce mishi komai, Abutturab ne ya kalleta yace "baza ki bud'e baki ki fad'a mishi abinda ke damunki ba", kanta ta kauda gefe, likitan ne da kanshi ya mike yace "its okay, let me examine", tashi yayi ya matsa gaban computer shi sannan yace mata ta taso ta kwanta kan gadon dake office din, a hankali ta mike ta isa kan gadon, kallonsu kawai Abutturab keyi ganin yadda take ta gyara hijabin jikinta bataso a d'age, sai da likitan yayi y'an gwaje gwajenshi sannan ya dawo kujeranshi ya zauna yana kallon Abu yace "Is she married?" Kai kawae Abuturrab ya gyada masa, likitan yace "Alryt! she is having menstrual cramps which is caused by the condition of the reproductive tract, such as the endometriosis, uterine tissue that appears outside the uterus, it also happens because the contradictions in the uterus or womb, which is a muscle, if it contracts too strongly during her menstrual cycle, it can press against nearby vessels. This briefly cuts off the supply of oxygen to the uterus, it's this lack of oxygen that causes the pain or cramping", har saida yayi shiru tukunna Abutturab yace "But can it be avoided or controlled?, I mean the pain", murmushi likitan yayi yace "well yeah it can, the pain usually stops when they get married or even after delivery, so maybe when she delivers as you say she is married and she still encounters d pain, If its a mild menstrual cramp, she should take aspirin or another pain reliever, such as ibuprofen, naproxen or acetaminophen, its for d best relief as soon as bleeding cramps start", kallon inda take kwance yayi yaga idonta na lumshe, sannan ya juyo yana jin sharhin da likitan ke mishi, Kowa da inda kwarewarsa take, ya kalli doctor yace "Doctor but is there any home remedy for it, like first aid treatment", kai likitan ya gyad'a yace, "Heat can also help, placing a hot pad or a hot water bottle on her back or lower tummy, taking a hot water bath may also provide some relief, rest when needed, avoid food that contain caffeine and salt, not use tobacco or drink alcohol, too much sugar also should b avoided and chocolates also, massaging of the lower back and abdomen, women who exercise regularly often have less pain also", ajiyar zuciya Abu yayi, murmushi likitan yayi yace "its normal you should not worry, just that others experience more pain, I will b giving her an aspirin injection now, she will b okay", mik'ewa yayi ya isa inda take kwance ya shiga had'a alluran da zaiyi mata, ji tayi kamar mutum na tsaye a kanta, a hankali ta bud'e idonta, kan Alluran dake hannun likitan idonta ya fad'a, a zabure ta mik'e tana girgiza kai, da murmushi a fuskanshi yace "It won't hurt much young lady" hawaye kawai takeyi tana kallon Abu, tasowa yayi shima ya dawo gaban gadon yana mata wani irin kallo, kuka ta fashe da tace "Yaa Abu allura zaimin, banaso xae daina min da kanshi after somedayz", rik'ota yayi jikinshi yace "shhhh, he said it, it won't, close your eyes", rintse ido tayi, shi ya janye hijabin dake jikinta, k'ank'ameshi tayi idonta rufe har aka tsikara mata alluran, sai da aka gama ya d'agota , drugs likitan yayi musu prescribing daga nan sukayi mishi sallama suka wuce, shi ya taimaka mata har wajen mota sannan ya zaga ya shiga shima, a wajen wani saida abinci ya tsaida motanshi, juyawa yayi suka had'a ido tayi maza ta janye nata, "I will b right back", ya fad'a mata sannan ya wuce, kafin ya dawo harta yi bacci dan ciwon ya fara saketa, ganin tana bacci yasashi murmushin da baisan dalilinshi ba ya shiga motan, k'ok'arin gyara mata kwanciya yayi, a hankali ta bud'e idon baccinta ta kalleshi, yana kallonta yace "sleep back", gyara kwanciyarta tayi taci gaba da baccinta har suka isa gida, a hankali ya shiga tashinta bayan ya gama parking, lumsassun idanunta ta bud'e, yace mata "we are home", jiki ba k'wari ta sako k'afa waje ta fito, shi ya d'auko ledan magani da abincin da ya siyo ya biyota dashi a baya, d'akinta ta wuce kai tsaye ta fad'a gado taci gaba da baccinta. Ajiddeh kam suna barin gidan dama ta shige dakinta da gudu tana rusa kuka ta dauki wayarta ta shiga kiran layin uwarta, sae da ya kusa katsewa aka d'aga, ta fashe da wani matsanancin kuka daga daya bangaren uwartata a rude ta shiga cewa "subhanallahi, lafiya Ajiddeh me ya faru?" Cikin kuka tace "Wayyo Mumy ni na gaji da wnn wahala da nake yi kan Aliyu, Mumy ina cikin tashin hankali don ga dukkan alama wllh aiki ya lalace gaba daya, sae kin ga abinda yake min ynxu, walakancin yau daban na gobe daban, ga shegiyar da ya dawo tare da ma na rasa yanda xan yi da ita a gidan, yanxu haka fa tare suka fita don iskanci wae tana al'ada ta ishe mu da kuka a gida, sae kin ga walakancin da yayi min da na tambayesa inda xa su, wayyo ni Mumy kar ta kwace min miji ya ji yana sha'awar aurenta don wallahi sae kin ga yanda ta iya girki yarinya" cikin matsanancin kuka ta kare maganar, Mumy tace "Ke dae shashasha ce wllh Ajiddeh, ina ruwan ki da wata yar iska can ke da xa ki turo kudi mu koma gun bawan Allahn can a san abun yi, da yyi niyyar aurenta ae ba ke xae aura ba ita xae aura tunda sun fi kusa can munafukae, kawae dae an hado shi da ita ne don take maki lekan asiri ke kuma wawuya baki gane ba, har xaki wani d'aga hankali ke da xaki saita ma shegiyar xama ta ji xaman gidan ma ya isheta, yarinyar da ba ma wani kyau gareta ba in ban manta ba sae wani dogon hanci kmr tsiya, meye kuma xaki damu kan ki, yana da kamar ki fara doguwa siririya kyakkyawa ga diri, g'ashi har gadon baya, yanxu dae ko kudinsa ya kama ki dauka kawae ki dauke ki turo mu san abun yi, ita kuma shegiyar ki daina d'aga hankali kanta baxa ta dade maki a gida ba nasan abinda xan yi" Ajiddeh na share hawayen idonta tace "Toh shknn Mumy xan turo ko xuwa gobe" nan Momy ta dinga mata hudubar tsiya tana digesting har taji tsayawar motar Abuturrab, ko kan ta fito har Batuul ta shige daki dama, hakan yasa ta nufi stairs, suka kusa cin karo da shi, kallo daya yyi mata ya ga ynda idonta ya kumbura saboda kuka, ya bi gefenta xae wuce ta sha gabansa tana masa kallon raini tace "Wllh yau sae dae ka xaba ko ni ko wancan karuwar a gidan nn, idan ba karuwanci ba don tana jini har sae ta so ka sani tana wani murkushe murkushe kana daukar ta? Ta ina ta xama muharramar ka, to Allah baxa ta kwanan min a gida ba yau, ka je ka biya mata hostel" banda tafasa bbu abinda xuciyarsa ke yi, acting gently yace "Bani hanya in wuce" tana masa matsiyacin kallo tace "Naki sae ka xabi ko ni ko karuwan can" cikin kakkausar murya yace "Xa ki sa na maki abinda ban taba maki ba Ajiddeh" wani shewa ta saki tace "Ka Dade baka yi ba Aliyu, uwar meye baka min ba daga cikin walakancin ka har...." Bata rufe baki ba taji saukan lafiyayyun mari har biyu ya shaketa ya ja tun daga sama har suka sauko k'asa ya jefar da ita yyi wani irin ball da ita, ae daina gani tayi na 'yan dakiku, bin ta yyi yana huci ya kuma fixgota yace "Don kaza kazan ki ke kika koya mata karuwancin?" Cikin tsawa yace "Answer me kar in sumar da ke a nn, kin san matsayin ta a gidan nn kike kiranta da karuwa?" Jefar da ita ya kuma yi ya nufi sama yana huci. [8/22, 14:48] Umar Dalha: 💖💝BATUUL💖💝 53 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* D'akinshi ya shiga bayan ya kwashe ledojin da ya zubar corridor tun lokacin da Ajiddeh ta fara mishi shirmenta, babu abinda yake buk'ata irin ya watsa ruwa a lokacin, toilet ya wuce ya sakarwa kanshi hot shower, har saida yaji ya fara komawa daidai sannan ya fito daga cikin cubicle d'in wankan, alwala yayi a sink sannan ya fito cikin toilet d'in, gaban vanity table ya tsaya ya shafa mai sannan ya fesa turarukanshi masu k'anshi, closet d'inshi ya bud'e ya ciro farar jallabiya cikin jerin jallabiyoyin dake a ciki, xirawa yayi har xai fita idonshi ya fad'a kan ledojin dake ajiye a k'asan d'akin, d'an tsaki yaja ya kwashi wasu daga ciki ya fice waje, d'akin Batuul ya wuce kai tsaye ya tura k'ofan ya shiga, tana kwance kan gado ta kifa cikinta, rabin k'afanta duk ya sauk'o daga kan gadon, d'an tsaki yaja ganin bacci takeyi ya ajiye ledojin dake hannunshi ya fita, makulli ya sa ma kofar dakin ya rufe, snn ya sauk'o kasa don tafiya masallaci, bai tarar da Ajiddeh a palon ba ya fice masallaci, sai da akayi isha sannan ya shigo gidan, wutan palon ya kashe ya haura sama, har lokacin Batuul na bacci, a hankali ya d'an tab'a ta alamun ta tashi, a hankali ta bud'e idonta daga nannauyan baccin da take yi, ganinshi a tsaye yasa tayi maza ta mike zaune, had'e rai yayi yace "tashi kici abinci kisha maganinki", baki ta bud'e zatace mishi ita bata jin yunwa, wani kallo da ya bita dashine ya sata zumb'uro baki ta miqe a hankali, yana tsaye ta shiga toilet tayi brush ta fito, kamar zatayi kuka lokacin da ta fito daga toilet d'in dan har ta fara bleeding kuma bata san inda xata samu pad ba, har lokacin da hijab a jikinta, kan gadon ta koma ta zauna a d'arare, tana tsoron b'ata bedspread d'in, "Ni zan tashi in kawo miki abincin", ya tambayeta yana jifanta da wani irin kallo, jiki a sanyaye ta mik'e zata sauk'o daga kan gadon ta take dogon hijabin dake jikinta, fad'uwa tayi k'asa ji kake tim, y'ar k'ara ta saki da yasa Abu saurin k'arasowa wajenta, d'agota yayi yana kallon idonta da ya cicciko yace " c'mon kin cire hijabin nan ko sai na b'ata miki rai yanxun nan, yhu are bothering me fa a gidan nan", raurau tayi da idonta tana tsoron ta cire hijabin dake jikinta ko tayi staining kayanta, ganin ta tsaya taqi yin abunda ya sata ya sa ya d'age hijab d'in da take qin cirewan, y'ar k'ara ta saki ta d'urk'ushe a wajen, binta yayi ya kamota yace "ina miki wasa ko", kai ta shiga girgiza mishi tana hawaye, yace "Au kuka ma kika sami daman yi?", sulalewa ta shiga yi daga rik'on da yayi mata zatayi k'asa, ya wani fixgota yana mata mugun kallo yace, "I will slap you right now, meke damunki?", shiru tayi ta kasa mishi magana, tsaki yayi ya turata "tashi ki d'auki abincin nan" ya fad'a mata a tsawace, jiki a sanyaye ta tashi ta isa inda ledojin suke tana hawaye, a hankali ta shiga bud'e ledan, pad ta fara cin karo da, ajiyar zuciya ta sauk'e ganin pad d'in a ciki, a hankali ta d'ago idonta taga ita yake kallo a tsayen, harara ya sakar mata da yasa tayi saurin d'auke kanta, maza tayi ta ciro pad d'in daga cikin Leda ta miked da sauri ta shige toilet ta banko k'ofar, bin inda tabi yayi da kallo, tsaki yayi tareda girgiza kai, sae kuma yyi murmushi ya fita daga d'akin. Palo ya koma ya kwanta, remote ya d'auka yayi powering TVn, yunwa yakeji amma bazai iya tashi ba, he is too stressed, kitchen ya koma ya had'a coffee, snn ya dawo parlour ya jinginar da kanshi kan sofa yana kurb'an coffee d'inshi a hankali, tasha ya canja daga TLC zuwa NATgeo Gold, don Ajiddeh ke kallon TLC, d'an tsaki yaja tunawa da yayi da ita da shirmen da ta gama yi mishi d'azun, ko kadan bae yi nadamar abinda yyi mata ba don ta kai sa bango, iska ya furzar daga bakinshi yaci gaba da shan coffeensa a hankali, ta baya yaji an rungumeshi, ko ba k'anshin turarenta ba yasan ita ce, ya b'ata rai, a hankali cikin rad'a tace mishi, "baby fushi kayi", k'in kulata yayi kamar baisan tana wajen ba sae dae he was so surprise bae yi tunanin xata sakko da wuri haka ba, kai it's vry unusual of her ma kawae, sae dae if she's up to something, zagayowa tayi ta gabanshi ta zauna kan cinyarshi tareda sak'alo hannayenta duka biyun wuyanshi tace "babe, am am sorry", ci gaba yayi da kallonshi kamar baiji mey take cewa ba, fuskanta ta kawo daidai nashi tace "talk to me mana babe, am truely remorseful wllh, sae daga baya naga ban kyauta ba forgive me plss, in dae akan....." Kasa ambaton sunan tayi, cije leb'enta tayi daga baya ta d'anyi murmushi ta kalleshi tace "indae akan Sister Batuul ne I promise baxa mu sake samun matsala ba", rintse ido tayi jin sunan Batuul ya fito daga bakinta, da mamaki shi kam yake kallota jin ta ambaci Batuul as her sister, anya Ajiddeh bata da brain disorder ma kuwa, k'ara shigewa jikinshi tayi tace "Yes our sister, I mean it, I was so stupid da na dinga yin abubuwan da nayi maka, I don't know what came over me that I reacted that way calling her names, but babe I promise bazan sake ba, kayi hak'uri kaji, I was just being pessimistic about her , thinking zaka sota if she stays here, but yanxu I have realised my mistake, she is like a sister to me also, I will gladly keep her in my house, I promise" a hankali ta kare maganar ta d'ago kanta tana kallon kyakkyawan fuskanshi, lumshe idonshi yayi sannan ya bud'esu, rungume shi ta sake yi murya can kasa tace "Trust me babe" rungume ta shi ma yyi sosae, ya lumshe ido yace "why didn't you realise it since then, but anyway am happy that you finally realised it, kinga yarinyar nan bata da matsala, nasan she will b obedient to you indai har kika kwantar da hankalinki kika jata a jiki, zakiji dad'in zama da ita, am also sorry for everything Honey" kai ta gyad'a mishi tace "nima nasan bata da matsala baby, kasan sharrin shaid'an kuma da irin son da nakeyi maka, I can't risk seeing you with another woman, zan Iya mutuw....", hannu yasa a bakinta yace "shhhh, I will always be yours alone" kallonshi tayi tace "promise", bakinshi ya d'aura kan nata tare da janyota jikinshi, sai da ya gaji dan kanshi ya saketa, k'ank'ameshi tayi jikinta ta saki wani mugun murmushi, hiran da suka gama da Mummy d'azu ta tuna, da kuka dama ta shiga d'aki bayan Abu ya haura sama ya bar ta falo, waya ta d'auka ta shiga neman layin Mum, bugu biyu ta d'aga, wani irin razanannnen k'ara Ajiddeh ta saki da har ya tsorata Mum d'in ya sata janye wayar daga kunnenta tana tabbatarwa ko da Ajjideh take waya, a rikice ta maida wayan kunnenta ta shiga tace "keh daina shirmen nan kiyi min magana, mey ya faru kuma", Cikin sheshek'a ta gama zayyanewa Mum yadda akayi, da mamaki da tsoron jin abinda Ajiddeh ta gama fad'a mata ta sauk'e ajiyar zuciya tace, "wane rashin hankalin ne ya kaiki zagar mishi y'ar uwa harda ce mata karuwa a gabanshi, keh kinsan halinshi mey ya kaiki yin abunda har zai dakeki, wama yace kije ki tafka wannan haukan wai", cikin sheshek'a tace "Mum ni bansan ya zanyi bane, I was furious a lokacin, raina duk ya gama b'aci, bazan iya jurewa ba shiyasa nayi mishi wannan haukan, ko ba komai dai ai shima ranshi ya b'aci, sai ita wannan y'ar iskar, da na samu nayi laying hannuna kanta wlhy da sai yadda Allah yayi da ita dan tsanar da nake mata baya misaltuwa", katseta Mummy tayi da cewa, "naji ya isa, d'azun nan su Zainab suka wuce Tchad, kuma duk kan aikin namu na turasu dan ni Daddynku ya hanani zuwa, toh yanzu abinda nakeso dake, siyasa zaki shiga yi masa ki nuna masa kinyi kuskure kuma kin gane laifinki amma hakan bazai sake faruwa, ki nuna mishi kina k'aunar ita yarinyar har sai ya aminta da hakan, itama ki nuna mata k'auna har sai mun samu munyi maganinsu shi da itan dukkansu da ma duk wani munafiki dake gefe, ni yanxu haka ba kud'i hannu na kuma Dad d'inku rabon da ya bani kud'i har na manta dan cewa yayi baisan mey nakeyi dasu ba, wai har sai na nuna mishi abu d'aya da na tsinana mai amfani da nayi da kud'in, yanzu haka nayi niyyan k'iranki in miki bayani akan tafiyansu Zainab d'in sai kika rigani, kud'i kawai xaki turo har Zainab d'inma wani senator da yazo wajen Babanku ya ganta yace yana sonta amma kuma yanada mata sannan Babanku yace ya turo dan ya bashi ita shine mukeso musan yadda za ayi da Matan nashi dan bazan yadda da kishiya ba, kinga kina turo kud'in sai ayi komai a gama, an jefi tsuntsu da dutse d'aya", Hankalin Ajiddeh ne ya fara kwanciya jin bayanin da Mummy ta gama yi mata tace "Mummy wannan kud'i duk ba matsala bane, yau da safen nan ya rubuta min cheque d'in miliyan uku da nace mishi ina buk'ata, banmaje nayi cashing d'insu ba a bank, xan turo sai ayi abinda ya kamata, amma Mummy d'ayan ne ban iyawa, wlhy na tsaneta yadda baki zato, bazan iya nuna ina sonta ba, Kawai in ansamu anyi abinda za ayi ta tattara nata ta barmin gida", tsaki Mummy taja tace "ai kinji ki, toh kije kiyi abinda kika ga dama tunda baza ki d'auki abinda na fad'a miki ba", cewa tayi "Mum ba hakane bane, kawai ni kallonta ma bana son yi ne", Mummy tace "na fahimceki, amma kowane mutum yana son a so d'an uwanshi, da hakan sai ya dad'a kyautata miki, kinga ko ta dalilin ta zaki moreshi bare shi dake son y'an uwanshi, lokaci d'aya zai Iya rabuwa dake ya maida wata gurbinki, amma y'an uwanshi bai tab'a iya canja su, shiyasa nakeso ki nuna mata so", cikin hanzari Ajiddeh tace, "Mummy abar wannan maganan, ni yanzu xan turo komai a gama", ta tsorata da jin da tayi za a iya canja ta, Mummy tace "toh shikenan yanxu ki tashi ki shirya kije ki bashi hak'uri ki nuna kinyi nadaman duk abubuwan da kikayi", wani munafikin murmushi tayi ta sake shigewa jikinshi da ta dawo daga tunaninta, shi kam Abutturab tunani yadda zaiyi da Batuul Kawai yakeyi duk randa Ajiddeh ta gano ita d'in matarsa ce yasan gidan nn sae yayi musu kadan, tunanin Batuul kawai yakeyi zamansu a wajen, Ajiddeh ta kalleshi tace "baby na fara jin bacci muje mu kwanta", kallonta yayi dan shi sam bayajin bacci, Batuul ma kawai yakeson gani yaga halin da take, yace Mata "I will b coming dear, bari in gama program d'innan its interesting, I will meet you up there", peck yayi mata daga haka ta mik'e tayi hanyan stairs, har ta fara tafiya ta juyo ta kalleshi tace "Baby, I will check on my Sister before leaving", da wani munafikin wide smile shimfid'e fuskanta da kana gani kasan yak'e take, kallonta kawai yayi har ta juya ta tafi, ya sauke ajiyar xuciya cikin ransa yace Allah sa har cikin ranki Ajiddeh. Batuul kam bayan ta saka pad d'in sai da ta leqo kanta taga ya bar d'akin sannan ta sauk'e ajiyar zuciya ta fito dan mugun yunwa takeji, direct wajen ledojin ta nufa ta tsugunna wajen ta shiga bubbud'esu, na farkon drugs d'inta ne ciki, matsar dasu gefe tayi ta bud'e sauran, da murna ta shiga bud'ewa ganin abincin favorite restaurant d'inta Gordon Ramsay, pack d'in ta bud'e taga roast chicken, lavender, apricot, honey, d'ayan bowl d'in ta duba taga starter ne green apples, turnips sai watercress, wani irin farin ciki kawai takeyi, d'ayan pack ta sake dubawa pasta ne with shrimps kebab, babu b'ata lokaci ta tashi ta wanko hannunta, ko using spoon d'inma baza ta iya ba, sai da taci ta k'oshi ta maida ledojin gefe ta tashi ta cire kayan jikinta ta fad'a toilet, ko ta kan Maganin ma bata bi ta shiga tayi wanka abinta, ta fito kenan d'aure da towel taji an turo k'ofan d'akin, a razane ta d'ago kanta warce ta gani tsaye bakin kofa yasa hanjin cikinta mugun k'adawa, Ajiddeh ta karaso tana murmushi tace "Sannu sister ya jikin?" K'asa cewa komae Batuul tayi sae kallonta take, kuma da ganinta kasan a tsorace take, Ajiddeh bata damu da hakan ba sae ma murmushi da take tace "Amma kina da pad kuwa ko in dauko maki a daki" Batuul ta sunkuyar da kanta da kyar tace "Ina da shi" Ajiddeh tace "Toh Allah ya sauwake, kin sha magani kuwa?" Batuul tace "Ynxu xan sha," Ajiddeh tace "Toh sannu, ni na tafi in kwanta sae da safe" Batuul ta kalleta don har lkcn ta k'asa yarda Ajiddeh ce, a hnkli tace "Toh sae da safe na gode" Ajiddeh tace "Yauwa" sannan ta fice, Batuul ta sauke ajiyar xuciya ta isa inda kayanta yake cike da mamakin Ajiddeh, lotion ta shafa, snn ta shafa turarrukanta masu sanyi kamshi ta fiddo wani sabon sleeping gown dinta mara nauyi me d'an karamin hannu ta sa, ta xura gashinta cikin net, ledan maganinta ta bude ta fiddo magungunan ta sha snn ta ajiye su gaban mirror, ta nufi switch din dakin ta kashe wuta kenan don kwanciya xata yi aka bude kofar dakin, kin kunna wutan tayi don bata son ya ganta ba hijab kuma ta k'asa barin wajen, ya shigo dakin ya rufe kofar, da sauri ta nufi inda hijab dinta yake xata dauka yyi saurin fixgota yana mata wani irin kallo cikin duhun yace "Wae me kike boye min da ban sani ba a jikin ki, baki sanin muhimmancin Hijab sae na shigo dakin ki don rainin wayo koh?" Kokarin kwace kanta ta shiga yi a hannunsa yace "Stay still kar in mareki" sunkuyar da kanta tayi bata ce komae ba, a hankali yace "Ya cikin?" Kin cewa komae tayi ya D'ago kanta yace "Am talking" ta rufe ido kmr yana ganinta murya can k'asa tace "da sauki" yace "Sure?" Shiru tayi bata ce komae ba, yace "ko kina son a maki massaging Abdomen..." Da sauri tace "No na samu sauki" murmushi yyi yana kallon d'an karamin bakinta dake motsi a hankali, yace "Sure?" Runtse ido tayi ta janye hannunta xata bar wajen, ya fixgota jikinsa, wani irin faduwar gaba taji jinta a jikinsa, suka ji an bude kofa can corridor, saketa yyi da sauri ya juya ya nufi kofa. [8/22, 14:48] Umar Dalha: BATUUL 54 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Yana fita d'akin Batuul a corridor ya tarar da Ajiddeh a tsaye, wani irin kallo ta bishi dashi ganin ya fito d'akin Batuul, bak'in cikinta ta shiga dannewa dan batason tayi anything stupid, murmushin yak'e tayi tace "Baby naga har na fara bacci baka shigo ba shine nace bari in fito in dubaka, ashe kana d'akin Sis dinmu", ta fad'i da wani irin expression shimfid'e fuskarta ta sake kallon d'akin, hannunta ya kamo yace "Yeah ita na shiga dubawa, kinsan batajin dad'i", tace "hakane, nima saida na shiga na dubata before in shiga ciki", yace "kin kyauta", ya rungumota jikinshi suka shiga ciki. Batuul kam yana fita ta tabe baki ta fad'a gado, ko yunk'urin rufe k'ofarta batayi ba tayi kwanciyarta dan ko ta rufe in ya tashi bud'ewa yakeyi, addu'ar bacci tayi ta tofe jikinta da d'akin taja duvet ta kwanta, bata fi minti goma a kwance ba bacci ya d'auketa, k'arfe biyar daidai ta tashi da addu'a bakinta, tana zaune kan gadon har biyar da rabi, sai da taji an idar da sallah ta mik'e ta shige toilet, wanke toilet d'in ta farayi tukunna tayi wanka, mayukanta ta shafa ta gyara gashinta ta tufke da ribbon sannan ta isa closet d'in kayanta, tsayawa tunani tayi na kayan da zata saka, wani gown d'in atampa ta ciro ta saka, ta fesa turarruka sannan ta d'au vacuum cleaner ta tsaftace d'akin tsaf, ta gyara gadonta ta kunna electric burner ta saka turaren wutan, lokaci d'aya d'akin ya d'au k'anshi, sakkowa tayi k'asa ta shiga kitchen, wutan ta kunna taga kitchen d'in na nan yanda ta barshi, shiga tayi ta gama examining komai taga mey zata dafa, fridge ta bud'e , nama ta ciro ta shiga had'a lasagne, tayi peanut butter smoothie, Garlic egg Muffins, sannan tayi offals pepper soup, Abuturrab na dawowa masallaci yaga wutan kitchen a kunne sai dae bai bi ta kan kitchen din ba ya wuce sama dan a tunaninshi Ajiddeh ta sauk'o tayi wani abin, 7:30 Batuul ta gama duk abubuwan da zatayi ta jera komai kan dinning, gyara gidan tayi, takwas dai dai ta gama ta saka turaren wuta gidan ya bade da kamshi me ddi, tea ta hada jin cikinta ya fara ciwo don ta samu ta sha magani, tana gama sha ta haura sama ta dauki magungunan ta sha snn tayi kwanciyarta don sae goma take da lectures, abinda zatayi ne ta rasa kawai ta janyo macbook d'inta ta shiga kallon Boss Baby. 8:30 Abuturrab ya fito sanye da pyjamas d'inshi, tun daga bakin kofa yake jin k'anshin masu dad'i sun had'e gidan, kanshin turaren wuta da na abincin da ta dafa, sauk'owa kan stairs d'in yayi, yadda gidan ke shining ya bi da ido har ya k'araso dining, da mamaki yake kallon kan dinning d'in ganin anyi arranging abinci Kai, k'arasowa yayi ya bubbud'esu, aroma din abincin ya bugi hancinshi, maidawa yayi ya rufe, for the first yaji Batuul ta birgeshi, yasan training d'in Aunty ce ita din, murmushi yayi ya haura sama, d'akinta ya nufa ya tura kofar ya shiga, kwance ya ganta kan gado a kife, bayanta kawai yake gani sai screen din computer, ya karasa cikin d'akin don ganin abinda take kallo, har yazo bakin gadon bata sani ba sai tuntsirar dariyar da take ta faman yi, jin mutum ya zauna kan gadon yasa ta saurin mik'ewa zaune, matsawa tayi daga kusa dashi ta koma can k'arshen gadon, kallonta kawai yake, haka kawae ya samu kansa da murmushi, a hankali ta d'ago idonta taga ita yake kallo, maza tayi ta d'auke nata idon cikin sanyi tace mishi "ina kwana" ya bude ido yace "Morning! Ashe kin iya tashi da wuri?" Kauda kai tayi tace "Eh!" Yyi shiru yana kallonta, satan kallonsa tayi jin shiru suna hada ido ta dauke nata da sauri, ya d'aga kafada yace "Ya dysmenorrhea, ko dama na kwana daya yake maki?" D'an turo baki tayi ta juya masa baya, yyi murmushin da bae san dalilinsa ba, bae kuma ce mata komae ba ita ma bata juyo ba sae dae addu'a kawae take ya tashi ya tafi, wayarta ne dake gaban mirror ya shiga ring, ta mike a hankali ya bita da kallo har ta isa gaban madubin ta dauki wayar, wara ido tayi tana murmushi ta d'aga, sae kuma ta hade rai tace "Kin ban mamaki farida friendship din kenan dama sae yau kika san za ki kira ni koh?" D'aga daya bangaren farida tace "Wayyo Afuwan Besty, kusan kullum sae nayi xancen ki gun Ammah I just don't want to call ki fara min kuka ne wllh, waow hope you are enjoying ur new home, tell me how it is over there, have you made friends? Ina jarababbiyar matar ya Abu, how are you coping with her, hope she isn't giving u tough time...." Batuul ta xaro ido tace "Kai farida spare me those questions, hakuri ya kamata ki fara bani da yawa" Farida ta fashe da dariya tace "Ohhh yhu need to see how happy I am besty, ur voice is so lively, from all indication I guess u are enjoying it over there...." Batuul tayi murmushi a xuciyarta tace uhm lallai kam, ko ba enjoy ba, a fili tace "Ni dae ina Ammah fa?" Farida tace "Tana daki wllh let me put her on the line" Batuul tayi murmushi tace "Alryt!" Juyawa tayi tana kallon Abuturrab da ya kafa mata ido tayi maza ta dauke kanta, muryan Ammah ta ji da fara'a tace "Bitti?" Batuul tayi murmushi ta sulale nan k'asa ta xauna a hankali tace "Na'am Ammah ina kwana?" Ammah tace "Lfya lau Bitti ya gida? In ji ba matsala dae koh? Kar fa ki boye min don Allah" Batuul tace "Babu Ammah ya su Abui?" Ammah tace "Lfya lau suke, ya karatu kina xuwa dae koh?" Batuul tace "Ehh ina xuwa Ammah" Ammah tace "Ma'sha Allah! Ina Abuturrab din" kallonsa tayi taga ita yake kallo, a hankali tace "Ga shi nan, in bashi?" Ammah tace "Bashi!" Hade rae yyi yana kallonta, ta sunkuyar da kanta ta mike a hankali ta isa gabansa ta mika masa wayar, karba yyi ya fixgota lkci daya ta fado jikinsa tun kan tayi k'aran da take shirin yi ya rufe fuskarta a kirjinsa, tayi lamo tana shakan kamshin jikinsa me dadi, wayar ya kai kunne yayi ma Ammah sallama sannan ya gaisheta, da fara'a ta amsa masa don ba karamin dadi taji ba jin suna ma tare, tambayarsa Ajiddeh tayi yace tana dakinta, nan dae ta dinga masa nasiha kamar yanda ta saba a kan yaji tsoron Allah ya xama me adalci tsakanin matansa, dama irin abinda yake gudu kenan shi, don jikinsa sanyi yake, lumshe ido yyi yana sauraranta, ta kusa minti goma tana nasihan nata har lkcn kuma Batuul na jikinsa yaki saketa gabanta sae faduwa yake don she's not use to that, daga karshe ce masa tayi ya ba Batuul wayar, mika mata wayar yyi ta karba ta shiga kkrin kwace jikinta amma ya ki saketa, k'ara wayar a kunne tayi, Ammah tace "Kina jina Batuul" a hankali tace "Eh Ammah" Ammah tace "Kiyi ta hakuri kin ji Bitti, bbu ruwan ki da Abokiyar xaman ki tsakanin ki da ita sae girmamawa, ki kula da ibadun ki, ki xama me tsafta duk da nasan kina da amma ki kara kan na da, ko da yaushe dakin ki da jikin ki ya kasance cikin kamshi kin ji, Farida na nn xuwa idan sun yi hutu" Batuul ta wara ido cike da murna tace "Toh Ammah nagode, Allah kara girma" Ammah tace "Ameen Bitti sae mun kuma waya" nan suka yi sallama Batuul ta d'aga kai tana kallonsa ta ga idonsa lumshe, kokarin xame jikinta ta shiga yi ya bude ido yana kallonta, ta hade rae tace "Makaranta xan tafi ni" saketa yyi ya mike sanin lkcn tashin Ajiddeh yyi, ya fice daga dakin, bin sa da kallo tayi kafin ta lumshe ido ta kwanta kan gado. Karfe Tara da wani abu ta sakko da shirin tafiya makaranta, xaune ta same su shi da matar tasa kan dinning suna breakfast, Ajiddeh na ganinta ta sunnar da kai don bata so ta sakko ta sameta tana cin girkin ta ba, idon Abuturrab na kanta har ta karaso falon kanta a k'asa ta ce "Ina kwana Anty" Ajiddeh ta kirkiri murmushi tace "Lfya lau sister, ashe kin tashi, nace Aliyu ya shigo ya dubo ki muyi breakfast yace wae ba kya tashi da wuri" Batuul dae bata ce komae ba sae kofa da take kallo, Ajiddeh tace "Toh ki karaso ki karya mana" girgixa kai Batuul tayi tace "A'a na sha tea tun daxu" Ajiddeh tace "Ohk," kofa Batuul ta nufa jin Abuturrab bae ce komae ba, yana ganin hka yace "Ki jira ni gun mota, na aiki driver" toh kawae tace ta fita, Ajiddeh da mood dinta ya canxa lkci daya ta sunkuyar da kai kar ya lura, da sauri ta D'ago tace "Honey ko kuma in kai ta kawae tunda motar biyu ne kar ka makara" ba tare da ya kalleta ba yace "Ae ita ma ta iya driving din, Akwae kudin da xan bata ne shi yasa nace ta jira" Ajiddeh taji kmr ta kwala ihu, wato har kudi xae bata, murmushi ta kirkira tace "C'mon babe nima ae kanwata ce, nawa xaka bata in bata kawae?" Ajiye cup din coffeen hannunsa yyi yace "Don't bother suna da yawa kudin" mikewa yayi yana goge bakin sa da tissue yace "Na tafi babe, sae na dawo take care of ur self for me" yana kai wa nan ya nufi kofa, bin sa da kallo tayi xuciyarta na tafarfasa, tana ganin fitansa ta mike da sauri har tana neman faduwa ta nufi kitchen don lekawa ta window ta ga inda Batuul xata xauna a motar, ae ko dai dai lkcn da Batuul ta bude front seat ta shiga, shi ma ya xaga ya shiga maxaunin driver, ta fashe da kuka da karfi wani mugun tsanar Batuul na k'aruwa a xuciyarta, anya xata iya ci gaba da yin abinda momy tace tayi kan Batuul kuwa, ynxu idan Abuturrab ya ji tana burgesa d'an girkin nan da ta iya ya xata yi da rayuwarta ita da ko indomie ba lallai ta dafa shi ruwa bae yi masa yawa ba, tunanin hakan yasa ta rushe da kuka ta fito kitchen din tana rerawa. [8/22, 14:49] Umar Dalha: 💖💝BATUUL💖💝 55 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Har suka isa makarantar, Abuturrab bae ce ma Batuul komae ba ita ma window kawae take kallo abun ta, sae da yyi parking sannan ta dauki jakarta dake kafarta xata fita yace "Ki na da hankali kuwa, wa ya baki izinin fita" komawa tayi ta xauna ta jinginar da kanta jikin kujerar da take xaune, kallonta kawae yake, ita kam bata ma san yana yi ba, ya wani daure fuska yace "Kin yi breakfast ma kuwa" ba tare da ta kallesa ba tace "Na sha tea" a d'an tsawa ce yace "Hey look at me!" Juyawa tayi tana kallonsa yace "Yaushe na fara wasa da ke xaki wani dinga dauke min kai ina magana" tagumi tayi tana kallonsa ko kifta wa bata yi, dariya ta basa ganin yanda ta tsuke baki, yace "Ayt, naga alama don kin ga na fara bi ta kan ki ne ynxu, ina kare ki gun matata shi yasa kike son ki raina ni koh?" Ita dae bata ce komae ba kuma bata fasa kallonsa ba, kayan jikinta ya kalla da d'an karamin bakin gyalen da tayi rolling a kai yace "Wae ma kina matar aure xaki dinga irin wannan shigar kina xuwa makaranta kina da hankali kuwa" kallonsa take har lkcn kuma bata ce komae ba, kafin ya kara cewa komae ta kalli agogon wrist dinta tace "Its almost time for lecture" tana fadin hka ta dauki jakarta ta bude motar ta fice, bin ta yyi da kallo cike da mamakin ta, bae san lkcn da yyi murmushi yana shafa kansa ba, kamar wanda ya tuna abu ya bude motar ya fita ya kulle sannan ya bi bayanta, tafiya take kamar me tausayin kasa tana rataye da jakarta, ko kai ka ganta sae ta burge ka don a nutse take tafiyar, kamar ance ta waiga taga yana biye da ita a baya, ae bata san lkcn da ta tsaya ba gabanta na faduwa sosai, ya karaso ya xaga gabanta yana facing dinta, sunkuyar da kai tayi, yana mata wani irin kallo yace "Are yhu stupid? Yhu walked me out ina maki magana?" K'in cewa komae tayi, ya gyada kai yace "Gud nasan maganin ki?" Kudi ya ciro aljihunsa ya mika mata ba musu ta risina ta karba murya can kasa tace "Thank yhu" wayarsa ya mika mata fuskarsa daure yace "driver xae kira ki" ta karba tace "Toh" tafiya yayi ya bar ta nan tsaye ta bi sa da kallo snn ta ci gaba da tafiyarta ita ma, sae taji for the first Abuturrab ya burgeta, "Upon all, he is kind at heart kmr yanda farida ta gaya mata, he always care and show concern" murmushi tayi ta karasa Dept da sauri ganin few minute ya rage a fara lecture. Karfe sha biyu saura suka fito daga lecture, Batuul tace "Lets get something to eat frnd am hungry" Aisha tace "It's ok, same with me here" suna tafe ne bbu me cewa komae cikinsu har suka iso wani guri da Shaheed ke xaune da abokansa kusan su biyar, biyu bakake kmr sa uku kuma turawa, hiran su kawae suke shi kuma yana duba wani textbook dake hannunsa" Batuul ta hade rae ganin yanda suke kallonsu tun kan ma su karaso, suna Karasowa wani dake xaune gefen Shaheed yace "Hey Aysha!" Aysha ta tsaya tana murmushi tace "Hei Usman how you, how's lecture?" Usman yace "Alhmdllh, dat gal! Is she ur frnd? So haughty of her!" Sae a sannan Shaheed ya d'aga kai yana kallonsu, Batuul ya bi da kallo don ko tsayawa bata yi ba ta ci gaba da tafiyarta, ya lumshe ido ya bude ya ci gaba da karatunsa, Aysha tayi dariya tace "No, no, not at all, she's not! just dat ba ku saba bane, Well! We'll chat later Usman, bye for now" yace "Ayt! Take care of ur self bae" dariya tayi ta bi bayan Batuul da sauri. Xaune ta sameta waiter dake aiki a wajen yana tsaye kusa da ita yana tambayar me xae kawo mata, tace "Just caramel bun and frapuccino" mutumin ya juya yana kallon Aysha yace "yhu ma'am?" Tace "Same also!" Juyawa yayi ya tafi kawo masu. Aysha tace "Shine kika tafi kika bar ni koh?" Batuul ta kalleta murmushi dauke fuskarta tace "Yea naga yhu were busy ne" Aysha tace "Ayt, amma ko gaisawa ne ki dinga yi da mutane don ku saba mana" Batuul bata ce komae ba sae juya wayar Abuturrab dake hannunta take, Aysha ta ce "Kawo in sa maki digit dina, it's gud ace mun yi exchanging" mika mata wayar Batuul tayi ta karba ta kunna, "Woaww is this ur sister on the screen, kai she's so beautiful wallahi, ya aka yi ke baki yi hasken ta ba" hade rae Batuul tayi ba tare da tasan ta ma yi hakan ba, don ko lura da hoton screen din ma bata yi ba kawae ta fito da wayar daga jaka ne don ta duba agogo, Aysha bata damu da shirun da Batuul tayi mata ba tayi ta koda kyan Ajiddeh, daga karshe ta sa mata nmbrta tayi mata saving ta mika mata, Batuul na karban wayar ta maida jakarta snn ta maida hankalinta kan abincin da aka dire masu gabansu, ta riga Aysha gamawa snn ta fiddo wayar don hoton ya tsaya mata a rai haka kawae, kare ma hoton kallo kawae take, bata san lkcn da ta ja tsaki ba Aysha ta kalleta tace "Ya dae" yake tayi tace "Naga time ya wuce ne, baxa kiyi sllh ba?" Aysha tace "No bana yi" Batuul bata ce komae ba ta shiga gallery duk tayi mark din hotunan Ajiddeh dake wayar har na screen din ta watsa su a kwandon delete. Tana gama hakan ta ja tsaki ta fiddo kudi jakarta tace "Tambayar mana bill Aysha" ita ta biya kudin duk yanda Aysha ta so biya bata yrda ba, suka mike don komawa Dept. Karfe hudu da wani abu suka fito daga lecture, Aysha tace "kinga tare da aunt dina xa mu wuce tana jirana, Bus xa ki hau ko taxi?" Batuul tace "No xa a xo daukana ne daga gida" Aysha tace "Ayt sae gobe, don't forget Karfe 8 muke da lecture fa" Batuul tayi murmushi tace "Insha Allah ki gaida aunt din ki" Aysha tace "Xata ji, nima ki gaidar min da pretty aunt din ki, so fyn da ita ga gashi, ina nan xuwa wataran in ganta" dauke kai Batuul tayi kmr bata ji ba har Aysha ta bar wajen, waje Batuul ta samu ta xauna, ko minti goma bata yi a gun ba wayar jakarta ya shiga vibrate ta ciro, d'agawa tayi daga daya bangaren yace "Are yhu done for today?" Mikewa tayi tace "Yea!" Ya katse wayar, ta nufi inda tasan xata gansa. Sauke glass Abuturrab yayi yana kallonta, sae kuma ya fito ya bude mata back door sanin gaba xata taho kuma Ajiddeh na ciki, Ajiddeh ta bi sa da kallon mamaki baki bude taji kamar ta rusa ihu, don da kawae so tayi Batuul ta zagayo ta bude ta ganta a xaune sae ta ga ynda xata yi, meye haka Aliyu ke yi, abinda bae taba yi mata ba wae bude mata mota ta shiga, shine yake bude ma shegiyar nan, what have come over him haka, ita kanta Batuul tayi mugun mamakin abinda Abuturrab yyi sae kallonsa take, infact shi kansa sae da ya ji wani iri a lkcn, don bae taba yi ma wata 'ya mace haka ba apart from Ammahn sa, what's he doing, A hankali Batuul ta raba ta gefensa kanta a kasa ta shiga motar, k'asa komawa seat dinsa yyi ba tare da ya kulle mata motar ba duk da hakan ya so yi don ganin irin kallon da Ajiddeh ke yi masa, samun kansa yyi da rufe motar a hankali, snn ya juya ya koma seat dinsa, banda xufa babu abinda Ajiddeh ke yi cikin motar duk da Ac'n da ke kunne, Batuul tayi mamakin ganinta cikin motar sae a sannan ta gane me yasa yayi hakan sae ta ji ddi da bae bar ta taje gaban ba, does he really care haka dama, d'an murmushi tayi tana kallon Ajiddeh tace "ina yini?" Da kyar Ajiddeh ta Hadiye wani abu da ya tsaya mata a makogwaro tace "Lfya!" Abuturrab ya d'an sata kallonta kafin ya tada motar suka bar wajen, sae da ya fara biyawa domino's, yana isa yyi parking ya fito, Ajiddeh da ke cika har lkcn tana batsewa ta bude motar ta fito ita ma, Batuul dae ta bi su da kallo, kallonta Abuturrab yyi yace "No no ba sae kin fito ba kiyi xaman ki a mota" da sauri Batuul ta dauke kai tana kallon window ta gefenta tana danne dariyar da ke shirin taho mata, bae damu da halin da Ajiddeh ta shiga a lkcn ba na kunya ya bar ta nan yyi gaba abun sa ya shiga domino's din, bayan kusan 10 mins ya fito rike da kwalayen pepperoni pizza da ledoji har biyu me dauke da cold stone ice cream, yayi mamakin ganin Ajiddeh tsaye har lkcn kmr warce ruwa ya ci, ya bude back seat ya ajiye kwalayen hannunsa da ledoji snn yana kallon Ajiddeh yace "Shiga toh mu je" Batuul dae har lkcn waje take kallo tana murmushi. Da kyar Ajiddeh ta iya bude motar kamar mara laka ta shiga, shi ma ya shiga ya tada motar suka bar wajen, tafiyar minti goma yayi suka iso gida, yana gama parkin Ajiddeh ta fice tayi cikin gida kmr xata tashi sama, Batuul ta fito ta kwashi kwalayen, fitowa yyi shima ya fito da ledan ice cream din snn ya rufe motar ya fara tafiya, bin bayansa tayi har suka shiga falon, Ajiddeh na tsaye tsakar falon, Batuul ta ajiye kwalayen pizzan hannunta shi ma ya ajiye ice cream din hannunsa, kwashe kwalin da ice cream din gaba daya Ajiddeh tayi ta nufi sama don dama shi take jira a falon, Abuturrab ya bi ta da kallo yace "Hey! Guda daya fa kadae ne naki a wajen nan babe" ko kallonsa bata yi ba ta haura sama fuu, Batuul ta kauda kai tana murmushi, Abuturrab ya juya yana kallonta yace "Ohh dariya ma kike koh, ae ko xa ki tsaya da yunwa ko kuma ki shiga kitchen kiyi girki" yana kai wa nan ya haura sama, Batuul ta tabe baki ita ma ta haura sama, dakinta ta shiga ta cire kayan jikinta ta shiga bayi ta sakar ma kanta warm shower, ta jima a bayin kafin ta fito daure da towel tana goge dogon gashinta da karamin towel, bude kofar aka yi ta kwalalo ido ta tsaya cak gabanta na faduwa, Abuturrab ya shigo dakin, kauda kai yyi da sauri suna hada ido yace "Erm my.. my phone, ina wayata?" kmr munafuka ta nuna masa jakarta, ba tare da ya kalleta ba ya nufi jakar ya bude ya fiddo wayar, kunna wa yyi yaga blank screen sae wall paper bbu photon dake gaban screen din, kallonta yayi kafin ya shiga gallery, mamaki ya cika sa ganin wayam sae few photos dinsa da ya rage bbu na Ajiddeh ko daya, hade rae Batuul tayi sanin abinda yasa yayi still a wajen, ta ci gaba da goge gashinta ta nufi gaban mirror, bin ta yyi da kallon mamaki, ta ja kujera ta xauna tana ci gaba da goge gashinta, karasawa gun mirrorn yyi ya fixgota ya juyo da ita yana mata wani irin kallo yace "Yhu deleted my wife's pics from my phone" ta wani hade rae tace "Toh na sani ne, ko ba mistake bane" bude baki yyi yana kallonta, ta turo baki ta kauda kai, bae san lkcn da murmushi ya subce masa ba, yana kallonta a hankali yace "Me ya shigar dake gallery nah?" Ta bude ido tace "Mistake I said!" Kallonta ya shiga yi daga kasa xuwa sama, ta dauke kai fuskarta daure, bata ankara ba sae ji tayi ya fixge towel din jikinta, ta rike gam ta xaro ido a tsorace Tace "meye haka ya Abu" yana mata wani irin kallo yace "Mistake" ta bude baki xata yi magana sae gani tayi ya kuma fixge towel din, a rikice tayi kasa tace "Nashiga uku don Allah stop this" bin ta yyi kasan yace "Sae kin gaya min me hoton matata ya tsare maki a waya da kika goge" a rude tace "No plss, Don Allah kayi hakuri ban san...." Janye towel din yyi gaba daya ta kwala ihu yyi saurin jawota jikinsa ya hade bakinsu, daukewa ne kawae numfashinta bae yi ba lkcn, shi kansa sae da yaji wani shock a lkcn, ya lumshe ido a hankali ya shiga kissing dinta kamar xae hadiyeta. [8/22, 14:49] Umar Dalha: 💖💝BATUUL💖💝 56 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Ba karamin rudewa Batuul tayi ba a lkcn, duk jikinta ya dau rawa sae tutturasa take tana neman kwace kanta amma ta kasa, gajiya tayi ta tsaya ganin ba saketa xae yi ba, banda hawaye babu abinda take, duk jikinta yayi sanyi, ko lura da halin da ta shiga bae yi ba don idonsa a lumshe suke, yakai minti biyar yana abu d'aya kmr wanda ya tuna abu ya xame bakinsa daga nata a hankali, sae dae ya kasa kallonta, kuka ta fashe da ta xame jikinta daga nasa tayi saurin janyo towel dinta ta rufe jikinta, bae bari sun hada ido ba ya mik'e ya fice daga d'akin da sauri, kuka sosai ta shiga yi bayan ya fita, takai minti goma tanayi daga baya ta mik'e da kyar ta koma toilet ta wanke fuskanta, vanity stool d'in ta jawo ta zauna jiki a sanyaye, kallon lips d'inta da ya koma ja ta tsaya yi jikin mirror, a hankali ta d'aura babban yatsan ta kai tare da lumshe ido hawayen dake makale idonta ya gangaro, bud'e ido tayi ta janyo man shafanta, jiki a sanyaye ta gama shafa man taje ta sako kaya, har ta gama ta kwanta jin lips d'inta take ba daidai ba, gashi bata daina jin taste din bakinsa a nata ba, lumshe ido kawai tayi ta kwanta. Ajiddeh kam na xaune dakinta bayan ta watsar da kwalaye da ledan da ta shigo da, duk abun duniya ya taru yayi mata yawa, banda huci babu abinda take yi ita kadae, wannan wace irin jarabace aka turo mata gidan ta, anya ma kuwa zata iya ci gaba da yin wannan abinda Mummy ta fad'a mata, wai dan wulak'anci Aliyu har shi zai wani tashi ya zaga ya bud'ewa y'ar iskar nan k'ofa bayan ita ba yi mata yake ba, to me hakan ke nufi, fad'awa tayi kan gado tana maida numfarfashi, da tun farko tasan zuwansu Nigeria da Abutturab zai zama haka da bata barshi ya tafi ba, ko ita da taje ta dawo, wani hawayen bak'in ciki ne ya shiga zubowa daga idonta, ta mike xaune ta fashe da kukan takaici, ita kam ya xata yi da Batuul? wayanta ne ya shiga ringing, jawowa tayi da sauri ta kara a kunnenta, jin mai k'iran ya sata share hawayenta da sauri, daga d'aya b'angaren Mummy tace "Ajiddeh Jiddeh, jiddum fi khair ana, useki y'ar albarka, naga abin kirkin da kika turo, ba b'ata lokaci yanxu zan turawa su Zainab, daga can za a turo miki ba sai sun dawo gida ba, zamuyi maganan duka details d'in in suka iso", toh kawai ta iya cewa dan wani irin tuquqi da zuciyarta keyi mata, Mummy ce taci gaba da ce mata "kuma kici gaba da yi kamar kina son nata, dan komai yazo mana da sauk'i, ko meye ya sameta kinga baza ayi zarginki ba dan babu wanda yasan kina k'inta, shi kuma sai sun dawo d'in sai muji yadda nashi abun yake", tace "toh Mummy duk zanyi", da haka suka katse k'iran dan maganar ma wahala take bata, turo k'ofar d'akin yayi ya shigo, da ido yabi kwalayen da ice cream packs d'in dake zube a k'asa har wasu sun fara malalewa, tattarewa yayi yazo bakin gadon ya zauna, hannu yasa ya d'agota kanta yana kallon yadda idonta ya canja, "kina da lafiya kuwa, zaki d'ebo abincin kixo ki watsar dasu anan kamar a bola na tsinto kudin, kina ma da hankali kuwa?", zuciyarta ta shiga dannewa tasa hannu tana d'an murza kanta tace "Baby kaina ke min ciwo, har jiri jiri nake gani shiyasa ma kaga komai a k'asa, ba zubarwa nayi ba", kallonta yayi yana examining d'inta gabaki d'aya sannan yace "kin fad'amin? ko kuma kinada maganin sha ne", kai ta girgiza ta shige jikinshi tace "c'mon babe, kasan banso kana damuwa shiyasa ban fad'i maka ba, I will b fine, you don't worry", ta k'ara shige mishi jiki, hannu yasa kanta yana shafa gashinta mai d'an karan laushi ya lumshe ido sae dae ji yake kmr har lkcn bakinsa na cikin na Batuul, a hankali yace "tashi kici abinci sai ki kwanta", ba musu ta tashi ta janyo kwalin pizza, har ta bud'e ta d'au d'aya zata kai baki, ta kalleshi da wani irin murmushi fuskanta ta wara ido tace "babe", d'ago kai yayi ya kalleta tareda d'aga mata giranshi d'aya yana jiran jin mey zata ce mishi, "our Sister, bari inje in kai mata share d'inta, nasan she is famished, daga school ma take kaga dole taji yunwa", k'ok'arin mik'ewa tayi yasa hannu ya dawo da ita ta zauna tana kallonshi, murmushi yayi yace "rabu da ita, in tana jin yunwa zata sauk'o ta samarwa kanta abinci", kai ta shiga girgiza mishi zatayi magana ya sa hannu kan lips d'insa yace "shhhh, eat and get some rest, bakya jin dad'i you shouldn't bother, she will b okay", wani irin murmushi tayi murna fal ranta kamar tayi yaya, bata damu da ko yanaci ba, haka ta dinga tunkud'a abincinta, tunanin abinda ya faru tsakanin shi da Batuul kawai yakeyi yana kallonta don tun da yake kissing dinta bae taba samun natsuwa irin wanda ya samu gun Batuul yanxu ba, it was just amazing, lumshe ido yayi ya kwanta kan gadon Ajiddeh, gaba d'aya komai dawo mishi ya shiga yi a hankali, hotunan Ajiddeh dake kan wayar da ta goge ya tuna, baisan lokacin da wani slight murmushi yayi escaping lips d'inshi ba, then why did she delete the pictures ita da ba ma son shi take ba what made her jealous, wayanshi dake gefen Ajiddeh ne ya shiga ringing, zuciyanta ya bada sautin dam, ganin mey k'iran, jiki a sanyaye ta d'au wayan, wani zuciyan ke ce mata ta katse wayar dan ita tsoro takeji, kamin tayi abinda zuciyarta ke kissa mata ya bud'e lumsassun idonunshi, a tsorace ta mik'o mishi wayan ganin ya bud'e ido, tashi yayi daga kwance ya risina ganin mai k'iran ya karba wayar, a kunnenshi ya kara a nutse ya amsa da sallama yace "salamu alaikum, nda dubdo Ammah", amsa mishi sallamar tayi tace "Ya kuke Abu, yasu Hauwa'u", kallon Ajiddeh yayi sannan yace "suna lafiya Ammah, ya gida ya k'arfin jiki?", tace "Alhamdulillah, kana jina, kayan Batuul da aka turo yau zasu iso, dan haka in suka iso kaje ka karb'o su sannan sai inyi magana da ita, inaso in mata explaining abubuwan dake ciki da yadda amfaninsu yake, mik'amin Hauwa'u inyi magana da ita in tana kusa", Ajiddeh ya mik'awa wayan sai muzurai takeyi da ido don gaba daya hankalinsa ya tashi don bae san me Ammah xata ce mata ba, jiki a sanyaye ta karb'i wayan tasa a kunne, xuciyanta sai double flip yakeyi, sai da Ammah ta k'ira sunanta sannan ta amsa, a daburce kamar mara gaskiya tace "Na'am Ammah ina wuni", sau d'aya Ammah taji muryarta tun bayan aurensu da Abu, ba yabo babu fallasa Ammah ta amsa mata da "kuna lafiya Hauwa, ya y'ar uwarki", har cikin ranta take jin yadda Ammah ta k'ira Batuul y'ar uwarta, kamar munafika tace "muna lafiya", Ammah tace "yayi kyau, ki kula da ita kamar yadda zaki kula da taki k'anwar kin ji, nasan Batuul batada Matsala, nasan abin yazo miki bazata, ki d'auka kaddara ce, tun can da rubutacce ne, ki barwa Allah komai sai kiga yazo miki da sauk'i, Allah yayi muku albarka, ya kad'e duk wata fitina cikin zamanku, kuyi zaman lafiya keda Y'ar uwarki, Allah ya baku zuri'a d'ayyiba ya baku zaman lafiya, Allah yayi muku albarka", har Ammah ta gama maganan da zatayi k'wak'walwarta ta kasa processing maganganun da takeji, gaba d'aya kanta ya gama d'aurewa, suyi zaman lafiya ita da y'ar uwarta, wannan magana ai kishiyoyi ake fad'awa, maza tayi ta cire tunanin daga ranta tace "Toh Ammah mungode", daga haka ta mik'awa Abu wayan tana kallonsa, bayan sun gama maganan da zasuyi da Ammah sukayi sallama, kallon Ajiddeh yayi, she wasn't looking herself anymore dan abincin ma ta denaci, yana bud'e baki zaiyi mata magana wayarshi ta sake ringing, bai d'auka ba har ya katse dan lamba ce bak'uwa, sai da aka sake k'ira a karo na biyu ya dauka, muryan namiji yaji yace "This is Daniel speaking from Birmingham port authority, we call to notify you d arrival of your cointainer, we would like you to come and claim your property", ajiyar zuciya yayi, kayan da Ammah ta fad'i kenan, cewa yayi "Aiit, I will be there surely soon", "Thank you", mutumin yace mishi sannan suka katse wayan, Ajiddeh dae ta kafa mishi k'ananan idanuwanta ko kifta wa bata yi, iska ya hura mata yace "what are you thinking about wife, obviously me", a hankali ta kalleshi har lokacin hankalinta tashe tayi murmushi tace "Ba komai", ta juya taci gaba da cin pizza ta, ba wai dan ya yadda ba ya k'yaleta, mik'ewa yayi yana kallonta yace "I will b back soon, take care", da haka ya fita daga d'akin da ido kawai ta bishi dan ba daidai take jinta ba, sai da ya kalli kofar d'akin Batuul kamin ya sauk'a k'asa, d'akinshi yaje ya d'auko key ya fita, tafiyar minti 25 ya isa gun port authority, container number ya fad'a musu bayan ya k'ira Ammah ta sanar dashi number, da mamaki yake kallon kayan, bai tab'a tunanin haka kayan keda yawa ba, ta ina ma zai kai kayan nan gidanshi, kana gani kasan lefe ne na aure, idea ne ya fad'o mishi kawai yasa akayi loading kayan a babban mota, yana gaba babban mota na biye a baya, gaban wani gida da rabinshi duk glass ne suka tsaya, nan aka sauk'e kayayyakin, mutanen ne suka shigar da komai ciki, sai da suka gama ya sallamesu suka tafi, shiga yayi ciki ya kwanta kan sofar parlour, wayanshi ne ya shiga ringing, Ammah ce take k'ira , yana recieving tace "Ka amso kayan?", hannu yasa cikin gashin shi a hankali yace "Ehhh Ammah, but ban k'arasa gida ba", yasan tunda Ammah tace zatayiwa Batuul magana yau d'innan sai tayi, ya lumshe ido yace "In sha Allah Ammah, ina komawa zan bata wayan ", bata tsaya jin komai ba ta katse wayan, bai bar gidan ba sai bayan 30mins, Kai tsaye d'akin Batuul yaje da ya koma gida, kwance ya tadda ta tana bacci abinta hankali kwance, daga ita sai d'an bum short da crop top ta takure waje daya ga xanin ta a gefenta, yafi minti biyu tsaye yana kallonta daga baya ya janye idonshi ya bud'e closet d'inta ya Ciro mata dogon hijab, hannu yasa cak ya d'auketa, baki ta bud'e zata sa ihu ya matseta jikinshi, ajiyar zuciya ta sauk'e jin k'anshin turarenshi tayi lamo jikinshi sae dae gabanta faduwa yake, har sai da ya kaita mota sannan ya bud'e ya direta ya jefa mata hijab d'in da ya d'auko mata shima ya zaga ya shiga daga gefen driver ya tada ya bar compound d'in, kallonsa take a tsorace sae dae ta kasa cewa komae, a hankali ta saka Hijab dinta da ya jefa mata. [8/22, 14:49] Umar Dalha: 💖💝BATUUL💖💝 57 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Driving yake ba tare da yace mata komai ba, duk ta takure cikin motar a tsorace, ga sanyi da takeji dan gaba d'aya wajen sai traces d'in snow ake, a hankali ta juyo kanta daga kallon waje ta kalleshi, wani irin kallo da ya sakar mata yasa tayi saurin d'auke kanta, idonta har ya cicciko, kanta ta kifa kan k'afarta ta sake k'ank'ame jikinta sabida sanyi, bata d'ago ba har sai da taji yayi parking tukunna ta d'ago kanta a hankali, inda ya kawo su tabi da ido tana kallo, xaro ido tayi ganin irin gidan dake gabansu, bud'e k'ofar motan yayi ya fita ya fara tafiya, bata yi yunk'urin fita daga motan ba har saida ya juyo yaganta zaune har lkcn, wani irin kallo ya watsa mata, sannan ya dawo ya bud'e motan, bata jira yace komae ba ta fito, ya kama hannunta, yana tafe tana binshi a baya, kalle kalle Batuul ta shiga yi ganin irin gidan da ya kawo su, don rabin gidan duk glass ne, sosai gidan ya mata kyau, duk wanda yayi designing gidan yayi k'ok'ari, baki ta tab'e da ta tuna shima d'in architect ne fa, amma gaba d'ayanta a tsorace take, stairs yabi da ita ya nufi d'akin da aka zuba kayanta, da mamaki tabi kayan da ido, ta d'ago kai tana kallonsa, kallonta yayi shima snn ya d'auke ido ya xauna ya fixgota ita ma ta xauna daga gefensa, wayarsa dake hannunsa ya kunna yayi danne danne snn ya mika mata, sai da ta kalli fuskanshi taga shima ita yake kallo sannan ta karb'i wayan a sanyaye ta kara a kunnenta, muryan Ammah taji tana cewa "Bitti ya gida?", a kunyace tace "Alhamdulillah Ammah, ina yini?", Ammah tace "Alhamdulillah Bitti, kinga kayanki sun iso ko?", sai da ta kalli Abu, taga kallonta yake sannan ta gyad'a kai kamar Ammah na gabanta tace "Ehhh Ammah, gasu nan na gani", Ammah tace "Yawwa akwai wani kwali a ciki anyi packaging, ki bud'e yanzu in miki bayanin abubuwan ciki da yadda zakiyi amfani dasu", "toh tace" sannan ta mik"e ta isa wajen da kayan ke ajiye, a hankali tace "Ammah kwalin ba d'aya bane, suna da yawa", Ammah tace "Ehhh k'aramin ciki zaki bud'e, manyan duk turarrarukanki ne ciki", tace "toh Ammah", karasawa tayi inda k'aramin kwalin yake ta shiga k'ok'arin bud'e kwalin, kasa bud'ewa tayi harda sauk'e numfashi, a hankali ta juyo ta dubi Abu dake zaune, kallonta shima yayi yaga tayi rau rau da ido, ganin yaqi cewa komai ta juya taci gaba da kiciniyar bud'e kwalin, d'an murmushi yayi ya mik'e ya isa inda take, k'anshin turarenshi da taji yasa tayi Saurin juyowa, kamin ta tashi yazo ta bayanta ya mik'o hannayenshi daga gaba kan kwalin, sama sama ta rik'a jin numfashinta jin sauk'ar numfashinshi kan wuyanta, still tayi har ya gama bud'e kwalin, bai bar bayan nata ba sai ma sake kwantowa da yayi, jiki a sanyaye ta d'auki wayan ta maida wayan kunnenta, sai da Ammah ta gama mata bayanin komai sannan sukayi sallama, wasu ma duk ba fahimta tayi ba jin numfashinshi na sauk'a jikinta yana sending shivers to her spine, a hankali ta shiga k'ok'arin tashi daga wajen, hannayenshi yasa ya zagaye waist d'inta ya sake matseta jikinshi, babu abinda zuciyanta keyi sae double flips lkci daya jikinta ya dau rawa, bakinshi ya kawo daidai kunnenta, a hankali kamar me rad'a yace "nan zaki bar kayan naki har sai ranan da matata ta yadda ki zama co_wife d'inta, batace mishi komai ba sai ma hawayen dake dad'a taruwa idonta, jin tayi shiru yasa ya juyo da ita, hawayen da ya gani idonta yasashi yin murmushi yace "kukan meye zakiyi kuma?", lumshe idonta tayi hawayen dake tare ciki ya shiga gangarowa, murmushi yayi yasa hannu yana goge mata hawayen da ya zubo mata, hannunshi ne ya kai kan lips d'inta masu d'umi, wani irin shock taji yabi spine d'inta kuma har lokacin bata bud'e ido ba, a hankali ya shiga zagaye lips d'in nata da hannunshi, har ya sunkuyo ya kaj bakinshi dai dai nata har tana iya jiyo sauk'ar numfashinshi kan fuskanta, kirjinta sai heaving yake, ta kuma ki bude ido, ko me ya tuna sai kuma ya mike ya kamo hannunta, sai a lokacin ta iya bud'e idanuwanta ta ganshi tsaye, mik'ar da ita yayi, ba musu tabi bayanshi har sai da suka sauk'o k'asa, sai da suka s [8/22, 14:49] Umar Dalha: 💖💝BATUUL💖💝 58 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Murmushi yayi ya d'auke idonshi daga kanta, abincin dake gabanshi yaci gaba da ci, sae kuma ya ajiye fork d'in hannunshi ya juyo da wani irin smirk a fuskanshi ya sake matso da ita jikinshi yace "you didn't tell me, are you still on your period", tsoron tambayar ne ya kamata amma ta dake ta tsuke d'an k'aramin bakinta tace "nima ban sani ba", yanda tayi maganan ne ya bashi dariya, hannunshi ya d'aura kan mararta yace "Lemme check to see if you are still on it tunda kince keh baki sani ba", a razane ta yar da fork d'in dake hannunta ta zaro ido ta d'aura k'aramin hannunta kan nashi ta rik'e tace "Yaa Abu am still on it, kayi hak'uri, bai bi takanta ba yaci gaba da abinda yakeyi, kallon kyakyawan fuskanta da ya jik'e da hawaye yayi, yayi murmushi yace "Toh ai kema ba sani kikayi ba, kinga I should check for us both", babu abinda jikinta keyi in ba rawa ba, rintse ido tayi tana hawaye jikinta ya dau rawa jin yadda hannunshi ke yawo kan mararta, gaba d'aya jikinta ya saki, a hankali ya shiga daddana mata mara, hannu tasa ta sake rik'e mishi hannu, ido a rintse tace "Yaa Abu dan girman Allah ka bari, nace maka am still on it, yana min ciwo", murmushi yayi yace "dama doctor yace ayi massaging lower abdomen if it hurts, shi nake miki to reduce d pain", a hankali hawayen suka ci gaba da kwararowa, ji tayi kawai ya d'auketa cak, wara ido tayi ta shiga wutsil wutsil, wani irin kallo ya sakar mata yace "I will slap yhu in baki tsaya ba, da kinsan you are on it kika ce min baki sani ba, yanzun nan zan sake ki ki fad'i k'asa", shiru tayi jin yace zai saketa, bata bud'e ido ba saida taji ya direta kan lallausan gado, a hankali ta bude idonta tana kallon fuskanshi, tashi tayi da sauri ta zauna tana goge hawayen dake fuskanta da bayan hannu, muryarta na rawa tace "Yaa Abu nace kayi hak'uri fa, ", ta fad'a tana marairaice fuska, dariya ta bashi yanda tayi maganan ya zauna daga gefenta ya hade rai yana kallon fuskanta yace "kukan meye kike min", kin cewa komae tayi ya fixgota ta fad'a jikinshi, wani sabon kukan ta fashe da tace "ni wllh zan fad'awa Ammah", dariya sosai yayi yace "da kika nace aka aura min keh, sai kicewa Ammah meye"?, sadda kanta tayi k'asa ta mayar kan cinyarta, dabara ne ya fad'o mata ta d'ago kai ta kalleshi, suna had'a ido ta d'auke nata tareda juya kanta ta hade rai tace "toh zan fad'awa Ajiddeh ni dae", baisan lokacin da ya tuntsire da dariya ba ya juyo da kanta tana kallonshi, yana rik'e da hab'arta da ta kasa yadda su had'a ido, har lokacin murmushin nan na fuskanshi yace "da kinbar gidanta a yau ba sae gobe ba kuwa", bata kulashi ba yace "ko don kinga har ta fara kulaki", jin yayi shiru ta d'ago ta kalleshi taga ita yake kallo, ya daga kafada yaci gaba "in kin shirya barin gidanta sai ki fad'a mata in kin k'oma" mik'ewa yayi ya isa wani k'ofa, a jikin bangon ya danna abu k'ofan ya bud'e, shigewa yayi ciki, sai lokacin Batuul ta d'ago rinannun idanuwanta, d'akin ta shiga k'arewa kallo, Babba ne sosai da makeken walk-in closet d'in distressed raw wood da ya cinye side d'aya, daga gefe shelf d'in takaddu ne, sae wani sculptural rope lamp da ya sauk'o daga gefen shelf d'in, sai lokacin ta juya ta kalli gadon da take, traditional bed ne, makekene sosai da wasu brass lamps da suka bada wani irin unified look, da extra reading light, sai wasu faux leather headboard kujeru biyu daga gefe suna facing juna, hankali idonta ya fad'a kan crispy curtains, da glass d'in dake bayan curtains d'in, tab'e baki tayi snn a hankali ta mik'e ta isa wajen tare da yaye curtains d'in, numfashinta ne ya kusa d'auke ganin yadda wajen yake, sai a lokacin tasan sama ya hawo da ita, gaba d'aya filin grass ne shimfid'e da ya sha gyara, sai pond d'an madaidaici da swan farare a ciki suna ta shawagi, sai k'ananun kifi duk cikin pond d'in, daga can d'aya side d'in Lazy S-shaped pool ne, da toskana brown lounge kujeru biyu daga gefensu, bataji fitowanshi ba sai jin k'anshin shower gels da sabulun da yayi amfani dasu taji, juyowa tayi suka hada ido, da sauri ta d'auke kanta ganinshi daga shi sai d'an towel, kamin ta matsa daga wajen ya k'araso yasa hannayenshi ya zagayo waist d'inta, a hankali ya sauk'e fuskanshi kan wuyanta, sanyin ruwan dake jikinshi da sauk'ar numfashin shi wuyanta yasata shivering, a hankali yace mata "kina son gidan?" da k'yar ta iya gyad'a mishi jikinta na rawa, kafad'unta ya kama ya juyo da ita tana fuskantarshi, kasa d'ago ido tayi ta kalleshi, hannu yasa ya d'ago hab'arta yace "hmmmm well I built it for my love, my wife, kin santa?" ya tambayeta yana kallon cute face d'inta, batasan lokacin da ta murgud'a d'an k'aramin bakinta ba ta tsuke fuska ta dauke kai, murmushi yayi ya kuma juyo da fuskarta, d'aura d'an yatsanshi kan lips d'inta yayi yace "I like it when you twist your lips", a hankali ya sunkuyo ya lumshe ido yayi wa lips d'inta light kiss, lumshe ido tayi ita ma jin lips d'inshi kan nata, sai da ya d'ago yana kallonta yace "zaki sani sabon wanka ko", a hankali ta d'ago idanuwanta jin abinda yace eyes d'insu yayi locking, da sauri tayi k'asa da Kai, saketa yayi ya juya ya isa inda closet d'in yake, bayanshi tabi da kallo a xuciyarta tace is this the Abuturrab she knw, lallai namiji bashi da kunya, tab'e baki tayi tana kallon broad figure d'inshi, jiki a sanyaye ta sake curtains d'in ta dawo kan gadon ta zauna, kanta a k'asa har ya gama sa kayanshi ya tada sallah, tana nan zaune har ya idar, sai da ya mik'e daga kan abin sallah yace mata "Let's get going, nasan matata na nan tana jirana", tsuke fuska tayi ta mike ta nufi kofa, bin bayanta yayi yana murmushi, da mamaki ta dubeshi ganin kwanukan da suka bari gun basa nan, tab'e baki tayi taci gaba da tafiya abunta jin baice mata komai ba, Hijab d'inta dake kan sofa ta d'auka ta zira tabi bayanshi har suka fito inda yayi parking, da kanta ta bud'e gidan gaba ta shiga, takurewa tayi jin sanyin ACn dake kunne, observing d'inta da yayi yasa shi controlling temperature, hannunta na hagu ya kamo a hankali ya shiga murzawa, ta fixge hannunta don ta gama gano sa yanxu, jikinta kawae yake so kuma baxata bashi ba. Sai da suka shigo gida hankalinta ya fara tashi, Abu kam ko a jikinshi kai tsaye ya shiga cikin gidan ta bi bayansa kamar munafuka, Ajiyar zuciya ta sauk'e ganin Ajiddeh bata palon ta nufi sama da gudu, murmushi yayi dan yasan gudun mey takeyi shima ya haura sama, dakinsa ya shiga ya fada kan gado ya lumshe ido, murmushi kawae yake ba tare da yasan dalili ba. (Sorry 🙇 for d short chappy sisters, I got test to write tomorrow, wish me luck 🍀, I promise to update you guys tomorrow In sha Allah) [8/22, 14:50] Umar Dalha: 💖💝BATUUL💖💝 59 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Da mamaki Ajiddeh ke dubanshi daga bakin k'ofa ganin ya dawo da wani kayan ba da wanda ya fita ba, kuma tun biyar ya fita yace mata yanzun nan zaije ya dawo amma sai Yanzu yake shigowa, ga shegiyar nan ma tun d'azu take mata knocking taqi bud'e mata k'ofa, tsaki tayi ta k'arasa shigowa d'akin, kai tsaye gadon da yake kai ta nufa ta zauna daidai kanshi ta shiga tashin shi, a hankali ya bud'e lumsassun idanuwanshi ya d'aura kanta, had'e rai tayi a dole ya b'ata mata rai tace "Aliyu tun yaushe ka fita ka barni gidan nan, daga cewa yanzu zakaje ka dawo shine ka shanya ni nan", murmushin shi mai narkar mata da zuciya yayi ya riqo hannunta ya janyota jikinshi, a hankali ya d'aura bakinshi daidai kunnenta cikin rad'a yace mata "keh wai baki iya kula da miji ba?, ba girki, ba gyaran gida, babu tsaftace ko ina sai kanki kawae, amma kinfi kowa iya mita, a haka ake nuna son?", jikin tane yayi sanyi jin abinda ya fad'a mata, toh me kuma ya kawo wannan maganan, d'ago kanta tayi ta kalli fuskanshi taga idonshi na lumshe ne har lkcn, rolling idanunta tayi a ranta tace kai ka sani, har lokacin idonshi lumshe ya sake jawota ta fad'o jikinshi yaci gaba da cewa "ko kinaso in samo wacce zata na yi min dukka wannan abun kinga kema sai ki koya gunta?", a firgice ta d'ago tana kallonshi tace "mey kake nufi Aliyu", sai a lokacin ya bud'e lumsassun idanunshi ya zuba mata su, murmushi yayi ganin expression d'in dake fuskanta ba tare da ya damu ba yace "sai in qara aure mana, kinga kin samu mai koya miki nima na samu mai bani abinci ba sai ina zuwa restaurants ba", gaba d'aya ji tayi iskan d'akin yayi mata kad'an, hannu tasa ta warware dogon gashinta mai tsayi da laushi tana mishi wani matsiyacin kallo cike da masifa tace "A ina d'in wai zakayi aure, ba dai ina gidan nan ba, wlhy Allah indai da raina baka k'ara aure, sai ina maka girki sannan zaka san ina sonka?, tun farko daga gidanmu ni ban saba da wahala ba shiyasa aka nema min masu aiki kace baka sonsu ka koresu to ya kake son inyi da kai? sai yanxu kuma kace min wani ban Iya komai ba, dama can meye auren, abun da yake ciki ai ina yi maka, shine yanzu zaka tsiro da zancen aure, duk shegiyar ma da tayi gigin aurenka sai na lahanta ta ta rasa mai aurenta wllh", tana huci ta kare maganar, da mamaki yake kallonta, dariya maganarta ya bashi sosae, wai in tans raye bai k'ara aure", kanshi ya kad'a yace "calm down, wannan hargowa tun banyi auren ba, ki bari in nayi sai kiyi using energy d'inki sai kiyi fad'an dagaske", idonta ne ya cicciko da hawaye jin abinda Aliyu ke fad'a mata, a fusace ta mik'e zata bar d'akin yasa hannu ya fizgota ta fad'o kanshi, kokawa ta shigayi dashi a kan ya k'yaleta amma yaqi, ta fashe da wani matsanancin kuka, a hankali ya d'aura bakinshi kan wuyanta ya fara kissing har ya gangaro kan lips d'inta, kasa resisting d'inshi tayi da kokawar da takeyi dashi, lkci daya ta hadiye kukan ta bada Kai. Batuul na shiga d'aki ta fad'a gado, lumshe ido tayi tana tunanin abinda ya faru yau gaba d'aya, tunda ya sauk'e ta makaranta ya bata kud'i, bud'e mata k'ofa da kuma tafiyansu gidanshi mai kyau da abunda ya dinga yi mata yau, lumshe ido tayi tana tariyo duk event d'in da ya faru yau, wani iri ta dinga jin kanta, gaba daya ta k'asa daina tunawa, jiki a sanyaye ta mik'e ta cire Hijabin jikinta da kayan dake jikinta, jin k'anshin turarenshi jikin kayan yasa ta d'aura rigan kan fuskanta, wani irin weakness taji k'afanta ya fara, a hankali ta koma kan gadon ta zauna har lokacin rigan na fuskanta, a hankali ta cire ta ajiyeshi gefe, da kyar ta mik'e ta janyo towel ta d'aura ta fad'a toilet, nanma tafi 15mins cikin bathtub d'in da ta cika da ruwan zafi, sai da ta gaji da zama dan kanta ta mik'e ta fito daga ciki, alwala tayi ta canja pad d'inta sannan ta fito, gaban vanity table d'inta ta zauna ta shafa mai ta fesa turarukanta masu sanyin kanshi sannan taje closet d'inta ta ciro kayan bacci, short sleeping gown fari da fuskan Panda daga gabanshi ta saka, sai da ta karanta Qur'an a wayarta sannan ta kwanta bacci, ta dde kwance sae juye juye ta ke, da ta bude ido Abuturrab take tunawa, ta rasa dalili, sae kusan midnyt bacci ya d'auketa, washegari kamar yadda ta tashi jiya haka yau ma tayi, da kayan baccin nata ta sauk'o kitchen ta shiga had'a musu breakfast dan 8 take da lecture, pancake paste ta kwab'a sannan tayi strawberry syrup ta tafasa musu fresh milk ta juye a flask, a jikinta taji kamar ana kallonta daga bakin k'ofa, a d'arare ta juyo ta kalli k'ofan, wani irin k'ara ta saki zata bi k'ofan baya ta fita ganinshi tsaye bakin kofar yayi folding arms d'inshi yana kallonta, cikin hanzari ya k'araso cikin kitchen d'in yayi maza ya kamota, babu abinda jikinta yakeyi sai rawa gashi ta kasa barin su hada ido, a hankali ya jawota jikinshi ya rungumeta tsam ganin ta tsorata, patting bayanta ya shiga yi yana rad'a mata subhanallah kunnenta, har sai da yaga b'arin da jikinta keyi ya ragu sannan ya sassauta rik'on da yayi mata yana kallon kyakkyawan fuskarta da hawaye ya ziraro yace "sarkin tsoro, ni d'in kike tsoro, ina zakije da kika sa gudu, ko kamanni na ne ya canja maki?", ya sa yatsanshi yana share mata hawayen, d'an k'aramin bakinta ta turo snn ta d'ago kanta ta kalleshi tace "ni ba tsoro ka bani ba, meye xa ka tsaya a bakin k'ofa kana kallona", dariya maganarta ta bashi amma ya dake ya d'ago fuskarta da ta sauk'ar yace "jiya ma by this time kika tashi?", kanta kawai ta gyad'a mishi, saketa yayi ya koma inda burners d'in suke, pancakes d'in da ta fara soyawa ya tsaya yana kallo, "did you make all this?", ya fad'a tareda juyowa yana kallon fuskanta, a hankali ta gyad'a mishi Kai, d'ayan tukunyar dake kan wutan ya bud'e, aroma d'in ne ya sashi yaja d'an baya yana kallonta yace "wannan ya sunanshi?", wara ido tayi a hankali tace "cream in chicken soup", kai ya gyad'a yana murmushi don ji yayi ta burgesa ba kadan ba, dawowa yayi gabanta yana kallon fuskanta yace "who taught you all this", a tak'aice tace "Aunty", ya daga kafada don yasan amsan kenan, "What time do you have lecture today?", ya tambayeta yana kallonta, tace "8:00", waje ya samu ya zauna kan kujeran island din yana duba kitchen timer yace "and its 6:30 now" "kin iya kunu", mamaki tambayan ya bata a hankali tace mishi " Yeah na iya,wane iri?", murmushi yayi yace "any type", kai ta gyad'a mishi tace "Na iya kunun gyad'a, Mard'om, tsamiya, kanwa, alkama sai Kunun Accha", kai ya gyada alamun he is impressed yace mata "Na gyad'a nake son sha yanxu, zaki iya yi", d'an karyar da kai tayi tace "toh ai babu gyad'an yin kunun", bai ce mata komai ba ya tashi ya isa cabinet d'in ya bud'eshi sannan ya Ciro bucket d'in nik'akk'en gyad'a, da mamaki ta tsaya kallonshi, smiling yayi ganin irin kallon da take mishi yace "Ammah packed everything for me, I love traditional food yhu knw", tab'e baki tayi ta isa Inda bucket d'in yake ta bud'e tare da d'an duk'awa tana duba gyad'an, a hankali bayan ta d'ago ba tare da ta bari sun had'a ido ba tace mishi "zanyi", yana zaune yana kallonta cikin 25mins ta had'a kunun gyad'a mai scrippers, sai da yaga ta gama ta fara kaiwa dinning shima ya fito daga kitchen d'in ya koma Palo, shi yace basai ta share gidan ba yau tunda time ya k'ure, bata ce komae ba ta koma kitchen din don tsaftace ko ina. Ajiddeh kam K'aran wayanta ne ya tasheta daga bacci, tsaki tayi ta jawo wayar, time ta fara gani taga k'arfe shida da rabi na safe, juyawa tayi taga Abutturab baya d'akin sannan ta d'aga wayan a tsorace ganin mai k'iranta at wannan lokacin, a d'arare tace "Hello Mummy" tana jin tsoron kar ace wani abun ne ya faru a gida, daga d'aya b'angaren Mum tace "kina jina, Malamin nan yace aiki fa bazai yiwu ba sai kina nan kuma yace Cikin kwanaki uku in baki zo ba komai zai iya faruwa da shi kansa bae gano ba, dan haka duk yadda za ayi kisan yadda zaki yi ki iso yau d'innan ba sai gobe ba", a tsorace da jin abinda Mum ta fad'a mata tace "Mum ban san ko zai bari inzo ba", inji Ajiddeh, "kina ma da hankali kuwa, nace miki komai zai Iya faruwa shine kike cemin bazai barki ba, toh koh bai bari ba bazaki taho ba inyaso a San abin yi daga baya", maganganun Abuturrab na jiya ta tuna, hankalinta a tashe tace "toh toh naji Mummy, yanzu zanje in sameshi ince mishi an min waya ance bakida lafiya kuma kinason ganina, nasan in yaji haka zai bari, sai kiyi all things possible yadda bazai gane ba", da haka sukayi sallama akan zata k'irata duk yadda akayi, tashi tayi tana matsar k'walla yadda zatayi pretending wa Abu. Batuul ta d'auko flask d'in fresh milk d'in kenan zata fito daga kitchen taga Ajiddeh na sauk'owa hankali tashe, duk gashin nan an baje shi, ae fa nan gabanta ya shiga faduwa ta k'asa karasawa dinning, a tsorace take kallonta ganin yanayin da take, wani irin mugun kallo tabi Batuul dashi ganin irin kayan dake jikinta, har sai da tazo zata wuce ta dinning d'in a hankali Batuul tace "INA kwana", wani kallo ta watso mata tareda hararanta, tab'e baki Batuul tayi ta d'auke kanta, dama ita kirkin da Ajiddeh ke mata ba yadda tayi dashi ba, gara tana masifan da ta Saba kawae, tana dire flask d'in hannunta ta haura sama abinta da sauri. Da wani irin kuka ta fad'a jikin Abutturab dake kwance kan sofa da remote hannunshi yana kallon TV, don yi yayi kamar bae san ta sakko falon ba da farko, a rikice ya d'agota ya shiga tambayanta lafiya, tana kuka kamar zata had'iyi rai tace "Mummy", tashi yayi yana kallonta yace "What happened to her", cikin sheshek'a kamar dagaske ta kasa ce mishi komai, a d'an tsawace ya d'ago fuskarta yace "talk to me Ajiddeh, what happened to Mum", a sanyaye tace mishi "Yanzu Yaa Zee ta k'irani, wai Mummy ba lafiya kuma tana son ganina", ajiyar zuciya ya sauk'e ya jawota jikinshi ya rungume yace "shhhhh, its okay , she will be alright, okay?, gobe zamuje gida", da hanzari ta d'ago tana kallonshi tace "baby bazan iya ba, inason inje inganta yau, bazan Iya ba", ta k'arashe maganar da kuka sosai, tashi yayi ya kamata suka haura sama, sai da ya shiga d'akin ya zaunar da ita kan gado yace mata tashi ki shirya kayan da zakiyi amfani dashi, yanzu zamuje muyi booking flight ko na evening ne sai mu bi", rinannun idanuwanta ta d'ago tana tana kallonshi tace "Baby ai kana da aiki, ba komai ba sai kaje ba, you should stay back ka kula da abubuwan da kakeyi, In sha Allah she will b fine", haka tayi ta insisting har sai da ta samu tayi convincing d'inshi ya fasa bin ta, bakwai da arba'in da biyar daidai suka sauk'o shida Ajiddeh tana riqe da trolley d'inta a hannu, Batuul na palo suka sauk'o tare, mik'ewa tayi tsaye har suka k'araso inda take, Ajiddeh sai hararta takeyi ta gefen ido, sai lokacin ma ya tuna da ita, kud'i ya ciro daga aljihunshi ya mik'a mata sannan yace "David ya kaiki school", da haka suka fita suka barta nan tsaye ko wayanma bai samu ya bata ba yau. Haka kawae taji ranta ya baci ta bi bayan Ajiddeh da harara, suna fita ta ja tsaki ta haura sama don xuwa dauko jakarta ta bar gidan ita ma. [8/22, 14:50] Umar Dalha: 💖💝BATUUL💖💝 60 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* A bakin mota ta tarar da David tsaye yana jiranta, hannu tasa ta bud'e motan ta fad'a sannan shima ya shiga, sau biyu David na maimaita gaisuwarshi, sai a na ukun ta amsa mishi, zuciyanta ne taji yana mata xafi ta rasa dalili, ta ja tsaki yafi sau biyar zamanta cikin motan, hawaye ne mai d'umi ya shiga sirarowa daga idonta, hannu tasa ta shafo hawayen ta tsaya tana kallo da mamaki, kifa kanta tayi tsakanin cinyoyinta ta fara kukan da batasan dalilinshi ba, daga sama taji David na fad'in "We ve arrived", a hankali ta d'ago kanta ta k'arewa wajen kallo, batace mishi komai ba ta d'auki jakanta ta fita daga motan, department d'insu ta nufa taga Su Samantha da Aisha da wasu students d'in na tsaye hall way d'in, agogonta ta duba taga saura 15mins su fara lecture, tana juyawa zata bar wajen suka had'a ido da Aisha, d'auke kai Batuul tayi kamar bata ganta ba, can bayan faculty d'insu ta nufa ta zauna taci gaba da kukanta, k'anshin turare mai dad'i ne ya bugi hancinta amma bata d'ago taga daga ina k'anshin yake ba, cikin wani irin masculine voice mai dad'i da nutsuwa taji ance "Here, take this", ta d'ago rinannun idanuwanta ta sauk'e kanshi, da sauri ta d'auke idonta ta juyar da kai gefe ta hade rae, har lokacin bai bar wajen da yake tsayen ba, juyowa ta kuma yi ta ga har lokacin hannunshi na mik'a mata farin handkerchief d'inshi, a sanyaye tasa hannu ta karb'a, wani k'anshi mai dad'i ne ya bugi hancinta da takai fuskanta, ido ta lumshe ta shiga goge hawayen dake fuskanta, daga d'an nesa da ita ya zauna, bai ce mata komai ba har sai da ta juyo ta dubeshi sannan yayi mata murmushin shi mai kyau, kau da kai tayi ta fara wasa da biron da ta ciro cikin Jakarta, a hankali ya fara magana "if you don't mind, may I know d reason behind those tears, I might help", sai lokacin ta sake tunowa da yadda taga Abu ya riqe Ajiddeh, wani siririn tsaki ne yayi escaping lips d'inta ta fara k'ok'arin maida hawayen dake shirin dawowa, jin tayi shiru batace komai ba yasa ya sake kallonta, suna had'a ido ya d'aga mata girarshi d'aya yana jiran jin mey zatace, agogon hannunta ta duba taga lokacin lecture yayi, da hanzari ta mik'e ba tareda ta bari sun had'a ido ba ta miqa mishi handki d'inshi, ganin bai amsa ba ta ajiye mishi tace "Thank you, I need to go right away", bata jira jin cewarshi ba ta tafi cikin sauri ta bar wajen", murmushi yayi yabi bayanta da kallo tare da lumshe ido, tana isa taga har an fara shiga class itama taje ta zauna, waje d'aya suka zauna itada Aisha, bayan sun zauna ne Aisha tace "Fatima wai meye problem d'inki, ko yau you look pale, in bakida lafiya dolene sai kinzo school", had'e rai Batuul tayi tace "wa yace miki banida lafiya", dan bata jin yin magana da kowa, murmushi Aisha tayi tace "ai ba sai an fad'i ba, you look sick, red eyes, plump lips, pale face, nasan inda zan tab'a temperature d'inki nasan yayi sama", yak'e Batuul tayi tace "Am totally fine, bacci ne kawai ban samu nayi ba jiya", ta d'auke kanta tana sauraron maganan da lecturer d'insu ya fara, baki Aisha ta tab'e bawai dan ta yadda da abinda Batuul ta fad'a mata ba itama tayi concentrating da jin lecturer d'insu, Batuul dai na zaune ajin ne amma gaba d'aya mind d'inta is off, batasan ma dalilin da yake sata damuwa ba, har suka gama lecture l batayi grabbing komai ba, jiki a sanyaye ta mik'e suka fito daga lecture hall d'in, Samantha ce tace "Let's go and get some food, am hungry just as the glutton I'm, then we go home after then, no any other class, done for d day",ta fad'a tareda d'an tsalle, dariya sauran suka sa amma Batuul was absent minded bata ma san mey suke cewa ba, sai da Samantha ta sa hannu fuskanta ta fara waving sannan tace "Hello, you there", sannan ta dawo daga tunanin da take tace musu, "You carry on, I will b there right away, I need to clear somethings over here", Aisha dai batace komai ba tayi gaba abinta haka ma Samantha tare suka tafi, suna tafiya itama ta juya ba tare da tasan inda zata ba, wani guri ta hango duk bishiyoyi ne, wajen very serene, ba tareda wani tunani ba taje ta zauna abinta ta fiddo littafi kamar me shirin karatu sae dae ita kanta tasan ba karatun xata yi ba. Abutturab da Ajiddeh kam tunda suka fita airport suke abu d'aya, da k'yar ta samu kujera shima d'in ba first class amma tace taji ta gani zatayi managing, ai Uwa tafi komi, haka dai tayi convincing d'in Abu, wayanshi da ya ciro cikin aljihu don duba karfe nawa ya tuno mishi da Batuul, ba b'ata lokaci ya shiga neman number David ganin zai kai yamma bai dawo ba kuma bai bata wayan ba, David na d'agawa Abutturab yace mishi "Where are you?", David yace Sir av dropped her at school, am at the construction site now to give out d documents", d'an iska ya furzar yace "Did she tell you when she will be done?, i mean for today?", "David yace "No Sir, she didn't", Abu ya gyad'a kai yace "okay, you should leave d site now and b there at her school, make sure you wait for her to finish and take her back home", David ya amsa da "okay Sir", daga nan ya kama hanya ya koma makarantar su Batuul, inda ya sauk'eta nan yaje ya kafa motarsa, tunda yaje yake zuba ido ko zai ganta amma shiru, tun 10:30 yake makarantar gashi har 1 tayi babu Batuul, har lecture halls d'insu sai da ya riqa bi yana yi musu describing d'inta bata nan kuma an tabbatar mishi da sun gama lecture d'insu na yau, ba tare da b'ata lokaci ya ba ya kira Abutturab yace yaje bai ganta ba, calmly yace mishi ya koma yaje ya sake dubota, sau biyu yana komawa amma bata nan har wajen 4, sai lokacin hankalin Abuturrab ya fara tashi, Ajiddeh na lura da shi sae dae bata ce komae ba, Sallama yayi mata daga karshe yace xae tafi sae sun yi waya, ta wani hade rae tace " Ban gane ba Aliyu, a kan wata can xaka tafi ka bar ni jirginmu bae tashi ba, ita din yarinya ce da baxa ta iya kula da kanta ba duk xa ka wani tada hankali haka" ya daga kafada don bai son su rabu da fada yace "Chill babe, wani takardu xae kai min office to suna gida kuma wae ta kulle gidan da makulli shi yasa kika ga na takurasa ya nemota" tsaki Ajiddeh tayi tace "Toh gidanta ne xata wani kulle da makulli kuma wa ma ya bata makullin" peck ya manna mata a lip yace "Yi hakuri mai gida" turo baki tayi, yayi dariya yace "Don't worry babe, i promise to be back soon" bin sa da kallo tayi har ya bace mata kafin ta lumshe ido ta sauke ajiyar xuciya, Allah kadae yasan irin son da take ma Aliyu, kuma In'sha Allah nata ne shi din ita kadae. Abuturrab kam direct makarantar ya wuce daga airport din, har ya gama zagaye makarantar babu Batuul, a gajiye ya dawo gida lokacin biyar da rabi, ido ya lumshe ganin abincin da ta jera tun safe kan dinning ba a tab'a ba,sai lokacin ya tuna da zancen abinci, yasan dae baxa ta bata ba amma haka kawae ya kasa samun natsuwa. Batuul kam Na zaune wannan gurin har 4:15, sosai wajen ya mata dad'i har yasa ta manta damuwar dake ranta, sai kallon tsuntsaye takeyi suna shawaginsu kan bishiyoyi da water fountain d'in dake tsakiyar wajen, agogon dake hannunta ta duba taga 4:15, a razane ta miqe ta tattare kayanta ta fito daga gun, tasan dan bata sallah ne shiyasa time ya qure har haka bata sani ba, rana har ya kusa fad'i lokacin, tafiya kawai ta shiga yi har ta iso dpt dinsu ta tsaya tana kalle kalle, bataga kowa da ta sani ba, haka kawae taji hawaye sun cicciko mata ta nufi hanyan gate a sanyaye zataje ta tari cab ya kaita gida, tafiya takeyi tana ta share hawaye, har wani blur take gani, dab bakin gate taji mota na mata horn, matsawa tayi ta bashi hanya ta koma gefe taci gaba da tafiya, ji tayi horn d'in na dad'a k'aruwa, "Fatima", a tsorace ta juyo tana kallon mai k'iranta, parking yayi ya fito yazo ya sameta inda take tsaye, fuskanta ya gama examining sannan yace mata "do you always cry?", d'ago idonta tayi ta kalle shi tace "Are you stalking me?", dariya tambayarshi ya bata yace , "Mey ya faru baki tafi gida ba tun d'azu and you finished your lecture for d day tun 10", shiru tayi bata ce mishi komai ba, tambayanta ya sakeyi jin tayi shiru yace "ina zaki yanzu?", a hankali tace mishi "gida" ido ya wara yace "by yourself, do you normally go by yourself, mey kika zauna yi a school d'in har kika kai this time?", kai kawae ta girgiza mishi, ya juya zai koma mota yace "let's go, I will drop", ba musu ta shiga gaba yana biye da ita a baya, shi da kanshi ya zaga ya bud'e mata k'ofa, wani kanshi ne mai dad'i yayi mata sallama, ido ta lumshe ta jinginar da kanta jikin kujera, Hamdala ta dinga yi a ranta dan dama tsoron shiga cab d'in takeyi, sai da ya fita gate d'in ya juyo ya dubeta yace "yace where are we heading to?", sai a lokacin ta bud'e idonta tace mishi ST.Georges No 15, daga nan bai sake cewa komai ba ya d'au hanya. Waya Abuturrab ya bugawa Mr Steven akan ayi enquiring abt Batuul dan har yanzu bata dawo gida ba kuma school d'inma bata can, daga nan ya shiga yayi wanka ya canja kayan dake jikinshi, ko mai bai shafa ba ya sake d'aukan key yayi waje, yana zuwa bakin k'ofa yaga wata bak'ar Rolls Royce ta shigo compound d'in, sai da motan yayi wajen two minutes da parkin tukunna maishi ya bud'e ya fito, ajiyar zuciya ya sauk'e ganin Batuul ta fito cikin motar yayi tucking hannuwanshi cikin aljihu yana kallonta, "Thank you" tace da Shaheed tana kallonsa, Sam bata lura da mutum na tsaye ba sai da ta juyo zata shiga gida, gabanta ne ya bada sautin dam ganin Abu tsaye bakin k'ofa ya zuba mata lumsassun idanunshi ko kifta wa bae yi gashi ya wani hade rai, dakewa tayi ita a dole tana fushi taci gaba da k'arasowa, Sai da tazo dab dashi ta kasa d'aga k'afa ganin yadda idonshi ya canja kala yana kallonta dasu, shi kam Shaheed tuni ya bar compound din ba tare da ya lura da Abuturrab ba ma, a hankali Batuul tace "Ina yini" bae amsa ta ba ya kama hannunta suka nufi cikin gida fuskarsa a daure, gabanta ya dinga faduwa har suka shiga Palo, kulle kofar yayi ya juya yana facing dinta yace "Daga ina kike?" Sunkuyar da kai tayi ganin he's serious, murya can kasa tace "School" wani tsawa ya daka mata yace "I will slap you idan kika ce min school, I repeat my self where are yhu coming from, kuma waye yayi dropping din ki yanxu" hawaye ne ya xubo idonta har lkcn bata d'ago kanta ba. 💖💝BATUUL💖💝 61 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Hade rai Abuturrab yayi yana mata wani mugun kallo yace "if I shud slap yhu! Na maki wani abun ne kike min kuka, waye ya sauke ki a mota nace" share fuskar ta tayi ba tare da ta d'ago ba tace "A frnd!" Yana mata wani irin kallo yace "A frnd? Male or female" a takaice tace "Male" wani xaro ido yayi cikin tsawa yace "What, Male? Da aure nawa kanki kika hau motar wani kato, are yhu insane?" Wani takaici ne ya rufe ta wasu hawayen suka dinga xubo mata, bata san lkcn da ta mayar masa da amsa ba tace "Ohh ashe kasan da auren ka kaina, toh ai ni ban san da haka ba, nayi xaton wanda ka raka airport kadae auren ka ke kanta" tana kai wa nan ta nufi stairs ta bar sa wajen tsaye, bin ta yayi da kallo baki bude, har ta haura sama, sae kuma ya shafa kai yana murmushi ya koma cikin Palo ya xauna, ba dai kishin sa Batuul take ba, No! Ya ma san it's impossible tunda ba son shi take ba. Batuul kam tana shiga daki ta jefar da jakar hannunta tayi xamanta gefen gado, sae dae banda tukuki babu abinda xuciyarta yake, ta fi minti goma xaune kafin ta mike ta rage kayan jikinta ta shiga toilet, warm shower ta sakar ma kanta, ta kusa minti sha biyar a bayin sannan ta fito daure da towel, gaban mirror ta nufa tayi shafe shafenta, xata dauki kaya a closet dinta ta ji wayarta na ring, juyawa tayi ta koma gaban mirrorn ta dauki wayar, ganin me kiran yasa tayi murmushi ta daga tare da sallama "Tace Ammah ina yini?" Maimakon ta ji muryar Ammah sae taji kmr muryar Anty Amnah, daga daya bangaren Anty Amnah tace "Kina ji na Batuul?" A d'an kunyace Batuul tace "Ina ji Anty ina yini" don kunyar matar ita dai take, Anty Amnah tace "Lfya lau Batuul, ya ku ke gaba daya" Batuul tace "Lfya muke Anty" Anty Amnah tace "Toh madalla, cikin kayan da aka kawo maki kinga wani parcel da aka yi wrap kuwa" Batuul ta d'an yi shiru tana tunani, Anty Amnah tace "shi kadae ne karami cikin kayan" Batuul tace "Eh na gan shi Anty" Anty Amnah tace "Yauwa! Kin bude kuwa" girgixa kai Batuul tayi kamar tana ganinta tace "A'a Anty, ina ce turare ne ae" Anty Amnah tace "A'a ba turare bane, maxa dauko yanxu ki bude in maki bayani" xaro ido Batuul tayi tunawa da tayi ae duk kayan na can gidan, tace "Toh Anty bari in dauko" ajiye wayar tayi ta fita da sauri ta sauka Palo, Abuturrab na xaune har lkcn ya jinginar da kai jikin kujera idonsa lumshe, ta wani hade rae ta tsaya gabansa tace "Ya Abu, Anty Amnah ta kira wae xata min bayanin wasu daga kayan da aka kawo kuma basa nan ai" a hankali ya bude ido yana kallonta, gyara xama yayi da sauri yana ci gaba da kallonta, jin yaki cewa komae tace "Kaji, she's still on the line fa, ni ban san me xan ce mata ba" ko kadan bae san ma abinda take cewa ba, ganin haka yasa tayi saurin kallon kanta ta ga me yake kallo, wani kara ta saki ganin ashe towel ne jikinta har lkcn, ta juya da sauri xata bar wajen yayi saurin fixgota ta fado kansa, tsorata tayi ta shiga turasa xata mike yaki sakinta, tace "plss ya Abu, she's still on the line...." Bata rufe baki ba taji bakinsa cikin nata, still tayi na wasu yan dakiku kafin ta fara kokuwa da shi, duk ta rude, shi kam bae ma san tana yi ba, kan kace me sae ga su a kasa, nan jikinta ya dau rawa tana hawaye, danna bell da aka yi yasa ya saketa da sauri, ita ma ta mike a gigice ta koma baya don Ajiddeh ce kawae ta fado mata, a tare suka mike ita ta nufi sama da sauri shi koma yayi gun kofa, murda kofar yayi ya ga drivernsa ne David, ya sauke ajiyar xuciya yace "It's ok david, she's back minutes ago" Batuul kam daki ta shige ta fashe da kukan da bata san dalilinsa ba, wayarta ta dauka ta ga Anty Amnah ta kira ya fi a kirga, wani kiran nata ne ya kuma shigowa ta dauka da sauri, ta fara kame kame "Anty kiyi hakuri, dama naje ina dubawa ne, ga gashi na gani" Anty Amnah tace "Yauwa toh kin bude" xaro ido tayi sae kuma tace "Eh na bude" da sauri ta juya jin an murda kofar dakin, Abuturrab ya shigo, sunkuyar da kai tayi ta ci gaba da sauraran Anty Amnah, ganin ya nufota ta bar wajen da sauri ta koma can karshen dakin, bin ta yayi, ta kuma barin wajen da sauri ta ga ya kuma biyo ta, kamar xata yi kuka take kallonsa gashi ko kadan bata ma gane bayanin Anty Amnah, shi kam murmushi kawae yake yana kallonta, ta haye kan gado shi ma ya bi ta, rudewa tayi jin Anty Amnah na cewa "Hello Batuul are yhu there" kai ta shiga gyadawa tana koma wa baya tace "Eh eh Anty!" fixgota yayi ta fado kansa, bata san lkcn da tace "Wayyo ya Abu kayi hakuri pls" Anty Amnah da ta saki baki tace "Meye haka?" Kamar xata yi kuka tace "Anty ya Abu ne ya ki ya bar ni in ji me kike cewa" Anty Amnah tace "Ji min fitsararre da'alla ka fita ka ba mu waje" Abuturrab ya danne dariyarsa don ya ji ta sarai ya rungumo Batuul jikinsa yace "Toh Anty sorry na tafi" lamo Batuul tayi gabanta na faduwa, Anty Amnah tace "Ya tafi?" A hankali ta dago kai tana kallonsa ya mayar da kanta kirjinsa, tace "Uhm Anty" kunnensa ya kai dai dai nata don jin me Anty Amnah ke ce mata, Anty Amnah tace "Yauwa, wannan garin da kika gani me yawa da milk xaki kada ki dinga sha, shi kuma dayan da honey, you make sure you do that frequently," Batuul tace "Anty na Meye?" Anty Amnah tayi dariya tace "It will make yhu fresh kiyi kyau abun ki, sannan akwae tiger nut da date da aka hado maki cikin kayan sae ki sa ya siyo maki coconut kin dae san yanda xa ki sarrafa ba sae na gaya maki ba ki maida shi drink din ki, sannan ki xama me yawaita shan kayan itatuwa kin ji" daga nan Batuul ta fara gane inda xancen Anty Amnah ya nufa ta ji wani mugun kunya ya rufe ta ga Abuturrab na sauraren Anty Amnah shi ma, a hankali ta dago kai tana kallonsa ta ga kallonta yake yana murmushi turasa tayi ta mayar da wayar daya kunnenta, ya kuma kankameta yana dariya ciki ciki ya kai kunnensa inda ta maida wayar, bbu yanda ta iya haka ta tsaya tana sauraren Anty Amnah, kunya duk ya isheta, ita kanta Anty Amnah tana yi ne tana jin nauyin wasu abubuwan, can dae tace "Bari dae xan maki text kin ji" da sauri Batuul tace "Toh!" Anty Amnah tace "bari in kai ma Ammah wayar ku gaisa koh" Batuul bata iya cewa komae ba har bayan wasu 'yan mintuna ta ji muryar Ammah, suka gaisa Ammah na tambayarta gida tace "Lfya Ammah ina farida" Ammah tace "Tana lfya bitti, ina yayar ta ki" Shiru Batuul tayi sae kuma tace "Ae ta taho Nigeria daxu" saketa Abuturrab yayi da sauri yana kallonta, irin kallon me yasa xata fadi din nan, Ammah tace "Haba lfya dae koh?" Batuul bata damu da kallon da Abuturrab ke mata ba tace "Wae mumynta bata da lfya" Ammah tace "Ayya, ae ko ba mu sani ba nan ma, gobe xan je idan Allah ya yarda in dubo ta, Allah ya sauwake" Batuul tace "Ameen" Ammah tace "Ina Abun fa?" Batuul ta dan kallesa sannan tace "Yana Palo" Ammah tace "Toh ki dae maida hankali a karatu kin ji Bitti, ki kula da tsaftar jikin ki da na dakin ki, Allah maku Albarka" Batuul tace "Ameen Ammah na gode" nan suka yi sallama Batuul ta ajiye wayar, yana mata wani irin kallo yace "na aike ki kiyi announcing matata ta taho Nigeria" kokarin sauka Batuul ta shiga yi daga kan gadon ya fixgota, ta fashe da kuka tace "Don Allah ya Abu ka bari in sa kaya plss" d'an murmushi yayi yana kallon cute lips dinta yace "Wae me Anty Amnah take maki bayani a kai?" Da sauri ta dauke kai ta fara kokarin kwace kanta tace "Oho!" Ya bude ido yace "Oho ma xaki ce? Meye amfanin fruits din da tigernut drink da ta ce ki dinga sha?" Kamar xata yi kuka tace "Wayyo ni ma ban sani ba fa" a hankali ya daura bakinsa kan wuyarta wanda hakan sae da yasa jikinta ya dau rawa, murya can kasa yace "Toh in fada maki na menene ni?" Rikicewa tayi tace "Noo" yace "Okk then, which means kin sani, oya fada min kar in nuna maki abinda take nufi" ta fashe da kuka tace "Allah ban sani ba ya Abu" 💖💝BATUUL💖💝 62 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Jawota yayi ya d'aura ta kan cinyarsa yasa hannayenshi cikin towel d'in dake jikinta, numfashinta ne taji yana neman d'aukewa jin hannayenshi a k'ugunta, kuka ta saka sosai tace "Yaaa Abuuu dagaske ban sani ba, kayi hak'uri ka barni", dariya ta bashi ya sake janyota jikinshi ya d'aura bakinshi kunnenta, cikin rad'a yace mata "then, shine zan nuna miki abinda take nufi", girgiza kai ta shiga yi tana hawaye, bata ankara ba sai ji tayi ya juyo da ita tana fuskantarsa, rintse ido tayi dan bata iya kallon idonshi, jikinta sae rawa yake, cikin wani irin murya da taji har cikin ranta yace "open your eyes", sake rintse su tayi kamar abinda yace tayi kenan, a hankali ya sunkuyo yayi kissing idon nata d'aya, wani irin shock taji yabi jikinta, sake rintsewa tayi hawayen na dad'a silalowa, d'agowa yayi yana kallon yadda jikinta ke shivering, kirjinta sai heaving yake, murmushi yayi ya sunkuya ya sake kissing d'ayan, nan ma shivering jikinta ya dinga yi, d'agowa yayi ya sake kallon k'aramin pink lips d'inta da hawaye ya jik'a, har lokacin hannunshi bai bar cikin towel dinta ba, sunkuyawa ya kuma yi yayi brushing lips d'inshi kan nata, a tsorace ta bud'e ido tayi 'yar kara dan ita yanzu Yaa Abu ya fara bata tsoro, murmushi yayi ganin ta bud'e ido don dama haka yake so, lips d'inshi ya maida kan nata ya shiga yi mata wani deep kiss, wani irin ajiyar zuciya ta sauk'e jin yadda yake kissing d'inta, a hankali ya kwantar da ita kan gadon har lkcn bakinsa na nata, ta rike towel dinta gam jin yana kkrin cire mata, kuka sosae take tana kokuwa da shi, da kyar ta kwace bakinta ta turasa da duk karfinta ta mike xaune tana kuka sosai ta shiga komawa baya tace "Am on my period ya Abuu" kallonta ya tsaya yi da idanuwansa da suka sauya kala ko kifta wa bae yi yana sauke numfashi a hankali, ta tsorata ba kadan ba, xata sauka daga gadon ya fixgota yana kallonta cikin husky voice dinsa yace "Na fiki sanin u are not clean, Laifi ne don nayi kiss din ki, ke baki ji dadi ba ma na hada baki na da naki?" Sunkuyar da kai tayi jikinta na rawa bata ce komae ba, murmushi yayi yana kallonta cikin sanyayyan muryarsa yace "xaki gaya min ma'anar tsoron nan nawa da kike, soon" mikewa yayi ya nufi kofa ya fice daga dakin, ta bisa da kallo xuciyarta na bugawa. Bayan Ammah ta gama waya dasu Batuul, Ammah ta juyo ta dube ta tace "Amnah ashe mahaifiyar Hauwa bataji dad'i ba wae", da mamaki Anty Amnah ta dubi Ammah tace "wacce Hauwa?", Ammah tace "Ajiddeh ko, matar Abu", baki Aunty Amna ta tab'e tace "Au! Allah ya bata lafiya", taci gaba da abinda takeyi, Ammah tace "kaji min yarinya, toh fa har Hauwan ta taho wae yau, kin ga kenan jikin yayi tsanani, ai baza a daka ta halinta ba, auren d'an uwanku ne kanta, dan shi zakuyi ba dan ita ko halinta ba", Aunty Amna tace "Ammah bance komai bafa, addu'a nayi mata", Ammah tace "kin dai ji, tun wuri ku gyara halin nan naku", da murmushi Aunty Amnah ta dubi Ammah tace "Allah ya k'ara nisan kwana Hajiya Ammah, yadda kikace haka za ayi", hararanta Ammah tayi tace "tashi ki koma gidanki, nasan su Nawal da Babansu na can suna jiranki", girgiza kai tayi tace "Ammah kullum sai kin korani in nazo gidan nan, can ma in Babansu na nan babu ruwansu dani shima haka, tare sukeyin komai nasu basa sani, in kuma a can ne baya nan har rasa yadda zanyi dasu nakeyi, shiyasa nake zuwa gidan nan, amma kullum sai an korani", Ammah tace "da bakya barinsu ai da zasu na sakoki a abubuwan nasu, ni yanxu tashi ki tafi, nima yanzu zan shirya a kaini gidansu Hauwan inji ya jikin mahaifiyar tata" mik'ewa Aunty Amna tayi tareda ziran gyalenta tace "Ammah kinga sai muje a tare mu dubata, ko na koma babu abinda zanyi musu in banda wahala da zasu taramin", Ammah tace "A ah ban yadda ba, kama hanya ki koma gidanki sun fi buk'atarki fiyeda zuwa gaisuwan da zakije yi, nima da driver zanje yanzu in dubota, daga baya sai mu koma da Abui", kamin Ammah ta gama magana Aunty Amnah ta shiga dialing number a wayarta, ana d'auka tace "Hello honey, zamuje mu duba Maman matar Abutturab tareda Ammah bataji dad'i ba wllj, you guys should not miss me nasan zakuyi, I will b back shortly", murmushi yayi yace "as though bamu saba ba, you know we are not going to do that, ki gaida Ammah, Allah ya bata lafiya ita kuma, ki gaishesu", tafiyanta Ammah tayi dan tasan halin Amnah, sama ta haura daga nan, Aunty Amnah ma dariya tayi tabita a baya, basu jima da hawa ba suka sauk'o, Aunty Amnah na riqe da keyn mota, tare sukaje har gidansu Ajiddeh a WUSE II, a bakin gate suka tarar da masu gadin su Ajiddeh, da sauri d'aya daga cikinsu ya taso ya fara musu magana cikin Hausarshi da ba dai dai ba yace "Sannunka da zuwa Hajiya, kazo wajen dayan Hajiya na ciki ne", kai Aunty Amnah ta gyad'a mishi tareda cewa "Ehhh", Allahumma salli Ala, kamar jira yake ta gyad'a Kai ya fara zuba "Hajiya, ai Hajiyan ciki dinma baya nan, kwananshi biyu Kenan, dayan Aunty dinne ya fara tafiya tun ya dade sai kwana guda biyu sun wuce sai babban Hajiya din shima ya tafi, toh tun rana din har yanzu basu dawo ba, Alhaji ne kawai yana nan sai masu yin aiki din na gidan suma y'an iska tun Hajiya Babba da ya tafi basa bamu abinci mai dadi yirin na da, toh munason Hajiya ya dawo, Dan Allah kayi mishi waya sai kace mangal ne yace ya dawo Dan ........", hannu Aunty Amna ta d'aga mishi tace "Kai ka tabbata, Hajiyar gidannan fa nake nufi", ta nuna mishi gidansu Ajiddeh, juyawa yayi ya dubi gidan sannan ya juyo yana kallonta yace "Ye shine gidanmu din ai, gida na Alhaji namu, sunanshi ya fada a TV munji ma lokacin Abba Ahmad Jidda", kallon juna Aunty Amna da Ammah sukayi jin bayanin mai gadin, Ammah ce tayi magana wannan karon tace "Hajiyar gidan ba rashin lafiya tayi aka kaita asibiti ba?", kai ya shiga girgizawa kamar zai yadda k'asa . "Hajiya baije asibiti ba, yapot ne Abor ya kaishi ya tafi gari nasu can", da mamaki Ammah take dubanshi tace "Toh Hauwa kuma fa, ta dawo itama ko tare sukayi tafiyan", kai ya d'aga alamar yana tunani sannan ya kallesu yace "Hauwa din ni ban sanshi ba, ba a gidan nan yake ba", dariya Aunty Amnah tayi tace "Toh mangal ai Hauwan macece ba namiji ba, Ajiddeh fa muke nufi, wacce tayi aure", yace "Owo, ai baka fadamin Aunty ne kana nema ba, ai shi din yayi auren tun ya dade, so daya ne naga ya dawo gida tun lokacin da yayi aurenshi ya tafi da miji mai kyau wannan, yana bamu kudi in yazo kullum, Kai wannan mutum da Aljanna ne nace", Kai Aunty Amna ta gyad'a tace mishi "Toh Mangal mun gode, in sun dawo zamu dawo muma", ta ciro kud'i daga jakarta ta mik'a mishi, godiya ya dingayi musu yana washe baki, suna barin k'ofar gidan Aunty Amnah ta dubi Ammah dake tunani tace "Ammah kinji wai basa nan, kuma Ajiddeh ma batazo ba, can kuma su Abu sunce miki ta dawowa mamarta ba lafiya, anya wannan abin da akwai kanshin gaskiya kuwa?", Ajiyar Zuciya Ammah ta sauk'e tace "Amina koni abinda na kasa fahimta kenan, kuma kinji fa wai ita Ajiddeh ma bata nan, toh Allah dai ya tsare", baki Aunty Amna ta tab'e tace "dama can ni Ammah hankalina bai kwanta ba, Allah dai ya rufa asiri", "Amin",basu sake yin maganan ba har suka isa gida, sai da ta sauk'e Ammah sannan tayi mata sallama ta wuce nata gidan, Ammah na isa gida ta buga waya Maiduguri, nan take ta bada order akan ayi addu'a da sauk'an Qur'ani ta tura musu kud'in sadaka, don ga dukkan alama ba abun kirki ya dawo da Ajiddeh gida ba. Batuul ta kusa minti sha biyar xaune kan gadon bayan fitarsa ga yunwa da taji ta fara ji, mikewa tayi daga karshe tana share hawayen fuskarta ta nufi closet dinta, shiryawa tayi cikin y'ar gown mara hannu purple mai kyau, tana kkrin fiddo hijab da xata daura kan kayan ya shigo dakin, still tayi gabanta na faduwa, dad'da'dan kamshin turarensa ya cika dakin, a hankali ta juya tana kallonsa ta ga tsayawa yayi bakin kofar dakin yayi folding din hannunsa yana kallonta, maxa tayi ta dauke kai ta ciro hijab dinta xata sa yace " Drop that!" zumb'uro baki tayi tace "Ni sanyi nake ji" murmushi yayi yace "Did you just pout?", maza tayi ta maida bakin da ta zumb'uro ta girgiza Kai, karasawa yayi ya fizgo hannunta ta kusa fad'awa kanshi, bata ankara ba sae ji tayi ya hade bakinsu, sai da yayi kissing d'inta son ranshi sannan ya saketa, yana kallon idonta dake xub da hawaye yace "if you pout again, I will do more than this", hannunta ya kama tana hawaye suka fita daga dakin suka sauka downstairs, makullin motarsa ya dauka a palon sannan suka fita, shi ya bud'e mata motar ta shiga sannan ya zaga nashi side d'in, sai da ya tada sannan ya rik'o hannunta ya fara driving, a hankali yace "kin ma ci abinci yau kuwa?" Kin cewa komae tayi, yayi murmushi yana driving dinsa, har suka isa babu wanda yace komai sai murza hannayenta da yake cikin nashi, ganin gaban gidan da yayi parking yasata yin murmushi don haka kawae take son gidan ita dae, juyowa yayi ya dubeta ganin yadda fuskanta yayi lighting da murmurshi, hannu yasa ya juyo fuskanta tana kallonshi, a hankali ta sauk'e idonta kasa, giranshi ya d'aga yace "My wife's house, don't be over joyed being here uhh?", baki ta tab'e ta had'a rai ta janye fuskanta tareda bud'e motan ta fita, shima d'in murmushi yayi ya bud'e ya fita. 💖💝BATUUL💖💝 63 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Had'e rai tayi tareda zumb'uro d'an bakinta ta tsuke shi tayi gaba ta bar sa nan tsaye, sai da taje bakin k'ofa ganin k'ofar glass d'in rufe yasa ta tsayawa, rau rau tayi da ido ta juyo xata kallesa suka kusa cin karo, sadda kanta tayi k'asa zata juya ya saka hannunshi waist d'inta ya juyo da ita, fuskanshi dab da nata har tana jin numfashin sa na brushing jikinta da kamshin turarenshi mai dad'i, ya dan wara mata ido yace mata, "mey ya hanaki shiga, ai na fad'a miki its my wife's house, ni kad'ai keda access to it, da kinace zaki iya bud'eshi ne", bakinta ta zumb'uro mishi ta d'auke kai zata juya, hannu yasa ya juyo da kanta yana kallon fuskanta yace "Did you just pout again", kai ta shiga girgizawa da sauri dan ita bata ma san tana yi ba cikin murya kamar zatayi kuka tace "Yaa Abu banyi ba, kayi hakuri", murmushi yayi ya d'auke idonshi daga kanta sannan ya jawo hannunta sukayi k'ofar gidan, hannunta ya d'aura kan security lock d'in dake mannne jikin bangon, k'ofan ne ya bud'e da kanshi, da mamaki ta kalleshi, smirking yayi tareda d'age mata girarshi d'aya, kauda kanta tayi kamar bataga abinda yayi d"in ba, hannunta ya kamo cikin nashi su shiga, tur jewa tayi nan gun taqi motsi, da mamaki ya juyo don ganin mey ke damunta, dawowa yayi gabanta yana kallon fuskanta yace "Are you okay", tsuke bakinta tayi ta juyar da kanta, hannunshi yasa ya juyo da fuskan nata tana fuskantar shi yace "Hey!, talk to me, what's wrong with you", raurau tayi da idonta taqi ce mishi komai, sassauta muryanshi yayi yace "mey ke damunki wai", baki ta sunkuyar da kanta cikin sanyi tace "you just said I shouldn't be overjoyed being here, its your wife's house, so why asking me wats wrong?", abinda ta fad'a da yadda tayi maganan ne ya bashi dariya amma ya dake, had'e rai yayi yace "and what does that have to do with entering in, in zaki shigo ki shiga, you are wasting my time", hawaye ne ya shiga taruwa idonta, juyawa tayi zata bar wajen, yasa hannu ya fixgota, cak ya d'agata ya rungumota, ko'k'arin sauk'a ta shiga yi daga jikinshi tana wuntsila k'afafu, matsetata yayi k'irjinshi sannan ya sunkuyo daidai kunnenta yace "if I should slap you right away, ina miki wasa ne", lamo tayi jikinshi ta rintse ido tana shak'ar k'anshin turarenshi mai dad'i, bata bud'e ido ba sai da taji ya direta kan lallausan gado, a hankali ta bud'e lumsassun idanuwanta ta sauk'e kansa, ya kwanta gefenta ya lumshe ido, kyakkyawan fuskanshi ta tsurawa ido, lumsassun hazel like idanunshi da lashes yabi ya kwanta, sai chiseled nose d'inshi, da d'an k'aramin plumpy pinks lips d'inshi, tab'e baki tayi ta d'auke Kai a ranta kuwa haushin kanta taji na kallonshi da ta tsaya yi bayan bama wani kyau bane dashi, a hankali ta sake juyowa bayan kamar 3mins, har lokacin yana kwance kuma bai bud'e ido ba, Idonta ne ya fad'a kan broad k'irjinshi da buttons d'inshi na sama guda biyu da suka bud'e, gabanta ya fadi ba kadan ba, a hankali ta dinga jin abu na yawo spines d'inta, rintse ido tayi dan batason cigaba da jin abinda take jin, samun kanta tayi da son jinta kwance jikinshi, ita kanta ta rasa gane dalilin hakan, ta kuma runtse ido xuciyarta na double flipping, dai dai lkcn da ya bude nasa ya juya yana kallonta, a hankali ya mirgina kusa da ita ya dagota ya mai da ita kan faffad'an k'irjinshi, kamar wacce akayi electrocuting a firgice ta bude ido ta yunk'ura xata sauka daga jikinsa, kamin ta sauka taji ya sako hannayenshi a waist d'inta ya dad'a rungumota jikinshi, ajiyar zuciya ta sauk'e tareda yin lamo tana jin yadda heartbeat d'insu ke gudu lokaci guda, hannu yasa kan gashinta ya warware k'ullin da ta yiwa gashin, ya d'aura fuskanshi kan lallausan gashin nata yana shak'ar k'anshin da sukeyi mai dad'i. Ajiddeh kam tun a airport tayi magana da Mummy tace mata suna Ndjamena, tana sauk'a airport a Nigeria ta sake booking wani ticket d'in da zai kaita har can d'in, awanta shida tana zaune kamin jirgi yazo suka tafi ko cikin gari bata shiga ba, taxi ta tara ya kaita har hotel d'in da su Mummy sukace mata sunyi lodging, kai tsaye ta wuce d'akin da suke bayan ta sallami d'an taxi, knocking k'ofar d'akin tayi ta tsaya tana jiran a bud'e mata k'ofa, Yaa Zee ce ta bud'e mata k'ofan, babu yabo babu fallasa suka gaisa tun daga bakin k'ofa, Mummy da Aunty Jainaba ne zaune d'akin hotel d'in, k'arasawa tayi itama ta zube kan makeken gadon tana maida numfashi, takai minti biyu a haka sannan ta mik'e daga kwancen da take tana kallon Mummy tace "Mum sannunku", sannan ta juya ta dubi Aunty Jainaba dake kallonta itama, murmushi tayi mata tareda mik'ewa tana k'ok'arin rage kayan jikinta tace "Mummy duk abinda zamuyi cikin kwana biyu zamu gama dan cewa zaiyi zai biyoni, dan da k'yar na samu ya hak'ura bai biyonin ba, jarababbe, dan haka yau da gobe ayi komai mu koma da wuri", baki Aunty Jainaba ta tab'e tace "Dan shi sarkin k'wak'war mata ai sai ya biyo kin, kwana biyun da zakiyi shine harda wani kuzo tare, ai ko da yaxon ma kuma babu abinda zai hanamu tahowa", Yaa zee ce ta taho riqe da can drink da ta d'auko fridge ta bayan ta rufe k'ofan, zama tayi tana kallon Mum tace "mummy kinsan mutumin nan appointment yake badawa, in bakazo ba time ya wuce sai dai a sake booking, Ku shirya mu wuce tun wuri kamin time d'inmu ya k'ure muyi asara, ba musu su Mum aka hau shirin tafiya, lokacin Ajiddeh ta fito cikin toilet d'aure da towel har ta watsa ruwa, itama shirin ta hau yi, suna gamawa suka fito waje, taxi suka tare sukayi mishi kwatancen inda suke son zuwa, babu b'ata lokaci ya fad'a musu amount d'in da zasu bashi sannan suka d'au hanya, tafiyar awa uku suka isa, driver ya tsaya dab inda suka mishi kwatance, gidane d'an madaidaici mai kyau, gabanshi da bayanshi kuma duk jeji ne, da mamaki Ajiddeh ta juyo tana kallonsu tace "nan ne gun?", kai suka kad'a mata a tare, cewa tayi "ca nake wajen wannan mutumin zamu koma na kwanaki", Aunty Jainabace tace "wa?, wa zai koma wajen munafikin nan, ai kud'inmu kawai yacinye babu wani aiki da ya iya, macuci ne, bok'an k'arya", (Lol boka ma harda na k'arya da gaskiya, Allah ya tabbatar damu kan shiriya), Ajiddeh ce ta ciro kud'in ta baiwa mai taxi kud'inshi, yana tafiya suka shiga knocking, mai gadine ya bud'e musu gate d'in gidan bayan ya gama yi musu tambayoyi sannan yayi musu jagora har palon gidan, palone babba, babu komai ciki sai carpet da aka shimfid'a su wasu throw pillows, wani farin dattijo ne zaune yana sanye da farin kaya da dogon farin gemunshi, gefenshi kuma littafai ne tuli guda, a tare sukayi sallama, saida ya amsa musu sannan suka shigo daga ciki suka samu waje suka zazzauna, shi ya fara yi musu magana kamar haka, "nasan abinda ke tafe daku baki d'ayanku, Keh!", ya nuna Yaa Zee yace "senator Gamji ke son aurenki amma yana da mata ku kuma baku son mai mata, ita kuma wannan", ya nuna Ajiddeh yace "tabbas akwai wani al'amari tattare da ita mai rikitarwa da ni kaina na kasa fahimta, abune babba da ya shige min duhu na kasa gano komai game dashi duk iyawata, kuma shi wannan abun na tare da ita dan har ya faru ya k'are sannan ba alheri bane gareta", a tsorace suke jin bayanin malamin da abinda yake fad'a musun, a d'arere mummy ta kalli malamin tace "Allah gafarta malan, wane abune haka har zaifi k'arfinka, mu nan munyi maka alk'awari daga miliyan goma har zuwa hamsin zamu iya badawa in dai aikinmu zai yi yadda mukeso, Allah gafarta malan, a taimaka a dubo mana wannan abun dake shirin jawo mana matsala", wani shu'umin murmushi yayi yace "ai ni d'in nan duk abinda kikaga banyi shi ba a fad'in garin nan toh tabbass babu mai iya yi dan ni keda iko ga kowanne aljani da muke amfani dasu, dan haka ku kwantar da hankulanku, anjima da yamma za a fara aiki, yanzu haka masauki za a kaiku kamin yamma tayi, su wad'anda za ayiwa aikin kowacce d'akinta daban, ku kuma za a had'eku d'aki d'aya ku da babu aikin da zaku buk'ata, Dan aikin nada son sirri", hakan kuwa akayi, wani d'an saurayi ne ya kaisu d'akunan da aka umurceshi da ya kaisu, y'an madaidaitan d'akuna ne masu kyau ba laifi, Zainab da Ajiddeh aka basu d'ad'd'aya kowannesu sai mummy da Aunty Jainaba aka had'esu a guda d'aya. A hankali Abu ya d'aura plumpy lips d'inshi kan goshin Batuul yayi pecking, haka ya dinga yi har saida ya sauk'o wuyanta, babu abinda jikinta keyi in banda rawa, k'ok'arin barin jikinshi ta shiga yi amma bai saketa ba, a nutse ya kwantar da ita kan gadon ya d'an sunkuyo kanta, sai lokacin tayi regretting dadewan da tayi kwance kan gadon, hawaye ne ya shiga silalowa daga idonta, baki ta bud'e zatayi magana Abu ya had'e bakinshi da nata, sosai ya shiga kissing d'inta, numfashinta ne ya kusa d'aukewa jin irin abubuwan da yake mata, kuka ta fasheda tace "Yaa Abu dan Allah kayi hak'uri plss bana son irin haka", baima san tana yi ba yaci gaba da abinda yakeyi, Batuul kam kuka takeyi sosai, saida taji ya fara wuce limit kuma duk magiyarta bai sarara mata ba tace "Yaa Abu am not pure wllh, kayi hak'uri ka barni bazan sake ba dagaske", sai da ya jagwalgwalata son ranshi kamin ya saketa ya fad'a gefenta yana maida numfashi, hannu yasa ya jawota jikinshi ya rungumeta tsam jikinshi ta gefe tareda kwantar da ita kan faffad'an k'irjinshi, kuka kawae take idonta a rufe, a hankali yayi brushing lips d'inshi kan nata tareda mata light kiss, har lokacin idonshi lumshe suke shi ma, sunfi awa d'aya a haka sai ajiyar zuciya Batuul ke sauk'ewa da haka har bacci ya d'auketa, a hankali ya kwantar da ita daga jikinshi ya mik'e ya shige toilet, wanka yayi ya fito ya canja kaya, murmushi yayi yasa hannu cikin gashin kanshi ya bajesu ganin tiny figure d'inta na bacci peacefully, karasawa yayi gadon yayi pecking d'inta, motsi tayi tare da gyara kwanciyarta, wani nutsuwan da bae taba sanin da shi ba yake samu gun Batuul, gown d'inta ya d'age har zuwa cinyoyinta, ya janyo duvet d'in gadon ya ninka biyu ya rufa mata, kanta kawai ya bari a bud'e, key d'in motanshi ya d'auka kan side drawer ya fita, if he can clearly remember yau babu abinda taci, driving yakeyi amma gaba d'aya hankalinshi na kan Batuul, murmushi kawai yakeyi ba tareda yasan dalili ba, but shi dai yasan being with Batuul na sashi jin exceptional feeling d'in da bai tab'a experiencing ba, a wani restaurant d'in kusa dasu ya shiga ya siyo musu abinci, baifi thirty minutes ba da fita ya dawo, har lokacin tana bacci, kan gadon ya hau ya d'agota jikinshi, daidai kunnenta ya rad'a mata "Wake up, sleepy head", a hankali ta bud'e lumsassun idanunta ta sauk'e kanshi, komawa tayi zata kwanta ya d'agata cak ya zaunar da ita, a tsorace ta wara ido, abubuwan da suka farune ya dinga tariyo mata, rintse ido tayi bata son ganinshi ga wani kunyansa da take, a ranta ta godewa Allah da yasa tace mishi she is not pure, iska ya hura mata fuska yace "Hey tashi kici abinci", sai lokacin ta bud'e ido ta kalli inda ya zuba ledojin, ce mata yayi "Brush first", a hankali ta yaye bargon da ya rufa mata, ganin cinyoyinta waje yasa tayi maza ta rufesu, a hankali ta kalleshi ta gefen ido taga ita yake kallo yana murmushi, zumb'uro baki tayi ta sauk'o daga kan gadon ta nufi toilet da sauri, ya bi ta da kallo, brush d'aya kawai ta gani, fitowa tayi ta tsaya bakin k'ofan baki a tsuke, ya tsaya yana kallon yadda ta tsuke bakin, a ranshi yace "she is cute, Not beautiful", ce mata yayi "fito mana, ko tsayuwan bakin toilet d'in ke miki dad'i?", raurau tayi da ido tace "Ai ba brush ciki, guda d'aya na gani", ba tareda ya kalleta ba yace "then you use that one, it's mine", wara ido tayi jin abinda yace, ta had'e rai tace "I can't use it, its yours", murmushi yayi ya tashi ya isa inda take ya fixgota ta fasa ihu, ya had'a bakinshi da nata, ya kai two minutes yana kissing d'inta sannan yace "you can now go and brush", hawayen da ya zubo mata ta goge da bayan hannu ta koma cikin toilet d'in jiki a sanyaye, ruwan d'umi ta kunna zata wanke brush d'in sai kuma tayi tsaki ta shafa toothpaste d'in ta wanke bakinta a haka, a d'akin ya baje abincin da ya siyo musu, a hankali ta k'araso ta zauna bakin gadon, kallonta yayi yace get down and eat", ba musu ta sauk'o dan yunwan da takeji, a hankali ta dinga cin abincin har saida taji ta k'oshi, shi kam babu abinda yakeyi banda kallonta, birgeshi tayi yadda takecin abincin, ganin ta dena ci ya harareta yace "me?", a hankali tace mishi "am full", had'e rai yayi yace c'mon finish dat before I meet you there", baki ta zumb'uro ta matso taci gaba da ci a haka har suka gama, ita ta tattare packs d'in duka waje d'aya, hannunta ya kamo yana kallon fuskanta yace "kin manta ma mey ya kawoki ko, you were busy engrossed in being hugged by me and feeling the warmth of my body huhh?", had'e rai tayi ta d'auke kai kamar bata ji shi ba, murmushin shi mai kyau yayi ya jata suka tafi d'akin da ya zuba kayanta, ce mata yayi "Get what you are here for" sannan ya sake mata hannu, k'arasawa tayi ta d'auko d'an kwalin da kayan ke ciki, hannu yasa ya amshesu daga gunta, kallon mamaki ta bishi dashi, wai wannan Yaa Abun da ta sani ne kuwa, har wani trying yake ya zama gentle, Lol, kallonta shima yayi tareda smirking yace " Hey kina kallewa Ajiddeh miji ko, zata dawo ne, before then let's get going", ya kamo hannunta, kin tafiya tayi har saida ya juyo yana kallonta "What's up", ya fad'i tareda d'age mata girarshi d'aya, raurau tayi da ido kamar mai shirin kuka a shagwab'e tace "Yaa Abu I don't want to leave, ni nafi son xaman nan kai ka tafi", sai da ya tsaya for some seconds yana kallonta bayan ta gama maganan sannan yayi murmushi yace "har kin manta, d house is my wife's, my love, we have to leave", had'e rai tayi ta tsuke baki jin abinda yace mata, warce hannunta tayi daga nashi tayi gaba abinta, dariya ta bashi shima ya biyota a baya, yana danna lock d'in motar ta bud'e ta fad'a ciki, shima baice mata komai ba ya bud'e ya shiga yana murmushi. 💖💝BATUUL💖💝 64 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Bai ce mata komai ba ya tada motar sukayi gaba, lokaci lokaci yake juyowa yana kallon yadda ta tsuke fuska, murmushi kawai yake yi yana tuk'in, Batuul kam ko sau d'aya bata juyo ta kalleshi ba sai ma window da ta juya tana kallon waje, hannunshi ya mik'o ya kamo nata cikin nashi har lokacin bata juyo ta kalleshi ba wai a dole fushi takeyi anqi barin ta a gidan glass, gaban wani fruit stall yayi parking, sai snn ya sake mata hannuwa ya fita, ba a jima ba ya dawo riqe da paper bags da fruits a ciki, daga bayan mota ya zuba su ya zagayo ya shiga ya tada suka tafi, har lokacin su Batuul rai a had'e, a hankali ta juyo da kanta suka had'a ido, tsuke baki tayi ta d'auke kanta da sauri, ganin expression d'in fuskanta bai san lokacin da dariya ya k'wace mishi ba, dariya sosai ya shiga yi harda dukan steering wheel, juyowa tayi tana kallonshi da idanunta da suka cicciko, ganin yana kallonta baice komai ba ta kifa kanta a cinya ta fashe da kuka, kuka sosai takeyi kamar wacce aka Zane, dariya hakan ya dad'a bashi, dakewa yayi yace "Wai What's wrong kike cikamin kunne da kuka, mey akayi miki?", bata d'ago ba, saima k'arawa da tayi, daidai nan yayi parking, k'ofa ta bud'e zata fita ya fixgota, d'ago kanta yayi yana kallon yadda cute lips d'inta suka koma ja, kallon idonta yayi in a serious tone yace "mey ya sameki"?, fashewa tayi da wani sabon kukan, janyota yayi ya rungumeta jikinshi tsam, babu abinda take sai sauk'e ajiyar zuciya jinta kwance kan faffad'an k'irjinshi da k'anshinshi mai dad'i, har saida yaji tayi shiru sannan ya d'agota yana kallon fuskanta yace "tell me mey ke damunki kike kuka", zumb'uro baki tayi ba tareda ta bari sun had'a ido ba tace "ba kai ne ke min dariya ba, kuma kace baxan tsaya wancan gidan ba", baisan lokacin da dariyan ya sake kubce mishi, rai b'ace ta tsaya tana kallon yadda ya dage yana mata dariya, a fusace ta bud'e k'ofar motan ta fice, bata tsaya ko ina ba saida ta shige d'akinta, kan gado ta fad'a taci gaba da kukanta, sai da ya gama dariyarshi ya fito cikin motar, abubuwan da ya siyo da kuma wad'anda suka d'ebo can gidan ya kwaso sannan ya rufe motar shima ya shigo gida, a kan kitchen island ya xuba kayan da suke hannunshi ya haura sama, direct d'akin Batuul ya wuce, kwance ya tarar da ita a kife har lokacin kukan takeyi, hannu yasa ya d'agota yana kallonta yace "I told yhu d house is my wife's, dariya kuma ai ke kika sani yin dariyan", d'an murgud'a bakinta tayi ta janye jikinta ta juya mishi baya, murmushi yayi ya matsa inda take ya rungumota ta baya, ajiyar zuciya ya sauk'e jin k'anshin jikinta mai dad'i, cikin sanyin murya yace "okay sorry, I will ask my wife, if she permits then you stay there", wani bak'in ciki ne ya sake turnik'e ta jin sai ambatar wife d'inshi yakeyi, d'an k'aramin tsaki tayi daga ciki ta shiga k'ok'arin kwace kanta daga rik'on da yayi mata ta miqe ta shige toilet ta rufo k'ofar da k'arfi, dariya yarinyar ke bashi in tayi wani abun, waje ya samu kan gadon yayi kwanciyarshi abinsa, tafi minti talatin cikin toilet tana zaune cikin bath tub, sai da tayi wankan tsarki sannan tayi normal wankan ta ta fito, ganin dad'ewan da tayi tasan ya bar d'akin, tana d'aure da towel jikinta d'aya kuma tana goge gashin kanta dashi ta fito, gaban mirror taje ta jawo stool ta zauna tana goge gashin, sunkuyawa tayi ta d'auko hand dryer, d'agowan da xata yi ta hango mutum jikin mirror, wani irin k'ara ta fasa zata koma cikin toilet don bata yi tunanin yana nan har lkcn ba, da hanzari ya mik'e ya fixgota kan ta shiga bayin, kuka ta fashe da zata sulale k'asa dan ta tsorata sosai, k'afafuwanta duk suka yi weak, tsam ya rik'ota ya rungumeta, har lokacin kuka takeyi, hannu ya d'aura bayanta ya shiga patting, a kunne ya dinga rad'a mata addu'a har ta samu nutsuwa, "sorry i didnt mean to startle you", kan gado ya maidasu suka zauna, kallonta kawai yakeyi, gashinta dake d'igar da ruwa ya kalla sannan ya kalleta yace "wankan mey kikayi?", wani kunya ne taji ya kamata da ta gano inda tambayarshi ta nufa ta had'e rai tace "wanka nayi", still yana kallonta yace "did you hear me say kinyi wasa da k'asa?, I said wankan mey kikayi?", kwace jikinta tayi daga nashi zata tashi ya fixgota, had'e rai yayi yace "na fara miki wasa ko?", baki ta zumb'uro ta shagwab'e fuska tace "Yaa Abu ni wanka kawai nayi", hannu yasa cikin gashinta dake jik'e ya yamutsa, hannu da ya jiqe da ruwa ya kawo gaban fuskanta yace "And this", a hankali ta d'ago kai kalleshi taga babu alamun wasa a fuskanshi tace "Yayi datti ne kawai shine na wanke", murmushi yayi ya saketa ya mik'e yayi hanyan fita, har yaje bakin k'ofa ya juyo yana kalleta yace "kin iya fruit salad?", a hankali ta kad'a mishi kanta tace "na iya", yace "make some, and don't add apricot", kamar yarinya k'arama haka ta kad'a mishi kai, yana fita ta sauk'e ajiyar zuciya ta koma gaban mirror tayi y'an shafe shafenta ta gyara gashinta ta kameshi waje guda, kaya ta canja tasa ash wando da pink tank top, hijab ta d'auko sannan ta shimfid'a abin sallah ta hau ta rama wanda ake binta, ta dad'e zaune tana azkars, tana gamawa ta nad'e abin sallah kenan aka turo k'ofar d'akin, a tsorace ta juyo ganin waye, da sauri ta sake abin Sallah hannunta tace "Yanzu zan fito inyi", da gani kasan batada gaskiya, murmushi yayi yana kallon sallayan ya k'araso gabanta yace "Didn't I tell you not to wear hijab in my presence", a daburce tace "sanyi ne nakeji shine na saka", da kanshi ya k'arasa inda take tsaye ya cire mata hijabin yace "Move now", ba musu tayi gaba ya biyota a baya, a d'arare ta dinga tafiya, kad'an kad'an ta riqa juyowa ko yana bayanta, haka, tana juyowa suke had'a ido ta d'auke nata har ta iso kitchen, paper packs d'in da ta gani kan island d'in ta shiga bubbud'ewa, fruits ne iri iri ciki, ciccire su tayi ta d'ebi wad'anda zatayi amfani dasu ta maida sauran Fridge, sai da ta fara d'aura syrup kan wuta tukunna ta d'ebi fruits d'in tayi sink dasu, ganin kwakwa ciki yasa ta tunawa da abinda Aunty Amna tace mata ta had'a tasha, sai da ta fara jik'a ayar sannan ta wanke fruits d'in ta shiga yankasu, a fridge ta saka sannan ta d'auko coconut breaker ta fasa kwakwar, ta kankare ta had'a ta markadesu a blender da dabinon, ta hada rich drink din ayar da kwakwa sae dabino, tana gamawa ta ciro fruits din da ta yanka ta zuba a glass bowl snn ta zuba syrup d'in da yaji flavours iri iri a ciki, juice d'in da ta had'a ta tsiyaya kad'an cikin tumbler ta juye sauran cikin jug ta saka fridge, a tray ta d'aura bowl d'in fruit salad d'in da spoon ta d'auka zata fita kenan ya shigo kitchen, yana kallonta yace "har kin gama?", kai ta gyad'a mishi , amsan trayn yayi ya koma cikin kitchen d'in ya ajiye shima ya zauna ya d'auki spoon tareda d'iban fruit salad d'in ya kai baki, lumshe ido yayi jin taste mai dad'i, a hankali ya bud'esu yana kallonta yace "Thank you, yayi dad'i", murmushi tayi mishi kawai ta d'auki tumbler da ta zuba juice d'in a ciki zata fita, yana kallonta yace "ke baki sha ne?", kai ta girgiza tare da nunamishi abinda ke hannunta tace "ni wannan zan sha", "meye shi wanna d'in?", ya tambaya tare da tsareta da ido, sunkuyar da kai tayi tace "coconut juice", smirking yayi tare da ce mata "Ai ba shi kad'ai Aunty Amna tace kisha ba, harda fruits ma naji tace kisha", sai lokacin ta tuna da yaji abinda akace tasha d'in, kunyane ya kamata tace "ni wannan kawai nakeson sha", alama yayi mata da tazo ta zauna, ba musu ta dawo ta zauna kan kujeran dake facing d'inshi, d'ayan spoon d'in ya mik'a mata, ansa tayi daga hannunshi tana kallonshi yace "sha mana", a hankali ta dinga tuttura fruit salad d'in har saida suka gama a tare, "lemme have the drink", yace mata, wani tumbler d'in ta d'auko ta tsiyaya mishi ciki, karb'a yayi tareda kashe wutan kitchen d'in ya janyo hannunta sukayi waje, har suka isa parlour nanma duk ya kashe wutan sai TV kawai da yake aiki, sai da ya zauna a k'asa sannan ya fizgota jikinshi, a tsorace ta riqe tumbler da hannayenta tana tsoron kar drink d'in ciki ya zube, gashinta ya baje ya sa fuskanshi ciki yana shak'ar k'anshinsu, take jikinta ya fara rawa jin hannayenshi cikin rigarta, ba tareda ta bari sun had'a ido ba tace "Yaa Abu zanje in kwanta", shima d'in bai kalleta ba idonshi na kan TV yace "tsaye kike yanzu?", shiru tayi ta koma ta kwanta tayi lamo jikinshi, sai da ya gaji dan kanshi ya barta, wajen k'arfe tara ta fara jin bacci tace mishi "Yaa Abu I have school tomorrow, zanje inyi bacci", baice mata komai ba kamar ma bai ji ba, ta sake maimaita mishi, d'ago fuskanta yayi yana kallonta yace "kina damuna fa da surutu, na hanaki bacci ne", hawaye ne ya cicciko idanunta ta koma ta kwanta, a ranta taji dad'i tayi sallah, a hankali ta dinga kuka batasan lokacin da bacci ya d'auketa ba, sha d'aya ya kashe TVn, cak ya dauketa kamar wata baby yayi sama da ita, a kan gadon d'akinshi ya direta sannan ya saka pyjamas d'inshi ya hawo kan gadon, jawota yayi jikinshi tsam ya rungumeta sannan ya kashe musu wutan ya tofa musu addu'o'in bacci ya kwanta tare da rufa musu duvet, tun lkcn da ya dauketa dama ta farka, duk ta tsorata ba kadan ba, ganin inda ya kai ta maimakon dakinta ya kara rikitata, sae dae bata nuna masa ta farka ba har taji ya direta kan gado, a hankali ya shige jikinta bayan ya rufesu, nan jikinta ya dau rawa jin hannunsa a cikinta, bata san lkcn da ta saka kuka a hankali tace " Yaa Abu pls allow me to sleep" murya can kasa yace "dama baccin karya kike koh?" Girgixa kai tayi tace "Allah bacci nake fa" bata rufe baki ba ya tura bakinsa cikin nata, nan ya fara mata abubuwan da suka tsoratata, ta kwace bakinta jikinta na rawa tace "Don Allah kayi hakuri ya Abu, am not clean" wani murmushin rainin hankali yayi yace "Really?" Cikin kuka tace "Yess" ihu ta saka jin abinda yake shirin yi tace "Ya Abuu stop, don Allah kayi hakuri" murya can kasa yace "No! I will check for my self" 💖💝BATUUL💖💝 65 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Kuka ta fasheda ta shiga tutturashi tana cewa "Yaa Abu dan Allah kayi hak'uri am not clean", kamar kukan nata dad'a tunzurashi yakeyi, hannunshi yasa ya d'age y'ar rigar dake jikinta, sosai ta tsorata da abubuwan da yakeyi mata, tana kukan tace "Yaa Abu dagaske fah nake", hankalinta bai gama tashi ba saida taji hannayenshi kan mararta, rawa jikinta ya fara, ajiyar zuciya kawai ta koma yi sai hawaye ihun ma ta kasa, d'agota yayi yana kallonta jin tayi shiru, rintse ido tayi dan baza ta iya had'a ido dashi ba, sosai takejin kunyarshi ga jikinta sae rawa yake, hawayen da ya gani shimfid'e fuskanta yasa jikinshi yayi sanyi, yasa yatsunshi ya goge mata hawayen, tsam ya rungumota jikinshi kamar zai maidata ciki tareda rufa musu duvet d'in, a hankali ta dinga sauk'e ajiyar zuciya, gashin kanta ya dinga shafawa har saida tayi bacci, kwanciyanta ya gyara mata tareda manna mata kiss goshinta. Su Aunty Ajiddeh ko tunda aka kwanta bacci, bata tashi ba saida taji motsin ana tab'a mata k'ofa, tashi tayi daga kwanciyar ta zauna da wuri, malamin nasu ne ya k'araso da wani d'an roba a hannunshi, waje ya samu ya zauna daga bakin gadon tareda washe mata hak'ora yana jan carbi, matsawa tayi daga baya tana kallonshi a k'ek'ashe tace "Malan lafiya", dariya ta bashi yace "ai duk lafiyarce ta kawo haka", roban dake hannunshi ya mik'o mata yace "ko ba biyan buk'ata kike nema ba", kai ta gyad'a mishi batareda ta ce komai ba, ganin yanda take yasa shi yin murmushi yace, "wannan wanka zaki shiga kiyi dashi, sannan wannnan turare za ayi dashi kuma babu ke ba yin sallah har na kwana d'aya, kallonshi tayi tace "kana nufin yau baki d'ayan banyin sallah?", gemunshi ya shafa yace "k'warai kuwa, harma da gobe", karb'a tayi tace "toh kaje in nayi wankan nayi turaren", kai ya girgiza mata ya tsareta da ido yace "ai yanzu zaki shiga kiyi ki fito, mu zamu turarakin", ba musu kamar wata wawiya ta karb'i roban da akayi tsubbe tsubbensu ta shige toilet d'in d'akin dashi, yana nan zaune ta fito da d'aurin k'irji sai wani da ta rufa a kanta, lokacin har an kawo kaskon da za ayi turaren dashi, babu abinda yakeyi sai binta da ido, gaba d'aya ta tsargu dashi, ce mata yayi ta cire towel d'in dake d'aure jikinta, ba musu kamar shashasha ta cire wanda yake kanta kawae, kallonta ya tsaya yi yace "duka zaki cire", wani kallon raini ta bishi dashi tace "wannan kawai zan cire in zaka yi a haka malan kayi", dariya kawai yayi ya miqe ya dinga gumbud'a garin maganin nan cikin wuta, cikin lokaci k'anin d'akin ya gauraye da hayaqi, ba a ganin komai, kanta ya fara juyawa, kamin ace komai ta juwa ya yadda ta, shi ya kinkimeta ya d'aura ta kan gadon sannan ya gama asiranshi ya fita. Bacci b'arawo ne kawai ya sace Batuul dan batasan lokacin da tayishi ba, da asuba ma tanaji Abu ya kwantar da ita daga jikinshi ya gyara mata kwanciya snn ya shiga toilet yin wanka, tana jinshi ya gama shirinshi ya fice masallaci, yana fita itama ta miqe a guje tayi nata d'akin, toilet ta fad'a itama tayi wankan ta daura alwala sannan ta fito ta tada Sallah, Abu na dawowa masallaci d'akinshi ya nufa, murmushi yayi ganin bata nan ya nufi d'akinta, a hankali ya tura k'ofan d'akin, ganin tana Sallah yasashi jawo mata k'ofan ya koma parlour yayi kwanciyarshi, sai da ta gama y'an shafe shafenta ta ta tattare d'akin snn ta sake kaya ta sauk'o kitchen, breakfast ta shiga had'a musu lafiyayye, oat soup tayi da grilled chicken salad sai kunun gyad'a da garlic bread, ido ya lumshe jin aroma d'in abincin duk ya cika gidan, sai da ta gama ta jera musu komai kan dinning, parlour ta k'araso nanma zatayi y'an gyare gyare, ganinshi kwance yasata tsayawa tana kallonshi, lumsassun idanuwanshi ya bud'e ya sauk'e a kanta, da sauri ta sadda kanta k'asa ta kasa ci gaba da kallonshi, kunyanshi takeji gaba d'aya, a guje ta juya ta haura sama ta rufo k'ofa, goma da wani abu bayan ya shirya yayi d'akinta ya ganta zaune kan gado da waya a hannu ga jakanta daga gefe, da alama ta gama shirinta, a hankali ta d'ago ta kalleshi ta maida kanta taci gaba da abinda take shima kallon nata yake yace "bakida class ne yau", a sanyaye ba tareda ta kalleshi ba tace "inadashi by eleven", yace "kinci abinci ne?", kai ta gyad'a mishi alaman A'a, a d'an tsawace yace "talk to me, and don't you dare nod your head to me again, get down and have your breakfast", ganin ba wasa tattare dashi yasa tayi maza ta ajiye wayan tayi hanyan waje, saida tayi gaba snn ya biyota, shi ya fara jan kujera ya zauna snn itama taja ta zauna, kunun ta fara mishi serving ta mik'amishi snn tace "mey zan zuba maka", binta kawai yakeyi da kallo, ta dinga jin wani iri, yayi murmushi yace "serve me anything", plate ta jawo ta zuba mishi duk abinda ta girka, snn ta xuba nata, ita ta fara gamawa amma bata tashi ba har saida ta jira ya gama, sai da ya miqe yana goge bakinshi da napkin yace mata "let's get going" miqewa tayi itama ta haura sama, ba a jima ba ta sauk'o riqe da jakarta a hannu da mayafi, a cikin mota ta tarar dashi ta shiga ya tada suka tafi, shiru cikin motar babu mai cewa komai sai k"ira'ar Shuraim ke tashi yana karanta suratul Yusuf, sai da yayi parking cikin makarantarsu sannan ya rage volume yana kallonta yace "What time zaki gama lecture yau?", kamin tayi magana yace "anyway here is my phone, call me when you are done", ya mik'o mata wayanshi da kud'i, a sanyaye ta karb'a dan batason irin kallon nan da yakeyi mata, har saida ta shige class tukunna yaja motanshi ya bar premises d'in makarantan, yana tafiya wayanshi ya hau ringing, sai lokacin ya tuna da Ajiddeh ganin ita ke k'iranshi, ya sauke ajiyar xuciya yayi receiving yasa a kunnenshi. K'arfe hud'u saura ya k'ira Batuul a wayarshi da ya bata, bata d'aga ba har saida ya sake k'ira a karo na uku, tana d'agawa yace "Are you done", "ehh" tace, yace mata "am by d court", daga haka ya katse wayan, da sallama ta shigo motar tare da ce mishi "ina wuni", bai amsa ba sai jeho mata tambaya da yayi yace "ina kika shiga na k'ira twice bakiyi picking ba", a hankali ta d'ago idanunta tace "I was prayi.....", kasa k'arasawa tayi ganin irin kallon da yake mata tayi Saurin Sadda kai k'asa, murmushi yayi ya d'auke idonshi daga kanta ya tada motar, jin baice mata komai ba yasa ta sake cewa, "Wayan nefa na silent, I didn't know you called shiyasa banyi picking ba", juyowa yayi da lumsassun hazel like eyes d'inshi yace "Did I say anything?", d'auke kanta tayi ganin irin smirk d'in dake fuskanshi, kamar jiya haka yau ma yasa ta yi Mishi fruit salad da magrib, bai shigo ba sai wajen k'arfe takwas har anyi Isha, a kitchen d'in ya tadda ta, sai da ya jira ta gama ya d'au tray d'in tare da kamo hannunta sukayi d'akinshi, bayi ya nufa ya bar ta tsaye dakin duk a tsorace, ya tsaya daga bakin kofa ya juya yana kallonta yace " Kar ki kuskura ki fita" marairaice fuska tayi, ya juya ya shiga bayin, alwala ya dauro ya fito, ya sameta inda take tsaye har lkcn, yace "Ki shiga kiyi alwala" hade rai tayi tace "Ni fa nayi sllh" ya mata wani kallo yace "I know, but are yhu trying to tell me ba kya alwala kike kwanciya" shiru tayi tana kallonsa, pray mat ya dauka ya shimfida, ta nufi bayin a sanyaye ta dauro alwalan ta fito, dai dai nan shi ma ya shigo dakin rike da hijab dinta ya mika mata, karba tayi yace "Nafila xa muyi, ko shima ba kya yi" turo baki tayi bata ce komai ba, yayi murmushi ya hau kan pray mat din, kamar mara laka ta bi sa tana kkrin sa hijab din da ya bata, sallah raka'a biyu ya ja su, ya dade yana addu'a bayan sun sallame sannan ya juya yana kallonta, murmushi yayi ganin yanda tayi jigum, ya shafe adduar ya mike, ya dago ta ya kai ta gado ya kwantar da ita yace "Sleep" rufe ido tayi da sauri, shima ya hau gadon ya kwanta, yau ma jawo ta jikinshi yyi ya kwantar da ita yasa musu dim light tare da janyo system d'inshi ya kunna yana danne danne, wajen sha d'aya ya kashe yana kallonta, ya ga ynda ta runtse ido wai tana bacci, dariya ta basa, ya daura lips dinsa a hankali kan nata, numfashinta ne taji ya fara yin sama sama jin abinda yayi, ae da sauri ta bude ido ta marairaice tace "No! Yaa Abu plss, am not cle....", bai bari ta k'arasa abinda zata fad'a ba ya bige mata bakinta da d'an yatsanshi ya had'e bakinshi da nata, a hankali ya dinga kissing d'inta idonsa lumshe har ya sauk'o wuyanta, rikicewa tayi jikinta ya dau rawa sae cewa take she's not clean, ihu ta saka jin yana neman raba ta da kayanta, cikin wani Husky voice da ya kara tsoratata yace " I will slap you idan kika sake min ihu" tsit tayi jikinta na rawa sosai, tana ji tana gani ya rabata da kayanta, ta rike hannunsa hawaye na bin kuncinta cikin rawar murya tace "Don Allah don annabi kayi hakuri ya Abu, wllh tsoro nake ji plss" tausayinta ne ya rufesa sae dai bai ce komae ba don bai jin xae iya kyaleta yau, bata gama rudewa ba sae da ta ga da gaske yake ashe, kuka ta dinga yi kamar ranta xae fita jikinta na rawa tana kiran sunansa tana hada sa da Allah ya bari, ko kadan Abuturrab bai san abinda take cewa ba don yayi nisa yau kam, tuni ya dawo mata kamar wani xautattce shi ma yana rokonta, suka hadu suna ta rokon juna Lol, kokuwa ta shiga yi da shi ganin baya gane abinda take cewa, nan kuma ya nuna mata ba karfinsu daya ba, tana ji tana gani a daren nan Abuturrab ya raba ta da pride dinta, axaban da bata san da shi ba ta dinga ji a wannan lkcn, tayi rokon har ta gode Allah amma yaki sarara mata, ajiyar xuciya ta dinga saukewa daga karshe tana jin kamar numfashinta xae dauke, sai da ya ji sa dai dai sannan ya sarara mata, ya dade kwance gefenta idonsa lumshe yana sauke numfashi a hankali, har cikin ransa yake jin yanda take kuka a wahale muryarta bae fitowa, duk ya ji bae kyauta mata ba, ga wani nauyinta da yake ji, a hankali ta samu ta mike da kyar tana neman sauka daga kan gadon ya jawo ta xuwa jikinsa, cikin sanyin murya yace "Am sorry Fatima," ta fashe da kuka sosai har da shessheka, lumshe ido yayi ya [truncated by WhatsApp] 💖💝BATUUL💖💝 66 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* A firgice ta tashi daga baccin da ta kwanta dan bata san sanda tayishi ba, d'akin ta k'arewa kallo gaba d'aya, sai a sannan ta fara tariyo abunda ya faru jiya, ba karamin tsoro ne ya kamata ba, jikinta na rawa ta jawo wayarta da ta sa k'ark'ashin pillow taga 9 na safe, da sauri ta shiga dudduba kanta hankali a tashe, ajiyar zuciya ta sauk'e ganin bata ga alamar komai ba, d'akin ta sake examining taga jakanta a bude an barbaje kayan ciki, mik'ewa tayi ta isa inda jakar yake da sauri tana dubawa taga an yashe duka kud'in dake ciki, a guje ta fito daga d'akin, kalle kalle ta tsaya yi ganin d'akuna dayawa a Jere, a guje ta bankad'a d'aya ta shiga, gabantane ya fad'i ganin irin kwanciyar da yayartata tayi, Yaa zee itama na kwance lakad'an tana bacci abinta, duka ta d'aka mata a baya tace "Yaa Zee ki tashi dalla kin kwanta sai bacci kikeyi", da k'yar ta iya bud'e ido tana kallon Ajiddeh dake tsaye, kanta ta koma kallo, a firgice ta tashi tace "keh meye zaki zo kina min ihu?", wani irin kallo Ajiddeh ta dubeta dashi wani xufa na keto mata tace "dallah ki tashi kin kwanta bacci sai kace gawa, toh mutumin nan wllh Yahoo guy ne, in zaki farka ki farka kisan inda dare ya miki", a firgice ta sauk'o daga kan gadon, sai lokacin ta lura da kayanta dake zube a d'akin, a wulak'ance ta kalli Ajiddeh tace "toh kuma meye na hargitsa min kaya?", wani dogon tsaki Ajiddeh taja tace "dallah can bakiji mey nace miki bane?, wannan taqadarin da kuka kawo mu gunshi ba malami bane, macuci ne b'arawo", a rikice Yaa Zee ta shiga duba kayan nata dake zube, wani irin ihu ta kurma tana fad'in ta shiga uku, kafad'un Ajiddeh ta kamo tana ihu tace "Keh ya cuceni, mutumin nan ya cucemu, har golds d'ina da akwai cikin jakan nan ya kwashe, na shiga uku", tsaki Ajiddeh taja ta janye hannun Zee dake jikinta, a guje Zee ta juya ta bar d'akin, a bakin k'ofa suka ci karo dasu Mummy suma sun fito jin ihun da sukayi, Aunty Jainaba ce ta rik'ota tace "shinu?, bakal abuki, ki fad'amin ihun mey kikeyi?, babu abinda Zee ke yi in banda ihu sai cewa take "Ya anahe, mun shiga uku", Ajiddeh suka hango itama tana tahowa duk ta birkice, Mummy ce ta k'arasa gun Ajiddeh tace "keh shinu dige?", baki ta tab'e tace "Oho, wai malamin nan naku ne d'an 419, ya kwashe mana komai namu, ni dama tun farko ba yadda nayi dashi ba, tun farko ma wai wa ya hada ku da shi?", hannu Mummy ta d'aura aka sukayi ta kurma ihu, straight parlourn da aka fara kaisu sukaje, ko carpet d'inma da aka shimfid'a d'azun babu bare alamar mutum, wani sabon kukan suka sake sawa wannan karan harda Jainaba, dan takaici Ajiddeh kasa cewa komai tayi sai ido da ta zuba musu tana gumi, sunkai minti talatin suna abu d'aya, tsaki taja ta mik'e tana kallonsu daga karshe tace "in zaku tashi mu nemawa kanmu mafita ku tashi, don zaifi mana da wannan zaman kukan mara amfani da kukeyi", da rinannun idanuwansu suka d'ago suna kallonta sukace "toh ya zamuyi", a k'ufule tace "Ku zauna kuyita kuka", ta juya ta koma d'akin da aka sauketa, sauran kayan da ya bar mata ta kwasosu a akwatin ta fito janye da kayan, da ido suka bita su dukkansu har tazo ta wucesu, da hanzari suka miqe sukayi ciki suma suka tattaro nasu komatsan, kiciniyar bud'e gate d'in suka tarar da ita tanayi, juyowa tayi ta kallesu tace "D'an iskan ta waje ya rufemu, yanxu sai an samu wani ya haura ya bud'emu, Mummy duk keh kika janyo wannan abin da kika wani ce mishi har miliyan hamsin zamu bashi, ai ko yana da niyyan aikinma dole shed'an ya rud'eshi da tunanin muna da kud'i yayi mana sata (Lol, nikam nace ko ba shed'an ba), yanxu sai kusan yanda za ayi a bud'e mu fita daga nan", hawaye Mummy ta share tace "Wlhy Zainab da Janaiba ne suka samoshi, bansan a ina ba", shawara suka yanke da ayi hawa hawa sai mutum d'aya ya dira ta waje ya bud'esu, Mummy ce ta fara tsugunawa, Janaba ta haye kanta sai Zee, Ajiddeh ce ta samo ta dirqo, chain d'in aka rufe k'ofan da ta warware ta bud'e musu suka fito, ba a jin motsin kowa sai kukan tsuntsaye, a haka suka fito suka kama hanya, saida sukayi tafiya mai nisa duk sun galabaita har sun fara canza kamanni tukunna suka ga wata mota da aka kwaso bunsurai a ciki, tsaida mai motan sukayi sukace mishi ya kaisu cikin gari, cikin bunsuran nan suka kutsa suka zazauna duk wari, Ajiddeh dae kasa kuka ma tayi don takaici, sai da ya kaisu cikin gari sannan Mummy ta ciro kud'in can ta bashi dan bai wuce d'ari biyar ba, sai da suka nemi abinci sukaci daga nan suka fara tunanin yadda zasu koma gida, Ajiddeh ce tace "Mum nifa ban kuma kwana garin nan, kusan yadda zanyi In koma dan in Aliyu ya gano k'arya nayi mishi to kowa sai ranshi ya b'aci", Aunty Jainaba da tayi tagumi tace "yanzu abinda za ayi, ni akwai kudi guna tunda shi d'an iskan can bai shigo ya tsiyata mu ba, amma kud'in ba masu yawa bane, ba zaiyi sponsoring mu duka ba, sai dai in zaki fara tafiya ke sai ki turomana mu koma muma, kamin nan zamu zauna wajen Ayyi har ki turo sai a San abin yi, da haka suka yanke shawara suka rakata airport suka yankar mata ticket, Mummy ta share xufa tace "Toh ae ynxu sai mu koma gun mai mana aiki da, don dama ba wai bae iya aikin bane, aikinsa daukan lkci gare shi kafin ya ci," ko kallonta Ajiddeh bata yi ba, don abun duniya sun taru sun mata yawa, ga uban asaran kudin da tayi. Kuka Batuul ta dinga yi tana sauk'e ajiyar zuciya jikinsa, ya kasa cewa komae don har cikin ranshi yake jin kukan nata, dad'a rungumeta yayi sosae ya daura kanta a kirjinsa, a haka har ya samu tayi baccin amma har lokacin tana sauk'e ajiyar zuciya, shi kam sam ya kasa rintsawa gashi yana son yayi wanka amma ya kasa dauketa daga jikinsa, sai wajen k'arfe biyu ya samu bacci ya dauke sa shi ma, da asuba ya dad'e da tashi har lkcn tana jikinsa ya kasa kwantar da ita jin yanda jikinta ya dau xafi, kallonta yake yana kwantar mata da dogon gashinta da ya barbaje a hankali, kamar ya maidata ciki haka ya dinga ji, wani irin feeling yake ji a tattare dashi da ya kasa gane ko wane iri ne, a hankali ya lumshe ido yayi kissing lips d'inta ya kwantar da ita ya shiga toilet, da k'yar ta iya bud'e idanuwanta da suka kumbura sukayi ja jin ya shige toilet don tuni ita ma ta tashi sai dai bata nuna masa idonta biyu ba, tayi yunk'urin tashi taji wani azababben ciwo, bakinta ta toshe dan kar tayi k'ara ya jiyota, da k'yar ta samu ta miqe daga gadon tana d'ingishi ta fice daga d'akin, babu abinda takeyi sai hawaye, tana shiga d'akinta xani kawae ta iya daurawa ta fad'a kan gado ta fashe da kuka abin tausayi, sunan Aunty da Baba ta dinga k'ira, ita kadai tasan abinda take ji a lokacin, wani baccin wahala ne yayi gaba da ita, Abuturrab na fitowa daga toilet yaga bata dakin, murmushi yayi, yayi hanyan kofa zai fita yaji wayarshi na ringing, komawa yayi ya d'au wayan, da mamaki yake kallon screen d'in ganin mai kiranshi, yana d'auka yaji tace "Hello bae na dawo fah, yanxu na baro airport ina hanya, na ma kusa" girarshi d'aya ya d'age kamar tana wajen a daburce yace "ke hankalin ki d'aya kuwa? bakice min zaki dawo ba kika d'auko hanya kika taho" da mamaki tace "Haba babe, sai nace maka xan dawo, beside kwananmu nawa bamu had'u ba, ko d'okin ganina ma bakayi" ya sauke ajiyar xuciya a hankali yace "ohk then, Fine naji" da haka ya katse k'iran ya jefar da wayar kan gado, hannu yasa ya baje gashin kanshi ya lumshe ido, duk ya rasa abun yi, he is just confused, idonshine ya fad'a kan bedsheet d'in da yayi staining, d'an tsaki yaja ya yaye bedsheet d'in yayi toilet dashi ya jefa cikin washing machine, fitowa yayi ya canja wani, ya juya kenan zai koma toilet Ajiddeh ta turo kofan dakin ta shigo wani iska mai d'umi ya furzar daga bakinshi, a guje ta k'araso ta rungumeshi cike da farin ciki, murmushi ya kirkira yana kallonta kawae, tace "Babe jikin Mummy Alhmdllh, duk ita ce ta takura sae na dawo Wai ta ji sauki, taki bari na inje gidan 'yan uwa mu gaisa, kai babe kaga yanda nayi missing dinka kuwa" kallonta kawae yake sai dai gaba d'aya hankalinshi baya kanta, kallon gadon tayi tace "A'ah Baby kai ka canja bedsheet d'in?" kai kawai ya iya gyad'a mata da sauri, d'agowa tayi tana kallon fuskanshi tace "Baby toh mesa ka canja? Me ya same shi, ae sabo ne na shimfida" murmushi ya k'ak'aro yana kkrin controlling kansa kar ta gano sa yace "Yeah, yea coffee ne ya zube jiki, and I changed it just now" bata bari ya gama ta had'a bakinshi da nata, janye jikinshi yayi daga nata ya zaunar da ita kan gado yana murmushi yace "Am, am coming babe" toilet ya shige, yyi saurin tarawa bedsheet din cikin machine ruwa dan yasan halinta zata iya zuwa ta duba, da kanshi ya dirje sannan ya maida cikin washing machine din, fitowa yayi ya sameta zaune inda ya barta, kissing d'inshi ta shiga yi passionately, amma gaba d'aya hankalinshi na gun Batuul, so yake yaga halin da take ciki, da k'yar ya samu ya lallab'ata har tayi bacci wajen k'arfe takwas, tana fara bacci ya sauk'e ajiyar zuciya ya janye jikinsa daga nata ya dauki makullin mota ya fice daga d'akin, kai tsaye d'akin Batuul ya nufa, tana kwance kan gadon har lkcn bacci take, amma kana gani kasan a wahalce take, wani tausayinta ne yaji ya ratsa shi, dab bakin gadon ya tsaya ya d'auketa cak, kara ta saki a tsorace, yyi saurin rungumota jikinsa, har cikin ranshi ya dinga jinta" k'asa ya sauk'o da ita ya bud'e mota ya sakata ciki snn shima ya zagaya ya shiga ya tada motar suka bar compound din, hade kai tayi da gwiwa tana rera kuka a hankali, duk ya ma rasa me xai ce mata har suka isa daya gidansa, yana gama parking ya bude motar ya fito ya xagaya ta inda take ya bude, daukarta yayi kamar daxu suka shiga cikin gidan, bai direta a ko ina ba sai kan gado, ya xauna kusa da ita ya rungumota cikin sanyin murya yace "I said am sorry, kiyi hakuri plss" kuka take har da shessheka, a hankali yace "Its painful ko? forgive me plss" bata ce komai ba, ya lumshe ido yana shafa bayanta a hankali, kwantar da ita yayi jin tayi shiru sai ajiyar xuciya da take saukewa ya mike ya shiga toilet, very warm water ya hada a bathtub ya fito ya dauketa, sai da suka shiga toilet din ya fara cire mata xanin jikinta, ta rike da sauri hawaye na xubo mata tace "A'a ka bar ni xan yi da kai na" yace "But you are in pain ki bari in taimaka maki" ta fashe da kuka tace "No plss" bai kara bi ta kanta ba ya cire xanin ya saka ta cikin ruwan dumin, ihu ta kwala jin wani sabon axaban, ta dinga kiran Anty tana yarfe hannu idonta rufe don baxata iya kallonsa ba, sosai yaji tausayinta, yasan bai kyauta mata ba, tunda ba haka yayi ma Ajiddeh ba, ko da yake ita wannan bbu gardama ta bashi kanta kamar jira take, sau uku yana canxa ruwan sannan ya taimaka mata tayi wankan tsarki, tayi wanka ta wanke baki, ta dauro alwala ya dauketa suka fito, rufeta da bargo yayi ganin yanda take rawan sanyi, ya sauka downstairs don hado mata tea, da kyar ya lallabata ta sha tea ta koma ta kwanta, makullin mota ya dauka ya fita xuwa phamarcy don siyo mata pain reliever jin yanda jikinta yayi xafi sosai, ko kan ya dawo har tayi bacci, ajiye ledan drugs din yayi ya xauna gefenta yana kallonta, sai lokacin ya tuna ashe fa bai yi sallah ba, mikewa yayi da sauri ya nufi bayi ya dauro alwala ya fito ya shimfida darduma yayi sllhn. Yana xaune kan darduma har lkcn wayarsa ya fara ringing, ya mike ya dauka yaga Ajiddeh ce, d'agawa yayi daga daya bangaren tace "Babe ina ka tafi haka har yanxu?" A takaice yace "Aiki, I saw yhu were sleeping shiyasa ban tashe ki ba kawae na wuce" a d'an shagwabe tace "Toh come back early plss," yace "Ayt!" Tace "Babe ban ga yarinyar nan ba fa tun da na dawo" ya lumshe ido yace "Yea bata nan, tana gidansu wata kawarta wai, tun da kika tafi" Ajiddeh ta tabe baki a xuciyarta tace Allah sa ma tai ta tsayawa gidan kawar tata, a fili kuwa ca tayi "Eyya, ashe tasan mutane a nan" kallon Batuul dake motsi yayi, da sauri yace "look babe, We'll tok later, am busy yanxu" daga haka ya katse wayar ya nufi Batuul da sauri. 💖💝BATUUL💖💝 67 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* A firgice ta tashi daga baccin da ta kwanta dan bata san sanda tayishi ba, d'akin ta k'arewa kallo gaba d'aya, sai a sannan ta fara tariyo abunda ya faru jiya, ba karamin tsoro ne ya kamata ba, jikinta na rawa ta jawo wayarta da ta sa k'ark'ashin pillow taga 9 na safe, da sauri ta shiga dudduba kanta hankali a tashe, ajiyar zuciya ta sauk'e ganin bata ga alamar komai ba, d'akin ta sake examining taga jakanta a bude an barbaje kayan ciki, mik'ewa tayi ta isa inda jakar yake da sauri tana dubawa taga an yashe duka kud'in dake ciki, a guje ta fito daga d'akin, kalle kalle ta tsaya yi ganin d'akuna dayawa a Jere, a guje ta bankad'a d'aya ta shiga, gabantane ya fad'i ganin irin kwanciyar da yayartata tayi, Yaa zee itama na kwance lakad'an tana bacci abinta, duka ta d'aka mata a baya tace "Yaa Zee ki tashi dalla kin kwanta sai bacci kikeyi", da k'yar ta iya bud'e ido tana kallon Ajiddeh dake tsaye, kanta ta koma kallo, a firgice ta tashi tace "keh meye zaki zo kina min ihu?", wani irin kallo Ajiddeh ta dubeta dashi wani xufa na keto mata tace "dallah ki tashi kin kwanta bacci sai kace gawa, toh mutumin nan wllh Yahoo guy ne, in zaki farka ki farka kisan inda dare ya miki", a firgice ta sauk'o daga kan gadon, sai lokacin ta lura da kayanta dake zube a d'akin, a wulak'ance ta kalli Ajiddeh tace "toh kuma meye na hargitsa min kaya?", wani dogon tsaki Ajiddeh taja tace "dallah can bakiji mey nace miki bane?, wannan taqadarin da kuka kawo mu gunshi ba malami bane, macuci ne b'arawo", a rikice Yaa Zee ta shiga duba kayan nata dake zube, wani irin ihu ta kurma tana fad'in ta shiga uku, kafad'un Ajiddeh ta kamo tana ihu tace "Keh ya cuceni, mutumin nan ya cucemu, har golds d'ina da akwai cikin jakan nan ya kwashe, na shiga uku", tsaki Ajiddeh taja ta janye hannun Zee dake jikinta, a guje Zee ta juya ta bar d'akin, a bakin k'ofa suka ci karo dasu Mummy suma sun fito jin ihun da sukayi, Aunty Jainaba ce ta rik'ota tace "shinu?, bakal abuki, ki fad'amin ihun mey kikeyi?, babu abinda Zee ke yi in banda ihu sai cewa take "Ya anahe, mun shiga uku", Ajiddeh suka hango itama tana tahowa duk ta birkice, Mummy ce ta k'arasa gun Ajiddeh tace "keh shinu dige?", baki ta tab'e tace "Oho, wai malamin nan naku ne d'an 419, ya kwashe mana komai namu, ni dama tun farko ba yadda nayi dashi ba, tun farko ma wai wa ya hada ku da shi?", hannu Mummy ta d'aura aka sukayi ta kurma ihu, straight parlourn da aka fara kaisu sukaje, ko carpet d'inma da aka shimfid'a d'azun babu bare alamar mutum, wani sabon kukan suka sake sawa wannan karan harda Jainaba, dan takaici Ajiddeh kasa cewa komai tayi sai ido da ta zuba musu tana gumi, sunkai minti talatin suna abu d'aya, tsaki taja ta mik'e tana kallonsu daga karshe tace "in zaku tashi mu nemawa kanmu mafita ku tashi, don zaifi mana da wannan zaman kukan mara amfani da kukeyi", da rinannun idanuwansu suka d'ago suna kallonta sukace "toh ya zamuyi", a k'ufule tace "Ku zauna kuyita kuka", ta juya ta koma d'akin da aka sauketa, sauran kayan da ya bar mata ta kwasosu a akwatin ta fito janye da kayan, da ido suka bita su dukkansu har tazo ta wucesu, da hanzari suka miqe sukayi ciki suma suka tattaro nasu komatsan, kiciniyar bud'e gate d'in suka tarar da ita tanayi, juyowa tayi ta kallesu tace "D'an iskan ta waje ya rufemu, yanxu sai an samu wani ya haura ya bud'emu, Mummy duk keh kika janyo wannan abin da kika wani ce mishi har miliyan hamsin zamu bashi, ai ko yana da niyyan aikinma dole shed'an ya rud'eshi da tunanin muna da kud'i yayi mana sata (Lol, nikam nace ko ba shed'an ba), yanxu sai kusan yanda za ayi a bud'e mu fita daga nan", hawaye Mummy ta share tace "Wlhy Zainab da Janaiba ne suka samoshi, bansan a ina ba", shawara suka yanke da ayi hawa hawa sai mutum d'aya ya dira ta waje ya bud'esu, Mummy ce ta fara tsugunawa, Janaba ta haye kanta sai Zee, Ajiddeh ce ta samo ta dirqo, chain d'in aka rufe k'ofan da ta warware ta bud'e musu suka fito, ba a jin motsin kowa sai kukan tsuntsaye, a haka suka fito suka kama hanya, saida sukayi tafiya mai nisa duk sun galabaita har sun fara canza kamanni tukunna suka ga wata mota da aka kwaso bunsurai a ciki, tsaida mai motan sukayi sukace mishi ya kaisu cikin gari, cikin bunsuran nan suka kutsa suka zazauna duk wari, Ajiddeh dae kasa kuka ma tayi don takaici, sai da ya kaisu cikin gari sannan Mummy ta ciro kud'in can ta bashi dan bai wuce d'ari biyar ba, sai da suka nemi abinci sukaci daga nan suka fara tunanin yadda zasu koma gida, Ajiddeh ce tace "Mum nifa ban kuma kwana garin nan, kusan yadda zanyi In koma dan in Aliyu ya gano k'arya nayi mishi to kowa sai ranshi ya b'aci", Aunty Jainaba da tayi tagumi tace "yanzu abinda za ayi, ni akwai kudi guna tunda shi d'an iskan can bai shigo ya tsiyata mu ba, amma kud'in ba masu yawa bane, ba zaiyi sponsoring mu duka ba, sai dai in zaki fara tafiya ke sai ki turomana mu koma muma, kamin nan zamu zauna wajen Ayyi har ki turo sai a San abin yi, da haka suka yanke shawara suka rakata airport suka yankar mata ticket, Mummy ta share xufa tace "Toh ae ynxu sai mu koma gun mai mana aiki da, don dama ba wai bae iya aikin bane, aikinsa daukan lkci gare shi kafin ya ci," ko kallonta Ajiddeh bata yi ba, don abun duniya sun taru sun mata yawa, ga uban asaran kudin da tayi. Kuka Batuul ta dinga yi tana sauk'e ajiyar zuciya jikinsa, ya kasa cewa komae don har cikin ranshi yake jin kukan nata, dad'a rungumeta yayi sosae ya daura kanta a kirjinsa, a haka har ya samu tayi baccin amma har lokacin tana sauk'e ajiyar zuciya, shi kam sam ya kasa rintsawa gashi yana son yayi wanka amma ya kasa dauketa daga jikinsa, sai wajen k'arfe biyu ya samu bacci ya dauke sa shi ma, da asuba ya dad'e da tashi har lkcn tana jikinsa ya kasa kwantar da ita jin yanda jikinta ya dau xafi, kallonta yake yana kwantar mata da dogon gashinta da ya barbaje a hankali, kamar ya maidata ciki haka ya dinga ji, wani irin feeling yake ji a tattare dashi da ya kasa gane ko wane iri ne, a hankali ya lumshe ido yayi kissing lips d'inta ya kwantar da ita ya shiga toilet, da k'yar ta iya bud'e idanuwanta da suka kumbura sukayi ja jin ya shige toilet don tuni ita ma ta tashi sai dai bata nuna masa idonta biyu ba, tayi yunk'urin tashi taji wani azababben ciwo, bakinta ta toshe dan kar tayi k'ara ya jiyota, da k'yar ta samu ta miqe daga gadon tana d'ingishi ta fice daga d'akin, babu abinda takeyi sai hawaye, tana shiga d'akinta xani kawae ta iya daurawa ta fad'a kan gado ta fashe da kuka abin tausayi, sunan Aunty da Baba ta dinga k'ira, ita kadai tasan abinda take ji a lokacin, wani baccin wahala ne yayi gaba da ita, Abuturrab na fitowa daga toilet yaga bata dakin, murmushi yayi, yayi hanyan kofa zai fita yaji wayarshi na ringing, komawa yayi ya d'au wayan, da mamaki yake kallon screen d'in ganin mai kiranshi, yana d'auka yaji tace "Hello bae na dawo fah, yanxu na baro airport ina hanya, na ma kusa" girarshi d'aya ya d'age kamar tana wajen a daburce yace "ke hankalin ki d'aya kuwa? bakice min zaki dawo ba kika d'auko hanya kika taho" da mamaki tace "Haba babe, sai nace maka xan dawo, beside kwananmu nawa bamu had'u ba, ko d'okin ganina ma bakayi" ya sauke ajiyar xuciya a hankali yace "ohk then, Fine naji" da haka ya katse k'iran ya jefar da wayar kan gado, hannu yasa ya baje gashin kanshi ya lumshe ido, duk ya rasa abun yi, he is just confused, idonshine ya fad'a kan bedsheet d'in da yayi staining, d'an tsaki yaja ya yaye bedsheet d'in yayi toilet dashi ya jefa cikin washing machine, fitowa yayi ya canja wani, ya juya kenan zai koma toilet Ajiddeh ta turo kofan dakin ta shigo wani iska mai d'umi ya furzar daga bakinshi, a guje ta k'araso ta rungumeshi cike da farin ciki, murmushi ya kirkira yana kallonta kawae, tace "Babe jikin Mummy Alhmdllh, duk ita ce ta takura sae na dawo Wai ta ji sauki, taki bari na inje gidan 'yan uwa mu gaisa, kai babe kaga yanda nayi missing dinka kuwa" kallonta kawae yake sai dai gaba d'aya hankalinshi baya kanta, kallon gadon tayi tace "A'ah Baby kai ka canja bedsheet d'in?" kai kawai ya iya gyad'a mata da sauri, d'agowa tayi tana kallon fuskanshi tace "Baby toh mesa ka canja? Me ya same shi, ae sabo ne na shimfida" murmushi ya k'ak'aro yana kkrin controlling kansa kar ta gano sa yace "Yeah, yea coffee ne ya zube jiki, and I changed it just now" bata bari ya gama ta had'a bakinshi da nata, janye jikinshi yayi daga nata ya zaunar da ita kan gado yana murmushi yace "Am, am coming babe" toilet ya shige, yyi saurin tarawa bedsheet din cikin machine ruwa dan yasan halinta zata iya zuwa ta duba, da kanshi ya dirje sannan ya maida cikin washing machine din, fitowa yayi ya sameta zaune inda ya barta, kissing d'inshi ta shiga yi passionately, amma gaba d'aya hankalinshi na gun Batuul, so yake yaga halin da take ciki, da k'yar ya samu ya lallab'ata har tayi bacci wajen k'arfe takwas, tana fara bacci ya sauk'e ajiyar zuciya ya janye jikinsa daga nata ya dauki makullin mota ya fice daga d'akin, kai tsaye d'akin Batuul ya nufa, tana kwance kan gadon har lkcn bacci take, amma kana gani kasan a wahalce take, wani tausayinta ne yaji ya ratsa shi, dab bakin gadon ya tsaya ya d'auketa cak, kara ta saki a tsorace, yyi saurin rungumota jikinsa, har cikin ranshi ya dinga jinta" k'asa ya sauk'o da ita ya bud'e mota ya sakata ciki snn shima ya zagaya ya shiga ya tada motar suka bar compound din, hade kai tayi da gwiwa tana rera kuka a hankali, duk ya ma rasa me xai ce mata har suka isa daya gidansa, yana gama parking ya bude motar ya fito ya xagaya ta inda take ya bude, daukarta yayi kamar daxu suka shiga cikin gidan, bai direta a ko ina ba sai kan gado, ya xauna kusa da ita ya rungumota cikin sanyin murya yace "I said am sorry, kiyi hakuri plss" kuka take har da shessheka, a hankali yace "Its painful ko? forgive me plss" bata ce komai ba, ya lumshe ido yana shafa bayanta a hankali, kwantar da ita yayi jin tayi shiru sai ajiyar xuciya da take saukewa ya mike ya shiga toilet, very warm water ya hada a bathtub ya fito ya dauketa, sai da suka shiga toilet din ya fara cire mata xanin jikinta, ta rike da sauri hawaye na xubo mata tace "A'a ka bar ni xan yi da kai na" yace "But you are in pain ki bari in taimaka maki" ta fashe da kuka tace "No plss" bai kara bi ta kanta ba ya cire xanin ya saka ta cikin ruwan dumin, ihu ta kwala jin wani sabon axaban, ta dinga kiran Anty tana yarfe hannu idonta rufe don baxata iya kallonsa ba, sosai yaji tausayinta, yasan bai kyauta mata ba, tunda ba haka yayi ma Ajiddeh ba, ko da yake ita wannan bbu gardama ta bashi kanta kamar jira take, sau uku yana canxa ruwan sannan ya taimaka mata tayi wankan tsarki, tayi wanka ta wanke baki, ta dauro alwala ya dauketa suka fito, rufeta da bargo yayi ganin yanda take rawan sanyi, ya sauka downstairs don hado mata tea, da kyar ya lallabata ta sha tea ta koma ta kwanta, makullin mota ya dauka ya fita xuwa phamarcy don siyo mata pain reliever jin yanda jikinta yayi xafi sosai, ko kan ya dawo har tayi bacci, ajiye ledan drugs din yayi ya xauna gefenta yana kallonta, sai lokacin ya tuna ashe fa bai yi sallah ba, mikewa yayi da sauri ya nufi bayi ya dauro alwala ya fito ya shimfida darduma yayi sllhn. Yana xaune kan darduma har lkcn wayarsa ya fara ringing, ya mike ya dauka yaga Ajiddeh ce, d'agawa yayi daga daya bangaren tace "Babe ina ka tafi haka har yanxu?" A takaice yace "Aiki, I saw yhu were sleeping shiyasa ban tashe ki ba kawae na wuce" a d'an shagwabe tace "Toh come back early plss," yace "Ayt!" Tace "Babe ban ga yarinyar nan ba fa tun da na dawo" ya lumshe ido yace "Yea bata nan, tana gidansu wata kawarta wai, tun da kika tafi" Ajiddeh ta tabe baki a xuciyarta tace Allah sa ma tai ta tsayawa gidan kawar tata, a fili kuwa ca tayi "Eyya, ashe tasan mutane a nan" kallon Batuul dake motsi yayi, da sauri yace "look babe, We'll tok later, am busy yanxu" daga haka ya katse wayar ya nufi Batuul da sauri. 💖💝BATUUL💖💝 68 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Lumshe ido yayi bayan ta fita daga d'akin, tunani kawai yakeyi na yadda zai sanar da Ajiddeh Batuul matarsa ce, sai yanzu yake ganin rashin kyautuwar fad'a mata da bai yi ba tun farko, yasan da ya fad'a tun lokacin da duk wani rikici ya kau by now, amma gaba d'aya kanshi a k'ulle yake as of then, yana ce komai zaizo da sauk'i amma yadda yake jin Batuul a ranshi, bazai iya yin nisa da ita ba, not for a second, d'an siririn tsaki yaja ya mik'e ya koma gaban desktop d'inshi yana duba ayyukan da baiyi ba yau a office, kamar wanda aka tsikara ya mik'e ya fita daga d'akin ya shiga d'akin Batuul, har ta canja doguwar rigar dake jikinta ta saka wani d'an bingel d'in gown pink ta baje gashinta kan pillow dan yasha iska, tana kwance ta d'aura Laptop d'inta saman cikinta tana danne danne, wani irin ajiyar zuciya ya sauk'e ganin she is fine, a hankali ta juyo da kanta ganin shine ta maida kallonta ga abinda takeyi, tura k'ofan d'akin yayi ya shigo ya maida ya rufe, daga bakin gadon ya zauna yana kallonta, ya kai wajen 3mins amma ko sau d'aya bata juyo ta kalleshi ba, hannu yasa ya d'auke laptop d'in, sai a lokacin ta d'aga ido ta kalleshi, idanunsu na locking cikin na juna tayi maza ta sadda kanta k'asa ta juya mishi baya, hannu yasa cak ya d'agota yana kallonta yace "are you okay?", kai ta gyad'a mishi ta sulale zata koma ta kwanta ya rik'ota yace "then why are you like this, aman ne har yanzu?", har lokacin batace mishi komai ba sai gyad'a mishi kai da tayi, hannu yasa ya d'ago hab'arta yace "talk to me and stop nodding, wani abun ke damunki?", ganin idonta ya fara ciccikowa yasa yace "stop that, don't you dare drop a tear, tell me mey ke damunki", kamar cewa yayi ta fara kuka ta fashe mishi da wani matsanancin kuka, har cikin ranshi yakejin kukan nata, rintse ido yayi ya janyota jikinshi ya rungumeta, patting bayanta ya shiga yi har saida ya samu tayi shiru, sai ajiyar zuciya take sauk'ewa, a hankali ya d'agota yasa hannu ya share mata d'an guntun hawayen dake fuskanta ya had'e rai yace "Look at me", bata d'ago ba sai da ya sake maimaitawa jin yayi maganar in a serious tone ya sata d'agowa tana ajiyar zuciya yace "Fatima kinada hankali kuwa, keh abin kuka baya miki kad'an, ko don kinga ina k'yaleki kullum sai kinyi kuka, gari baya wayewa ya wuce bakiyi kuka ba, tell me what your exact problem is", ajiyar zuciya ta sauk'e ta zumb'uro mishi baki tace "ni ai ba kullum nakeyi ba sai in kaine ka.....", tsareta yayi da ido yace "ehhn, sai in nine nayi mey?", sadda kanta tayi k'asa tace "You always talk abt your wife, kullum sai kace min your wife your wife, I know she is your wife, but ai ba sai ka dinga tunamin ba", baisan lokacin da dariya ya k'wace mishi ba, dariya ya dinga har sai da abin ya bata haushi, haushin kanta ma taji da ta fad'a mishi hakan, takaicin dariyan da yake yasa taja bargo tayi kwanciyarta, sai da yayi mai isarshi sannan ya d'agota har lokacin yana murmushi, kwace jikinta ta shiga yi zata kwanta amma yaqi saketa, fuskarta ya kamo da duka hannayenshi yana kallon idonta da duk ya cicciko yace "Toh ni yau duk yaushe na ambaci my wife", baki ta zumb'uro mishi tace "ko d'azu ma ba ka....", sai kuma tayi shiru, saketa yayi sannan yace "indai wannan ke saki kuka baza ki sake ji ba, you won't hear that from me okay?, ya hade rai ya ci gaba "but promise me kema baki sake yin kukan, kinga Farida will b coming so banso tazo taga kina wannan koke koken tayi tunanin wani abun ake maki", kamar wata y'ar yarinya ta gyad'a mishi Kai, ajiyar zuciya ya sauk'e ganin yayi convincing d'inta kan kukan nata, yanzu saura Farida, itama sai yayiwa tufkar hanci tun wuri, hannunta ya kamo yace "inason shan kunu, can you make some now?", kai ta gyad'a mishi yayi d'an murmurshi yace "Thank you", tsuke baki tayi zata tashi daga kan gadon yayi saurin janyota yace "Did you just pout?", da sauri ta kad'a mishi kai tace "baka ganiba, ni ba pouting nayi ba", murmushi yayi ya janyota jikinshi sosai ya d'anyi brushing lips d'inshi kan nata yayi mata light kiss, lips d'inta na d'aya daga cikin abinda bazai Iya resisting ba akan Batuul, suke tempting d'inshi yayi abubuwan da ma bai shirya yinsu ba, mik'ewa yayi itama ya mik'ar da ita, kallonta yayi yace "muje?", a hankali tace mishi "Ehh", Hijab d'inta ta d'auka zata saka ya riqe yace "Do you really need to put on this?", kai ta gyad'a mishi kawai taci gaba da saka Hijabinta, ita tayi gaba ya biyota a baya, turus ta tsaya bakin k'ofa ganin mutanen da suka hauro wa sama, kallon mamaki suka tsaya yi mata, wani irin bugawa Ajiddeh taji k'irjinta nayi ganin ya fito daga d'akin Batuul, tun bayan dawowanta bata tab'a tunanin har lokacin yana shiga d'akin ba, baki ta bud'e zatayi magana Jainaba tayi saurin rik'o mata hannu, murmushi ta k'irk'iro tace "Aliyu ashe ana ganinku a gari", shima d'in murmushi yayi yace "ai sai in ba a nemi ganinmu ba Aunty, Ya hanya?" Ya tambaya yana k'arasa fitowa daga d'akin, murmushin nan dai taci gaba dayi tace "Alhamdulillah, hanya mun baroshi, mun sameku lafiya?", kai ya gyad'a yace "Alhamdulillah, ya jikin Mummy, kwanaki bata ji dad'i ba, I wanted going with her", ya nuna Ajiddeh da zuciyarta ke tafasa "but abubuwa held me hear", dariya tasa tace "Ai ba komai ma, ai zuwan Ajiddeh ma yayi,taji sauk'i yanzu sai dai Allah ya kiyaye gaba", "Amin" yace sannan ya juya yana kallon Batuul da ta tsaya daga bayanshi kamar wata munafika yace "baki iya gaisuwa bane kika tsaya kallon mutane?", ido ta d'aga ta kalleshi sannan ta kalli Aunty Jainaba da ta bita da wani shu'umin kallo tana jira ta gaida ta, juyawa tayi ta shige d'aki ta banko musu k'ofa, gaba d'ayansu freezing sukayi ganin abinda Batuul d'in tayi, tsabar mamaki kasa magana Abu yayi, Ajiddeh ce a fusace tayi k'ofar d'akin zata bankad'a Jainaba ta rik'ota, "shegiya karamar matsiyaciya har kin isa ki wulak'anta min y'an uwa, toh koma uban wa ya d'aure miki gindi, ko kuma aka zugoki kizo ki min iskanci ko, toh dama hak'uri nakeyi nake k'yaleki, yau sai kin bar min gida y'ar abu kazan uba", Aunty Jainaba ce ta janyota da k'arfi ta d'an kanne mata ido sannan tace "Haba Ajiddeh, bakya ganin yarinya ce, kema ai kinsan hankali ba isanta yayi ba, yarinta ne ke damunta", wani irin kallo ta jefawa Aliyu da ya kasa cewa komai sai kallonsu yakeyi, a masifance tace "ai dama nasan kai ke d'aure mata tana min abinda taga dama, gashi ka janyo min raini da bai tsaya iya kaina ba, har kan y'an uwana ya koma, toh Allah zamanta ya k'are gidan nan ko kuma ni in bar muku gidan sai kuyi xaman auren da ita", Aunty Jainaba ce ta d'anyi magana a tsawace tace "keh wai wace irin yarinyace Jiddah, haka ake yiwa miji magana dama, wuce mu shige tunda bakida hankali wawiya kawae", taja ta sukayi gaba, wani irin iska mai d'umi ya furzar daga bakinshi yasa yatsunshi cikin gashin kanshi ya bajesu, juyawa yayi ya bud'e d'akin Batuul tana tsaye tana waya da alama da Farida suke wayan, a hankali ta juyo ta dubeshi, sai da y'an hanjin cikinta suka kad'a ganin irin kallon da yake tunkarota dashi, dakewa tayi da k'yar ta bud'e baki tace "Hey hold on, I will call you ltr", bata cire wayan a kunnenta ba taji ya fizge ya jefar kan gado tareda fizgota gabanshi, yana mata wani irin kallo yace "What's d meaning of what you just did, kinada hankali ma kuwa?", babu abinda k'irjinta keyi sai heaving kamar zai fito amma ta dake tace "ni kuma mey nayi?", fizgota ya sakeyi jikinshi yana mata wani irin kallo yace "you are asking, i will slap you yanzun nan in baki min magana ba, meye dalilinki na tafiya ba tareda kin gaidata ba, are you stupid?", k'wace kanta daga rik'on da yayi mata tayi zata matsa daga gabanshi ya kuma fizgota a tsawace yace "kehh! na fara wasa da ke koh, I will right away slap you, bakida hankali ne", hannunshi tacire daga rik'on da yayi mata tace "wai ni mey nayi ne na rashin hankali, dan ban gaishesu ba?, dole ne sai na gaishesu? Naga ai dama ba dole bane gaida kishiya, ita yaushe ta tab'a gaidani? Let me be plss", ta k'arashe maganan tana rolling eyes d'inta cike da masifa, kafeta da ido yayi cike da mamaki, baisan lokacin da gasp yayi escaping lips d'inshi ba jin abinda take ce masa, ci gaba tayi da cewa "kuma ni daga yau na dena gaisheta tunda itama bata gaishenin take ba", daga haka ta juya fuu zata tafi ya fizgota, kankamesa tayi jikinta na rawa tana kiran Anty, murmushi ne ya subce masa jin yadda k'irjinta ke heaving, kana ganinta kasan a tsorace take, yace "Huh kishiya?, waye kishiyar taki, ko kuma kinji nayi declaring d'inki matata ne da har kike fad'in baki gaida kishiyarki?", hawaye ya cika idonta tace "Ai ko bakayi declaring d'ina ba nidai bazan sake gaishesu ba, period", jefata kan gado yayi yace "Fine, duk ranan da ta koreki daga gidanta sai kisan inda kika nufa", da haka ya fita ya barta a d'akin, mikewa tayi a fusace ta sa key a kofarta, k'ofar d'akinshi ya tura ya shiga, nan ya tarar da Ajiddeh da Aunty nata zaune tana mata magana can kasa, d'an tsaki yaja ya koma da baya dan baisan ranar hankalin Ajiddeh ba, duk d'akunan dake gidan nan ta rasa wanda zata shigo da bak'i sai nashi, key d'in mota kawai ya d'auka ya fice daga gidan, bai dawo sai bayan Sallah Isha, direct d'akinshi ya wuce amma har lokacin suna ciki, sai ma dad'a littering d'in d'akin da sukayi da kayayyakinsu, ganin shi ne yasa Aunty Jainaba jin kunya tace "Laah Aliyu ashe har ka dawo, gashi mun b'ata maka d'aki", Ajiddeh kam ko kallonshi batayi ba, Murmushi yayi wa Aunty Jainaba yace "Nah its okay, ba komai, I will use another room", da haka ya fice ya jawo musu k'ofa, d'akin Batuul ya koma ya murda kofar yaji a rufe, komawa yayi ya dauko spare key sannan ya dawo ya bude ya tura kofan a hankali, as usual yana k'anshin da ya saba, kayanta ya tarar da ita tana gyarawa, kallo d'aya ta mishi ta d'auke kanta taci gaba da abinda takeyi fuskarta daure, k'arsawa yayi ciki ya kamo hannunta ya jata, tirjewa tayi a waje d'aya tana kallonshi tace "Lafiya, ko ka mance hanyar dakin matar taka ne?", ita kanta mamakin sabon halin nan nata takeyi, shi ma haka ya tsaya kallonta cike da mamaki, ta juya ta ci gaba da abinda take yi, ganin zata b'ata mishi lokaci yasa ya d'agata cak "baki ta bud'e zata sa mishi ihu ya sa yatsa ya bige mata d'an baki yace "shout and I will drop you down d stairs, dare me ki ga", gaba d'aya kanta ne taji yana juyawa kamar d'azu ga tashin zuciya, wani k'arfi ne yazo mata ta sauk'a daga hannunshi tace "zan tafi da kaina, ba sai ka d'auke ni ba", ta fad'a tana murgud'a mishi baki, shi mamakin sabon halin nan nata kawai yakeyi har ta fito daga cikin d'akin shima ya biyota rik'eda hijab d'inta, ganin Hijab a hannunshi yasa ta ce mishi "wai ina zamu?", baice mata koma ya rik'ota ya sa mata Hijab d'in ya jata sukayi waje, mota ya bude ya saka ta ciki sannan ya xaga shi ma ya shiga ya tada motar suka bar compound din, eatry ya nufa da ita ya siyo masu abinci suka dawo gida, yana gama parking ta fice daga motar ya bi ta da kallo yana murmushi, fitowa yayi shi ma ya kwashi ledojin abincin ya rufe motar ya bi bayanta, dakinta ta shige ta fada kan gado jin yanda xuciyarta ke tashi, ya hauro sama shi ma, yayi knocking dakinsa da su Ajiddeh suke, Ajiddeh ta leko fuskarta daure ya mika mata leda daya, wani matsiyacin kallo tayi masa tace "Ae nayi xaton da yunwa xaka bar 'yar uwar tawa" daga haka ta maida kofa ta rufe ta bar sa nan tsaye, girgixa kai yayi cike da takaici ya juya ya nufi dakin Batuul, ajiye ledan hannunsa yayi ya karasa kusa da gado ganinta kwance ya xauna daga gefenta yana kallonta yace "Tashi ki ci abinci" ba tare da ta kallesa ba tace "Am OK ka kai ma matar ka" dariya ta basa ba kadan ba yace "Uhnn! Ae sai da na fara kai mata kafin in kawo maki" tace "Nawan ma ka hada mata ta cinye" dariya yayi ya dago ta yace "Ashe kema haka kika iya masifa, wannan ba halin Anty bane" kwace kanta tayi tace "Ni ka kyaleni" yace "Sakko ki ci abinci toh" tace "Ban ci" sakko da ita yayi kasa ya jawo ledan yace "Look am not joking fah" bude kofa aka yi daga waje, yyi saurin mikewa yana kallonta yace "Kafin in dawo ki tabbata kin cinye" daga haka ya juya ya nufi kofa ya fita, mikewa tayi da kyar ta koma ta kwanta don duk ta rasa me ke mata dadi ga tashin xuciyar da yasa ta gaba, tana kwanciya bacci ya dauketa. Shi kam Abuturrab duk ya kagu Ajiddeh ta koma gun 'yar uwarta ya je yaga ko Batuul ta ci abincin don xuwa tayi ta sa shi gaba a palo, har sha biyu bai ga alaman xata tafi ba yace "Kin bar Anty ita kadae" tace "Ehh ita tace in tafi gun mijina bacci xata yi" bai kuma ce mata komai ba, har dai ya mike daga karshe yace "Am going to bed yanxu" ta mike tana mitsika ido, ya kashe kayan kallon parlour'n da wuta ya nufi sama ya bar ta, ta bi bayansa, kwanciyarsa yayi a bedroom ya juya mata baya ta shige jikinsa, ko ta kanta bae bi ba ya lumshe ido kamar me bacci, yana jin alaman tayi bacci ya xame jikinsa daga nata ya mike daga gadon ya fita daga dakin, dakin Batuul ya shiga, ya karasa yana kallonta, kwata kwata bai ji dadin rashin cin abincin da bata yi ba, ya xauna gefenta ya cire duvet din da ta lulluba da a hankali, ya ji jikinta da d'an xafi, ya jima yana kallonta sannan ya lumshe ido yayi pecking lips dinta ya mayar mata duvet din jikinta ya mike ya dauke ledan abinci yasa a fridge ya fita daga dakin ya koma nasa. 💖💝BATUUL💖💝 69 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Washe gari da safe kamar yadda ta saba tashi haka ta tashi, sai da tayi Sallah tukunna tayi wanka ta gyara d'aki, ta koma toilet ta wanke sannan ta fito tayi kwanciyarta kan gado saboda jirin da take ji, jin jikinta ya d'anyi dama dama yasa ta mike ta fita daga dakin ta sauk'o k'asa yin breakfast kamar yadda ta saba, a gurguje ta shiga gyaran parlour dan bata son yin latti, lecture 11 ne da ita, gashi jiya ma bata samu taje ba, kitchen ta shiga ta harhad'a kayan abincin da zata dafa grilled fish da salad ta shiga had'awa, tana jin saukowan sa parlor da Ajiddeh ta tabe baki ta ci gaba da aikinta, kunun gyad'a ta dama sannan ta shiga baking musu chicken pie, Oven d'in da kifin ke ciki ta bud'e zata duba ko yayi, tiririn dake fitowa ciki yasa taji kanta ya fara juyawa ga tashin da zuciyarta ya fara, ba shiri ta yadda hand napkin dake hannunta jin amai na yunk'urin zuwa mata ta fito daga kitchen din da sauri, yana kwance a parlour ya lumshe ido, Ajiddeh na kwance jikinshi duk ta wani kanainayeshi, abubuwane kawai suke mishi yawo akai, duk he was just confuse, Ajiddeh kuma ba hankali ta cika ba da komai zaizo mishi da sauk'i, dan ko jiya shirmen da ta dinga mishi darajar Auntyn ta dake gidan taci da yayi maganinta, gaba d'aya bayajin zai iya yin nesa da Batuul, she has become part of him, duk da shi dai yasan ba wai sonta yake ba amma har cikin ransa yake jin ta, dole ne ma yasan yadda zai sanar da Ajiddeh dan bazai iya cigaba da b'oyewa ba, inma ya b'oyen to dole attitude da movements d'inshi su nuna, lumsassun idanunshi ya bud'e jin motsi kamar an fito a guje, inda yaji motsin nan yabi da ido, Batuul ya gani bakin staircase ta durkushe wajen tana kwarara amai, baisan lokacin da ya ture Ajiddeh dake jikinshi ba ya mik'e a rud'e ya iso inda take, rik'ota yayi ya jawota jikinshi yana rik'e da ita har saida yaga ta gama aman, Ajiddeh ce ta k'araso wajen ta rik'e k'ugu sai karkad'a jiki take taja wani dogon tsaki tace "iskancin banza, ke iskancin naki har ya kai da yi min k'azanta a parlour, jibi yadda kika b'ata min gida da amai, toh wlhy sai kin gyarashi tsaf, nan yayi maki kama da toilet", ko ta kanta Abu baibi ba ya d'aga Batuul da ta gama galabaita cak yayi sama da ita, bai ajiyeta ba sai da ya shiga toilet d'in d'akinta sannan ya taimaka mata ta wanke bakinta, tana rik'e jikinshi har lokacin, suna fitowa ya kalleta with care yace "mey ki kaci ya saki amai?", ko kulashi batayi ba saima k'ok'arin k'wace jikinta da ta shiga yi daga hannunshi, suna zuwa bakin gado ya saketa, kamar jira takeyi yana saketa ta sulale tayi kwanciyarta kan gadon ta lumshe ido tana maida numfashi, ganin ta lumshe ido yasa kawai ya k'yaleta ya gyara mata kwanciyarta yayi waje, k'asa ya sauk'o ya tarar Ajiddeh bata nan, kitchen ya shiga ganin stoves a kunne duk ya kashesu sannan ya d'auko Vacuum cleaner ya shiga gyara gun da tayi aman, d'akin ya koma yaga alamun tayi bacci, ya sauke ajiyar xuciya yaja k'ofan ya rufe, toilet d'in d'akin da ya kwana ya shiga yayi wanka ya canja wasu kayan, key d'in motarshi ya d'auka ya fita daga gidan yaje eatery siyo musu breakfast, har lokacin baiga Ajiddeh ba, d'akinshi da yasan zai samesu yayi knocking, ita ta taso ta bud'e mishi k'ofa, tana ganin shine cike da masifa tace "inji dai ta fito ta gyara min parlourn dan ni I can't withstand wannan K'azantar," wani mugun kallo ya sakar mata sannan ya dungure mata ledan ya juya ya barta nan tsaye baki a sake, kwafa tayi ta d'auki ledan ta juya ciki, d'akin Batuul ya koma da sauran ledojin dake hannunshi yaga tana bacci har lkcn, bakin gadon ya zauna ya zuba mata lumsassun idanunshi, tausayinta ne gaba d'aya yaji yana ratsashi, har ta d'an fad'a, to wai ma me ke damunta haka, deciding yayi idan ta tashi still not ok su tafi hospital kawai, hannu yasa ya gyara mata gashin da ya zubo mata fuska sannan ya d'an shafi fuskan nata ya miqe ya fita waje, yunwa yakeji amma baijin cin abincin waje at all, kitchen ya shiga yaga kunun data fara, k'arasawa yayi ya ciro kifi da meat pie d'in da tayi baking, ya nufi dining ya zauna yaci, sai lumshe ido yakeyi yana cin abincin, a ranshi kuwa cewa yakeyi "She is angel, always different", addu'a samun sauk'i ya dinga yi mata har ya gama cin abincin shi, parlour ya koma ya kwanta dan bai tunanin yau zai iya fita ya bar Batuul, duk bayan 30mins sai ya shiga ya dubata, Sallah azahar ma yau a gida yayi baije masallaci ba, baiso ta tashi baya nan, mamaki ne ya kamshi ganin har la'asar tayi amma bata farka ba, kuma baccin nata normal, yasan bata irin wannan baccin haka, ita kuwa da ta tashi wani baccin ke dauketa, bayan yayi sallahn magrib a gurguje ya fita ya siyo musu abinci, sai da ya fara kaiwa Ajiddeh nata sannan ya shiga d'akin Batuul har lokacin tana bacci, deciding kawai yayi ya tasheta sabida baccin yayi yawa, a hankali ya shiga tashinta bayan ya hau kan gadon, da k'yar take iya bud'e ido tana maidasu ta lumshe, d'agota yayi ya jinginar da ita jikinshi yace "Hey wake up, wannan wani irin bacci ne, tashi kici abinci, its already late, bacci tun safe", a hankali ta bud'e lumsassun idanunta ta k'arewa d'akin kallo, a kanshi ta tsaida kallonta tace "Farida bata iso ba?", tana sake lafewa a jikinshi, d'agota yayi yace "tashi kici abinci", had'e rai tayi ta zumb'uro mishi baki tace "Ina Farida nace?", tana magana tana dad'a sulalewa jikinshi, ganin baza ta tashi ba yace "Farida anyi delaying flight d'insu sabida bad weather baza su iso yau ba sai gobe da safe", daga haka ya d'agata ta zauna, hannu yasa ya janyo pack d'in abincin yace "C'mon zo kici abinci", ya bud'e pack d'in, da sauri ta matsa baya tace "mey wannan d'in?, ni banaso", da mamaki yake kallonta yace "ba kya so kuma, duk yau baki ci komae ba fa, c'mon have it, ya d'ebo daga cikin spoon d'in ya kawo mata baki, da sauri ta toshe bakinta da d'ayan hannunta d'ayan kuma ta ture hannunshi da ya mik'o mata gabanta tace "Nace banaso, banason k'anshin abinci bazan ci ba, ka fita dashi", kallon mamaki kawai yake mata, rai b'ace cike da masifa tace "ka matsar mana, nace fa bazanci ba", abincin ya matsar gefe kamar yanda tace ya rik'ota da damuwa yace "toh mey zakici", kamar jira takeyi da sauri tace "Ni ice cream zansha", baki ya bude yace "kina ma da hankali kuwa, ina tambayanki mey zakici kina ce min ice cream, I will slap you right away in baki bar wannan shirmen naki kin fad'amin abinda zakici ba, duk yau mey kikaci da zakice min wani ice cream zakisha, you were sleeping all day kamar wata jaririya", tutturashi ta shiga yi daga jikinta tana murgud'a baki tace "Ni dama bance dole sai ka samomin ba ai, kuma ma ni da kaina zan iya zuwa inyi, bana ma so na fasa, ko ka kawoma bazan sha ba, ka tafi min daga d'akina ni", ta d'an ja tsaki tayi kwanciyarta ta juya masa baya, ya kai minti biyu zaune yana kallonta da mamaki, can dai ya mik'e daga karshe ya nufi kofar d'akin, jin motsin kofa ta juyo da sauri tace "ice cream d'in zakaje kawo min?", wani irin kallo ya watsa mata, bata damu da kallon da yakeyi mata ba tace "Ni kar kaje Cold stone fa, ko na lick ko scoop, ba na can nakeso ba, na gelatorino nakeso, sai flavour Kuma pistachio, strawberry, Madagascan vanilla, kuma banason na corn, su min scooping a cup, yawwa with a couple of some more exotic options kamar su coconut lemon grass, pepper mi.....", bai jira ta gama surutun nata ba ya kad'a kai ya fice ya rufo k'ofan, baya ya jefa key d'in aljihunsa, gaba d'aya ya kasa gane what came over this girl, mota ya shiga sannan ya kunna map navigator yayi searching wajen da ta fad'a mishin, dan shi baisan ma inda gun yake ba, tafiyan 15mins ya isa wajen, duk abubuwan da ta lissafo mishi sai da ya siya harda k'ari, da snacks, bai jima ya dawo gidan, har lokacin bai ga Ajiddeh ba, d'akin Batuul ya wuce kai tsaye da ledojin hannunshi, tana jin motsinshi ta mik'e da sauri, daga bakin gado ya zauna ya mik'o mata ledan hannunshi, da sauri ta anshe, na snacks d'in ta fara ansa, rai b'ace ganin abinda ke ciki tace "nifa ba abinda nace inaso ba kenan", ta tura mishi gabanshi, jin d'ayan ledan da sanyi yasa tayi hanzarin jawoshi ta shiga bubbud'ewa, ba tareda b'ata lokaci ba ta shiga shan ice cream d'in, kallonta kawai yakeyi ganin yanda takesha d'agowa tayi suka had'a ido, murmushi ta mishi tace "Thank you, you can have some", tayi mishi nuni da ledan dake ajiye, kai kawai ya iya girgiza mata, tab'e baki tayi taci gaba da shan abinta, ko rabin na cup d'in batasha ba ta ajiye tace "Alhamdulillah, am full", ta ajiye zata juya ta kwanta yayi maza ya rik'ota yace "meye hakan?, wai kina nufin har kin gama sha? kai ta gyad'a mishi tareda d'age mishi girarta d'aya tace "Ehh", yace "abincin kuma fa?", d'an had'e rai tayi jin ya ambaci abinci tace "Nifa bana jin yunwa, am okay", ya d'an yu shiru sannan yace "toh brush d'in kuma fa da kike k'ok'arin kwanciya, and baki yi sallah ba, tace "nifa bacci nakeji, xan yi anjima wllh", "Bacci?", ya tambayeta dan yau wuni yaga tayi tana bacci kuma its just 8:08 yanxu, bata bashi amsa ba ta kwanta abinta, tana kwanciya kuwa bacci ya d'auketa, ya dad'e zaune yana kallonta daga baya ya tashi ya ciro mata kayan baccinta cikin closet ya cire mata na jikinta ya saka mata wanda ya ciro?, mamakin irin baccin nata kawai ya dinga yi dan har ya canja mata kayan bata tashi ba ita da bata da nauyin bacci, addu'ar bacci ya tofa daga baya ya kashe mata wutan ya tafi d'akin da ya kwana jiya, wanka yayi sannan ya d'auro alwala yayi sllhn Isha ya koma gado, kamar jiya yau ma a waya ya dudduba ayyukan office da baiyi ba snn ya kwanta, sai wajen sha biyu snn Ajiddeh ta shigo d'akin, yana jinta sai wani shige mishi jiki takeyi, ganin yayi bacci ta k'yaleshi itama ta kwanta. Washe gari da asuba bayan yayi Sallah direct airport ya wuce d'aukan Farida, arrivals ya wuce kai tsaye bayan ya gama parking, dai dai lokacin da Farida ta fito daga terminal janye da akwatinta, ita ta fara hangoshi, da gudu ta k'araso ta rungumeshi, shima d'in rungumeta yayi, cike da farin cikin ganinsa tace "Yaa Abu ina kwana, thought tare xa ku xo da Anty Batuul" da xolaya ta kare maganan da wide smile d'inta mai kyau shimfid'e fuskarta, murmushin shima yayi yace "Lafiya Alhamdulillah, Ya hanya?", zumb'uro mishi baki tayi jin yace ya hanya tace "hmmmm ai ni shiyasa bana son bin wani flight inba B.A ba ko Emirates, kasan transit kawai muka tsaya amma suka fake da wani wai bad weather, baza mu taso ba sai bayan nan da 14hrs , ni ai da so nayi in koma Nigeria, amma sabida ina son ganin my other half", ta wani lumshe ido tana d'aura duka hannayenta biyu a k'irji tace "Allah dan ita kad'ai na yadda na k'araso, kuma kasan wani abu......", bai barta ta k'arasa ba yace "Let's get going, d'an wannan surutun naki zamu kwana nan baki gama ba", suna tafiya yake tambayanta Yasu Ammah da kowa a gida, kamar jira takeyi ta dinga mishi zuba, wasu abubuwanma ba ji yakeyi ba har suka isa inda yayi parking mota, butt ya bud'e mata ta saka jakarta a ciki, sannan ta xagayo ta zauna, sai da ya tada motar suna tafiya sannan ya juyo ya dubeta yace "kina jina?", gaba d'aya hankalinta ta tattaro ta kalleshi jin yana mata magana, yaci gaba da cewa "Babu ruwanki da duk wani abu da zaki gani in mun je, Ajiddeh isn't aware Batuul is my wife", a firgice ta kalleshi tace "What?", kallonta yayi ya wani hade rai yace "Yeah you heard me right, dan haka babu ruwanki da duk abinda ke faruwa cikin gidan, am repeating it, don't try anything stupid like you did last time, babu ruwanki da Ajiddeh", tabe baki tayi ta kauda kai, yace " Baki da hankali ina maki magana kina dauke min kai" xumburo baki tayi ta gyad'a mishi kai alamar ta ji, ya hade rai sosai yace "bakida bakine?", ta dan murguda baki tace "Toh naji mana", kwafa yayi ya ci gaba da driving dinsa, ta d'auke kai ta juya tana kallon window, ranta ne taji ya baci ba k'adan ba wai Ajiddeh batasan Batuul matarsa bace, toh does that mean they weren't intimate ko me, shine har Ammah ta fara lissafin jikoki, "Chabdi" ta fad'a a ranta ba tare da tasan ya fito fili ba, juyowa yayi yana kallonta yace "kikace meye?", maza tayi ta kad'a mishi kai tace "No ni bance komai ba", ya harareta ya maida hankalinsa kan driving din da yake,farida taci gaba da sak'e sak'enta, a ranta tace masifaffe wai wani I shouldn't try anything stupid, tabdi ai kuwa wlhy sai dai in wannan matar tasa mai kama da bishiyar gwanda sai tsawo babu shape tayi hankali itama, dan indai ta tab'ani ba yadda za ayi in k'yaleta wlhy sai na rama, kuma sai nasan ynda nayi tasan wacece Batuul, "kutt, ai wlhy bama zai yiwu ba", batasan a fili tayi maganar ba saida taga yayi parking yana mata wani irin kallo yace "meye d'in ne bazai yiwu ba?", da sauri ta shiga girgiza mishi kai a rikice tace "I wasn't talking to you fa", ya jima yana kallonta fuskarsa daure kafin yayi k'wafa ya ci gaba da driving, bata kuma gigin wani tunanin ba bare har ya fito fili, kamin su isa har gari ya washe, bayan yayi parking kamin ta fito in a serious tone yace mata "hope you heard all I said clear?", kai kawai take girgiza mishi dan ita ta matsu taga Batuul, yana bud'ewa ta fita guje ta shige gidan, tun daga bakin k'ofa ta fara ihun "His beloved, His First Lady, kina ina na iso", A guje Batuul dake kitchen ta d'an samu karfi tana gyare gyaren kitchen din ta fito jin muryar Farida, Ajiddeh da Aunty dake d'aki ma fitowa sukayi lokaci d'aya ganin wake ihun, Abu kam mamakin Farida ne ya cikashi jin abinda take fad'i, ya k'asa karasawa parlorn, ita ko ta tafi da gudu suka rungume juna da Batuul cike da murnan ganin juna, farida ta tura Batuul daga jikinta tana kare mata kallo ta wara ido har da d'an tsallanta tace "Waoww waow, yayana ya iya kiwo wllh, kinga yanda kika yi wani fresh kika yi kyau kuwa love, OMG" wani tsawa da ya rikita ta daga ita har Batuul din Abuturrab ya daka mata. 💖💝BATUUL💖💝 70 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Wani mugun kallo yake yi ma Farida yace "kin wuce kin bar nan ko sai na zo na sameki, are you stupid ku ke min ihu haka a gida", duk da tsoron da taji hakan bai hanata dakewa tayi kamar ba da ita yake kamar ba, ta d'aga kai ta kalli su Ajiddeh da ido ya k'ank'ance da masifa, harara ta galla mata daga haka ta kuma maida dubanta kan Batuul tana washe baki tace "keh kin ga gashinki kuwa yadda ya wani dad'a cika yayi tsawo, meye sirrin 'yan mata, sea foods da salads kike ci ne? Kai Amma gaskiya gidan Yayana ya......", bata k'arasa ba taga yana tunkarosu, hanjin cikinta ne suka kad'a ganin haka, Batuul kam ko a jikinta sai dariya take, yana zuwa yasa hannu ya fincikosu a tare yayi hanyan stairs yana rik'e da hannunsu, ko lura da Ajiddeh da yayarta bai yi ba a sama, Batuul ta finciketa nata hannun daga rik'on da yayi mata ta tsaya cike da masifa tace "meye haka kake wani jana kamar igiya, ni nace maka inason zuwa sama ne?", da mamaki ya tsaya kallonta da har bai san lokacin da ya sake hannun Farida ba ta sulale a guje tayi sama abinta tana 'yar dariya, abubuwane kawai ke mishi yawo a kai, badai har yarinyar nan ta raina shi ba, ita kanta Ajiddeh da yayarta sakin baki suka yi suna kallonsu, juyawa Batuul tayi zata tafi ya fizgota gabanshi yana kallon fuskanta yace "Are you stupid?, ni kike ma magana haka, are you out of ur senses?" sauk'owa Ajiddeh ta shiga k'ok'arin yi daga saman da take tsaye dan bataji zuciyarta zata iya jure wannan abinda take gani gabanta, Aunty Jainaba ce tayi saurin riketa a hankali tace mata "keh shashasha tsaya, ki bari muga iya gudun ruwansu, ai inaga ma lokacin maganinta yayi a gidan, kema dai kinyi sakaci, meye na barin budurwa haka a gidanki", da mugun kallo "Ajiddeh ta dubi Jainaba tace "dalla can toh da duk abinda nake gaya muku Kun zata wasa nakeyi, toh yau koma menene, k'arshen xamanta yazo wllh" Batuul kam turashi ta shiga yi tana murgud'a d'an k'aramin bakinta tace "Ni ka rabu dani", duk wannan abinda sukeyi baisan su Ajiddeh na sama ba, matseta yayi jikinshi ya murd'a mata hannu yace "sai kin fad'a min sudden change of behavior nan naki, wato na fara miki wasa shine zaki rainani", had'e rai tayi hawaye taf idonta ta turashi daga jikinta tace "Ni kam ka sakeni", sauk'owan da yaji ana yi daga stairs ya sa ya daga ido da sauri, Ajiddeh ya gani tana sauk'owa furiously, with full rage a fuskanta, tura Batuul d'in yayi yana mata mugun kallo yace "b'ace min daga nan", juyawa tayi a fusace ta nufi stairs, karo suka kusa yi da Ajiddeh ta koma baya da sauri ta raba ta gefenta xata wuce, a zuciye Ajiddeh ta fincikota ta hade ta da bango tana huci tace "Keh dan ubanki nayi miki kama da sa'ar uwarki da har zaki dinga min isa a gidana, to wllh xaman ki ya kare yau a gidana yanxun nan kuma ba sai anjima ba" turata Batuul tayi tace "kar ki sake ki sake gigin tab'ani wllh, zagi kuma wannan training din da aka maki kenan gidan ku, banida time d'inki", da haka ta juya ta haura sama ta bar ta nan tsaye, kwalalo ido jainaba tayi, Ajiddeh kam mutuwar tsaye tayi gun ta kasa kwakkwaran motsi, bata tab'a tunanin Batuul zata iya yin abu kamar wannan ba, a zuciye ta k'araso wajen Abu har wani rawa jikinta ya shiga yi sai hargowa take tace "Aliyu wlhy wlhy, kadai ji na rantse koh, toh yarinyar nan sai ta bar gidan nan yanxun nan, in kuma bata bari ba ni zan bar maka gidanka, ai dama nasan wannan kareta da kakeyi duk sabida kana samun wani abun gunta ne, wa ya sani ma ko zagayawa kakeyi gunta da daddare zaman dadiro kakeyi da ita, in ba haka ba, yaushe har zata rainaka ta rainani, dubi yanda ka wani rungumeta yanxu, ni za a rainawa hankali a wani ce karatu tazo yi, toh koma meye ta zo yi ni bazan zauna da ita gidan nan ba , kuma in ba karuwanci takeyi ba Meye ma'anar aman da naga tana kwararawa jiya kamar mai ciki, ko daxu sai da naji kakarin amanta har sau biyu a daki, ohh wato karuwa ka kawo min gida ka.....", bata k'arashe maganan ba ya d'aga hannu ya sharara mata mari da ya gigitata, har Aunty Jainaba saida taji tsoron jin irin marin, Aunty Jainaba ce tayi saurin saukowa ta rufe mata baki tace "ke don uwar ki Meye haka kike yi, yaushe ne zakiyi hankali Ajiddeh, jibi fa irin maganganun dake fitowa bakinki, mijin naki kike yiwa magana haka?, dama bakida hankali ashe", tana yi tana k'iftawa Ajiddeh ido tayi shiru, fincike hannunta tayi daga rik'on da yayi mata, idonta har ya canza kala duk ya k'ank'ance hawaye na xuba idonta tace "ai ka mari aurenka Aliyu, akan gantalalliyar y'ar iskar nan kake mari na, ai ba sai ka mareni ba zansan mey ke tsakaninku, kuma yau zan bar maka gidanka", ta juya fuuuu tayi sama, Aunty Jainaba ce ta kwantar da murya tace "Aliyu ashe haka kake fama, ai ni ban tab'a sanin haka yarinyar nan take mara hankali ba, Dan Allah kayi hak'uri ba sai ka daka ta tata ba, kasan hankalinmu ba d'aya da naku ba, kayi hak'uri kaji?, zanje yanzu in ci uwarta, Allah ya k'ara maka hak'uri", kasa cewa komai yayi tunda yaji abinda Ajiddeh tace "wai cikine jikin Batuul, ciki kuma? toh wane irin ciki", a hankali ya maida dubanshi kan Aunty Jainaba yace "Ba komai", da haka ya barta nan tsaye ya haura sams, d'akin Batuul ya wuce kai tsaye, bud'e k'ofan d'akin yayi ya shiga rai a had'e, Farida dake zaune tana ta zuba bata san lokacin da ta fasa ihu ta mik'e tsaye daga kan gadon ba tana yarfe hannaye, sau d'aya Batuul ta kalleshi ta d'auke kanta tana kallon Farida tace "Keh wai meye haka kika hau gado kina wani tsalle, ko ce miki akayi bouncing castle ne?", kallonta Farida tayi sannan tayi mata nuni da Abu dake k'arasowa cikin d'akin da baki, kallonshi tayi ta tab'e baki tace "toh mey zai miki?", fuska a daure yana kallon Farida yace "get down", sake matsawa tayi jikin gadon tace "Dan Allah kayi hak'uri Yaa Abu, bazan sake ba", k'arasawa yayi bakin gadon ya fizgota yana mata mugun kallo, ihu ta fasa ta rintse ido tana jiran jin sauk'ar mari, "ni nayi kama da sa'an ko koh? all those warning I made clear to you basu shigeki ba?", a hankali ta bud'e idon jin bataji sauk'ar mari ba, kamar munafuka tace "Yaa Abu nifa bance komai ba, kawai cewa nayi ai ka Iya reno, Batuul tayi kyau", tsaki yayi ya hankad'ata har sai da ta fado daga kan gadon yace "Baxa ki kwana min a gida ba yau" Ajiyar zuciya Jainaba ta sauk'e a fili ta furta "Lallai da aiki a gabanmu", sannan ta juya ta haura saman itama, a bakin k'ofa sukaci karo da Ajiddeh janye da akwati, da mamaki take kallon Ajiddeh sannan ta riqe akwatin tace "Keh meye hakan?, ina zaki da akwati", Ajiddeh tace "kema in zaki tattaro naki ki d'auko kizo mu wuce dan ni na gama zaman gidan nan indai wannan bak'ar yarinyar tana nan, ni wlhy right from day one ba santa nakeyi ba, bare yanzu da tazo ta tare take zama min a gida, gashi har wata suka k'aro mishi dan munafurci da sa ido", kuka sosai ta fashe da, Aunty Jainaba ta ja ta suka koma dakim ta zaunar da ita, Fridge ta bud'e ta mik'o mata ruwa, ta sha sannan ta karb'a ta ajiye tace "ashe keh bakida hankali ban sani ba Ajiddeh, ashe ba da kai kike tunani ba?", kallonta Ajiddeh tayi hawaye na sakko mata tace "ban gane ba", zama itama Jainaban tayi daga gefenta tace "Gashi ko kin nunamin alamu, in banda rashin hankalinki ina kika kinkimi akwati zaki da?, wa yace miki ana yiwa namiji haka bare wannan mijin naki d'an isa da kallo ma mutane basu isheshi ba, kina gani fa ko kunyata baiji ba ya sharara miki mari, toh ina ga in kin bar gidan, ai sai abinda yaci gaba, duk danginmu kaf cikinmu babu wanda ya tab'a auren mai irin kud'in mijinki kin sani, duk da kema naki uban nada kud'i amma ko k'afar nashi uban bai kamo, gashi shima yaro dashi amma arzik'inshi yafi k'arfinshi gashi komai kikace kinaso sai ma ya miki dad'i badai ragi ba, zancen zaki bar mishi gida bai zo ba, Allah ne yayi zanzo inga rashin hankalin da kike kwab'awa, duk da nazo da shiri amma dai nasan sai mun sake akan nada, wannan duk yadda akayi ya riqe ibadarsa sosai shi yake hana aikinmu ya kamashi, kuma ina jin iyayensa ma basu bar shi haka ba, yanzu watanmu uku muna abu d'aya amma bama tab'a cin nasara, wannan karan kuwa ba da wasa zamu shigeshi ba, itama wannan yarinyar gaba d'aya b'atar da ita zamu sa ayi tunda har a dalilinta yake marinki, dan haka dole ne abi ta kanta a magance matsala, sati d'ayan da nazo yi na fasashi, jibin nan zan koma in fad'awa Yaya duk abinda ake ciki, sosai zamu tashi tsaye akanshi, sai mun sa ya gwammace kid'a da karatu", kamar wata wawiya tana nan zaune har sai da junaiba ta gama sannan tace "Toh yanxu ya zanyi, dan ni duk matar da ta rab'eshi ko tace zata shigo rayuwarshi wlhy Allah sai na hallaka koma wacece, sai dai nima a kasheni, Anty baxa ki gane irin son da nake ma Aliyu ba" cikin matsanancin kuka ta kare maganar, junaiba ta sauke ajiyar xuciya tace "Ai babu wani zancen wata matar in ba ke zakiyi sake ki bashi dama ba, yanzu ki tashi ki kintsa kije ki bashi hak'uri daga nan sai kiyi mishi zancen tafiyata dan ya bamu d'an tsoka mu samu na aikin, suma Malaman na yanzu ba abin yadda bane sai kaga da k'yar ake samun na gaske, dubi fa abinda wannan d'an isakan mutumin yayi mana", mikewa Ajiddeh tayi har lkcn xuciyarta na tafarfasa don da xa a bata wuka a lkcn babu abinda xae hanata caka ma Batuul, Allah sa ma cikin ne jikinta kamar yanda take xargi, shikenan xamanta ya xo karshe gidan cikin ruwan sanyi, kwafa tayi ta mik'e ta shiga cire kayan jikinta tana naxarin abinda Anty jainaba tace. Ficewa Farida tayi daga dakin tana xumbura baki a xuciyarta tace "Ae ko da na kira maka Ammah yanxun nan, kuma in fita in fasa gaskiyan komai" bin ta yayi da harara sannan ya dawo daga gefen Batuul fuskarsa daure, kamar bata ganshi ba ta mik'e k'afafuwa zata kwanta ya rik'ota cikin kaushin murya yace "I will slap you idan baki tsaya kin saurareni ba", kuka ta fashe masa da, nan da nan ya rude ya dago kanta yace "me ya faru kuma, me nayi maki" kin cewa komai tayi sai kukan da take, nan ya shiga rarrashinta kamar wata jaririya, da kyar ya samu tayi shiru, ya rungumota jikinsa ya lumshe ido yayi shiru, mamakin kansa kawai yake, ya rasa gane dalilin da yasa yake behaving haka, maganar Ajiddeh ne ya fado masa, ya bude idonsa a hankali yace "Are you noticing some changes a jikinki?, I mean do you feel anything unusual?", had'e rai tayi ta dago kai tana kallonshi tace "Meye toh kake tambayata", yanda ta had'e ran ne ya kusa bashi dariya amma ya dake yace "wai yaushe kika koyi rashin kunya ne, ina miki magana kina had'e min rai, ehhn tell me", ya k'arashe maganan tareda zame mata hular dake kanta, tsuke mishi baki tayi tace "Ina ruwanka da hulata da zaka ciremin, ni ka maida min abuna", yace "bazan mayar ba har sai kin fad'a min mey ya canja ki lokaci d'aya", sake had'e fuska tayi tace "wai wani canjawa, ni dama can haka nake kaine baka sani ba", dariya yayi yace "d'azu fa naga har my wi.....", sai ya tuna alk'awarin da yayi mata na cewa bai sake k'iran Ajiddeh da my wife gabanta, kwana biyu bata yi kuka ba har wani dad'i yakeji, kallonta yayi yaga ta tsareshi da ido yace " I meant Ajiddeh, d'azu har gani nayi kin kare kanki gunta, hmmm I lyk that courage, d new you, but banda wannan sabon attitude d'in towards me, kuma idan xaki mata fitsaran ki tabbatar ina gida", kallonshi tayi ta d'an tabe baki tace "ni ka tafi bacci zanyi", yace "bacci? mey ke damunki ne, we have to see a doctor, dan baccin nan naki ba na lafiya bane", zumb'uro mishi baki tayi tace "inji waye banida lafiya, am fit and fine", yace "ina wani fit and fine, bakida aiki sai amai da bacci, ko breakfast ma bakiyi ba yanzu, ko jiya ma bakici dinner ba", kamar jira takeyi ya gama magana tace "Yawwa kaga ma ko, ice cream nakeso in sha yau ma, amma ba na Gelatorino ba yau, na Cold stone nakeso, sai ka siyo ma farida breakfast", kallonta kawai ya tsaya yi yadda cute lips d'inta ke moving, ganin baice komai ba ta tsuke baki tace "I knew it dama baza kayi min ba, toh kaje zanyi da kaina", lumshe ido yayi ya janyota ya had'ata da jikinshi ya shiga kissing d'inta passionately, ita kam sai tutturashi takeyi amma yaqi saketa, Farida ce ta tura k'ofan d'akin ta shigo riqe da waya, turasa Batuul tayi da sauri ta koma baya, ganin condition d'in da suke ciki yasa tayi maza ta juya ta riqe bakinta tace "Oooops, am sorry, Ammah ke son yin magana da Batuul", Batuul dai kasa d'agowa tayi ta kalleta sai shine da ya bita da harara yace "out", da sauri taja musu k'ofar ta fita tana kyalkyala dariya. 💖💝BATUUL💖💝 71___72 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* D'ago kai tayi ta kalleshi bayan Farida ta fita, suna had'a ido tayi maza ta dauke nata tace " kagani ko, ni dai ka tafi daga d'akina", hannu yasa ya d'ago hab'arta yace "ita tace gidanta (Ajiddeh) keh kice d'akinki, kamar kun ma san sanda aka yishi", yana murmushi ya kare maganar, janye hannunshi tayi tace "toh ba d'akina ba, d'akinka, ka tashi ka tafi ni dai" ta k'arashe maganan tana zumb'uro mishi baki, ya buda ido yace "You are totally changing from what you were, kin koyi fad'a da rashin kunya, korata fa kikeyi, I can decide to stay with you for a whole year if you didn't change, beside I lyk being with you all d time, I can't get enough of you, your warmth, body texture, scent everything, next time bakin ki ya sake ce min in tafi sai na dawo d'akinki gaba d'aya da xama, ko kuma keh in maidaki nawa d'akin da zama", zumb'uro mishi k'aramin bakinta tayi tace "toh ba turarenka bane kullum sai ya rik'a min yawo akai, ni bana sonsu yanxu", ta fadi tana kauda kanta, kalllonta yakeyi har ta gama maganan snn yace "baki sonsu?", kai ta gyad'a mishi da sauri, yace "toh wanne kikeso in na amfani da? nuni tayi mishi da kan vanity table d'inta tace "ba ga nawa ba, kaita using ni bazan hana ka ba ai", dariya ta bashi yace "yanzu keh sai ki yadda in shafa turarenki, toh su meye ma naki turaren in banda humra, ni kuma mey ya had'ani da shafa humra", had'e rai tayi tace "ai akwai wasu ba Humra bane kawai", yace "naji toh, yanzu zaki rakani in sai wasu sabbin turaren wanda basa damunki", da sauri ta kad'a mishi kai tace "Ni babu inda zani", girarshi ya d'age mata yace "woooh , fine I will go by myself, but in na kawo wani karki ce min shima na damunki tunda kece kika qi zuwa kiyi selecting", murgud'a Mishi bakinta tayi tace "Na yadda", mamakin kanshi yake gaba d'aya, shi kanshi baisan mey ke damunshi ba, wai shine yayi stooping to Batuul's level har yake biyewa shirmenta, har wani murgud'a mishi baki takeyi amma he couldn't do a thing sai ma burgeshi da take, kallonta yayi yace "Okay, now tell me mey zakici, I will get it right away", ya had'e rai yace "don't tell me bakijin yunwa ko kuma ice cream zakisha, solid abinci nakeson kici", kallonshi tayi tace "Toh sai ka had'o min ice cream d'in da Burger na burger kings, kada a samin cheese, sai pizza shima na pizza hut amma fa beef, da chips d'in KFC sai kace su baka spice d'in da yawa, sai daga gefen school d'inmu akwai wani road side food vendor, shi kuma sai ka siyamin Tacos da chicken rolls a wajenshi, shima ya samin spice da cream dayawa", shikam kallonta ya tsaya yi tana magana tana lumshe ido, har wani tsayawa tunanin abinda zatacin takeyi , tace "Yawwa sai kuma Raffaello, a pack of twix and what keeps me moving Nutella", ta k'arashe maganan da dariya abinta tana wara ido, shi kam kasa cewa komai yayi sai kallonta yake ko kiftawa bai yi, ganin irin kallon ta had'e rai tace "Kaji?", d'an tab'e baki yayi ya kalleta yace "Naji, amma wai ke zakici duka wannan abinda kika lissafo?", kai ta gyad'a mishi tareda d'age girarta tace "toh zance ka siyo ne in baxan ci ba?, duka nikeson ci", yace "Fine", tareda da d'age mata hannayenshi, yace "wannan lissafin naki its better we order it, kowanne fa venue d'inshi daban", da sauri tace "Ah ah, nikam its better you go by yourself, kar suje sumin mistake", mik'ewa kawai yayi dan yasan rigima take jin yi, ta kalleshi tace "sai ka tambayi Farida ma abinda zataci", har ya kai bakin k'ofa tace mishi "kaga ko, baka maidamin hulata ba", sai ta fashe mishi da kuka, da har bazai juyo ba jin ta fashe da kuka yasashi dawowa da sauri ya wara ido ya sa mata hularta ya gyara mata kwanciya murmushi dauke fuskarsa yace "I've done that" mikewa yayi yana kallonta yace "I will send in Farida", da haka ya juya ya fita, a corridor ya tadda Farida na waya, harara ya bita dashi ya sauk'a batareda ce mata komai ba, dariya tayi ta juya ta shige d'akin, da sauri Batuul dake kwance ta juya mata baya, zuwa tayi ta fad'a kan gadon ta yaye bargon da Batuul d'in ke rufa da tace "Hey c'mon get up, ya tafi shine zaki wani kwanta, toh ga Affan nan, he is on the line", d'an tsaki taja tace "Riri you will never change wlhy", lumshe Ido tayi ta fad'a da baya snn ta d'ago tace "Ohhh how I missed this name, babe I missed you sooo much baza ki ganeba", dariya ta bawa Batuul, jin muryar Affan cikin wayan tayi maza ta mik'a mata tace "he is on the line", ture wayan tayi tace "ba ruwana dashi ai ni, ba ya manta dani ba, I don't want to talk to him nima, he promised to call me back rannan but he never did", ta k'arashe maganan tareda lank'washe hannayenta a k'irjinta, Farida ce ta maida wayan kunnenta tace "Mine", da sauri Batuul ta d'ago ta kalleta jin sunan da ta k'ira Affan dashi, a ranta tace "Sabon salo", "Mine kaji ko, kayi mata lefi, ita fushi take dakai", tace "Baby mine ina jinta, samin wayar speaker muyi maganan da ita", speaker ta danna snn ta ajiye wayan, yace "Hey sweetheart best friend, am so sorry for not calling back, these days kullum busy nake sabida shirin exams dake gabanmu, nayi miki alk'awari I will come immediately after my exams, not even before going home", da sauri ta d'auki wayan jin yace zaizo tace "Yaay that's my best friend", haka dai sukaci gaba da hirarrakinsu har ta gama ta mik'awa Farida wayar sukaci gaba da hirarsu ta soyayya, saida suka gama sannan Batuul tace "wai ke yanzu Farida dagaske kike son Affan dinnan?, he just 3yrs older than us fa", Farida tace "of course I do know, shiyasa ma nake son nashi, ni wlhy na tsani saurayina ya fini koda five yrs bazan iya auren babba ba, ni kunyanshi ma zan rik'aji, Affan is d perfect guy for me, I soooo much love him to d extent da in akace za a rabani dashi I can jump through d window", dariya sukasa dukkansu biyun, Batuul tace "kin manta from d terrace dai", suka sake sa dariyan, Farida tace "Kinsan I had a crush on Affan tun farkon ganina dashi, I always get jealous yadda kuke, I tot ma soyayya kukeyi yadda naga you guys are so close, saida kikace min wai he wants to ask me out, wai inja mishi aji, ai ba Iya zan ba, wlhy ranan I couldn't sleep, Allah na rik'a yiwa godiya, dan dama kullum sai na rokeshi, I was just happy", dariya Batuul tasa tace "We have been best friends tun childhood d'inmu, His Mom and Aunty were cousins, kuma best friends, Aunty tana fad'a min lokacin suna Uk tareda su Ammah, she have been married for nine years amma bata samu haihuwa ba, Shekaran da akayi aurenta shekaran aka haifi Yaa Abu da Massa, kuma lokacin Ammah da Yaa Mera suna aiki, gidansu a Jere yake su ukun, dama mazajensu abokai ne sosai tun yarinta, Baba, Abui sai shehu, toh Aunty ce kad'ai bata aiki, kinsan Fulani tana gama secondary school akayi mata aure, Baba kuma yace yafi son saita haihu taci gaba da zuwa makaranta, toh a lokacin nefa sai su Ammah su rik'a kawo mata su Yaa Abu gunta in zasu aiki, ita tayi rainonsu, daga baya ma sai komai nasu ya dawo wajen Aunty, har lokacin da suka shiga school, lokacin da suka cika Nine years, lokacin Aunty ta samu cikina, kowa yayi murna sosai, cikin Aunty nada wata shida aka yiwa Baba transfer ya koma Nigeria, lokacin yace zai tafi da Aunty, su Abui sukayita insisting ya bar Aunty dan its risky tana yawo at this stage of pregnancy, gara ya riqa zuwa yana dawowa, yace hankalinshi bazai tab'a kwanciya ba, gara ya tafi da matarshi, lokacin su Yaa Abu sun gama year 6 dinsu na makaranta shida Massa, sunsha kuka da Aunty zata tafi, especially Yaa Abu, dan komai da Uwa zatayiwa d'anta tayi musu, tacema su suka sa mata sunan Aunty har yabita muma muke k'iranta dashi,dan shi Yaa Abu cewa ma yayi zai bita, da k'yar aka samu Baba ya rarrasheshi yace anytime sukayi hutu zai turo a d'aukesu, Da haka ya tattara suka koma Nigeria, dama lokacin Maman Affan(Sakina) ta haifeshi shekaranshi biyu da wata goma, da zai cika shekara uku Aunty ta had'a mishi birthday party a gidanmu, wai zatayi compensating rashin zuwa sunanshi da batayi ba, ana cikin shagalin party Aunty ta fara labour, nan akayi rushing d'inta asibiti, bata sha wani wahala ba ta haifeni, toh kinji wannan shine yasa I became close with Affan, mun shak'u sosai, he became d elder brother I never had, He is my birthday mate, kullum tare ake mana celebrating, kuma shi gidansu Affan sai sun sauk'e Qur'an suke shiga school, su Yaa Abbass duk saida sukayi sauk'a kamin suyi joining school, Affan ne kad'ai ya shiga school lokacin yanada haddar izu sittin, kinsan yadda kan mutumin naki yake, yanaja sosai, shiyasa aka turashi makaranta akace zai iya hada duka biyun, lokacin da nake shekara biyu, lokacin Kakan Massa ya rasu aka nad'a Baban Massa sabon sarki, Amma ma tacewa Abui itama baza ta zauna ba tunda duk y'an uwan nata basa nan, shima haka suka tattaro suka dawo, su Yaa abu kuma nan aka barsu sabida school, kin dai ji how I became close with Affan", Farida tace "Wow, so you know this much shine baki tab'a fad'amin ba", dariya Batuul tayi tace "komai da lokacinshi, gashi nan yanzu da lokaci yayi kin sani", Farida tace "Tell me, how does it feel to b married, like how do you feel, ya kikeji duk lokacin da kika tuna kinyi aure?", bata amsa ba sai ma tambayar da ta jefa mata itama tace "How does it feel to b in love, ya kikeji?, wara ido Farida tayi tace "Lallai ma, keh zan tambaya wannan ma ai, ko zakice min you are not in love ne har yanzu, I just saw it da idanuwa kina nunawa Yayana soyayya", ta k'arashe maganan tareda kashe mata ido d'aya, dariya Batuul tayi ta mik'e tace "You are not serious", daidai lokacin Yaa Abu ya shigo d'akin, Farida ya kalla yace "abincin suna k'asa go and arrange them", simi simi kamar munafuka ta mik'e ta fita, Batuul ya kalla yace "nan zakici abinci ko k'asa?", cewa tayi "Ni na tab'a cin abinci a k'asa ne, a d'akina zanci, ko dan kaga Farida?", kai ya kad'a, baya ji da rigimarta yace "sai ki sauk'a ki kwashi abubuwan naki" da haka ya fita D'akin da ya zama nashi ya koma, a bakin gado ya tarar da Ajiddeh zaune da wata irin shiga, d'auke kanshi yayi kamar bai ganta ba ya shiga cire kayan jikinshi, tasowa tayi ta shige jikinshi, had'e rai yayi ya turata daga jikinshi, sosai ranta ya b'aci amma da yake nema take su shirya haka ta koma gun nashi, ta sake mannewa a jikinshi, hannu yasa zai janyeta tace "Haba babe meye ne haka kake min, indan abinda nayi d'azu ne am sorry, I promise you bazan sakeba, d'azun ma sharrin shaid'an ne da kuma irin son da nake maka, bana iya jure ganin wata mace kusa da Kai, amma kayi hak'uri kaji babyna", cire hannayenta yayi daga jikinshi yace "Ai this is not your first time na bani hak'uri, kinsha bani kuma kike sake aikata laifin, abinda kikaga yafi dacewa dakene kikeyi, keep on with it", marairaice mishi fuska tayi kamar dagaske tayi nadama tace "Am serious this time, bazan sakeba kaji?, in kanaso har ita zanje in bawa hak'uri", ajiyar zuciya ya sauk'e yace "Ban aike ki ba", tace "toh ka hak'uran?, tsakanin mata da mijinta sai Allah, kai kawai ya gyad'a mata ya juya yayi toilet, biyoshi tayi tana cewa "Let me help you", tare sukayi wankan, shi ya d'aukota a hannunshi suka fita, bayan sun kintsa take ce mishi "Baby jibi fa Aunty na zata koma", ya kalleta yace "Soon?, mey tazo yi dama?", shiryayyar k'aryar da zatayi mishi ta rasa, batasan lokacin da tace "kasan dama d'an mijinta anan yake karatu, toh wai zasuyi convocation d'insu shine tazo tayashi murna", kai kawai ya gyad'a yace "Okay Allah ya kaimu, gobe kamin in fita you remind me", saida suka gama shiryawa yace "Food is downstairs, sai ki d'ebi na Aunty ki kai mata", da haka ta fita shi kuma yayi shirin fita, washe gari ma haka yaje ya samo musu abinda zasuci, da yamma Batuul take ce mishi Farida zata kai wa wata k'awarta da tayi aure ziyara a Birmingham saida ya gama musu tambaye tambayenshi tukunna ya yadda sannan ya had'ata da David suka tafi. Washe garin ranan da Aunty Jainaba zata tafi, da safe Batuul ta sauk'o, wainar fulawa kawai takejin ci tunda asuba, tana kitchen tana y'an aike aikenta taji su Ajiddeh sun sauk'o, bata bi ta kansu ba ta tab'e baki taci gaba da aikinta, zama sukayi a parlour suna cin abincin da sukayi ordering, a guje sukaga Batuul ta fito toshe da bakinta, bata bar parlour ta tsuguna ta dinga kwarara amai a wajen, da ido suka kalli juna, Aunty Jainaba ta xaro ido tayi kasa da murya tace "Keh anya wannan shegiyar yarinyar ba ciki gareta ba kuwa, kullum sai tayi amai, toh na menene?", Ajiddeh dake ta kallon Batuul ita ma murya can kasa tace "Ai ni so nake ma hakan ya kasance ta tattara ta barmin gida, nasan in har ya tabbatar cikine toh ba yadda za ayi ta zauna, maidata gidansu zaiyi, ya Allah ka tabbatar da hakan", dai dai nan Abutturab ya sauk'o don shima ya ji k'ak'arin aman nata, da sauri ya k'araso ya d'agota ya rungume yana k'iran sunanta, suna ganinshi suka mik'e, gaba d'ayansu sai da zuciyarsu ta doka ganin yadda ya rungumeta, ita kam Ajiddeh ma sai gani tayi sun mata kama, Aunty Jainaba ce ta wayance da cewa "yi sauri ki mik'a mata ruwan Ajiddeh, sannu kinji", Batuul kam bata ma san mey suke cewa ba, haka shi ma don duk hankalinsa ya tashi ganin yanda take aman, k'arasawa wajensu Aunty Jainaba tayi damuwa dauke fuskarta kamar gaske tace "Aliyu bai kamata a barta haka tana ta ciwo ba a gida, akai ta asibiti dan aman nan nata yayi yawa, kar aje ba a saniba wani ciwon ne yake damunta har yayi mata illa, ku kaita asibiti yanzu gskya, dubi yanda duk ta galabaita" sai da ya tabbatar ta gama aman snn ya d'auketayayi sama da ita, Ajiddeh ta bi su da harara xuciyarta na tafarfasa, jikinta ya gyara mata ya canja mata kaya snn ya sauk'o da ita, numfashi kawai take mayarwa duk jikinta yayi laushi, David ne ya shigo daidai lokacin, Abu ya kalli Ajiddeh yace "Tunda ga david ku tafi airport kawae ni xan kai ta asibiti" caraf Jainaba ta anshe tace "Kai haba mu tafi asibitin gaba daya kawae Aliyu babu komai" yace "Xa ki iya missing flight kuma, kawae ku je bbu damuwa" bata so haka ba amma bbu yanda ta iya tace "toh shikenan, bari muje in d'auko kayana, Allah ya kara miki lafiya y'ar nan" ta ja hannun Ajiddeh sukayi sama, suna shiga d'aki tace "kina jina, kada ki sake ki wani bini airport, kije asibitin ayi komai kan idonki, sai muga ta fad'i, shegiyar yarinya mai kama da y'an Ethiopia ni na tabbata ba komai bane wannan banda ciki, ni kaina yanzu tsanarta k'aruwa yakeyi a raina wllh", Ajiddeh tace "toh", suka janyo akwatin suka sauk'o, inda tayi aman ya gama gyarawa snn ya koma ya d'auki Batuul d'in zasu fita, daidai nan suka sauk'o, har ranta takejin yadda ya rungume Batuul a jikinshi, danne zuciyarta tayi tace "Baby kaga why not mu tafi tare, kaga jikinta is very critical, you might need help, I will go with you, Anty xata tafi airport din ita kadai, she will understand", kallonta yayi yace "No ki tafi Airport din da ita its okay I will manage", Aunty Jainaba ce tace "Ah ah Aliyu ba komai ai, ba sai ta bini ba, ga mara lafiya nan, ita tafi buk'atarta ai, kuje kawai, Allah ya bata lafiya" ganin suna b'ata mishi lokaci kawai ya d'auki Batuul yacewa Jainaba, "Allah ya kiyaye hanya ya fita", Jainaba tace "maxa Bishi", da sauri Ajiddeh ta bishi ta shiga gaban mota, badan yaso ta bishi ba, a baya ya kwantar da Batuul snn ya dawo gaba ya seta rear mirror d'inshi daidai yadda zaina monitoring d'inta, motar su Jainaba ce ta fara fita sai nasu daga baya, kowa yayi nasa hanyan, suna isa asibitin ko reception bai tsaya an duba mishi file ba ya shiga office d'in doctor d'inshi kai tsaye, Ajiddeh ma jiki na rawa tazo zata kutsa kai cikin office d'in ya kalleta rai a had'e yace "stay outside, ki tsaya daga waje, bbu amfanin shigan ki", ba dan taso ba haka ta koma daga baya ta zauna kan d'aya daga cikin kujerun wajen rai b'ace, da sauri likitan ya taso ya karb'eta suka kwantar da ita kan gadon office d'in, gaba d'aya abin nan da akeyi batasani ba dan bacci takeyi abinta tun mota, hannu kawai Abu ya kalmashe sai rocking yake kan kujera yana ganin likitan na aikinshi cikeda k'warewa, saida ya ya gama gwaje gwajensa sannan ya dawo ya zauna kan kujera, Hannu ya mik'a mishi da murmushi a fuskanshi yace "congratulations, you are going to be a Father, your wife is one month and few days pregnant", gaba d'aya jin maganar yayi wani iri, ya kasa daina kallon likitan, he wasn't expecting it, Batuul is pregnant?, bai janye hannunshi ba har saida likitan ya janye nashi snn yayi maza ya janye hannunshi, ganin irin kallon da likitan ke mishi yyi saurin k'irk'iro murmurshi, take ya nunawa likitan yaji dad'i sosai, a kanshi kuwa Ajiddeh yake hangowa idan taji wannan lbrin da yake ji, likitan ne ya katse mishi tunani tareda prescribing mata magunguna da advises kan abinda zata riqaci, da kuma wad'anda are not good to her health, ita dai har lokacin baccinta takeyi, mik'ewa likitan yayi zai bar office d'in yace "Mr Kyaree, I will be right back" a hankali ya mik'e ya isa bakin gadon yana kallonta ko kiftawa bai yi, likitan na fita a bakin k'ofa ya kusa cin karo da Ajiddeh, da sauri ta koma baya tana yak'e, murmushi yayi mata yayi gaba abinshi, a guje ta biyo bayanshi da damuwa kamar gaske fuskarta tace "Excuse me doctor" juyowa yayi yana kallonta, tace "Hope she will be okay, I don't want anything to happen to her, she is my only Sister, tell me what is wrong with her Doc", murmushi yayi yana girgiza mata kai yace "Yeah she is okay, she will b fine surely, congratulation your sister is pregnant", kwalalo ido tayi waje da dafe k'irji tace "What?", ganin irin kallon da yake mata yasa tayi maza ta kirkiro murmushi tace "Omg, Am happy, Thank you sooo much Doctor", ya mayar mata da murmushin yace "you are welcome" ya juya ya tafi, wani irin farin ciki da ta dad'e bataji irinshi bane taji yana ratsa ta, tana zama ta k'ira Aunty Jainaba dake airport ta sanar da ita komai, Anty junaiba tace "Wayyo ni da ban tafi yau ba" nan dai sukayi ta murnan k'arshen zaman Batuul gidan yazo karshe cikin ruwan sanyi tunda cikin shege ke jikinta, Abutturab kam jikinshi duk yayi sanyi, daidai kanta ya tsaya yana kare mata kallo, yasan yana da son yara, yanada burin ganin yayanshi amma bai taba sa damuwa ranshi ba na Ajiddeh bata haihu ba, tunda yasan Allah ke badawa a lokacin da ya dace but with Batuul, its totally out of it, yana d'aura ido kan cute face d'inta yaji wani courage yazo mishi na son ganin babyn da Batuul zata haifa mishi, wani abu da bai tab'a ji bane yau ke mishi yawo gaba d'aya jikinshi, d'an murmushi ya saki ya d'an sunkuya yayi kissing y'an cute lips d'inta da bai iya resisting, cak ya d'auketa ya rungemata tsam jikinshi yana jin abin nan na mishi yawo a jiki, barin office din yayi yana rike da ita ya fito, a zaune ya tadda Ajiddeh tana waya da sauri ta katse ganinsu, kamar ta samu wuk'a ta cakawa Batuul takeji amma ai k'arshen zamanta ma yazo, fuskarta d'auke da murmurshi ko tambayarshi abinda ke damun Batuul batayi ba sai murmushinta takeyi, shima d'in baice mata komai ba, kallonta yayi yace "muje", tasa kai gaba suka tafi, ganin gaba d'aya mood d'insa ya canja a ranta sai cewa takeyi, "wato so yake ya rufa mata asiri ko, toh ai ta Allah ba taku ba, Allah ya toni asirinta yau", mota ya bud'e ya kwantar da Batuul ya gyara mata kwanciyar kallonsa take tana lullumshe ido sbda irin baccin da take ji, ya zaga ya shiga ya tada suka fita, suna isa gida Ajiddeh ce ta fara fita daga motan ta shige cikin gida ya bi ta da kallo, da sauri ta haura sama ta shige d'akin Batuul ta shiga fiffido mata akwatinanta, kafin su Abu su shigo har ta sauk'o downstairs dasu, yana rike da hannun Batuul suka shigo parlon, da mamaki duk suka tsaya kallon ikon Allah, shewa ta saki tana tafa hannaye tace "In kana tunanin ni xa ayi ma wasa da hankali kayi karya Aliyu, don zaman karuwan nan ya k'are gidan nan," ta juya tana kallon Batuul tace "Munafuka algunguma, ashe karuwanci kike yi dama, toh yau Allah ya toni asirinki, iskanci ba a gidana za ayishi ba dan ban gada ba, a tafi can inda aka saba aci gaba dayi, Dan ni dai kam ban zama da mai cikin shege a gidana", kallonta kawai Abu yake da mugun mamaki don baisan ya akayi ta sani ba, Batuul kam d'aurewa kanta yayi ga jirin da ke d'ibarta, Jiki na rawa Ajiddeh tayo kanta ta fizgota da kargi tayi k'ofa da ita ta hankad'ata waje tana hakki tace "k'arshen karuwanci dai yau ya k'are gidana, aje gaba aci gaba daga inda aka tsaya," da sauri Abu ya k'araso ya d'ago Batuul duk ya gama rud'ewa ya shiga dubata ko taji ciwo, ita ko banda kuka babu abinda take, ganin komai normal babu abinda ya sameta ya mik'e, cikin zafin rai ya fixgo Ajiddeh ya wanka mata lafiyayyun mari har biyu ta both sides, ya shaketa cikin tsawa yace "kika kuskura ki sake tab'ata ko kika yi gigin k'iranta da karuwa sai na hallaka ki wllh, don matsayinta d'aya yake da naki a gidan nan" ranshine ya dad'a baci cikin kaushin murya yana mata wani irin kallo yace "Let me tell you what you don't know jiddah, kamar yadda kike matata a gidan nan, toh haka Batuul ma take matata ta sunna, snn cikin dake jikinta ba na kowa bane, nawane", yana kai wa nan ya Kama Batuul da komai ya tsaya mata yayi sama da ita, nan yabar Aunty Ajiddeh da numfashinta ke neman barin jikinta, idanunta sun firfito. Take a minute of silence and pray 🙇 for Burma, (our Muslim brother and Sisters) Ya Allah, Dan sunayenka kyawawa, Dan tsarkin mulkinka ya Zul jalali wal Ikram, Ya Allah ka kawowa bayinka sassauci cikin al'amarinsu, ka gafartawa wadanda magabatanmu, wad'anda suke raye Ya Allah ka kubutar dasu daga sharrin masharranta, Allah ka kawo musu Agaji Ya Rabbal Alamin.Amin Hey to everyone reading Batuul, zaku jini shiru kwana biyu, abubuwane suka min yawa snn ga Exams da zan fara next week (Allah ya bamu sa'a), am not promising you guys update all the time, but In sha Allah I will try my best inga nayi muku update whenever I get d chance, and I thank you all for your prayers, naji dadi sosai gaskiya, Allah yasa mudace 💖💝BATUUL💖💝 73 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Sulalewa kasa tayi wasu hawaye masu d'umi na bin kuncinta bayan tayi recover daga shock din da ta tafi na kusan minti goma, ta kai minti ashirin xaune nan gun ta kasa motsi, so take kawai taji wani yace mata a mafarki take jin duk abin nan da ya faru a while a ago, kuka ta fashe da da karfi, wanda hakan ya tabbatar mata ba mafarki takeyi ba, komai a zahiri yake faruwa, ba gizo kunnenta ke mata, sai a lokacin taji zuciyanta na bugawa kamar mai shirin fitowa, a hankali ta shiga girgiza kai tana tariyo duk abinda ya faru kanta, yanzu duk wannan abinda Abu ya fad'a mata duk gaske ne, Batuul matar Abu ce, ji tayi zuciyarta na shirin fitowa don wani irin bugu yakeyi da ya tsorata ta, a hankali ta kai hannu kan fuskarta ta shafo hawayen dake ta kwaranya ba tareda ta shirya fitowansu ba, maganganun Abuturrab ne ya rik'a dawowa a hankali yana mata yawo kwakwalwarta "kika kuskura ki sake tab'ata ko kika yi gigin k'iranta da karuwa sai na hallaka ki wllh, don matsayinta d'aya yake da naki a gidan nan, "Let me tell you what you don't know jiddah, kamar yadda kike matata a gidan nan, toh haka Batuul ma take matata ta sunna, snn cikin dake jikinta ba na kowa bane, nawane" wani irin ihu ta saki tana toshe kunnuwanta ta fad'a k'asa tana rik'e da kanta tana birgima kamar wata yarinya, gaba d'aya ta fita hayyacinta sai ihu takeyi, abunka da farar fata har ta canja kamanni tayi jajir, tun ranar da ta fara ganin Batuul a gun graduation d'insu har aka sashi yin pictures da ita kawae ke tariyo mata, ranan dinner d'insu da ya d'aukota a motarshi, ranan da ya dawo mata da Batuul gida wai karatu tazoyi har yau da ya bud'i baki yake ce mata Batuul matarsace kuma shi keda cikin jikinta, wani abune taji ya tokare mata mak'oshi ta rintse ido ta bud'e jikinta ya dau rawa, wani kara ta kuma saki tace "Inaaaa, Bazai yiwu ba wlhy, zakuyi dana sanin rainamin hankali da kukayi daga ku har iyayenku, bakusan wacece Ajiddeh ba, Aliyu sai na sa kayi dana sanin cin amanata da kayi wlhy, ita kuma tsinanniyar nan wlhy na rantse sai ta d'and'ani azaba da zata gwammace gara ta mutu da ita snn in aikata Lahira da ita da shegen dake cikinta, wlhy sai nasa na Lahira ya fiki jin dad'i, da haka ta mik'e ta haura sama da k'yar dan ji take zuciyarta kamar zata fito ga wani mugun jiri da take gani, tunda take bata taba shiga tashin hankali da rudani irin na lokacin ba. Shi kam yana haurawa sama, kan gadon d'akin da yake kwana ciki yanzu ya kwantar da Batuul da kanta yake a d'aure, gaba d'aya jiri ke damunta, idonta taf da hawaye, k'ok'arin rage mata kayan jikinta ya shiga yi, dukda bata jin k'arfin jikinta hakan bai hanata rik'e rigan ba, lumsassun idanunshi ya sauk'e kan fuskarta yace "stay still or I slap you", ture hannunshi tayi daga jikinta tace "Ni ka bari sanyi nakeji", mik'ewa yayi yaje ya kaso ACn d'akin ya dawo ya zauna kan gadon, kallonshi kawai Batuul keyi har saida yayi noticing d'in kallon ya d'age girarshi d'aya yace "Anything", d'auke kanta tayi daga kallonshi ta rintse ido, gaba d'aya maganganun da Ajiddeh ta fad'a mata ke dawo mata yanzu, "In kana tunanin ni xa ayi ma wasa da hankali kayi karya Aliyu, don zaman karuwan nan ya k'are gidan nan, Munafuka algunguma, ashe karuwanci kike yi dama, toh yau Allah ya toni asirinki, iskanci ba a gidana za ayishi ba dan ban gada ba, a tafi can inda aka saba aci gaba dayi, Dan ni dai kam ban zama da mai cikin shege a gidana, k'arshen karuwanci dai yau ya k'are gidana, aje gaba aci gaba daga inda aka tsaya", idonta taf da hawaye take kallonshi, a hankali ta bud'e baki tace "I don't get abinda matar ka ke cewa, waye mai ciki a gidan?" jin tambayar da ta mishi yasashi juyowa yana kallonta, had'e rai yayi yace "wane cikin? were you eavesdropping?", had'e rai tayi itama ta harareshi tace "Ba ina wajen ba naji ta fad'a", had'e rai ya sakeyi yace "look! Lie down and sleep, bana son shirme", daga haka ya Shiga k'ok'arin kwantar da ita, ture hannayenshi ta shiga yi tana kokarin saukowa kan gadon tace "I have classes today, ni zan shirya in tafi" ta fad'a tana k'ok'arin sauk'a daga kan gadon, jiri ne ya d'ebeta tayi baya zata koma yayi sauri ya jawota jikinshi yana mata wani irin kallo yace "ina miki wasa ko, I will slap you if you dare move an inche daga nan", da k'arfi ta shiga janye jikinta daga nashi tace "Nikam ka kyaleni, I told you school zanje, av missed a lot", har lokacin yana rik'e da ita yace "You are going no where," kuka ta fashe mishi da tace "nikam sai naje, kuma zan fad'awa Ammah baka barin ina xuwa makaranta", kallon fuskarta yakeyi yanda hawaye ke kwaranya daya na bin d'aya har cikin ranshi yakejin kukan da takeyi, ji yakeyi kamar zaiyi affecting abinda ke cikinta, yace "not just today, daga yau baki sake fita ko ina, and dare going anywhere kiga abinda zan miki", birkice mishi tayi tana kuka ta shiga dukan k'irjinshi tana turashi ya saketa tace "I knew it dama you are always against my happiness and you will surely stop it someday, gashi yanzu ka fara da hanani zuwa school, why? What have I done to you to deserve all this, why why why me?", rintse ido yayi dan ji yakeyi ko improper motsi tayi wani abun zai sami babyn cikin dake jikinta, a hankali ya bud'e lumsassun idanunshi da har sun fara canja kala, shoulders d'inta yayi gripping firmly yana kallon face d'inta da ya jik'e da hawaye da d'an k'aramin lips d'inta da ya sake rinewa saboda kukan da takeyi, cikin husky voice d'inshi in a serious tone yace mata "Fatima you are carrying my baby, I can't risk losing my child, zaki koma school bayan kin haifa min babyna", ya sassauta muryanshi ya kamo fuskanta yace "I promise you zaki koma school kinji Fatima, for now kiyi hakuri I need to take care of my child and in kina zuwa school you will b stressed har yayi affecting babyna kuma bazan samu time d'in kula da Babyna ba, kinji", ya fad'a yana d'an kad'a kanshi yana son yayi convincing d'inta, tsit tayi tana kallonsa da mamaki fuskarta, baby kuma, which baby is he referring to, kamar yasan tunanin da take a hankali yace "Yea our baby!" Wani matsanancin kuka ta fashe da, wato ita ce me cikin da Ajiddeh ke nufi, jawota yayi ya shiga lallashinta, wani haushin shi kawae ta dinga ji a lokacin, kenan wannan aman da take tayi da bacci duk cikin ne ya jawo mata, ita da anytime sooner or later take tunanin zai maidata gida shine wai itace harda haihuwa, d'an k'aramin tsaki yaja daga ciki jim kamar ana d'ada tunxurata, yarinyar nan na birkita mishi kwakwalwa ba kadan ba, ko shirmen da Ajiddeh ta gama yi mishi bai d'aga mishi hankali ba kamar yadda kukanta ke yi ynxu, duk wani motsi nata yanzu a ranshi yakeji, rungumota yayi jikinshi sosai a kunnenta yace "Batuuul mana, its okay tell me, duk mey kikeso zanyi miki shi, I promise", har ranta taji yadda ya k'ira sunan nata, this is his first time calling her Batuul, shi baima san ya fad'i ba, a hankali ya sassauta rik'on ya d'ago hab'arta yana kallon fuskanta yace "kinji?", bata bashi amsa sai tambayar da ta jefo mishi tana shessheka tace "zaka maidani gidan Aunty in na baka babyn ka toh?", ya kai 2mins yana kallonta jin mey tace, it caught him off guard, lumshe ido yayi ya bud'e sannan yace "will that make you happy?", kai ta gyad'a mishi, yace "Fine, but for the time being xakiyi duk abinda nace, babu arguments, zaki barni in kula da Babyna dake kanki, you will do everything as I say, and then we will b best of friends, babu tsiwa kuma", da sauri ta shiga gyad'a mishi kai tace "na yadda, kuma dama ai can ni bana tsiwa", yace "That's my girl, I will do that for you", murmushi ne yayi escaping lips d'inta ta dunk'ule hannunta tare da miko mishi tace "Deal?", shima murmushin yayi ya miqo nashi hannun yace "Deal", janyota jikinshi yayi daga haka ya shiga kissing lips d'inta da suke tempting d'insa passionately Ajiddeh na shiga d'aki ta shiga k'iran Aunty Jainaba dake airport waya, kamar zatayi hauka haka ta riqa ji a ranta, abunda kawai zai kawar mata da damuwarta take nema, wani zuciyar ke raya mata kawai ta tashi taje ta shak'e Batuul d'in har sai ta bar numfashi snn ta saketa inma yaso itama a kashetan, har wayan ya gama ringing ya katse ba a d'auka ba, jefar da wayan tayi zataje yin abinda zuciyarta ke raya mata har wani rawa jikinta yake, tana kaiwa bakin k'ofa taji wayar na ringing, komawa tayi ta d'auka, Aunty Jainaba na d'auka, cikin rawan murya tace "What time jirginku zai tashi?", jin yadda muryan Ajiddeh yake yasa tace "Ke Ajiddeh, shafa min, ya aka yi da xancen cikin?", har a mak'oshinta taji ambaton cikin da Jainaba tayi bata ansa mata ba saima cemata da tayi "ki dawo ki fasa tafiyar yau, gobe zamu tafi tare", da sauri Jainaba tace "keh kuwa mai ya faru da zaki taho gobe, ki fad'amin an tabbatar muku cikin ne da ita?", ta fashe sa kuka ta xube kasa kamar yarinya tace "na shiga uku Anty, wayyo ni, matarsa ce, cikin jikinta nashine", Jainaba batasan lokacin da ta miqe ba daga zaunen da take tace "Kinada hankali kuwa?, kinsan mey kike cewa ma?, banason shirme, wannan bak'ar yarinyarce matarshi?, kamar xata shide don kuka tace "haka yace min Anty kuma baya karya, he was so serious, har marina yayi antyy" Jainaba na huci xufa na karyo mata tace "rabu da d'an abu kazan uba, karya yakeyi munafiki, asirinta kawai yakeson rufewa, amma duk sai sunci ubansu, ina komawa gida za a san yadda za ayi, ki kwantar da hankalinki zamuyi maganinsu, karya ma wllh yake maki, kar ma ki bi ta Kansu, ki maidasu kamar bakisan suna nan ba", haka tayi ta convincing Ajiddeh tana kwantar mata da hankali, ita ko sai kuka take sosae ta daura hannu a ka, har ta d'an ban tausayi. Kwantar da ita yayi jikinshi yana shafa gashin kanta, a hankali yace "Mey zakici", tace "Ni ban sani ba, Ice cream zan sha", yace "And what?", tace "toh da Burger da lasagne da .....", yace "da cream rolls da pizza da Tacos da sandwich da.....", ta d'ago kanta ta marairaice fuska tace "Ni bance ba", yayi dariya yace "But Babyna yace ai", tayi shiru ta koma ta kwanta jin ya ambaci Babynshi, ya d'agota yace "muje tare?", ta tab'e baki tace "No am not going, Farida yanzu zata dawo", sai lokacin ya tuna da zancen Farida na gidan yace "Ohhh yeah, don't mention our deal to anyone kinji?" ta gyad'a mishi kai, ya kwantar da ita ya mik'e yace "Not even Farida", tace "toh", da haka yayi pecking d'inta yace "Be right back, ki kula min da Babyna", zumb'uro mishi baki tayi batace komai ba, murmushi yayi ya juya ya fita yana jin wani irin feeling da bai tab'a experiencing ba a kanta, sae da ya fita ya tuna da wata Ajiddeh nan fa hankalinsa ya fara tashi, juyawa yayi ya koma ya sa ma kofar dakin da Batuul take key sannan ya nufi d'akin da yasan Ajiddehn take, dai dai nan ta fito daga d'akin, kallonta yayi ya d'auke kanshi kamar bai ganta ba, ita ko takowa takeyi inda yake sai dai fa hawaye ne kawai ke bin kuncinta. Hi there! Pherreeedah, av seen your msg, I really appreciate dear, Thank you soo much and to tell you, I really do like you too dear❤ , And for all those that prayed for my success, Nagode Sosai, Allah ya bar k'auna, to all those saying ban cika alk'awari ba, ina jan rai and whatever, typing is not my priority, inada abubuwan yi dayawa, but i try to keep on with you guys, sha that is how life is, you can't please anyone, Batuul is nothing without you guys, Thank you to all those that supported me💖 [10/12, 9:52 AM] naxeeba: 💖💝BATUUL💖💝 74 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Har ranshi ya dinga jin wani tausayin Ajiddeh, Sam ba ta haka yaso tasan wacece Batuul ba, yaso ya zaunar da ita yayi mata bayani yadda zata fahimta snn ya lallab'ata har ta hak'ura, shi kam yama rasa ya akayi taji zancen cikin nan dan yasan bata shigo office d'in doctor ba, toh ko lab'e takeyi har ta jiyo abunda suke fad'i, kafad'a ya d'aga alamar ita ta sani inma laben tayi, gashi gaba d'aya bayason ganin hawayen idonta dan its making him feel guilty, ji yakeyi kamar yaci amanarta da bai sanar da ita tun da wuri ba, Ajiddeh kam tsayawa kallonsa tayi ganin ya ki ce mata komai Sae ma barin wajen da yayi, zuciyanta ne taji kamar ya fito tsabar bugawan da yakeyi, shikenan yanzu ta sake tabbatar da gaskiyan al'amarin, lallai Batuul matarsa ce tunda har ya iya wuceta tana hawaye ba tare da yace mata komai ba, so take kawai taji wani ya tado ta daga wannan mugun mafarkin da takeyi amma ina bata samu hakan ba dan ba mafarki bane take, ji tayi k'afafuwanta na rawa baza su iya d'aukanta ba, da k'yar ta juya tabi bayanshi itama, zaune ta taddashi bakin gado ya dafe kanshi, zuwa tayi ta tsaya mishi aka kamar wacce ta hadi'yi tab'arya, a hankali ya d'ago kanshi yana kallonta, goge hawayen fuskarta ta shiga yi tana kallonsa a k'ek'ashe, duk wani so da tasan tana yiwa Aliyu yau ji tayi ya koma tsana lkci daya, kyan da take gani yanayi mata yau duk babushi sai tsanarsa da takeji kamar ta shakeshi, da k'yar ta iya bud'e bakinta tanajin wani abu tokare a mak'oshinta tace "Ka sallameni, ka bani takardata zan tafi gidanmu", kallonta yayi da kyau jin abinda take fad'i, hannayensa ya mik'ar zai kamo nata dasu ya zaunar da ita gefenshi tayi maza ta janye hannayenta tana mishi wani matsiyacin kallo tace "kar ka kuskura kayi gigin tab'ani, ni ba mazinaciya bace bare ka goga min najasar dake tattare dakai", ido ya rintse jin abinda Ajiddeh ke fad'a mishi, yasan koma dai menene shi yayi causing da tun farko bai sanar da ita ba, hannunta ya fizgo a karo na biyu ya zaunar da ita gefenshi, idonshi dake rikitata ya zuba mata tanajin yadda sonshi da ta dad'e tana dako da kuma tsanarshi da ya shigeta lokaci d'aya ke kokawa cikin zuciyarta, ta fashe da kuka tayi saurin d"auke idonta daga nashi dan har cikin ranta takejin kallon na piercing through her, k'ok'arin danne d'aya b'angaren zuciyarta dake son rinjiyarta akanshi tayi cikin dakewar murya ta sake ce mishi "nace maka bana auren, free me from this hell so called marriage, ai ba kaine kad'ai namiji ba a duniyan, kaje kuci gaba da zaman da kukeyi, ni dai saken....", bai bari ta k'arasa ba ya d'aura yatsunshi biyu kan lips d'inta, gaba d'aya pulses d'inta saida sukayi responding to abinda takeji gameda Aliyu amma yanzu ba shine gabanta ba, ji take komai zata iyayi kan Aliyu yanzu dan tuni tausayinshi ya fita daga ranta tun daga lokacin da ya bud'i baki ya fad'i mata matsayin Batuul, ko da rabasu da ransu ne ji takeyi zata iya a daidai wannan lokacin, matso da ita yayi kusa da shi yana kallon yadda hawaye ke zirya a fuskarta, hannu yasa ya shafe mata hawayen, kamar yayi electrocuting d'inta haka takeji jin hannunshi kan fuskarta, rintse ido tayi tana jin sabon al'amarin dake faruwa da ita a yanzu, a hankali yave "Ajiddeh open your eyes and look at me", Kin budewa tayi sai kukan da take har da shessheka, ya kuma maimaita abinda yace a karo na uku, a hankali ta bud'e rinannun idanunta ta sauk'e kanshi, cikin sanyin murya yana murxa hannunta dake cikin nasa yace "Everything happened so fast, naso fad'a miki tun farko but I don't know wat draw me aback from telling you, I....", yaja wani dogon numfashi snn yaci gaba a hankali "Just take it as our fate wife, kaddarar muce tazo da haka, bamu isa tsallake ta ba, Duk da ba haka naso ki San wacece Batuul ba, I wanted calming you, in nutsar dake da sanin who she is but yadda kikayi approaching d'inta was so stupid", ta fashe da matsanancin kuka jin abinda yake ce mata, wato dai this is real ba mafarki take ba, turasa tayi kamar mahaukaciya tace "abinda yafi stupid ma duk zaka fad'i tunda kaci amanata, ka cuce ni, ka yaudareni Aliyu, I won't forgive you for this", bai dakatar da Ita ba har saida tayi shiru yace "Hear me out Ajiddeh, its been over a year tunda mukayi aure, ban tab'a ce miki inason ki haifa min baby ba despite inaso amma nasan Allah ke badawa at d right time shiyasa ban tab'a bothering d'inki ba, get this Batuul is my wife and tana d'auke da d'ana a cikinta," kamar ya watsa mata mai mey zafi cikin ranta haka ta rik'a ji jin ya ambaci shegen dake cikin Batuul da d'anshi, shikenan tata ta sameta tana zaune wata can xata Haifa masa d'a ba Ita ba, matsowa yayi kusa da ita yaci gaba "I can't risk anything happening to my baby, Inaso ta haifamin abinda ke cikinta ko wane iri, am destined to auren Batuul, babu mai iya gujewa Destiny, there is nothing more for me to say saidai am sorry for hiding the truth from you all this while, nayi hakan ne dan kada in tada miki hankali a lokacin, I was waiting for d right to let you know of everything amma Allah yayi sai yanzu zaki sani, I promise you myself being married to Batuul bazai canza komai gameda Son da nake miki ba Ajiddeh, ki kwantar da hankalinki ki d'auketa as a sister, kinga yarinyace sosai, help in all ways you can, in kikayi min haka nasan son da kike min dagaske ne, I want to have that Baby Ajiddeh", ya k'arashe maganan tareda cupping fuskanta a tafin hannunshi, a hankali ta janye fuskarta daga rikon da yayi mata tace "Ka gama?", ta tambaya tana kallonshi a k'ek'ashe, shi da kanshi yasan he have wronged her ta kowanne b'angaren, babu matar da mijinta zaiyi aure ba tareda saninta ba har sai matar ma nada ciki snn ta Sani kuma ta yadda hankali kwance, bazai biyewa duk wani shirme da zatayi mishi ba yanzun dan yasan ranta ya gama b'aci, ta ja wani arnen tsaki tace "kai duk zamanka duniya ka tab'aji ance familyn mu mun zauna da kishiya?, toh ko tarar da ita mukayi sai ta bar mana gidan bare kuma har har tazo ita ta sameni in zauna da ita, bamai yiwuwa bane wlhy, gidanmu zan tafi, in ka tashi ka aiko min takaddar sallama ta dan ban zama da munafiki, ita waccan shegiyar da tayo shege daga waje kake ikirarin matarkace sai kayi zaman da ita amma badai ni ba" ta k'arashe tareda mik'ewa zata tafi, da sauri yasa hannu ya fizgota ta fad'o kanshi, idanun nan nashi da bata son gani su ya zuba mata, kallon da yake mata yasa ta d'auke kanta da sauri, hannu yasa ya juyo da fuskanta yace "babu saki a tsarina, nace miki am sorry for everything, ki fad'i min duk abunda kike so zan baki shi amma babu cikinku wacce ta isa tasa na rabu da d'aya, and mind you, don't try anything stupid dan duk lokacin da kikayi gigin barin gidan nan bada Sanina ba, you ain't gonna like it", kwace kanta tayi daga rikon da yayi mata ta fashe da kuka tace "munafiki mey xakayi da ya wuce wanda kamin, ai wlhy ka janyowa kanka, kwanciyar hankali ma ka rasa at this very minute, mugu kawai, sai meye in baka sakeni ba, ai ba kai kad'ai keyin auren ba, gidanka kuma sai na bar maka shi kaci uwar da zakaci da kaida karuwar taka", rintse ido yayi dan bayason losing cool d'inshi, amma yarinyar nan na d'aga mishi hankali har cikin ransa yake jin dacin sunan da take k'iran Batuul da, mik'ewa yayi bayan ya bud'e idonshi ya tashi ya bud'e side drawer d'in d'akin ya fiddo makulli yayi waje, dan yasan zamanshi d'akin zaisa yayi abinda bashi da niyya, yana fita yaja k'ofan ya kulle ta baya ya bar makullin daga jiki Yana fita ya waiga ya kalli d'akin Batuul, da hanzari ya sauk'a ya fad'a mota ya tada ya d'au hanyan Inda zaije siyowa Batuul abinda take buk'ata, cikin 15mins ya siyo komai ya dawo mota dan hankalinshi sam bai kwanta ba barin Batuul da Ajiddeh da yayi a gida tare su kad'ai dukda ya rufe musu k'ofa su biyun duka, yana parking a gida ya fito ya d'ebo wasu daga cikin ledojin yayi sama dasu, d'akin Ajiddeh ya bud'e ya lek'a yaga babu kowa cikinshi, da mamaki ya k'arasa shiga jin motsinta a toilet yasashi sauk'e ajiyar zuciya ya ajiye ledojin dake hannunshi ya fita ya sake rufe k'ofan ta baya yayi d'akin Batuul, a kwance ya tadda ta kan gadon, ajiyar zuciya ya sauk'e ganin she is fine, wani irin feeling yakeji sauk'e idonshi da yayi a kanta, duk wannan stress da damuwar da ya kwaso gun Ajiddeh ji yayi duk ta b'ace mishi, idonta a kanshi har ya k'araso cikin d'akin, kwanciya yayi bakin gadon snn yasa hannu ya jawota jikinshi, ido ta wara zata b'ara mishi baki yayi saurin d'aura d'an yatsanshi kan lips d'inta yana kallon Idonta, da sauri ta rintse su hakan da tayi yasashi yin murmushi, y'ar crop top d'in dake jikinta yasa hannunshi ciki ya d'aura hannunshi kan cikinta, da sauri ta bud'e idonta jin inda ya d'aura hannunshi, hannu tasa zata ture nashi hannun ya rik'o hannun nata da d'ayan nashi, a hankali yayi brushing lips d'inta da yasa gasp escaping lips d'inta, ta shiga k'ok'arin turashi, dariya yayi yace "Hey Babyna keh missing d'ina, am just checking on him", baki ta zumb'uro mishi ta d'auke kanta tace "Ina abincin da zanci? yunwa fa nakeji", ta k'ara turo baki ta juya mishi baya, da hanzari ya mik'e yace "Damn, I was checking ko Babyna na lafiya that I forgot kinajin yunwa, sorry let's get going", jin har ya manta da yunwar da takeji yasa hawayen dake idonta silalowa, shi dai kawae ta haifa masa yaro, hannunta ya kamo yace "muje", tace "ni baxanje ba, ba babynka yasa ka manta inajin yunwa ba, ka bashi abincin yaci ni baxan ci ba", ta koma ta kwanta, dariya ta bashi ya mik'e cak ya d'auketa, ihu ta fara mishi ya sauk'eta tana cewa "Ka sauk'eni Yaa Abu, ina zaka kaini", daidai neck pulse d'inta ya rank'wafo har tana jiyo numfashinshi da ke kalar mint na bugun fatar jikinta yace "Babyna zanje inyi feeding, just stay still before in jefar dake downstairs", aikam kamar cewa yayi taci gaba haka ta dinga wuntsila k'afa, bai bi ta kanta ba ya ya bud'e k'ofa ya fito, har saida ya bud'e mota sannan ya sata ciki ya zaga ya shiga, tana zama idonta ya fad'a kan ledojin, da sauri ta janyo ta shiga bud'ewa ta ciro ice cream d'in ta shiga sha, zama yayi da murmushin da baisan sanda yayishi ba shimfid'e a fuskanshi yana kallonta, a hankali ta juyo da lumsassun idanunta ta sauk'e kanshi, ganin kallonta yakeyi yasa ta d'an tsuke fuska ta mik'a mishi robar tace mishi "you want some?", murmushi yayi ya d'auke kanshi yace "No, kisha kayanki", ta tab'e baki itama taci gaba da shan abinta, saida ya tada motar ya fara tafiya snn ya juyo ya kalleta ganin yanda ta dage sai shan ice cream d'in takeyi yace "bad manner", da sauri ta kalleshi jin abinda yace mata ta zumb'uro baki tace "mey nayi?", mirror dake gefenta ya jawo mata ta kalli fuskanta, dariya ta fashe da ganin abinda ke fuskanta, ice cream d'in ne gaba d'aya gefen fuskanta, ta kalleshi ganin baya dariya itama ta tsaida nata tace "toh ai sune basu saka tissue ciki ba", daidai nan yayi parking k'ofar d'aya gidan nashi, robar ice cream d'in nata ya jawo ya d'auki cokalin dake ciki ya shiga goga mata a lips d'inta, tsuke fuska tayi tace "you messed my face" tasa hannu zata goge yayi maza ya rik'o hannunta ya d'age mata girarshi yace "No you look cute", ta zumb'uro baki tace "ba yanzun nan kace min bad manner bane", yace "No ai yayi miki kyau", ta sake jawo mirror tana kallon kanta ta fashe da dariya tace "kamar moustaches d'in santa ko?" shikam kallonta ya tsaya yi ganin dariyar da takeyi ya k'ira Sunanta a hankali, juyawa tayi ta kalleshi jin mey zaice, taji yace "You are cute", kallonshi takeyi ta kasa d"auke idonta kanshi, a hankali yayi leaning ya shiga kissing d'inta har saida ya lashe duk cream d'in da ya bata mata fuska, daga nan ya d'auketa cak yayi waje da ita. Suna barin gidan motar su Farida ya shigo gidan, saida tacewa David "Thank you" snn ta shigo gida, tun daga parlour take kwalawa Batuul k'ira taji shiru, kitchen ta lek'a taga bata nan, sama ta haura d'akin Batuul d'in nanma bata nan sai wayarta dake ajiye kan gado, tana fitowa d'akin taji ana bubbuga k'ofar d'akin Abu da k'arfi kamar ana shirin b'allashi, a tsorace ta k'arasa k'ofar d'akin, ganin mukullin a jiki yasa jikinta na b'ari ta kama ta bud'eshi, da k'yar ta iya sa hannu ta tura k'ofan, da mamaki ta tsaya kallon wacce ke cikin d'akin tana dukan k'ofar, wani dogon tsaki ta ja ta juya xata bar wajen, Ajiddeh da dama jira take ta fixgota da karfi tana huci tace "Uwar ki kike ma tsaki bani ba," [10/12, 9:53 AM] naxeeba: 💖💝BATUUL💖💝 75 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Wani matsiyacin kallo Farida ke bin Ajiddeh da ta tsaya tana hararanta taja tsaki tace "ke wllh kika sake gaya min maganar banxa baxa kiji da dad'i ba, ko ce miki akayi nice na rufe miki d'akin" juyawa tayi xata bar wajen ta ji Ajiddeh ta kuma damk'ota tayo cikin d'akin da ita, taga taga Farida tayi kamar zata fad'i tayi saurin regaining balance d'inta ta tsaya tana kallon Ajiddeh da mamaki tace "ke anya kanki daya kuwa, ko dai kina da tabin hankali ne" a fusace Ajiddeh tayo kanta, idon nan ya k'ank'ance dan jaraba tace "ke uwarki ke da tabin hankali ba ni ba, ni sa'ar uwarkice y'ar iskar mai kama da tsuntsaye da shegun dogayen k'afafuwanki, toh yanzun nan zanci ubanki shegiya munafuka, har ni za a ciwa mutunci a ci amanata, ku da munafukar uwar taku har kun isa ku wulakantani, ai sai nayi muku abinda duk baku zata ba, yadda kuka tozartani sai nasa kunyi kuka da idanunku, matsiyata munafukai, nafi k'arfin wulak'ancinku matsiyatan banza da wofi.....", tsabar frustration ma ta rasa tak'amai mai abinda zata fad'i sai huci take kamar karya, Farida dai kallonta ta tsaya yi baki bude dan ta tabbata yanzu cikin biyun nan da akwai d'aya inma dai tab'in hankali ko Kuma shigar aljanu, tana gyada kai tace "lallai ya Abuu na cikin masifa, ina ga tun farko bai san kina da tabin hankali ba ya auro ki, tun da ba ni na daura maki ba baxan maki addu'ar samun sauki ba sai dai ince Allah ya dauwamar da ke a haka" daga haka tayi gaba abinta ta wuce ta, cikin d'aga murya Ajiddeh tace "Uwarki ce mara hankali, Ehh Bilkisu ba, ita ce mara hankalin dan uwar....", bata k'arasa ba taji wani lafiyayyen mari har guda biyu da ya gigitata kan fuskarta, hawaye cike a idonta take kallon Farida zata tabbatar daga inda marin ya isota, Farida na huci tace "kika sake kika kuma zagina bama iyayena ba sai na zubar miki da rub'ab'b'un hak'oranki wllh, kazama kawai jahila wawiya wacce batada wayo, in shi da ya ajiyeki kin zageshi ya k'yaleki wlhy ni sai na lakad'a miki duka a cikin gidan nan kuma na daki banza tunda ke bakida hankali, kucaka dake har kin isa ki zagar min iyaye, toh koh Yaa Abun da kanshi in yana nan kika aikata haka bai hukunta ki ba toh ni a gabanshi zanyi wanda yafi haka ma, kuma aure an aura mishi d'in, keh har wata matace da za a k'ira da sunan mata in banda tsawo da kika sa a gaba kamar bishiyar dabino, in banda kaddara mey ma ya had'a Yaa Abu da auran irinki, bakida aiki sai kici ki kwanta, toh ko zaki rabe biyune dan takaici BATUUL matar Yaa Abu ce ta har abadan kuma mutu ka raba aurensu, sai dai in zaki mutu da takaici ki mutu, shasha kawai", ta watsa mata wani irin kallo ta juya taci gaba da tafiyarta, Ajiddeh dake tsaye kamar statue ji tayi zuciyarta na neman rabewa tsabar bakin cikin da ya taru ya mata yawa, wai har Farida ce zata mareta,wani irin k'arfi ne taji yazo mata, tsalle ta daka ta cakumo Farida da har ta kai k'ofa tayi baya da ita, Rai b'ace Faridan ke kallonta tace "ke wllh darajar auren Yayana dake kanki kike ci wlhy da kuma tarbiyar da aka min a gida inba haka ba yanzun nan sai na nuna miki k'aramin hauka kikeyi jahila kawai, cika ni", ta turata ta juya zata tafi Ajiddeh tayi wani kukan kura ta kuma cakumo Farida tace "Dan uwarki yau zakiga k'arshen rashin hankali" gaba d'aya ran Farida ya gama b'aci da wannan rashin hankalin na Ajiddeh, in ba tayi dagaske ba baza ta shafa mata lafiya ba, matsowa tayi dab da ita ta ta k'ara mata wasu lafiyayyun marin da suka fi na d'azu girgizata, a harzuk'e ta shiga dukanta ta ko ina kamar ta kama y'arta, Ajiddeh kam baki ya rufuwa sai ihu take tana cewa "dan uwarki dani kike , sai kin barmin gida tunda ba na ubanki bane shegiya gantalalla", sai da farida ta likid'eta iya son ranta ta nanata da k'asa, banda ihu da tsine tsine babu abinda Ajiddeh keyi bakinta na jini, Farida na huci tace "dama a cike nake dake, gobe ki kuma zagar min iyaye kuma ke in gidan na naki uban ne sai ki koreni", daga haka ta fice daga d'akin, Ajiddeh in banda kuka ta kasa yin komai, ko tashi ta sake cakumo Faridar bata sake yunk'urin yi ba. Abuturrab Bai direta a ko ina ba sai kan gado bayan sun shigo ya haura sama da ita, ita kam sai kallonshi takeyi idanunta na lumshewa dan bacci takeji, fita yayi ya dawo da ledan abincin dake mota, da mamaki ya tsaya kallonta ganin har ta fara bacci, k'arasowa yayi ciki ya ajiye ledan abincin daga k'asa ya hau kan gadon ya d'agota, a hankali ta bud'e lumsassun idanunta ta kalleshi, sulalewa tayi da muryar bacci tace "bacci zanyi" ta koma zata kwanta yayi saurin rik'ota yace "Eat before you sleep", ta zumb'uro mishi baki tace "Na k'oshi ni, bana jin yunwa", tanayi tana lumshe ido, had'e rai yayi yace "cmon kin tashi kinci anbinci kokuwa?, da kikaci mene d'inne kika k'oshi?", bata bud'e ido ba ta bashi amsa tace "ba nasha ice cream ba", d'an tsaki yaja ya d'agota ya d'aurata kan cinyarshi ya janyo ledan ya shiga d'ebo abincin yana bata a baki, da k'yar ya samu taci kad'an tace mishi ta koshi, badan ya so ba ya bar bata abincin hakanan, kayan jikinta ya shiga k'ok'arin cire mata, da sauri ta tashi zaune ta wara ido tana kallon abinda yake son yi, kallonta shima d'in yakeyi yace "Meye, har kin gama baccin?" ta gyara zamanta tace "bafa bacci nakeji ba dama", bai kulata ba yaci gaba da cire mata kayan snn yace "wanka zanyi miki, yau duk bakiyi wanka ba, I want my baby to stay clean", ta tsuke baki jin yace babynshi tace "ni banyin wankan kuma sai anjima" baibi ta kanta ba ya cire duka kayan dake jikinta sai nonnokewa takeyi wai ita kunya ya rage daga ita sai inner wears ya janyo towel ya d'aura mata, cak ya d'auketa yayi hanyan toilet da ita, sai da yaje bakin toilet ganin dagaske yake tayi maza ta sauk'o daga jikinshi, har cikin ranshi yaji wannan wuntsilawar da tayi yayi saurin rik'ota ya had'e rai yace "kinada hankali kuwa, bakisan da Babyna a jikinki ba, I will slap you next time you try this shit", zumb'uro mishi baki tayi tace "Toh zanyi wankan da kaina nace", tsaki yaja ya kamo hannunta suka shiga toilet d'in, tana nan tsaye har lokacin yana rik'e da hannunta d'aya ya had'a mata ruwan wanka a bathtub, ya juyo zai cire mata towel d'in tayi maza ta riqe da k'arfi tayi raurau da ido tace "Dan Allah mana Yaa Abu, zanyi da kaina nace", kallonta kawai yakeyi ganin yadda tayi maganan har idonta ya cicciko ya janye hannunshi a hankali yana kallonta yace "be careful", ajiyar zuciya ta sauk'e ya janye mata curtain d'in yaje ya zauna daga gefe yana jiran ta gama bata fi 8mins ta fito daga cikin abin wankan d'aure da towel d'inta, da sauri ya mik'e ya d'auketa cak yayi waje da ita, kan vanity chair ya ajiyeta, itakam sai mamakinshi takeyi gaba d'aya ganin ya janyo wani d'an box ya fidda hand dryer a ciki, wai Yaa Abu ke yin duka wad'annan abubuwan, wani part d'in zuciyarta kam dad'in abinda ya ke mata ta dinga ji, a hankali ya shiga drying gashin kamar mai tsoron tab'awa, itakam Batuul har wani lumshe ido takeyi dan jin dad'i, sai da ya gama drying ya d'auko man gashinshi ya shiga shafa mata su yayi parking mata gashinta, dariya yadda yayi parking gashin ya bata, murmushin shima yayi, yana gamawa ya shafa mata nashi man jikin ya fesa mata cool turarukanshi, tana zaune ya bud'e wardrobe d'inshi ya fiddo wata shirt d'insa blue mai dogon hannu da boxer d'inshi shima blue and black sabbi duka ya mik'a mata, shi da kanshi mamakin kanshi yakeyi kan abinda yake aikatawa, he never tot he will b doing abubuwan nan for a lady, wara mishi ido tayi tace "Na meye?" Yace "Wear them, ko kinada kayan da zaki sa ne a nan?", da sauri ta kad'a mishi kai tace "Yeah akwai su a wancan d'akin", shi sam yama manta dasu baki d'aya, yace "Yeah I know, I want you to wear these", ta marairaice mishi zatayi magana ya rik'ota zai janye mata towel d'in ta fasa ihu ta riqe tace "Ai zan saka", mik'a mata yayi ta karb'a a sanyaye tace "toh nikam ka rufe idonka", dariya ta bashi yace "in karb'a in saka miki kenan?", da sauri ta girgiza mishi kai, da murmushi a fuskanshi yace "Then wear them", kamar zatayi kuka ta shiga b'are boxer daga cikin leda, shi ya karb'a ya bud'e mata su ya mik'o, da sauri ta juya zatayi toilet a guje yayi maza ya fizgota, had'e rai yayi yace "ban hanaki tsalle ba", ta marairaice tace "toh bazan sake ba", ganin ya tsareta da ido ta fara saka kayan shiko sai mugun smirking yakeyi, baisan lokacin da ya furta "Wow" ba bayan ta gama saka kayan, itakam kasa d'ago kanta tayi ganin y'ar rigar iya cinya, takowa yayi yazo gabanta ya d'ago hab'arta yana kallonta, daidai fuskarta ya sunkuyo yace "You look cute", itakam kasa d'agowa tayi ta kalleshi sai ji tayi ya d'agata yayi gado da ita, a jikinshi ya kwantar da ita ya warware gashin da ya tufke da kanshi ya shiga kwantar mata da gashinta, a hankali ya rad'a mata a kunne "kiyi baccinki", kamar ya sani kuwa bacci ne ke fizgarta, kamin yace komai har tayi bacci a jikinshi, ido ya tsura mata yana kallon tiny figure d'inta dake kwance, ita komai nata k'arami ne, a hankali ya sako hannunshi ta cikin rigarta yana shafa cikinta da yake a shafe tareda lumshe ido yana jin wani exceptional feeling na daban da bai tab'a experiencing ba, da sauri ya d'an d'age rigar yana kallon flat tummy d'inta, wai wannan cikin ne yanzu mutum xai fito a ciki, murmushine yayi escaping lips d'inshi, a hankali ya d'aura lips d'inshi kan cikin nata yayi kissing yace "Fatima can't wait to see our baby, I will love her till my last breath", da sauri ya d'ago kanshi jin yace her, wa yace mishi mace zata haifa, kai ya kad'a yana murmushi yace "I want a baby girl Fatima, just like you", ya kalli Face d'in Batuul dake kwance tana baccinta peacefully ya d'aura yatsunshi kan face d'in nata yace "Including your cute lips Baby", Batuul dai baccinta takeyi bata ma san mey yakeyi ba, a hankali ya gyara zamanshi ya gyara mata kwanciyarta dan taji dad'in Baccin nata, wayanshi ne yaji ya fara ringing amma sabida baccin da ta fara yanzu baya son ya katse mata shi, k'iran na katsewa wani na shigowa, haka aka dingayi mishi har wajen missed calls 8, ganin anqi dena k'iran yasashi jan d'an tsaki ya kwantar da Batuul a hankali ya mik'e ya isa gaban vanity table d'in ya d'auki wayan A bangaren Ajiddeh kuwa kuka ta dinga risga kamar an aiko mata lbrn mutuwa, ganin kukan ba taimakonta zaiyi ba ta d'auko waya ta shiga neman layin Aliyu, har ya gama ringing bai d'auka ba, bata dena k'iran ba har saida taji an d'auka snn ta fashe mishi da wani matsanancin kuka tareda sakin wani razananne k'ara da ya sashi rintse ido, kuka takeyi sosai ta shiga koro mishi jawabin k'arya da gaskiyan abinda ya had'ata da Farida kuma yazo ya fita da Farida inba haka ba zata bar mishi gidanshi, shi yasan Farida bataji amma bai tab'a kawowa har zata iya yiwa Ajiddeh duka ba, ce mata yayi gashi nan zuwa, kan gadon ya koma yana tunanin barin Batuul ita kad'ai a gidan, gaban desk top d'inshi yaje yayi activating CCTV snn yayi securing gidan, pecking d"inta yayi snn ya fita ya bar gidan, cikin minti kad'an ya isa gida, kai tsaye d'akin Ajiddeh ya isa ya tarar da ita xaune kan gado sai kuka takeyi duk bakinta ya kumbura, nan taci gaba da shirgo mishi k'arya da gaskiya, ba karamin baci ransa yayi ba ya shiga rarrashinta, ganin yadda ranshi ke b'ace ta fara murnan zai yiwa Farida koran kare a gidan, da murna ta biyo bayanshi, k'ofan d'akin Batuul ya tura, Farida na kwance kan gado tana playing Word Crush a wayar Batuul, mik'ewa tayi xaune tana kallonsu duk da yanda gabanta ke faduwa ganin yanayin fuskanshi hakan bai hanata daure fuska ba, ta mike tsaye tace "Yaa Abu tun d'azu fa na dawo ina ta nemanku, ina Besty na take itama bata nan", ta shiga lek'a bayanshi ko zata hango Batuul, sai lokacin ma Ajiddeh tasan Batuul bata gidan ashe, fizgota yayi yace "in the next 5 mins ki tabbatar kin gama tattara kayanki you are going back home", ganin murmushi shimfid'e fuskan Ajiddeh ta had'a rai tayi kamar bataji mey yace ba tace "Yaa Abu kace ta bamu waje zanyi maka magana, bana son gayyar sa ido", wani tsawa yayi mata yace "Ba magana na miki ba?", had'e rai tayi tace "Toh Yaaa Abu mana, nifa hutuna bai k'are ba kuma ni ba wajenku nazo....", wani tsawan da ya daka mata yasa ta razana ta kasa k'arasa maganan, tace "Yaa Abu ni gun Batuul Ammah ta siyamin ticket nazo fa", gnin yana yiwowa kanta yasa ta fasa ihu ta isa wardrobe ta shiga had'a y'an kayanta, Ajiddeh duk da tana murna amma ba haka taso ba, taso ya rama mata dukan da Farida tayi mata yayi mata korar kare, suna tsaye Farida ta shiga had'a kayanta tana hawaye har ta gama tazo ta tsaya gabanshi tace "Toh ina Batuul d'in, mu jira ta dawo sai in tafi", bai kulata ba ya kamo hannunta ya shiga janta har suka sauk'o k'asa, Ajiddeh kam hakan ba k'aramin dad'i yayi mata ba dan dama so take a barta daga ita sai Batuul a gidan, har k'asa ta biyosu tana yiwa Farida habaici, itakam ko kallo bata isheta ba, suna shiga mota ya tada suka tafi. [10/12, 9:53 AM] naxeeba: 💖💝BATUUL💖💝 76 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Har jirginsu Aunty Jainaba ya sauk'a Nigeria hankalinta yaqi kwanciya kan abinda Ajiddeh ta fad'a mata, inko gaskiya ne ai da sun kad'e dan kishiya ba abar so bace ko cikin mafarki, bazai ma yiwu bane, Aliyu ya raina musu hankali, amma koma menene zasuyi maganinshi maci amana kawai, so take kawai ta isa gida ta fesawa Mummy lbrn cin amanan da d'an matsiyatan nan yayi musu, Dan ba Ajiddeh kad'ai yayiwa ba, ko jiran driver batayi ba ta tari Taxi tayi hanyar gida, suna isa tacewa driver taxi ya jirata a kawo mishi kud'inshi ta shige cikin gida jikinta sai b'ari yakeyi kamar ita aka yiwa kishiyar, a hakimce ta tadda Mum d'in Ajiddeh zaune a parlour, da mamaki Mum ke duban Jainaba da ta fad'o cikin d'akin ko sallama babu tace "Keh kuma daga ina haka kamar ana tunkud'oki, mey ya faru kika dawo da wuri haka keda zakiyi har sati biyu", waje ta nema ta zauna jiki na b'ari, Mummy ta gyara zama tace "Keh ko lafiya haka, Ya Ajiddehn take?", gumin da takeyi ta goge snn ta shiga korowa Mummy bayanin duk abinda ya faru tun zuwanta har zuwa zancen cikin dake jikin Batuul da kuma abinda Ajiddeh ta fad'a mata kan cewa Batuul matar Aliyu ce, wani irin zabura Mummy tayi daga kan kujerar da take zaune ta dafe k'irji tana rafka salati tareda cire d'ankwalin kanta da ya bayyana gashin kanta mai tsawo da shek'i tana fifita dashi dan wani irin zafi takeji duk da Acn dake aiki, tace "Jainaba bana son zancen banza, wane Aliyun ne yayi aure?, ba dai na Hawwa ta ba, ina ba Aliyun Ajiddeh bane ya k'ara aure" Jainaba dake zaune ta mik'e tace "Shi d'in ne kuma ma dan wulak'anci irin nasa har ciki ke gareta yanzun, wannan tsinanniyar yarinyar wai itace matarsa duk ba a sani ba", Cikin d"aki Mummy ta shiga sai gata rik'e da gyale da jaka tana ta sababi tace "Ni Bilkisu zata wulak'anta, duk burin da naci kan Ajiddeh? Su da zaman lafiya saida su ga wasu nayi, shima munafikin Aliyun shine harda dukar min y'a ko?, toh duk sai sunci ubansu gabaki d'ayansu dan sai nasa sunyi kuka da idanunsu munafukai kawai, wannan ciki sai ya zama sanadin rushewar farin cikinsu baki d'ayansu, sai na nuna musu kan kishiya babu abinda bamayi, munfi k'arfin zama da ita koda tadda ta mukayi bare kuma an kawo mana ita a munafurce" ta fad'a tareda wani d'an guntun murmushin takaici ta kalli Jainaba da ta koma ta zube kan kujera tsabar gajiya tace "Yaya ina kuma zamu? Ni wlhy duk na gaji, in na huta sai mu tafi", ta watsa mata wani irin kallo tace "bakida hankali inaga, ace miki anyiwa Ajiddeh kishiya keh har lokacin hutu ke gareki?, ai in kinga mun huta to sai naga na d'agawa Bilkisu hankali itada Zuri'arta baki d'aya naga sun wulak'anta sun d'and'ani bakin cikin da suka jefa y'ata snn zaki samu damar hutawa, kan y'ay'ana biyun nan babu abinda bazanyiwa mutane ba, bare ma Ajiddeh wacce tafi komai soyuwa a gareni, duk burina yana kanta, sun jawowa kansu, maza ki tashi muje", Rai b'ace Jainaba ta mik'e da k'yar dan duk jikinta ciwo yake mata ga gajiya suka fita waje, Sadi driver na ganin Mummy ya washe baki tareda k'arasowa wajenta yace "Hajiya fita zamuyi kenan?", tace "Ehhh maza d'auko mota, Kuje zamu yanzun nan", Jainaba batace komai ba sai bin Mummy da takeyi a baya kamar wata doluwa, saida ya fita da motar bayan sun shiga sun zauna ta dubi Mummy tace "wai gun wa zamu a Kuje?" Mummy ta kad'a kai tace "wajen wani Malamin zamu mana, wannan ma yafi kowa iya aiki danshi baima San Allah ba, Matsafine sosai na bugawa ma a Jarida snn shi ba kowa yakewa aiki ba sai in kanada connection, kin dai San y'an cikin k'auyen garin Abujan nan da basu San wani Addini ba, toh gunshi zamu, Hajiya Ramatu ta dad'e da cemin zata kaini gunshi ban samu munje ba sai kwanaki ne dana rakata kuma naga aikinta ya kammalu in no time kinga har ta samu ta auri wannan Ambassador, matanshi kuma sun shiga gari yanzu daga ita sai y'ay'anta da ta kawo suke zama a can, y'ay'an mijin nata ma ta koresu kuma mijin bai isa cewa komai ba , yanzunma can d'in zamu, dan ni na tabbata banida mak'iyi kamar wanda zai tab'amin y'ay'a", a bakin gate suka tadda driver d'in taxi shida Mangal yanata mishi zuba, Sadi Aunty Jainaba tacewa ya bada kud'in motar ya ciro ya mik'a suka d'au hanyar Kuje, saida suka shiga can cikin k'auyen snn tacewa Sadi sun kawo, nan yayi parking suka fito suka isa y'ar bukkar hatsabibin bokan nasu mai suna Namurje Hawaye kawai Farida keyi dan ita Sam bata shirya tafiya ba yanzu, Abu kam driving yakeyi hankali kwance ko kallonta baiyi ba, a hankali ta bud'e baki tace "toh Yaa Abu kaga bari in k'ira Ammah in fad'a mata ina zuwa kar taga nayi dawowan baza....", wani irin kallo da ya wurga mata yasa ta saurin sunkuyar da Kai, bata sake d'agowa ba saida taji yaja ya tsaya da motar, jiki a sanyaye ta d'ago kai tanace airport suka zo, duk ranta ba dad'i batayi sallama da Batuul ba, ganin ba airport bane yasata sauk'e ajiyar zuciya tareda murmushi, fita yayi daga motan yayi gaba itakam tana nan zaune dan baice ta fito ba, saida yaje bakin k'ofar shiga yaganta zaune cikin mota ya daka mata harara yace "kin fito cikin motar nan ko sai nazo na fidda ki mara kunya", ba shiri ta fito tana zumb'uro mishi baki tabi bayanshi, numfashinta ne ya kusa d'aukewa ganin irin tsaruwar gidan, tasha ganin gidaje masu kyau ko designs d'in Yaa Abu amma wannan daban yake, ya tafi da ita ba kad'an ba, binshi kawai takeyi har suka k'arasa hawa sama ya bud'e wani d'aki ya shige ciki, bayanshi tabi itama ta shiga, Batuul ta hango kwance kan gado tana bacci hankalinta kwance, batasan lokacin da ta fasa wani ihu tana fad'in "Sweetheart ashe kina nan shine kika barni so lonely inata Nemanki....", tana yi tana nufar gadon da niyyar hawa, da hanzari ya fizgota yana mata mugun kallo yace "bakida hankali ko? Tashinta zakiyi daga baccin", ta zumb'uro mishi baki tace "toh aini ban sani ba" , yaja tsaki ya jefar da ita ya koma gaban computer da alama tunda ya fita baccinta takeyi hankali kwance, d'an murmushi yayi ya dawo bakin gadon tareda hawa yana kallon kyakyawar fuskarta, hannu yasa ya gyara mata gashinta da ya bazar tun d'azu snn ya gyara mata duvet, a hankali ta bud'e lumsassun idanunta dake cike da bacci ta sauk'esu kanshi, murmushinta mai kyau tayi mishi ta sake maida idanun ta rufesu, shima har lokacin murmushin ne a fuskanshi, Farida ikon Allah ta tsaya gani, a hankali ya sunkuya yayi kissing goshinta snn ya sauk'o daga kan gadon, Farida ya gani duk ta wara ido tana kallon Abunda yake, harara ya sakar mata yace "kallon na lafiya ne, mara kunya kawai saura ki tada ta, kuma if you try something stupid sai nayi maganinki dan yanzun ma ba k'yaleki nayi ba" daga haka ya fita, itakam yana fita ta murgud'a bakinta tace "masifaffe" tayi windown d'akin tana kallon yadda tsarin gidan mai kyau yake Mummy zaune gaban boka Namurje bayan ta gama zayyano mishi abinda ke tafe dasu tana haki, saida ya gama jin bayanansu snn ya d'ago kanshi tare da janye abunda ke kife akan nashi mai kamada hood, innalillahi wa inna illaihi rajiun, wani irin mutum ne zaune gabansu da ko kad'an bashida kyan gani, bak'i ne k'irin snn ga wani shafteten maki shimfid'e a fuskanshi, irin mazan nan ne murd'ad'u, Su Mum hankali kwance ko tsoron halittarsa basuji ba, magana ya fara da wata irin razananniyar murya yace "duk naji bayananku kuma zaku sami aiki daidai bud'ewar jakarku, Mummy tayi caraf tace "ai In kud'i ne bakada matsalarsu, ranka shi dad'e munason wannan yarinyar a fara ta kanta, ba abinda ke cikinta kad'ai za a halaka ba har itama in san samune munaso tabishi inyaso daga baya sai musan yadda za ayi da sauran matsiyatan, dan ni har iyayen yarinyar sai naso ganin bayansu tunda suma ganin bayanmu sukeson yi", ya saki wata shegiyar dariya da gama jin maganganunta yace "Aikinki ya gama, a mik'osu tukunna sai kiji kanun bayanin", jiki na rawa Mummy ta janyo jakarta ta shiga zazzage mishi mak'udan kud'in dake cikin jakar masu uban yawa, kai kace ita akayiwa kishiyar sabida yadda jikinta ke b'ari, sai da ta juye tas snn tace "gasu nan ranka shi dad'e, inma da k'ari za a biyoka dasu", baice komai ba ya d'auko wata jaka ya ciro wani abu shi ba nama ba snn ba jini ba k'ulle a leda ya mik'o mata yace "wannan abin da na baki zaki jefa cikin kogi, bazaki bud'i baki ba har sai kin gama aiwatarwa , yadda zai b'ace cikin ruwan nan haka nan cikin jikinta zai b'ace itama tabi sahu", Mummy jiki na rawa tasa hannu biyu ta amsa kamar wacce aka mik'owa abin kirki ta shiga ce mishi "Nagode ranka shi dad'e", Aunty Jainaba tace "muna nan dawowa bada dad'ewa ba", shidai baice musu komai ba har suka gama b'ab'atunsu suka fita, Aunty Jainaba tace "Yaya kinga wannan mutumin da gani bana wasa bane dan har firgitani yayi da farko", Mummy tayi murmushi tace "Ai Bilkisu da zauri'arta wasa suke dani basu san wacece Zuwaira ba har yanzun, sunana kawai sukeji", suka sa shewa gaba dukkansu biyun sukaci gaba da hiran abubuwan sharrin da zasu jefi Zuri'ar Ammah dasu har suka iso inda motar Sadi take, a firgice ya tashi daga baccin da yakeyi jin an bud'e motar ya Shiga mitsike ido yace "Hajiya ashe har an fito" basuce mishi komai ba tunawa dasukayi da gargad'in da bokansu yayi musu kawai suka fad'a mota, tab'a baki yayi ganin babu wanda ya kulashi yaja k'ofar ya tada mota suka tafi, wajen sha d'ayan dare suka iso garin Abuja, saida suka zo dab Jabi lake snn Mummy ta shiga tab'a Aunty Jainaba ta tsaida Sadi a wajen, hakan kuwa akayi yayi parking suka fito suka gama tsafe tsafensu suka dawo mota sunata murna tareda fatan samun Nasara har suka isa gida Kanshi ya kifa jikin steering motar yana tunano stress d'in da ya shiga kwanakin nan, sam hankalinshi yaqi kwanciya da barin Batuul, ga wannan sarkin y'an rawan kan tazo zata k'ara mishi akan na da, iska ya furzar bakinshi ya tada motar yayi hanyar gida yana tunanin yanda zai shawo kan Ajiddeh ya bata hak'uri, parking yayi ya fito daga mota ya shiga gidan, kamar kullum tana nan kwance idonta a kumbure, tana ganinshi ta fashe da wani kukan, yasan hakan zai faru shiyasa ya shigo a shirye, rarrashinta ya shigayi da bata baki as usual don aikin kenan kullum, itakam murna cike fal ranta jin bayanin dasu Mummy sukayi mata a waya, sai da ta gama bashi wahala snn ta sauk'o kamar ko da yaushe, daga nan suka fad'a wata duniyar, ko masallaci bai fita ba nan gida yayi Magrib da Isha itakam tana kwance har saida yayi dagaske tukunna ta tashi tayo alwala ta had'e sallolin da duk ma babu nutsuwa cikinsu, tana idarwa ta dawo jikinshi ta shiga yi mishi wasu abubuwan amma gaba d'aya hankalinshi na wajen Batuul, so yake yaje ya ganta dan yasan ba kowanne abincin takeci ba sai kayan kwad'ayi amma fir Ajiddeh taqi kyaleshi, ita ko tambayar inda ya kai ta ma bata yi. Kamar yadda yace kar ta tada ta batayi karambanin tada ta ba, k'asa ta sauk'o tana zagaye gidan tana yaba kyan da yayi mata, sai da ta gaji dan kanta ta hawo sama, bata dad'e da dawowa ba Batuul ta farka da mamaki take kallon Farida ta wara tace "Laaah yaushe kikazo, wa ya kawoki?" Farida tayi dariya tace "wannan baccin naki ai har a saceki baki sani ba, tun d'azufa kike kwance", "Wanne irin tun d'azu? Bai jima bafa da na kwanta" inji Batuul tana k'ok'arin sauk'owa, Sallah azahar ta d'auro alwala tayi daga nan suka sauk'a k'asa sukayi kitchen Farida sai santin gidan takeyi, Farida ce ta shiga had'a musu lunch Batuul kuma na zaune kan island d'in kitchen d'in, in no time Farida ta had'a musu spaghetti lasagne tanayi sunata shan hira, saida ta gama snn tayi musu serving a bowl d'aya, tana tunkaro Batuul dashi dariyar dake fuskarta ta d'auke ta toshe bakinta, Farida tace "A'a meye hakan" da k'yar ta samu ta iya bud'e baki tace "kin saka cheese bana so", da mamaki Farida ta tsaya kallonta Dan tasanta da son cheese, sabida itama ta zuba tace "Cheese d'in ne ya saki kamar zakiyi kuka?", ta bud'e baki kenan zata yi magana taji amai na yunk'uro mata, da gudu ta sauk'o tayi sama, Faridan ma a guje ta ajiye fork d'in hannunta tabita a baya tana tambayarta ko lafiya?, saida ta gama kwarara amanta a toilet snn ta d'ago a galabaice duk batada k'arfi, Farida duk ta rud'e sai hawaye take ta rasa yanda zatayi gashi ta baro wayoyinsu wancan gidan sabida tsabar masifan shi, kamo Batuul tayi daga toilet d'in ta wanke mata fuska snn suka fito, kan gado ta kwantar da Ita sai maida numfashi take, tashi tayi ta fita ta dafo mata noodles cikin lokaci kad'an, nanma Batuul turewa tayi tace batason kamshinshi, Farida duk ta damu tace "Besty wai mey ke damunki?, dama yana miki haka kuma yaushe kika zama allergic to cheese da har zai na saki amai",Batuul dai shiru tayi mata tana maida numfashi, a hankali kamar mai rad'a tace "Orange Juice zansha da Toast", da sauri Farida ta mik'e bata dad'e ba ta dawo riqe da abinda Batuul d'in ta fad'a mata, kad'an taci ta ture tace ta k'oshi, ta kwanta bacci, Farida kam kallonta kawai takeyi jikinta duk yayi sanyi, saida ta tabbatar baccin Batuul keyi sannan ta tashi ta sauk'a k'asa dan ta fara jin yunwa, sai a snn ta tuna da girkin da tayi musu, warming tayi ta tsiyayo juice tayi sama dashi, duk bayan seconds sai ta kalli Batuul ta tabbatar tana lafiya, Batuul kam Bacci takeyi sosai, lokaci lokaci takan bud'e ido suna had'a ido da Farida zata sakar mata murmushi taci gaba da baccinta abin har tsoro ya fara bawa Faridan, Har magrib Batuul bata tashi ba sai da Farida taga gari yayi duhu snn ta tada ta suyi sllh magrib, tana farkawa tace "Yaa Abu fa?, bai dawo ba?", Farida tace mata "Ehh", take mood d'inta ya canja ta had'e rai tayi toilet abinta, koda ta fito kin yin magana tayi, Farida har saida ta gaji dan kanta tayi shiru, Kallonta Farida tayi tana murmushi dan ta kasa daurewa da sudden behavior nan nata tace "uhnnm Besty ko dai Baby za a samawa Yayana ne wannan rashin lafiya haka?", kunya duk ya rufe Batuul tayi kicin kicin da fuska tace "Baby kuma, wani irin baby, Malaria nake ya kama ni", dariya maganan ya bawa Farida tace "Ko ba Malaria ba, ai 9ja muke dole kice Malaria kikeyi", bata kulata ba dan ita rashin zuwan Abu ke damunta, itama Faridan badan ta yadda ta k'yaleta ba, haka ta zama wata shiru shiru har goman dare tana tsammanin dawowanshi amma baizo ba har sha d'aya har saida Farida ta gane, shima Abu gaba d'aya hankalinshi na kan Batuul, gashi ta zama so choosy akan abinci duk hankalinshi ya tashi Washe gari da sassafe ya fito lokacin Ajiddeh na bacci ya tafi can gidan, a d'aki ya tadda Batuul kwance, kallo takeyi amma gaba d'aya hankalinta baya wajen, da k'yar ta samu bacci ya d'auketa jiyan nan, gaba d'aya haushinshi takeji, d'auke kai tayi kamar bata ganshi ba taci gaba da abinda takeyi, hawowa yayi kan gadon ya d'agata cak yace "Wannan shariyan haka kuma fa? How is my baby?, ya fad'a yana shafa cikinta daidai nan Farida ta shigo riqe da d'an tray da glass cup a kai, had'e rai tayi ta k'araso ciki tareda gaisheshi, bai amsa mata ba saima harara da ya bita dashi, zumb'uro baki tayi tacewa Batuul "Ga lemonade d'in" ta juya zata fita, kai Batuul ta kad'a mata kawai dan kunyan yadda tazo ta samesu ta ji" Farida na fita ya juyo da Batuul yace "Hey bana son wannan silent treatment d'in mana, shout and yell yafi min da wannan shirun da kikemin", kamar ba da ita yayi maganan ba ta sake d'auke Kanta, a hankali ya fara mata magana yace "Hear me out, kinga Ajiddeh ce fa batajin dad'i shiyasa ban dawo ba jiya", kuka ta fashe mishi da ta shiga turashi daga jikinta tace "ai ni lafiyar ce dani, ka koma wajenta tunda nata lafiyan yafi damunka", dariya ne ya k'ufce mishi ganowa da yayi kishi ke damunta, nan ta k'ara k'arfin kukanta, janyota yayi jikinshi ya rungume ya shiga lallashinta, da k'yar ya samu tayi shiru, sai wajen 10 d'in safe ya fita siyo mata abubuwan da ta lissafa mishi zataci ya fita ya samo mata, lokacin da ya dawo gida a parlourn k'asa ya tadda Farida zaune tana kallon Tv yace mata "Ammah tace min Monday zakiyi resuming school dan haka nanda kwana hud'u zaki koma", tace "Ehhh", har ya fara tafiya tace "Yaa Abu wayoyinmu a gidanka, dan Allah ka kawo mana, koh jiya haka Batuul tayi ta amai kuma na rasa wanda zan fad'awa dan babu waya", har ranshi yaji aman da Batuul tayi dan yasan tana wahala sosai amma yaqi nunawa ya dake yace "anqi a kawo d'in, da uban wani ne ya saki bari can?", ya haura sama ya barta nan zaune, kullum haka yakeyi da sassafe zai zo ya dubata har sai ya sata yin bacci yake komawa wajen Ajiddeh, Ajiddeh ma bata sake mishi maganan Batuul ba, ko tambayanshi Ina take batayi ba, Dan Mummy tace mata ta kwantarda hankalinta cikin kwana biyu za ayi maganin Batuul, Farida kuma ce mata yayi ta koma Nigeria. Bayan kwana uku ana gobe Farida zata koma da yamma Batuul na baccinta a d'aki ita kuma Farida na gefenta tana chatting da Affan d'inta sai murmushi takeyi abinta, a firgice Batuul ta farka tareda sakin k'ara, Farida dake gefenta ta mik'e a rude ta rik'ota tana tambayarta ko lafiya, kasa yi mata magana tayi sai riqe cikinta da tayi ta sulale k'asa tana yarfe hannu, hankali tashe Farida ta shiga neman layin Abutturab dan ko 2hrs baiyi da barin gidan ba, baccin ma da takeyi ajikinshi tayi snn ya kwantar da ita ya fita, kullum a rana yakan shigo sau biyar kuma da sassafe yake shigowa, watarana sai dai ta farka ta ganta a jikinshi, kwana ne kawai bayayi, kuka Farida ta fashe da ganin har ya katse bai d'auka ba, a karo na biyu ne da ta k'ira yana fara ringing ya d'aga, cikin kuka ta fad'a mishi abinda ke damun Batuul, bata gama ba ya katse wayan cikin tashin hankali, in few minutes ya iso kamar dama can yana area, a guje a ya hawo sama, ganin Batuul riqe da cikinta tanata murk'usu ya sake tada mishi hankali, nan ya rungumota ya shiga tambayarta mey ke damunta taqi cewa komai sai kukan da takeyi tana riqe da cikinta duk yanda yaso tyi magana batayi ba sai juye juye da takeyi, Shida Faridan duk hankalinsu tashe yake sosai, ganin sae gaba abun yakeyi duk ya rud'e, Farida daketa hawaye tayi k'arfin halin cewa Yaa Abu mu kaita asibiti Dan Allah kar wani abin ya sameta, sai lokacin tunanin Hospital ya fad'o mishi, ko second d'aya bai k'ara ba ya d'auke ta cak yayi waje da ita, mota ya sata shima ya shiga yaja motar duk hankalinsa tashe, a gurguje doctors suka karb'eta suka shiga dubata, duk iya kwarewarsu sun nuna amma basuga komai ba, haka suka hak'ura suka yi mata allurar pain reliever suka k'ara mata ruwa Dan ganin yanda taji jiki ta jigata, har ta fad'a daga d'an lokacin nan, likitocin na fita ya taso ya rungumeta yana sake tambayanta ta fad'a mishi inda ke mata ciwo, duk yanda yayi da ita k'in cewa komai tayi sai kukan da take tana juye juye, iyakar rudewa ya rude, Farida har fuskarta ya kumbura tsabar kukan da tasha, shikam ji yakeyi kamar ya cire mata ciwon ya dawo dashi jikinsa, Farida ce ta matso gaban gadon ta riqe hannunta d'aya ta shiga tofa mata addu'a a hankali, ta kusa minti sha biyar tana mata addu'a, ko Abutturab baisan abinda takeyi ba, a hankali ta fara tsaida kukan da takeyi jin ta fara samun relieve har dai tayi shiru tayi lamo jikinsa tana sauk'e numfashi, a hankali ya d'ago kanta yana kallon idonta da ya kumbura tsabar kukan da tasha, cikin sanyin Murya yace "Fatima don Allah tell me mey ke damunki, ina ke maki ciwo?", kyar ta iya bud'e baki tana nuna masa cikinta tace "cikina kemin wani iri", rungumeta yayi tsam jikinshi kamar wacce za a k'wace ya dinga rad'a mata sannu a hankali. 💖💝BATUUL💖💝 77 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Tana nan rungume jikinshi har tayi bacci, a hankali yaji numfashinta na sauk'a kad'an kad'an alamun baccin nata ya fara nauyi, ajiyar zuciya ya sauk'e amma har lokacin tana nan kwance jikinshi bai kwantar da ita ba, sai bayan 15mins snn a hankali ya d'an d'agota daga jikinshi ya kwantar da ita kan gadon, kallon k'aramin cute face d'inta ya tsaya yi yana lumshe ido, ciwon rana d'aya amma duk ta fad'a ta rame, dama can ba wani jikin bane da ita, sai haske da ta k'ara, yafi five minutes idonshi na kanta daga baya ya d'auke idanunshi ya sauk'esu kan Farida dake tsaye gefe duk tayi sanyi yace "Taci wani abune bayan na fita?", kai ta girgiza mishi a hankali tace "Babu abinda taci, ko baccin daka sa tayi ma fa bata tashi ba, kawai ina kwance naga ta mik'e ta riqe cikinta, shine tace yana mata ciwo ne", kallon Farida kawai yakeyi har tayi shiru snn yasa hannu cikin gashin kanshi masu santsi ya bajesu yace "take care I will b right back", daga haka yayi exiting d'akin, har ya dawo bacci Batuul keyi, Farida na zaune kan kujera ta jingina kai ta baya ta tsura ma Batuul idanu, tausayinta kawai take cikin ranta, ji takeyi kamar ta fasa komawan gobe ko kuma su tafi tare, motsin k'ofan da taji ne yasata duban wajen, Abuturrab ne ya shigo riqe da paper bags a hannyenshi har ya k'araso cikin d'akin snn Farida ta miqe tana mishi sannu da zuwa ta anshi kayan dake hannun nashi, zama yayi daga kan kujeran idonshi nan kan Batuul d'in, sai da Farida tace mishi sannu da zuwa yaya snn ya dubeta ba tareda ya amsa ba ya jeho mata tambayar "Ta tashi bayan na fita?", kai ta kad'a mishi tace "No! Bata tashi ba, baccinta takeyi tun d'azu" bai ce komai ba ya juya ga kallon Batuul d'in da yakeji kamar ya cire mata ciwon gaba d'ayanshi ta huta, hannunta da babu drip ya kamo cikin nashi ya rik'e gam yana jin wani feeling na circulating dukkanin nerves d'inshi, a hankali ya juyo ya dubi Faridan yace "Kinci abinci ne?", ta kad'a mishi kai alamar a'a, yace "gashi nan ki duba packs d'innan", yayi mata nuni da bags d'in da ya shigo dasu, bags d'in ta janyo ta shiga bubbud'esu, tab'e baki tayi ganin irin abincin da ya siyo musu, ita bata cika son jagwalgwalon turawa ba, daga k'arshe dai pasta with Lamb ragu da cauli flower crisp ta ciro ta ajiye gefe, kallon Abu tayi tace "Yaa Abu in ciro maka?", kamar me nazari yake kallonta snn ya girgiza mata yace "No am okay", batayi mishi musu ba ta koma kan kujera ta shiga cin abincinta, sai da ta gama tayi disposing packs d'in yace mata ta mik'o mishi ruwa, Fridge d'in d'akin ta bud'e ta mik'o mishi bottle d'aya bayan ta bud'e, har lokacin hannunshi na cikin na Batuul, yana jin yadda pulses d'inta ke kaiwa da komowa, basu fi thirty minutes ba bayan nan ta bud'e lumsassun idanunta a hankali, kanshi tafara sauk'esu, ido ya wara shima ya matso kan gadon ya d'agota sai ji tayi ya rungumeta jikinshi, ya kai minti biyu rungume da ita bata yi k'ok'arin k'wace kanta ba har saida ya saketa ya d'ago hab'arta yace "Ina ke miki ciwo yanxu Fatima?", murmushi tayi mishi kawai ta shiga k'ok'arin tashi ta zauna, da kanshi ya d'agata ta zauna yana making sure bata takura ba, ganin yanda Farida ta tsaya tsuru tana kallonta ya bawa Batuul dariya, tace "Hey what's up duk kin zama wata iri, am okay fa", murna ne ya cika Faridan tayi maza ta dawo kan gadon ta zauna, tace "Don't get sick pls, you scared d hell out ta me pls kinji?" murmushi tayi kamar ba ita ke ciwo ba d'azu snn ta kalli Abu da yake lumshe ido yana bud'esu yana kallonta ta d'an shagwab'e fuska tace "Mu tafi gida Yaa Abu, ni bana son asibitin nan", kai ya girgiza mata yace "No sai kin fad'amin mey ke damunki, baza mu tafi ba bamusan mey ke damunki ba", had'e rai tayi tace "Yaa Abu nifa na warke, mu tafi gida", ta fad'a tana k'ok'arin sauk'owa kan gadon, hannunta ya rik'o ya k'ura mata hazel brown idanunshi, cikin wani irin murya yace "Fatima mana, I want you to fully get better, bana son kina shan wahala kamar na yau, nafiso ki zama under medication, under proper care kinji?", zumb'uro mishi baki tayi tace "Toh fa na warke ni, bazan sake yin rashin lafiyan ba", Ido kawai ya zuba mata yanason ta gano abinda yake hange amma baya son stressing d'inta tunda ba isasshen lafiya bane da ita, a sanyaye yace mata "ina zaki yanzun?", ta zumb'uro mishi baki tace "toilet", da sauri Farida ta mik'e ta riqota tace muje in rakaki, kai ta kad'a tace "zanfa Iya da kaina na warke", kamar jira yake ta rufe baki ya sunkuceta yayi toilet da ita itako sai wuntsila k'afa takeyi ya sauk'eta, bai bi ta kanta ba har saida ya Isa toilet snn ya ajiyeta a hankali, d'an murgud'a mishi bakin tayi snn ta kalleshi tace "Toh ka tafi", wani irin kallon da yayi mata yasata yin shiru ta kasa motsi, ganin ta nemi waje ta tsaya yasashi k'arasawa gabanta ya shiga k'ok'arin d'age mata skirt d'inta, ihu ta fasa ta riqe skirt d'in da k'arfi tace "Bafa komai zanyi ba, alwala nakeson yi", kallonta kawai yakeyi snn ya kamata suka koma gaban hand wash basin d'in, kamar wata yarinya shi yayi mata alwalan, bags d'in da ya shigo dasu ya janyo bayan ya sata ta zauna kan gadon, pack d'aya ya Ciro mai d'auke da malted custard roast da Lamb Kebab salad, da kanshi ya bata abinci har saida tace ta k'oshi snn yace tayi sllhn shi kuma ya fita wajen doctor yayi maganan discharging d'inta, bai jima ya shigo lokacin har ta idar da sllh suna hiransu da Farida, ce musu yayi zasu tafi, murna Batuul ta shiga yi dan ta tsani asibiti ita kam, da murnarta ta shige gaba kamar ba ita aka kawo a galabaice ba, driving yakeyi amma duk bayan seconds biyar sai ya juyo ya dubeta, cikin lokaci kad'an suka isa gida lokacin ana k'iran Magrib,saida sukayi sllh snn suka kafa hira ita da Farida, ganin ya shigo d'akin yasa Farida fita, daidai tazo wuceshi yace " You should Get ready gobe flight d'in by 8 ne", sai a lokacin Batuul ta tuna da tafiyan Farida, jiki a sanyaye ta amsa da "toh", sam hankalinta bai kwanta da barin Batuul ba gashi shi bama zama yakeyi ba, cikin d'akin ya k'araso ya zauna bakin gadon yana kallon Batuul da har idonta ya cicciko yace "How you feeling now?", baki ta bud'e zatayi magana hawayen dake tare idonta ya shiga gangarowa, har ranshi ya ji zubowansu da hanzari ya gyara zamanshi kan gadon ya rungumota tareda cewa "Yasalam, Fatima what is it again?, I told you mu zauna asibitin amma kikayi insisting mu dawo gashi nan yana damunki kuma koh", ji yayi ta sake lafewa jikinshi a hankali tace "Does she have to leave tomorrow?", sai da ya tsaya for some seconds snn ya gano abinda take nufi, ajiyar zuciya ya sauk'e jin ba ciwon cikin nata bane ta d'ago kanta yace "School zata koma, dama mid semester break ta zo", a hankali ta d'ago ta dubeshi tace "toh ni yaushe zaka kaini gidan, I want to go home" muryarta na rawa ta kare maganar, rungumota ya sakeyi jikinshi yana shafa kanta yace "very soon, ko har kin manta deal d'inmune?, ba nace zan kaiki gida da kaina ba in kika haifa min baby na", d'an zumb'uro baki tayi jin ya ambaci Babyn shi ta kauda kanta, murmushi yayi tareda juyo da kan nata, idonshi kan lips d'inta yace "I like them when you pout, I miss them so much", kamin ta ankara har kai nashi lips d'in kan nata, passionately yake kissing d'inta kamar yau ya fara kissing d'in nata idonsa lumshe, haka yayita tarairayarta har wajen sha d'aya bayan yayi mata wanka ya jasu Sllh Isha ya kwantar da ita ya shiga sata bacci, a jikinshi tayi baccin wajen 11:30, saida ya tabbatar tayi nisa a baccin tukunna ya saka mata temperature d'in d'akin ya koma moderate, ya tabbatar she is fine snn ya fita, a parlourn k'asa ya tadda Farida ta kashe wutan ko ina tana kallon CBS, Ce mata yayi ta koma d'aki gun Batuul snn yayi mata sai da safe ya fita akan gobe da safe zaizo kaita airport ta zama cikin shiri, sai da ya shiga mota tukunna ya tuna da wayoyinsa, missed calls ya gani babu adadi daga mutane daban daban amma duk na Ajiddeh yafi yawa, d'an murza goshinshi yayi snn yayi igniting motar ya d'au hanyan gida, lokacin da ya isa Ajiddeh na kwance parlour tayi bacci da alama tasha kuka ba kad'an, tausayinta yaji Sosai har cikin ranshi yasan bai kyauta mata ba, kashe appliances d'in yayi snn ya dawo ya d'auketa yayi sama da ita Washegari kamar kullum da ya tashi sllh saida ya tashi Ajiddeh amma bata tashi ba, shi kam daga masallaci d'ayan gidan ya wuce, a kitchen ya taddasu su biyun duka Farida har ta shirya, k'arasowa yayi cikin kitchen d'in yana amsa gaisuwan Farida ya isa inda Batuul ke jingine jinkin Fridge, yana zuwa ya jawota jikinshi ya d'aura hannunshi kan mararta a hankali, da sauri ta d'aga ido taga ko Farida na kallonsu, ai kuwa ido hud'u sukayi da Faridan, maza tayi ta d'auke idonta cike da kunya snn ta riqe mishi hannu, rankwafowa yayi daidai wuyanta da muryan shagwab'a da ya sauqe mata kasala gaba d'aya yace "Ina duba Baby na", cike da jin kunya a hankali tace "Yaa Abu Farida fa na nan" kallon Faridan yayi, suna had'a ido ya sakar mata wani irin kallo, babu shiri ta bar abinda takeyi ta rage wutan stove d'in tayi waje da sauri, tana fita ya juyo da Batuul d'in, y'ar rigar dake jikinta ya d'age ya shiga making circles a flat tummy d'inta da yasata jin wani sabon feeling na daban na ratsata, a hankali yace mata "Meh zaki bawa Farida?", sai lokacin abin ya fad'o mata d'ago kai tace "Nima ban sani bafa, kawai zan bata kosu bracelets d'ina ko?", ta tambayeshi, murmushi yayi ya janye hannunshi cikin rigan nata ya kamota yace "muje ki gani sai ki duba ki ga In yayi a bata", babu musu ta bishi a baya suka fita waje, Farida na ganin fitansu ta koma kitchen taci gaba da abinda takeyi tana murmushi cike da jin dadin irin xaman Bestyn nata da yayanta, suna shigowa daidai nan Faridan ma ta fito riqe da bowl d'in oat a hannuta tana jujjuyashi, a nan ya bar Batuul ya haura sama, ba a jima ba ya sauko yace su wuce, cikin y'an minutes suka isa airport, sai lokacin Batuul ta dad'a tabbatar da tafiyan Farida, kamar kar su rabu harda k'wallanta, k'ok'arin fitowa ta shigayi daga motan zata raka Farida yayi maza ya rik'ota yana kallonta yace "Ina zakije haka?" , zumb'uro mishi baki tayi cike da shagwab'a tace "zan rakata mana", kai ya girgiza yace "kinada hankali zaki fita a haka ko mayafi babu?, dubi kayan dake jikinki?", kallon kanta tayi taga koh kayanta are, wandone jikinta sai jacket iya gwiwa da hood amma yake fad'a mata wai kada ta fita a haka, rai b'ace ta koma ta kwanta sai Faridan ce ta zagayo tayi hugging d'inta, dan takaici kasa magana tayi sai hawaye da ta dinga yi, shi ya d'auki jakan tsaraban ya rakata dashi yace mata inji Batuul, ya k'ara mata da kud'i masu yawa, har saida yaga ta shiga jirgi sannan ya juyo, a mota ya tadda Batuul har tayi kukanta ta gode Allah, ko sau d'aya bata kalleshi ba bayan ya dawo, haka ya k'arashi surutunshi suka isa gida, yana parking ta bud'e mota ta fita a guje, a gujen shima ya bita dan har ranshi yakejin gudun nata snn gashi ba lafiyane da ita isasshe ba, daidai takai k'afanta kan 5th stair case ya cimmata, wani razanannen k'ara ta saki da yasata durk'ushewa k'asa, binta yayi ya kamota jikinshi yana mata wani irin kallo yace "Fatima ban hanaki tsalle ba?, bakida hankali koh?, next time you try this shit I will slap you", gaba d'aya bata sanma mey yake fad'i ba sai yarfe hannu da takeyi, kuka sosai ta shiga yi tana k'iran sunan Auny tana riqe da cikinta, rud'ewa yayi ganin da gaske take ya d'agota yace "Batuul talk to me, cikin ne?", a hankali ta shiga gyad'a mishi kai a wahalce, duk ya rasa mey ma zaiyi dan duk ya rud'e, cak ya d'auketa sukayi asibiti, ikon Allah ne kawai ya kaisu lafiya dan baisan irin driving d'in da yayi ba, likitocin this time ma cikin gaggawa suka amsheta, sai kukan wahala take tana k'iran sunan Aunty, har dare likitocin na kan Batuul sun kasa gano Ina matsalar take gashi duk wani taimako da zasuyi sun mata shi amma babu wani ci gaba, Abu kam tsayawa kawai yayi yana kallonsu ya kasa cewa komai, kamar shi ke ciwon har fad'awa yayi daga yini d'aya. Sai karfe takwas da wani abu na daren bacci ya dauketa shi ma sai juye juye take, Abuturrab dake xaune gefenta ya tsura mata ido cike da tausayinta ganin yanda ta wani rame daga safen xuwa dare, mikewa yayi da kyar ya nufi office din likita, nan ya shaida ma likitan in dai cikin xai bada matsala kawai a cire sa, ficewa yayi daga office din ya nufi gida kafin ta tashi don dauko wayarsa, Ajiddeh na xaune parlor kamar ko da yaushe, yau dai sai ya gaya mata ma'anar fitar da yake da asuba ko sallama babu baxa kuma ta kara ganinsa ba sai dare, bin sa da kallo tayi ganin ko kallonta bai yi ba ya haura sama, mikewa tayi ta bi bayansa, xaune ta samesa gefen gado, da ganinsa kasan akwai matsala, ta karaso da sauri ta xauna gefensa tace "Me ya faru babe? What's wrong?" Rike kansa yayi bai ce komai ba, ta dago kansa tace "Talk to me mana, me ya faru" Da kyar ya iya bude baki yace "Batuul!" Ji tayi kamar ya soka mata mashi, lokaci daya xuciyarta ya shiga tafarfasa, ta dake tace "What about her?" Cike da confusion yace "I just don't know, tana asibiti" wani farin ciki ya lullube Ajiddeh, sai dai cike da damuwa kamar gaske tace "Ayya, Allah ya bata lafiya" mikewa yayi da kyar ya dau wayarsa xai fita, tace "plss xan bi ka muje in dubata babe" bai tanka ta ba ya fita, ta mike cike da murna ta dau hijab ta sa ta bi bayansa da sauri, har ta shiga motar bai ce mata komai ba ya tada suka kama hanyar asibitin, ba karamin tashi hankalinsa ya kuma yi ba ganin likitoci a kanta, su Ajiddeh kamar na kirki ta dinga kwantar masa da hankali wai she will be fine. Likitocin na fita ya shiga Ajiddeh na biye da shi a baya, rungumeta yayi ta kankamesa tana kiran sunansa cikin kuka, a rikice yace "Don't worry Fatima xa a cire babyn ki huta kin ji" girgixa masa kai kawai take tana kuka sosai, Ajiddeh ta xauna gefenta tana '' tana kallonta lokaci daya jikinta yayi sanyi jin ta ambaci mutuwa. [11/15, 11:14 AM] ‪+234 810 957 2036‬: 💖💝BATUUL💖💝 78 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* A hankali Ajiddeh ta shiga girgixa kai da kyar tace "No! Baxa ki mutu ba, Allah xai baki lafiya kin ji" Abuturrab da ya gama rudewa jin abinda tace ya rike hannayenta yace "Noo no baxa ki mutu ba Fatima, don't worry xa a cire babyn ki huta, bana so kuma, xa a cire soon kin ji, kar ki kuma cewa xa ki mutu plss" ko kadan Batuul bata san abinda suke cewa ba don ita kadai tasan abinda take ji a lokacin, tayi wani kara da ya kuma rudar da Abuturrab da Ajiddeh tace "Don Allah Anty ki ce ya kai ni gun Antyna nasan mutuwa xan yi, wayyo cikina" Abuturrab ya rungumeta a rikice yace "Stop this Fatima, ki daina kiran mutuwa plss" hawaye ne ya ciko idonsa yace "No! Baxa ki mutu ba wife, baxa ki mutu" Ajiddeh da duk jikinta yayi sanyi ita ma ta shiga hawayen a hankali tace "Baxa ki mutu ba, Allah xai baki lafiya" mikewa tayi da kyar ta fice daga dakin, ta tafi nesa da ward din, layin Mum dinta ta shiga kira, bugu uku aka daga, bangaren Mum tace "yauwa 'yar gari dama yanxu nake kokarin kiran ki, ya ake ciki kin ga alamar...." A sanyaye Ajiddeh ta katse ta tace "Mum kinsan me? don Allah kice a dakatar da aikin nan tukun....." Cike da mamaki Mum tace "A dakatar da aiki? Saboda me?" Da kyar Ajiddeh muryarta na rawa tace "Mum kinga fa kila mutuwa xata yi, kuma..." Sai ta fashe da kuka tace "Mum ni dai a dakata tukunna....." Wani uban ashar mum ta kunduma mata a fusace tace "Shegiya sallamammiya, kin san nawa na kashe 'yar abu kaza kaza, a dakatar da aiki??? Wani irin zagi Mum ta kuma k'undumo mata da har saida ya tsorata ta, a fusace ta diro daga kan gadon da take cikeda masifa tace "Keh kinsan mey kike cewa? to kinyi kadan Ajiddeh, a xuri'armu bbu warce ta taba zama da kishiya, baxa kuma a fara a kan 'yar cikina ba, Aliyu naki ne ke daya don ubanki, Ajiddeh cikin kuka tace "Mum nifa bance zan zauna da ita ba, kawai dai bana son ta mutune", Fusata Mummy ta sakeyi har wani gumin masifa ke tsattsafo mata a goshi, rai a b'ace tace "keh don ubanki ki fita idona kinaji, shegiyar yarinya da bata san abinda takeyi ba, zur'armu kaf babu wacce ta zauna da kishiya, mey ma za ayi da zama da kishiya, Allah bai d'aura mana ba kema kuma baki zama da ita, ita da take gantalalliyar kishiya ma har aka munafurce ki akayi komai shine kike tausayinta, indai ni haifeki kika kuma tausayin yarinyar nan sai. na tsine dan haka in zaki dawo hankalinki tun wuri ki dawo kisan inda dare yayi miki, wawiyar yarinya kawai, kina abu sai kace bani na haifeki ba, K'anwar uwarki ce yarinyar da zakice mituwa zatayi ko kuma in ta mutun asara ne dake, mutuwa kuma kamar tayi shi daga ita har shegen dake cikinta, kaji min wahalalliya mara wayo, to kin yi k'adan yanxu ma shiri nake xan koma kauyen don ba a gama aikin ba" Ajiddeh ta fashe da kuka sosai tace "Allah mum ni dai ba ruwana, kar ta je ta mutu...." Wani raxanannen tsawa Mum ta daka mata ta dinga kunduma mata zagi tace ", Ajiddeh ta katse wayar ta jingina da bango hawaye na sakko mata, da kyar ta ja kafa ta koma ward din, hankalin ta ya kuma tashi ganin halin da Batuul ke ciki, likitoci biyu a kanta, karasawa tayi da sauri ta xauna kusa da ita jin abinda take ta cewa, ta rike hannunta hawaye na sakko mata tace "Baxa ki mutu ba, sai lokacin ki yayi" Abuturrab dake xaune ya rike kai ya d'ago da kyar yana kallonsu da idanuwansa da suka kada, ya karbi wayar Ajiddeh don bai ma san inda nasa yake ba, ya fita don kira Ammah shi da likitocin xa su ji ta nasa da an cire cikin a nn take kawai amma sun ki wai sai bayan awanni idan suka gama binciken da suke, rungume Batuul Ajiddeh tayi, sai ce mata take cikinta, dubara ne ya fado ma Ajiddeh ta shiga tofa mata addu'a a hankali, Abuturrab na fita ya kira Ammah, tana d'agawa ya kasa ce mata komai, tayi sallama yayi uku kafin da kyar yace "Ammah, Batuul...." Jin muryarsa Ammah tace "Abuturrab, lafiya me ya faru" da kyar ya kuma cewa "Batuul..." Nan hankalin Ammah ya tashi ba kadan ba tace "Kayi min magana mana Aliyu, me ya samu Batuul din" k'asa bata amsa yayi hawaye na sakko masa, nan hankalin Ammah ya kuma tashi barin da taji yayi shiru kuma tasan hawaye yake shirun nan, don ita ta haifi abunta, tsawa tayi masa tace "Kana da hankali kuwa Aliyu, baxa ka fadi abinda ya samu Batuul din ba" da kyar ya bude baki yace "Bata da lafiya ne" tayi kokarin boye tashin hankalinta tace "Subhanallah! Tun yaushe?" Yace "jiya" sosai hankalinta ya tashi don tasan ba abu kadan bane Abuturrab xai ma hawaye, tace "Me ya sameta?" Ya girgixa kai bai ce komai ba, Ammah tace "ka bude baki ka min magana Aliyu, farida fa?" Da kyar ya iya cewa 'Daxu na Kai ta airport " Ammah tace "Dawo min da ita immediately" "toh" kawai ya iya ce mata ta katse wayar hankali tashe tayi part din Abui. Juyawa yayi ya koma ward din, har lokacin Batuul na jikin Ajiddeh idonta lumshe, sai dai a hankali take kukan yanxu sai ajiyar xuciya da take saukewa jin kamar an xare mata ciwon, ita ko Ajiddeh bata fasa to fa mata addu'a ba, don bata ma san Abuturrab ya shigo dakin ba, tsaye yayi jikin bango yana kallonsu hankalinsa ya d'an kwanta ganin Batuul ta nutsu, karasawa yayi gun gadon ya xauna gefensu ya kamo hannun Batuul yana kallonta, a hankali ta bude rinannun idonta tana kallonsa, Ajiddeh ma ta juya tana kallonsa, kauda kai Batuul tayi, murya can kasa tace ma Ajiddeh xata je bayi, Ajiddeh ta mike ta d'agata ya bi su da kallo har suka isa bayin, a nan bakin kofa Ajiddeh ta jira ta tafito ta kuma kama hannunta suka koma kan gadon, A hankali Abuturrab na kallon Batuul yace "Ya daina cikin?" Kai kawai ta gyada masa, ya kalli Ajiddeh yace "We are leaving for Nigeria gobe" ita ma ta gyada masa kai kawai. Wayarta ne ya shiga ring a hannunsa ya mika mata ta karba ta ga Jainaba ce, gabanta ya fadi ba kadan ba taki d'agawa ta ajiye, ta juya tana kallon Batuul da ta rufe ido har bacci ya fara daukanta ta ci gaba da mata addu'a a xuciyarta, Abuturrab ya mike ya fita, ba a dau lokaci ba ya dawo, yana kallon Ajiddeh yace "Xa a cire cikin yanxu, it's time" Ajiddeh tayi shiru tana kallonsa sai kuma tace "saboda me?" A hankali yace "She's suffering babe" girgixa masa kai tayi duk da wani abu da taji ya tokare xuciyarta tace "No! Allah xai bata lafiya a bar mata" a sanyaye yace "A'a gwara a cire mu samu rest of mind" da kyar Ajiddeh tana kokarin maida hawayenta tace "if dat's ur only child or hers a duniya fa," d'an murmushin karfin hali yayi yace "baxan iya jure ganin tana wahala haka ba, ke kya haifa min masu yawa idan Allah ya yrda" duk yanda Ajiddeh ta so convincing dinsa a bar cikin kin yarda yayi, mikewa tayi daga karshe ganin da gaske cire cikin xa ayi, ta dau wayarta ta fita, Ammah ta kira yana fara ringing ta d'aga, sama sama Ammah ta amsa gaisuwarta don tun kiran Abuturrab bata da nutsuwa barin da ta kira can Maiduguri taji ciwon Batuul har da sa hannu, Ajiddeh da ta ma rasa abinda xata ce a hankali daga karshe tace "Ammah dama wai Batuul ce ba lafiya kuma laulayi take, shine Aliyu wai a cire cikin nayi masa magana ya ki saurarata" tana maganan ne da kyar don wani tukuki take ji a xuciyarta ta rasa dalili, a dakile Ammah tace "Toh don uwarsa tunda bashi da hankali ba sai yasa a cire ba muga, wawa da shi ba xai rike addu'a ba an tasa shi da iyalinsa a gaba sai haukan banxa shi d'an boko, ni ban taba gani soko mara wayau kamar Aliyu ba, kuma yana tare da wahala in har baxai rike addu'a ba, Batuul kuma ta Allah ba ta mutane ba, bbu abinda xai sameta sai Wanda Allah ya rubuto mata, babu abinda aka isa ayi mata, ciki kuma sai ta haifesa lafiya idan Allah ya yrda, ki bani gantalallen" jikin Ajiddeh yayi sanyi ba kadan ba lokaci daya hawaye ya cika idonta ta ja kafa da kyar ta koma ward din ta mika ma Abuturrab wayar, hannu yasa ya karb'a batareda yasan ko waye ba ya kara wayan a kunnenshi Thank you to these amazing beautiful Sisters, I feel motivated to type whenever i see your messages, thank you for your prayers and all, Allah ya karamin lafiya to keep on with you girls ~MRS ❣❣SPLENDID❣❣ JAMMY JAMMY SUGRAH❤ MEELA ADEEL MOM SADIQ RUQAYYA (ZUMA) NAJA'ATUU UMMIEE MISS😍 SOFTIE JUWAIRIYYA [11/15, 11:14 AM] ‪+234 810 957 2036‬: 💖💝 *BATUUL*💖💝 79 *By Phatiemarkh* Jin muryar Ammah ya d'aga kai yana kallon Ajiddeh, a fusace Ammah tace "Kana ji na ka min shiru Aliyu" yyi kasa da kai yace "A'a Ammah ina yini?" cike da fada tace "Rike gaisuwar ka, maxa tun muna mu biyu gobe ka taho min da Batuul gida, ai tun ba yau ba nasan kai shashasha ne, uwar ka cikin ya tsare maka kake son a cire" kasa cewa komai yayi, Ammah tayi ta bambami ya bari tayi mai isarta sannan a hankali yace "Ammah tana wahala ne, ki tambayi farida in ta iso gobe" Ammah tace "Ya baxa tayi wahala ba kana xaune da makira a gida a matsayin mata sun sa min ita a gaba, ina me tabbatar maka xaka ga the other side of me idan abu ya samu Bitti, maxa ku bar asibitin nan gobe ku biyo 1st flight ka dawo min da ita Nigeria" Ammah na kai wa nan ta katse wayar, ya daga kai yana kallon Ajiddeh dake jingine jikin bango duk jikinta a sanyaye, ajiye wayar yayi yace "Why did you call her?" Bata ce komai ba ta juya ta fice daga ward din, juyawa yayi a hankali yana kallon Batuul dake bacci, dawowa yayi kusa da ita ya daura hannunsa a hankali kan fuskarta, sosai ta rame daga jiyan xuwa yau, lumshe ido yayi cikin sanyin murya yace "Get well soon wife" mikewa yayi jiki ba kwari ya koma gun likitocin don dakatar da su, A asibiti suka kwana ranan don gani yake suna komawa gida ciwon xai tashi, sai dai throughout daren ko farkawa Batuul bata yi ba, a spare bed din dake dakin Ajiddeh ta kwanta, sai dai kwata kwata ta kasa bacci ta rasa me ke damunta, Abuturrab dake xaune kan darduma a dakin yana kula da yanda take ta juye juye sai dai bai ce mata komai ba, da asuba suka bar asibitin don bai son suyi missing 1st flight kamar yanda Ammah ta bukata duk da he is not sure xa su samu, a mota yana driving ya d'an kalli Ajiddeh yace "We will be leaving for Nigeria, xan maida Batuul gida, you take care...." Bai karasa ba ta katse shi tace "Nima xan je" kallon ta ya kuma yi sai dai bai ce komai ba ya ci gaba da driving dinsa yana yi yana kallon Batuul da har ta koma bacci a bayan motar. Ba tare da bata lokaci ba duk suka shirya, Batuul dama shi ya taimaka mata tayi wanka ta shirya don yaga alamar in suka biye ta nata bacci kawai xata yi tayi, Biyar saura suka isa airport yayi masu booking, biyar da rabi suka yi set off for Nigeria, duk motsin da Batuul dake rungume jikinsa xata yi idonsa na kai don waje daya suka xauna har lokacin kuma bacci take, lkci lkci kuma ya kan juya ya kalli Ajiddeh dake gaba ta saka earpiece, sai a sannan ya fara tunanin sudden change dinta is it for real, maganganun da Ammah ta fadi masa jiya suka fado masa, wai sun sa Batuul a gaba, ya sauke ajiyar xuciya don shi bai yrda da wannan belief din ba, a hankali Batuul ta bude ido tana kallonsa, ganin yanda ta bata fuska gabansa ya fadi a hankali yace "What?" Ta rike hannunsa tace "Ya Abu cikin xai fara" hankalinsa ne ya tashi ya daura hannunsa a cikin yace "No, no baxai fara ba idan Allah ya yarda" runtse ido tayi jin kamar ana murda mata cikin ta sakar masa kuka tace "Wllh ya Abu ya fara" ya rungume ta sosai yace "Noo wife baxai fara ba in'sha Allah, ko yunwa dai kike ji..." Ta fashe da wani kukan tace "Wayyo ya Abu cikin ya fara min" Kallon su kawae Ajiddeh ke yi, can kuma ta maida kanta kan wayarta, ganin kuka sosai Batuul ke yi jikinsa tana rike da cikinta ya kalli Ajiddeh suka hada ido, dauke kai tayi, ya sake Batuul ya mike ya tafi gunta cike da damuwa yace "Babe kin ji wai cikin ya fara, how are we going to do it, gashi ba muyi rabin journey ba har yanxu fa" ba tare da ta kallesa ba tace "Ba sai kayi ta tofa mata addu'a ba" yace "Yea haka ne kuma" juyawa yayi da sauri ya koma gun Batuul da ta hade kanta da gwiwa har ta hada xufa don axaba ita kanta baxa ta ce ga yanda cikin yake mata ba, ya xauna ya dagota ya kwantar da ita jikinsa yace "Sorry wife xai daina in'sha Allah" a hankali ya dinga tofa mata addu'a tana jikinsa, sun kusa awa biyu a haka har dai yaji ta daina kukan da take a hankali, ya leka fuskarta ya ga bacci tayi, ya sauke ajiyar xuciya ya lumshe ido ya manna mata kiss a forehead dinta, yana bude ido suka yi ido hudu da Ajiddeh dake kallon su, dauke kai tayi da sauri, ya ji wani iri shima ya dauke nasa kan. Shidda na yamma jirginsu yayi land a Nnamdi Azikwe Airport, ya kunna wayarsa ya shiga kiran layin Sadeeq, yana d'agawa yace "Hello Bro, ka taho kayi picking dinmu muna airport" daga haka ya katse wayar, ya kalli Batuul dake kwance jikinsa idonta lumshe duk da ba bacci take ba and he can see how happy she is to be home, ko bata fadi ba, Ajiddeh kam nesa da su ta xauna, bude ido Batuul tayi da sauri, yace "What?" Kallon matar dake xaune daga gefensu tana cin popcorn tayi ta bata fuska tace "Bana son kamshin xai sa ni amai" mikewa yyi da sauri ya d'agata suka bar wajen, Ajiddeh ta bi su da kallo, wani gun ya koma suka xauna, boye fuskarta tayi da sauri a kirjinsa yace "What again?" Kamar xata yi kuka tace "Bana son kamshin turaren mutumin nan" juyawa yayi ya kalli Mutumin dake xaune gefensu, ya mike ya dagota suka kuma barin wajen suka koma wani gun suka xauna, plantain chips taga wani yaro na ci ta kallesa da sauri tace "Ya Abu xan ci" yace "Me za ki ci?" Ta turo baki ta nuna masa chips din, kallon ta yayi, sai kuma ya mike ya nufi inda yaron da Mamarsa ke xaune yayi masu sallama yace "Don Allah a ina ku ka siya chips din nan Anty" matar tace "Ai kam ba nan muka siya ba" yace "Toh nagode" juyawa yayi ya koma gun Batuul ya xauna yace "Ki bari idan xa mu gida in siya maki a hanya suma ba nan suka siya ba" kamar xata yi kuka tace "Noo Ya Abu yanxu nake so wllh, kila anjima baxan iya ci ba xai fita raina" murmushi yayi ya jawota jikinsa yana shafa cikinta a hankali yace "Shi babyna yake son ci yanxu koh?" Bata fuska tayi, yayi dariya ya manna mata kiss ya cheeks dinta yace "Don't worry, it's nothing don babynmu yasa mu roko a airport" mikewa yyi ya koma gun masu chips, yana d'an Shafa kai yace "Anty ko xaku d'an san mana chips din k'adan, matata ce wai shi ke ranta taki bari mu fita mu siya" dariya matar tayi tace "Allah sarki duk mun cinye a jirgi amma bari in dibar mata na Kamal" yayi murmushi yace "Toh mun gode" ta karbi na hannun yaronta tace "Kamal idan mun fita xan siya maka wani ka ji" ya gyada mata kai, ta d'an dibar masa k'adan ta mika ma Abuturrab sauran na ledan ya karba yana murmushi ya shafa kan yaron yace "Toh mun gode kwarai Anty da kamal" tayi dariya tace "Babu komai, Allah dai ya raba lafiya" murmushi yayi ya juya yace "Toh Ameen" duk wannan abinda suke Ajiddeh na kallon su kuma tana ji, ya koma gun Batuul ya d'ago kanta yace "Oya ga chips Maman twins" hararansa tayi ta fada kansa ta shagwabe murya tace "Ni Allah bana so" dariya yayi ya dauki chip daya yace "toh na daina, bude bakin" ba musu ta bude ya d'an gutsura k'adan ya saka mata sauran a baki. Mikewa Ajiddeh tayi ta fice daga waiting room din ba tare da ya lura da hakan ba, haka yayi ta ba Batuul chips din har tace ya isheta, wayarsa ya shiga ring ya fiddo ya ga sadiq ne, mikewa yayi ya dagota yace "Sadeeq na jiranmu" sai a sannan ya kalli inda Ajiddeh take ya ga ba ta, waige waigen inda xai ganta ya fara yi amma bai ganta ba, yana rike da Batuul suka fita. [11/15, 11:14 AM] ‪+234 810 957 2036‬: 💖💝BATUUL💖💝 80 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Suna cikin tafiya ta tsaya, ya juya yana kallonta yace "What?" Murmushi ta k'irk'iro ganin irin kallon da yakeyi mata tace "Am fine", kallonta yakeyi har lokacin yace "are you sure? Ko dai ya fara?", da sauri ta shiga girgiza kai tana sake wani murmushin da kana gani kasan ba na gaske bane, kyaleta yayi badan ya yadda ba ya tallafota jikinshi tareda kwantar da kanta kan kafad'unshi yace "okay let's get going Sadiq is waiting", suna d'ago kai suka hango Sadiq na waving musu da wide smile shimfid'e a fuskanshi, ya tara gashi a kanshi sai ya k'ara mishi kyau, ido ya wara ganin Batuul yace "Batuulan Aunty is that you?", baki ta zumb'uro mishi tayi raurau da ido tace "Its Batuul ba Batuula ba", dariya ta bawa Sadiq yace "kin ganki kuwa?, Yaa Abu mey kake bata haka, you can see her glow from a far, she has changed tayi kyau sosai", harara Abu ya sakar mishi tareda turo mishi trolley d'in yace "Let's get going, you are tiring her da unending surutunka", tafiya Sadiq d'in ya fara yana dariya yace "Its okay ba sai kin fad'amin yanzu ba, we will meet ltr ko Batuulan Aunty, rabu da Yaa Abu, he doesn't know", ya fad'a mata yana kashe mata ido d'aya, tsaki Abu yaja yace "hand me the key, in ka gama surutun ka samemu a gida", dariya kawai Sadiq yayi bai sake cewa komai ba, a mota suka tarar da Ajiddeh, sai lokacin ya tuna fa suna a tare tun lokacin da ta bar wajen, da unreadable expression d'in dake fuskanta ta kalleshi ganin yanda yake riqe da Batuul tace "bari in dawo baya in zauna da ita, you can sit here ta fad'a tana k'ok'arin barin gaban motan, kai ya kad'a mata yace "No you can stay back babu komai, she will be fine", shiru Ajiddeh tayi tana kallon yadda yake handling Batuul d'in har ya zauna ya gyara mata zamanta, a hankali ta janye idonta a kansu tana jin wani abu har cikin ranta ta maida kallonta gaba jin mey Sadiq ke fad'i, da k'yar ta bud'e baki tace "Handsome you said?", hannu Sadiq yasa a cikin gashinshi jin dad'in sunan da Ajiddeh ta k'irashi da yana murmushi yace "Naga ne kun canja Batuul totally, tayi wani irin fresh da zuwanta for months, ko nima in zo ne a rik'a bamu abinda ake batan tare" kallon Batuul dake d'an mutsu mutsu Abutturab na mata magana k'asa k'asa tayi ta mirror sannan tayi maza ta d'auke kallonta daga kansu tayi murmushi tana kallon Sadiq, ya kad'a kai yace "gaskiya UK ya karb'eta, haka sukayi ta hira yana tuk'in, suna cikin hiransu sukaji kukan Batuul d'in, a hanzarce suka juyo ganin mey ke faruwa, rungume suka ga Batuul jikin Abutturab sai kuka take tana riqe da cikinta, da sauri Sadiq ya ja brake gefen titi yace "What's wrong with her Yaa Abu ko mu k'arasa asibiti ne if she isn't feeling well?", kasa magana yayi sai alama da yayi mishi da yaci gaba da driving, Ajiddeh ce tayi k'arfin hali tace "Sadiq let's get going, she needs rest", hakan akayi Sadiq ya tada motan sukaci gaba da tafiya, Batuul kam sai kuka takeyi tana riqe da cikinta duk ya rikice ya rasa ya zaiyi, tunda Ajiddeh taga an d'auki hanyan gidansu Abu jikinta yayi sanyi gabanta ya rik'a fad'uwa, taso a kaita gidansu ko kuma gidanta da bata tab'a sanin ya yake ba dan ba tab'a zuwa tayi ba amma tasan yanzu its already late, horn Sadiq yayi bakin k'ofa yana jira a bud'e gate daidai nan Ajiddeh ta d'ago kanta jiki a sanyaye tana kallon cikin gidan, tun Sadiq bai gama parking ba Abu ya bud'e k'ofa ya fita, duk tsayawa sukayi suka bishi da ido ganin yanda ya rikice gaba d'aya, jiki a sanyaye ta sauk'e idonta, Sadiq ne da yayi noticing uneasiness da restlessness d'in dake tattare da ita yayi maza ya bud'e ya zagayo ta gefenta ya bud'e mata k'ofa da murmushinshi mai kyau yace "Muje ko Anty?", haka ta janyo handbag d'inta ta fito daga motar, Sadiq yace "Let me help with d bag Ma'am", wai ko ta d'an saki jiki, batace komai ta mik'a mishi jakar ya shiga gaba ta biyoshi a baya, da sallama ya Abu ya shigo parlour dake d'auke da wani ni'imtaccen k'anshi da sanyi kamar kullum, Ammah dake zaune cikin hanzari ta mik'e tana kallon yanda Batuul d'in ke jin jiki tace "Subhanallah, Abu yanzu haka yarinyar nan ke wahala amma kaje ka zauna kaqi dawo min da ita, wane irin hali ke gareka wai?", kasa cewa komai yayi sai kwantar da ita da yayi kan doguwar kujera, ya zauna daga gefenta ya dafa kanshi da duka hannayenshi biyu, Farida ce ta sauk'o a guje tana fad'in "Ammah na fad'amiki haka yakeyi mata kullum, koh ranan fa tana bacci kawai cikinta ya fara ciwo, Ammah mu kaita asibiti Dan Allah kar wani abin ya sameta, am with a key", ta fad'a tana k'ok'arin jin d'umin jikin Batuul, Ammah ce ta dubi Abu tace "Abu ba magana nakeyi maka ba, tun yaushe ta fara ciwon?", jajayen idanunshi da suka rine ya d'ago saura kad'an hawayen dake cikinsu ya zubo, ji kawai Ammah tayi ya rungumeta, cikin sanyi yake cemata "Ammah plss help her, bazan iya jure rashinta ba I need her to get well Ammah, kuyi wani abu nima bansan mey ke damunta ba, I don't want to lose her, Plsss Ammah", daidai nan Ajiddeh da Sadiq suka shigo parlour, kallo d'aya Ammah tayiwa Ajiddeh ta d'auke kanta ta d'ago Abu da ya kwantar da kanshi jikinta ta kama fuskanshi da hannayenta duka biyun tace "You have to be strong, babu abinda zai sameta da izinin Allah, just pray for her kaji?", Kai kawai ya iya d'aga mata kamar wani k'aramin yaro, gaban Batuul d'in ta dawo ta rik'e mata hannaye tace "Bitti sannu kinji, kin kusa samun sauk'i In sha Allah", Batuul kam bata iya cewa komai sai kuka da take tana k'iran sunan Aunty, Ajiddeh har lokacin tana tsaye ta rasa mey ma zatayi gashi babu wanda yabi ta kanta har Abutturab d'in, kamar dama baisan da ita wajen, wayanta ne ya fara ringing cikin jaka, gabanta ne ya shiga fad'uwa ganin mai k'iran nata, Mumm ce ke kiranta, bata d'auka ba saima sawa da tayi a silenta, tana gani haka Jainaba ma ta k'irata amma har lokacin bata d'aga ba daga k'arshe ma kashe wayan tayi gaba d'ayanshi, Addu'a Ammah ta shiga tofa mata, da kad'an kad'an kukan nata ya fara yin sauk'i sai juye juye da take, snn ta d'ago ta dubi Abu tace "kai min ita d'aki", Sadiq dake fitowa part d'insune yaga Ajiddeh tsaye har lokacin yace "Noo, badai tun d'azu kike tsaye nan gun ba, find a place and settle yourself", d'an murmushi ta k'irk'iro mishi ta nemi waje ta zauna bakin kujerun parlourn kamar wata mara gaskiya, ko kallonta Ammah batayi ba tayi side d'in Abui, Abu ta kalla tace "Babe ya jikin nata?", kai ya d'aga mata tareda cewa "she needs rest", ya haura sama da ita, a kan gadon d'akin Ammah ya kwantar da Batuul d'in, samun kanshi yayi shima da kwanciya daga gefenta, rungumeta yayi tsam jikinshi ya saka hannayenshi cikin nata, a hankali kamar wani d'an yaro ya fara mata hawaye, "Fatima I promise to give you all you ever requested for, kiyi hakuri ki tashi ki fad'amin abinda ke damunki, its gonna be hard to live with out you kinji, am used to you kinji Fatima, I will keep you and my unborn baby happy, no harm will befall you just get up and we will live happily", duk surutun nan da yakeyi ko kad'an Batuul bata san abinda yake fad'i ba don tuni baccin wahala yyi gaba da ita, haka yayi ta surutunshi, vibration d'in wayanshi ya katse shi ya kwantar da ita a hankali yayi snn yayi receiving call d'in, "Man ba yau mukayi dakai zaka dawo ba, but Ammah ta qirani wai tana nemana snn kaima ka dawo", ajiyar zuciya ya sauk'e snn yace "I had to comeback, Batuul batajin dad'i", "Subhanallah mey ke damunta, how is she feeling now?", juyawa yayi ya dubeta tana bacci snn yace "Alhamdulillah she is getting better, in kazo we talk", da haka suka gama wayan, fuskanshi ya shafa yana salati ya mik'e, kamar kar ya barta a d'akin ya fice, Ajiddeh na ganinshi yana sauk'owa kan stairs ta mik'e tsaye, saida ya ka'araso parlour ya lura da ita, jiki a sanyaye tace "Zan tafi gida", kallonta ya tsaya yi for some seconds snn yace "nanma gida ne, you can't live ke kad'ai to a new home da ba a tab'a shiganshi ba", kai ta girgiza mishi tace "gidanmu fa zan tafi", "You can stay here in zan tafi sai mu tafi tare", da haka ya k'yaleta nan tsaye yayi side d'in Abui. Hi everyone, Alhamdulillah Exams is finally over and am getting better, Thank you for d prayers, I can't really express how happy I am to know ppl out there are praying for my Health, Alhamdulillah and abt the previous page, it was from the same source you guys used to get BATUUL from, it wasn't a pirate or fake, ppl have been misunderstanding d whole thing, page 79 is genuine.Thank you all💖 [11/15, 11:15 AM] ‪+234 810 957 2036‬: 💖💝BATUUL💖💝 81 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Ta kai 10mins tsaye tana jiran ganin Abu ya fito amma har lokacin shiru, jikintane ya k'ara sanyi taja k'afafuwanta ta koma kan kujeran palon, in banda masu aiki dake kaiwa da komowa bata ganin kowa, ko Farida ma bata sake ganinta ba, haka nan ta zauna jigum sai sak'e sak'e take tana warwarewa, can bayan wajen minti ashirin ta jiyo motsi, da sauri ta wartsake daga gyangyad'in dake shirin d'aukarta, k'ofan ta kafawa ido, Abui ne ya fara fitowa kamar kullum yana cikin shigarshi ta girma, murmushin nan na fuskanshi, Ammah ce daga bayanshi sai Abutturab k'arshe, kamar wata mara gaskiya tana hangosu ta mik'e tsaye, a diririce ta bud'e baki da k'yar ta iya gaishesu, Ammah kam ko kallonta batayi ba bare ta amsa mata gaisuwar, Abui ne yace "Lafiya kalau, ya gida ya kuma mai jiki, ashe y'ar uwartaki bataji dad'i ba", murmushi ta k'irk'iro tace "Alhamdulillah, tama fara jin sauk'i", Abui ya kad'a kai yace "Allah ya bata lafiya yasa kaffara Ne", daga haka yayi hanyan waje tareda Abu, itakam tsayawa kawai kallonshi tayi ganin ya fita baice mata komai akan tafiya gidansu da zatayi ba, haka ta koma ta zauna jiki a sanyaye kamar ta kurma ihu, wayarta ta ciro cikin jaka ta kunna ta, kamar jira ake ta kunna nan da nan msgs suka fara shigowa kuma duk yawancinsu daga Mum ne, ignoring d'insu tayi baki d'aya ta mik'e tayi d'akin Abu. Ammah kam na hawa sama bayan fitansu Abui d'akinta ta wuce kai, Batuul na kwance abinta tana bacci kamar ba itace d'azu ke kukan ba, amma da gani baccin baya mata dad'i, daga gefenta ta zauna tana kallon yanda ta k'ara haske tayi kyau ta rame, hannu ta d'aura saman goshinta taji babu wani zafi, kallon Batuul d'in kawai takeyi tana jin yadda tausayinta ke ratsata, yarinya k'arama da ita amma saida aka samu wani Mara imanin yayi mata wani abin, duniya babu kyau, babu ruwanka da rayuwar mutum amma idonshi yana kan naka rayuwar, in banda rashin adalci da rashin tausayi meye ma Batuul da har za ayi mata asiri, babu komai da izinin Allah sai aikinsu ya lalace, a hankali ta furta "sannu Fatima, Allah ya baki lafiya", sannan ta mik'e ta bud'e closet d'inta ta ciro wani d'an kwalba mai d'auke da ruwan Zamzam ta dawo bakin gadon ta bud'eshi ta tsiyaya kad'an a hannunta ta shafawa Batuul d'in a fuska, wani irin numfashi taja jin ruwan a jikinta, juyawa tayi ta gyara kwanciyarta daga haka taci gaba da baccinta, intercom Ammah ta d'auka ta k'ira d'aya daga cikin masu aikinta, babu b'ata lokaci d'aya daga cikinsu tazo, "inaso ki wanko min Baby cucumber, ki tabbatar ya wanku da vinegar snn ki tafasa fresh milk sai ki jefa cinnamon da cardamom kad'an kada a saka sugar, ki Juyo min a flask, bada dad'ewa ba, snn a d'ora soup d'in offal's", yarinyar dake sanye da uniform d'in cooks tace "okay Ma, za ayi wani abin ne kuma?", Ammah tace "No for now dai babu, ba kun d'ora lunch ba?", yarinyar ta kad'a kai tace "Ehh Ma", Ammah tace "toh shikenan kije ku gama wannan, and be fast", da sauri yarinyar ta amsa ta fice abinta, Ajiddeh na zaune d'akin Abu duk abin duniya ya taru yayi mata yawa, ta rasa mey ma zatayi taji dad'i, har ga Allah ba son Batuul takeyi ba bare ma a matsayin kishiya amma batason ta zama silar mutuwarta, ko ba kishi musulmace kuma ta san hukuncin kisa kan musulmi, ita inda yadda za ayi kawai ayi koma meye a rabata da gidan amma banda kisan kai, ko haukatata ne ayi, gabanta na fad'uwa take kallon wayan da ta saka silent na ringing, tun d'azu ake k'ira amma ta kasa d'auka, da k'yar ta sa hannu tayi sliding ta kara wayar a kunnenta, tun kamin tayi magana taji muryar Mum na cewa "Dan ubanki tunda yarinyar kanwar uwarkice dole kiqi d'aukan wayata, wlhy Ajiddeh kina jina, kada ki kuskura raina ya b'aci kanki, wani abu ya shiga kanki ne shegiyar yarinya inace akanki nayi sa'ar haihuwa ashe wahalar banza nasha, toh tun wuri kisan abunda kikeyi tun kamin inyi maganinki" Kamar wacce za a jiyo maganan da takeyi tace "Mum mey yayi zafi toh hka, naji kiyi duk yadda kike so amma fa babu ruwana inta mutu, I just want to be happy, yanzu haka mun dawo Nigeria kan ciwon nata muna gidansu Aliyu yanzu haka", kirji Mum ta dafe tace "Naga ta kaina ni Zuwaira, yanzu dan uwarki Ajiddeh kina garin nan shine baki fad'a mana ko kizo gida ba, gidansu miji yafi miki dad'i ko, ina zansa kaina yau dan takaici ni Zuwaira, anya kanki d'aya kuwa Hauwa, lokaci d'aya ki juye ki zama wata sakarya sallamamiya, Wato Bilkisun asirce min keh tayi ko, Ta Allah ba tata ba, duk sai nayi maganinsu daga ita har y'ay'an nata, kuma ki tabbata kinzo gida yau", shiru Ajiddeh tayi tama rasa mey zatace, "Toh" kawai ta iya cewa ta katse wayan, tashi tayi ta fito daga d'akin tayi hanyan d'akin Ammah, saida tayi sallama snn tajiyo muryan Ammah na cewa "Bismillah shigo", tura k'ofan d'akin tayi ta shigah Ammah na zaune kan abin Sallah ta idar da Sallah kenan, waje Ajiddeh ta samu ta zauna tana kallon Batuul dake kwance, takai 5mins kamin ta iya bud'e baki tace "Ammah ya jikin nata?", Ammah ta kalli Batuul dake kwance snn tace "Bacci takeyi tun d'azun, kuma da izinin Allah zataji sauk'i", daga haka basu sake cewa komai d'akin shiru, Farida ce tayi sallama ta shigo, da mamaki ta tsaya kallon Ajiddeh, rabonta da ganinta a d'akin tun satin bikinsu da Yaa Abu, tab'e baki tayi ta k'arasa shigowa, daga gefen Batuul d'in ta zauna tana kallonta da tausayi tace "Ammah ya jikin nata?, ta farka tun bayan fitana?", kai kawai Ammah ta gyad'a mata alamar A'a, Hannu tasa ta kamo na Batuul tace "Allasarki bestfriend , you will get well soon kinji, In sha Allah", tacewa Ammah, "Ammah mu tafi asibiti mana, turawan nan duk ba aikin kirki sukayi ba, a kaita wajen Dr Zakaa tunda gynaecologist ne zai iya duba matsalarta, tunda cikinta take cewa kullum", Har saida Farida tayi shiru kamar baza tace komai ba can tace "Ai ciwon nata bana asibiti bane, Abui sun tafi tahowa da Ashiekh Zai mata addu'a ya gane mana matsalar", k'ululu cikin Ajiddeh yayi k'ara, gani kawai takeyi Ammah tasan abinda ke faruwa, har zufa taji yana tsattsafo mata, Farida tace "Subhanallah, Ammah Jinns ne suka tab'ata?", Ammah tace "tashi kije ki kitchen ki dubamin ko sun gama aikin da na sakasu, kice su hanzarta, banaso ta farka babu komai a kusa", "Toh", Farida tace tasa kai ta fice, Lokacin dasu Abutturab suka fita kai tsaye airport sukaje d'auko Asheikh, shike tuk'a motar Abui da malamin a baya amma gaba d'aya hankalinshi na Kan Batuul, wayan Batuul dake wajenshi ya katse mishi tunani jin yana ringing, dubawa yayi yaga ansa Anty with all sort of hrt Emojies, baiyi picking call d'in ba har ya katse, haka a karo na biyu ma bai d'auki wayan ba, uku da rabi suka iso gida, a guest side aka sauk'eshi, saida Abu ya tabbatar komai daidai snn yayi d'akin Ammah, so kawai yake yaga lafiya, a hankali ya tura k'ofan d'akin ya shiga, babu kowa cikin d'akin sai sanyi da k'anshi mai dad'i, har lokacin Batuul na kwance tana bacci, ajiyar zuciya ya sauk'e snn ya k'arsasa shiga, bargon ya janye bayan ya zauna daga gefenta,murmushinshi mai kyau yayi ganin cute face d'inta da ya k'ara haske, a hankali ya d'aga y'ar rigar dake jikinta ya tsurawa flat tummy d'inta ido, hannunshi yakai kai yana shafawa, bakinshi ya kai ya d'ora mata kiss kai a hankali ya furta "Your Mommah will get better soon kinji Lil princess", jin hannu jikinta yasa ta bud'e lumsassun idanunta tana scanning d'akin, murmushi ya sakar mata da yasa itama ta mayar mishi, da sauri yaga ta tashi ta zauna idonta tab da hawaye, tace mishi "Aunty", hannu yasa ya rungumota ya zaunar da ita kan cinyarshi yace "No Fatima kar ki fara, kiyi hak'uri kinji, kinga bakida lafiya, Aunty da kanta zatazo wajenki kinji, keda zaki koma gidanta ma gaba d'aya ko kin mantaa ne", k'ara widening smile d'inta tayi ta d'ago tana dubanshi tace "Bazan koma UK ba?", yana kallon idonta yace "a ba haka kikeso ba, kince in kin bani Babyna zan maidaki wajen Aunty", zumb'uro mishi baki tayi tace "Toh ai nafison gidan Aunty ne kuma kaine kace in na baka Baby zaka kaini", kallon d'an k'aramin lips d'inta da yafiso kawai yakeyi, yadda ta zumb'uroshi tana pouting, a hankali ya d'aura d'an yatsanshi kai yana zagayesu ya kafeta da ido yace "Will you miss me in kin koma gidan Aunty?", kai ta shiga gyad'a mishi da sauri kamar wata yarinya tace "Ehhen, sosai ma, you are kind ai, you have stopped being bad to me", dariya ta bashi yayi murmushi yace "Was I?", tace "Of course , but that was then ai, da fa ko bansan kana waje ba if nayi approaching wajen heart beat d'ina increasing yakeyi, it runs at a faster pace, I thought ma mayune suka kamani, Aunty kuma sai tayi ta cewa banida gaskiya, but daga baya sai ya dena, I don't know mesa?", matseta yayi jikinshi a kunne ya rad'a mata "Its same with me, duk Inda kike indai naje wajen toh I feel that restlessness, shiyasa I don't want you kusa dani but nima nawa ya daina, kinsan mey ya janyo duka haka?", jiki a sanyaye tace "A ah ni ban sani ba", yayi murmushi ya kamo d'an k'aramin hancinta yace "Its gonna be an assignment, shima sai kin nemo reason d'in before in kaiki gidan Aunty", ta kalli idonshi da ya fara canja kala tayi murmushi tace "Toh ai zan tambayi Aunty ta fad'amin", ya d'age girarshi yace "okay..., yanzu malami yazo yayi miki addu'a, kinga hospital duk ba asan mey ke damunki ba, kuma kinga in ya fara kina shan wahala, so we will try na Asheikh, he is a great scholar", tayi murmushi tace "But ai na warke, kaga I can even jump, dama d'azun kawai shine ya fara", ta shiga k'ok'arin mik'ewa zatayi tsalle, da sauri ya jawota jikinshi ya had'e rai yace "Baby mana, you will get hurt, da Babyn dake jikinki", ganin ranshi b'ace itama taji ba dad'i tace "Na dena toh, but ni ai ba baby bace, your other wife is baby, haka kake ce mata itama haka take qiranka", yayi murmushi ya lakuce mata hanci yace "Okay then you are?.....", ya tsaya kamar mai tunani, caraf tayi tace "Am Batuul", kai ya girgiza mata yace "Yeah nasan wannan, I want a name da ni kad'ai zan na k'iranki dashi", tace "Ni bana so just call me Batuul d'ina, nafisonshi", tayi maganan tana barin jikinshi, kamata yayi yace "Wait, ina zaki", tsuke baki tayi tace "Na gaji da magana ka tafi", ido ya wara yace "Yaushe kikayi magana, I was d one talking fa, do you know how much I missed you?", kamin tace wani abu ya had'e bakinsu, tun tana tureshi bataso har ta hak'ura ta biyeshi, jin an tab'a k'ofa yasata saurin turashi amma har lokacin tana jikinshi, Ammah ce ta shigo d'akin, da mamaki ta tsaya kallon Abu da batasan lokacin da ya shigo d'akin ba, raurau Batuul tayi zata sauk'a daga jikinshi amma yaqi sakinta, Ammah ce tace "Kai yaushe ka shigo, yarinyar ba lafiya tana bacci shine saida ka tadata dan neman magana?", murmushin jin kunya yayi ya shiga sosa kai yace "Ammah ki tambayeta bani na tasheta ba, zaune nazo na sameta tana game", Batuul kam nok'ewa ta dingayi wai ita kunyan Ammah, ido ta wara jin abinda ya fad'a, da sauri ta sauk'a daga jikinshi, Ammah tace "Bitti ya jikin, yayi sauk'i kenan", da k'yar Batuul ta iya gyad'a Kai, Ammah ta k'araso gaban gadon tace "Tashi kici wannan zaisa kiji dad'in jikinki, tun d'azu nake jira ki tashi", Ammah ta mik'o mata plate d'in baby cucumber da akayi slicing akayi cling filming, sannan ta tsiyaya mata fresh milk d'in dake ta k'anshin Cinnamon da cardamom, kasa karb'a tayi sai Abune ya karb'a yace "Ammah ai baza taci ba, sai na bata", Ammah ta hararesa tace "Make sure taci, Asheikh ne yace a fara bata, tasha madaran sosai", yace "In sha Allah" daga haka Ammah ta juya ta fita daga dakin, mikewa yayi ya kuma jawota jikinsa ta fashe da kukan karya tana cewa "Ya Abu ni bana son haka gashi kasa Ammah ta gan ni naji kunya" ya wara idonsa yace "So? Ae bari ma ta dawo ta hada mana ruwan wanka in maki" cusa kanta tayi kirjinsa ta rufe ido tana kai masa duka tana kukan karya, ya kai bakinsa a hankali kan wuyarta ya lumshe ido murya can kasa yace "I... I like you..." Da sauri ta bude ido tana kallonsa, ya wara ido ya shafa cikinta yace "Yes I like my baby" [11/15, 11:15 AM] ‪+234 810 957 2036‬: 💖💝BATUUL💖💝 82 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Duk da batayi tsammanin fiyeda haka daga maganganunshi ba amma jikinta saida yayi sanyi, janye jikinta tayi daga nashi ta sauk'a ta zauna kan gadon, wani iri ta dinga ji ranta batasan lokacin da hawaye ya shiga zubo mata ba, a d'an tsorace ya kalleta ganin ta fara hawaye da sauri ya kamo hannunta yace "Not again, tashi muje malamin na k'asa.....", bata bari ya k'arasa ba ta warce hannunta daga nashi had'e da murgud'a d'an k'aramin bakinta, da serious expression shimfid'e kan fuskarshi yace "Hey watch out", yayi sauri ya sake rik'ota ganin yanda ta mike kamar zata tashi sama, hawaye ne ya cicciko idonta cikin b'acin rai ta tureshi tace "Let me be, I don't wanna talk to you", ta fizge jikinta hawayen dake fuskanta na k'arasa gangarowa, cikin zafin nama ya dad'a fizgota yana mata wani irin kallo yace "Fatima are you okay?, kinada hankali kuwa, na fad'a miki you should stop being rough okay?, you are carrying my baby, i cant risk anything happening to my baby, beside kema bakida lafiya, are you trying to hurt yourself?, mesa bakijin magana ne", ido ta lumshe snn ta bud'esu a hankali hawayen na ci gaba da zubowa, wani matsanancin kuka ta fashe dashi, baisan lokacin da ya furta "Yasalam", ba ya rungumota sosai jikinshi, zama yayi bakin gadon yana patting bayanta tareda d'an rocking d'inta, yanzu ne yake tabbatar da zancen da yayi da Ammah d'azu da ta ce ciwon Batuul ba normal ciwo bane da sa hannu, in ba haka ba she was jovial yanzun nan lokaci d'aya ta fara acting strangely, ajiyar zuciya ya sauke a hankali ya sunkuyo daidai kunnenta yace "Kinaso nima inyi kukan ko Fatima, I don't like you crying yana d'agamin hankali fiyeda komai, I can feel it a duka pulses d'ina in kina kukan nan, Dan Allah ki dena kinji?", bata d'ago ba sai ma ci gaba da kukanta da takeyi, ido ya lumshe tareda sake matseta jikinshi yayi pecking goshinta snn yace "Tell me mey ya saki kukan", a hankali ta iya bud'e baki tace "zanje wajen Aunty?", kallonta ya tsaya yi for seconds snn yace "I thought we were done with that Fatima, haka kikeso Aunty ta ganki ba lafiya?, ko kinfiso hankalin Aunty ya tashi in taga yadda kika koma, kinga fa duk kin rame", ya fad'a yana d'aura hannunshi saman wuyanta, "I want you to get better kamin Aunty ta ganki kinji, she will b happy okay?", d'agota yayi yana share mata hawayen dake fuskarta, idanunshi gaba daya na exploring fuskarta kamar maison gano wani abun, Four months back da za a ce mishi akwai ran da zai zauna rarrashin mace kallon you are sick upstairs zai yiwa maishi, amma yau shi da kanshi ya zauna rarrashin yarinya k'arama har yakejin shima kamar zai biye mata suyi kukan tare, murmushi yayi ya jawo plate d'in Baby cucumbeya d'auki slice d'aya ya kai mata shi baki, batayi musu ba ta bud'e mishi baki ya saka mata, haka ya dinga bata har ta cinye slices uku tace mishi ya isheta snn ya d'auki cup d'in madaran nan ya fara bata, shima saida ta kusa shanyewa snn ta kauda kanta, zaiyi magana wayarta dake aljihunshi ta fara ringing, hannu yasa ya ciro wayar, ganin mai k'iran yasa ya mik'a mata Tagumi tayi ta zubawa wayar dake hannunta idanu, yaushe ma ya zama mutum da har zai wani nemi ta dawo, Mummy ce ta fito daga bedroom dinta sai k'anshi take zubawa ta tsaya kallon Jainaba da tayi tagumi tana kallon wayar hannunta tana mata magana bata amsawa, a d'an tsawace Mum tace "Keee kinada hankali kuwa, tunanin uban wa kike tun d'azu na fito ina miki magana baki sani ba kuma koh shiryawar bakiyi ba bayan tun d'azu nace miki zamu fita", a firgice Jainaba ta juyo snn ta sauk'e Ajiyar zuciya tace "kinga ni banma jiki ba, wai wannan shasha shan ne yake son d'aga min hakali wai lallai lallai gobe in dawo", Mum tana kallonta tace "Waye kuma, shi Idrees d'inne yake ce miki sai kin dawo a goben?, sai yayi himma yazo ya kinkime ki ai, in kinje can dinma uwar mey zai miki in banda jaraba, y'ay'ansa ai kin samo masu kula dasu toh meye zai wani ce ki koma", tab'e baki Jainaba tayi tace "jarababbe d'aya ko biyu, ni da kaina bansan mey zan mishi ba, ni Lagos dinnan ba sonshi nakeba, zama cikin k'abilu ba iyawa zanyi ba", "Mum tace rabu dashi tashi muje inda zamu, zamuyi maganinshi ne ai, so nake inyi maganin wannan sallamammiyar yarinyar nan da batasan mey takeyi ba, wai har ni take cewa babu ruwanta in wannan tsinanniyar ta mutu, kai nasan ba banxa ba har da sa hannu Ajiddeh da hankalinta baxa tayi haka ba", Jainaba tace "Nima haka nake gani wllh in banda haka yaushe ne Ajiddeh zataji tausayin wanna yarinyar, tsanar da tayi mata koda wuk'a aka bata tsaf zata kasheta amma lokaci d'aya ta wanice ita ba haka ba, gaskiya da ayar tambaya", Mum tayi k'wafa tace "ni tashi muje inma yi mata akayi inma yin kanta ne duk zasuci uwar ubansu, badai ni Bilkisu tayi shirin tozartawa ba, ta Allah ba tata ba, ki taso muje kada raina ya kuma b'aci", Mik'ewa Jainaba tayi tace "muje", a parking lot suka had'u da Daddy zai fita, tsuru tsuru suka tsaya suna muzurai kamar wasu munafukai, har zai shiga motar ya fasa ya kallosu, a d'arare Mum ta k'arasa gurinshi tace "yanxu nakeson shiga wajenka, ashe har zaka fita", kallon shigar dake jikjnta yayi alamar fita zatayi yace mata "ki sameni a part d'ina", ya kalli driver da guard d'inshi yace musu "zaku iya tafiya", da haka ya juya ya koma ciki, gaban Mum na fad'uwa tabi bayan Dad, tasan shi ba mai magana bane kan abu koda yana damunshi amma inhar yayi magana toh lallai abin ya girmama, babban parlour shi ya koma ya shiga tana biye dashi a baya, waje ta samu ta zauna bayan ya zauna cikin nutsuwa yace "Ina Zainab ta tafi sati d'aya kenan rabona da ita", murmushi ta k'irk'iro tace "Laah ai tana gidansu Salma, ai inace ta fad'a maka kafin ta tafi tunda Salman tayi kwana biyu da zata koma shine suka tafi tare", kai ya kad'a yace "Zuwaira keh yanzu zaman yarinyar nan gabanki bai isheki ba har sai ta had'a da yawo", ido ta wara tace "Bafa yawo ta tafi ba, gidansu Salma taje ko nan dinma yawo ne", kallonta kawai ya tsayayi yama rasa mey zaice mata can yace "shirin ina kuma kikayi keh yanzun", tsuke fuska tayi ta had'e rai tace "Y'ar Sa'adatu da akayiwa aure kwanaki toh ta haihu kuma aiki aka mata shine zanje dubata a asibiti", d'an k'aramin tsaki yaja snn yace "in baki nutsu yanzu ba Zuwaira sai yaushe zaki nutsu, shekara kusan nawa da aure kin haifi yara har sunyi aure suma amma bakisan abinda ya kamata ba, ba dole a sako miki y'a ba tunda abinda taga kinayi shi zatayi a gidanta kuma su na tabbata da hankalinsu shiyasa suka dawo miki da y'ar, tunda abinda kike so kenan sai ki barta tayi ta shirme kina biyeta, aikinki kenan kullum bin k'awaye kamar wata yarinya k'arama? da girmanki bakisan kula da miji ba, gabaki dayanshi hakkin auren ma ba saninshi kikayi ba", had'e rai tayi tace "Nasani ai dama cin fuska zakamin, zumunci zaka hanani yinshine, menene a cikin auren da banayi maka masu aikine gasu nan kai kake biyansu, komai sunayi, so kake sai in riqa zuwa ina baka abincin a baki ina maka wanka, dududu ma sau nawa ake ganinka a wata, ni wlhy bazan iya da zaman matsi kamar wata y'ar k'auye ba, a matsayinka kamata yayi ina matar perm sect ace duk bayan sati biyu bana Nigeria, ka tsare ka hana kuma cikin gari ma ka hanani, wlhy bai yiwuwa, exposure ko wane irine yaci na ganshi amma duk kabi ka datse, toh ni ban iyawa", kallonta kawai yakeyi da mamaki, murmushi yayi yace "Tashi kije", dan yasan babu abinda zai fad'a taji tayi aiki dashi ta riga da tayi nisa, babu kunya ba tsoron Allah ta mik'e ta kad'a gyale ta fice daga parlourn Da murnarta ta kara wayar a kunnenta tace "Hello Aunty ina wuni", sai kuma ta fashe da kuka, "Yasalam", kawai Abu ya iya furtawa snn ya rungumeta yana kad'a mata kai alamun tayi shiru ta bar kukan da takeyi, daga d'aya b'angaren Aunty tace "Kukan na meye kuma Batuul sai kace wata Yusra, ya jikinki", cikin sheshek'a tace "Aunty naji sauk'i, Aunty inaso inzo in ganki", ji tayi Abutturab ya sassauta rik'on da yayi mata ya saketa ya ja baya, kallonshi tayi idonta cikeda hawaye, maganan Aunty ya katseta daga kallon da take mishi Aunty tace "keda bakida lafiya yawon mey zakiyi, kiyi zamanki har sai kinji sauk'i sai kizo kinji", kamar Auntyn na gabanta ta kad'a kai a hankali tace "Toh", Aunty tace "yawwa maza goge hawayenki bana so a ganki kina kuka kinji, ga Yayya nan za a kai mata wayan kuyi magana da ita", muryan Yayya taji tana cewa "Kaji ja'irar yarinya kukan na meye kikeyi, yaro na zaman zamanshi kinsa ya baro aikinshi, laulayin cikin kikewa wannan rakin, maga yadda zakiyi idan lokacin haihuwar tayi", Zumb'uro baki Batuul tayi tace "keh ina ruwanki, wama ya fad'a miki hakane", Yayya tayi dariya tace "zauna can, ina uwargida har sai an fad'amin, maigidan naki da kanshi duk sati sai ya kiran a waya kuma duk ya fad'a min tab'arar da kike mishi, ai nace mishi ma had'ani dake zaiyi in wuce dake Yerwa, maga ta fad'i", Batuul tace "keh Yayyan nan ko, babu inda zan biki, wajen Aunty kawai zanje", Yayya tayi shewa tace "Aunty taki ma basai in tafi da ita Maidugurin ba, dama naji tana wani rarrashinki dan lalacewa, ita ke dad'a tunzuraki nasani", "Ni kinga tunda ba abun arziki zaki fad'amin ba sai anjima", Yayya tace "gantalallu duk halinku d'aya da y'an uwan naki, ku masu uwa ba'a fad'in lafinta koh, in Baban naku ya dawo ya kawoni gun naki dan ni na raba kaina da tuk'in gantalallun k'annenki, wataran sai nasa shi Baban naku ya tasa su su d'auki tasu uwar suyi gudun da sukeyi dani akan titi, mugaye kawai", dariya Batuul tasa tace "toh keh ki koyi tuqin mana nan gaba basai ana gudu dake ba", Yayya tace "Ina nan tafe ne badai dariya kike min ba", haka sukayita hira, saida suka gama wayan ta kalli Abu dake daddana wayarsa, saida gabanta ya fad'i ganin irin kallon da ya jefeta dashi, zatayi magana yace "tashi ki shirya in kaiki", kallonshi tayi tace in shirya? Ina zaka kaini?", mik'ewa yayi ba tareda ya kalleta ba yace "inda kika gama cewa zaki yanzu", raurau tayi da ido ganin he is so serious, hawaye ne ya cika idonta, a hankali ta tako gabanshi tace ta fad'a jikinshi ta fashe da kuka, cikin shesheka tace "Yaa Abu nifa kawai na fad'a ne, am sorry toh na fasa, kaji bazan sake cewa Zani ba dagaske", hannu yasa ya zagayeta, hakan da yayi ya sata sauk'e ajiyar zuciya, ya d'aura fuska kan gashin kanta tareda lumshe yana shaka'ar kanshinta mai dad'i yace "Its okay, bana son kukan nan", da sauri ta d'ago tace "kayi hakuri dagaske?", kai ya gyad'a mata yana murmushi yace "I can't be angry with you Fatima, bana so kina tadawa Aunty Hankaline, in taji kina kuka she might think wani abun ke damunki", sake k'ank'ameshi tayi tana girgiza kai tace "nace bazan sake ba", ya sunkuyo yayi pecking lips d'inta yace "that's my princess, muje Malamin na jiranmu", Hijab d'in da ya gani kan gadon ya janyo yasaka mata ya riqe hannunta sukayi waje. Suna fitowa corridors ta kallesa a hankali tace " Ya Abu ina take?" Ya d'ago kanta yace "Wa?" Ta d'an yi shiru sai kuma tace "Ita" sai a sannan ya tuno da Ajiddeh ya d'an bude ido yace "Ohh Ajiddeh? She might be at the parlor" daga haka ya ja ta suka sauko parlor, janye jikinta ta shiga kokarin yi daga nasa jin muryar Ammah da Anty Amnah a parlon da alama shigowarta kenan don gaisawa suke da Ammah Am not actually so good with words but imma thanking these lovely girls for their love Meenarh parrot💖 Rahma lurv💖 and every single soul that loves BATUUL💖💝 [11/15, 11:15 AM] ‪+234 810 957 2036‬: 💖💝BATUUL💖💝 83 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Bayan Mum ta bar parlour rai b'ace ta fito ta dawo parking lot, da k'arfi ta shiga k'walawa driver k'ira, a guje ya taho yace "Hajiya gani", kallonshi Kawai tayi ya ciro makulli daga Aljihu ya bud'e motar ya fad'a, daga ganin yanayin yayar tata tasan ba lafiya ba, batace komai ba saida ta Shiga ta zauna tace "Yaa Zuwaira mey ya sameki naga kin canza daga shiga ki fito, wani abun ne ya faru?", Mum taja wani dogon tsaki cike da masifa tace "Dan uwarka kai jahilin ina ne iyye?, ina zaka kaini da ka karyo kwanan nan", Driver da duk ya rikice yace "Hajiya ranki shi dad'e ca nake kasuwa za....", bai gama rufe baki ba a hasale tace "bukkar uwarka zaka kaini ba kasuwa ba, shasha Kuje zamu, jahili", shidai baice komai ba dan inda sabo ya saba indai ran Mum b'ace yake a rana toh sam bai son ya zama shike duty, jiki a sanyaye yace "Ayi min afuwa Hajiya, kuskure aka samu", daga haka ya d'auki hanyar Kuje, Jainaba da ta gama tabbatarwa babban abune ya tab'a Mummy ta tab'a baki tace "Wai Daddy ne ya bata miki rai", Mum tayi k'wafa tace "Abun nayi ne Jainaba, wato ina saka ban sani ba warwara nakeyi, bamuga ta zama ba, wannan karan da zafi zamu shigi kowa, da zafi zafi akan daki k'arfe, bazanyi sanya ba wannan karon, sai naci uban kowama, baza a d'aga min hankali ina zamana ba wlh sai nayiwa abun tufkar hanci", wayarta ta d'auko daga gefenta ta shiga dialling number tasa a kunne, har ya katse ba a d'aga ba, Jainaba taja d'an siririn tsaki tace "Yaa Zuwaira nifa bakice min komai ba har yanzu, mey ya faru kuma banda matsalar Ajiddeh", Mum ta sauk'e wani nannauyan ajiyar zuciya tace "Shifa wannan baban nasu ne ya sani gaba da surutunshi na banza da wofi, akan mene zai dameni nida rayuwata, kinji wai wa'azi ya zauna zai min wai ina abubuwan da basu dace ba", Jainaba tayi dariya tace "baki mik'a mishi microphone ba dan kifi jin wa'azin da kyau", Mum tace "birki na taka mishi, inji da abinda shashashar yarinyar ta Sani ko kuma in biye mishi ya dad'a bata min rai, kuma fa duk sai nayi maganinsu, in banda taurin kanshi ma na jaraba duk abinda akayi kwana biyu yake barin jikinshi amma dai wannan karon alwashi naci sai na samu komai yadda nakeso", Jainaba tace "Yaya wai ina laifin wannan karan ayimana yadda Daddy kullum komai nashi zai koma naki, a badda hankalinshi da tunani ya zama komai a hannunki", Mum tayi k'wafa tace "Dan ubanki wace makarantar nayi da zan iya riqe wadannan abubuwan, ai sai yanxu nake takaicin kin zuwa makarantar da nayi ina Karama, da yanzu komai nashi nasan takansu", Jainaba tace "Ai ba sai Lallai ke din ba, dama su Zee ne zasuyi ai", "kinga fa dad'a tunzurani kikeyi kina b'atan rai, wadanne yaran marasa wayo ne zasuyi min abin kirki, kiga kayan takaicin da Ajiddeh ke k'unsa min, itakuma Zainab in banda yawo kamar wata hadari a cikin gari babu abinda takeyi, kedai bari duk na kusa kawo k'arshen komai", Jainaba tace "Toh Allah yasa", Mum taci gaba da k'iran wayan Zee da har lokacin taqi d'auka, Driver dake gaba yana jin komai Addu'a ya riqa Allah ya rabashi da masu irin halin Mum, kamar kullum yauma tafiya mai nisa sukayi kamin su isa gurin bokan nasu, da zuwansu Mum ta gama zayyane mishi duk abinda ke tafe dasu, k'asar dake gabanshi ya buga yace "itafa wannan yarinyar abinda muka tura Mata yana nan jikinta har yanzu kuma yana kan aiki saidai bansan mey ya hana aikin ci ta mutu ba, dan yaci ace ta mutu tun bayan kwana biyu", Mum tace "gaskiya ne yana aiki dan y'ar tawa da nayi maka bayani tanason kawo mana matsala tace min mutuwa zatayi, in da yadda za ayi ranka shi dad'e ta mutu a huta, kaga in ta mutun, ta wajen nawa zata dawo hankalinta sai musan nayi akanta itama", haka dai Mum ta dinga Zayyanowa boka abinda za ayi tun daga kan Daddy, Ammah, Abu da kuma Batuul, boka yace indai jaka a bud'e take zasuga aiki da cikawa, nan ya duk'ufa ya fara da na Batuul, Suna zaune a wajen wayar Jainaba ta shiga ringing, saida aka kira wajen sau shida snn ta d'aga, shiru tayi tana sauraren mai magana a wayan, sai da yayi shiru tace "Toh naji", ta katse wayar, boka ya gama masu tsubbe tsubbensu yace "kuje, kamin ku k'arasa gida zaku ci karo da lbrn mutuwarta" da murna fal ransu suka zube mishi kudi suka tashi akan zasu dawo in da wata matsalar, sai da suka fita zasu gun mota Mum tace "Wane d'an iskan ne yake damunki a waya, yaga baki d'au na farko ba ai sai ya rabu dake koma wani jarababben ne", Ajiyar Zuciya Jainaba ta sauk'e ta tab'e baki tace "Idrees ne", Mum taja tsaki tace "Shifa wannan k'aramin mara kunya ne, ko ba d'azun nan ya k'iraki ba", Jainaba tace "Shine ya k'irani, wai tuna min zai sakeyi indai ban dawo gobe lallai lallai ba toh inyi zamana a inda nake ba sai na dawo ba", Mum taja tsaki tace "Karamin mara kunya, sai yazo ya kinkimeki ya maidaki", da haka har suka isa mota Driver ya tada sukayi gaba suna ci gaba da hiran abinda zai faru Aunty Amna dake tsaye tana magana ta hango Abu rik'e da Batuul suna sauk'owa downstairs, juyawa tayi ta dubi Ammah snn ta juya tayi stairs d'in, tana zuwa ta rungumo Batuul jikinta tace "Ayyyyy Batuul Habibty, bakiji dad'i ba ashe, Allahumma yashfiki, Allah yasa Kaffara ne Allah ya k'ara miki lafiya, baiwar Allah kina zamanki mutane na binki da sharri, kiyita Addu'a kinji, In sha Allahu duk wani mugun nufinsu akanki bazai tabbata ba da izini Allah", murmushi Batuul tayi tana tunanin maganganun da Aunty Amna ta gama fad'a mata yanzu, ita bata gane ma zancen mey takeyi ba", lumshe ido tayi ta bud'e snn tace "Namafa ji sauki Alhamdulillah Anty", Aunty Amna tace "Zaki warke kinji, Allah ya rabaki da sharrin masharranta", daidai nan Ajiddeh ta fito d'akin Abu zata sauk'o down stairs itama, jin maganan da Aunty Amna keyi yasa ta kasa d'aga k'afarta kuma, ta tsaya tana kallonsu, Aunty Amna ta dubi Abutturab da ya had'e rai tace "kai kuma yarinya batada lafiya kaje ka ajiyeta baka fadawa mutane ba", hannun Batuul ya janye ya dawo da ita gabanshi yace "Bata fa jin dad'i, she is weak", wara ido Aunty Amna tayi tace "Iyye, kaji mara kunya, da kasan she is weak ka barta tana shan wuya a can, kai a dole mai mata ko, ai sai ka kinkimeta tunda she is weak" sunkuyar da kai Batuul tayi dan kunya, kamar jira yakeyi ko sai gani sukayi yasa hannayenshi duka biyu zai d'auketa, wara ido Batuul tayi tareda matsawa baya tana girgiza mishi kai alamun kar ya mata haka, kamar bai gane mey take nufi ba ya sa hannu ya kamota zai d'agata taji kamar ana kulle mata ciki ta fasa wani razanannen k'ara da yafi na ko yaushe had'e ta rike cikin tana kiran Anty da kyar, lkci daya ta sulale yayi maza ya bita ya kamata a rikice yace "Ya salam, Not again baby, you will get well soon", Aunty Amna da ta tsaya kallon tsiyar Abutturab a tsorace da jin karan ta tsuguna itama ta kamo Batuul duk ta rud'e tace "Abu ciwon nata ne", kasa bata amsa yayi sai d'aukarta da yayi cak yayi k'asa da ita yana k'iran sunan Ammah, Ajiddeh da ke tsaye har lokacin tana kallonsu idonta ciccike da hawaye ta kasa d'aga k'afarta, ta rasa me ke mata dadi a duniylar, ganin yayi k'asa da Batuul ta fashe da kuka ta koma d'akin da take da sauri, a rikice Ammah ta fito tana tambayan mey ya faru, Farida da Sadiq dake side d'in Abui tare suka fito suna tambayan mey ya faru, Aunty Amna ma na tambayarshi ko ciwon nata amma ya kasa ce mata komai sai sunan Ammah da yake k'ira yana girgiza Batuul d'in ta tashi, Gaba daya duk sun rud'e kowa ya rasa abinda zaiyi ganin jikin Batuul d'in duk ya saki, Farida na kuka tace "Ammah ni kam nace ku kaita wajen Dr Zakaa zai dubata ya fad'a mana abinda ke damunta," hawayen dake idonta ta goge tace "Sadiq Abui na Guest room tareda bak'onshi, kace ciwon nata ya dawo", a rud'e Sadiq d'in ya amsa ya fita amsa aiken da Ammah ta mishi, da k'yar Ammah tayi k'arfin hali ta kamo Abun dake riqe da Batuul ya kasa cewa komai tace "Babana kawota ka kwantar da ita, zataji sauk'i In sha Allah, yanzu za ayi mata magani", ta fad'a tana k'ok'arin karb'an Batuul daga hannunshi, girgiza kanshi yakeyi hawaye na gangarowa idonshi, zama yayi kan kujerar Batuul na rungume jikinshi, gefenshi Ammah ta dawo ta zauna zatayi magana kenan Abui yayi sallama shida Ashiekh da Sadiq, Abui yace "Subhanallahi, jikin nata ne kenan", Abu bai iya cewa komai va don shi kadai yasan mey yakeji cikin ranshi, bayason kowa ya tab'ata sbd fargaban abinda za a ce mishi ya biyo baya, bayajin ko d'aya daga cikin nerves da pulses d'in jikinta na aiki, Ammah ce ta kawo hannunta ta rik'o na Batuul d'in, gabanta ne ya rik'a fad'i ganin hannun Batuul d'in ya saki, d'agowa tayi tana kallom Abu da idanunshi suka kad'a, lumshe ido yayi snn ya bud'e yace "Ammah babu abinda ya sameta ko?, I know she will be alright, nasani Fatima zakiji sauk'i i know you won't leave me just like that isn't it Batuul, you have to get up", Aunty Amna Abui ya kalla yayi mata alamun taja Farida da Ammah da ta matsa baya tana girgiza Kai, hakan ko tayi ta kama hannun Ammah tace "Ammah zataji sauk'i fa, ba dama haka yakeyi mata ba, yanzun nan zata farfad'o, muje muyi mata addu'an samun sauk'i", Itama Aunty Amna k'arfin hali kawai takeyi gaba d'aya jikinta yayi sanyi sai hawaye da takeyi, Farida ce ta karb'e hannunta daga rik'on da Aunty Amna tayi mata ta dawo gaban Abu ta tsuguna dab fuskar Batuul d'in tana kallonsa hawaye na sakko mata tace "Yaaa Abu saida nace maka a kaita asibiti fa, don Allah mu tafi", ta kalli Abui dake tsaye ta mike ta isa kusa da shi cikin kuka tace "Abui don Allah nace mu kaita asibiti da yanzu ta warke, ka ganta yanxu kwance ko motsi batayi, Dan Allah muje a kaita", Hannu Abui ya d'aura kanta ya shafa snn yace "Babu abinda ya sameta kinji, zataji sauki" yacewa Sadiq " *Sadiq tai sha samiro Leno*, Sadiq kamata ka kaita sama", tana girgiza kai tana kuka haka Sadiq ya jata yayi sama da ita ya rage daga Abui sai Abu dake riqe da Batuul snn Asheikh, Asheik ya dubi Abui yace "Alanguro akwai Zamzam a kusa?" Abui yace "Ehh bari a d'auko", [11/15, 11:15 AM] ‪+234 810 957 2036‬: 💖💝BATUUL💖💝 84 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Wani nannauyan ajiyan Zuciya Aunty ta sauke lokacin da Yusra ta mik'o mata wayanta tace "Mama ga wayan inji Yayya wai ta gama", karb'an wayan Aunty tayi tace "Kuje ku shirya, its getting late, kice wa Fa'eezah a gama sa muku kaya ku tafi", kai Yusra ta kad'a tace "Toh Mama", daga haka ta fice tana tsalle, wayar ta sake janyowa ta dialling number Baba, ringing biyu ya d'aga, jin muryan Aunty a sanyaye ya sashi saurin cewa "mey ya samu muryanki haka, its so weakening", kamar jira takeyi taji muryan Baba hawayen dake cike idonta ya gangaro, ido ta bud'e ta lumshe snn tace "Uncle ashe Batuul ce bataji dadi ba saida aka dawo da ita d'azu Ammah tamin waya tana fad'amin wai sun dawo da ita tana can gidansu, shine nakeso in ganta koma mu taho gidan tare, we should treat her here a gida hankalina sam yaqi kwanciya, inason ganinta Uncle", "Maryam", Baba ya kirata daga d'aya b'angaren, kasa amsawa tayi har saida ya sake cewa "Maryam", kuka ta fasheda ta kasa amsa kiran da yakeyi mata, Baba dake zaune office yace "Subhanallahi Maryam kuka kuma, mey kikeso?", cikin sheshekar kuka tace "Uncle gida nakeso ta dawo, hankalina zaifi kwanciya in ina ganinta, kaga fa cewa Ammah tayi batasan mey ke damun Batuul d'in ba, toh haka zatayi ta zama da ciwo ba'a nema mata magani ba Uncle", D'an Murmusawa Baba yayi yace "Haba Maryam, kada son y'arki ya rufe miki ido ki manta da cewa tanada aure, kinfi kowa sanin yanzu duk wani nauyi da responsiblity d'inta na kan mijinta, in kikace zaki dawo da ita gabanki bakya tunanin kin musu shishigi har ma suyi tunanin gazawar su muka gani, am very sure kin san su masu kula da Batuul ne dama duk sauran yaran nan ko bama nan", tana share hawayen dake zubo mata tace "Uncle nifa bawai gani nayi sun kasa ba, rashin sanin takamaimai abinda ke damunta da ba ayi bane yafi d'aga min hankali", Abui yace "Duk naji wannan, ki kwantar da hankalinki da izinin Allah zata samu sauk'i, tunda shi Aliyun ya sanar dani rashin lafiyarta, yanzu haka sun d'auko masu magani ana dubata, kiyi mata add'ua sosai kinji, sai kiga ta samu lafiya kamar da, amma in taga kina tada hankalinki itama nata hankalin kinsa tashi zaiyi", kamar Baban na gabanta ta shiga gyad'a kai tana share hawayen fuskarta, da haka ya samu ya rarrasheta ya kwantar mata da hankali Sadiq ne ya d'auko Zamzam d'in da ake buk'ata a side d'in Abui, a cup Asheikh ya d'an tsiyaya snn ya samu waje ya zauna ya fara tofi cikin ruwa, Abu dai har lokacin ya kasa cewa komai sai ido da ya zuba mata idonshi duk ya kad'a, motsin kirki ya kasa yi, he is so freaked, gani yakeyi duk wanda ya tab'ata ce mishi za ai ta bar rayuwa, Asheikh da ya gama tofin shi ya miqe ya dawo gaban kujerar da Abu ke riqe da ita, Abui yace "Aliyu ko zaka samu a gyarata tasha maganin", kamar badashi akayi maganan ba, saida Asheikh ya sake maimatawa snn ya d'ago rinannun idanunshi dake cike taf da hawaye kamar wani yaro, kai Abui ya kad'a mishi alamun he should be strong tare da zuwa kusa dashi ya zauna ya dafa mishi kafad'a yace "Abutturab you have to be strong okay?, zata samu lafiya In sha Allah kaci gaba da yi mata addu'a, ido ya lumshe snn yace "Abui bata mutu bako, baza ta mutu ba In San Allah", sosai Abui ya tausaya mishi yace "ciwo ai ba mutuwa bane Aliyu, zataji sauki da yardar Allah, kayi yadda yace d'in ka kwantar da ita a nema mata lafiya", gani yakeyi kamar in ya sauketa daga jikinshi wani abun zai sameta, kallonta yayi for some seconds snn jiki a sanyaye ya shimfid'eta kan doguwar kujerar amma har lokacin hannunta na cikin nashi, Asheikh ya karaso gaban kujeran ya tsuguna daidai kan Batuul snn ya mik'awa Abu ruwan yace "amshi ka shafa mata a fuskarta", hannu Abu ya mik'o ya tsiyaya mishi ruwan snn ya shafa mata shi a fuska, bayan ya gama ya sa a mik'o k'aramin spoon yace Abu yana sa mata droplet a baki, jiki a sanyaye ya anshi cup d'in ya d'ebi kad'an ya d'iga mata shi a baki, wani irin dogon numfashi taja da ya sa Abu saurin kamota yace "Batuul am glad you are alive, don't leave me again kinji, don't plsss", sai ga hawaye nan idonshi, bata bud'e ido ba haka nan batasan abinda akeyi ba, kamar ba ita tayi wannan numfashin ba ta koma yadda take d'azu, Asheikh yayi gyaran muryan yace "Alhamdulillah, wannan ruwa da ta sha ya dad'a tabbatar mana da lallai asiri akayi mata kuma yana nan cikin jikinta, yawo yakeyi gaba d'aya jikin nata dan a ruwa aka jefa sihirin da akayi mata, yadda yake yawo cikin ruwa haka itama yake yawo cikin jikin nata snn gaba d'aya rayuwar aka so ta bari da ita da abinda ke cikinta amma da yake Allah yayi tana da saurin numfashi bata mutu ba sai dai za a ci gaba da magunguna snn anayi mata sauk'ar Qur'ani da kuma tofi kullum, In sha Allah da yardar Allah zata samu sauk'i", Abui yace "Subhanallahi, La hawla wala quwata illa billahil aliyyil Azim", Sadiq dake tsaye shi ma tun d'azu ya rasa ma abin fad'a, yanzu har Batuul abar ayi ma asirice, duniyan nan is so cruel, Allah ya bata lafiya su kuma Allah ya toni asirinsu koma su waye sukayi mata", kamar wanda aka tsikara haka Abu ya mik'e ya isa gaban Asheikh yace "Asheikh inaso in san su waye sukeson cutar da ita da dalilinsu na cutarta, yanzun nan bama sai anjima ba, Ko su waye su sai nasa sun gane kuaransu na cutar min mata da sukayi", Asheikh yayi murmushi yace "Toh mu dai baza muce ga wadanda sukayi mata ba har sai ta samu sauk'i, in akwai likita sai a samoshi ya riqa dubata da abinda ke jikinta, snn tunda ba abinci zata ci ba, su sai su duba suga yadda za ayi tana samu, mu kuma a namu b'angaren zamuyi kok'arin ganin mun taimaka da addu'a", Jinshi kawai Abu yayi amma ba wai ya aminta da zancen ba, Abui yace "Toh Asheikh mun gode sosai", yace a k'ira mishi Aunty Amna ko Ammah yayi musu bayanin sauran magungunan nata da yadda za ayi amfani dasu, Aunty Amna ce tazo amma Abu sam ya kasa ya tsare sai shi aka bawa magungunan yace "Zaitun d'in za a riqa shafa mata shi a dukkan jikinta, Ma'ul ward d'in kuma ana d'iga mata shi a baki, kad'an kuma a saka a wool a kai mata hanci ta shak'a, Habbatus saudanma jikinta za a riqa shafewa dashi kamin ta kwanta, Abu ne ya anshi komai. Tuk'i sukeyi hanyar Jere, Driver sai dariya lbr raha yake yi yana kyakyatawa, yana son fita irin wannan da Dad keyi ba tareda entourage d'inshi ba, kamar daga sama sai ganin mata sukayi sanye da Hijab d'inta ta shigo titin a guje, ji kake k'iiii ammma ina saida suka buge ta, daga nan sukayi losing control d'in tasu motar, Babu abinda Daddy yake fad'i sai "Innalillahi wa inna illaihi rajiun", abinda ya dinga nanatawa kenan har motar taje ta bugi wata bishiya snn motar ta tsaya, kan kace meye mutane har sun cika wajen wasu suna wajen matar da aka buge wasu kuma sunyi wajen motar, jin surutun mutane yasa Dad sanin lallai da sauran ransu, a hankali ya d'aga hannunshi da yakeji kamar ba nashi ba ya tura k'ofar motar, Driver dake gaba sai faman kokuwa yakeyi da airbag da ya rufe mishi fuska, mutanen dake wajen ne suka taimaka musu suka fito daga cikin motar, daga can Side d'in sukaji ana ihun "ta mutu", wasu suna "ba mutuwa tayi ba ayi saurin kaita asibiti", da sauri Daddy ya karasa gurinsu, ganin matar taji ciwo sosai yasa cikin hanzari yace "Dan Allah bayin Allah akwai wani wanda ya santa cikinku sai muje dashi asibiti dake cikin gari", duk mutanen dake gurin kowa yace su gaskiya basu tab'a ganinta ba, haka duk suka riqa zuwa suna kallonta suna basu santa ba, ganin ana b'ata lokaci yasa Dad yace musu "Toh koh zaku had'a mu da wani da kuka yarda dashi mu tafi asibitin dashi, sai yaje ya gano inda muke ko daga bayane in Allah yasa an samu y'an uwanta sai mu dawo da ita", duk yawan mutanen dake gurin nan kowa mak'e kafad'a yayi yace shi baxa shi ba, Mutumin birni ba abun yadda bane", d'an k'aramin tsaki Dad yaja yace "Ado zo mu taimaka mu sata mota, mutanen nan ba lafiya ne dasu ba", Ba b'ata lokaci Ado yazo suka kamata suka sata mota, mutanen ganin dagaske suke tafiya zasuyi da ita yasa suka kama surutu, kota Kansu Daddy baibi ba yacewa Ado yaja motar su tafi, Abuja suka karaso direct suka wuce asibiti lokacin ana kiraye kirayen Sallar Magrib, suna zuwa aka karb'eta aka fara bata taimakon gaggawa Bayan Asheikh ya koma guest side ne Abu ya d'auki Batuul yayi d'akin Ammah da ita ya kwantar da ita kan gado, ya jima yana yi mata addu'a da fatan samun lafiya kamin Ammah tace yaje ya watsa ruwa yayi Sallah dan ko azahar da la'asar d'inma duk a gida yayisu, sam yaqi barin wajenta, abinci kam har lokacin ba a samu ya shiga cikinshi ba, tunda ya dawo sai yanzu ya shiga d'akinshi, gaba d'aya ya manta da zancen wata Ajiddeh a gidan, ajiyar zuciya ya sauke ganinta zaune bakin gadon kamar mai jiran ace cas ta sa gudu, K'araswa yayi cikin d'akin ya zauna kan gadon tareda riqe kan da duka hannayenshi, a hankali ta dawo gefenshi ta zauna ta d'an dafashi tace "Sannu, how is she feeling now?", bai bata amsa ba sai rungumeta da yayi tsam a jikinshi, har saida ta tsorata jin irin force d'in da yasa a hug d'in, kok'arin kwace kanta takeyi amma sam bai saketa ba, maganganun Asheikh kawai yake tunawa da yace da abinda akayiwa Batuul ta fara wannan ciwon, a hankali ya d'aura fuskarshi kan wuyanta ya fara magana a hankali "I can't risk losing her for anyone, they were trying to hurt her, so suke su rabata da rayuwarta, Mey tayi musu zasu maka haka?", kyarma jikin Ajiddeh ya fara bugun zuciyarta ya tsananta har wani danshi takeji yana bin jikinta, saketa yayi ya rik'o kafad'unta yace "Hauwa do you know they wanted killing her?, an encounter with them will have to b their worst nightmare, I will make them pay for each pain they caused her", da sauri Ajiddeh ta d'ago itama idonta duk ya cicciko da kyar tace "Its okay babe, they will surely pay for it, amma kasan su waye?", kai ya girgiza mata alamun No, ta saka hannayenta cikin gashinshi tace "Everything will b fine kaji, kaje kayi wanka, you need rest", mikewa yayi ya shirya ya shige toilet, baki Ajiddeh ta toshe ta saki wani irin kuka, tausayin rayuwarta ta fara, in dai Abu ya gano she is behind komai tasan zamansu ya xo karshe, har ya fito daga wanka tana nan inda ya bar ta, cikin few minutes ya shirya cikin kananun kaya ya dawo kusa da ita ya xauna yace " You also need some rest, ki tafi kiyi wanka, farida will get you something to eat sai ki kwanta" mikewa yayi ya fiddo mata da towel ya mika mata ta karba a sanyaye ta mike ta shiga bathroom din, kwanciya yayi ya lumshe ido ya dafe kansa da yayi masa nauyi, ji yake kamar ciwon Batuul ya dawo jikinsa kawai, da yake a gajiye yake gashi tun jiya rabonsa da bacci, lokaci daya baccin ya daukesa. Washegari Aunty Jainaba bata koma gida ba sai da ta k'ara kwana har biyu snn ta shirya Mum ta had'ata da kulle kullensu da suka koma gun boka suka amso bayan sun gama planning irin wulakancin da za ayiwa Idrees, shi da kanshi yaje ya d'aukota a airport, tun daga airport d'in taga yadda yanayin shi suka canza, ganin yana wani shan kanshi itama ta watsar da kashinshi a ranta tana ayyana yadda zataci ubanshi har suka isa gida, Babu kowa a gidan tasan duk yaran na makaranta masu aiki na b'angarensu, d'akin ta bud'e ta shiga, turus tayi ta tsaya ganin komai na d'akin an canja shi snn ga jerin sabbin akwatuna an a d'akin har set uku, juyowa tayi zata mishi magana cikeda bala'i, dama kan wannan surprise d'in nashi ne ya sata baro aikin da takeyi can Abuja ta taho amma ganin ba fuska ta kasa bud'e baki [11/15, 11:15 AM] ‪+234 810 957 2036‬: 💖💝BATUUL💖💝 85 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Cikeda masifarta take kallonshi, shiko karasowa yayi hannunshi cikin aljihun wandonshi yace "Sit!, magana zamuyi", kallonshi ta tsaya yi a tsagere kamin ta zauna ganin duk ya canja mata kamar ba Idrees d'in dake shakkarta da gudun b'acin ranta ba, wanda in ta fad'i abu jiki na rawa zai d'auki maganan, had'e rai tayi ta dake tace "Wai kai yanzu sabida tsabar wulakanci kan wadannan tsinannun kayan naka kasa na taso na baro muhimman abubuwan da nakeyi a Abuja na taho Lagos?, toh wlhy yanzu maza maza ka kwashe tsiyarka kuma gyaran ma ni ba irin wannan nace maka inaso ba ai", ba yabo ba fallasa ya fara magan yace "Tun baki san kayan mene ba kike wannan b'ab'atun, toh kaya dai nakine in baki sonsu ki zubar dan haka al'ada yace min kuma itama d'in haka nayi mata", katseshi tayi da hannu tace "Kayi wa uwar wa irin wadannan kayan, dan cin mutunci irin naka ma ba ni kadai kayiwa wadannan kayan ba harda had'ani da banzaye, nasan bazai wuce wad'annan masu kafar sauron bane da ke yawo a cikin gari kayi mana tare dasu, nasha fada maka ka dena had'ani da wadannan matsiyatan kana mana kaya tare......", bata rufe baki ba sai ji tayi yace "Aure zanyi next week, Kayan fad'ar kishiya ne gashinan snn wannan yawon naki daka yau kin barshi kenan, in har badaa izinina kika fita ba toh koma inane kikajeshi karki dawo min gida, kiyi zamanki a can", brain d'inta ne ya dena functioning for a minute, kamar a planet Neptune take jinta sbd yadda taji tana yawo saman iska, komai na juya mata, ido kawai ta zuba tana kallonshi har saida hankalinta ya dawo snn ta miqe tana cire duk wani abu dake kanta dan ji takeyi sun mata nauyi, takowa tayi tazo gabanshi tana mishi wani mugun kallo tace "Kace meye?, Aure?, Idrees ashe ko lallai zaka tafka babban kuskure na rayuwanka da baka taba yi ba wlhy, tun wuri ka gyara maganarka, kai d'in banza har ka isa tozartani kayi min kishiya?, wlhy Allah baka isa ba, bamu gaji ayi mana kishiya ba, You had better take back your words tun muna mu biyu da kai kamin duniya ta jimu, kai ka ma isa kayi aure, toh duk munafikan da suka saka yi dan ganin bayana sunyi kad'an, Ka koma kace musu ta Allah ba tasu ba ni nafi karfinsu, ai babu mai yimin wannan tijarar ni nasani inba wannan tsohuwar da ka ajiye can gida ba", Tasss ya d'auketa da mari da yasa hawayen dake idonta ya shiga zubowa, mik'ewaKame tayi cikin zafin rai ta cakumo rigarshi tana "Wlhy sai kasan ka mareni, munafiki kawai maci amana, azzalumi, wlhy ba ni ka wulakanta ba sai tsohuwar banzar da ko tafiya batayi daka ajiye a gida, kwace rigarsa da ta cukwuikuye yayi daga hannunta snn ya kara mata wasu lafiyayyun marin, cikeda fushi ya shiga bugunta ko ta ina, duka yakeyi tana ihu tana zage_zage, duka yayi mata sosai har saida yaga ta jikata snn ya jefar da ita yayi yace "Keh kinyi kad'an, nan gaba koda wasa kika kuma zagar min Family sai nasa kinyi regretting, keh d'in har wata matar kirki ce da baza ayiwa kishiya ba?, mey kika iya a auren da har zai hanani yi miki kishiya kullum in kika fice kika bar gari sai lokacin da kika ga dama kike dawowa, wane mijin ne zai yadda matarsa take irin wannan shashancin, Y'ay'an da kika haifa da kansu basu san dad'in uwarsu ba, basu taba samun time d'inki, I have finally made my decision, aure ne nan da sati biyu zanyi shi" ya tsallaketa yayi ficewarsa daga d'akin amma har lokacin bakinta bai mutu ba sai zazzaga rashin mutunci takeyi, da k'yar ta iya samu ta mik'e ta janyo jakarta ta ciro wayarta daga ciki, tana kuka ta shiga neman layin wayar Mummy, bugu d'aya ta d'aga daga d'aya b'angaren tace "Wai uwar mey ya miki da ya uzzura miki da dawowa, jarababbe", Jainaba ta fashe da wani matsanancin kuka tace "Nikam na shiga uku, Yaya kasheni yakeson yi", Mummy tace "Kasheki? Dan uwarsa shi ya haifake da zai kasheki, shege matsiyaci", Jainaba na sheshek'a tace "Yaya wai aure zaiyi shine ya kirani harda kayan fad'ar kishiya", Mummy ta buga k'irji ta miqe tsaye tace "Ni Zuwaira, Jainab Bakal Abuki, da hankalinki kike kiramin mijinki aure zaiyi?", Jainaba na kuka ta gama fayyacewa Mummy gaskiya da karyar abinda ya faru, Mum tasa salati, nan ta rarrashi Jainaba akan zasu nemo maganin matsalar snn suyi maganinshi, daga nn sukaci gaba da zaginshi da yadda za aci uban nashi daga nan sukayi sallama Tun da suka karb'eta sukayi emergency suka fara aiki akanta basu fito ba saida suka tabbatar she is fine, sai bayan awa uku suka fito suka barta ta huta bayan sun mata allura, Office d'inshi doctor ya dawo bayan ya sa an maidata Amenity, nan ya tarar da Dad zaune anyi mishi treating hannunshi da yaji ciwo, bayan ya zauna ne ya fara yiwa Dad bayanin abinda ya sameta "Sir she is fine, Yeah she had a minor cut on her at her back, some wounds on her head which made her lose a lot of blood, that's what cause the fainting and a broken arm, but she will be awake in some hours time and then she can be taken home", wani irin ajiyar zuciya Dad ya sauk'e jin tana raye snn zata samu sauk'i In sha Allah yace "Can we see her now?", Doctor ya kada kai yace "Yeah sure Sir, lemme calk the Nurse to lead you there", haka akayi yana danna bell Nurse ta shigo ya fada mata inda zata kai Dad da haka yayi mishi sallama tareda godiya yabi Nurse har d'akin da aka kwantar da matar, a hankali suka tura kofar d'akin suka shiga, kwance take abinta tana bacci amma da gani ba mai dad'i bane, sun canja mata kaya zuwa wani blue yard, tausayinta yaji a ranshi ganin duk an d'aura mata bandage, daga bakin gadon yace "Sannu Baiwar Allah, tsautsayi ya ritsa dake, Allah ya baki lafiya",,, sosai yake jin tausayin nata har ya fara tunanin ko ina y'an uwanta suke, yanzu hankalinsu gaba d'aya ya gama tashi duk Inda suke, Allah ya basu hakuri, da ta warke zai maidata gida yayi musu bayanin komai snn ta basu hak'uri game da tsautsayin da ya samesu, daga haka yacewa Nurse d'in zai turo masu zama da ita, da haka ya fita lokacin Ado ma an gama duba shi lafiyarsa kalau, sukayi waje suka nufi gida Tashi yayi ya zauna yana salati tareda fad'in "Innalillahi wa inna illaihi raji'un", juyawa yayi gefenshi yaga Ajiddeh kwance daga d'aya side d'in tana baccinta hankali kwance, mafarkin da yayi keh mishi yawo akai, cikin hanzari ya sauka daga kan gadon ya fita daga d'akin, d'akin Ammah ya nufa kai tsaye ya bud'e k'ofan ya shiga, ko ina babu haske, karasa shiga yayi snn ya kunna wutan bedside lamp, Batuul ya gani kwance sai juyi takeyi a hankali kamar wani abin ke damunta, goshinta duk yayi zufa, Tashi yayi maza yayi switching Ac d'akin, a nan yaga Farida dake kwance kan Sofa, stool ya jawo ya zauna gaban gadon yana kallon Batuul dake kad'a kai, siririn hawaye na bin kuncinta, hannu ya d'aura kan goshin nata tareda k'iran Sunanta shima yana jin kamar yayi hawayen "Fatima", a hankali, kamar taji kiran sunan ta bar yatsina fuskarta da takeyi, gumin ya soma share mata snn ya cire hular dake kanta ya fara tofa mata addu'a, tun tana motsi a hankali har ta dena alamun tayi bacci, nan ya zauna yana tofa mata addu'a har bacci ya d'auke sa zaune kan stool d'in, Ammah da ta shigo da asuba ta ganshi yana bacci zaune kan stool hannunshi cikin na Batuul sosai ta tausaya mishi, a hankali ta matso gabanshi ta d'an tab'ashi, a d'an firgice ya mik'e yana kallon Ammah, tausayin na fuskarta tace "Abu lokacin Sallah yayi kaji", kallon Ammah yayi snn yace "Ammah Batuul ta tab'a zuwa Ndjamena ne?", kallonshi tayi tana son gano wani abu snn tace "Menene?", Kai ya kad'a snn yace "No its okay, am just asking", bata matsa ba ta kyaleshi tace "Jeka masallaci kaji, lokacin zai wuce", mikewa yayi yana Kallon Batuul haka ya fita yayi nashi d'akin, Ajiddeh na nan kwance kamar kullum, wanka ya shiga yayi a toilet snn ya fito ya tadata yace tayi Sallah, har ya fita bata tashi ba, haka nan akaci gaba da yiwa Batuul magani, kullum doctor sai yazo ya dubata kuma, Ajiddeh sau d'aya in ta shigo ta dubata take komawa d'akin Abu, sai in an gama abinci ta sauk'o in taga dama, in kuma batayi niyya ba haka zata zauna, amma ko da wane lokaci gabanta fad"uwa yakeyi, ta rasa yadda zatayi da Mum har ta kashe wayarta gaba d'ayanshi, fargabanta d'aya kada Batuul ta farka asirinsu ya tonu, wata zuciyar nace mata ta fad'i gaskiya ko don son da take yiwa Abu amma sam d'ayar zuciyar ta haneta, bayan sati ranan da za a gama yiwa Batuul sauk'ar Al Qur'an ranan ta yanke shawaran fad'iwa Abu gaskiya koda zaiyi sanadiyyan rabuwarta dashi, daren ranan kasa bacci tayi sai juyi takeyi, har Abu ya fita ya barta idonta biyu, lokacin da ya dawo tashinta sallah ma zaune ya ganta tayi tagumi, kallonta yayi yace "Babe what's wrong with you?", ajiyar zuciya ta sauk'e tace "Ba komai", bai sake ce mata komai ba yace "tashi kiyi Sallah, its time", daga haka yayi hanyan waje "Har yaje bakin k'ofa yaji tace "Aliyu", juyowa yayi yana kallonta , kasa fad'a mishi abinda tayi niyya tayi jiki a sanyaye tace "Naga ka rame ne, you should rest, ka rage stress d'in", murmushi yayi mata kawai yace "I will babe, je kiyi Sallah" daga haka ya fita, fad'awa tayi kan gadon ta saki kuka mai cin rai, tasan ko Abu ya hakura ya barta iyayenshi baza su hakura ba, har ya dawo daga masallaci tana nan batayi Sallah ba, ganin ta kwance inda ya fita ya barta yasa ya shigo ya zauna bakin gadon tareda d'agota, jikinshi ne yayi sanyi ya rungumeta a jikinshi yana patting bayanta, kamar wacce aka dad'a tunzurawa ta fashe da wani sabon kukan, cikin rad'a a kunne yace "Shhhh baby, its alright, she will b fine okay?, pray for her", hawaye na zuba idonta ta shiga girgiza kai ta d'ago tana kallonshi, cikin kuka tace "Aliyu pls forgive me, kaji Dan Allah ka yafemin, wlhh ban San mey ya kaini........", kallonta ya tsaya yi da kyau snn ya sake jawota jikinshi ya matse yace "She will be fine kinji, babu abinda kika mata, it wasn't your fault, azzaluman da suka sata in this condition will pay for each pain they caused her, its okay ki dena kuka kinji, she needs your prayers more than your tears, your sister is gonna be alright kinji", kuka sosai ta shigayi har saida ya tausaya mata, ya d'agota ya kama mata gashinta da suke a baje yayi making mata messy bun snn yace "kinyi Sallah ne?", kasa bashi amsa tayi hakan ya tabbatar mishi da cewa batayin ba, kamo hannunta yayi ya kaita toilet ya jirata har tayi brush tayi alwalan snn suka fito ya shimfid'a mata abin sallah ta hau tayi, yana nan zaune har ta idar kuma har lokacin hawaye takeyi, gado ya maidata ya kwantar ya lulluba mata duvet yayi mata peck snn yace "Get some rest and pray for her, she is gonna be alright and back to us okay?", kai ta kad'a mishi, murmushi yayi mata da ta kasa maida mishi snn ya juya ya fita tareda rage mata wutan d'aki [11/15, 11:15 AM] ‪+234 810 957 2036‬: 💖💝BATUUL💖💝 86 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* D'akin Ammah ya koma bayan ya fito d'akinshi, bai tadda kowa ba sai Batuul dake Lullub'e cikin comfy bargo tana bacci, d'akin ya shigo ya tura k'ofar ya karasa ya hau gadon ya zauna, bargon nata ya janye yaga gashinta da ya bud'e tun jiya na nan a bud'e, kallonta yakeyi with so much affection da tausayinta a idonshi, hannu yakai ya gyara mata gashinta ya maida shi baya, kallon face d'inta da ya kara haske ya tsaya yi kamar ba ciwo takeyi ba, dukda ta rame amma kyanta na nan, satinta d'aya kenan kwance anan batareda tasan ina kanta yake ba, d'an murmushi yayi tunawa da yayi yau za a gama yi mata magani in Allah ya yadda ta samu sauk'i ya kai hannu ya shafi gefen fuskarta tareda lumshe ido yace "Haya", hannunta ya kamo cikin nashi cikin sanyin murya yace "Fatima you are more than life itself, nasan kina jina ko Fatima, you are worth everything good life can offer, GWS kinji, I need to tell you how much you mean to me, you've become part of me, you know I never thought I could love anyone, I never tot someone could mean this much to me until I met you, The first moment I saw you, I knew there was something great about you, some vibes I can't explain, Mesa tun a da ban dawo gareki ba, I wish I had known you long ago, You have become a part of me, my Haya, I never knew I had life until I met you, in such a small period you have made me understood what love means, I never knew how it felt to b loved, at the beginning inace k'in ki nakeyi sabida effect da kike casting a kaina, but I was wrong, I was growing fond of you, you became an acquaintance, a friend and the very best person I could ever ask for", d'agota yayi ya d'aura kanta kan cinyarshi ya kama fuskanta da duka hannayenshi, idonshi ya rine har ya fara hawaye yaci gaba "Fatima pls get up, get up and don't leave me, I need to tell you how much you mean to me, I promise to keep you Happy all the time, Plssss Fatima, I really need you, just give me a second Chance to show you how much I love you, I really do", bai damu da drip d'in dake hannunta ba, rungumeta yayi Idonshi duk ya kad'a, a haka Ammah ta shigo ta sameshi, tun daga bakin k'ofa take jiyo maganganun da yakeyi, sosai take tausaya mishi itama har idonta ya cicciko, jiki a sanyaye tazo ta zauna daga gefenshi ta dafa kafad'unshi tace "Babana I've told you times without number addu'a zakayi mata, zataji sauki yau d'innan In sha Allah", kallon Ammah yayi da rinannun idanunshi ya kad'a kai yace "Ammah cewa fa yayi in har aka cikata na kwana bakwai ba a samu nasara saidai wadanda sukayi abin nan sun karya da kansu, su waye haka zasuyi mata irin haka, mey tayi musu Ammah?", Ammah ta girgiza kai hawaye taf idonta tace "Abu be optimistic, Da izinin Allah ya fisu, kuma zata samu sauk'i, mu jira har anjiman a gama mata magani sai muga abinda zai faru, kaci gaba da yi mata addu'a", shiru kawai yayi ya kasa cewa komai, tashi Ammah tayi tace "bari inje in sa a shirya shigowan Asheikh d'in sai inzo in shiryata", da haka ta fita daga d'akin zuciyanta duk ba dad'i ga fargaban dake tattare da ita, bayan ta fitane ya gyarawa Batuul d'in gashinta snn ya saka mata hularta K'arfe bakwai Ajiddeh taji wayarta na ringing, kin dagawa tayi ganin Mum keh kira, duk fargaba ya cikata har wani sanyi sanyi takeji, zata kashe wayar kenan taga text ya shigo, budewa tayi ganin daga Mum ne, ce mata tayi "In baki d'auki wayan nan ba toh wlhy yanzu zaki ganni gidan da kika maida yafi iyayenki", jiki a Sanyaye ta gama karantawa kamin tayi wani abu aka sake Kira, saida ya kusa katsewa ta d'aga da k'yar tasa a kunneta, muryar Mum taji da daki dodon kunnenta tace "Don uwarki har kinyi girman da zan rika kiranki kina kashemin waya ko Ajiddeh, toh gani nan tafe gidan naku sai kin fad'amin dalilin da ya sa duk kika canja, kamin tayi magana taji kiit an kashe wayar, b'ari jikinta ya hau yi jin abinda Mum tace mata, hawayen ma kasa yinshi tayi tsabar tashin hankali, a ina zata samu mafita ita yanzu, tana yiwa Aliyu son da har in ya rabu da ita toh lallai itama zata rabu da tata rayuwar, d'aukar wayar tayi zata kira Mum tace mata zatazo ita gidan basai Mum d'in tazo ba amma har k'iran ya katse Mum bata d'auka ba, sau uku tana k'ira amma har lokacin bata d'aga ba, hannu tasa a ka ta saki wani razananna ihu ta tsuguna a wajen ta saki matsanancin kuka, shawara kawai ta yanke ta fadawa Abu ganin batada wata mafita, wayar ta jawo ta kirashi taji wayar na ringing a cikin d'akin, takaici duk ya isheta, mikewa tayi taje ta sameshi ta fad'a mishi komai, a ganinta hukunci da zai yanke mata ba zai zama mai tsauri ba snn yana sonta zata bashi hakuri tace duk sharrin shaidan ne, hakanan ta fito ko d'ankwali babu daga ita sai y'ar rigar baccinta, gashin da Abu ya tufke duk ta baje shi, Tana fitowa ta kusa cin karo da Ammah, kallonta Ammah tayi ganin duk ta rikice, da k'yar Ajiddeh ta iya had'a kalmomin daga bakinta tace "Ina kwana", Ammah da ta tsaya kallon yanayinta tace "Kin tashi lafiya?", kai kawai ta iya gyad'awa, Ammah ta tab'e baki tayi tafiyarta tana mamakin Abunda ya sami Ajiddeh yasa duk ta rikice da idonta ya kumbura ya rine kamar wacce tasha kuka, ganin Ammah da Ajiddeh tayi ya sake tsoratata, ji tayi jikinta duk yayi sanyi a haka take ganin baza ta iya tunkarar Abu da zancen ba don tun da suka xo gidan har yau bata ga fuskarta da na Farida ba, Sadiq kadai ke kulata gidan, shi kansa Abu ba wani lokacinta garesa ba, komawa d'akin tayi ta zube kan gadon ta rasa inda zata sa ranta taji dad'i K'arfe bakwai daidai Abu ya sauk'o da Batuul rungume da ita bayan ya gama shiryata ya shafa mata su Zaitun da habbatus sauda ya gama mata duk abinda ya kamata kamar yayi side d'in Abui inda ake mata magani, sauk'ar Qur'ani aka fara mata kamar kullum, Kowa zama yayi kawai yana zuba mata ido ganin mey zai faru, Farida na jikin Abui har wani rawa jikinta yakeyi, Abu kam ko kusa da ita bai bari ba yana nan rik'e da hannun nata, anayi Abu na d'an d'iga mata ruwan Zamzam da Ma'ul Ward snn ya shafa nan fuskar tata, Kaskon turaren wuta Asheikh yace a mik'o mishi nn aka had'a komai aka bashi, daga cikin jaka ya ciro wani gari a cikin roba ya barbad'e cikin wutan, nan da nan hayaki ya gauraye ko ina na d'akin, wani dogon numfashi Batuul taja tareda tari, ihu tasa tana k'ok'arin tashi ta xauna, baka jin komai a d'akin sai Kabbara da Hamdala da su Ammah keyi ganin ta farfad'o, Abu kam ido ya zuba mata ya kasa motsi, rungumeta yayi hawayen da ya taru idonshi ya gangaro, fuskarta ya lalubo yana kallonta yace "Haya, bud'e idonki ki ganni kinji, dont leave me again pls, I promise to keep you safe In sha Allah but don't try leaving", kantane taji yana juya mata ga wani irin amai datakeji, cikinta jinshi take duk ya hautsine, gaba d'aya bata da karfi, so take ya saketa amma batasamu yayi hakan ba, duk da kakarin Aman da takeyin, kamin yayi yunk'urin taimaka mata ta fara kwararo amai, wani irin amai takeyi bak'i kirin da wasu irin tsaba, kwararo shi kawai take ba ji ba gani, har wani sama sama numfashinta yakeyi, Abu zaiyi magana Asheikh ya d'aga mishi hannu alamar yayi shiru babu komai, amai ta dinga yi sosai, wani razanannen ihu tasa saiga cikin aman wani abu ya fad'o kamar blood clot, abin na fad'owa ta lumshe ido ta sulale, har lokacin bai bari ta bar jikinshi ba, tana kwanciya bacci ya d'auketa. Mum a can gida duk hankalinta a tashe ta rasa da wanne zata fara, mijin Jainaba dake shirin tozartasu ko kuma Ajiddeh dake kunsa mata bakin ciki tana son jawo mata attack, ga wata munafika da Dad ya dawo gida da wai accident sukayi amma yanzu ita duk ba ta tasu takeyi ba, so take ta fara magance Jainaba da Ajiddeh tukunna inyaso asan abin yi kan buzuwar da ya kawo mata gida, bayan sun gama waya da Ajiddeh ta jefa wayarta cikin Jaka ta fito ta sami driver ta fad'a mishi inda zai kaita, gidan su Abu tace mishi tanaso, umarni yabi har saida sukazo gidan ta fita tace ya jirata ba jimawa zatayi ba, baki ta sake tana karewa gidan kallo, duk kallonta da manyan gidaje hadaddu wannan daban yake, a ranta kuwa cewa tayi "Shine waccan sallamamiyar take son janyo mata asara, irin wannan daula sai sun kwashi rabonsu ai", har ta shigo cikin gidan sake sake takeyi cikin ranta, Da Ammah suka fara cin karo, rikicewa tayi ganin Ammah amma ta dake ta kirkiro murmushi tace "Hajiya Bilki kin ganni da sammako ko, wlhy abubuwane nayi dayawa gashi Ajiddeh tace min satinsu d'aya yar uwarta bataji dad'i ba shine nazo dubata, in banyi sammakon bane bazan samu time ba", Ammah tsabar mamaki kasa magana tayi, mamaki fal ranta kuma hankalinta sam bai kwanta da zuwan Mum ba, dakewa tayi tace "Alhamdulillah mai jikin ma ta fara jin sauki, Allah bada lada", Mum ta tab'e baki tace "ko ba sauki ba, saukinta d'aya ai mutuwa", amma a fili tayi murmushi tace "Allasarki baiwar Allah, tasha wuya Allah yasa kaffara ne", Mum dai ce mata tayi "Amin", snn tace "Hauwa na sama ko, kamin kiga mai jinyar", Mum tace "Ahh toh shikenan, ba jimawa zanyi ba", Mum ta kira d'aya daga cikin masu aikin gidan tace ta kaita d'akin da Abu yake snn tace a kai musu refreshments can sama, saida sukayi gaba tayi inda aka kwantar da Batuul take bacci, lokacin babu Sadiq da Farida da kuma masu yi mata sauk'an sun fita, Asheikh ta tarar yana magana yace" Hajiya keh muke jira dama, Alhamdulillah yarinya ta samu lafiya kuma kamar yanda muka fad'i sihiri akayi mata snn Allah cikin ikonshi ya bayyana mana wad'anda sukayishi", dafe k'irji Ammah tayi tace "Innalillahi wa inna illaihi raji'un", Abui ya kad'a yace "La hawla wala quwata illa billahi aliyul azim, Subhanallah", Abu dai kai kawai ya d'ago yana jiran jin karashen bayani, Ammah tace "Allah ya kyauta, yarinyar nan bana tunanin tana da matsala da mutane", Asheikh ya d'anyi murmushi yace "Ai yanzu ba sai kayiwa mutum komai ba zaiso ganin bayanka", Ammah ta sauk'e ajiyar zuciya tace "Allah ya kyauta", Abu duk ya k'osa yaji wad'anda suka sa Batuul cikin wahala, har wani zafi ranshi keyi dan shi kad'ai yasan abinda zaiyi musu, sai yasa sun d'and'ani azaba fiyeda yadda suka sa Batuul ko su din su wayene kuwa yace "Asheikh munaji, zamu iya sanin sunayensu?", Asheikh yace "Ehh kaga wannan abinda ta amayo shi ya nuna mana ko su waye su, dama shi irin wannan sihiri mugune, sosai yake lahanta mutun dan bama sihirine na haka ba, yarbawa sunfi yinshi , ba kowa ke iya juresa ba, in har aka yiwa mutum shi toh indai maishi ya mutu, ko ba dade ko ba jima sai ya koma kan wanda yayi shi, inko bai mutu ba, a irin haka duk abinda ya fito jikinsu toh da sunayensu zai fito kamar yadda nata yayi", Abu dake tsaye kai kawai ya dafe dan ya fara losing cool d'inshi, baya tunanin inyaji sunayensu zasu k'ara minti talatin ba a prison ba, cikin tunanishi kamar daga sama yaji ana ambaton, "Zuwaira, Jainaba da Ajiddeh", da sauri ya d'ago dan gaskata abinda yakeji, wani irin nauyi yaji kanshi yayi mishi kamar an d'aura mishi dutse, bai ankara ba sai ji yayi hawaye na bin kuncinshi, kai ya shiga girgizawa yana matsawa da baya, if his memory still serves him right sunan matarsa Ajiddeh yaji daga bakin sheikh itada iyayenta, jirine yaji yana neman d'ibanshi da sauri ya samu bango ya dafa, Ammah da ta tsaya itama da mamaki tayi hanzarin rik'oshi ganin zai fad'i, banda ance Azzanu zambin, zato zunubine amma hankalinta Sam bai kwanta dasu Ajiddeh ba, ido ya lumshe ido ya bud'e hawayen na ci gaba da zubowa yace "Ammah kinji?, kinji wai Su Mum d'in Ajiddeh su sukeson kashe min Fatima, Ammah mey tayi musu zasu kasheta, mey tayi musu?", rungumeshi Ammah tayi tace "Shhhh Babana, Allah yayi da sauran kwananta a duniya, babu abinda zai sameta", kuka ya fasheda kamar wani karamin yana rungume da ita. [11/15, 11:15 AM] ‪+234 810 957 2036‬: 💖💝BATUUL💖💝 87 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Can a asibiti lokacin da Matan nan ta farfad'o, Daddy da nurse na d'akin, nurse d'ince ta taimakawa matar ta gyara kwanciyarta, sai a snn taji duk jikinta ya rirrike ga wani ciwo da takeji a ko ina na jikin nata, k'arewa d'akin kallo ta shigayi har saida taji muryar Dad yana cewa "Sannu baiwar Allah", da sauri ta dubi inda yake snn ta d'ago kai tana k'arewa d'akin kallo, a hankali ta shiga rera kuka, Dad da hankalinshi ya fara tashi ganin tana kuka yasashi tunanin ko kad'eta da sukayi ne ya sata yace "Subhanallahi sannu kinji, Allah ya baki lafiya kiyi hak'uri ki bar kukan haka kar ya k'ara miki da ciwon", yayi ma nurse alama da a kira doctor, har doctor ya shigo bata tsaida kukan da takeyi ba, yana zuwa bayan ya duddubata yayi mata allura, bata jima ba bacci yayi gama da ita, har aka cika kwana uku bata cewa komai, kullum Daddy yakan zo ya dubata safe da yamma, abinci ma sai nurse d'in tayi dagaske take daurewa taci kad'an, a ranan da ta cika kwana uku tun da safe da Dad yazo aka sallameta bayan magunguna da doctor ya bata, gida Dad ya kaita ya sa aka gyara mata snn ya zuba mata masu aiki, washegari bayan ta huta Dad ya shigo ya sameta bayan sun gaisa ya fara tambayarta inane gidansu, kamar jira takeyi ta fashe mishi da kuka, da kyar ya samu tayi shiru snn tace "Ba mu da gida", Dad ya d'an wara ido ya gyara zama yace "ban gane ba ku da gida ba baiwar Allah, akwai wadanda basuda gidane?, kiyi hakuri ki sanar dani mu samu mu maidaki muyi musu bayanin tsautsayin da ya sameki", cikin kuka ta fara "mu biyu iyayenmu suka haifa nida Yayata Sa'adah, ranan da aka haifeni Allah yayiwa mahaifiyarmu cikawa, ban girma nasan dad'in uwa ba saidai rashinta, Babana da Yayata sune suka hanani kewar rashin uwar da nayi, mu yan k'asar Niger ne, ina shekara bakwai lokacin yayata ta auri wani d'an Nigeria da suke kasuwanci tareda Mahaifinmu, bayan an gama biki za a tafi da ita tasa kuka tacewa Babanmu Dan Allah ya bata ni mu tafi tare, da kyar iyayenmu suka yadda akan cewa in nayi kwana biyu a dawo dani, niko da murnata na biyota dan inason Nigeria, gidane mai girman gaske a garin Kaduna yayata take zaune, part hudu ne a gidan, nashi d'aya, yayata d'aya, uwar gidanshi sai kuma na uwar mijin, tun bayan biki yayata tasa mijinta ya nemamin makarantar kud'i da Islamiyya ta sakani batareda Babanmu ya sani ba, sai bayan wata biyu yace ta dawo dani sbd makaranta tayi magiyar ya bar mata ni, badan yaso ba ya kyaleni a wajenta, har Yayata tayi shekara bata taba koda batan wata ba, daga nan tsangwama ya fara mata a gun dangin miji, numfashi kwakwara bata isa yi ba yanzun zasu fara mata habaici ana zaginta, duk da ina k'arama amma na fahimci bata cikin kwanciyar hankali, maigidanta kullum shike kwantar da hankali kasancewarshi mutumin kirki, Hutu hutu takan shiryani inje gida watarana kuma tare muke zuwa, shekara biyar da aurenta akayi mata waya Babanmu babu lafiya, gaba d'aya hankalinmu ya tashi tunba Yaya Sa'adah ba, mijinta Ishaq ne ya kwantar mana da hankali yayi mana shirin tafiya, washegarin ranar muka isa gida muka tarar Babanmu rai a hannu Allah kwana mukayi yana mana Nasiha kan zaman rayuwaa snn yacewa Yayata ya bata Ni ta riqeni amana, kwananmu uku ya cika, munsha kuka ba kad'an mana, a ranan Ishaq mijin ta yazo bayan bakwai muka koma Nigeria mukaci gaba da rayuwa, duk bayan shekara sai Yaya sa'a tayi b'ari, tun bata damuwa abun ya fara damunta, duk inda taji ana bada magani sai taje nema amma ba a samu sa'a ba, shekara biyar tana yin asarar ciki, a shekara na shida ta samu cikin ya zauna snn nima a shekaran aka min aure da wani d'an unguwarmu malamin university da mukayi soyayya, bayan wata shida da bikina Yaya ta ta sake samun wani cikin da ya bata wahala, ranan da zata haihu muna tare take ce min duk abinda ta haifa kada in barshi hannun kowa inyi mata alkwarin riqeshi, kamar tasan mutuwa zatayi tana haihuwa ta rasu, abinda ta Haifa ma bayan awa hudu ya bita, tashin hankali babu irin wanda ban gani ba, da kyar na samu na saba da rashinta, haka na koma rayuwa banida dangi, bayan shekara d'aya na haifi Yayana maza yan biyu daga nan ban sake wani ba sai bayan shekara bakwai na haifi mace", tsananta kukanta tayi sosai, Dad da ya tausaya mata ya mik'a mata tissue paper ta ansa ta goge hawayenta taci gana da bashi lbr tace "Safeena na jinjira rannan da rana wata mata ta shigo mana gida wai gidantane, nidai ban kulata ba na tattara yarana muka shiga ciki dan yanayin matar ma abin tsoro ne, da daddare bayan Sulaiman ya dawo ya huta nake sanar dashi abinda ya faru, yaje ya dubo mata ya dawo yace min ai matarsa ce anma tun kamin muyi aure tabar gidanshi ta tafi makkah shine ta dawo yanzu, tunda matan nan tazo mukayi sallama da kwanciyar hankali, masifar yau daban ta gobe daban, bayan watanni da zuwanta rannan muka tashi da safe Sulaiman ya rasu, tashin hankali babu irin wanda bamu gani ba, Yaya Ishaq mijin Yayata babu yadda baiyi in dawo gida ba nace zan zauna tareda Yarana in kula dasu mungode, rannan Hussaini ya shigo min d'aki duk ya rikice nake tambayarsa mey ya faru yace min yaji Larai suna hira itada wasu mazan wai su suka kashe Daddy, na jawoshi na rungume nace kada in kuma jin haka a bakinshi ba abinda ya jiyo ba kenan, tun daga lokacin na tsorata da lamarinta, na dena barin yarana a ko ina kusa da ita, wata d'aya kenan yanzu da na san rasa komai na rayuwa, nima lokaci nake jira in bar rayuwar, ranar ina kwance na jiyo kamar Hussaini keh ihu daga waje, na tashi na fita, ai kuwa wasu katti na gani riqe da Hussaini zasu kasheshi, da sauri na isa ina tambayarsu abinda ya musu su rabu dashi, wani irin maka da d'ayansu ya kaimin ban kuma sanin ina kaina yake ba, saidai tashi nayi naga d'akinsu Safeena na hayaki alamun ya k'one kurmus, kukan da kanshi ranan nemansa nayi na rasa, lokacin da na farfad'o naji muryar Larai tana wadanne irin banzaye ne ku da baku iya aikinku ba, ba ita nake gani tana motsi ba can, wani k'arfine da bansan da ina dashi ba na ji yazo min dan naci alwashin d'aukar wa yarana fansa, gudu kawai na shiga yi batareda nasan inda zan jefa k'afa, ina cikin gudun ne na hau titi amma bansan mey ya faru ba bayan nan", Wani irin tausayinta kawai Dad yaji yana ratsa shi, a hankali yace "Innalillahi wa inna illaihi rajiun", sau uku yana maimaitawa snn yace "Haka kaddararki tazo, kiyi tawakkali ki rungumeta da ikon Allah zaki samu kyakyawan sakamo a wajen Allah, in bazaki damu ba zan tafi dake gidana kiyi zamanki a can, inada mata da yara mata biyu in har bazaki damu ba", Lokacin da Mum ta haura sama, d'akin da Ajiddeh take mai aikin tayi mata jagora ta kaita snn ta juyo k'asa kawo mata ruwa, har Mum ta shiga d'akin Ajiddeh batan sani ba tana nan kife kan gado sai kuka takeyi, saida taji k'aran rufe k'ofar Mum snn ta d'ago ganin waye, dasauri ta mik'e har tana k'ok'arin fad'uwa ta k'araso gaban Mum tana leqen ko da wani bayan Mum d'in, cikin kuka Ajiddeh na girgiza kai tace "Na shiga uku Mummy, mey kikazo yi kuma, shikenan in auren nawa kikeson kashemin sai ki nemi waje ki zauna, dama gab asirinmu yake da ya tonu, tun daga Maiduguri aka d'auko Malamin da zai duba yarinyar nan kuma yau za a gama, saida nace miki a lalata aikin nan kikaqi gashi yanzu asirinmu zai tonu, Mummy kiyiwa Allah kiyi min rai ki bar gidan nan" ta k'arasa maganan tana mai tsananta kukanta, Mum da ta gama sauraren Ajiddeh ta wara ido tace "Keh don uwarki wasa kike, wane malamin aka kawo mata, ni Zuwaira naga rayuwa, ka haifi d'a baka haifi halinshi ba, Ajiddeh wai mey ke damun kwakwalwarki ne anya kinason gamawa da duniyar nan lafiya kuwa, yanzu har ke da bakinki kike cemin an nema mata mai magani amma baki sanar dani ba sabida ga kanwar uwarki Jainaba ake wa magani ko" Ajiddeh ta d'ago tace "Mum nifa mutuwan ne banaso tayi, mey zamu cewa Allah idan munje gabanshi, mey rayuwarta ta tsaremana da zamu karar mata da kwanakinta, tunda wuri saida nace miki ba kasheta za ayi ba amma kika qi ji", kuka Mum ta fasheda tana "Na shiga uku ni Zuwaira, Hauwa wlhy Allah ya isa haihuwarki da nayi, duk rayuwata ta k'are akan nema muku farin ciki keda y'ar uwarki amma yau bud'ar bakinki nayi abu kike cemin banyi daidai ba", jikin Ajiddeh ne yayi sanyi ganin Mum na kuka tace "Mum nifa ba abinda nake nufi kenan ba, wlhy duk ranarda Aliyu da iyayenshi suka san inada sa hannu cikin ciwon nan nata wlhy sai ya rabu dani Mum, Mum ko bashi ba iyayenshi bazasu yadda ya zauna dani matsayin matarsa ba, Mummy kinfi kowa sanin irin son da nake mishi, rabuwa dashi na nufin rabuwa da farin ciki na kuma bani kad'ai ba har Ku ba bari zaiyi ba dan ko yau da safe saida ya dad'a jaddadamin cewa in ya samu wad'anda suka yi mata wannan aiki toh hukuma ce zata rabasu dashi", Mum da ta fara tsurewa jin har su Abu sunsan asiri ne akayiwa Batuul yasa ta sake matsowa kusa da Ajiddeh tana wara ido tace "Shirman banza, waye yace musun asirine ke sata wannan ciwon", Ajiddeh tace "Yanzu haka fa Mum magani ake mata kumafa na fad'a miki yau d'innan za a gamashi kinga kuma dole komai ya bayyana", Tsaye Mum ta mik'e tana cire mayafin kanta dukda Acn dake aiki cikin d'akin amma gumi takeyi tace "Inaaa!, bazai yiwu ba, Wace irin masifa ce wannan da take shirin kunno min kai lokaci d'aya haka, karya sukeyi wlhy dukkansu sunyi kad'an, bokan nan saida yayi assuring d'ina mutuwa zatayi kuma babu wani wanda zaisan sukeda sa hannu", cikin hanzari ta lalubo wayarta ta shiga k'iran layin Jainaba, bata d'aga ba har ya katse, tsaki taja gaba d'aya jikinta sai rawa yakeyi taci gaba da k'ira, sau uku yana katsewa kamin aka d'aga, Ajiddeh dai kallon Mum kawai takeyi tana fatan Allah yasa kada asirinsu ya tonu, gaba d'aya hankalinta ya gama yin inda akewa Batuul magani, so kawai take taji mey ke faruwa taji meye makomarsu, Mum najin an d'aga waya tace "Jainaba kome kikeyi ki biyo jirgi ki shigo Abuja yau, abin ya min yawa nikad'ai, komai dad'a lalacemin yakeyi", sheshek'ar kuka taji daga d'aya b'angaren, Jainaban dake kuka tace "Yaya kizo ki fitar dani cikin wannan masifa, na gaji da zaman gidan Idrees", Mum ta katseta tace "Mey kuma ya faru bayan wanda kika fad'amin", Jainaba na kuka tace "Banda duka babu abinda nakesha gurinshi, yasa masu gadi sun hanani fita daga gidan, duk ma'aikatan gidan ya koresu babu kowa cikin gidan nan sai ni kad'ai sai kace mayya, yaran ma ya kwashesu bansan inda ya kaisu ba gashi babu kud'i wajena bare in siya kati in miki waya kiji halin da nake ciki, kwakwaran motsi ban isa inyi shiba yanzu zaki ya fara hantara yana tamin habaici kan matar da zai aura", Mum da k'afafunta suka fara rawa jin bayanin Jainaba dawowa tayi kan gadon ta zauna taci gaba da cewa "Yaya ki taimaka kiyi koma menene cikin yau d'innan in samu in fito daga gidan nan, in yaso daga baya musan yadda zamuyi dashi", Mum da abu suka fara cakude mata tace "Ki kwantar da hankali Jainab kina jina, yanzun nan zan fita in San abin yin akanshi, yanzu haka ina wajen shashar nan, daga nan zamu wuce tareda ita, kwantar da hankalinki komai ya kusa zuwa k'arshe", Jainaba tace "Shikenan Yaya ina jira", da haka suka katse waya ta dafa kanta tana tunanin yadda abubuwa sukayi mata yawa lokaci d'aya, can ta juyo ta dubi Ajiddeh dake ta hawaye tace "Ki tashi yanzun nan muje musan abinda za ayi tunda kince yau za a gama mata maganin, Ya Allah mey nayi nake cin karo da masifu iri iri a cikin kwanakin nan", Ajiddeh tace "Mum bafa masifar da kike ciki, in ta tawa kike kije....", Mum cike da fusata tace "Dan uwarki bakida hankali ko?, ganin ina binki a hankali yasa kika fitsare har kike ce min indan taki masifarce in rabu dake ko toh bari kiji, mijin Jainaba aure zai k'ara kullum narka mata duka yakeyi a gida, Wanda zai auri Zainab ya fasa , matarsa da mukayi sanadin fitanta daga gidan ya maidata, Babanku yazo da wata mata gida yasa an gyara mata part guda ya zube mata y'an aiki, bansan tsakaninshi da ita kullum hankalina a tashe na tambayeshi wacece ita yace wannan ba matsalata bace snn gaki, akan wata can banza kikeson b'ata min rai, komai dan ku nake yinshi dan Ku samu farin ciki mai d'orewa amma bakya ganin k'ok'arina, yanzu babbar matsalar da muke ciki duk akanki sbd kin fifita miji da danginsa akanmu, har a samo mai magani bakiyi tunanin sanar dani ba", Mum ta fashe da kuka tace "In sha Allah na barwa Aliyu ke Hauwa, kafata ta bar d'akin nan toh ki manta kinada wata uwa", ta miqe ta zari Jakarta tayi hanyar waje, tana kaiwa bakin k'ofa zata bud'e taji an turo k'ofar, Abutturab ne tareda da Ammah suka shigo d'akin a tare, Ajiddeh na ganin yanayin sa durk'ushe a wajen ta saki wani irin kuka, cikin d'akin ya k'arasa shigowa, Mum da duk yan hanjinta sun kad'a ta dake ta dubi Ammah tace "Yanzu nake shirin inje in duba mai jiki, yarinyar nan ce take ta kuka nace addu'a zatayi mata", ko kallonta Mum batayi ba, Hannun Ajiddeh dake durk'ushe tana kuka ya kamo ya mik'ar da ita, cikeda kuka kamar ranta zai fita tace "Aliyu tsaya kaji Dan Allah, Let me explain kaji, wlhy Allah....", wani irin fizga da yayi mata yasa ta toshe bakinta da d'aya hannun nata, Mum da ta tunkarosu tana "Kai banza ina zaka kaimin y'a kake fizgarta haka", wani mugun kallo da ya jefeta dashi yasa tayi shiru ta matsa da baya, Har ya fita da Ajiddeh daga d'akin baice komai har saida ya kaita d'akinshi da yakeyin ayyukanshi kamin yayi aure, sake hannunta yayi yana kallonta da idanunshi da suka rine yace "Hauwa did you really hurt her? Kune behind suffering din Fatima all this while?", shiru yayi yana jiran jin amsar da zata bashi, ganin tayi shiru tana kuka yasa shi daka mata wani mugun tsawa yace "Answer me" har saida yasa Ammah yiwowa wajen tareda Mum, a kid'ime Ajiddeh ta kalleshi tana kuka tace "Am sorry, am so sorry, I wanted telling you Dan Allah kayi hakuri wlhy sharrin shaid'an ne, forgive me pls Aliyu", wasu hawaye ne masu d'umi ya shiga zirarowa daga idonshi, lumshe ido yayi ya bud'e ya kalleta snn yace "Get out of my sight, don't you ever cross my way not now not ever", tsananta kukanta tayi tana girgiza kai ta shiga matsowa kusa dashi tana "Aliyu you know I love you, karka horani da rashinka, I can't endure ko wane irin punishment amma banda rashinka dan Allah kayi hak'u.....", wani mugun kallo ya jefeta dashi da ya sata had'iye maganarta ya daka mata tsawa yace "I said get out", ganin yanayinshi tasan komai zai iya faruwa a lokacin, toshe bakinta tayi ta juya ta ruga a guje ta fice daga d'akin. [11/15, 11:15 AM] ‪+234 810 957 2036‬: 💖💝BATUUL💖💝 88 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* A guje ta fice daga d'akin tana riqe da bakinta, ko Ammah dake shirin shiga d'akin bata lura da ba tayi wucewarta , hanyar staircase tabi zata yi k'asa taji an rik'ota, Mum ta gani riqeda hannun nata, kuka kawai take tana girgiza kai alaman ta sakar mata hannu, wani uban harara da ta bita dashi ta fincikota tace "Sallamamiya Ce mishin kikayi kinada masaniya kan abinda ya samu tsinanniyar yarinyar?, toh Dan Ubanki duk abinda ya biyo baya ki kuka da kanki tambadadda, In banda lalaci irin naki Dan uwarki har ya isa ya wulakantaki ina gidan nan?, banda sunci darajar gidansu nake daga shi har uwar tasa da na karta musu rashin mutunci, shashashar yarinya, yanzun ma bata baci ba muje in keh baki iya kare kanki ni zan yi, wlhy ban san asarar haihuwa nayi ba da na zubdashi tun kamin kizo kina cusa min kuttu", ganin Ajiddeh na k'ok'arin k'wace hannunta yasa Mum cikeda fusata tace "kinsan Allah in baki kiyayeni ba sai naci mutuncinki, yarinya ana neman k'watar miki y'anci kina neman yi min tijara? Kuma wlhy kika kuskura kika tozartani saidai gidan wata uwar bani ba, tsine miki zanyi ki k'arasa lalacewa kibi duniyar gaba d'aya", ta fizgota sukayi hanyar d'akin, kan kujera Ammah ta tarar da Abu zaune ya dafe kai yana kallon marbles d'in d'akin, hannun Ammah da yaji jikinshine ya sauk'ar mishi da nutsuwa, hannayenta duka biyu tasa ta tallabo kanshi tareda shafa kanshi tace "Are you okay?", ido ya lumshe kamar maijin bacci da k'yar ya bud'esu yana kallonta ya girgiza mata kai alamun "Yeah am fine", kan nashi ta sake ta kamo duka hannayenshi tace "Badai dukan yarinyar nan kayi ba ko Aliyu, naga ta fice a guje tana kuka", ya kalli Ammah for some seconds snn ya bud'e baki da k'yar yace "I just don't want to see her anywhere around, not now not ever", Ammah da taji dad'in maganganun shi taja wata kujerar ta zauna tace "Alhamdulillah, Allah yayi mana tsari da masharranta, tayi maka admitting d'in sunada hannu ciki koh?," ido kawai ya lumshe ya bud'e dan gaba d'aya hankalinshi na wajen Batuul, ganin baison zancen tace "Ba komai ai ka kwantar da hankalinka, zamu jirayi hukuncin Abui, muji ya za ayi dasu, amma albasa batayi halin ruwa ba dan mahaifinta ba halinsa ba kenan, kuma nasan in har yaji wannan ta'asa da sukayi sai ransa ya b'aci, baiwar Allah yarinya k'arama da ita sun sata cikin azaba, mey sukeso mucewa Maryam ya sami y'arta?", ta matso kwallar dake idanunta tace " koma dai menene dukdai nina jawo shi tunda yarinya na gaban iyayenta hankali kwance nasa aka nema maka aurenta, bayin Allah ba tareda second thought ba suka bamu, Allah dai ya mata katangar k'arfe da mugaye", har Ammah ta gama magana bai bud'e bakinshi yace uffan ba, tunanin Batuul dake dad'a yi mishi yawa yasa ya zame hannayenshi cikin na Ammah ya mik'e yayi hanyar k'ofa, hannu yasa zaiyi sliding k'ofar yaji an rigashi ta d'ayan gefen, Mum ce janye da Ajiddeh ta shigo tana sababi, "Har mu za ayiwa sharri, Bilki kinyi kad'an kuma wlhy hukumace zata rabamu daku, wato tun kiyayyar da kikemin muna yarinta shine ya koma har kan y'ay'ana sai kin bisu da sharri ko, mu za ayiwa k'azafin yiwa wata figaggar yarinya can asiri, billahil azim sai kinyi Dana sani", Ajiddeh da damuwa ya cika ta rasa inda zata sa rai taji dad'i zubewa k'asa tayi tana kuka, Mum ta dubeta tace "Sun sallameki kin zama bakida amfani shine suke tunanin muma munyiwa wata can ko, kai kuma d'an mace an tura maka karuwa kanata cin amanar y'ata shine Dan Allah ya kamaku zaka lak'awa y'ata da bata san zance ba", ido Abu ya rintse yana fisting hannayenshi jin ta dangana Batuul da karuwa, kai yasa zai fice daga d'akin Ammah ta rik'oshi ta jawo shi gabanta tace "Abutturab inajin aure ne ya had'aka da y'arsu tun farko, inaso yanzun nan ba anjima ba ya rabaka dasu, mey za ayi da mugun iri irin wannan?, maza sallamar musu y'arsu, Allah ya had'a kowa da rabonshi", a firgice Ajiddeh ta tashi har wani dishi dishi take gani tazo gaban Ammah ta had'a hannayenta duka biyu tana kuka tace "Ammah Dan Allah kimin rai, nasan ban tab'a zame miki sirikar kirki ba, babu abin arziqi da na tab'a yi miki amma Dan Darajar Annabin tsira da aminci kar kisa ya sakeni, nasan ko bai sakeni ba tunda yace bai kuma son ganina nasan mutuwa zanyi, ki yafemin, ki roka min yafiyar Batuul ki rok'a min yafiyarshi in mutu da aurensa akaina, badan halina ba sai dan nasan ke uwace ta gari mai halin dattako, inayiwa d'anki son da bansan adadinshi ba a rayuwata", sanyi jikin Ammah yayi amma ko kallonta batayi ba tace "Babana ina jiranka, ka sallamesu su bar min gida", Jiki a sanyaye itama Ajiddeh ta kalleshi amma ko kallon inda take baiyi ba ya karb'e hannunshi daga rik'on Ammah ya fice daga d'akin, Duka Mum ta d'aka mata tace "Dan uwarki sai ki tashi tunda ke asararriyace, ban taba sanin ke mara hankali bace sai yau, har uwarsa ta bud'i baki tace ya sakeki uwar mey zaki zauna yi gidanta, kike wani cewa keh kinsan uwace ta gari ita, da y'arta ce baza ta tsaya....", ko kallonsu Ammah batayi ba ta fice daga d'akin itama, a guje Ajiddeh ta biyo Ammah tana ci gaba da magiya, Sau d'aya Ammah ta dubeta tace "Ba yafiyata zaki nema ba, wacce kika cutar zaki tambaya ta yafe miki", har ta sauk'o k'asa bata dena binta abaya ba, Abui da Farida tare suka fito jin hayaniyar Ajiddeh da Mum, kallon Mum yayi yace "Bilkisu lafiya?, mey ya sameta?", jin muryar Mum sukayi tana cewa "Ki fita harkar k'ananan mutane kizo mu wuce, kema uban ki nada gidan", Abui ya kalleta jin mey take fad'i snn ya kwalawa Abutturab k'ira, ba b'ata lokaci ya fito d'akin da Batuul ke kwance, yana ganin Ajiddeh ya had'e rai, Abui ya dubi Ammah yace "Mey yayi mata kina wajen baki hanashi ba", Ammah ta had'e rai ta tab'e baki tace "cewa nayi ya saketa", Abui ya dubeta da kyau jin abunda ta fad'i yace "Kan wane dalilli zakisa ya saki matarsa?, kaji shirme, kai Aliyu da hankalinka zaka saki matarka, kuskurene tayi kuma yarinya Allah ya tashi kafad'unta sai dai fatan Allah ya tsare gaba", Ammah ta fashe da kuka tace "Abui ya saketa kawai, dubi fa yadda suka cutar da Fatima amma uwarta ke musun sharri mukayi musu har da cewa k'ara zata kai mu munyi musu sharri", Sai lokacin Farida ta fuskanci kan zancen, Ajiddeh ta duba da wani mugun kallo ta tab'e baki ta matso wajen Ammah, Mum cikeda masifa tace "Yo ba Sharrin kukayi mana ba, wacece Maryam ma bare Fatimar har a wani yi mata asiri, kai kaga", ta nunawa Abu yatsa taci gaba "In ka fasa sakin nata baka cika haifaffen d'an bilki ba", Abui da mamaki yake kallon Mum, Abutturab da tunda yazo ya kasa d'ago kai a hankali cikeda nutsuwa batareda ya kalleta ba yace "I don't need a second thought, get out of my sight before I loose my cool, before you regret ever knowing me", yana fad'in haka ya juya batareda yabi ta kan kowa ba", Ajiddeh na jin haka ya fito daga bakinshi kuma a gaban Abui tasan zamanta gidanshi ya k'are, har wani dishi dishi take gani ta miqe tayi waje cikin hanzari batareda ta kula kowa ba ta fita a guje, Mum ce ta bita a baya tana kwala mata k'ira, girgiza kai Abui yayi yace Allah ya kyauta yayi sama , bayan kamar minti biyu Mum ta sake shigowa ta nuna Ammah da d'an yatsa tace "duk mey zai Samar min 'ya wlhy ki kuka da kanki", ta juya ta fice fuuu kamar wata iska Yana komawa d'aki ya d'auki Batuul cak a hannunshi ya rungume ya fito da ita, ganinshi riqe da Batuul Ammah ta tambayeshi "lafiya ka d'aukota, ko ta tashi ne?", kai ya kad'a mata yace "Inaso ne ta huta a saman" snn ya k'ira Farida ta biyoshi, yana shiga d'akinshi ya kwantar da ita kan gado, dai dai nan Farida ma ta shigo, yace "Je ki samo mata kaya mara nauyi, I want her to change", kai ta kad'a mishi tace "okay", ta fice, ya kurawa fuskan Batuul ido y'ana kallonta a hankali ya kamo siraran yatsunta ya kai bakinshi ya manna mata kiss yace "I love you Batuul", kamar taji abinda ya fad'a a hankali ta bud'e ido ta kalleshi, ido ya lumshe ya bud'e yana so ya tabbatar dagaske ta farka, da sauri ya matso yana riqeta yace "Alhamdulillah, am glad kin farka", murmushi tayi mishi ta shiga k'okarin tashi ta zauna, shima d'in murmushin yayi mata ya rungumeta jikinshi yana lumshe ido yana shak'ar k'anshinta da yakeso a koda yaushe, jin yaqi saketa yasa ta d'an turashi, ya d'agata daga jikinshi yana kallon fuskanta, hawaye ya gani cike da idonta kuma har lokacin da murmushinta a fuska ta k'arewa d'akin kallo tace "Yaa Abu inane nan?", ya dad'a matso da ita kan cinyarshi yace "Cry no more kinji, baza ki sake kuka ba sai na farin ciki In sha Allah, We are home, and you will be safe here in sha Allah", Farida ce ta shigo riqe da kaya a hannunta, watsar da kayan tayi ta fasa ihu ta hawo kan gadon ta k'ank'ame Batuul tace "Alhamdulillah, omg Batuul am happy kin warke, don't fall sick Dan Allah kinji?", sai kuma ta fashe da kuka, Abu ya kalleta yace "Keh mey haka, kin shigo kina ihu, ina aiken da nayi miki?", Farida ta cunno baki tace "Yaa Abu am just happy my friend is well again", Batuul tayi murmushi ta kamo hannunta tace "Yeah Alhamdulillah, am feeling much better now, Ammah fa", zata bata amsa yace mata "Leave", ta zumb'uro baki ta sauk'o daga kan gadon, Batuul ta kalleshi da idanunta da sukayi raurau tace "Yaa Abu mana, let her stay", bai kulata ba ya sake kallon Faridan data fita kamar mai shirin karya k'ofan, ya kalleta yace "Baby you hungry ko?", kai ta girgiza mishi, hancinta ya d'an ja yace "Nasan kina jin yunwa, and my lil champ too", ya kai hannu kan mararta, sam ta manta da wani ciki a jikinta sai yanzu, murmushi kawai tayi mishi, yace "Let's freshen you up, sai kici abinci", tace "Ni bacci zanyi, am not hungry", tashi yayi ya tattare kayan da Farida ta watsar snn ya dawo kan gadon ya shiga k'ok'arin cire mata kaya, hannunshi ta riqe tace "Zan cirefa", kamar baiji mai take cewa ba yaci gaba da abinda yakeyi, cak ya d'agata yayi toilet da ita, wanka yayi mata tayi brush snn tayi alwala ya d'aukota suka fito, shi ya shiryata ya canja mata kaya, a lokacin Ammah da masu aikinta suka shigo da abinci, ba abin mamaki bane dan tasan irin son da Ammah ke yi mata tun kamin ta auri d'anta, ranan ko Sallah Abu bai fita ba a d'aki yake yinshi ya jasu jam'i, lokaci lokaci Ammah ke shigowa dubata, da daddare ma shi yayi mata wanka ya shiryata cikin kayan bacci snn ya tofa mata addu'a tareda ja mata bargo,wutan d'akin ya kashe ya jawota jikinshi yayi pecking lips d'inta yace "Have a sound sleep Haya", sake shigewa jikinshi tayi, a hankali kamar mai rad'a tace "Ban ganta ba duka yau?, ina ta tafi?, kamar baiji abinda tace ba ya dad'a gyara mata kwanciya yace "You need rest, kiyi bacci", sake maimaita mishi tambayar tayi tace "Yaa Abu mana, she needs to know na warke, ina Ajiddeh?", jin ambaton sunan Ajiddeh yasa yaji abubuwa da dama na taso mishi, hannunta ya kamo cikin nashi yace "Fatima Kiyi bacci Dan Allah", k'ok'arin tashi ta shigayi tace "Toh ina taje mana, I just need to know", a fusace ya janyota yace "I will slap you right away in baki kwanta ba, bakisan you are still weak bane? komawa tayi ta kwanta, ajiyar zuciya yaji ta sauk'e, yaja d'an tsaki, bada son ranshi yayi mata fad'an nan ba, so yake ya dena tunawa da Ajiddeh, gabanshi har fad'uwa yakeyi in ya tuna abinda tayi, he have to caution Batuul d'in da kanta ta dena tuna mishi da ita, atleats for the mean time, ajiyar zuciya ya sauk'e ya rungumota jikinshi yace "Am sorry Fatima", bata ce mishi komai ba, hakan yasa ya mirginota tana fuskantarshi yace "You should rest Fatima Dan Allah, I love you" [11/22, 11:21 PM] ‪+234 803 698 6494‬: 💖💝BATUUL💖💝 89 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR*       Ba Zuciyarta kad'ai ba , har jikinta rawa yakeyi jin kalaman da suka fito bakin Abu, tasha jin ana fad'in wadannan words d'in a films da kuma novels amma bata tab'a tunanin  haka mutum keji ba in aka furta mishi su, bata tab'a jin irin wannan abinda take experiencing ba yanzu, wani irin fad'uwa gabanta ya shiga yi lokaci d'aya zuciyarta na mata nauyi, hawaye ne taji yana gangarowa kan  fuskarta, ta d'auka baza ta tab'a jin wad'annan kalaman daga wajen wani ba bayan y'an uwanta, shak'ik'anta, tasha jin Farida na ce mata "I love you" duk randa wani abin farin ciki ya giftasu a lokacin, batasan mesa wannan ya fita daban ba, wannan har cikin ranta take jinshi gabanta na tsananta faduwa, she wasnt expecting it, not from him, tunani takeyi itama kamar yadda taji ana fad'a a movies "I love you too zatace?, ta dad'e da sama ranta salama akan jin wadannan kalmomi sabida tasan har sai in ana sonka za a nuna maka, batasan ko tana son nashi ba but tasan yayi casting effect ba kad'an ba cikin rayuwarta, jin tayi shiru snn jikinta na kyarma yasa Abuuturab dafata, kamar jira take taji hannunshi jikinta ta fashe da wani irin kuka, da hanzari ya miqe ya zauna tareda kunna bedside lamp d'in snn ya d'agota, ganin hawaye shimfid'e fuskarta yasashi furta "Subhanallah, Batuul kuka kuma, kinsan I hate jin kukanki, Dan Allah kiyi shiru, am sorry kinji, you don't have to love me back, its okay, ni d'in I will love you with all my myth kinji, just keep yourself safe for me, Be happy", kamar wacce aka daka sai ci gaba da kukan nata takeyi, hannayenta duka biyu ya kamo cikin nashi ya d'an murzasu a hankali yace "Its okay I won't say it to you again tunda bakiso, I promise, kwanta ki huta kinji, its getting late", har lokacin batace komai ba sai jinta take kamar akan iska take zaune, rungumeta yayi ganin kukan nata yaqi tsayawa, jin ya rungumeta yasa feeling d'in da take experiencing yafi Nada,bakin shi ya d'aura daidai kunnenta ya d'an hura mata iska yana patting bayanta snn cikin rad'a yace "Shhhhh, I won't say it again kinji, its a prom....", kasa k'arasa maganar yayi jin fragile tiny hannayenta da tasa ta zagayeshi ta baya dukda ba k'arasawa sukayi ba, nutsuwa da baisan yana da ita ba a yau yaji na ratsa shi jin hannayenta zagaye jikinshi, wani irin ajiyan zuciya ya sauk'e tareda sake k'ank'ameta a jikinshi ya lumshe ido yana shak'ar k'anshinta, dukda yadda yakejin heartbeat d'inta is at a faster pace amma bayason wannan yanayin ya wuce shi ko kad'an, sunfi minti biyar a haka snn ya d'an sassauta rik'on ya d'ago hab'arta, har lokacin idonta lumshe suke, kallon kyakkyawan cute face d'inta yayi da yadda lips d'inta suka koma pink sbd kuka tana d'an twitching d'insu,murmushi ya saki yanajin wani kasala na sauk'o mishi tareda sunkuyowa ya had'e goshinsu waje d'aya sunajin sauk'ar numfashi su na fanning juna, a hankali ta bud'e idonta jin yayi shiru ko motsi bayayi, suna had'a ido tayi maza ta mayar ta rufesu, hannunshi ya d'aura bayan kanta d'ayan kuma kan waist d'inta ya matso da kan nata ya cikata gap d'in dake tsakaninsu, lips d'inshi yayi crashing kan nata har wani sauk'e ajiyar zuciya yayi ya shiga kissing d'inta with passion, batasan sanda ta fara maida masa martanin kiss d'in da yakeyi mata ba a hanKali, saida ya gaji dan kanshi ya k'yaleta yana maida numfashi, jawota yayi ta fad'a kanshi shima ya fad'a ya kwanta, hannu yasa kan lips d'inta yana making circles,yana shaping lip d'in nata a hankali, yana sata jin kamar ana royal rumble a cikinta, rintse ido tayi da k'arfi dan baza ta iya d'aukan feeling d'in da takeji ba yanzu, cikin maganarshi da ke dad'a sata jin wani iri yace "I missed you, your kiss though.....", sake shigewa jikinshi tayi batace komi ba ta k'ank'ameshi dan tasan mey yake shirin cewa, dukda bata ma ganin fuskanshi tasan murmushi yayi jin chuckles d'inshi datayi, turo baki tayi ta kai mishi dukan wasa tace "But I did well today ai", caraf ya rik'e hannun ya d'an matse, d'an k'ara ta saki tace "oucchh, it hurts mana Yaaa Abu, let me be I want to sleep", "That's exactly what I want you to feel, its okay you not loving me, but then missing me, shima bakiyi?", shiru tayi kamar bazata yi magana ba, batasan much about love ba ita, batasan ya yakeba, dukda taji wani al'amari na daban d'azu da ya furta mata yana sonta amma har yanzu ta kasa gane yaya wanan feeling d'in yake, she doesn't know if she loves him but missing d'inshi, ko bata fad'a mishi yasan she did, yasan tayi kewarsa, she is used to him now, kamar zatayi kuka a shagwab'e tace "Toh do I have say it, ai kasan nayi, much more than you do, I missed you more", ko da wannan ta barshi zaiyi baccin farin ciki ba sai ta furta son da take masa ba, yasan with time kamar yadda ya samu kanshi da sonta, yadda ya shigeshi farat d'aya ba tareda ya tab'a kawo hakan a ranshi ba, itama zata soshi da yardar Allah, murmushin dake fuskarshi ya fad'ad'a ya gyara mata kwanciya, bayanta na a jikinshi yayi cuddling tiny figure d'inta da duka hannayenshi biyu, Addu'a ya kuma yi, saida ya gama ya tofa ya shafeta dashi , ya sauk'o da hannunshi saman cikinta cikin rad'a yace and "Lil princess too, sleep safe Daddy loves you" snn ya shafawa kanshi ya dad'a matso da ita jikinshi yaja duvet ya  kashe musu bedside lamp d'in, Batuul duk rufe ido da zatayi kalmar "I love you" d'innan ke ringing cikin kanta, ta kasa dena jiyoshi, batasan lokacin da bacci ya d'auketa ba a haka, saida ya tabbata tayi bacci snn ya fara tunanin abinda ya faru yau, mesa Ajiddeh zata mishi haka, does he really deserve this?, laifin nashi ne, meyasa suka zab'i Batuul ba shi ba, how could she be so heartless and cruel, duk irin wannan azaba da Batuul tasha was because of her, wani d'aci yakeji daga mak'oshinshi, ya tabbata da wani ne ba Ajiddeh ba to da saidai yayi kwanan prison, ido ya rintse yana son kawar da tunanin, daga haka bacci ya d'aukeshi                 Tana fita Allah yasa taci karo da cab, lokacin da Mum ta fito bata ganta ba drivern ta dake zaune yana jiran ta tambaya ko yaga Ajiddeh yace yaga fitanta a guje, komawa tayi ciki tayiwa Ammah gargad'in wani abin in ya samu Ajiddeh she wont take it lightly, snn ta fito suka tafi da driver, sai kalle kalle takeyi ko zataga Ajiddeh, saida sukaje gida taga cab d'in parke k'ofar gida, ta tambayeshi ko shi ya kawo Ajiddeh by description yace ehhh amma bata bashi kud'i ba kuma ta fita ba tareda bayani ba, Mum ta ciro kud'i cikin jakarta ta mik'a mishi ta koma mota driver ya k'arasa da ita cikin gida, sak'e sak'e kawai takeyi a ranta, abubuwan sun mata yawa as of this time, batasan da wanne zata fara bama, komai ya dagule mata lokaci d'aya, masu aikinta ta kwalawa kira sukazo su biyu a tare, ta tambayesu ko sunga shigowar Ajiddeh, "Ehhh ta shigo amma tayi side d'in can na gefen na Sir", Mum ta wara ido duk da tasan nan ne wajen zuwan Ajiddeh duk lokacin da ranta ya b'aci tace "Ba nan aka ajiye matar nan ba da Daddy ya mask?", sukace "Nan ne Hajiya", tace "Kuje, Keh Sadiya ki tabbata kin kai mata abinci da duk abinda zata buk'ata snn ku zauna kuna lura da ita da duk motsinta", suka amsa kai da baki suka fita, suna fita ta janyo waya ta shiga neman layin mutum d'aya da tasan lallai zai samar mata mafita          K'arfe hud'u Abu ya farka, har lokacin yana jin Zuciyarshi bata mishi dad'i, idonshine ya fad'a kan Batuul da yasashi jin wani sanyi cikin ranshi, ya lumshe ido ya bud'e snn ya gyara mata kwanciyarta kamin ya sauk'o da k'afafunshi a hankali dan bayason yayi motsin da zata farka ya mik'e ya shiga toilet, wanka yayi tareda yin alwala ya fito ya zira farar rigarsa ya shimfid'e abin Sallah ya hau, raka'a biyu yayi snn ya d'auko Qur'an kan shelf ya fara karantawa a nutse yadda bazai tasheta ba, saida ya karanta Rabin Suratul Tauba cikin kira'arsa mai dad'i snn ya dakata yayi addu'o'insa, jin ana k'iran Sallah ya tashi ya gabatar da raka'atanil fajr kamin ya koma kan gadon, bayason fita ya barta ita kad'ai a d'akin, shi zai jasu suyi Sallah tare , hannu yasa ya shafi gefen fuskarta a hankali ya shiga k'iran sunanta, "Fatima wake up, lokacin Sallah yayi", a hankali ta bud'e idon da ya cika da bacci snn ta mayar ta lumshesu, murmushi yayi yace "You sleep too much, Sleepy head", tashi kiyi Sallah, its time", sai a lokacin taji mey yake fad'i, zuciyantane ya fara pounding tunawa da jiya da tayi, words d'innan na ringing cikin kanta, sake rintse ido tayi ta kasa bud'ewa, tsoron bud'e ido takeyi kar daren jiya ya zame mata mafarki, She have longed to hear someone say he love her, duk da ba sani tayi tana son nashi ba bataso wannan karon da ta samu taji ya zama mafarki, "Fatima", sulalewa tayi daga jikinshi tace "Toh kayi nima zanyi nawa anjima", mamakinta ne ya cikashi ganin taqi bud'e ido amma tana magana yace " Fatima Open your eyes", kamar baza ta bud'e ba a hankali ta bud'esu ta sauk'esu kanshi, cak ya d'auketa yayi toilet da ita, ya zaunar bakin bathtub d'in, brush d'inshi ya samata toothpaste ya mik'o mata, turo baki tayi ta ansa ta shiga wanke bakinta, tana gamawa ya jawo kan shower ya shiga tsiyaya mata ruwan, saida ta gama alwalan snn ya sake d'aukarta cak ya fito da ita ya saka mata dogon Hijab d'inta dake ninke gefe, saida suka idar yace "Tashi kiyi rak'atainil fajr", mik'ewa rayi ta jero raka'a biyu snn ta bishi suka ci gaba da addu'a, Hannu yasa jikinta yaji temperature d'inta yace "Good morning", kallonshi tayi taga murmushi shimfid'e fuskarshi, bata tab'a ji ya gaidata ba sai yau, kuma from his look its sincere, a hankali cikin jin kunya tace "ina kwana", ya rik'o hannunta yace "Baki amsa min ba", sunkuyar da kai tayi batace komai ba, "How you feeling right now?, kinajin wani ciwo?", kai ta girgiza mishi tace "Am fine", ya sauk'e ajiyar zuciya yace "Mai idon bacci, go back and sleep", mik'ewa tayi ta cire Hijabin ta ninke zata koma gadon taji ya rik'o mata hannu, yace "Hey, My princess, I couldn't say Hi to her", juyar da kai tayi tayi murmushi snn ta dake ta kalleshi tace "Its not like I care" ta k'wace hannunta ta koma kan gado, yayi dariya yace "Really?, well her Papa cares, Say Hi to her for me pls and tell her that Papa Loves her so much ", murmushi tayi ta shige cikin bargo tanajin kamar moment d'innan yayi ta zama haka, kada komai ya canja mata, cikin baccinta taji an rungumeta ta baya, gyara kwanciyarta tayi suka koma bacci, k'arfe goma ya farka itama ya tasheta, wanka ta farayi snn ya k'ira Farida a waya ta kawo mata kaya ta saka, bacci ma takeyi kasancewar yau weekend, idonta cikeda bacci ta taso ta kawo mata kayan, sai wani irin kallo take bin Batuul dashi tana dariya k'asa k'asa, Hararta Batuul tayi ta anshi kayanta tace "Kyaji dashi dai", bakin gadon ta zauna tace "Keh ni mey nace miki toh, kawai dan nayi dariya", Abu ya fito daga toilet, ya kalleta yace "kayan fa?", nuni tayi mishi dasu tace "gasu nan", yace "zaman na meye toh?", ta zumb'uro baki ta mik'e zata fita tace "Ammah tace ince muku breakfast is ready" kallonta kawai yayi ta fice Batuul na murmurshi, suna gama shirayawa ya rik'ota hannunta suka fito, tun tana qi har ta hakura, suna sauk'a downstairs ta fakaici idonshi ta warce hannunta tayi gaba abinta, kowa na kan dinning su biyune basa nan, Ammah da Abui da Sadiq ta gaida sukayi mata ya k'arfin jiki, a kunyace ta amsa da Alhamdulillah snn ya ja mata kujera ta zauna sukayi breakfast tare Da yamma suna zaune itada Farida a main parlour, kamar daga sama ta jiyo muryar su Ahmad, rabonta da jin muryarsu watanni kenan in ba a waya ba, da wani irin murna ta tashi t isa inda take jiyo muryar, da gudu ta isa ta rungumeshi hawaye na k'ok'arin zubowa idonta ganin duka kannenta a gabanta, d'aya bayan y'ata ta dinga rungumarsu snn ta karb'i Aabid dake hannun Sayyid tayi pecking d'inshi, sam ya manta da ita sai kallonta yake kamar yaga sabon mutum, jiki a sanyaye ta kallesu tace "Aunty fa?, batace zata zo bako?", Ahmad ya dubeta yace "ita tace muxo, zasu zo tareda Baba su dubaki wai", kai kawai ta gyad'a tana k'ok'arin maida hawayenta da bataso su gani tace "Ku shiga ku zauna, duk kunyi wani tsayi, Sayyid gashin meye haka ka tara kanka kamr wani black cotton?", dariya kawai ya mata ya sunkuyar da kanshi suka karaso ciki, Farida ta d'auki Hafiz tace "muje ka rakani sweet boy", basu jima ba ta sauk'o tareda Ammah, Ammah tace "Ashe manya bak'i ke tafe bamu sani ba, ya kuka baro gida, Ya Auntyn Ku?", Duk suka gaisheta snn suka amsa mata da tana lafiya, nan tasa aka cika musu gabansu da kayan abinci iri iri, suna nan zaune Abu da Sadiq suka shigo a tare, tausayinta yaji ganin yanda take farin ciki ganin yaran, bama yadda take yiwa Aabid wasa ba, ya k'araso wajenta batareda tasan ya shigo ba ya sunkuya daidai kunnenta yace "Hey am happy to see you happy", a d'an tsorace ta juyo ta dubeshi tayi mirmushi tace "Thank you", ya girgiza mata kai yace "You look cute holding the baby, can't wait to see you babysitting my princess", wara ido tayi tana kallon koda wanda yaji, ganin babu mai kallonsu ta sauk'e ajiyar Zuciya ta d'an bugeshi cikin wasa, dariya yayi ya mik'e ya anshi Aabid hannunta yana cakud'a mishi gashi yace "Hey Champ", dariya Aabid yayi mishi cute dimples d'inshi na appearing, da maamki ta bishi da kallo, gaba d'aya ba shine Abutturab d'in da ta sani ba months back, murmushi kawai tayi tana jin wani farin ciki a ranta da takeson ya d'ore a haka,d'aya bayan yaran suka gaisheshi yana amsawa, ya kalllesu yace "Maybe we should go out for ice cream ko, Movie or anything? am offering the treat, who wants to join?", Yusra da kamar jira take tace "Ni zanje, muje Blue cabana, they got the best ice cream and Chapman, yafi na ko ina and their Kebab, omg its so yummy, kasan ko Aunty sai ince mata akaini weekends wai saitace saidai a siyomin, am happy you are taking me.....", bata k'arsa ba Khalil ya sakar mata da wani harara, shiru tayi zata koma ta zauna ganin an harareta Abutturab da tunda ta fara magana yake murmushi ya kamo hannunta yace "Then you will get us all in munje ko" kai ta kad'a mishi, Batuul da mamaki take kallonta ganin yanda yarinyar ta k'ara tsayi, Abu yayi dariya yace ku fad'awa Ammah we are going tunda yamma tayi, Farida ta mik'e tareda Batuul zasuje su shirya, Abu yace "Farida ki sauk'o mata da Hijab in kinje sama", kallonshi tayi idonta yayi rau rau har hawaye ya ciko jin yace a kawo mata Hijab ta dawo kusa dashi a hankali tace "Hijab kuma?, dashi zanje?", ya kad'a kai yana wasa da Aabid ba tareda ya kalleta ba yace "Yeah, anything?", matsawa tayi daga kusa dashi ta zumb'uro baki ta zauna kan sofa, Farida ta sauk'o tareda Amamh riqeda Hijab d'in Batuul ita kuma ta d'aura veil kan cape top da skirt d'in dake jikinta, ta mik'awa Batuul hijab din, duk suka mik'e Ammah tayi musu Allah ya kiyaye sai sun dawo, Batuul ce kad'ai bata tashi ba tana fushin da babu wanda ya lura da ita, Ammah ce tace "Bitti tashi ki bisu kema ki warware jikinki kinji, zaman gidan ai babu dad'i, tashi kije", batason yiwa Ammah musu, mike we a tayi ta zura Hijab d'inta ta fita, koda taje k'in shiga motar Abu tayi dukda taga ya bud'e mata front seat, zagayawa tayi ta shiga ta Sadiq tayi zamanta batareda ta kalleshi ba, baima lura da Fishin da takeyi ba, bayan kowa ya shiga yaja mota suka fita tasu Sadiq ta biyosu a baya. [11/22, 11:21 PM] ‪+234 803 698 6494‬: 💖💝BATUUL💖💝 90 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR*       Har suka Isa Blue Cabana duk surutun da akeyi a motar batace komai ba, Sadiq ma duk tsokanarshi haka ya gaji ya kyaleta, bayan anyi parking da kamar bazata fito ba ganin kowa ya fito itama ta fito sai b'ata fuska takeyi, Abu na gama parking shima bayan yaran sun sauk'a ya rufe motar yacewa Farida ta karb'i Aabid hannun yaran nan ta rik'eshi snn ya zagaya ta wajen Side d'in da Batuul take, cikin wasa ya harareta ya kamo hannunta yace "Keh wa yace miki ana shiga motar Sadiq, he drives roughly, bare keda kike carrying baby na", ya d'aura hannunshi kan cikinta, da sauri ta wara ido ta kalleshi jin hannunshi a jikinta tayi maza ta ture hannun tana kalle kallen ko wani ya gansu, ko a jikinshi saima tsareta da yayi da ido, kauda kanta tayi ta matsa baya, yaci gaba "Kina ganin irin gudun da ya riqa shararawa kamar mai shirin barin garin, plss kar ki sake shiga driving d'inshi, I will be there for you always, In sha Allah kinji, Let's get going", d'an k'aramin bakinta ta tsuke tareda murgud'ashi tana janye hannunta, daidai kan idonshi, ido ya lumshe ya bud'e su kanta a ranshi yace "Damn, komai tayi kyau yake mata koda kukane, shi bai tab'a ganin wanda kuka keyiwa kyau ba kamar ita, badan bayason ganin kukanta ba yana damunshi yana sashi jin wani iri da kullum sai tayi mishi ya gani sbd in tanayi face d'inta na zama cute, ainihinta yake gani batareda k'arin komai ba sai lips d'inta da suke sake komawa pink, matsowa ya dad'a yi gabanta yace "Hey mey ke damunki", yasan wani abin ne ya sameta wannan attitude d'in da ta fara displaying, kamar jira takeyi ya tambayeta hawaye ya fara bin kuncinta, wani abin yaji har cikin ranshi, wlhy ko kad'an baya son ganin hawayenta, "Ya salam" ya furta snn da sauri ya jawota ya rungumeta sosai a jikinshi, duk da hijabin dake jikinta hakan bai hanashi jiyo d'uminta dake soothing d'inshi ba, Su Sadiq suka k'araso ganin basu taho ba, "Bro, for real?, a nan d'inma?", ya fad'a muryarshi cikeda tsokana, wani kallo Abu ya jefa mishi da yasashi fashewa da dariya, sai a lokacin ya lura da Batuul dake hawaye yace "Subhanallah, mey ya sameta haka?", ya juya yana tambayan su Farida da su Ahmad da suka tsaya cirko cirko suna kallonsu, kafad'a Farida ta d'aga mishi alamun she has no idea, muryan Abu yaji yace "You guys should get going, make sure kowa ya sami abinda yakeso, anything okay?", ya mik'o mishi ATM card d'inshi da ya ciro cikin aljihu yace "We will join you shortly", Sadiq da damuwa duk ya cikashi yace "Yeah okay....but then is she fine?, like babu matsala", Kai Abu ya kad'a mishi yace "Bakomai, Farida ki kula da yaran nan, let them have all they want", Farida ta kad'a kai ta kama hannunsu suka fara tafiya, suna tafiya ya jasu suka jingina jikin mota a hankali yake patting bayanta yace "Hayat meye kuma?, what is it now, kukanki yafi komai tada min hankali, you should please stop it and tell me mey ya sameki, mey kikeso?", ajiyar zuciya takeyi har lokacin, sassauta rik'on yayi snn ya d'ago kanta yana kallon fuskarta da ta b'aci duk da hawaye, sauk'e idonta tayi k'asa bata bari sun had'a ido ba, yasa hannu ya share mata hawayen yayi cupping fuskarta da duka hannayenshi yace "Okay now tell me, mey kikeso", kamar baza tayi magana ba a hankali tace "Ko ba kaine ba", jin tace shine ya wara ido ya kalli fuskanta da kyau yace "Huh?, Really?, Ni na saki kukan?, Me nayi toh, tell me please , I will rectify it right away kinji", ya k'arashe maganan kamar zaiyi kukan shima jin shi ya sata kuka, cikeda shagwab'a kamar zata sa wani sabon kukan tace "Ko ba kai bane ba kace sai in saka hijab bayan zafi akeyi kuma fa its an evening outing sai kowa ya rik'a ganina kamar matar aure fa", sosai magananta ya bashi dariya da mamaki, bai san shirmen nata har ya kai haka ba, d'ago kanta yayi yana kallonta tareda sa hannu yana zagaye shape d'in da Hijabin yace "Fatima Hijab din ne baki so?", bata d'ago ta kalleshi ba tace "Ni ai bance banaso ba, kawai fa Kaine, kowa sai yace ni matar aure ce", ta sake fashewa da wani kukan, rungumeta ya sakeyi yanzu kam dariya yayi da kyau yace "And that's exactly dalilin da yasa nace ki saka Hijab, banason ana kallemin keh, bazan saurarawa duk wanda yayi miki wani irin kallo ba, you are married Fatima, married to me, you are just mine", ajiyar Zuciya ta sauk'e jin maganunshi tace "Ba toh zan iya saka Abaya ba or any gown", yayi murmushi yace "Yeah hakane but then, hijab zaifi rufemin keh all, nafison ganin ki so modest da kowa na ganinki yasan yes you are married, don't you know immodest dressing shike attracting filth, shike janyo duk wata musiba ta yanzu da ake facing tsakanin opposite gender", dogon numfashi taja jin abinda yace kuma tasan gaskiya ya fad'i, a hankali ta janye daga jikinshi tace "toh shikenan, am sorry", kamota yayi yayi pecking goshinta yace "I love you", wani irin rumbles taji a cikinta kamar jiya jin ya sake maimaita mata I love you, yace "Let's help you ki cire Hijabinki sai muyi zamanmu cikin mota tunda kinga zafi kikeji, I will order duk abinda kike so here", ya fad'a yana ciro wayarsa daga aljihu, da sauri ta riqe mishi hannu ta girgiza kai tace "No am fine, ai na dena jin zafin", murmushi yayi yace "Sure?", ta kad'a mishi kai tace "Yeah", da haka ya riqe hannunta suka isa wajen dasu Sadiq suke, lokacin har kowa yayi ordering abinda yakeso,  ido suka zuba musu su dukan suna jira suji mey ya sameta , kujera Abu Abu ya ja mata ta zauna snn shima ya zauna, raurau tayi da ido ganin duk ita suke kallo ta kalli Abu, murmushi yayi ya kallesu ya d'aga musu gira yace "She is fine, babu abinda ke damunta, y'all should relax", explanation d'in abinda ya sata kuka suke jira yayi musu amma ganin kamar bazai yi ba sukayi shiru kowa yaci gaba da abinda yakeyi, waiter ya k'ira ya bashi order abinda za a kawo mishi snn ya ce Batuul ta fad'i abinda take so, tace "Chicken wings in marinated sauce with plenty garlic, Large Lasagne, cream in chicken soup with emm french bread... ", tsayawa kowa yayi ya zuba mata ido jin taqi dena ordering, a hankali Farida tasa hannu ta d'an tab'a ta tace "kee ina zaki zuba duka wannan abinda kike ordering, mey zakiyi dasu?, k'asa k'asa tayi maganar, murgud'a mata baki tayi tace "Keh kam ina ruwanki, inma zubdawa zanyi", ta juya taci gaba da bashi order "With spicy lamb kebab, sour cream sauce, butter scotch ice cream with some toppings, just any and strawberry shake", Abu kam danna wayarsa yakeyi har saida ta gama ya kalleta yace shikenan?, kai ta kad'a mishi yace "Okay you can go",  ganin Expressions dake shimfid'e fuskarsu ta d'aga musu kafad'a tace "Wai meye nayine, nifa zanci kayana",  Sadiq ya saka wani irin dariya da  yasa Abu ya d'ago yana neman mey yakewa dariya, cikin dariyar yace "Do you eat this much ko kuma dai da wani abun, am not getting this seriously", ya sake saka dariya, Farida ma tasa dariya, wara ido tayi snn tayi raurau dashi ta kalli Abu kamar  zatayi kuka, kujerarshi ya ya matsar kusa da nata with stern voice yace "Saaadiqq", snn ya watsawa Farida dake k'ok'arin had'iye dariyarta harara, "don't mind them, shiyasa kikaga basuda lafiya, Eat as much as you want, babu ruwanki dasu", ta tsuke baki tace "Bafa dayawa ma nayi ordering ba, kad'an ne fa dan inajin kwad'ayinsu ne duka", ya jawota jikinshi yace "Shhh don't worry, ya kwantar da kanta kan kafad'arshi, suna zaune har aka kawo mata duk abinda tayi ordering        Tunda Ajiddeh ta shiga d'aki bata fito ba sai washegari da safe, tasha kuka har ta godewa Allah, da yamman ranan ta fito daga d'akin da ta kwanta ta taga masu aiki sai kai kawo suke wani d'aki, k'arasawa tayi taga waye cikin d'akin, ta manta da sam Mummy tace mata akwai matar da Daddy ya kawo gidan, wata mata ta gani da bandage d'aure jikinta, sai kuma a kanta, sosai ta tsaya tana kallon matar snn ta tab'e baki ta juya ta koma d'akin da ta kwana ciki ta ci gaba da zamanta, ko sau d'aya Mum bata lek'o ta ganta ba sai masu aiki da take tura mata, wayarta da Mum ta bada a kawo mata ta d'auk'a ajiye nan kan gadon, samun kanta tayi da logging wajen calls da neman sunanshi, a hankali ta shafa sunan hawaye na zubowa idonta, tana son Aliyu amma abinda tayi mishi bata tunanin zai yafe mata shi, dialling number tayi, tun kamin yayi ringing tayi maza ta katse k'irar, gallery ta shiga tana kallon hotunansu da sukayi a tare, tana jin inama ya saurareta ko sau d'aya ya bata chance d'in nuna mishi she has changed for good, koda bazai sota ba ita zata soshi, tana cikin tunanin nan ta jiyo tafiyar Dad, sai a lokacin gabanta ya shiga fad'uwa, batasan mey zata ce mishi ya dawo da ita, tashi tai zata shige toilet ta b'oye daidai nan ya hangota, da mamaki k'arara a fuskarshi yake kallonta da ta k'ame waje d'aya hannunta rik'e da knob d'in k'ofar, da mamaki a muryarshi yace "Hauwa, yaushe kika dawo gida?", a hankali ta shiga takowa gabanshi hawayen da take k'ok'arin maidawa na zubowa, a hankali ta k'araso tace "Daddy ina wuni", kallonta kawai yakeyi da ganin yanayinta snn mey take nema side d'in nan, "lafiya", abinda yace kenan snn yace "Tun yaushe kike gida haka, tareda Aliyun kuka dawo?", kai ta shiga girgizawa ta fashe da kuka mai tsanani da k'yar ya lallasheta tayi shiru snn ta da kyar tace, "jiya muka zo shine banajin dad'i nazo gida", kallonta kawai Dad keyi yasan there is more to wannan maganan ba abinda ya faru kenan ba, yace "Shine da shirme da bakida lafiya zaki taho gida, mu lafiyan zamu baki anan gidan d'in kome?", jiki a sanyaye ta rik'o hannun Dad tace "Dad kuma ina missing d'inku shiyasa fa nazo, kayi hak'uri zan koma gobe", tanayi hawaye na ci gaba da zubowa, yace "Its okay, bar kukan, but next time kar ki sake wannan wautar, bakida inda yafi gidan mijinki daraja, yaron kirki mai mutunci ma da yasan darajar mutane, he calls me every two weeks and kowane Sallah da previous azumi in zai bada Sadaka, sai ya k'aramin da wanda zan bawa mutane, he is a good son really, ki kula dashi sosai Hauwa kinji, I don't want you to be like your Sister da ta zama kamar itace k'anwarki, kiyi hak'uri kiyi zamanki gidanki, Allah ya miki albarka", wani kuka taji yaxo mata da batasan yana shirin zuwa ba ta rungume Dad, murmushi yayi ya d'agota yace "Karki damu, my prayers are always with you", ya kamo hannunta yace "I got a patient a wannan d'akin, muje ki gaisheta", suna tafiya yana bata labarin yanda accident d'in nasu ya faru, har suka k'arasa d'akin, ko da sukaje zaune suka tarar da matar da Qur'an gefenta alamar karatu ta gama yanzu, bayan sun gaisa yayi mata ya jiki yace "Ajiddeh wannan itace Kulthum, Kulthum ga d'ayar y'ar tawa sunan ta Hauwa", da murmushi matar tace "Masha Allah, Allah ya rayata, d'azu naga ta lek'o banma san itace ba", Dad yace "Toh ni zan koma inda matsala sai a nemini, Ajiddeh stay here with her for today, keep her company", kai ta kad'a ya fita daga d'akin, kallon Kulthum Ajiddeh ta tsayi, mata mai kyau da ita ko ina y'an uwanta suke, baki ta tab'e ta nemi guri ta zauna dan tunanin nata matsalar      Koda aka kawo musu abincin, babu wanda tayiwa ci biyu, shake d'in nema tasha da d'an yawa, sudai da mamaki kawai suke kallonta, Su Yusra ne sukace sunason a kaisu XD cinema, Farida da Sadiq sukace su tashi su kaisu, Batuul dake shan shake d'inta Farida ta duba tace "You going?", d'auke kanta tayi tace "Kuje, kaina zaimin ciwo in na shiga wajen nan, harara Farida ta sakar mata tace "Kedai kyaji dashi, you and your unending problems", had'e rai tayi ta  kalli Abu snn ta kalli Farida zatayi magana Abu yace "Farida!!!, ta zumb'uro baki ta kama hannun yaran tace "Kunga kuzo mu tafi, mulki take ji dashi yau d'innan", daga haka suka k'ara gaba abunsu, Abu ya kalleta yayi murmushi yaci gaba da danna wayarsa, sau biyu tana kallonshi taga danna waya kawai yakeyi yana murmushi, yana zaune bai lura da  lokacin da ta tashi daga kujerar ta bar wajen ba, wasu mata ne suka zo suka zauna kan kujerun, da mamaki ya d'ago yana kallonsu jin wasu muryoyi daban, kallonsu ya tsaya yi yana so ya tuno inda ya sansu, they look familiar, d'ayar ce yaji tace "AAK, ashe ana ganinku a gari, tun daga makaranta shikenan kun b'uya ba a jinku, though kwanaki naje ance ka auri wannan yarinyar Ajiddeh, ya kk ya kwana biyu", sai a lokacin yayi recalling faces d'insu amma bazai ce ga sunayensu ba, kallonsu yake d'aya bayan d'aya snn yace "Excuse me Dan Allah, baku had'u da wata zaune nan kujerar ba?", tab'e baki sukayi sukace, "No we didn't meet anybody gaskiya, ya kk toh ya matar taka?", gaba d'aya hankalinshi baya kansu yace "Yeah she is fine, sorry excuse me, I need to go now", daga haka ya mik'e ya barsu nan zaune, ransu duk ya b'aci amma inda sabo sun san halinshi ne hakan, wayar Batuul ya shiga k'ira amma bata d'auka daga baya ma kasheta akayi, hankakinshi gaba d'aya ya gama tashi, su Sadiq ya k'ira yaji ko tana tare dasu sukace mishi bata zo ba, ya ma rasa ina zai fara nemanta, itakam bakin wani pond taje ta zauna tana kallon swans d'in dake cikin ruwan, sosai suke birgeta, tana daga zaune lokaci lokaci take kallon shi taga yana zaune abunshi, ita da kanta bata san haushin mey take ji ba, wani irin fad'uwa gabanta yayi lokacin da ta hango matanan nan zaune wajenshi, da sauri ta d'auke idonta daga kansu amma curiosity ya sata juyawa ta sake kallonsu, dariya taga sunayi, da sauri ta sake juyawa sbd yadda taji zuciyanta na bugawa, hawaye ne taji ya tarar mata a ido, tana ganin kiranshi tasa wayar a silent, daga baya ta kasheshi gaba d'aya, duk inda yasan zai ganta sai da ya zaga, duk abin nan da yakeyi idonta na kanshi, yana d'aga ido ya fad'a kanta, tana zaune tana kallonshi, da wani irin hazari ya k'araso wajenta tareda fizgota yana k'are mata kallo ya tabbatar if she is fine, wani irin kallo ya bita dashi yace "kinada hankali kuwa?, mey ya tadaki daga wajen da kike, are you even okay wai?, mey ke damunki, tell me now", d'auke kai tayi ta ki yadda ta had'a ido dashi sai da ya sake dad'a k'arfin rik'on yace "I will slap you right away, ina miki magana kina d'aukemin kai, what's wrong with you?", wani irin kuka tasa da yasa jikinshi yayi sanyi, d'an tsaki yaja yasa hannayenshi duka cikin gashinshi ya bajesu, d'aukarta yayi cak ya nufi hanyar mota da ita, lamo tayi jikinshi gabanta na fad'uwa, sai da ya bud'e mota ya sakata ciki snn ya kira Sadiq a waya yace "Sadiq you can take the kids home when they are done, daga nan sai a kaisu gida", bai jira mey Sadiq zaice ba ya kashe wayan [11/22, 11:21 PM] ‪+234 803 698 6494‬: 💝BATUUL💖💝 91 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* "Lukman get the key to my house, right away", daga d'aya b'angaren Lukman ya amsa da "Hokay Sir but which of the Ouses?", "Mississippi Street, you should get there right now, I will soon be there", yace "Hokay Sir Hi will do that", ya katse wayar ya ajiye, kallonta yyi har lokacin hawaye ne idonta ya bud'e baki zaiyi magana kenan suka iso bakin gate,  ya mik'owa masu gadin card d'insu ya fita daga harabar Blue cabana, kallo d'aya yayi mata ya maida hankalinshi kan tuk'in da yakeyi, hijabin jikinta taja taci gaba da goge hawayen dake zubo mata, ita da kanta ta rasa hawayen mey takeyi, attention d'in da bai bata bane ya zauna yana danna waya  ko kuma matan da ta gani suna magana dashi harda dariya ya sata b'acin rai, wani iri taji da ta tuna da matan har saida gabanta ya fad'i, batayi yunk'urin goge hawayen ba dan ba daina zubowa zasuyi ba, hannunshi taji a fuskarta yasa ya shafo hawayen yana murzasu yana kallonta, a hankali ta sauk'e idonta k'asa, zaiyi magana wayarsa ta fara ringing ya duba ganin mai k'iran yasa ya d'aga tareda cewa "Sorry badai har kun fito ba", daga d'aya b'angaren Massa ya amsa da "Yanzu haka ita na d'auko, baku dawo bane?", d'an siririn tsaki yaja yace "God man am sorry wlhy ba yanzu zamu dawo ba, I had to but am sorry", Massa dake d'aya b'angaren yace "For real?, I told you gobe zata koma Sokoto kuma dan Batuul zata, ita ta tsaya dubawa", Abu yace "I know, I understand, am having issues over here so nake inyi clarifying before getting back home, bawa Rahamar waya muyi magana da ita", Tsaki Massa yaja yace "You are a jerk kaima ka sani ko", dariya Abu yayi yace "Not better than you, d'an bata wayar nikam, da ita zanyi magana ba kai ba", cikin siririyar muryarta tace "Hello", Abu yace "Hey, am so sorry, wlhy abune ya tsaida mu nan kiyi hak'uri, next time har gida zan kawo miki ita ku gaisa kinji", ya juya ya kalli Batuul yaga har lokacin kanta a k'asa yake, a hankali Rahama tace "No fa, ba komai, there will surely be next time, Allah ya bata lafiya ya k'ara mata lafiya", wani irin sanyi yaji har cikin ranshi jin addu'ar da Rahaman tayiwa Batuul da murmushi a fuskarshi yace "Amin ya Allah, sorry once again and Thank you", murmushin tayi itama tace "Ba komai fa", yace "Yawwwa mun gode Allah ya kiyaye hanya", ta amsa da Amin snn ta mik'awa Massa wayan, Abu yace "Ita mai zuwa dubiyan da kanta ta hak'ura, ka dawo goben ka dubata", Tsaki Massa yaja yace "Kaga ni kai ta sani, zan kaita ta gaida Ammah in kuma ka dawo daga gantalin naka ka samemu, fine", Abu yayi dariya yace "kaima zaka fito  gantalin ne anytime soon, just get married", Massa yace "My regards to her, kayi mata ya jiki pls", Abu yace "Sure zataji", ajiye wayan yayi ya d'ago kanshi suka had'a ido, da sauri ta d'auke nata idon tana twitching d'an k'aramin bakinta, murmushi yayi ya kamo hannunta yana murzawa a ranshi yace "She will b the death of me", bata yi yunk'urin k'wace hannunta ba kuma batace mishi komai ba, yace "Rahama tace inyi miki ya jiki?, they wanted coming now kuma nace musu bama gida", d'ago kanta tayi tana kallonshi tanaso ya fad'a mata wacece Rahama dan batasanta ba, yayi murmushi ya sak'e damtse hannunta yace "Mustapha's fiance", batace komai ba ido ta lumshe kawai hawayen da ta kasa riqewa na dad'a taruwa,  shima bai sake cewa komai ba amma yana riqe da hannunta d'aya yaci gaba da driving d'inshi, bakin wani baqin gate taga sun tsaya, horn yayi aka wangale musu gate d'in suka shiga  tunda suka shiga gidan take k'arewa gidan kallo , ba wani babba bane sosai, duplex ne amma yayi kyau sosai, fitowa yayi daga mota, Lukman dake tsaye jingine jikin tashi motar ya k'araso wajenshi, saida ya gaisheshi snn ya mik'a mishi key d'in, Batuul ya hango zaune cikin mota yace bari su gaisa da Madam, Abu ya girgiza kai yace "No Lukman not now okay, next time", Lukman da murmushi fuskar shi yace "Hokay Sir, Hi will leave now", daga haka ya koma motarshi ya shiga ya tafi, Abu ya zagaya ta wajenta ya kamo hannunta sukayi gidan, parlour ne mai girma sosai, sosai tsarin gidan yayi mata kyau, bai sake mata hannu ba har saida ya zauna bakin gadon bedroom d'in gidan dake sama, Wani fridge ya bud'e ya fiddo ruwa roba d'aya kamin ya dawo ya zauna daga gefenta snn yasa hannu ya juyo da ita tana fuskantarshi ya bud'e ruwan ya mik'a mata, a hankali tasa hannu ta karb'i ruwan tasha kad'an, sai kallonta yakeyi yana lumshe ido ya bud'e, Miko mishi tayi yace "Ya isheki?, ta d'aga mishi kai alamar ehhh, shima shan ruwan yayi ya ajiye gefe snn ya rik'o hannayenta duka biyun, wani irin bugawa kawai zuciyarta keyi, a hankali ta lumshe ido, kamar daga sama taji muryanshi yace "Do you need to see a therapist?", bata san lokacin da ta bud'e ido ta kalleshi ba jin abinda yace", wara ido tayi a sanyaye ta fara k'ok'arin janye hannunta ya riqe da k'arfi, rungumeta yyi yana d'an rocking d'insu yace "sorry its okay baza ki ga wani therapist in baki so,", a hankali ta d'ago kanta da wani irin smile fuskarta tace "I look mental huh?, ta goge d'an hawayen dake fuskarta, kai ya girgiza mata ya sake rungumeta yace "ko kad'an Fatima,  I just want you to be happy, banason ganinki kina wannan kukan, you barely spend 5hrs batareda kin zubda Hawaye ba, and  yana damuna, gani nakeyi kamar ban kyauta miki ba, its hurting me nima", kallonshi takeyi har yayi shiru batace komai ba, yace "Say something, bana son kallon nan, I just want you to be happy, I love you sosai Fatima", kamar yanzu ta fara jin kalmar I love you d'in bakinshi, abin nan da takeji kullum shi taji yauma, a hankali tace "Then why where you ignoring me if so d'azun?", wara mata manyan idonshi yayi yace "Dagaske?, I did that?", kau da questions d'in tayi ta sake cewa "those ladies da suka zauna suna maka magana suna dariya fa?, who were they?", sai yanzu ya lura da kishi ya sata kukan nan, shi sam ya ma manta da dasu wlhy, dariya ya fasheda da ya sake kufular da ita, rai b'ace ta tashi daga kan gadon zata bar wajen yayi sauri ya fixgota ta fad'a kanshi, idonshi yasa cikin nata da yasa tayi saurin rintse su zata mik'e, hannu yasa ya zagayeta ya matseta jikinshi har yana jiyo heartbeat d'inta,  cikin wata iriyar murya tace "Nikam let go of me, ba dariya kayi min ba", dariyan ya sakeyi yace "ashe kina kishina tinda har kikayi kuka dan kin ganni da wasu", tsuke baki tayi tana son barin jikinshi yaqi saketa, ya tsagaita dariyan yana k'arewa fuskanta kallo yace "You have changed me Fatima, you have changed me a lot cikin k'ank'anin lokaci, ban tab'a kawo zama ina rarrashin mace ba sai gashi kin sani na fara, I get emotional anytime nayi tunanki", "your eyes", ya d'an hura mata iska a fuska, "your lips", ya fad'a yana zagaye lips d'inta da k'aramin yatsanshi, "your cute chiseled nose", ya fad'i tareda  had'e hancinsu, "I like everything about you, duk wani uneasiness da nakeji a da yanzu nasan mesa nake jinshi, inasonki but I couldn't realize", hawaye yaga ya ziraro mata a ido, d'an murmushi yayi yace "Bana son zama sanadin zubar precious hawayen nan pls kinji, anytime nayi miki abu just yell, shout, tell me na b'ata miki rai amma banda kuka kinji?, kuka sosai tasa tana son ta tashi daga jikinshi ya sake matseta yace "fad'amin kukan mey kikeyi?", kasa motsi tayi zuciyanta na tsananta bugu, tsorata yayi jin yadda zuciyanta ke bugu ya mik'e tareda zama yana kallonta yace "Fatima are you okay wai, meke damunki ya Allah?", a hankali kamar mai koyon tace "I... love.... you", kamar wani shigewar iska haka yaji maganan ta daki dodon kunnenshi, kallonta yakeyi yanason tabbatar da abinda yaji ya fito daga bakinta, idonta yake nema ya gani dan ko zai tabbatar mishi da abinda ta fad'an, hab'arta ya d'ago yana kallon fuskarta, sauk'e ido tayi tanajin nauyin abinda ya fito daga bakinta, ta d'auka iya zuciya kad'ai ta fad'eshi saida ta gama furtwa tasan a fili ta fad'eshi, yace "Look at me Fatima, pls", da k'yar a hankali ta iya d'ago kai ta kalleshi, suna had'a ido tayi maza ta kauda nata, wani irin runguma taji yayi mata, tare suka sauk'e ajiyar zuciya, a kunnenta yace "son nawa ne ya saki kukan da kikeyi?", a hankali ta girgiza mishi kai, ya d'agota kamar da damuwa a ranshi yace "Toh mey ke saki kuka?" Cikin sanyin magana tace "The very first day i met you, i know something in me has changed da har uanzu bai koma daidai ba, You came into my life lokacin da banyi zato ba, na d'auka you are just here to snatch my happiness, na d'auka duk wani farin ciki da zanyi ragagge ne tunda ka shigo rayuwata, I never thought I could fall for anyone so easily but then I realised kullum anytime nayi tunaninka, I get emotional, anytime I see you, I feel happy, anytime you come in contact I feel shivers down my spine, that feeling that I can't express, tsoro nakeji Yaa Abu, am scared", ta rik'o hannayenshi duka biyu ta rik'esu da k'arfi, kallonta kawai yakeyi, Batuul ce zaune gabanshi tana expressing mishi son da take Mishi, jiya ya gama expressing mata but bai tab'a kawowa kanshi anytime soon Batuul will fall for him, ta fad'a mishi itama heartbeat d'inta is  never stable when ever they are close amma ya d'auka tsoronshi ne duka ya janyo hakan, ya sake damtse hannunta ya sunkuyo yana kallon fuskarta yace "Kalleni, mey ke tsorataki, tsoron mey kikeyi when you have me?", ido ta lumshe ta bud'e tayi d'an murmushin jin dad'in abinda yace, mey zai bata tsoro bayan tana dashi, ajiyar zuciya ta sauk'e da tayi tunanin ba nata bane ita kad'ai, she have to share him da wata, "Fad'a min mana, tsoron mey kikeji?", a sanyaye tace "Of losing you", wani irin farin ciki yaji har ranshi, ya sake tabbatarwa dagaske take tana sonshi, wani lallausan murmushi ya saki ya d'ago hab'arta da tak'i yadda su had'a ido yace "And you think this will happen?, kin rigada kin sameni Fatima sai yanda kikayi dani, I don't need to remind you how much you have changed me, but zan fad'a miki cewa you have gotten Aliyu sai yadda kikayi dashi, Aliyu nakine ke kad'ai, baza kiyi sharing d'insa da wani ba", batason yana mata irin wannan alk'awrin, tun kamin ta sameshi tasan wata ta sameshi kuma babu yadda za ayi ya zama nata ita kad'ai, tasan ba mantawa yayi ba, badai yasone yayi ruining moment d'innan shiyasa yaketa wannan zubar haka", hannu tasa tayi cupping faces d'inshi tace "Ka dena fad'an haka, before me there was someone a rayuwarka, she got you before me", tayi wani irin murmushi tace "am okay with it, just love me, kar ka dena sona that's I want", sai lokacin ya lura da maganan da takeyi, sai lokacin hankalinshi ya nuna mishi cewa da Ajiddeh take, wani irin b'acin raine yaji ya ziyarce shi lokaci d'aya, ya kai hannu kan hannyenta dake fuskarshi ya riqe yace "ki riqe a ranki ke kad'ai keda ni and no one else", kallonshi take tana dad'a tabbatar da what he is saying, from his eyes tana ganin he meant what he is saying, kai ta girgiza mishi zatayi magana yace "I promise, ke kad'ai kike dani nima ke kad'ai gareni", ajiyar zuciya ta sauk'e ta lumshe ido zuciyarta na bugawa tana kokonton abinda zuciyarta ke shirin sata tayi, a hankali tayi leaning ta cikata gap d'in dake tsakaninsu ta had'e bakinsu waje d'aya, wani irin dogon numfashi yaja kamin ya amshi bak'uncin abinda yakeji yanzu, a hankali yayi parting lips d'inshi suka  shiga kissing junansu with so much affection, kamar wacce ta tuna abu tayi maza ta janye bakinta daga nashi, a raunane ya d'ago ya kalleta da puppy eyes yace "Plssss", had'e rai tayi tace "Su waye y'an matan d'azu da suka zauna suna maka magana harda dariya?", ajiyar zuciya ya sauk'e tareda lumshe ido ya sake kamota ya had'a bakinshi da nata, saida ya gaji don kanshi ya k'yaleta ya cire mata hijab tareda da kwantar da ita jikinshi ya na yamutsa mata gashinta da yake a tsefe, ya bud'e baki zaiyi magana  daidai lokacin wayarsa tayi ringing, dubawa yayi yaga Ammah ke k'ira, jiki ba k'wari ya d'aga, muryar Aunty Amnah yaji tana cewa "Sannunka Abu, ina ka kai y'ar mutane ana zuwa dubata bata nan?, Massa da Rahama tun d'azu suke zaune baiwar Allah kasa ta zaman jira, ka dawo da ita", murmmushi yayi yace "She is my wife, nafi kowa buk'atarta, suyi hak'uri su barni da ita, I need my wife", baki Aunty Amnah ta bud'e tace "Lallai Abu, yanzu ko kunyata baka ji kake cewa a bar maka matarka you need her ko?, toh ga Ammah nan kayi mata bayani", muryar Ammah yaji tana cewa "Abu bana son wasa, ina ka kai yarinyar mutane?", a hankali yace "Ammah she is my wife kuke magana kamar wata nayi kidnapping", Ammah tace  "Kana jina ko, Batuul d'in da bata da lafiya ko k'warin jiki bata gama samu ba shine zaka d'auketa ka tafi da ita gantali?", kallon Batuul dake kwance jikinshi yayi suna had'a ido ya sakar mata murmushi har lokacin hannunshi d'aya na cikin gashinta, itama ta maida mishi murmushin a ranta tana tunanin yadda zatayi facing Ammah,  yace "Ammah relax, dagaske babu inda na kaita, muna gida fa, she will be safe, I promise" tace "Ban gane gida ba, yanzu haka k'annen nata zasu tafi basuyi sallama da ita ba?", yaja numfashi yace "Ammmaaahhh, we will be back soon, ayi mana hak'uri, kuma ma zan kai ta ta gaishesu ai some other time", Ammah taja tsaki  tace "inace jikinta lafiya babu matsala?", yace "She is fine, yanzu zamu dawo", da haka ta katse k'iran, yaja numfashi ya sauk'e ajiyar zuciya, da sauri ta mik'e ta zauna tace "Kaga mu tafi, su Ammah na nemanmu", ya maidata position d'inta na da yace "We are staying here for the night", ta wara ido tace "No Yaa Abu, inajin kunyan Ammah fa", ya d'aura hannu kan flat tummy d'inta yana shafawa yace "Kin manta ma da tambayar da kika min, well those ladies da kika gani, all I can remember is we had classes together when I was in college", tace "toh shine suka zauna har kuka dad'e kuna magana dasu", yayi pouting lips d'inshi yace "Bake kika tafi kika barni ba, you unveiled me kika barni ni kad'ai, they thought banida mata shiyasa suka zo wajena", D'auke ido tayi da sauri, a ranta tace "Subhanallah", wani irin kyau yayi mata da yayi pouting, he will be the dead of her in har taci gaba da kallon face d'inshi da yayi pouting da girarsa da suka had'e waje d'aya, tace "su basusan mey mata bane Kai, I cried because of that, my heart was aching da na ganku a tare", ya sake tab'are fuska yace "Noooo, karki damu baki sake ganinsu anywhere close to me, kema promise not to leave me", pouting d'in tayi itama tace "I can't even do that, I love you", wani farin ciki na daban ke ziyartarsa, ya sunkuya yayi pecking d'inta "You know I do more", lumshe ido tayi tana jin wannan sabon yanayi da ta samu kanta ciki, a hankali tace "kaga fa kukana shi da kanshi yake zuwa, bani keyi ba", ya d'agota yace "And you know it hurts me ba?, I hate to see you cry", a hankali kamar zatayi kukan tace "I promise not to again", yace "Thank you, tashi muje kiyi alwala muyi sallah, its Magrib, ita ta fara yi snn ta jirashi ya fito shima yayi  suka dawo ya jasu sukayi sllh, zama yayi bayan sun idar yace zai musu ordering abinci su dan nan zasu kwana, da k'yar ta samu ya yadda suka koma gida, gabanta har fad'uwa yakeyi tana tunanin Ammah zata gane komai ga kunyarta da takeji yau, da Aunty Amnah suka fara had'uwa da ta bishi da harara tayi hugging Batuul tace "kika yadda kika bishi yawo?, gantalinshi fa ba mai k'arewa bane da kike ganinshi", murmurshi kawai tayi ta sunkuyar da kai, ya kalli Aunty Amnah yace "Nima haka zanje in samu uncle ince mishi ya dena zuwa ko ina dake, dama gashi kin fara tsufa, sai a d'auka yayarsa ce",  Aunty Amnah ta wara ido tasa salati tana tafi tace "Abu ka gama rainani, zamu had'une da kai har gida zakazo ka sameni", dariya kawai yayi dai dai lokacin Ammah ta k'araso ta harareshi tace "ai ka kyauta", murmushi yayi yana sosa kai yayi mata k'asa da puppy eyes d'in da yayi alamar tayi hak'uri, Ammah ta kama Batuul tace "muje kisha magani, ga soup d'in  kifin tun d'azu Amnah taxo dashi", ta manta sam da tacewa Aunty Amnah ma tana son soup d'in kifi, a kunyace tabi Ammah a baya, k'arfe tara Uncle yazo suka tafi da Aunty Amnah bayan ya yiwa Batuul ya jiki tareda yi mata alk'awrin kawo su Nawal kamin su koma Paris, wanka Batuul tayi ta shirya ta sulale d'akin Farida, hiransu sukeyi abinsu sukaji an bud'e k'ofa, duk suka dubi k'ofan a tare suka ga Abu ne, bai cewa kowannensu komai ba ya shigo yad'auki Batuul cak, tace "Yaaa Abu kayi hak'uri ka sauk'eni, kaga fa akwai su Ammah a gida", yace ba guduwa kikayi kika barni ba?", tace "naga fa kana wanka ne shine na tafi kamin ka fito", bakinshi ya d'aura wuyan da yasata kasa yin wata maganr, ranan kwanan farin ciki sukayi , sosai Abu ya gwadawa Batuul irin son da yake mata da missing d'inta da yayi a daren.       [11/22, 11:22 PM] ‪+234 803 698 6494‬: 💖💝BATUUL💖💝 92 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR*   Tunda Dad ya fita ya barta d'akin Kulthum Ajiddeh  bata sake cewa  komai ba, angle ta samu daga gefe ta zauna a takure, duk bayan minti d'aya sai ta duba wayarta tana jiran tsammanin k'iran, a hankali siraran hawayen ke bin fuskarta, rayuwarta a baya take tunawa, tun ranan da ta fara ganin Abutturab a school Allah ya d'aura mata sonshi, babu irin wahalar da batasha ba dan kawai ya fara koda kallonta ne amma yaqi, babu irin nacin da batayi akanshi ya nuna duk baisan abinda takeyi ba, gashi ko aboki d'aya bata tab'a ganishi tareda ba, shekarar da zai gama ita tana third year, sosai hankalinta ya tashi ganin har zai gama ya tafi, shawara ta yanke kawai na ta sanar da Mum, at first mum bata biye mata ba saida taji ko d'an waye shi d'in, lokacin ne Mum tace mata ko sau d'aya ta samu ya bud'e bakinshi yayi mata magana daga nan zasusan abin yi, baza ta manta ranar da suka shirya itada friends d'inta akan in taga ya shigo makaranta ran sunday ta shige gaban motarsa ba ya bigeta ko dan yayi mata magana ne, tunda duk Sunday a school yake yinta kuma babu mutane da yawa, hakan kuwa sukayi ranan Sunday babu mutane da yawa school, daidai ta hango motarsa ta tashi ta shiga drive way shikam da ya taho sam bai lura da ita ba, kiiiii ya taka brake, da hanzari ya fito, ranshi b'ace zai fara yiwa maishi fad'an rashin kula, sai a lokacin ya gane mace ya kad'e, duk nacin da take mishi baisa ya gane wacece ita ba, baki ya bud'e zaiyi magana ta fashe da wani irin kuka, babu sautin da yafi tsanar jin irin kuka bare na mace, duk masifar da ya kwaso kasa k'arasa yin ta yayi, kuka take sosai tana yarfe hannuwa dukda ba wani ciwo taji ba, d'aukarta yayi ya sata mota, friends d'inta na daga gefe sukayi mata signalling zata wuce, ido d'aya ta kashe musu alamun taji dad'in accomplishing mission d'inta, murna fal cike ranta tana jin ta jikinshi kamar lokaci yayi ta zama a haka, a mota ya sakata yace mata sannu daga haka ya fara driving, asibitin da yake zuwa can ya kaita aka dubata sukace bata wani ji ciwo ba amma sam taqi yadda ta taka k'afar, ya tausaya mata ganin yadda take kuka, Wheel chair yayi requesting da a bata, badan taso ba ta zauna Kai, sai da suka fito yake tambayarta makaranta zai kaita?, tace mishi kada ya damu ya kaita gidanta, yana tsaye bai shiga gidan ba yasa tayi waya aka zo aka shigar da ita, yana barin wajen da mortarsa ta daka wani uban tsalle, tayi hugging kawayenta, take ta bugawa Mum ta fad'a mata duk yadda abin ya faru, tun daga lokacin suke asiransu kanshi, wasu suyi tasiri wasu baza suyi ba, lokacin da yazo mata da zancen aurensu suma ne kawai batayi ba sbd dad'i, kamar a mafarki takejin lbrn, tasan Aliyu baya mata son da har zaice zai aureta, son da yake mata baifi 2% ba cikin 100% d'in da take mishi, tsoron kada wani abu ya sa ta rasashi ta shiga neman maganin mallaka, duk inda tasan za a bata abinda zaisa Aliyu ya sota ita kad'ai har abada saida suka zagaya itada su Mum da Aunty Jainaba, wani hawaye mai d'umi ta share daga fuskarta tana ci gaba da tunani, tunda ta zauna Kulthum ke kallonta, a hankali taji muryarta tace "Komai yayi zafi maganinshi Allah, ki fawwalawa Allah dukkan lamuranki shi zai miki jagora", wani iri taji maganar kamar ma ba da ita akayi maganan ba amma sanin su biyu  ne kad'ai d'akin yasa ta gane da ita take, bata kulata ba har lokacin, da dare ma haka Ajiddeh bacci kad'an tayi, washe gari ne ganin yanayin Ajiddeh duk ya canja tace "Hauwa tunane tunanen nan da kuka duk da kikeyi matsala zasu k'ara miki, ki samu ki sassautawa kanki, bance ni ba ko inason sanin matsalarki ba, a ah, ki samu wani amintacce da kika yarda dashi kika san zai baki shawara mai kyau ki fad'a mishi matsalarki zaki samu sauk'i a ranki, ko da mahaifiyarki ce ko mahaifinki, zasu fahimceki ko da wacce iriyar matsala kikazo musu, kallonta kawai Ajiddeh keyi ta kasa ce mata komai, batasan komai game da matar ba amma daga yanayinta tasan bazata cutar da ita ba, tashi tayi ta fice daga d'akin tayi side d'in Mummy, masu aiki ne sukace mata Mummy tun da asussuba ta fita amma tace kada a bari ki fita ko inane, wani kallo ta jefeshi dasu kamar in tayi niyyan fitan zasu iya hanata, juyawa tayi ta koma side d'in can, a hankali ta fara magana ta shiga zayyanowa matar abinda ke damunta, matsalarta da kuskuren da duk ta aikata, batace dai asirin kisa sukayiwa Batuul ba, tace kawai na zubda ciki ne da kuma barin gidan sukayi mata         Da asuba shi ya fara tashi, bai tada Batuul ba dan yasan bacci bai wani isheta ba, kwanciyarta ya gyara mata snn yayi wanka ya zira jallabiya ya fesa turarukanshi masu sanyin k'anshi ya fita zuwa masallaci, a masallaci ya had'u da Abui da Sadiq, Bayan an idar da Sallah snn suka gaisa, Abui yana tambayanshi ya jikin Batuul ya amsa mishi da "Alhamdulillah taji sauk'i", Sadiq ma ya gaisheshi yayi mata ya jiki daga haka suka shigo gida kowa yayi side d'inshi, a hankali ya turo k'ofar d'akin,  da mamaki ya kalleta ta kunna bedside lamp tana zaune kan abin Sallah riqe da Qur'an tana karanta Suratul Qasas cikin muryarta mai dad'i, Ido ya lumshe ya bud'e snn ya shigo d'akin tareda mai da k'ofar ya rufe, tunda yake da Ajiddeh bai tab'a ganin ta tashi Sallah batareda ya fad'a mata ba, ko ya fad'a sai lokacin da ta ga dama take tashi tayi, da sauri ya kawar da tunanin Ajiddeh yayi da sauri, daga gefenta yazo ya zauna, godiya ya dinga yiwa Allah cikin ranshi da ya bashi Batuul, a zuci yana bin duk ayoyin da take karantawa, kamar yau ya fara jin Qissoshin Annabawa dake cikin surar jin yadda take karanto shi, har saida tayi kusan rabi snn ta rufe ta shafa addu'o'inta ta maida Qur'anin kan bedside drawer, a hankali ta juyo ta kalleshi tace "Ina kwana", wani farin ciki yakeji a ranshi da ganinta, ji yakeyi kamar ya d'auketa ya kaita wajen da babu kowa, inda babu abinda zai sameta sai farin ciki, ido ta d'an wara ganin yana kallonta bai amsa mata gaisuwarta ba tace "Yaa Abu ina kwana", sai lokacin ya lumshe ido ya bud'e yace "Waye malamin da ya koya miki Qur'an?", cike da farincikin tuna mata malamin da baza ta tab'a mantawa dashi ba tace "Malan Ahmad shine malami na, mey yayi?", ta fad'a tana d'an yatsina fuska yace "Har Tajweed duk shi ya koya miki?", ta kad'a kai tace "Har komai ma shi ya koya mana dukkanmu dasu Ahmad da Sa'eed", yace "Ya complete sunanshi yake and yana ina yanzu?", tunanin mesa yake son sani a hankali tace "Sunanshi Ahmad Abu Hamira Daiba, su Ahmad sun san  inda yake, nasan har yanzu yana koyar dasu", a hankali ya janyota jikinshi yayi wrapping duka hannayenshi jikinta yace "In na bashi kujerar Hajj da Umara this year yayi?", da sauri ta shiga k'ok'arin juyowa taga dagaske yake nufin abinda yake fad'i amma bai saketa ba saima k'ara gyara mata zama da yayi ya d'aura fuskanshi kan wuyanta, duk da hijab a jikinta bai hanata jin d'umin numfashinshi dake sata jin wani a iri a jikinta ba, da k'yar ta iya bud'e baki tace "Dagaske?", yace "Kuma a bud'e mishi Tahfeez, inaso in princess ta girma ya koya mata", ya fad'a tareda sauk'e  hannunshi kan cikinta, "Inaso in ta girma itama tana min irin k'ira'arki", wani irin juyawa tayi ta rungumeshi sosai, yana jin yanayin bugun zuciyarta, shima d'in sake rik'ota yayi, kamar mai jin tsoron abinda zata fad'a tace "I love you", ido ya lumshe ya bud'e yana jin kamar kullum ta zama magana da zata fito daga bakinshi, ta d'ago da sauri tana kallon fuskarshi tace "Yaaa Abu tun yanzu ka fara sani farinciki, am scared yayi min yawa and mayb you might change nan gaba", kallonta kawai yakeyi for seconds ya kasa ce mata komai, da k'yar ya iya samu yace "Baki yadda da son da nake miki ba ko?, baki yadda I can forsake duk wani farin ciki nawa for you to be happy ba ko?", kunya ce taji ta kamata, lafewa tayi jikinshi hannunta kan k'irjinshi tana jin yadda yake heaving a hankali tace "Na yadda, bana so ne yayi min yawa", bakinshi ya d'aura kan nata ya rufe mata baki, saida ya d'ago yace "You deserve all happiness, ki kwantar da hankalinki kinji, you have got me for yourself", shiru tayi lafe a jikinshi, d'agata yai cak ya kwantar kan gado yace "You need sleep, kwanta kiyi bacci", ya shiga k'ok'arin cire mata Hijab d'in dake jikinta zai gyara mata kwanciya, kai ta girgiza mishi tace "Yaaa Abu da sanyi, I don't want to remove the hijab", bai ce mata komai ba har saida ya cireshi sannan ya rungumota jikinshi ya ja musu duvet yace "I will keep you warm", murmushi kawai tayi tana tuna ranan da sukaje gidanshi a London yanda yayi keeping d'inta warm har ta gama duk abinda zatayi, a hankali ta matsa jikinshi ta gyara kwanciyarta, cikin kunnenta ya rad'a mata "are you still cold?", juyowa tayi tana fuskantarshi da kyau tace "Will you always keep me warm all the time?", ya saka hannayenshi duka biyun yana zagayeta yace "Always and forever", daidai lokacin ta tuna da Ajiddeh, tana son ta tambayeshi ina take tana tsoron kada ya sake mata fad'a kamar na ranan, a hankali taji yace "Yaushe zamu koma gida?", idonta a lumshe batareda ta bud'esu ba tace "Nanfa?", yace "This is Ammah's house", ta zumb'uro baki tace "Ni I want to stay here", yace "No gidanki kuma fa, wa zai zauna ciki?", tace "Inada gida ne ni?, d'ayan ai gidanta ne, d'ayan Kumar kace na love of your life ne", dariya yayi yace "So baki manta ba?", tureshi tayi daga jikinta tace "Ni kam ka dena min dariya, a nan zan zauna", yace "Toh bud'e idonki in fad'a miki wacece love of my life d'in?", kamar yana ganinta ta murgud'a mishi baki, juyo da ita yayi yace "Plsss mana, ki bud'e idonki in fad'a mki gidan waye?", a hankali ta bud'e idonta suna had'a ido tayi maza ta rintse su, dariya yayi ya d'agota yace "Fatima get up and listen, gidan nanfa nakine, I built it for the woman I will love, I designed everything for her, banida ra'ayin k'ara aure, I want to live with just a single wife and then Allah yayi Hauwa baza ta zauna gidan ba, then it was you, tun lokacin da akace zan aureki a raina nasa gidan zai zama naki, I then programmed everything ya koma naki, censor and all but God so kind you turned out to be the love I wanted, the love I wanted to give and take and there the house is yours, kinga sai mu koma ko tunda kinada gida, only I and you have access to wannan gidan", jin shirun yayi yawa a hankali ya k'ira sunanta bata amsa ba, da wayarshi ya haska yaga bacci take, murmushi yayi tareda pecking goshinta ya gyara mata kwanciya suka kwanta bacci Tunda Ajiddeh ta fara Magana Kulthum ke karanto Innalillahi wa inna illaihi raji'un, sosai ta tsorata da jin lbrn snn ta tausayawa Ajiddeh, tasan duk so ne ya sata aikata abinda take nadama a yanzu, ta jima kamin ta bud'e baki da k'yar "Kuskure kikayi Babba, shirka ba k'aramin laifi bane, da lokacin kin mik'awa Allah lamuranki da ko baki had'a da kowa ba yaron nan zai zama mijinki tunda Allah ya kaddara da aure tsakaninku, amma da yake komai rubuttace ne babu yadda za ayi ki tsallake hakan, gashi nan yanxu koda ya hak'ura bazai dena kallonki da abinda kika aikata ba, kada ki gaji da bashi hak'uri koda yana korarki ne, itama yarinyar da ki nemi ta yafe miki dan ita akafi zalinta, batada haqqin kowa sai dai nata da kuka d'iba, ni bansan Mummy d'inki ya take ba da zai yiwu sai kije ki sameta kuyi magana da ita, yanda na fuskanci mijinki yana sonki har yanzu, ki sameshi ki sake bashi hak'uri", d'agowa Ajiddeh tayi da idanunta da suka rine tace "Baya sona, ya dena sona, cemin yayi in fita kada in sake nuna mishi fuskata", ta fad'a tana share hawaye, Kulthum da har ranta ta tausaya mata tace "Fushi yayi, in ya huce zai saurareki, ki bashi lokaci ya sauk'o, snn ki fad'awa Babanki cewa bazai yiwu ki koma gidanshi ba, sbd yace baya son ganinki", a tsorace Ajiddeh ke kallonta, batasan da ya Dad zai d'au zancen ba,haka tayi ta rarrashinta tareda kwantar mata da hankali, da yamma Dad da ya dawo duba ya jikin Kulthum da mamaki yake kallon Ajiddeh yace "baki tafi ba Hauwa?", hawaye ne ya fara zirya idonta, da kyar ta samu ta iya cewa "Dad ya koreni, yace I should not show my face to him ever", kallonta kawai yakeyi har ta gama magana, bayason raising family issue gaban Kulthum duk da hankali ya kwanta da ita amma baijin yin magana gabanta, Kulthum ya duba yace "ya jikin yayi sauk'i ko?", wani awkward haka take jinta, ce mishi tayi "Alhamdulillah tana jin sauk'i", yayi mata sannu da jiki snn yace in tana buk'atar abu ta fad'awa masu aikin a sama mata, ya juya kamar Ajiddeh bata d'akin ya fice, da gudu Ajiddeh tabi bayanshi, wani kallo da ya bita dashi yasa ta tsaya with pleading eyes tana so ya barta ta mishi bayani tukunna kamjn ya yanke kowane hukunci kanta, jiki a sanyaye ta durk'ushe wajen ta fasheda kuka, Daddy kam a ranshi yake tunanin irin tashi kaddarar, ko jiya da daddare saida Mum ta gama mishi tijara harda cewa mey ya tab'a mata duk zamansu, da yake ba mai son hayaniya bane bai biyeta sunyi surutu, masifa ta dinga yi akan zaman kulthum gidan, ganin yaqi kulata ta fice ta banko mishi tana cewa zai gani, duk sai tayi maganinsu, kanshi ne yaji yana sara mishi Dan abin yayi mishi yawa, Ajiddeh da yake ganin gara ita itama gashi tana fad'a mishi wani zancen daban, nan inda Ajiddeh ta durk'ushe ta jiyo k'arar wayarta, addu'a take a ranta Allah yasa Abutturab ne, da k'yar ta mik'e taje ta d'auki wayan, ganin Mum ce yasa ta maida wayar ta ajiye dan batasan mey zatayi mata ba in banda k'arin b'acin rai, har ya katse bata d'aga ba aka sake k'ira, d'auka tayi tasa a kunnen tana jiran jin mey zata fad'a mata, kamar a mafarki ta dinga jiyo abinda ake fad'a Mata, ta kasa yadda da Mum d'inta ce ake cewa tana Illorin, yaushe ta bar Abuja har ta tafi Illorin, wayar ce ta kubce mata daga hannu itama ta sulale tayi k'asa. 💖💝BATUUL💖💝 93 By phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Gabanta ne ke fad'wa, batason son tabbatar da abinda kunnuwanta ke jiyo mata, yaushe Mum ta bar gida har ta tafi Illorin, so take ta k'aryata zancen amma tunanin da wayar Mum aka k'irata ya sata saurin mik'ewa, a guje kamar wata mara lafiya tabi bayan Daddy, ba tareda tasan ta inda zata fara ba ta isa gabanshi tace "Daddy Mummy", Kallonta yayi yanason jin mey ya samu Mummy, a ranshi yace mey ma zai sameta, a daburce cikin kuka tace "Daddy wai Mummy ce wai sunyi accident", duk da maganar tazo mishi a ba zata bai nuna ba, dakewa yayi yace "Hauwa mey kuma kikeson sake aikatawa bayan wanda kikayi, burinku ne a kullum ku kunyata ku tozartani ku sani magana, dake da y'ar uwar taki duk kunyi nasarar cikar burinku, kun biyewa son zuciya, ki koma kiyi zamanki tunda shi d'in ya fiye miki shi kika zab'a", wani sabon kukan ta fasheda hawaye d'aya na bin wani tace "Dan girma Allah Dad kayi hak'uri ka saurareni, wlhy ba k'arya nake ba, yanzun  nan aka min waya da wayar Mum akace tayi accident hanyar Illorin, Dad dagaske ne dan ko da naje side d'inta bata nan, kayi hak'uri kasa a bincika muji ko itance dagaske", kallon Ajiddeh kawai yake a ranshi yana tunanin abinda zai kai Zuwairah Illorin, wa ta ajiye wa take dashi can garin da har zata tafi bada sanin shi bs", juyawa yayi ya tafi Side d'inshi a Ajiddeh na biye dashi a baya tana hawaye, yana k'arasawa d'aki ya d'auki waya yasa a bincika mishi ko dagaske ne abinda Ajiddeh ta fad'a mishi, ba a jima ba aka k'irashi aka tabbatar mishi da "Ehhh gaskiyane, matane uku da Driver d'insu sukayi accident d'in", ajiyar zuciya ya sauk'e dan ya rasa tak'amaimai abin fad'a, tashi yayi zai fita Ajiddeh dake zaune tana hawaye gefenshi ta taso tace "Kaji ko Daddy, an tabbatar maka da Mummy ce ko?, Na shiga uku Dan Allah Dad muje mu dubata, wayyo Mummy na",wani irin kallo da ya watsa mata ne ya sata saurin had'iye maganar dake bakinta, tun da take harara Dad bai tab'a yi mata shi ba sai yau, jiki a sanyaye ta koma ta zauna, fita yayi shida driver yana neman yanda za ayi a dawo dasu gida dan sai an had'a da police, baisha wahala sosai ba kasancewarshi d'an siyasa ko ina sunada mutane,       Wanka tayi ta zauna bakin gadon daga ita sai d'an towel, shima lokacin ya fito daga toilet d'in yace "Bata kawo kayan ba har yanzu?", kallonshi tayi ta zumb'uro mishi d'an k'aramin bakinta tace "Nace fa zanje In d'auko ka hana, nasan bacci takeyi ka tada ta", bai kulata ba ya d'auko wayarshi ya k'ira Farida a waya, yana bugawa ta d'aga yace "Har kin kawo kayan kenan ko?", kamar tana gabanshi ta girgiza kai tace "Yanzu nakeson in k'irata ta fad'amin wanda zata saka fa",  yace "Get the whole box here", ido ta wara kaman yana gabanta tace "Kai Yaaa Abu, da nauyi fa", bai jira mey zatace ba ya katse wayan", kayanshi dake ajiye kan gadon ya d'auka ya sanya, kinkiman akwatin ta shiga yi a ranta tana mitar tada da yayi daga bacci, gefen Batuul ya zauna ya shafi gefen fuskarta tareda juyota ta fuskanceshi yace "Fushin meye ne wai har yanzu haka?", ya fad'a yana shagwab'e mata fuska, d'auke kai tayi tace "Ni fa sanyi nakeji ka hana kuma inje in d'auko kayana", kallonta yayi cikin ido da ya sata tayi saurin sadda kai k'asa yace "bana son kina stressing kanki, am there all the time", ya kamo hannunta ya damtse cikin nashi, daidai lokacin Farida tayi knocking tareda turo k'ofan ta shigo da akwatin tana haki,Batuul na jin k'arar tab'a k'ofa dama ta janyo hijab d'inta ta saka, jan akwatin tayi har cikin d'akin ta snn ta dubi Abu tace "Ina kwana", daga gani daga bacci ta tashi yace "Baki iya jiran izini ba kawai you barged into d'akin mutane ko?", zumb'uro mishi baki tayi a ranta tace "Hmmmm ai saidai idan ba Yaa Abu ba", a fili kuwa cewa tayi "yayi nauyi ne shinefa na shigo kuma saida nayi knocking", idonta ne ya fad'a kan Batuul dake zaune daga ita sai d'an towel da hijab, duk ta shagwab'e fuska kamar zatayi kuka, batasan lokacin da dariya ta kubce mata ba, dariya takeyi harda hawaye snn ta tsagaita dariyar tayi pointing Batuul tace "Ya Allah, you have started gaining weight, Affan have to hear of this, kin ganki kuwa?" Abu da ya tsaya kallonta da mamaki ya daka mata tsawa yace "kina da hankali kuwa?, c'mon get out kamin in tashi in sameki", kallon Batuul da tayi raurau da ido yayi, yasan kuka take shirin mishi, Farida da ke tsaye wayarta ta ciro cikin aljihun rigan baccinta zata k'ira Affan, tsawa ya sake daka mata yace "Na fara wasa dake ko Farida?", kamin tace wani Abu ya tashi ya fizgota ya karb'e wayan ya turata waje, dawowa yayi bakin gadon yana kallon Batuul dake jiran k'iris ta fashe da kuka baki a tab'e, a hankali tace "Dagaskene av gained weight?", in banda iskanci irin na Farida babu ta inda yaga Batuul ta k'ara jiki, dalilin da yasa ma kenan bayason kaita gida sbd yadda duk ta rame, ya d'aura hannu kan wuyanta yana tab'a collar bone d'inta yace "I want you to, kin rame dayawa kuma banaso ni", tasan bazai fad'a mata ba, cire hannushi tayi ta mik'e ta isa gaban human size mirror dake d'akin tana kallon kanta, itama d'in babu ta inda taga ta k'ara k'iba, tasowa yayi ya biyota gaban mirror ya rungumota ta baya tareda tareda sauk'e ajiyar zuciya yana shak'an k'anshinta masu dad'i, ido ya lumshe ya bud'e dai dai nan hawayen da take ta rik'ewa suka gangaro, da sauri ya juyo da ita yana girgiza kai yace "Glitter noo, kar kiyi kuka plss", muje kisa kaya yau sai Farida ta fad'amin yadda akayi kikayi gaining weight" ya  fad'a tareda kamo mata hannu, d'ayan hannunta ta saka kan nashi, juyowa yayi ya dubi fuskanta yaga duk sai glittering d'in hawaye suke, rungumota yayi, bai tab'a ganin mutumin da hawaye bai mishi wuyar zuba kamar Batuul ba, jawota yayi suka koma bakin gadon, a hankali tace "Nasan ban k'ara jiki ba but nan gaba in nayi fa?, you will stop loving me ko?", yanzu ya sake tabbatar da harda yarinta cikin lamarin Batuul, dan kawai tayi jiki sai ya dena sonta?, he love her for whatever she is and whatever she will become of, wani light peck yayi mata a goshi ya rik'o hannuta cikin nashi yace "Hey look at me", kasa d'agowa tayi ta kalleshi saida taji yace "Glitter look at me", d'azu ma taji word d'innan daga bakinshi sai yanzu ta san da ita yake, sunaye biyu kenan ya saka mata yanzu, Haya da Glitter, har cikin ranta takejin sunan, a hankali ta d'ago ta dubeshi, Hannu yasa ya share hawayen dake shirin zubo mata yace "what will make you change the way you feel about me?", shiru tayi ta kasa cewa komai saida yace "Uhmm ina jinki", jiki a sanyaye ta girgixa mishi kai, yace "Ki bud'e baki kiyi min magana a hankali tace "Babu", yace "mesa kike tunanin gaining weight zaisa in dena sonki, wa yace miki jikinki nakeso Haya, wa yace miki structure d'inki nakeso?, Ina sonki for who you are da kuma what you are yet to be, banason sake jin kin sake fad'an haka, zamuyi fad'a kinji ko?", kai ta gyada mishi yace "Good" yana sa hannu cikin gashinta da bai bushe ba yace "zakiyi mura fa kina barin gashinki da ruwa", tace "yanzu fa zansa kaya inyi drying d'inshi", ta fad'a tana k'ok'arin tashi ya rik'ota yace "No ki bari in mun sake jik'ashi sai kiji dad'in drying da kyau", sarai tasan abinda yake nufi da hanzari ta mik'e tana dariya tace "A ah nikam, I can dry it haka nanma", dariyan yayi shima ya kamata ya zaunar kan stool ya shiga drying mata dogon gashin kanta mai santsi da shek'i, sai da ya gama snn ya taimaka mata ta shirya cikin navy blue lace mara nauyi mai k'ananan jan patterns yace su sauk'a ya fara jin yunwa, ya rik'o hannunta suka sauk'o dinning area, suna k'arasowa tayi maza ta janye hannunta cikin nashi, kallonta kawai yayi baice komai ba har ta zauna snn ya zauna, daga kitchen Ammah da Sadiq suka fito, da alama daga exercise yake saboda kayan jikinshi, yana riqe da apple yana taunawa biye da Ammah yana mata magiya, juyawa tayi ta dubi Sadiq tace "Kana jina fa Sadiq nace bansan zancen ba, ka samu Abui kuyi maganan dashi", ta k'arasa dinning d'in, Da sauri Batuul ta tashi ta karb'i pan d'in dake hannun Ammah tace " *Ammah Nda wattu* Ina kwana Ammah", "Ammah da murmushi fuskanta tana goge hannunta tace " *Bitti k3lewa selai, k3lewan fanema? Lafiya Kalau Bitti, kin tashi Lafiya?", ta tambaya tana gyara tray d'in fruits, a kunyace Batuul ta ajiye pan d'in dake hannunta tace "Alhamdulillah", ta dubi Abu tace "Ya jikin nata?", Saida ya gaisheta snn ya amsa da Alhamdulillah, ya dubi Sadiq da duk ya shagwab'e fuska yana tauna Apple d'inshi yace "Shi kuma wannan mey ke damunshi?", ya fad'a yana tambayan Ammah, Ammah ta zauna ba tareda ta dubi Sadiq ba tace "Ka tambayeshi gaka gashi, kunfi kusa inajin", kallon Sadiq yayi yace "Whats wrong?", a hankali Sadiq yayi wata magana da babu wanda yaji, Abu da ya had'e fuska yace "In ka shirya fad'an matsalarka ka biyoni ka fad'amin", Ammah tace "Shima da kanshi yasan hauka yake shirin yi shiyasa bazai iya fad'a makan ba, ni bara in fad'a mishi yaji yasan rashin hankalin da yake min", Ammah taci gaba tace "Wai aure yakeson a mishi", daidai lokacin Abui ya k'araso dinning d'in yana cewa "wakeson ayi mishi auren?", Sadiq da sam baiso Abui ya Karaso at this time ba yayi maza ya sadda kai k'asa, Abutturab tsabar mamaki kasa cewa komai yayi sai baki da ya bud'e yana kallon Sadiq d'in, Ammah tace "Wai Sadiq keson a mishi aure", murmushi Abui yayi yace "Har ka shirya kenan, ka shirya kula da y'ar mutane", d'agowa yayi suka had'a ido da Abutturab, Abutturab yayi mishi kallon you are not okay yace "wace yarinyar ce zata aureka bakada aikin yi?, Serving d'inma ba gamashi kayi ba bare ka fara maganan settling ", D'an kafad'a ya d'aga alamun am due fa snn yace "But ai inada gida, what else?" Sosai Sadiq ya bawa Abui dariya, Ammah da Abutturab kam ko kad'an abun wasn't funny to them, Farida ce ta sauk'o sanye da kayan bacci da hula kanta tana danna waya, jin maganan da akeyi ya sata k'arasowa da sauri tana maida wayar cikin aljihu tace "Laaah Ammah ku baku San ma yarinyar bafa, wai fa Layla k'anwar Uncle d'in Aunty Amna yakeso, ina jinshi yana waya da ita kullum, ko wallpaper d'inshi picture d'inta ne, bara ma ku gani" taja kujerar gefen Abui ta zauna tana mik'a hannu zata d'auki wayarsa dake ajiye gefe, Hannu Sadiq yasa y make nata hannun, b'ata rai tayi ta zumb'uro baki ta kalli Abui tace "Abui kana ganinshi ko", tunda Abu ya harareta tayi shiru ta d'auki plate ta d'ebi pomegranate tana sha, Sadiq ma harara ya sakar mata, Abui yace "Sadiq ba gida bane aure, it takes a lot fiyeda wannan, you are just 22, kana buk'atar time da kuma nutsuwa kamin kace zakayi settling, ka bari in ka gama Service ka samu aiki then you talk of settling amma banda yanzu, parents d'in yarinyar da kanta ma ba yadda zasuyi da zancen ba in ba aiki ka fara ba", Ammah da tayi serving Abui soup tana mik'o mishi tace "Sadiq in baka rabani da shirman nan ba ranka zai b'aci, itama Laylan da ta biye maka", Wani kallo ya jefi Farida dashi da ta tona mishi asiri, d'auke kanta tayi tana jin haushin make mata hannu da yayi, Sai da kowa ya nutsu yana cikin cin abinci Abu ya kamo hannun Batuul ta k'asa yana kashe mata ido, kallonshi tayi na ya sakar mata hannu, bai sake ba saima sunan Abui da Ammah da ya k'ira, a tare kowa ya kalleshi suna jiran suji mey zaice musu, Batuul dai gabanta sai fad'uwa yakeyi tana tunanin abinda zaice musu tana k'ok'arin kwace hannunta amma ya dad'a k'arfin rik'on, jin yayi shiru Abui ya maida hankalinshi kan abincin da yakeci, Ammah ce tace "Muna jinka", a nutse yace "Ammah inaso mu koma ne, inada aikin dayawa that are pending", tace "Dama can kai ne kayi zamanka, tunda taji sauk'i ka tafi abinka ka rik'a dawowa kana dubata, ido ya lumshe ya bud'e jin abinda Ammah tace snn yace "Ammah tare fa nakeson tafiya da ita, ba nan zan barta ba", Wani kallo Ammah tayi mishi a taqaice tace "baza ta koma gidan nan ba, ka barta nan in ya so ka riqa dawowa kana dubata", marairaice fuska yayi ya kalli Abui da puppy eyes d'inshi, yace "Ammah ba gidan nan zata zauna ba, tun kamin ta fara ciwo take d'aya gidana, Plss Ammah", Abui yace "Anytime you are ready ka d'auki matarka ku tafi", Kallonshi Ammah tayi zatayi magana yace "Meye amfanin barin nata da zaiyi a nan, ko ya tafi hankalinshi ba kwanciya zaiyi ba, su koma kawai zai ci gaba da kula da ita In sha Allah babu abinda zai sameta", Badan ta yadda ba ta hak'ura, Abu kam dariya yayi yace "Nagode Abui, Allah ya k'ara girma da d'auka, Allah ya k'ara Nisan kwana, Allah ya gafartawa magabata yasa a gama da duniya lafiya", "Amin" dukkansu suka amsa, dariya ma ya bawa Abui Dan kawai yace zai iya tafiya da matarsa shine duka wannan addu'a haka, yace "Kaje ka dubo Hauwa?", gaban Batuul sai da ya fad'i jin sunan Ajiddeh, take expression d'in fuskan Abu ya canja jin sunan Ajiddeh, har idonshi ya fara canja launi yace "Abui am not ready, bana so inyi taking decision out of anger, kar inyi abinda we  all will regret", kai kawai Abui ya gyad'a mishi alamar he understands him, Batuul dai gaba d'aya kanta ya gama d'aurewa, mey zaiyiwa Ajiddeh da har zaisa suyi regretting, kuma meye sa tunda ta farka bata gidan, tana sak'e sak'enta har suka gama cin abincinsu, Da yamma aka dawo dasu Mum asibiti aka wuce dasu kai tsaye, ita Jainaba, sai wata mata da Dad d'in bai Santa ba, babu wanda baiji mugun ciwo ba cikinsu, Da ya dawo gida suka taho tareda Ajiddeh, in banda kuka babu abinda Ajiddeh keyi, ta rasa bakin cewa komai, Zainab ma sai da Daddy ya qirata snn ta taho, itama kukan ta saka ganin yanayinsu, Dad baice musu komi ba ya tafi wajen Doctor, Doctor yayiwa Dad bayanin cewa Mum ta sami raunika hannu da k'afa da kuma spine d'inta, babu ita babu tafiya a yanzu, d'ayar matar kuma Brain d'inta ya tab'u amma suna fata in ta farfad'o a samu a sake dubawa, sai Jainba ita kuma hannayenta ne kawai suka ji raunin sai kuma kafar ta da sai an yanke sbd ya lalace, tunda doctor ya fara magana Dad ke danne zuciyarshi yana addu'a sbd wani irin abu da yakeji yana taso mishi, saida likita ya gama bayani yayi mishi godiya ya fita, gida ya wuce kai tsaye dan bayajin zai iya komawa cikin d'akin, har ya isa gida yana tunanin abinda ya kai Zuwaira Illorin. 💖💝BATUUL💖💝 Da 94 By Phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Da yamma suna zaune garden itada da Farida da take ta mata iya shege kan ta k'ara k'iba, bata kulata ba dan Yaa Abu ya fad'a mata babu wani k'iba da ta k'ara, gaba d'aya hankalinta yana kan fruit Bump game d'in da take bugawa, Juyo mata da Macbook d'in dake kan cinyarta Farida tayi tace "Kinga nacewa Affan in zaizo ya taho min da wannan cradle d'in, its cute ai ko?", sai a sannan ta d'ago ta kalli cradle mai kyau dashi snn ta kalli Farida with confusion fuskarta tace "Huh?, cradle nefa, kwana zaki koma yi kai?", Farida ta d'ago ta dubeta tayi mata kallon you ain't okay ta girgiza kai snn tace "Babynmu na siyawa, the newest niece/ Nephew, kinga fa unisex nace ma tunda bansan mey zaki haifa ba, Dan Allah kicewa Yaa Abu kuje a duba cuz in san irin kayan da zan riqa keeping", ta fad'a with soo much excitement a muryarta, Sai lokacin Batuul ta fahimci ina ta dosa ta tsuke fuska tace "Ni nace miki zan haihu toh?", Farida ta kyalkyale da wani irin dariya da ya bawa Batuul haushi tace "Wake jiran sai kin fad'a mishi, tun da naje wajenki UK na gano, shiru kawai nayi maki ina kallonki kawai", Jin ambaton sunan UK ta tuna da Ajiddeh, jiki a sanyaye tace "tun yaushe ne bata nan, ni tunda naji sauk'i ban ganta ba", ba tareda ta dubeta ba Farida tace "Wa kenan?", a hankali Batuul ta furta Ajiddeh, kafad'a Farida ta d'aga tace "Oho, da yake she is not my cup of slush", Batuul ta dawo kusa da Farida tana k'ok'arin rufe System d'in tace "Riri mana, dagaske fa nake, she was nice to me da banida lafiya, har Addu'a fa tayimin", wani irin kallo Farida tayi mata, kallon lallai you are not okay, har ta bud'e baki zatayi magana ta fasa, ta sake janyo System d'in zata bud'e, Batuul tayi maza ta riqe tace "dagaske nake I could remember everything har da kukanta, she insisted mu dawo fa ayi min magani a nan, amma tunda na warke ban ganta ba, kuma d'azu naji Abu na cewa bayason ganinta cuz bayason taking decision out of anger, mey ya sameta Dan Allah?", Sai yanzu Farida ta tabbatar da Lallai Batuul batasan mey ke faruwa, kuma baza taji daga bakinta ba, gyara zamanta tayi tana fuskantar Batuul da kyau kamar wacce zatayi wani maganan kirki tace "Kina jina dai koh?", Batuul ma ta gyara zama dan ta fad'a mata, Farida taci gaba "Naga kin fi kusa da Yaaa Abu, just ask him about her, baza kiji daga bakina ba", had'e rai Batuul tayi tareda kaiwa Faridar duka a kafad'a tace "You are a jerk Allah, shine kika b'atamin lokaci kamar wacce zata fad'i abin kirki", mtewww taja tsaki daidai lokacin wayanta ya hau ringing, dubawa taga unknown number ne, har baza ta d'auka sai kuma ta fasa tayi recieving tasa a kune, cikin masculine voice d'inshi taji yace "Are you ready?", lumshe ido tayi ta bud'e tareda cire wayar  ta sake kallon screen d'in da kyau snn ta maida kunne tace "Hello?", yace "Glitter you there?", a hankali cikin siririyar murya tace "Inace fa sai dare zamu tafi kuma", yace "Nah get ready yanzu zanzo mu tafi kinji?", tace "Okay", yace "Yeah sai na k'araso, take care", a hankali ta lumshe ido, this is the first time Yaaa Abu ya k'irata, ko ina ya samu number d'inta, ko dai dama yana dashi ne, kauda tunanin tayi ta d'ago taga Farida ta kafeta da ido tana wani irin smirk tace "And you will later tell me kefa baki iya soyayya ba, dubi yadda kika wani kashe murya kina magana, badan shegen son jin gulmana ba da bazanji ma mey kike cewa ba", Harararta Batuul tayi ta mik'e tace "You have a problem these days kin sani ko, ni matsa min in tafi, kya ji dashi, I pity best friend", ta fad'a tana mik'ewa zata bar wajen, da sauri ta ajiye Macbook d'in hannunta ta biyota tana dariya tace "exactly why he can't do with me", tsaki Batuul taja taci gaba da tafiya abinta Farida na biye da ita tana ta zuba, ko da suka shigo a parlour suka tarar da Ammah, Ammah tace "Bitti badai baki shirya ba kam, inace da yamma yace zaku fita", sauk'ar da kai tayi k'asa tace "Shine nazo in shirya yanzu Ammah", Ammah tace "Toh shikenan" Farida tace "Ohhh ashe fita zakiyi shine kike shamin k'anshi dan kada in biki, toh nikam sai naje bara inje in shirya nima", dariya kawai Batuul tayi dan tasan in ta biyewa Farida sai ta hanata shiryawar ma gaba d'aya, tana shiga d'aki ta fad'a toilet tayi wanka snn ta fito, akwatin da Farida ta shigo dashi d'azu ta bud'e ta ciro wani swiss voile purple had'e da underwears suma purple, saida ta shafa mai snn ta saka kayan, turarukanshi dake gaban vanity table d'in ta fesa wad'anda taji sun kwanta mata, Farida na zaune parlour suna hira da Ammah wayarta tayi ringing, da sauri ta d'aga ganin Yaa Abu rubuce jiki takai kunnenta tace "Hello Yaa Abu ina wuni", bai amsa ba sai cewa da yayi "Kina jina?", ta kad'a kai tareda cewa "Ehhh", yace "Har ta gama shiryawan ne?", sarai tasan wacce yake nufi amma ta dake tace "waye kenen?", yace "I mean Fatima, ta shirya ne?", daga yadda yayi maganan tana jiyo how stern muryarshi take, murmushi tayi tace "Yeah ta dai hau sama shiryawa, inaga ta gama by now", yace "ita kad'ai ce saman nan ko?", kamin tayi magana yace "Anyway, kina jina koh?, inaso ne ki taimaka mata ki shiryamin ita yadda duk wannan ramar da tayi zata koma, I mean she should look all presentable, har wannan make up d'in naku na mata if possible kiyi mata", murmushi kawai takeyi tace "Tohh Yaa Abu, lemme check on her rn", ya sauk'e ajiyar zuciya yace "Okay Plss do, Thank you" cikeda da murna yau Yaa Abu yace mata Thank you ta ajiye wayan ta dubi Ammah tace "Wai Yaa Abu ne yace in taimaka wa Batuul ta shirya", batareda ta kalleta ba Ammah tace "Toh shine kike zaune?", mik'ewa tayi ta haura sama ta tura k'ofar d'akin da tasan Batuul na ciki, gaban vanity table ta tarar da ita zaune tana faman taje dogon gashinta da yake gajiya mata da hannu, hannu tasa ta anshi comb d'in tana cewa "Kedai har yanzu baza ki fara retouching ba", bakinta ta tsuke dan in da abinda ta tsana bai wuce a tab'a mata gashi ba ace za ayi mata kitso ko taji amma da yake yanzu yana bata wahala babu yadda ta iya, dariya Farida tayi tace "Hey chill!, bafa ni na kar zomon ba, rataya aka bani, start retouching zaki bar k'uncin nan da kikeyi yanzu", d'an tsaki taja tace "Nikam kiyi shiru ki tajemin", haka ta gama taje mata tayi bun dashi ta baya snn tacewa Batuul "ina zuwa", ta fita daga d'akin bata dad'e ba ta dawo riqe da Makeup kit kan madubin ta fara jera komai, Batuul ta dubeta da kyau tace "You also going", Farida ta kad'a kai tace "Nah, ke zanyi wa d'an touch up", Batuul ta yatsina fuska tace "dayake nace miki inason yi koh", Farida tace "Nifa am trying to help, babu ruwana in kukaje yaga y'anmata masu kyau wajen, kuma kinsan dukkansu y'an matan nan yanzu abinda sukeyi kenan ko", da kyau Batuul ke kallon Farida gabanta na fad'uwa jin abinda take cewa, gyara zama tayi kan stool d'in tace "Toh kiyi min", murmushi kawai Farida tayi tazo ta fara shafe shafe fuskar Batuul, d'an touch up tayi mata da ya k'ara fito da kyan Batuul d'in snn ta fita, bata jima da Fita ba taji an turo k'ofar d'akin, batareda ta damu ta juyo taga waye ba taci gaba da rataya towel d'in da take ratayawa, shikam tun daga corridor yakejin k'anshin turaruka masu dad'i, ido ya lumshe ya bud'e ganinta tsaye tana k'ok'arin rataye towel, a hankali ya shigo d'akin ya rungumeta ta baya tareda sauk'e ajiyar Zuciya, itama abinda tayi kenan jin k'anshin shi da d'umi jikinshi, ajiye towel d'in tayi dan yana neman fad'uwa jin d'umin lips d'inshi a wuyarta tana jin sauk'ar numfashinshi, a hankali ya juyo da ita tana fuskantarshi idonshi na zagaye ko wane angle d'in fuskan, hab'arta ya d'ago yace "Kinyi kyau Glitter", duk da rashin haskenta zaka iya ganin blush d'in da Farida ta shafa mata na dad'a turuwa, a hankali tace "Thank you, kaima ai kayi kyau", hannu yasa ya lakuto purple ombre lipstick d'in da aka shafa mata yana yatsina fuska yace "wa yace mata ta shafa miki wannan?, I can't take wani ya kallemin keh har idonshi ya kai kan lips d'inki", kamin tace wani abu ya sunkuya ya had'e bakinsu waje d'aya, sai da ya tabbatar ya tsotse dukan lipstick snn ya saketa yana maida numfashi raurau tayi da ido tace "ka b'ata min fa kenan", ya rik'o hannunta yace "Na gyara dai, ni kad'ai za ayiwa irin wannan kwalliya ba in zamu fita ba", agogon shi k'irar Hublot ya duba yace "Glitter muje, its getting late", ya mik'o mata mayafinta dake ajiye kan gadon, sauka sukayi k'asa har lokacin Ammah na zaune falo, tana ganin Batuul tace "Masha Allah Bitti, ya babu d'an kunne kuma bare sarqa, Farida maza jeki ki d'auko mata d'akina", Da hanzari Farida ta tashi taje ta d'auko wani gold chain da earring d'insu da agogo, ita ta taimaka mata ta saka Ammah tace "Masha Allah, yayi daidai yanzu, ki gaida min su in kinje Bitti", ta amsa da toh dukda batasan inda zasun ba, ta kalli Farida tace "Muje mana?", Farida tace "Wa zai biku?, keda ma bakisan inda zaku ba, marairaice mata tayi tace "I have assignment kuma gobe zanyi submitting, kuje kawai sai kun dawo", juyawa kawai tayi ta bi bayan Abu, shi ya bud'e mata k'ofar mota snn ya zagaya side d'inshi ya shiga ya tada motar, hira sosai ya dinga yi mata yana driving, har mamakinshi takeyi yadda yake ta magana, gidan Yaa Mera suka fara Zuwa, basu wani jima ba suka yi mata sallama suka tafi tana ta saka musu albarka snn suakje gidan Yayan Abui dake unguwarsu d'aya da Yaa Meran, sai gidan Aunty Amna, sosai taji dad'in ganinsu ta bawa Batuul abubuwa dayawa tareda bayanin yadda zatayi amfani dasu, bayan sun bar gidan Aunty Amnah taga sunyi hanyan gidansu, with so much excitement ta juyo ta dubeshi, ido d'aya ya kashe mata yace "Surprise", cikeda murna ta kamo hannunshi d'aya tayi kissing tace "I love you", murmuahi yayi this time ya kai hannuta bakinshi yayi kissing yace "I love you too Glitter", a hankali tace "Thank you", har tausayi ta bashi ganin murnar dake fuskanta yace "Shhh anything for you", daidai bakin gate d'in gidansu Batuul wayarshi tayi ringing, dubawa yayi ganin mai k'iran nashi take expression d'in dake fuskarshi ta b'ace, Batuul dake ta murna bata ma lura da yanayinshi ba, yana parking ta bud'e k'ofa da gudu ta fita, bayanta yabi ya had'e rai yana mata wani kallo tareda d'aura hannunshi kan cikinta yace "Gudun mey kikeyi?", rau rau tayi da ido tace "Am just happy ne zan ga Aunty fa", yace "Na fad'a miki bana son kina tsalle, my Baby", ya fad'a yana kallon idonta,sai lokacin ta fahimci inda maganar ta dosa, ita mantwa ma takeyi da wani halitta cikinta, puppy eyes tayi mishi tace "Tohh, toh ka sakeni sai in shiga gida", bai saketa ba saida ya koma ya rufe k'ofar motan snn ya kamata suka shiga ciki a tare, suna shiga ya saketa, tana son gudu tana tsoron fad'anshi , Sunan Aunty ta shiga k'ira, jawota yayi yace "Glitter meye haka kikeyi?, zamu koma tunda haka zaki rik'ayi", kai ta girgiza mishi tace "Na daina fa", Daidai nan Aunty ta fito side d'in Baba, da gudu taje ta rungumeta ta fashe da kuka, Aunty da mamaki ya cikata ta d'ago tana kallonta tace "Aa a, Batuul daga ina haka ke Kam harda kuka?", sake kwanciya tayi jikin Aunty tace "Aunty I Missed you, 4months ban ganki ba fa", dariya ta bawa Aunty, itama tayi kewar y'ar tata sosai tace "Keda yanzu kin girma, ba kullum zaki na ganina ba dama", Ta shagwab'e fuska tace "nikam wane girma nayi?, am still your kid Batuul", Aunty tace "naji toh, keda waye haka da magrib d'inna?", juyawa tayi ta kalli inda Abu ke tsayawa ya zuba musu idanu yana kallon bond da affection d'in dake tsakaninsu yana murmushi", Aunty ta fad'a murmushinta tace "Aliyu ashe tare kuke tafe shine ta k'yaleka a tsaye, shigo ka zauna", bai ce komai ba ya k'arasa shigowa ya zauna snn suka gaisa da shi, Aunty ta juya zata tafi Batuul ta bita a baya, text ne ya shigo wayan Abun ya duba yaga, bai damu da ya karanta ba sabida ko ganin maishi bayason yi bare kuma har ya kai ga karanta text d'in, yana gogewa k'ira ya sake shigowa wayan, bai d'auka ba ya ajiye wayar gefenshi, Batuul da ta fito riqe da tray ta kawo mishi ruwa ta tsiyaya mishi cikin tumbler ta mik'a mishi, yayi mata murmushinshi mai kyau ya karb'a yana sha, wayarshi ce ta sake ringing, duban wayan tayi gabanta na fad'uwa ganin sunan da ta gani rubuce, wani irin curiosity ke fizgarta da yasata d'aukar wayar tayi receiving ta kai kunne, muryar Ajiddeh taji tana cewa "Aliyu Dan girman Allah badan halayena ba ka taimaka kazo Mum tayi accident ko sau d'aya ka ganta ta nemi yafiyarka", ido ta lumshe hawaye na taruwa idonta lokaci daya jikinta yayi sanyi, yana sauk'e cup d'in yaga wayarshi kunnen Batuul, da sauri ya karb'e wayan yana kallonta yace "Do you have to?", ido ta rintse hawayen da suka taru suna zubowa. 💖💝BATUUL💖💝 95 By Phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Da mamaki yake kallonta ganin hawaye idonta, wayar ya d'auka ya duba da wa sukayi magana, kallonta yayi snn ya sake duban wayan yace "Glitter mey tace miki?", ido ta lumshe ta bud'e hawayen na sirarowa, da sauri ya sauk'o daga kan kujerar yana fad'in "Subhanallah, Glitter talk to me mey tace miki?, kar kiji tsoro tell me all", "Ina take?", abinda kawai ta iya fad'a mishi kenan, so yake kawai yaji abinda Ajiddeh ta fad'awa Batuul a waya, ganin baza ta fad'a mishi ba yasa shi d'aukan wayan zai k'irata, a hankali tana share hawayenta tace "She said Mum had an accident tana son ganinka", ajiyar zuciya ya sauk'e jin abinda tace snn ya juyo yana kallonta yace "Toh kukan mey kikeyi Glitter?", "kaje ka duba Mum d'in, in ka dawo sai mu tafi", He is not ready to tell her duk wani ciwo da tayi da sa hannun Ajiddeh ba, yana jiran right time ne ya fad'a mata amma yanzu he is not ready, hannunta ya kamo ya riqe yace  "shine kike zubar min da precious hawayenki bayan nace banaso?", ya fad'a yana kawar da maganan, kallonshi ta tsaya yi ganin ta fad'a mishi Mum d'in Ajiddeh tayi accident kuma baice komai ba, hannunta ta karb'a daga wajenshi tace "Yaa Abu nace fa Mum na Ajiddeh fa batada lafiya", idonshi ya d'aura cikin nata yace "Naji, mey zanje inyi mata Glitter?, I don't wanna see her, I don't wanna talk to her", ya fad'a muryarshi becoming stern,da tsoro da mamaki sosai take kallonshi jin abinda ke fitowa daga bakinshi, anya wannan Yaa Abu ne da ta Sani har yake cewa bayason ganin Ajiddeh, koma meye tsakaninsu dai yaje duba Mummy tunda itace tayi accident d'in ba Ajiddeh da bayaso ba, ya bud'e baki kenan zaiyi magana ganin mood d'inta ya canza yaji takun tafiya, da sauri ya kai hannu fuskar ya shafe ragowar hawayen dake shirin zubowa yace "Kina so Aunty ta ganki kina kuka tace nayi miki wani abun ko?", itama hannu takai ta shafe hawayen, tashi yayi ya koma kan kujerar da ke Zaune, Aunty ta k'araso parlour zatayi Side d'in Baba ta ganshi zaune tace "dama kana nan Ashe, inace ma ka juya, shiyasa na jiki shiru kenan", duk kunya ya kamata suna had'a ido da Abu ta langab'ar da kai, yayi murmushi tareda shafa gashin kanshi yace "Yanzu nake shirin fita zan barta inje in dawo anjima", Aunty tace "Toh shikenan sai ka dawon", daga haka tayi wucewarta, pie d'in da ya fara ci ya k'arasa snn ya ajiye sauran tareda mik'ewa yace "Glitter I will b going, 9 zan dawo sai mu tafi, yayi miki ko?", kai kawai ta gyad'a mishi ya dawo ya matso gabanta ya d'aga hab'arta yace "ki kalleni kimin magana, yayi miki?", a hankali tace "Ehhh", yayi murmushi yace "that's my baby, muje ki rakani", tare suka jera har suka fita waje, saida ya shiga mota snn yace "ki koma gida I will b back shortly", ya shafi gefen fuskarta, yana ganinta har ta shige gida snn ya sauk'e ajiyar zuciya ya koma cikin mota ya d'auki wayarshi daketa ringing da ya maida silent d'agawa yayi yace "Kai shikenan dan bakada family sai kayi ta damun mutane", tsaki Massa yaja yace "Kai d'an duniya nefa, da anyi magana kace kai Family, gashi family naka ke damuna ai, kaifa d'an iska ne wlhy, yarinya nata k'iranka kaqi d'aga waya", girarshi ya had'e ya dubi hanyar da Batuul tabi yace "a ina ka gantan har take damun naka?", yace "Am in Tripods, let's meet there", juya motar yayi ya fita daga gidan, a tripods suka had'u, Massa yayi musu ordering abin sha snn yace "Ajiddeh, she called me like thrice yau wai tana son ganinka banma gane whole abin ba but tace tana k'iranka you weren't picking", har saida yayi shiru Abu ya dubeshi yace "is this why am here?", harara Massa ya sakar mishi yace "nifa wulakanci ne bana so, in gama maka bayani kana tambayata dalilinka na zama a nan?", Abu ya lumshe ido har sai da Massa yayi shiru ya bud'e ido yace "Mustapha kasan ni yanzu tsoro take bani, seeing her infuriates me", kallonshi Massa keyi na lallai kaima the saying goes with you, maza bakuda tabbas yace "Dan kayi amarya shine har zaka manta da matarka, I wasn't expecting this from you Aliyu, ka bani mamaki, har tsoronta kakeji sbd kana da wata matar kuma kana sonta ko, tana ma inane haka take ta nemanka bata samu d'in?", Abu da ya fahimce sam Massa bai gane mai yake nufi ba yace "kasan rashin lafiyan nan da Fatima tayi was all because of her?, su suka kwantar da yarinyar mutane sukayi ta bata wahala, they wanted killing her Mustapha, the mere thought of it weakens me inji na tsanesu gaba d'ayansu, am sure setting eyes on her again bazai mana da dad'i ba daga har ita shiyasa bana son ganinta, Massa da gaba d'aya kanshi yayi nauyi jin abinda Abu yake fad'i yace "For real?, Innalillahi wa inna illaihi raji'un×2, badai akan ka akayi duka wannan abin ba?" Abu ya sauk'e ajiyar zuciya yace "Har yau ni bansan dalilinsu na aikata hakan ba, all I know is itada da Mamanta da Aunty sukayi conspiring to end Batuul's life, su sukayi causing mata duka wannan pain d'in sbd rashin tausayi, kuma har yau yarinyar bata sani ba", Massa yace "Subhanallah, amma mata ma dai wani sa'in matsala ne dasu, what on earth could make you try such shit, akan so koko meye?", Abu ya d'age kafad'a tareda yarfe hannayenshi duka biyun yace "Ita ta sani yanzu, kai kafi kowa sanin yanda nake tausayin yarinyar nan, I married her badan ina sonta ba, she was never my type of woman, it was just a compromise, son da take min yasa nake ganin yeah zan sota and maybe even change her but i was wrong, you were a witness tunda na aureta everything changed abt me, sai da nayi shekara without visiting home, my siblings, dukkkansu sunyi kewata, Abui, he needed me to be his support a business, Sadiq wasn't matured enough bare yayi handling business d'in Abui, Ammah cried because of me, tayi enduring wannan ko fad'a min batayi cewa shima bayin kaina bane asiri akamin ba, amma su bar kaina su koma kan y'ar mutane kaga that is insane, ya rigada ya zama hauka, in sonta take so inyi am trying on that, bata tab'a tambayana kud'i na rage koda single penny bane cikin abinda ta buk'ata, If she were an ideal wife da su Ammah basu sani auren Batuul ba, cuz ko ni banida ra'ayin mata biyu, but she caused it all, hakanma bai isheta ba sai sunbi y'ar mutane da jafa'i?, No am not taking it, I have no problem with her saidai inma gafara ne ta roqi wacce suka cutar, wacce sukaso halakawa", Massa ya sauk'e ajiyan zuciya mai nauyi yace "Allah ya rufa asiri, yanzu hakan tana ina?", "I don't know, gidansu ta tafi maybe", wayar Massa tayi message tone, dubawa yayi snn ya mik'awa Abu wayar, karb'a yayi ya duba msg d'in snn yace "Da take damuwa da zuwana in naje zan bawa mahaifiyar tata lafiya ne?, Whatever but I know she is paying for her crimes, alhakin baiwar Allah nan ba barinsu zai yi ba su zauna lafiya", Cikin gida ta koma kai tsaye ta wuce kitchen tana kokarin mance duk abinda ta gama ji yamzun, Freezer ta bud'e ta ciro wani babban rubber assorted ne soye ciki duk sunyi block, plate ta d'auka ta d'ibi kad'an ta saka ciki snn ta saka a micro wave zatayi warming, kan freezer ta koma ta zauna bayan ta ciro ta d'auki fork tana cin kayan cikin, ta Bawa dake wanke fruits tace "Yaa Batuul naga baki nemi yaji ba kuma akwai su iri iri", Batuul ta d'an yatsina fuska tace "Aunty ta Bawa kinsan a can bamuyi wani aikin nama ba, masallaci kawai mukaje muka dawo, ya dai yi mana yanka", Ta bawa ta riqe baki tace "kai haba, toh ina aka kai ragunan?", Batuul ta tab'e baki tace "Ehhhm, Sadaka akeyi dashi kasashen mabuk'ata", "Ahhh lallai an gaisheku, ai koda za ayi sadaka ba duka ba, nan gaba kice a bar miki naki ko nan kya turo na gyara miki in aikace shi, wa yace duka ake sadakar?", Batuul tayi dariya tace "Toh shikenan", ta dubi Janet dake ta faman goge plates d'in da ta wanke tace "Janet miqo min yajin na tafarnuwa, da sauri ta kawo mata shi ta koma bakin aikinta, tana zaune tana ci Aunty ta dawo kitchen d'in taga Batuul zaune kan freezer tana take kayan ciki tace "har ya tafi?", kai ta gyad'a tareda amsawa bayan ta cinye wanda yake bakinta, Aunty tace "in kin gama ki sameni sama", Aunty bata gama bama ta sauk'o kan freezer tana ajiye plate d'in ta biyo bayan Aunty, sosai sukayi having mother daughter time d'insu, ta bata addu'o'i da shawarwari masu kyau, tace ta shiga tayi wanka bayan ta had'a mata ruwan da sinadarai masu yawa, bayan ta fito ta taga wata da ganinta y'ar Tchad ce zaune, gyaran jiki Aunty tasa matar nan tayiwa Batuul tayi mata, cikin lokaci kad'an Batuul ta canja sai shek'i takeyi, saida aka gama suka sauk'o dining cin abinci, sai lokacin taga Baba da y'an k'annenta, da murna shima ta rungumeshi, koda zata fara mishi shagwab'a wayo yayi mata yace ai ta girma yanzu sai dai su Yusra suyi, haka suka zauna cin abinci murna fal ranta, har wani emotionally ta rik'a ji a ranta, bayan sun gama cin abinci mai gyaran nan kuma. tayi mata kitso, k'arfe goma daidai ya dawo, tun da ya shigo gidan idonshi ke kanta, babu abinda yake furtawa cikin ranshi sai "Subhanallah, Masha Allah cikin ranshi", har ya k'araso cikin parlour, da murmushinta mai kyau ta juyo ta dubeshi, a nutse suka gaisa da Baba ya sake gaida Aunty, yaran ma dukkansu suka gaisheshi, a nan yake sanar da Baba gobe sha d'aya jirginsu zai tashi, Albarka Baba yayi ta saka musu tareda Nasihohi, Aunty ta cikata da abubuwa dayawa da wasu ma bata san amfaninsu ba, kamar kar ta tafi haka tayi sallama dasu suka wuce, yana barin compound d'in gidan yayi parking gefen titi ya ciro wayarshi yana haskata yace "Glitter kinyi kyau da yawa", murmushi tayi tace "Aunty tasa aka min duka, kaga har kitso anyi min", ta cire d'an kwalinta tareda nuna mishi sabon kitson nata, gaba d'aya motar k'anshinta mai dad'i yakeyi, hannu yakai yana shafa kitson yana lumshe ido a hankali ya dunga furta wasu addu'o'i da shikad'i yakeji snn ya bud'e idon yace "Glitter plss ki tayani addu'a ki haifa min Baby girl mai kama dake", tayi dariya tace "nikam baby boy nakeso, kaga I want to name him after this fav name" hararanta yayi yace "wane sunane favorite d'in naki?", batareda tunanin komai ba tace "I have loved the name tun ina yarinya, I wanted marrying someone with such a name ko kuma in haifi mai sunan, I just have a thing for the name ALIYU", ta fad'a kanta tsaye, ajiyar zuciya ya sauk'e jin sunan da ta ambata, sai da ta ambata ta tuna mey ya fito daga bakinta, ta tun. a shima fa sunanshi kenan, ido ta rintse tana dariya, hannu yasa yana cupping fuskarta yace "Every Aliyu have his own Fatima, it happened you are mine, I can't imagine life without you now, I love you", itama tayi murmushi tace "I love you too", da haka yaja mota sukayi gida, koda suka isa har Ammah tasa an gama shirya musu kaya, d'an hira suka tab'a snn sukayi sama suka kwanta, washe gari tunda suka tashi da asuba basu koma sun kwanta ba har suka gama shirin tafiya, 9 Sadiq ya fita dasu airport, Batuul dai sai kallon ikon Allah takeyi jin babu mai zancen Ajiddeh, Sadiq na dropping d'insu bai jima ba ya juyo, duk motsin da zatayi idonshi yana kanta, candy floss ta hango wani d'an yaro naci, a hankali ta juyo ta dubeshi tace "Yaa Abu inaso", ya kalleta yaga inda take kallo yace "we should go nd get", tayi raurau da fuska tace "Nifa na gaji, ka samomin kai zan jiraka a nan, in na tashi zan gaji dayawa", yayi murmushi tareda lakuce mata hanci yace "okay take care, bara inje duty free nan in duba", har ya juya yaji tace "da spicy French fries plss", murmushi yayi mata kawai ya tafi, baifi five minutes da tafiya ba ya dawo, baisan lokacin da murmushi ya k'wace mishi ba ganinta zaune k'ark'ashin wasu manan rose Petals a wani perfume stall, sosai tayi kyau sbd kayan dake jikinta suma pink ne, abubuwan dake hannunshi ya ajiye ya ciro wayarshi daga aljihu yayi snapping d'inta pictures batareda ta lura ba, har ya isa wajenta yana murmushi, gabanta ya tsuguna tareda mik'a mata floss d'in, da wide smile ta karb'a tayi mishi mouthing "Thank you", kai ya girgiza mata yana nuna mata cheeks d'inshi, wara ido tayi tana blushing tana girgiza mishi kai, baza ta iya ba, kunyan shi duk ya gama cikata, ganin taqi yi ya zumb'uro mishi bakinshi ya miqe zai bar wajen, hannu tasa ta riqoshi, saida yayi murmushi snn ya juyo yana kallonta, a hankali tace "da mutane anan, in munje gida pls", hannunshi zai sake karb'a tace "toh close your eyes", lumshe ido yayi a hankali ta dawo gabanshi, d'age tayi sbd tsawonshi, ji tayi ya d'aura hannu waist d'inta ya d'agata sama, pecking kumatunshi duka biyu snn ta maida kanta ta sinnewa jikinshi, tafi taji duka wajen ya d'auka, tsabar kunya kasa d'agowa tayi, tana jikinshi ya mayar dasu wajensu sukayi zamansu, 11 daidai sukayi boarding jirgi, in banda bacci babu abinda takeyi, lokaci lokaci take tashi, murmushi kawai zai mata ko kuma ya tambayeta in tana da buk'atar wani abin, har suka isa UK [12/16, 12:14 AM] ‪+234 808 135 1434‬: 💖💝BATUUL💖💝 96 By Phartiemarhk Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Hawayen da kanshi nema take ya zubo ko zataji dad'i ta rasashi, ido ta k'urawa Mummy dake kwance duk jikinta anyi bandaging gwanin tausayi, tunda taga yaqi d'aga k'iranta tasan babu yadda za ayi yazo, tunanin Abutturab yasa ta jin silalowar hawayen da take ta neman zubowarsu ko zata samu y'ar nutsuwa, amma Sam abun ba haka yake ba, saima rad'ad'i da ya k'arama zuciyarta, tun da Dad ya fita bai sake shigowa ba har yau, a hankali taga Mum na k'ok'arin bud'e ido, da kyar ta bud'esu tana k'arewa d'akin kallo, kan Jainaba dake kwance ta d'aya b'arin idonta ya fad'a, hawayene kawai ya dinga silalo mata, a hankali ta maida dubanta ga Ajiddeh dake zaune, rintse ido Ajiddeh tayi ta bud'e snn tace "Mum wani irin fitina ne wannan nake gani a rayuwa?, duk wata masifa ta rayuwa na gama ganinta, Mum kece silar duk wani tashin hankali da nake ciki yanxu, tun ina k'arama tun Dad baiyi arzik'i ba, tun kamin inyi hankali na fahimci duk abinda kike so sai kin sameshi ko da ya kaucewa shari'a, tun bamuda arziki kike cewa mucewa k'awayenmu mufa y'ay'an wane da wanene, tun ban fahimta ba har na gano ma'anar inda kika dosa muka fara biye miki, babu yanda Dad bai nuna k'ok'arisnhi kanmu ba dan mu gyara amma kan ya faskara saboda kullum tare dake muke, zamanmu dake yafi yawa dole mu d'au ak'idarki, Mum kece uwa ta farko da na fara ganin bata tab'a yiwa y'ay'anta fad'a kan abinda babu kyau ba, baki tab'a tsawatar mana akan laifinmu ba, Dad ne kad'ai ke mana fad'a, ana haka Dad yazo ya samu arziki, d'an time d'inshi da muke samu yazo ya zama bama samu, duk wani jin dad'in rayuwa mun samu saboda irin son da yakeyi mana, amma ko shi Dad naga ba time d'inshi kikeda ba sai abinda yake dashi, kin koya mana son abin duniya da muka d'auka muka girma da, nima nasa a raina zanso mutum amma saboda kud'inshi", tayi shiru tana shesheka ta kalli Mummy da ta rintse ido tana kuka, taci gaba, "Allah mai yi yadda yaso da bayinshi ya had'ani da Aliyu da kallo na d'aya naji duk duniyar nan babu wanda nakeso kamar shi, babu possible ways d'in da ban bi dan yasoni amma ko zamana baisan da ba, a haka na tareki da zancen, tashin farko Mum cewa kikayi zamuyi maganinshi, haka mukayi ta bin bokaye, duk basuyi tasiri akanshi ba har saida na samu nayi plan d'in da ya bigeni da mota, ni nasan Aliyu bai tab'a sona ba, amma saboda son da nake mishi yasa bazan iya barinshi ba, ya aureni bawai dan yana so ba, nasan ya rasa abin yine saboda matsa mishi da akayi a gida, na samu fatana ya cika, my dream came true na zama matar Aliyu amma son zuciya da tsoron rasashi suka rinjayeni, babu abinda na tashi saka mishi da sai rabashi da nayi da iyayenshi da danginshi har tsawon shekara, Allah da yake shi ba azzalumin bawanshi bane ya saka mishi, iyayenshi sanin da sukayi ba haka kawai zaiyi haka ba, ba zasu zauna suna gani d'ansu ya halaka ba suka nema mishi aure", dariyan takaici ta saki tana girgiza kai taci gaba tace "Dole ma Allah ma yayi mishi sakayya ta alheri, mey na tab'a yi mishi na zamantakewar aure?, ko tsinke ban tab'a dagawa gidana ba bare inje ga zancen girki, a haka ya dawomin da yarinyar gida, tun had'uwata ta farko hankalina bai kwanta da ita ba, dukda kullum ina admiring duk wani abu nata, nutsuwa, kunya, k'awaici amma hakan baisani ganin gaskiya ba sabida son zuciya, Baiwar Allah jikina dama yana bani da wani abu a tattare da ita mai girma, amma son zuciyata yasa na cutar da ita, da na tab'a sanin akwai ranan da zan bud'i ido inji Aliyu na korata kan yarinyar nan da ko kallon banza ban jifarta dashi bare mugun kaba'iri, gashi a dalilin cutarta da nayi yasa yace ko kallona bai sakeyi, am not putting all the blame on you Mum, I have a commision a ciki, in kinyi abu mara ai nima nasan daidai zan iya gyarawa, shiyasa Allah ya bani hankali amma naqi aiki dashi,  gashi we are accounting for all our deeds, we are reaping what we sow, Mum ni bansan mey kikaje yi har illorin ba amma nasan ba alheri bane ya kaiki, gashi nan Allah yana nuna mana ishararsa, Na kirashi yazo mu nemi yafiyarsu Mum yaqi d'agawa, ko yafiyarshi ne yazo in roqa", Sai lokacin Mum ta bud'e idonta da suka kad'a da k'yar tace "Hauwa duk wani abu da nayi dan Ku nayishi, babu wanda nakeso da k'auna duk duniyan nan sai ku da Allah ya mallakamin, banida kowa sai y'ar uwata Jainaba, mun taso cikin k'unci nida Jainaba da nayiwa kaina alk'awarin y'ay'ana bazasu fuskanta ba, ba haka naso rayuwa ta juya mana ba, kuyi hakuri Ajiddeh, nafiku jin ciwon duk abin nan da yake faruwa, tafiyan nan da nayi duk dan nema muku farin ciki na fita yinshi, farin cikinku shine nawa, ku yafemin, ta fashe da wani sabon kukan Suna sauk'a cab ya tara suka wuce d'ayan gidanshi, ko da sukaje Bacci Batuul keyi, ita kawai ya d'auka a hannu cak ya shiga cikin gida ya kwantar snn ya dawo ya kwashi Luggages d'insu ya shigar, saida ya fara wanka ya rama sallolin da ake binshi kanshi kamin ya dawo gefenta ya zauna, hannu yasa ya shafi gefen fuskarta tareda matsar da kitsonta dake kwance kan fuskartata, baccinta har dariya yake bashi, slight opportunity take jira ta rufe ido, a hankali ya furta "Glitter", kamar ma bataji ba sai juyawa da tayi tana gyara kwanciyarta, hannu yasa d'agota yace "Sleepy head tashi kiyi Sallah kici abinci", zumb'uro mishi baki tayi tana sulalewa saga jikinshi tace "um um, bacci nakeyi nikam", ya d'agata ta zauna snn ya hura mata iska a fuska yace "Its getting late Glitter, kinga kuma bakiyi Sallah ba, and my Baby needs to eat", a hankali ta bud'e ido tana mik'a, tashi yayi ya tsayar da ita taje toilet, saida tayi wanka snn tayi alwala ta fito d'aure da towel, yana zaune gaban Desktop yana danne danne, ido ya kafa mata ko k'iftawa bayayi yana roaming dukan jikinta, duk kallon da yake mata bata lura saida ta zauna zata shafa mai ta ga idonshi a kanta, zumb'uro baki tayi tace "ashe kai ke kallona shine naji towel d'ina yana so ya fad'i?", murmushi yayi yace "ai inma bai fad'i ba ni da kaina zan cireshi", dariya kawai tayi  ta janyo hijabi ta saka dan tasan zai iya cirewan shiyasa batace komai ba, saida ta idar tukunna ta tayi shafe shafenta ta saka kaya, y'ar sweat doguwar riga ta d'auka ta saka navy blue, tashi yayi ya dawo kusa da ita yana girgiza mata kai yana isa wardrobe d'inta yace "we are going out to eat, sai mu wuce hospital, kinada appointment, kayan nan basu min ba, change into something light, waje akwai sanyi", kaya ya ciro mata ya mik'a mata, karb'a tayi ta saka kayan, straight gown mara hannu  da beach kimono peach mai brown patterns snn ta d'auki brown veil ta yafa, tare suka fita ya bud'e mata front seat ta zauna ya zagaya d'aya side d'in ya shiga, asibitin ya fara zuwa suka ga doctor, bayan ya gama dubata yace itada Babyn are all fine, shawarwari ya basu sosai akan abinda ya kamata tanayi da wanda zatayi avoiding, snn yace ta fara Exercises ko da kad'an na 30 minutes ta na kuma wasu sporting activities ko indoors ne, tun suna zaune office d'in take yatsina fuska tana jin yunwa ta k'osa subar wajen taje taci abinci, suna fitowa ta marairaice mishi fuska tace "Yaa Abu", shi da kanshi yasan yunwar takeji amma, a hankali ya rik'o hannayenta cikin nashi yace "Yunwa ko?", kai ta gyad'a mishi yace "sorry yanzu zamuje kici abinci, okay?", a hankali tace "Ehen", saida ya zaunar da ita a mota snn ya zagaya ya shiga side d'inshi, driving yakeyi yana ta mata hira duk dan ya d'ebe mata damuwar yunwar da takeji, duk inda taga restaurant sai ta kalleshi taga ko zai tsaya amma sai taga ya wuce har taga sun d'auko hanyan gida, a gaban Orwell's restaurant taga ya tsaya da motar, ajiyar zuciya ta sauk'e amma ganin kamar babu kowa wajen ta dubeshi tace "kaga bafa su bud'e ba", baice komai ba sai hannunta da ya kamo sukayi bakin restaurant d'in, gaba d'aya wutan a kashe yake kamar ba a aiki a restaurant d'in, bakin k'ofan taja ta tsaya, raurau tayi da ido tace "mey zamuyi a nan?, nikam tsoro nakeji, mu tafi", hab'arta ya d'ago yana kallon idonta dake glittering yace "The trust?", idonta ta sauk'e k'asa tace "toh fa cikin duka duhu, basu bud'e bama yau naga", hannunta ya kama suka kutsa ciki, dukda duhun da wajen keda wani irin k'anshi mai dad'i ke tashi a wajen, a hankali taji ya sake mata hannu, sai nemanshi tayi ta rasa a wajen, gabantane ya shiga fad'i ta shiga lalubenshi, har idonta ya fara tara hawaye jikinta ya soma rawa, a hankali kamar wacce bataso a ji abinda take cewa tace "Yaa Abu", sau biyu tana maimaitawa taji shiru bai amsa ba, da k'yar ta iya d'aga k'afa zata juya kenan taga haske ya dallare ko ina, wani irin view take gani ko ina na hall d'in sai glittering sukeyi, komai na wajen peach ne da brown, yunwar da takeji ma gaba d'aya nemanshi tayi ta rasa, sosai wajen yayi mata kyau ba kad'an ba, daga tsakiya ta hango isle dayake da wani irin haske, Abu ta hango daga gefen isle d'in jingine yasa hannunshi cikin wandon riganshi yana mata murmushinshi mai kyau, sai lokacin ta lura da itama murmushin ne a fuskarta, a hankali ya tako inda take tsaye ya mik'o mata hannayenshi duka biyun, har ta mik'ar da nata zata kama nashi ko meye ta tuna ta zumb'uro baki ta fasa, a hankali ya juyo da fuskarta ya rik'e kunnuwanshi duka biyun yace "am sorry Glitter", idonshi kad'ai bazai barta ta iya fushi dashi ba, space d'in dake tsakaninsu ta cike tareda yin d'age ta zagaye hannayenta duka biyu ta bayanshi, shima hannayenshi yasa ya zagayeta, sun kusa minti d'aya a haka snn ta janye jikinta ta kalleshi tace "This is beautiful", hawaye ya gani tare a idonta, kai ya girgiza mata alamun kada ta bari hawayen su zubo, dariyan da tayi yasa su zubowa a tare, shima dariyan yayi yasa hannu ya goge mata duka hawayen snn yace "Anything for you", ya rik'o hannunta suka taka takan flower petals suka k'arasa isle d'in, suna zama wasu mutane da kana gani kasan waiters ne sukazo wajen, da hannu Abu yayi musu alama da su koma, kujerarshi ya matsar kusa da da nata ya warware mata veil d'in dake kanta ya maida matashi turban snn ya d'auki plate yayi serving mata abinci, da kanshi ya d'auki spoon ya d'ebi abincin ya kai mata bakinta, kallonshi kawai takeyi a ranta tana yiwa Allah godiya da ya sa Abu ya zama mijinta, a hankali ta bud'e bakinta ya saka mata, murmushi yayi mata yace "Yayi miki?", ta gyad'a mishi kai tace "sosai", sake d'ebowa yayi zai kai mata baki ta riqe cokalin ta juyar bakinshi , bai musa ba ya bud'e ta zuba mishi abincin, haka sukayi ciyar da junansu cikeda farinciki, sai suka gama cin abinci ya zagaya ta bayanta, a aljihunshi ya ciro wani diamond pendant sark'a, da kanshi ya saka mata snn ya sumkuya daidai wuyanta yayi tareda kwanto ta baya yana kissing wuyarta, ido ta lumshe tana jin d'umi da laushin lips d'inshi a wuyanta, saida ya d'ago yace "For Everything Fatima, I will forever Love you", snn ya dawo ya zauna kan kujerar, hannunta ya kama ya zaunar da ita kan cinyanshi, wani plate ya bud'e, shima zobe diamond ne ciki sai glittering yakeyi, ido ta wara ganin kyan zoben, she wasn't expecting it, ta kalleshi taga murmushi yakeyi tace "This too", girarshi dake cike ya d'aga mata tareda kamo yatsanta, tace "You are not proposing to me right, we are married", yace "You will b the girlfriend I will always want to hear from your melodious Voice, the fiance I will always dream of and the wife that will be be my responsibility to care for, my strength and weakness, a wife that will help me complete my life", bata tab'a voicing wa kowa dreams d'inta ba amma gashi Yaa Abu kamar zuciyarta ya shiga ya gano komai, wani irin murna takeyi da tunda ta dad'e batayi irinshi ba, kai kawai ta gyad'a mishi dan bakinta ya kasa bud'uwa, shima cikeda murna yayi slipping zoben cikin d'an yatsanta na dama, ya sunkuya yayi pecking zoben, batasan mey zatace mishi ba ya nuna cewa itama mai sonshi ce, ta nuna mishi cewa shine completion d'in duk wani mafarki nata da takeyi tun tana k'arama, a hankali tayi leaning ta had'e lips d'insu, yau ita tayi dominating, sosai tayi kissing d'inshi saida ta gaji dan kanta ta zama submissive ta bashi entrance, kwanciya tayi lamo a jikinshi ta maida numfashi, a hankali ta furta "I love you more", goshinta yayi pecking snn shima yace "I know and I love you more", haka suka zauna suna savouring each moments tareda nunawa junansu yadda suke son juna, sai yamma suka tashi tafiya, ganin basu shiga motarsu yasa ta tambayeshi yace "Let's walk down tunda babu nisa, I need a walk with you, zasu kawomin motar har gida", murmushi kawai tayi ta sak'ala hannunshi cikin nata suna tafiya cikeda farinciki, a hanya take tambayanshi yaushe duka ya shirya wannan Romantic Lunch d'in, yace ya dad'e yana son yayi but yafi son sai tayi confessing tana sonshi itama, ranan da tayi confessing ranan ya fara shirye shiryen komai, ta kad'a kai tana dad'a jinjina mishi tace "Orwell's fa babban restaurant ne, one of the best in Uk, you paid for it all?", dariya yayi yace "tunda na fara gina wannan gidan naga yadda ake partronising na sayi franchise d'insu, wanda yake Manchester nawa ne, so we are partners, inda kud'i anything is possible" kai ta kad'a sai yanzu ta sake sanin lallai mai kud'i ne shi tunda ya iya siyan franchise d'insu ya bud'e branch a Manchester, suna hira har suka k'arasa gida da k'afa, suna tafiya yana ta d'aukanta hotuna, farinciki fal ransu basuda wata damuwa, itace ma lokaci lokaci take tuna Ajiddeh duk sai taji babu dad'i Washe gari tunda sukayi Sallah asuba ya sata shiryawa wai doctor yace tana yin exercises, yau zasuyi ball tare, batayi baccin asuba ba ta saka bak'in jeans da jar rigar Adidas, sosai tayi kyau abinta, face cap d'in na NY ta saka, ita ta fara sauk'owa k'asa ta had'a teashi kuma ta had'a mishi coffee, bayan ya gama sha suka fita filin gidan daga baya akwai recreational fields iri iri, football pitch sukayi, dariya ya dinga mata ganin yanda take wasan har suka gama, duk ta gaji, ita ta fara wanka snn ta had'a mishi ruwa ya shiga shima yayi, kamin ya fito har ta shirya ta sauk'o kitchen ta dama mishi kunu ta had'a fish roast a oven tq kunna snn ta ciro bread d'in da zatayi musu musu toasting, snn ta koma sama bayan ta gama kamin ya dahu, zaune ta tarar dashi dagashi sai towel, taimaka mishi tayi ya shafa mai ya shirya snn suka sauk'o sukaci gaba da aikin tare, in ka gansu gwanin sha'awa basuda wata damuwa *SEVEN MONTHS LEAP.....* [12/16, 12:14 AM] ‪+234 808 135 1434‬: 💖💝BATUUL💖💝 By Phartiemarhk 97 Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* *.........SEVEN MONTHS LEAP*           Tsaye take a kitchen da yamma tana soya wainar fulawa, wayarta da tayi k'ara ta duba, ganin mai k'iran yasa ta sakin wani k'ayattacen murmushi, da wannan sunyi waya a yau kad'ai yafi sau goma sha biyar, har face time sunyi amma yanzu ma k'iranshi ke sake shigowa, hannunta ta goge da napkin snn ta d'auki wayar tasa a kunnenta, tana d'agawa taji yace "Glitter ki dena bari yayi ta ringing before you pick", murmushi tayi tace " Amore aiki nakeyi before ka bugo", ido ya wara kamar yana gabanta tareda dafa goshinshi yana tafiya yace "Ya Allah, aikin mey kikeyi?, ba nace bana so ba?", ji tayi maganarshi na kusantota, a hankali ta juya inda take jiyo muryan, k'ara ta saki tareda yar da wayan zata gudu ganinshi jingine bakin k'ofa yayi tucking hannunshi d'aya cikin aljihun wandonshi yana kallonta, da hanzari ya k'araso wajenta ya janyota jikinshi ya rungume, sosai ya matseta jikinshi sabida yanda ta tsorata, shi da kanshi saida ya tsorata ganin irin gudun da ta saka kamar wani abin zai sameta ita da cikin da ya bayyana a jikinta, a hankali ya dinga patting bayanta yana karanta mata ayatul kursiyu cikin kunne, a hankali ta dinga sauk'e ajiyar zuciya, muryarta na rawa kamar mai kuka tace "Amore you scared me", saida yaji ta nutsu snn ya rad'a mata a kunne "am sorry Glitter, I didn't mean, I just wanted surprising you", sake shigewa jikinshi tayi tace "You just did ai", dariya yayi tareda d'agota daga jikinshi "I just remembered, aikin mey kikeyi glitter?", ya tsareta da ido, sunkuyar da kai tayi tareda turo d'an bakinta, cikeda sanyin murya tace "Kagani ko wainar fulawa nake ta son inci kuma bansan ya zanyi ba, kai kuma baka nan shinefa na shiga kitchen ina dafawa, bama dayawa bane muje in nuna maka", tasan babu abinda zatayi ya b'ata mishi rai, koda zai b'aci kallonta na sashi manta komai, bare yanda take mishi magana yanzu, d'an k'aramin bakin nata ya kama yace "wayo zaki min ko, shine harda pouting min lips d'inki?" Da sauri ta girgiza mishi kai tana mirmushi tace "dagaske nake", ya mik'ar da ita shima ya mik'e yace "ba nace ki dinga bari zanyi miki ba, sai kin bawa babyna wahala?", juyowa tayi ta fuskanceshi ta tallabo fuskanshi da duka hannayenta biyu tayi pecking duka tace "ai kam bana so ka wahala, kuma fa ", ya sakar mata hararan  wasa yace "meye shi wainar fulawan da ya saki kin jin maganata?, muje in gani", raurau tayi da ido tace "Amore banqi jin maganan ka bafa?", ta fad'a tana tsaye inda take, juyawa yayi ya kamo hannunta yace "its been long I see these tears, bana son ganinsu yanzu ma", baki ta zumb'uro mishi tace "toh ka yadda ban qi jin maganan ka ba?" Ya had'e rai yace "Muje dai in gani", ya riqo hannunta suka k'arasa gaban stove d'in, yatsina fuska yayi yace "wannan Ne?", a hankali ta gyad'a mishi kai, stool ya janyo mata ta zauna akai snn ya ciri apron d'in dake rataye ya d'aura, cikin watanni ya koyi abubuwa da bai tab'a tunanin yinsu ba, sauran paste d'in da ya rage ya shiga soyawa a pan d'in, tana daga zaune tana kallonshi, tasan ko zata kwana tana cewa ya barta tayi da kanta ba yadda zai ba, a hankali ta bud'e baki tace "Amore", volume d'in stove d'in ya rage yana kallonta yana jiran jin mey zatace, kamar mai jin tsoro tace "Amore fushi kakeyi har yanxu ko?", gabanta ya dawo yana janyo d'aya stool d'in stool d'in ya zauan yana lakuce mata hanci yace "cute face d'innan naki zai bari inyi fushi dake ne?, ko nayi fushi idona na fad'awa d'an lips d'innan nake hucewa", kai ta girgiza mishi dan ita ba abinda take nufi ba kenan, amma tunda bai gane ba sai tace "koh nayi laifi baza ka min fad'a ba?", yace "zan miki fad'a but ban iya fushi dake, you are too cute da son da nake miki bazai barni in iya fushi dake ba, nasan in nayi fushi dake nima zan ji jiki,", tace "Yaa Abu itama kayi mata fad'a mana kaji, fushin nan da kake yi da ita ba tareda tasan makomarta ba yana wahalar da ita, Kayi hak'uri ka yafe mata, kayi mata fad'an amma kayi hak'uri ka janye fushin nan da kakeyi mata plsss", take far'ar dake fuskanshi ya b'ace, hannunta dake cikin nashi ya janye tareda mik'ewa zai bar wajen, da sauri ta riqo mishi hannu tana girgiza mishi kai idonta tab da hawaye, d'an siririn tsaki yaja yana girgiza mata kai dan bayason hawayen nan su zubi yace "Glitter I thought we were done with that, ba nace bana son zancen nan ba", tace "Allah ni har raina na yafe mata, wlhy son da take maka ya sata aikata abinda duk tayi, Amore tayi hak'uri sosai, batareda da ka sani ba kayi auren nan, mey kake so tayi?, she was angry, she was feeling betrayed, tunaninta duka kaci amanarta ne", wani irin rik'o da yayiwa hannunta saida ya tsorata ta, with stern masculine voice d'inshi yace "shine take so ta kashe min, akwai wani abu da yakeda hujjan kisa a duniya?, in kin mutu me zatacewa Allah?, because she was feeling betrayed sai ta nemi yin kisa?", kai kawai Batuul ke girgiza mishi tana hawaye, tana son ya fahimci kishi babu abinda baya sawa indai kana son maishi, ba kishi saida so, hab'arta ya d'ago yace "Look at me", a hankali ta d'ago idonta ta kalleshi, yace "goge hawayen", babu musu tasa hannu tana goge hawayen, hannu yasa yana goge mata sauran hawayen yace "This should be the last time we will talk about this kinaji?", a hankali ta kad'a mishi kai, yace "Look at me and talk", a hankali tace "toh, am sorry kaji?", ido ya lumshe ya bud'e yace "tashi muje kici wainar taki", ya d'agata ya sauk'ar kan kujera snn yayi mata plating wainar, Fridge ta bud'e ta ciro jug d'in zob'on da ta had'a, kallon jug d'in yayi snn ya kalleta yana langab'ar mata da kai, tayi murmushi tace "inasone fa insha, tun safe nake kwad'ayinshi", baice komai ba ya sa hannu ya karb'i Jug d'in daga hannunta, flask d'in dake ajiye kan island d'in yaga ta d'auka, ido ya wara yace "again?", this time ita ta langab'ar da kan, da sanyin murya tace "kunun kane nayi maka", kai kawai ya jinjina ya d'au flask d'inma, palo yaje ya baje mata komai snn ya koma ya d'auko cups d'in, ganin yanda ta baje tana cin wainar fulawan har dariya ta bashi, d'agowa tayi tana kallonshi da tsukakken bakinta da yaji ya dama, ruwa ya mik'o mata yana dariya yace "dole ne cin yajin?", bakinta ta sake tsukewa tace "yafi dad'i da yaji", zama yayi yana janye plate d'in gabanta yace "nidai kar a koyawa babyna cin haji", raurau tayi da ido tace "toh buh lemme have my plate back", kai ya girgiza mata yana juye yajin a d'aya plate d'in da babu komi, marairaicewa tayi tace "Da yajin fa yafi dad'i", kai ya girgiza mata yace "am not taking the risk, ga wannan na rage miki", ya mik'a mata plate d'in da d'an kad'an ciki, karb'a tayi ta zumb'uro mishi baki tana cin abinta, zama yayi yana shan kununshi bayan ya gama yace ta rakashi pool d'in dake bayan gidan, tare sukaje tana zaune ya shiga ya gama wankanshi dan ya hanata koda k'arasawa wajen bare ta shiga pool d'in, bayan sunyi sallahn magrib suka fita tare tafiya asibiti dan EDD d'inta ya kusa, snn akayi reffering d'insu asibitinsu na Nigeria dan Ammah tace Lallai Lallai su dawo tunda ta kusa haihuwa, a waje suka ci abincin dare snn ya biya dasu Trotters, waje ya samar mata ta zauna, da kanshi ya dinga zagayawa yana kwaso kayan baby da maternity clothes tunda ga kan coats, jumpers, leggings, shauls, towels, Baby bathing sets, craddles, ds duk saida ya tanada kuma duk designers, daga M&S sai Ck, duk in ya d'auko sai ya kawo mata ta gani tukunna kuma yawanci na mata yake kwasa ko kuma unisex, tun tana ganin yawansu tana cewa ya bari in ta haihu lafiya a siya sauran yana qi har tayi shiru ta zubawa sarautar Allah ido, da tayi mishi maganan yayi mata addu'a kawai, ba lallai ta haihu da rai ba, had'e rai kawai yakeyi yace mata shi tana dena fad'a, shiru kawai zatayi dan batason ranshi yana b'aci, sai wajen sha d'ayan dare ya gama siyayyan nashi yasa akayi packaging wasu aka tura Nigeria saura ya barsu a nan, kamar ba kud'i yake zubawa ba haka suka dawo gida, washegari ma da ddare suka sake fita ya sake kafa wata sabuwar siyayya, ana gobe zasu dawo Nigeria suna zaune parlour tana jikinshi yace "Glitter?", d'agowa tayi ta kalleshi yace "Kina da sunan da kike so a sawa Babyn?", kallonshi ta tsaya snn ta girgiza mishi kai a hankali tace "A ah, duk wanda ka saka ma zaimin", kitson da shi ya kama mata yake warwarewa yace "you sure?", kai ta kad'a mishi, a hankali ya sunkuya yayi pecking goshinta "I love you", murmushinta mai kyau tayi tace "I love you more", tara ya kashe musu wata ya taimaka mata suka haura sama, baccin su sukayi peacefully cikeda shak'uwa, washe gari suka shirya suka tafi Nigeria, babu yadda Abu baiyi Ammah ta barshi su sauka gidansu ba tace sam bata San zancen ba, a gidansu zata zauna, tun a waya yace "Ammah Al'ada nefa duka wannan, ya za a raba miji da matarsa bayan ba fad'in Allah bane, tun lokacin ta balbale shi da masifa, badan yaso ba suka sauk'a a gidan Ammah akan bayan kwana biyu zai kaita, ana gobe zai kaita gidan Aunty tana zaune kan gadon tana shan cream in chicken soup, shi kuma yana gaban desk top yace "Glitter yanxu kema yadda zakiyi a d'aukemin keh har tsawon wata da wani abu?, I can't even imagine a day without you, nasan in keh kika fad'awa Ammah zata yadda", murmushi tayi tace "Amore you know I will miss you more ko, with every passing second?, its a tradition, yanzu zaka ga ya wuce", pouting bakinshi yayi yace "Shikenan", ta bud'e baki kenan zatayi magana taji wani suka ta bayanta, ido ta rintse tana ambaton sunan Allah, plate d'in dake hannunta ta ajiye ta a hankali tana k'ok'arin mik'ar da k'afanta, lip d'inta na k'asa ta cije tana cewa "Yasalam", juyowa yayi ya kalleta, da hanzari ya sauk'o yana d'agata yace "Glitter mene, cikinki ne?", ido ta rintse tana riqe mishi hannu tace "Yaa Abu bayana", duk ya gama rikicewa yama rasa ya zaiyi, d'agota yayi yana yi mata sannu zai fita da ita, kamin su fita Ammah ta shigo d'akin kawowa Batuul kunu, da sauri ta ajiye abinda ke hannuta ta k'araso tana "Subhanallah, Bitti ciown ne?", Batuul da ta kasa magana Ammah ta k'araso ta riqe tace "Aliyu d'auko key, I think its delivery, duk ya gama rikicewa ya d'auko key snn ya ciccib'i Batuul dake ta cije lips sbd azabar zafi, a parking lot suka had'u da Farida ta dawo daga school tana parking mota, da gudu ta k'arasa wajensu tana tambayansu, ganin babu mai bata amsa ta koma motan ta bi bayansu, suna zuwa asibitin aka karb'e cikin gaggawa akayi Labour room da ita [12/16, 12:15 AM] ‪+234 808 135 1434‬: 💖💝BATUUL💖💝 By Phartiemarhk 98 Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* Binsu yayi a baya zuwa d'akin da aka shigar da Batuul d'in, daidai bakin k'ofa wata nurse tace "We are sorry Sir, but you can't get in", wani irin kallo ya jefeta dashi da yake mata nuni da bakida hankali ko, da sauri ta sauk'e idonta k'asa tana cewa "am sorry sir", hannu yasa ya matsar da ita gefe ya tura k'ofar shiga d'akin, kan gado ya tarar da Batuul kwance har an bata maternity wear, sun fito da duk wani abu da ake buk'ata, da sauri ya k'arasa gadon da take kwancen, ido kawai ta rintse tana ambaton sunan Allah dan yau hawayen ma nemanshi take ta rasa, dukda azabar da take sha hakan bai hanata jin d'umin hannunshi cikin nata ba, a wahalce ta bud'e idanunta ta sauk'e cikin nashi, ido ya lumshe ya bud'e, bayason ganin wannan yanayi da take ciki, a hankali tace "Yaa Abu Aunty", kamar wacce ta watsa ruwa haka sweat duk ya jik'ata, hannunta dake cikin nashi ya riqe ya kai bakinshi tareda kissing yace "You will be fine Babyna, we will make it together, am here kinji?", ido ta lumshe tana kad'a kai cikeda azaba tace "inaso inga Aunty, plss call her for me kaji Yaa Abu, inaso in ganta", ta fad'a tana sake cije leb'e, gaba d'aya ta gama rikitashi, shima so yake kawai yaga hawaye ya zubo mishi ko zaiji dad'i da wannan irin ciwon da yake jimata, daidai fuskarta ya sunkuyo yace "Glitter you will b okay, Aunty will be here anytime,Ammah zata fad'awa Aunty, am upright sure, she will b here shortly, sannu kinji?", daidai lokacin da doctor da nurses d'in suka k'araso cikin shirin aikinsu, ganin Abu zaune Doctor yasa yace "Good Afternoon Mr Kyaree, we are sorry but we need you to stay outside to carry out our work efficiently", fiyeda kallon da yayiwa Nurse d'in d'azu yayiwa Doctor dukda sabon dake tsakaninsu amma yau mantawa yayi da hakan, gaba d'aya ranshi ya gama b'aci, matarshi in such a pain maimakon yayi attending to her yake kawo masa shirmen banza wai ya fita, a fusace yace "Get yourself composed Doctor and attend to my wife, She is my wife, we are in this together, I ain't moving an inch from here", ya sake maimatawa sternly snn yace "And if anything happens to her?, am gonna shut d whole hospital down, you will all pay for it", yayi maganan idonshi na kad'awa, "Damn it, Doctorrr", ya fad'a kamar zai make doctor, ganin dagaske yake kuma zai b'ata musu lokaci yasa kawai suka fad'a aikinsu cikeda k'warewa, duk wani kuka na Batuul yau nemanshi tayi ta rasa, Addu'o'in da Abu keyi yana tofa mata duk wanda ta kama shi takeyi, da taji azaba lokacin take tuna Aunty, take zata fara Rabbir Ham huma kama rabbayani Sagira, duk wani motsi da Batuul zatayi har cikin ranshi Abu ke jinshi, sosai ya tausaya mata ganin irin wahalan da take sha, a lokacin ya sake ganin kima da daraja irin ta mata had'e da tausayinsu, in basu ba wazai iya enduring irin wannan ciwon, addu'a yayiwa duk wata mace wacce aka haifa da wacce ta haifa, a hankali ya fara tofa mata "wa tilka hujjatuna atainaha Ibraheema ata qaumihi, narfa'u darajatin man nasha, inna rabbaka hakeemun aleem", a zuci ta dunga maimaita aabinda taji yana fad'i, a hankali taji ciwon na raguwa, ba a cika one hour ba ta sumb'ulo y'ar Babynta k'arama mai kyau itama, Hamdala Abu yayi yana kai hannu zai tab'a Babyn Doctor yace Mishi "No pls, not now", yatsina fuska yayi ya janye hannunshi, tareda shi suka taimaka aka gyara aka kimtsa Batuul da Baby, bayan an fito da Babyn yana zaune bakin gadon da Batuul ke kwance yana mata sannu suka mik'o musu Babyn, da Bismillah yasa hannu ya karb'eta daga wajen nurse, gaba d'aya komai na jikinta farine, babu komai nata a waje sai d'an k'aramin face d'inta, wani irin k'auna da nutsuwa da baisan daga inda yake sauk'o mishi ba yakeji jin d'umin Babyn jikinshi, murmushi ne ya kufce Mishi ganin komai na fuskan Babyn irin nashi, lips d'inta ne Kad'ai irin na Batuul hatta heart shape d'in bottom lip d'in nata irin na Batuul ne, a hankali ya matso da Babyn kusa da Fuskan Batuul yace "Fatima our child, our Baby, kyautar da Allah yayi mana Fatima, look at her please, she is too cute for me", murmushi kawai Batuul tayi dan bata jin k'arfin jikin nata sosai, daidai kunnen Babyn ya sunkuya tareda k'ira mata Sallah, ya karanto "inni sammaituha (A'eesha) wa inni u'ixuha bika wa xurriyatiha minash shaaid'anir rajim" yayi mata addu'o'i sosai tareda yi mata Hud'uba da Suna A'eesha, Dabinon Ajwan da dama yana cikin kayansu yasa aka mik'o mishi da ruwan Zamzam ya tauna ya d'iga mata tareda ruwan Zamzam d'in, kamar wacce tasan abinda akeyi ta yatsina fuskarta tana lashe baki, dariya yayi ya sunkuya yayi kissing goshinta snn ya matsa jikin Batuul d'in yace "Glitter?", a hankali ta d'ago lumsassun idanunta ta dubeshi, yace "kin bani kyautar da duk duniya babu mai bani irinta, you have given me the best gift I would ever ask off, I will forever be grateful, Allah ya barmin keh Glitter kici gaba da bani wasu Babies d'in, just tell me anything you want, ko meye shi indai akwai shi a nan duniyan, I promise to get it for you, you have given me the best gift of life, I promise you, just ask me duk abinda kikeso zanyi miki shi, just tell me jinni", a hankali ta bud'e idanunta da suke a lumshe, kallonshi takeyi da murmudhi d'auke kan fuskarta tana tunanin abinda takeson cewan, tasan duk murna ne ya cikashi amma da wuya ta samu abinda takeson, a hankali ta bud'e baki tace "You Promise?", kallonta yayi for seconds kamin ya kad'a mata kai, zai yi magana doctors da nurses d'in suka zo za a canja mata d'aki, tana kwanace suka turata zuwa wani d'akin, badan ta saba da ireirensu ba da zatace d'aki ne kawai ba na asibiti sbd girma da kuma kyansu, saida Nurses d'in suka gama duk wani necessary abu da ya kamata suyi mata itada Babyn snn suka kwantar da Babyn gaban Batuul suka fita suna mata sannu, kallonsu yayi with so much adoration yana yiwa Allah godiya da kyautan nan da Allah yayi mishi, Batuul is one part of him da baya tunanin zai iya rayuwa babu ita, hannunshi yasa ya kamo na Batuul d'in yana d'an murzawa a hankali yace "Fatima you are the best thing that ever happened to me kinsan da haka ko?", a hankali ta kad'a mishi kai yaci "I know I love, ban san amfanin kud'ina ba if I can't give you abinda kike nema, komeye shi kike so indai bai sab'awa addini back just mention the anything, zanyi miki shi Glitter", ya fad'a yana sassauta muryarshi tareda sak'ale yatsunsu waje d'aya, a hankali ta bud'e baki tace "Yaa Abu ka dawo Ajiddeh gidanka, zamanta haka ya isa batareda sanin makomarta ba, banasone ka shiga hakkinta, na fad'a maka nikam na yafe mata wlhy, nobody is above mistake, kuma everything happens for a reason, maybe for us to realise each others worth, how much we mean to each other, Yaa Abu plssssss", ta k'arasa maganan tana lumshe ido , shi kad'ai yasan irin impact d'in da Batuul ta yiwa rayuwanshi, mesa baza ta fad'i wani abin ba sai wannan, har ga Allah ko jiya da Abui ya sake mishi zancen Ajiddeh  ce mishi yayi zai rabu da ita, zai sallameta, duk da ya yafe mata shima amma ya kasa samun wajen da zai ajiye abinda ta aikata ya manta dashi, baya tunanin zai iya d'aukan wani abin da zai sami family d'inshi ya qyale maishi nan gaba, amma its about Batuul yanzu, she is worth more than that, He can sacrifice that atom of happiness da ya rage mishi for her to be happy, tana son ya maida Ajiddeh d'akinta, kuma alk'awari yayi mata akan ta fad'i abinda takeso, how can he just deny her , a hankali ya sauk'ar da idonshi kan fuskan Batuul ya shafi gefen fuskarta da d'aya hannun nashi yace "will that make you happy?", kai ta kad'a mishi, murmushi yayi mata yace "Anything for you Fatima, just know I will always love you", murmushin ta mishi amma jin yanayin da yake  sab'ule hannunshi cikin nata yasa murmushin dake fuskarta bajewa, duk da rashin k'arfin da takeji hakan bai hanata damqe hannunshi ba, kallonta yayi, ganin hawaye idonta yasashi zama da wuri yana girgiza mata kai, cikin siririyar muryarta tace "Are you sad, angry about what I requested for?, ka bari na fasa if you are not okay with .....", bai bari ta k'arasa ba ya d'aura dogayen yatsunshi kan lips d'inta yace "Shhhh, am happy with whatever that makes you happy, okay?", kai ta kad'a mishi yayi murmushi yace "Good girl, get some rest", ya fad'a yana d'aga mata girarshi d'aya, murmushin tayi mishi itama tareda lumshe ido, ido ya tsura musu itada y'ar Babyn dake gabanshi yana kallonsu yana dad'a yiwa Allah godiya da ya bashi wad'annan precious kyautan a rayuwanshi, yana nan zaune yana kallonsu aka turo k'ofar d'akin, Abui ne sai Ammah, Farida sai Sadiq, lokacin doctors suka sanar dasu da Batuul ta sauk'a lafiya zasu iya shiga su kanta, tsabar murna Farida har rawa jikinta keyi sbd d'okin zuwa taga niece d'inta, y'ar yayanta y'ar Bestyn ta that turn out to be a sister, Abui ne ya fara d'aukan Babyn da murmushi a fuskanshi yana tuna lokacin da ya fara riqe Abu for the first, yace "This is how I held Aliyu , kamar jiya fa gashi yanzu Allah ya bani tsawon rai nayi witnessing haihuwar y'arshi, Allah yayi muku albarka baki d'ayanku", ya fad'a tareda kissing goshin yarinyar, duk suka amsa da "Amin", Ammah ce ta karb'eta daga hannun hannun Abui murmushi d'auke fuskanta snn ta kalli Batuul dake kwance tana bacci tace "Allasarki Bitti, yadda kukaga wannan jaririyar haka Fatima take lokacin da aka haifota, tun ranan Allah ya dasa min sonta a raina kamar ni na haifeta, ashe itace zata fara samar min jika, Allah ya k'ara miki lafiya ya d'ayyiba miki zuri'a", duk suka amsa da Amin, Abu ya dubi Ammah yace "Ammah an fad'awa su Aunty? Tun d'azu take nemanta", ya fad'a yana kallon Batuul, Ammah tayi murmushi jin Batuul nata Neman Aunty tasan zafin haihuwar yasa ta neman Aunty, tace "Dama ana shiga da ita na fad'a musu toh bayan doctor ya fad'a mana sauk'arta lafiya nayi maza na sanar dasu, da yake ma can d'in za a kaita basai sunzo nan d'in ba ai", ya d'an tsuke baki yace "Ammah har yanzu wai zancen kaitan na nan?, wlhy hankalina zaifi kwanciya in ina kusa dasu, zan kula dasu Sosai In sha Allah, Plssss Ammah", ya k'arashe maganan kamar mai shirin yin kuka, dariya ma yaso ya bawa Ammah amma ta dake tace "Kai nifa ban cike da shirme kana jina, ba al'ada bace da zaka wani ce kafison a bar maka su?, toh ba kanka za a dena ba, gidansu ne sai ta tafi yin wanka", badan yaso ba ya hak'ura ya miqe tareda yin sallama dasu, Farida da batasan me ke faruwa ba duk hankalinta na kan jaririyar kamar zata maidata ciki ya duba yace "Farida let her be plssss, bacci takeyi", kallonshi tayi da murmushi a fuskanta tace "nifa nasan da ni take Kama, bari ta tashi zaku gane abinda nake fad'a muku", kai kawai ya kad'a yace "Naji ai ke zakiyi rainaonta but for now barta ta huta, bata ma saba da iskan duniyar ba bare wahalar cikinta", cikeda murna Farida jin yace ita zata yi raino ta matsa da baya da sauri tace "Ai na ma matsan, Allah ya raya mana Babyn mu, Sunan waye za a saka mata?", har ya fara tafiya kamar ya fad'a mata ko sunan wa yarinyar zataci ya fasa, Abui ne kad'ai yasan meye sunan jaririyar, yayi murna sosai ya sa musu albarka su dukkansu, tareda fatan Allah ya k'ara had'a Kansu, Sallama yayi da Ammah da Farida ya fice daga d'akin, Kai tsaye gidan Aunty ya, yasa akayi mata magana dan bata parlour ko kince, kamar kullum cikin shigarta ta alfarma da gayu ta sauk'o, ganin Abu ne yasa ta d'an fad'ad'a murmushin dake fuskarta, yana hangota ya sauk'o daga kan kujeran tareda d'an duk'awa ya gaidata, wani kunyan Aunty yakeji yau na daban, ta amsa mishi snn ta mishi barkan k'aruwan da ya samu tareda addu'o'i, murmushi kawai yakeyi yanajin dad'in addu'ar da take musu, tasa aka kawo mishi refreshments, ruwan kawai ya bud'e bai kai ga sha ba ya fad'a mata abinda ke tafe dashi, might murmishi Aunty tayi, ita da kanta taji tausayin Batuul, tasan wahalan haihuwan da ta sha ya sa take son ganinta, da murmushinta tace "Kaima Aliyu sai ka biyewa shirmenta Batuul kaima, me zuwan nawa ma zai mata in banda shirme irin na Batuul, addu'a kawai zamuyi mata da fatan sauk'a lafiya kuma Alhamdulillah Allah ya amsa mana addu'a, sai kuma yanzu muce Allah ya k'ara musu lafiya ita da abinda ta haifa", kanshi a k'asa yace "Aunty ayi hak'urin dai muje in ta farkan ta ganki dan tun d'azu take ambatonki, she will be to wake up to you by her side", Murmushi kawai Aunty tayi tace "Tohh shikenan bara insa a shirya mata abubuwan da na sa akayi mata sai insa Baa Liman ya kaini in tq gannin hankalinta ya kwanta na dawo", Sam Abu yaqi yadda saidai Aunty ta bishi, badan taso ba ta haqura suka tafi, a asibiti da kanshi ya bud'e mata k'ofa tareda samo ma'aikata su shiga da kayayyakin dake baya, har lokacin Batuul bacci takeyi, har mamakin yawan mutanen dake d'akin yayi, sai barka suke mishi da Allah ya raya, gaisawa yayi dasu snn yayi musu sallama ya fita, yana fita ya qira Massa akan zaizo ya sameshi zai rakashi, kai tsaye gidan ya wuce, Abu ke tuk'a motar Massa na daga gefe yana taya Abun murnar k'aruwa, sai shak'iyanci yake mishi, ganin yaqi kulashi yace "Wai kai inama zamune haka?", Abu ya shafe fuska yace "Gidansu Hauwa zani, I promised Batuul to take her back", Massa ya wara ido yace "Amma kai duniyanci duk ka iyashi, are you telling me all these while tana gidansu da aurenka kuma kanta?", Tsaki yaja yace "Kaga ni karka dameni, she caused everything, and I can do it bitter and better than what I did, am talking about Fatima, she is my reality, I can't risk anything da zai cutar da ita, and taking back Ajiddeh is a compromise, she told me she dd be happy, so please spare all these naggings", Kafad'arshi Massa ya dafa yace "You are a man, you can take whatever, kawai Addu'a zakayi Allah ya shige maka gaba", a sanyaye ya amsa da "Amin", shi gaba d'ayanshi baisan ta ina zai fara ba, seven months amma bai tab'a waiwayarta ba sai Yanzu, har yazo k'ofar gidansu Ajiddeh yana sak'e sak'e a ranshi, masi gadi da sauran ma'aikatan dake bakinta da murna suka dinga gaidashi dan sun sashi da kyauata da yi musu alheri, saida yayi parking yasa a duba mishi ko Dad na gidan, in yana nan ayi masa iso dashi, hakan kuwa akayi akace musu yana daga garden, can wani yayi musu jagora suka isa, yana zaune kan d'aya daga cikin kujeraun dake k'ark'ashin hut d'in wajen da ruwa gabanshi, da mamaki Dad ke kallon su har suka k'araso wajenshi, a ladabce suka gaida Dad, da fara'a ya amsa musu kamar wani abu bai shiga tsakaninshi da y'arshi ba, har saida Abu yaji kunya ganin yanda Dad ke janshi a jiki, shiru ne ya biyo baya kqmin Abu yayi k'arfin hali a sanyaye yace "Dad munzo mu bada hak'uri kan abinda ya faru, kuskurene da muka aikata bisa son zuciya, nazo in koma da Hauwa d'akinta, Allah ya have mana baki d'ayanmu" Dad da ya k'ura mishi ido ya cire glass d'in dake idonshi yana kad'a kai yace "Aliyu tun lokacin da Hauwa tazo min da zancen kai zata aura nasan tayi sa'an miji, nayi murna sosai dan nasan zaka kula da ita iya gwargwado, tun kana k'arami lokacin Ina aiki k'ark'ashin mahaifinka nasan kai yaro ne mai dattako, Aliyu ta fad'amin duk abinda ya faru tsakaninku da ita saidai kunyar mahaifinka da nakeji bazai barni inje baku hak'uri, nasan sunyi muku kuskuren da bai canci wannan yafiya ba, saidai duba da irin gidan da ka fito yasa bazanyi mamaki ba, ina mai sake baka hak'uri kan abinda suka aikata muku,, maganar kkmawar Hauwa kuma Aliyu tunda ka tako da k'afarka bazan iya hanaka ba, amma tunda hakane inason duk wani kuskure da zata sake maka ka hukuntata fiyeda yanda zanyi dan in har ta yadda ta sake takowa gidan nan da sunan tayi maka laifi toh saidai ta nemi wani uban ba ni ba kuma", daidai Abu zai amsa wata mata ta k'araso da babbar rigan a hannunta, bata lura da mutannen dake wajen ba ta k'arso tana cewa "Daddy nikam baka gama karanta Jaridan ba, you are getting late fa", sai lokacin ta lura da su Abu, dukda face d'in Abu looks familiar but ta kasa tuna inda ta sanshi, Dad yayi musu introducing juna kan itace sabuwar matar da ya aura 4months back sunanta Kulthum, su kuma ya nuna Abu yace "wannan shine mijin Hauwa Aliyu, wannan kuma d'an uwanshi ne Mustapha", sai lokacin ta tuna inda ta sanshi, duk d'akin Ajiddeh hotunan shine hatta gaban wayarta hotunanshine, da murmushi suka gaisa, Dad ya karb'i riganshi yace "Sai su shiga daga ciki, ni inada meeting, yanda kukayi duk ka sanar dani Aliyu", ya Amsa mishi da Insha Allah da yi mishi fatan a dawo lafiya, a d'akinta Aunty Kulthum ta tarar da ita kwance duk ta rame tayi duhu, kamar ba ita bace ba wannan Ajiddeh sarkin gayu da d'osana lipstick ba, gashin nan ma da yake shan gyara duk ya kad'e, wutan d'akin Aunty Kulthum ta kunna tana mai k'iran sunan Ajiddeh 💖💝BATUUL💖💝 By Phartiemarhk 99 Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR* lolllx Binsu yayi a baya zuwa d'akin da aka shigar da Batuul d'in, daidai bakin k'ofa wata nurse tace "We are sorry Sir, but you can't get in", wani irin kallo ya jefeta dashi da yake mata nuni da bakida hankali ko, da sauri ta sauk'e idonta k'asa tana cewa "am sorry sir", hannu yasa ya matsar da ita gefe ya tura k'ofar shiga d'akin, kan gado ya tarar da Batuul kwance har an bata maternity wear, sun fito da duk wani abu da ake buk'ata, da sauri ya k'arasa gadon da take kwancen, ido kawai ta rintse tana ambaton sunan Allah dan yau hawayen ma nemanshi take ta rasa, dukda azabar da take sha hakan bai hanata jin d'umin hannunshi cikin nata ba, a wahalce ta bud'e idanunta ta sauk'e cikin nashi, ido ya lumshe ya bud'e, bayason ganin wannan yanayi da take ciki, a hankali tace "Yaa Abu Aunty", kamar wacce ta watsa ruwa haka sweat duk ya jik'ata, hannunta dake cikin nashi ya riqe ya kai bakinshi tareda kissing yace "You will be fine Babyna, we will make it together, am here kinji?", ido ta lumshe tana kad'a kai cikeda azaba tace "inaso inga Aunty, plss call her for me kaji Yaa Abu, inaso in ganta", ta fad'a tana sake cije leb'e, gaba d'aya ta gama rikitashi, shima so yake kawai yaga hawaye ya zubo mishi ko zaiji dad'i da wannan irin ciwon da yake jimata, daidai fuskarta ya sunkuyo yace "Glitter you will b okay, Aunty will be here anytime,Ammah zata fad'awa Aunty, am upright sure, she will b here shortly, sannu kinji?", daidai lokacin da doctor da nurses d'in suka k'araso cikin shirin aikinsu, ganin Abu zaune Doctor yasa yace "Good Afternoon Mr Kyaree, we are sorry but we need you to stay outside to carry out our work efficiently", fiyeda kallon da yayiwa Nurse d'in d'azu yayiwa Doctor dukda sabon dake tsakaninsu amma yau mantawa yayi da hakan, gaba d'aya ranshi ya gama b'aci, matarshi in such a pain maimakon yayi attending to her yake kawo masa shirmen banza wai ya fita, a fusace yace "Get yourself composed Doctor and attend to my wife, She is my wife, we are in this together, I ain't moving an inch from here", ya sake maimatawa sternly snn yace "And if anything happens to her?, am gonna shut d whole hospital down, you will all pay for it", yayi maganan idonshi na kad'awa, "Damn it, Doctorrr", ya fad'a kamar zai make doctor, ganin dagaske yake kuma zai b'ata musu lokaci yasa kawai suka fad'a aikinsu cikeda k'warewa, duk wani kuka na Batuul yau nemanshi tayi ta rasa, Addu'o'in da Abu keyi yana tofa mata duk wanda ta kama shi takeyi, da taji azaba lokacin take tuna Aunty, take zata fara Rabbir Ham huma kama rabbayani Sagira, duk wani motsi da Batuul zatayi har cikin ranshi Abu ke jinshi, sosai ya tausaya mata ganin irin wahalan da take sha, a lokacin ya sake ganin kima da daraja irin ta mata had'e da tausayinsu, in basu ba wazai iya enduring irin wannan ciwon, addu'a yayiwa duk wata mace wacce aka haifa da wacce ta haifa, a hankali ya fara tofa mata "wa tilka hujjatuna atainaha Ibraheema ata qaumihi, narfa'u darajatin man nasha, inna rabbaka hakeemun aleem", a zuci ta dunga maimaita aabinda taji yana fad'i, a hankali taji ciwon na raguwa, ba a cika one hour ba ta sumb'ulo y'ar Babynta k'arama mai kyau itama, Hamdala Abu yayi yana kai hannu zai tab'a Babyn Doctor yace Mishi "No pls, not now", yatsina fuska yayi ya janye hannunshi, tareda shi suka taimaka aka gyara aka kimtsa Batuul da Baby, bayan an fito da Babyn yana zaune bakin gadon da Batuul ke kwance yana mata sannu suka mik'o musu Babyn, da Bismillah yasa hannu ya karb'eta daga wajen nurse, gaba d'aya komai na jikinta farine, babu komai nata a waje sai d'an k'aramin face d'inta, wani irin k'auna da nutsuwa da baisan daga inda yake sauk'o mishi ba yakeji jin d'umin Babyn jikinshi, murmushi ne ya kufce Mishi ganin komai na fuskan Babyn irin nashi, lips d'inta ne Kad'ai irin na Batuul hatta heart shape d'in bottom lip d'in nata irin na Batuul ne, a hankali ya matso da Babyn kusa da Fuskan Batuul yace "Fatima our child, our Baby, kyautar da Allah yayi mana Fatima, look at her please, she is too cute for me", murmushi kawai Batuul tayi dan bata jin k'arfin jikin nata sosai, daidai kunnen Babyn ya sunkuya tareda k'ira mata Sallah, ya karanto "inni sammaituha (A'eesha) wa inni u'ixuha bika wa xurriyatiha minash shaaid'anir rajim" yayi mata addu'o'i sosai tareda yi mata Hud'uba da Suna A'eesha, Dabinon Ajwan da dama yana cikin kayansu yasa aka mik'o mishi da ruwan Zamzam ya tauna ya d'iga mata tareda ruwan Zamzam d'in, kamar wacce tasan abinda akeyi ta yatsina fuskarta tana lashe baki, dariya yayi ya sunkuya yayi kissing goshinta snn ya matsa jikin Batuul d'in yace "Glitter?", a hankali ta d'ago lumsassun idanunta ta dubeshi, yace "kin bani kyautar da duk duniya babu mai bani irinta, you have given me the best gift I would ever ask off, I will forever be grateful, Allah ya barmin keh Glitter kici gaba da bani wasu Babies d'in, just tell me anything you want, ko meye shi indai akwai shi a nan duniyan, I promise to get it for you, you have given me the best gift of life, I promise you, just ask me duk abinda kikeso zanyi miki shi, just tell me jinni", a hankali ta bud'e idanunta da suke a lumshe, kallonshi takeyi da murmudhi d'auke kan fuskarta tana tunanin abinda takeson cewan, tasan duk murna ne ya cikashi amma da wuya ta samu abinda takeson, a hankali ta bud'e baki tace "You Promise?", kallonta yayi for seconds kamin ya kad'a mata kai, zai yi magana doctors da nurses d'in suka zo za a canja mata d'aki, tana kwanace suka turata zuwa wani d'akin, badan ta saba da ireirensu ba da zatace d'aki ne kawai ba na asibiti sbd girma da kuma kyansu, saida Nurses d'in suka gama duk wani necessary abu da ya kamata suyi mata itada Babyn snn suka kwantar da Babyn gaban Batuul suka fita suna mata sannu, kallonsu yayi with so much adoration yana yiwa Allah godiya da kyautan nan da Allah yayi mishi, Batuul is one part of him da baya tunanin zai iya rayuwa babu ita, hannunshi yasa ya kamo na Batuul d'in yana d'an murzawa a hankali yace "Fatima you are the best thing that ever happened to me kinsan da haka ko?", a hankali ta kad'a mishi kai yaci "I know I love, ban san amfanin kud'ina ba if I can't give you abinda kike nema, komeye shi kike so indai bai sab'awa addini back just mention the anything, zanyi miki shi Glitter", ya fad'a yana sassauta muryarshi tareda sak'ale yatsunsu waje d'aya, a hankali ta bud'e baki tace "Yaa Abu ka dawo Ajiddeh gidanka, zamanta haka ya isa batareda sanin makomarta ba, banasone ka shiga hakkinta, na fad'a maka nikam na yafe mata wlhy, nobody is above mistake, kuma everything happens for a reason, maybe for us to realise each others worth, how much we mean to each other, Yaa Abu plssssss", ta k'arasa maganan tana lumshe ido , shi kad'ai yasan irin impact d'in da Batuul ta yiwa rayuwanshi, mesa baza ta fad'i wani abin ba sai wannan, har ga Allah ko jiya da Abui ya sake mishi zancen Ajiddeh ce mishi yayi zai rabu da ita, zai sallameta, duk da ya yafe mata shima amma ya kasa samun wajen da zai ajiye abinda ta aikata ya manta dashi, baya tunanin zai iya d'aukan wani abin da zai sami family d'inshi ya qyale maishi nan gaba, amma its about Batuul yanzu, she is worth more than that, He can sacrifice that atom of happiness da ya rage mishi for her to be happy, tana son ya maida Ajiddeh d'akinta, kuma alk'awari yayi mata akan ta fad'i abinda takeso, how can he just deny her , a hankali ya sauk'ar da idonshi kan fuskan Batuul ya shafi gefen fuskarta da d'aya hannun nashi yace "will that make you happy?", kai ta kad'a mishi, murmushi yayi mata yace "Anything for you Fatima, just know I will always love you", murmushin ta mishi amma jin yanayin da yake sab'ule hannunshi cikin nata yasa murmushin dake fuskarta bajewa, duk da rashin k'arfin da takeji hakan bai hanata damqe hannunshi ba, kallonta yayi, ganin hawaye idonta yasashi zama da wuri yana girgiza mata kai, cikin siririyar muryarta tace "Are you sad, angry about what I requested for?, ka bari na fasa if you are not okay with .....", bai bari ta k'arasa ba ya d'aura dogayen yatsunshi kan lips d'inta yace "Shhhh, am happy with whatever that makes you happy, okay?", kai ta kad'a mishi yayi murmushi yace "Good girl, get some rest", ya fad'a yana d'aga mata girarshi d'aya, murmushin tayi mishi itama tareda lumshe ido, ido ya tsura musu itada y'ar Babyn dake gabanshi yana kallonsu yana dad'a yiwa Allah godiya da ya bashi wad'annan precious kyautan a rayuwanshi, yana nan zaune yana kallonsu aka turo k'ofar d'akin, Abui ne sai Ammah, Farida sai Sadiq, lokacin doctors suka sanar dasu da Batuul ta sauk'a lafiya zasu iya shiga su kanta, tsabar murna Farida har rawa jikinta keyi sbd d'okin zuwa taga niece d'inta, y'ar yayanta y'ar Bestyn ta that turn out to be a sister, Abui ne ya fara d'aukan Babyn da murmushi a fuskanshi yana tuna lokacin da ya fara riqe Abu for the first, yace "This is how I held Aliyu , kamar jiya fa gashi yanzu Allah ya bani tsawon rai nayi witnessing haihuwar y'arshi, Allah yayi muku albarka baki d'ayanku", ya fad'a tareda kissing goshin yarinyar, duk suka amsa da "Amin", Ammah ce ta karb'eta daga hannun hannun Abui murmushi d'auke fuskanta snn ta kalli Batuul dake kwance tana bacci tace "Allasarki Bitti, yadda kukaga wannan jaririyar haka Fatima take lokacin da aka haifota, tun ranan Allah ya dasa min sonta a raina kamar ni na haifeta, ashe itace zata fara samar min jika, Allah ya k'ara miki lafiya ya d'ayyiba miki zuri'a", duk suka amsa da Amin, Abu ya dubi Ammah yace "Ammah an fad'awa su Aunty? Tun d'azu take nemanta", ya fad'a yana kallon Batuul, Ammah tayi murmushi jin Batuul nata Neman Aunty tasan zafin haihuwar yasa ta neman Aunty, tace "Dama ana shiga da ita na fad'a musu toh bayan doctor ya fad'a mana sauk'arta lafiya nayi maza na sanar dasu, da yake ma can d'in za a kaita basai sunzo nan d'in ba ai", ya d'an tsuke baki yace "Ammah har yanzu wai zancen kaitan na nan?, wlhy hankalina zaifi kwanciya in ina kusa dasu, zan kula dasu Sosai In sha Allah, Plssss Ammah", ya k'arashe maganan kamar mai shirin yin kuka, dariya ma yaso ya bawa Ammah amma ta dake tace "Kai nifa ban cike da shirme kana jina, ba al'ada bace da zaka wani ce kafison a bar maka su?, toh ba kanka za a dena ba, gidansu ne sai ta tafi yin wanka", badan yaso ba ya hak'ura ya miqe tareda yin sallama dasu, Farida da batasan me ke faruwa ba duk hankalinta na kan jaririyar kamar zata maidata ciki ya duba yace "Farida let her be plssss, bacci takeyi", kallonshi tayi da murmushi a fuskanta tace "nifa nasan da ni take Kama, bari ta tashi zaku gane abinda nake fad'a muku", kai kawai ya kad'a yace "Naji ai ke zakiyi rainaonta but for now barta ta huta, bata ma saba da iskan duniyar ba bare wahalar cikinta", cikeda murna Farida jin yace ita zata yi raino ta matsa da baya da sauri tace "Ai na ma matsan, Allah ya raya mana Babyn mu, Sunan waye za a saka mata?", har ya fara tafiya kamar ya fad'a mata ko sunan wa yarinyar zataci ya fasa, Abui ne kad'ai yasan meye sunan jaririyar, yayi murna sosai ya sa musu albarka su dukkansu, tareda fatan Allah ya k'ara had'a Kansu, Sallama yayi da Ammah da Farida ya fice daga d'akin, Kai tsaye gidan Aunty ya, yasa akayi mata magana dan bata parlour ko kince, kamar kullum cikin shigarta ta alfarma da gayu ta sauk'o, ganin Abu ne yasa ta d'an fad'ad'a murmushin dake fuskarta, yana hangota ya sauk'o daga kan kujeran tareda d'an duk'awa ya gaidata, wani kunyan Aunty yakeji yau na daban, ta amsa mishi snn ta mishi barkan k'aruwan da ya samu tareda addu'o'i, murmushi kawai yakeyi yanajin dad'in addu'ar da take musu, tasa aka kawo mishi refreshments, ruwan kawai ya bud'e bai kai ga sha ba ya fad'a mata abinda ke tafe dashi, might murmishi Aunty tayi, ita da kanta taji tausayin Batuul, tasan wahalan haihuwan da ta sha ya sa take son ganinta, da murmushinta tace "Kaima Aliyu sai ka biyewa shirmenta Batuul kaima, me zuwan nawa ma zai mata in banda shirme irin na Batuul, addu'a kawai zamuyi mata da fatan sauk'a lafiya kuma Alhamdulillah Allah ya amsa mana addu'a, sai kuma yanzu muce Allah ya k'ara musu lafiya ita da abinda ta haifa", kanshi a k'asa yace "Aunty ayi hak'urin dai muje in ta farkan ta ganki dan tun d'azu take ambatonki, she will be to wake up to you by her side", Murmushi kawai Aunty tayi tace "Tohh shikenan bara insa a shirya mata abubuwan da na sa akayi mata sai insa Baa Liman ya kaini in tq gannin hankalinta ya kwanta na dawo", Sam Abu yaqi yadda saidai Aunty ta bishi, badan taso ba ta haqura suka tafi, a asibiti da kanshi ya bud'e mata k'ofa tareda samo ma'aikata su shiga da kayayyakin dake baya, har lokacin Batuul bacci takeyi, har mamakin yawan mutanen dake d'akin yayi, sai barka suke mishi da Allah ya raya, gaisawa yayi dasu snn yayi musu sallama ya fita, yana fita ya qira Massa akan zaizo ya sameshi zai rakashi, kai tsaye gidan ya wuce, Abu ke tuk'a motar Massa na daga gefe yana taya Abun murnar k'aruwa, sai shak'iyanci yake mishi, ganin yaqi kulashi yace "Wai kai inama zamune haka?", Abu ya shafe fuska yace "Gidansu Hauwa zani, I promised Batuul to take her back", Massa ya wara ido yace "Amma kai duniyanci duk ka iyashi, are you telling me all these while tana gidansu da aurenka kuma kanta?", Tsaki yaja yace "Kaga ni karka dameni, she caused everything, and I can do it bitter and better than what I did, am talking about Fatima, she is my reality, I can't risk anything da zai cutar da ita, and taking back Ajiddeh is a compromise, she told me she dd be happy, so please spare all these naggings", Kafad'arshi Massa ya dafa yace "You are a man, you can take whatever, kawai Addu'a zakayi Allah ya shige maka gaba", a sanyaye ya amsa da "Amin", shi gaba d'ayanshi baisan ta ina zai fara ba, seven months amma bai tab'a waiwayarta ba sai Yanzu, har yazo k'ofar gidansu Ajiddeh yana sak'e sak'e a ranshi, masi gadi da sauran ma'aikatan dake bakinta da murna suka dinga gaidashi dan sun sashi da kyauata da yi musu alheri, saida yayi parking yasa a duba mishi ko Dad na gidan, in yana nan ayi masa iso dashi, hakan kuwa akayi akace musu yana daga garden, can wani yayi musu jagora suka isa, yana zaune kan d'aya daga cikin kujeraun dake k'ark'ashin hut d'in wajen da ruwa gabanshi, da mamaki Dad ke kallon su har suka k'araso wajenshi, a ladabce suka gaida Dad, da fara'a ya amsa musu kamar wani abu bai shiga tsakaninshi da y'arshi ba, har saida Abu yaji kunya ganin yanda Dad ke janshi a jiki, shiru ne ya biyo baya kqmin Abu yayi k'arfin hali a sanyaye yace "Dad munzo mu bada hak'uri kan abinda ya faru, kuskurene da muka aikata bisa son zuciya, nazo in koma da Hauwa d'akinta, Allah ya have mana baki d'ayanmu" Dad da ya k'ura mishi ido ya cire glass d'in dake idonshi yana kad'a kai yace "Aliyu tun lokacin da Hauwa tazo min da zancen kai zata aura nasan tayi sa'an miji, nayi murna sosai dan nasan zaka kula da ita iya gwargwado, tun kana k'arami lokacin Ina aiki k'ark'ashin mahaifinka nasan kai yaro ne mai dattako, Aliyu ta fad'amin duk abinda ya faru tsakaninku da ita saidai kunyar mahaifinka da nakeji bazai barni inje baku hak'uri, nasan sunyi muku kuskuren da bai canci wannan yafiya ba, saidai duba da irin gidan da ka fito yasa bazanyi mamaki ba, ina mai sake baka hak'uri kan abinda suka aikata muku,, maganar kkmawar Hauwa kuma Aliyu tunda ka tako da k'afarka bazan iya hanaka ba, amma tunda hakane inason duk wani kuskure da zata sake maka ka hukuntata fiyeda yanda zanyi dan in har ta yadda ta sake takowa gidan nan da sunan tayi maka laifi toh saidai ta nemi wani uban ba ni ba kuma", daidai Abu zai amsa wata mata ta k'araso da babbar rigan a hannunta, bata lura da mutannen dake wajen ba ta k'arso tana cewa "Daddy nikam baka gama karanta Jaridan ba, you are getting late fa", sai lokacin ta lura da su Abu, dukda face d'in Abu looks familiar but ta kasa tuna inda ta sanshi, Dad yayi musu introducing juna kan itace sabuwar matar da ya aura 4months back sunanta Kulthum, su kuma ya nuna Abu yace "wannan shine mijin Hauwa Aliyu, wannan kuma d'an uwanshi ne Mustapha", sai lokacin ta tuna inda ta sanshi, duk d'akin Ajiddeh hotunan shine hatta gaban wayarta hotunanshine, da murmushi suka gaisa, Dad ya karb'i riganshi yace "Sai su shiga daga ciki, ni inada meeting, yanda kukayi duk ka sanar dani Aliyu", ya Amsa mishi da Insha Allah da yi mishi fatan a dawo lafiya, a d'akinta Aunty Kulthum ta tarar da ita kwance duk ta rame tayi duhu, kamar ba ita bace ba wannan Ajiddeh sarkin gayu da d'osana lipstick ba, gashin nan ma da yake shan gyara duk ya kad'e, wutan d'akin Aunty Kulthum ta kunna tana mai k'iran sunan Ajiddeh An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels