Downloaded from GNOVELS.COM.NG This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG For feedback and support Facebook : https://facebook.com/gnovels Twitter : https://twitter.com/gnovels Telegram : https://t.me/gnovels 💫GABA DA GABANTA 💫 Page1 Cool ce! Free book ne, Comment kawai nake buƙata please, if not zanyi abunda bakwa so 🌝 Typing ba kullum ba, sai an ganni kawai. Ƙirƙirarraren labari ne, ban yi shi dan cin zarafin wani ko wata ba. Wannan rubutun mallakina ne, ban yadda a juya shi ta kowacce siga ba sai da izinina, kuma ban yarda a sɗora mini shi a kowane website ba sai da izinina. BISMILLAHIRAHMANNIRAHIM Dattijo ne wanda a ƙalla zai kai shekaru hamsin, zaune akan benci hannunsa riƙe da 'yar ƙaramar radio, yana saurara. Wata Haɗaɗɗiyar mota ce ƙirar Annoconda, aka kwararo dogon layin da Ita, wanda gudun da motar take ta haddasa tashin wata 'yar ƙaramar guguwa. A ƙofar wani makeken gate motar tayi birki, aka fara wani irin horn, sai kace yaƙi. A gigice ya yasar da radiyon da ke hannunsa, ya miƙe a zabure ya nufi gate ɗin, yana gaganiyar buɗe shi. Yana buɗe gate ɗin, aka turo hancin motar, zuwa wani sashi na gidan. Wata matashiyar budurwa ce ta fito daga Motar, gata nan dai kamar bata cin abinci, ban da yanayin jikin ta da kuma kayan da suke sanye jikinta, ba ka ce mace bace, saboda tsabar rama, sai dai fatar jikinta za ka kalla ka gane 'yar hutu ce, da ga ita sai doguwar rigar material, da hula a kanta tana sanye da wani uban takalmi me shegen tsini. Ta nufo gurin da dattijon nan yake kokawar maida gate ɗin ya rufe tsigil- tsigil, tana zuwa ta ƙare masa kallo sannan tace "wai kai dan Allah wani irin mutum ne? Kai ta abu kamar mara jini a jiki ko wanda baya cin Abinci? Duk Abincin da kake ci kamar gara amma ba ka da wani Amfani iye?, wallahi daga yau na kuma dawowa, ka barni a waje ina horn sai na tatala maka rashin mutunci, aikin banza ni ban ga amfanin ajiye ka a gate ɗin gidan nan ba, Daddy ya nace lallai sai kai za kai gadi" Shiru dattijon ya yi, ya sunkuyar da kai, yana jin yadda Yarinyar ke surfa masa fitsara, 'yar da ba ta fi 'yar cikin sa ba. Ta buɗe jakarta ta ɗakko dubu uku ta zubar da ita a ƙasa, ta ce "gashi nan ka ɗauka ka siyo mini Irish, za'a dafa mini, na store ya ƙare" Cikin girmamawa ya duƙa ya ɗau kuɗin yace "ranki ya daɗe sai dai ban gane me ki ka ce in siyo ba" Ta kalleshi a wulaƙance sannan ta ce "Kai abun naka ma ya yi maka yawa, to dankali nake nufi, kai Allah ya rabamu da rayuwar ƙauye rayuwar jahilci" Bace mata uffan ba, ya juya ya fara tafiya, ita ma ta nufi hanyar shiga cikin gidan. Wani ɗaki ta shiga cikin muryarta ta iyayi take faɗin "Mummy, Mummy" "Na'am har kin dawo?" "Eh na dawo, ina wannan yaran suke?" "Suwa kenan?" "Maids ɗin nan mana" "Suna sashin su" "To na bawa wannan tsohon kuɗi ya siyo mini Irish, dan na gidan nan ya ƙare, ni kuma shi nake son ayi min fatensa da dafaffen ƙwai in yi lunch da shi" Mummy ta ce "shikenan, Allah sa kar ya yi miki shirme" "Wallahi kuwa, ni wallahi da za'a bi ta tawa kawai a sallami mutumin nan, shekara da shekaru ya ci abun da ya ci ai, Amma Daddy ya dage lallai sai shi ze din ga gadin nan, dan Allah Mummy ki ba shi shawara a canza tsohon nan" Zare ido Mummy tai tace "ke Fadila rufa mini Asiri ina zaman zamana, ba ruwana" Ɗan tura baki ta yi, sannan ta ce "Any way, bari in je in kwanta dan na gaji sosai, idan ya kawo sa karɓa, ayi mini fatensa a saka yaji sosai, sai a dafa mini ƙwai guda uku a ɗora a kai ". Mummy ta ce "Ina fatan kin gaya musu da kan ki?". Fadila tace "Ai ni ƙarasawa kitchen ɗin ma wahala zai bani, ni dai kya gaya musu". Ta ƙarasa Maganar tare da juyawa, ta bar ɗakin. Tana zuwa nata ɗakin, ta jefar da takalmanta a tsakar ɗakin, ga gurin ajiye jakunkuna, amma ta yi jifa da ita wani gurin, ta cire hular kanta ta yar a ƙasa, ta haye kan ɗan matsakaicin gadonta tana hamma, tare da yin miƙa". ******* Zaune take a gaban murhu, tana tura busassun kararen tafasa, sai uban hayaƙi ne yake tashi, sai fifita wutar take da wani ɗan ƙaramin murfin bokiti, tana jan majina, ga idanunta sun yi jawur saboda yajin hayaƙi. Can da ƙyar wutar ta kama, a hankali ta furta "Alhamdilillah" ta sake gyara zaman tukunyar da ke kan murhun. Sai da ta tabbatar wutar ta kama sosai, sannan ta miƙe ta tattare duk tarkacen da ta tara a gurin, ta gyara gurin, ta bar iya murhu da kararen da ke cikinsa. Ta koma ta ɗakko garin masara a cikin buhu, da ƙwarya da rariya, ta samu guri ta zauna akan tabarmar kabar da ke shimfiɗe a ɗan ƙaramin tsakar gidan, ta fara tankaɗe. Wata farar mata ce ta fito daga wani ɗaki, hannunta riƙe da carbi, take faɗin "Masha Allah, yarinyar kirki wutar ta kama kenan?". Shiru tayi ba ta amsa ba. "Ke Amina magana fa nake miki". Firgigit ta dawo daga tunanin da take, ta fara kokawar kwance buhun garin masarar nan. Matar tace "Amina, wai tunanin me kike yi haka ne?". Wadda aka kira da Amina, ta yi ajiyar zuciya tace "Inno, Wallahi tunanin jarrabawar placement ɗin mu nake yi". Inno ta taɓe baki tace "Ai sai ki yi tayi, wannan bokon ko ita ce karatun shiga aljanna yaci ace kin haƙura haka". "Inno, dan Allah ki fahimce ni, ina matuƙar son karatun nan ne, dan Allah ko rance ne, ki aro kuɗin nan, in biya jarabawar nan, kafin Baba ya turo kuɗi". Inno ta ce "ba abunda zan aro Wallahi, shegiyar boko da bata da wani amfani, kin yi abun da ki ka yi, sai ki haƙura haka, ki dawo ki yi Aure, amma ana ta ƙananun maganganu akan ki a garin nan, saboda baban ki ya ɗaure miki gindin wani wai sai kin yi boko, har yanzu banda tarkacen takardu, ba uban da ki ka ajiye a bokon, shekara da shekaru kina galmashura a titi yawon boko, kullum sa dai ki kawo takaddun banza ki ajiye. Ni na kusa ɗakko buhun takardun ma, in yi makamashi da shegu kowa ma ya huta". Ba tare da gazawa ba, Amina ta kuma cewa "to dan Allah Inno, ni ki bari in rubuta wasiƙa a kaiwa Baba, ya taimaka mini, ya aikon da kuɗin in biya jarrabawar, tun da ba zaki biya mini ba". Inno tace "Ke Yanzu ya turo da kuɗi ai muna da tarin buƙatun da suka fi na wannan bokon banzar ta ki amfani, ba wani kuɗi da zan bari ki kai wata makarantar boko". Amina ta ɗan tura baki tace "Inno dan Allah ki dena cewa bokon banza, Wallahi ilimi yana da matuƙar mahimmanci ga rayuwar 'ya mace". "Dalla rufe mini baki, mahimmancin me? Mu da ba muyi bokon ba mutuwa mu kayi? Ko kuwa wani abu ya same mu? Ni yi sauri ki yi ki gama mini aikina, kije wancan tijararren ƙanin uban naki, yace kije ki kaiwa matarsa Niƙa". Take Amina ta tsuke fuska tace "ba in da zani, 'ya'ya nawa ne a gidansa, amma ni aka mayar kamar jaka, in yi aikin gidanmu, na gidansa sai naje na yi musu, Wallahi ba zani ba, idan na gama girki ruwa zan ɗebo mana". Inno ta ce "Ni dai ba ruwana, kin san halinsa, kar ya zo yana mana ihu a cikin gida". "Yayi da wata ba dai da ni ba" Amina tai maganar tana hura hanci. *********** "Ke! Meye sunan naki ma? Ina Abincina da nace ku girka mini?". Wadda aka yiwa kiran wulaƙancin, ta ɗan risuna tace "Anty ai ba'a kawo dankalin ba" "What? Kamar yaya?" "Eh, Hajiya tace Baba Hassan zai kawo dankali, mu karɓa mu girka miki, amma be kawo ba". "Yanzu duk wannan yunwar da nake ji, ba'a kawo dankalin bama, balle in saka ran a dafa a bani, wato yunwa ta kasheni ba shi da asara ko? Lallai wannan an yi tsohon kawai". "Kaiii, Fadila ya ne? Tun daga ɗakina ina jiyo muryarki kina faɗa, ke da waye ne haka?" Tai maganar tana ƙarasowa cikin falon. Fadila kamar za ta yi kuka tace "Mummy, kinga tsohon nan ko? Tun da na dawo fa na aike shi, saboda yunwar da nake ji, amma wai haryanzu be dawo ba" tai maganar ƙwalla na taruwa a idonta, saboda ɓacin rai. "Sorry sweetheart,yi haƙuri a kawo miki ko custard ne ki sha, kar ki zauna da yunwa, ni kaina lamarin tsohon nan na ƙular da ni, amma kiyi haƙuri". Haka ta dinga rarrashin Fadila, kamar wata jaririya. Kaɗan ta sha Custard ɗin, ta nemi guri ta kwanta a kan kujera tana chatting, Matar gidan kuma ta maida hankalinta kan kallo. Sallama ya din ga kwaɗawa a ƙofar falon, amma daga Fadila har mahaifiyarta, babu wanda ya iya amsawa. Hakan ya sa shi shigowa, da uban buhu a kansa, a zatonsa ba kowa a falon. Yana shiga yai kiciɓis da Fadila, da babarta a falon, wanda hakan ya haddasa masa faɗuwar gaba. Ya dake tare da faɗin "Hajiya sannunku da gida, nace dan Allah dan Annabi kiyi haƙuri, Wallahi na sha wahala sosai kan in samo saƙon naki, dankali yayi wuya, kiyi haƙuri dan Allah". Takaici ya hana Fadila Magana, sai wani uban tsaki da ta ja, ta gyara kwanciyarta. Ganin ba ta da niyyar Magana, ya sa ya miƙe ya kuma sunkutar buhun, zai yi ciki da shi, har ya kai ƙofar da zata sada shi da kitchen, A sukwane Fadila tace "Kai zo nan, zo da sauri". Ba shiri ya juyo cikin hanzari, ya dawo falon. "Wane irin dankali ka siyo ne?" Tai maganar tana kallonsa cike da masifa. Yace "ranki ya daɗe dankali ne dai da kika ce". "Oya kwance buhun nan, in ga wane iri ne?". Ba musu ya sunkuya, ya kwance buhun, ya zura hannu ya ɗakko wane irin murgujejen dankalin Hausa, jikinsa duk ƙasa, kamar a jefi mutum da shi yana nunawa Fadila. "Innalillahi, meye wannan? Nice zanci Wannan abun? Mummy kalli abunda ya siyo, ni na taɓa cin wannan abun ne?". A dirirce yace "hajiya ai shine dankalin". "Shut up please, ba Irish nace ka siyo mini ba? Banda jahilci i even repeat myself, irish potatoes, kawai sai ka kawo mini wannan abun? Is not late for you, yakamata ko yaƙi da jahilci ka je kayi, ko ka dinga gane abubuwa, kar ka yadda tsufa ya ƙarasa riskarka cikin jahilci. And Carry that rubbish and leave my view, before I open my eyes, ka ɗauka kaje ka ci, wannan abincin yunwa ba zan iya ci ba, ka tashi ka bani guri" Kalmar Jahilci, ta fi komai ɓatawa Baba Hassan rai, tare da tsaye masa a wuyansa, wani irin zafi da raɗaɗi ya dinga ji a zuciyarsa, duk da kasancewar sa mutum mai haƙuri, amma yau ya ƙulu, tabbas ba dan yana duba wasu abubuwa ba, da tuni ya bar aikin nan, amma maigidan mutum ne mai alkhairi da karamci a gareshi, kuma idan ya bar wannan aikin be san wanne ze yi ba. Haka nan ya tashi, ya ɗau buhun dankalin nan, ya baro falon zuciyarsa a cunkushe, yana jin kamar yayi kuka, amma ya danne, saboda be san me hawayen na sa ka iya haifarwa Fadila a rayuwarta ba. Fadila kuwa saboda tsabar ɓacin rai, sai da tayi kukan baƙin ciki, saboda yadda tsohon ya ɓata mata lokaci, ga kuma yunwa tana ji, amma ba yadda ta iya. ******* Tana zaune a ajinsu, wanda galibi 'yan ajin nasu, 'yan wasu ƙauyukan ne, amma daga ƙauyensu su biyu ne suke zuwa Makarantar haryanzu, sauram duk an musu Aure, wasu tun a primary ma. Abun duniya ya ishi Amina, ta rasa yadda za ta yi ta samu wannan kuɗaɗen, ta biya kuɗin jarrabawar nan. Ga lokaci yana ta ƙurewa, idan aka riga aka yi jarrabawar nan babu ita, shikenan karatunta ya koma baya. Duk yadda za tayi ta samu kuɗin nan ta yi, amma ba ta samu ba, gaba ɗaya dabararta ta gama ƙarewa. "Amina Hassan, ki zo inje Malam Lawan" cewar wata ɗaliba da ta zo ta tsaya a kan Amina. Amina tace "to ina zuwa". Sannu a hankali ta tashi, ta bar ajin, jikinta duk a sanyaye, damuwa ta hanata sukuni gaba ɗaya. Sallama ta yi a Staff room, ta tarar da Malam Lawan a zaune shika ɗai. Ta durƙusa ta gaishe shi, ya amsa Sannan yace "Amina, yaya haryanzu shiru ba ki kawo kuɗin jarrabawar ki ba, ga lokaci yana ta ƙurewa, yaya ne?". Jiki a sanyaye tace "Malam zan kawo insha Allah". "To ai lokaci ne yake ƙurewa, bana son a rufe baki biya ba". Amina tace "Insha Allah, zan kawo malam". "To shikenan, Allah ya dafa". Ta amsa da Ameen, ta fita ta koma aji, tana cigaba da tunani. Duk da tsananin zafin ranar da akeyi, ba ta ji, sannu a hankali take tafiya, ita zafin ranaf sam ba ya damunta Kamar yadda biyan kuɗin jarrabawar ta ya dameta. "Aminatuu" aka kira sunanta. Tsayawa ta yi ta waiwaya, wani dogon matashi ne baƙi a gefen wata bishiya. Murmushi tayi tace "Laa Saminu, ina wuni". "Lafiya ƙalau Alhamdilillah, ya Makaranta?" "Lafiya ƙalau, ashe ka shigo garin namu?" Saminu yace "eh na shigo jiya, babanki har ya bani saƙo na kaiwa Inno ɗazu da safe". Amina tace "kashh, ina ta neman yadda zan magana da shi, kafin yayo mana aike, har an biya albashi ne?". Saminu yace "A'a, ai wata ko rabawa be yi ba, naje gaisheshi ne nace ko yana da saƙo, shine ya bani dankalin Hausa kaya guda yace a kawo muku, da dubu ɗaya". A ranta tace 'dana san za'a kawo dankalin nan, da siyar da shi a kayi, aka bani kuɗin in biya jarrabawa, dan yanzu ko me zanyi, Inno ba za ta bari a saida dankalin nan ba'. Ta kalli Saminu tace "dan Allah Saminu, ka aramini Salularka, in kira Babanmu, ina son yin magana da shi". Saminu yace "ba damuwa" ya ɗakko wayarsa, ya kira lambar baban Amina ya bata wayar. Baba Hassan kuwa yana zaune, yau tsawon kwanaki huɗu kenan, da cin zarafinsa da Fadila ta yi, amma ya kasa mantawa, ya dinga tuna lokacin da ake binsu za'a kama su a kaisu Makaranta amma iyayensu suka hana, Yanzu ga ranar ilimi. Wayarsa da ya ji tana ruri, ya ɗauka ya kara a kunnensa, tare da yin sallama. Cikin farinciki Amina tace "Babana". "Na'am Aminatu na, ya kike?". "Lafiya ƙalau Baba, munga saƙo mungode Allah ya saka da alkhairi". "Ameen Aminatu na, kuyi haƙuri ba ayi albashi bane, ya Innar ta ki?". "Lafiya ƙalau Baba, sai dai.... "Sai dai me?". "Baba ance mu kai kuɗin jarrabawa, kuma bani da kuɗi, Inno kuma tace ba zata biya mini ba" Amina ta ƙarasa Maganar Kamar za ta yi kuka. Jiki a sanyaye Baba yace "nawa ne kuɗin?". "Baba dubu huɗu ne" Baba Hassan yai shiru yace "Uwata kinga ba'a daɗe da yin wancan albashin ba, ki kai rashin lafiya na turo muku da duk kuɗin, kuma yanzu wata ko rabawa be yi ba, amma in Allah ya yadda, zan laluba, sai in bayar a kawo miki". Amina tace "to Babana, nagode Allah ya saka da alkhairi, Allah ya bani ikon yin karatu, in zama wata ka bar aikin gadin nan". "Ameen uwata, Allah ya yi miki albarka, ki gaida mini da babar ta ki". "To Baba sai anjima" ta katse wayar, ta koma gurin Saminu, ta miƙa masa wayar tana murmushi tace "Saminu ga salular, nagode sosai Allah ya saka maka da alkhairi". Saminu yace "Ameen, ki gaida gida". Daga haka,ta kuma saɓar hanyar da zata sadata da gidansu. Ko da taje gidan, ta tarar da Inno ta dafa dankalin da Baba ya aiko da shi daga birni. Amina tayi murna sosai, ko bakomai yau za su huta da cin tuwo, su ci sakakken Abinci. Tai shiru da bakinta, ba ta gayawa Inno ta yi waya da mahaifinta, akan zai aiko mata da kuɗin Makaranta ba, dan muddin ta sani, ƙwacewa za ta yi, dan bokon nan da Amina take zuwa, a wuyan Inno take. Amina na ta dangwalawa da ƙuli tana ci, tana korawa da ruwan randa mai sanyi. "Salamu Alaikum" "Wa'alaikum salam" Amina ta amsa. "Wai inji Babarmu tace ki zo, ki samo musu ruwa zasu ɗora girki". Cewar yaron da yai sallama. Amina ta kalli yaron tace "ka tambayesu nawa suka sa kuɗi suka siyoni a kasuwar bayi? Idan har ba zaku ɗebo musu ruwan ba, to ku mutu da yunwa". Inno na ɗaki tana salla, amma sai wata uwar gyaran murya take yi,kamar ba salla take ba "Eheeem, Mmm, Eheeem" kamar ta kira sunan Amina a sallar nan. Amina kuwa sai da ta dire ayar zancen da take yi, yaro ya juya ya fice. Amina tace "Inno, ba fa a irin wannan gyaran muryar a salla, a bokonmu mun karanta a littafin addini, ba'a son wani sauti ya fita idan kana salla, amma kamar za kiyi magana". "Kyaci ubanki ke da bokon, wato ki kai musu wannan aiken, salon su zo su tayar mana da bala'i a gidan nana da tsakar ranar nan ko? Wai ke meyasa ba kya gudun magana ne?". Amina tai shiru ba ta tankawa Inno ba,ta cigaba da cin Abincinta. "Salamu Alaikum, kina ina ja'ira mara kunya, har a aiko kije aike, amma kice ba zaki je ba, har da baƙar magana, 'yar banzar Yarinya da ido kamar bururin gawayi" wani mutum ne ya shigo yana surfa bala'i, yana saɓa babbar riga kamar zai fuka fuki ya tashi saboda masifa. Amina ta sunkuyar da kai ƙasa, tai shiru, ya dinga zazzaga mata masifa,a ƙarshe yace "Na fuskanci wannan bokon wofin da kike zuwa, ita ce take sawa kina yiwa Mutane rashin mutunci, naga uban da ze sake bari kije bokon, Aure zan miki kan Hassan ɗin ya dawo, tun da dama shine yake goya miki bayan yiwa mutane fitsara, Wallahi ko sadakar ki ne bayarwa zanyi, uban kowama ya huta, algunhuma me suffar munafukai". Sai da yayi ya gama ya fice, daga Inno jar Amina babu wanda ya tanka masa, sai da Ya fita sannan Inno tace "kinga abunda nake jiye miki ko? Ai gara ai miki Auren, kowama ya huta, ƙila kyayi hankali, ga abunda bakinki ya janyo miki nan" Amina tace "na fuskanci bokon nan ce tasa duk aka tsaneni, ni kuwa tunda faɗar Annabi ce Sallallahu alaihi Wasallam, yace mu nemi ilimi, ko daga nan zuwa birnin Sin ne, to Wallahi a shirye nake in ɓata da kowa. Dan kawai ina zuwa boko da na motsa sai zagi, dan me zasu maida ni baiwarsu? Kawai dan banyi Aure ba ina zuwa Makaranta kowane aikin wahala sai ya dawo kaina?, To idan ba'ai mini Aure kan Baba ya dawo ba, ni zan gudu kan ai mini Auren dole, dan Wallahi na zaɓi karatuna akan wannan mutanen". Inno ta zaro ido tace "ke Amina, ba ki da hankali, ƙannen uban naki?". "Su ɗin fa, me suka taɓa tsinana mini a rayuwa? Kullum burinsu su ganni a wahala ni da mahaifina, Wallahi aka takurani, zan tattara kayana in koma birni, in ta bulayi har in gano in da Baba yake, muyi aikin gadin tare!. Domin gyara sharhi, ko shwara 07063065680GABA DA GABANTA Page 2 By Aisha Adam (Ayshercool/Jakadiyar Arewa) (Shin kin karanta littafin DARE DA DUHU?, Wanda yake daga gamayyar alƙaluma uku, daga haziƙan marubuta uku, Zee kumurya, Nimcyluv da kuma Ayshercool, kar ku bari a baku labari, ku mallaki na mu akan Kuɗi Naira 300 kacal. *DARE DA DUHU* _Allahamdulillah Babu Abinda bright pens za su ce sai godiya a gareku. Kun amshi littafin fiye da kima. Duk cewa Fiction story amma da yawan Labarin abune na da muke fuskanta reality🌚😢_ *DARE DA DUHU* ₦300 NE Via 0116886423  Sulaiman Na'ima s union Bank. Idan katin waya ne mtn na 500 idan transfer ne ɗari uku kacal. Evidence of payment 07063065680 ko 09047871750) Amina na zuwa nan a maganarta kawai sai ta fashe da kuka. Sai kuma jikin Inno ya yi sanyi, ta kalli Amina ta ce "Amina, ta wani fannin ƙannen mahaifinki suna da gaskiya, ba abin da ya dace da 'ya mace, mai shekaru kamar ki sai zaman aure, wannan gararambar da ki ke yi a titi, da sunan karatun boko gaba ɗaya bai dace da ke ba, yanzu da za kiyi aurenki babu me binki gidanki ya ce sai kin zo kin masa wani aiki, amma ki duba maganata". Amina ba ta ce komai ba, ta cigaba da share hawayen fuskarta, daga bisani ta tashi ta saka hijjabinta, kasancewar babban gidane ɓangare-ɓangare ne a gidan, ta zagaya ɓangaren Baffa Lawan, ƙanin mahaifinta dan kai musu niƙan. Baba Hassan kuwa ya shiga tsananin damuwa da tunanin yadda zai samo Wannan kuɗin da Amina ta tambayeshi, tabbas ya na son Amina ta yi karatu me zurfi, ko bakomai ba za a yi mata gorin Jahilci ba, kamar yadda a kayi masa, har abun ya ke masa ciwo ba. Amma a ina zai samo kuɗin? Shi ne babbar damuwar sa. **************** Kallo ɗaya za ka yi mata kasan a gajiye ta ke, hannunta riƙe da wani ƙaramin bokiti, bayanta kuma wani yaro ne da kaya a kansa ya ke binta a baya. Ƙofar wani ɗan ƙaramin gida ta tsaya, shi ma yaron ya tsaya, ta sauke masa kayan kan sa, ta buɗe jakarta ta ɗakko masa Naira ɗari ta bashi, sannan ta shiga da kayan cikin gidan. Sallama ta yi ta shiga cikin tilon ɗakin da ke tsakar gidan. Matar da ke zaune akan sallaya daga cikin ɗakin ta amsa tare da ce cewa "Sannu da zuwa". Cikin siririyar muryarta ta ce "Yawwa mama, ya jikin naki?" "Jiki da sauƙi Hafsa, ya cinikin?" Ɗan ɓata fuska Hafsan ta yi ta ce "To, Alhamdilillah amma dai yau babu daɗi, dankali be ƙare ba, na dawo da sauran fal". Matar ta ce "Bakomai, ki kwantar da hankalinki, sai mu ci da ranar nan, sauran sai ayi sadaka da shi". "To Mama, bari in je in yi wanka in zo in yi salla, in ƙarasa ayyukan gidan". Mama ta ce "Ai na gama komai ma, kiyi wanka ki ci Abincin". Hafsa ta ce "Mama, ba ki da lafiya ki kayi aikin, da kin bari na dawo ai". "A'a babu komai ai, na ji daɗin jikina Alhamdilillah". "To Allah ya ƙara afuwa, bari in yi wankan". "To shikenan" Mama ta amsa tana ƙoƙarin miƙewa daga kan sallayar. **************** Kimanin kwanaki huɗu kenan da Amina ta yiwa Baba waya akan kuɗin jarrabawarta, amma shiru bai yi mata aike ba, hakan ya ƙara tabattar mata da ba shi da kuɗin ne, ga wannan 'yan uwan na sa, suna da shi ba basu da shi ba, amma ta san ko giya ta ke sha, ba ta isa ta tunkaresu da wani batu akan makarantar boko ba. Dan sun ɗau karatun bokon 'ya mace kamar wani karatun saɓon Allah, mussaman ita da suka sanyawa ido, suna ganin mahaifinta ya bata goyon baya ta cigaba da yawon boko, ya ƙi yi mata Aure, duk sa'aninta duk sun yi Aure, dan galibi tun a sha uku wasu ake aurar da su. Ita kuwa har yanzu babu ma batun Auren a gabanta, ta ƙi bawa kowa dama balle a nemi Aurenta.   Misalin ƙarfe biyar na yammaci, Amina tana kan hanyarta ta dawowa gida da ga makarantar allo, ita kanta makarantar Allon duk babu sa'anninta, sai ƙannenta amma hakan bai dameta ba sam, haka ta ke shiryawa ta tafi makarantar allo idan ta dawo daga ta boko, ita ma a makarantar bokon ma ana yi musu ƙarin litattafan addini sosai, hakan ya sa a ilimin addini ma daidai gwargwado ta samu.    "Kula mana karki faɗi". Da sauri ta dawo da ga duniyar tunanin da ta tafi, ta kalli mutumin da suka kusa yin karo da juna. "Yi haƙuri"  shine abunda ta furta ta na ƙoƙarin wuce Mutumin. Mutumin ya yi murmushi ya ce "Aminatu, ba gaisuwa ne?" "Ina wuni" ta faɗa a daƙile, dan ba ta son doguwar magana, kowani abu da zai haɗata da shi sam. "Lafiya ƙalau,ya Baban ki ko har yanzu bai shigo gari ba?". "Eh bai shigo ba". "Yawwa Amina, ni na gode Allah ma da yasa muka haɗu Yanzu, Amina ya Maganar mu ta kwanaki da na taɓa yi miki ne? Kinga yanzu lokacin kaka ne, da 'yan kuɗaɗena a hannuna, anyi mini girbi amfanin gona yayi kyau sosai, ki bani dama inje in ga babanki ayi Maganar Aurenmu". Ta kalle shi, fuskarta babu walwala ta ce "Idan ka Aureni kakar kuma ta wuce fa? Da me zaka riƙeni?" Ta yi maganar tana watsa masa wani mugun kallo. Mutumin ya gyara tsayuwarsa ya ce "Amina, kamar ba ki san waye ni a garin nan ba, ina da tarin gonaki da dabbobi, wanda ke kanki kin san ni ba talaka ba ne, yanzu haka wani daga cikin amfanin gona da na siyar, baki ga kuɗin da na sake tarawa ba, noman bana ba abin da zamu ce da Allah sai godiya". Amina ta yamutse fuska ta ce. "To ina ruwana da kuɗinka? Kuɗin da ba cib ake yi ba, kamar yadda na gaya maka a baya, yanzu ma zan maimaita maka ne, ni ba zan iya Auren ka ba, ka mini tsufa, duk garin nan ba wanda bai san ka akan auri saki ba, duk shekara lokacin kaka, sai ka yi Aure ka saki wasu, 'ya'ya a gidanka kamar babu me su dan yawa, sunata gararanba a gari, ba kulawa, nima haka ka ke so ka Aureni ka sakeni da 'ya'ya? Dan Allah ka yi haƙuri, ka ga a cikin 'ya'yanka ma akawai ƙawata ai ana barin halak da kunya ma. Ka dinga duba makomar wadda zaka aura, da tarin 'ya'yanka, sannan ni karatuna shine ya dameni ba aure ba a yanzu, dan haka dan Allah ka ƙyaleni". Galala ya bi Amina da kallo, be taɓa zaton tana da baki haka ba, duba da ƙarancin shekarunta. "Ke Yanzu kin gwammace ki tsufa a gari, ba kiyi aure ba? Kuma aike zan kashe miki kuɗi sosai, sai gidan da kike so zan sai miki, ba a cikin iyalina zan haɗaki ba". "In dai Auren irin ka ne, da shi gara babu Wallahi, ni ka ga tafiyata ma" ba ta kuma saurarsa ba, ta tafi ta bar shi a gurin a tsaye cike da takaici. ************** Mummy ce ta fito Falo, cikin wata dakakkiyar shadda ruwan toka, ta sha stone work, wuyanta zuwa hannunta duk gold ne, hannunta riƙe da mayafinta da jakarta. A falo ta tarar da wata mata da yara guda biyu, kai da ganin matar ka san a wahala take, saboda yadda suke sanye da kaya tamkar tsumma, saboda koɗewa. A wulaƙance Hajiya Zainab, wato Mummy ta bisu da kallo, ya yin da suka risina suna gaisheta. Ba ta amsa ba, ta ce "Lafiya daga ina?" Matar ta risuna ta ce "Hajiya baki gane ni ba? Azumi ce maƙociyarku ta nan bayan layi". Mummy ta sake ɓata fuska ta ce "Ohhh, sai yanzu na gane ki, ke ɗin ce kullum ƙara lalacewa ki ke kina ƙara muni, lafiya kuwa?" "Hajiya taimakon nan dai da ki ka saba, shine na sake zuwa yau ma a taimaka, Wallahi marayuna ne yau kwana uku ba abin da na iya ba su suka ci, su masu sickler ga ciwo ya tashi, ga babu Abinci, na buga na buga na rasa yadda zan yi, shine na ce bari in zo don Allah ko ƙanzo ne ki taimaka ki bani in ba su" ta ƙarasa maganar ta na fashewa da kuka. "Ya isa ni dan Allah yi mini shiru, ku zo ku takurawa mutane, kuna wani kuka kamar ragon mayya ku a dole sai anji tausayinku, ku haifi yara kaɗan ba zaku iya ba, ku daɗi miji su yi ta kwanciya da ku kuna haihuwa, ƙarshe ko su gudu ko su mutu su barku da 'ya 'ya". Fadila ce ta fito ita kuma cikin wani tsadadden material me kyau, tana faɗin "Mummy am ready" tana ganin su Azumi a falo, ta yi turus tare da toshe hanci ta ce "Mummy Warin meye haka?, su kuma wannan mai suke yi mana haka a falo?". A wulaƙance Hajiya Zainab ta ce "Wai yau ma dawowa ta kuma yi, ta na neman taimako". "Kuma shi ne za su shigo mana falo, sai warin datti suke yi, mai yasa ba su zauna a waje ba in kin fito kya same su?" "To ya zan yi? Wannan sakaran mai gadin ya buɗe musu sun shigo". Cike da ƙyama Fadila ta ce "dan Allah ku ɗan jirata a haraba mana, wannan gaba ɗaya kun canza tempreture ɗakin kamar zan yi amai. Ke wa kuke da suna Asabe ki ke kowa? Wata a cikin ku ta zo ta sake mopping ɗin ɗakin nan, a kunna turaren wuta". Azumi ta ji haushin abun da Fadila ta yi mata, ita da babarta amma babu yadda ta iya, haka ta koma waje ta jira. Duk wannan wulaƙanci da cin zarafin, dubu biyu kacal Hajiya Zainab ta iya bawa Azumi, wanda sai da Azumin ta durƙusa tana mata godiya. Suna tafe a mota, Mummy na cigaba da mita, da nuna tsantsar ƙyamarta ga talaka, tare da nuna kamar iyawarta ce ta sa Allah yayi ta a cikin daula. ******** Abun duniya ya saka Amina a gaba, yau saura kwanaki uku ya rage, a rufe karɓar kuɗin jarrabawar su, gaba ɗaya ta sare, ta san Baba ba shi da kuɗin nan ne, dan da akwai su da tuni ya aiko mata da su. Gefe guda baba Rabi'u ya uzzurawa rayuwarta da takura, akan Lallai sai ta amince da shi, ta yadda ya aureta.    Fafur ita kuma ta ce ko maza sun ƙare, ba zata auri tsohon da bai san darajar mace ba, balle 'ya'yan da yake haifa. Ga matsin lamba na gidansu, daga ɓangaren 'yan uwan mahaifinta, na takura da aike saka ta aiki kamar baiwarsu, ga gore-gore, har da sharrin yawon banza ta ke yi a gantalin makarantar bokon da ke yi. Hakan ya haifarwa Amina shiga cikin matsananciyar damuwa, da tunani daban-daban a cikin ranta.         Baba Hassan kuwa, ya yanke shawarar kiran maigidan a waya, wato baban Fadila kasancewar ba ya gari, ya roƙi Alfarmar ko a cikin albashinsa ne, a taimaka a bashi rancen kuɗin da zai biyawa 'yarsa kuɗin Makaranta. Haka kuwa aka yi, ya kira maigidan ya sanar masa da halin da yake ciki, da buƙatar da yake da ita, ba tare da wani ɓata lokaci ba ya ce masa 'Zai kira Hajiya a waya ya sanar mata, ya je ya karɓa kawai a biya mata'. Baba Hassan ya yi farinciki matuƙa, yayi ta godiya da karamcin Alhaji Ahmad, sai dai yadda zai tunkari Hajiya Zainab da maganar kuɗin kawai yake tunani, saboda rijiya ta sha bada ruwa guga ya hana a gidan nan. Ƙiri-ƙiri mai gidan zai yi alheri ta hana, ko ya ce ayi taƙi yi, kusan duk me son wani abu agurinsa sai ya biyo ta hannun hajiya Zainab, idan kuwa ka na son abun a gurinta, sai ka ƙasƙantar da kanka tamkar bawa, ta gama wulaƙantaka kafin ka samu. AMINU KANO, INTERNATIONAL AIRPORT. Tafiya yake sannu a hankali, yana jan wata 'yar madaidaiciyar Akwati, hannusa ɗaya ɗauke da wayarsa ya kara ta a kunnensa yana tsumayin a ɗaga wayar da yake kira. A ɗan hasale ya fara Magana "Wai dan Allah kana ina ne? Na sauka fa ina sauri inje gida, ni da nasan haka zaka yi mini, da babu abun da zai sa in ce kazo ka ɗaukeni" Yana gama maganar, ya sauke wayar zuwa cikin aljihunsa, yana jan guntun tsaki. Sannu a hankali ya cigaba da tafiya, ba tsammani ya ji an ce "To shugaban masu haƙuri, ina daf da kai fa, amma ka kirani kana ta wannan masifar haka" Ya kalli Matashin da yake maganar ya ce "Dalla ware malam, kana sane ma ka shanyani kenan? Dana sani gida na yi waya azo a ɗaukeni". Matashin yayi murmushi ya ce "Kai dai can da yawarka, masifaffe kawai, bani in tayaka ɗaukar jakar". Ba tare da ya ce masa komai ba, ya sakar masa akwatin, yayi gaba abunsa. Suna tafe a mota, ba wanda yake magana a cikinsu, can ɗayan ya kalli abokin tafiyar tasa ya ce "Haba Khalil, ka ɗan yi murmushi mana, ko har yanzu fushin ne?" "Ban sani ba, ni dalla ka ƙara speed ɗin motar nan, mu yi muje gida". "Ba zan ƙara ba, in ban sauke ka a titi ka hau Napep ba ba sunana Abdul ba" Khalil ya ce "Saboda na hau motarka ka ke mini rashin mutunci?". "Eh, uban waye ya sa ka kirani? na zo na taimaka maka amma kana mini wulaƙanci". Jinjina kai Khalil Yayi ya ce "Good". A bakin gate ɗin gidansu Khalil Abdul yayi parking, ya kalli Khalil Ya ce "Mun zo sai ka sauka". "Wai a nan zaka ajiyeni?". Abdul Ya ce "Au ban maka ba? Wai kai mai yasa ba a iya maka ne? Ware Malam" "Wallahi zaka gane ba ka da wayo, zan zo har gida in maka rashin mutunci" Abdul ya ce "Rashin mutunci yau ka fara yi mini? dalla fita". Ƙwafa kawai Khalil yayi, ya fice da ga motar. Asabe ce ta shiga ɗakin Fadila, za ta gyara mata, tana gyaran tana mita ƙasa-ƙasa saboda yadda Fadila ta ke watsar da komai a ɗakin yadda ta ga dama. Hatta kwano sai ta ci Abinci ba zata ɗauke ba sai an ɗauke mata. "Dan Allah kalli ɗakin nan kamar sheƙar mahaukaciya, yarinya ta na mace amma ba ta san gyara ba, saboda tsabar sangarta da iskanci, ɗan kanfai ma, sai da ta saka ta tara sai mun wanke mata, Aikin banza kawai" haka Asabe ta cigaba da tattare shirgin da Fadila ta tara a ɗakin na ta, ta gyara ta wanke mata banɗaki, tare da wanke mata ƙananan kayanta da ta tara a cikin bokiti a banɗaki". Asabe na kammalawa ta fito falo, ta tarar da Fadila ta na kallo, a wulaƙance Fadila ta kalli Asabe ta ce "ki cewa wannan wadda ku ke aikin tare, meye sunanta Hajara kowa? Za ta bar uwarta da yunwa ne, kamar yadda ta yi mini? Ta bar ni ina jiran ta kawo mini Abinci amma shiru". Asabe ta risuna ta ce "zan gayamata insha Allah". "Kar ki kuskura ki sake zuwa gabana da wannan ƙazamin hijjabin, ba kya jin yadda yake wari ne?" Wani irin haushi ya kama Asabe, amma haka ta dake ta ce "To insha Allah" Asabe na zuwa ɗakin girki, ta tarar da Hajara na ta ƙoƙarin haɗowa Fadila Abinci, ta kalli Hajara ta ce "Ance idan uwarki ce za ki bar ta da yunwa?" Hajara ta kalli Asabe ta ce "Kamar yaya?" "Kamar yadda aka ce in gaya miki" Jiki a sanyaye Hajara ta ce "Allah ya bamu abun yi mu bar aiki a ƙarƙashin mutane marasa mutunci irin wannan, tun da na shigo gurin nan fa aikin Abincin nake" "Hmm, ke dai bari, ni kaina na gaji, da ina da wata hanyar samun kuɗin, da tuni na bar gidan nan". Haka suka cigaba da tattauna matsalolin gidan aikin nasu. Bayan saukarsa daga motar Abdul, gate ɗin gidan ya nufa, ya na zuwa ya tura ƙofar gate ɗin ya ga ta buɗe. Baba Hassan ya taso yana faɗin "Waye a nan?" "Baba ni ne" Khalil ya furta a hankali. Murmushin fuskar Baba Hassan ya faɗaɗa da yaga Khalil ya ce "Kai ne da zuwa haka ba sanarwa? Maimakon ka kira a zo a ɗauke ka". "Bakomai Baba, Abdul ne ya ɗakko ni na same ku ƙalau?". "Lafiya ƙalau Alhamdilillah, ya aikin?" "Aiki Alhamdilillah". Baba Hassan ya ce "bari in kai maka jakar" Khalil ya ce "A'a ka bar shi Baba, na gode, kayi zamanka" Khalil ya nufi cikin gidan. "Oh my God Mummy brother" Fadila ta faɗa da ƙarfi, tana maƙalƙale Khalil. Tureta Khalil yayi ya ce "Ni cikani kar ki kada ni". Mummy ce ta fito tana faɗin "Au, ashe da gaske kike, wane irin zuwa ne wannan ba sanarwa a safiyar nan, kamar korarre?" Khalil yayi murmushi ya ce "Mummy kullum idan zan shigo kuma sai na faɗa?". "Ahh ai sanarwar yana da kyau, amma dai ba wannan babur ɗin ɗan sahun ka hawo ka dawo gida ba ko? Kar kasa maƙota su mana dariya" "Mummy kenan, Abdul ne ya ɗakkoni daga filin jirgi". Fadila ta tura baki ta ce "Sai murna na ke ka dawo, amma ko kallo ban isheka ba". "To zan ɗauke ki ne ina ihu nima?" Mummy ta ce "Amma yadda ta damu da kai ɗin nan, ai yakamata kaima ka nuna mata ka damu da ita". Khalil ya ce "waye zai damu da wannan fitsararriyar? Bari in tafi ɗakina in ɗan watsa ruwa in huta". Mummy ta ce "Bari a saka masu aikin nan su gyara maka, na san yayi ƙura, tun da saukar safe kayi, akwai sauran kayan karin kumallo, sai ka karya" Ya ce "Ok shikenan". Ya tashi ya tafi dining, ya zuba abinci yana ci, Fadila sai surutu ta ke masa". Zuwa ƙarfe huɗu na yammaci, Khalil ya shirya cikin ƙananan kaya ya fice, da ƙudurin tafiya gidan su Abdul ya je ya ƙare masa rashin mutunci. Yau kwana guda, da Baba ya roƙi Alhaji Ahamad kuɗin da zai biyawa 'yarsa kuɗin jarrabawa, kuma ya bashi damar ya karɓa a gurin matar gidan, amma sanin halinta ya sanya shi a fargabar yadda zai tunkare ta da wannan maganar. Amma a rashin tayi akan bar arha, dan haka ya yanke shawarar zuwa ya nemi Alfarmar, ko Allah yasa ya dace. Jiki ba ƙwari, ƙasan zuciyarsa yana Addu'a, ya tunkari babban falon gidan. Da sallama ya shiga falon, sai dai duk da girman nan nasa da shekarunsa, baya hana shi shiga fargaba, idan har yayi tozali da Fadila, saboda gudun tozarci da wulaƙanci, kamar yadda ta kasance yanzu, ya tarar da ita hakimce a falon tana aikin na ta, na danna waya wanda a shi tafi ƙwarewa, danna waya kallon talabijin kai lomar Abinci sai kuma bacci da tarin rashin mutunci. "Barka da yamma ranki ya daɗe" Baba yayi Maganar yana risunawa. Ba ta ɗago ta kalleshi ba ta amsa sa da 'Yawwa'. Ya ɗan yi shiru sannan ya ce "Dan Allah hajiya fa". "Tana sashinta". 'Dama Alhaji ne ya aiko ni gurinta". "Sai ka zauna ka jirata, sai ta fito". Bai ce komai ba, ya rakuɓe a falon, yana rarraba ido. Fadila ta kara waya a kunneta tare da faɗin "Uwar bacci, tun ɗazu na ke kiranki a waya, amma shiru ba kya ɗagawa, dama ce miki zan Brother ya shigo gari fa, gara ki shirya ki bayyana". "Girl are you serious?". "Amma kin san bana miki wasa a irin wannan lamarin ko". "Wow, Alhamdilillah aikuwa zaki ganni yanzun nan" suka yi shewa a tare, sannan suka yi sallama. Baba Hassan tun yana zaman da marmari, sai da ƙafafunsa suka yi sanyi, ya gaji sosai, dan a ƙalla ya kai awa guda a zaune. Ba tsammani sai ga Hajiya Zainab ta fito, ita ma ɗauke da waya a kunnenta. Ta zauna ta cigaba da wayarta, ba tare da ta saurari in da Baba Hassan yake zaune ba, hirar kasuwancinta kawai take yi, tare da ambaton Manyan kuɗaɗe a cikin wayar. Sai da ta ƙare wayarta sannan ta kalleshi ta ce "Malam lafiya ka shigo mini falo ka ƙwafe haka kamar ana zaman fada?". Baba Hassan ya gyara zamansa ya ce "Amm, dama gurinki na zo Hajiya, Alhaji ne ya aiko ni". "Ya aiko ka, ya ce me?" "Dama na kira shi a waya ne, yarinyata zata zana jarrabawa, bani da kuɗi, shine ya ce in zo in karɓa a gurinki". "Kai kuwa malam Hassan, yakamata ka dinga jin tsoron Allah, yaushe aka baka albashi har da zaka dawo ka ce ga zance ga magana?" Cikin rauni Baba Hassan ya ce "Dan Allah Hajiya ki taimaka, ni ko rance ne, bana son karatun 'ya ta ya samu naƙasu, idan ya so sai a cire a albashi na". "Allah wadaran halin talaka, sam ba ku da godiyar Allah, mutum ko naman jikinsa ya ke yanka yana baku ba zaku gode ba. To ni bani da cash a hannuna, sai ka haƙura sai zuwa lokacin da aka ɗakko mini kuɗi a banki". Ya sake duƙawa ya ce "Hajiya ki taimaka, za su rufe karɓar kuɗin ne". Fadila a ƙufule ta ce "wai baka ganewa ne? Babu kuɗi a hannunta Yanzu, amma sai magiya ka ke". Baba Hassan ya ce "to shikenan Hajiya, Na gode" ya tashi jiki a sanyaye ya bar Falon. ******** Zuwa yanzu Amina ta gama fidda rai da samun kuɗin da zata biya na jarrabawa, dan yanzu haka tana zuwa makaranta ne kawai, kafin wanɗanda suka biya kuɗin jarrabawar su fara. Kamar kazar da ƙwai ya fashewa a ciki, haka take tafiyar, tana ƙoƙarin shiga gida ta hangi Kawu Bala, a ƙofar gida yana alwala, kai da ganin alwalar ta sa kasan jahilci ya samu gindin zama a tare da shi, saboda yadda watsa ruwan alwalar nan ko ta ina. Tana ƙoƙarin durƙusawa ta gaishe shi cikin masifa ya ce "Ke Amina zo nan". Ba musu ta zo ta durƙusa ta ce "Gani kawu". "Da ga gidan ubanwa ki ke?". "Daga makaranta" "Yawon barbaɗa da ta zubar ba?" Kallon Kawu Bala tayi, tare da jin haushin mummunar kalmar ta zubar da ya jinginata da ita. Ya kalleta ya ce "Ina son sanin dalilin da yasa, Malam Rabi'u ya nuna yana sonki, amma dan iskanci ki ka yi masa rashin mutunci". Ta ɗan yamutsa fuska ta ce "Kawu, ta yaya zan iya Aurensa, mata nawa ya aura ya saka a garin nan? Kalli yadda yaransa suke babu cikakkiyar kulawa, idan na Aureshi yayi yaya dani? Kuma ban fa gama Makaranta ba har yanzu". "Kinga idan na kuma magana kika yi mini zancen bokon nan, saina karairaya ki, shashasha mara kan gado, na fuskanci akan bokon nan kike wannan iskancin, na fuskanci a can suke hure miki kunne, to ba zai yuwu ba, ubanki ya tsallake ya tafi nasa guri ya bar mu da ke, ke kuma ki ɗakko mana abun kunya ba, saboda wata boko ba, dan haka daga yau na kuma ganin kin je makarantar boko, Wallahi sai na saɓa miki kin ji na gaya miki. Kuma kiji da kunnenki, zamu karɓi kuɗin Auren Malam Rabi'u, ba zaki cigaba da gandamewa a gida ba, sa'oinki na gidan Aure suna neman aljanna, ke kuma kina tamɓele a titi da uwar jaka da sunan boko, shegiyar bokon da ke ba kuɗi a ke baki ba sai wahala, da wannan wahalar banzar gara in ba zaki yi Auren ba, ki shiga cikin maza a dinga zuwa da ke gona kina noma". Tuni hawaye ya wankewa Amina fuska ta ce "Dan Allah kawu kayi haƙuri, ku bari in ƙarasa makaranta, ko ina gamawa ne sai in yi Auren, in ya so ku aura mini wanda ku ke so, amma banda Malam Rabi'u dan Allah". "Au ke zaki faɗi abunda ki ke so ayi?, ai kuwa ba ki isa ba, ko Hassan ubanki bai isa ya ja da maganata ba balle ke, tashi ki bani guri, Allah ya ƙara nuna mini kin fita daga cikin gidan nan da sunan wata makaranta, wuce ki bani guri, da ido kamar gujjiyar mayu". Cikin kuka Amina ta shiga cikin gida, kai tsaye ɓangarensu ta wuce, ta tarar da Inno tana surfe. Sakin taɓaryar Inno ta yi, ta nufo in da Amina ta shigo tana kuka, tare da faɗin "Ke Amina lafiya? Waye ya rasu kike wannan kukan?". Cikin kuka Amina ta ce "Kawu Bala ne wai ya ce kar in sake zuwa makarantar boko, wai Aure za suyi mini". Tsaki Inno tayi ta ce "Shine za ki shigo kina mini wannan uban ihun, bokon banza da na wofi, matsa daga kusa da ni kar in makeki". "Haba Inno, kema haka zaki ce? Yanzu kin yarda su aura mini Malam Rabi'u baban su Furera?" Zaro ido Inno tayi ta ce "Malam Rabi'u kuma? Wannan mara mutuncin?" "Shi fa, kawu Bala ya ce wai za su karɓi kuɗinsa na Aurena". Jiki a sanyaye Inno ta ce "To Amina kiyi haƙuri, kin san duk gidan nan babu wanda yake musu da Kawu Bala, ciki kuwa har da mahaifinki, shi yasa na so kafin su farga su yanke makamancin wannan hukuncin, ki fitar da mijin Aure, amma yanzu lokaci ya ƙure Amina, kin san tun da ya waiwaye ki ba wanda ya isa ya sanya shi canza Magana". Amina ta ɗora hannu a ka, ta zunduma ihu ta durƙusa a gurin ta na faɗin "Wallahi idan aka aura mini mutumin nan an gama da rayuwata, sunana bazawara, dan Allah ku ƙyaleni in yi karatuna". Inno ta ce ki rufa mana Asiri, kar ki sa su ɗauka wani abun ne, ki sa su shigo su yi mana tijara". Miƙewa Amina tayi ta shige ɗakinsu, tana cigaba da kuka har cikin ranta. ******** Tamkar wasu taɓaɓɓu haka suke ta shewa a falon. Wata siriyar yarinya ce Kamar Fadila, cikin skirt high west, da wata body hook, sai hula a kanta, ta yi simple make up. Hatta yanayin rawar kanta da iyayinta irin na Fadila ne. Dama hausawa suka ce, sai hali yazo ɗaya ake abota. Fadila ta kalli ƙawar tata ta ce "Yusra kin ga yadda ki kayi kyau kuwa? Ni kaina na yaba, ina ga shi wanda aka yiwa kwalliyar?". Yusra ta ce "Girl brother nan naki sai a hankali, Allah ya sa in ishe shi kallo". Fadila ta ce "dalla kar ki damu, zai yaba haba sai kace ba namiji ba, dole ya ƙyasa, yanzun nan zai shigo, muje ɗakina in ƙara gyara miki kwalliyar nan, a ƙara powder da turare". Haka kuwa aka yi, suka shiga ɗakin Fadila, da yake Fadila gwanace gurin kwalliya da gyaran jikinta, tsaftar muhalli ce komai sai dai ayi mata. Yusra ta kuma fitowa ta yi ras da Ita, suka dawo falo suka cigaba da hira. Suna tsaka da hirar ne, suka ji shigowar mota gidan, Fadila ta leƙa ta window, da sauri ta dawo tana faɗin "Girl, gashi nan, shine ya dawo". Cikin hanzari Yusra ta sake feffesa turare, da sake gyara zama. Khalil ne ya shigo falon, hannunsa riƙe da wayarsa da makullin mota. Yana shigowa gaba ɗaya Yusra ta rasa nutsuwarta, saboda tsananin kwarjinin da Khalil yake da shi. "Ina wuni Brother" Yusra ta faɗa cikin fargaba. "Yawwa sannunki" ya amsa yana ƙoƙarin shigewa. Fadila ta ce "Brother, baka gane ta bane? Yusra ce fa". Khalil yayi murmushi ya ce "Na ganeta mana, ai nace mata Hi ko?". Yayi Maganar yana hararar Fadila. Ba Yusra ba, Fadila kanta ta ji haushin yadda Khalil y nunawa ƙawarta halin ko in kula, duk da wannan tarin hoda da turare da ta saka saboda shi. Gyara sharhi ko shawara 08081012143 Ayi following account ɗina a Arewabooks@ Ayshercool7724 Da kuma Watpad Ayshercool 7724 Share Please 🙏GABA DA GABANTA        Page3               By Aisha Adam (Ayshercool) (Shin kin karanta littafin DARE DA DUHU?, Wanda yake daga gamayyar alƙaluma uku, daga haziƙan marubuta uku, Zee kumurya, Nimcyluv da kuma Ayshercool, kar ku bari a baku labari, ku mallaki na mu akan Kuɗi Naira 300 kacal. *DARE DA DUHU* _Allahamdulillah Babu Abinda bright pens za su ce sai godiya a gareku. Kun amshi littafin fiye da kima. Duk cewa Fiction story amma da yawan Labarin abune na da muke fuskanta reality🌚😢_ *DARE DA DUHU* ₦300 NE Via 0116886423  Sulaiman Na'ima s union Bank. Idan katin waya ne mtn na 500 idan transfer ne ɗari uku kacal. Evidence of payment 07063065680 ko 09047871750) DADICATED TO BRIGHT PENS Saroro suka yi gaba ɗaya suka bi bayan Khalil da kallo. Yana shiga sashin Mummy ya dawo falo, ya kalli Fadila ya ce "Ke ina Mummy ne?" Fadila ta tsuke fuska ta ce "Ba ta nan". Ya ce "ok" Yusra ba ta gajiya ba ta ce "Yaya a dawo lafiya". "Ameen thanks" daga haka ya fice. Fadila ta ja wani uban tsaki, ya yin da Yusra ta yi shiru tana tunani. Fadila ta ce "Girl, ki yi haƙuri dan Allah, ki kwantar da hankalinki, na miki alƙawari insha Allah sai Brother ya so ki". Yusra ta ce "Till when dear? Wallahi ba zaki gane yadda nake son Yayan nan naki ba, amma kwata-kwata ya ƙi damuwa dani". "Kin san me? Kar ki damu, You know he is very classic, shi komai nasa baya son raini, shi yasa amma zamu shawo kansa very soon". Yusra ta ce "Shikenan, Allah yasa, bari in wuce gida". Fadila ta ce "Muje in raka ki" suka fito harabar gidan, suna cigaba da tattauna yadda za su ɓullowa lamarin Khalil. **************** Ta gama shirinta tsaf, cikin dogon hijjabinta, sai dai ta janyo kujerar tsugono ta zauna, ta zubawa kayan gabanta ido. "Hafsa, ya har yanzu baki tafi ba, ko almajirin da zai taya ki ɗaukar kayan ne bai zo ba?". Hafsa ta ce "Mama, jarin mu ne yayi ƙasa, ana samun ciniki Alhamdilillah, amma kin ga a ciki muke komai, har magungunanki a ciki muke siya, kuma jarin ba ƙaruwa yayi ba,  itace ma bashi na karɓa, mai ma kuɗin rabi na bayar aka bani, na cika sauran daga baya idan nayi cinikin yau". Mama tayi ajiyar zuciya ta ce "Na sani Hafsa, ni babban abun da ya dameni, shi ne mu zamana bamu da taro ko sisin da muke juyawa, amma insha Allah komai zai wuce, watarana sai labari, Allah ya kawo dalilin da zai rabaki da wannan siye da siyarwar bakin hanyar, bana so raina ba ya mini daɗi". "Bakomai Mama, Allah ya kawo mana mafita ya baki Lafiya, dangin mahaifina abun da suka yi mana, Allah ya ninka musu" ta ƙarasa Maganar hawaye na zubowa daga idanunta, alamun tana cikin damuwa. Mama ta girgiza kai ta ce "A'a Hafsa, Allah ya shirye su kawai, ki daina kukan nan" Mama tayi Maganar tana share mata hawaye. Hafsa ta share hawayenta ta ce "Naji tsayuwar Napep a waje, bari in tafi kar in yamma, me zan taho miki da shi?". "A'a bana buƙatar komai, Allah ya tsare, ki kula da kan ki, kar ki wasa da mutuncinki". "To Mama insha Allah" ta kwashi kayan sana'arta, ta fita da su. ********** Fadila na falo tana kallo, duk tayi kaca_kaca da falon, in da suka ci Abinci ita da Yusra sun bar komai a falon, ga tarkace duk ta tara shirgi, Asabe na ta kaiwa tana komowa tana gyarawa, ita kuwa ta hakimce akan kujera tana ciye-ciye. Mummy na zaune a gefe, tana danna wayarta, tana chatting da abokan kasuwancinta. "Hmm, wai kin san me Yaya Khalil yayi mini kuwa Mummy?". "A'a sai kin faɗa". "Gaba ɗaya ya gama yarfani yau ɗin nan, mussaman na yiwa Yusra waya akan ya zo gari, ta bar abun da take ta zo gidan nan, amma kin ga da ta gaishe shi da yadda ya amsa?". Mummy ta ce "Ai ni na rasa gane kan yayan nan naki, sam ba shi da alƙibla, yarinyar tana da kirki da hankali, gata 'yar masu kuɗi, sam banga aibunta ba". "Kema dai kya faɗa Mummy" suna tsaka da hirar sai ga Khalil yayi sallama". Mummy ta amsa ban da Fadila, da ta kuma haɗe rai. Khalil ya ce "Mummy na dawo ɗazu ki bani National id card ɗina, zan cike wasu takaddu, amma ba kya nan". "Eh naje duba shagona ne na zoo road, sun yi mini waya wai wasu kayan sun ƙare". Khalil ya sauke idanunsa a kan Fadila ya ce "Yawwa, ke kuma na dawo gareki, daga yau idan yarinyar nan ƙawarki ta kuma zuwa, ki ka sa tana mini shishshigi sai na makeki a gabanta". Mummy ta ce "wai kai shikenan ba'a masa abun Arziƙi kenan? Meye laifin Yusran nan ne?". "Ba na son raini, kawai sai in fara Soyayya da ƙawar ƙanwata, dan abun Kunya? Wata bushshiya da ita ba fasali". "Kai dai ba'a yi maka abun arziƙi, ban da wulaƙanci meye laifin yarinyar nan? dan ma ka samu ance ana sonka da wannan masifar taka da zafin rai". Khalil ya ce "Dama bance ace ana sona ba, a bar ni in samo Yarinya daidai da ni, wadda ta yi karatu me zurfi mai hankali da tunani". Mummy ta taɓe baki ta ce "Ka ji da shi dai, a garin zaɓen zaka zaɓo mummuna, ni dai fatana a samo mini 'yar babban gida, kar a kwaso mini 'yar talakawa, wanda ba su san mutunci ba". Khalil ya ce "Mummy kin ga yadda ginina na Abuja yayi nisa kuwa? Tunanin yarinyar da ta dace da gidan nan nake". "A samo wadda za'a iya kai maka kayan Arziƙi dai shine fatana" Khalil ya kalli Fadila da ta haɗe rai ya ce "Ke yaushe zaku fara lectures ne?". "Saura sati biyu" ta faɗa tana cunkusa baki. "To ki maida hankali dai, dan Jami'a ba gurin zuwa ayi sakarci bane". Hararsa ta yi a fakaice, dan ya gama ƙular da ita yau ɗin nan. "Ki yiwa yaran nan magana su kawo mini Abinci na kan dining, and Abdul ya ce yana gaisheki". Fadila ta ce "Waye wani Abdul kuma?". "Ban sani ba" Khalil ya bata amsa. "Nifa ya dena wani rawar kai a kaina, me zan yi da shi?, yana lecturer mai na sama ya ci balle ya bawa na ƙasa?". "Fadila me kike cewa?" Khalil yayi Maganar a fusace. "Ai nima naga cewa kayi ba ka son ƙawata, ita da tafi wani Abdul komai, nima dan me zan so shi, kuma shima ya san ni ba kalarsa ba ce, Nasan albashinsa ko mayukana da turaruka na ba zai siya ba". Khalil zai yi Magana Mummy ta dakatar da shi ta ce "Kar ka takura ta ƙyaleta, nima ban goyi baya ba". "Amma Mummy me yasa? Naga Abdul ɗin nan abokina ne, tare muka yi School, kun san halayensa gaba ɗaya". "Kai babanka ne ya biya maka kaje karatu, shi kuma gwamnati ce ta bashi tallafi, aikin da yake ma ba babanka ne ya samo masa ba? Idan yana da kunya ai ya san Fadila ba sa'ar sa ba ce". Shiru Khalil yayi jin Mummy ta goyi bayan Fadila, amma har ga Allah bai ga aibun abokin nasa ba, kuma ya san da Fadila za ta Aure shi, za ta ji daɗi saboda yana da kirki, kuma yana matuƙar sonta, amma ya kasa gaya mata saboda yadda Izzarta take masa kwarjini. ************ Amina ce zaune a ɗaki, ta sanya langar koko a gaba, tana ta uban kuka tamkar wadda aka cewa babanta ya mutu. Inno ce ta ɗaga labulen ɗakin ta ce "Wai ba zaki daina kukan nan ki tashi ki karya kumallo ba?". Shiru Amina ta yi, ta cigaba da raira kukan ta". "Ji min 'yar abar da malam ya hana ni faɗa, ba magana nake miki ba, ai ni Kawu Balan ya gama yi mini komai da ya hanaki zuwa bokon nan". Sake fashewa da kuka Amina ta yi ta ce "Haba Inno, haka zaki ce?". "Eh haka nace, me ake da wata boko? Ki tashi ki karya ki zo ki ɗebi kayan wankin nan, ki je ki wanko mana su". Haka Amina ta tashi, ta ɗauki kokon nan ta kafa kai, babu siga sam a cikin sa ga gasarar ta yi tsami sosai, amma haka ta kafa kai tana zuƙarsa kaɗan-kaɗan. ************** Baba Hassan ya zabga uban tagumi, ya san ko ba'a gaya masa ba, Amina na can a cikin damuwa akan kuɗin da ta tambaye shi, amma babu yadda ya iya dan yayi iya yin sa, amma bai samu ba, kuma ya san da gayya Hajiya Zainab ta hana shi kuɗin nan, ba wai dan babu kuɗin ba. Yana ganin shige da ficen Khalil a gidan, amma ba zai iya tambayarsa ba, duk da ya san idan ya tambaye shi zai bashi, amma yana jin nauyin yaron sosai. Gashi ya san idan ya kira mai gidan ya ce ba'a bashi kuɗin ba, nan ma wata matsalar ce, yana gudun haɗa fitina a tsakanin ma'auratan, kuma dama shi kansa mai gidan akwai taƙama, ba ya son takura sam. Haka Baba Hassan ya din ga tunani, amma ya kasa gano mafita gaba ɗaya. ************** "Mummy wai Ina Fadila ne? Tun da na shigo ban ganta ba". Mummy ta ce "zai wuce ace tana bacci ne?". "Bacci a yanzu Mummy? Ƙarfe sha biyu da rabi fa" "To ta fito ta yi breakfast, ta koma ɗaki ta kuma kwanciya". "Amma Mummy kika ƙyaleta, da haka za'a Jami'ar?" "To yanzu dai tun da ba Jami'ar ta shiga ba, ai ka bar ta ta huta ko? Gwanin na iya, sarkin hantara da zare idanu". Girgiza kai ya yi ya ce "Idan ta shiga makaranta, wani sakarcin idan ance tayi ba za tayi ba". "Ai ni shiyasa na so babanku ya kaita ƙasar waje, kamar yadda ake kai kowacce 'yar gata, amma ya ƙi wai rawar kanta ta yi yawa, da shikenan ba ruwanta da tashin hankalin Jami'oin Nigeria" "Aikuwa tun da haka ba ta samu ba, dole ta koyo sabawa da tashin hankalin Jami'oin Nigeria, kuma ko ina aka kaita ba'a samun ilimi ta sauƙi". Mummy da ta gaji da tsarin Khalil ta ce "Jeka na ji Babana". Be kuma cewa Uffan ba ya fice. Daga gida kuwa kai tsaye gidansu Abdul ya wuce, wanda ɗakinsa ya ke jikin gidansu da banɗakinsa da komai, dan haka Khalil ba sai ya shiga cikin gidansu Abdul ba. Abdul yana zaune yana marking tes ɗin ɗalibai, Khalil ya yi sallama. Abdul ya amsa masa tare da cewa "Daga ina haka?". Khalil ya zauna ya ce "Wallahi da ga gida, ni duk garin ma ji nake ya isheni". "To sai ka tattara ka koma in da ka fito, dama ni mamaki ma na ke, kawai ka baro aikin ka ka dawo gida ka zauna". Khalil yayi murmushi ya ce "Har wani aiki ake? Ni Wallahi ginina ne ya dameni, ka san wannan Plan ɗin da muka fitar shi nake yi fa". Abdul ya ce "Kai, amma fa zai ci kuɗi da yawa". "Aikuwa yana ci sosai, amma ka san kuɗi ba matsala ta bane". "Na sani, kana ta gini ba matar Aure, kuma maimakon kayi ginin a nan, amma ka tafi Abuja" "To ba'a can nake aiki ba, Kano ina da gida, Yaushe za'a ƙarasa naka ginin ne malam Abdul?" Abdul ya yi murmushi ya ce "Abubuwa ne sai a hankali, ka san siblings ɗina, ni ke hidimar karatunsu, rayuwar sai Alhamdilillah, ga yaran Yaya Hameed da ya rasu ya bari, nine kamar babansu Yanzu, ni ke kula da su, ka ga ba zan bari su wulaƙanta ba dan ba ransa". Khalil ya yi murmushi ya ce "Allah sarki, duk faɗan da muke yi da kunna ni da ka ke wasu lokutan, Halayenka abun koyi ne Abdul, Allah ya ƙara maka Arziƙi, Insha Allah da an samu wani space ɗin aiki zamu haɗe a Abuja". Abdul ya ce "Kai Khalil, wannan aikin ma da na samu ta silarka na ke yi na ji daɗi, bani da bakin godiya, amma ka bar ni kawai, na nemi kasuwanci in haɗa". "Wallahi ba ka isa ba, dole mu tafi tare, kuma filin jikin in da nake gini a Abuja, ka kawo half ɗin kuɗin, in cika maka kawai ya zama naka". Abdul yayi dariya ya ce "Ba zaka ƙare a kai na ba, amma Allah yasa ginin da na ke a Kano ya burge Fadila, wai ni kana ma miƙa mata saƙon gaisuwata kuwa?" Jikin Khalil ne yayi sanyi amma ya dake ya ce "Malam kawai ka rabu da wannan yarinyar". "Saboda me? Ko dai ba zaka bani ita bane, saboda ni talaka ne?" "Kai haba dai, wace irin magana ce wannan, ni ba ruwana ka nemi soyayyarta kawai, zan wuce maka gaba gurin Daddy, yanzu dai ka tashi muje yawo". "Yawo kuma? Kai zaka mini aikin marking ɗin?". "Kai dalla ka dena takurawa kan ka malam, zo muje Chilling kawai". "Gaskiya ka hanzarta ka zo ka koma in da ka fito, duk ka addabeni tun lokacin da ka dawo". "Wallahi sai ka taso" Abdul ya ce "To Jarababbe ai ka bari in tashi in kintsa ko a haka zan fita?". "To kintsa mu fita". Khalil yana jin daɗin abotarsa da Abdul, iyayen Abdul talakawa ne, ƙoƙarin sa da kuma rahamar ubangiji ya sanya ya samu Scholarship, na karatu a Malesia, wanda a nan suka haɗu da Khalil, Mahaifiyar Khalil ba ta son mu'amalarsu Saboda shi ba ɗan masu kuɗi bane, amma Khalil ya nacewa Abdul. Abdul ya fuskanci Mahaifiyar Khalil ba ta son sa, dan haka ba ya son zuwa gidan sam, Khalil yana da izza irin ta yaran masu kuɗi, saboda ko ba komai ɗabi'a naso take, amma bai san yana yi ba, kuma sam baya nunawa Abdul Izzar. Babban abun da yasa yake son Abdul shine, mutum ne mai wadatar zuci, ga girmama mutane, dan idan mahaifin Khalil yana gari, wataran ya kan sai abun da yake da shi, yaje ya gaisheshi, hakan yasa shi kansa mahaifin Khalil yake son Abdul. Ganin ba yadda Hajiya Zainab ta iya ne, ya sa ta ƙyalesu suke abota, hatta motar da Abdul yake hawa, Khalil ne ya bashi. Mahaifin Khalil shine ya samarwa da Abdul aikin lecturing, ya yin da nasa ɗan ke can Hukumar Land a Abuja. Abdul ya daɗe yana son Fadila, amma ya kasa gaya mata, saboda yanayin yadda ta ke gudanar da al'amuranta. Hakan ya sanya ya gayawa Khalil yana son ƙanwarsa, Khalil ya ji daɗi, amma ya san ba abune mai yiwuwa ba, saboda yadda ahalin su ke ƙyamar talaka!. ************** Yau ta kasance ita ce ranar Fadila ta farko a Makarantar Jami'a, sai da aka sha yaƙi da ita, sannan ta tashi ta shirya da safe, tamkar wata ƙanƙanuwar yarinya. Mummy sai mita take tana in dai haka Fadila zata cigaba, Wannan karatun ba mai yiwuwa bane ba sam.   Da kanta tayi driving motarta zuwa School, sai dai ta dinga bin 'yan ajin nasu da wani irin kallo mai kama da na ƙasƙanci. Guri ɗaya ta ware, can gefe guda ta yi zamanta, ba tare da ta shiga sabgar kowa ba, sai hura hanci kawai da take yi. Malamar farko da ta shigo fara yi musu lectures, ta yi musu nasiha sosai a kan mahimmanci mai da hankali a kan karatu, da irin yanayin yadda rayuwar Jami'a ta bambanta da ta sakandare. Ba laifi malamar ta sha gayu tsaf da ita. Ajin ya haɗa da waɗanda suna kammala Sakandire suka samu gurbin karatu, da waɗanda suka shafe lokaci a gida ba a samu gurbin karatu ba, a taƙaice dai ajin ya haɗa yara, matasa da kuma dattawa. Ƙarfe sha biyu, Fadila ta ɗau jakarta ta koma gida, ba dan an gama lectures ɗin ba, sai dan yadda gaba ɗaya zaman makarantar ya ishe ta, ga warin hammata da wasu daga cikin samarin ajin suke yi, duk da wadattaciyar iska da fankoki da suke ajin, amma bai hana wasu idan suka gifta taji ba, wanda hakan ya sa ta fara jin tashin zuciya ta ce ba zata iya zama ba. *********** Kamar kullum bayan sallar magariba sannan kayan sana'ar Hafsa suka ƙare, ta tattara kayanta ta nufo gida, sai dai tun daga yadda ta ji Mama ta amsa mata sallama ta san jikin Maman babu daɗi. Cikin azama Hafsa ta shiga ɗakin tana faɗin "Mama ya naji muryarki haka? Jikin ne?". Mama dake kwance ta tashi zaune da ƙyar ta ce "A'a lafiyata ƙalau Hafsa har kin dawo" ta yi maganar tana haki. "Mama gashi kina haki, amma kice mini lafiyarki ƙalau? Bari in ɗauko miki maganinki" Hafsa ta tashi da sauri ta nufi in da take ajiyewa Mama magungunanta, Mama kuwa bin Hafsa tayi da ido, cike da tausayawa. Hafasa na duba gurin magungunan babu sai fankon ledar maganin, ta kalli Mama jiki a sanyaye ta ce "Mama dama maganin ya ƙare baki gaya mini ba?" "Bana son tayar miki da hankali ne, kuma dama kin ce jari yayi ƙasa, bashi yayi yawa, kinga dole a lallaɓa kar mu cinye jarin gaba ɗaya". "Haba Mama, ai lafiya gaba take da komai, kuɗi kona waye ai gara in taɓa  in sai miki magani, bari im je gurin Magaji, idan yana nan ya zo ya duba jinin naki, sai in taho miki da maganin". "To Hafsa, kar ki daɗe amma, kiyi maza ki dawo ga wani Abinci can na ajiye miki" Hafsa ta ce "To mama, daga nan ta fice". Kai tsaye chemist ɗin Magaji ta tafi, ta tarar ba kowa a shagon sai shi da wani abokinsa, wanda duk unguwarsu ɗaya. Tayi musu sallama suka amsa mata, ta kalli Magaji ta ce 'Magaji dan Allah so nake a duba mini awon jinin Mama, idan ya hau ne sai a bata maganinta, na dawo na tarar tana haki". Magaji ya ce "Gaskiya ina da abun yi yanzu". "Don Allah ka taimaka, bata da lafiya sosai" tayi maganar cikin damuwa. Magaji ya ce "Ashe alfarma tana da daɗi Hafsa? Ai da har gida nake zuwa ina yiwa mahaifiyarki gwajin, amma na nuna ina sonki, ba kunya kika nuna ba kya sona, kuma saboda kina da kunya shine kika kuma dawowa neman alfarma a gurina". "Ita Alfarma ana nemanta ne a in da ya dace, ana alfarma akan komai amma banda So, ban taɓa keta bulle na na nemi Alfarmar wani ba, saboda gudun ƙasƙanci sai a gurinka, kuma ka nuna mini iyakata, daga yau ka rubuta ka ajiye, idan ni Hafsa na kuma neman Alfarma a gurinka, kai mini duk cin mutuncin da ka ga dama" tana gama faɗin haka ta juya ta bar Chemist ɗin. Tana tafiya Magaji ya ce "Aikin banza, yarinya ba 'yar uban kowa ba, sai izza da girman kai, tana 'yar talaka futuk, tana suyar awara akan kwalbati, amma zan nuna ina sonta ta wulaƙantani". Abokin Magaji mai suna Nura ya ce "Nikam burgeni take, ba ruwanta da shirme da rawar kan 'yan matan unguwar nan, a nutse take". "Kai dalla ware, ba wata nutsuwa, duk buge ce, ni ban ma san tsautsayin da ya kaini cewa ina sonta ba, bayan ma 'yar mace ce, har wata nutsuwa ko tarbiyya ce da 'yar mace?". Nura ya ce "A'a Magaji, da ta yarda da soyayyarka, ba zaka kirata 'yar mace ba". Haka Magaji ya cigaba da sukan Hafsa, Nura yana karewa. Hafsa kuwa ganin kuɗin hannunta ba su da yawa, ta san ba zasu isa ta kai Mama Asibiti ba, haka ta haƙura taje wani Chemist ɗin ta sai mata irin maganinta, duk da akwai buƙatar a sake gwada jinin amma babu yadda ta iya. Khalil ne ya shigo ya tarar da Fadila tana gayawa Mummy yadda 'yan ajinsu suke, da yadda wasu suke addabar su da warin hammata. Khalil ya ce "Zaki ga warin hammata, kije ki yi musu hauka suyi miki dukan tsiya, dan ba kowa zai ɗau rashin kunya ba". "Aikuwa da na saka an kulle mini yaro kowaye ubansa a garin nan" Mummy tayi Maganar tana zazzare ido. Khalil ya girgiza kai ya ce 'To ni dai jibi in Allah ya kai mu zan koma gurin aiki". Mummy ta ce "Allah ya kiyaye hanya, dama ka takurawa 'ya ta, gashi kuma next week babanku zai shigo gari". Khalil ya ce "Allah bai yi zamu haɗu ba, ma yi waya da shi". ************** Gaba ɗaya yau Amina ta wuni jikinta babu daɗi, wanda tsabar damuwa da kuka ya haifar mata da ciwon kai, yau 'yan ajinsu suke zana paper ƙarshe babu ita, haka ta sha kukanta ta godewa Allah. Inno ta tursasa mata cin abincin dare, dan wuni tayi ba ta ci komai ba, sai kwanciya. Tana tsaka da cin tuwon ne, ɗan gidan Baffa Lawan yayi sallama ya ce "Amina kije Malam Rabi'u yana sallama da ke a waje". Amina ta ce "Ka je kace masa bana nan". Yaron ya juya ya fice. Inno ta ce "Wato ke dai Amina ba kya gudun magana ko?". "Inno to ni ya ake so in yi? Ni Wallahi ba zan iya Auren wannan mutumin ba". Suna cikin Magana Baffa Lawan ya shigo yana hayagaga yana ɗaga murya. "Wato wuyanki ya yi kaurin da za'a ce ana sallama da ke ki ce aje ace ba kya nan? Zaki tashi ki je ko sai na kakkarya ki, sakarya yarinya mara Albarka". Amina na kuka ta tashi ta Sanya hijjabinta, Baffa Lawan ya cigaba da sababi yana cewa Inno ce ke goya mata baya take rashin mutunci. "Kuma ki san da saninki, na saka gonar babanki a kasuwa, an samu mai saye gobe za muje mu karɓo kuɗin, ai miki kayan ɗaki ds su, Hassan ko yana nan ko ba ya nan, zamu aurar da ke" Ƙara fashewa da kuka Amina ta yi, ta nufi hanyar fita tana goge hawaye. Malam Rabi'u yana tsaye a ƙofar gida, yana ganin Amina ta fito ya fara murmushi, duk da babu wadataccen haske a gurin, amma hakan be hanashi ƙare mata kallo ba. "Amaryata barka da wannan lokaci, ya Mutanen gidan?". "Yanzu tsakani da Allah ka yi mini adalci kenan? Dan me zaka takura sai ka Aureni? Nace maka ba zan iya aurenka ba, ana dole ne?". Malam Rabi'u ya ce "Ai ko ba kya so na ni ina sonki, kuma wan mahaifinki ya ce ya bani ke, kuɗin Aure kawai zan kawo wani satin, kuma ba za'a sanya lokaci mai tsawo ba". Wani haushi ne ya sake kama Amina, ba ta kuma ce masa uffan ba, ta juya ta koma cikin gida tana wani tunani a ranta. *************** Ku san sati biyu da fara lectures, amma kullum sabbin ɗalibai zuwa suke yi, sai dai haryanzu Fadila ta kasa sakewa da 'yan ajin, sai wasu 'yan mata su biyu, suma dan ta ga irinta ne 'yan ƙarya yaran masu kuɗi, suma ba wani sakewa take da su sosai ba. Ana tsaka da lectures, sai ga wani matashin saurayi ya shigo, dogo ne sosai wankan tarwaɗa, yana sanye da wani yadi ash, amma yadin nan yayi haske saboda tsufa, amma ya sha guga, kansa ya sanya hula tashi ka fiye naci, sai ɗan ƙaramin asuwakinsa a bayansa, hannunsa ya naɗa shi da wani ɗan ƙaramin carbi. Sallama ya yi, wanda ya sanya gaba ɗaya hankalin 'yan ajin dawowa kansa, saboda yadda yayi Maganar Kamar cikin iyayi. Aka amsa masa, lecturer ya ce "Kai Ustaz da ga ina?". "Daga gida Malam" ya faɗa cikin girmamawa. "Gida dama yanzu ne lokacin da yakamata ka zo aji?". "A'a malam ayi mini afuwa dan Allah, Insha Allah ba zan sake ba" Lecturer ya bashi iznin ya je ya zauna. Ƙafarsa Fadila ta kalla, ya sanya takalmi soso irin na maza, takalmin duk ya cinye, ga ƙafarsa tayi futu-futu tamkar an haƙo shi daga rami. Aikuwa Fadila ta tuntsire da dariya, gaba ɗaya aka juyo ana kallonta, shima waigowa yayi ya kalleta, ya ga ƙafarsa take kallo tana cigaba da dariya, ganin abun da take wa dariya, ya Sanya wasu daga cikin ɗaliban suma yin dariya ƙasa-ƙasa, gaba ɗaya sai wata kunya ta kama shi, sai ya ji babu daɗi sam akan abi nda Fadila ta yi masa. Lecturer da ya juyo ya ga Fadila ce tayi wannan dariya, bai tsaya jin me take yiwa dariya ba ya ce ta fita ta bar ajin. Domin gyara sharhi ko shawara 08081012143 Kar a manta ayi following account ɗina na Arewabooks https://arewabooks.com/u/ayshercool7724GABA DA GABANTA AISHA ADAM (AYSHERCOOL) P4 Arewabooks https://arewabooks.com/u/ayshercool7724 Watpad Ayshercool 7724 Ko a jikinta, Fadila ta ɗauki jakarta, ta fice daga ajin. Shi kam wannan bafulatanin ustazu, ya nemi guri ya zauna, yana ɓoye ƙafarsa, dan ba ƙaramin kunya ce ta kama shi ba, a saboda dizgin da Fadila tayi masa.   Fadila kuwa gida tayi tafiyarta abin ta, hankali kwance dan tama manta da abin da ta aikata, kuma ba ta damu da korarta da malami ya yi daga aji ba, dan ita gani tayi ma ya taimaketa. ************ A 'yan kwankin nan da dangin mahaifi, suka sako Amina a gaba, duk ta rame ta yi zuru zuru, ga rashin samun damar zana jarrabawa, gashi Kawu Bala ya hanata zuwa ko ina shi da Kawu Lawan idan ba aike ba, ciki har da makarantar allo, kuma dan wani tsabar wulaƙancin, daga can cikin gidan ma, gurin iyalansu, sai a aiko taje a aiketa, ko a sata wani aiki mai wahala, duk dan a cuzguna mata a ɓata mata rai, abin duniya ya haɗu yayi mata yawa, gashi ba ta da waya balle ta kira Baba ta sanar da shi halin da take ciki, gashi su kawu sun matsa a kan lallai ko yana nan ko ba ya nan, sai sun siyar da gonarsa sun mata Aure. Abin da yake ƙara mata damuwa shi ne, bayan aikin gadin nan, da ɗan gurin da suke zaune a cikin gidan nan, to da Allah suka dogara da Wannan gona kuma guda ɗaya tal, siyar da ita na nufin tozarta Mahaifin Amina ne. "Amina, wai ke sai kin ɗorawa kan ki wata rashin lafiyar saboda wannan tunanin da kike, sannan hankalinki zai kwanta?" Cikin damuwa Amina ta ce "Ba haka bane Inno? Tunanin ne yake zuwa ko ban shirya ba". "Yo dama wani tunani ne zai tsaya jiran sai kin shirya? Na san ba zai wuce tunanin boko ba". Amina ta girgiza kai ta ce "Inno ni na haƙura da karatun boko ma, ni yanzu auren nan nake tunani bana son Auren nan sam, sai kuma gonar Baba da zasu sayar, dan Allah Inno ki saka baki, su ƙyale mana gonarmu" Buɗe baki Inno ta yi ta ce "Ni kaza! Rufamini asiri, kin san ko mahaifinki ba ya jayayya da maganar kawu Bala, balle ni 'yar karo da aka auro". "To ko ni inje in same shi, in masa maganar?, bamu fa da Komai sai gonar nan, kuma ni wallahi ba zan yadda ayi mini wannan auren ba". "Ke ki rufawa kanki asiri, kin ga Amina kiyi haƙuri ki runugumi Auren nan, tun kafin su yi miki wani sharrin, kin san kawu Bala da kaidi kamar mace" "Aikuwa a aurawa wata ba dai ni ba, dan Wallahi da raina da lafiyata ba zan auri Wannan mutumin ba, mara imani wanda bai san darajar Aure ba, mata nawa ya mayar zaurawa, ya auri mace ya saketa ita da 'ya'yanta banda 'ya'yan da ke gidansa, duk kaka sai ya saki mata ya auri wasu haka kurum a kashe mini rayuwa". "Rigimar ki tayi yawa Amina, ke ba a gaya miki gaskiya ki bi, amma ki rubutawa babanki wasiƙa a kai tasha, gara ya zo garin nan a san abun yi, ya san halin da ake ciki". Amina ta yi murmushi ta ce "Ashe dai bokona na da muhimmanci Inno, amma ai baba bai iya karatu ba, wa zai karanta masa, ni nafi son muyi magana da shi a waya" "To a ina zaki samo tarhon?" Amina ta ɗan yi jimm sannan ta ce "Ashirun gidan Jimmale kamar yana da waya". "A'a ni kin san bana san alaƙa da wannan matar, yanzu sai kiji ƙananun maganganu". Amina ta ce "to idan na tuna wata mafitar na gaya miki". Inno ta ce "To shikenan". ************ Sai haki take ta rasa wace kwanciyar za ta yi, domin ta ji daɗi, komai ba ya mata daɗi, Hafsa na zaune a gefenta, tana ta jera mata sannu, tana yi mata fifita. Cikin Muryar marasa lafiya Mama ta ce "Hafsa, ki tashi ki dafa ƙullin awarar can, kar yayi tsami". Cikin damuwa Hafsa ta ce "Mama ba zan iya zuwa gurin suyar awarar nan ba, alhalin kina cikin yanayi na ciwo, ni yanzu hankalina ya koma kan yadda zan samo kuɗi mu tafi Asibiti". "Haba Hafsa, jikina fa da sauƙi kece kike sanyawa kan ki damuwa, amma da sauƙi Alhamdilillah". Cikin halayarta ta miskilanci Hafsa ta ce "Wannan nishin ma da kike duk cikin sauƙin ne? Kin ji yadda ki ke numfarfashi kuwa? Na san fa kina jin jiki sosai, ni dama ciwon ya dawo kaina in ga kina walwalar ki da lafiyarki". "Auzubillah, haba Hafsa, sai kace wata mara imani, ni aka ce miki zan iya jurara ganinki cikin ciwo ne? Ki mini Addu'a kawai, Allah ya bani lafiya, kije gurin sana'arki, ko ba yawa ki samo wani abun, mu sai sabulun wanki". Da ƙyar Mama ta takura Hafsa, ta tashi ta fara kiciniyar haɗa kayan sana'ar, ba dan ranta yana so ba. ***** Duk yadda ya so zuwa Makaranta da wuri, Allah bai yi ba, dan be samu ba sai da ya makara, yana zuwa tuni hall ya cika an fara gabatar da darasi. Baya son zama a can baya, saboda baya ƙaunar zafi ko kaɗan. Wani space ya hango, dan haka cikin hanzari ya nufi gurin yana ƙoƙarin ɗosanawa ya zauna, tare da ciro wata 'yar jotter da ga aljihunsa. "Kai meye haka a kusa dani zaka zauna dan ba ka da hankali?". Cikin magiya ya ce "Dan Allah kiyi haƙuri, ba kusa da ke zam zauna ba, gani na yi da sauran guri, dan Allah ki bari in zauna". "Wallahi ba ka isa ba, kut haka kurum Wallahi ba za a kashe ni da warin hammata ba, ka nemi wani wurin". Ganin ta fara ɗaga murya har an fara kallonsu, ya sanya shi cire takalminsa a ƙasa ya zauna a kai. "Kai ba gurin zama ne ka zauna a ƙasa?"Cewar malamin da ke darasi a lokacin. "Malam bana son zaman baya ne, kuma na makara" "Ba ka gudun ka ɓata kayan ka?". "Ba komai, na karkaɗe". Malamin yayi murmushi ya ce "kun ga irin wannan ustazan, da basu ɗau duniya da zafi ba, su ne ƙwarin aji they make it in life". Fadila ta kalli uwar hular kan gayen nan, tashi ka fiye naci ce a kansa, saboda tsabar tsufa har zaren hular ya fara tashi, babu datti a jikinta, sai azabar tsufa, ya takure ƙafafunsa da suka yi busu-busu da ƙura, ya zauna akan takalmansa. Kamar kullum wata dariya Fadila ta kuma yi, tana cigaba da ƙare masa kallo ta ce "wai su ƙwarin aji manya" yana jinta, sai dai ko ɗagowa bai yi ba ya kalleta ba, ya cigaba da 'yan rubuce rubucen sa, duk da ba ya jin daɗin abin da yarinyar take masa. Malamin ya cigaba da gudanar da darasinsa, sai da ya kusa kammalawa sannan ya bada damar tambaya, aikuwa ɗan ustazun nan ya ɗaga hannu, malamin ya bashi dama ya miƙe, ya fara tambayarsa sai dai da harshen turanci yake yi, kuma da alama turancin bai zauna a bakinsa ba, dan sai fama yake ya tattara yayi bayani yadda malamin zai fahimta. Fadila ta ce "Wai turanci ya ga ta kansa, kai kuwa kayi da hausa mana tunda turancin baka iya ba" iya na kusa da su wanda suka ji mai ta ce, suka kwashe da dariya, wanda hakan ya sanya jikinsa yayi sanyi. Malamin ya ce ya cigaba da tambayar, dan tambaya ce mai matuƙar mahimmanci, wadda za'a ƙaru da ita sosai, ya girgiza kai ya ce wa malamin ya gama tambayar.   Aikuwa malamin ya dinga fashin baƙin tambayar nan, dan iliminne mai zaman kansa a cikin tambayar. A ka kammala lectures, kowa ya fita sabgar gabansa, masu neman Abinci su siya da sauransu. Fadila na tsaye a jikin motar ta ustaz ya zo wucewa, tana ganinsa ta tuna yadda ya dinga kokawa da turanci ɗazu a aji, aikuwa ta sake bushewa da dariya, yana jinta amma ya sake sunkuyar da kansa ƙasa ya wuce ba tare da ya ko ɗaga kai ya kalli in da take ba. ********** Amina ta dawo daga siyan itace, ta shigo sashinsu taji kawu Bala yana yiwa Inno bayani, wai ranar juma'a Malam Rabi'u zai turo magabatansa, su kuma sun sanya gonar Baba a kasuwa, malam Rabi'u yace zai siyi gonar. Jiki a sanyaye Amina ta ƙarasa ta ajiye itacen, ya mai da dubansa kan Amina ya ce "Au to faɗuwa ta zo daidai da zama, iyayen mijinki zasu kawo kuɗi ranar juma'a in Allah ya kaimu, kuma zai sai gonar mahaifinki ya siya ya bamu kuɗin mu yi miki kayan ɗaki". "Amma baffa idan ka siyar da gonar baba, mai zamu dinga nomawa?". "Rufen baki, mara kunya, ko shi Hassan ɗin ubanki bai isa in magana ya ce zai yi jayayya ba, ke kin je 'yan kwangilar yahudawa sun hure miki kunne har zan faɗa ki mayar ko? To na yanke hukunci na gama" Shiru Amina tayi, zuciyarta na wani irin raɗaɗi, har ga Allah bata son a salwantar da 'yar gonar nan ta su, ga uwa uba wannan Auren da bata ƙaunarsa sam. Bayan tafiyar Kawu Bala, Inno ta ce "Amina yanzu meye abin yi, ta yaya zamu samu mahaifinki balle a sanar masa da halin da a ke ciki?". Amina ta ce "'Nima ban sani ba" Inno ta ce "Ni dai bana son a sayar da gonar nan, kuma da idan sun sayar wata uwar arzikin zasu saya miki na kayan ɗakin da sauƙi, amma na san abin da Allah ya nufe su zasu saya miki, sauran su riƙe abun su". Ita dai Amina ba tace komai ba, saboda takaici ya hanata Magana sam. ********** Abun duniya ya isheta, duk yadda Ummanta ke nuna jikinta da sauƙi, amma ita hankalinta dai yafi kwanciya da ace sunje Asibiti an duba umman nata sosai, sai dai idan har suka ce za suyi jigilar zuwa Asibiti a dubata, to zasu shiga cikin jarinsu sosai, duk da haka ba yadda Hafsa ba tayi ba, a kan Umman ta amince su tafi Asibiti Allah ya kawo wata hanyar, amma Umman taƙi haka Hafsa ta ƙyaleta. Hafa na zaune a bakin rariya, tana wankin waken awara, Umma ta kalleta ta ce "Yanzu Hafsa har yanzu shiru ko ba kowa?" Sarai Hafsa ta gane abin da Umma ke nufi, amma tayi shiru taƙi amsawa. "Nifa wannan miskilancin naki ne yake ƙular da ni, da ke fa nake Magana". "Umma to me zance, kema fa kin san ba kowa ɗin". "Ko a gurin sana'ar taki baki haɗu da kowa ba?" "Umma kefa kike cewa in tsare mutuncina, ni da na fita sana'a ina ni ina kule kulen maza?". "Ba haka nake nufi ba Hafsa, daidai gwargwado kina samun masu sonki, amma kin ƙi ki tsaida hankalinki, kuma ko wannan rashin fara'ar taki da haɗe rai, ya isa ya hana samarin kulaki". Hafsa ta ce "Aikuwa su sha zamansu, dan ni ba su ne a gabana ba". "Au haka ma zaki ce? Ai shikenan idan dangin ubanki suka kuma waiwayoki kya shiga hankalinki ai". "Ai ba su da wani iko da ni, dan haka ba su da damar da zasu ɗaga mana hankali, har yanzu ban manta da wahalar da muka sha a hannunsu ba". "Ki manta ɗin dai shine yafi alkhairi, dan akwai gaɓar da dole a neme su a rayuwarki, mussaman a gurin Aure, dan kin san dai ni ba zan aurar da ke ba ko?". Shiru Hafsa tayi, dan ko zancen Mutanen nan ba ta ƙaunar ayi sam. *********** "Daddy" ta faɗa da ƙarfi tana rungume shi, kamar wata 'yar yarinya. "Fadila ke dai ba kya girma ko? Don't you know, that you are now a big girl?" Mutumin yayi Maganar yana murmushi. Tura baki Fadila tayi ta ce "Daddy wannan karon ka daɗe da yawa, kuma mu kayi waya da kai jiya baka gaya mini zaka dawo ba". "Eh dama nace bari in yi surprising ɗin ku ne kawai" "Kamar yadda Yaya Khalil yayi mana kenan, sai ganinsa kawai muka yi a gida". "Eh munyi waya, ya gaya mini yazo, na so in biya in ganshi ma, amma Allah bai nufa ba, ya school ɗin, dama Mum ɗinku tace mini kin fara zuwa". "School gata nan so boring and frustrated". "Da haka duk muka yi karatun, kawai ki maida hankali kiyi abin da ya kai ki, abin da duk baki gane ba, idan da wanda ya fiki ganewa ki zauna ya koya miki". "Taɓ, salon a rainani ace mini daƙiƙiya, i better Google what ever i dont understand". "But is not as accurate as what someone will guide and teach you, anyway i wil find someone to be assisting you at home after school" Cewar Alhaji Ahmad. "A nice idea Daddy, thank you ina Mummy?" "Nima ita nake jira, tana sashinta go and have some rest" Fadila ta miƙe tare da yasar da jakarta a nan falo ta wuce. Hajara ce ta shigo tana kwashe kayan da Fadila ta zubar a falon, ta risuna ta gaida Alhaji Ahmad, hannu ya ɗaga mata tare da faɗin sannu kawai. Hajiya Zainab ta fito cikin gayu, ta zauna kusa da maigidan nata tana ta kwarkwasa, kamar Amarya. Fadila ce ta kuma fitowa ranta a ɓace, ta tarar da Hajara na gyaraa falo, cikin faɗa ta fara yiwa Hajara magana "Wace ta gyara mini ɗakina a cikinku?" Hajara ta ce "Asabe ce" "Wai wasu irin banzaye ne ku? Kira mini ita, yarinya sai daƙiƙancin tsiya, kira min ita". Alhaji Ahmad ya ce "Yaya, mai ya faru ne?". "Daddy na gaji da halin maids ɗin nan, sai ka yi ta maimaita musu abu ɗaya amma basa ganewa". Mummy ta ce "Wallahi ni kaina ina mamakin rashin tunanin na yaran nan, kai ta maimaita magana basa ganewa". Asabe ce ta ƙaraso ta ce "Gani". "Eh gaki na ganki, wai jahilar ina ce ke? In ta maimaita magana ba kya ganewa, na gaya miki kar ki sake maimaita mini bedsheet, da na tashi a cire shi a wanke, na bar underwear a toilet, kin wanke banɗaki kawai amma baki wanke mini ba, ni kike jira inje School in dawo in wanke? Idan naki ne zaki bar su baki wanke ba? Ko da yake ku dama ƙazanta a jininku take". Asabe ta duƙa ta ce "dan Allah ki yi haƙuri, Hajiya ce ta samu aiki, ayyukan sun yi yawa yau saboda dawowar Alhaji". "Shut up I don't care malama, aikina na sani dana saki kiyi mini, idan ba zaki yi ba you can park your load and go back to your useless village, 'yar ƙauye mara ganewa kawai" Tun ɗazu Hajiya Zainab suna falon, suna jin yadda 'yar su ke wannan zazzaga amma ba su tofa ba, sai yanzu Alhaji Ahmad ya ce "Easy Daughter, ai ta baki uzurinta, ke ki je kiyi mata aikin, and ke kuma 1ki daina yiwa mutane shouting haka ba daɗi". "Daddy ni kaina ba jin daɗin shouting ɗin nan nake ba, suke sani Wallahi". Haka Asabe ta wuce sashin Fadila ranta a matuƙar ɓace, da jin zafin cin zarafin da Fadila tayi mata. Da sassafe, bayan kammala ayyukan gidan, iyalan na kan dining suna cin abinci. Hajara ta tarar da Asabe tana ta haɗa kaya. "Asabe wannan kayan da kike haɗawa fa?". Asabe ta ce "Ƙauyenmu zan koma". "Saboda me?" "Ba zan iya jure zama ana cigaba da ci mini mutunci ba, na haƙura da aikin na nemi wani gurin". "Haba Asabe, yanzu kan ki samu wani gidan aikin fa?". "Allah ba zai hana ni ba, na gaji da cin mutuncin nan". Hajara ta ce "Na shiga uku ni Hajara, Asabe idan kika tafi aiki da jarabar mutan gidan nan kashe ni zai a gidan nan". "Allah ya baki yadda zaki, amma ni ba zan iya ba na gaji, zan iya wankawa yarinyar nan mari". Asabe ta fito falo da kayanta, ta kuma gaishe da su, Alhaji Ahmad ne ma ya ɗan saki jiki ya amsa. Asabe ta ce "Dama ina so zanje gida ne, ance mahaifiyata babu lafiya, zan je jinyarta bani da tabaccin zan dawo". Mummy ta ce "To ki gaida gida" Fadila ta ce "Allah raka taki gona" Asabe jiki a sanyaye ta miƙe, Alhaji Ahmad ya kirata, ya sa hannu a aljijunsa, ya ɗauko kuɗi masu yawa zai miƙawa Asabe. Mummy ta yi caraf ta ce "Na meye kuma zaka bata wannan uban kuɗi haka? Naga an biyata kuɗin aikinta, wannan kuma na menene?". Daddy ya ce "Ai wannan watan ya kai a biyasu, tun da  jibi in Allah ya kaimu zai mutu, kuma ai tayi aikin watan, gara a biyata kuɗin aikinta, kuma a bata na siyan magani, ai ko bakomai an moreta a gidan nan" ba dan Mummy ta so ba, ya bawa Asabe kuɗi kusan dubu sittin ya sallameta. Hajara kuwa zullumi ta shiga da taradaddi, ta san duk wata wahala da ɗawainiyar gidan nan kanta zata dawo ita kaɗai, ga mutanen gidan da shegen sa aiki su kuma ga son jiki, in an bar 'yar aiki ta huta to fa dare ne yayi, suna su biyun ma da ya suka ƙare, balle yanzu sai ita kaɗai. ********* "Yawwa Hanne, yau da Yamma Malam Rabi'u zai kawo kuɗin Auren Amina, duk da ina samun labarin yadda kike zigata take masa rashin mutunci, bata saurarsa to ki sani duk wani ƙulle ƙullenki da makircinki ba zai hana Auren nan ba". Inno ta ce "Ni wani ƙulle ƙulle zan akan auren nan, ni da nake 'yar karere?" Tayi maganar cikin ladabi kuma a sanyaye. Kawu Bala ya ce "Oho miki dai, kuma anwa gonar Hassan kuɗi, dubu ɗari uku, zai kawo kuɗin gonar da na Auren, sati biyu kawai za'a saka ba wata bidi'a za a tsaya yi ba". Amina dake ta ƙoƙarin tuƙa tuwo ta zabura ta ce "Gonar baban ce dubu ɗari uku? Wallahi kawu cutarku zai yi gonar nan tafi haka". "Zaki rufe mini baki ko sai na zo na danna kanki a murhun nan? Fitsararriya mara kunya ina Magana kin tsoma baki, naga uban da ya isa ya hana a siyar da gonar nan ayi auren nan" Amina ta sunkuyar da kai, ranta na mata ƙuna, Shikenan duk wata kadara da Baba ya mallaka an kaɗar da ita. Albarkacin Asabe, ya sanya Alhaji Ahmad ya biya sauran ma'aikatan da ke gidansa kuɗaɗen albashinsu, duk da watan bai mutu ba. Hakan ba ƙaramin daɗi ya yiwa ma'aikatan ba, dan idan baya nan sai sabon wata ya kwan bakwai, matar gidan ba ta biyasu haƙƙoƙinsu ba. Baba Hassan ji yake ina ma tun kan a rufe jarrabawar su Amina, aka biya albashin nan, da ko duka kuɗin ya kama zai bada albashin nasa ta biya jarrabawar. Da yamma Baba Hassan ya nemi izini, ya tafi tasha in da su Saminu ke lodin can garin su Baba Hassan, Saminu ɗan garinsu ne, shi yake bawa duk wani saƙo da yake kai wa su Amina. Kamar yadda ya saba yi, ya ɗan yi siyayyar kayan Abinci, da sabulun wanka da wanki da su man shafawa, ya ɗora kuɗin kashewa ya kaiwa Saminu tasha ya ce ya kai wa su Amina, ace musu yana nan tafe yazo ya gansu da ya samu lokaci. Amina ta yi murna da ganin Saminu, dan har satar hanya tayi, da ƙafafuwanta ta tafi babbar tasha ta garinsu, tana neman Saminu amma baya nan. Sai gashi katsam ya kawo musu aike daga wurin Baba Hassan. Bayan gama gaisawa da Inno da Amina, Amina ta gyara zama ta ce "Dan Allah ka kira mana Baba a waya, ina son Magana da shi". Saminu ya ce "Sai dai wayar tawa babu kuɗi sosai, amma bari in jarraba kiransa a waya". Saminu ya kira wayar Baba Hassan, amma shiru ba ta shiga. Saminu ya ce "Amina wayar ba ta shiga, idan da wani saƙo ne ki bani in kai masa". Shiru Amina ta yi, tana jin yadda zuciyarta ke wani irin zafi. Inno ce ta ce "Hmm, ka sanar masa 'yan uwansa za su aurar da Amina ga Malam Rabi'u Jarmai, kuma zasu sayar da gonarsa su yi mata kayan ɗaki". Saminu ya kalli Amina ya ce "Wace irin magana ce haka? Ina laifin su jira ya dawo? Kuma kamar ba su san halin Rabi'u Jarmai ba, karatun nata fa" Inno ta ce "Kaga kar ka tunzurata, Aure ba laifi bane gallafirin da take a titi da sunan boko sam bai yi ba, amma wanda zasu haɗata da shi ɗin ne ba mutumin kirki ba ne" Saminu ya jinjina kai ya kalli Amina da hawaye suka wanke mata fuska ya girgiza kai ya ce "Kiyi haƙuri Amina, insha Allah zan sanar wa da Baba Hassan ɗin, ki daina kuka". Amina ta jinjina kai, tana ji a jikinta idan har Baba ya samu labari, wataƙila ya iya taimaka mata ta samu sassauci. Su kayi sallama da Saminu ya tashi ya tafi. Tun da Saminu ya tafi, jikin Amina yayi sanyi, tana tunanin ya Baba zai ji idan yaji ana shirin katse cikar burinsa a kanta, da kuma salwantar da 'yar gonar da ta rage ya mallaka. Bayan tafiyar Saminu, Inno ta shirya ta fita, saura Amina kaɗai a gidan. "Assalamu alaikum, wai ana sallama da Amina" cewar wani yaro da ya afko ba sallama. Amina ta ce "Kai kar ka sake shigo mana gida ba sallama, kuma ka koma kace masa ba zan zo ba, ya san in da dare yayi masa" Amina ta shige ɗaki abin ta, tamkar ba da ita ake sallama ba, sai da yayi kusan aike huɗu amma mirsisi ta ƙi fita. Allah ya taimaketa Inno ba ta nan, balle ta tursasata sai ta fita. Amina na nan zaune, tana sake duba litattafanta na makarantar boko tana hawaye, ta ƙallafa ranta a kan karatu, ta ɗakko littafin da ake shigar mata da makinta na haddar Alqur'ani a makarantar boko. Ta haɗa kai da gwiwa ta din ga kuka, tana tunanin meye mafita, dan ko a ƙafa a ka ɗaura mata Malam Rabi'u Jarmai, sai ta gutsure ƙafar ta huta, amma ta yaya zata iya daƙile wannan Auren? Tana cikin kukan wani tunani ya faɗo mata, cikin hanzari ta miƙe tsaye. Sai dai murayar da ta jiyo ana kwaɗa sallama ce ta sanya gabanta ya faɗi, ta dafe ƙiji tana faɗin "Innalillahi wa Innalillahi raji'un"! Domin gyara sharhi ko shawara 08081012143GABA DA GABANTA Page 5 AISHA ADAM (AYSHERCOOL) Litatafaina na AƘIDATA DA RUƊIN ƘURUCIYA duk na kuɗi ne Please. Ta taga Amina ta leƙa, sarai ta ɗau Muryar su waye, kasa amsa sallamar ta yi dan bata san da wani idon zata kallesu ba. Yadda suke kwaɗa sallamar ba ƙaƙƙautawa ne ya sanyata amsawa, tare da fitowa daga cikinu ɗakin. Kallo ɗaya ta yi musu gabanta ya faɗi, dan bata san da wacce suka zo ba, 'ya'yan Malam Rabi'u jarmai ne, wanda ƙawayen ta ne, sai dai su duk sun yi Aure, har da mai yara biyu, Iklima da Shema'u. Amina ta ɓoye damuwarta ta ce "Shema'au sannunku da zuwa, ku shigo". Iklima ta ce "Ji munafuka, mu shigo ina, algunguma ki rasa wanda zaki aura a garin nan dan rashin ta ido sai mahaifinmu, Wallahi kin ji kunya Amina". Shema'u ta karɓa da "Ai zuwa mu ka yi mu ja miki kunne, Wallahi baki isa kiyi kishi da iyayenmu ba, gidanmu kamar kabari ne, Wallahi kika shiga azaba da wahala sai sun koreki da ƙafafuwan ki, gara tun wuri ki san abin yi". Jiki a sanyaye Amina ta ce "Shema'u ku yi haƙuri, ni kai na ba son Auren nan nake ba Wallahi, kuma har yanzu ban ji a jikina zan iya Auren mahaifinku ba.... "Ba wani nan rufe mana baki, kwaɗayi ne ya sanya zaki auri baban mu ba wani abu ba". Amina ta ce "Wallahi ba haka bane, ku tambaya ku ji Wallahi ni ba son mahaifinku nake ba". "Yi mana shiru munafuka, har akwai yarinyar da ta isa ta ce ba ta son babanmu, zaki aure shi dan kwaɗayi,  an yi kwantai a gari an ƙare a hanyar boko, ba abin da bokon ta amfana miki, kin gama gantalinki za a liƙawa babanmu, Wallahi ki ka aure shi ƙannenmu sai sun illata ki". Amina ta ce "Naga ina ta lallaɓa ku kun kasa ganewa, to bari in fito muku a yadda kuke so, ni bana son mahaifinku shine ya nace mini sai ya aure ni, sai wani ihun kwaɗayi kuke yi, meye a gidan naku kuɗin baban naku da ba ci ake ba, tuwo safe rana dare, miyar gidanku kamar ruwan tsarki, kullum a wahala kuke, ya auri wannan ya saki waccan, insha Allah babu abin da zai sa in Auri babanku iyayenku ma fama suke, ta kan su suke yi". Shema'u ta ce "Kutt, baban namu kike gayawa haka?". "An gaya masa ɗin, yayi zuciya ya daina mayar da 'ya'yan mutane dan yana da kuɗi". "Gara namu uban an san aure yake yi yana saki, wayasan me naki uban yake aikatawa a birni". "Bakomai tun da ba'a san me yake ba, naku uban kuwa kowa ya san me yake yi, me ake da mutumin da bai san martaba da darajar Aure ba" ganin Amina ta fisu baki ya sanya suka fita suna ƙananun maganganu. Amina ta koma ɗaki tayi shiruu, tana tunanin mafita, tabbas ta san idan ta auri Malam Rabi'u kashinta ya bushe, dan a gidan nan babu kalar yaran da babu dan wasu daga manyan 'ya'yansa yayyen su Shema'u 'yan daba ne, ga uwar gidansa ita ce babbar masifaffiya, gidansa tuwo kwano uku zuwa biyar ake tuƙawa, idan ranar girkin ki ce ke zaki tuƙa wannan tuwo, sai a kwan uku ana cinsa. "Kai ba zai yiwu ba, Wallahi ba zan yadda in auri wannan mutumin ba". "Ke Amina, au zama ki ka yi kina koke-koke, har da surutai ba zaki dangana ba?" Ta jiyo muryar Inno. Cikin kuka Amina ta ce "Wallahi Inno ba zan auri Malam Rabi'u ba, yanzun nan su Shema'u suka bar gidan nan, ba ki ga cin mutuncin da suka yi mini ba, wai kar in auri babansu ni ce musu nayi ina son babansu, Inno wallahi bana son Mutumin nan ki gaya musu". "Amina ta yaya zan ce musu ba kya son sa ni a wa? Yanzu haka da na dawo ya tsareni a ƙofar gida, wai sun karɓi kuɗin Aurenki, da kuma kuɗin gonar mahaifinki, wai za'a kawai Jamila dillaliya dubu hamsin a samo miki gado ɗan hannu, a kaiwa Liti kafinta shima wai idan da kujeru na hannu a sai miki, an saka sati uku bikin". Fashewa Amina ta kuma yi da kuka ta ce "Wallahi ba zan auri wannan mutumin ba, tun yanzu 'yan'yan sa sun fara zuwa suna ci mini mutunci, kuma dan tsabar mugunta an siyar masa gonar babana da arha ya siya, kuma a siya mini kayan ɗaki 'yan hannu, dan an mayar da ni mara galihu". Bakinta Inno ta gwaɓe ta ce "Dan ubanki 'yan uwan mahaifin naki kike gayawa haka, salon su zo su ji suce ni nake ziga ki? Ke a rayiwarki ba ki san tawakalli ba da duk abin da Allah ya tsarawa bawa ba shi da ikon kuskurewa ba, kamar iyaye suke a gurinki fa". "Ni Wallahi ba iyaye na ba ne, tin da suke son kassara rayuwata, da tozarta mahaifina an cutar da shi an raba shi da gonarsa ba da saninsa ba". Inno ta bi Amina da kallo, Amina kenan akwai haƙuri wasu lokutan, wasu lokutan kuwa akwai gardama da taurin kai, dan Inno ta fara fagabar yadda Amina ke cigaba da adawa ƙarara da Auren da ake son a yi mata. ***************** Kamar kullum sun kammala lectures, lecturer ya ce zai yi musu wata test, amma ya bawa kowa damar ya yi amfani da wayarsa wurin samo amsar tambayoyin da zai yi. Suka dinga murna ɗaliban, malamin ya rubuta tambayoyi uku, a kan allo ya ce su amsa a mintuna goma kacal! Nan da nan suka duƙufa suka ɗauko wayoyinsu, suka fara binciken aikin da aka ba su. Rarraba idanu ya shiga yi, dan ba shi da wayar da zai amfani da ita wurin gudanar da aikin, ya juya hagu da damansa kowa ya duƙufa yana yi, amma ban da shi. Takarda ya samu ya sunkuya ya fara rubutun sa cikin nutsuwa. Fadila ta ɗago ta kalleshi, yana ta rubutu amma ba daga waya yake kwafa ba. Ta taɓe baki ta taɓo ƙawarta Ta nuna mata shi ta ce "Kalli ko mai yake rubutawa oho, mutumin da ba turanci ya iya ba, kuma ba waya ce da shi ba amma yana ta rubutu shi dole ga ƙwaro" kamar yadda suka saba suka kwashe masa da dariya. Bai ko ɗagoba ya cigaba da rubutun, sai dai duka bun nam da ake, ɗaliban suka gaza samo amsoshin tambayoyin a Google, ƙarshe abin da ya sawwaƙa suka rubuta lokaci ya cika suka bayar. Fitar malamin ke da wuya, ɗaliban suka fara ƙoƙarin fita daga ajin, tafiya yake sannu a hankali, babu gaggawa gashi ita kuma sauri take, so take ta bar ajin ya tsare mata hanya kuma ya ƙi sauri. "Dalla malam ka bani hanya, sai tafiya ka ke kamar mace, ko nan ɗakin ka ne?" Tsayawa ya yi, ya waiwayo ya kalli Fadila ido cikin ido, ya rasa mai ya tsarewa yarinyar nan haka, bata hanya ya yi yace "Bisimillah, wuce" ratse shi ta yi ta wuce tana cigaba da mitar yadda yake tafiya kamar mara lafiya. Shi dai bece mata uffan ba, ta wuce. Department ɗin su Yusra ta tafi, kasancewar duk a makaranta ɗaya suke, ta yi sa'a ajinsu Yusra ba kowa dan haka ta shiga kan ta tsaye. Yusra ta duƙufa ta na ta chatting a waya, Fadila ta zare wayar hannun Yusra, hakan ya tilasta mata ɗagowa, tana ganin Fadila ta yi murmushi ta ce "Beb daga ina haka?". Fadila ta zauna tare da faɗin 'Daga class, nace bari in zo in ganki". "Kai amma naji daɗi, ya lectures ɗin?". "Alhamdilillah, muna nan muna fama, ya naku?". "Alhamdilillah, muma hakan ne". "That's good, da wa ake chatting ne haka?". Yusra ta yi murmushi ta ce "Wallahi ba kowa, ina duba wani ankon da za muyi ne, na bikin Sister ɗina, so ina duba IG ne ko zan samu style". Fadila ta ce "Ok na zata sabon kamu aka yi mana". Yusra ta girgiza kai ta ce "Ba wani sabon kamu, samari akwai su, amma ni hankalina duk baya kan su". "Don't mind girl, in dai brother na ne, insha Allah ina nan ina miki fighting ina ta kafa ki a wurin Mummy, mu bi komai a sannu zai amince ne". "To beb, Allah ya amince. Ni wai ke ya ake ciki ne? Ko haryanzu ba ki da gwani" "Hmm ni fa ba ta wannan shirmen nake ba, ni ban baki labari bama, wannan abokin Yaya Khalil ɗin Abdul yake kowa? Wai shine ya ke nuna yana sona" "Ohh wannan abokin yayan naki da muka taɓa haɗuwa, wani mai abin dariya?". "Shi fa" "To meye aibunsa beb? Yana da kirki sosai". "Taɓ, lecturer ne fa mai ya samu ya ci balle ya bani? Aikin ma fa Daddy ne ya samo masa". "Ai ba wani abu Fadila, idan har kina son sa wannan duk ba abin damuwa bane". 'Bama na son sa dan ba class ɗina ba ne, wani baƙi da shi mara aji, sai surutun tsiya Mummy ma ba zata amince ba". Yusra ta yi murmushi ta ce "To Ubangiji Allah ya zaɓa mana abin da ya fi alkhairi gaba ɗaya". "Ameen dear, tashi muje mu samu abin da zamu ci". Suka rankaya gaba ɗaya suka fita daga ajin. ******** Saminu kuwa bayan tafiyarsa daga gidan su Amina, ya koma tasha, sarkin tasha ya sanar da shi an samu wasu 'yan biki da zasu je kai amarya can Lagos, a jira su kwana biyu a dawo da su, idan ya amince zai kai su zasu biya shi, biya mai kyau sun ce ba sa son Manyan motoci saboda tsaye tsaye. Jin zai samu kuɗi masu yawa, ya sanya Saminu ya amince, ba tare da ya tuna saƙon Amina zuwa ga mahaifinta ba, washegari da Asubar fari ya ɗebi 'yan kai amarya yayi Lagos. Amina kuwa ta din ga zuba ido taga ta ina Baba zai dawo gari, sai dai babu Baba babu alamar sa, kullum garin Allah ya waye cikin zuba ido take ta ga Baba ya dawo, amma shiru. Gashi ta ƙara tsangwamar kanta, duk ta yi baƙi saboda damuwar da ta sanyawa zuciyarta, gashi 'ya'yan Rabi'u Jarmai kusan kullum cikin zuwa gidansu suke suna ja mata kunne a kan Auren mahaifinsu. Ga su Kawu Lawan suma kullum da kalar ta su tijarar da suke zuwa su yi mata, hakan ya sa ta ƙara tsangwamar kanta, ko Abincin kirki ba ta iya ci sai kuka. Gashi tuni su Kawu Bala suka karɓi kuɗin Aurenta, Naira dubu hamsin komai da komai har sadaki, kuma suka amshe kuɗin gonar mahaifinta. Tana kwance a ɗaki da yamma, wani irin zazzaɓi ya rufeta, dama duk dare da shi take kwana, yanzu kuwa tun yamma ya rufeta, tana ƙudundune a bargo tana ta rawar sanyi, Inno na tsakar gida tana dafa mata rai ɗore ta bata ko zazzaɓin ya sauka, sai ga hayaniyar mutane. Uwargidan kawu Bala da ta Kawu Lawan ce suka shigo, suka kalli Inno suka ce "Ke Hanne kayan Amina muka kawo, ki gyara wurin da za a ajiye". Inno ta ce "Ga filin tsakar gida nan, a zo a ajiye su". Nan fa samarin 'ya'yan su suka fara kokowa da shigo da kayan, wasu irin ruɓaɓun kayan gado ne, aka yi musu fentin ha'inci, dan garin shigo da su ƙasan sip ya ɓare, zanin kujerun nan kuwa daƙal daƙal, ga ƙamshin fenti ga warin rima kayan suna yi, kai da gani ka san na ha'inci ne. Inno ta yi shiru tana bin kayan nan da kallo, duk sun ɓare garin kokowar shigowa. Uwargidan kawu Bala ta ce "To Inno, su Malam sun fita sun yi iya yin su ga kayan gadon Amina nan, saura kema naki ɓangaren aga irin bajintar da zaki yi a ɗakin amarya". Inno ta yi murmushi mai ciwo ta ce "Haka ne, Allah ya nuna mana ya sa ayi da mu". Suka amsa da Ameen, suka ringa guɗa, suka gama hayaniyar su suka fice. Amina ta ɗaga labule ta fito daga ɗakin su, ta kalli kayan nan, ta kalli bayan sif ɗin nan, yadda wani wurin ya kusa burmawa, da in da ya ɓare wurin shigo da kayan, shi kansa allon gadon, sari ya cinye wani wurin aka liƙe shi da fenti. Ta fashe da kuka ta ce "Yanzu a kan wannan matsiyatan kayan aka siyar da gonar Baba? Wallahi sai Allah ya saka mana". Inno ta ce "Dan Allah ki rufa mana Asiri, kar su dawo su ji abin da ki ke faɗa" "To su ji ɗin ina ruwana, Wallahi su da Allah, duk cikin yaransu da aka aurar, ba wadda aka yiwa wannan wulaƙanci sai ni, kalli wasu irin kaya kamar wata mara galihu, Allah ka saka mini" tayi maganar kamar zata shiɗe, saboda yadda haƙoranta ke haɗuwa saboda zafin zazzaɓi. Inno ta ce "Ni dai haƙurin nan dai shi zan baki, ki barwa Allah Komai dan Allah karki wani abu da zai sanya su zo su ɗaga mana hankali". Ta share hawayenta ta ce "Inno, anya Saminu ya gayawa Baba halin da ake ciki?" "To gashi dai har yanzu shiru ba muji ɗuriyarsa ba" "Inno ko bokonmu zanje, wurin malamanmu in ari waya in kira Baban?". "A'a ni bana son abin da zai janyo magana, ko kin manta da sun hanaki zuwa bokon nan, ki kiyayeni. Zan shiga banɗaki ki ɗau kofi ki tsiyayi rai ɗoren can ki sha, ki ɗau Abinci ki daure ki ci". Amina ta jinjina kai. Tana ganin Inno ta shiga banɗaki, ta ɗau hijjabinta ta fice daga gidan. Duk da yadda take jin jiri, kanta yana juyawa, amma zuciyarta ta bushe, sai zuba sauri kawai take yi. Uwar tafiya ta kwasa ba ta wasa ba, ta isa ƙaramar tashar garinsu, cikin rukunin direbobin nan taje ta gaishe su. Suka amsa wani mai suna Lado kan kara ya ce "Ya aka yi ne? Amarya da yawo ke da aka kusa ɗaura miki Aure?". Banza ta yi masa ta ce "Dan Allah Saminu nake nema". Wani ya ce "Saminu ya je Ikko, amma ya kamo hanyar dawowa gida". "Dan Allah ko zaku taimaka ku kira mini shi a waya, na bashi saƙo zuwa wurin Baba amma na ji shiru". "Ba matsala, bari a kira shi" cewar Lado. Amina ba tayi niyyar tankawa Lado kan kara ba, amm ganin zai taimaka mata ya sanya ta ɗan saki fuskarta. Ya kira Saminu ya miƙa mata wayar, cikin azama ta karɓa ta koma gefe. "Salamu Alaikum, Saminu Amina ce 'yar wajen Baba Hassan". Saminu ya rafka salati ya ce "Amina, dan girman Allah kiyi haƙuri, Wallahi na manta shaf da saƙonki na tafi ikko, amma kin ganni a hanyar dawowa, na miki alƙawarin yanzun nan, zan kira Baban in sanar masa". Amina cikin kuka ta ce "Dan Allah ka taimake ni Saminu, kar a wulaƙanta rayuwata" "Kar ki damu Amina, zan sanar masa Insha Allah" suka yi sallama ta bawa Lado wayarsa, ta yi musu godiya ta kama hanyar gida. Tun a hanya duhun magariba ya fara rufawa, ba ta damu da yadda sanyin dogayen zangarniyar bishiyoyin hatsi ke kaɗawa suna ratsata ba, wanda hakan ya ƙara asassa tsananin zafin da jikinta ke ɗauka, ga gefen cikinta da ya ƙulle, saboda yunwa amma ba ta damu ba, sai sauri take yi, in da ba mutane ta kwasa da gudu dan ta isa gida da wuri. Allah ya taimaketa ba wanda ya ganta suruf ta shige gida. Ta tarar Inno bata nan, ta shiga banɗaki tayi alwala ta koma ɗaki ta tayar da sallar magariba. Inno ce ta shigo gidan tana 'yan maganganu, tana ɗaga labule ta hango Amina na salla, aikuwa ta rafka salati ta ce "Ke daga ina haka? Kika ɗaga mini hankali nake ta yawon nemanki?". Amina ta idar da salla ta yi Adduointa, sannan ta kalli Inno ta ce "Inno tasha naje ko Saminu yana nan, wai ashe bai gayawa Baba saƙon nan ba, yana Ikko ma, aka kira mini shi a waya, shine ya ce mini zai gaya masa". "Kuma shine sai ki tafi baki gaya mini ba, kin ɗaga mini hankali, nan suka aiko suna neman ki, amma ba kya nan na rasa ƙaryar da zan musu, wato ke dai Amina ba kya gudun magana ko? Ke duk abin da zai sa su zo su ci mana mutunci kin san shi kuma zaki aikata ko?" Shiru Amina ta yi taƙi magana, Inno ta yi ta banbaminta ta gama, Amina ba tace komai ba. Baba Hassan kuwa kusan suman zaune yayi, bayan Saminu ya kira shi a waya ya wassafa masa irin katoɓarar da 'yan uwansa suke shirin aikatawa, na cefanar da gonarsa da kuma aurar masa da tilon 'yar sa ga mutumin banza da suke shirin yi. Baba Hassan bai iya cewa Komai ba sai kashe wayar da ya yi, ya san nan duniya ko me zai yi bai isa ya hana wannan auren ba, sayar da gonarsa bai ɓata masa rai ba kamar yadda ake shirin salwantar da rayuwar 'yar sa, dan abin da ya shirya shine, shekara mai zuwa ya biya mata kuɗin jarrabawar, kuma ya dinga tattala 'yan kuɗaɗe saboda harkar makarantar ta, sai dai kash ga abin da 'yan uwansa ke shirin aikatawa. Amina har zuwa sallar isha'i zazzaɓin jikinta bai sauka ba, ga wani irin koren amai mai ɗaci da take tayi, Inno sai jiƙe-jiƙe take tana ɗura mata, Amina mirsisi ta ƙi sha, saboda wannan jiƙe-jiƙen da take sha su suke ƙara sanyata amai. Yarone yayi sallama, wai Amina ta je in ji Malam Rabi'u Jarmai. Inno ta ce "Ka je ka ce masa ba ta da lafiya". Yaron ya fita ba jimawa, ya dawo ya ce "Wai Kawu Lawan ya ce idan ba ta je ba ya zo sai ya zane ta". Inno ta kalli Amina ta ce "Amina, lallaɓa kije, bana son fitina da tashin hankali". Amina ta buɗe baki za tayi Magana, Inno ta girgiza mata kai ta ce "Yi haƙuri, daure kije" haka ta ɗau hijjabinta tana kuka, ga zazzaɓi a jikinta ta fita. Jarmai na ganinta ya washe baki yana faɗin "Amaryata ba faɗa mai ya kawo gaba fisabilillahi?". "Kaga saurara mini, Azzalimi kawai aka sayar maka da gonar Baba ka saya, alhalin ka san kuɗin gonarsa ba haka yake ba, to Wallahi ba zan auri Azzalimin mutum irinka ba, ga yaranka marasa tarbiyya da suke mana zarya a gida suna zagina, ba zan iya ba". "Aikuwa zaki iya, da kin shiga gidana kin sha jar miya zaki watstsake muyi zaman mu". "Jar miya a Ina? Da jar miyar a gidan naka ka ke kai yaranka bara wasu suna talla? Ina alamar jar miya a jikinka ko jikin 'ya'yanka, saboda tsabar cuta da zalunci ina kai ina ni, da ƙanan shekaru na ka haɗani a wannan gidanka na gayya, to bari kaji in gaya maka, ko da sarƙa a ka ɗaura Aurena da kai sai na warware shi, kuma ba dai in je gidanka ba sai dai a kai maka gawata". "Ni kike gayawa wannan miyagun maganganun?" Yayi Maganar yana matsawa kusa da ita, wani azabar warin baki gami da na sigari ya daki hancinta, ga ƙarin rana yana yi, kayan jikinsa ne kawai wankakku, suma sai ƙarnin koren sabulu suke. Ja da baya ta yi ta ce "Kar ka sake matsowa kusa da ni, na gaya maka ɗin, idan kana da zuciya ka biya ka karɓe kuɗin Aurenka ka fasa Aurena, idan kuwa ba haka ba idan ba a kai maka gawata gidanka ba, sai gidanka ya zama sansanin tashin hankali da bala'i na gaya maka". "Yaro man kaza, mu zuba mu gani ni da ke shege ka fasa, gidana ne Wallahi sai kin shige shi sai na Aureki". "Za kuwa mu gani, na bika ta lallalami kaƙi fahimta, zan fahimtar da kai ta hanyar nuna maka ni 'yar zamani ce, tsohon kawai". Saroro ya bi Amina da kallo, bai taɓa zaton za ta iya gasa masa miyagun maganganu haka ba, dan kowa kallon saliha yake mata, ga haƙuri da biyayya, a zatonsa duk irin halin mahaifinta ne da ita zai samu tuɓus, ashe abin ba haka yake ba. Ita kuwa Amina gida ta shige abinta, Inno na tambayarta yaya aka yi, amma tayi shiru saboda yadda zuciyarta ke tafasa, ko ƙaunar jin sunan Rabi'u Jarmai ba ta yi, balle a kai ga batun Auren su. Ta haɗa kai da gwiwa ta dinga rusa kuka, Inno kam ta gaji da rarrashin Amina dan haka ta zuba ido. Baba Hassan kuwa bakinsa ɗauke da Addu'a, ya shiga falon gidan da sallama, a zatonsa ya je daidai lokacin da zai samu Alhaji Ahmad, sai dai kash bai fito ba, sai Hajiya Zainab ya tarar a falo, tana ta bawa Hajara umarni cikin tsawa da wulaƙanci. Kasancewar abu ne na gaggawa, ya yanke shawarar sanar da Hajiya Zainab, Alfarmar da ya zo nema, ya risuna ya gaida ita cikin girmamawa, ta amsa ba yabo ba fallasa. "Hajiya dan Allah wata alfarma na zo nema a wurinki". "Haka dai, Alfarma ba yau ba gobe ina  jinka". Ya gyara zamansa ya ce "Wallahi wani al'amari ne ya taso mini a garinmu cikin gaggawa game da iyalina, nake son dan Allah a bani dama, ko kwana biyu in je in yi in dawo". Ta ɗago ta kalleshi ta yatsina fuska ta ce "Idan zamu fita ko mun dawo, mu zamu dinga kokowa da ƙofa wurin buɗewa da rufewa kenan?". "A'a hajiya, ga Hadi nan sai ya riƙa mini kan in dawo". "Ban lamunta ba, aikin Hadi daban a gidan nan, naka daban dan haka ba in da zaka a yanzu, idan kuwa ka tafi, to ka tafi kenan" Baba Hassan yayi shiru ya rasa abin da yake masa daɗi, ya tashi gwiwa a sanyaye ya bar falon. Idan ya kuskura ya bar aikin gadin nan, tofa rayuwarsa da ta iyalansa za ta shiga wani hali, dan ba shi da wata sana'a da ya iya. Amina kuwa tun Asuba take amai, ciwo ya ƙi sauƙi kullum sai gaba yake yi, ƙarfe shida da rabi sai ga Kawu Bala da Lawan tare da matansu, da wasu daga cikin yaransu kamar wanda za su je ritsa kwarto, sun shigo suna zazzaga bala'i tun daga hanyar shigowa. Suna zuwa suka tarar da Amina a zaune dirshen tana amai. Ladiyo Uwar gidan Kawu Bala ta ce "Wallahi malam zancen ya tabbata, abin da ake ta gudu, wannan aman ai irin na masu ciki ne". Inno ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, wane irin masu ciki kuma bata da lafiya ne fa". "Ƙarya kike munafuka, dama ance mini an ganta a tasha wai taje wurin Saminu, dama zuwan da Saminun yake gidan nan kenan, Kuna lalacewa, kafira mai siffar munafukai, har an samu wanda zai rufa miki asiri ya Aureki, amma zaki tozarta mu, ashe dagaske ne kullum sai kin je tasha kin bada jikinki a baki kuɗi, wannan cikin ba zaki haife shi a gidan nan, jibi in Allah ya kaimu idan an sakko daga sallar juma'a za'a ɗaura aurenki da Rabi'u, kuma ba wata bidi'a da za a yi, ɗaurin Aure kawai za ai a kai ki dama da ke da bazawara ba maraba, kin gama tsufa a titi da rabawa maza jikinki". Wani malolon baƙin ciki ya tokarewa Amina ƙirji, ba ta san lokacin da zafin maganganun wan mahaifin nata suka sanyata jan tsaki a fili ba. Ai kuwa hakan ya tunzura shi, ya nufi dangar kara, ya ciro kara suka rufar mata da duka. Inno ta dinga kururuwa tana faɗin "Kuyi haƙuri, ba ta da lafiya". Ladiyo ta ce "Wallahi ku casa ta, ko Allah ya sa cikin jikinta ya zube". Tun Amina na iya motsi tana kuka, har ta sare sai wata irin ajiyar zuciya take, jikinta duk ya farfashe saboda duka. Bayan tafiyarsu Inno ta ɗumama ruwa, ta gargasawa Amina jikinta tana faɗin "Kin ga Abin da nake gaya miki ko, shiyasa na gaya miki taurin kai ba shi da rana Amina" Kwanaki biyun nan, jikin Amina ya ƙara zafi, wai sunan amarya ba kitso ba ƙunshi tana kwace ba lafiya, iyalan su Kawu Bala suka kwashi raftar kayan da suka yiwa Amina aka kai mata gidan Malam Rabi'u. Ranar Juma'a kiran Sallar farko, Amina ta ɗebi kuɗi, daga kuɗin da ake bawa Inno gudunmuwar Aurenta, dama tun dare ta haɗa kayanta Inno na bacci, kiran sallar farko, ta kwashi kayanta ta fice daga gidan. Tana tafe a hanya tana kuka ta ce "Babana maganin kukana, na san wataƙila har yanzu saƙona bai riske ka ba, shi yasa baka kawo mini ɗauki ba, duk da ban san wurin da zan sameka a birni ba, amma gara in tafi da tambaya har Allah ya sanya in dace in gano in da kake, dan da in auren nan gara in mutu a hanya". Arewabooks https://arewabooks.com/u/ayshercool7724 GYARA SHARHI KO SHAWARA 08081012143GABA DA GABANTA AISHA ADAM (AYSHERCOOL) P6 Follow my Arewabooks account Ayshercool7724 https://arewabooks.com/u/ayshercool7724 Tafiya take tana ratsa tsakanin gonaki, ga duhu ga babu haske, amma hakan bai dameta ba, babban burinta shine ta ga ta baro cikin ƙauyen nan cikin salama, ba tare da wani ya ganta ba. Baba Hassan kuwa bacci ma ɓarawo ne ya ɗauke shi, tunanin mafita kawai yake yi, zuciyarsa ta dinga raya masa kawai ya haƙura ya tafi ƙauye, komai zai faru ya faru, idan ya so ya haƙura da aikin, amma gefe guda yana tunanin idan ya bar aikin gadin me zai yi? Wace sana'a zai yi? Wata shawara yake ta jujjuyawa a ransa wadda ba shi da tabaccin zata karɓu. A haka har garin Allah ya waye, gaba ɗaya jikinsa a sanyaye yake gudanar da komai, yana nan zaune a bakin gate yana ta jujjuya yadda zai ɓullowa lamarin, wajen ƙarfe goma Fadila ta fito ta fita, wajen ƙarfe sha ɗaya kuma Alhaji Ahmad ya fito, cikin wani ash ɗin yadi, an fito masa da motar sa da zai fita da ita. Alhaji Ahmad yana ƙoƙarin shiga mota, Baba Hassan ya cin masa, cikin girmamawa ya gaisheshi, Alhaji Ahmad ya amsa cikin mutuntawa. Baba Hassan ya duƙa ya ce "Yallaɓai dan Allah alfarma nake nema". Alhaji Ahmad ya gyara tsayuwa ya ce "Ina jinka". Baba Hassan ya ce "Dama Yallaɓai game da 'yar wajena ce, jarrabawar nan ba a samu damar yin ta ba" "Subhanallah, garin yaya?" "Kuɗin aka kai a ƙurarraren lokaci, to yarinyar tawa tana son ta yi karatu sosai da sosai, to ka san mutanenmu na karkara, 'yan uwana ba son karatun nata suke ba, to rashin samun damar rubuta jarrabawar ya sanya suna ƙoƙarin su Aurar mini da ita. Shi ne nace dan Allah tun da dama Asabe ta tafi, a taimaka mini a ɗauki yarinyar tawa ta maye gurbin Asabe, idan ya so kuɗin aikin nata sai a sakata a makarantar boko, a dinga biya mata kuɗin makarantar". Alhaji Ahmad ya ce "Malam Hassan wannan ai ba wani abun damuwa bane, bakomai ka kawota ai ilimi ga 'ya mace abin so ne, idan na dawo an jima ka tuna mini zan yiwa mutan gidan magana, ka kawota". Wata ƙwallar farinciki ta cikawa Baba Hassan ido, ya zube ƙasa yana faɗin "Na gode, Na gode Allah ya jiƙan magabata ya yauƙaƙa Arziki, Allah ya biya maka buƙatunka na Alkhairi duniya da lahira, yadda ka Sanya farinciki a cikin zuciyata da ceto 'yata ubangiji Allah ya faranta maka, yayi maka tukuici na Alkhairi". Alhaji Ahmad ya ce "Haba Malam Hassan, kar ka damu dan Allah wannan ai ba wani abin damuwa bane, Allah yayi wa yaranmu albarka baki ɗaya". "Ameen Yallaɓai godiya nake". Baba Hassan ji yake kamar an yaye masa damuwar da yake ciki, dan yana zuwa ɗakinsa yayi sujudu shukur, ya lalubo wayarsa ya kira Saminu. Sai da ta kusa tsinkewa Sannan Saminu ya ɗaga, suka gaisa Baba Hassan ya ce "Saminu, dan Allah idan ka tashi tahowa, duk yadda zaka yi ka taho mini da Amina garin nan, ko a tasha ka ajiyeta sai ka kirani in zo in tafi da ita". Saminu ya ce "To shikenan, amma ba zan taho yau ba gaskiya, sai dai gobe in Allah ya kaimu" "Bakomai, amma dan Allah kar ka bari su farga su san da ita zaka taho, idan kuka taho daga baya nazo in musu bayani, idan suka san zaka kawo mini ita ba zasu bari ba". Saminu ya ce "ba komai, kar ka damu Baba insha Allah zan kawo maka ita lafiya". "To shikenan Saminu, na gode sosai Allah ya saka da alkhairi" ************ Yau Juma'a dan haka wankan hijjabi ta yi, pink tun daga sama har ƙasa, ba ƙaramin kyau ya yi mata ba, ta shigo tana rataye da jakarta pink, hannunta riƙe da robar ruwa da mukullin motarta, bai san yadda aka yi ya shagala da kallonta ba, tayi kyau ƙarshe, ga wani irin sassanyan ƙamshi da take yi. Sai dai ta yi missing ɗin lectures ɗin farko da aka yi, dan suna takun saƙa da malamin, dan haka yau ba ta yi attending darasin sa ba, kuma darasin da yayi da lissafi a ciki, kuma ko da kai aka yi lissafin a ajin, abu ne mawuyaci mutum ya fahimta saboda yayi tsauri da yawa. "Kai lafiya kar ka cinye ni dalla" tayi masa maganar cikin tsawa. Sunkuyar da kansa ya yi daga kallonta, ya koma kallon wani wurin daban. Class rep ne yayi dariya ya ce "Kai Fadila wannan tsawar haka?" "To ya sani a gaba da kallo, sai na faɗi tukuna aikin banza". Dariya ƙawayenta suka din ga yi, wata wadda ake cewa Amra ta ce "Kyau ki ka yi masa ko ustaz?" Tsaki Fadila ta ja ta ce kwaji da shi. Babu jimawa wani lecturer ya shigo, wanda ya basu class work ya ce su yi da waya, nan ya dinga yi musu mita ya ce "Ace gaba ɗaya ajin nan babu wanda ya fahimci tambayar da na yi sai mutum ɗaya, ina sane nace ku duba waya, dan na san idan har baku fahimci tambayar ba, babu yadda za ayi ku samo amsar. Waye Yazeed Hashim Shareef?". "Sir" ya faɗa tare da ɗaga hannunsa sama. Gaba ɗaya idanun mutan ajin suka dawo kansa. "Wow, dama na gaya muku ustazan nan sune ƙwarin ajin, Malam Yazeed fito ka mana bayanin yadda ka fuskanci tambayar da na yi, har ka samu damar amsawa" Yazeed ya fita gaban aji, ya ce "Sir zan iya yi da Hausa?". "Yi da duk yaren da kafi iyawa" Yazeed na haɗa ido da Fadeela ta ƙunshe baki tana sinne dariya, ta ɗan ɗaga murya ta ce "Sir gara yayi mana da hausar dai, da turancin nan bama ganewa" Malamin bai kawo komai a ransa ba, ya yin da 'yan ajin suka gane me Fadila take nufi da faɗar hakan, su kai ta yi masa dariya. Tun a nan ya rasa karsashin da zai yi bayanin, duk ya ji jikinsa yayi sanyi, amma ya daure ya aro jarumta, ya daidaita nutsuwarsa, cikin kamalarsa ta zance da iya sarrafa harshe, yayi bayanin yadda ya fuskanci tambayar da yadda ya bi amsa tambayar. Malamin da kansa ya tafawa Yazeed ya ce "Weldone Ustaz, you are genius man, ka burgeni ƙwarai mutane masu sharp brain irinka ba su da yawa, Allah ya ƙara basira" Yazeed ya ce "Thank you sir". Malamin ya ce "Gaskiya duk ajin nan babu wanda ya amsa daidai sai Malam Yazeed, dan haka kowa yaje ya sake faɗaɗa bincike a kan bayanin da yayi, zan yi test a kansa, idan kuma kuna buƙata ku tuntuɓe shi yayi muku bayani sosai". "Gaskiya mu dai Sir kai mana bayanin da kan ka" cewar Fadila. "Meye baki gane ba a bayanin da yayi?". "Ni ban gane komai ba" ta faɗa cike da rainin hankali. "Well, zaki iya zuwa ki same shi ya yi miki bayani". "A'a Sir gaskiya gara ka yi mana da kanka". "Ba zan ba" ya bata amsa. Tura baki tayi cike tsiwa da harare-harare. "Leave my class" malamin ya faɗa yana nuna mata hanyar fita. Kamar kullum, ta saɓi jakarta ta fice, tana fita ya kalli 'yan ajin ya ce "A ciro takarda, kowa ya rubuta attendence, attendance 30 marks, test 10 marks. Takardar attendence ta fara zagawa, har ta zo kan Yazeed, ya kalli takardar attendance ya kalli wurin zaman Fadila, ya rubuta sunansa sannan ya rubuta Fadila Ahmad Musa. Bayan kammala lectures, malamin ya ƙirga ɗaliban ajin, ya ga mutum ɗaya ya hau kai, aikuwa ransa ya ɓaci, ya ce "Waye ya rubutawa wani attendance? Kowaye ya faɗa kafin in binciko shi da kaina". Yazeed ya miƙe tsaye cikin jin kunya ya ce "Ni ne Sir". "Wa ka rubutawa?" Yayi shiru. Malamin ya kalli Attendance ɗin ya ɗago ya kalli Yazeed ya ce "Yazeed Hashim Sharif, Faidla Ahmad Musa, da kai da ita kun rasa wannan 30mrks ɗin". Tana ƙarasawa ƙaramar tashar garinsu, ta tarar an fara lodi, kasancewar fuskarta sanye da niƙabi ne, babu wanda ya gane wacece, ta samu wuri ta shimfiɗa ɗankwalinta ta yi sallar asuba, daga nan ta shiga motar da za ta kai ta babbar tashar ƙaramar hukumar su. Gari da sauran duhu, haka suka ɗauko hanyar barin ƙauyensu, babu abin da Amina take a zuciyarta sai Addu'a, da fatan Allah ya kaita lafiya ba tare da kowa ya ganta ba. Ƙarfe bakwai suka isa babbar tasha, ta shiga tambayar direbobin nan Saminu, tare da yi musu kwatancen sa, wasu suka ce ba su gane shi ba, wasu kuma suka ce sun gane shi, amma ya kwan biyu bai shigo tashar ba, ganin gari na cigaba da haske, ya sanya ta fara tsoron kar a biyo sawunta, dan haka ta shiga motar da ake lodin Kano!. Haka tayi ta rarraba ido, kamar agola a rabon gado, tana kallon hanya, tare da mamakin manyan gine gine da tituna da ababan more rayuwa da suke shimfiɗe a maraya, yayin da ƙauyuka ko oho, banda yau da Allah ya sa ta fito maraya ta gani da idanunta, da sai ta ce ƙaryane a garin Kano babu irin wannan manyan ababan more rayuwar, duba da yadda rayuwar karkara take da wahala, saboda rashin isar da ayyuka yadda yakamata har karkarkara. Sai da suka yi kusan tafiyar awanni biyu cir a mota, sannan suka iso babbar tashar mota ta kabuga da ke cikin ƙwaryar birnin Kano. Ware idanunta tayi a kan manyan motocin da ke shiga suna fita a cikin tashar, wadda ta sha banban da tashar su ta ƙauye, sai a yanzu ta gane tayi wauta, ta ina zata fara neman Inda Baba yake? Ga Saminu ya ce mata yana Ikko, amma yau zai ƙaraso, to idan ya ƙaraso ina za shi? Nan Kano ko can gida? Gaba ɗaya ta rasa abin yi, ga jikinta babu daɗi, cikinta sai hautsunawa yake, saboda yunwa da kuma doguwar tafiyar da suka yi ta mota wadda ba ta saba ba. Ta samu can wani wuri a ƙarƙashin wata bishiya, ta rungume kayanta tayi zamanta tana kalle kalle. Saminu kuwa cikin dare suka sauka, dan haka washegari da safe baccinsa ya kwanta ya sha hankali kwance saboda gajiyar tafiya. Sai wajen sha biyu saura ya tashi yayi wanka kasancewar juma'a ce, ya shirya dan ya fara biyawa ta gidansu Amina, ya sanar mata da saƙon Baba sannan ya ce ta shirya su haɗu a tasha washegari da safe, ba tare da sanin a ranar za a ɗaurawa Aminan Aure ba. Ko da yaje gidansu Amina, sahsensu ya nufa ya tsaya a bakin ƙofa yayi salama, aka amsa masa tare da bashi izinin shiga. Sai dai yana shiga yayi tozali da Inno a zaune, idanunta sun yi jawur sun kumbura, sai ajiyar zuciya take yi, ga mata duk a zazzaune a kusa da ita. Saminu ya ce "Subhanallah, babar Amina lafiya kuwa? Aminan ce ta rasu ko kuwa mai ya faru?". Aikuwa Inno ta sake fashewa da kuka,maƙwabciyar su Inno ce ta iya cewa "Ka san yau za'a ɗaurawa Amina aure, har kafi anje an yi an gama komai yau ɗaurin Aure, an wayi gari an nemeta an rasa". "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, an nemeta an rasa kamar yaya? Ba sai wani satin ɗaurin Auren ba?". "A'a an dawo da shi yau, sai wayar gari aka yi babu Amina babu dalilinta a garin nan". Saminu ya girgiza kai ya ce "Ta ina zan fara gayawa mahaifinta wannan mummunan labarin haka? Kunga illar Auren dole kenan". "Wallahi Hanne ba ki isa ba, duk in da yarinyar nan ta shiga garin nan kin sani, Wallahi sai kin nemota dan ba zaki mayar da mu ƙananan mutane ba, yau ɗaurin Aurenta ace an nemeta an rasa, duk mun zagaye garin nan kowa yace bai ganta ba" Kawu Bala kenan, har wani irin yawu ne yake tsartuwa daga bakinsa, saboda azabar masifa da jaraba. Inno kuwa ta sake fashewa da kuka, ita ba batun Auren ne ya dameta ba sanin in da Amina ta tafi ne ga bata da lafiya shi ne babban damuwata. "Wallahi yau duk in da yarinyar nan take sai an nemota, ko gawarta aka tsinto a gidan Jarmai za a mata sutura, Wallahi Hanne ko ki fito da Amina, ko in je har birni in ɗauko miki 'yan doka su kama ki. Kuma bari kiji in gaya miki ko kuna so ko ba kwa so, ko tana nan ko bata nan sai an ɗaura mata Aure dan ubanta Hassan". Saminu ya ce "Haba Baba Bala, a fara mayar da hankali wurin gano in da Amina ta shiga mana, wannan faɗan ai duk ba shi ne abun yi ba". Aikuwa ya dawo da idonsa kan Saminu "Au munafuki Algungumi, ashe kana nan, bana raba ɗaya biyu da haɗin bakinka yarinyar nan ta gudu, dan na lura da take takenka, ance har tasha take zuwa wurinka". "Me za ta je tasha ta yi mini, iyakacina da iyalan Malam Hassan saƙo ne su bani in kai masa ko ya bani in kawo musu, kaga tafiyata ba zaka ɓata mini suna ba, Babar Amina Allah ya bayyana ta" dag haka Saminu ya fice, yana jinjina lamarin mugunta na 'yan uwan mahaifin Amina, su b ta ɓatan yarinyar suke ba, ta yadda za a ɗaura kar sunan su ya ɓaci suke yi. Malam Rabi'u Jarmai ne ya zo har gidansu Amina yana bala'i a kan idan har ba a ga Amina ba, a dawo masa da kuɗinsa, idan an ganta a san abun yi. Kawu Bala ya dinga ba shi haƙuri ya ce "Haba Jarmai, ka kwantar da hankalinka za a ganta duk in da ta shiga, idan ma ba a ganta ba, za a ɗaura muku aure a haka, duk in da ta shiga da Aurenka a kanta idan ya so ds ta dawo sai a daƙumota a kaita gidanka". Jaramai ya ce "Amma ka raina mini hankali, tana nan baku kula ba ta gudu saboda kun mayar da ni mahaukaci, sai a aura mini gaibu, ni ba zan yadda da wannan sagegeduwar ba, na baku daga nan zuwa ranar Lahadi, idan an ganta to idan ba a ganta ba, ku san yadda za kuyi ku sallame ni". "Ke Fadila, jarida zazzafa" cewar Amra da ta samu Fadila a Cafeteria. Fadila ta ce "Jaridar me fa?". "Bayan fitar ki daga class, Mutumin nan ya ce ayi Attendance, 30mrks duk wanda baya nan babu shi a 30mrks ɗin nan, ba kawai sai gayen nan yayi miki ba" "Wane gayen?". "Wannan Zaidu yake ko Yazeed, wanda aka ce shi ya ci class work, aikuwa ya gano shi ya ce da ke da shi ba ku da 30mrks ɗin nan". Fadila ta ja tsaki ta ce "To uban waye ya sashi yayi mini? Allah ya ƙara" "Kai mutuniyar baki da dama, Allah ya ƙara ma zaki ce?". "Idan ba Allah ya ƙara ba me zance? Ni muje class ɗin ma in ƙare masa ta tas kar ya sake mini shishshigi a lamurana". Aikuwa Amra ta dinga zigata, suka nufi aji, suka tarar da shi yana wurin zamansa, yana motsa bakinsa a hankali da alama karatu yake yi. "Kai wurinka na zo" Fadila ta yi maganar tana tsare shi da manyan idanunta. Ya ɗago kai ya kalleta, ba tare da ya ce komai ba. "Uban waye ya saka ka yi mini Attendance? Na ce maka ina buƙata ne? Ai ni malamin nan ya gama mini komai da kaima ya soke naka Attendance ɗin, uban shishshigi kawai" lumshe idanunsa yayi a hankali, ba tare da ya ɗago ba, balle ta sa ran zai tanka mata. "Da kai nake magana fa" "Wai ni?" Yayi Maganar yana kallonta. "Au duk maganar da nake, baka ma san da kai nake ba saboda ka raina mini hankali?". "Yi haƙuri" ya faɗa a taƙaice. "Aikin banza kawai" ɗan murmushin gefen baki yayi, tare da kau da kansa gefe, dan tuni idanun sauran 'yan ajin ya dawo kansu. Class rep ya ce "Haba babbar yarinya, duk ajin nan babu wanda ya tuna da ke ya yi miki Attendance sai shi, amma sai taimako ya zama faɗa?". "Kaga saurara mini babu ruwanka da ni, ai ba da kai nake ba, na gaya masa ina buƙatar taimakonsa ne? Ya ji da tsummar rayuwarsa kan yayi tunanin shiga rayuwata ya taimaka mini". "Dalla class rep ka daina shiga sabgar yarinyar nan, gaba ɗaya ba ta da kunya Wallahi" cewar wani matashi shima mai ji da kansa, wanda suke kira da Babson. "Lokacin da aka raba kunyar ni ba a haifeni ba, idan an raba kana nan zaka iya ɗebar mini a taka". Babson ya ce "Ni kike gayawa haka?". "Na gaya maka ɗin waye kai? Banza useless" Ganin Babson ya miƙe ya hayayyaƙowa Fadila, kuma bakin Fadila ya ƙi mutuwa, sai cigaba da tunzura Babson take. Yazeed ya miƙe ya riƙe Babson ya ce "Ɗan uwana dan Allah kayi haƙuri ka ƙyaleta. Fadila ba mutuncinki bane ki dinga rigima da mutane mussaman maza, muryarki al'aura ce, sai ɗagata ki ke yi... "Dalla yi mini shiru, ji yadda kake ambatar Sunana kamar kai ka raɗa mini, idan ba ka kiyayi shiga sabgata ba saina kwarfeka na bi ta kanka a gaban mutane" Dariya jama'ar wurin suka fara, tana fama da kayan rama, kamar a busheta ta faɗi, amma ta kalli zabgegen namiji kamar Yazeed ta ce zata kwarfe shi. Babson ya ce "Dan Allah ku ƙyaleni in tattaka wuyan yarinyar nan, in kawo ƙarshen fitsararta". "Sai dai kayi ka kaɗai, ƙazami mai warin hammata kawai" ba dan Yazeed yana riƙe da Babson ba, da ba abin da zai hana ya yiwa Fadila mahangurɓa. Baba sai kiran wayar Saminu yake, a kan batun tahowar su tare da Amina, Saminu ya tabattar masa da cewar Amina ta ɓata an nemeta an rasa. "Innalillahi wa Innalillahi raji'un" shi ne abin da Baba Hassan ya dinga maimaitawa, tare da dana sanin rashin zuwansa ƙauye akan lokaci, take ya fara dana sanin zaɓar aikin nan a kan zuwa ƙauye wurin tilon 'yar sa. Gaba ɗaya Baba ya rasa abin yi, jikinsa banda rawa babu abin da yake, banɗaki ya fara zagawa yayi gudawar fargaba, sannan ya ɗauro alwala ya zo ya tada salla ya kaiwa Allah kukansa, sannan yayi tunanin mafita. Baba Hassan mutum ne mai matuƙar tawakalli, dan haka ba lallai ka karanto damuwar da yake ciki a halin yanzu. "Baiwar Allah, ke tun safe na ga mota ta sauke ki, amma kin zo nan kin duƙunƙune a nan, lafiya kuwa?". Amina da ke jin jiki ta kalli mutumin ta ce "Dan Allah a tashar nan kake?" "Eh a nan nake". "Dan Allah ka san wani Saminu, ɗan garin Shanono, direba ne shima" Yayi shiru sannan yayi ajiyar zuciya ya ce "Gaskiya ban san shi ba, amma ke ina zaki je?" "Wurin Babana na zo, kuma Saminun ne kawai ya san in da Baban yake". "Idan ba zaki damu ba muje in baki masauki mana" "Nace maka ina buƙatar masauki ne? Ka bari na gode kawai". Amina na nan zaune ta ji ana cewa wani Sarkin tasha, miƙewa ta yi tabi bayan Sarkin tashar, zuwa wani Office da ya shiga, ba tare da ya san tana bin sa ba. Yana ƙoƙarin zama ya ga Amina a tsaye a bakin ƙofar ofishin, ta zuba masa ido. "Lafiya kuwa?". "Dan Allah yayana tambaya nake" "To Allah ya sa lafiya, ya sa kuma na sani" "Dan Allah ka san Saminu direba, yana zuwa daga Shanono?". "Ahh na san Saminu wani dogo baƙi, yana jan mota KIA?" "Eh shi, dan Allah idan kana da lambar wayarsa ka kira mini shi" "Eh ina da ita, amma ta sayarwa ce" "To nawa ce?" Amina ta faɗa da mamaki. "Eh, amma ba da kuɗi ba, ƙofar ofishin nan kawai zamu rufe, mintuna kaɗan sai in baki wayar ma kyauta". Amina ta kalleshi tsaf tayi ajiyar zuciya, kawai ta juya ta bar wurin, tana tunanin wannan wane irin abu ne haka? Babu wanda zai iya yi maka alfarma a birni, sai ya nemi mutuncinka?. "Da in koma gida a mini wannan Auren, gara in cigaba da yawo a nan" ta faɗa a fili. Ta koma in da ta bar kayanta ta yi alwala tayi sallar Azahar Tana nan zaune, sai ga wanda ya fara yi mata magana da farko ya dawo wurinta, ya ce "Ke, na gane Saminun da kike nufi, ke 'yar uwassa ce?". Amina ta jinjina masa kai, alamar eh. "Ok bari in kira miki shi a waya" ya kira wayar Saminu ya bawa Amina. "Saminu gani a tashar Kano, dan Allah ka gaya mini ina zan bi inje wurin Baba?". "Amina, dama nan kika tafi, kin sa ana ta nemanki a gida?". "Dan Allah ni dai ka taimaka mini, kuma kar ka gaya musu in da nake dan Allah". "Shikenan, kwantar da hankalinki, kin ganni a hanya na kusa shigowa 1 21Kano, idan na shigo zan kai ki in da yake". "Yawwa na gode sosai, Allah ya kawo ka lafiya" Ta miƙawa mutumin wayarsa, tare da yi masa godiya, ta zauna tana jiran zuwan Saminu. Mutumin nan ya zauna ya dinga yiwa Amina surutu, amma ko uhmm ba ta ce masa. Sai bayan la'asar Sannan Saminu ya iso, wata irin ajiyar zuciya Amina ta dinga saukewa tana murmushi. "Yi haƙuri Amina na barki kina jira, Amina wannan ramar da kika yi fa?" Maimakon ta bashi amsa sai ta hau kuka, Saminu ya ce "Yi haƙuri, share hawayenki, nayi miki laifi nima dan ban gayawa Mahaifinki da wuri ba, kuma da na gaya masa dama cewa yayi in kai masa ke. Muje maza in kai ki" Mutumin da ya kirawa Amina Saminu ya ce "To Amina ba sallama?" Shiru ta yi masa tana cigaba da share hawaye. Saminu ya ɗaukar mata kayanta, ya sa a motarsa ta shiga, ya je ya sayo mata gurasa da nama da lemo ya bata, ta riƙe a hannunta amma ta kasa ci. Suna tafe yana bata labarin yadda gidansu ya hargitse, ita duk tausayin Inno ne yafi damunta. Ko da suka shiga cikin unguwar tudun Yola, rukunin gidajen da Baba Hassan yake gadi, Amina ta saki baki, tana ganin gidaje tamkar a ɗauka a ci. Da Saminu yayi parking ya ce mata sun zo, nan mamaki ya ƙara baibayeta, gate ɗin gidan ma kawai abin kallo ne. Saminu ya ƙarasa ya ƙwanƙwasa ƙofar gate ɗin, amma ya ji shiru, ya tura ƙofar suka shiga, lokacin Baba Hassan na fitowa daga ɗakinsa na gadi, a guje Amina ta ruga da gudu ta nufi in da Baba yake ta riƙe hannunsa ta fashe da kuka. Baba kasa Magana yayi, sai kallon Amina yake yana murmushi, shi dai a duniya ba abin da ya rage masa da yake ƙauna kamar Amina. Saminu ya ƙaraso yayi masa bayanin komai, Baba Hassan ya dinga yi masa godiya, sannan ya ce dan Allah idan ya koma garinsu, ya haɗa shi da Inno a waya yayi mata bayani, amma bayan ita kar ya gayawa kowa abin da ya faru. Saminu ya tabbatar masa da zai yi hakan, daga nan suka yi sallama ya tafi. Baba ya zauna Amina ta gaya masa duk abin da ya faru a ƙauye, ya jinjina kai shi kuma ya gaya mata yadda suka yi da Alhaji Ahmad. Amina ta dinga murna jin batun cigaba da makaranta. Amma Baba ya ja mata kunne a kan yanayin mutanen gidan da halayarsu, A ƙuruciya ta Amina gani tayi ai dan wannan ai mai sauƙi ne. Baba ya dinga jadadda mata "Sai kin yi haƙuri, rayuwar birni da ta karkara ba ɗaya bace, su mutane ne masu ƙyamar talaka ki iya kan ki, kiyi musu aikinsu su biya miki kuɗin Makaranta". Amina sai murna take, ashe da rabon burinta zai cika a rayuwa. Baba ya ce "Muje in gabatar da ke a wurin su". Amina ta bi bayan Baba da kayanta a bagco, tana ta kalle-kalle, kamar zata faɗi. Ya yin da Baba ke ta Addu'a Allah ya sa Amina ta shigo a sa'a, ta samu ta kammla makarantar Sakandire ɗin ta. Ayshercool 08081012143GABA DA GABANTA AISHA ADAM (AYSHERCOOL) P7 Tuni Amina ta manta da zazzaɓin da take fama da shi, dama na fargaba da damuwa ne, ita wancan Auren da ta baro ya fi komai yi mata daɗi, ga kuma wannan abin farinciki da ta zo ta riska, ba ta taɓa zaton abubuwa za su zo da sauƙi haka ba. Har sun kai bakin ƙofar da zasu shiga cikin falon gidan, Baba ya tsaya ya kalli Amina ya ce "Uwata ina sake jadadda miki, sai kin yi haƙuri kin kauda kan ki, ki kwantar da hankalinki duk abin da suka ce ki yi, babu musu haka wanda suka ce ki bari, banda shishshigi ki zauna kiyi haƙuri mu samu ki kammala makarantar ki lafiya ƙalau". Amina ta yi murmushi ta ce "Insha Allah Baba ba zan baka kunya ba, zan yi duk abin da kace" ya jinjina kai sanan ya tura ƙofar ya shiga da sallama. Alhaji Ahmad ne kawai ya amsa, Hajiya Zainab kuwa na zaune, Fadila na kwance a kan cinyarta, tana kallon T.V. Baba na gaba Amina na biye da shi, suka ƙarasa cikin falon, Amina ta zube har ƙasa ta gaida Alhaji Ahmad, ya amsa mata cikin mutuntawa. Ta kalli Hajiya Zainab ita ma ta gaisheta, sai da ta yi mata kallon sama da ƙasa sannan ta ɗauke kanta ta amsa da ƙyar. Alhaji Ahmad ya ce "wannan ce yarinyar taka?". Baba ya ce "Eh ranka ya daɗe" Alhaji Ahmad ya kalli Mummy ya ce "Madam, ga yarinyar da na yi miki magana ɗazu, 'yar wurin Malam Hassan, dan haka sai ku haɗata da masu aikinku ku nuna mata aikin da zata ringa yi. Sannan yanzu ana hutun makaranta ne, amma da zarar an koma Makaranta za'a kai ta makaranta insha Allah". Baba ya ce "Na gode Ubangiji Allah ya ƙara Arziƙi". Amina ma ta ce "Na gode Allah ya saka da alkhairi". "Ba komai, ki nutsu ki mayar da hankali kiyi karatu da kyau kin ji ko?". "Tom insha Allah na gode sosai". Duk wannan abun Mummy da Fadila basu tofa ba, Baba Hassan ya gama godiyar sa ya tashi ya koma bakin gate in da yake aikinsa. Amina na zaune tana jiran a bata masauki, amma babu wanda ya kuma kulata, sai ma cigaba da hirarsu da suka yi. Kusan mintuna arba'in tana zaune, ga yunwa tana ji, gurasarta na cikin kayanta, tana so ta keɓe ta samu ta ci, amma ba wanda ya kuma saurararta. Ba tsammani ta ji muryar Fadila tana kiran "Hajara" Amina a ranta ta ce "Ji wata murya kamar aljana". Hajara ta ƙaraso falon hannunta riƙe da duster, ta ce "Gani". "Dan Allah kai yarinyar nan can wurinku, ta zo ta sanya mutane a gaba da kallo". Sai yanzu Mama ta ce "Ki kaita ɗakin da Asabe ta bari, da safe zan mata orientation" Hajara ta ce "to" ta kalli in da Amina take, yarinya ɗanya sharaf, tubarkallah baƙa ce mai kyau da ita, sai dai kayan jikinta zai tabattar maka da akwai rangwamen gata. Hajara ta yi matamurmushi ta ce "Ta so muje ciki". Amina ta ce "To bari in ɗakko takalmana a bakin ƙofa, kar wani ya samin". Wani irin kallo Fadila ta yiwa Amina, jin abinda tace, Daddy kuwa murmushi kawai yayi. Amina ta ɗakko takalmanta silifas ɗan madina mai zanen yatsu. Hajara ta ɗaukar mata jakarta suka shiga ciki, Hajara ta buɗe wata ƙofa suka shiga wani falon. Amina ta ce "Kai, sanyi sosai, naga lokacin bazara ne, amma sanyi sosai nan" Hajara ta ce "Na'ura ce take sanyaya ɗakin ai" Amina ta ce "Ok ita ce A.C air condition?" Hajara ta kalli Amina jin ta yi turanci ta ce "Eh ita ce". Ta kai Amina ɗakin da Asabe ta bari, ɗan madaidaici ne da ƙatuwar katifa, akwai mudubi da banɗaki a cikin ɗakin. Hajara ta ce "Ga ɗakin ki nan" Amina ta zaro ido ta ce "Wannan duk ni kaɗai? Amma tare zamu dinga kwana a ɗakin ko?" "A'a kowa da ɗakinsa, ga banɗaki nan bari in kawo miki sallaya ko zaki salla, bari in je kitchen in samo miki Abinci" "To Na gode" bayan fitar Hajara, Amina ta dinga kallon ɗakin, ta leƙa banɗakin tas da shi. 'Allah sarki Inno, da na san haka zan samu komai a wadace da mun taho tare, wannan aljannar duniya haka?" Ta shiga banɗakin, ta dinga taɓe- taɓe, Dan Amina akwai rawar kai wasu lokutan, hakan ne ya sanya take iya wasu abubuwan. Ta yi alwala, ta yi sallar magariba, ta janyo kayanta tana ƙoƙarin ɗauko gurasarta ta ci, sai ga Hajara ta shigo da kwanuka, ta ajiye a gaban Amina, sannan ta zauna kusa da Amina ta ce "Ya sunan ki ne?". "Sunana Amina". "Masha Allah, ni kuma Hajara" Nan Hajara ta dinga bawa Amina labarin yanayin mutan gidan, tare da sukar Hajiya Zainab da Fadila, ita kuwa Amina hankalinta sam baya kan Hajari, yana kan daddaɗar doya da miyar ƙwan da Hajara ta kawo mata, lokaci guda kuma tana tunanin Inno. Daren ranar Amina kasa bacci ta yi, saboda tsoro da rashin sabo, haka ta kwana da fitila a kunne. ************* Alhamdilillah kwanakin nan Hafsa tana yin ciniki sosai, dan har da dankali take haɗawa yanzu bayan awara. Dan har da miya take haɗawa idan mutum yana so ya siya da miya. Wata mota ce tayi parking a ɗan gaban in da Hafsa take suyar awarar ta, mutumin ya sauke glass ya leƙo da kansa, ya kalli Hafsa yayi mata alama da taje. Kallo ɗaya ta yi masa gabanta ya faɗi, ta ɗauke kanta ta cigaba da abin da take yi irin ba ta ganshi ɗin nan bama. Wani almajiri ne yaje kanta ya tsaya ya ce "Wai ki zo inji mai motar can". "Kace masa ba zan zo ba" Almajiri ya koma ya sanarwa mutumin saƙon Hafsa. Mutumin ya ce "Ka nuno mata ni kace ni nake kiranta". Ko da yaron ya zo ya kuma sanar mata saƙon mutumin, ta kalli yaron a fusace ta ce "Zaka matsa daga kai na ko sai na kwaɗeka?" Ba shiri yaron ya matasa ya bar wurin, da Hafsa ta iya tsare gida bata son wargi. Mutumin ne ya fito daga motar ya ƙaraso kan Hafsa ya tsaya, ya dubeta a wulaƙance ya ce "Ke ni nake miki magana ki ka share ni?" Ko nuna ta san ƙurar da ta kwaso shi ba ta yi ba, ta cigaba da fifita wutar gabanta. "Aikin banza wulaƙatancciya, a haka zaki ƙare rayuwarki a wahala, daga ke har mahaifiyar ki haka zaku ƙare, kaɗan ma kuka gani, muddin ina raye sai kun fito titi kuna bara" Wani murmushi ta yi mai ciwo, ta cigaba da sabgar gabanta. Ya dinga jifanta da miyagun maganganu, a gaban mutane. Mai shayin da ke gefen in da Hafsa ke sana'arta ne ya ce "Haba bawan Allah, ta yi shiru ba ta tanka maka ba, sai ci mata mutunci kake a gaban mutane ya haka ne?" "Kaga saurara mini, ba da kai nake ba, ba ka san meye tsakanin mu ba" "Koma meye tsakaninku wani abu ne da ya shafe ku, nan kuma titi ne bai kamata ba abin da kake yi". Banza yayi masa ya cigaba da surfa rashin mutunci son ransa, amma duk yadda ya so Hafsa ta tanka masa taƙi, ya gama bala'in sa ya hau motarsa ya tafi. Bayansa ta bi da kallo har ya ɓacewa ganinta, sai da ya bar wurin wasu hawaye masu zafi suka shiga zubowa daga idanunta 'Allah ka nuna mini ƙarshen mutumin nan da ire irensa kan ƙasa ta rufe idona'. Ganin tana kuka, Mansur mai shayi ya ce "Kiyi haƙuri Hafsat, mutane irin wannan sai haƙuri ba su da mutunci ba su da kirki" Hafsa ba ta ce masa uffan ba ta cigaba da share hawaye, haka ta kammala cinikin nan babu daɗi ta haɗa kayanta ta koma gida. Tun da Hafsa ta koma gida Mama ta fuskanci akwai damuwa a tattare da Hafsa, duk da Hafsa ba mai yawan magana ba ce, kuma ba Yarinya ce mai fara'a ba, amma shirunta da ƙaruwar haɗe fuskarta ya sanya Mama ta gane hakan. "Hafsa lafiya kuwa?" "Lafiya ƙalau" ta amsa a ciki. "A'a ba lafiya ba, mai yake faruwa ne?" "Mama bakomai fa". "To koma meye Allah ya ye miki, Idan ba ki gaya mini damuwarki ba, ban sani ba ko akwai wani wanda ki ke da shi a waje da zaki gaya masa" Hafsa ba ta kuma cewa Mama komai ba, ta cigaba da abinda take yi. Wasu lokutan Mama tana jin haushin miskilancin Hafsa, amma kuma gado ta yi haka mahaifinta ma yake, amma har gara shi a kanta, babban abin da Mama take ji shi ne, ba kowane namiji ne zai iya jure halin Hafsa ba. Mama ta zuba mata ido, saboda kar Mama ta cigaba da takura mata da tambaya, ya sanya ta dinga ƙaƙalo aiki tana yi, ta kwaso kayan wanki ta wanke a daren, ta tsiri wanke wanken  kayan kitchen gaba ɗaya, ta je ta sayo waken awarar gobe, duk wannan aikace-aikace da take yi, ba ta kula Mama ba, ta zauna zata fara gyaran wake, Mama ta yi gyaran murya ta ce "Ajiye waken nan, ki zo ki zauna ki huta, ba zan sake tambayar ki meke damunki ba, tunda dan gujewa tambayar tawa ya sa ki ke ta wannan aikace aikace". Aikuwa sum sum kamar munafuka Hafsa ta koma ɗaki, ta nemi wuri ta kwanta ba tare da ta ko ci Abincin dare ba, Mama kuma ba ta kulata ba ta ƙyaleta. Amina ta wayi gari a birni, ta gabatar da sallar Asubahi, ta zauna ta na karanto azkar ɗin ta kamar yadda ta saba, tana nan zaune ta ji motsi dan haka ta tashi ta fita, aikuwa taga Hajara ce ke kaiwa tana komowa. Amina ta gaida Hajara cikin girmamawa, dan dama Hajara ta girmeta, Hajara ta amsa tare da cewa "Har kin tashi?". "Eh na tashi, nuna mini hanyar fita waje, in je in gaida Baba". Hajara ta nuna mata, Amina ta fita ta tafi. A ƙofar ɗakin Baba ta tsaya ta ƙwanƙwasa, ya ce "Waye a nan?" "Baba ni ce" Baba Hassan ya buɗe ƙofar, ta durƙusa ƙasa ta gaishe shi, ya amsa sannan ya ce "Ya a kai kika fito da duku-duku haka?" "Baba gaisheka na zo na yi, sannan in ganka" Yayi murmushi ya ce "To bismillah" suka shiga ɗakin da Baba yake, abin ka da 'ya da uba, an daɗe ba a haɗu ba, suka dinga hira ta bashi labarin abubuwan da suka faru a ƙauye, har ƙazafin cikin da suka yi mata, da sayar da gonarsa da irin kayan da suka saya mata ta gaya masa. Baba ya yi ajiyar zuciya ya ce "Bakomai, watarana sai labari, ni dai fatana da burina ki mayar da hankali kiyi karatun nan kin ji uwata" "To Baba zan yi insha Allah" "Yawwa uwata, Allah yayi miki Albarka". "Ameen Baba, amm ai zakaje ƙuye su biyaka gonarka ko?" "A'a Amina, ai gona ta riga ta salwanta, zan dai je garin in musu bayanin kina wurina". "Baba ba wani mataki da zaka ɗauka? Dubu ɗari uku fa suka sayar da gonar". "Ba komai, Allah ya mayar mini da alkhairi". "To Wallahi Baba ka yi musu Allah ya isa". Baba Hassan ya buɗe baki ya ce "Uwaki nace, yayyen nawa zan yiwa Allah ya isa?" Sai Amina ta fara hawaye "Haba Baba, tun da na buɗe ido suke cutarka, kai baka cewa komai, su yi ta zaluntar ka dan sun ga babu mai tare maka, Wallahi Allah zai saka maka" Baba Hassan ya ƙurawa Amina ido, yana jin soyayyar 'yar ta sa a ransa, ita dai a duniya kar a taɓa mata shi, ko a cutar mata da shi. Ya sa hannu ya share mata hawayen fuskarta ya ce "Tashi maza ki koma ciki, kar su neme ki, zamu cigaba da hirar" da ƙyar Baba ya sa Amina ta tashi ta koma cikin gidan. A falo ta tarar da Hajara, na ƙoƙarin fara moping, a nan ta tsaya Hajara ta dinga nuna mata yadda ake ayyukan gidan, da wuraren da suke ajiye kayan amfani. Daga nan suka shiga kitchen, suka fara ƙoƙarin haɗa Abincin karin kumallo. Ƙarfe takwas da rabi suka kammala komai, Hajara ta lura Amina ba ta da ƙyuwa sam, ga kaifin basira. Sun gama shirya Abincin a kan dining, Hajiya Zainab ta fito daga sashin Fadila, tana gaba Fadila na binta a baya. Hajara ta risuna kamar baiwa tana gaida Mummy da Fadila, Amina kuwa da murmushi a fuskarta ta gaida su, sai dai yadda suka amsa gaisuwar a wulaƙance ne ya bawa Amina mamaki, dan ita Fadila ma ko amsa gaisuwar ba tayi ba. Hajiya Zainab ta kalli Amina sannan ta mayar da kallonta ga Hajara ta ce "Ina fatan kin fara nuna mata yadda aikin gidan nan yake?". "Eh Hajiya na fara nuna mata" "Yawwa, ki buɗe kunnenki da kyau ki ji abin da zan gaya miki, da dokokina na gidan nan, idan kika karya mini doka korarki zan ki koma in da kika fito. Na farko bana son ƙazanta, bana son munafunci da sa ido, duk abin da zaki ga an yi a gidan ba ruwanki, tun da ba gidanku bane ba. Sannan bana son munafunci da gulma, sannan duk wanda ya saki a gidan nan kome kike dole ki ajiye kiyi abin da aka saki. Ina da yara biyu ɗayan namiji ne baya nan amma yana zuwa hutu gida, ba na son shishshigi a kan abinda ya shafi rayuwata da ta yarana. Abu na ƙarshe idan kin san ki na da wani mugun hali na sata ko makamancin haka ki tabattar kin baro su can a ƙauyenku, dan ba zan ɗauki duk wani rashin daraja da rashin ɗa'a ba" Amina ta ji haushin kalaman da Mummy ta yi amfani da su wurin yi mata bayanin aikin nata, amma ba ta nuna hakan ba sai ma cewa ta yi "Insha Allah zan kiyaye" Mummy ta ce "Fadila do you have anything to say?" "Nothing much, you have said it all. Kawai ni dai a bi abinda nake so a gidan nan a zauna lafiya, idan kuma akasin haka ya faru, za a ga abin da zai biyo baya" Mummy ta ce "To, kar ki sa ran zuwan ki gidan nan, kamar buƙata ta biya ne, zan jarrabaki na 'yan kwanaki in ga kamun ludayin aikin naki, idan yayi mini shi kenan, idan bai mini ba kuma ki koma in da ki ka fito, idan yayi mini ɗin, sai in ga sashin da zaki din ga kula da shi a gidan nan". Amina dai ta yi shiru tana wasa da yatsun hannunta. Hajara ta ce "Amina ta so muje mu cigaba da aikin" Amina ta tashi ta bi Hajara, tana mamakin yadda Hajiya Zainab da 'yar ta ke gatsa magana ba girmama ɗan Adam sam. Hajara ta ce "Amina sai fa kin yi haƙuri, idan har kina son zamanki a gidan nan dole ki ji ki ƙi ji, dan ba ki ga komai ba in dai wannan matar ce" Amina tayi ajiyar zuciya tare da jinjinawa Hajara kai. Ɗakin Fadila suka nufa, Suna shiga ɗakin Amina ta yi turus, ɗakin kaca kaca, har da kwanukan Abinci a ɗakin. Ga takardu da litattafai ko ina, har da kofi a kan gado, ta cire kaya duk ta watsar a ɗakin, banda takaddun biscuit da na chocolate duk a ɗakin a watse. Ga ɗaki har ɗaki mai kyau, amma kamar makwancin mahaukaciya. Amina ta ce "Wannan ɗakin waye?" "Ɗakin 'yar masu gidan ce, kin ganshi nan dai kamar ɗakin jaka, gashi ba ta son ƙazanta, amma fa Komai sai dai a yi mata. Idan ta tashi daga kan gado, cire bedsheet ake a bayar a wanke, ana wanke mata banɗaki sau uku a rana. Haka ma gyaran ɗaki, kuma idan zaki gyara mata ɗaki sau goma idan ta shigo komai a in da ta ga dama zata watsar da shi. Idan ta dawo daga unguwa ko Makaranta, tun daga falo take fara zubar da kayanta, sai dai ki bi Falon ki kwaso mata kayan, tana da kyauta ba kamar uwatta ba, amma duk alkhairinki a gareta, rana ɗaya idan ki ka yi mata abin da bata so, sai ta ƙare miki cin mutuncin da sai kin rasa ina zaki saka kanki, idan ba ki sa'a ba kuwa har uwatta zasu haɗu su ci miki mutunci, dan haka sai ki shirya! Sai kin mayar da kan ki baiwa a wurinsu zaku zauna lafiya". Nan take jikin Amina yayi sanyi, tana iya jure komai aiki wahala da makamantansu amma ba ta son wulaƙanci, ta fara wasi wasin anya zata iya kuwa? Zata iya jure a ci mata mutunci a kan abinda bai kai ya kawo ba?. Haka suka gyarawa Fadila ɗakinta, suka koma sashin Hajiya Zainab suka gyara ko ina, amma babban abin da ke sake bawa Amina mamaki bai wuce yadda Hajiya Zainab ke ta faman yi musu tsawa ba, ko Magana za a yi musu, sai cikin tsawa da harara. Kwanaki biyu kenan ɓatan Amina ya karaɗe ƙauyen nan gaba ɗaya, ga Jarmai ya ɗagawa su Baffa Bala hankali, dan ya riga ya gama saka rai da samun Amina. Inno kuwa tsawon kwanakin nan, ba ta iya cin Abinci, duk ta zube saboda kuka, da tashin hankali ko bacci bata iya yi, kullum tana kan sallaya tana riƙe da carbi. Har malaman makaranta su Amina sai da suka zo, suka yiwa Inno jajen ɓatan Amina. Kamar ko yaushe, Inno na zaune ta duƙufa tana jan carbi, ta jiyo muryar Saminu yana sallama. Ta amsa masa tare da bashi damar shigowa, ya shiga ya zauna suka gaisa,  sannan ya ce "Baba Hassan ne ya aiko ni wurinki". Inno ta ce "Ka sanar masa da batun ɓatan Amina ne?". "Ai Amina ba ɓata tayi ba". Inno ta kalleshi da mamaki, amma ta sunkuyar da kai ta ce "Na sani, Amina guduwa ta yi saboda wannan auren da za ayi mata, ba yadda ba ta yi dani ba a kan in sa baki, amma nasan ko na yi magana ba su ji ba, ni babbar damuwata babu wanda ya san in da take, ta ɓatawa kanta suna a garin nan" ta ƙarasa Maganar tana share hawaye. "Maman Amina ki kwantar da hankalinki, Amina na tare da babanta a birni" Dafe ƙirji Inno ta yi ta ce "Kamar yaya?". Nan ya kwashe komai ya gaya mata, sannan ya ɗora da cewar "Baba Hassan ya ce, kar ki gayawa kowa, ya ce zai zo da kansa garin nan idan komai ya lafa, wayata ta ci speaker ne jiya, da na kira miki shi a waya". Inno ta kuma ƙasa da muryarta ta ce "Dan Allah Saminu da gaske ka ke, tana lafiya ƙalau a wurin babanta?". "Wallahi Babar Amina ba zan miki ƙarya ba, tana wurin Baba Hassan". "To Alhamdilillah, Allah kai ne abin godiya, Allah na gode maka, Saminu Allah ya yi maka albarka, insha Allah zan shiru da bakina, babu wanda zan faɗawa sai ya zo da kansa" Inno ji tayi tamkar ta zuba ruwa a ƙasa ta sha dan tsananin farin ciki. Kwanakin Amina huɗu a gidan, Alhaji Ahmad ya shirya komawa wurin aikinsa, ya tabattar wa da Baba Hassan cewa, Khalil zai shigo gari, idan an koma Makaranta shi zai kai Amina Makaranta. MEYE HASASHEN KU GAME DA LITTAFIN NAN? INA JIRAN RA'AYOYIN KU. DAN ALLAH BANA SON THANKS ƊIN NAN, KO STICKER. Domin samun update a kan lokaci Follow my Arewabooks Account @ Ayshercool7724 My Watpad account@ Ayshercool 7724 Ayshercool 08081012143GABA DA GABANTA P8 AISHA ADAM (AYSHERCOOL) Amina ta yi murna sosai a kan batun kai ta makaranta, tsananin ɗoki da shauƙi ya sanya ta manta da duk wani batun rashin mutuncin da Hajiya Zainab da 'yar ta ke musu. Kafin Alhaji Ahmad ya tafi, Baba ya tambaye shi yana son a bashi dama sati mai zuwa ya je ganin gida. Alhaji Ahmad ya amince masa da ya je. Bayan an idar da sallar Asubahi, Rabi'u Jarmai ya ritsa kawu Bala yana masifa "Gaskiya Bala na gaji, yau kwanaki goma kenan ba yarinyar nan babu labarinta, dan haka na haƙura, kuje ku kwashe ruɓaɓun kayan da ku kai gidana, sannan ku dawo mini da kuɗaɗe na". Kawu Bala ya ce "Haba Jarmai, ya zaka yi mana haka? Dan Allah ka yi haƙuri, na gaya maka ana ganin yarinyar nan, za a ɗaura muku aure a kai maka ita gidanka" Jarmai ya ce "Allah ya sawwaƙe, yarinyar da ta iya guduwa daga gidan iyayenta tsawon kwanakin nan, ai kowa ya san bariki ta tafi, dama can waya sani ko a ɓoye yawon bokon nan abin da take yi kenan, kawai ku biyani kuɗina ko in kai ku wurin 'yan sanda a birni". "A'a ba za ayi haka ba, insha Allah zamu dawo maka da kuɗaɗenka, ba zata kaimu ga haka ba" "Ato a san abin yi tun da wuri, kan ta kacame mana". Kawu Bala ya tafi gida yana jujjuya lamarin a zuciyarsa, ya san jarmai ba shi da mutunci a kan kuɗi ba abin da ba zai iya aikatawa ba. Kawu Bala na zuwa gida, ya sa aka taso masa Lawan suka keɓe. "Lawan, Jarmai fa na neman ya tona mana asiri a garin nan, yanzun nan ya tare ni a masallaci ya ce mu dawo masa da kuɗinsa ko ya kai mu wurin 'yan sandan birni" "Kai Jarmai ba shi da mutunci Wallahi" "Ai ba laifin Jarmai ba ne, duk laifin wannan shegiyar yarinyar ce, da ta na nan ai da duk haka ba ta faru ba, Allah wadaran yarinyar nan" Kawu Lawan ya ce "matsiyaciya ba, na san tana can ta bazama bariki, dan da tana garin nan da tuni an ganota, ko ubanta ya san ta gudu oho" "To waya san musu" "Ni anya makuwa ba da haɗin bakin Hanne yarinyar nan ta gudu ba?" "Nima na fara zargin haka, dan ban yadda da matar nan ba, amma yanzu yaya za muyi da Jarmai" "To yanzu dai ya za ayi a mayarwa da wannan masifaffen kuɗinsa?" Kawu Bala ya ce "Yanzu dai idan gari ya yi haske, aje gidansa a kwaso kayan nan, a mayarwa da Larai dillaliya, kai kuma ka lalubo abin da za a samu a wurinka". "Me kuwa za a samu a kuɗin, kar ka manta a kuɗin aka saiwa Gali babur, ka cika kuɗi ka sai babbar gona, ai ni ban wani mori kuɗin nan ba". Kawu Bala ya ce "Haka ne, amma duk da haka dole kayi wani abu, ko 'yar wurinka Abu zamu ba shi a madadin Amina?" Kawu Lawan ya zaro idanu ya ce "Ni in ɗauki 'ya ta in bawa Jarmai, Allah ya kiyaye ya sutura, Wallahi gara ta mutu ba aure, sai ka ce baka san waye Jarmai ba? Ka aura masa Sa'a mana ai ita ma ta isa Aure". "Kai baka Aura masa Abu ba, sai ni zan aura masa sa'a? Wannan mutumin banzan Allah ya kiyaye, dama dai Aminan ce. Yanzu dai idan gari ya yi haske, za a kwaso kayan a mayarwa dillaliya, mu san yadda za mu yi a haɗa masa kuɗinsa". "To shikenan, Sai an jima, amma dai Wallahi ka je ka ritsa Hanne, dan wataƙila ta san komai, matar munafuka ce". Bala ya ce "Bar ni da ita, zata gane kurenta" Yauma wankan doguwar rigar da ta yi, ba ƙaramin yi mata kyau yayi ba, sai da tun da ta shigo kallo ɗaya yayi mata suka haɗa ido, ya sauke idanunsa cike da fargabar kar ta yi masa wata tijarar a cikin mutane, dan ya fuskanci tamkar wani jin daɗi take yi idan ta ci mutuncin sa. Kasancewar babu malami a ajin, ya sanya Captain ya ce wa Yazeed, ya fito ya ɗan yi musu tutorial, a kan wasu courses ɗin. Yazeed bai musa ba, ya fito ya karɓi abin rubutu, sai da ya fara da addu'a, sannan ya kalli 'yan ajin ya fara yi musu bayani da yadda ya fahimci tambayar da malamin nan yayi a ranar da ya ce suyi amfani da waya, sannan ya shiga gaya musu dabarun da ya bi wurin gane amsar tambayar. Fadila ji tayi ba zata iya zama jin shirmen da Yazeed yake yi ba, duk ajin a rasa wanda zai yi tutorial sai shi, ita gaba daya ta gama raina shi, ta ɗau jakarta tana mita, a fili take cewa "Instead of a nemo malamin da ze mana covering Wannan period ɗin, kawai an samu a gaba wani yana shirme, mutumin da ko turanci bai iya ba me zai koyawa wasu?". "Babbar yarinya wai dan Allah mai yasa ki ke haka ne? Wannan fa ba girmanki ba ne, bawan Allah nan mutum ne, ba zai ji daɗi ba abin da ki ke yi masa". "To kar Allah ya sa ji daɗin mana, ya daina shishshigi da son nuna ya fi kowa iyawa" Babson ya ja wani uban tsaki ya ce "Dalla ku share wannan mahaukaciyar ku cigaba da yi mana abin da yakamata". "Ba zan kula ka ba, barber ka ke ko me? Talauci ne yake ɗawainiya da kai ka ke wannan shirmen" ta yi tsaki ta fice. Har ta yi ta gama Yazeed bai ko ɗaga kai ya kalleta ba, ya karɓi wayar Captain, ya cigaba da yi musu bayani. Captain ya ce "Yazeed, dan Allah ka yi haƙuri, na sani abin da yarinyar nan take yi maka babu daɗi, amma dan Allah ka yi haƙuri" Cikin dakiya da basarwa Yazeed ya ce "Kar ka damu Captain, ni ban damu ba" ya cigaba da abin da yake yi. "Kina Ina? Munafukar banza fito nan" Sai da cikin Inno ya kaɗa, dan tun da taji muryar su Kawu Lawan, ta san ba alkhairi. Fitowa ta yi daga ɗaki tana faɗin "Lafiya kuwa?" "Kya tambayi lafiya mana, munafuka ha'ina, ki zo ki fito mana da in da yarinyar nan Amina ta ke, dan babu yadda za a yi ta gudu ba tare da haɗin bakin ki ba". "Haba Yaya Bala, ni meye nawa a ciki? Ya za ayi in goyi bayan Amina ta bijire muku, ko ta gudu? Nima fa Amina 'ya ce a wurina, ba zan goyi bayan ta aikata abin kunya ba, ni ban san in da take ba". Bala ya ce "Ai kuwa ƙarya ki ke yi, kuma yadda ki ka haɗa baki da ita kika sa ta gudu, sai ki koma ki haɗo abin da ya samu a mayarwa da Jarmai kayan aurensa, tun da ta gudu". "Meye haɗina da kayan auren Jarmai? Bayan kuɗinsa da komai ku ya dabƙawa kuma babu abin da kuka bamu a ciki?". "Rufewa mutane baki, amma dai kin san abin da aka yi kuɗin ko? Kayan katako aka sayawa Amina da su" "Amma yaya Bala, ina a kuɗin gonar mahaifinta aka saya mata kayan? Ni dan me za a ce in bada wani kuɗi" "Au tuhumar mu zaki yi, to Wallahi sai kin kawo wani abu, dan sunan mu ba zai ɓaci a banza ba a dalilin ku ba, mutanen banza kawai" Galala haka Inno ta bi su Lawan da kallon mamaki da kuma ƙarfin hali. Amina aiki suke sha a gidan nan kamar ba gobe, kasancewar Amina nai kaifin ƙwaƙwalwa ya sanya nan da nan ta iya abubuwa, ita aikin fa suke ba ya damunta, dan in dai aiki ne ta riga ta saba da shi tun a ƙauye, dan sam ba ya mata wahala, ita wulaƙanci da kallon ƙasƙantattun da ake musu ne yake damunta, shima da tuna ga burinta da yake ranta wanda take sa ran cikawa sai ta yi ƙoƙari ta manta komai. Dan kusan kullum idan ta je wurin Baba nasihar sa kenan a gareta, ta yi haƙuri. Amina na ta saka ran ganin wanda zai kaita Makaranta ya dawo, amma shiru ba ta ga ya dawo ba, kuma ba ta ji ana batun dawowar ta sa ba, ta dai yi shiru ta danne abun a ranta, dan abin ya fara damunta, idan aka aiketa ita da Hajara, tana ganin 'yan Makaranta hakan ya tabattar mata da an koma Makaranta. Yau sun gama aikin su kaf, sun gyara ko ina, wanda ƙarfin aikin ma Amina ce ta yi shi, ta zauna a falo tana kallon TV, sai ga Fadila ta dawo daga makaranta, ta shigo falon ba ko sallama, ta dire jakarta a falon, da mayafinta ta kalli Amina ta ce "Ki kawo mini su ɗaki". Amina tabi bayan Fadila da kallo ta taɓe baki, a ranta ta ce "Kin shigo ba ki mini sallama ba balle sannu da gida, kuma kin yi dakon jaka da mayafi tun daga makarantar, ƙarasawa da su ɗakin ki shi ne aiki a wurinki, ai kuwa ba zan kai ba' daga haka ta tashi ta bar falon, tayi tafiyarta wurin Baba. "Uwata, in ce ko dai kin gama duk ayyukan da aka saka ki kan zo nan?" "Eh Baba, na gama komai". "Yawwa Uwata ta kaina, banda ganda ko gardama dan Allah, yi nayi bari na bari". "Insha Allahu Baba, nace yaushe zaka je ƙauye ne? Da na ji kace a wannan satin" "Eh a wannan satin na so zuwa, amma nafi son in ga yaron nan da zai kai ki Makaranta ya dawo, an kai ki kin fara zuwa sai inje". "Wallahi Baba kamar ka san abin da ke raina, na yi shiru ne kawai dan kar in takura maka, amma naga an koma Makaranta". "Mu ƙara haƙuri dai, tun da ya ce za a kai ki, na san za a kai ki insha Allah" "To shikenan Baba, amma nace mai zai hana idan zaka ƙauyen muje tare ina kewar Inno da yawa". "So kike muje su sake riƙe ki ko?" Da sauri ta girgizawa Baba kai. "To idan ba haka ba, ki cire rai da zuwa ƙauye, har sai Allah ya sa kin kammala sakandirenki" "To Baba Allah ya zaɓa mana abin da ya fi alkhairi". "Ameen Uwata ta kaina" Ta shantake abinta, ta cigaba da hira Baba, har sai da aka yi kiran sallar magariba, sannan ta koma ciki. Kamar yadda Fadila ta bar jakarta da mayafi suna nan a wurin, Amina kuma bata bi ta kan su ba, ta wuce ɗakin da take. Fadila ba ta tashi sanin Amina ba ta kai mata jakarta ɗaki ba, sai da ta tashi tafiya makaranta da safe, ta nemi jaka ta rasa, ta duba ɗakinta kaf ba ta jaka ba, dan haka ta fito falo tana neman Asabe, dan ta ji in da ta ajiye mata jaka bayan ta gyara mata ɗakinta, sai dai tana fitowa ta ga jakarta da mayafinta a in da ta ajiye su, buɗe baki ta yi da mamaki, bayan ta tuna taga 'yar mai gadi jiya a falo. Cikin fushi ta fara ƙwalawa Hajara kira, Hajara da ke kitchen ta jiyo kiran Fadila ta taho da gudu, ta durƙusa. "Ina wannan yarinyar da ku ke aiki da ita?". Hajara ta ce "Wai Amina?". "Ko ma wacece, ki kira mini ita yanzun nan". "To bari in kirata, naga yau tun da aka yi sallar asuba bata fito ba, kuma ba ta saba hakan ba" "Ke dalla ɓace mini daga gabana ki je ki kira mini ita, kin tsaya kina mini wasu surutan banza" Cikin hanzari Hajara ta bar wurin, ta nufi ɗakin Amina, ta tsaya a ƙofa tana ƙwanƙwasawa. Amina ta na zaune, tana rubutun Alƙur'ani a cikin littafin da ta taho da shi daga ƙauye. Saboda yau ji ta yi tana kewar makarantar Allo, da tana ƙauye da tuni tana nan ta wanke allonta, ta yi rubutu, dan haka yau ta zauna bayan sallar Asubahi ta fara rubutunta.   Tana jin Hajara na buga ƙofa tana faɗin "Amina ki buɗe ƙofa, Fadila tana nemanki". Yamutsa fuska Amina ta yi, tare da tura baki, ta cigaba da abin da take yi. "Amine ki buɗe mana" "Dan Allah Hajara ki ƙyaleni, kullum da wuri nake fitowa, yau wani aiki nake yi, kiyi abin da zaki iya, sauran ayyukan ki bar mini idan na fito zan yi" "Ke bafa saboda aiki ba, Fadila ce take neman ki". Tsaki Amina ta yi ta ce "Kwa ci kan ku, ba wanda ya isa ya ɗagani daga zaman nan idan ba Allah ba, ko Baba ne ya kirani ba". Fadila ganin zata makara Hajara ba ta dawo ba, ya sanya ta ɗau jakarta ta fice ranta a ɓace, ta ƙudurce a ranta idan ta dawo sai ta koyawa su duka biyun hankali. Amina ba ta fito ba sai ƙarfe tara na safe, dan rubutunta ta zauna tai ta yi. A kitchen ta tarar da Hajara, "Anty Hajaru sannu da aiki". "Zaki ga Hajaru ganin idonki, yau kin caza mana bala'i, ba yadda ban ba ki fito amma ki ka yi mirsisi ki ka ƙi, ƙarshe sai tafiya ta yi, yau kashin mu ya bushe daga ni har ke idan ta dawo". Amina ta ɗage kafaɗa ta ce "Oho, duk masifar 'ya dai na san ba zata ɗauki raina ba, sai dai tayi ta ci kanta ita kaɗai". Buɗe baki Hajara ta yi tare da riƙe haɓa ta ce "Ke Amina dama haka ki ke?". Amina ta share Hajara, ta nufi ƙofar fita tana cigaba da ƙunƙuni. Tana fita harabar gidan ta hango Baba, ya shirya cikin wani milk ɗin yadi. Ta ƙarasa ta gaishe shi ta ce "Baba ya naga kamar fita zaka yi?". "Eh mana, dama ke nake jira in ga fitowarki in yi miki sallama, ƙauye zani". "Baba da gaske?". "Ahh ji ja'ira zan miki ƙarya ne?". "Wayyo Allah, Baba ka gaishe mini da Inno, na so zuwa in ganta, sannan dan Allah ka bata haƙuri, na san na sata a tashin hankali tahowar nan da na yi, bari inje cikin gida in ɗauko maka Abincin karina ka kai mata". Baba ya ce "A'a ba za ayi haka ba, zan musu tsaraba a hanya". "Baba dan Allah ka tsaya, yanzu zan dawo". Amina ta ruga cikin gida. "Hajara, dan Allah bani leda in zubawa Baba Abincin karina ya kaiwa Innota". "Au yau zai je garin naku?". Amina ta ce "Eh yau zai je". Hajara ta ce "Wane irin in baki leda, viva zaki samu, har kayan marmarin nan na cikin firinji da suka kusa lalacewa, duk ki bashi ya kai mata". "Ahh Hajara sata fa kenan, ba a bani ba". Hajara ta ce "Dalla bari kiga, idan ki ka tsaya sai sun baki, ba zasu taɓa baki ba, sai dai su ruɓe ki kwashe ki zubar, kuma ai ba ayi mana iyaka a kan Abincin gidan nan ba" Hajara ta ƙulle soyayyen dankali kaya guda da miyar ƙwai, da manyan magwaro da lemo, ga uwar kankana har da su biscuit. Ita dai Amina taji a ranta duk babu daɗi, tamkar sata suka yi. Hajara ta rakata suka kai wa Baba, Baba ya duba kayan nan ya ce "Amina wannan kayan fa, kin tambaya ki ka ɗakko?" Hajara ta ce "Baba Hassan, ai ba ayi mana iyaka da Abincin gidan nan ba, kuma idan aka barsu ma a banza za su lalace, su ba su ci ba kuma ba su bayar ba, sai dai mu kwashe mu zubar". Baba ya karɓa ya kama hanyar tafiya. Fadila a gaggauce ta shiga ajinsu, kasancewar yau ta makara sosai, sai dai tana shiga ta tarar da lecturer ya na arranging ɗalibai, zai yi musu test. Lecturer da farko ji yayi tamkar ya koreta, saboda ba ta da kunya, amma ya ƙyaleta ya sakata a bencin gaban Yazeed. Sai wani haɗe rai take, tana hura hanci ita a lallai bata so aka ajiyeta a wurin da yake ba. Nan malamin ya rubuta musu test ɗin, tare da sake tuna musu, test ɗin maki Ashirin ce, Attendance ɗin da yayi kuma maki talatin, zai yi jarrabawar sa maki hamsin. Sannan ya kawo wani lecture yayi invigilating ɗin su, shi zai je wani ajin yayi lectures. A tambayar da ya yi musu ciki har da abinda Yazeed ya koya musu a aji, hakan ba ƙaramin farantawa ɗaliban rai ya yi ba. Kowa ya duƙufa ya fara rubutu, amma Fadila ta shiga rarraba ido, kamar an kwashewa karya 'ya'ya. Yazeed yana ta rubutunsa, yayin da malamin ke ta zagawa yana dudduba su. Yazeed ne ya lura babu abin da Fadila ta rubuta, banda sunanta lambar Admission ɗinta da question. Ya girgiza kai, a gurguje ya ƙarasa nasa, sannan ya waiga ya ga lecturer ba ya kusa da su, ya sanya bironsa ya taɓo Fadila. "Dalla meye haka?" "Ya naga ba ki rubuta komai ba?". "To ina ruwanka da ban rubuta komai ba? Aikin banza ɗan sa ido kawai". "Sorry ba sa miki ido na yi ba, bari in karanto miki". "Bana so". "A'a, kar ki manta fa bamu da Attendance ni da ke, kuma ya ce exams ɗin ma 50mrks ce, kar a kafe exams a ga kin faɗi, za a raina ki. Buɗe papern, in dinga karanto miki kina rubutawa". Ba kunya ta ware paper, ta gyara zamanta, yana karanto mata tana kwashewa a ta ta paper. Cikin rashin sa'a, invigilator ya hango su, aikuwa yana zuwa ya rubuta wa Yazeed -10 marks a paper ɗin sa, ba tare da ya hukunta Fadila ba. Babu wanda ya san mai ya faru, sai Fadilan da Yazeed, dan lecturer bai yi magana ba, kawai zuwa ya yi kan Yazeed ya tsaya, yayi masa minusing, yana yi masa minusing ɗin kuma, Yazeed yai submitting paper ya tashi ya fita. Fadila kuwa ko a jikinta, ita dai tun da Allah ya sa ta samu abin da ta rubuta shikenan, Yazeed yayi asarar maki arba'in a test. Inno kamar ta zuba ruwa a ƙasa ta sha, ganin Malam Hassan a gida, ta dinga murna, nan ta tashi ta fara ƙoƙarin ɗora girki, ya ce "Ba sai kin dafa komai ba, dafa ruwan zafi ga kayan shayi na taho da shi, 'yar ki kuma ta bada kayan kari a kawo miki". Inno ta ce "Aikuwa Malam ina ta baza ido in ganku tare, ni nan Saminu ya ce mini tana wurinka, ko dai ƙarya yayi mini?". "A'a bai miki ƙarya ba, ke dai gama ki zo mu yi Magana". Bayan Inno ta dafo ruwan zafi, Baba Hassan ya ajiye mata tulin soyayen dankali da miyar ƙwai, Inno ci take tana santi, tana anya na taɓa cin abinci mai daɗin wannan a duniya? Baba Hassan ya yi murmushi, ya ce "bani labari, yaya aka yi da ba na nan game da Amina?". Nan Inno ta kwashe komai ta gaya masa, har zuwa ɓatan Amina. Shima nan ya warware mata cewar, Amina wurinsa ta je, kuma ga hukuncin da ya yanke a kanta. Inno ta ce "Amma malam kaja ganin hakan daidai ne? Yarinyar nan ba ta ɓatawa kanta suna ba kuwa? Kun ɗau bokon nan kun sa a ranku kai da ita kamar ibada". "Hannatu, boko ba ibada ba ce, amma ba zaki gane rashin boko na cutar mu ba, sai kinji birni kin ga amfanin boko, insha Allah zamu yi alfahari da ilimin da Amina za ta samu". "To ubangiji Allah ya sa". "Salamu Alaikum! Salamu Alaikum!" Aka shiga kwaɗa sallama. Murayar kawu Lawan ce yake kwaɗa sallama shi da Bala. Baba Hassan ya fita cike da fara'arsa yana musu sannu da zuwa, ya shimfiɗa musu tabarma a tsakar gida, suka zazzauna Baba Hassan ya gaida su cikin mutuntawa a matsayin su na yayyensa. Maimakon su amsa sai kallon Banza da Bala ya yi masa ya ce "Ina fatan labri ya iske ka na abin kunyar da 'yar ka ta yi? Mun zaɓa mata miji za muyi mata aure, amma ta tsallake ta gudu ta shiga yawon duniya". Baba ya ce "Ashsha, ba yawon duniya ba dai Yaya Bala". "To yawon me ta tafi? Waye ya san in da take, ta bi ta ɓata mana suna da zuriyar mu a gari". Baba ya ce "Yaya ba ina goyon bayan abin da Uwata ta aikata bane, amma sanin kan ku ne duk garin nan ba wanda bai san Jarmai ba mutumin kirki ba ne, maiyasa za a bashi Aurenta?" Lawan ya ce "Idan ba a bashi ba haka za a barta ta cigaba da yawo a gari soƙai-soƙai sa'ar iayyenta ba aure, saboda wata matsiyaciyar bokon banza, to ka sani idan ta dawo daga yawon banzan nata ba dai a gidan nan ba, ta je idan dai bariki ce, na baya ma ba su ci riba ba". Baba ya ce "Subhanallah, Amina dai ba wani ta tafi ba, tana tare da ni a in da nake aiki a can birni, kuma gidan da nake sun ɗauketa aiki, da albashinta zasu dinga biya mata kuɗin Makaranta". Tafa hannu suka shiga yi suna salati. "Hassan, yanzu abin da ka aikata ka yiwa kan ka adalci kenan? Yanzu wannan zabgegiyar budurwa ka kai birni ta yi boko? A ƙauyen ma ya muka ƙare da ita, har muna faɗa ta faɗa saboda ta yi boko, shi ne ka kaita birni ta yi boko?" Cewar Lawan yana zazzaro idanuwa. Bala ya ce "Ka kyauta da kuka haɗa kai da 'yar ka kuka ɓata mana suna, mun gama shirin biki da gayawa jama'a ɗaurin Aure, amma ta gudu, ga Jarmai ya ɗaga mana hankali mu biya shi kuɗinsa. Amma in Allah ya yadda, tun da aniyar alkhairi muka yi niyyar ɗaurawa, amma kasa ƙafa ka rusa kai da ita, ku ka nuna bamu isa ba, insha Allah naku burin ba zai cika ba, in Allah ya yadda sai ta yi cikin shege a birnin nan, sai ta dawo da mummunan abin kunyar da sai ka kasa haɗa ido da mutane, sai bokon nan ta zame muku bala'i da masifa kai da ita!!!" Dafe ƙirji Baba ya yi ya ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un" Inno da take ɗaki tana jiyo su ɗora hannu ta yi a ka, jin jafa'in da ake janyowa Amina. Lawan ya ɗora da cewa "Ai yadda ya ja mana abin kunya a garin nan, sai 'yar ta sa ta janyo masa abin faɗa da nunawa, ka ɗau balagaggiyar yarinya ka kaita cikin wani ahalin da ba muharammanta ba, wai dan ta yi boko, muna nan za aje a dawo da abin nunawa, zaku gani daga kai har ita, hakkinmu ba zai bar ku ba da kai da ita, muna nan mun zuba ido, zaka gani. Yaya Bala tashi mu tafi". Gaba ɗaya jikin Baba yayi sanyi ƙalau da mugun bakin da yayyaensa suka yiwa Aminan, anya ba za a haƙura da bokon nan ba Amina ta dawo ayi Auren nan ba?! Domin samun update a kan lokaci, Follow me at Arewabooks Ayshercool7724 Watpad Ayshercool7724 Ayshercool 08081012143GABA DA GABANTA    P9 AISHA ADAM (AYSHERCOOL) Haka su kawu Bala suka ƙaraci faɗansu, kamar zasu tashi sama, suka kaɗe rigunansu suka fice. Baba ya yi shiru ya rasa abin da yake masa daɗi. Inno ce ta fito jiki a sanyaye tana kallon Baba. "Malam, an ya ba za'a haƙura da wannan karatun ba, ka dawo da Amina gida ba, irin wannan mugun alkaba'i da suke janyowa yarinyar nan, nifa gaba ɗaya jikina ya yi sanyi Wallahi". Baba ya ɗan yi jimm sannan ya ce "Insha Allah, babu abin da zai faru sai alkhairi, ina sa ran a sanadiyyar Amina mutanen garin nan su ga amfanin ilimi mussaman ga 'ya mace". "Amma Malam, ni fa na karaya wallahi". "Ki kwantar da hankalinki, babu abin da zai samu Amina sai alkhairi Insha Allah". Hajara na dininga tana kwashe kwanukan da aka karya a kai, Amina kuwa duk ta sauke kayan kallon falon, tana musu duster saboda ƙurar da suka yi. Hajiya Zainab ta fito daga sashenta, tana ƙarewa falon kallo, dan ta samu wani laifi da zata sauke musu masifa amma ba ta samu ba, zuwa yanzu ta fara jin daɗin aikin Amina, dan sam bata da ƙyuya, kafin ace ta yi ma tayi, kuma ba ta son ƙazanta sam. Hajiya Zainab ta ce "Yawwa Hajara, in an jima Khalil zai dawo, ki ɗauki mukullin sashinsa a shiga a gyara masa, sannan ku sanarwa da Isyaku ya wanke masa motarsa, dan na san da ya dawo zai buƙaci ya fita da ita, sai kuma a yi girkin rana da shi, ni zan fita wataƙila har ya dawo ban dawo ba". Hajara ta risuna cikin ladabi ta ce "To Hajiya, insha Allah za ayi yadda ki ka ce, sai kin dawo". Har Hajiya Zainab ta kai bakin ƙofar falon, ta waigo ta kalli Amina da take ta aikinta ko kulasu ba ta yi ba ta ce "Ke, wato kin fi ƙarfin ki gaishe ni ko?" Amina ta ɗago ta kalli Hajiya Zainab ta ce "Hajiya na gaishe ki ɗazu da ki ka fito karyawa". "To kin fi ƙarfin ki sake gaishe ni ko kice mini sai na dawo ne?" Amina ta ce "A'a ki yi haƙuri, A dawo lafiya Allah ya tsare". Ba ta amsa ba ta ce "Ki shiga ɗakina ki tattara kayana suna nan ki ninke ki shirya mini su, amma sai kin musu kabbasa tukuna". "To zan yi insha Allah" Hajiya Zainab ta juya ta fice. Amina a ranta ta ce "Dan jaraba, dole sai an ƙaƙalo abin da za a ƙasƙantar da kai' Ta ɗago ta ce "Yaya Hajaru, wanda zai dawo ɗin nan, shi ne wanda zai kai ni makarantar?". Hajara ta ce "Eh shi ne". "Allahu Akbar, to shi ya yake? Yana da kirki ko shima dai duk haka suke?". Hajara ta ce "Eh to, ba na ce ba, shi dai gashi nan miskili ne dai sosai, kuma bai fiye shiga abin da ba ruwansa ba, kuma ba ya wani shiga sabgar 'yan aiki, shi yasa idan nace miki ba shi da kirki na yi ƙarya, dan bai taɓa yi mini ba" Amina ta washe baki ta ce "Allah ya sa dai kar yayi mini nima, koma ba shi da kirkin lallaɓa shi zan yi, in bishi a sannu in ta masa biyayya dan ya kai ni Makaranta, ni ɗauko mukullin sashin nasa, muje a gyara". Hajara ta riƙe haɓa ta ce "Ohh ni Hajara, yadda ki ke ƙaunar karatu Amina, Allah ya cika miki burinki ya sa al'umma su amfana" "Ameen Yayata". Ko da su Amina suka shiga sashin Khalil, mamaki Amina ta dinga yi, ɗakinsa har ya fi na Fadila tsaruwa, komai akwai sashinsa har da kitchen da kwanukansa da komai, hatta fridge da cooking gas duk akwai. Amina ta zage suka ƙara tsaftace ko ina, sannan suka baro sashin. Amina na ta fatan Allah ya sa yana dawowa babu ɓata lokaci ya kai ta Makaranta. Alhamdilillah, Hafsa ciniki ya nata haɓɓaka, sai ai babban abin da yake ci mata tuwo a ƙwarya bai wuce yadda maza ke zuwa su taru a wurin ba wanda sam hakan ba ya yi mata daɗi, gashi wasu 'yan iska wasu na kirki, da yake gata ga wurin mai shayi, wasu ma haka zasu zo su zauna suna shan sigari a wurin.  A haka wasu suke nuna suna sonta, da zarar ta musu halin nata na miskilanci, sai zagi da cin mutunci, ita dai bata taɓa ɗaga kai ta kula kowa ba balle ta bar abin faɗa. Abin na damunta, amma ba ta gaya wa Mama ba, dan da zarar ta ji abin da yake faruwa, zata iya dakatar da cigaba da sayar da awarar, kuma idan ta dakatar sana'ar me za suyi?. Dan haka ta ja bakinta ta yi shiru, take ta Addu'a Allah ya kawo musu mafita. Tun bayan fitowar su daga test, Fadeela sai murna take yi, ko bakomai ta samu abin da ta rubuta, amma sam ba ta ji ta damu da abin da ya faru da Yazeed ba, dan a ganinta ai ba ita tace ya taimaka mata ba.   Tana tsaye tana waige-waige, ta hango Yusra tana ƙarasowa in da take, ta kalli Fadila ta ce "Girl ya na ganki duk wani iri ne?" "Bari kawai unexpected test aka yi mana". Yusra ta yi murmushi ta ce "Baki shirya ba kenan?". Fadila ta ɗan yamutsa fuska ta ce "Ina na wani shirya, ni gaba ɗaya ma bana gane course ɗin, gashi dama muna takun saƙa da lecturer, kinga wata applied question da ya yi mana, abin ba a magana". "Amma dai kin rubuta wani abu ko?". "Me kuwa na rubuta? Wani ne ya gaya mini na rubuta, shi kuma aka yi masa minusing marks". Yusra ta ce "Subhanallah garin yaya?". Nan Fadila ta bata labarin Yazeed. "Girl gaskiya ba kya kyautawa, ban ji daɗin abin da kike masa ba". "Ni na sashi ya dinga mini shishshigi? Kinga ni muje in samu wani abun in ci yunwa nake ji". Yusra ta kalli agogon hannunta ta ce "No, kinga yau Friday, zo muje masallacin cikin school mu saurari huɗuba, idan aka yi sallar juma'a, sai mu je muci Abincin daga nan mu tafi gida". Fadila ta ce "Masallacin Juma'a sai ka ce wasu maza?". "Kin ji ki, ai mata ma na zuwa sallar juma'a, ma samu muji huɗuba" Haka Yusra ta takurawa Fadila, suka tafi masallaci, a hanya Fadila take sanar wa da Yusra da batun dawowar Khalil. Suka dinga planing ɗin yadda zasu shawo kan Khalil a kan ya so Yusra. Suka ƙarasa masallacin mata, suka shiga suka zauna. Sai dai shiru liman bai zo ba, balle a fara huɗuba, can aka fara gyaran murya aka fara da buɗewa da addu'a, can kuma ya fara gabatar da huɗuba cikin harshen larabci. Subhanallah, kai ba ka ce mai yin huɗubar ya taɓa jin yaren hausa ba, duk da Fadila ba ta jin larabci, amma ta nutsu tana sauraren yadda huɗubar ke ratsata, bugu da ƙari yaren larabci na matuƙar burgeta, aka jima ya fara huɗubar da Hausa, wanda yayi huɗubar akan tsoron Allah da riƙon gaskiya yayi, ya yi amfani da hikima sosai a wurin gabatar da huɗubar. Bayan ya kammala kuma, aka tada salla. Subhanallah sai da ya fara karatun Alkur'ani, a lokacin wata nutsuwa ta sake saukarwa Fadila, muryarsa mai daɗin amo da saurare, ga wurin yayi tsit kamar ruwa ya cinye su. Fadila ji ta yi tamkar kar a idar da sallar nan, saboda tsananin daɗin karatun, tabbas makarancin gwani ne wurin iya sarrafa harsashe, dan hatta a cikin huɗubarsa akwai salo na narka zuciyar mai sauraro, karatunsa akwai amo mai sanyawa zukata nutsuwa. Haka aka idar da sallar nan suka nufi wurin cin abinci, amma still Fadila na cigaba da jiyo karatun nan a cikin kunnuwanta, tamkar ta magantu sai kuma ta yi shiru, suka tafi cin Abinci. Bayan sun kammala cin abincin, Yusra ta tafi don ta kammala lectures ɗinta na ranar, Fadila kuwa suna da lectures 2-5. Ko da ta shiga ajinsu, ta tarar da duk matasan samarin nan na ajin su, sun kewaye Yazeed, shi kuma ya ɗan ɓata fuska duk da da wuya ka ga fushi a fuskarsa, dan mutum ne mai yawan murmushi, da alama dai sun takura masa, sai sunkuyar da kansa yake yi. Captain ya cire hular kan Yazeed, ya duƙa a gaban Yazeed yana cewa ya Sheikh, a shafa mana karama. Wani siririn kyau ne ya bayyana a fuskar Yazeed, bayan Captain ya cire masa hula, yana da wani kwantaccen baƙin gashi, da ya haɗe da sajensa ya kwanta a fuskarsa, zuwa ɗan madaidaicin gemunsa. Ya miƙa hannu ya karɓi hularsa tare da mayarwa kansa. Yamutsa fuska Fadila ta yi ta ce "Dan Allah ku tashi ku bani wuri, kawai kun kafa daba kun cikawa mutane kunne da hayaniya". Captain y kalli Fadila ya ce "Ke kul, mun kafa dabar kwasar tabarraki ne, ashe muna zaune da babban malami amma babu labari, ai tun da nake zuwa sallar juma'a ban taɓa jin huɗubar da ta ratsani kamar wadda Sheikh, Malam Yazeed ya yi ba" Saroro Fadil ta kalli Captain ta ce "Kamar yaya?". "Ai duk wanda ya je sallar juma'a yau a masallacin school ɗin nan, ya ji yadda ya dinga zuba larabci, sai ma da ya fara karatun Alqur'ani, kamar mutum ya suma dan daɗi" She can't believe that Yazeed ne ya yi wannan karatu, guntun tsaki ta ja, ƙila ma ƙaryar Captain ce kawai. Zama ta yi a wurin zamanta ta yi shiru, tana tunanin muryar da aka yi huɗuba, tabbas muryar Yazeed ce, ko da be fiye surutu ba, amma muryarsa a nutse take cike da nutsuwa da kuma iyayi, kamar yadda take faɗa. Shi kuwa Yazeed tuni ya bar ajin, dan baya son abin da suke masa sam. Nan taji ana hirar, limamin masallacin ne ba lafiya, ya shirya zai taho, ya yanke jiki ya faɗi, kuma ba a samu information da wuri ba, an tsaya mujadalar wanda zai ja Sallar, shi ya karɓa ya yi. Har aka shigo lectures, Fadila na satar  kallon Yazeed, da son tabattar yanzu daga bakin wannan ɗan tahalikin wannan karatun ya dinga fitowa ɗazu? Sam babu kama. Karaf Yazeed ya ɗago ido, suka haɗa ido da Fadila, wata uwar harar ta watsa masa, kamar ba ita take kallonsa ba. Ɗauke idonsa yayi, yana fatan Allah ya sa ba wata tsiyar Fadila take shirya yi masa ba. Amina wuni tayi tana sintiri tsakanin falo da harabar gidan, dan ganin me kaita makaran ya dawo, amma babu shi babu alamar sa. Gaba ɗaya har ranta ya fara ɓaci ta fara tunanin ko dai ba yau ɗin zai dawo ba. Shi kuwa Khalil tuni ya dawo, dan tun bayan azahar ya dawo, ya shiga sashinsa, ya yi wanka ya yi kwanciyarsa dan a gajiye yake sosai. Ya makara sallar la'asar, dan haka a ɗakinsa ya yi ta, sannan ya shirya ya fita. Amina kuwa tana zaune a falo, ta zubawa TV ido, tana kallo, tana fuskantar wani abu daga larabcin da ake fassara yaren jaruman. Ba tsammani ta ga mutum ya faɗo falon, dogo da shi kawai ya sa kai ya nufi sashin Hajiya Zainab, ba tare da ko sallama ya yi ba. "Kai bawan Allah daga ina? Zaka faɗowa mutane haka ba sallama kawai ka miƙa wuya kamar raƙumin jeji zaka wuce". Cak ya tsaya, ya waiwayo ya kalli bakin mai wannan maganar, gabanta ne ya faɗi da suka yi ido huɗu da shi, sai yanzu ta tuna da uwar ba'ar da tayi masa, ga kammaninsa sak da Alhaji Ahmad sun bayyana, ba in da ya bar mahaifinsa a kamanni, sai dai yafi Alhaji Ahmad ƙuruciya ko ba a gaya mata ba ta san wannan shi ne wanda aka ce zai dawi. Amina ta hau kame-kame "Yi haƙuri dan Allah, na manta Hajiya ta ce zaka dawo, kuma kaga kaine ma da ka shigo ba ka yi ko sallama ba, amma dai Hajiyar bata nan ta fita, ina wuni". Ƙare mata kallo ya yi a ransa ya ce "Ko wacece wannan, a ina aka samota kuma oho?" Bai kula ta ba ya cigaba da tafiyarsa. Yana wucewa Amina ta ce "Subhanallaahi, na yi shirme wannan shegen bakin nawa, Allah ya sa kar ya gayawa babarsa na masa rashin kunya. Amma ai ba rashin kunya ba ce gaskiya ce ka shigo zalau-zalau babu sallama". Amina na nan zaune ta taradaddin abin da ta aikata, Hajara ta fito falon, sai dai Amina ba ta gaya mata me tayi ba. "Amina ya na ganki wani iri ne haka?" Amina ta girgiza kai ta ce "Ba komai". "To shikenan, mai yakamata a dafa ne yau da daddare?" Amina ta ce "Nima ban sani ba, a dafa abin da ya sawwaƙa" "Wai naga gaba ɗaya yanayinki ya canza". "Ba komai fa, kawai ina tunanin Baba ne". "Ke Amina, baban da ɗazu ya tafi kuma zai dawo". "Ai ba yau zai dawo ba, wataƙila sai gobe ko in Allah ya kaimu jibi" suna tsaka da hirar sai ga Khalil ya fito, nan da nan Amina ta yi shiru. Hajara ta risuna ta ce "Ina wuni Yallaɓai, ashe ka dawo?". "Eh na dawo, Fadila ba ta dawo daga school bane?". "Eh har yanzu ba ta dawo ba". Khalil ya ce "Well Shikenan". Hajara ta sake risunawa ta ce "A kawo maka Abinci ne?" "Eh ajiye mini a kan dining, zan shigo in ci". Amina dai ba tace komai ba, sai zazzare ido da take yi. Bayan fitarsa Hajara ta ce "Shi ne fa wanda zai kai ki makaranta, da ki ke ta jira ya dawo, ya dawo amma ba ki iya gaishe shi ba". "Na gaishe shi mana, ai ina zaune a nan falon ya zo ya wuce". Hajara ta ce "Au to, ai na zaci baki kula shi bane, shi gaskiya ba shi da matsala sosai, be fiye wulaƙanci kamar ƙanwarsa ba". Ita dai Amina fatan ta, Allah ya sa kar abin da tayi masa ya sanya ya ce ba ze kaita makaranta ba. Fitarsa babu daɗewa ya dawo, ya zaune a kan dininga ya zuba Abinci ya fara ci. Amina sai satar kallonsa take, ko zai yi magana amma bece komai ba. Tana cikin wannan zullumin Fadila ta faɗo falon babu ko sallama, ranta a haɗe da alama ta gaji matuƙa. Sai dai tana ƙarasa shigowa falon, tayi tozali da Khalil ta saki murmushi. Ya kalli Fadila shima ya yi mata murmushin ya ce "'yan Jami'a" dire jakarta ta yi ta nufi dining ɗin tana cigaba da murmusawa cike da gajiya, ta janyo kujerar kusa da Khalil ta zauna tare da furta "Welcome home dear". "Ai ke zan yiwa welcome, ya school ɗin?". Ta taɓe baki ta ce "School gamu, muna ta shan wahala". Ya tsiyayo lemo mai sanyi ya kai bakinta, ta buɗe bakin tana sha tana lumshe ido, Amina zuba musu ido ta yi a ganinta wannan ai fitsara ce, su a ƙauye ai ko kusa da yayyanka namiji baka zama, balle a kai ga bada abu a baki. Khalil kuwa hirarsu suka cigaba da yi cike da kewar juna. Allah ya rufawa Amina Asiri ganin Khalil ya sanya Fadila ta laifin da Amina tayi mata da safe. Fadilan ta shiga bawa Khalil labarin abin mamakin da taji game da Yazeed cewa take "Brother bai fa iya turanci ba, ka ji kwaɓar da yake yi idan zai turanci, amma baka ji larabci ba, ni fa har yanzu mamaki nake, anya kuwa shi yake yi?". "Dama waye ya gaya miki sai ka iya turanci shi ne ka ke da ilimi?". "Ai ni na gama raina gayen ne gaba ɗaya, kai ka ganshi, kaga dressing ɗin da yake idan zai zo school? Wannan aka bashi taimako karɓa zai yi" Khalil ya ce "Ke kika ga haka, irin wannan basu da duniya ba balle abin da yake cikinta". Ta ɗan taɓe baki, tare da janyo plate ɗin gaban Khalil, ta sanya cokali ta fara ci. Labarin batun Amina tana wurin Baba a birni, za ta yi karatun boko kuwa ya cika gari, wasu suka dinga Allah wadai da tirr da abin da Baban ya aikata shi da Amina a ganinsu wannan tsantsar rashin hankali ne, da rashin sanin ya kamata. Ko da labari ya iske Jarmai, a ƙulu iya ƙuluwa, yayin da iyalansa suka dinga Allah ya ƙara. Gidansu Amina ya tafi, zuciyarsa cunkushe da takaici, na yadda ya ga samu sannan ya ga rashi. Ya sa aka yi masa sallama da Baba Hassan. Babu wani jinkiri kuma Baba Hassan ya fita, ya ƙarasa in da Jarmai ke tsaye tare da yi masa sallama ya miƙa masa hannu su gaisa, Amma Jarmai ya ce "ka ga ni ba wannan ne ya kawo ni wurinka ba, illa in zo in tabattar maka da na samu labarin abin a ya faru, ka haɗa kai da 'yar ka ta gudu, bayan nan an karɓe ni kuɗin Aurena, to tun wuri kaje ka samu 'yan uwanka, ku haɗu ku dawo mini da kuɗina, kafin in ɗauki matakin da ya dace a kan ku". Baba ya girgiza kai ya ce "To ai kaga ni ba ni na karɓi kuɗin Auren nan ba, bani da masaniya akan komai sai yanzu, dan haka bani zaka tambaya ba". "Oho dai, ni dai a biyani kuɗina kawai, aikin kawai mutanen banza" Baba dai bin Rabe kawai ya yi da ido, yana mamakin ƙarfin hali da rashin ta ido irin na Jarmai. Da Hajiya Zainab ta dawo, kusan raba dare suka yi da 'ya'yanta a falo suna hira, kowa yana kawo hirar abin da ya dame shi, suka ci Abincin dare tare, suka yi ta hira sai bayan sha biyun dare, sannan suka watse. Har washegari shiru, Amina ba ta ji Khalil ya yi Magana ba, hakan ya sa ta fara sarewa, wata zuciyar ta ce 'kije ki masa magana' wata kuma ta ce "Ki ƙara ba shi lokaci, kar ki yi garaje' gaba ɗaya ta bi ta ƙosa, gashi idan suka haɗu ko gaishe shi ta yi, sai dai ya kalleta ya ɗauke kansa, amma ba zai amsa ba. Ko aiki ne sai dai ya kira Hajara ya sata, amma ba zai kula Amina ba. Amina ba ta da zaɓin da ya wuce ta cigaba da Addu'a, dan haka ta duƙufa da sallar dare tana fatan Allah kar ya kawo abin da zai mata katanga da samun ilimin ta. Idan taga Fadila ta shirya zuwa Makaranta, abin ba ƙaramin burge Amina yake ba, tana da burin zuwa Jami'a amma ba ta da tabbacin Baba zai iya ɗaukar nauyinta zuwa Jami'a, shiyasa take taƙaita burinta a iya Sakandire kawai. Yadin jikinsa kawai ta hango ta san shi ne, saboda zuwa yanzu zata iya ƙirga adadin kayan da yake sawa idan zai zo, dama takalmansa guda biyu ne kacal yake zuwa da su. Sai da taje daidai in da yake, sannan ta tada wata irin ƙura, ta bule shi da ƙura ta yi gaba abinta. Duk wanda suka ga abin da ya faru ba su ji daɗi ba, su kai ta bashi haƙuri, ya nuna musu bakomai ya cigaba da tafiya zuwa ajinsu. Yau a bencin bayan Fadila ya zauna, yayin da ita kuma take jikin window.    A nata gudanar da lectures kamar kullum. Tari ne ya sarƙe Yazeed, ya saka hankici ya toshe bakinsa, ya kifa kansa yana ta fama, yana tarin ƙasa ƙasa, ya ɗago idanunsa sun yi jawur. A lokacin  lecturer ya fita amsa waya, dan haka Yazeed  ya fara kira sunan Fadila a hankali, ta waiwayo tana yamutsa fuska ta ce "Meye?". "Dan Allah ki taimaka mini, jikin window nake so ki bani, ki dawo wurina dan Allah ba dan ni ba, bana son zafi, bana iya numfashi sosai". Wata uwar harara ta yi masa ta ce "Au Allah, Sannu ajebo ai ni banga alamar hakan a tare da kai ba, ai da sai ka dinga dakon A.C ko fanka daga gida kana dasawa a wurin zamanka, ba in da zan tashi in je" ta juya ta cigaba da rubuce rubucen ta, shi kuma lecturer ya ɗora da bayani. "Dan Allah Fadila" ya faɗa yana jan numfashi. "Excuse me sir, kaga Wannan mutumin ya takura mini, sai kiran sunana yake ya hanani jin abin da ake yi". Lecturer ya ce "Malam meye haka? Kalleka da gemu a haka kamar na Allah, tashi daga wurin nan ka koma baya, seat ɗin ƙarshe na last row" Jimm Yazeed ya yi, sannan ya tashi tsaye a hankali ya nufi in da malamin ya yi masa umarni. Babson da ke kusa da Captain ya ce 'Shima gayen nan kamar wani maye, duk in da yarinyar nan take yana nan, tai ta sawa ana dizga shi, ni gani nake kamar sonta yake yi". Captain ya ce "Wallahi ƙila ƙarya take masa, ka san yarinyar 'yar wulaƙanci ce, ta gama raina shi, ni dama ƙanwata yake so, matar da ta auri wannan ta huta, mutum sai haƙuri kamar me". "Aikuwa in dai wannan shegiyar ce ba zata taɓa son sa ba, idan ta auri irinsa cutarsa zata yi, wai ita 'yar mai kuɗi wata banza da ita". Captain ya yi dariya Ya ce "Kai dai kawai ba kwa shiri ne". Tun yana iya ƙunshe tarin da yake, har ya kasa ya miƙe da sauri, saboda ya ɗau excuse ya hanzarta barin ajin, amma kan ya kai ga haka, ya silale ya faɗi a wurin. Nan 'yan ajin suka waiwaya dan ganin meke faruwa, sai dai Yazeed ko motsi ba ya yi, lecturer ya sa a ɗauke shi a fita da shi, ya samu wadattaciyar iska, dan da alama He is asmatic. Ita kuwa Fadila ko waiwayawa ba ta yi ba, balle ta san waye ya faɗin. Mintuna sha biyar, malamin ya ƙarƙare lectures ɗinsa, Fadila ta zari jakarta ta yi waje, dan gidansu Yusra zata je, saboda yau Yusra ba zata shiga school ba. Har ta gota in da ta ga 'yan ajinsu suka yi cincirindo, kawai sai ta ji tana son sanin waye ya samu asmatic attack ɗin. Ta koma da baya ta leƙa Yazeed ta gani a kwance, babu alamar yana numfashi, idanunsa a rufe! AYI TA HAƘURI DA NI RASHIN POSTING A KAN LOKACI, KU SANYA NI A ADDUOINKU, ALLAH YA BANI INGANTACCIYAR LAFIYA. TO GET THE LATEST UPDATE OF THE BOOK, FOLLOW ME ON WATPAD AYSHERCOOL7724 AREWABOOKS AYSHERCOOL7724 08081012143GABA DA GABANTA AISHA ADAM (AYSHERCOOL) P10 Zaro idanu Fadila ta yi, ganin Yazeed tamkar ya mutu, a mimmiƙe a wurin, jikinta ne ya yi wani irin sanyi, ta tuna yadda ta ji muryarsa yana roƙonta, ta bashi wurin zamanta saboda ba ya son zafi. Cikin rawar baki Fadila ta ce "Class rep ba za a kai shi Clinic a duba shi ba?". "Eh, A motar Hamisu muke so a kai shi, kuma motar tayi faci, sun je a gyara a zo tafi da shi". Cikin rawar murya ta ce "Kaga ku ɗauko shi da sauri, muje a kai shi a tawa motar". Babu wanda ya taɓa zaton Fadila zata iya abin Arziƙi haka, ganin yadda ta uzzurawa Rayuwar Yazeed. Cikin hanzari ta yi gaba, ta je ta buɗe motar, aka ɗauko Yazeed aka sa shi a motar Fadila, amma ta haɗe rai ta ce Mutum biyu ne kawai za su shiga, dan ba zata kwashi ƙartin banza a motar ta ba su hautsina mata ciki da warin hammata ba. Aikuwa Fadila ta sha zagi a wurin samarin ajin nan, ba ta bi ta kan su ba, ta take motar da ƙarfi ta bula musu ƙura, ta bar harabar wurin da gudun tsiya. Suna tafe lokaci lokaci, numfashin Yazeed yana dawowa, sai dai baya wuce ƙirjinsa, ga wani irin sound da fitar numfasin nasa ke fitarwa kamar numfashin zai rabu da gangar jikinsa. Gaba ɗaya hankalin Fadila a tashe yake, tana ji a ranta idan Yazeed ya rasa ransa, to tana da kamasho a cikin faruwar hakan. "Fadila ya naga kin fita daga cikin School, ba Clinic ɗin School za a kai shi ba?" Cewar Captain da ke rungume da kan Yazeed. "Gara a kai shi wani Asibitin, i don't want too much wahala, akwai asibitin da muke da retainership file, a nan muke ganin likita, bari muje can kawai". Shi Captain ma abin na Fadila mamaki yake bashi, ganin yadda duk ta ruɗe. Suna zuwa aka karɓi Yazeed, cikin kulawa aka shiga da shi Emergency room, Nurse ta kawo family file ɗin su Fadila. Doctor Aliyu ya kalli Fadila ya ce "Fadila wannan kuma a ina kika samo shi?". "Doctor he is my class mate, ya samu asmatic attack ne, shine nace mu kawo shi nan". Doctor Aliyu ya gyara zaman glashinsa ya ce "Dama can yana da Asma ne?". Fadila ta ce "I don't know fa, i have no idea kawai a duba shi ni dai kar ya mutu, amma ga abokansa nan a tambaye su". Captain ya ce "Ni dai ban sani ba, kin san ba shiga mutane yake ba, balle ayi hira ya faɗi yana da wani ciwo, ko kai Aminu ka taɓa jin ya faɗa?" Ya yi maganar yana kallon wanda suka kawo Yazeed tare. Aminu ya ce "kai baka sani ba balle ni, ni da banda gaisawa babu abin da yake haɗamu". Doctor Aliyu ya ce "Baku taɓa ganin yana shan wani magani ba?". Captain ya ce "Doctor, bawan Allah nan fa ba magana yake ba, ba ya kula kowa ba ya son hayaniya, kaga ƙawarsa nan Fadila ita yake kulawa ita kuma ba ta saurararsa, wataƙila da tana saurararsa, da ita ya gaya mata". Fadila ta haɗe rai ta harari Captain ta ce "Zan maka rashin mutunci ka kuma haɗani da shi, a ina na zama ƙawarsa? Yanzun ma akwai dalilin da ya sa na tsaya a kan a kawo shi Asibiti". Doctor Aliyu yayi murmushi tare da girgiza kai, kasancewar sa family doctor ɗin su, kuma nan Asibitin suke zuwa idan ba su da lafiya ya sanya ya san Fadila da halayenta. Gaba ya yi suka bishi a baya. Suna shiga Emergency, suka tarar da Yazeed kwance an sa masa Nebulizer, yana mimmiƙe a kan gado. Gaban Fadila ya kuma faɗuwa ganin halin da Yazeed ke ciki, ta tuna yadda ta baɗe shi da ƙura da hayaƙin mota, wataƙila ma hakan ne ya sa ciwon ya tashi. Doctor Aliyu ya cewa Aminu, ya zo ya taya shi a caje Yazeed, ko akwai magani a jikinsa, dan galibi masu irin wannan matsalar suna yawo da magani a jikinsu. Suka caje jikin Yazeed, jotter shi ce kawai a jikinsa da biro, sai carbi da Naira hamsin, suka ajiye a drower kusa da shi. Doctor Aliyu ya ce "Na so inga irin maganin da yake sha, amma bakomai bari mu gani zuwa anjima ko zai farfaɗo, na rubuta allurai a yi masa". Fadila ta ce "Amma Aliyu, kana ganin zai warke gani nake kamar mutuwa zai yi fa" tayi maganar ƙwalla na ciko idanunta. Aliyu ya ce "Ikon Allah, dama akwai abin da zai raunata miki zuciya haka Madam? Zai warke insha Allah, your besty will recover insha Allah, amma ki dinga kula da shi sosai, kin san ciwon nasu baya son wannan weather, banda yawo ba mask, ko zuwa wurin hayaƙi ko ƙura". "Dan Allah ka daina haɗani da shi, wai wani besty" Yayi murmushi ya ce "To na daina" Aminu ya yi musu sallama ya tafi gida, Captain ma yace zai je school ya dawo, suka bar Yazeed da Fadila kawai a Asibitin. Fadila sai kaiwa take tana komowa a reception ta kasa zama wuri ɗaya, tana yi tana leƙawa ɗakin da Yazeed yake, kasa jurewa ta yi, ta shiga ɗakin da Ya ke kwance. Ta taka a hankali, ta ƙarasa gaban gadon da yake kwance, ta kalli abubuwan da aka ciro a aljihunsa, ta ɗauki jottersa da carbinsa ta saka a jakarta, saboda kar idan ya tashi, zasu tafi a manta da su. Gani ta yi yana motsawa a hankali, ta ƙura masa idanu, tubarkallah idan ta ce Yazeed yana da muni tayi ƙarya. Gani ta yi yana rirriƙe katifar gadon da yake, yana ɗaga ƙirjinsa sama, sai kuma ya saki katifar, yana miƙe mata hannu, amma idanunsa a rufe. Ƙara matsawa ta yi jikin gadon, tana masa sannu, sai dai bai san me take yi ba, hasali ma bai san meye yake yi ba. Sai miƙa hannu yake yana riƙo duk abinda ya ji a kusa da shi, cikin sa'a ya riƙo hannun Fadila, hannunsa kamar ba na namiji ba, saboda taushi, sai ta zama kamar wata sokuwa ta rasa abin yi, a hankali yake murza yatsunta, yana jujjuya kansa, hawaye na zuba a gefen idanunsa, ga wani irin gumi da yake tsatstsafowa a goshinsa. Fadila zama ta yi tamkar wata gunki, wani irin abu ne ya fara kai kawo a jikinta, tun daga kanta zuwa ƙafafuwanta, wani baƙon yanahu ya ziyarce ta, tsigar jikinta na tashi, wani irin yanayi na ratsata, saboda a rayuwarta idan ba Khalil ko Daddy ba, babu wani namiji da taɓa samun wannan kusancin da shi haka, har hannunta a cikin nasa, sai doctor Aliyu, idan ba ta da lafiya zai mata allura ko sa ruwa, shi ma faɗa suke yi da shi, ta ce "Ba zai taɓa ta ba". Ƙoƙarin zame hannunta take daga na Yazeed, cikin jin zafin ciwo ya matse mata yatsu da ƙarfi, wanda har sai da ƙasusuwan yatsunta suka yi ƙara. "Washhh Allah, kai dalla ka sakar mini hannuna sai ka karya ni tukuna?" Ta faɗa a shagwaɓe. Ƙoƙarin miƙewa zaune Yazeed ya fara yi, ya kai hannu zai cire abin Nebulizer, ta riƙe hannunsa ta ce "Ka bari magani fa aka samaka" ta faɗa raunane. Bai saurareta ba ya cigaba da ƙoƙarin cirewa, da sauri ta fita ta kirawo doctor Aliyu, har Yazeed ya cire Nebulizer ya kifa ya kusa faɗowa daga kan gadon. Da hanzari Aliyu, ya gyara masa kwanciyar ya mayar masa da Nebulizer, ya je ya ɗauko wata allura ya yiwa Yazeed. A hankali bacci ya kwashe shi. Aliyu ya ce "Gaskiya ciwon nan nasa ya zama chronic, ki kirawo masa wani daga gidansu mana, a san halin da yake ciki". "Ni ina na san wani nasa, ɗan ajinmu ne fa kawai". "I see, amma kin damu da shi da yawa". "Ni ban damu da shi ba, kawai dai na san koma menene ya sameshi nice sila, idan ya mutu zan iya cewa ina da hannu a ciki shiyasa na damu". "Shikenan, ki zauna tare da shi, duk abin da kika gani ki mini magana". Fadila ta ce "to" Ta koma ta samu kujera, ta zauna a kusa da gadon nasa, ta ɗauko wayarta ta hau chatting da Yusra, a nan take bawa Yusra haƙuri, saboda rashin zuwanta gidansu, kuma ta bata labarin abin da ya faru. Amina na ɗakinta, sun kammala aiki tayi wanka, ta shirya tana ƙara gyara nata ɗakin, Hajara ta yi sallama. Amina ta amsa tare da kallon Hajara. "Ki je in ji Khalil". Amina ta ce "Waye kuma Khalil?". "Wanda zai kai ki makaranta" Ta buɗe baki ta ce "Haba da gaske?". Hajara ta ce "Zan miki ƙarya ne?" Kan Hajara ta gama rufe baki, Amina ta yi waje, ta nufi falo. Ta tarar da Khalil ya kammala breakfast, Hajiya Zainab na zaune a kusa da shi tana masa hira. Amina ta ƙarasa ta durƙusa a gabansa ta ce "Gani". Bai kalleta ba ya ce "In the next 30minutes, ki shirya zamu je a kai ki makaranta" Washe haƙora Amina ta yi cikin murna ta ce "Tom, Na gode Allah ya saka da alkhairi, ai ni na shirya ma, bari in je in jiraka". Hajiya Zainab ta kalli Khalil ta ce "Ban gane ba, kai ne zaka kaita makaranta?, ka bari babanta ya dawo ya kai ta mana". Khalil ya ce "No, kin san bakomai zai iya yi mata ba, Daddy ne ya bada umarnin hakan". Tsaki ta yi ta ce "Ni bana son irin haka, a ɗorawa mutum wahalar da ba ta sa ba, ba damar ka janyo mutum ɗaya, sun dinga ɗora maka ɗawainiya da wahalarsu kenan". Amina da ba ta kai ga barin falon ba, tana jin hajiya Zainab, amma tayi shiru ta wuce ɗakinta, ba tare da ta yi magana ba. Tana zuwa ɗaki, ta canza hijjabi, ta ɗauko littafi ɗaya a litattafanta da ta taho da su daga ƙauye, da bironta ta samo leda ta zuba su a ciki, ta ɗaure murmushin kan fuskarta ya kasa gushewa. Hajara sai kallon Amina ta ke "Amina sai kace wadda aka yiwa bushara da zuwa makka, wannan fara'a haka". Murmushi Amina ta yi ta ce "ni dai na tafi, sai na dawo" tayi waje a guje cike da farinciki. Wuri ta samu a nan harabar gidan ta zauna, tana jiran Khalil, ba ta wani daɗe ba saiga shi ya fito da waya a kunnensa yana waya, bai kula Amina ba ya nufi hanyar gate zai fita, ba ta da zaɓi illa ta tashi ta bi bayansa. Abdul ne zaune a cikin motarsa, ya ƙurawa gate ɗin ido. Khalil ya ƙarasa ya buɗe gaban motar, ya shiga. Amina kuwa tsaye ta yi, tana zazzare ido, Abdul ya miƙa hannu, ya buɗe mata motar, ta shiga ta zauna sannan ta risunar da kanta ta ce wa Abdul "Ina kwana?". "Lafiya ƙalau, ya kike ya gida?". "Ina lafiya ƙalau Alhamdilillah". "To Masha Allah, sannunki" ya mayar da dubansa kan Khalil da ke danna wayarsa ya ce "Malam ba gaisuwa ne?" Hararsa Khalil ya yi ya ce "Dan Allah ja mu tafi, anƙi a gaishe kan". Abdul ya ce "Haka ka iya, sarkin faɗa" A hankali Abdul ya ja motar suka fara tafiya, cikin motar ga sanyin AC, ga ƙamshin turaren jikinsu, ga ƙamshin droomer, duk ya cika motar, yanayin ya yiwa Amina daɗi sosai, sai kallon gari take ta jikin baƙin glass ɗin motar. Gaba ɗaya tsarin zubin ginin makarantar ya sha banban da irin zubin makarantunsu na ƙauye, ginin kawai ba ƙarmin burge Amina ya yi ba. A wurin parking Abdul ya tsayar da motar, Amina na ƙoƙarin buɗe motar, Abdul ya ce "Ki zauna muje mu fito tukuna, ni ya sunanki ne ma?". "Amina Hassan" Ya ce "Masha Allah, nice name, ki zauna muje mu dawo". Amina ta amsa da to. Abdul da Khalil, suka nufi dogon ginin da ke cikin harabar makarantar. Tana nan zaune a mota, kusan mintuna sha biyar, sai ga Abdul ya dawo, ya buɗe wa Amina motar ya ce "Bismillah zo muje" Amina ta fito daga motar, cike da farinciki tana sake ƙarewa makarantar kallo. Cikin ofishin shugaban makarantar suka shiga, suka tarar da shi a zaune tare da wasu malamai biyu, sai kuma Khalil. Har ƙasa Amina ta zube tana gaishe su. Director yayi murmushi ya amsa mata, tare da yi mata umarnin ta zauna. Ta samu wuri ta zauna, tana cigaba da ƙarewa ofishin kallo, a ranta ta ce "Allah sarki principal ɗinmu, insha Allah sai na gina masa Office irin wannan, mai irin wannan kujerun, shima a dinga sa masa turaruka masu ƙamshi". Muryar director, ta ji yana tambayarta sunanta da harshen turanci, ta ɗago tare da amsa masa, ya tambayeta sunan makarantarsu, ajinta nawa? Shekarunta nawa? Gaba ɗaya cikin harshen turanci, kuma ita ma cikin harshen turanci take mayar masa. Gaba ɗaya Khalil bai zaci ko Makaranta ta taɓa zuwa ba, dan a haka ya yiwa director bayani. Nan malaman nan suka fara yiwa Amina interview, sai dai duk ta basu mamaki, saboda kaifin basirarta, gashi duk abin nan cikin harshen turanci suke yi, kuma ko tangarɗa babu a bayanan nata da turanci. Aka yi mata tambayoyi a fannin lissafi, gaba ɗaya tayi soliving ba tare da amfani da calculator da aka bata ba. Director ya ce "Kai Khalil kace gifted ku ka kawo mana? Alhamdilillah na yi farinciki sosai da sosai, yanzu zamu bata aji, ƙarfe biyu muke tashi daga makaranta, na ji daɗi sosai na yaba da ƙwazanta, insha Allah zamu yi ƙoƙarin bata ilimi yadda ya dace, yanzu za'a kaita aji insha Allah". Amina ta ce "Ai bani da litattafai, littafi ɗaya na ɗauko". Director ya ce "Kar ki damu, duk kayan rubutu mu zamu baki, har da jakar Makaranta ma" Amina ta sake faɗaɗa fara'arta ta risuna ta ce "Na gode, Allah ya saka da alkhairi ya jiƙan magabata". Suka amsa da Ameen, babban abin da ya ƙara burge su da Amina, shi ne yadda take da tarbiyya da ladabi sosai. Suka fito daga Office ɗin tare da director, da su Khalil. Abdul ya kalli Amina ya ce "Idan an tashi daga Makaranta, kar ki je ko ina, ki tsaya a wurin da muka ajiye mota yanzu, zamu dawo mu ɗauke ki, saboda kinga baki san hanya ba". "To yaya Na gode, Allah ya biya muku buƙatunku na Alkhairi, ya sa ku gama da duniya lafiya, Allah ya shiga lamarin ku, ya saku farinciki kamar yadda ku ka sani" ta ƙarasa maganar har da hawaye a idonta, dan ba zata iya misalta farincikin da take ciki ba. Abdul ya yi murmushi ya amsa da "Ameen, ki dage kiyi karatu da kyau Allah ya bada sa'a, ga wannan in an fito break ki sayi wani abun" yayi Maganar yana bata ɗari biyar. Girgiza masa kai ta yi ta ce "A'a na gode zan iya zama har a tashi ban ci komai ba, a ƙoshe nake" tayi gaba tana ɗaga musu hannu. Wani irin murmushi ne ya suɓucewa Abdul, yarinyar ta burge shi, duk da ɗan karen surutunta, amma acting ɗinta zai tabattar maka da ga gidan tarbiyya take. Tsakin Khalil ne ya dawo da shi daga tunanin da yake, ya bi bayansa zuwa mota, suna tafe Abdul na yiwa Khalil hirar Amina da yadda ta burge shi. Banza Khalil ya yi masa, dan tun haɗuwar sa farko yarinyar ta yi masa tsiwa yake jin haushinta, ga ta da shegen surutu da iyayi kamar jefaffiya. An samu numfashin Yazeed ya daidaita, sai bacci da yake yi, saboda allurar da aka yi masa, har azahar Fadila ta je ta yi salla ta dawo bai farka ba, tana nan zaune taga ya fara motsawa a hankali, ta zuba masa dukkanin idanunta, dan babban fatanta dama shi ne taga ya tashi ya warware. Captain ya kira Fadila a waya cewar 'yan ajinsu zasu zo duba Yazeed, amma tace ya ware an sallame shi, saboda bata son ƙananan maganganu. A hankali ya buɗe idanunsa, yana ƙarewa ɗakin kallo, ya kalli hannunsa dake ɗauke da canular anyi hanging ɗin drip. A hankali ya juya ɗaya ɓangaren, ya yi tozali da fuskar Fadila, sai da gabansa ya faɗi, ƙoƙari yake ya gane, zahiri ne ko mafarki. "Sannu" ta furta kamar an mata dole. Ya jinjina mata kai alamar yauwa. "Ina ne nan?" Ya yi maganar yana kallonta. "Da ina ya yi maka kama?" "Yi haƙuri gani na yi ban san environment ɗin ba, dan Allah zan sha ruwa" ya ƙarasa maganar da sigar magiya, tare da tashi zaune ya jingina. Kamar ya yi mata dole, ta tashi ta buɗe ɗan ƙaramin fridge ɗin ɗakin, ta ɗauko ruwan roba mai sanyi ta miƙa masa. Ruwan sanyi ƙarara dan haka ya karɓa ya ajiye a gefe. "Ba zaka sha ba ka sa na ɗauko?" Ta yi maganar tana tsare shi da ido. "Yayi mini sanyi da yawa" Doctor Aliyu ne ya shigo ɗakin, ya tarar da Yazeed a zaune "Masha Allah, Alhamdilillah ka farfaɗo kenan?" Ganin farar riga a jikin Aliyu ya sanya Yazeed gane cewa likita ne. "Eh doctor". "To yaya kake jin jikin yanzu?" "Alhamdilillah, bana jin ciwon komai, sai rashin ƙwarin jiki". "Ok, shima insha Allah zai ware, for how long kake da Asma?" Yazeed ya ɗan yi shiru sannan ya ce "Gaskiya an jima, da farko pnuemonina ne, sai ya koma asma, to daga baya ya zama chronic, a hankali kuma da na ƙara girma, sai na rage samun attack ɗin, dan har ina aiki a cikin hayaƙi, ƙura idan ba tayi yawa ba ba ta damuna, rabona da ciwon ya tashi nafi shekara huɗu, sai yau na sheƙi hayaƙi da ƙura, na fara tari kuma daga nan ban san abinda ya sake faruwa ba" Haka kurum Yazeed ya bawa Fadila tausayi, ya sha wahala sosai daga ɗazu zuwa yanzu. Nan Aliyu yayi ta bawa Yazeed shawarwari tare da rubuta masa wasu magungunan, ya ce a sayo masa wani abun ya ci. Fadila ta fita ta bawa security Asibitin kuɗi, dan ya siyo wa Yazeed Abinci. Mamaki ne fal da tambayoyi a cikin ran Yazeed, amma ya san idan ya tambaya ba zai samu gamshashiyar amsa ba, sai ma dai baƙar Magana. Sallamar Yusra ce ta katse masa tunaninsa, Fadila na ganin Yusra ta miƙe tana faɗin "Beb sai da ki ka zo?" "Na kasa jurewa ne, na ce gara in zo in ga mai jikin, kuma naga Alhamdilillah shi ne a zaune ko?" Fadila ta ɗan taɓe baki ta ce "Sannu bawan Allah" Yazeed ya ce "Yauwa sannu da zuwa" "Allah ya sa kaffara ne" Ya amsa da Ameen. Security ne ya shigo da ledar wani restuarant, ya miƙawa Fadila ta sa hannu ta karɓa ta ciro dubu ɗaya ta bashi, ta fito da takeaway ɗin, ta buɗe dankali da miyar jajjage sai uban yankan naman kaji a kai, ta ajiye wa Yazeed ta ce "Gashi nan kaci, Aliyu ya rubuta maka sallama, in ka gama sai in ajiyeka a gida in wuce gida". Yazeed ya ƙurawa Abincin ido, amma yaƙi ko motsawa balle ta sa ran zai ci. "Magana fa nake maka kai mini banza" "Alhamdilillah na ƙoshi" ya furta yana kaucewa haɗa ido da ita. "Ban gane ka ƙoshi ba, amma a gabanka ya ce a samo maka Abinci ko?" Yusra ta ce "Kai kuwa ka daure ka ci mana, ko baka cin irin wannan?". Yazeed ya ce "Wannan ba cimata bace ta ɗan talaka, ba zan iya cin Abincin nan ba, Na gode sosai da kulawarki a gareni Fadila, ba zan manta ba har abada, amma wannan cimar ku ce ba irin tawa ba, zan ƙarasa gida na samu abin da zan ci a can" Tsaki Fadila ta yi ta miƙe tsaye, ta kalli Yazeed cike da masifa "Ni zaka rainawa hankali ka gayawa baƙar magana, in wuni a Asibitin nan saboda kai, na san silata ciwonka ya tashi amma ka raina mini hankali, tun safe nake Asibitin nan saboda kai, ko ruwa ban kai cikina saboda zullumi, amma daga tashin ka ka fara ɓata mini rai" ta cillo masa ledar magungunan da aka kawo daga Pharmacy ta ce "Gashi nan, idan ka ga dama ka ɗauka shima idan ba ka ga dama ba ka barshi a wurin aikin banza kawai" Yusra ta riƙota tana faɗin 'Haba Fadila ba a haka, ai sai ki zobe ladan ki, baki ga ba shi da lafiya ba, ki dinga haƙuri dan Allah" "Dalla sakar mini hannuna, ba za ai haƙurin ba" ta figi jakarta tayi waje fuuu. Yazeed kam murmushin gefen baki yayi, ya sauko daga kan gadon a hankali, Yusra tayi ta bashi haƙuri ya ce "Bakomai kar ki damu" sun kai ruwa rana da Yusra kafin ya yarda ya karɓi maganin, shima mutuncin yarinyar ya gani ya karɓa. Ya shafa aljihunsa ya ji babu komai, dan haka ya sadaƙar jotter sa, da hamsin ɗin jikinsa sun zube, a halin da yake ciki ya fara daɓawa da ƙafafuwan sa dan tafiya gida, ya samu masallaci ya rama sallolin da bai yi ba, daga nan ya wuce gida. Ƙarfe biyu Abdul ya addabawa Khalil a kan su koma su ɗauko Amina, ko da suka koma tana in da Abdul ya ce ta tsaya, goye da ƙatuwar jakarta ta makaranta. Tana ganin motarsu ta faɗaɗa fara'arta, ta ƙarasa ta buɗe motar ta shiga, wannan karon Khalil ne yake tuƙi dan a motarsa suka zo, ta gaishe su Abdul ya amsa, amma Khalil ya yi mata banza. "Amina 'yan makaranta, ya makarantar ya baƙunta?". "Lafiya ƙalau Alhamdilillah, bari in nuna maka litattafaina an cika mini jakata da litatafai, gobe in Allah ya kaimu za a bani Uniform, Baba ya sai mini takalmi da safa" Ta zuge jakar tana nuna masa, yace "Masha Allah, Allah ya sa a amfana, bari da yamma zanje da kaina in sayo miki takalmin". Amina ta girgiza kai ta ce "A'a Baba fa zai saya mini, kar ka damu, sai daɗi nake ji na koma Makaranta". Abdul ya ce "Sai kice Alhamdilillah, wai ni kuwa ya aka yi kika iya turanci haka?". "Malaman mu ne suke koya mini, a makarantar mu ana zuwa da ni debate ko quiz, su suke koya mini, kaga kuma muna da ƙaton Library, amma babu ɗalibai sosai 'yan garinmu ba su damu da karatun ba, akwai litattafai sosai a ciki, kuma ina da dictionary da nake duba Words, mu uku ni da wasu ƙawayena ake mana extra lessons a ƙauyenmu" Abdul ya jinjina kai ya ce "Lallai ashe gifted ce?" "A'a ni ba gifted ba ce, dagiya nake yi in gaya maka" "To ya aka yi ki ke son cigaba da karatu a nan? Ko can babu senior secondary School". Yamutsa fuska ta yi, ta tura baki sannan ta ce "Ƙannen Baba ne za su yu mini Aure, wai ba sa son ina zuwa boko, ni kuma na gudo wurin Baba" "Da an yi asarar talent, wannan ƙwaƙwalwar ta ki atleast yakamata ko secondary ki kammala ai" Amina ta sake ta dinga bawa Abdul labarin yadda tai karatu a ƙauyensu faɗi ba a tambayeka iri iri. "Ke shut up dalla!" Khalil ya buga mata wata uwar tsawa, da sai da cikinta ya kaɗa. Abdul ya ɓata fuska ya ce "Khalil ya haka?, Ya muna hira da yarinya zaka yi mata tsawa?". "Duk ta bi ta cikawa mutane kunne, ko haɗiyar yawu ba ta yi, i hate nonsense, ta kuma magana Wallahi sai ta sauka". "Khalil waye ya gaya maka irin wannan yaran ana katse musu hanzari? A irin wannan surutun nasu ba sa na banza, kuma ba a kan karatu take Magana ba?" Khalil yai wa Abdul banza ya cigaba da tuƙi. Tun da Amina ta firgita da tsawar da Khalil ya yi nata kasa magana ta yi, sai jikinta da ke ta tsuma. A ƙofar gida suka sauketa, ta yiwa Abdul godiya ta shiga gidan. Khalil ya wuce kai Abdul gida, suna tafe suna faɗa. Abdul ya ce "Kana hantarar 'yar mutane ba abin da tayi maka, ƙila ma ita zaka saka a wannan gidan da kake ta ƙerawa" Khalil ya ce "Kai fa mahaukaci ne wasu lokutan, da Mummy kaɗai ta isheni, kai idan aka ce zan auri wannan yarinyar sai ka yadda?" "Eh mana ba mace ba ce? Meye aibunta 'yar duma duma black beauty" "Yawwa an zo wurin, sai kace mini sonta ka ke yi" Abdul ya ce "Ai ni ka san wadda nake so, kuma alamu sun nuna ba za ka bani ba" Kalil Yayi guntun tsaki ya ce "Kai ka fiye shirme Wallahi" daga haka ya basar da zancen ya kai Abdul gida ya sauke shi yayi gaba. Wata hanya ya biyo, domin ya yi yanke, ya samu sauƙin go slow. A ƙofar wani kanti yayi parking, dan ya sai ruwan roba, na motarsa ya ƙare, ya miƙawa wani yaro kuɗin ya ce ya karɓo masa. Ya gyara zamansa, ya kashingiɗa da seat ɗin motar, ya ɗan waige ya hango wata matashiyar budurwa tana juya awara a cikin mai, tana sanye cikin gogaggen hijjabi ash, sai dai fuskar nan tata a ɗaure tamau, wani matashi na gefenta a kan babur, da alama tsarata yake yi, amma ko sau ɗaya ba ta ɗaga kai ba, balle ta kalle shi!. Follow my Arewabooks Account Ayshercool7724 Watpad Ayshercool7724 08081012143GABA DA GABANTA AISHA ADAM (AYSHERCOOL) Domin samun update a kan lokaci, ko samun book ɗin daga farko Follow me on Watpad Ayshercool7724 Arewabooks Ayshercool 77724 What's app 08081012143 P11 Zuba mata idanu ya yi, yana kallon yadda take gabatar da sana'ar ta ta cikin nutsuwa, ba hayaniya ko ƙazanta komai nata a nutse, amma mamaki ne ya biyo bayan tunanin da yake yi, me wannan budurwa take haka a titi? Yafi dacewa ace  tana gidan Aure, ko kuma tana makaranta, amma kalleta a titi tana suya. Yaron da ya aika ne ya kawo masa ruwan, ya barwa yaron sauran canjin, ya cigaba da kallon in da Hafsa take, sai dai yadda take gudanar da lamarin nata ne, da gani ka san za ta yi izza, saboda sai shan ƙamshi take, tare da haɗe rai dan kar ma wani ya kawo wargi. A hankali Khalil ya yi you tune, ya koma hannun da Hafsat ke zaune tana gudanar da sana'ar ta. Parking ya yi a gefenta, ya fito daga motar, ya ƙaraso in da take suyar awarar ya kalleta ya ce "Sannu dai" ba tare da ta ɗago ba ta amsa masa ƙasa ƙasa da 'Yawwa". Ya miƙo mata dubu biyu ya ce "Zuba mini abin nan na 2k" wani irin kallo Hafsa ta yiwa Khalil, irin kallon ka raina mini hankali ma, ba ta ce masa uffan ba, ta cigaba da sallamar yaran da ke gabanta. Khalil gani ya yi ba ta da niyyar sake ko ɗaga kai ta kalleshi, ya kuma matsawa ya ce "Magana fa nake yi, ki sa mini na 2k" "Ka bari idan ka san sunan abin da nake sayarwa, sai ka dawo in sayar maka" ta bashi amsa. Khalil ya ce "To, ikon Allah am serious ki karɓa ki bani". "Malam nace ka bari ka san sunan abin da nake sayarwar sai ka siya". Yaron da ke tsaye zai sayi awara ya ce wa Khalil, "Sunan abinda take sayarwa Awara". Khalil ya ce "Ok na gode sosai, ki bani awara ta dubu biyu". Ba tare da kalleshi ba ta ce "Ni awarata ba ta kai ta dubu biyu ba, ta ɗari biyar kawai za ka iya samu". "To bani ta ɗari biyar ɗin, sai ki riƙe canjin" Hafsat ta ɗago idanunta ta harari Khalil ta ce "Malam ba fa bara nake ba, sana'a nake yi". "Ai nima bance bara kike ba, kyauta ce kawai na baki, ta ɗari biyar ɗin ki rabawa yara sadaka, sai ki riƙe canjin". Ba ta kuma tankawa Khalil ba, ta cigaba da iza wutarta, ya tsaya ya zuba mata ido, ta gama soya awarar dake cikin mai, ta zuba masa a leda ta miƙa masa . Khalil ya ce "Ai ba ni zaki bawa ba, sadaka zaki bayar". Hafsa ta ce "Ai kai ma kana da hannu, zai fi kyau ace kai ka raba musu da kanka" Nan Khalil ya shiga jinjina halin yarinyar, ana mata abin Arziƙi amma ba ta gani, sai jin kai da tsabar taƙama. Ya sa hannu ya karɓi ledar awarar, ya miƙa mata dubu biyun, ta kalli hannunsa da yake riƙe da dubu biyun, ta ɗauke kanta ta cigaba da sabgar gabanta. "Ikon Allah, yau Allah ya haɗani da gamona, to ga dubu ɗaya tun da ba zaki karɓi dubu biyu ba". Nan ma ɗauke kai ta yi, ta ƙi kallon in da Khalil ya ke. "Idan ba zaki karɓa ba zan tafi da awarar ba tare da na biya ba". "Ka daɗe baka tafi ba" ta furta a hankali. Khalil ya durƙusa ya sa mata dubu ɗayan, a gefenta sannan ya juya ya fara tafiya. Ko ɗago kanta ba tayi ba, balle ta dubeshi, fifita wutar ta kawai take yi. Yayi gaba ya bawa wasu almajirai awarar, ya kuma waiwayawa yana kallon Hafsa, cike da mamakin wannan tsatstsauran ra'ayi nata. Amina kuwa tana shiga gida, ta tarar da Baba ya dawo daga ƙauye, wurinsa ta nufa cikin fara'a, shima ya tareta da murmushi yana faɗin "Alhamdilillah". "Baba an kai ni Makaranta, na zama 'yar Makaranta". "Alhamdilillah, Allah yayi miki Albarka ya cika miki burinki 'ya ta". Amina ta ce "Ameen, ka san wani abu Baba?". "A'a sai kin faɗa uwata". "Baba sufa wannan makarantar a aji biyar ake gamawa, babu aji shida, zuwa baɗi ta gaba insha Allah zan gama sakandare". Baba ya ce "To Alhamdilillah, Allah ya baki miji na gari a birni kiyi Aure, wanda zai kula da cigaban karatunki" Jikin Amina yayi sanyi ta ɗan yi shiru tana nazari. Baba ya ce "Ya kika yi shiru, ko kin fi son ki koma ƙauye ki auri Jarmai?" Da sauri ta ɗago ta kalli Baba ta ce "A'a Baba, nifa ko sunan Mutumin nan bana ƙaunar ji, ni ban tambayeka ya hanya bama, ya ka baro  Inno?". "Duk suna lafiya sunce a gaishe ki, Jarmai kuma ya sa su Yaya Bala a gaba a kan lallai su biya shi kayan Auren da ya kai, yazo ya sameni wai nima saina biya shi, ni kuwa nace masa sisinsa ban gani ba balle in ci, dan haka yaje can wurinsu ya karɓa, amma da ina da kuɗi da na rage masa wani abun". Amina ta kalli Baba ta ce "Ka jika Baba, Mutanen da ba tare da kai suka ci kuɗin ba, akan ne za ka biya abinda ba kai ka ci ba, banda asarar da suka yi maka ma. Baba kalli litattafaina fa, wai duk wannan litattfan nawa ne" tayi maganar tana nuna masa cikin jakarta. Baba ya buɗe baki, text books kawai sun kai goma sha shida, banda na rubutu, ga math set, da calculator komai akwai, shi kansa Baba ya san wannan kayan sun fi ƙarfin kuɗin aikin da Amina take yi musu. Baba ya ce "Uwata mutanen nan sun mana karamci, duk na san kina da ƙwazo, amma ki ƙara sannan ki ƙara yi musu godiya, idan mai gidan ya dawo, ki kuma yi masa godiya". "Insha Allahu Baba zan masa, idan na yi salla fa har Addu'a nake masa, Allah ya ƙara masa Arziƙi da lafiya, ba zan manta alkhairinsa ba" "Yauwa uwata, har 'ya'yansa ma da matarsa da ahalinsa duk ki dinga saka su a Addu'a". Amina ta ɗan tura baki ta ce "wannan 'ya'yan nasa da basu da kirki". "A'a fa uwata, yanzu ba Makaranta ɗansa ya kai ki ba? Idan mutum ya miki ba daidai ba, ki bishi da alkhairi albarkacin addu'a da kike musu, sai Allah ya miki abin da ba ki zata ba" "To Baba zan dinga yi musu insha Allah, bari in je in wanka nayi salla, ka ci Abinci kuwa?" "Eh naci, Hajara ta kawo mini, maza kije ki yi salla" Ta amsa da to Baba, ta miƙe ta shiga cikin gidan, cike da fara'a da jin daɗi. Kallo ɗaya Mummy ta yi mata tare da kwaɓe baki, ganin yadda ta goyo uwar jakar Makaranta tana washe baki. Amina tayi mata sannu da gida, amma da ƙyar ta iya amsa mata. Hajara ma tsokanar Amina ta dinga yi, tare da tayata murnar samun cigaba da zuwa makaranta. Fadila ba ta dawo gida daga Asibiti ba, sai bayan biyar na yamma, ta dawo a gajiye matuƙa, kuma rai a ɓace saboda abin da Yazeed ya yi mata, kai tsaye sashenta ta wuce, ba tare da ta nemi ko in da Mummy take ba, dan ba abin da take son yi, banda ta yi wanka tai salla ta ci Abinci. Duk da ranta a ɓace yake, amma abin da ta tarar a part ɗinta, yayi mata daɗi sosai. Tayi wanka tayi salla, ta fito ta nufi kitchen da kanta, a kitchen ta tarar da Hajar da Amina na ƙoƙarin ɗora girkin dare, sai bawa Hajara labarin makarantarsu Amina take yi. "Wacece ta gyara mini ɗaki a cikin ku yau?". Amina ta ce "Nice". "Biyoni" ta yi maganar cikin bada umarni. Bayan Fadila Amina ta bi, tana fargabar kar abin Arziƙi ya zama na tsiya. Da suka ƙarasa ɗakin Fadila, Fadila ta ƙare wa ɗakin kallo sannan ta ce "Naga aikin da ki ka yiwa ɗakin nan, kin canzan labulaye kin wanke waɗancan, kin ɗaga gado da wardrobe kin gyara kin canza musu fasali, na ji daɗin hakan, keep it up Ina son sauye sauyen Abubuwa lokaci zuwa lokaci". Amina ta ce "To insha Allah" Fadila ta ce "ɗan tsaya" ta ƙarasa ta ɗakko wata babbar ledar siyayya ta store, ta sakawa Amina turamen atamfa uku, da dogayen riguna, sai hoda da turare ta ce "Gashi nan kije kya saka" Amina ta karɓa cikin fara'a ta ce "Na gode Ubangiji Allah ya ƙara Arziƙi" ta amsa da Ameen. Sai da Amina ta fara zuwa ta nunawa Baba kayan, sannan ta je tana nunawa Hajara, sai dai ran Hajara ya sosu, dan tun da take ba'a taɓa bata makancin wannan kyautar ba a gidan. Amina ta ce "Yaya Hajaru, ki ɗau doguwar riga ɗaya, zan ɗinka atamfa biyu in ajiyewa Inno ɗaya". A fuska Hajara ta ce "An gode madalla" amma a zuciyarta kuwa sam ba ta ji daɗin hakan ba. Tun da Khalil ya baro wurin Hafsa yake tunanin mai ya fito da ita zaman titi da irin wannan sana'ar haka? Gashi ita ba gwanar fara'a ba, balle ya samu ya tambaye ta, to matar da ko fara'a ba ta yiwa kwastomominta, ga taƙamar tsiya ina zata saki jiki har kayi mata wasu tambayoyi? Duk yadda ya so ya manta da batun Hafsa, ya cigaba da sabgarsa, amma ya kasa, duk in da ya motsa tunaninta kawai yake yi, har haskowa yake irin kyan da zata yi, idan har tayi dariya ko murmushi. Bala'in Jarmai ya sanya su Bala a uku, dan duk in da ya tsuguna zaginsu yake a garin nan, kuma duk inda ya gansu ya dinga yi musu tijara kenan a kan kuɗin aurensa. Haka suka ƙuƙuta, suka mayarwa da dillaliya kayan gadon da suka saiwa Amina, amma tayi musu sayen wulaƙanci, suka tattara dubu talatin da ƙyar suka kai masa, a wulaƙance Jarmai ya karɓa sannan ya kalli Kawu Bala ya ce "Amma dai ka san na baku kuɗi sun kai dubu tamanin ko?" Bala ya ce "Haka ne" "To banci nanin ba, nanin ba zata ci ni ba, ba ƙira ba abin da zai ci gawayi, ina ganin mutuncinku ne shi yasa ban kai ku ƙara birni ba, kuma wannan dubu talatin na karɓeta ne dan kar nayi biyu babu, amma daga nan zan fara wucewa wurin mai gari, in fara kai masa ƙarar". Kawu Lawan ya ce "Haba Jarmai, dan Allah kar mu yi haka da kai mana, insha Allah zamu ciko maka sauran kuɗinka, kayi haƙuri". Jarmai ya gyara wata daƙalƙalalliyar babbar rigarsa ya ce "Ai haƙuri shi ne kawai in ga uwar kuɗina a hannuna". Kawu Bala ya ce "Insha Allah, zamu cigaba da lalubawa zamu baka sauran kuɗinka" da ƙyar suka lallaɓa Jarmai, ya haƙura bai kai su ƙara ba. Washegari da Fadila ta koma Makaranta, Captain ya tambayeta ya mai jiki, ta sanar da shi tun a jiyan aka sallame shi ya tafi gida, 'yan aji suna son suyi tsurku su ji yadda abubuwa suka wakana, amma sanin halin Fadila ya sanya ba wanda ya tanka mata. Ta dinga zuba ido, ta ga ta ina Yazeed zai shigo aji, amma babu Yazeed babu alamar sa, har aka yi lectures ɗin ranar aka gama. Nan cikin Fadila ya sake ɗurar ruwa, ta san ba zai wuce ace jikin ne ya hana shi zuwa Makaranta ba, nan zuciyarta ta dinga saƙa mata abubuwa daban daban, ciki har da tunanin ko jikin ne ya tayar masa ya mutu? Nan da nan ta yi saurin kawar da wannan tunanin daga ranta. Da aka tashi daga Makaranta ta samu Captain ta ce "Musa, kun yi waya da gayen nan ne?" Captain ya ce "Wa kenan?". "Wanda muka kai Asibiti jiya" Murmushi ya yi ya ce "Hajiya Fadila ta mu, sunan nasa ne ma ba za a iya faɗa ba. Wallahi tun jiya nake kiran wayarsa, amma ba ta shiga, kuma ina kyautata zaton jikin ne ya hana shi zuwa yau" Fadila ta ce "Ok shikenan" Daga haka ta wuce ta nufi motarta, tana cigaba da tunani. A kwanakin nan kowa da abin da ya dame shi a jama'ar gidan, Khalil ya kasa sukuni saboda tunanin Hafsat, gashi ya kuma komawa amma bata nan bai sameta ba. Fadila kuwa gaba ɗaya tunanin halin da Yazeed yake ciki ne ya dame ta, dan a rayuwarta bata taɓa aikata abin da ya dameta ba kamar abin da ta yiwa Yazeed ba, saboda ta tsorata da irin yanayin ciwonsa.  Bata taɓa ganin mutum a mawuyacin yanayi na ciwo kamar Yazeed ba. Tana zaune a aji, tana ƙoƙarin ɗauko littafi tayi rubutu, ta ga jotter Yazeed, ta ɗauko jotter ta fara bubbuɗewa, rubutunsa a tsare yake kamar musamman yake shirya rubutun, sai dai fahimtar abinda ya rubuta ɗin sai ƙwaro ko kuma shi kansa da ya rubuta abin sa. Rubutu ne na turanci, jotting ɗin lectures ɗin da ake yi ne, sai yayi sentence ɗaya biyu ya gauraya su da rubutun larabci, ga wasu irin manyan Words na turanci, da bata taɓa jinsu ba. To ya akai ya iya turanci a rubuce, amma bai iya a baki ba? 'Maybe yana da matsalar public speaking ne' ta bawa kanta amsa. Bakomai ta iya ganewa a jotting ɗin nasa ba, saboda yadda yake rubutun larabci kamar rubutun yarensa na haihuwa. Ɗan taɓe baki tayi, ta ajiye jotter, tana fatan Allah ya sa dai ba jikinsa ne ya hana shi zuwa Makaranta ba. Khalil musamman sai ya shirya ya tafi unguwar su Abdul, yayi shawagi domin kawai ya ga Hafsat, cikin ikon Allah yau yayi sa'a ya tarar da ita a bakin kaskonta bayan magariba, tana ta harhaɗa kayanta ta tashi. Parking ɗin motarsa ya yi, ya fito da sauri ya ƙarasa in da take. "Sannu dai" Ɗagowa tayi ta kalleshi ta ce "Yawwa". "Ba dai har kin tashi ba?" "Me kaga ina yi?" "Oh sorry haka ne, na gani haɗa kaya ki ke yi, yanzu ba zan samu ba?". "Eh ta ƙare". "Kwana biyu na zo ba na ganinki, meyasa ba kya fitowa?" Hafsa ta ce "Eh da yake ai ba aikin gwamnati nake ba, kuma ba wani ne ya ɗauke ni aiki ba balle a tuhume ni" Murmushi Khalil ya yi, yana jinjina hali irin na Mai awara, ya ɗan sosa kai ya ce "Haka ne, am sorry" "Yawwa dama ina nemanka" tai maganar tana saka hannu a jakarta. Khalil ya ce "Kina nemana kuma? Allah ya sa ba laifi na miki ba" Ɗari biyar ta miƙo masa tana faɗin "Karɓi canjinka da ka tafi ka bar mini ranar" "Ai ba bashi bane, kyauta na baki". "Ai bance maka ina buƙata ba, ka karɓi canjinka". Khalil ya ce "Ai kyauta na baki, kuma ba kyau mayar da kyauta". "Meye tsakanina da kai, da haka kurum zaka bani kyautar kuɗi" "Alkhairi ne tsakanina da ke. Naga kamar gida zaki tafi, ko zamuje in sauke ki?" "Malam ka karɓi kuɗinka, zan tafi dare nayi" "Da ban dawo ba ya zaki?". Ƙoƙarin saƙala masa kuɗinsa take a hannunsa da harɗe a ƙirjinsa. Ja da baya yayi yana kallonta tare da sakin murmushi ya ce "ke dai kin fiye gaddama, dama zuwa na yi in ganki, kuma na sai awara, tun da ban samu awara ba na samu ganinki, shikenan, ki gaida gida" galala ta tsaya tana kallon Ikon Allah, Khalil kuma yayi gaba abin sa yana jin wani nishaɗi da ya rasa na menene. Yana tafe a mota yana tuna yadda tai kicin-kincin da rai tana bashi kuɗinsa, sam bai gaji da ganinta ba, amma ya lura ba ta son takura, magana kuma na bata wahala, shiyasa ya tafi ya ƙyaleta. Shiru yayi yana tunanin menene haka yake ji game da yarinyar nan? Wani irin baƙon al'amari yaji yana ratsa zuciyarsa, duk Hafsa daga gaban kaskon wuta ta tashi, ƙamshin turarenta ya haɗe da ƙaurin mai da na hayaƙi, amma a hancin Khalil ƙamshi ya bashi mai daɗin gaske. Amina kuwa zuwa makaranta ya kankama, dan ta gane hanya, Baba ne yake bata kuɗin mota, ta hau abin hawa ta tafi, idan an tashi ma ta taho gida. Kullum da kiran sallar farko, Amina idan ta tashi bata komawa, duk wani aiki da zata yi, sai ta tabattar ta yi shi, har karin kumallo sai ta dafa, ta gyara ko ina sannan take shiryawa ta tafi makaranta. Sati ya shuɗe kusan kwanaki takwas, Yazeed bai dawo Makaranta ba, gaba ɗaya hankalin Fadila a tashe yake, dan ba wanda ya san gidan su Yazeed balle a samo information akan halin da yake ciki, gashi wayarsa ba ta shiga sam. Fadila Addu'a take, da fatan Allah ya sa ba mutuwa yayi ba, dan da ƙyar in ta tambayi malamai ba a ce tayi azumi sittin ba, saboda abin da ta aikatawa Yazeed, dan da gayya ta balbale shi da hayaƙi da kuma ƙura, duk dan ta muzguna masa. Yau Saturday, kuma suna gaf da fara exams, dan haka akwai lecturer da ya ce, lallai su shiga Saturday, dan bai yi covering course ɗinsa ba. Jiki a sanyaye take tafiya dama gashi ta makara, dan ƙarfe goma ya ce aje, yanzu kuma sha ɗaya saura mintuna goma sha biyar, haka ta tunkari ajinsu tana fatan Allah ya sa malamin ya bari ta zauna, tuni har malamin ya fara lectures, Allah ya taimaketa bai koreta ba. Tun da ta shiga ajin ya ƙura mata ido, ɗaga idon da za tai suka yi ido huɗu da Yazeed. Gabanta ne ya faɗi ganin yadda yayi wata muguwar rama, sauke facemask ɗin sa yayi, tare da yi mata murmushi, gaba ɗaya ya rame sosai, sai dogon hancinsa da ya sake fitowa. Tsuke fuska tayi, ta basar kamar ba ta ganshi ba, ta nemi wani wurin ta zauna, tare da ɗauke kanta da sashen da Yazeed yake. Sai dai lokaci lokaci ta kan kalleshi, tare da sake tabattarwa da kanta yayi rashin lafiya sosai. Haka aka gudanar da lectures ɗin aka gama, aka yi Attendance. Da yawa ɗaliban zasu zauna ne a school, suyi karatu, saboda gabatowar exams, wanda ita ma Fadilan ta yanke shawarar ta zauna ta yi karatu, dan idan taje gida bacci zata yi, sai dai kafin nan akwai buƙatar ta ɗan samo abun motsa baki, da zai ɗebe mata kewa yayin karatu. Bayan tafiyar malamin daga aji, akai ta yiwa Yazeed ya jiki. Fadila tana ta hanzari ta tunkari motarta, ta saka key tana ƙoƙarin buɗewa ta ji an kira sunanta "Fadila" waiwayawa tayi, taga Yazeed a bayanta. Cikin murmushinsa da ya zame masa ɗabi' ya ce "Kina lafiya?" Ta ɗan yamutsa fuska ta ce "Lafiya ƙalau". "Dama na ce bari in zo in sake yin godiya ne, game da taimakon da ki ka yi mini, na gode sosai Allah ya bar zumunci" Wata uwar harara ta watsa masa, ta buɗe ƙofar motar. "Au ashe fa ni mai laifi ne, na manta a ranar na ɓata miki rai, kiyi haƙuri dan Allah, naga baki ji daɗin abin da nayi ba". "Ashe kana sane kai min abin da kayi mini ko?" Tayi maganar tana hararasa. "Ai nace kiyi haƙuri ban kyauta ba" "Kaji da shi" tayi maganar tana ƙoƙarin shiga mota. Cikin harshen larabci Yazeed ya ce "هل يمكنني الحصول على jotter الخاص بي" (*Can i have my jotter*) Kallonsa ta yi saroro, ba tare da ta gane me yake faɗa ba. Ya kuma maimaita mata abin da ya faɗa. Tsaki tayi ta ce "Malam speak what I can understand". Wani irin ƙasaitaccen murmushi Yazeed ya yi ya ce "Ni kuma gashi ban iya turanci ba, amma dai ina roƙon ki bani jotter ta ne, zan ɗan kwafi lectures da na yi missing, ance mini suna wurinki" Tura baki tayi, tana wani basarwa, ta fara duba jakarta, ta zaro jottersa da bironsa ta miƙa masa. Sansana jotter ya yi ya ce رائحته جميلة ( *It smells nicely*) Ƙaramin tsaki ta ja tana kuma ƙoƙarin shiga mota. Riƙe ƙofar motar yayi ya ce "Malama kayana da saura" kamar ba shi yayi Maganar ba, ya wani basar, dan ba zaka taɓa cewa yana magana haka ba. "Ban gane ba" ta faɗa tana kallonsa. "Ina kuɗina?" Ya faɗa ransa a haɗe. "Hamsin ɗin?" Ta faɗa a wulaƙance. Yazeed ya ce "Eh ai tawa ce ko?" Tsaki tayi ta saka hannu a jakarta ta ɗauko ɗari biyar ta ce "Ungo". "Ni tawa nake so, amma dai shikenan na bar miki, ki zo muje muyi karatu tare, ki koya mini abin da aka yi bana nan, sannan baki mini ya jiki bama, kin kusa halaka ɗan marayan Allah, ni yakamata ma ki gaya mini laifin da na yi miki kika tsane ni haka". "Dan Allah ka bani wuri in tafi, ka tsayar da ni kana ta mini surutan banza". "Subhanallah, yi haƙuri na takura miki, shikenan ki gaida gida" ya matsa ya bata wuri, ta shige motar ta, ta sauke glashin ta ce "Ka matsa kar in tada ƙura ka kama sumewa mutane". "Idan na suma ma in dai kina nan ai ba damuwa" hararsa tayi, ta bawa motarta wuta ta wuce ta bar wurin. Shi kansa Yazeed bai san yadda aka yi ya tsinci kansa, da ƙoƙarin tsawaita hira da Fadila ba, dan a rayuwarsa kusan shi mutum ne mai tsoron duk wani abu da zai haɗa shi da mata. Sake shanshana jotter yayi, sai ƙamashin turaren Fadila take, ya fara bubbuɗewa, kawai ya ci karo da rubutun da ba nasa ba, kusan duk lectures ɗin da aka yi baya nan, ta rubuta masa a ciki. Zubawa Jotter ido yayi, a hankali ya ce "Allah ya sa ki fara jin abin da nake ji a kanki" can kuma ya ce "Subhanallah, ba ajina bace" shikaɗai yake wannan surutan, daga baya kuma ya ja jiki ya nufi masallaci. Amina ta gama aikinta tsaf, ta zauna a falo tana karatu, Hajiya Zainab bata nan, Hajara kuma ta tafi yin sayayya. Turo ƙofar falon aka yi, Amina ta waiwaya, taga baƙuwar fuskar da bata saba ganinta ba. Yusra ta ce "Ina mutan gidan kuwa, naji kamar ba kowa?" "Sun je Islamiyya a koya musu sallama, da yiwa wanda suka tarar sannu" Amina ta bata amsa. "Ke, wacece ke kika gaya mini wannan maganar?" "Ahh musulma mana Hajiya, ai a koyarwar addinin musulunci idan ka zo wuri da sallama kake farawa, kuma ka yiwa na zaune sallama, amma kawai kya shigo kanki tsaye ki hau Magana. Bisimillah shigo amma dai nan gaba ba a haka" saroro Yusra ta bi Amina da kallo, dan ba su taɓa haɗuwa ba sai yau. Ƙoƙarin ƙarasowa cikin falon Yusra take, amma Amina ta miƙe ta ce "Hajiya ba fa banɗaki zaki shiga ba, ya zaki shigo mana da takalmi falo, ciresu a nan wurin ki ƙaraso" Yusra cire takalman tayi tana kallon Ikon Allah wurin Amina, dan ba ta san matsayinta a gidan ba. Yusra ta zauna, Amina kuma ta wuce kitchen, ta haɗowa Yusra ruwa da lemo, ta kawo gabanta ta ajiye mata ta ce "Ga ruwa ki sha, 'yan gidan basa nan, idan kuma zaki ci Abinci ne ki faɗi wanne zan dafa miki? Dan an cinye na rana, na ɗan gidan nan ne kawai ya yi ragowa" Sai yanzu Yusra ta gane matsayin Amina, a ranta ta ce 'Ina Mummy ta samo wannan tantiryar mara mutuncin 'yar aiki? Ka rashin kunya ga karrama mutane'. "Ba Abinci na zo ci ba, ai ban miki kama da mai jin yunwa ba" Dariya Amina ta yi ta ce "Haba Yayata,. Idan a jiki ake gane yunwa ko rashinta, ai cewa za ai baki taɓa cin abinci ba ma" ai gaba ɗaya Amina ta kashewa Yusra bakin Magana. Ƙamshin turaren da ya karaɗe falon ne, ya sanar musu da zuwan Khalil, sai dai tun kan ya shigo, Yusra ta rasa nutsuwarta. Kansa tsaye ya shigo, da sallama iya wuyansa wadda shika ɗai yaji kayarsa, jiki na rawa Yusra ta risuna tana gaishe shi. Amma ya amsa ba yabo ba fallasa, haka ya shigo falon da takalmansa, sai da yaje dining ya ajiye takalman a kan step ɗin dining ɗin. Amina kuwa ta ƙulu, saboda yadda ya biyo har ta kan carfet da takalmansa, a fusace ta miƙe taje ta kwaso takalman Khalil ta je ta watsa su waje tana mita cike da tsiwa "Ai ni ba baiwarku ba ce da zan dinga aiki kuna takawa, sai na sake!" SHARE PLEASEGABA DA GABANTA AISHA ADAM (AYSHERCOOL) To get the latest update of the story Follow me on Watpad Ayshercool 7724 Arewabooks Ayshercool 7724 What's app 08081012143 P12 Sai da ta watsa takalman waje ta dawo falo, ta lura da yadda duk suka bita da kallo, mussaman Khalil da ya ke mata Wani irin mugun kallo, sai a lokacin ta sha jinin jikinta ta gano ta yi wauta. Ɗan marairaicewa ta yi ta ce "Dan Allah kayi haƙuri ba dan halina ba, na gaji ne sosai yau na sha aiki, bayana har ciwo yake, na canza wancan carfet ɗin na bayar wanki, na saka sabo wankakke kuma ka taka mini da takalimi ai kaga ba zan ji daɗi ba, aikin da wahala, dan Allah kayi haƙuri ba zan sake ba". Rai a haɗe ya ce "Ke na fuskanci ba ki da kunya ko? Tun ranar farko da na fara ganinki a gidan nan na fuskanci haka". Amina kamar zata fashe da kuka ta ce "To ai na ce kayi haƙuri, ba zan sake ba insha Allah, kuma rashin kunya ba halina ba ne, ba zan sake ba kayi haƙuri" "Rufe mini baki malama, ki ɓace mini daga nan wurin 'yar ƙauye mara kunya kawai" Amina ta juya baya ta murguɗa masa baki, tana yatsina baki a ranta ta ce "Ko ba komai, na faɗi abin da ke raina, ba zaku mayar da ni baiwarku ba" Yusra ta jinjina hali irin na Amina, yarinyar akwai iya nuƙufurci, yanzu za ta maka laifi, kuma ta nemo abin da zata goge laifin nata. Ta ɗan ƙurawa Khalil ido da yake zaune yana cin Abinci, cikin son lallai sai ya kulata ta ce "Yaya Khalil ita ma wannan maid ɗin Mummy ce?" Ba tare da ya kalli in da Yusra take ba ya ce "Me ya hana ki tambayeta tun tana nan?" Yusra ta ji haushin amsar da ya bata, amma ta haɗiye ta tsuke bakinta, tana cigaba da satar kallonsa. Yusra gajiya tayi da zaman Jiran Fadila, ta kirata a waya amma taƙi shiga, gashi Khalil ko kallon in da take ya ƙiyi, gasjiya tayi ta tashi ta kalli in da Khalil yake ta ce "Na tafi sai anjima, na kira lambar Fadila ba ta shiga". "Ok ki gaida gida" Yusra ta fito gwiwa a saɓule, a harabar gidan ta ci karo da Abdul, a jikin motarsa, yana ƙoƙarin kiran waya. Murmushi Abdul ya yi ya ce "Wata sabon gani, Yusra dama kina nan?". "Ina nan Yaya Abdul, ya kake ya gida?". "Lafiya ƙalau Yusra, yaushe rabon da na ganki, ya school?". Yusra ta ce "School Alhamdilillah". Abdul ya ce "Masha Allah, kin zo wurin ƙawar taki ne?" "Eh, na tarar ma ba ta nan, ta je school wai za suyi lectures yau". "Allah sarki, to shikenan, ki gaida gida" "Yauwa gida ya ji, na gode". Abdul ya kira wayar Khalil, "Gani a cikin gida, naga baka part ɗinka" "Shigo falo, ina cikin gida" Abdul ya ɗan yi jimm, ya ce "To bari in shigo". Ya nufi cikin gidan, yana fargabar karɓar da zai samu a wurin matar gidan. Da sallama ya shiga falon, ya hangi Khalil a kan dining, yana cin Abinci. "Ashe kana nan kana kintsa cikinka". Khalil ya ce "Ai sai da kintsa cikin, ƙaraso mu ci". "Ni bana jin yunwa, na ji gidan shiru ko ba kowa ne?" Abdul ya yi maganar yana zama a kan ɗaya daga cikin kujerun da ke ɗakin. "Eh basa nan, Fadila tana Makaranta, Mummy kuma ba ta nan". "Allah sarki, na so inga Fadila ko ba zata kulani ba, ai yau na ga ƙawar nan ta ta Yusra, rabona da ita ina ga tun kan mu tafi karatu". Khalil ya ce "Hmm ka san wani abin takaici kuwa?" "A'a sai ka faɗa" "Wai wannan yarinyar Yusra ce, suka haɗa kai da Fadila wai sona take". Dariya Abdul ya yi ya ce "Amma ta taimaki ƙaton tuzuru, to kai ya ake ciki? Yarinyar ai ba laifi". Khalil ya yi tsaki ya ce "Ƙawar ƙanwar tawa, dan rainin hankali ni sa'anta ne?" Abdul ya ce "Ji wani zancen banza, dan sa'ar ƙanwarka ce shi ne ba zaka aureta ba, ai masoyi abin a kula da shi ne, meye dan ta ce tana sonka?". "Dalla, bana son raini, kuma ni bana son ramammiyar mace, na fi son in ga mace a cike" Abdul ya ce "Banda cin fuska dai malam" "Kaji da shi, ni idan an yi sallar magariba, zamu je ka rakani wani wuri, in nuna maka wani abu" Khalil ya ce "Me zan gani?" "Kai dai ka bari, idan muka je ka gani" "Ni ina Amina 'yar Makaranta ne?". Wani dogon tsaki Khalil yayi ya ce "Sai ka tashi ka tafi nemanta ai". "Wai kai kowacce magana akai maka sai ka kushe" banza Khalil ya yiwa Abdul, ya kammala cin abincin sa, ya dawo ya zauna a falo, suka kunna tv suka cigaba da hira da Abdul. Fadila kuwa keɓe kanta tayi a makaranta, ta sha karatu sosai da sosai, duk wasu abubuwan sun mata tsaurin da ba ta gama gane su ba, tana buƙatar wanda zai ƙara yi mata bayani. Tana kallon yadda aka haɗa group group, Yazeed yana sake yiwa ɗaliban bayanin abin da ba su gane ba, amma taƙi zuwa gani take idan ta je ta faɗo. Sai bayan la'asar Sannan ta bari school ta tafi gida, a Falo ta tarar da Khalil da Abdul suna kallon ball suna hira. Tana ganin Abdul ta wani haɗe rai, Abdul kuwa faɗaɗa murmushinsa ya yi ya ce "Sannu da Zuwa". Cikin ko in kula ta amsa, dan ya fidda ran zata amsa ma. Khalil bai kulata ba ta wuce ɗakinta, sai da ta bar falon sannan ya ce "Dan Allah Abdul ka daina shiga sabgar yarinyar nan tana yarfaka". "Kawai dai kace in haƙura ba zaka bani ita ba?". "A'a ni bance ba, amma yarfin da take maka yayi yawa" "Ba komai a hankali zamu daidaita". "Ai sai kai tayi" Sai da aka yi sallar magariba sannan suka bar falon, suka tafi masallaci domin yin salla. Bayan sun fito daga sallar ne Khalil ya cewa Abdul "Muje ka rakani in nuna maka abin da nake gaya maka, amma mu fara biyawa in gaida Mama" Abdul ya ce "To muje, Allah ya sa abin kirki zaka nuna mini, ba shiririta ba". "Ni ne ma nake maka shirirtar?" "To ai kai ɗin ne wasu lokutan sai a hankali, muje dai in gani" Haka suka tafi, suna tafe suna faɗa suka isa unguwar su Abdul, suka shiga Khalil ya gaisar da Maman Abdul, kamar yadda yake ɗabi'arta ta karɓi Khalil hannu bibbiyu, tana ta kwarara musu Addu'a da sa musu albarka, saɓanin mahaifiyar Khalil idan ta ga Abdul, ta dinga masa kallon banza kenan tana hura hanci. Bayan fitowarsu daga gidan su Abdul, Khalil ya ja mota zuwa unguwar su Hafsa, wanda take a gaban ta su Abdul, bai yi parking a ko ina ba sai a wurin suyar awarar Hafsat. "Wai mai za muyi a nan ne?" Abdul ya tambayi Kahlil yana kallonsa. "Zo muje zaka gani" Suka fito daga motar suka tunkari wurin mai awara. Abdul ya kasa haƙuri ya sake cewa "Wai wurin wa zaka ne?". Khalil bai bashi amsa ba, sai janyo hannunsa da yayi suka ƙarasa. Hafsa na ganin Khalil ta tsuke fuska, tana ɗauke kai. Sallama Khalil ya yi, Hafsa ta amsa tamkar an mata dole, suka zauna a bencin da ke wurin, Abdul kuwa sai bin Khalil yake da kallo ransa cike da tambayoyi. "Barka da warhaka 'yan mata" Khalil ya faɗa yana murmushi. Wani irin kallo Hafsa ta yi masa, wanda bai gane ko na meye ba, sai dai kawai yaji tsigar jikinsa ta tashi da kallon da tayi masa. "Ke baki gaishe ni ba, kuma na gaishe ki kin ƙi amsawa". Hafsa ta ce "Ni gaskiya malam takura mini kake yi, wai me kake nema a wurina ne?". Khalil ya ce 'Ban taɓa ganin wanda ba ya maraba da coustomer ba sai ke Hafsa" ɗagowa tayi da sauri ba tare da ta yi niyyar magana ba ta ce "Waye ya gaya maka sunana?" "Ban sani ba" ya bata amsa. Ɗan ɗage kafaɗa tayi ta cigaba da fifitar wutarta, Abdul dai sai bin su yake da kallo. "Zuba mana ta dubu ɗaya" yayi Maganar yana kallon zobunan hannunta. "Ba zan sayar ba, sai dai in baka ta iya canjinka ɗari biyar da ka bar mini" Khalil ya ce "Ƙadiran ala man yasha'u, wai ke wace irin Yarinya ce haka, Wallahi ba zan karɓi ɗari biyar ɗin nan ba, ki zuba mana ta yadda na ce mu tafi". Murguɗa baki tayi ta ƙi magana, ta cigaba da sallamar mutane. "Sauri fa muke, ki sallame mu mu tafi" ya faɗa yana nazartar ta. "Amma kamar ba ɗaure muku ƙafafuwa na yi ba ko?" Khalil ya kwantar da murya ya ce "Zuciyata ki ka ɗaure, ba ƙafafuwana ba" Abdul yayi gyaran murya ya ce "A taimaka a sallame mu ƙanwata, ya damu yana son cin awarar ne, shiyasa na rako shi". Hafsa ta ce "Ba fa ci yake ba, yana zuwa wurin nan ne kawai dan takurawa rayuwata, bana son yi masa wulƙanci, amma gaskiya yana takura mini, sana'a nake bana son yadda maza suke taruwa a wurin nan, ba yadda zan yi ne, shi kuma sai ya zo ya sani a gaba da surutai". Abdul ya ce "Kina da gaskiya, amma kiyi haƙuri dan Allah, Yanzu zuba mana sai mu tafi". Hafsa ta ce "Ba zata kai ta yadda ya ce ba". "To zuba mana wadda ta samu, sai mu tashi" Hafsa ta zuba ta ɗari shida, ta kalli Abdul ta ce "Ta ɗari shida ce, akwai ɗari biyar ɗin sa a wurina, ɗarin kuma na bar maka" Abdul ya ce "A'a ba za ayi haka ba, ai mun cinye ribar, bari dai in biya" Hafsa ta ce "A'a ka bar shi Wallahi, ka bashi ta ɗari biyar ɗin sa, wadda na baka kuma, ka ci ko ka bayar, ka  yiwa mamana Addu'a Allah ya bata lafiya". Abdul cikin tausayawa ya ce "Allah sarki, ubangiji Allah ya bawa Mama lafiya, ya sa kaffara ne" "Ameen na gode" Sai Khalil ya zama hoto, yana mamakin yadda Hafsa, ta ɗan saki jiki ta yiwa Abdul magana, amma shi take nuna yana takura mata. Suka miƙe zasu tafi, Khalil ya sa hannu a aljijunsa, ya ciro dubu uku, ya ajiye wa Hafsa. Miƙewa tayi da sauri ta ce "Malam karɓi kuɗinka, ya zan yi da su?" Khalil ya ce "Yi makama shi da su" Yayi gaba abinsa, ta kalli Abdul ta ce masa "Dan Allah ungo ka bashi kuɗinsa, ni bana son irin wannan abun, meye haɗina da shi zai dinga yi mini haka?". Abdul ya ce "Nima fa yanzu kika mini kyauta na karɓa, dan haka ba a mayar da kyauta, ki saiwa Mama lemo da shi ba yawa, sai mun sake dawowa" yayi gaba ya barta baki a sake da kuɗi a hannu. Har suka fara tafiya, Khalil bai ce komai ba, can Abdul ya numfasa ya ce "Khalil, me kake nufi ne? Khalil ya yi ajiyar zuciya ya ce "Shi ne abin da haryanzu ban tabattar ba, a kallon Farko da na yi mata, na shiga wata duniya da na kasa tantance, tausayi ne ko menene" "Khalil soyayya kenan fa" "Ba zan musa maka ba Abdallah, abin da nake ji game da ita, yayi yawa ina jin zan iya komai dan in dinga ganinta a kusa da ni, haka kurum nake jin kishin sana'ar nan ta ta, tana zaune kiwa na kallonta". Abdul ya ce "Tirƙashi, kai Izza ita miskilanci da rashin son raini". "Ai Abdul baka ga komai ba, yarinyar nan tana da jin kanta, ga ta da ba kowa ba, sai jan aji, kamar zata wahalar da ni, amma na yi mamakin yadda tai maka Magana, ni sai dai ta harareni ta gaya mini baƙar magana" Abdul ya ɗan murmusa ya ce "To ai kaine mutumina, kai ma izzar ce da kai da faɗan tsiya, mata kuma ba a musu haka, mussaman idan ana son farautar zuciyarsu. Idan har kana son Yarinyar nan ka ajiye taka Izzar, ka bita a yadda ta ke" "Abdallah wai wace irin izza, bani da wata izza Wallahi". "Haka dai kake gani, yanzun nan kana mini describing ɗin ta, amma kana cewa gata dai ba kowa ba, meye wannan idan ba izza ba, koma dai menene ai sonta ka ke" "Au dan na faɗi haka izza ne?" Abdul ya ce "Khalil kenan, Amma tsakaninka da Allah, son Aure kake mata, ko dai wani abu daban?". "Haba Abdullahi, ka taɓa ganina da harkar banza ne?" "Ba haka nake nufi ba, akwai so wanda kake wa mace dan ka aureta, wata kuma burgeka take kana son ka mu'amalance ta kamar ƙanwarka, wata kuma tausayinta ka ke ji kawai" "Nifa da gaske nake, Aurenta zan yi tayi mini". Abdul ya ce "Ina muku fatan Alkhairi, Allah ya tabbatar da alkhairi" a ransa kuwa yana jinjina yadda iyayen Khalil zasu amince ya auri mai 'yar talakawa mai suyar awara a bakin hanya. Fadila shirye shiryen fara exams ya yi nisa, tana ta fama da karatunta, sai dai girman kai ya hana ta koyi abin da ba ta iya ba, a ganinta hakan tamkar ƙasƙanci ne a gareta. Tana zaune ita kaɗai a seat ɗin baya, ta ƙurawa littafi ido, Yazeed gabansa na faɗuwa ya tunkari in da take a zaune, sallama ya yi mata, ta amsa a ciki ba tare da ta kalleshi ba. "هل يمكنني الجلوس" (Can i seat) Kallonsa ta yi, ta ɗauke kanta, Yazeed ya zauna a kusa da ita, ya kalli littafin hannunta ya ce "Sannu da ƙoƙari". "Dan Allah malam kar ka zo ka isheni karatu zan yi". Yazeed ya ce "Nima karatun zan yi ai" ya ciro jottersa ya ce "Ban miki godiya ba, naga kin rubuta mini duk abubuwan da aka yi bana nan, Na gode sosai ubangiji Allah ya ƙara basira. Amma dan Allah ina son ki ɗan yi mini bayani, akwai abin da ban gane ba". "Baka iya karatu bane da sai na maka bayani ko yaya?". "Karanta rubutu a rubuce ba shi ne ba, ka gane me ake nufi ko da ba ka iya karantawa ba shi ne mafi mahimmanci". "Dan Allah ka tashi ka bani wuri". "Ok, zan tashi amma bari in nuna miki wani abu" Ya ɗauki littafin gabanta ya kalla sannan ya ce "Ba wannan topic ɗin yakamata ki duba ba, idan har ki ka gane bayanin wannan topic ɗin shikenan, malamin ba zai tsawwala tambayoyi a nan ba". Ya buɗo wani topic ɗin ya ce a "A wannan yakamata ki fi mayar da hankali" Yamutsa fuska tayi, tare da tura baki kamar zata yi kuka. Yazeed ya ce "Ya dai?". "Ni fa na gaji da karatun nan, kaina kamar zai fashe bana gane komai ma" "Kece kika wahalar da kan ki, ki ke karanta abin da ba shikenan ba, idan Malami yana bayani, ki dinga rubuta abin da kike fahimta a game da darasin, idan kika koma gida sai ki faɗaɗa bincike, sai ki haɗa ki tsinci abin da zaki tsinta ki haɗa, amma idan ki ka ce handout zaki haddace baki fuskanci darasin ba, zaki iya samun idea escape ma a wurin exams. Dan haka idan ana lectures a daina yiwa malamai tsiwa ana korar mutum daga aji, wani abin idan har aka yi baka nan ya riga ya wuceka kenan" Murguɗa masa baki tayi, jin statement ɗin sa na ƙarshe, tare da cewa "Ina ruwanka da an koreni, bana son sa ido, ban littafina". "Zan baki littafinki, amma kan in baki duba wannan, sai in ƙara yi miki bayani, zaki ga yafi sauƙi a kan wanda kike yi" kallon rubutun nasa tayi, har da wani larabci a ciki. "Kaga nifa bana gane larabci" tai maganar tana wani basarwa. Aikuwa Yazeed kamar an kunna fanfo, ya dinga zuba yana mata bayani tana saurarensa, babban abinda ya sanya shi farinciki, bai wuce saurarensa da take yi ba. Sai da ya gama, tayi ajiyar zuciya, dan idan ta ce ba ta gane me yayi mata bayani ba tayi ƙarya, dan duk abin nan da ake, haddacewa kawai take ba ganewa ta yi ba. "Na fahimta, Na gode sosai". "Never mind ranki ya daɗe, bari inje masallaci" Ta jinjina masa kai, bayan tafiyarsa, ta ɗau jakarta ita ma tayi waje ta nufi gida. Khalil an fara yi masa way da ga wurin aiki, a kan lallai ana buƙatar sa, ji yake kamar ya ce Ya fasa komawa, saboda yadda yake jin Hafsa a zuciyarsa, ji yake kamar ba zai iya tafiya ya daɗe bai ganta ba. Ana gobe zai koma, ya je gidansu Abdul ya yi masa sallama, suka sake tattaunawa a kan yadda Khalil zai ɓullowa Hafsa, suka yi sallama Khalil ya tafi wurinta. Wannan karon ba Mutane sosai a wurin nata, dan da alama ta kusa tashi ne ma. Yana yin sallama a wurin, ta haɗe rai tare da amsawa ta ɗauke kai. "Ina wuni tun da ke baki iya gaisuwa ba". "To ai nima bance ka gaishe ni ba". Khalil ya numfasa ya ce "shikenan, ba faɗa na zo muyi ba, sallama na zo muyi zan koma wurin aiki insha Allah". Hafsa ta ce "To ni ina ruwana da zaka tafi?". "Amma dai at least ai kya yi mini A dawo lafiya ko?". Hafsa ta ce "To Allah ya kiyaye hanya" "Ameen Hafsat, ya jikin Mamana?" "Wace maman taka?". "Mamanmu mana, mamanki ai mamana ce ko abin ba kara ne?". "Jikin Mama da sauƙi". Khalil ya ce "Masha Allah, Alhamdilillah, amma sauƙi na bahaushe ko kuma ta warke?" "Da sauƙi sosai" Hafsa ta bashi amsa a lokacin da hankalinta ya koma kan wata coustomer. Khalil ya sa hannu ya ɗau wayarta mai madannai, wadda ta sha jiki da yawa, lambarsa ya sa a wayar, ya kira lambarta ta fito a tasa, ya ajiye mata wayar. Ya yi gyaran murya, wanda ya sanya ta waiwayo. Ya ce "Ko zamu je in duba Maman ne?" Ta ɗan waro idanunta ta ce "Saboda me? Ince ga wa ya zo dubata?". "Coustomer ɗinki, mai takura miki, kuma wanda yake fatan ya Aureki. Duk da ban gaya miki dalilin da ya sanya na nace ina ta bibiyarki ba, Hafsa ina sonki ne, kuma Wallahi da gaske nake, ni Aurenki zan yi, ina kishin ganinki a wurin nan kina wannan aikin" Ai tuni ɗan annurin yau da ya gani a fuskarta, saboda zancen Mama da ya yi, ya gushe daga fuskarta, ta haɗe rai sosai da sosai tayi shiru taƙi magana. "Hafsa maganata ce ta ɓata miki rai?" "Dan Allah ka rabu dani, kar ka sake zuwa in da nake, ni ban fito sana'ata dan wani ya tausaya mini ba, ba ruwanka da sana'ata, kuma kar ka sake zuwa wurin nan, idan ba haka ba zan iya dena zuwa ni, in bar maka wurin". A ɗan rikice Khalil ya ce "Amma Hafsa... "Malam bana son jin wata magana, ka ƙyaleni" tayi maganar a hasale. Haka Khalil ya tashi ya baro wurinta, jiki a sanyaye, yana mamakin halayen Hafsa, wace irin Yarinya ce haka, dan ance ana sonki ki birkice ki kama masifa?. A sanyaye haka ya koma gida, yana tunanin mafita, amma dole ya san abin yi, da zuciyarsa ba zata iya haƙuri da Yarinyar nan ba. Da ya koma gida, a Falo ya tarar da Mummy, da Fadila suna kallo, suna hira, Amina nata gyara dining, in da suka ci Abinci suka bar wurin. Fadila na ta bawa Mummy labarin Yazeed, yadda ya iya larabci amma bai iya turanci ba hadda cewa "Mummy kin gan shi kuwa, kayan da yake sakawa? Amma sai ƙwaƙwalwa kuma baya iya turanci a baki". Mummy ta taɓe baki ta ce "Wasu lokutan dama haka ne, yaran nan marasa galihu da suke tashi a wahala, suna da ƙoƙari, sai dai na banza ne, dan ko sun gama karatun ba aiki suke samu ba, sai da su zama masinja a manyan ofisoshi". Amina da ke aiki a ranta ta ce "Ji mata da mugun baki, wato ɗan talaka ba zai huta ba, iyayenmu su yi muku bauta, muma muyi muku da 'ya'yanku, insha Allah ta Allah ba taku ba' "Khalil lafiyarka kuwa, ka zo ka zaun kayi shiru haka?". "Mummy bakomai". "Ya fa bakomai? Ga yanayinka duk ya canza". "Mummy wata Yarinya ce" sai kuma yayi shiru. "Mai Yarinyar ta yi?" Mummy ta tambaya cike da zaƙuwar son jin ƙarshen zancen. "Mummy Bakomai" ya faɗa cikin damuwa. "A'a ka fara magana kace bakomai, ko dai ka fara Soyayya ne?". "Eh to, Yarinyar ce dai haryanzu ban samu shawo kanta ba". Mummy tayi murmushi ta ce "Ikon Allah, dama akwai lokacin da zaka samu macen da tayi maka, sarkin kushe kushe? A ina take kuma 'yar waye? Ina fatan ba gidan tsiya zaka je ka ɗauko mana sirika ba?" Gaban Khalil ne ya faɗi, be bawa Mummy amsa ba ya miƙe, ya ce "Idan komai ya daidaita za muyi maganar". Fadila kuwa wani takaici ne ya mamayeta, da tausayin Yusra da take ji, gaba ɗaya haushin Khalil ya kamata, ta tashi ta bar falon ita ma. Haka Khalil ya kwana yana tunanin dalilin da ya sanya, Hafsa ta canza fuska dan kawai ya ce yana sonta, shi dai ya san ba muni ne da shi ba, dan ƙarewa ma mata ne suke rushing a kansa, bai taɓa tunanin Soyayya zata iya kai shi wurin mai awara ba, dan da shi a yadda yake tsara rayuwarsa, macen da ta kammala degree ma yake so, very matured lady, haka yayi bacci rabi da rabi. Washegari tun sassafe, Fadila da Mummy zasu je unguwa, dan haka suka raka Khalil airport, su kuma suka wuce in da zasu. Hajara ma shiri tayi, ta tafi kasuwa saboda akwai kayan da babu, mai zuwa kasuwar sayowar kuma Hajiya Zainab ta koreshi. Amina taje wurin Baba suka sha hira, daga nan ta koma cikin gidan, tana ɗan ƙara dudduba abin da za tayi. Ta dawo babu daɗewa aka fara bubbuga ƙofar falo. Amina ta je ta buɗe ƙofar falon, wasu mata ta gani su huɗu, sai yara su ku san biyar. Amina ta ce "Sannunku da zuwa" Suka amsa mata da yauwa, ta basu wuri suka shiga falo, suka zazzauna. Ɗaya daga cikin matan ta ce "Ahmad ɗin yana nan ne?" Amina ta ɗan yi jimm, tana tunanin wanene Ahmad. Matar ta ce "Me gidan" Amina ta ce "Au, ai ba ya gari bai dawo ba, sai da ki kai magana naga kuna kama, 'yan uwansa ne ku?". Matar ta yi murmushi ta ce "Eh ƙannensa ne da iyayensa". Amina ta faɗaɗa murmushinta ta ce "Allah sarki, sannunku da zuwa gashi duk ba sa nan, sannunku" nan da nan Amina ta tafi kitchen, ta dinga jido ruwa da lemuka a fridge, tana kawo musu, ta koma ta haɗo musu fruit a ƙaton faranti, ta zo ta zube musu, cikin hanzari ta koma kitchen, ta ɗora girki, ta sake dawowa falo tana musu sannu da zuwa. Ɗayar ta kalli Amina ta ce "Amma dai ke baƙuwa ce a gidan nan ko?". Amina ta ce "Eh baƙuwa ce, aiki nake yi ban cika wata biyu bama". "Allah sarki yarinyar kirki, Allah ya yi miki Albarka. Mun zo duba wani ɗan uwa ne da aka kwantar a Asibiti, muka ce bari dai mu biyo mu duba Ahmadu, tun da shi ya watsar da mu mu bari muzo". Amina ta ce "Allah sarki, ai kuwa kun kyauta zumunci ai Akwai daɗi". Nan da nan kamar sun san juna tun tuni, Suka saba da Amina, abinka da wanda ya ce maka ungo. Ta shirya musu lafiyayyen girki, yaji uban nama, ta kawo ta ajiye musu, aikuwa suka zage, suka ci Abincin nan, suka yi sallar azahar, Amina ta ware musu A.C ta kunna musu kallo. Hajara ce tayi sallama, daga kasuwa ta dawo wujiga wujiga. Sai dai tana ganin matan da ke Falon tai turus, ta gaishe su, suka amsa mata, Amina ta tashi ta tayata ɗaukar kayan da tazo da su zuwa kitchen. Suna zuwa kitchen Hajara ta kalli Amina ta ce "Amina, waye ya saki bawa baƙin nan hidima haka, har da girki?" Amina ta ce "Ban gane ba" "To ki shirya hukuncinki a wurin matar gidan nan, Allah ya sa ƙarshen zamanki a gidan nan bai zo ba, dan wannan mutanen arziƙin ruwan pure water suke samu idan sun zo, shi yasa suka daina zuwa". Amina ta ce "Amma Hajara 'yan uwan mai gidan ne fa". Amina ta faɗa cikin damuwa. "Ke ki ka san 'yan uwan mai gidan ne, amma ki shirya karɓar mummunan hukuncin da zaki fuskanta a wurin!!!. IDAN BA A COMMENT ZAN DAI NA TYPING TABBAS, KO YA KOMA PAID, IN ƁATA LOKACI INA TYPING, KU BINI DA THANKS😏😏😏GABA DA GABANTA AISHA ADAM (AYSHERCOOL) To get the latest update of the story Follow me on Watpad Ayshercool 7724 Arewabooks Ayshercool 7724 What's app 08081012143 P13 Gaba ɗaya jikin Amina ya yi sanyi, jin abin da Hajara ta gaya mata, mussaman batun korar nan da ta ambata, jiki a sanyaye ta ce "Amma Hajara ai baƙon ka annabinka, ka yi baƙi 'yan uwan mai gida ka wulaƙanta su?". "Na gaya miki kefa ki ka san wannan, ita ba ruwanta, kawai ki saurari kwandon bala'in da zata zo ta sauke miki a ka, kiyi fatan ya tsaya a iya tijarar da zata miki" Jikin Amina yayi sanyi, amma babu yadda zata yi, tun da har ta riga ta musu kyakywar tarba, kuma ita ba taga aibun abin da ta aikata ba. Jiki ba ƙwari ta fito falon, ta tarar sun fara haramar tafiya. Amina ta ɓoye damuwarta ta ce "Ya naga kun fara shirin tafiya? Ba zaku jira su dawo bane?". "A'a kar yamma ta yi mana, gara muje mu tari motar garinmu". "Au dama ba a garin nan ku ke ba?" Ƙaramar cikinsu ta ce "A'a, mu daga jigawa muka zo" suna tsaka da maganar, Hajiya Zainab ta turo ƙofar falon,  Fadila na bayanta. Tana shigowa ta yi turus ganin mutane a falon, ta bi su ɗaya bayan ɗaya da kallo, ta sauke idanunta a kan farantan da ke falon, alamar an ci an sha, dan har da taunannun ƙasusuwa, da ragowar kabeji a cikin farantan, ta sauke idanunta a kan Amina, da tayi tsuru-tsuru kamar ta yiwa sarki ƙarya. Cikin takunta na isa da taƙama ta ƙarasa shigowa falon, tana cigaba da yi musu kallon ƙasƙanci. Ɗaya daga cikinsu ta ce mata "Sannu da zuwa" Sai da ta sha ƙamshi sannan ta ce "Yauwa" tayi gaba ta nufi sashinta, Fadila ta bita ba tare da ko gaida su ba. "Hmm mai hali baya fasa halinsa, ayi dai mu gani idan tusa zata hura wuta, Ahmad dai ɗan uwanmu ne, ko anƙi ba za a taɓa canzawa tuwo suna ba" Amina ta ce "Dan Allah ku yi haƙuri". "Babu komai, ke dai mun gode sosai da karamcin da kika mana, dan rabon da mu zo gidan nan a kalle mu da mutunci har mun manta, mu mun tafi sai an jima". To muje in rakaku. Amina ta bisu Suka fita tare,  na ta sake basu haƙuri, ta rakasu har haraba, sannan ta dawo ta kwashe kwanukan da suka ɓata, ta gyara falon tsaf, ta shirya wa su Hajiya Zainab na su Abincin a kan dining, ta koma kitchen ta yi wanke-wanke, tana ta tsumayin jin kiran Hajiya Zainab amma shiru, ba tace mata komai ba. La'asar liƙis, Bayan an idar da sallar La'asar, Khalil ya kasa jurewa, ya ɗau wayarsa ya fara lalubar lambar Hafsa. Hafsa kuwa ta kammala haɗa kayanta na fita wurin sana'a, ta tsaya yin sallar la'asar. Wayarta ce ta fara ringing, har ta katse ba a ɗaga ba, aka sake kiran wayar, Mama ta gaza haƙuri ta ɗaga ta ce "Salla take" ta katse wayar. Da Hafsat ta idar sa salla, ba ta bi ta kan waye ya kirata ba, ta cigaba da shirin fitarta, tana daf da fita aka kuma kiran wayar a karo na uku. Ba tunanin komai ta ɗaga tare da yin sallama "Assalamu alaikum warahmtullah". Khalil ya yi wata ajiyar zuciya sannan ya amsa ya ce "Babyna ya kike?". Sarai ta ɗau muryarsa, amma ta haɗe rai ta ce "Wake magana?". "Khalil ne". "Wane Khalil ɗin" ta faɗa tana yatsuna fuska. "Khalil coustomern ki, kuma masoyin ki" ɗif ta kashe wayar, tare da wani guntun tsaki, ta ja kayanta ta bar gidan. Hajiya Zainab ce ta fito cikin taƙama, fuskarta babu annuri ta kalli Hajara, da ke ta kiwa tana komowa a falon ta ce "Ke kina gidan nan ki ka bari aka saukar mini wannan mutanen a gida? Uban waye ya bada izinin aikata hakan" Jiki na rawa Hajara ta ce "Wallahi Hajiya bani bace ba, ba laifi na bane, ni bama na gida na je kasuwa sayayya, Amina ce" Hajiya Zainab ta wani hura hanci, tana huci ta ce "Tana ina?" "Tana wurin Babanta" "Wuce ki kira mini ita, daga ita har shi ɗin" Hajara ta ce "To" ta bar falon jiki na rawa ta nufi harabar gidan. Amina na zaune tana karatu, suna hira da Baba jefi jefi. Hajara ta ƙaraso ta ce "Wai kuje in ji matar gidan" cikin Amina ne yayi wata tsuwwa, saboda tashin hankali. Baba ya kalli Amina ya ce "Uwata, lafiya kuwa? Ina fatan ba wani laifin kika aikata ba?" Amina ta girgiza kai ta ce "Ban yi laifin komai ba Baba" Baba ya ce "To Allah ya sa, tashi muje muji". Amina ta tashi suka bi bayan Hajara, ko da suka shiga falon, kallo ɗaya Amina ta yiwa Hajiya Zainab, ta san babu mutunci, babu afuwa a tare da fuskarta. Baba ne ya gurfana a gaban Hajiya Zainab, hakan ya sa Amina ma ba ta da wani zaɓin da ya wuce ta gurfana ɗin. "Waye ya baki iznin ki ɗau Abincina ki girka ki bawa wannan wahalallun mutanen?" Tai maganar cikin isa tana tsare Amina da idanu. Amina ta ce "Ba kowa". "Abincin naki ne, ko kuma da izinin wa ki ka yi hakan?" Amina ta ce "Wallahi ni ban san ba a bawa baƙo Abinci a gidan nan ba, naga idan wasu suka zo ana basu, kuma ce mini suka yi daga nesa suke, 'yan uwan maigidan ne, shi yasa na basu Abinci". "Kin taɓa ganin ire-iren wannan mutanen a gidan nan da zaki basu abinci na?, har ki kwashe mini kaya a fridge ki ba su? Talakan ubanki ne ya saya ya ajiye, da zaki ɗebar mini kaya kiyi gwaninta da su?" Damm! Ƙirjin Amina ya buga da ƙarfi, talakan ubanki ta maimaita abin a zuciyarta. Baba ya ce "Dan Allah, dan Annabi kiyi haƙuri, laifina ne da ban gaya mata dokar ki ba, amma dan Allah kiyi haƙuri ba zata sake ba". "In yi haƙuri ko kar in yi bai shafeni ba, zaka biya kuɗin abin da ta salwantar a albashinka, kuma wannan shi ne na farko kuma na ƙarshe, idan ta sake makamancin laifin nan, sai ta bar mini gida, ta koma ƙauyen da fito, ta je can ta cigaba da hauka da jahilicin da ta zo da su" Wata irin ƙunar rai ce ta kama Amina, jikinta har rawa yake saboda baƙi ciki, da ɓacin rai, da gari banza ne wani ya hɗata da Baba ya ci mutuncin ta, da sai in da ƙarfinta ya ƙare, amma yanzu babu damar magana. Baba ya ce "Ba damuwa Hajiya, insha Allah ba zata sake ba" ya kalli Amina ya ce "Uwata ki bata haƙuri" Amina kamar zata fashe, haka ta risuna ta ce "Allah ya baki haƙuri, ba Baba ne ya sai Abinci ba, insha Allah ba zan sake aikata haka ba". Hajiya Zainab ta ce "Kima sake, kiga ƙarshen rashin mutunci" Baba dai ya kwantar da kai, ya cigab da bawa Hajiya Zainab haƙuri. Sai da ta sallame su sannan suka tashi, Baba ya ja Amina waje, ya kalleta ya ce "Uwata, yanzu har kin manta da nasihar da na miki a kan zamanki a gidan nan? So kike sai kin yi dalilin rasa damarki ko?". Amina ta ce "A'a Baba, ban san dokar gidan ba ce ba saukar baƙi, amma insha Allah ba zan sake ba". Baba ya ce "To ki kiyaye, ki daina shiga abin da babu ruwanki, ko kuma aikata abin da ba a saka ki ba, kin ji ko?". "To Baba insha Allah ba zan sake ba" "Yauwa uwata, Allah yayi miki Albarka, maza koma ciki abinki" Amina ta juya ta koma, ranar na mata ƙuna, yadda aka ƙasƙanta mahaifinta a gabanta, a kan laifin da ita ta aikata ba shi ba. Haka ta koma ɗakinta sukuku, ta zauna baƙin ciki ya isheta, ta tuna yadda Baba ya gurfana a gaban matar da ya girmeta nesa ba kusa ba, ba ta kalli furfurar kansa ba, ta dinga zazzaga masifa, da Amina tana da burin idan ta samu ta cigaba da makaranta, amma taga kamar abin ba mai yiwuwa bane, saboda gaba ɗaya zaman gidan ya fara sire mata. Sai wajen ƙarfe tara na dare, sannan Hafsa ta dawo daga wurin sana'arta, ta tarar Mama ta dafa mata ruwan wanka, ga kuma girkin dare ta yi, ta zauna ta ci Abinci, tayi sallar isha'i sannan ta shiga ta yi wanka da ruwa mai zafi sosai, kasancewar dul zafi duk sanyi Hafsa ba ta wanka da ruwan sanyi, saboda tana jin daɗin zuba ruwan ɗumi ko mai ɗan zafi a jikinta. Ko da Hafsa ta fito daga wanka, mai ta nema ta shafa, tana yi suna hira da Mama, wayarta ta fara ringing, ta kai hannu ta duba, taga lambar Khalil, wanda sai a yanzu taga missed calls huɗu ya yi mata tana wanka, katse kiran ta yi, tare da kashe wayar gaba ɗaya. Mama tana kallonta ba tace mata komai ba, sai da ta bari Hafsa ta gama shirinta tsaf tana ƙoƙarin jan bargo. "Hafsa" Mama ta kira sunanta. "Na'am Mama". "Waye ya ke kiranki a waya?". "Mama ba kowa" "Ba na miki magana ne dan muyi jayayya ko ki mini musu ba, amsa kawai nake buƙata daga gareki" Mama tayi maganar babu alamar wasa a tare da ita. Hafsa ta ce "Mama kawai fa.. "Kar ki mini ƙarya Hafsa, namiji ne yake kiranki waye?". "Mama, ba komai fa tsakanina da shi, kawai zuwa yake ya sai awara a wurina". "Ina jinki sai kuma aka yi yaya?". "Cewa ya yi yana sona" Hafsa ta ƙarasa maganar kamar wadda tai saɓo. "Shi ne kuma ki ke wulaƙanta shi, har ya kira ki katse wayar? Anya Hafsa rayuwa zata cigaba a haka? Bai kamata kowa ya nuna yana sonki ki koreshi ba, ki bashi dama mana, na ɗaga wayar kina banɗaki, ya gaisheni, naji alamun nutsuwa a tare da yaron. Amina ina buƙatar in ga aurenki kan bar duniya, kina gani yau ina da lafiya gobe babu, ina son in ganki a hannu na gari kan in mutu Hafsa". Cikin matsananciyar damuwa Hafsa ta ce "Mama dan Allah ki daina irin wannan maganar, kin san fa komai Mama, mai zai sa in yi wani ganganci,gara kawai mu cigaba da rayuwarmu ni da ke a haka". "Hafsa, duk abin da ya wuce, to ka bar shi a baya kawai, karki waiwaya kan abin da ta wuce idan har ba na Alkhairi bane, ki sa ka magogi ki goge abin da ya shuɗe ki fuskanci rayuwarki, zama haka ba zai yiwu ba, ke macece zamanki a bakin hanya kina wannan sana'ar dan babu yadda zan yi ne, zamanki a ɗakin ki shi ne rufin asirinmu gaba ɗaya". Hafsa ta kwaɓe fuska za ta yi kuka ta ce "Ni dai dan Mama... Mama ba ta bari ta ƙarasa ba, ta ɗaga mata hannu ta ce "Ya isa, tun da ke dai ba a baki shawara, ki je kiyi abin da kike ganin daidai da ke ne" "Mama dan Allah kiyi haƙuri, ba nayi ne dan in ɓata miki rai ba". "Rabu dani ni" Mama ta faɗa a ƙufule. Haka Hafsa ta kwanta cike da damuwa, ta shiga tuno irin hali da yanayin ƙaddarori, da suka haɗu da su na rayuwa ita da Mama. Saura kwanaki uku a fara exams, akwai teses ɗin da Yazeed ya yi missing, lokacin da bai zo ba ba shi da lafiya, wasu malaman sun karɓi uzurinsa sun yi masa, wasu kuwa sai wahalar da shi suke yi. Ɗaya daga cikin malaman da ke wahalar da Yazeed, saboda ya rasa Attendance ɗinsa, kuma ya ce wanda bai yi Attendance ɗinsa na ƙarshe ba, ya sa a ransa ya faɗi jarrabawarsa. Sannan ya fito da wani littafi ya ce lallai kowa sai ya saya, littafin naira dubu biyu ne, kusan sati biyu kenan ana sayar da littafin. Kwatsam, saura kwanaki uku jarrabawa, ɗalibai na ta fama da karatu, ya shigo ajin, ya ce zai yi musu lecturer, kuma da wannan littafin zai yi amfani, duk wanda ba shi da littafin ya tashi ya fita, ko kayi Attendance idan baka da littafin nan, to baka da exams ɗin sa, ko da kuwa ka cinye duka. Idan kuwa baka da Attendance, amma ko baka da Attendance, muddin kana da wannan littafin to ka haye exams ɗin sa. Idonta ne ya sauka a kan Yazeed, da ya yi shiru, ko motsawa bai yi ba, balle a sa ran ya fito da nasa littafin, A kunyace tsirarun waɗanda ba su da littafin, suke tashi suna fita daga ajin, malamin yana ta musu bala'i cikin tozarci. Fadila ce ta miƙe tsaye, ta nufi hanyar fita, ta ajiyewa Yazeed littafinta ita kuma ta wuce zata fice. "Hey Madam zo nan" sautin muryar malamain ta daki dodon kunnuwanta, cak ta tsaya sannan ta waiwayo fuskarta babu alamar wasa, cike da izzarta ta kalli malamin, tana sauraren mai ze ce. "Ina littafinki?" Ya tambayeta yana tsareta da ido. "Bani da shi sir, ban samu na saya ba" ta faɗa ba tare da wata shakka ko damuwa ba. "Shi kuma wancan littafin da ki ka ajiye masa fa" ta yi mamakin yadda aka yi ya ga ta ajiyewa Yazeed littafi. "Ba nawa ba ne, na sa ne ya ara mini". "Ƙarya ki ke yi, Malam fito nan" Yazeed ya fito jiki a sanyaye, yana jinjina irin ƙasƙancin da za a masa a gaban mutane. Ga ajin yayi shiru an maida ido kan su. Lecturer ya kalli Yazeed ya ce "Littafinka ne ko nata?" Yazeed zai yi magana, Fadila ta ce "Sir ba fa ƙarya nake maka ba, littafinsa ne ba nawa ba" Yazeed baya son ya faɗi wani abin da zai janyowa Fadila matsala, ko cin mutunci, hakan ya sanya ya kasa magana. Lecturer ya karɓi littafin daga hannun Yazeed, sai dai yana buɗewa ya ga sunan Yazeed da Admission number ɗinsa. Shi kansa Yazeed bai san ya aka yi ta rubuta ba, Ya miƙawa Yazeed littafin sannan ya kalli Fadila ya ce "Kina nufin baki sai littafin ba?" "Eh na saya, amma nayi karatu na manta shi a aji, na dawo ban ganshi ba". Malamin ya ce "Ok, ku koma ku zauna, amma ki sake sayan wani". Yatsina baki ta yi, suka koma wurin zamansu. Har malamin ya yi ya kammala karatun, Yazeed yana kallon Fadila lokaci lokaci, yana jinjina abin da ta yi masa, ba dan tayi hakan ba da ya fuskanci tozarci da ƙasƙanci a gaban 'yan aji. Bayan fitar malamin, Yazeed yana son yiwa Fadila magana, amma 'yan aji sun saka ido, suna son ganin Action ɗin da su Fadila za suyi, amma Fadila ta haɗe fuska tamau, wani na kawo raini zata balbale shi da masifa da tsiwa. Yazeed ma basarwa yayi, amma ƙasan zuciyarsa so yake ya yi mata magana. Class rep ne ya shigo da takaddu a hannunsa, na wata test da suka yi. Ya fara rarrabawa kowa test ɗin, sai dai abin da ya ƙara bawa Yazeed mamaki, bai wuce yadda aka miƙo masa takadda ba, ya karɓa yana dubawa, wannan dai ba rubutunsa ba ne, dan lokacin da aka yi test ɗin ma ba ya nan, gashi nan ya ci 7/10. Shiru yayi yana sake nazartar rubutun, tabbas na Fadila ne, dan bai manta wanda ta rubuta masa a littafin sa ba. Yana waigowa ya hangeta ta tashi zata bar ajin, cikin sauri ya tashi ya bi ta ƙofar baya, ya bi bayan Fadila, tana ta sauri ta nufi in da motar ta ke ajiye. Sauri yake sosai, yana kiran sunanta, tazararsa da ita ba yawa sosai, tana jinsa ta share shi, ta cigaba da sauri. Sai da taje in da motar take sannan ya cinmata. Ajiyar zuciya ya yi ya ce "Ina ta magana kin mini shiru". "Malam lafiya ta yi maganar kamar bata taɓa ganinsa ba" "Dama... "Kaga sauri nake tafiya zan yi" "Ga littafinki" ya yi maganar yana miƙa mata littafin. Sai a lokacin ta waiwayo ta kalleshi da fararen idanunta da ke matuƙar narka zuciyar Yazeed. "Ka riƙe kawai" ta faɗa tana ƙoƙarin ɗauke kanta daga fuskar Yazeed. "A'a ba za ayi haka ba, Halaccin da ki ka yi mini yanzu ma, Na gode sosai ubangiji Allah ya saka da alkhairi, kuma ga test ma kin yi mini, duk da hatsarin da ke cikin hakan, Na gode sosai ƙanwata". Ɗagowa tai ta kalli Yazeed "Wacece ƙanwar taka?". "Fadila mana" ya bata amsa, ta yamutsa fuska ta ce "Ka kiyayeni, ni na maka kama da ƙanwarka, ƙila ma na girmeka tsaurin ido kawai, na ce ka bar littafin, ka bani hanya zan kunna mota in tafi". Wani irin murmushi Yazeed yake, wanda sai da haƙoransa suka bayyana, wanda ya ƙara masa kyau, daga murmushi ya fara dariya, har da rufa baki, dan ba ƙaramin dariya Fadila ta bashi ba. "Saboda kina ganin tsayin mu ɗaya, shi ne ki ke cewa kin girmeni, ai ko da ki ke doguwa tubarkallah na fiki tsayi, balle ki kalli wannan tsofaffin idanuwan nawa, ki ce mini wai kin girme ni" "To sannu tsoho" ta faɗa tana kallonsa. "Yau ba zaki tsaya karatun ba?". "Eh" "To shikenan, Allah ya sauke ki lafiya?" "Kamar yaya Allah ya sauke ni lafiya, masu ciki fa ake gayawa haka" Yazeed ya ce "Subhanallah, ba haka nake nufi ba, ina nufin Allah ya kai ki gida lafiya". "Inyee me ake tattaunawa ne haka besty da besty, yau munga ƙarshen ƙauna, kowa na ƙoƙarin kare ɗan uwansa a kowacce gaɓa da ɗayan yake fuskantar barzana" Cewar Captain da ya ƙaraso yana dafa Yazeed. Fadila ta haɗe rai ta ce "Nifa bana son sa ido, kar ka kuma ce mini wani bestynsa na gaya maka". Yazeed ya ce "A'a Nothing like besty in Islam, she's my sister in Islam, ƙanwata ce ta Addinin Musulunci ko Fadila?" "Kai ka sani" tai maganar tana hararasa. "Kwa dai ji da shi, muna nan mun kasa mun tsare mun zuba ido, muga yadda ƙarshen wasan zai kaya, kwana biyun nan, kullum sai naga ka lallaɓo jikin motar nan kun keɓe kuna ƙusƙus, idan tai wari zata bazu mu ji ai" daga haka ya juya ya tafi yana murmushi. "Kaga ustaz ka ke ko Sheikh, ka Matsa zan kunna mota, ni bana son damuwa yanzu ka zo kana suma, ace ni ce". "Sunan nawa ma baki sani ba, amma kin iya rubutawa a cikin littafi ko? Da kuma test ɗin da kika rubuta mini, ni ina ga zanje in gayawa malamkn nan gaskiya, ni ban yi test ɗinsa ba, ƙanwata ce ta yi mini". "Sai ka dawo" da haka ta rufe motar, ta kunnata ta ja ta a hankali ta bar wurin. A hankali Yazeed ya dinga shafa sajensa yana murmushi, shi dai in dai Fadila ta kula shi, yana kasancewa cikin farin ciki mara misaltuwa tsawon wannan wuni. Khalil ya riƙe wuta, wurin yawan kiran Hafsa a waya, kuma sai ya daidaici tana gida yake kiran, gudun kar Mama ta ɓata rai, sai ta ɗau wayar ta amsa masa ciki ciki. Idan ha ji haka sai ya ce ta bawa Mama ya gaisheta. Duk wulaƙancin da take masa, baya gajiya da safe da yamma sai ya kirata, bayan saƙonnin Soyayya da yake tura mata, amma ko ɗaya bata kulawa, balle ya sa ran zata amsa saƙonnin nasa. Sai dai kasa jure ganinta yayi, dan haka ya ƙudurce a ransa zai zo ko a ranar ne ya ganta ya juya ya koma, ba tare da yaje gida ba Tana zaune tana fama da masu sayan awara, ta samu ta sallami da yawa daga cikin masu sayen, katsam ta ɗaga kai, taga fitowar wanda ta fi tsana a rayuwarta. Gabanta ya faɗi dan ba ta san da wacce ya zo ba, dan a kullum idan zasu haɗu ba shi da burin da ya wuce yaci mutuncinta, haka kwanaki ya zo ya sameta har wurin sana'arta a gaban mutane ya ci mutuncinta ba tare da kunya ko shakka ba. Kallo ɗaya ta yi masa ta ɗauke kanta, ta cigaba da abin da take yi. "Au haryanzu kina aikin wahalar nan? Ko da yake ba abin mamaki bane ba, tun da ke da uwarki ba ku gaji arziƙi ba, titi dai a nan zaku ƙare" Hafsa ta sunkuyar da kanta, tana jin wata irin ƙuna a cikin zuciyarta, wanda suka haddasa mata zubar hawaye. Mai shayin kusa da Hafsa ne ya taso ya ce "Haba Malam, kai wani irin mutum ne mara tunani, kullum sai ka zo cikin mutane kana cin zarafinta, haba malam kamar ba musulmi ba". A fusace mutumin ya ce "Ba ruwanka da ni malam, ka fita harkata a wannan sabgar, waye ya sa da kai, wannan Yarinyar har wadda za a tausayawa ce, uwatta ta goya mata baya tan zama a kan titi tana tallan kanta, ta ɓige da suyar awara tana karuwanci, ko da yake ai barewa bata gudu ɗanta yai rarrafe, abin da taga uwarta na yi ne" Yadda miyagun matashin suka daki zuciyarta, ba tare da ta shirya ba, ko wani tunanin ba, ta daki kaskon man da ke kan wuta, ya ƙonawa mutumin ƙafa. Wani irin uban ihu ya saki, nan da nan ƙafa ta yi ja, ya yin da babu alamar nadama a tare da Hafsa. Salati da salallami mutane suka fara yi da ganin abinda ya faru. Har Hafsa ta yi wannan aika aika ta gama, kuka take yi, mutane suka dinga bashi rashin gaskiya. "Ba dai ni ki ka yiwa haka ba, to Wallahi zaki gani, zaki ga abin da zan miki, sai kin gwammace kiɗa da karatu da ni ki ke zancen". Mai shayi ya ce "Ai ni kin mini daidai Hafsa, ɗan iskan banza kawai, bari in aika yaro ya sayo miki man ki, ki ƙarasa ki tashi. Amina ta girgiza kai ta ce "A'a, gida zan tafi" ta yi maganar tana share hawaye. Mai shayi ya sai mata mai, ya bata, da ƙyar ta karɓa, ta tattara kayanta ta tafi gida, dan ba zata iya cigaba da zama ba. Da ta je gida ma ba ta bari Mama ta gane ba halin da take ciki ba, Maman ma ba ta bi ta kanta ba, dan ta  fuskanci Hafsa yau tambotsan nata take ji. Washegari da sassafe, Hafsa na shirin zuwa ta kai markaɗen wake, aka ƙwanƙwasa ƙofar gida. Hafsa na shirin zuwa ta buɗe, Mama ta ce "Ƙarasa bari in leƙa in ga waye" Mama ta sanya mayafi, ta ƙarasa ƙofar gidan, tana buɗewa sai ga 'yan sanda biyu a tsaye da motarsu a farkon layi. Gabanta ne ya faɗi ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, Yallaɓai lafiya kuwa?". "'yar ki muka zo nema" "Me 'ya ta tayi muku?" "Yanzu ba lokacin yaɗa rahotanni bane, idan muka je can kya ji abin da tayi". Jin Mama shiru ne ya sanya Hafsa ta tashi ta bi bayanta, sai dai tana zuwa soro ta yi turus, ganin 'yan Sanda. "Mama lafiya kuwa?". "Kece Hafsa?" "Eh nice" "An bamu iznin mu kama ki, dan haka ki zo mu wuce station". Ayshercool 08081012143GABA DA GABANTA AISHA ADAM (AYSHERCOOL) To get the latest update of the story Follow me on Watpad Ayshercool 7724 Arewabooks Ayshercool 7724 What's app 08081012143 Page14 "Innalillahi wa Innalillahi raji'un" shi ne abin da Mama take ta maimaitawa, ya yin da Hafsa tayi tsumu tsumu tana tunanin wani lafin ta yi, da har 'yan sanda za su zo gida kamata?. Mama ta kalleta cikin tashin hankali da firgici da yaya mamaye fuskarta ta ce "Hafsa me kika aikata haka, da za a zo har gida ana ƙoƙarin kamaki?". Hafsa ga girgiza kai ta ce "Ni Mama ban yi komai ba, ban taɓa kayan kowa ba ba abin da ya haɗani da wani". "Ke malama, ba lokacin tattauna wannan maganar ba ne, wuce mu tafi"  Suka ingiza ƙeyar Hafsa, tana kuka tana kiran Mama, a gaban maƙota, wani maƙocinsu Hafsa ya yi ƙoƙarin dakatar da su, ya ji ba'asi amma suka ƙi saurarsa, Mama ta ce su bari ta ɗauko mayafi su tafi tare, nan ma suka ƙi suka ce ta biyo su a baya. A kiɗime Mama ta shiga gida, ta yafo mayafi, ta rufe gidan hankali tashe ta nufi titi. Tuni Maman ta fara jin haki, saitin zuciyarta ya mata nauyi, alamun hawan jininta zai tashi, kai tsaye station ɗin unguwarsu ta nufa, amma da taje aka ce mata ai ba wannan police station ɗin aka kai Hafsa ba. Rushewa Mama tayi da kuka, tana tunanin ina aka kai Hafsa, 'ya mace a hannun 'yan sanda, ta kuma bazama ta tari wani abin hawan ta tafi wani division ɗin. Khalil ji yake tamkar ana hura masa wuta a ƙirjinsa, babban burinsa kawai shi ne ya ganshi a garin Kano, a gaban kaskon wutar suyar awarar Hafsa, ya yi tozali da fuskarta da take sa shi nishaɗi da nustuwa. Da fari ya jira ya yi booking ɗin jirgi, ya taho bayan kwana biyu, amma ya ji ya kasa jurewa, kawai ya ɗauki motarsa da yake amfani da ita a nan Abuja, ya nufo gida, yana tafe yana murmushi, zuciyarsa cike da muradin tozali da fuskar Hafsat.   Kusan wuni Mama ta yi tana bulayi, amma ta rasa station ɗin da aka kai Hafsa. Gaba ɗaya hankalinta a tashe yake, kuka kam babu irin wanda ba tayi ba, 'ya mace a hannun 'yan sanda abin da tayar da hankali sosai. Tana komawa gida maƙota suka fara tambayarta yaya ina Hafsan, cikin kuka ta ce ta rasa station ɗin da aka kai Hafsa, yanzu ma kuma bazama za tayi neman in da aka kaita. Maƙocinsu mai suna Malam Sani ya ce "A'a Maman Hafsa ba za ai hak ba, bari in ɗauki babur ɗina in je in zazzaga nima, amma ki nemi wuri ki zauna ki huta, tunda dama ba cikakkiyar lafiya ce da ke ba". Da ƙyar suka rarrashi Mama, ta haƙura ta zauna, Malam Sani shima ya tafi zagawa stations ɗin da suke nan shiyarsu. Ko mintuna Arba'in ba ayi ba, Mama ta kasa jurewa, ta sake ɗaukar mayafi, ta cigaba da yawon neman Hafsa.   Khalil kuwa, a Hotel ya sauka, yayi wanka ya ci Abinci, dan kwana ɗaya zai yi ya koma, baya son Mummy ta tuhume shi dalilin dawowarsa a yanzu, bayan bai daɗe da tafiya ba. Wajen ƙarfe biyar na yamma, yayi kwalliya ya ɗau motarsa zuwa wurin sana'ar Hafsa, amma ya tarar bata nan. Ya ɗakko wayarsa ya kirata, wayar ta shiga amma ba a ɗauka ba. Fitowa yayi daga motar, ya ƙarasa wurin mai shayin dake kusa da wurin da Hafsa ke sana'a, suka gaisa sannan Khalil ya ce "Dan Allah Hafsa fa?". Mai shayi ya ce "Gaskiya yau ba ta fito ba, kuma ban jin zata zo, da zata zo da tuni ta almajiri ya fara kawo mata kaya". "Dan Allah ina ne gidansu?" "Taɓ, yo wannan ina zata saki jiki da wani har a san gidansu, ni dai na so naji ance gidansu a nan wajen makarantar brilliant yake, daga nan sai ka tambaya". Khalil ya ce "Masha Allah, na gode sosai, Allah ya sa dai tana lafiya". Har Khalil ya juya zai tafi, wani a cikin rumfar mai shayin ya ce "Ai nifa ina ga rashin fitowar tata yana da nasaba da abin da ta yiwa mutumin shekaranjiya, dama ya ce zata gani, maybe ko tsoro ta ji kar ya mata wani abu". Cak Khalil ya tsaya, ya waiwayo, ya kalli mutumin da ke maganar, ya ce 'Malam wani abin ne ya haɗata da wani?". Mai shayi ya ce "Wallahi wani mutumi ne yake yawan zuwa wurin nan, ya yi mata zagin rashin mutunci a gaban Mutane ya tafi, babu wanda ya san abin da ya haɗata da shi, aikuwa shekaranjiya ta watsa masa mai a ƙafa ya ce zata gani, wataƙila shi ya sa yau bata fito ba" Cikin hanzari Khalil ya ce ya gode, jikinsa na rawa ya koma mota, gidansu Abdul ya fara zuwa, dan ya fishi sanin kan unguwannin. Yana tsaye a ƙofar shagon Abdul, ya kira shi a waya, Abdul ya ɗaga tare da "Assalamu alaikum". "Wa'alaikum salam, kana ina ne? Na zo shago baka nan?". Abdul ya ce "Wane shagon?" "Shagonka mana, ina Kano fa, dan Allah kana ina akwai matsala ne". "Subhanallah, Allah yayi mana maganin matsala, fito titi mu haɗu" Khalil ya ajiye wayar, ya ja mota ya koma titi. A titi ya samu Abdul ya ɗauke shi suka tafi. Abdul ya ce "Wai ina zamu ne? Tukuna ma me ka dawo yi?, kwata kwata yaushe ka tafi da har ka dawo?". Khalil ya kwashe komai ya gaya masa, Abdul ya jinjina kai ya ce "Ikon Allah, to Allah ya sa lafiya muje mu nemi gidan" Suka ƙarasa makarantar da aka kwatanta musu, da tambaya da ƙyar suka gano gidan, sai dai suna zuwa suka tarar gidan a rufe. Khalil yayi mamakin ganin gidansu Hafsa, ɗan ƙuƙuta kamar ɗakin tattabaru. Hakan yayi daidai da dawowar Malam Sani daga taya Mama neman Hafsa. Ganin yana ƙoƙarin shiga gidan kusa da na su Hafsa, ya sanya Abdul ya ƙarasa, ya yi masa sallama, Malam Sani ya amasa masa, suka gaisa. Khalil ma ya ƙaraso, suka gaisa da Malam Sani, Abdul ya ce "Dan Allah munga kaine maƙwabcin wannan gidan, munzo wurin su Hafsa ne, kuma basa nan ga layin ba kowa balle mu tambayi wani". Malam ya ce "Kunga dawowar nan tawa? Daga neman in da yarinyar take nake Hafsa, tun safe 'yan sanda suka tafi da ita, ba wanda ya san ina suka kaita, mahaifiyarta sai bulayi take tana neman ta, duk station ɗin da taje sai ace bata nan, shine nima na ɗau babur na zaga nima ban dace ba, gashi mu bamu san wani nasu ba, kowani tsayayyen namiji, balle muje tare a cigaba da nemansu, su kaɗai suke zaune a nan" Khalil ya ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, me Hafsa ta yi haka har da za a kamata? Yarinyar da babu ruwanta da kowa ya za ai ace tayi laifin da za a kamata?" Nan da nan fuskar Khalil ta sauya, ya harzuƙa matuƙa. Abdul ya ce "Ka kwantar da hankalinka mana, yanzu ba kumfar baki ce abin yi ba, mota zaka ɗauka muje division ɗin unguwar nan, muje mu ji me zasu ce" Da ƙyar Khalil ya kwantar da hankalinsa, Abdul ya karɓi tuƙin, suna tafe Khalil sai zufa yake duk da sanyin AC dake motar, ace an kama Hafsa tun safe, amma babu wanda ya san ina ma aka kai ta. Kallon tausayawa Abdul yake wa Khalil, dan da alama ya faɗa soyayyar yarinyar nan da yawa, babban abinda yake fargaba shi ne yadda mahaifiyar Khalil zata karɓi batun auren Khalil da Hafsat ba. Abdul na parking, Khalil ya buɗe motar da sauri, kamar zai faɗi ya shiga cikin station ɗin. Abdul ya ƙarasa kashe motar da hanzari, ya fito ya bi bayan Khalil, dan kar yaje yayi kataɓora. Khalil ya yi sa'a D.P.O yana nan, aka yi musu iso suka shiga cikin ofishin DPO. Bayan sun gaisa Khalil ya yi masa bayanin meke tafe da su. DPO ya ce "Gaskiya ba station ɗin nan aka kawota ba". Khalil ya ce "Ai a shiyyarka take, dan haka ka bincika mana in da aka kai ta" Abdul ya ce "Haba Khalil, ka bi a hankali mana, ya kake magana a haka?" "Bar shi yayi mini rashin kunya, yanzu in sa saka mini shi a cell". Khalil ya ce "Ni zaka dubi kamata kace a sakani a cell, ai ko kisan kai nayi nafi ƙarfin sarƙa Wallahi" "Shut up Khalil, meye haka wai?" Cewar Abdul da yake zarewa Khalil ido. "Malam ka daina zare mini ido, kana ji zai raina mini hankali dan yana kan wannan kujerar" da ƙyar Abdul ya sa Khalil ya yi shiru, ya lallami DPO da ƙyar, sannan ya bincika musu in da aka kai Hafsa. Tuni su Fadila sun fara jarrabawa, kuma ba ƙaramin ganin amfanin abin da Yazeed yake koya mata tayi ba, a sauƙaƙe take karatunta, kuma take rubuta jarrabawar ta cikin nasara. A gobe ne zasu rubuta jarrabawar course ɗin da ta tsana, saboda bata ganewa, tana matuƙar buƙatar taimakon Yazeed, amma ba zata iya cewa ya koya mata ba, dan a ganinta idan tayi hakan ta faɗo. A haka ta tunkari ajinsu, ranar ba su da jarrabawa, wasu daga cikin ɗalibai ne suka shigo karatu. Sassanyan ƙamshin turarenta ne ya shiga hancin Yazeed, wand ya saukar masa da wata irin nutsuwa ta mussaman. Yana zaune cikin ɗalibai, yana musu tutorial, galibinsu mata ne, duk sun kewaye shi, ciki har da wata yarinya Azima, sai nanuƙar Yazeed take, shi kuma yana takure jikinsa, yana matsawa, kallo ɗaya zaka yi masa ka san a takure yake musu koyarwar nan. A hankali ya ɗaga idanunsa ya sauke su a cikin Fadila, da take tsaye tana kallonsa. "ماذا حدث ىااختي" Ya faɗa yana kallonta fuskarsa ɗauke da murmushi. A hankali ta janye idanunta, tare da lumshesu, ta nufi wurin da take zama, hakan ya so tafiya da hankalin Yazeed, dan ta ƙasan idonsa ya cigaba da binta da kallo, har taje ta zauna, saboda ba ƙaramin kyau ta yi masa ba, ta ɗanyi kwalliya yau, sai dai abin da bai masa daɗi ba shi ne yadda ta yi parking ɗin gashinta, ta fito da shi. Captain ne ya kalli Fadila ya ce 'Babbar yarinya, irin wannan wanka haka kamar zaki gasar sarauniyar kyawawan Nigeria?" Harar captain ta yi ta basar, wani irin kishi ne ya kama Yazeed, amma ya danne ya cigaba da ƙoƙarin cigaba da abin da yake. "Malam Yazeed wai ya ne, sai gaba muke kana dawowa baya?" Azima ta yi maganar tana ƙoƙarin taɓa shi. Cikin sauri ya janye jikinsa ya cigaba da koya musu, sai dai lokaci lokaci ya kan ɗaga kai ya kalli Fadila, da sun haɗa ido, sai ta harareshi ba gaira ba dalili. Gaba ɗaya suka kasa gane kan Yazeed, hankalinsa yana kan Fadila. Haka ya ƙarasa musu ya tashi. Azima ta ce "Aikin banza, wannan gayen ba shi da zuciya, da yaga yarinyar nan yayi ta rawar kai, tana wulaƙanta shi". Amra da a baya ƙawar Fadila ce, amma yanzu ƙawancen na su ba sosai ba ta ce "Ke ina ruwanki to, tunda bake yake shigewa ba". Fadila ta bar ajin, amma motarta na wurin da ta saba ajiyeta, haka Yazeed yai ta dubawa, har ya gano ta, tana zaune a wani wuri ita kaɗai, tana waya. Ba tsammani taga Yazeed ya zauna kusa da ita, wani irin shocking ta ji a jikinta, gaba ɗaya ta nemi nutsuwarta ta rasa. Bakinta ne ya hau rawa ta kasa cigaba da wayar da take yi, ta waiwayo ta kalli Yazeed, taga ita yake kallo gaba ɗaya jikinta ya ƙara yin sanyi, haka kurum ta ji wasu hawaye da bata san na menene ba suka taru a idonta, ga wani irin mugun kwarjini da yayi mata, wanda da bata taɓa sanin yana da shi, musamman kasancewar kusan kullum da facemask a fuskarsa, yau kuma ya cire, ga sajensa ya ƙara yawa, gashi ya ɗan tsare ta ido. Yazeed ya yi murmushi ya ce "Gani naga kamar kina son ganina". Kallonsa tayi ta sake haɗe rai. Kamar ba za tai magana ba ta ce "Ka matsa daga kusa da ni". "Zan matsa, amma meyasa hannunki yake rawa, ko baki da lafiya ne?" Ɓoye hannun tayi tana jin yadda jikinta ke cigaba da rawa, ba tare da tasan dalilin hakan ba. "Fadila" ya kira sunanta. "Kallonsa ta kuma yi, amma ta ji idanunsa sun yiwa nata nauyi a nata idon" "Naga kina nema ne ne, shiyasa na biyoki nan". "Ni ba nemanka nake ba" ta faɗa tana kauda kanta gefe daga kallonsa. Yazeed ya ce "Ba nemana ki ke ba, amma kika tsaya kina kallona? Shikenan na ji, ɗauko littafin in koya miki, kina son in koya miki abu, amma kin kasa gaya mini, ba ke kika ce in koya miki ba, ni nace zan koya miki, ɗauko mu yi" Kallonsa tayi da mamaki, tana tunanin yadda akai ya san abin da ke ranta. "Ba mamaki zaki tsaya yi ba, ɗauko muyi abin da yakamata". "Malam ka Matsa daga kusa da ni" ta faɗa tana haɗe rai. Yazeed yayi murmushin sa mai ƙayatarwa ya ce "Ko na matsa ba zaki daina jin abinda kike ji ba, kuma hannunki ba zai daina rawa ba, amma gashi na matsa, kawo littafin in ga me kika karanta a kan course ɗin". Miƙewa tsaye tayi ta ce "Dan Allah malam ni ka ƙyaleni, sai kace dole, ka fita daga harkata kar ka sake zuwa in da nake, bana buƙatar taimakon naka, ni ai bance maka ina son ka koya mini abu ba". Shima ya miƙe tsaye ya ce "Am sorry, Allah ya baki haƙuri, na yi miki shishshigi, ba zan sake ba insha Allah" Jakarta ta ɗauka tai gaba, tana cigaba da yadda jikinta ke tsuma kamar wadda tai artabu da aljan. Cikin ikon Allah su Khalil suka gano in da aka kai Hafsa, tun safen nan ba ta ci komai ba, sai kuka da take yi, kuma taƙi magana, fuskarta duk tayi jawur saboda kuka, an rufeta a ceil. Su Khalil basu tarar da DPO division ɗin ba, sai yaransa, bayan sun gaisa Aminu ya sanar da su cewar sune wanda suka zo wurin Hafsa. Ɗansandan ha kallesu ya ce "To mintuna uku kacal zaku yi, dan kotu zamu kaita". "Wai a kan ta aikata wane laifin?" Khalil ya yi maganar a hargitse. Abdul yayi saurin dakatar da Khalil ya ce "To Yallaɓai, a bari mu gantan". Aka fito da Hafsa, idanunta jawur, tana rarraba ido taga Mama, kawai taga Khalil da Abdul, aikuwa tayi sak tana kallonsu, ta ƙaraso gaban teburin ta tsaya tana sunkuyar da kai. "Hafsat, me kika yi aka kawo ki nan?" Khalil ya yi maganar yana kallonta cikin kulawa. Fashewa da kuka Hafsat tayi, ta kasa magana. "Ai na zata faɗa ba, tayi attempting illata mutum, kina mace amma kina abin 'yan daba, ta ƙonawa mutum ƙafa da mai, kuma ta rarumo makami tana nema ta sokawa mutum" cewar wani ɗan sanda mai jajayen idanuwa. Tsaki Khalil yayi, ya ce "Wanan dalilin ne ya sanya aka kawota nan, wace irin magana ce wannan? Ta yaya zata ɗau makami tace zata illata wani, Yarinyar da ko kuzarin kirki ba ta da shi?" "Kaga shi mugu fa ba a ido ake ganinsa ba, wanda ya kawo ƙararta ya ce bai yadda da sulhu ba, a kai su kotu a bi masa hakkinsa" Khalil ya ce "Shi dabban ina ne da zai kai mace kotu ya tsaya a kotu ya ce wai ta ɗau makami zata masa illa? Wace doka ce ma ta bada damar a riƙe mutum tsawon wannan lokaci family ɗinsa ma ba su sani ba, a bani belin ta". DPO ne ya shigo yana zazzare ido "Yaya, Yaya, meke faruwa nake jin hayaniya haka?" "Welcome sir, wannan ne ya zo zai mana tsageranci, wai sai an bashi belin wannan 'yar dabar". "Wallahi ka kuma ce mata 'yar daba, saina ɓata maka rai". "Kai nutsu, nan station ne, kar kai mana fitsara" Cewar DPO yana zarewa Khalil ido. Abdul ya ce "Dan Allah Khalil abi komai a sannu". Khalil ya ce "Wallahi ba zan bi a sannu ba, ya za'a kama yarinya ba bisa ƙa'ida ba, kuma aci zarafinta, sun ajiyeta daga ita sai su a wuri ko danginta basu san in da take ba?" DPO ya ce "Au rashin kunya zaka mini, kai ku mayar da ita ceil, ba za a bada belin nata ba, sai ta ɗau nauyin maganin wanda ta illata". Khalil ya ce "Bari in ɓullo muku in da ya dace" kawai ya fita daga cikin station ɗin, kuka Hafsa ta saka, da taga Khalil ya juya ya fita. Abdul ya bi bayansa da sauri. Mintuna bakwai, DPO ya fito a gigice yana faɗin "Suna ina? Wannan wane irin ɗan tijara ne, maimakon ya tsaya a sasanta sai ya kunno mini wuta daga saman ƙololuwa? Ku kira mini shi mana". Khalil ne ya shigo ya ce "To zaku bani ita ko kuwa?". "Za a baka, ai ban sai kai waye ba, ashe ɗan gidan controller Ahmad Dutse ne". Khalil Ya ce "Wannan matsalarku ce, a bani ita kawai". DPO ya ce "Ai irin haka bayani ake yi, ba bankaɗo mini wita daga sama ba, wadda zata ƙone 'yar kukeear tawa ba, a fito da ita". Aka fito da Hafsa, DPO ya ce "Amma zaku dawo gobe in Allah ya kaimu, za'a kashe case ɗin da wanda ya shigar da ƙarar". Aka bawa Khalil wata takarda ya yi rubuce-rubuce, Sannan aka bawa Hafsa damar bin Khalil. Suna fitowa harabar wurin Khalil ya ce "Babyna ba suyi miki komai ba dai ko?". Ta jinjinawa Khalil kai. "Ki gaya mini ko sun miki wani abun?" Ta kuma girgiza masa kai. "To Allah, maza muje mota, Mama na can gida bata san in da ki ke ba". Ba musu ta bi Khalil, ya buɗe mata bayan motar ta shiga, Khalil ya shiga ɗaya gefen ya zauna, Abdul kuma ya ja motar suka tafi. A ƙofar gida suka tarar da Mama, tana ta kuka, maƙota sun kewayeta suna ta bata haƙuri suna rarrashinta, amma sai gursheƙen kuka take yi. Da gudu Hafsa ta fito daga motar ta rungume Mama tana kuka, Khalil da Abdul suka ƙaraso, suka gaida Mama sannan Abdul ya ce bari suje suyi sallar magariba, sai su dawo dan an fara kiran salla. Maƙota suka dinga shiga yiwa Mutane su Mama jaje, wasu dama zuwa ganin ƙwaƙwaf suke yi. Bayan sun dawo daga salla, suka koma gidan su Hafsa, Mama tayi mus iso zuwa cikin gidan, ta shimfiɗa musu sallaya suka zauna, yayin da ita da Hafsa suke zaune a kan tabarma, Hafsa tana kusa sa Mama kamar za a ƙwace mata ita. Khalil kuwa sai mamakin ƙanƙantar gidansu Hafsa, kai da gani ba sai an gaya maka ba suna fama da rayuwa, wani irin tausayin Hafsan ya ƙara kama shi. Suka kuma gaisawa, Mama ta ce "Sai dai ban gane ku ba, ko jami'ansa tsaro ne na farin kaya?". Abdul ya ce "A'a Mama, ni sunana Abdul, wannan kuma Khalil" nan ya kwashe yadda suka gano Hafsa har suka dawo da ita gida. Mama ta ce "Allah sarki, yau gani ga Khalil muna gaisawa a waya, ubangiji Allah ya saka muku da alkhairi, Allah ya jiƙan magabata, idan suna raye Allah ya ja da ransu, yadda kuka faranta mini ubangiji Allah ya faranta muku" Abdul ya ce "Ameen Mama, bakomai ai yiwa kai ne" Mama ta mayar da dubanta ga Hafsa ta ce "Hafsa, meya haɗaki faɗa da namiji a wurin sana'arki har ki ɗau makami?". "Mama wai kin yadda zan ɗau makami in illata wani?" Tayi maganar a raunane. "To Hafsa meya haɗaki faɗa da wani, har a kai ki wurin hukuma?". "Mama ni ban nunawa kowa makami ba, Ƙona shi nayi da mai a ƙafa". Mama ta buɗe baki ta ce "Hafsa wa kika ƙona da Mai?" Cikin kuka ta ce "Mama Najib ne fa, yana zuwa wurin sana'ata ya ci mini mutunci, na kasa jurewa na ɗau wannan matakin" "Amma Hafsa kin taɓa gaya mini? Sai ki yanke wannan hukuncin haka?" Khalil ya ce "Mama ayi haƙuri, kinga kamar haryanzu a tsorace take" Mama tayi ajiyar zuciya ta ce "Shikenan, na gode muku sosai Allah ya jiɓanci lamuranku" Abdul ya ce "Ameen Mama, gobe in Allah ya kaimu zamu zo muje station ɗin, a rufe case ɗin gaba ɗaya". "To Allah Ubangiji ya kai mu na gode sosai". Har ƙofar gida Mama ta rako su Abdul, tana ta cigaba da sa musu albarka. Khalil ya buɗe motar ya ɗauko wata ƙatuwar leda ya ce "Ga Abincinta da muka sai mata a hanya ba ta samu taci ba" da haka suka yi sallama su Abdul suka tafi gida. Suna tafe Khalil na sake jinjina yanayin rayuwa da su Hafsa ke fama da shi. Hall ɗin exam ya cika ya batse, ɗalibai sun duƙufa suna ta rubuta abin da suka sani. Fadila kuwa abin da ta sani bai kai ya kawo ba, ta ɗaga kai taga yadda Yazeed idaan ya samu dama yake taimakawa na kusa da shi, ga lokaci ya ja, tuni wasu ɗaliban sun fara bayar da tasu jarrabawar suna fita, amma ita tana zaune bata rubuta abin kirki ba, kanta ya ɗau zafi sai gumi take ta goshi. Cikin sa'a ɗalibai suka ragu daga hall ɗin, invigilator ya mayar da Fadila kusa da Yazeed, hakan ba ƙaramin daɗi ya yiwa Fadila ba, tana sa ran Yazeed ya taimaka mata. Sai dai taga Yazeed ya yi mursisi ko kallon in da take yaƙi yi. Wankin hula na neman kai Fadila dare, lokaci na ta tafiya, a kowane lokaci za a iya karɓewa, saboda lokaci ya kusa cika. Bata ƙara tsinkewa da lamarin ba, sai da taga Yazeed yana tattara takardunsa, zai tashi yayi submitting. TOFA, ZATA BAR YAZEED YYO SUBMITTING, KO KUMA ZATA SAUKE IZZA TA NEMI TAIMAKO? Domin gyara, sharhi ko shawara 08081012143READ THE CHAPTER 15 AT AREWABOOKS https://arewabooks.com/chapter?id=6386388f094c9b1220e3fdb9. GABA DA GABANTA AISHA ADAM (AYSHERCOOL) To get the latest update of the story Follow me on Watpad Ayshercool 7724 Arewabooks Ayshercool 7724 What's app 08081012143 P 15 Ganin da gaske Yazeed yana shirin tashi ya tafi ba tare da ta kammala ba, ya sanya a hankali fadila ta ce "Ban gama ba fa" Wani miskilin murmushi ya yi, ba tare da ya bari Fadila ta gani ba, ya ɗan tsuke fuska ya kalleta ya ce "Magana kike?" Ta jinjina masa kai alamar eh. "Ban ji me kika ce ba?" "Ban gama ba?" Ta furta a hankali. "Kina buƙatar taimakona ne?" Ta jinjina kai alamar eh. Yazeed ya gyara zamansa ya ce "Me kike buƙata?" Nan ta gaya masa wanda ba tayi ba a tambayoyin. Ya ajiye mata takardarsa ya ce "Gashi nan kwafi". "Ka karanto mini, bana iya ganowa sosai". Murmushi Yazeed ya yi, yana karanta mata a hankali. Invigilator ne ya fita, hakan ya bawa sauran ɗaliban ajin, damar cigaba da taimakawa junansu, tuni Fadila ta manta ta matsa kusa da Yazeed tana wanke takardarsa, jin jikinta ya fara rawa ne ya sanya ta lura tana kusa da shi, dan haka da sauri ta ja da baya, tana sauke numfashi. Kallonta yayi yai murmushi ya ce "Kin gama ne kika matsa?" "Ban gama ba" ta faɗa a raunane. "To ƙarasa mana, zan tashi in kai fa". "To ka karanto mini mana" "Ki kwafa mana ni na gaji" ya faɗa yana jin daɗin yanayin. A hankali ta kuma matsawa kaɗan ta cigaba da kwafa, amma tuni gumi ya fara yankomata, tana rubutu hannunta na rawa. "Ki nutsu mana, lokaci ya kusa ƙurewa kuma sai rawar jiki ki ke, kin kasa rubutun" da ƙyar Fadila ta ƙarasa saboda gaba ɗaya bata iya tantance yanayin da take shiga idan tana kusa da shi, idan yana nesa da ita ne take iya tatala masa rashin mutunci son ranta, amma da sun samu kusanci sai ta rasa nutsuwarta, sai da ta gama sannan Yazeed yaje yayi submitting. Ajiyar zuciya ta dinga saukewa a jere, saboda yadda ta sha da ƙyar, bayan ta fito ta hango Yazeed a wurin motarta yana waya, da 'yar ƙaramar wayarsa, ya jingina da jikin motar dan haka ba halin ta buɗe motar. Tsayawa tayi ya kammala wayar, tana ta tunani a zuciyarta, godiya zata yi masa ko kawai ta share shi? Ya juya harshe sai zuba larabci yake a waya tamkar bai taɓa jin hausa ba, abin ya ƙara bata mamaki, abubuwa da yawa suna bata Mamaki game da Yazeed. Ya kammala wayar sannan ya waiwayo ya ce "Am sorry na tsayar da ke". "Never mind" ta faɗa a sanyaye. "Za muyi karatu ne ko yau ma tafiya za ayi?" Yayi Maganar yana tsareta da idanunsa. "Ni yunwa nake ji, kuma na gaji sosai". انت جميل ياحببتي Ya faɗa yana lumshe idanunsa. Kallonsa ta yi dan bata gane me yake nufi ba. "Yunwa ki ke ji, kuma ke kin gaji, kar ki nuna kin san Yazeed gobe in Allah y kaimu a exam hall". "Eh ai nima ba daƙiƙiya ba ce, yau ɗin ma dai kawai na kakare ne" tai maganar cikin tsiwa tana masa kallon up and down. "Ni a ina nace miki daƙiƙiya ukhti? kalen faɗa ne dai kike yi, kuma ba zaki yi dani ba, aje gida a ci Abinci lafiya". Ɗan taɓe baki tayi, ta hau motarta ta kunna ta ja ta bar wurin. Ƙarfe goma na safe, Su Khalil suka je suka ɗauko su Mama, Khalil sai kallon Hafsa yake yi, amma tun da ta gaishe shi bata sake ce masa uffan ba, sai hira da suke da Mama jefi jefi. Goma da rabi suna station ɗin da aka karɓo Hafsa, suka isa wurin, DPO sai haba haba yake da su, har da yiwa Hafsa wasa, wai "Hajiya Hafsa babu gaisuwa ne?" Wata uwar harara ta watsa masa ta kauda kanta. Suna nan zaune sai ga Najeeb ya ƙaraso da shi da wasu matasa guda biyu. Mama na ganinsa ta haɗe rai, taƙi ko kallon in da yake, ya shigo yana ɗingisa ƙafa. Shima wani banzan kallo ya yiwa su Hafsan sannan ya ƙarasa ciki ya zauna, suka gaisa da DPO ya maida idonsa kan Khalil da Abdul dake wurin, yana mamakin su kuma wannan daga ina?. DPO ya ce "Yauwa Najeeb, ga wanda suka zo suka yi belin Hafsat a jiya, dama na gayyace ku ne gaba ɗaya a zo a zauna a teburin sulhu, tun da dai shi sulhu alkhairi ne". "Kamar yaya aka bada ita beli, haba DPO haka muka yi da kai? Yarinyar da ta nemi ta halakani". "Dama kai ne kasa aka kamata? Har kake iƙrarin dan me aka bada belinta?, kai ko kunya baka ji, wannan ce zata halaka ka garjejen ƙato da kai?" Khalil yayi Maganar yana zaro ido. Najib ya ce "Kai kuma awa? Me ya kawo ka cikin wannan case ɗin, abu ne na family issues 'yar uwata ce ina ruwanka?". "Wallahi ni ba ɗan uwan bane, babu wata alaƙa tsakani da shi, dan Allah Yallaɓai ka mini tsakani da shi kar ya sake zuwa in da nake, ba ruwanshi dani, dan Allah" Hafsa tayi maganar tana kuka. DPO ya ce "Wai dama ka santa ne?" Ya  tambayi Najib. "Yallaɓai 'yar uwata ce, wani misunderstanding ne kawai ya gifta ake samun wannan akasin" Duk da sanyin hali irin na Mama, amma nan da nan fuskarta ta sauya, ta ce "Kar ka ƙara danganta kanka da 'yata, baku da wata alaƙa da mu". Najib ya ce "Ai dama ba dake na ce ba, bani da wata alaƙa da ke, amma ina da ita da Hafsa". "Shut up malam" Khalil yayi masa tsawa. "Wallahi kai mana rashin hankali a nan, sai na saka an samaka sarƙa, mahaukaci kawai". DPO ya ce "Dan Allah ya isa haka, wannan hayaniyar duk ba mafita bace. Ke Hafsa meye haɗinki da shi, da har kika ƙona shi?". Hafsa ta share hawaye ta ce "Karo kusan uku kenan, yana zuwa wurin sana'ata yana ci mini mutunci yana zagina a gaban mutane, ni kuma na gaji na rasa yadda zan yi kawai na zuba masa mai a ƙafa, kuma ina da shedu a gaban mutane yake zuwa kaina yana ci mini mutunci". "Amma me yasa baki yi wannan bayanin jiya ba, da muka tambayeki?". Khalil ya ce "Amma duk ba kuyi wannan binciken ba, kuke iƙrarin zaku kaisu kotu, anya makuwa ka san aikinka?" DPO ya ce "Wannan abu dai duk kuskure ne an riga anyi shi, saboda shi abin da ya zo ya gaya mana daban, ita kuma taƙi Magana, amma insha Allah yanzu za a rufe case komai ya wuce". "Eh, a rufe case amma ba komai zai wuce ba, idan aka rufe wannan case ɗin ni kuma zan shigar da ƙararsa a kan cin mutuncin da yayi mata, kuma Wallahi CID zan kai shi, ba dai abun wa ka sani wa ya sanka bane? Zan masa abinda ya yi". Abokan Najib da suka rako shi wanda ba suyi magana ba tunda suka zo, ɗaya daga cikin su ya ce "Dan Allah dai kayi haƙuri komai ya wuce, kuskure ne an yi, ayi haƙuri". "Dalla rufe mini baki, waye ya sa da kaiz' ba dai kuna ƙaryar rashin mutunci ba, kawai ya sa aka kama yarinya aka rufe, bayan laifinsa ne, ba zaku bar nan wurin ba zan waya azo a tafi da shi, koma a haɗa da ku duka" yayi Maganar yana zaro wayarsa daga aljihu, aka dinga bawa Khalil haƙuri,ƙarshe sai da Mama ta saka baki ta ce "Bakomai Khalil, wannan taimakon da ka yi mana ma mun gode, bana son wani abu ya sake shiga tsakaninsa da 'ya ta, kawai ka sa a musu iyaka, kar ya kuma zuwa wurin da take". Da ƙyar Khalil ya haƙura aka rufe case ɗin nan, dan sai da Abdallah shima ya saka baki, sannan aka rufe case ɗin, suka ɗau su Hafsa a mota suka tafi mayar da su gida. Najib kuwa mamaki ya dinga yi, waye Khalil a ina su Hafsa suka samo wanda ya tsaya musu haka? A iya saninsa basu da kowa basu da Komai, amma ya akai Khalil ya shigo rayuwarsu, ya so ya kuma amfani da damrsa ya wulaƙanta Hafsa son ransa, daga ita har Mama, amma ya lura wannan Khalil ɗin yafi shi zafin kai da masu gidan rana, idan ya matsa shi ne zai kwana a ciki. Khalil ya so yaji alaƙar dake tsakanin su Mama da Najib, amma ganin kamar basa son zancen ya sanya shi yin shiru. Yau ma har gida suka kai su Hafsa, Mama nata musu godiya da sa albarka, Mama ta nufi gida, Hafsa ma ta biyo ta. Mama ta kalli Hafsa ta ce "Ke wace irin Yarinya ce mara lissafi? Har a miki wannan abin Arziƙi amma ba zaki tsaya ki sake masa godiya ba? Maza koma kije ki kuma yi masa godiya". Cikin sanyin jiki ta koma inda su Khalil ke ƙoƙarin tafiya, taje ta tsaya ba tare da ta ce uffan ba. Khalil ya sauke glashin motar, ya kalleta ya ce "In zo ne?" Ta jinjina masa kai alamar eh. Ya buɗe motar ya fito, ya tsaya a gabanta ya ce "Gani ranki ya daɗe". Ta ɗan yi turus, Sannan ta ce "Dama, ce maka za yi Na gode sosai da taimakon da kayi mini, Allah ya saka da alkhairi". Khalil ya yi murmushi ya ce "Meye abin godiya, dan mutum ya yiwa matarsa abin daya dace?" Da sauri ta ɗago ta waro masa manyan idanunta. "Kin san wani abu Hafsat?" Ta girgiza kai. "Ina kishinki da yawa, bana son zaman da kike a titin nan, dan Allah ni dai ki daina". "Idan ban zauna a titi na yi sana'a ba, da me zamu rayu?". "Ba zai gagara ba Hafsa, ni dai dan Allah ki daina, kuma very soon nake son ayi zancen aurenmu". "Na gode sosai da taimakon da ka mini, amma ni ba zan aureka ba, ka ƙyaleni a yadda ka ganni kawai" "Amma Hafsa saboda me?" Ƙwalla ta taru a idanunta ta ce "Dan Allah kar kayi amfani da damar ka taimakeni ka turasasa mini yin abin da bani da ra'ayi a kansa, dan Allah ka ƙyaleni". "Hafsa ba kya tausayina ko? Kin san so kuwa? Saboda ke fa na baro aikina na taho, kawai dan na ganki, meyasa ba zaki dubeni ba. Ko ina da wani aibu ne ban sani ba?". "A'a, baka da wani aibu ni dai kawai ka rabu da ni". "Shikenan tunda haka kike so, jibi in Allah ya kaimu zan koma, zan zo muyi sallama, ina sonki sosai Hafsat. Kalmar ina sonki, ta daki Hafsa sosai, dan har cikin kwayarta taji tasirin kalmar, amma ba ta jin zata iya yadda da soyayya balle tayi aure, gara su cigaba da lallaɓa rayuwa ita da Mama. Khalil bai taɓa zaton akwai ranar da zata zo, ya dinga 'yar talakawa kamar Hafsa yana neman soyayyarta tana gara shi ba. Aminatun Baba Hassan kuwa, ta ƙara kilewa sosai da sosai, tayi sababbin ƙawaye, gashi nan da nan ta zama sananniya a makarantar saboda ƙoƙarinta da kuma surutunta, suna ta shirye shiryen fara jarrabawar zango na farko. Amina ta mayar da hankali wurin tattalin haddar Alqur'aninta bata zube ba, dan tana yawan tilawa kuma ta cigaba da rubutun alƙur'ani tana sake gyara kura kuranta,ta ɗora haddarta tana samun masu duba mata a makarantar. Hajara ce a sashen Mummy, tana ta aikace aikace, Hajiya Zainab ta fito ta tarar da ita a falonta, ta kalli Hajara ta ce "kira mini 'yar mai gadin nan" Hajara ta ce to, ta tafi kitchen ta kirawo Amina. Suka dawo tare. Hajiya Zainab ta kalli Amina ta ce "Muje sashen maigidan na nake so a gyara a yiwa kwalema, gobe in Allah ya kaimu zai dawo". Amina ta ce "To, amma na ɗora girkin rana". "Bar shi ita ta ƙarsa, muje in buɗe miki wurin" Amina tabi bayan Hajiya Zainab, zuwa sashen da take kyautata zaton shi ne na Alhaji Ahmad. Masha Allah, yafi ko ina kyau da tsaruwa a gidan, duk ya yi ƙura amma hakan bai hana sashin yin kyau ba, duba da kayan alatun da aka ƙawata wurin da shi. "Gashi nan, ki gyara duk abin da yakamata, karki mink rawar kai ko kiyi abin da ban saki ba, ki gama aikin da na saki ki fito". Amina ta ce "To insha Allah". Bedroom kawai guda biyu ne a sashen, kowanne ya sha furnitures na alfarma. Falon kawai gari ne guda, dan set ɗin kujeru biyu ne a falon. Amina mamaki ta dinga yi, duk wannan aljannar duniya, amma ace mutum sai ya bar gida har wurin watanni uku ba nan, yana wata uwa duniya ta daban. Amina haka ta dinga tular uban aiki, da tana ganin kamar aikin babu yawa, amma da ta fara taga aikin nayi ne, haka ta zage, wanke wannan goge wancan, karkaɗe can haka ta kusa wuni tana fama, sai dai idan za tayi salla ta ajiye aikin taje tayi. Sai da ko ina ya zama tsaf ta gyara, sannan ta koma da baya, tana ƙarewa ko ina kallo, ta tabbatar komai ya gyaru tsaf, hankalinta ya sauka a kan katafariyar plsma tv wadda ta kusa cin rabin bango, tunani ta fara yi a ranta, ko a cikin wannan tv mutane sunfi girma a kan sauran ƙanan tv. Take zuciyarta ta raya mata ta kunna taga ya zata ga mutanen cikin. Aikuwa Amina ta ƙarasa, ta kunna Tv da fari sai da ta rage yadda ta ware idanunta, saboda hasake da kuma yadda taga mutane sun bayyana a tv, kamar ta zura hannu ta ɗauko su. A hankali ta buɗe idon, ta cigaba da kallon mutanen tv, shaf ta manta da a ina take, ta samu wuri ta zauna a kan kujera, tana cigaba da kallon Tv. Sai ga Amina ta bararraje ta shantake, ta cigaba da kallo abinta hankali kwance. "Ke ubawa ya baki izinin zama a kan kujerar nan? Lallai ne gidan ubanki ne nan ɗin?" A tsorace Amina ta waiwaya ta kalli in da Hajiya Zainab ke tsaye tana nunata da yatsa. Da sauri Amina ta tashi tsaye, tana rarraba ido. "Waye ya ce ki zauna a falon mijina, har ki harɗe ƙafa kina kallo, nawa ne a ciki kuɗin babanki da aka haɗa aka gina ɗakin aka zuba furnitures ɗin?" Babu babban abin da ke ƙular da Amina irin da tayi laifi, sai a fara ambaton Baba ana ci masa zarafi. Amina tayi shiru tare da sunkunyar da kai, tana jin yadda sautin maganganun Hajiya Zainab ke amsa kuwwa a cikin kunnuwanta, suna sukar zuciyarta. Maganganun Baba ta tuna, da yake nanata mata ba yau ba gobe a kan tayi haƙuri, dan ta samu ta kammala karatun ta lafiya, hakan ya saka nutsuwa da haƙuri ya shigeta, a sanyaye ta ce "Dan Allah kiyi haƙuri, insha Allah ba zan sake ba". "Ki ma sake, munafuka sai kin yi rashin mutunci ki koma kina wani kwantar da kai, ni zan fita Yanzu, ki zo ki wuce ki bar sashen nan, idan na fita daga ke sai halinki a gidan, idan kin ga dama, ki kuma aikata wani rashin mutuncin, sai kin koma in da ki ka fito" Amina dai ba tace uffan ba, sumi-sumi ta bar falon, ƙasan zuciyarta kamar ta ƙundumawa Hajiya Zainab ashariya, dan ɓacin rai. Ɗakinta ta koma kawai ta fashe da kuka, dan ta samu sassauci daga zafin da maganganun Hajiya Zainab ke mata a zuciyarta, gaba ɗaya zaman gidan ya sire mata, sai da tayi ta gaji, sannan ta wanke fuskarta ta fito, tana fitowa babban falon gidan ta ci karo da wasu manyan mata, kai da ka gansu kaga gogaggun 'yan duniya, sun sha ado sai baza ƙamshi suke. Ɗaya ta kalli Amina ta ce "Ashe da mutane a gidan, muke ta kwaɗa sallama amma shiru". Amina ta ce "Eh da mutane, amma masu gidan basa nan". "Tayi nisa ne?" Suka tambayeta. Amina ta ce "Ai da yake ni ɗin ba 'yar ta bace, balle in san in da ta tafi, bata gaya mini ba sai dai ku kirata a waya" "Ikon Allah, ke baki iya magana bane?" Amina tai shiru ba tace komai ba, suka sami wuri a kan kujera suka zauna, Amina ta kalli ƙafar ɗaya daga cikin su, fuskarta fara tas ta sha mai, amma ƙafarta kamar ta ƙone ga ƙafar ta ta kamar ta maza, ga taƙi ɗaukar bleaching ɗin. A zuciyarta ta ce "Ikon Allah, wata ƙatuwar ƙafa kamar ta Jarmai". "Ke ɗan bamu ruwa, ƙishirwa ta dameni". Amina ta koma ciki ta ɗoro pure water biyu a plate ta kawo ta ajiye musu. "Hajiya Sarah, yau nake ganin ikon Allah, wace irin 'yar aiki Zainab ta samo haka bagidajiya, ke mun miki kama da wanda zasu sha wannan ruwan? Babu na roba?". "Ai gidan nan baƙi ba su da hurumin shan ruwan roba, na leda kawai aka ce in bayar guda ɗaya" tayi maganar tana ɗan hura hanci, alama matan sun fara takurata. Nan suka cigaba da hirarsu da 'yan zage-zagensu, Amina kuwa ta bar musu falon. Kusan Mintuna talatin Amina ta kuma fitowa da niyyar idan sun tafi, ta gyara falon amma ta tarar da su basu da niyyar tafiya, sai ma ƙure tv da suka yi suna kallo. Ba tunanin komai ta wuce ta kashe socket ɗin tv gaba ɗaya. "Ke lafiya, meye haka?" Cewar Hajiya Turai. "Ai ba wuta solar ce, kuma ta fara ƙara a kowane lokaci zata iya ɗaukewa, mai siyo fetur kuma baya nan, dan haka idan ta ɗauke ni za a saka zuwa sayen fetur ni ba namiji ba, kinga ai gara in kashe ai reserving solar". "Ke wai ke meye matsayinki a gidan nan ne?". " 'yar aiki" ta faɗa kanta tsaye. "Kin san mu suwaye da kike mana wannan iskancin?". "A'a Anty, ba laifina bane dokar matar gidance a haka". Hajiya Sarah ta ce "To bari Zainab ɗin ta dawo muji daga bakinta" Komawa kitchen Amina tayi, a ranta tana ƙunƙuni. Sai daf da magariba sannan Hajiya Zainab ta dawo gidan, ko da ta shigo falo ta tarar da su Hajiya Turai, suka sanya wata uwar shewa. "Hajiya Turai yaushe ki ka shigo ƙasar nan?" Hajiya Zainab tayi maganar tana ƙoƙarin zama, cike da mamakin da ya mamaye fuskarta. Turai ta ce "Sati na ɗaya, nace bari nayi miki zuwan bazata". "Amma Sarah meyasa baku gaya mini zaku zo ba? Ai da ban fita ba. Hajiya Turai mutanen Saudiyya" Nan suka ɓarke da hirar yaushe gamo. "Kun ci abinci kuwa?". "Wane Abinci, ke dai a garin yayime yayimenki sai kin yayi mo mai zane ki, wata tsigalalliyar yarinya muka tarar marar mutunci, ko ruwa hanamu tayi sai pure water ta bamu". Hajiya Zainab ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, wannan Yarinyar ta zame mini jaraba, tun da tazo gidan nan nake fama da ita". "To ki sallameta mana" Hajiya Sarah ta faɗa tana yatsuna fuska. "Yarinyar ce tunda nake masu aiki, ban taɓa samun 'yar aiki mara son jiki kamarta ba, ba ta jin jikinta wurin aiki, ba ta da ƙyuya ba munafunci, sai iya shege da rashin mutunci a cikinta. Sai naji kamar in koreta amma sai in tuna irin aikin da take mini in ƙyaleta". "Ai irin haka warning zaki kasa mata, koma ki bata suspension, Yarinyar bata da kunya sam". Rai a ɓace Hajiya Zainab ta dinga ƙwalawa Amina kira, ita sam Amina ma bata san ta dawo ba, ƙasa-ƙasa take jiyo kiran, ta fito falon tana sussunkuyar da kai kamar mara gaskiya. "Ke shine nayi baƙi kika wulaƙanta su, ki ka basu ruwan leda dan baki da mutunci?" "Hajiya kefa kika ce kar in sake bawa duk wani baƙo ruwan roba balle Abinci sai pure water, shiyasa na basu". "Kuma dan baki da hankali wannan sun miki kam da waɗancan ne? Ƙawayena ne wannan tun na ƙuruciya saboda baki da mutunci sai ki wulaƙanta su? Ke nifa na gaji da wannan iskancin naki, bari shi me gidan ya dawo, ki koma ƙauye ki cigaba da shan baƙar kuka. Kin zo birni kin sha miya zaki miƙe ƙafa kina mini iskanci" ta sunkuyar da kai tayi shiru ba ta ce uffan ba, suka haɗu su uku suka mata wankin babban bargo. Tun abin na damun Amina, ta fara daina jin komai, ta fuskanci kamar ɗabi'a ce ta masu kuɗi, wulaƙanta wanda suke ƙarƙashin su, suka ƙare mata zagi da cin mutunci tsaf, sannan suka sallameta. Harabar gidan ta koma, tayi zamanta ya yin da Baba yake bakin gate yana aikinsa. Abdul da Khalil ne zaune a ɗakin Abdul, Khalil ya zuba uban tagumi. Abdul ya ce "Wai kai Khalil meye haka ne? Sai ka sanya damuwa a ranka ka kasa sukuni?". "Abdul ba zaka gane bane, ni kaina ban taɓa zaton abubuwa zasu cakuɗe mini haka ba. Baka san yadda nake jin yarinyar nan a raina ba, amma naga tana da taurin kai, babu alamar zan sameta na karaya Abdul". "Haba Khalil, kar ka karaya, ka san meye matsalarka? Garaje da gaggawa idan kabi komai a sannu zai zo maka a sauƙaƙe, yanzu kana jin abin da nake ji game da ƙanwarka ko? Hmm haka al'amarin so yake, na san babban yaro kamarka da mata ke rushing a kansa, abin mamaki ne ace ya maƙalewa 'yar talakawa kamar wannan, amma haka sha'anin so yake. A yanayin Hafsa kamar akwai wani ɓoyayyen abu da yake damunta a zuciyarta, dan haka domin shawo kanta, sai ka rage shishige mata, da cigaba da nuna mata soyayya, ka danne son kawai ka nemi ku saba da ita. Ka dinga kyautata mata da kulawa ka fara gano meye matsalarta kan ka cigaba da nuna mata soyayya". Khalil ya ɗan yi shiru sannn ya ce "Kana ganin hakan mafita ne?. "Ita ce babbar mafita, tunda soyayyar ce ba ta so, to ka bar shi a friendship ka gama fuskantar ta tukuna". "Shikenan, zan jarraba hakan, insha Allah gobe in Allah ya kaimu zan koma wurin aiki, zan jarraba shawarar taka". "Wai da gaske ba zaka gida ba?" "Abdul idan naje Mummy tuhumata za tayi a kan dalilin dawowata, ba sai naje ba, sai nan da kamar 3weeks zan kuma dawowa insha Allah" "To shikenan, Allah ya kaimu sannan ya daidaita ku". Yau sai shida na yamma suka kammala jarrabawar yau, kanta har wani juyawa yake yi saboda ta gaji yau sosai da sosai, da ƙyar take iya ɗaga ƙafafuwanta, saboda zaman ajin. Jarrabawowin yau Alhamdilillah tayi abin Arziƙi da kanta, dan tayi karatu sosai da sosai. "Hmmm Madam, glucose yayi ƙasa ne naga kina tafiya da ƙyar?" Cak ta tsaya tana ɗan sauke numfashi, ta waiwayo ta sauke masa gajiyayyun idanuwanta da suka ɗan yi ja saboda gajiya. "Yau ko nemana ba ayi, tun shekaranjiya ko kallon in da nake ba balle a harareni. Amma ina fatan kin gama komai dai ko?". "Ban gama ba, jira nake kazo ka ƙarasa mini" Sauke facemask ɗinsa ya yi ya ce "Me kika ce?". "Ban sani ba" ta faɗa ba tare da ta kalleshi ba. "Kalleni ki faɗa mana idan ba tsoro ba" ɗagowa tayi ta kalli Yazeed, sai dai tayi saurin janye idonta daga nasa. "Dan Allah ka rabu dani". "Muje in rakaki wurin motar". "Ina da ƙafa ai" ta faɗa tana cigaba da tafiya sannu a hankali. "Ai ƙafar taki ce kamar ta gaji, da ƙyar kike tafiya, ko in ɗauke ki in kai ki motar ne?" Ɗagowa tayi ta kalleshi ta mayar da hankali a kan tafiyarta. Yusra ce ta tunkaro in da suke tana murmushi, ta kalli Yazeed ta ce "Patient ɗinmu, kai ne ka warware haka?" Yazeed ya yi murmushi ya ce "Alhamdilillah, jiki ya ware". "Haka ake fata dama, madam zuwa nayi mu tafi gida tare, yau ba mota a hannuna". Fadila ta ce "Gaskiya a gajiye nake gida zan tafi sai dai in ajiye ki a hanya". "Aikuwa baki isa ba, nima a gajiyen nake, ka sa baki ta kaini gida mana" Yusra tayi maganar tana kallon Yazeed. Yazeed ya ce "Wane ni, ku gaida gida". "A'a ka tsaya, saita ɗaukemu wallahi, muje ko rage maka hanya muyi". "A'a ba zan hau ba, Allah ya kai ku lafiya". Yusra ta ce "Dan Allah ka zo muje, ko a hanya mu ajiye ka". "A'a ni ba zan hau ba, wa zai hau motarta, ko tuƙinma bata iya ba, ta watsar da mu a hanya, ku sauka lafiya" kallon Yazeed tayi, tama rasa me za ta ce masa. Fadila na ƙoƙarin kunna mota ne, Yusra ta ce "Wallahi Fadila kun dace da gayen nan, anya ba sonki yake ba?" "Amma baki da hankali ko? Ke na miki kalar sa, karki ɓata mini rai". "Wallahi Fadila ni tausayi yake bani gaba ɗayansa, Wallahi kamar sonki yake" Fadila ta haɗe rai ta ce "Yusra bana so, karki sake haɗani da shi" "Ai shikenan, bari mu zuba ido mu sha kallo". Wani irin horn Fadila take yi a ƙofar gidan tamkar zata daki gini idan ba a buɗe ba, Baba kuma ya shiga banɗaki a lokacin, ba tare da ya kammala abin da yake ba, ya fito bagatatan ya buɗe mata gate ɗin, ai ko kashe motar ba tayi ba, ta fito ta hau Baba da bala'i ta in da ta shiga bata nan take fita ba, ya risuna ya dinga bata haƙuri. Haka ta nufi cikin gida fuuu kamar guguwa, ba ta tsaya ta saurari Mummy tana da baƙi ba ta hau bala'i a falon "Gaskiya Mummy ku sallami wannan tsohon, haba ai ko aikin gwamnati ne ha kai yayi retire mutum sai bai san aikinsa ba, ya bar mutane a waje ina ta faman horn sai kace wani kurma, gaskiya na gaji a sallame shi. Ga securites nan na kamfani Daddy ya ɗauko amma ya dage a kan wannan baƙauyen, mara kuzari, saura kaɗan in zage shi yau". Jikin Amina ne ya ɗau rawa, ta kalli Fadila ta ce "Baban nawa zaki zaga?". DOMIN GYARA SHARHI KO SHAWARA 08081012143READ THE CHAPTER 16 OF GABA DA GABANTA AT AREWABOOKS https://arewabooks.com/chapter?id=638b441e942c7e82ce7bfb71 GABA DA GABANTA AISHA ADAM (AYSHERCOOL) To get the latest update of the story Follow me on Watpad Ayshercool 7724 Arewabooks Ayshercool 7724 What's app 08081012143 P16 "Eh, shi zan zaga ko akwai abin da zaki iya yi a kai?" Fadila tayi maganar cikin isa da iko. Maganganun Baba ne suka dawowa Amina a cikin kunnuwanta, tabbas idan ta ɗau mataki, ta san dole ta koma ƙauye, kuma babu abin da zai hana aurenta da Jarmai, jikinta na rawa hawaye na zuba daga idanunta, ta juya ta koma jikinta a sanyaye, Allah kar nuna mini ranar da za'a zagi Baba a gabana, ba zan iya jurewa ba. Fadila ba ta kalli baƙin Mummy ba, ta wuce ɗakinta tana cigaba da huci kamar wata mesa. Hajiya Turai ta ce "Wai dama 'yar mai gadinku ce?" Mummy ta ce "Eh, 'yar sa ce". "Lallai ne, ai gara da Fadila tayi mata hakan, yaran nan idan ana saurara musu miƙe ƙafa suke yi su yi ta iskanci kamar a gidan ubansu" Hajiya Zainab ta ce "Wallahi kuwa, ai Fadilan ce dai-dai da su". Fadila kuwa a gajiye ta ƙarasa ɗakinta, ta jefar da mayafinta, ta tuɓe doguwar rigar jikinta, ta shiga cikin banɗaki, ta haɗa ruwa mai ɗumi tayi wanka, ta yo alwala ta fito, sallar magariba ta gabatar ta idar, sannan ta shirya kanta cikin riga da skirt, na English wears ta fito. Sai a wannan karon sannan ta gaida baƙin Mummy, ta wuce kitchen. Amina ta gani a tsaye idanunta sun yi jawur, kamar ta kwana ta wuni tana kuka. "What do you cook for dinner?" Fadila ta tambaya cikin ko in kula. Zuciyar Amina na tafasa, tamkar ta ce mata ubanki na dafa, amma ta dann ta ce "Tuwon semovita". "Ban ci Abincin rana ba, dan haka ba zan ci tuwo ba, ki dafa mini cous cous vagetable cou cous da irish, ki hanzarta kuma" tana gama maganar ta jiya ta fice. Muciya Amina ta rarumo, ta ɗaga sama kamar ta bi bayan Fadila, ta sauke mata wannan dogayen kafaɗun nata, masu kama da dirakun firamaren garinsu.   Amina tana kuka tana yiwa Hajiya Zainab Allah ya isa, ta yiwa Fadila girkin nan ta kai mata, ta koma ɗakinta. "Hafsa ni dai ina tsoron sake komawarki wurin sana'ar nan, bana son wannan yaron ya zo ya kuma ɗaga mana hankali". "Mama idan ba wannan sana'ar ba wacce za muyi? Idan a gida nace zan cigaba da saida awarar nan, ya zama mu uku muke awara a layin nan fa, kusan duk wata sana'a da zamu yi, a na yinta a cikin unguwar nan, zama haka ba zai yiwu ba Mama". "Haka ne, amma dama can sana'ar nan ba sonta nake ba, bana ƙaunar zaman titin nan da kike yi, ni ban san ma yadda aka yi yaron nan ya san inda kike sana'a ba". "Mama ba zai ƙara zuwa ba insha Allah, kuma kinga ai Khalil ya sa an mana tsakani da shi". Mama ta ce "Ni kuwa naga kwana biyu ko kiranki ba ya yi a waya, ko wani abun ki ka yi masa ne?" Hafsa ta ɗan yi jimm, sannan ta ce "A'a babu abin da nayi masa". "Ai maganrki ba abar yadda ba ce wasu lokutan, bana raba ɗaya biyu wani abun ki ka yi masa, ai shikenan kan ki kika yiwa, sai muyi ta jerawa a gida, 'yan unguwa suna mana ƙazafi, Da kin amince wa yaron nan, na tabattar zai riƙe mini ke amana, yaro mai rufin asiri kamar wannan, ya liƙe miki alhalin ke ba kowa ba, ai kuwa Wannan son shine na gaskiya".   Gaba ɗaya jikin Hafsa ya yi sanyi, ta tuna maganganun da ta gayawa Khalil, kan ya tafi duk da abin arziƙin  da yayi mata, wanda ba dan shi ba, da bata san iya wulaƙancin da Najib zai yi mata ba. Ko ya dai na sona ne, tunda ya daɗe haka bai kirani ba? Ta tambayi kanta. 'gara ma ya haƙura ya daina sona, dan ba zai iya aurena ba' ta sake bawa kanta amsa.   Khalil kuwa daurewa kawai yake yi, amma zuciyarsa na raya masa ya kira Hafsa yaji lafiyarta, kar yaje wani abun ya sake samunta, amma idan ya tuna da shawarwarin Abdul, sai ya haƙura da kiran nata. Har washegari Amina bata sake ba, tana jin ɗacin abin da aka yi mata a zuciyarta, sai da taje makaranta ne ma, ta ɗan haɗu da ƙawayenta shine ta ɗan sake, amma cikin zuciyarta babu daɗi sam. SHANONO. Can garin su Amina kuwa, facalolinta matan su Bala, suka sakota gaba, da zagi da kums habaice habaice, tare da yiwa Innon fatan masifu daban daban, a kanta da kuma Amina da Baba Hassan. In anjima suma su Lawan ɗin da kansu suke zuwa su isketa suyi mata bala'i, suka tattara wani tsohon keken Baba na hawa suka sayar, suka harhaɗa dan biyan Jarmai kuɗinsa, saboda yadda ya sako su a gaba, da fitina da cin mutunci, abu har gaban mai gari ana musu sulhu. Ƙauye dama tuni ya ɗauka, batun guduwar Amina birni, dan tayi karatun boko, mutan ƙauyen nan suka dinga Allah wadai da abin da Amina da babanta suka aikata. Yau su Fadila suka kammala jarrabawar wannan zangon karatun, ji take kamar gama makarantar tayi, saboda yadda duk jarrabawar ta takurata. Sir Abdulmaleek Kankia, wanda suke kira da Sir Kankia, ya zo wucewa ya kalli Fadila da ke tsaye, tana ƙoƙarin kiran waya cikin nishaɗi. "Fadila Ahmad Dutse" ya kira sunanta. Ta ɗaga kai ta kalleshi, shi ne lecturer da ya so ya kori Yazeed a kan littafi ranar, zuba masa ido tayi ba tare da ta ce komai ba. "Ko ba sunanki bane?". "Suna na ne mana" "In ba zaki damu ba, ina son ganinki a office ɗina". "For what?" Tayi maganar tana kallonsa. "For something very important to discuss" "Ka faɗa mini a nan mana, meye sai na bika Office?" "Abu ne da ya shafi jarrabawar ki". "Jarrabawata kuma?" Ta faɗa da mamaki. Ba tsammani ta ɗaga kai, ta hango Yazeed ya zuba mata idanunsa, ta rasa wani irin kallo ne, na tuhuma ne, ko kuma na menene ta kasa ganewa. Bayan sir Kankiya tabi da kallo, a hankali kuma ta ja jiki ta nufi wurin da Yazeed yake tsaye ya ƙureta da ido. "Fadila meya ke ce miki ya tsare ki haka? Fadila ta tsuke fuska ta ce "Meye na tuhumata kuma ina ruwanka?". "Da ruwana Fadila, ki gaya mini dan Allah". Ta ce "Cewa yayi wai in je, a kan wani abu ne da ya shafi jarrabawata". "Meya faru da jarrabawarki?". "Nima ban sani ba, ko dan mun yi iri ɗaya ne da kai" tayi maganar cikin sanyin jiki. "Ai ba jarrabawarsa ce muka yi iri ɗaya ba, amma kije kiji mai zai ce". "Am scared gaskiya" ta faɗa da rauni. "Meye abin tsoro kuma babbar yarinya, ai babu damuwa ina jiranki, kije ki dawo" Fadila duk tunaninta a kan jarrabawar su ne, haka ta nufi hanyar da zata tafi office ɗin Sir Kankiya. Ƙwanƙwasa ƙofar Office ɗin yayi, "Yes come in" A hankali ta tura ƙofar Office ɗin, ta shiga. Tun da ta shiga ya zuba mata ido, har ta ƙarasa cikin Office ɗin. Haushi ne ya kama Fadila, saboda ta tsani kallo a rayuwarta. Zuwa tayi ta tsaya tana kallonsa ta ce "Gani" Kankiya ya yi murmushi ya ce "Zauna mana". Ta ɗan hura hanci, ta ja kujera ta zauna, tare da basar da Kankiya. "Fadila Ahmad Dutse" ya kira sunanta. Ta ɗago fararen idanunta ta kalli Sir Kankiya. "Ke 'yar garin Dutse ce?" Ya tambayeta yana kallonta. "Babana ne ɗan garin" ta bashi amsa a daƙile. "Garin babanku ai garinku ne". "Sir dan Allah meyasa ka kirani? Meya faru da jarrabawata?". Sir Kankiya ya ce "Eh to, ba wani abu bane na damuwa da tashin hankali, akwai yiwuwar komai zai daidaita, amma ki rubuta mini lambar wayarki". "Me yasa zan bada lambar wayata?" "Saboda idan da buƙatar sake neman ki sai in neme ki kai tsaye" "To ai ni har yanzu ban san meya faru da jarrabawar tawa ba". "Zaki sani nan gaba kaɗan, ki rubuta mini lambar wayarki" ba tunanin komai, Fadila ta rubuta masa lambarta, sannan ta tashi ta fice daga Office ɗin. A harabar rukunin ofisoshin malaman ta tarar da Yazeed, ta kalleshi da mamaki, ta ɗauka tuni ya tafi. "Yaya aka yi? Meyafaru da jarrabawar?" Ya tamabayeta cikin ƙosawa. "Nima ban sani ba, bai gaya mini ba, sai dai karɓar lambar wayata yayi, ya ce idan akwai buƙatar a neme ni, za a kirani". Yazeed ya kalleta da mamaki ya ce "Ya karɓi lambar wayarki?" Ta jinjina masa kai alamar eh. "Hmm Mutumin nan sonki yake yi, ba wata jarrabawar ki da ta samu matsala". "What, ka san me kake cewa kuwa?" "Eh mana, think, idan wani abu ne ya faru da jarrabawarki shi ke da alhakin kiranki, You have all his attendance, kina da Attendance ɗinsa, teses ɗinsa kina da 25mrks, ga exams ɗinsa kin rubuta, meye matsalar kuma?" Ita babban abin da ya bata mamaki, ya a kayi Yazeed ya san makinta na test da kuma Attendance, ita wasu lamuran nasa ma tsoro yake bata. Gashi ya wani haƙiƙance sai masifa ya ke yi. "Idan ma sona yake ina ruwanka?" Ta faɗa cikin tsiwa. Cikin dakewa da maziya, Yazeed ya ce "Babu ruwana, Allah ya sanya Alkhairi, ya kaimu lokacin aure Mrs Kankiya". Wani mugun kallo Fadila ta yiwa Yazeed, tare da jan guntun tsaki tayi gaba. Da sauri ya sha gabanta, ya ce "Am sorry Please, yau fa zamu tafi hutu, Yakamata mu rabu lafiya ko ƙanwata?". "Ni ka ƙyaleni" tayi maganar a ɗan hasale. Zuba mata idanunsa tayi, wanda hakan ya sa taji wani abu na yawo a jikinta, da bata san menene ba. "Fadila me yasa kika tsane ni, me nayi miki, kina gani bana iya sakewa da kowa a makarantar nan, duk da ba kya ƙaunar ganina, amma ni ina jinki tamkar ƙanwata ciki ɗaya, dan Allah ki sassauta tsanar da kike mini, ko nayi miki wani laifin ne?" Shiru Fadila tayi, tana bin Yazeed da kallo, a hankali ta lumshe idanunta. "Fadila" ya kira sunanta. Ta ɗago ta kalleshi. "Me nayi miki kika tsane ni ne? Ko dan ni bagidaje ne, ban iya wanka ba, kuma ban iya turanci ba?" Ya ƙarasa Maganar yana kallonta. Gaba ɗaya jikinta yayi sanyi, ta kasa ko motsawa. "Let's be friends" Yazeed ya faɗa cikin sigar rarrashi. Ɗan tura baki tayi tana fici fici da ido, wata irin kasala na cigaba da tsirga mata, tun daga kanta har ƙafafuwanta. "Talk Fadila" ya faɗa yana marairaicewa "To wai ni me zance?" Ta faɗa tana tura baki gaba. "Be my sister" ya furta saɓanin abin da yake zuciyarsa. "Kaga, dan Allah ka bani hanya in wuce, gida zan tafi" tayi maganar a shagwaɓe. Babu tsammani, suka ga Kankiya ya ɓullo daga wajen da ofisoshin nasu suke, ya ɗan yi turus yana kallon su. Tunani Fadila ta shiga yi, da gaske mutumin nan sonta yake ya karɓi lambarta, amma da ya rainawa kansa hankali, wannan suka jero ai cewa za'a yi mai aikinta ne, wani sirirn tsaki ta ja ba tare da ta san ya fito ba.   Wucesu ya yi ba tare da ya ce musu uffan ba, duk suka bishi da kallo, har ya bar wurin. Fadila ta yi ajiyar zuciya ta ce "Kaga ni na tafi" "Ok muje, nima tafiyar zan yi" ba wanda ya kuma cewa wani uffan, kowa yana saƙawa da warwarewa a ransa. Ta buɗe motarta ta shiga, Yazeed ya kalleta ya ce "To ayi hutu lafiya, kar a ajiye litattafai a daina karantawa, i will miss you ukty" Kallon Yazeed tayi, ta ɗan yi murmushin gefen baki. Har motar Fadila ta ɓacewa ganin Yazeed, yana tsaye yana kallonta, yana jin yadda zai yi kewarta. Da yamma Amina na harabar gidan, wurin Baba, tana ta zuba masa surutu, gabanta ga littafi da biro, tana karatun jarrabawa. Horn ɗaya aka yi ƙwaƙƙwara, Baba ya miƙe jiki na rawa, yaje ya buɗe gate ɗin, Zakiru direban Alhaji Ahmad, ya silalo da hancin motar, cikin harabar gidan. Ɗan dakatawa Zakiru yayi da motar, Baba ya ƙarasa Alhaji Ahmad ya sauke glashin motar suka tsaya magana da Baba. Amina haushinsa take ji yanzu, tun da Allah ya sa 'yar sa taci wa babanta mutunci, kwasar litattafanta tayi, ta bar wurin dan karma ta gaishe shi, ta shige cikin gida, a falo Hajiya Zainab ta dakatar da ita "Ke daga ina haka nake ta nemanki?". "Ina wurin Baba ne". "Ke nifa bana son sakarci, idan baban naki kika zo yiwa aiki, sai ki koma can bakin gate wurinsa, idan ya so ya dinga biya miki kuɗin Makarantar". Fadila da ke kwance a kan doguwar kujera, ta ɗan taɓe baki tana kallon yadda Amina ta haɗe rai. Alhaji Ahmad ne ya yi sallama a falon, zumbur Fadila ta miƙe jin Muryar mahaifinta, da sauri ta ƙarasa in da yake ta rungume shi "Oyoyo Daddy". "Welcome sweetheart" yayi Maganar cike da kulawa yana sake rungume Fadila. Hajiya Zainab ta ce "Ashe ka sauka?". "Wallahi kuwa, kin ganni nan sai yanzu" Amina tabi Fadila da kallo,  Yadda ta ƙanƙame mahaifinta cikin kulawa da ƙauna. Ji tayi ina ma zata iya zagin Alhaji Ahmad, Fadila taji abin da ta ji, lokacin da taci mutuncin nata mahaifin, sai dai kash hakan ba tarbiyyar Amina bace, ko da wasan wasa ba zata iya aikata hakan ba, haka ta wuce ta bar musu falon suna cigaba da farincikin dawowarsa. Hafsa fa ta ɗan shiga damuwa, saboda rashin kiran wayarta da Khalil ya daina yi gaba ɗaya, gashi kuma ita ba zata iya kiransa a ta ta wayar ba, saboda a ganinta hakan bai dace ba. Amina ma sun fara jarrabawa a makaranta, ayyuka sun ɗan yi mata sauƙi, kasancewar yanzu Fadila bata zuwa Makaranta, ta rage tashin sassafe. Tun da Alhaji Ahmad ya dawo basu haɗu ba, har ta tafi makaranta bai fito ba, wasu lokutan baya dawowa sai dare sun kwanta. Duk kashedin da ake mata a kan zuwa wurin Baba tayi zamanta, ba ta ji ba, dan yau ma tana wurinsa suna hira, kasancewar yau Asabar, Baba yana gyara flowers ɗin harabar gidan, tana taya shi. Ƙamshin turaren Alhaji Ahmad ya cika wurin, Baba ne ya miƙe da sauri fuskarsa ɗauke da murmushi, yana yiwa Alhaji Ahmad barka da fitowa. "Ina wuni" Amina ta faɗa kamar an mata dole, dan ta san Baba zai iya yi mata faɗa idan bata gaishe shi ba. Ya waiwaya ya kalli in da Amina take "Lafiya ƙalau, ya school ɗin?". "Lafiya ƙalau". "Good" ya mayar da dubansa kan Baba ya ce "Malam Hassan ya aikin? Babu dai wata matsala ko?" Baba ya ce "Babu matsalar komai ranka ya daɗe". "To Alhamdilillah, Allah ya yi jagora". Baba ya amsa da "Ameen". Amina a ranta ta ce "Shi dai gashi nan, shima yana da wannan taƙamar, sai dai baya wulaƙanci kamar yaransa da matarsa' ta ɗan taɓe baki ta cigaba da sabgar gabanta. Fadila ce zaune a kan gadonta, tana zazzage jakarta ta Makaranta, ita kanta bata san me take nema ba, wata takarda ce mai ƙyalƙyali ta faɗo daga tsakanin litattafanta. A hankali ta miƙa hannunta ta ɗau takardar ta buɗe, rubutun larabci ne a jiki, an cika paper da rubutun larabci. Ba rubutun kowa bane face na Yazeed, tamkar inji ne ya tsara rubutun ba hannun mutum ba, ta dinga jujjuya takardar amma ba ta fahimci komai ba, sai sunansa da ya rubuta da Larabci da signing, haka nan taji tana son sanin me takardar ta ƙunsa, ƙarshe ma sai ta fara tunanin ya aka yi takardar ta shiga jakarta?. Bacci take ji sosai, dan haka ta watsa litatafan ƙasa tai kwanciyarta a kan takadar, wani nannauyan bacci ya yi awon gaba da ita. "Ukty, yau kin yi kyau fiye da koyaushe, idanunki kamar ƙara musu kyau ake masha Allah" ya faɗa yana murmushi. Haɗe rai tayi tana kauda fuskarta gefe guda, matsawa yayi jikinta Sosai yana mata magana. Jikinta ne ya hau rawa, taji tamkar ta fashe da kuka, ga wannan baƙon yanayi da yake kaiwa yana komowa a jikinta. Fuskarta duk hawaye ta kalli Yazeed "Wai ni meyasa nake jin haka idan ka masto kusa dani?". Ya ɗora kansa a kan kafaɗarta ya ce "Me kike ji?" "Nima ban sani ba" ta faɗa muryarta na rawa. Bakinsa yake ƙoƙarin sakawa a nata, amma ta fara ƙoƙarin kauda kanta, sai dai riƙon da yayi mata bana wasa bane. "Yazeed dan Allah" ta faɗa fuskarta duk hawaye, jikinta kuma na cigaba da rawa. Sai da Yazeed ya yi galaba a kanta, wurin saka bakinsa a nata. Ba zata iya misalta ko rarrabe wane yanayi haka suka wanzu a ciki ba ita da Yazeed. "Yazeed" ta faɗa da ƙarfin gaske, ta tashi daga baccin a razane, fuskarta duk hawaye, tana haki. Amina dake durƙushe tana tattare litattafan da Fadila ta zubar a ƙasa ta kwashe ta gyara ɗakin, sai da ta razana, ta saki litattafan. Ita ma ta maimaita "Yazeed kuma" Fadila sai haki take tana rarraba ido, ta kai hannu fuskarta taji hawaye. Ta kalli in da Amina ke tsaye tana binta da kallo. Ji tayi tamkar yawun Yazeed ne a bakinta, saboda bata taɓa zaton mafarki ne ba gaske ba. Da sauri ta duro daga kan gadon, ta tafi banɗaki tana zubar da yawun bakinta. Amina tabi bayanta da kallo, tana tunanin dama ana mummunan mafarki da rana tsaka haka? Kodayake in mutum baya Addu'a ba abin da ba zai sameshi ba. Haka Fadila ta dinga zubar miyau, tamkar a gaske mafarkin ya faru, har irin ƙamshin turaren da ke jikinsa, take ji a hancinta. Bata haƙura ba sai da ta sa brush ta wanke bakinta, sannan ta fito daga banɗakin. La'asar liƙis, Khalil ya shigo garin Kano, salla kawai ya tsaya yayi, kai tsaye gidansu Hafsa ya nufa. A ƙofar gida ya tsaya yana sallama, Mama ce ta leƙo da kanta, tana ganin Khalil ta fara murmushi, ya duƙa har ƙasa ya gaida ita, ta amsa masa cike da kulawa tana faɗin "Khalil kwana biyu" "Mama ayyuka ne suka yi mini yawa, kuma da yake ba a nan Kano nake aikin ba, shiyasa". "Allah sarki to Allah ya dafa, kuma gashi bata nan, tana wurin bikin wata ƙawarta" Khalil ya ce "Dama Hafsa na ƙawaye?". Mama ta ce "Kaima ka fuskanci halinta kenan, tana da su irin wanda suka yi Makaranta a baya". "To Mama ina ne wurin bikin?" Mama ta gaya masa yayi mata godiya ya tafi. Ba tsammani taga lambar Khalil yana kiranta, duk da bata yi Saving lambar ba, amma ta haddacce ta tsaf. Cikin hanzari ta ɗaga wayar, sai dai bata iya jin komai saboda hayaniya. Tashi tayi ta fita harabar wurin bikin, jikin wata mota ta tsaya, ta saka wayar a kunnenta tare da yin sallama. "Wa'alaikum salam, Baby ya kike?" Taji maganarsa a bayanta. Da sauri ta waiwaya taga Khalil a tsaye a bayanta. "Ya aka yi ka san ina nan ka zo?" Ta faɗa cikin mamaki. "Miracle" ya faɗa yana dariya. Ƙare mata kallo ya shiga yi, tana sanye da riga da skirt na atamfa, ta kashe ɗauri, hannunta ya sha lalle. "Ina wuni" ta faɗa a taƙaice. Maimakon ya amsa mata sai ya shiga ɗaukarta hoto a wayarsa. Haɗe rai ta yi ta ce "Ka bari bana so". "Tom na bari, kin yi mamakin ganina ko kya ce na fiye naci, ba laifina bane, laifin zuciyata ne". Hafsa ta sunkuyar da kai tana wasa da yatsunta. "Kin yi shiru, ashe biki kuke babu labari. Nayi mamaki da mama tace mini bikin ƙawarki ne, ashe kina da ƙawaye?". Abinda ba ta taɓa yi masa ba tayi, murmushi wanda sai da dimples ɗinta da bai taɓa sanin tana da su ba suka lotsa. A hankali ya furta masha Allah beautiful. "Ina da ƙawaye mana, kana mini kallon bani da kirkin da zan yi ƙawaye ko? Babbar ƙawata ce tun muna yara muka tashi tare shiyasa na zo bikinta". "Ashe ma bikin namu ne, duk da ba a gayyaceni ba muje, a bani wurin zama da Abinci daga Abuja nake ko gida banje ba Wallahi" ɗan zaro ido tayi dama ga idanun nata tubarkallah. "Me yasa baka je ka huta ba?". "Ganinki nake son yi" ta jinjina kai, ta shiga gaba ya bita a baya, wurin taron yayi kyau da tsari, ta sama masa wurin zama, tasa aka kawo masa Abinci da abubuwan sha. "Shikenan ko kana buƙatar wani abun?". "Eh ke nake buƙata a kusa da ni, ki zauna idan kika tafi ban san kowa ba, kar ace na zo gayyar soɗi. Ta ɗan murmusa kaɗan ta samu wuri ta zauna. Ba kunya Khalil ya fara cin Abincin nan, duk da hakan ba ɗabi'arsa bace, cin kowane irin Abinci, kuma a gaban mutane, amma so yake Hafsa ta sake da shi, dan haka ya zage yana ziri. "Allah ya nuna mana ranar bikinmu, muna kan high table kamar wannan couples ɗin, wane irin kaya zamu saka?" Shiru tayi masa tare da ɗan taɓe baki. "Hafsa meyasa ba kaya sona ne?" Yayi Maganar da dukkan nutsuwarsa. Ta ɗauke kai tamkar ba ta ji abin da yace ba. Ya kalli agogon hannunsa ya ce "Tashi muje in mayar da ke gida, tara saura yanzu". "Dama jira nake ka gama, yanzu zan tafi nima". "Na gama muje" ba tare da ko sallama ta tsaya ta yiwa Amaryar ba suka fito ita da Khalil. Suna zuwa inda motarsa take ta ce "To ka gaida gida". "Me kike nufi?" "Zan hau Napep in tafi gida" Khalil ya ce "Ke kin isa ma? Dan Allah kar muyi haka da ke" da ƙyar Khalil ya lallaɓata, ta amince ta shiga motarsa. Suna cikin tafiya ta ce "Ina Yaya Abdul?" "Yana nan, ko wurinsa ban je ba, sai Allah ya kaimu gobe, ya batun case ɗin nan kuwa, ina fatan dai bai kuma dawowa ba?" "Eh bai sake ba" "Ai ba dan Mama ba, da sai na sa an rufe mini shi Wallahi, in ga ƙaryar iskanci, amma naji ya ce "Shi ɗan uwanki ne ko?" Shiru tayi ba tayi magana ba, Khalil ya kalleta ya ce "Ya naji kin yi shiru?". Kawai sai ta fashe da kuka, irin kukan nan me taɓa zuciya da bayyanar da tsantsar damuwa da ma'abocin yinsa ke ciki. Da sauri ya yi parking ɗin motar, ya ce "Dan Allah kiyi haƙuri, ban san maganata zata ɓata miki rai ba, kiyi mini afuwa" Sake rushewa tayi da kuka, tamkar zata shiɗe, wanda hakan ya sake ɗaga wa Khalil hankali, bai san lokacin da ya kai hannu ya ɗago fuskarta cikin damuwa ba "Dan Allah kiyi haƙuri" yayi Maganar a hankali yana share mata hawayen dake ta zubowa ba ƙaƙƙautawa daga cikin idonta. Duk rarrashin da ya yi mata, bata yi shiru ba, sai da tayi mai isarta, sannan ta kalli Khalil ta ce "Mu tafi dare yana yi". "Ai ba zan iya tuƙin ba, kin sani a zullumi, ina son sanin dalilin wannan kukan naki, da kuma dalilin da yasa ba kya sona, Hafsat ban miki bane ko ina da wani aibu". Ta kashingiɗa da jikin seat, a hankali ta ce "Baka da wani aibu, hasali ma a karamcinka duk da halin ko in kula da nake yi maka, bai hana ka taimake ni ba, Amma meye amfanin fara son ka bayan a gaba na san zan iya samun tangarɗa a aikata hakan?" "Wace irin tangarɗa? Ina sonki Hafsa" Ɗago kai tayi ta kalli Khalil cikin rauni "Ina ganin hakan a idonka, amma... Sai kuma tayi shiru hawaye na zubowa daga idanunta. "Akwai ƙaddarar da zata iya zame mana shamaki, bana son in fara sonka, wani abu yazo ya kawo mana tangarɗa, ka san wacece ni ka guje ni". Khalil ya haɗa hannayensa ya ce "Dan Allah Hafsa, ni ba ruwana da wata ƙaddara in dai bata haramta mana aure ba a shari'a, Ina sonki, amma wace ƙaddara ce haka da kike tunanin zata zame mana shamaki da cikar burinmu, tunda ai kina sona ko?" MASU BUƘATA DAGA FARKO, AKWAI A AREWABOOKS KO MANHAJAR WATPAD. AYSHERCOOL 08081012143https://arewabooks.com/chapter?id=638e2c023cc3212f4202c4d8 GABA DA GABANTA AISHA ADAM (AYSHERCOOL) To get the latest update of the story Follow me on Watpad Ayshercool 7724 Arewabooks Ayshercool 7724 What's app 08081012143 P17 Shiru Hafsa tayi, ba tayi magana ba. Khalil ya ce "Yau Allah ya haɗani da gamona ni Ibrahim, Baby magana nake Please answer me" yayi Maganar yana kuma marairaicewa. Kwaɓe fuska tayi kamar za tayi kuka "Ni ka ƙyaleni ko in yi kuka Subhanallah, ba ƙaramin narka zuciyar Khalil Hafsa tayi ba, saboda a rayuwarsa yana son shagwaɓaɓɓiyar mace. "Kar ki yi kuka Please" yayi Maganar yana kwaiwayonta. "Ni ba haka nake magana ba" "To ya kike yi?" Yayi Maganar yana kallon in da take. "Kaga muyi sauri, kar Mama taga na daɗe ta hanani zuwa na gobe in Allah ya kaimu". "Allah ya sa ta hanaki zuwa" ya faɗa yana kunna motar. "Allah ya sa ta hanani zuwa ko?" Ta maimaita tana leƙa fuskarsa. "Eh mana, gaba ɗaya ma ni kishi ne ya ke damuna, duk an gama ganinki, ga mayafinma ba wani babba ba" Kallon kanta tayi da mayafin, ta sake jan mayafin tana rufe jikinta. "Me zaki rufe bayan an gama ganin komai?" "Me aka gani?". "Kyakywar surarki mana, shiyasa duk naji haushi ai" haɗe rai tayi, tana sake gyara zamanta. Haka Khalil ya yi ta janta da hira, ga mamakin Khalil ashe Hafsa na magana sosai, duk a hirar tasu ma, idan ba ta ga dama ba, shiru take taƙi tanka masa, amma yau ta ɗan sake da shi. Har ƙofar gida ya kaita, sannan ya kalleta ya ce "Babyna, yau zan kwana cikin farinciki, duk da ban samu amsar tambayar da nayi miki ba, amma naji daɗin kulani da kika yi, Ina sonki Hafsa" Hafsa ta ɗaga ido ta kalli Khalil, haka nan taji tana tausayinsa, tabbas ya nuna mata so, ko ga wannan sintirin da yake yi a kanta. "Sai da safe, ka samu kaje gida ka huta, Allah ya kiyaye hanya". "Ameen my love" ya furta a hankali, ta buɗe motar ta fita ta nufi gida, har ta shige gida, yana tsaye yana kallonta, sannan ya ja mota ya bar wurin. Sai ƙarfe goma Sa'annan Khalil ya isa gida, Mummy ce ta rage ba ta kwanta ba, taji ana knocking ƙofar Falon taje ta buɗe, mamaki ne ya cikata da ta ga Khalil. "Kai, saukar yaushe?". "Yanzu Mummy". "A wannan daren? Baka samu Flight ɗin yamma ba ne?". Ya shiga cikin falon yana faɗin, a mota fa na dawo. "What, mota kuma? Amma baka da hankali, da wani abu ya faru fa, yadda gari babu tsaro?". "Ai ba abinda ya faru Mummy, baki bacci ba ashe?". "Eh ban kwanta ba tukuna, bari in taso masu aikin can, su girka maka wani abun ka samu ka ci". "No bana jin yunwa, a ƙoshe nake, na shigo ne ma kawai dan kusan na dawo, naga motar Daddy a waje yana gari ne?". "Eh yana nan kusan sati guda kenan yana gari". "Masha Allah, shikenan sai da safe" "To Allah ya kaimu lafiya" ya fice daga falon ya nufi sashinsa. Mama ta lura da yadda Hafsa ke murmushi lokaci lokaci, amma ba taji ta ce mata komai ba. "Nace Khalil ya biki wurin bikin ne?". Hafsa taji tambayar a bazata. "Eh yaje mun gaisa" "Yazo nan nemanki ai, nace masa kina wurin biki" Hafsa tayi shiru tana cigaba da tuna yadda suka kasance yau, haka nan take jin nishaɗi itama a ranta, Khalil ya damu da ita sosai. Bayan ta kwanta, ta shiga cikin abin rufarta, ta ɗau wayarta ta turawa Khalil saƙo kamar haka    _*Ya kaje gida? Na gode sosai. Hafsat*_ Khalil yana ƙoƙarin saka wayarsa a silent ya kwanta, saƙon Hafsa ya shigo wayarsa, jujjuya saƙonya dinga yi yana murmushi. 'insha Allah sai kin zama tawa Hafsa'. Ya yi mata reply da *"Na koma lafiya, amma ai kamata yayi ki kirani kiji, mura fa ta kamani saboda sanyi na daɗe a waje"*_ Ta yi masa reply da "Subhanallah, Allah ya baka lafiya, Asuba ta gari". Kissing ɗin screen ɗin wayar ya yi, ya kwanta, tare da ƙanƙame wayar a ƙirjinsa. Ya ƙudurce a ransa washegari zai jewa Abdul da labari me daɗi a kan Hafsa na daf da fara soyayya da shi. Fadila har fargabar kwanciya bacci take, saboda babu wani abu da yake zuwa mafarkinta, Kamar yadda Sheikh Yazeed yake zuwa, abun har mamaki yake bata, gashi ta rasa wanda zata gayawa, kawai ta yanke shawarar washegari za taje gidansu Yusra ta bata labari, ko da wata shawara da zata iya bata. Ba ƙaramin farinciki Alhaji Ahmad ya yi ba, da ganin Khalil, dan a wata shida sau ɗaya suka haɗu, tun bayan fara aikin Khalil, Alhaji Ahmad mutum ne mai son iyalinsa da kyautata musu, duk abin da suke so shi yake musu, baya son duk wani abu da zai taɓa masa su. Yau gaba ɗaya sun haɗu a kan dining, suna karyawa, sai hira suke cikin nishaɗi da jin daɗi, tamkar basu da wata damuwa a rayuwarsu. Amina ta kallesu sai taji sun burgeta, ita kuwa gidansu duk sun rarrabu, dan nemwa kansu mafita, sun baro Inno ita kaɗai a ƙauye cikin jarabar su Kawu Lawan, nan Baba yana gadi ita kuma tana aikatau, duk dan samun abin da zasu rufawa juna asiri. "Ya Ubangiji Allah ka wadatamu, ka wadatamu da halal ka nesanta mu da haram, Allah ka sake haɗa kanmu a wuri guda cikin farinciki, Allah yasa sanadin karatu nan nawa, ya kawo canji a rayuwarmu" tayi Addu'ar a zuciyarta. Haka ta jira suka kammala, ta kwashe kayan da suka ci Abincin, ta gyara wurin kamar ba ayi Komai a wurin ba. Suka kuma komawa falo suka baje, suna ta hira da iyayen nasu. Daga bisani Alhaji Ahmad yayi musu sallama ya koma ɗakinsa, dan gabatar da wasu ayyuka. Khalil ya yi shiru yana kallon hotunan da ya yiwa Hafsa jiya, duk da bata so ya yi mata hotunan, amma tayi kyau matuƙa, Kamar a saceta a gudu. Mummy ce ta fizge wayar ta ce "Bani nan in ga abin da kake kallo haka ko ƙwsƙwaran motsi baka yi" Mummy ta zubawa hoton Hafsa ido, ta kalli Khalil ta ce "Ita kuma wannan fa?" Khalil ya yi shiru bai ce komai ba. "Ko ita ce wadda kake so ɗin?". Jin abin da Mummy ta ce, ya sanya Fadila tashi da sauri, ta karɓi wayar. Ta kalli hoton Hafsa kwaɓe baki ta ce "Taɓ dan Allah kalleta ga kumatunta da ido kamar wata Philippines, ko ɗan murmushi babu a fuskarta gaskiya ka faɗo". "Bani wayata dan ubanki, ta fi ki kyan gani dai". "Wallahi na fita kyau, Dan Allah Bro dame wannan tafi Yusrana, amma ka watsa mini ƙasa a ido". Haɗe rai Khalil yayi ya ce "zan tattakaki Wallahi". Mummy ta ce "Kar kuyi mini faɗa ni, ita wannan ɗin a ina take? Kuma 'yar wanene?". Gaban Khalil ne yayi mummunar faɗuwa, shi kansa sai yanzu ya sake ankarewa akwai damuwa a soyayyar su. Miƙewa yayi ya kalli Mummy ya ce "We will talk later" yana gama maganar ya fice. Fadila ta ce "Mummy, ke sai ki bari ya auri wannan mummunar?". "Ke Fadila, kina taya Yusra kishi dai, amma ai ba ta da muni, ba laifi". "Wallahi Mummy ba ta da wani kyau, kalleta fa wata 'yar lukuta da ita, ko fara'a babu a fuskarta Wallahi Mummy kar ki bari ya kwaso mana 'yar wahala". "Barni da shi tukuna na ga iya gudun ruwansa". Fadila ta miƙe ta ce "Mummy, a round 11 zan je wurin Yusra". "Ok sai kin dawo" Khalil kuwa bayan ya fita daga falon, ɗakinsa ya wuce, ya shirya don zuwa wurin Abdul su tattauna, a kan yadda suka yi da Hafsat a daren jiya. Yana tafe a mota yana saƙe-saƙen yadda zai ɓullowa lamarin, amma shi babbar damuwarsa a yanzu shi ne ya tabattar da soyayyarsa a wurin Hafsat. Fadila na gaban mudubi, tana shiri dan zuwa gidansu Yusra, wayarta ta fara ringing, ta janyo wayar da ke kan mudubi, ta ɗaga ta sakata a speaker, ta ajiye ta cigaba da abin da take yi. "Assalamu alaikum warahmtullah" aka yi sallama daga cikin wayar. "Wa'alaikum salam" ta amsa tare da yin shiru dan jin wanda ya kirata. "Fadila Dutse ya kike?". "Wake magana?". "Ai kya amsa gaisuwar tawa da fari ko" "Idan baka da abun yi ni ina da shi koma waye". "Kankiya ne" ita gaba ɗaya ta manta da waye ma wani Kankiya, banda yanzu da ya kirata, maganganun Yazeed ne suka dawo mata, da ya gaya cewar sonta kankiya yake yi. Tsuke fuska tayi ta ce "Ina jinka" "Ya kike ya hutun, hope kina jin daɗin hutun?" "Sir ya aka yi ne, kace jarrabawata akwai matsala zaka kirani, kuma ka kirani kana tambayata wasu abubuwa daban" "Eh, saboda ba saboda jarrabawa na kiraki a wannan karon ba, saboda inji lafiyarki ne" "But you have no Business with that" "Who told you so, nafi kowa buƙatar son sanin lafiyarki". "Sir sai anjima, am busy now" ta katse kiran ta ajiye tana huci, tare da harar wayar. Nan da nan ta kammala shirinta, ta ɗau mota ta nufi gidan su Yusra. A ƙofar gidan su Abdul, Khalil yayi parking ɗin motar, kan ya fito sai da ya fara kiran Hafsa a waya, dan yaji ya take, a wannan karon yadda take amsa masa wayar ba ƙaramin daɗi yake masa ba. "Ina kwana" bayan ta amsa salamarsa ta gaishe shi. "Yau wace rana an gaishe ni" yayi maganar yana murmushi. "Mhmm shi ne abin da ta iya cewa kawai". "Kin tashi lafiya ya mamana?". "Mama lafiya ƙalau Alhamdilillah, ya mutan gidan? Ya jikin naka?" "Kowa lafiya ƙalau, amma meya same ni?". "Kace mini kana mura mana" "Lallai kin fara damuwa dani, mura na warware Alhamdilillah, ina fatan kina lafiya ba wata matsala?" "Ƙalau nake Alhamdilillah". "To Masha Allah, zan shigo anjima insha Allah, da ƙarfe nawa zan zo?" Khalil yayi Maganar yana shafa sumar kansa. "Idan an yi sallar isha'i, lokacin ne na dawo gida" "To shikenan dear, me zan taho miki da shi?". "Bakomai" ta bashi amsa. "A'a nifa bana son haka, dan Allah ki gaya mini" yayi Maganar cikin shagwaɓa. Dariya ya bawa Hafsa, "Wai shagwaɓa kake yi, gaskiya Mama na fama". Dariyar shima yayi ya ce "Ai kuma kece yanzu zaki dinga faman, duk shagwaɓata ai ban kai ki ba, haka fa kike cewa malam ka rabu dani kar ka sake zuwa in da nake" ya yi yana kwaiwayonta in zata yi masa tsiwa. Rufe fuska tayi kamar yana gabanta "Am sorry, kayi haƙuri na san na gaggaya maka maganganu marasa daɗi, ba halina bane bana son kowa ya matsi ratuwata ne" ta ƙarasa maganar a sanyaye. "Na fahimta, kar ki damu sai na zo ki gaishe mini da Mama" "Zata ji insha Allah" ya katse kiran, sannan ya fito daga motar. " 'yar yarinya da wa kike wayane haka kike ta wannan fara'a?" Mama tayi maganar bayan ta shigo cikin ɗaki, Hafsa na kan katifa tana ta murmushi, shiru tayi tana ɗan mazewa ba ta zaci Mama na jiyo ta ba. "Ya kika yi shiru, ko Khalil ne?" Hafsa ta gyaɗa mata kai. Mama ta zauna a gefen katifar tana faɗin "Yauwa ko ke fa? Ki dinga sakar masa fuska, shi har abada wanda yace yana sonka ya gama yi maka komai" A raunane Hafsa ta kalli Mama ta ce "Amma Mama... "Shhh na san mai zaki ce Hafsa, ki kwantar da hankalinki, in dai da gaske Khalil yake sonki, na san ba zai gujeki dan ƙaddararki ba, nayi farinciki da shigowar wanda yake saki walwala rayuwarki, duk da halinki na miskilanci da taurin kai". "Mama taurin kai kuma?". "Eh taurin kai mana, ke baki san yadda kike da taurin kai ba, ai sai dai Allah ya shirya mink mini ke". Hafsa kam shiru tayi tana tunani, tabbas ta fara jin Khalil a zuciyarta, dan ma tuntuni basar da shi take, amma Khalil ya haɗu ta kowane ɓangare amma tana tsoron tayi zurfi a sonsa ya san ko ita wacece, ya zo ya rabu da ita, kamar yadda ya faru da ita a baya. "Girl, kince mini akwai Magana, kuma tun da kika zo kin yi shiru, yakamata muyi magana" Fadila ta ɗan yi shiru tana kallon Yusra, sannan ta ce "Ai ke rainin hankali ne ya miki yawa, ina tsoron in gaya miki ki raina mini hankali" Dariya Yusra tayi ta ce "Idan ma na raina miki hankali, ai mun saba kema kina mini, ina jinki". "Zan gaya miki damuwata, idan kika gayan ba daɗi zan zage ki ne tsaf in tashi in tafi gida". "Nima ina da bakin ramawa ai". Fadila ta labartawa Yusra abin da ake ciki, game da mafarkin da take yawan yi a game da Yazeed, da kuma abin da Yazeed ya gaya mata a game da Kankiya. Yusra ta ce "To sai me dan kina yawan mafarkinsa, kin sa shi a ranki ne, kuma kuna yawan haɗuwa a school shikenan". Fadila ta ɗanyi tsaki ta ce "Ke ba kya gane abubuwa, ba fa Normal mafarki nake kawai in ganshi ba" Kan Fadila ta gama maganar, Yusra ta tuntsire da dariya. "Ke nifa bana son iskanci, gayen nan ya taimakeni lokacin exams, duk da yadda na raina masa hankali, Wallahi idan ya zo kusa dani bana iya cewa komai, sai dai jikina yayita rawa, jikina yayi wani iri, inji kamar zan yi kuka, wasu hawaye su cika mini ido". Me Yusra za tayi banda dariya, harda hawaye, dan sai da Fadila ta fara ƙuluwa, can Yusra ta ce "Ba faɗa da malam ba daren, yarinya ƙila zuwa yayi yai tsayuwar dare a kanki, saboda iskancin da kike masa, sai ki shiga hankalinki ai" "Ban gane me kike nufi ba ai" "Wataƙila Addu'a yayi miki yarinya, waye ya gaya miki ana ja da malamai?". "Ke ni ki bani shawara kawai" "To ni wace shawara zan baki? Tun da dai bani nake haɗaku a mafarkin ba, you need each other maybe shima yana mafarkin da ke, kin sashi a ranki ne kawai". "Wai ya za ayi in sa shi a raina, a kan me zan a shi a raina? Ni shishsigin da yake mini ma haushi yake bani, dan dai kawai yana taimaka mini sosai ne". Yusra ta ce "To ni yanzu me zance miki, idan ba damuwa ki kayi da shi ba, yawan mafarkinsa da kike alamane da yake nuna ruhinku na tare da juna, kuma jikinki na gaya miki yana buƙatar Aure, kuma ɗan ustazu yake so" tayi maganar tana dariya. Haɗe rai Fadila tayi ta ce "Laifina ne da na zo wurinki" "To idan ba haka ba, duk mazan duniya da wanda kike gani yau da kullum ba wanda kike gani sai shi, na fassara miki abin da kike buƙata kina jin haushi na. Meke saka miki rawar jiki dan kuna tare? Idan baki wasa ba, wataran sai dai kiga kin rungumeshi. Zahiri ki zata mafarki ne, shi zuciyarki da gangar jikinki ke buƙata" Tsaki Fadila tayi, ta tashi ta ɗau jakarta ta ce "Sai kiyi da wata dan ubanki". "Ubana ya gode matar Ustaz". "Allah ya isa shegiya, kije dan kanki, Allah ya tsareni haɗa jiki da wannan yarom". "Zaki ga yaro, Amma dai kin san ba ƙazami bane" Banza Fadila tayi mata ta nufi hanyar fita. Yusra ta ce "Amaryar Ustaz ko Kankiya, ranar Saturday ki aiko a karɓar miki chocolate cake zan yi" Ko waiwayowa Fadila ba tayi ba, ta yiwa maman su Yusra sallama ta fice. Khalil ma cike da farinciki ya je wurin Abdul, sun sha hira sosai, yayin da Abdul ya ƙara bashi shawarwari tare da bashi ƙarfin gwiwa a kan yadda zai cigaba da neman Soyayar Hafsat. Bayan sallar isha'i, Khalil ya sha kwalliya cikin cofee ɗin yadi mai laushi, ya sanya hula tare da feshe jikinsa da turare. Ya ɗau hanya ya nufi gidansu Hafsa. A kan dandamalin ƙofar gidansu tayi musu shimfiɗa, ta kalleshi tana murmushi ta ce "Kayi kyau sosai" "Ko baki faɗa ba ai ni mai kyau ne" "To ai sai ka bari a faɗa, na ma janye ba kai kyau ba" Khalil yayi dariya ya ce "Daga baya kenan, ina Mama" "Mama na ciki tana gaisheka" Hafsa ta kawo masa ruwa a Jug, suna hira yana sha, rabon da Khalil ya sha ruwan borehole har ya manta, sai dai ya sha na roba, amma ya sai gashi zaune yana ɗaɗɗakar ruwan borehole.   Sosai ya dinga jan Hafsa da hira, yau kam ta biye masa sosai, ita kanta ta san ta samu farincikin da ta daɗe ba tayi ba. "Hafsa kina sona?" Ya jefo mata tambayar. Gaba daya annurin fuskarta ya ɗauke, tayi shiru ba ta ce komai ba. "Hafsa meyasa kike gudun amsa mini tambayar nan ne?". "Saboda ƙaddarata" "Mecece ƙaddarar taki gaya mini, zan fahimceki". Ta share hawayen da suka fara zubo mata ta ce "Zan gaya maka idan ka sake dawowa, amsarka bayan jin mecece ƙaddarata ita zata amsa maka tambayar da kake mini na idan ina sonka" "Ki gaya mini yanzu ko zan samu nutsuwa mana". "A'a dare ya fara yi kuma ga sanyi, zan gaya maka insha Allah" "Shikenan, jeki ki gayawa Mama zan shigo in gaisheta" Hafsa ta tashi ta tafi, shi kuna ya buɗe jug ɗin ruwan, ya zubar da sauran, ya ƙulle kuɗi a leda ya saka mata, dan ya san idan ya ce zai bata ba zata karɓa ba. Ya shiga suka gaisa da Mama, Bayan ya fito Hafsa ta biyo shi da wata leda babba, ta bashi. Ya sa hannu ya karɓa ya ce "Ni kome kika bani karɓa zan yi, ni ba irinki bane" "To ni ɗin ya nake?" "Kin fini sani ai, ranar ai a kan 500 kika kusa yi mini tijara" Murmushi Hafsa tayi ta ce "Baka da mantuwa ko?" "Ina zan manta, sai da safe" yayi mata sallama sannan ya tafi gida, aikuwa a hanya Hafsa ta dinga kiransa a waya, ya san a kan kuɗin nan ne, dan haka yaƙi ɗagawa. Gaba ɗaya zuciyarsa ta tafi a kan son sanin ƙaddarar da ke cikin rayuwar Hafsa. Da yaje gida a falo ya shigo da ledar, jin ledar da zafi tun lokacin da Hafsa ta bashi, ya san cewa abin ci ne a ciki. Ya sa Amina ta kawo masa plate da cokali, Mummy sai binsa take da kallo, tana tambayarsa daga ina yake. "Wurin Abdul" ya bata amsa. Ya zazzage ledar, Awara ce fal, da miyar jajjage ga kabeji da cucumber fal a gefe. Murmushi yayi ya juye a kan plate ɗin, ya sa cokali ya fara ci" "Me kake ci haka ne?" Mummy tayi maganar tana leƙa plate ɗin. "Mummy awara ce fa" ya faɗa yana cigaba da ci. Yamutsa fuska ta yi ta ce "Awara Khalil? Kaima ka fara irin wannan cimar yunwar? Meye haɗinka da wata awara?" Khalil ya ce "Mummy amma naga Abinci ce itama, ta burgeni ne shi ne na saya". "Duk Abincin da yake gidan nan ka rasa me zai burgeka sai awara? Me akayi a ka wata awara, wannan ƙazantar da ake sayarwa a bakin hanya, wato shi dai Abdul ɗin nan dole sai ya maida kai irinsa, shike koya maka duk wani halin ƙauyanci da shirme, yanzu idan cikin ka yayi ciwo fa?" "Mummy ba Abdul ne ya sani saya ba, ni na saya da kuɗina fa". "Tun da kake a gidan nan ka taɓa ganin an sa kuɗi an sai wanna abar? Saboda kalan yunwa da nemawa kai masifa shine kaje ka saya kana sawa a cikinka, baka san da yadda aka yi ta ba, ke zoki ɗauke wannan a bar kuje ku cinye ta" tayi maganar cikin tsawa tana kallon Amina. Mamaki ne ya kama Amina, duk a kan awarar ake wannan tashin hankalin, wato idan ma abun mutuwa ne su suci su mutu kar ɗanta ya ci. Khalil yana ji yana gani, Amina ta ɗauke awarar kitchen ta kai awarar ta ce "Aikuwa ba zamu ci ba, shi ɗin ne zai cinye a barsa, wannan matar lamarin nata ya wuce tunani" Khalil yayi fushi ya bar Falon, dan ba ƙaramin daɗi awarar tayi masa ba, dan da gani ta musamman ce Hafsa tayi masa. Ta ƙofar corridor Amina tabi, taje ta ƙwanƙwasawa Khalil ƙofa. Kamar ya share sai kuma ya buɗe. Amina ta miƙa masa plate ta ce "Ga awararka nan na kawo maka, Naga kana so" ya ɗan ƙura mata ido sannan ya karɓa ya ce "Na gode sosai". "Never mind" ta faɗa a taƙaice ta juya ta koma. Fadila tai ta jujjuya maganganun Yusar a kan Yazeed, ƙarshe kawai tayi tsaki ta bar zancen Yusran a shiririta. Sai dai ba abinda ya sauya, daga yawan mafarkin Yazeed da take yi. "Baba ga karin kumallo na kawo maka" Amina tayi maganar hannunta riƙe da wani ɗan madaidaicin faranti, tana kallon Baba. "Yauwa uwata, Allah ya yi miki Albarka". "Ameen, amma ya aka yi naga idonka yayi ja?" "Mura ce ta sakani a gaba, ta saka mini ciwon kai da zazzaɓin dare". Cikin kulawa Amina ta ce "Baba to ka karya sai in raka ka Asibiti mana". "A'a uwata, zan warware insha Allah, zan dafa rai ɗore in sha, na kuma karɓo magani a Chemist" "Baba gara dai muje Asibitin" "Ki bari idan ban warke ba zuwa gobe in Allah ya kaimu sai inje" ya ƙarasa maganar tari na taso masa" "Sannu Baba, ka karya sai ka kwanta, hannunka ma ya ɗau zafi sosai". Baba yana tsaka da karyawa, Fadila ta fito tana ta wani hura hanci, ta yiwa Baba alama da yazo. Baba na shirin tashi, Amina ta ce "Baba zauna, bari ni naje" ta tashi ta nufi in da Fadila take. Fadila ta kalleta a wulaƙance ta ce "Ba ke nake kira ba, Babanki nake kira". Amina ta ce "Bashi da lafiya ne shiyasa na zo". "And so? Baki ji me mace bane babanki nake kira bake ba" ganin kamar suna jayayya ya sanya Baba tasowa, ya ƙarasa in da suke tsaye ya ce "Gani". Fadila ta kalleshi ta miƙa masa kuɗi ta ce "Gashi nan, kaje ka tari Napep kaje gidan su Yusra zata baka saƙo ka kawo mini" Amina ta ce "Ni ki kwatanta mini gidan sai inje, Baba bashi da lafiya fa". Cikin tsawa Fadila ta ce "Nace Babanki na aika bake ba, karki sake saka mini baki a maganata" "Kiyi haƙuri dan Allah ni ki aike ni, jikinsa da zazzaɓi" "Baban naki ma ya aka cika idan an aike shi, shi da ya daɗe a birni balle ke bagidajiya 'yar ƙauye kije gidan mutae kiyi musu hauka da jahilicin naki da kika saba ki zubarwa da mutane mutunci" Baba yayi gyaran murya ya kalli Amina ya ce "Uwata, ai jikina da sauƙi sosai Alhamdilillah, bari inje maza jeki ɗau Abincina ki rufe mini yanzu zan dawo" Baba ya juya ya nufi gate, yana takawa a hankali saboda jikinsa ba daɗi. Fadila kuma ta koma ciki abunta, Amina kuwa tamkar an dasata, sai ma wasu hawaye masu zafi da suka fara biyo kuncinta. Tana nan tsaye Alhaji Ahmad ya fito, cikin suffarsa ta kwarjini da kamala, tun da ya fito Amina ta zuba masa idanuwa, har sai da ya tsargu, amma har ya gifta ta ko gaishe shi bata iya yi ba. Ya wuce ya hau motarsa, wannan karon ba direba da kansa yake tuƙi, Zakiru ya buɗe masa gate ya fice. "Tabbas kan in bar gidan nan, sai nayi maka abin da har 'yarka ta koma ga Allah ba zata manta ba, sai taji abin da nake ji idan taci zarafin mahaifina". Ayshercool 08081012143GABA DA GABANTA AISHA ADAM (AYSHERCOOL) To get the latest update of the story Follow me on Watpad Ayshercool 7724 Arewabooks Ayshercool 7724 What's app 08081012143 *Littafina Aƙidata da kuma Ruɗin ƙuriciya, na kuɗi ne, sauran duk free me* 18-19 Amina ta ja jikinta a hankali, ta koma wurin zaman Baba ta zauna, tana jin yadda sanyi ke ratsata, wani irin tausayin Baba ya mamaye zuciyarta, Allah kaɗai ya san irin ƙalubale da wulaƙancin da ya dinga fuskanta a gidan nan, amma yake dakewa yana shanyewa. A ƙalla Amina ta shafe awa guda a zaune, amma Baba bai dawo ba, haka ta tashi ta koma cikin gidan, zuciyarta na mata ƙuna game da abin da Fadila ta yi wa Babanta. Ta tagar corridor Amina ta hango Baba ya nufo hanyar shigowa cikin gidan. Da sauri ta fito falo, idon Baba duk yayi ja, saboda yadda ya sha ƙura a hanya. Fadila kuwa na zaune sai kaɗa ƙafa take, tana latsa remote hankali kwance. Baba ya ƙaraso ya ɗan risuna yana miƙa mata ledar hannunsa. "Wai kai dan Allah duk lokacin da aka aikeka, sai kaje kai zamanka?" "Yi haƙuri ba haka bane, titunan ne akwai cunkoson ababen hawa, mussaman yau da aka tashi da hazo". "Ajiye a wurin ka je, Na gode" ya ajiye mata ya miƙe, Amina ta fito ta biyo bayansa, amma Fadila ta kalleta ta ce "Ke zo nan" Amina ta tsaya cak ta waiwayo tana kallon Fadila. "Akwai undeas ɗina a toilet, ki je ki wanke mini, sannan ki sauke jakunkuna na daga hanger duk ki goge mini su" Wani abu mai ɗaci ya tsirgawa zuciyar Amina, Baba ya kalleta yayi murmushi, yana gyaɗa mata kai cikin bata ƙwarin gwiwa da kwantar mata da hankali. Amina ta juya ƙafafuwanta suna rawa, ta nufi sashin Fadila. Sai da Hafsa ta yiwa Khalil mita a kan kuɗi da ya bata haka da yawa, ta dinga mita tare da cewa ya zo ya karɓi kuɗinsa, a karo na farko da ya nuna mata ɓacin ransa tun bayan haɗuwarsu, sai kuma taji babu daɗi dan ƙarshe ma kashe wayarsa yayi. Sai da ya wuni be kirata ba, idan ta kira shi kuma yaƙi ɗagawa, gaba ɗaya ta shiga damuwa. 'Kenan da gaske na fara son Khalil? Idan kuma ya san wacece ni ya ƙi aurena fa ya zan yi?' ta tambayi kanta, take kuma taji kanta yayi mata wani irin dumm babu daɗi, ta shiga taradaddin halin da zata shiga idan Khalil ɗin ya kasa ɗaukar ƙaddarar da ta faɗa mata.   Kasancewar an tashi da hazo sosai, ya sanya Hafsat take ta kula da Mama, dan kar ta fito tsakar gida ko tace za tayi wani aiki, saboda yanayin jikinta, ba ta da cikakkiyar lafiya, amma hakan bai hana tari ya sarƙe Mama ba, duk wani taimako da Hafsa zata iya bata ta bata, amma abu yaci tura, dan har numfashinta ya fara sama sama. Cikin hanzari ta tashi ta samo abin hawa, suka tafi Asibiti. Suna zuwa aka basu gado, likitoci suka fara ƙoƙarin suga numfashin Maman ya daidaita. Hafsa ta ƙurawa Mama ido, an saka mata Nebulizer, ga drip a rataye. Hafsa ta sa kujera ta zauna, ta cigaba da kallon Mama, ta riƙo hannun Mama tana tuno abubuwan da suka gabata a rayuwarsu, da kuma yadda aka yi Mama ta haɗu da wannan larurorin da suka mamayeta. A hankali wasu irin hawaye suka shiga zubowa daga idanunta, ba dan kuɗin da Khalil da ya bata ba da bata san ya zata yi da ciwon Mama ba.   Kwanansu biyu a Asibiti, amma Khalil baya ɗaga wayarta, gaba ɗaya ta shiga cikin damuwa, sai da hakan ta faru sannan ta gane a 'yan kwanakin nan ba ƙaramin sabawa tayi da Khalil ba. Shi kansa Khalil daurewa yake yi, baya jin daɗin rashin wayar da ba ya yi da Hafsa, amma dole ya dinga nuna mata fushinsa idan ba ta kyauta ba, yana matuƙar son ta, kuma yana son ya taimakesu, mussaman duba da yanayin halin da suke ciki, amma taurin kan Hafsa yafi ƙarfinta. A kwana na uku ne, Hafsa na saka ran a sallami Mama, dan a kwanakin nan kuɗin wurin Khalil da ke hannunta sun ƙare, harta fara shiga na sana'arta, dan kullum cikin kawo kawo ake a Asibitin kamar ba na gwamnati ba. Ba tsammani taga kiran Khalil, amma ta share, sai da Mama ta kalleta ta ce "Ba kiran wayarki ake ba?" "Eh wayata ce". "To ki ɗaga mana" "To zan ɗaga" ta amsawa Mama amma taƙi ɗagawa. Ganin Mama ta ƙura mata ido ne, ya sanya ta ɗaga wayar, tana tura baki ta amsa masa sallamar da yayi da ƙyar. "Na je gida ba kowa, kuna ina ne?" Ta kalli idon Mama sannan ta ce "Muna Asibiti Mama aka kwantar" "What? Amma baki gaya mini ba, wane Asibitin ne?". "Ai sallamar mu za ayi yanzu, likitan dare muke jira ya sake dubata mu tafi". "Ba wannan na tambayeki ba, wane Asibitin ne?" Har ga Allah Hafsa bata son yawan ɗawainiyar da Khalil yake yi da su. "Hafsa magana nake miki fa" "Mhm nifa nace maka gida zamu taho" "Wai ya kike mini jayayya ne?" Ya faɗa a hasale. Haka ta haƙura ta gaya masa tana tura baki, dan taji haushin ɗaga mata murya da yayi. Da hanzari ya shiga falo yana dube-dube. "Ya aka yi ne?" Mummy ta tambayeshi. "A nan na bar car keys ɗina?" "Me zaka yi da makullin mota yanzu da daddare ba ka dawo gida ba kenan?". "Eh zani wani wuri ne". "Ina ne wani wuri?" Tayi maganar tana tsare shi da ido. "Mummy sai kace wani mace, wani wuri zani fa, yanzu zan dawo" yayi Maganar yana ɗaukar key ɗin da yake kan dining yayi waje. Fadila ta ce "Wurin wata zashi, ina ga wannan Yarinyar ce, ko ita aka kwantar Asibiti, ko wani nata, kan ki fito ya shigo yana waya". Mummy ta ɗan yi shiru sannan ta ce "Wai ni 'yar waye Yarinyar nan, yakamata in sani tunda wuri". "Waya san masa, shi zaki tambaya". Bai fi mintuna Arba'in ba, Khalil ya sake kiran Hafsa, ya ce ta zo ta shiga da shi, amma taƙi fita, ta gaya masa lambar ward ɗin da suke. Sai da ya daure sannan ya iya shiga ɗakin, marasa lafiya sun kai mutum Ashirin a ciki, sai ƙarni da warin Asibiti da ke surnanowa daga cikin ward ɗin, haka ya daure ya shiga, tun da ya shigo ta hango shi, amma ta basar yaita lalube ya gano su.   Sai da ya ƙaraso sannan Mama ta gane shi, ya nuna kamar bai ga Hafsa ba, ya durƙusa ya gaida Mama, ta amsa masa cikin kulawa. Nan ya zauna yana yiwa Mama sannu, Mama ta kalli Hafsa ta ce "Ke baki iya gaisuwa ba?". Fuskarta ba fara'a ta ce "Ina wuni" ba tare da ta kalli Khalil ba. "Mama ƙyaleta, bana neman gaisuwata, Fushi nake da ita, Mama kwana uku kina Asibiti amma yarinyar nan ta kasa kirana a waya ta gaya mini, sai ma wani cika da take tana batsewa". "Da na kiraka kana ɗagawa ne?" tai maganar tana kuma ɓata rai. Mama sai da ta ƙulu da abin da Hafsa tayi, amma tayi shiru ta rabu da ita, kasancewar likitan da zai sallami Mama bai shigo da wuri ba, ya sanya ya ce Mama ta bari sai da safe. Ya tashi zai tafi, ya sanya hannu aljihunsa, ya ciro kuɗi ya ajiye a kan side bed, Mama za tayi magana Hafsa ta rigata "A'a ka barsu gaski... Ba ta ƙarasa ba Khalil ya watsa mata wani irin kallo, da ya sanya ta haɗiye maganar da take son ƙarasawa. Ya kalli Mama ya ce "Mama in dai ni ɗanki ne, bai kamata ki ƙi karɓar abin hannuna ba, Allah ya baki lafiya, gobe Insha Allah in an sallameki, zan zo gida in sake dubaki" yayi sallama da Mama ba tare da ya ko kalli Hafsa ba, yayi gaba abin sa, tabi bayansa da kallo tana jin haushin yadda ya shareta. Bayan fitar sa sai da Mama ta yiwa Hafsa ta tas, a kan abin da take yiwa Khalil.   Amina tana ta ƙoƙarin kula da Baba, amma Hajiya Zainab da Fadila suka tsiro da wani wulaƙanci, da sun fuskanci tana son wurin Baba, sai a tsiro da aikin da za'a sakata su hanata zuwa, haka kurum 'yan kwanakin nan suke tsangwamarta, ta rasa me ta tare musu.   Yau ɗaya daga cikin 'yan ajinsu Amina take sauka Alqur'ani, kuma an gayyaceta, tana son zuwa ko dan ta ƙare sanin kan cikin birnin Kano. Ta nunawa Baba katin gayyatar, ya amince taje, tare da yi mata nasiha sannan ya ce ta tambayi Hajiya Zainab, kar fitar tata ta zamana laifi. Ba dan Amina ta so ba, ta tambayi Hajiya Zainab, ba ta sa ran ma zata barta ba, amma cikin ikon Allah kawai taji ta amince.   Amina ta dinga murna, dama sun yi da ƙawarta Azima, zata biya gidansu su tafi tare, dan bata san gidan saukar ba. Duk da gidansu Azima bai kai na su Fadila girma da kyau ba, amma suma da gani suna da kuɗi sosai, sai dai halayyar 'yan gidansu Azima ya sha banban da na su Fadila, Maman Azima na ganin Amina, ta karɓeta da fara'a tana faɗin "Yau ga Aminan Azima a gidana, kullum sai an bani labarin Amina H shanono, yau dai gani gata" Amina ta ƙunshe fuska tana murmushi. Maman Azima ta ce "Tana can tana wanka, ita da idan ta shiga banɗaki, tamkar tana ɗakinta, bari a kawo miki Abinci". "A'a Ammi na ƙoshi" ta ɗan tsuke fuska ta ce "Hala ita Aziman bata gaya miki idan an zo gidan nan ba na bada abu aƙi karɓa ba? Dole ki ci Abinci Amina, ga ɗakin Aziman can, ki shiga sai a kai miki Abincin can" Amina ta shiga ɗakin Azima, ɗakin ya haɗu sosai da sosai. Azima na fitowa daga wanka, taga Amina, ta daka tsalle ta rungume Amina. "Ke cikani kar ki tsirara malama" Azima ta ce "Ashe zaki zo ɗin 'yar rainin hankali kawai, amma dai ba da wannan shigar zamu je wurin saukar ba?". Amina ta kalli kanta ta ce "Me shigata tayi?" "Ke ba zamuje a raina mu ba, kin san halin 'yan ajinmu, bari in shiga shagon Ammi, in ɗauko miki sabuwar riga" Amina ta zaro ido tana shirin magana, mai aiki ta shigo ɗakin, ta dinga ajiyewa Amina kayan ciye-ciye. Azima ta fita ta dawo da wata rantsatiyar doguwar riga purple da takalmi da jaka duk kalar rigar. Azima ta ce "Gashi nan Ammi ta ce a baki ki saka" da yake Ammi na da shagon botiques a cikin gidan. Jiki a sanyaye Amina ta ce "Azima, kin san ni wacece, dan Allah ki bar kayan nan, in je da na jikina" "To sai ki je ki gayawa Ammin ai" Amina fafur taƙi yadda ta saka kaya, sai da Ammi ta zo da kanta, Amina ta ce "Ammi ba ƙin karɓa nayi ba, Baba zai tambayeni ina na samo kayan nan, kuma gidan aikina zasu tambayeni". "Kar ki damu, direba ne zai kai ku, ya mayar da ke gida, sai a yiwa Baban naki bayani" Da ƙyar Amina ta yadda, ta cire hijjabin jikinta, da yayi haske saboda ya gaji, tun irin wanda ta zo da su daga ƙauye ne. Ta canza kaya zuwa doguwar rigar nan, ga uban gashinta da yake natural, ta tattare shi da tsohon ribbon. Azima ta sakata a gaba, ta saka comb tana taje mata gashin nan, ta shafa mata mai, ta kawo kayan make up, tayi mata simple make up. Azima ta ce "Ke yarinyar nan Allah yayi miki kyau, amma ko hoda ba kya shafawa haka kike yawonki" "Ke ni ƙyaleni da wata hoda" yadda Amina tayi kyau, ba zaka ce daga ƙauye take ba, Azima ta buɗe wani irin turare mai ƙamshin gaske, ta shafawa Amina ita ma ta shafa. Suna fita falo Ammi ta rungume Amina, "Kai Masha Allah da wannan kyakykyawar yarinya, bani wayata in mata hoto" Amina har mamakin karamcin Maman Azima take yi, ita babu ruwanta kamar ba mai kuɗi ba, 'to kenan masu kuɗin ba kowane me irin halin su Hajiya Zainab ba?' Da zasu tafi har harabar gidan Ammi ta rakosu, ta cewa direba "Ga su nan ka kula mini da su, ka kai su wurin walimar saukar, kar a bari magariba tayi, duk in da suka yi awa ɗaya da rabi, kai mayar da Amina gida, ga kaya nan na bata, ga wasu a ledar nan, ka yiwa Abbanta bayanin ni na bata, sai ku taho kai da Azima". Amina tai ta yiwa Ammi godiya, tayi mamakin tsananin karamcinta, sam ba ruwanta da wata ɗagawa. Haka kuwa aka yi, suka fara zuwa wurin sauka, aka yi walimar sauka a cikin ƙawayensu, Amina taji daɗin wannan fitar sosai da sosai. Kamar  yadda Ammi tayi umarni, har gida aka mayar da Amina, direba ya yiwa Baba bayani kamar yadda Ammi ta umarce shi. Bayan tafiyar su Azima, sai da Baba yaita yiwa Amina nasiha tare da gargaɗinta a kan ta iya talaucinta. Khalil da ke zaune a mota yana shirin fita, ya zubawa Amina ido, bai taɓa ganinta ba hijjabi ba sai yau, rigar kamar da jikinta aka auna aka yi ta, saboda yadda ta zauna cif a jikinta, yana cikin motar ta zo ta wuce cikin gidan, hannunta riƙe da wata babbar leda. Ajiyar zuciya ya yi, ya kunna motar ya bar gidan. Amina a falo ta zauna, ta buɗe robar gugguru ta fara ci, ƙamshin turaren Alhaji Ahmad ne ya fara cika wurin kan ya bayyana, ya turo ƙofar falon da sallama, Amina ta amsa  ƙasa ƙasa. Duba falon yake yana son gane daga ina yake jin tashin ƙamshin wani turare na musamman. Har ya zo zai gifta kunnuwansa suka jiyo masa muryarta "Daddy sannu da zuwa" kallon in da Amina take yayi, sai dai ba shi tabbacin ko Aminan ce, saboda yadda ta ke haɗe cikin riga mai kyau, kuma shi da hasali ma yarinyar sai ta ga dama take gaishe shi, dan haka kawai ya wuce bai amsa ba.   Amina ta gama ciye-ciyenta, sannan ta tashi da nufin ta je wurin Hajiya Zainab, ko da aikin da zata yi mata, saboda tana son ta shiga ɗakinta tayi rubutunta na Alqur'ani, wanda idan tana yi, bata buƙatar takura. Kanta a ƙasa tana sauri, suka yi karo da Alhaji Ahmad dake ƙoƙarin fitowa daga sashin Mummy. Amina ta firgita sosai ɗan ƙaramin mayafin kanta ya sauka, tarin gshinta ya bayyana. Ganin ya zuba mata ido ya sanya ita ma ta ɗan tsare shi da nata idanuwan, tana ƙoƙarin gyara mayafinta. "Ba kya gani ne?" Ya furta yana kuma tsareta da ido. "Yi haƙuri ban san ka taho bane" guntun tsaki ya ja, ya raɓa gefenta ya wuce. Amina ta taɓe baki ta ƙarasa ciki. Bayan sallar isha'i, Khalil ya koma gidan su Hafsa, 'yan kwanakin nan ya sarƙi zuwa gidan, Jikin Mama yayi sauƙi sosai, Khalil ya ji daɗin yadda ya ganta, suka taɓa hira tare da sake yi mata sannu. Yau ma bai kula Hafsa ba bata kula shi ba, sai da zai tafi Mama ta ce Hafsa ta raka shi. Ba ta son yiwa Mama gardama, ta rako shi har gaban mota, ba tare da ta ce masa uffan ba, suna zuwa bakin motarsa ta juya zata koma gida abinta, cikin zafin nama Khalil ya riƙo hannunta, ya buɗe motar sa ya sakata a ciki, ya rufe ƙofar, ya zaga ɗaya site ɗin ya shiga. "Meye haka? Dan Allah ka buɗe mini in fita, sai kasa mutanen unguwa sun mini wani sharrin?" "Idan sun miki sai me? Ke da mijinki ne ai ko? Hafsa meyasa kike mini haka ne, kin fi son in ta wahala ko baki damu da ni ba?". Ta tura baki ta ce "Eh ai nima baka damu da ni ba, da na dinga kiranka ka ƙi ɗauka" "Ba dole in ƙi ɗauka ba, Hafsa komai na baki ba zaki karɓa ba, sai kin yi mita da ƙorafi bana son abin da kike mini bana jin daɗi" ya ƙarasa maganar cikin marairaicewa. Cikin shagwaɓa ta ce "To Shine sai ka daina kirana, kuma daina ɗaga nawa, dan ka sani damuwa" "Dagaske kin damu kema da bama waya?" Ta jinjina masa kai alamar eh. "Kina sona kenan?" Yayi Maganar da dukkan nutsuwarsa. Shiru ta ɗan yi, sannan ta kalleshi ta ce "Kana sona da gaske?" "Ina sonki mana" "Bari in fara gaya maka waceceni, da ƙaddarar da ta sameni, ban sani ba ko zaka iya cigaba da sona a haka". Hafsat Usman Dikko, shi ne cikakken sunan Hafsa, mahaifinta haifaffen garin Kano ne, mahaifiyarta ma haka. Mahaifin Hafsa shikaɗai mahaifiyarsa ta haifa a gidansu ta rasu wurin haihuwa, ya taso a tsakiyar 'yan uba, cikin tsangwama da kyara. A haka a wahale yayi karatun Addini da na zamani, kasancewar Usman mutumin kirki, mai ladabi ga kowa da kowa ya sanya 'yan unguwarsu kowa yana son sa. Ya haɗu da mahaifiyar Hafsa, mai suna Safiyya, a nan wani filin ƙwallo da yake zuwa, a nan cikin unguwar gwale. Sai dai itama basu da ƙarfi, dan marainiya ce, yayanta ne yake ɗawainiya da su. A lokacin da  Usman ya auri Safiyya, ba shi da wata tsayayyiyar sana'a, sai dai mutum ne mai zuciyar nema, sai dai yana da kwalin degree har biyu amma babu aikin yi, gidan da suka tare ma a ciki, gadonsa ne na mahifiyarsa a nan cikin unguwar ɗorayi, wani ɗan ƙaramin gida, haka suke rayuwa. Kwatsam, Chairman ɗin unguwarsu tsohon abokin mahaifin su Usman ne kan ya rasu, ya bawa Usman offer, a hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta ƙasa. Yayi murna ba kaɗan ba, a lokacin 'yan uba suka sake sako shi a gaba, da sharri da jafa'i kala kala dan su cikinsu babu wanda ya yi karatun boko sai shk. Lokaci ɗaya Allah ya ɗaukaka shi a kan harkar aiki, ya mallaki gida da abin hawa, ya mallaki shaguna a nan cikin umgu su, wasu ya bada haya wasu ya zuba kasuwanci ya janyo 'ya'yan 'yan uwansa, amma suka dinga cutarsa. Amma duk da haka Allah bai sa yayi baya ba, kullum gaba yake yi, cikin ikon Allah a nasarorin da ya samu, har da karramawa daga fadar shugaban ƙasa, saboda gaskiyarsa da gudun rashawa. Gidansa kullum cikin jama'a yake, masu neman taimako, hannunsa a sake yake hakan ya ƙara masa farinjini. Kusan shekara biyar Safiyya na ɓari, bata haihu ba, sai da aka dage da addu'a da neman magani sannan Allah yasa ta samu cikin jikinta ya zauna, watanni tara Allah ya sa ta haihu, ta haifo ɗa namiji kyakywa mai kama da Usman sak, aka sha shagalin suna aka sanya masa suna Abubakar Sadik, sunan mahaifin Safiyya. Sadik ya taso cikin gata da kulawa, shekararsa uku a duniya, dangin Usman suka dinga mita a kan Cewar ba a kai musu Sadik, a dinga kaishi saboda ya saba da 'yan uwansa. Ba dan Safiyya ta so ba, aka haɗa kayan Sadik, aka kaishi gidan wan Usman, mai suna Aminu, sai dai kwanan Sadik biyu aka dawo da shi wai bashi da lafiya, duk ya fita hayyacinsa, aka kaishi Asibiti aka yi gwaje-gwaje aka tabattar da wani abu yaci, kwana ɗaya ya rasu, daga Safiyya har Usman sun shiga tashin hankali na gaske, wanda a sanadiyar damuwa da rashin lafiya da Safiyya tai tayi, aka gano tana laulayin wani cikin, a haka ta haifo Hafsa. Lokacin da aka haifi Hafsa, Usman Arziƙi ya ninka na baya, Hafsa ta tashi cikin gata da kulawa. A can wurin aiki, abokan aiki suka sako Usman a gaba saboda cigaba da yake samu, mussaman ta fuskar tsayawa a kan gaskiya, a dangi kuma 'yan uba na ta son ganin bayansa, banda 'yan unguwa da tasu hassadar duk da tarin kyautatawarsa a gare su. Bayan haihuwar Hafsa, Safiyya tayi ɓari yafi bakwai, wanda sai da likitoci suka bata shawarar, a ɗaure bakin mahaifarta ta haƙura da yinƙurin ɗaukar ciki saboda lafiyarta. Kasancewar Hafsa ce 'ya ɗaya tilo a wurinsu ya sanya suka ɗora mata duk wata so da ƙauna, Safiyya take ta kulawa da ita, taƙi yarda ta saki jiki ta bawa su Aminu da iyalansu 'yarta. Shekarar Hafsa goma sha ɗaya, aka yiwa Usman wani ƙarin girma, yaje Abuja aka yi walima, tun da ya dawo ya fara rashin lafiya, aka dinga yawon Asibiti amma babu wani cigaba ba a gano abinda ke damunsa ba, kullum ciwo gaba yake yi, wanda hakan ya yiwa 'yan uwansa daɗi, dan sam basu damu da halin da yake ciki ba, daga matarsa sai mahaifiyarta da wanta ne suke ta ɗawainiya da shi. Shekara guda yana jinya, Allah ya karɓi abin sa, Safiya ta shiga cikin tsananin tashin hankali da damuwa, tayi kuka kamar babu gobe, mutane aka cika gidan makoki dan an san za a ci a sha, tun kan a share sadakar uku, Aminu da 'yan uwansa Hadi da Ashiru suka fara maganar rabon gado, wani ɗan uwan mahaifinsu ya ce ai sa bari a rufa Arba'in. Kwanaki Arba'in da ɗaya da rasuwar Usman, suka zo da wani mutum wai shine Alƙali zai yi rabon gado, gaba ɗaya sun sa ran dukiya ta su ce, saboda ba shi da ɗa namiji, Safiyya ta fito da wani rubutu da yayi kan ya rasu, yayi rubutu fiye da rabin dukiyarsa ya sakata a harkar cigaban Addini, manyan kadarorinsa kuwa duk ya saye su da sunan Hafsa, ya mallaka mata su, ɗan abin da ya bari babu yawa sam. Nan fa suka ce basu yadda ba, ƙarya take ita ta rubuta, ganin suna neman su gwada mata fin ƙarfi, ya sanya ta garzaya kotu, Allah ya taimaketa Alƙali ya tabattar da wasiyyar da Usman ya bari. Bayan Safiyya ta gama idda, ta dinga samun manema, amma ta ce ita ta gama aure a kan Usman, saboda ta san ba zata samu madadinsa ba. Mahaifiyarta da ɗan uwanta suka dsge a kan dole tayi wani auren, wani mutum mai suna Musa, shi Safiyya ta tsayar, saboda yana da matuƙar kirki da halaye masu kyau kwatankwacin Usman. Sai dai su Aminu yayyen Usman na jin batun za tayi aure, suka tada husuma, wai ba za tayi aure ta kai dukiyar marainiya wani wurin a cinye ba, ƙarshe ma suka ce sai dai ta basu Hafsa, ba zata yi agolanci a wani gidan ba, ko kuma ta auri Aminu. Da suka tada masifa da tashin hankali, mahaifiyar Safiyya ta ce tayi haƙuri ta auri Aminu, ko ba komai Hafsa ba zata tashi gidan wasu ba, ba dan Safiyya na so ba ta yiwa mamanta biyayya. Bayan auren Safiyya da Aminu, yayanta shima ya rasu, ɓarayi suka tare shi a hanya, suka kashe shi, abubuwa suka sake yiwa Safiyya zafi, na rashin da tayi gaba da baya. Bayan aurenta da Aminu, ya dinga basu kulawa da tattali, duk da a gefe guda iyalansa suna nuna musu tsantsar ƙiyayya da kyara. A haka ya lallaɓa Safiyya, tayi musu gyaran gida, aka sai motoci biyu a gidan dan amfanin mazauna gidan. Ya dinga lallaɓata da kyautatawa da asiri, ya dinga karɓe dukiyar nan ɗaya bayan ɗaya, dan ba ta iya masa musu a kan komai, da ya ce ta bashi take bashi. Sai da ya tabattar ya ƙwace komai, ya shiga bushasha shi da 'yan uwansa da iyalinsa, ya fara azabtar da Safiyya da 'yar ta, Hafsa da take 'yar gata gaba da baya, ba ta san wahala ba, amma a tilas aka mayar da ita tamkar baiwa saboda wahala da ita da mahaifiyarta. Duk wata azabar aikin gidan nan suke yinta, ga hantara da wulaƙanci, Abinci sau ɗaya tal a rana ake basu, kuma Safiyya ba ta isa ta fita daga gidan ba ko wani ya zo in da take ba. A haka duk wasu alamun girma suka bayyana a tare da Hafsa, kasancewar tana da jiki, duk da wahalar da suke ciki, bai hana surarta fitowa ba. Nan samarin gidan suka fara kai mata hari, suna nema su keta mata haddi. Ta kasa gayawa Mama, sai dai tai ta kula da kanta, tana koke koke. Duk san Hafsa da makaranta ƙarshe sai da suka rabata da Makaranta. Saboda yawan kuka da Safiyya take ba ji ba gani, ya Sanya ta haɗu da wani matsanancin ciwon ƙirji, da ya haifar mata da larurar numfashi. Cikin samarin gidan nan ba wanda yafi uzzura mata, kamar Najib, Najib bashi da mutunci ko ɗa'a, ya samu dukiyar marainiya a wurin mahaifinsa kullum cikin yawo da abokai da shaye-shaye yake, bashi da burin da ya ga Hafsa yayi ƙoƙarin haɗata da jikinsa, ganin taƙi amincewa da hilatarta da yake yi, ya sanya ya fito ya ce Aurenta zai yi, yana sonta. Babansa ya ce ya bashi, sadaki kawai za'a bayar a ɗaura Aure, ai 'yar uwassa ce. Hafsa idan abu na damunta ba ta fiye faɗa ba, ita hasali ma bata magana sai ta ga dama, dan haka sai dai tayi ta faman kuka. Aka aiko wa Mama cewar mahaifiyarta babu lafiya, da ƙyar Aminu ya barta ta je, amma ya ce ba zata tafi da Hafsa ba. Haka ta rarrashi Hafsa ta shirya ta tafi, sai dai ko da taje gida, ta tarar jikin mahaifiyarta yayi tsananin, da ba zata iya komawa gida ba, ta barta a halin da take ciki ba. Har dare Mama bata dawo ba, hakan ya jefa Hafsa cikin damuwa, tun tana jiran dawowar Mama, har ta haƙura ta kwanta bacci. Cikin dare taji mutum  a kanta, tana ƙoƙarin tashi, aka danne ta ana ƙoƙarin rabatabda suturar jikinta, shaƙa mata wani abu aka yi, ba ta shaƙi abin sosai ba, jikinta yayi sanyi ƙalau ta kasa motsawa, sai gani take dishi-dishi, wani abu mai nauyi yana rinjayar kanta. Tabbas ko ba a gaya mata ta gane shi, Najib ne ba wani ba. Ba ta sake farkawa ba, sai da garin Allah ya waye, gari yayi haske, ta ji saukar ruwa a fuskarta, ta buɗe idanunta a hankali, tana kallon Mama da ke kanta a rikice tana kuka tana tambayar Hafsa meyasameta?. "Mama Najib ne" shi ne kawai abin da ta iya furtawa. Mama tayi kuka tamkar ranta zai fita ita da Hafsa, ta taimakawa Hafsa ta gyara jikinta, ta kama hannun Hafsa zuwa wurin Aminu, mahaifin Najib, ta gaya masa abin da ɗansa ya aikata. Amma ya hau bala'i, sai da ya janyo hankalin mutanen gidan, uwar Najib ta ce sun yiwa ɗanta sharri. Mama ta ce "Tun da haka ne, wurin 'yan sanda zata kai ƙara" Aminu ya hanata fita, ya cigaba da azabtar da su, kullum Hafsa cikin kuka take ita da Mama, Mama tun bata magana, har Mama ta buɗe baki ta yiwa Aminu Allah ya isa a gaban iyalansa. Babu tausayi ko imani, ya ware ƙwanji ya dinga dukanta, Hafsa taje cetonta, ya haɗa da ita da Hafsa ya dinga jibgarsu, duka na wulaƙanci kamar dabbobi sannan ya haɗawa Mama da saki uku ba tausayi ba tsoron Allah. Haka suka koma gidan da mahaifiyar Mama ke jinya, ba Abinci babu mai basu kulawa, ita ma ta zo ta rasu, hakan ya jefa Mama cikin tsananin damuwa ta haɗu da larurar hawan jini, da ya haɗu da Asma suke addabar rayuwarta tamkar zata rasa ranta. Duk da haka Najiba bai fasa bibiyar Hafsa ba, saboda rashin Kunya, Mama ta kaisu wurin 'yan sanda shi da mahaifinsa, amma yayi amfani da dukiyarsu ya toshe bakin 'yan sanda, saboda Najib, Mama ta sayar da gidan da suke ciki na mahaifiyarta, suka tashi suka koma ɗorayi, gidansu na farko da ta rayu ita da Usman farkon Auren su. Da kuɗin gidan, ta mayar da Hafsa Makaranta, sai dai Hafsa ta ƙara rasa kuzari da shiga damuwa, tun bayan Najib ya keta mata haddi. Zamansu a gidansu Najib da tashinta cikin tsnagwama da takura, ya ƙara nesanta da farinciki ko cikakkiyar walawala ba ta yi, balle fara'a. Ƙarshe suka cinye ragowar kuɗin, babu mai basu Abinci, duk da tarin alkhairan mahaifinta ga al'umma, babu wanda ya dube su bayan rasuwar su, da ƙyar Hafsa ta kammala karatun sakandare, daga baya Hafsa ta fara wannan sana'ar ta sayar da awara. Hafsa ta rushe da wani irin kuka, jikinta har karkarwa yake yi, Khalil ya yi shiru, ya kasa ko da ƙwaƙwƙwaran motsi. Ayshercool 08081012143 RUƊIN ƘURUCIYA https://arewabooks.com/chapter?id=6220844388e1ec3a041032a8 _*ƘURUCIYA: Ita ce mataki mafi hatsari da kowane ɗan Adam yake tsallakewa kan ya zama babban mutum me cikakken hankali. Sai dai wannan mataki da ɗan Adam ke tsallakewa shekaru ne masu hatsarin gaske, idan ya wuce su lafiya ana saka masa ran samun kyakywar rayuwa zuwa tsufa, idan kuwa aka samu tangarɗa rayuwa ta samu tawaya zuwa tsufa. SHIN KE UWA CE? SHIN KINA CIKIN WANNAN MATAKI NA ƘIRUCIYA HAR YANZU, KO KUWA KAI NAMIJI NE KANA DA 'YAN UWA MATA? Ya dace ki karanta wannan littafi. Rayuwar matasanmu a makarantun sakandare, hatsarin wasu al'adun bahaushe ga 'ya'yayensu mussaman mata, illar sangarta, Cutar depression, shaye-shayen matasan yara mussaman mata, dama abubuwa da baku yi zato ba, suna nan a cikin wannan littafi, ku garzaya manhajar Arewabooks don mallakar naku, ko ku kira wannan lambar don sayen naku a kan kuɗi ƙalilan 08081012143*_ Ayshercool.GABA DA GABANTA AISHA ADAM (AYSHERCOOL) To get the latest update of the story Follow me on Watpad Ayshercool 7724 Arewabooks Ayshercool 7724 What's app 08081012143 *Littafina Aƙidata da kuma Ruɗin ƙuriciya, na kuɗi ne, sauran duk free me* 20-21 Wani irin abu mai bala'in ɗaci ne, ya shiga tsirgawa Khalil tun daga maƙogwaronsa zuwa cikinsa, duk da sanyin AC dake cikin motar, bai hana shi tsatstafar da wani irin gumi ba, idanunsa suka yi jawur. Yayi shiru ya rasa abin da zai ce, sai kukan Hafsa da ya cika motar ya ke masa amsa kuwwa a cikin kunnunwamsa. Tamkar mai koyon magana ya fara shirya jimlar da zai rarrashi Hafsa da ita, sai dai suka maƙale a iya wuyansa, ya kasa furata su a kan harshensa. Da ƙyar ya iya cewa "Is ok, kukan ya isa haka, kije gida, ki samu wuri ki kwanta ki huta" Hafsa ta kalli Khalil tana son karantar wani abu a fuskarsa, amma ta kasa kasancewar, ya kauda kansa gefe. Cikin ɗan ragowar kuzarin da ya rage mata, wanda take jin tamkar ba zai iya ɗaukarta ba, ta buɗe murfin motar, ta ja ƙafafuwanta da suka gama yi mata sanyi kamar ba a jikinta ba, zuwa cikin soron gidansu, wanda duhu ya mamaye, ta durƙusa ta haɗa kanta da gwiwa ta cigaba da rera kukanta. Sai da Khalil ya tabbatar ta shiga gida, sannan sannu a hankali ya kunna motar ya bar wurin, cikin tsananin tunani da damuwa Khalil ya nufi hanyar gida. Ikon Allah ne kawai ya kai Khalil gida, saboda tuƙi yake sam hankalinsa baya jikinsa, dan lokaci lokaci ya kan daki sitiyarin motar tasa da ƙarfi yana huci. Amina ta zazzage kayan da Ammin Azima ta bata, har da kayan kwalliya, da wasu dogayen riguna da atamfa, ga kayan ciye-ciye. "Ohh ni Amina, Allah sarki ashe akwai masu kuɗi masu mutunci, matar nan har da rungumeni kamar 'yar da ta haifa, a gidan nan kuwa bayan hantara da kyara ba abin da suka saka gaba, muma Allah kai mana arziƙi na halal muyi ta jawo 'yan uwa talakawa muna ci tare. Hafsa kuwa sai da tayi kuka mai isarta, sannan ta share hawayenta ta shiga gida. Mama ta ce 'Khalil ɗin ya tafi ne?" Jinjinawa Mama kai kawai tayi, ta shiga ƙoƙarin gyara shimfiɗarta ta kwanta. "Ko dai halin naki na wulaƙanci kika yi masa ne? Naga kin dawo ba walwala jiki duk a sake" Murmushin yaƙe wanda yafi kuka ciwo Hafsa tayi ta ce "Haba Mama, ba abin da nayi masa, lafiya ƙalau muka rabu, bacci nake ji ne". "To shikenan, ba zaki ci Abinci ba zaki kwanta". "Eh, na ɗumama da safe, cikina ya ɓaci ɗazu" "To shikenan, Allah ya sawwaƙe" Hafsa ta nemi wuri ta kwanta, ta shige cikin bargo, ta ɗauko 'yar wayarta ta zuba mata ido, tana tunanin ko Khalil zai kirata a wayar, har ku san sha ɗaya na dare, ta kasa bacci tana dakon saƙon Khalil kamar yadda ya saba, amma shiru nan da nan wata karaya ta zo mata, ta sawa zuciyarta cewa Khalil babu lallai ya cigaba da sonta ko ya aureta, Gashi ta kamu da soyayyarsa ba da wasa ba. A hankali ta sanya hannu ta toshe bakinta, ta lumshe idanunta hawaye suka dinga zuba daga idanunta. "Hafsa ya naji kamar kina nishi? Ko mura kike?" "Eh Mama" "Sannu, daga yanzu idan ya zo ki dinga yi muku shimfiɗa a soro, kinga garin da sanyi sosai, har da wannan iskar ta saki mura" Hafsa ji tayi tamkar ta ce "Mama ba zai dawo ba' Amma ta ce "To" ta ja bakinta ta tsuke. Khalil juyi kawai yake a kan gadonsa, ya rasa in da zai sa kansa yaji daɗi, idan aka jima sai ya tashi zaune yayi tagumi ya rirriƙe kansa, idan ya gaji sai ya koma ya kwanta. Tunani daban daban a zuciyarsa, me yasa dangin Mahifin Hafsa suka kasance a haka? Tuna nasu dangin mahaifin yayi, yadda suke nuna musu ƙauna da soyayya, amma sam Mummy ba ta son alaƙar su da su, tabbas da sune suka tsinci kansu a halin da su Hafsa suka tsinta, ya san babu yadda za ayi, dangin mahaifinsu su wulaƙanta su haka. Gaba daya bacci ya gagari idanun Khalil, saboda damuwa. Washegari da safe ma haka ya tashi duk babu daɗi, dan haka ya kashe wayoyinsa, dan karma wani ya takura masa. Har ƙarfe sha biyu na rana ba Khalil babu dalilinsa bai fito ba, balle ya karya kumallo. Mummy ta kasa jurewa ta tafi sashin Khalil, abin mamaki ta ganshi a ƙudundune a kan gado. Da sauri ta ƙarasa tana kiran sunansa, tare da janye bargon. A hankali ya ware idanunsa a kan Mummy, sai da ta tsorata da yadda taga idanunsa sun yi jawur, jijiyoyin kansa duk sun kumbura. "Khalil lafiyarka ƙalau kuwa?" A hankali ya gyara kwanciyarsa, ya tashi zaune yana sauke ajiyar zuciya. "Magana nake maka fa, baka da lafiya ne?". "Da ciwon kai na kwana ne" "Amma shi ne baka gaya mini ba? Kalli yadda duk ka koma wani iri, kwanciyar ce zata yi maka magani? Tashi kayi wanka ka karya, muje in kai ka Asibiti". Ya ɗan ɓata fuska ya ce "Mummy ki bari ba sai naje Asibiti ba, zan warke". "A'a ban yadda ba, tashi kayi wankan, sai in kira Aliyun ya zo gida ya dubaka" haka Khalil ya tashi ya nufi banɗaki, yana jan ƙafa kamar wanda yake maye. Ko da Mummy ta koma ta tura Amina, taje ta gyarawa Khalil ɗaki ta kai masa Abinci. Wasa-wasa kan Doctor Aliyu ya zo, wani irin zazzaɓi ya rufe Khalil, ga jiri da yake ɗibansa yana daga kwance. Nan da nan kowa hankalinsa ya tashi a gidan, suka shiga damuwa Daddy da baya nan ma ya dawo gida, duk suka kewaye Khalil da Mama ta lallaɓo shi, ta dawo da shi falo ta bashi Abinci, shi ma da ƙyar ya ci ya ce ya ƙoshi. A tambayoyin da Aliyu ya yi masa, ya fuskanci kamar wani abu ne a ransa yake damunsa, amma ganin Khalil na kakkaucewa ya Sanya ya ƙyaleshi, ya rubuta allurai da ruwa ya bayar aka sayo. Ita Amina har mamaki abin yake bata, murƙusheshen ƙato kamar Khalil, amma dan yana zazzaɓi an kewaye shi, sai sannu suke masa, wanan na shafa kansa wannan na wannan, fuskokinsu duk damuwa. Suna nan zaune aka ƙwanƙwasa ƙofar falon, Amina ce ta tashi ta je ta buɗe, Abdul ta gani a tsaye. Murmushi tayi masa tare da gaishe shi, ya amsa mata cikin sakin fuska ya ce "Khalil na ciki ne? Na kira wayarsa a kashe, kuma na zo ɗakinsa tun ɗazu baya nan". Amina ta ce "Shigo gashi nan bashi da lafiya" "Subhanallah" shi ne abin da ya furta, ya shiga falon da sauri. Mummy na tozali da Abdul ta haɗe rai, haka ma Fadila, suka wani tsuke fuska tamkar sun ga kashi. Abdul ya sha jinin jikinsa, amma ya basar, ya ƙaraso ya gaida Daddy, Daddy ya amsa masa cikin sakin fuska, Mummy kuwa da ƙyar ta amsa masa, ya miƙawa doctor Aliyu hannu suka gaisa. Abdul ya ce "Daddy meya sameshi haka? Shekaranjiya mun haɗu lafiyarsa ƙalau". Daddy ya ce "Ka san shi Allah ba yadda ba ya juya lamuransa, yau dai ya tashi jiki babu daɗi, ni ban sani bama, na fita muna shirya wata seminar da za ayi da a Kano. Khalil ya buɗe idonsa ya kalli inda Abdul yake. Abdul ya ce "Khalil, sannu ya jikin" Khalil baya son yin magana, dan haka ya yiwa Abdul alama da ya matso kusa da shi. Abdul ya matsa kusa da Khalil yana masa sannu. Ya kamo hannun Abdul, ya ɗora a goshinsa, a hankali ya furta "Abdul kaina kamar zai fashe". "Sannu zai daina, ya a kai ka kwana babu lafiya baka gayawa kowa ba?" "Ka bari kawai, ka zauna a nan kusa dani" "To ina nan kusa da kai" Haushi ya kama Mummy, Fadila kuwa kallon da Abdul ke mata ne, ya sa ta ja tsaki, tana harare harare. Doctor Aliyu ya kalli Fadila ya ce "Autar Mummynta, ina abokin nan naki kuwa ya jikin nasa?" "Ya warke" ta bashi amsa. "Masha Allah, yana nan dai ƙalau ko? Ko shi ne sirikin Mummy ne?" Haushi ne ya kama Fadila ta ce "Ban sani ba" ta miƙe ta bar falon, Mummy ta bita da kallo. Ta kalli Aliyu ta ce "Wai a kan wa kake magana ne?" "Wani abokin karatun ta ta kawo mana Asibiti, bashi da lafiya yana fama da asma, shi ne nake tsokanarta". Mummy ta ɗan gimtse baki, tana hura hanci. Abdul yana nan zaune, har ruwan da aka sakawa Khalil ya ƙare, lokacin la'asar tayi, Khalil ya ce masallaci zai tafi. Mummy ta ce "Ka haƙura kayi salla a gida, saboda jirin". "A'a Mummy, zan bi Abdul" ba dan Mummy ta so ba, ta ƙyale shi. Khalil ji yayi kamar ya gayawa Abdul, halin da ake ciki, amma yaji wannan sirrin Hafsa ne, idan ya bayyana bai yi mata adalci ba. Suka je suka yi salla, Abdul ya ɗau Khalil zuwa wurin da suke zuwa shan fura, dan yaji daɗi, ya bawa Abdul labarin abin da dangin Mahaifin Hafsa suka yi musu, amma ya ɓoye masa batun fyaɗen nan. Ya ɗora da cewa "Abdul, nayi mamakin jin yadda dangin mahaifinta suka yi musu haka, dangin Daddy nake tunawa, irin karamcinsu da soyayyarsu a garemu, danma Mummy ba ta son alaƙarmu da su". Abdul ya ce "Khalil, lokaci yayi da yakamta ka cigaba da zumunci da dangin mahaifinka, ko da Mummy ba ta sani ba". "Ka san wani abu, ina ganin zan shigar da ƙarar yayyane mahaifin Hafsa a ƙwato musu hakkinsu". Abdul ya ce "A'a Khalil, bakomai ne ake amfani da dukiya ko ƙarfi wurin ƙwatarsa ba, ka mayar da hankali wurin mallakar yarinyar, da kyautata musu, su bar su da Allah kawai, ba abin da dukiyar zata amfana musu, dan ba guminsu bane a banza zasu kaɗar da ita". "Abdul, ji nake tamkar in nemo yaron nan da ya kai Hafsa wurin 'yan sanda in kashe shi" a razane Abdul ya kalleshi ya ce "Kayi hauka ne kake zancen zaka kashe wani, me yayi maka?" Taune lips ɗinsa na ƙasa yayi, yana jin yadda zuciyarsa ke wani irin lugude, kansa na sarawa, yayi shiru bai kuma cewa komai ba. Ba dan Hafsa na gudun kar Mama ta gane wani abu na faruwa ba, da ba zata fita wurin sana'ara ba ma, haka ta fita wurin sana'ar nan sama sama haka take, loka lokaci tana duba wayarta, ko zata ga kiran wayar Khalil ko saƙonsa, amma shiru ba ta gani ba. Hakan ya ƙara jefata cikin damuwa da karaya, ta saddaƙar Khalil ya rabu da ita kenan, ba zai iya ɗaukar ƙaddarar da Allah ya jarabceta ba. Gashi wani irin son Khalil take ji a ranta. Khalil ya ɗan samu sauƙi, amma sam ya kasa kunna wayarsa, saboda gaba ɗaya kaɗaici yake so baya son damuwa sam, saboda ciwon kai da yake damunsa haryanzu, duk da tunanin Hafsa da tausayinta sune suka haifar masa da halin da ya tsinci kansa a ciki, yana son ya kirata a waya yaji ya take, amma ganin idan ya kirata bai san me zaice mata ba ya sanya ya fasa kiran nata. Amina ta lura ƙarfe bakwai saura, Daddy ya ke shiryawa ya fita, ko karyawa ba ya yi. Ƙarfe shida saura tana kitchen tana aiki, taji motsi a falo, dan haka ta fito falon, Daddy ta gani yayi shirin fita, sai zuba ƙamshi yake. "Daddy ina kwana" ya ɗaga idonsa ya kalli Amina, dake tsaye tana kallonsa. "Lafiya ƙalau" ya amsa mata. "A kawo breakfast ne? Naga zaka fita baka karya ba". "No, ina daf da makara, ba saina karya ba". "Ok, bari in kawo maka mota, sai ka tafi da shi". "Ok, shikenan" Amina ta koma kitchen, ta haɗo Abinci a cikin kwanuka ta saka a kwando, ta kaiwa Daddy mota. Mama tana banɗaki tana wanka, Hafsa ta saka wayarta a gaba, tana ta gursheƙen kuka, sam ba ta san Mama ta fito daga wanka ba, sai ganin Mama tayi a tsaye a kanta. Da sauri ta wayance ta fara ƙoƙarin goge hawayen. Mama ta ce "A'a, ai ba sai kin wayance ba, kin san adadin lokacin da na ɗauka atsaye a kanki? Ni dama a kwana biyun nan tun da muka dawo daga Asibiti naga kamar kina cikin damuwa, sai dai bana son takura miki ne, saboda ke idan baki ga dama ba mutum in zai mutu, ba zaki faɗa masa damuwarki ba. Yanzu gaya mini meye dalilin wannan kukan?". "Mama bakomai". "Bakomai Hafsa, ba zaki gaya mini ba kenan, me kike kallo ko kike jira a wayar da kika sata a gaba kina kallo?". Bata san lokacin da ta sake rushewa da kuka ba, tare da faɗin "Mama Khalil". Mama ta zauna kusa da ita ta ce "Meyafaru da Khalil ɗin?". "Mama na gaya masa, be sake kirana ba, ina ga ba zai iya aurena a haka ba, Mama ba zan taɓa yafewa dangin mahaifina ba, sun mini mugun tabo, ba kowa zai yadda da ni ba" Jikin Mama yayi sanyi ƙalau, ta rungomo Hafsa a jikinta, ta runtse idanunta hawayen tausayin Hafsa na tsiyaya daga idanunta. "Taki ƙaddarar kenan Hafsa, a haka Allah zai baki wanda zai so ki a haka, ki daina kukan nan" ƙanƙame Mama Hafsa tayi, ta cigaba da rusa kuka tamkar wadda uwarta ta mutu. Sai bayan la'asar Sannan Alhaji Ahmad ya dawo gida, da Amina ya fara tozali, tana kunna wa falo turaren wuta, tana sanye da doguwar rigar atamfa, ta ɗaura ɗankwalin atamfar. "Sannu da zuwa" ta faɗa cikin girmamawa. Ya amsa mata da cewa "Yauwa sannu, ga kwanukan ki can a mota, kije ki ɗauko na gode sosai". "To Daddy, bari in gama kunna turaren zan ɗauko" ta cigaba da zaga falon, dan ko ina ya samu ƙamshin turaren, ya nufi sashinsa kai tsaye. Sai da Khalil ya kwana uku, sannan ya samu ya rabu da wannan matsanancin ciwon kan, ya ɗan ji ƙwarin jikinsa, yaji ba abin da yake buri banda ya ga Hafsa. Da magariba ya shirya cikin ƙanan kaya, ya sha turare bai ko tsaya yiwa Mummy sallama ba, saboda baya son ta tutsiye shi da tambayar ina za shi?. Fadila na ɗakinta, tana game a waya, Mummy ta shigo tana ɗan tsareta da ido. "Mummy ya dai?" "Wace maganar na ji doctor Aliyu yana yi ɗazu?" "Wace magana kenan Mummy?" "Wa kika kai Asibiti?" Fadila ta ce "Ba wani bane, wannan Yazeed ɗin ne da nake baki labari" "To meye haɗinki da shi da zaki kai shi Asibiti? Nifa bana son jaye-jaye me haɗin kanwa da kuka?" "Mummy, bani da wata alaƙa da shi, bani da wani zaɓin da ya wuce in kai shi Asibiti Mummy, na taimaka masa ne saboda.. "Saboda me? Wanene ɗinki shi?" "Mummy matsalata da ke saurin ɗaukar zafi, ki tsaya ki saurareni Mummy, da ban yi hakan ba da tuni ina nan ina rama azumi sittin". Mummy ta ce "Kamar yaya?" Nan ta warwarewa Mummy abin da ya faru, ta ɗora da cewa "Shi ne saboda son gulma yake wani tambayata a gabanki, ni babu wata alaƙa tsakani na da Yazid". "To ai shikenan, duk da haka a dai kiyaye, dan ba zan amince a kawaso mini gayyar tsiya cikin zuriya ba". Fadila tayi murmushi ta ce "Mummy kenan, ki sha kuruminki, ai nima na san ni ba kalar talaka ba ce" "Ƙwarai kuwa, ai mun tattauna da Hajiya Turai, akwai ƙaninta da ya taɓa ganin hotonki ya ce mata yana sonki, a U.K yake aiki, ina jiran ya dawo ne tukua kan in sanar da ke, sai kuma Allah ya kawo hira na ke gaya miki" Yamutsa fuska Fadila ta yi, taƙi magana. "Ya kika yi shiru?" "To Mummy me zance? Ni dai in bai mini ba, ba ruwana da wata U.K" "Ke dalla can, zai ma yi miki" Fadila ta ɗan taɓe baki, sai dai kawai taga fuskar Yazeed na mata gizo. Har Mummy ta ƙarasa surutanta ta fita daga ɗakin, ba wani gane me take faɗa take ba. Wayarta ta miƙa hannu ta ɗauko, ta ci karo da saƙon Kankiya, da yake addabarta da su. Wani uban tsaki ta ja, ta kashe wayar, maganar Yazeed na ƙoƙarin zamowa gaskiya, Sir Kankiya sonta yake yi. Ɓangaren Hafsa kuwa, wunin da tayi koke koke ita ma ya sanya, ciwon kai ya kamata, dan ko wurin sana'ar ba ta fita ba, ta kasa cin abinci sai aikin rarrashi da Mama take yi. Wayarta ce ta ɗan yi vibrating, ta miƙa hannu ta duba.   Message ne. "Ina waje" Da sauri ta tashi zaune ta ce "Mama, Khalil ne wai yana waje" Mama ta ce "Alhamdilillah" da sauri Hafsa ta tashi zata zari hijjabi. "Haba ke kuwa, kije ki wanke wannan kumburarriyar fuskar ta ki, ki canza wasu kayan mana" Cikin azama Hafsa ta je ta wanke fuskarta, jiki na rawa ta fara neman kayan da zata sauya. Tausayin Hafsa ya kamata, tabbas Hafsa ta kamu da son Khalil sosai. Ta ɗau dadduma ta nufi hanyar fita har da tuntuɓe. Yana tsaye a jikin motarsa tana ganinsa ta tsaya cak, tana kallonsa. "Shi ne kika shanya ni, da juyawa zan yi in koma ai" Kawai ta fashe da kuka. Khalil ya ce "Subhanallah, Kuka kuma? Me nayi?" Kuka take sosai, ta kasa cewa komai. Ya karɓi sallayar hannunta, ya shimfiɗa a kan dakalin gidan, sannan ya zaunar da ita, ya fuskanceta "Am sorry, na tafi ban kuma kiranki ba, bani da lafiya ne, baki ga na rame ba?" "Na zata ba zaka dawo ba" ta faɗa cikin kuka. "Baby me zai hana ni dawowa?" Magana take son yi, amma ta kasa. Khalil ya gyara zamansa ya ƙara matsawa kusa da ita ya ce "Ya isa haka dan Allah, so kike ki kuma sani a damuwa? Ki daina Please" da ƙyar ya samu ta sassauta kukan da take ta ce "Na zata ka daina sona ba zaka dawo ba, saboda abin da na gaya maka, ko kana ganin ƙarya nake yi". "Haba Hafsa, Wallahi ba haka bane, labarinki ya tsma zuciyata to the extent tun da na bar wurinki bani da lafiya, sai yau na samu sauƙi. Ina da ƙanwa mace, mai rawar kan tsiya da tsiwa, sai dai idan makamanciyar ƙaddara irin taki ta sameta wani ya muzanta ta yaƙi aurenta, ko ya ce ƙarya ne abin da ya sameta bai mini adalci ba, Saboda na fi kowa sanin halinta, duk rashin jinta, tana da kamae mutuncinta, kwatankwacin yadda kike. Meyasa zan ƙi dawowa gareki, dan wani abu da kika rasa a sanadin ƙaddara wanda ko ni ɗin ne na karɓe shi, iya na lokaci ɗaya ne, kyawawan ɗabi'unki da halayarki da su zan rayu tsawon rayuwata?. Matasa da yawa bama yiwa kanmu adalci, wurin zubar da mutunci da ƙimarmu kan mallakar abin da Allah ya halarta mana na aure. Sai dai akwai tsautsayi da ƙaddara, abin da kika gaya mini na yarda ɗari bisa ɗari, kuma ni banji cewar zan iya rabuwa da ke saboda haka ba, ina son ki Hafsa, kuma ni aurenki zan yi, dan Allah ki daina wannan kukan" "Dan Allah haryanzu kana sona?" Tayi maganar tana kallonsa. Yayi mata murmushi ya ce "Ina sonki mana, kema kina sona?" Murmushi take haɗe da hawaye ta ce "Na zata ba zaka dawo ba ka daina sona, shiyasa nayi ta kuka" "Allah sarki Sweetheart ɗina, ni damuwa ce ta sani rashin lafiya, na kashe wayoyina, amma kina zuciyata am sorry for not hearing from me" Hannayenta biyu ta haɗa a fuskarta ta cigaba da kuka. "Babu ya isa haka mana, ki daina kukan nan mana" "Kukan farinciki nake ka ƙyaleni" Murmushi yayi ya ce "Dole ki kuka, Allah ya azurta ki da ɗan shawalwalin saurayi kamata, ɗan beauty da ni" Murmushi tayi, duk da akwai hawaye kwance a fuskarta. "Yanzu gaya mini, kina sona?" "Sai nayi shawara" ta faɗa tana dariya, wadda ke ƙara mata kyau. "Kin ma isa? Sai kin faɗa ai". "Ina sonka Ibrahimul mu'azzam" ta faɗa tana kauda kanta gefe guda. "Alhamdilillah, Masha Allah, bana jin ko Daddy da ya raɗa sunan nan, ya taɓa daɗi a bakinsa kamar yadda ya yi a naki bakin, Ibrahimul mu'azzam. Kai amma na sha gwagwarmaya kan in shawo kan wannan Japanese baeb ɗin" "Nice Japaneese ɗin kuma?" "Eh mana, My Japanese doll" murmushi suka yi gaba ɗaya, Khalil ya dinga kwantar mata da hankali, da sake bata tabbacin iya wuya, zai aureta yana tare da soyayarta. Suka kasance cikin nishaɗin da sai da ya wanke musu zukatansu daga dukkanin damuwowin da suke ciki. Khalil ya nisa ya ce "Ina ga idan na sake dawowa, zan shigar da ƙarar dangin mahaifinki, in ɗaukar muku lawyer, a ƙwato muku hakkinku. Hafsa ta girgiza kai ta ce "A'a, ni bana son duk wani abu da zai sake haɗamu da su, mun barwa Allah, wanda ya tara dukiyar ma yau yana ina? Allah ya karɓi abunsa, ni fatana Allah ya bamu mafita kawai" "Allah sarki babyna, insha Allah very soon zan aureki, mu wuce wurin nan, sonake ai komai da komai a abinda bai wuce 6months ba" Hafsa ta ce "Kai, yayi wuri da yawa ai". "Ba wani wuri, amfanin soyayya aure, sai munyi aure za muyi soyayya ta gaske" "Ni ban isa aure ba" ta faɗa a shagwaɓe. "To ni na isa, ki bari idan muka yi auren, sai mu gani in dagaske baki isa auren ba" Jin Khalil zai ɓaro magana ya sanya ta ja bakinta ta tsuke.   Kayan ciye-ciye ya bata, tare da bata saƙon gaisuwar sa zuwa ga Mama, ya yi mata sallama ya tafi. Ba kowa a falo, sai Daddy yana ta aiki a computer, Amina ta hango hasken lantarki a falo, ta fito falon da nufin ta kashe wutar, ta tarar da Alhaji Ahmad yana ta aiki a kan system. Komawa tayi kitchen, ta yayyanka fruit ƙanana, ta ha ɗa cofee, ta ɗoro a plate ta fito falon. "Daddy sannu da aiki" Ya ɗaga kai ya kalleta ya ce "Yauwa sannunki" Ta ƙarasa ta ajiye tray ɗin a gabansa ta ce "Ga wannan naga kana ta aiki" "Masha Allah, na gode sosai kuwa" "Ba komai" ta juya zata koma ya ce "Yauwa, an kirani daga makarantarku ɗazu, sun ce kije ranar Saturday" "Ok Allah ya kaimu, zan je insha Allah" "Good". "Gobe in Allah ya kaimu ma da wuri zaka fita?" Daddy ya ce "Eh da wuri zan fita muna seminar ne" "Ok, to shikenan sai da safe" Ta juya ta nufi in da ɗakinta yake, ta ci karo da Hajara a tsaye tana binta da kallo. Shareta Amina tayi ba tare da ta kula Hajara ba, ta wuce ɗakinta tare da faɗin "Kema Allah zai mini maganinki" RUƊIN ƘURUCIYA https://arewabooks.com/chapter?id=6220844388e1ec3a041032a8 _*ƘURUCIYA: Ita ce mataki mafi hatsari da kowane ɗan Adam yake tsallakewa kan ya zama babban mutum me cikakken hankali. Sai dai wannan mataki da ɗan Adam ke tsallakewa shekaru ne masu hatsarin gaske, idan ya wuce su lafiya ana saka masa ran samun kyakywar rayuwa zuwa tsufa, idan kuwa aka samu tangarɗa rayuwa ta samu tawaya zuwa tsufa. SHIN KE UWA CE? SHIN KINA CIKIN WANNAN MATAKI NA ƘIRUCIYA HAR YANZU, KO KUWA KAI NAMIJI NE KANA DA 'YAN UWA MATA?  Ya dace ki karanta wannan littafi. Rayuwar matasanmu a makarantun sakandare, hatsarin wasu al'adun bahaushe ga 'ya'yayensu mussaman mata, illar sangarta, Cutar depression, shaye-shayen matasan yara mussaman mata, dama abubuwa da baku yi zato ba, suna nan a cikin wannan littafi, ku garzaya manhajar Arewabooks don mallakar naku, ko ku kira wannan lambar don sayen naku a kan kuɗi ƙalilan 08081012143*_ Ayshercool. 08081012143 AyshercoolGABA DA GABANTA AISHA ADAM (AYSHERCOOL) P22-23 Arewabooks Ayshercool7724 Amina ta shige ɗakinta, ta cigaba da saƙa da warwara a cikin ranta, daga bisani ta tashi ta hau gyaran kayanta, dan ba ta jin bacci sam, ita wannan hutun duk ya isheta so take ayi a koma makaranta.   Kamar yadda Daddy ya gaya mata, ranar asabar ta shirya ta tafi makaranta, taje ta tarar Quiz ne aka yi musu, domin fitar da gwanayen da za'a tafi da su Abuja, wurin yin babban Quiz na ƙasa. Suka gabatar da quiz, da kuma mini exam da aka yi musu, wanda iyayensu suka je, suka karɓar musu results ɗinsu, Amina na ji tana gani, haka ta dawo gida ba a bata result ɗin ta ba, haka ta dawo gida duk ranta babu daɗi. Khalil jinsa yake tamkar an masa bushara da wani abu na musamman, wata irin Soyayya da shaƙuwa ce suka shiga yi a tsakaninsa da Hafsa, a haka hutunsa ya ƙare, ya koma wurin aiki, cike da kewar Hafsa. Ya labartawa Abdul yadda yayi nasara, Hafsa ta karɓi soyayyarsa, Abdul ya taya shi murna sosai, sai dai a ransa yana tausayawa Khalil gwagwarmayar da zai sha da mahaifiyarsa kan ta amince. Hutunsu Fadila ya ƙare, ji take tamkar ta ɗora hannu a ka tayi kuka, dan sam bata son stress da takurar makaranta. Wannan semester da sabuwar mota dal ta koma school. Bayan ta ƙara kusan kwanaki uku a kan hutun nasu. Kwanaki ukun da ba ta zo ba, har an yi wasu lectures ɗin bata nan. Haka kawai ta fara waige-waige a ajin, ko zata hango Yazid, amma sam ba ta ganshi ba, tana cikin tunanin ko shi ma bai dawo hutun bane, Kankiya ya shigo ajin. Yana shigowa ta haɗe rai, dan ko san ganinsa ba ta yi, tun da ta fara ganin zancen Yazid na daf da zama gaskiya, saboda yadda yake uzzura mata da saƙonni, da kuma kiran waya ba gaira babu dalili.   Har kankiya yayi lectures ya gama yana satar kallon Fadila, da ba kowa ne ya san yana mata ba, sai ita ɗin da ya addabawa da ido. Amina na zaune a gaban TV stand, tana gogews, aka turo ƙofar falo haɗi da sallama. Ta ɗaga kai tana amsa sallamar. Hajiya Turai ta gani a tsaye, ta gama ƙarewa Amina kallo daga sama har ƙasa, tana sanye da doguwar riga ta ɗaura ɗankwalin atamfar, kai ba ka ce 'yar aiki ba ce. Ta ɗan taɓe baki ta ce "Hajiya Zainab na nan ne?" Amina ta ɗan kalleta ta ce "Eh tana nan, ki zauna yanzu zata fito". Hajiya Turai za tayi magana, sai ga Hajiya Zainab ta fito cikin shiri, da alama fita za tayi. "Hajiya Turai, har kin ƙaraso?". "Eh, yanzu na shigo ashe ma kin shirya" "Wallahi kuwa, ai na san ba kya son jira, bari muyi mu tafi" ta mayar da hankalinta kan Amina ta ce "Ki kula mini da gida da kyau, ki kammala girki da wuri, bana son Fadila ta dawo ba a gama girki ba". "To insha Allah" Amina ta faɗa cikin girmamawa. "Wai ni kuwa Zainab, haka kika bar Yarinyar nan tana miki yawo a gida, ga mijinki ga ɗanki, ba zata dinga saka hijjabi ba, naga wancan zuwan da muka yi da hijjabi a jikinta, tafa fara girma kalli ƙirjinta a cike fam, kalli ƙugunta" Amina a ranta ta ce "Ji 'yar bala'i har ta ga ƙirjina, ta rasa in da zata kalla sai nan, wannan ai iskanci ne, tubarkallah". Mummy tayi wata dariyar ƙeta ta ce "lallai Turai kin manta wacece Zainab ne, Ai Alhaji Ahmad na riga na zame masa teku, na sha kansa ba yadda ya iya da ni, gidan nan daga ni sai 'ya'yana, da can bai ƙara aure ba sai yanzu da girma ya kama shi, Khalil kuwa shima ya san bai isa ya kawo mini jinin babu cikin zuriyata ba" Sukayi dariya tare da yin shewa suka fice. Kwaɓe baki Amina tayi, ta cigaba da aikinta a ranta ta ce "Ko ni me zanci da dattijo ma oho, in banda tsautsayi wa zai auri jinin wannan matar ko ya auri mijinta, bala'inta ya ishi mutum?' ƙarshe dai Amina ta manta da batun Hajiya Zainab, ta fara tilawarta tana yi tana aikinta.   Ta kammala goge gogenta, ta miƙe zata bar wurin, tayi ido huɗu da Alhaji Ahmad, da ke tsaye yana kallonta. Shan jinin jikinta tayi kamar mara gaskiya, ta ɗan diririce, dan sam ba ta zata yana gidan ba. "Ina kwana" ta furta tana kauda kanta gefe. Bai amsa mata ba ya ce "Kawon breakfast" "Ai ban san kana gida ba, an cinye komai sai dai in wani abun zan dafa maka" "No, haɗo mini coffee kawai, ina da biscuit sai in haɗa" yana gama maganar ya juya ya bar wurin. Mamaki ne ya kamata, babban mutum kamar wannan ya ce zai karya da biscuit. Kitchen ta nufa, cikin azama ta fara feraye dankali. Hajara ta shigo kitchen ɗin ta sameta tana gyara dankali. "Amina me kuma zaki da dankali?" "Babansu Fadila ashe yana gida, hajiya ba ta yi mana bayani ba, ba a yi breakfast da shi ba, shi ne nake haɗa masa" "Yayi" shi ne abin da Hajara ta ce ta bar kitchen ɗin. Nan da nan Amina, ta dafa tea da dankali, ta haɗa a tray ta tafi kai masa, sai dai ta shiga tunanin ina zata kai masa?. Ta yanke shawarar kai masa kan dining, taje ta ajiye ta cigaba da sabgoginta, sai kuma ta tuna ba yadda za ayi ya san ta kai masa, idan ba gaya masa tayi ba. Cike da faɗuwar gaba, ta nufi part ɗinsa, ta shiga da sallama, yana zaune a falonsa yana kallon labarai. Bai waiwayo ba ya amsa mata. Cikin ladabi ta ce "Ga Abincin can a kan dining". "Kawo min nan" ya faɗa a taƙaice. Amina ta ɗan yamutsa fuska ta koma falo, tana mitar Alhaji Ahmad ya fiye mulki, sai dai shi baya wulaƙanci kamar matarsa da 'ya'yansa, sai dai miskili ne na gaske. Da sallama ta koma falon, taje gabansa da tray a hannu ta tsaya, ta kalli kan Centre table ya miƙe ƙafafuwansa a kai, ta wuce Kan dining ɗin dake falon, ta ajiye masa. Har ta juya zata fita a hankali ya ce "Nan zaki kawo mini" Amina ba ta san lokacin da tura baki ba, ta sake ɗauko trayn ta dawo gabansa, ta kalli ƙafafuwansa dake kan Centre table, in da yakamata ace ta ajiye kayan Abincin. "To a ina zan ajiye?" Tayi maganar tana satar kallonsa, dan ba ƙaramin kwarjini yake da shi ba. Shareta yayi, ya cigaba da latsa remote ɗinsa. Ta ajiye a saman carfet, ta juya zata fita "Zo nan" ya faɗa ba tare da ya kalli in da take ba. Ta dawo ta tsaya. Ya sauke ƙafafuwansa daga kan Centre table ɗin, yayi mata nuni da ido, a kan a nan zata ajiye masa Abincin. Kamar Amina ta fasa ihu, dan ta ƙulu sosai, haka ta ɗau tray ɗin ta ajiye a kan table. "Come back in the next 30minutes" ya faɗa yana gyara zamansa. Amina ta bar falon tana "yau naga tsiya da wasali, da iko da mulkin mulaka'u na masu kuɗi, a haka kamar na Allah ashe shima ya iya tsiya, aikuwa ba zan koma ba" ta leƙa ɗakin Hajara ta ce "Mai gidan nan ya ce kije nan da mintuna talatin" Hajara ta zare ido, ita a zamanta a gidan nan banda gaisuwa ba abin da yake haɗata da Alhaji Ahmad, ko aiki baya sata, me zai sa ya ce ta je? "Amina  nayi laifi ne?" "Nima ban sani ba, ya ce dai kije" A rikice Hajara ta ce "Na shiga uku Allah ya sa ba korata zai yi ba ni Hajara" Amina ta koma ɗaki abin ta, yayin da Hajara ta tasa agogo tana lissafin mintuna talatin cikin zullumin rashin sanin dalilin kiran da mai gidan yake mata. Sai da Hajara tayi Addu'oi sosai sannan ta tunkari sashin Alhaji Ahmad. Tayi sallama ya amsa mata, ta ƙarasa ta shiga falon, ta zube a ƙasa ta ce "Alhaji gani, Amina ta ce kana kirana". Da mamaki ya kalli Hajara ya ce "Ni kuma?" "Eh haka ta ce mini, tun ɗazu ta ce bayan mintuna talatin kana kirana" ya ɗan yi shiru tare da jinjina kai ya kalli Hajara ya ce "Kirawo mini ita" Hajara ta koma ta kirawo Amina, sai dai bata ɗakinta, sai da tai ta dubawa ta ganota a ɗakin Fadila tana gyara mata. Nan Hajara ta isar mata da saƙon Alhaji Ahmad na kiranta da ya yi. Sai kuma a lokacin ita ma cikinta ya ɗuri ruwa, sumi-sumi tabi bayan Hajara suka koma falon Alhaji Ahmad. Ya kalli Hajara ya ce "zaki iya tafiya" Sai a lokacin Amina ta ga tayi wauta, ya mayar da hankali ya cigaba da kallon TV, tamkar bai san da wanzuwar Amina a wurin ba. Amina tun tana sanya ran zai kulata, har ta sare gashi ta gaji da tsayuwa, ya ɗago ya kalleta, yayi mata alama da ta je gabansa. Ba musu ta je in da yayi mata nuni. "In zauna?" Ta faɗa a raunane. Ya ɗaga manyan idanunsa masu matuƙar haske da kwarjina, ya tsareta da idanunsa ya ce "Na ce ki dawo in the next 30minutes, amma kin turo mini wata, kin kyauta kenan? Ko kuma kin san dalilin kiran?" Amina ta ɗaga kai ta kalleshi, amma tayi saurin janye idanuwanta ta ce "Dan Allah kayi haƙuri, nima sai da ga baya na ga nayi laifi, kayi haƙuri" "Kwashe kwanukan nan, kije ki dawo, ko bana falon ki jirani" ta amsa masa da to, ta kwashe kwanukan ta fita sai dai tana zuwa kitchen ta tarar Hajara na tsaye na jiran dawowar ta. "Amina me ya ce miki? Naga kin daɗe" haɗe rai Amina tayi tana tura baki taƙi kula Hajara, ta lura kwanakin Hajara ta koyi munafunci da sanya ido. Ko da ta koma Alhaji Ahmad baya falon, dan haka ta zauna a kan carfet tana jiransa, dan bata manta kashedin Hajiya Zainab ba a game da zaman kan kujera ba. Ta daɗe a zaune, sai ga Alhaji Ahmad ya fito, sanye cikin wani baƙin yadi, ya haska yadin kasancewarsa fari, sai zuba ƙamshi yake yi. Yaje ya buɗe wata drower ya tako in da Amina take, wadda tuni ta miƙe tsaye, ba tare da ya kalleta ba ya ce "Ranar Sunday in Allah ya kaimu, zani wani ɗaurin Aure haɗeja, ƙarfe shida da rabi zan fita, a ɗan sama mini abin da zan ci kan in tafi" Kamar mara gaskiya Amina ta sunkuyar da kai ta ce "To, insha Allah" "Karɓi nan" Ya miƙa mata envelope ɗin hannunsa. Ta ɗago ta kalleshi sannan ta kalli envelope ɗin, amma ta kasa karɓa. "Karɓi mana" yayi Maganar yana sake miƙa mata. Jiki a sanyaye ta sa hannu ta karɓa, ganin tambarin makarantarsu a jiki ne, ya sanya hankalinta ya ɗan kwanta. "Buɗe da sauri, zan fita" jiki na rawa Amina ta fara kokowa da envelope ɗin, tana ganin takarda ta san result ne, aikuwa gabanta ya faɗi, hannunta ya hau rawa. "Ko ba kiyi abin Arziƙi bane, kika tsorata haka?" Bata san lokacin da ta ɗaga masa kai ba alamar eh. "To ciro mu gani" ya faɗa yana cigaba da tsareta da ido. Ta zaro paper, ta shiga dubawa duk grades ɗinta A ne, First position ta gani a jiki. Wani irin farinciki mara misaltuwa ya ziyarci zuciyarta, ta ɗago ta kalli Alhaji Ahmad fuskarta ɗauke da murmushi, ga hawaye a lokaci guda na farinciki da suka zubo mata a kan fuskarta, a kan gwiwarta ta zube ƙasa tana kallonsa. "Yadda ka faranta mini, ta hanyar maida ni makaranta, Ubangiji Allah ya faranta maka, ya sa ranar alkiyama ka karɓi littafinka a hannun dama" har cikin kansa addu'a da tayi masa ta tsirga masa. "Ameen ya Allah, Na gode tashi tsaye" A hankali ta miƙe tana cigaba da share hawayen fuskarta. "Makarantarku sun kirani, naje na karɓo result ɗin ki, nayi farinciki sosai da yabon da suke miki, na ƙoƙari da jajircewa, sai dai an ce ba kya jin magana haka ne?" Amina ta sunkuyar da kai alamar a'a. "Ya zaki ce a'a bayan nima kinyi na gani" "Dan Allah kayi haƙuri na daina, kar ka gayawa Baba" "Anyway, an sanar da ni cewar kin ci wannan jarrabawar da suka yi muku, 15th December in Allah ya kaimu, zaku je Abuja, wurin baban Quiz na ƙasa da sauran festival da ake yi na makarantu, zasu fara yi muku lessons na mussaman" Amina ta ɗan yi jimm, da ta san abu ne mawuyaci Baba ya barta taje Abuja, amma ta dake tayi murmushi ta ce "Allah ya kaimu, na gode sosai Allah ya ƙara buɗi yasa ka fi haka, inje in nunawa Baba result ɗin?" Ya jinjina mata kai. Ta juya da sauri ta bar falon. A harabar gidan ta tarar da Baba da Zakiru direban Alhaji Ahmad, suna hira, da fara'arta ta tunkaresu, ta miƙawa Baba takardar hannunta. Ya karɓa tare da kallonta ya ce "Uwata menene wannan?" "Baba sakamakon jarrabawata ne, ka duba ka gani". "To ai kin san sai dai ki karanto mini". "Baba ta ɗaya na zo, duk ajinmu na fi kowa maki" Baba ya faɗaɗa murmushinsa yana faɗin "Alhamdilillah, dama na san uwata ba zata bani kunya ba" Zakiru ya karɓi result ɗin yan dubawa, ya murmusa ya ce "Baba Hassan lallai wannan 'yar taka ƙwaruwa ce, Allah ya dafa 'yar gidan Babanta" Amina tayi murmushi ta ce "Amin Malam Zakiru na gode sosai, ka mini alƙawarin cigaba da koya mini karatun addini, amma haryanzu ka ƙi saka lokaci" Zakiru ya ce "Ba ƙi nayi ba Amina, kinga yanayin aikin namu, wasu lokutan nike kai Alhaji duk in da za shi, idan ba haka ba kuwa gyaran harabar gidan nan kaɗai da aike ta isa ɓata lokaci. Kuma da zarar sun ga muna karatun nan za'a iya tsiro wani abu daban, amma insha Allah zan saka mana lokaci" "To shikenan, na gode sosai" Alhaji Ahmad ne ya fito harabar gidan, Zakiru ya nufi in da motarsa take, dan shi zai fita da shi. Baba kuwa ya nufi Alhaji Ahmad, ya cigaba da yi masa Addu'a da godiya. Alhaji Ahmad ya ce "Ba komai, ai ɗa na kowa ne, naji daɗi sosai kaga zan cigaba da samun ƙwarin gwiwar biyan kuɗin makarantar, tun da tana abin da ake so" Baba ya ce "Haka ne, Allah Ya ƙara arziƙi" Ya amsa da Ameen ya nufi mota. Yau da azahar Fadila ta dawo gida, duk da Sir Kankiya yayi ƙoƙarin ganawa da Fadila a Office ɗinsa, dan har ya tura mata saƙo yana son ganinta a Office ɗin sa, amma ta share tayi tafiyarta, dan zuciyarta raya mata take taje ta tatala masa rashin mutunci, dan ta fara gajiya da takurar  da yake mata. Haka nan take mamakin meye ya hana Yazid dawowa Makaranta. Amina tayi farinciki sosai da sakamakon ta na makaranta, ta fara ƙoƙarin cigaba da hora kanta a kan darrussan kimiyya, tun kan a neme su a makaranta, a fara yi musu lesson. Amina ta rage jin haushin Alhaji Ahmad a kan abin da iyalansa suke mata da kuma shima abin da yayi mata. Ranar lahadi tun da ta idar da sallar Asubahi bata koma ba, ranar lahadi da su da masu gidan basu fiye tashi da wuri ba, saboda ba wanda yake fita a ranar. Amina ita kaɗai ce idonta biyu, ta ɗora girki saboda Alhaji Ahmad zai fita. Kan ƙarfe shida da rabi, Amina ta kammala girkin, har ta tsaftace falo ta kukkuna turaren wuta. Tana ta sake goge kan dining, sai hamma take, saboda baccin da take ji. "Sannu da aiki" ta jiyo muryarsa. da sauri ta waiwaya, ta kalli in da yake tsaye "Ina kwana" ta faɗa tana ɗan lumshe ido. Maimakon ya amsa sai ya kuma maimaita mata "Sannu da aiki". Ta fuskanci baya son yayi magana a share, dan haka ta ce "Yauwa na gode, ga breakfast ɗin". Alhaji Ahmad ya ƙarasa ya zauna, ya kalleta ya ce "Afuwan na katse miki bacci" ta ɗan girgiza kai ta ce "Bakomai" Ya bubbuɗe flask ɗin, yayi mamakin ganin ƙosai da soyayyen dankalin Hausa, da kuma koko. Kawai sai ta ga murmushi ya mamaye fuskarsa. "Ke kika yi girkin nan?" Haka nan Amina ta tsinci kanta da tura baki, to wa yayi idan ba ita ba, saboda kawai ya raina mata hankali yake tambayarta. "Hajiya am talking to you" "Eh nina girka" Ya jinjina kai, ya zuzzuba ya fara ci, yaji daɗin girkin nan sosai, yana son Abincin gargajiya sosai da sosai, amma sam Hajiya Zainab bata so, gashi na wuraren sayarwa baya masa daɗi sam ko a Lagos haka nan yake maleji ba daɗinsa yake ji ba. Ya tsare Amina ya hanata tafiya, sai da ya gama, ta kwashe komai, sannan ya tashi zai tafi, Amina ta bi bayansa, har ya shiga mota ya hangota, ya tsaya yana jiran ƙarasowarta, ta miƙa masa wata jaka, be tambayi ta meye ba, ya karɓa ya duba, akwai manyan robar ruwa guda biyu a ciki, sai babban kwalin lemo, sai wata jarka guda ɗaya, ya ɗauko jarkar yana dubawa, fura da Nono a ciki. Ya kalleta ya ce "Ina kika samu fura?" "Mamana ce ta aiko mini da ita daga garinmu, na baka ne saboda hanya amma idan ba ka sha shikenan bani". Yayi murmushin gefen baki ya ce "Bayan wauta ashe kina da hankali, ga ruwa ga lemo ga fura duk an bani kar inji yunwa a hanya, Na gode sosai" "Bakomai Allah ya sanya Alkhairi" "Ameen ya Allah" ya zura hannu a aljijunsa ya ɗauko kuɗi ya miƙa mata ya ce "Ungo wannan, kya sayi wani abun na gode sosai" ga mamakinsa sai ta girgiza masa kai alamar ba zata karɓa ba. "Meyasa ba zaki karɓa ba?" "Baba zai mini faɗa, kuma yana bani kuɗi shima" "Ke kuma sai ki gayawa Baban na baki kuɗi?" Cike da wauta ta ce "Ai ni duk abin da aka yi sai na gaya masa, saboda idan nayi ƙarya yana ganewa" "Ai yanzu ba zai sani ba, idan ma kika gaya masan, kice ni na baki" "Ni dai a'a gaskiya, ban taɓa riƙe kuɗi me yawa ba, ba ruwana, kuma dama ai aiki nake kuna biyana meyasa zaka bani kuɗi?" "Ai nima babanki ne, ki karɓa" Girgiza kai tayi ta ce "Babansu Fadila ne, ni Baba ne Babana" shi mamaki ma ta bashi, yaran yanzu da son abin duniya, amma ta dage ba zata karɓa ba, baya son cigaba da takura mata, dan haka ya ce "Shikenan, na gayawa Baban idan na baki abu ba kya karɓa" ba ta ce komai ba ta juya sumi-sumi ta koma ciki. Tana zuwa ɗakinta, ta nemi wuri ta kwanta, dan ta samu ta rintsa, cikin barci, taji hayagagar Hajiya Zainab a ƙofar ɗakinta. "Uban waye ya ce a girka mini wannan abin a gida, gidan nan yayi miki kalar in da za a sha wannan kayan fitsarin da saka gudawar, taso ki fito ki girka mana wani abin da zamu ci" iya ƙuluwa Amina ta ƙulu ƙarshe, bata ga meye aibun koko da ƙosai ba, kuma banda wulaƙanci ga Hajara nan amma ba za a sata aikin ba sai ita. A gajiye take matuƙa tana son hutawa, amma an tasheta da tijara, duk aikin da tayi a gidan kan su tashi ba su gani ba, haka ta fito rai a ɓace ta kuma shiga kitchen. Ranar Litinin lectures da komai ya cigaba da gudana, amma ba Yazid babu dalilinsa. "Bismillah" taji sautin murayarsa ya shiga cikin kunnuwanta, a rikice ta kalleshi, sai ka ce Aljani sam ba ta ga shigowarsa ba sai zamansa a kusa da ita. Ɗaga kai ta yi ta kalleshi, tana son yin magana amma ta kasa. "Ukty, ko nemana ba kya yi, ban dawo school ba babu ko cigiya" "Ni nake biya maka school fees da zan damu da rashin zuwanka?" "Kar mu fara haka dake daga dawowata mana, ya kike ya hutun?" Ɗan kallonsa tayi amma taƙi magana, Sir Kankiya ne ya shigo ajin, hakan ya sa kowa shiga hankalinsa saboda ba shi da wasa sam ga kwarjini da yake da shi. Yana ganin Yazid a zaune kusa da Fadila, ya haɗe rai "Kai malam babu wani wurin zaman ne, sai nan kusa da mace?" Yazid ya kalli ajin kowa in da ya ga dama yake zama, kuma ba wai matsarta yai ba, amma Kankiya na neman ya dizaga shi a cikin mutane. Fadila ta ce "Tare muke zama da shi" "Yaushe kika fara ƙarya? Ai ba dake nake ba, next time ka nemi wani wurin daban ka zauna" Yazid ya jinjina kai tare da sunkuyar da kai. Fadila ba ƙaramin ƙular da ita Kankiya yayi ba, amma ta basar, aka cigaba da lectures. Mistakenly biron Yazid ya faɗi ƙasa, ya durƙusa ya ɗauko amma ya kuma jiyo muryar Kankiya yana faɗin "Kai wane irin mutumin banza ne, kalleka a haka kamar mutumin kirki, zo ka fita ka bar mini aji" Saroro Yazid yayi yana son gane laifin da yayi, gaba ɗaya idon 'yan ajin ya dawo kan Yazid. "Zo ka bar mini aji nace" Yazid ya miƙe ya bar ajin, ba tare da yayi ƙoƙarin kare kansa ba. Fadila taji haushin abin da Kankiya yayi, ya kammala lectures ɗinsa ya fice, ta ɗauki biron Yazid da littafinsa, ta nufi ofishin Sir Kankiya. "Me Yazid yayi maka kake ta ƙoƙarin tozarta shi?" Tayi maganar cikin ɓacin rai. "Yana bibiyar abin da nake so, idan yana son zaman lafiya ya kammala karatunsa hankali kwance a makarantar nan, to ya nesanta kansa da ke". "Wai kai wane irin mutum ne? Ni nace maka ina sonka ne? Nayi maka kala da ajinka, nayi maka kalar auren mutum kamar kai? Babu wata alaƙa a tsakanina da Yazid, abokin karatuna ne kawai, dan haka kar ka ɓata masa career" "Wannan ke ta shafa, da ke da shi, muddin ya cigaba da shiga sabgarki, zan iya kawo ƙarshen karatunsa a makarantar nan, idan kuma kin musa mu zuba mu gani, ba zan cutar da ke a harkar karatunki ba, Saboda ina sonki, amma gwargwadon wulaƙancin da kike mini, gwargwadon yadda zan cigaba da taka Yazid a cikin Jami'ar nan!!! Ayshercool 08081012143GABA DA GABANTA AISHA ADAM AYSHERCOOL P 24_25 Iya wuya Fadila ta zo, saboda tsabar takaici da ɓacin rai, ta kalli Sir Kankiya ta ce "To mu zuba ni da kai, idan baka ɓata Career Yazid ba, ni zan ɓata taka rayuwar, na ga alamar baka san wacece ni ba, ba zan saka a hukunta min kai haka ba, kaci bulus, saina fara nuna maka ka ba kowa bane ba, face me sanye da rigar tsiya da zai ƙare a cikinta". "Fadila ni kike gayawa haka dan ina son ki?" "Na gaya maka ɗin, da na gaya maka ne? Me Yazid yayi maka? Koma menene tsakanina da kai ne, meye nasa, Wallahi ko na rasa mijin Aure ba zan auri mutum irinka ba" tayi maganar cikin huci, ta ja jakarta ta fice fuuuu kamar iska, ta bar office ɗin, cike da ɓacin rai.   A haraba ajinsu ta hango shi, yana tsaye shi da wasu 'yan ajinsu, fuskarsa babu wata damuwa, kamar abin da ya faru bai ɓata masa rai ba. Ganinta a tsaye tana kallonsa ne, ya sanya shi takowa zuwa in da take tsaye "Ukty daga ina?" So take tayi masa magana amma ta kasa, ta miƙo masa littafinsa da bironsa. Yayi murmushi ya karɓa ya ce "Na gode, ni nama manta da na ajiye su, da sa anzo wata lectures ɗin in tuna" Kallonsa take tare da tunanin wai shi a rayuwarsa baya fushi ne, babu wani abu da yake ɓata masa rai, taje ta gama baloƙoƙo a kansa, amma shi abin da ya farun ko a jikinsa. Juyawa tayi ta nufi department ɗin su Yusra, dan tattaunawa a kan wannan matsalar. Ta kira Yusra a waya, Yusra ta gaya mata a in da zasu haɗu. Tun da Yusra ta hango Fadila, da yadda ta ɗaure fuska ta san akwai damuwa, Fadila ta ƙarasa ta zauna tana huci. "Baby me, waye ya taɓa mini ke ya sanya ki fushi haka?" "Yusra zuciyata na raya mini wani abu, amma ina gudun aikatawa daga baya ace nayi laifi, shiyasa na zo wurinki". "Subhanallaahi, me zaki aikata?" "Wani lecture ɗinmu zan saka a kama mini" Yusra ta zaro ido ta ce "Kina da hankali kuwa?" "Na taɓa ciwon hauka ne? Malama Wannan Kankiyan zan saka a kama mini" Nan ta labartawa Yusra komai cike da ɓacin rai. Yusra ta jira Fadila ta gama baloƙoƙonta, sannan ta nisa ta ce "Yanzu duk a kan Yazeed ɗin kike wannan tada jijiyar wuyan haka? Karo na farko da naga tsantsar tausayi a fuskarki kodai kodai?x 'Yusra ya kike nema ki mayar da maganata shirme, ko wani abu daban? Ke da kinga Yazeed kin san ba masu hali bane, karatunma Allah kaɗai ya san da yadda yake yinsa, idan aka ɓata masa career saboda ni, an masa adalci kenan? Bafa mahaukaciya bace ni, zanje in aikata abin da ya dace tun da ba zaki bani shawara ba" Yusra ta ce "Tuba nake, Allah ya baki haƙuri. Shawarata a gareki shi ne kamar yadda Kankiya ya buƙata kawai ki nesanta kanki da Yazid, ke har ki gama makarantar nan, kin da gatan da babu wanda ya isa ya taka ki, Yazeed kuwa fa, ko kuma kije ki kai ƙarar Kankiyan, a miki tsakani da shi" ɗan shiru Fadila tayi, daga bisani ta ɗauki jakarta ta kalli Yusra ta ce "Ni banji wannan shawarwarin naki, sun ratsani ba, zan san abin yi" Yusra ta riƙo hannun Fadila ta ce "Fadila kar ki je aikata abin da zai janyo muku Matsala" Fadila ta zame hannunta daga na Yusra ta fice. Khalil ne zaune a Offi, sai jujjuyawa yake a kan kujera, hannunsa riƙe da waya ya saka a kunnensa, yana jiran Hafsa ta ɗaga. "Assalamu alaikum" ta faɗa muryarta ƙasa-ƙasa. "Sweetheart, ko bacci kike na tashe ki?" "Bakomai, na ɗan koma bacci ne ina kwana?" "Eyya am sorry, ban san bacci kike ba, na fito Office ne na kiraki in ji lafiyarki" "Ina lafiya ƙalau, ya aikin?" "Aiki Alhamdilillah, bari in barki ki huta, anjima mayi waya, koma ki cigaba da baccinki" "No ai na riga na tashi, gara in tashi in fara shirin kayan sana'ata" "Hafsa" ya kira sunanta. "Na'am" ta amsa. "Bana son fitar da kike titi" "To idan ban fita ba me zamu ci?" "Haba Hafsat, ni haryanzu ban gane ba, kin ƙi ki bani dama yadda Yakamata, Wallahi Hafsa dan abin da zaku ci, zuwa abin buƙatar ku ba zai gagara ba" Hafsa cikin sanyin muryarta ta ce "Ba hakkinka bane, ka bari zuwa lokacin da Allah ya sa ka aureni, ko me kai mini a wannan lokacin ba laifi, amma yanzu.. "Shhhh Hafsat, kina kokwanton ba zan aureki bane? Wallahi ina matuƙar kishinki fiye da yadda kike tunani, zuciyata bata mini daɗi sam ganinki a titi Wallahi". "Ka raina matsayin da Allah ya ajiyeni ne?" "A'a subhanallah, ba haka nake nufi ba Sweetheart, da haka ne ai ba zan tunkareki da batun soyayya ba, dan Allah ki bani haɗin kai, ɗaukar ɗawainiyarku ba komai bane, muna da kuɗi sosai, mijinki ya tara muku kuɗi, ki kwantar da hankalinki mu ci guminmu" Murmushi Hafsa tayi ta ce "Rana ta fara yi, bari in tashi in ɗora girki, ka kula mini da kanka sosai" "Wayo zaki mini ko?" "Ba wayo bane" Khalil yayi murmushi ya ce "A girka dani, in an gama a zo a ciyar da ni a baki, ina kallon kyakywar fuskarki" "Kayi aikinka My, see you later" ta katse kiran. Khalil ya sumbaci wayar, tare da ƙanƙameta a ƙirjinsa. Amina tuni ta fara zuwa extra lessons da suke a cikin hutu, ta mayar da hankalinta sosai a kan zuwa makaranta. Duk da yau juma'a bata iso gida ba sai ƙarfe biyar na yamma, ta dawo a gajiye, a falo ta tarar da doctor Aliyu yana gwada BP Alhaji Ahmad. Saroro ta tsaya tana kallon Alhaji Ahmad, da doctor Aliyu, gefe ga Hajiya Zainab a zaune, tana so tayi magana, amma taga hakan tamkar shishshigi ne, dan tsaf Hajiya Zainab zata iya dizgata, dan haka ta yi musu sallama ta wuce ɗakinta. Ta isa ɗakinta, ta canza kaya tayi salla, amma ta kasa cin abinci, haka nan taji tana son sanin meyafaru ake masa gwaji. Ta sake fitowa falon, a wannan karon Hajiya Zainab hankalinta na kan TV, Alhaji Ahmad kuma yana kwance a kan kujera, ya lumshe idanunsa, lokaci lokaci yana ɗan yamutsa fuska. Amina a ranta ta ce "Wata ƙila bashi da lafiya" Amina ta je ta nemi Abinci ta ci, ta fito ta tafi wurin Baba, suna nan zaune suna hira ita da Baba, tana son tayi masa maganar Alhaji Ahmad, amma ta fasa ta cigaba da hirarta. Wani razananne horn da ake yi tamkar yaƙi, ya sanya a gigice suka miƙe ita da Baba, Baba ya nufi gate ɗin, yana kiciniyar buɗewa, amma aka cigaba da horn ɗin. Baba ya buɗe gate ɗin, Fadila ta kwararo motarta tamkar zata bar doron ƙasa ta tashi sama. A hasale ta fito, dan kallo ɗaya zaka yi mata ka san a fusace take, ƙiris take jira dama, ta nufo Baba cikin masifa, Amina ta miƙe cike da shirin ko ta kwana, ta shirya mayarwa da Fadila duk wani rashin mutunci da take shirin aiwatarwa. "Ka kurmance ne bamu sani ba?" Baki a ɗan sake ya girgiza kai ya ce "A'a" "To wulaƙanci da rainin hankali ne ya sanya zan zo in tsaya ina horn ka ƙyaleni?" "Amma naga ai ba wani daɗewa ki kayi kina horn ɗin ba, kuma baki ga jikin girma ba, kan ya buɗe gate ɗinma ai sai a hankali". Cikin tsawa Fadila ta ce "Na saka da ke ne? Jikin tsufa waye ya masa dole ya zauna, ku koma in da kuka fito mana, idan ya san ba zai iya ba sa ya bari amma sai ka ce.. "Fadila kar ki kuskura ki faɗi maganar banza a kan mahaifina, uba talaka da mai kuɗi duk ubane, dan haka kar ki sake ki zagar mini uba a gabana, na gaji" "Idan na zageshi me zaki yi, baki da abin da zaki ja da ni, ki ka sake kika yi mini wani rawar kai, a yau ba sai gobe ba sai kun bar gidan nan daga ke har shi, shashasha, wawuya 'yar ƙauye kawai" Jikin Amina har wani rawa yake yi, Bana ya riƙo Amina, yana girgiza mata kai, tare da hanata Magana, wasu irin zafafan hawaye ne suka shiga sintiri a kan kuncinta. Fadila ɓacin ran da Kankiya ya cusa mata ta zo ta sauke a kan Baba Hassan. Fadila na gama saukalen rashin mutuncinta, ta shige cikin gida. Amina takaicin Baba ya hanata magana, ya sanya ita ma ta nufi hanyar shiga cikin gidan, A falo ta tarar da Fadila zaune a kusa da Daddy tana masa sannu. Amina ce ta shigo fuuu, idanunta jawurr tana kuka. Haka nan hankalin Daddy ya koma kan Amina, da ta wuce idanuwanta jawur, yana tunanin meyafaru da ita take wannan kukan haka?. "Ke zo nan" ta jiyo muryar Hajiya Zainab. Ran Amina a matuƙar ɓace ta tsaya cak, saboda ji take tamkar ta jiyo, ta zazzagi Hajiya Zainab ita da Fadila. "Ko ba zaki zo ba ne kina jin ina kiranki" Amina ta dawo falon ta tsaya, ta sunkuyar da kanta ƙasa. Hajiya Zainab ba ta damu da kukan da ta ga Amina tana yi ba ta ce "Je ki kira mini Babanki" Amina ta ɗago idanunta da suka yi jawur, ta sauke a kan Amina. "Ko ba zaki bane ina miki magana saboda salon iskanci kina jina kin yi shiru" Amina ta jiya jiki a sanyaye, ta koma harabar gidan ta samu Baba yana jin radiyo. "Uwata lafiya kuwa kukan dai kike? Ko wani abun suka sake yi miki?" "A'a cewa aka yi ka zo" "Ba dai wani abun kika yi ba ko?" "Eh, kawai cewa aka yi ka zo" Baba ya miƙe yana faɗin "Muje to Allah ya sa lafiya" Suka koma falon tare, ta ƙasan ido yake kallon Amina. Amina ta tsaya tana jiran taji me za'ace wa Baba kuma. Alhaji Ahmad tashi yayi ya wuce ɗakinsa, dan baya son hayaniya. "Gidan Hajiya Turai zaka je, ka karɓo mini saƙo, kaje ka dawo da wuri kar ka barni ina jira" Cewar Hajiya Zainab da take kallonsa a wulaƙance. Cikin girmamawa Baba ya fice, dan aiwatar da aiken da Hajiya Zainab tayi mata. Amina tun da ta ƙule ɗaki bata sake fitowa ba, ko Abincin dare ba ta samu ta iya ci ba, saboda yadda ranta yake a ɓace, Amina ta rasa dalilin da yasa Fadila ba ta da abin da yake mata daɗi irin cin mutuncin Baba a kan buɗe ƙofa, Babu wani laifi da Baba yake yi ta ci mutuncin sa sai a kan buɗe gate. Bayan sallar isha'i, Amina tayi kwanciyarta, ba tare da ta nemawa cikinta abin da zata ci ba, amma ta ɓige da juye-juye bacci ya gagara, har dare ya raba, ga ɓacin rai ga yunwa da ta uzzurawa cikinta. Ba shiri ta tashi ta nufi falo, dan neman abin da zata zuba a cikinta, ta fara alwala tare da gabatar da salla raka'a biyu, sannan ta kwaso litattafanta ta fito falo, ta yanke shawarar zuwa barandar waje, tayi karatun a can, ta san idan tayi hakan zata iya mantawa da damuwarta ta fuskanci gobenta a kan karatun da ta saka gaba, daga ranar da ta kammala karatun sakandare zata bar gidan nan, dan ji take tamkar kan tabar gidan nan sai ta yiwa Fadila dukan da sai an kaita Asibiti. Amina tayi nisa a tunani, jefa ƙafarta kawai take a cikin falon, tana son ta lalubi ƙofar falon ta buɗe, ba tsammani tayi karo da wani abu, ware baki tayi za tai ihu, amma taji an rufe mata baki. Mutsu mutsu ta fara yi, zata ƙwace jiki ba ƙwari ya ce "Shhh Ahmad ne" yayi Maganar yana sakar mata baki. "Waye Ahmad kuma?" Ta faɗa bakinta na rawa, duk da ta gane ƙamshin turarensa. "Daddy" ya faɗa a hankali. Amina ta dafe ƙirjinta ta ce "Wayyo Allah, na zata aljani ne Wallahi" "Idan Aljanin ne shikenan, ba zaki addu'a ba sai ihu?" "Ai wannan tunanin ana yinsa ne idan mutum yana cikin hayyacinsa" tayi maganar tare da ɗan ja da baya, saboda kusancin da ke tsakanin su. Cikin duhun ya ce "Me kike yanzu baki bacci ba?" "Baranda zani karatu" "Ok, yayi kyau" ya furta ya raɓa ya bi gefen in da yake jin alamun tana tsaye. Amina ta ƙarasa ta buɗe ƙofar, ta fita baranda, hasken lantarki ko ina, ta zauna ta bubbuɗe litatafanta, ta fara duddubawa. Gani tayi an kunna wutar falon, haske ya gauraye falon. Tashi Amina tayi ta leƙa falon, taga Alhaji Ahmad ne ke ta zagaya falon. Ji yayi kamar ana kallonsa, dan haka ya waiwayo, sai ya ga Amina a tsaye tana kallonsa. Amina ta ce "Jikin ne dai?" Ya jinjina mata kai yana cigaba da zaga falon. "Wai me ya sameka, naga kana ta zagayawa?" Tayi tambayar kanta tsaye. "Suga na ne ya hau, da kuma jinina shima ya hau, ƙafafuwana ne suke zafi da cikina" ya samu kansa da bata amsa, ba tare da shi kansa ya san dalili ba. Cikin tausayawa Amina ta ce "Allah sarki sannu, dama kana da suga amma komai ma kake ci, ba'a tsara maka Abincin da yakamata ka ci? Naga bakomai masu ciwom suke ci ba fa" Daddy ya cigaba da aikin zagayensa ba tare da ya kuma cewa komai ba. "Allah ya baka lafiya" ta faɗa tare da juyawa ta koma wurin karatunta. Kusan mintuna talatin ta tashi ta kuma leƙawa, ta ganshi a zaune ya mimmiƙe ƙafafuwansa sai lanƙwasa yatsun ƙafarsa yake yi. "Sannu Daddy, Allah ya baka lafiya" ya jiyo siriryar muryata a kunnensa. Murmushi kawai ya yi bai amsa ba. "Haryanzu ƙafar na maka zafi ne?" Ya jinjina mata kai alamar eh, tare da lumshe idanunsa, da ganin yadda yake gumi zaka san yana jin ciwon sosai. Komawa tayi, mintuna kaɗan ta dawo ta ce "Daddy zo ga ruwa na zuba maka a bokiti, kazo ka sanya ƙafafuwan ko zasu daina" "To zan zo" ya bata amsa ba tare da ya buɗe idonsa ba. Ta koma ta cigaba da karatunta, harta fidda ran zai fito, sai gashi ya fito, ta ajiye masa kujerar zama, da bokiti ta zuba ruwa. Ya zauna a kan kujerar, ba tare da ya ce mata komai ba, ya janye jallabiyarsa, ya zura ƙafafuwan a cikin ruwan, a hankali ya lumshe idanunsa jin yadda sanyin ruwa ke ratsa shi, yana samar masa da releif, tun daga ƙafafun nasa zuwa ga ilahirin gangar jikinsa. Amina ta cigaba da rubuce-rubucenta,  a hankali yake samun releif daga zugin da ƙafarsa ke masa, ya buɗe idanunsa ya na kallon Amina, da take ta aikin karatunta. Shi dai Allahn da yayi shi ba mutum ne mai shiga sabgar mata ba, shi ko wasa da yara bai fiye yi ba, dan magana ma bata dame shi ba, amma har cikin ransa yake jin daɗin yadda take nuna damuwarta da shi. "Naga kin kasa wannan, kawo mu gani" yayi Maganar yana kallon littafin gabanta Ba musu ta miƙa masa littafin dake hannuta, tare da biron. "Me aka yi miki kike kuka ɗazu?" Yayi tambayar yana kallon littafai da ke hannunsa. "Wai ni?" Amina ta tambaye shi. "A'a" ya bata amsa. Shiru tayi ba ta bashi amsa ba, ta fara wasa da littafin gabanta. A hankali yake rubutun cikin nutsuwa, mintuna kaɗan ya miƙa mata littafin. Buɗe baki tayi tana kallonsa, "ya aka yi kayi mini, tun ɗazu nake fama na kasa" Be ce mata komai ba, ya cigaba da kallonta, ita kuma ta cigaba da bin littafin da kallo tana murmushi. "Wane course zaki karanta, idan kika kammala sakandare?" "Ni sakandare kawai nake son nayi, Baba bashi da halin da zai biya mini jami'a". "Wane course zaki karanta a jami'a idan kin kammala sakandare" ya maimaita mata. "Bani da zaɓi" "Meyasa?" Ya faɗa a taƙaice. "To idan na sakawa raina ga abin da nake so, ai babu me biya mini, shiyasa ni bana tunanin wata jami'a". "Zaki iya medicine?" Yayi Maganar yana kallonta. Ƙwalalo ido Amina tayi ta ce "Taɓ, korata za a ayi, bani da ƙoƙari" "Kina wahal dani, bana son doguwar magana, ke in an tambayeki sai kin yi amfani da different formulas kafin ki amsa". "To yi haƙuri" Ya sunkuyo da fuskarsa kunnenta, wanda hakan ya haddasa mata faɗuwar gaba "Gaya mini, me zaki karanta?". "Kome Allah ya sa na samu, ina so". Ta amsa tana janye jikinta gefe. "Idan kin yanke shawara ki gaya mini, zan ga abinda zan iya yi a kai" "You mean zaka barni in cigaba da karatu a gidan nan, naji ance ɗawainiyar jami'a ba kamar na sakandare bane" "In dai karatun bai fi ƙarfin talaka kamar ni ba, zan yi wani abu a kai Insha Allah, kina da ƙwaƙwalwa bai kamata a barta haka ba ki tsaya iya Sakandire ba" Daddy ji yake tamkar suka ɗai ne a duniyar, dare ya tsala, ko tunanin wani ya zo wurin baya yi. Hawaye ne ya wanke fuskar Amina, tana kallon Alhaji Ahmad, amma ta kasa Magana. "Komai aka yi miki sai kuka?" "Na gode sosai Daddy, kana da kirki sosai ba kamar.." Sai kuma tayi shiru. "Ba kamar wa ba? Hmm ko kusa karki bari ta ji kin faɗi wani mummunan abu a kanta, kin san abin da zata iya yi miki, let's keep this as our secret, kar ki gayawa kowa sirrinmu ne, ciki har da Baba, idan kuwa kika bari zancen ya fito, to abinda ya biyo baya ba ruwana, dan ba lallai Zainab ta bari" Amina ta ɗan kalleshi, yana da zuciyar taimako, amma yana shakkar matarsa. "Insha Allah ba zan gayawa kowa ba, na rufe bakina, Allah ya baka abin da kake so duniya da lahira" "Ameen" ya amsa tare da jingina a kujera. Bacci ne ya ɗauke shi, ƙafafuwansa na cikin bokitin ruwa, Amina ma bacci ne ya kwasheta, ta kife kanta a gefen kujerar ta hau bacci. (ALLAH YA SA HAJIYA ZAINAB TA ZO TA KAMA KU🥴) Ayshercool 08081012143GABA DA GABANTA AISHA ADAM AYSHERCOOL 26-27 Tsananin sanyin da yaji yana ratsa shi ne ya sanya ya buɗe idanunsa, gari ya ƙara yin duhu baƙi ƙirin, ba kajin motsin komai sai haushin karnuka a waje, ya kalli in da Amina ta dunƙule a wuri ɗaya, ta jingina da kujerar da yake kai tana bacci, da alama tana jin sanyi sosai, amma bacci ne a kanta. A hankali ya zare ƙafafuwansa daga cikin bokitin ruwan nan, ya tattara litattafanta da ta baza a wurin, bironta ya ɗauka yana shafa mata a fuska, yamutsa fuska ta yi, ta kai hannu ta kori abin da yake bin fuskar tata, amma ya kuma shafa mata. "Ki tashi kije ki kwanta" Amina ji take tamkar a kan katifarta take, dan haka tayi wani irin juyi tana ƙoƙarin faɗawa jikinsa ta cigaba da baccinta. Cike da rashin sabo, da yi mata kallon 'yar cikinsa, ya sanya hannayensa ya ɗagata ya tsayar da ita a kan ƙafafuwanta, ya ɗan girgizata ya ce "Open your eyes" a hankali take buɗe su tana lumshewa, tamkar zata faɗi. Ya danƙamata litattafanta, ya buɗe musu ƙofar falon, ya kunna fitilar wayarsa, ya rakata har bakin part ɗinsu, sannan ya wuce sashen Hajiya Zainab. Ya tarar da ita ta rashe, sai baccinta take hankali kwance. Ya lallaɓa ya hau kan gadon, cikin ikon Allah, ya rage jin zafin da tafin ƙafarsa ke yi masa sosai. Ya janyo bargo, ya rufa musu shi da Mummy, ya kwantar da kansa a wuyanta, yana shaƙar ƙamshin turaren da take fitarwa mai daɗin gaske a hancinsa. Tuna halinta ne ya sanya shi sassauta rungumar da yayi mata, dan yanzu sai ta farka ta hau shi da masifa. Amina bata farka ba sai asuba, dan sai da ta kusa makara, sai da ta farka ta ganta a tsakar ɗaki a kan litattafanta tana bacci, sannan ta tuno abubuwan da suka faru jiya da daddare, gaba ɗaya ta ɗauka mafarki take yi, a hankali ta tashi ta shiga toilet, tayi alwala ta dawo tayi sallar auba. Bayan ta idar, ko karatun Alqur'ani da azkar ba ta samu yi ba, saboda kanta har wani nauyi yake yi mata, ta haye kan katifarta ta hau aikin bacci. Hajara tamkar ta tashi Amina, ganin har ƙarfe takwas bata fito ba, sai kuma ta fasa, saboda itama ko ƙarfe nawa zata kai ba ta fito ba, Amina ba ta damuwa balle ta taso ta, aikinta kawai take yi, dan haka taga idan ta ce sai Amina ta taso, to tabbas bata kyauta ba.   Wasa² har goma saura, Amina baccinta take yi, A lokacin Alhaji Ahmad ya fito karyawa, tare da Hajiya Zainab. Ya tarar da Hajara na ta shirya Abinci a dining ɗin, haka nan yaji yana son ganin Amina, dan galibi ita yake gani tana shirya Abinci, amma har Hajiya Zainab ta zuba masa Abinci, yana son ganin ta ina zai ga Amina, kamar ba raba dare suka yi tare ba jiya. Ɗanɗanon Abincin kawai ya ci, yaji ya banbanta da nata, ya kalli in da Hajara ke mopping ya ce "Ina wannan Yarinyar take?" Hajara ta kalleshi ta ce. "Wace yarinyar ranka ya daɗe?" " Wadda kuke aiki tare?" "Bata tashi ba" Hajara ta faɗa tana sunkuyar da kai. "Yau ba taje makaranta ba ne?" "Ai sun yi hutu" ta bashi amsa, bai ce komai ba ya cigaba da cin Abincin da a bakinsa na Amina yafi daɗi. Hajiya Zainab ta kalleshi ta ce "Kai meye damuwarka da taje Makaranta ko ba taje ba?". "Saboda kuɗina nake biya, dan haka yakamata in bibiya" "Shiyasa tun farko ni ban so ka kaita makarantar kuɗi ba, sai a kaita ta irinsu, amma ka kaita cikin yaran da ba sa'aninta ba a fannin rayuwa da arziki" Alhaji Ahmad yayi mata shiru ya cigaba da cin Abincinsa. Ƙarfe goma saura, gaba ɗaya ɗalibai sun tattara hankalinsu a kan malamin da yake tsaye yana kaiwa yana komowa kamar mazari, a ajin yana gabatar da darasi, sai ga Yazid a wahale, kamar an koro shi, cike da fargaba ya fara yinƙurin shiga ajin. "Hey stop their, ko ɗakin babarka idan zaka shiga sai ka nemi izini, balle aji" cewar malamin da yake yiwa Yazid kallon banza. "Am sorry sir" ya faɗa cikin ladabi. Gaba ɗaya ajin suka yi shiru, suka mayar da hankalinsu kan Yazid. "Yanzu ne lokacin da yakamata ka zo aji? Ni in baro gidana tun bakwai takwas tayi mini a nan, amma ka zo yanzu kuma kai tsaye ka ce zaka shigo mini aji?" "Ayi mini afuwa malam, insha Allah ba zan sake ba" "Sorry for yourself malam, ɓace mini daga nan" Yazid ya yunƙura zai kuma magana, amma malamin ya buga masa tsawa ya kore shi. Duk iya wulaƙanta mutum da Fadila ta ƙware a kai, taji babu daɗi yadda malamin ya kyari Yazid ya koreshi, ga shi 'yan aji gaba ɗaya sun zuba masa ido, duk da Yazid mai sa'a ne a wasu lokutan, kuma mutum mai haƙuri da ladabi, amma wasu lokutan yana yawan shiga komar malamai su wulaƙanta shi. Duk da Yazid ya bar ajin, hakan bai hana malamin cigaba da ƙananan maganganu, a kan Yazid ba. Bayan fitar malamin daga ajin, Yazid ya shigo ya samu wuri ya zauna, ba tare da ya kalli kowa ko ya kula wani ba. "Kowa ya tabattar ya mallaki littafin da Sir Bello ya ce a saya, dan da alama wani abun yake shirya mana a kan littafin nan, zai iya kada mutum idan ba shi da shi a jarrabawa, dubu uku ne, ga takadda nan ta na zagawa, duk mai so ya rubuta sunansa, na bada aron kuɗina naje kasuwa na sayo mana, duk mai so sai ya bada kuɗinsa in bashi" Cewar Captain dake tsaye a gaban ajin, yana bayani daki-daki kamar me koyar da karatu. Tana hangen Yazid daga in da take zaune, kamar mara lafiya, sai ya kifa kansa a kan benci, sai kuma ya tashi yana ɗan lumshe idanunsa yana buɗewa, idanun duk sun yi ja, sai tayi tunanin ko duk dan saboda abin da lecturer yayi masa ne. Aka miƙawa Yazid takarda, ya rubuta sunansa in zai sai littafi, amma ya girgiza kansa, ya mayar da kansa ya kifa kamar yadda yake da farko. Da takardar ta zo kan Fadila, sai ta sayi kwafi biyu a take, ɗaya nata ɗaya na Yazid, amma tana jinjina yadda zata bashi littafin, dan bata son yawan shiga sabgarsa. Tana nan zaune taga ya tashi ya fita, ita ma ta tashi ta bi bayansa, tana biye da shi, ba tare da ya sani ba, taga ya shiga wani aji da babu kowa, 'yan ajin suna wurin excursion, mutanen da ke ajin 'yan tsirari ne, wasu na cin abinci wasu na abin da ya damesu. Wuri ya samu can ƙarshen ajin, ya je ya samu wuri ya zauna ya kifa kansa. Ta tsaya daga bakin ƙofa tana saƙawa da warwarewa, daga bisani ta yanke shawarar shiga. Har taje inda yake bai ɗago ba, ta saka hannu ta ɗan daddaki ka bencin da yake kai. A hankali ya ɗago ya kalleta, idanunsa sun yi jawur, ta kalli ƙafarsa tayi futu futu, kamar wanda yayi tafiya a sahara. Sauke mask ɗin fuskarsa yayi, tare da sakar mata murmushin ƙarfin hali "Ya aka yi kika san ina nan?" Ɗan taɓe baki tayi, ta saka hannu a jakarta, ta ɗauko littafin da ta saya masa da handout ta ajiye masa "Gashi nan, kuma ya rarraba group a aji, ya bada assignment za'a yi presentation next week in Allah ya kaimu, na saka sunanka, sai kaje ka dudduba handout ɗin" Zuba mata idanunsa yayi gaba ɗaya amma ya kasa magana, sai kallonta kawai da yake yi. "Magana fa nake maka, amma ka zuba mini ido". A hankali ya ce "Yi haƙuri zan yi magana, numfashina ne yayi mini nauyi" A ɗan tsorace ta kalleshi "Jikin ne?" Lumshe idanunsa yayi, ina ma yana da damar gayamata abin da yake damunsa, rabonsa da Abinci tun kunun jiya da safe, Ulcer ta riƙe masa ciki da ƙirji har bayansa, haka ya lallaɓa ya taso ya taho Makaranta da wuri, saboda saurin da yake yi, yaji numfashinsa yana isa huhunsa da ƙyar, a wahale ya ƙaraso makarantar. "Yazid" ta kira sunansa, karo na farko da yaji sunansa a harshen Fadila, wanda kiran sunan nasa ba ƙaramin tasiri yayi a zuciyarsa ba, ya haifar masa da wata nustuwa ta mussaman ba. "Kaje Asibiti ne?" "Eh na sha magani" ya bata amsa da ƙyar, dan baya son yin ƙarya ko kaɗan. Ya jingina da teburin, ya lumshe idanunsa, ita kuma ta tsaya a tsaye, ita bata zauna ba ita bata tafi ba tana kallonsa. Kamar wadda aka yiwa dole, ita a lallai bata damu da shi ba ta ce "Ko zaka tafi gida ne?" Ya girgiza mata kai ya ce "Zan ji sauƙi yanzu insha Allah, ganinki ɗin nan ma kawai ya sanya mini nutsuwa da jin na warke" tsuke fuska tayi ta harare shi, tare da ɗan hura hanci. "Allah ya sawwaƙe, ni na tafi" ta juya ta nufi hanyar ficewa, ta bar masa handout ɗin da littafin ya zubawa bayanta ido, har ta bar ajin. Ɓangaren Amina kuwa, bayan tayi wanka ta nemi abin da za ta ci taci, bayan ta tabattar da an kaiwa Baba nasa Abincin, ta koma ɗakinta ta ɗora da rubutun Alqur'ani da take yi. Sai wajen azahar sannan Amina ta fito, ta haɗa wanke wanke tayi, tare da gyara duk in da aka ɓata, duk da Hajara taji haushin yadda yau Amina taƙi kataɓus ta sha baccinta, haka ta jure ta danne fushinta, saboda ita ma Aminan ba ta mata ƙorafi.   Yau Alhaji Ahmad a gida ya wuni, sai ƙarfe huɗu sannan ya shirya zai fita, yau ba da Zakiru direba zai fita ba, shikaɗai zai fita, ya shiga motar, yana ƙoƙarin kunnawa, ya hango Amina a wurin Baba, riƙe da littafi, tana ta aikin nata na surutu, tana yi tana kallon littafin hannunta, Baba kuma yana ta ɓare gyaɗa yana miƙa mata, tana karɓa tana ci. Ya ɗan jima a zaune a cikin motar yana kallonsu, gwanin sha'awa, ita 'ya mace duk in da Allah ya baka ita, ya baka Sarauniya ko da kuwa kai ba sarkin bane, Alhaji Ahmad yana son yaga ana tattala mace,baya son ya gansu a wulaƙance, shiyasa yake matuƙar ji da Fadila, shi namji duk in da yake zai iya kula da kansa, amma mace tana buƙatar kafaɗar da zata jingina. Sai karɓe gyaɗa take daga hannun Baba tana ci, tana nunawa Baba littafinta, duk da Baba mutumin karkara ne, kuma ba wanda yayi ilimin zamani ba, amma wasu lokutan yadda yake gudanar da rayuwarsa a waye, ba girman kai ba hayaniya. A hankali ya fara jan motar, zuwa wurin gate, daidai in da suke ya tsaya da motar, Baba ya taso da sauri, ya tsaya jikin motar ya risuna yana gaida Alhaji Ahmad, Ya amsawa Baba cikin sakin fuska, Amina ta wani basar, kamar bata san da wanzuwarsa a wurin ba. "Aminatu ina wuni" Alhaji Ahmad ya faɗa lokacin da ta ɗago suka haɗa ido, tana ƙoƙarin mazewa ta kau da kanta. Baba ya ce "Ja'ira ke wace irin Yarinya ce Uwata, baki iya gaisuwa ba?" "Yi haƙuri, ina wuni?" Ta faɗa a kunyace. "Ƙyaleta malam Hassan, tun da bata gaisheni ba, ai gara ni in gaisheta, tawa gaisuwar zaki amsa" Amina tayi shiru cike da kunya, dan ta san bata kyauta ba sam. "Zo" yayi Maganar yana kallonta. Ta tashi daga kan bencin, ta matsa jikin motar. "Meyasa baki je lesson ba yau?" "A makarantar aka ce mu huta yau" ta bashi amsa tana kallon ƙasa. "Kina gane karatun dai ko?" Ta ɗaga kai alamar eh. Alhaji Ahmad ya kalli Baba ya ce "Buɗe mini gate ɗin" Baba ya amsa da to, ya tafi buɗe gate. Ya sake mayar da dubansa gareta ya ce "Me zaku dafa yau da daddare?" "Hajiya ta ce, a dafa kuskus da miyar ganye" ta bashi amsa tana kallon ƙasa Alhaji Ahmad ya ce "Likita ya sanya mini ƙa'idoji, saboda sugar na da ya hau, ki dafa mini faten dankalin turawa, da alayyahu, zan yi dinner da shi, yau zaki karatun dare ne?" "Eh insha Allah" "Idan na dawo, zan miki magana ki kawo mini" Ta jinjina masa kai, shi kuma ya ja motar ya fice. Har aka yi lectures aka gama, Fadila na ankare da Yazid, a hankali yake komai, bashi da lafiya, faɗa ne ba zai yi ba, gefe guda kuma ta danganta abun da wulaƙanci da malamin ɗazu yayi masa, sai kuma ta tuna Cewar abu ne mawuyaci, kaga wani abu mai kama da fushi a tare da Yazid kome za a yi masa, wannan murmushi dai sai ka ganshi a fuskarsa. Amina ta koma cikin gidan, tayi sallar la'asar, ta shiga kitchen, dan ta san babu lallai Hajar ta kuma yin wani abun, tunda kusan ita tayi aikin yau. Tun azahar Fadila ta dawo gida, dan har tayi wanka ta kintsa ta dawo falo ta zauna, suna hira da Mummy. Da sallama aka buɗe ƙofar falon, daga Mummy har Fadila suka mayar da hankalinsu kan ƙofar, wata farar mata ce ta shigo, ita da wata matashiyar budurwa, suturar da ke jikin matar kawai ya isa ya nuna maka Arziƙi ya zauna. Suka yi sallama, Hajiya Zainab ta amsa tana bin su da kallon rashin sani. Suka ƙarasa cikin falon suka zauna, suka gaisa da Hajiya Zainab, ta amsa ba yabo ba fallasa, dan suma taga ba kalar talakawa bane. Matar ta faɗaɗa murmushinta ta ce "Na san ba zaki shaida ni ba, wannan 'ya ya ce Azima, suna Makaranta ɗaya da yarinyarki Amina, na shigo nan unguwar wurin wata ƙawata, Azima ta nuna mini gidan, nace bari in tsaya mu gaisa" Mummy ta haɗe rai ta ce " 'yar aiki dai ko?" Maman Azima ta ce "Eh to hakan, ai ɗa na kowa ne, dan in saya ya sanya na ce 'yar ki" "A 'a ba wata sayawa, meye haɗina da ita da zaki jingina mini ita wai 'ya ta? Aiki kawai take mini" Mamaki ya kama maman Azima, yadda Hajiya Zainab ke zaƙalƙalewa, tamkar wadda aka dangantawa ɗan shege. "To shikenan na fahimta, 'yar aikin ki, mu gaisa sai in wuce" A wulaƙance Mummy ta ce "Sai ku jira ta fito, dan dai bani zan tashi in tafi yawon kira muku ita ba, ko kume tashi kibi wannan ƙofar, kitchen na nan, ki kirawota" tayi maganar tana kallon Azima. Azima ta kalli Amminta, Ammi ta jinjina mata kai. Azima ta tashi, ta ta shiga ƙofar, cikin ikon Allah, ta tarar da Amina na ta aikinta. "H Shanono" Azima ta faɗa da ɗan ƙarfi, Amina na waigowa taga Azima tayi tsalle ta rungumeta tana murna. "Azima, ya akai kika zo baki gaya mini ba?" "Ke sauri muke, Ammi na falo muje ku gaisa zamu tafi" Cikin mamaki Amina ta ce "Dan Allah dagaske har da Ammi kuka zo, muje in ganta" Tare suka fito falon da Azima, Amina ta ƙarasa gaban Ammi ta durƙusa tana gaisheta. Cikin fara'a Ammin ta amsa "Lafiya ƙalau Amina, ya karatu Azima ta ce mini makarantarku ta zaɓe ki, a Quiz ɗin su na ƙasa" "Eh Ammi" "To a dage ai ta karatu, Allah ya bada sa'a, Azima ce ta nuna mini layn naku, na ce bari in Shigo mu gaisa" "Amma kuwa naji daɗi Ammi, bari in kawo muku ruwa ku sha" "Babanki ya saya ya ajiye ne?" Cewar Mummy, cike da son ta wulaƙanta Amina a gaban mutane. Jikin Amina yayi sanyi ta sunkuyar da kai, Azima tayi mamakin abin da Hajiya Zainab ta faɗa, dan bata taɓa sanin irin zaman da Amina take kenan ba, saboda duk surutun Amina bata wannan zancen. Ammi ta ce "Bakomai Amina, a ƙoshe muke ina da ruwa a mota" Ta ƙarasa maganar suna miƙewa tsaye, jiki a sanyaye Amina ta ce "Bari in rakaku mota". "Ke, da kika samu na barki ku ka gaisa, zaki wuce ki cigaba da yi mini aikina ko saina taso kanki?" Har cikinta haka Amina taji ɗacin dizgin da Hajiya Zainab ke mata a gaban baƙi, sai dai ta kasa daurewa sai da hawaye suka zubo mata, cikin ƙoƙarin mayar da hawayen, ta ƙaƙalo murmushi ta ce "Ammi ku gaida gida, Azima sai mun haɗu a school, next week za'a koma insha Allah, Ammi na gode sosai". Kasancewar Ammi mai matuƙar son 'ya'ya, ya sanya ita ɗa ko ba nata bane yanzu zai shiga ranta, ba ta son biyewa Hajiya Zainab, zasu iya yin babu daɗi, dan ita ta zo gidan, kuma bata san me hakan zai haifarwa da Amina ba, haka suka bar gidan rai a matuƙar ɓace. Ko da Amina ta koma kitchen, tana aiki tana kuka, kamar wadda babarta ta mutu. Fadila ta gyara kwanciyarta ta kalli Mummy ta ce "Mum, meyasa ki ka yi haka? A Arziƙin da yake gidan nan, meye dan an bada ruwa?" "To uwata, ai naji matar tana naniƙa mini yarinyar ne, gara in nuna mata matsayin yarinyar a gidan nan" daga haka Fadila ba ta kuma cewa komai ba. Wata irin shaƙuwa mai ƙarfi ta shiga tsakanin Hafsa da Khalil, duk da baya gari, amma kusan kullum suna tare a waya, gashi a wannan karon ya kasa samun excuse of duty ya koma gida, ko dan ya ga Hafsa, saboda yadda ya dinga komawa gida a kai a kai a baya. Yanzu yana zaune a ɗakinsa yana video call da Abdul, yana sake labarta masa irin so da shaƙuwar da ke tsakanin sa da Hafsa. Har yake ce masa "Ka san wani abu, ina kuma dawowa gida, zan yi magana a gida a san abin yi, dan ginina na nan Abuja ya kusa kammaluwa. Abdul ya ce "Mhmm haka ne, to yanzu tsakanin Mummy da Daddy, wa zaka fara sanarwa?" Ɗan Jimm Khalil ya yi, saboda Abdul ya tuna masa wani abu da yake yawan mantawa, ya san ko Daddy ya amince ida Mummy bata amince ba a isa an yi auren nan ba. Nan da nan ya yiwa Abdul sallama, ya ajiye wayar ya dulmiya kogon tunani. Ɓangaren Hafsa ma tun da Allah ya sa Khalil ya sanar da ita very soon zai turo iyayensa, take tunani wurin wa zai tura iyayen nasa? Dangin mahaifinta da basu ɗauke su a bakin komai ba ko kuma wa? Idan kuma dangin mahaifin nata suka mata sharri a wurin iyayen Khalil fa, mussaman idan suka ga suna da rufin asiri fa? Ire-iren wannan tunanin ya hanata sukuni, kuma ta kasa tattauna shi da kowa ciki har da Mama. Amina tun tana jiran Daddy ya dawo, har ta fara gajiya, dama a falo take zaman jiran nasa, ta kasa karatun sam saboda damuwa da ɓacin rai, ta zubawa TV ido tana kallon wani Film a MBC2 Captain Philips, gaba ɗaya tausayin jarumin ya cika mata zuciya, ji take tamkar ta shiga ta kai masa ɗauki, bayan damuwar da take ciki, ta ƙara da ta film ɗin da take kallo. Film ɗin ne ta samu ya ɗauke mata hankali, dan har ta fara tunanin ta ajiye masa Abincin a falo tayi tafiyarta, dan kowa ya kwanta sai ita kaɗai. Sai wajen goma saura ya shigo Alhaji Ahmad ya shigo falon, ya shigo da sallama, Amina ta ɗan kalleshi ta amsa a hankali ta mayar da hankalinta kan tv. Be kulata ba ya nufi sashinsa, da sauri ta ce "In kawo Abincin?" "Dama kin ganni?" Ya faɗa ba tare da ya waiwayo ba. "Eh" ta faɗa a sanyaye. "Zan fito in karɓa, ki jirani" ya wuce abinsa. Kawai Amina ta fashe da kuka, yadda aka mayar da ita kamar wata baiwa, kowa abin da ya ga dama yake mata, banda wulaƙanci wannan wane irin abu ne, bayan wancan jiran da tayi, sai tayi wani again? Ta cigaba da share hawaye, tare da dana sanin zuwanta birni. Sai goma da rabi, Alhaji Ahmad ya leƙo falon ya ce "Yauwa kawo mini falona, ki haɗo mini da apple guda uku, sannan ki taho da littafinki da biro" Amina ba ta amsa ba, ta tashi tana cigaba da share hawaye. Alhaji Ahmad ya bita da kallo, da tunanin meye ya sakata kuka. Ta ɗauko kayan Abincin, ta nufi sashin Daddy, tana ta Addu'a, tare da ƙudurce tana kai masa zata ajiye masa ta fito. Sai dai da ta shiga taga baya falon, ta tsaya saroro tana bin falon da kallo. Ta wani corridor ya leƙo, ya yi mata alama da hannu ta zo, gabanta ne ya shiga faɗuwa, tabi bayansa tana waige-waige, dan bata taɓa sanin da wurin ma a cikin gidan ba. Wani ɗaki ya buɗe ya shiga, Amina ta tsaya daga ƙofar tana leƙa ɗakin, ya haɗu ɗakin, an malaleshi da wani irin lallausan carfet, ga wani irin sanyin Ac da ƙamshin turare da ke tashi, sai kuma computer ta kai goma sha biyu a cikin ɗakin. "Ƙaraso mana" yayi Maganar yana ƙoƙarin kunna wani socket,kamar sokuwa haka ta ƙarasa shiga, tana waige-waige, ya nuna mata in da zata ajiye masa Abincin. Ta zo ta ajiye, zata juya ta fita, ya ce "Zo ki zauna a nan" ya nuna mata kujerar dake gaban wata Computer. Da ƙyar Amina ta ɗan ɗosana ta zauna, fuskarta duk sauran hawaye. "Kukan me kike?" Ai kamar ya kuma taɓo mata in da yake mata ƙaiƙayi, ta fashe da kuka. Be kuma ce mata komai ba, ya zuba Abincin, tare da gyara zaman gilashinsa, ya fara ci, sai da tayi ta gama, yana danna system ya ce "Ina jinki, kukan me kike?" Ji tayi kamar ta gaya masa abin da Mummy tayi mata, amma ta fasa ta ce "Bacci nake ji, kuma kaƙi ka zo ka karɓi Abincin, duk na gaji" Murmushin gefen baki yayi ya ce "Ko dai ke da matar gidan ne, kike ƙoƙarin hucewa a kaina?" Wasa ta shiga yi da hijjabinta, ba tayi magana ba. Ya miƙa hannu, ya kunna system ɗin gabanta, ya shiga wani video, yadda ake koyar da tips na cin quiz a sauƙaƙe. A nan ta mayar da hankalinta ta nutsu tana kallo, har tana jotting wasu abubuwan a littafinta, shi kuma ya cigaba da cin abinci. A haka video ya ƙare, ta ɗago tana kallonsa, sai dai hankalinsa na kan system ɗin gabanshi yana dannawa. "Kin gama gani?" Ta jinjina masa kai alamar eh. "To yi mini bayanin me kika fuskanta?" Nan ta yi masa bayanin abubuwan da ta fuskanta. "Masha Allah, kina fahimta sosai". "To zaka tambayar mini Baba zuwa Abujan, kar in ta wahalar banza ina karatu?" "Zaki je insha Allah" "Zaka tambayar mini Baban?" Tayi maganar tana sake tattara hankalinta a kansa. "Insha Allah, akwai abokina a Abuja, idan ma baya son in da za ajiyeki ne, sai ki zauna a can wurin abokina, zuwa a kammala ku dawo" "To kai a ina kake aiki?" "Lagos" ya bata amsa "Amma aka ce a Abuja kake, kuma meyasa baka koma ba?" "Eh na koma Lagos da aiki, na zo hutun ƙarshen shekara" "To wannan computocin me kake da su?" Amina tayi maganar tana kallon ɗakin. "Bayanai na, dana aikina ne a ciki" Amina tayi murmushi ta ce "Aikuwa ina son in iya danna computer Wallahi, ka koya mini aikin da kake nima in dinga danna computer" Alhaji Ahmad ya lumshe idanunsa ya a buɗe su a kan Amina, duk da baya son yawan surutu, amma abin da yafi buƙata a yanzu da shekarunsa suka fara ja, irin abubuwan ɗebe kewa, da zama ayi hira da shi, Hajiya Zainab kuwa hankalinta a kan kasuwancinta da kuma 'ya'yanta suke, bata fiye biyewa zama da shi ba, balle tayi masa hiraraki, shiyasa ya kan tsinci kansa da jin daɗin yawan tambayoyin Amina, da kuma surutan ta marasa ma'ana wasu lokutan. "Ba ka ce komai ba" "Me ma kika ce?" "Aikin da kake a computer zaka koya mini, nima in dinga taɓawa" "Sayar da kuɗi nake" ya bata amsa yana murmushi. "Sayar da kuɗi kuma, ta yaya za a sayar da kuɗi kuma?" "Ana yi mana, ni ina sayarwa" yayi Maganar yana murmushi. Amina ta ɗan yi shiru ta ce "Ban taɓa ji ba". "Yau ai gashi kin ji" ganin tana hamma ne ya sanya ya ce "tashi kije ki kwanta". Amina ta tashi ta nufi hanyar fita. "In biyoki da kwanukan ne?" Ya faɗa da ɗan ƙarfi dan ta ji". Ta waiwayo ta dawo ta kwashi kwanukan tayi waje. Kashe komai yayi, ya tashi shima ya bar ɗakin, sai dai ya bar shi a buɗe bai rufe ba ya tafi ɗakinsa. Da safe Alhaji Ahmad ya shirya da wuri, dan yana da wani uzuri na gaggawa. Hajiya Zainab tayi masa rakiya, yana shirin fitowa ya tuna ƙaramar wayarsa a ɗakin Computers ɗinsa ya barta, ya kalli Hajiya Zainab ya ce "Duba mini wayata a ɗakin aikina please" Ba tare da ta ce komai ba, ta tafi ɗauko masa wayar. Sai dai data tashi dawowa, yayi tozali da littafin Amina da ta bar shi a ɗakin a hannunta, ta nufo shi tana masa wani irin kallo da ya kasa tantancewa. AYSHERCOOL 0808102143GABA DA GABANTA BY AISHA ADAM (AYSHERCOOL/JAKADIYAR AREWA) PAGE 28-29 Sai da hantar cikin Alhaji Ahmad ta kaɗa, saboda tsananin tsoron da ya shiga, har wata ƙishirwar wucin gadi ce ta kama shi, amma cikin dakiya da maziya ya maze ya bari ta ƙaraso. "Meye wannan nake gani haka?" Tayi maganar tana nuna masa littafin. Cikin rashin fahimta ya kalleta ya ce "Ban fahimta ba" "Littafin 'yar aiki na gani a ɗakin aikin ka". Alhaji Ahmad ya miƙe tsaye ya ce "Eh, na shiga zan yi amfani da ɗakin, amma duk yayi ƙura, duk da ba na shiga sai ina buƙatar yin aiki, ai Yakamata ki dinga sakawa ana gyarawa, ko gogewa ne ayi, ganin ba ayi hakan bane ya sa na bawa yarinyar umarnin gyarawa, ina ga mantawa tayi da shi a ciki". Har zuciyarta ta ji ta gamsu da bayanin da yayi mata. 'haka ne, hankalina ne bai kai a gyara ɗin ba, kuma nafi son idan za a gyara ɗin, a gyara ina wurin kar ayi maka ɓarna. A dawo lafiya" "Yauwa na gode" ya amsa cikin mazewa ya juya ya bar Falon, yana yiwa Allah godiya da ya rufa masa asiri. Amina kuwa da shirirtarta, tunani ta dinga yi a kan ta yaya ake sayar da kuɗi, kamar yadda Daddy ya gaya mata, amma bata iya gano ta yadda za'a sayar da kuɗi ba. Lesson ɗin da take zuwa Makaranta ta fara gajiya, dan babu hutu sam, ga aikin gidan nan ba afuwa, kullum da abin da za'a ƙaƙalo a saka ka. Yau Fadila a makare ta zo ita ma, motarta ta so ta bata matsala a hanya, sai dai tana zuwa ta tarar da kankiya ne a cikin ajin, bata ko bi ta kansa ba ta shiga ajin, sai dai ta hango Yazeed a wurin zamanta, a jikin window. Tuno ranar da tayi masa wulaƙanci tayi, har ciwonsa ya tashi, dan haka ba tace masa komai ba ta zauna a kusa da shi. Wani irin warning glance sir Kankiya yayi mata, amma ta share shi, ta ciro littafinta daga jaka. Gaba ɗaya annurin fuskar Kankiya ya ɗauke, ya ɗaure fuska gashi baya son ya aikata wani abu, da zai sa wani ya fuskanci son Fadila yake, kuma yana adawa da Yazid. Haka ya gama lectures ɗin yana harar Fadila, ita kuwa ta nuna sam bata san ma me yake yi ba. Bayan fitarsa ta ɗan saci kallon Yazid, ta basar, shikuwa ƙamshin turarenta ya hanashi sukuni. Littafinta ya janyo, ya juya bayan yayi rubutu "Ina kwana ukuty?" Kallonsa tayi, gata gashi maimakon yayi mata magana, amma saboda wani salon rainin hankali shine ya rubuta mata. Banza tayi masa taƙi kulashi. Ya sake rubuta mata 'Ya kika yi shiru, ko in tasar miki daga wurinki, naga kin haɗe rai?" Babban abin da ya bata mamaki,bai wuce yadda yake rubutun da irin handwriting ɗinta ba. Kallonsa tayi cikin mamaki tana sake kallon rubutun, ba wanda zai ce ba nata bane. Ganin tana kallonsa tare da kallon rubutun ne ya sanya shi ɗage mata gira ɗaya. "Talk" ya sake rubuta mata. "Bani littafina, tun da kurmancewa kayi yau" Murmushi yayi ya ce "Ban kurmance ba, azumin magana nake". Ta zura littafin a jaka, ya miƙo mata wasu takardu, tasa hannu ta karɓa tana dubawa. Presentation ɗin da za suyi ne, na 'yan group ɗin su gaba ɗaya yayi musu, kuma a rubuce ya kai fullscap bakwai,tabi tsararren rubutun nasa da kallo, sannan ta kalleshi cikin mamaki 'Wai duk daga jiya zuwa yau kayi wannan?" Ya jinjina mata kai alamar eh. "Amma ai ka wahalar da kanka da yawa, wannan uban rubutun haka? Shikenan Sai mu kai Cafe a buga?" Duk da yau baya son yin Magana, amma yaji daɗin yadda ta yaba ƙoƙarin sa. Dan haka ya ce "Eh, da ina da babbar waya ko system, da a ciki zan mana sai ayi printing, kowa a bashi wanda zai yi presenting" Fadila ta ce "System ɗina na mota, bari in ɗauko sai in fara typing ɗin, kar aikin yayi maka yawa" ƙarara yake ganin tausayawa a idonta. "Muje in rakaki" Suka tashi suka jera zuwa in da motarta take, ta buɗe ta ɗauko system ɗin sannan suka dawo aji. Ya nemi wuri ya zauna, ta buɗe system ɗin ta kunna, hotonta ya bayyana a kan lock screen, ta saka password sai ga wani ya bayyana a wallpaper ɗin ta, ba ƙaramin tafiya da Yazeed hotunan suka yi ba. Amra ƙawar Fadila a baya, banda yanzu da ta daina shiga sabgar ta, saboda Amran na da wasu halaye da ba su yi mata ba, ta ƙaraso in da su Yazid suke zaune, suka gaisa sama-sama da Fadila. Sannan ta kalli Yazeed ta ce "Yaya Yazid dan Allah wurinka na zo, 'yan group ɗin mu zaka ɗan taimaka mana a kan presentation ɗin da zamuyi" "A yanzu dai aikin namu yake yi, kuna iya jira zuwa ya gama" Fadila ta bata amsa. "Bafa da ke nake ba" Amra ta mayar mata da martani. Yazeed ya ce "Afuwan Amra, bari in kammala namu, sai in zo" Guntun tsaki Fadila tayi, ta cigaba da operating system ɗin. Janyo System ɗin gabansa yayi, dan a ganinsa bata sauri a typing ɗin, tunda ya zuba yatsunsa a kan keyboard ɗin nan yake sarrafasu cikin gwanancewa kamar wani inji. Fadila ta ƙureshi da ido, shi kusan komai ya iya, ana batun Mutane gifted bata taɓa gazagata hakan ba, sai a kan Yazeed. Ji tayi kamar ta tambayeshi a ina ya koyi computer, amma ta basar. Lokacin sallar azahar yayi, Yazeed ya ce "Zai je yayi sallah, idan ya dawo zai cigaba. Ta tashi ta bashi wuri, ya tafi salla, ita ma tashi tayi ta bar System ɗin a wurin saboda careless, ta tafi yin salla da cin abinci. Bayan ya dawo ya tarar da komai yadda ta barshi, ya zauna ya tattara mata litattafanta, minimising yayi, ya zubawa kyakywar fuskarta da ke kan screen ɗin system ɗin ido, yana jin yadda wani abu ke sake fuzgarsa game da ita. "Ina sonki Fadila" ya furta yana cigaba da ƙarewa screen ɗin kallo. "Malam Yazeed wai haryanzu baka gama ba?" Ya ji murayar Amra a kunnensa. Yazeed ya kalli Amra ya ce "Ku mini haƙuri, na kusa gama namu, idan na gama zan zo in sha Allah" "To shikenan" ta amsa masa tana ƙoƙarin barin wurin, Fadila ta shigo hannunta da leda, ta ƙaraso ta zauna, tana kallon screen ɗin system ɗin. "Ka kusa gamawa ne?" "Eh, saura kaɗan, so nake in yi in gama, wancan group ɗin suna jirana". Fadila ta yamuatsa fuska ta ce "Kaga kayi mana abinmu a nutse Please, ba suna da waya ba suje suyi mana, ko su tafi Library" Yazida ya ce "A'a ba'ayi haka ba, zasu ga ban kyauta musu ba, kuma wulaƙanci babu daɗi" Taɓe baki tayi ta miƙa masa leda ɗaya gabansa. Ya kalli ledar ya ce "Meye wannan?" "Abinci" ta bashi amsa. "Alhamdilillah na gode, amma na ƙoshi" Cikin tsiwa ta ce "Saboda na zuba wani abu a ciki?" Ba tare da ya kalleta ba ya ce "Idan ma kin zuba wani abu a ciki da ina jin yunwa ba ruwana cimyewa zan yi" "Wannan shi ne karo na biyu na baka Abinci ka ƙi ci, meye dalili?". Yazeed ya ce "Nifa yau azumi nake" "Dama ana azumi ranar talata?" "Eh mana, azumin Annabi dawud, yau kayi gobe ka sha ruwa" Tsuke fuska tayi ta ce "Sannu waliyyi, kamar fa raina mini hankali kawai kake yi, ba wanda zai iya irin wannan azumin" "Inji wa? Gwauraye na yin irin wannan azumin, Annabi Sallallahu alaihi Wasallam ne ya bawa samari shawarar yawan yin azumi idan... Sai kuma yayi shiru. Gaba ɗaya Fadila bata gane in da zancen Yazeed ya dosa ba. "Kaga ni ban taɓa ji ba, ka dubo wata ƙaryara dai kayi" Ɗan tsuke fuska yayi, ya saka idanunsa a nata, "Ni ne nake ƙaryar?" Tsiwa ta so yi, amma sai ta kasa jikinta yayi sanyi, idanun Yazid suka yi tasiri a kanta, wanda sai da idanunta suka yi nauyi, ta janye idanunta tana ɗan tura baki. Ɗauke idonsa yayi shima, yana jin daɗin yadda yake yi mata kwarjini wasu lokutan, har ta kasa magana. Kusan mintuna goma, yana typing, ya ƙi taɓa ledar Abincin. Can ta kuma kallonsa ta ce"Wai ba zaka ɗau Abincin nan ko ruwan ka sha ba?" "Wai ina ruwanki dani ne, nace miki azumi nake" "Wane irin azumi ne da za'ace wani azumin samari, ba azumin tsofaffi kawai ake ba?" Sosai Yazid yake dariya, wata amsa ya so ya bata, amma yaga amsar tayi nauyi da yawa, dan haka ya ƙyaleta ya cigaba da dariya. Ganin yadda yake dariya sosai, haƙoransa suka bayyana ya sanya ta ce "Wallahi ba azumi kake yi ba" ta faɗa cike da tsiwa. "Subhanallah, ya aka yi kika san ba azumi nake ba? Shikenan ba azumi nake ba ba zan ci ba" Haushi ne Yakamata, ta miƙe tsaye ta fara jan system ɗinta. Ya kalleta ya ce "Ya dai?" "Bani System ɗina tafiya zan yi" riƙewa yayi yana murmushi ya ce "Sorry yi haƙuri, zan ci" yayi maganar wani irin farinciki yana ratsa shi, kamar a mafarki yake ganin faruwar al'amarin, wai Fadila ce take jin haushi dan be karɓi abin hannunta ba. "Kar ma kaci, bani tafiya zan yi" "Yi haƙuri in ƙarasa, sai muje Cafe a cire, nima sonake na gama da wuri, idan lecturer nan bai zo ba, zanje wurin sir Kankiya, mun haɗu a masallaci ya ce idan na gama lectures in je Office ɗinsa" Ɗan saroro tayi, ta kalleshi ta ce "Me kayi masa?" "Nima ban sani ba, kawai dai ya ce inje" "Yi sauri ka ƙarasa muje" "Muje ina?" "Wurinsa" ta bashi amsa. "Ai bece muje tare ba" Fadila ta ce "Ni dai yi sauri ka gama" Ita kanta har mamakin kanta take yi, yadda yau ta saki jiki da Yazeed, ita gaba ɗaya a rayuwarta bayan 'yan gidansu sai Yusra, sukaɗai ne mutanen da suke bata nishaɗi, dan ita ba shiga harkar mutane take ba, amma Yazid mutum ne mai matuƙar barkwanci, duk haushinsa da kake ji, sai ta fuskanci in ka zauna tare da shi zai baka dariya, sai dai shima ba kowa yake shiga harkarsa ba, balle ka gane tsananin sauƙin kansa, gashi baya fushi abinsa, ga rashin girman kai. Gaba ɗaya ya manta da su Amra da ke jiransa, ya kammala typing ya kalleta ya ce "to muje Cafe a cire, sai a rabawa 'yan group" "Sai fa kaci Abincin nan" Ya ɗan waro ido "In karya azumin nawa?" "Ai ba azumi kake yi ba" tayi maganar tana sake tsareshi da ido. Ta saka shi a gaba, ya ciro pack ɗin Abincin, soyayyar doya ce da miya sai uban nama fal a cikin miyar, sai ruwa da lemo. Ruwan yai bisimillah ya fara sha. Fadila ta ce "Kana malami kana ƙarya, yanzu azumin kenan?" "Niba malami bane, ɗalibi ne, kuma aike kika karya mini Azumin" "Wata ƙaryar again" tayi maganar tana hararasa. Bece mata komai ba, ya fara cin doyar da ƙamshin miyar kawai ya sanya yawun bakinsa tsinkewa, Fadila ta juya masa baya tana danna waya, yayin da shi kuma gaba ɗaya ya kasa sakewa, Yazeed yana da matuƙar gudun zuciya da abin da zai sa a masa gori wata rana, ya ci Abincin nan ne kawai dan yana son ganin yayi abin da zai sa Fadila taji daɗi, ba wai dan yunwar da ta addabi cikinsa ba. Ya kammala ya dinga yi mata Addu'a, har sai da ta haɗe rai, saboda godiyar tayi yawa. Sai da suka fara zuwa Cafe, suka ciro aikin, sannan Fadila ta ce suje wurin Sir Kankiya. Sai dai da suka je, suka tarar baya nan, suka zauna zaman jiran Kankiya, Yazid ya cewa Fadila ta tafi kawai zai jira shi, amma taƙi, saboda ba ta san me zai cewa Yazid ba. Ƙarshe Fadila ta gaji da zaman, tayi masa sallama ta tafi, a kan Cewar duk yadda suka yi da shi ya gaya mata. Yazid ji yake kamar yayi tsalle dan murna, saboda kulawar da Fadila ta nuna masa yau, zuciyarsa bata taɓa kamuwa da tsananin son abin da yake kasancewa da shi ba kamar Fadila. Alhaji Ahmad ya dawo gida, kusan ƙarfe biyar na yamma, sai dai daga yadda suka gaisa da Baba, ya lura kamar akwai damuwa a tare da shi. Alhaji Ahmad yayi parking, tare da kallon sa ya ce "Malam Hassan, lafiya naga kamar kana cikin damuwa?" Baba ya risuna ya ce "Amina ce haryanzu bata dawo daga Makaranta ba, gashi ban san makarantar tasu ba balle in bi bayanta, nayi wauta yakamata ace tun tuni na san makarantar ta su" Daddy ya ce "Subhanallah, kwantar da hankalika, bari in je makarantar da kaina" Baba ya ce "A'a ranka ya daɗe, da ka kwatanta mini ni sai inje in duba" "Haba Malam Hassan, Amina ai 'ya ta ce, idan Fadila ce zan wakilta wani ya nemota ne? Bari inje" yayi reverse ya ja motar ya ya nufi makarantar su Amina. Alhaji Ahmad kai tsaye cikin makarantar ya shiga, ofishin director ya shiga, suka gaisa, Daddy yake tambayarsa yaji shiru haryanzu Amina bata koma gida ba. Director yayi murmushi ya ce "Mun tsaresu ne, lesson ake tayi musu, lallai muna son wannan karon branch ɗin Kano, muci comptetions ɗin wannan shekarar, kuma Alhamdilillah Amina akwai basira, duk da ɗazu na zagaya ajin nasu, taƙi mayar da hankali wai ita ta gaji gida zata tafi" Daddy yayi murmushi ya ce "Dole ta gaji, tun safe fa, kuma gashi in Allah ya kaimu next week, za kuyi resuming makaranta, kaga ita gaba ɗaya bata huta ba kenan" "Haka ne, amma da anyi an gama shikenan, kuma idan Allah yasa tayi nasara, zaku yi alfahari da hakan, tana da ƙwazo sosai" "Gaskiya ne, yanzu dai a ƙyaleta, tun da tace ta gaji ba ganewa zata yi ba, a turota mu tafi gida" Director yayi murmushi ya ce "Dama yanzu za a tashe su su tafi, kuma dan wannan ranka ya daɗe ai da ko waya kayi, da kaina ma sai in dawo da ita gida ba sai ka zo ba" "Ba komai, a turo ta mu tafi" Suka fito daga Office ɗin tare da Alhaji Ahmad. Tunda aka sanarwa da Amina Babanta ya zo ɗaukarta, ita zatonta Baba ne, ta san a rina, yadda tayi yammar nan, dole hankalinsa ya tashi ya biyo bayanta. Sai jefa ƙafa kawai take, idanunta sunyi fuci-fuci sun yi jawur, jakar ma yadda ta saƙalata da gani ta mata nauyi. Mamaki ne yakamata ganin Daddy a harabar makarantar. Murmushi yayi mata ya ce "Sannu, sai kace wadda ake bawa training ɗin sojoji, duk kin yi wujiga-wujiga". Aikuwa kamar ƙiris take jira. Kamar za tayi kuka ta ce "Ni ba zan ƙara zuwa lesson ɗin nan ba, duk anfi wahalar da ni, gashi na gaji ga yunwa nake ji, bayana sai ciwo yake da cikina" tayi maganar a wahale, ƙwallar haushi na taruwa a idonta. Alhaji Ahmad yayi murmushi ya ce "Eh gaskiya kam basu kyauta miki ba, ace mutum yana jin yunwa, kuma ga mutum rago Sarkin kuka, ace an hana shi tafiya gida dole a sa mutum ya gaji ai, har ya fara kuka" ya ƙarasa maganar yana murmushi. Amina ta gane tsokanarta ya ke yi, sai kawai ita ma tayi murmushin, sannan ta ce "Ya aka yi ka san makarantar mu?" "Tunani nayi, zuciyata ta bani nan ce makarantar" ɗan shiru tayi tana tunanin ya za ayi haka ya yiwu. Buɗe mata gaban motar yayi ya ce ta shiga. "Wai gaban motar zan shiga?" "A'a tayar motar zaki hau". Ya faɗa tare da zagayawa mazaunin direba. Ƙarewa motar kallo take, irinta kusan uku ne a gidan, Alhaji Ahmad ne kawai yake hawansu, baya hawa ƙananun motoci sai manya manya, ko nauyi basa masa wurin tuƙawa. Tayi maganar a zuciyarta. Sai da tayi bismillah sannan ta hau motar, wani irin sanyi tare da ƙamshi suka ratsa hancinta, abinka da wanda yake a gajiye, ta sake kashingiɗewa a jikin seat ɗin motar. Ya sawa motar lock tare da rufe glasses ɗin, ya ƙaro sanyin A.C ya fara jan motar. "Tun da nake ban taɓa hawa mota me daɗin wannan ba, ko ta Khalil ba ta kai wannan daɗi ba". "Allah ko?" Ya faɗa yana murmushi. "Wallahi kuwa, kamar in bacci, to wai motar bata da nauyi ne, naga tayi girma da yawa kuma kana tuƙata a haka" "Ko in sauka in baki wuri ki gwada kiji" "A' a rufamini Asiri, ina zan iya" Sai kuma tana ɗan yamutsa fuska ta riƙe cikinta. Ya kalleta cikin kulawa ya ce "Ya dai?" "Cikina ne yake ciwo" "Yunwa kike ji, daga yau idan zaki zo lesson, ki dinga zuwa da Abinci, zan bawa babanki kuɗi, ya dinga baki kina sayen Abinci" A ɗan tsorace ta ce "Taɓ salon ya ce roƙonka nayi, ni bana roƙo, kuma daga yau ba zan sake zuwa wannan lesson ɗin ba, na gaji ai nasara ta Allah ce, ba wannan izayar ce zata sa in ci ba" tayi maganar ranta a ɓace. Alhaji Ahmad ya ce "Baki san abin da yake tattare da yin nasararki ba, kiyi haƙuri nasara sai an wahala take samuwa, sannan idan mun je gida, za kiyi wa Maman Fadila bayanin abin da ya kai littafinki ɗakin aikin mijinta" Zaro Amina tayi ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, a can na bar shi kenan? Na shiga uku me zance mata?" "I don't know" ya faɗa yana ɗage kafaɗa. "Na shiga uku ni Amina, Daddy kai ka jawo mini, baka gayamata kai kace in kai maka Abinci ba, shikenan wataƙila ta koreni karatuna shikenan, idan kuma tayi mini Afuwa kuma ta zageni ni da Baba" kan ta kai ƙarshen maganar, kuka ya ƙwace mata. "Ke kuka baya baki wahala ne? Da wasa nake miki na karɓi littafin, na gaya mata ni na saki aiki a ɗakin, littafin yana wurina, meyasa kika ruɗe haka?" Ajiyar zuciya Amina tayi, tana godewa Allah da ya ƙwaceta, da yau ta san tijarar da zata sha ba ta da iyaka. Tausayin ta ne ya kama shi, da alama ita ma zata sha gwagwarmayar rayuwa kan ta cinma nasara, ya ɗan lumshe idanunsa ya ce "Allah ya rangwanta miki" ya furta a hankali ba tare da Amina ta ji ba. A ƙofar gida yayi parking ya kalli Amina ya ce "Sauka ki shiga, idan kuma in shiga dake ne, idan ta ganki ki mata bayanin abin da ya kai ki motar mijinta kuma shikenan". "A'a yi haƙuri bari in sauka, Na gode Allah ya saka da alkhairi". Bai amsa mata ba, sai binta da yake da kallo. Baba na ganin Amina ya tareta, yana tambayar ba'asin meye ya faru ta daɗe haka? Amina tayi masa bayani, tare da gaya masa Alhaji Ahmad ne ya ɗaukota. "To ki dai kula Amina, hanklina ya tashi sosai" "To Baba ka cigaba da yi mini Addu'a" "Aminatu Addu'a kullum cikinta muke ai" A falo ta tarar da Hajiya Zainab da Khalil, ta durƙusa ta gaishe su, Khalil ya amsa Hajiya Zainab kuwa ko kallonta ba tayi ba, Amina da ta juya baya a hankali ta ce "kanki ki ka yiwa da baki amsa ba' Khalil ji yake kamar ya janyo dare, dan yaje ya ga Hafsa, sai wata fara'a yake ta mussaman. Alhaji Ahmad yayi sallama a falon, suka amsa masa gaba ɗaya, ya kalli Khalil ya ce "Kai saukar yaushe?" Khalil ya amsa da "Ɗazun nan Daddy" "Masha Allah, ya aikin?" "Aiki Alhamdilillah Daddy" "Masha Allah, Ina Fadila ne?" Mummy ta ce "Ta dawo tana ɗaki tana baccin gajiya" Ya jinjina kai ya wuce part ɗinsa. Fadila kuwa bayan littafinta ta juya, tana kallon rubutun da Yazid yayi, sai mamaki take yadda aka yi ya iya kwaikwayon rubutunta, Yazid yana da abubuwan ban al'ajabi. Tunowa tayi da maganarsa wai Azumin samari yake yi, kawai tayi murmushi ta rufe littafin. Khalil miƙewa ya yi, ya bar Falon saboda an fara kiran sallar magariba, yaje masallaci ya dawo, ya shirya cikin wasu haɗaɗɗun ƙananan kaya, ya feshe jikinsa da turare, ya ɗauki kayan siyayyar da ya yiwa Hafsa, ya ɗau motarsa ya fice. Ta wurin da take zaman suya ya fara bi, yaje ya tarar da ita tana ta fama da hayaƙi, ga masu siya sun zagayeta. "Ke ungo nan bani ta naira ɗari ki riƙe canjin" yayi magana yana bata dubu ɗaya, sam bata san Khalil ya zo wurin ba sai muryarsa da ta ji. Murmushi tayi tana kallonsa sanann ta ce "Gaskiya ni wannan zuwan be mini ba, kai kayi kwalliya ni kalleni cikin hayaƙi, kuma baka gaya mini zaka zo ba ba zan kula ka ba gaskiya" Dariya yayi ya tsuguna a kusa da ita "Ni ko a yaya na ganki ƙara kyau kike yi, kawo abun fifitar in fifita miki, sallami waɗan nan" "A'a ka bari kawai, kar kayi ƙaurin hayaƙi" Karɓe abun fifitar yayi, yana ffifita mata wuta, ita kuma tana sallamar masu saya. Suna yi suna hira cike da nishaɗi da jin daɗi. Khalil ya saka ta raba sauran sadaka, ya ce ya saya, ba dan ta so ba Khalil ya tayata suka kwashe kayan, ya rufe motarsa suka hau ɗan sahu tare suka tafi gidansu Hafsa, tare da ledar da yayi mata. Ya zauna a ƙofar gida, ya jirata ta shiga gida tayi kwalliya sama-sama ta fito. Sosai suke hira da Khalil, yana bata labarin wurin aiki. Can ya nisa ya ce "Babyna yaushe zan turo su Daddy ne? Na gaji da zaman Abuja ba mata" "To ni me zance?" "Ban gane me zaki ce ba? Zan sanarwa da Daddy insha Allah zuwa next months zan turo, ginina saura kaɗan, shiyasa zan bari sai na kammala sai in turo" ɗan shiru tayi, sannan tayi ajiyar zuciya. "Ya kika yi shiru, ko ba kya sona?". Murmushi tayi ta ce "Ina sonka Sosai, in ba kai ba sai maliya" tayi maganar cikin dariya. "Wayyo daɗi, dagaske Hafsa?" "Da gaske nake mana" "Kar ki saka in tattaro mutane a ɗaura mana aure yanzu" Hafsa ta ce "Sai kace auren sadaka" "Ai sai yafi albaraka, yakamata mu fara shirin biki ma" "Ka san wani abu, yanzu kaje gida ka huta, kaga yau ka dawo" "A taƙaice dai korata kike yi?" "Ya za ayi in koreka, ni kaina ban gaji da ganinka ba, kaga motarka tana can, ga sanyi ko so kake kayi mura? Kaje gida ka huta kaji nawan" "Yau ɗin nan jina nake wani na musamman, tattali da kulawa ta zahiri daga abar ƙaunata" "Ni kaina mamakin kaina nake yi, ka kawo sauyi da farinciki a rayuwata, na gode Allah da ya sa baka yi zuciya ka rabu dani ba" "Baby Hafsat, duk wanda yaji halin da kika shiga, dole zai tausaya miki, Hafsa ina sonki, zan ɓoye sirrinki zan miki adalci in sha Allah in kula da ke, dan Allah ki aureni kar ki canza ra'ayinki a kaina" "Zuciyata na gazgata duk kan kalaman da kayi mini, kuma ina sa ran ba zaka bani kunya ba, ina sonka Mu'azzam" "Kar ki sa in suma dan daɗi mana" tashi tsaye tayi tana dariya, "muje in raka ka titi" "A'a gari da sanyi, koma gida ki huta, idan naje gida zamu yi waya" "Allah ya kai mini kai gida lafiya" "Naga idan ban yi da gaske ba, yau a a soron Mama zan kwana" ya bata ledar siyayarta ya tafi. Jinsa yake kamar wani sabon ango, cike da nishaɗi da jin daɗi ya nufi gida. Kai tsaye cikin gida ya nufa, domin ya ci Abincin dare. Sai dai yana shiga falon ya tarar da Mummy a tsaye tana huci, tamkar wuta. "Mummy lafiya kuwa?" Ya faɗa yana binta da kallo. "Ban sani ba, daga gidan uban wa kake?" Khalil ya ce "Mummy ban gane.... "Nace daga gidan uban wa kake?" "Wurin Abdul" "Sai naci........... Kai da Abdul ɗin, ni zaka tozarta Khalil? Saboda tsiya da abin kunya? Uban me kake a gaban kaskon mai awara?" Ƙuuuuuuu cikinsa ya bada wani irin sauti gumi ya shiga tsatstsafowa daga goshinsa. Cikin dakiya ya ce "Mai awara kuma?" A hasale ta ce "A'a Ubanka" Ayshercool 08081012143.GABA DA GABANTA             BY AISHA ADAM (AYSHERCOOL/JAKADIYAR AREWA) Page 30-31 *Zuwa ga masau sanya mini litattafaina a shafukansu ba da izini na ba, na barku da Allah, Allah ya saka mini, ina wahala kuna ci da gumina* *Albishirinku masoya, littafin Dare da duhu, da ya samu kyakkyawan rubutu daga gamayyar marubuta uku, AYSHERCOOL, ZEE KUMURYA DA KUMA NIMCYLUV Ya kammala a document, ga mai buƙata ya tuntuɓi wannan lambar dan mallakar naku a kan kuɗi ₦500 kacal* Cike da matsanancin tashin hankali, Khalil ya ce "Dan Allah Mumy waye ya gaya miki?" "Au tuhumata ma kake yi? To ubanka ne ya gaya mini" "Mummy walla.. "Zan taka ka ka mini rantsuwa, mutumin banza da na wofi sakarai, dama ina ankare da take taken ka, na zuba maka idanu in ga in da ka saka gaba, Hajiya Salma da Turai sun je duba shago, suka ganoka a gaban kaskon awara, suna kallonka kuka hau napep, saboda kalen tsiya kuka tafi, har wurin suka je suka tambayar mini, aka ce kana zuwa wurinta wai sonta kake, wallahi Khalil ka bani kunya, kamar bani na haifeka, ko ka manta matsayin ubanka a ƙasar nan? Babu 'yar wanda zaka kalla a manyan attajiran ƙasar nan a hanaka, amma saboda lalacewa da rashin sanin darajar kai, saboda tsiya, bama 'yar masu abinci a restaurant ba, mai soya awara a titi, ashe ita ce gayyara tsiyar da kazo da ita nan kana ci ran nan ko, an maka barbaɗe a ciki ka ci, idan takensu sammako ni a tafe na kwana, ni Zainab ban durƙusa na haifi ɗan da zai kawo mini jinin matsiyat ba, daga kai har ita zan yi maganinku, zan tsananta bincike a kan yarinyar". Kamar Khalil zai ɗora hannu a ka cikin mariraicewa ya ce "Mummy, dan girman Allah kar ki yiwa Hafsa komai, ba ta da laifi ni na kai kana nace ina so" "Zaka rufen baki ko saina falla maka mari, sakarai sususu, dalla ɓace daga gabana ka bar mini falo, zan ga uban da ya tsaya mata har ta liƙe maka" "Dan Allah Mummy ni ki hukunta ni, marainiya ce fa" "Khalil ni nake faɗa kana faɗa? Zan kwarara maka ashar fita ka bar mini falo" ta ƙarasa maganar a fusace tana nuna masa hanyar fita. A sanyaye Khalil ya fice, yana jin yadda wani abu ya tokare masa ƙirji saboda tsananin damuwa da ɓacin rai. Amina ta sha jinin jikinta, ta tsorata da irin ƙyamar da take yiwa talaka, ta rasa me talaka yayi mata tayi masa wannan tsanar haka, ɗanta na cikinta ta saka a gaba, ta ƙare masa cin mutunci saboda ya nuna yana son 'yar talaka, ƙiyyyar ta wuce misali. Fadila kuwa tana tare da Mummy aka kirata a waya aka sanar mata da anga Khalil, tare da mai awara, dan haka bata ji tausayin abin da Mummy ta yiwa Khalil ba musamman idan ta tuna yadda ya watsa mata ƙasa a ido, a kan soyayyar da Yusra take nuna masa. Khalil kuwa wani irin gumi ne ya dinga tsatsatfo masa, saboda azanar tashin hankali, dama ya san a rina, amma yaso ace shi da kansa ya lallaɓata ya sanar da ita, amma wannan algunguman matan suka ɓata masa komai. A gaskiya yana son Hafsa, sai dai ya san babu yadda za ayi ya samu goyon bayan Daddy, muddin ba Mummy ce ta amince ba. Ya tashi zaune yayi shiru, yana cigaba da tunani, wannan shi ake kira da ga ƙoshi ga kuma kwanan yunwa, ya gama gwagwarmayar samo soyayyar Hafsa da ƙyar, a lokacin da ya ke ƙoƙarin ya miƙa hannu ya kamota kuma, Mummy na ƙoƙarin shiga tsakani. Hafsa kuwa cike da murna ta dinga bubbuɗa kayan da Khalil ya saya mata, turaruka da kayan kwalliya, sai kuma kwalin sabuwar waya mai tsadar gaske. Ta dinga murna tana jujjuya wayar nan, tana yiwa Allah godiya ashe ita ma zata yi ta'amalli da kayan zamanin nan. Vibrating ɗin wayarsa ce ya dawo shi daga tunanin da yake yi, ya kai idanunsa kan screen ɗin wayar yaga beauty. Ji yayi kamar kar ya ɗaga, amma ya miƙa hannu ya ɗauka cikin dakiya ya ce "Baby" "Sweetheart, na gode sosai da sosai, Allah ya saka maka da alkhairi, waya na gani sabuwa dal har da layuka guda biyu, Allah ya ƙara maka lafiyar neman halal, Allah yaja kwanan mahaifanka, ya biya musu buƙatunsu na alkhairi ya kare su a duka in da suke, yadda kake faranta mini, Allah yasa ka shiga aljanna kafaɗa da kafaɗa da Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam kamar yadda ya alƙwaratawa masu kula da maraya" Gaba ɗaya jikin Khalil yayi sanyi, idan Allah ya karɓi Addu'ar Hafsa, yasan ya gama dacewa a duniya da lahira, macen da tun kan ya aureta komai ƙanƙantar kyauta ta dinga kwarara masa addu'a kenan, ina ga idan ya aureta, Hafsa bata taɓa roƙarsa komai ba, kai hasali ma ita kanta tana ƙoƙarin ganin ta bashi kyautuka, duk da arzikin da yake da shi, lokaci lokaci, sai ta saka masa katin ɗari biyar wai ga rabonsa nan, yau tayi ciniki sosai. Wani irin ƙaunarta ya ƙara dabaibaye zuciyarsa, a hankali ya ce "Tare da ke Babyna" "Ya naji muryarka kamar baka walwala, lafiya kuwa?" "Lafiya ƙalau, bacci kawai nake ji" "Ok, to bari in barka sai da safe, ka kwanta" Yayi saurin cewa'No, ki yi mini hira mana, raina ne babu daɗi" Cikin damuwa ta ce "Subhanallah, ko na ɓata maka rai ne kan ka tafi?" "Haba, ni da kika faranta mini mana, ba abin da kika yi mini" "To Alhamdilillah, Allah ya yaye maka damuwarka, ka san shi ɗan Adam dama ba a ƙyaleshi haka, sai dai ka kasance mai yawan godiya ga Allah, da kuma ambatonsa a halin daɗi ko akasin haka" Khalil ya lumshe idanunsa yana sauraron bayananta sannan ya furta "Ina sonki Hafsa, dan Allah duk ƙalubalen da zamu fuskanta kar ki rabu dani, na saba da jin daɗin kasancewata da ke, musamman yadda kike kwantar mini da hankali. Kina da haƙuri sosai da hankali, ni dai ina sonki" "Nima ina sonka, dan kama fini haƙuri, ka kwanta kayi bacci" "Allah ya tashemu lafiya" Ta amsa masa da Amin. Ya ajiye wayar, ya rintse idanunsa yana hango irin halin da zai shiga, idan aka raba shi da Hafsa, ita kanta yana tausaya mata, saboda tana matuƙar son sa, kuma ta saka ran samun afuwar rayuwa ita da mahaifiyarta saboda shigowar sa rayuwarsu. Hajiya Zainab kuwa har ta kwanata tana mita da banbami, a kan abin kunyar da a ganinta Khalil yake shirin janyo musu, musamman a cikin ƙawayenta, haka ta cigaba da communicating da su Hajiya Turai, suna cigaba da zigata, a kan duk yadda za tayi ta yi ta raba Khalil da yarinyar nan, dan kar ya ja nata abin kunya, kuma kar ayi masa asiri a mallake mata shi. Amina kuwa ta gama tsinkewa da lamarin Hajiya Zainab, dan bata taɓa zaton al'amarin zai yi zafi haka ba. Washegari  Amina tayi shirinta cikin doguwar rigar da Maman Azima ta bata, ta tafi makaranta, kasancewar lesson ne kawai ba da uniform suke zuwa ba, bada ban Alhaji Ahmad ya rarrasheta a kan ta yi haƙuri, ta cigaba da Zuwa lesson ba, da babu abin da zai sanya ta kuma zuwa, dan gaba ɗaya ta gaji da yawon lesson ɗin nan. Ta bayan layin gidan tabi, sai dai duk da kasancewar unguwar ta masu hannu da shuni ce, akwai wanda suke masu ƙaramin ƙarfi ne a unguwar, wasu tsirarin mutane ta gano a ƙofar wani gida, ana ta fito da kayan cikin gidan waje, wata mata da tsohon ciki da yara kusan biyar suna gefe sunata kuka, yayin da wani mutum da alama shine mijinta, yake ta rirriƙe wani mutum yana bashi haƙuri tamkar zaiwa mutumin sujjada. Amina sai ta tsaya tana kallon ikon Allah, wasu tsirarin mutane kasancewar safiya ce, suka tsaya suna taya mutumin bada haƙuri, shi kuma wanda ake bawa haƙurin sai kumfar baki yake yi "Wannan wane irin wulaƙanci ne? Tun yaushe kuɗin nasu ya ƙare, amma ƙaryar yau daban ta gobe daban yaƙi biya, gaskiya ba wani ɗaga ƙafa, akwai mutane a ƙasa suna neman gidan nan, kuma ma sayar da gidan zan yi" "Dan girman Allah ka taimaka mini, maiɗakina tana watanta na haihuwa, idan Allah ya sauketa lafiya, kan nan na samu kuɗin biyaka, ka san asara na tafka kwanan nan a kasuwa, na gobara da ta ƙona mini kaya" "Kaga ni fa sayar da gidana zan yi, idan ka samu kuɗinka kawai ka kama wani gidan" Kasa jurewa Amina tayi, kawai ta wuce su ta tafi makaranta, tana tafe tana kuka, tare da tausaya wa mutumin nan da iyalansa, tabbas talauci babu daɗi, da ana taimako yadda Yakamata, masu kuɗin dake unguwar nan zasu iya sai wa kowane talaka gida, saboda sun ninka talakawan dake unguwar yawa, amma kowa kansa ya sani, sai ranar juma'a zaka ga can gidan ana rabon gurasa can gidan ana rabon alala. Amina ta dinga jin inama ita wata ce, yadda ta san raɗaɗin talauci, idan Allah ya yi mata arziki ba zata taɓa barin na kusa da ita a wahala ba. A haka ta ƙarasa makarantar, da tunane tunane daban daban a zuciyarta, tare da fatan Allah ya bata nasara a rayuwa ta zama wata. Yazid ya nemi afuwar su Amra, na rashin samun damar tsayawa jiya ya koya musu assignment ɗin su, sai yau ya tsaya yana koya musu, Fadila na hango shi, amma ba ta nuna tama ganshi ba, balle ta kula shi, sai da ya gama da su sannan ya taho wurinta. "Dan Allah yau ɗaya ki gaishe ni mana, ke kullum sana gaishe ki?" Ta ce "Ni na saka ka gaishe ni?" "A'a ni naga yakamata in gaisheki, in ji ya lafiyarki" Maimakon ta bashi amsa ta ce "Yauwa nace ya ku kayi da Kankiya jiya?" Yazid ya ce "Jiya har ƙarfe biyar ina school ɗin nan, amma bai dawo ba, yanzu haka ma da wuri na shigo yau, na je ofishin sa, amma sakatarensa ya ce mini baya nan, na zauna na jira shi amma bai zo ba" "Kaga ka share shi kawai" "Meyasa zan share shi? Ko wani laifin nayi masa ne dan Allah ki gaya mini?" Fadila ta kalleshi ta ce "Ni ya za ayi in sani idan ma laifi kayi masa?" "Saurayinki ne fa, zai iya gaya miki" Haɗe rai tayi ta ce "Ni nayi maka kama da sa'arsa? Ai zaren ba kalar yadin ne, nafi ƙarfinsa dan haka kar ka sake haɗani da shi". Wani irin sanyi jikin Yazid yayi, lecturer ma fa kenan, ina ga shi karan kaɗa miya, bai ajiye ba, bai bawa wani ajiya ba. "Meye naga ka wani yi shiru?" "Bakomai, kawai ina tunanin dalilin da yasa yake kirana ne, ko dai zai ja mini kunne ne akan ki?" Da sauri ta kalleshi ta ce "Me kake nufi?" "Ina nufin ya ce kar ya ƙara ganin mu tare" A ranta ta ce 'kai wannan sai kace aljani, ya fiye saurin gane abubuwa' "Ya kika yi shiru?" "Ai ni da zai ya kiraka yayi maka warning ɗin, da ya taimaka mini, ka liƙe mini da yawa, na rasa irin wannan abun, kai gashi kome mutum zai maka ba fushi kake ba". Murmushi yayi, ya sake matsawa kusa da ita, wanda hakan ya fara haddasa mata mutuwar jiki. "Idan yayi mini haka bai mini adalci ba, kina daga cikin mutanen da zuciyata ta aminta da su shiga rayuwata, daga ranar da kika fara yiwa takalmin ƙafata dariya, zuwa rashin iya turanci na, ban ji ba daɗi a kan yadda kike mini dariya ba, sai wadda sauran 'yan aji suka yi mini, rayuwata da ke maybe temporary ne, da mun gama school shikenan, amma wataƙila in Allah ya ƙaddara ke matarsa ce tare zaku rayu har abada" Ya ɗan yi shiru sannan ya ce "Dan Allah Fadila, ki bashi haƙuri kar yayi Wani yunƙuri da zai raba abotarmu, let's be friends" Ta ce "Kai ka gaya masa mana, kuma ina ka taɓa ganin ana abota tsakanin namiji da mace?" "Ba ayi, amma ina son mu mu fara" yayi maganar muryarsa can ƙasa. Share shi tayi ta cigaba da danna wayarta. Gaba ɗaya ya tattara hankalinsa a kanta yana kallonta, ko ƙiftawa baya yi. "Dan Allah ka daina kallona haka, ni gaskiya ka takurawa rayuwata wallahi" ta faɗa a tsiwace tana jujjuya ido. Ya ce "Kamar bani da zuciya ko?" "Dama ina ka ganta" murmushi yayi bai ce komai ba, ya tashi tsaye ya bar mata seat ɗin. "In kana da zuciya kar ka sake zuwa wurin da nake, kuma kar ka sake kulani" bai waiwayo ba, yayi gaba yana murmushin da shikaɗai ya san ma'anarsa. Amina ta na aji ana lesson, ƙarfe sha ɗaya na safe, malaminsu ya shigo ajin, ya kalli Amina a ya ce "Amina ɗauko jakarki ki zo" cikin mamaki ta bi malamin da kallo, ta ga dai lokacin tashi bai yi ba, to ina zata? Haka ta ɗauko jakarta, ta biyo bayansa cikin mamaki. Ga mamakinta Daddy ta gani a tsaye a ƙarshen barandar ajinsu. Ƙarasawa ta yi  ce "Daddy lafiya kuwa?" Maimakon ya amsa sai ya ce mata "Ina kwana" Ɗan sosa kai tayi sannan ta ce "Yi haƙuri, ina kwana?" "Ai ni na fara gaishe ki, yau bamu haɗu ba sai yanzu, kuma na riga gaishe ki" Amina ta ce "Yi haƙuri" "Ai ba laifi ki ka yi mini ba, amsawa kawai zaki yi" "Ai kunya nake ji, ba zan iya amsawa ba" tayi maganar tana sunkuyar da kai. Dariya yayi ya ce "Zo mu tafi" Ba musu tabi bayansa, zuwa mota, ya buɗe ya ce ta shiga. Mamaki ya mamaye mata, tana son ta tambayeshi, amma tana tunanin kar tayi wani laifin. Sai dai kasa jurewa tayi ta ce "Daddy ina zamu je ne?" "Sayar da ke zan yi" ya bata amsa. "To ai idan ka sayar da ni ba zan yi tsada ba" Ya ɗan buɗe baki ya ce "Inji wa? Tsada za kiyi sosai, har an biyani kuɗin ma" dariya Amina tayi tana cigaba da kallon titi, sai dai ga mamakinta, sai taga ba hanyar gida suka nufa ba. Ta sake kallonsa ta ce "Amma Daddy.. "Shhh" ya katseta. Haka ta zubawa sarautar Allah ido, sun ɗan yi tafiya mai nisa, suka shiga wata unguwa, titunan unguwar kanta sai lokaci lokaci ababen hawa ke wucewa. Gaban wani ƙaton gate Yayi parking, wani ɗan sanda ya leƙo, sannan ya koma ya buɗe gate ɗin. 'yan sandan sun kai huɗu a cikin gidan, suka dinga ɗaga masa hannu suna gaishe shi, amma bai kula su ba. "Daddy suna gaisheka fa" Amina tayi maganar tana waiwayawa. "Eh na gani" "To ya baka amsa ba?" "Kai ke kam tambayoyinki sun yi yawa" bata kuma magana ba tayi shiru. Yayi parking a ƙatuwar harabar gidan, ya kashe motar ya fice. Amina zamanta tayi a cikin motar, tana waige waige. Ya buɗe motar ya kalleta ya ce "sauko mana" A ɗan tsorace ta ce "Daddy dan Allah ina ne nan?" "Wurin wanda ya saye ki na kawo ki" Gaba ɗaya jikinta yayi sanyi, ta bi idonsa da kallo. "Sauko mana" ya kuma maimaitawa. Jiki a sanyaye, ta sauko daga motar, tana bin gidan da kallo. Yayi gaba tabi bayansa, gidan yafi wanda suke ciki girma sosai da sosai, kuma ya tsaru, ya ciro mukulli ya buɗe ƙofar shiga cikin gidan. Wani irin ƙaton falo ne, da sai ka taka steps Sanan zaka isa ga kujerun. Fuskantar da Amina tayi babu mutane a gidan ne, ya sanya jikinta yayi sanyi, ta ɗan tsorata. "Shigo mana" yayi maganar yana kallonta. Ƙarara yaga tsoro kwance a fuskarta, hakan ba ƙaramin burge shi yayi ba. Babu tsammani taji ya riƙo hannunta cikin nasa, aikuwa ta tsorata, tamkar zata zura da gudu. Murmushi yayi ya ja hannunta, zuwa wani tangamemen kitchen, sannan ya saki hannunta ya kalleta ya ce "Amina, ke 'ya ta ce, kar ki saka a ranki zan wani abu da zan cutar da ke, amma duk da haka naji daɗin reaction ɗinki akan hakan, kiyi haƙuri na ɗauko ki ba tare da na gaya miki dalilin hakan ba, nan gidana ne galibi ina saukar baƙina a ciki, Abokaina zasu zo garin nan, shi yasa na ɗauko ki ki musu girki dan Allah, bana son yin order na restaurant saboda na yadda da girkin ki, amma idan kinga da takura bakomai, ki bar shi". Jiki a sanyaye ta ce "Zan yi" "In kin san na takura miki ki bar shi kawai" Ta girgiza kai ta ce "A'a, baka takura mini ba, amma me zan girka" tayi maganar tana jin yadda kaɗaicewarsu ta takurata. "Ko me kika girka yayi, zuwa azahar zasu zo insha Allah, na ajiye komai, idan kina buƙatar wani abu sai ki mini magana" ta jinjina masa kai alamar to. Ya juya ya bar kitchen ɗin, sai da Amina ta tsaya ta gama ƙarewa kitchen ɗin kallo, tana tunanin to ita Hajiya Zainab zaman me take, da mijinta zai yi baƙi amma ba zai kaisu gidanta ba ayi musu girkin a can, sai a nan ba? Ganin bata da amsa, ya sanya ta fara tunanin abin girkawa. Khalil kuwa jinsa yake tamkar mara lafiya, gaba ɗaya ya rasa abin da yake masa daɗi, sai da yunwa ta ishe shi, sannan ya shiga cikin gidan neman abin da zai ci, sai dai jin Abincin yayi tamkar magani, ya ajiye Abincin ya tashi, shi babbar damuwarsa, kar Mummy ta ce zata yiwa Hafsa wani abu, gashi har ɗakinta ya je ya sameta ya sake bata haƙuri, yayi mata bayani, amma taƙi saurararsa, ta ƙare masa zagi ta koreshi. Ba zato babu tsammani, Sir Kankiya ya shigo ajin su Fadila, yana muzurai ya fara yi musu bayanin cewa yayi musayan lokacin gabatar da darasi, da malamin da yakamata ya shigo ajin, ya wuce ya ajiye litattafan hannunsa ya fara ƙoƙarin ciro maker daga aljihunsa, yana ɗaga ido, suka yi ido huɗu da Yazid. "Kai jiya bance maka kaje office ɗina ina son ganinka ba?" Yayi Maganar yana tsare Yazid da ido. "Naje sir ban sameka a office ba, har kusan biyar ina jiranka" "You Are very stupid, ni zaka yiwa ƙarya?" "Ba ƙarya nake ba sir" "Shut up, tashi ka bar mini aji, kar ka sake attending lectures ɗina, mara ɗa'a kawai, and mark you no 75% attendance no exams" Gaba ɗaya Fadila sai ta rasa me ma zata yi ko tace, abubuwan na Kankiya sun wuce misali sun zama hauka. Ga mamakinta Yazid ko yunƙurin bawa Kankiya haƙuri baiyi ba, ya tashi ya bar ajin. Kan azahar tayi, Amina ta gama girkin da Daddy ya sakata, duk ta gaji, ta wanke dukkan abin da ta ɓata. Ta bi hanyar da suka shigo ita da Daddy, ta koma ƙaton falon nan, sai dai baya nan, kitchen ta koma tayi alwala ta dawo carfet ɗin falon tayi salla. Bayan ta idar Alhaji Ahmad ya shigo, ya kalleta ya ce "Sannu da aiki" "Yauwa, na gama, sai in tafi gida ko?" Tayi maganar a ƙagauce. Yayi murmushi ya ce "Zaki tafi gida, yanzu dai ga ɗakin da zaki kai abincin can, zaki jirani, idan sun kammala sun tafi, sai mu koma gida tare. Amina ji tayi kamar ta fasa ihu, ita gaba ɗaya bata son wannan ƙeɓewar ta su. Da kansa ya tayata suka shirya komai a ɗakin, ya bubbuɗe kulolin Abincin sai ƙamshi yake yi. Ya kai Amina wani ɗakin, bayan ya sa ta ɗebi Abincin, ya rufeta a ɗakin. Ya koma taro baƙinsa. Amina dai gaba ɗaya a tsorace take, wannan gidan sai ayi garkuwa da mutum ma ba wanda ya sani, Amina ta ci Abinci, ta gama amma zaman ya isheta, dan haka ta kwanta a nan ƙasan carfet, wani nannauyan bacci ya kwasheta. Ya ɗan jima a tsaye a kanta yana kallonta, sannan ya durƙusa daf da ita "Amina ki tashi kiyi sallar la'asar mu tafi" A hankali ta buɗe idonta, firgigit ta tashi zaune, saboda ganin Alhaji Ahmad a tsaye a kanta. Miƙewa tsaye tayi, tana murza idonta. "Ni mu tafi kawai" "Ba zaki sallar ba?" Ta ɗaga kai alamar eh. Ta durƙusa zata ɗau kwanon da taci Abinci ya kalleta ya ce "Bar shi a nan, za a gyara komai insha Allah, muje sai kin yi salla zamu tafi, biyar da rabi fa" Hankalinta bai kwanta ba sai bayan tayi sallar,  taga sun fita daga gidan sun hau titi sosai, sun fito daga gidan nan. Suna tafe a hanya Daddy ya ce "Naji daɗi sosai, kin fitar da ni kunya, suna ta godiya, Allah yayi miki albarka, Ahmad ya gode sosai" Ta ɗan kalle shi "Waye Ahmad?" Ta tambaya, dan ta manta sunansa ne. "Baban Fadila da Aminatu" murmushi tayi ta ce "Au na manta sunanka ne" Ta kashingiɗa a jikin seat, tana lumshe ido. "Kin gaji ko?" Ta ɗaga masa kai alamar eh. "Eyya, sannu to, and please wannan ma sirrinmu ne, kin taimakawa Daddynki, ya fita kunyar abokansa is our secret" "Tom, ba zan faɗawa kowa ba insha Allah" tayi maganar tana murmushi. Ya zura hannu a aljihunsa, ya zaro kuɗi a envelope ya miƙawa Amina. Ta kalleshi ta ce "Na menene wannan?" "Kuɗi ne na baki, tukuicin abin da kika mini ne, na katse miki karatun ki kin mini aiki" "Ai dama dai sai ka nuna banbanci duk da kace ni 'yar ka ce" tayi maganar tana tura baki. "Banbancin me fa?" "Idan kasa Fadila aiki biyanta kake?" Mamakin Amina yake, sam yanzu bata shakkarsa, ko shakkar faɗa masa magana. "Eh to, na kan mata tukuici da wani abu, dan na faranta mata rai" "Ai ni kayi mini abubuwa da dama, kana ciyar dani, ga wurin kwana, ga kuma karatuna, me zai sa sai ka kuma bani wani abu?" "Wannan ai duk daban" Ɗan shiru Amina tayi sai kuma ta ce "Daddy" "Na'am 'yar Daddy" "In roƙeka wani abu?" "Kan ki tsaye makuwa, me kike buƙata?" Nan ta labarta masa, gidan da ta wuce ɗazu da safe, ana fito musu da kaya. "Yanzu me kike so ayi?" "Dan Allah ka biya musu, tunda kana da kuɗi" "Waye ya ce miki ina da kuɗi?" "Kai ka gaya mini sayar da kuɗi kake, kuma kalli motarka da gidanka, ai dai kana da kuɗi sosai" Murmushi yayi, ya shafi dogon gemunsa, da yake baƙi da fari kaɗan kaɗan a cikinsa. "Daddy baka ce komai ba" "Sai na tambayi mata ta, idan ta amince sai a biya musu" Haɗe rai Amina tayi ta ce "Ashe ba za a biya musu ba kuwa" "Me kike nufi?" "Ai wannan matar 'yar hana ruwa gudu ce, ba zata taɓa barin ayi abin arziki ba" Daddy ya haɗe rai ya ce "Matar tawa ce 'yar hana ruwa gudu?" Amina shiru tayi tana ɗan kallon gefe dan da zata samu dama, sai ta ɗuɗɗurawa Hajiya Zainab Ashar dan ta huce. "Kayi haƙuri, amma wallahi bata da.... "Ke!" Ya daka mata tsawa da sai da ta razana ta kalleshi. "A gaban nawa zaki zagi uwar 'ya'yana" ji tayi kamar ta ce "Nima a gabana take zagin babana' amma ya koma mata Alhaji Ahmad ɗinsa, dole ta haɗiye maganarta. Parking ya yi ya kalleta ya ce "Fitar mini daga mota" "Gida da nisa fa daga nan" ta faɗa kamar tayi kuka. "I don't care, get out" ya faɗa in a serious tone. Buɗe motar tayi a fusace, ta fice ranta a ɓace. Ɗan guntun murmushi yayi, ya ja motarsa yayi gaba. Da ƙafa Amina ta nufi hanyar gida, tana tunanin yadda zata ƙarasa gida a ƙafa. Ran Amina ba ƙaramin ɓaci yayi da abin da Alhaji Ahmad ya mata ba, yana ta mata kirki, amma dan ta faɗi magana a kan waccan azababbiyar matar ya mata wulaƙanci, duk wahalar da tayi masa, amma bai gani ba, meye ya hana ita 'yar lelen matar tasa tayi masa?. Haka Amina tayi ta zancen zuci tana mita a ranta. Horn ɗin motar da ta ji yayi mata yawa a kunnuwanta ne, ya sanyata waiwaya. Murmushi me motar ya sakar mata, gani tayi kamar ta sanshi, ta hau tunanin a in da ta san shi. "Gida zaki ne?" "Eh" ta bashi amsa. "Kamar baki gane ni ba, Bilal ne na nan layinku, muna gaisawa fa idan zaki tafi makaranta" sai yanzu ta tuna shi, yana yawan yi mata adawo lafiya, idan zata tafi makaranta. "Sannunka ya kake?" "Lafiya ƙalau Alhamdilillah, taho mu ƙarasa". Ɗan shiru Amina tayi, yamma tayi liƙis, ta san yanzu haka Baba ya fara tunanin ina ta tsaya, kuma idan ta ce da ƙafa zata ƙarasa kuma, magariba zata rufa mata. Dan haka bata da zaɓi illa tabi Bilal. Suna tafe a hanya yana mata hira, ita gaba ɗaya hankalinta baya kansa, fatanta kawai su ƙarasa gida. Suna zuwa ƙofar gidan, Amina ta fara ƙoƙarin buɗe motar tana masa godiya. Bilal ya ce "Bakomai, muje nima in gaida Baban" Amina dai ba ta ce masa komai ba, baya son gwaleshi, bayan ya taimaketa. Tare suka shiga cikin gidan, sai dai Baba baya nan, Dan an fara kiraye kirayen sallar magariba. Amina ta kalleshi ta ce "Ina ga ya tafi masallaci, na gode sosai". Bilal ya ce "To ko zaki bani lambar wayarki?" "A'a ai bani da waya" suna cikin maganar, sai ga Alhaji Ahmad ya fito zai tafi masallaci, tun daga nesa ya fara yi musu wani irin kallo, musamman Amina, Amma Amina ta basar ta mayar da hankalinta kan Bilal. TOFA ME KUKE TUNANI. MASU SAN POSTING KULLUM, SU BIYANI IN BUƊE MUSU VIP, ZAN DINGA POSTING KULLUM INSHA ALLAH AYSHERCOOL 08081012143GABA DA GABANTA AISHA ADAM (AYSHERCOOL) PAGE 32-33 Duk da Amina ta sha jinin jikinta da irin kallon da Alhaji Ahmad ya yi musu, amma ta maze ta ƙi ko ɗaga kanta, balle ta nuna ta san ita yake yiwa wannan kallon. Bilal ya gaida Alhaji Ahmad, amma ya amsa masa sama-sama ya fice, Amina na ganin fitar Alhaji Ahmad, ta yiwa Bilal sallama ta shige cikin gida. Fadila kuwa tun da Kankiya ya Kori Yazid daga ajin, hankalinta yake a tashe, ta rasa meya kamata ta yi, tamkar a kan ƙaya take haka ta dinga jiran Kankiya ya fita ita ma ta fita, ganin ba shi da niyyar fita ne, ya sanya ta tashi ta nemi excuse zata fita, amma Fafur Kankiya ya hanata, ji tayi tamkar ta je ta shaƙe shi ta gwara kansa, wata irin tsanarsa ta ninku zuciyarta. Sai da yayi kusan awa biyu da wani abu sannan ya bar ajin, yana fita Fadila ta fita, ta dinga duddubawa ko zata ga Yazid, amma babu Yazid babu dalilinsa, duk in da ta san zata ganshi ta duba amma bata ganshi ba, hakan ya sa tayi tunanin gida yayi tafiyarsa, alamar yayi zuciya. Tunani ta dinga yi, wani irin hukunci yakamata ta yiwa Kankiya, wani mataki yakamata ta ɗauka a kansa, amma sai ta yi tunanin kar tayi wani abu a kai, ya kuma cutar da Yazid, haka nan ba tare da ta yanke shawarar komai ba, ta shiga motarta ta tafi gida cike da damuwa.   A gidanma kasa sukuni tayi, gashi ita ba lambar Yazid ba, balle ta kira shi a waya taji meyafaru bayan fitarsa daga aji ba. Tana tsaka da wannan tunanin, sai ga kiran Kankiya, ji tayi kamar tayi jifa da wayar, amma tayi yaƙi da zuciyarta ta ɗaga. "Amincin Allah ya tabatta a gareki amaryata" ji tayi kamar ya watsa mata wuta a zuciyarta, ko muryarsa ba ta ƙaunar ji sam. "Me ka kirani kayi mini, wai ban maka kashedi a kan kirana ba?" "Kina fushi da ni dan na kori saurayinki daga aji ko? Ai abinda na gaya miki ne Fadila, muddin ba zai rabu da ke ba, zan ta wahalae da shi ne" "Wai kai waye ya gaya maka Yazid saurayina ne? Babu wani abu mai Kama da soyayya tsakani na sa Yazid, kuma bari in gaya maka wani abu, wallahi muddin baka kiyaye ni a kan batun soyayyar nan ba, sai na maka abin da har ka mutu ba zaka manta ba* Yayi dariya ya ce "Ni ma kuma zan yiwa Yazid ba, dan naga a duniya idan ana son ɓacin ranki, to a taɓa Yazid" Sai kuma yayi ƙasa da murya ya ce "Haba Fadila, duk ke kika saka al'amura suka zama so complicated like this, ni ina da kishi sosai da sosai, shiya sa ba zan iya jure ganinki da wani ba, wallahi idan Yazid ya fita daga harkarki babu ruwana da shi. Yanzu gaya mini yaushe zan zo gidanku?" "Abudrrasheed Kankiya, banda ina ganin darajar alli da duster, da sai na nuna maka wacece Fadila, na lura rashin sanin wacece ni ya sanya kake mini karan tsaye yadda ka ga dama" "Hmmm, koma dai menen ai nasan ke mutum ce, kuma duk matsayinki dole zaki aure wataran ƙarƙashin inuwar wani, Fadila mu daina samun wannan saɓanin, in daina wahalar da ɗan mutane, ki fita harkarsa ki bani dama in gwada miki soyayya" "Shikenan, ni da kai mu zuba mu gani,ka koma ka ƙarewa kanka kallo, sannan ka ƙare mini kallo kasan wacece ni, kan kace kana sona ka san matsayina tukuna, wallahi ka cigaba da takura masa zan nuna maka abin da zan iya yi a kai" Kankiya ya yi ajiyar zuciya ya ce "Saboda shi Yazid ɗin duk kike gaya mini wannan maganganun?" "An gaya maka ɗin, kayi abin da zaka iya" daha haka ta kashe wayar , tana jin tamkar ta sa a ɗaure Kankiya, ita tausayin Yazid take ji, idan aka ɓata masa career an cuce shi, amma Kankiya na son amfani da wannan damar ya tilasta mata ta so shi, bata taɓa tausayin wani ɗan Adam a rayuwarta ba, kamar yadda take tausayin Yazid. Ita kawai kyawawan halayensa take kallo, sai taga kamar idan aka cutar da shi ba a yi masa adalci ba, yana da halaye masu kyau, ba ya cutar da kowa to shi mai zai saka a dinga cutar da shi. Ta tuna irin kasadarsa mussaman a ɗakin jarrabawa, dan kar wani ya faɗi, da tsananin biyyarsa ga malamai, amma hakan bai hana a dinga dizga shi a gaban aji, ba tare da duba halayensa masu kyau ba. Dafe goshinta tayi, ji tayi kamar kanta ya fashe Saboda rasa mafita. Ɓangaren Khalil ma yana cikin ɗumbin damuwa, Hafsa ta buɗe what's app a wayar da ya bata, har tayi masa magana ta what's ɗin, sai wani ƙara lallaɓa shi take, tana bashi kulawa ta mussaman, da Adduoi, nasiha gami da kalaman soyayya, wanda hakan ke ƙara masa sonta a ransa. Gaba ɗaya Mummy ta ɗauke masa wuta, ta daina shiga harkarsa, duk dan saboda yana son Hafsa. Gaba ɗaya fushin da Mummy take yi da shi, bai yi masa daɗi ba, hakan ya sanya, ya kuma ƙoƙarin zuwa ya rarrasheta, sannan yayi mata bayanin halin da su Hafsa ke ciki, ko Allah ya sa ta fahimce shi. Da sallama ya shiga bedroom ɗin Mummyn, ya tarar da ita a kan gadonta, tana danna Computer, gefenta kuma ga calculator, da alama kuɗi take ƙirgawa. Tun da ta ɗaga kai ta kalleshi sau ɗaya, ta mayar da kai ta cigaba da abin da take yi. "Mummy sannu da aiki" "Yauwa" ta amsa a daƙile ba tare da ta kalleshi ba. "Mummy wurinki na zo" "Ai na ganka, ina kuma jinka" Khalil ya ɗan gyara zama tare da sosa kai ya ce "Mummy, dama game da Hafsa ne, yarinyar nan da aka ce miki an ganni a wurinta, Mummy yarinyar marainiya ce ne, Da mahaifinta mai abin hannunsa ne, kan ya rasu ya saya mata kadarori, sai dai bayan rasuwarsa dangin mahaifin suka ƙwace komai, shiyasa kika gansu a haka, amma tana da kirki da kuma hali mai kyau, ba ta da wata matsala yarinyar" Ai tamkar dutse yayi wa wannan dogon jawabin, dan danna calculator kawai take tana shigarwa cikin Computer. "Mummy ba ki ce komai ba" "Me kake so in ce maka, ai kai an shanyeka, ni kuwa ba a shanye ni ba a hayyacina nake, nayi mamakin wurin wani malami suka je haka, da har ka iya zuwa ka tunkare ni ni Hajiya Zainab, kake mini wannan maganar banzan, ban sani ba ko orphanage Home ka buɗe, zaka fara rainon marayu da marasa galihu, da har zaka yayi mo min wannan shirgin tsiyar, Khalil banda rashin hankali irin naka, ina kai ina mai suyar Awara a titi, ba bu ilimi mai zurfi, ta gama zaman titi maza sun gama kalleta, in anjima ta ci kwalar namiji, kuma ka ce mini ita ce sirikata,ai kai ma ka san kayi ƙarya" "Mummy wallahi ba haka Hafsa take ba, tana.... "Dalla rufe mini baki, ina magana kana wani kwantar da murya ce, cece, ni zaka lallaɓa in anince da auren 'yar matsiyata, ka buɗe kunnenka da kyau ka saurare ni, daga yau babu kai babu yarinyar nan, na yanke duk wata alaƙa da take tsakaninka da ita, wallahi na bibiya na tarar ba ka rabu da ita ba, hukuncin da zan yanke maka ba zai maka daɗi ba" "Mummy dan Allah, ki duba lamarin nan" "Ni kake cewa in duba lamarin nan, wato sihirin har ya kai ka fifita ta a kaina" Cikin rauni ya ce "Ba haka bane Mummy, wallahi ba suyi mini asiri ba, suna buƙatar tainako ne Mummy, kuma muna son juna sosai" Mummy ta jinjina kai ta ce "Da kyau Khalil, suna buƙatar taimako ko, sannu gwamnati kowa naka, tashi ka fita ka bar mini ɗaki" ta nuna masa hanyar fita. Zai kuma magana, ta sake haɗe rai ta nuna masa hanyar ficewa, haka ya haƙura ya bar mata ɗakin zuciyarsa babu daɗi. Amina kuwa ba ƙaramin haushin abinda Daddy yayi mata taji ba, haka ta shiga ɗakinta, tayi alwala tayi sallar magariba, ta shiga kitchen ta hau aikin Abincin dare, kasancewar Hajara ce tayi na rana tunda ita tana makaranta. Gaba ɗaya Amina a gajiye take, tunda kusan wuni tayi aikin da Daddy ya sakata, aikin da a ƙarshe ya sakamata da direta a titi yayi tafiyarsa saboda tayi maganar matarsa. Ta gama girkin, ta kai dining, ta ɗau na Baba ta tafi ta kai masa, ta tarar da Baban a cikin ɗakinsa na gadi, yana jin radiyo. Har zata fita, Baba ya kirawota, ta dawo ta zauna tana kallonsa. Ya ɗauko wata 'yar jaka ya miƙa mata, ta sa hannu ta karɓa, ta buɗe jakar wani babban kwalin waya ta gani a ciki, ta saka hannu ta ciro wayar tana kallon Baba. "Baba wannan wayar fa?" Baba ya ɗan yi shiru sannan ya ce "Alhaji Ahmad ne ya bani, ya ce in baki, wai saboda ki samu sauƙin karatu, sai dai har ga Allah ni bana son ki mallaki wayar hannu yanzu, amma bana son yi masa jayayya kuma naji ya ce saboda karatunki, ina fatan dai ba roƙonsa ki ka yi ba?" "Haba Baba, ka san bana roƙo, wallahi ni ban roƙe shi ba" "To sai kiyi masa godiya, duk da nima nayi masa" "To, insha Allah zan masa" Ta tashi tana jujjuya wayar ta bar ɗakin Baba. Har ga Allah tana matuƙar son waya, mussaman duba da yadda ƙawayenta ke da wayar, amma ita ba ta da ita, sai dai da ta tuna da abin da Daddyn ya yi mata, sai haushi ya kamata har ta ce "Mayar masa zan yi, ban so" ta jiye wayar a gefen katifarta tana harar wayar tamkar Alhaji Ahmad ɗin ne a gabanta. Washegari da Safe Amina bata da niyyar zuwa lesson, ta tashi ta hau aikace-aikacenta, ta shiga kitchen ta ɗora sanwa, ta yi girkin safe ta kammala, ta zo ta shiryawa masu gidan nasu Abincin, sannan ta kaiwa Baba nasa ta dawo, ta fara mopping ɗin falo. Hajiya Zainab ce ta fara fitowa, Amina ta gaisheta ta amsa mata da ƙyar kamar an yi mata dole, sai kuma Fadila ta fito, Alhaji Ahmad ne ƙarshen fitowa, ba tare da Amina ta kalli in da yake ba, ta gaishe shi, yana jinta ya shareta, kamar ba da shi take ba. "Good morning Daddy" Fadila ta faɗa tana ƙoƙarin haɗa tea. "Morning sweetheart, how are you" "Am fine Daddy" Ya ɗan ƙara kallon Fadila ya ce "Meke damunki ne, you look dull today" Fadila ta ɗan yatsuna fuska ta ce "Nothing much, stress ne na school kawai" "To Allah ya bada sa'a, yau weekends ki samu ki huta sosai" "Ok Dad" Ya mayar da hankalina kan Mummy ya ce "My Z ina Khalil ne?" Mummy da ta kai loma bakinta, ta ƙarasa taunawa sannan ta ce "ƙyale shi kawai" 'in ƙyaleshi kamar yaya, ban gan shi a wurin cin Abinci ba" "Ka san halinsa wasu lokutan, maybe bacci yake yi" "Is ok" Daddy ya faɗa yana cigaba da cin Abincinsa. Yana yi yana satar kallon in da Amina ke mopping, tayi kicin kicin da rai, ko kallon in da suke bata yi, aikinta kawai take. Ɗan guntun murmushi yayi, ya cigaba da cin Abincinsa. Bayan sun kammala ci, Mummy ta miƙe tsaye, ta kalli Fadila ta ce "Fadila je ki shirya muje ki rakani gidan Hajiya Turai" Fadila ta ɗan tsuke fuska ta ce "Mummy ki je ki kaɗai, ni bana son fita" "Aikuwa sai kin je, tashi maza muje" Fadila tana tura baki, haka ta tashi, ya wuce ɗaki, dan ta fara shirin yiwa Mummy rakiya, idan ba haka ba ta san halin Mummy, idan ta dinga mata mita sai taji babu daɗi. Suka wate suka bar Daddy a falo, Amina kuma na zaune na goge TV. "Ke da waye jiya na gani a tsaye a gidan nan?" Amina ta ɗaga kai ta duba falon, amma bata ga kowa ba, dan haka ta san da ita yake, maida kai tayi ta cigaba da aikinta. "Ko in zo in maimaita miki ne?" Ta ce "Ba kowa" "Kina nufin ƙarya nake kenan?" Ta girgiza kai alamar a'a. "Ke da waye?" "Bilal ne, a nan layin yake, bayan ka ajiye ni a hanya, ya ɗauko ni" Alhaji Ahmad ya ce "Ban tambayeki wannan ba, abu ɗaya nake son gaya miki, kar ki sake kawo mini wani gida, kin zo gidan nan ne dan kin yi aiki da karatu, idan saɓanin haka ne a ranki, to zan sanar da Malam Hassan tun wuri ya san matakin da zai ɗauka,  karki ƙara kawo mini wani gida kinji na gaya miki, idan kuma aure kike so sai kiyi bayani, amma gidana ba wurin tara maza bane" kamar kibbau haka ta dinga jin maganganun Alhaji Ahmad, ba ƙaramin ƙona mata rai suka yi ba, ba tace masa uffan ba, sai wasu hawayen ɓacin rai da suka cika mata ido, bata son ya ga lagonta, dan haka ta tashi ta kwashe kayan aikin nata, ta bar masa falon. Alhaji Ahmad ya shirya ya fita, sai dai ya ci karo da Wayar da ya sayawa Amina a cikin motarsa, ya ɗau wayar ya jujjuyata, ya ɗan yi shiru sannan ya jinjina kai tare da faɗin lallai ma yarinyar nan. Ya ajiye wayar ya cigaba da tuƙinsa. Hajiya Zainab ce tare da Hajiya Turai a falonta suna hira, yayin da Fadila ke gefe a zaune tana latsa wayarta. Hajiya Turai ta ce "Wallahi kar ki saurarawa yaron nan, kiyi dagaske ki miƙe a kan abinki, idan ba haka ba wallahi kina kallo za a shanye miki shi, sai yadda aka yi da shi" Mummy ta ce "Wallahi Turai Khalil ya bani mamaki, ban taɓa zaton yaron nan zai kai kansa wurin maƙasƙanciya kamar mak awara ba, me aka yi a kai mai awara? Banda kalen tsiya da rashin sanin darajar kai, ya janyo mini abin faɗa a cikin ƙawaye" "Bari Hajiya Zainab, yaran yanzu ka haifesu baka haifi halinsu ba, banda abin Kalil waye yake janyo talaka jikinsa, ai kowa arziƙi yake nemawa kansa, ai baki ga abin haushi ba yadda yarinyar ke washe baki, kamar gonar gyaɗa, Allah ya kashe ya bata" Mummy ta ce "To wallahi yayi kaɗan, muddin bai rabu da yarinyar ba, zaiga abin da zan masa daga shi har ita" Turai ta ce "Ai zuwa zaki har gida, mu kasawa yarinya warning ita da uwarta" Fadila dai ba ta tofa ba, dan a ganinta Khalil shi ne ya janyowa kansa, ga Yusra nan, ba abin da Allah ya rageta da shi, amma ya watsar da ita ya ce baya so. Turai ta kalli Fadila ta ce "Daughter, ke kuma wa zaki kawo mana, ina fatan dai ba wahalalle kema zaki kwaso mana ba" Fadila ta ɗan kwaɓe fuska da murmushin gefen baki. Turai ta ce "Ai ba murmushin ba, ni dai ɗana ya gani ya ce yana so, insha Allah da ya dawo zan haɗaku, dan har Babanaa ya zan zancen" Mummy ta ce "Ai na fara mata zancen kwanaki, kin san yaran naki ne, miskilaine kamar ubansu, na fara mata maganar ba ta ce mini komai ba dai tukuna, amma dai na san zasu daidaita" Fadila ta sake gyara kwanciyarta a kan kujera, dan wannan hirarrakin nasu ya isheta, so take su tafi gida kawai. Sai da Khalil ya tabattar da Mummy ta fita, sannan ya shiga falon, ya saka Hajara ta kawo masa kayan breakfast ya karya, ya ci ne dan kawai yana jin yunwa, ba dan yana son cin Abincin ba. Bayan ya gama ya fito daga ɗakin, ya haɗu da Amina a kan baranda, ya kalleta fuskarsa ba walwala ya ce "Daga yanzu idan kun gama girki a dinga zuba nawa ana kai mini ɗakina" Amina ta ce "To insha Allah" Fadila har suka taho gida, Mummy tana yi mata bayanin yadda ɗan Hajiya Turai yake, ita dai Fadila lissafin, yadda zata yi da Kankiya da kuma batun Yazid ne ya dame ta. Khalil kuwa gidansu Abdul ya wuce, dan ba shi da aminin da yake gayawa damuwarsa wanda ya wuce Abdul ɗin. Tun a kallon fako, da Abdul ɗin ya yiwa Abokin nasa, ya san tabbas akwai damuwa, dan a yadda Khalil ya saba, da yazo yake fara zolayarsa, amma yau yana shigowa, ya wuce kan gadon Abdul ya kwanta, yayi shiru ba tare da ya ce musu komai ba. Abdul bai kula shi ba, sai da ya kammala abin da yake yi, sannan ya dawo ya zauna a kusa da Khalil, ya kalli Khalil ya ce "Kalil, meke faruwa ne, tashi kayi mini bayani" Kamar Khalil na jiran ƙiris, ya tashi zaune, yana share gumin da ya tsatsafo masa, ya kalli Abdul ya ce "Abdul, na ga samu, ina shirin ganin rashi" "Kamar yaya kenan?" "Abdul, Mummy, Mummy" Abdul ya sake gyara zamansa ya ce "Me ya faru? Me Mummyn tayi" Kamar Khalil zai yi kuka ya ce "Bayan wahalar da na sha wurin farautar soyayyar Hafsa, na yi nasara na samu, tana sona mun shaƙu, sai dai ina shirin zuwar wa da Mummy maganar Hafsa, ƙawaywen Mummy sun gano ni a wurin Hafsat, sun sanarwa da Mummy, baka ga cin mutuncin da ta mini ba, yanzu haka ma ta ce lallai in rabu da Hafsa, dan Allah Abdul yanzu ta yaya zan koma in janye maganata da Hafsa, bayan ta gama bank dukkanin yarda, da saka ran samun salama a wurina tayaya Abdul" Abdul ya jinjina kai ya ce "Akwai damuwa, ka san iyaye gaba suke da dukkanin wani abu na san rai da son zuciyarmu, amma kuma yakamata ita ma Hafsa a duba a yi mata adalci, kaima kana da ƙanwa mace, alhakin Hafsa zai iya kama Fadila da bata ji ba bata gani ba" "Kai Abdul, ba zan iya haƙura da Hafsa ba, duk da ban san wane irin mataki Mummy zata iya ɗauka a kaina ba, bana jun zan iya rayuwa babu ita!!! DOMIN SHIGA VIP GROUP, POSTING KULLUM KU TUNTUƁENI TA WANNAN LAMBAR 08081012143GABA DA GABANTA BY AISHA ADAM (AYSHERCOOL/JAKADIYAR AREWA) P34 Abdul ya gyara zamansa ya sake fuskantar Khalil ya ce "Ibrahim, kai ka wuce aboki a wurina yanzu, kai ɗan uwana ne, ba zan so ka aikata abin da zaka zo kana dana sani ba, kar ka biyewa soyayya ka zo ka rasa yarda da soyayyar mahaifiyarka, Ka bi komai a hankali, har Allah yasa Mummy ta fahimta, shawara ta farko mai zai hana kaje ka samu Daddy, shi ka yi masa bayanin, na san zai fuskance ka kuma zai yiwa Mummyn bayani" Khalil yayi wani guntun murmushi sannan ya ce "Abdul ya kake abu kamar ba ka san wacece Mummy ba ne? Kai ka san babu yadda za a yi na samu goyon bayan Daddy, muddin Mummy ba ta son abu, ba zata taɓa yarda ba, kuma wallahi ina matuƙar jin tausayin Hafsa, idan na rabu da ita ban san wane hali zata shiga ba, bari ayi sallar magariba, muje tare ka shaida yadda yarinyar nan ta shaƙu da ni, ta yarda dani ta saki jiki zan Aureta, amma Mummy tana barazanar rabani da ita, dan Allah Abdul ko Hafsa na da wani aibu da so ya rufe mini ido ban gani bane?" Abdul a ransa ya ce 'Talauci, shine aibun da mahaifiyarka bata so' amma a fili ya ce "Ai Hafsa yarinyar kirki ce, ba ta da wani aibu, ba wanda ba zai so haɗa zuriya da ita ba, kuma tana cikin yanayin da take buƙatar taimako, zaman soya awarar nan bai dace da ita ba sam" "Yauwa Abdul, ashe ka gane, wallahi yana daga cikin dalilan da ya sanya nake son taimakonta, Hafsa da gidan Aure ko makaranta ta dace, ba da zaman titi ba, Abdul na tsara irin rayuwar da zan yi da ita, yadda ta sha wahala a baya duk da farkon rayuwarta 'yar gata ce, amma ina son in ɗauke mata komai, yadda ba zata taɓa kukan wani abu ta rasa ba, sai abin da bani da damar sama mata, Abdul ba zaka gane ba, that girl deserve a shoulder to rest, akwai matsala idan Hafsa ta auri mutumin da bai San mecece ƙaddara ba, kuma bai san kimar mace ba, ya zan yi Mummy ta gane ne?" Abdul ya jinjina kai, So kenan, mai sa mutum ya duƙa, ya susuce duk izzarsa da kuma taƙamarsa' A yadda Khalil yake ɗan gayu matashi mai ji da kuɗi, idan aka ce maka zai ɗauko mace kamar Hafsa ya ce yana so zaka ƙaryata, amma ya zauna sai sambatu yake yi. Abdul ya ce "Khalil, naji duk bayananka, kuma na fuskance ka, zan tayaka da Addua, sannan zan cigaba da tunanin menene mafita ga al'amarin nan" da ƙyar Abdul ya ɗan rarrashi Khalil, ya rage damuwar da yake ciki. Amina bayan barinta falo, da ta koma kitchen kuwa saida tayi kuka sosai, ita gaba ɗaya gorin nan da ake yi mata da kuma takura ya isheta, shikenan dan  tana karatu wani ba zai kulata ba, kuma ita Bilal ba cewa yayi yana sonta ba, 'yan ajinsu suyi ta bada labarin samarinsu, amma ita sai samarinta na ƙauye, gashi Alhaji Ahmad yayi mata gori kuma ya hanata tsayawa da saurayi, ta zauna a kitchen tana ta kukanta. Hajara ta shiga kitchen ɗin ta tarar da ita, a zaune tana share hawaye. "Amina kukan me kike kuma?" "Ba komai" Amina ta faɗa a daƙile. "Kawai jin daɗi ne ya sanya kika zauna kina kuka?" "Nace miki bakomai, ki ƙyaleni" Amina ta faɗa a ƙufule, dan sa idon Hajara yayi yawa, komai ta gani so take sai taji ƙwaƙwaf, yadda aka fara da yadda za a ƙare. Ta miƙe ta cigaba da aikin tana yi tana kuka, kamar ƙaramar yarinya. Tun daga wannan ranar, Amina ba ta yadda ko hanya ta haɗata da Alhaji Ahmad, ganin idan ta gaishe shi ya daina amsawa, sai dai ya tsaya ta ƙureta da ido, dan haka gaisuwarma ta daina gaisheshi. Idan suka haɗu sai ta basar ta wuce abinta. Da magariba Khalil ya takurawa Abdul, ya shirya suka tafi gidansu Hafsa, kasancewar ta san da zuwansu, ya kirata ya sanar mata, ya sanya ta shirya har da yi musu girki, ta saka ɗaya daga cikin kayan da ya kawo mata, a ɗinke, wani less mai matuƙar kyau da ya kawo mata shi a ɗinke. Tun da ta fito hannunta riƙe da babbar darduma, Khalil yake kallonta,  tayi masa kyau fiye da kullum, ga wani irin tausayinta da ya ƙara mamaye masa zuciya. Tana Zuwa tayi murmushi ta ce "Yaya Abdul, kwana biyu ka ɓuya da yawa" Abdul yayi murmushi ya ce "Ai tunda Allah yasa ku ka daidaita, bai kuma nemana in masa rakiya ba, shiyasa ba kya gani na" "Yaushe zan nemeka, ka zo ka samana ido" Khalil ya faɗa yana sake mayar da hankalinsa a kan Hafsa. Ta shimfiɗa musu sallaya, suka zauna ita kuma ta zauna daga gefe. "Babyna kina lafiya, ya kasuwa?" "Alhamdilillah, ya gida ya su Mummy?" "Suna lafiya ƙalau, kin yi mini kyau fiye da kullum, kamar in sace ki in gudu, Abdul ko zagawa zamuyi mu tataro mutane a ɗaura mana auren nan ne kawai mu huta?" Abdul a ransa ya ce "Da ka ci ubanka la'ada waje a wurin babarku' Amma a zahiri ya ce "Eh to idan ƙanwar tawa ta yadda, sai muje neman mutane a haɗu a ɗaura ai" Hafsa sai sunkuyar da kai take tana jin kunya, Khalil ya leƙa fuskarta ya ce "Babyna, ki gaya masa kin amince, mun Matsu mu mallaki junanmu, ko yanzu a shirye muke a ɗaura" Ƙunshe fuska Hafsa tayi, tana jin wata irin kunya tana ratsata, gaba ɗaya shi Khalil baya jin kunya. "Ya kika yi shiru, in dai Abdul ne ki daina jin kunyarsa, a ɗaura mana aure next year by now insha Allah idan baki haihu ba to muna nan muna rainon Babynmu a cikinki" Miƙewa Abdul yayi ya ce "Khalil wannan fitsarar ta ka, ba ita ba ni kaina kunyar kake bani, bari in koma mota In jiraka" Dariya Khalil yayi, Abdul ya nufi ƙarshen layi in da suka bar motarsu. Khalil ya matsa ya sake mayar da hankalinsa kan Hafsa ya ce "Amaryata, ɗago mana in ƙare miki kallo, baki ga yadda kika mini kyau ba" A ɗan shagwaɓe ta ce "Wai sai ka ta bani kunya a gaban mutane" "Suwaye mutanen, Abdul ɗin? Ni banga wani abin Kunya ba" "Ni na gani ai, amma kayi mini kyau sosai" "Da gaske?" Ta jinjina masa kai, yayi murmushi ya ce "Kyau sai ma ranar bikinmu yarinya" Tayi shiru ba tace komai ba. "Babyna" ya faɗa murya ƙasa-ƙasa. Ta ɗan ɗago ta kalleshi. "Kiyi magana mana" "Yau ba 'yan maganar, na rasa me zance" "You must say something, bari muyi Auren zobe, wata azurfa na saya mana tun last month, sai wannan watan Allah ya sa suka iso" Ya ciro wata 'yar ƙaramar box blue black, ya buɗe sai ga wasu zobuna masu matuƙar kyau a ciki. Ya ɗauko na matan, ya kamo hannun Hafsa, ya kama yatsanta ya saka mata zoben. Da ɗan sauri ta janye hannun nata, tana jujjuya zoben tana murmushi. Ya miƙa mata masa hannun, ya ce "Nima sa mini" Ya miƙo mata yatsansa, cikin rashin sabo, ta zira masa zoben. Hannunta ya kamo cikin nasa, ya ciro wayarsa, ya ɗauki hoton hannunsa da nata sanye da zobunan. Daga nan ya zarce yana ɗaukarta hoto, hannunta da ke cikin nasa ba ƙaramin takurata, yayi ba amma ta kasa cire hannunta daga nasa, yayi ta musu hoto. Ba tare da ya cire hannunsa a nata ba ya ce "Hafsa zaki aureni?" "Meyasa kake yawan maimaita tambayar nan? I will marry you in sha Allah My" tayi maganar tana masa murmushi. "Murmushin nan naki yana killing ɗina, ki ce kina sona?" "Ina sonka sosai, duk ka koya mini rashin kunya" "Kina da kunya sosai, amma naji daɗi da kika rageta sosai a kaina, ina son matata ta zama mai kula dani sosai, ina sonki Babyna, ki cigaba da yi mana addua, Allah ya tabattar da Aurenmu, ya bamu ikon cin duk wata jarrabwa da ka iya taso mana" "Ina yi mana" "Yauwa Habibty, zuba mini Abincin in ci, kuma a bakina zaki bani" Ta noƙe kafaɗarta ta ce "A'a zan dai zuba maka, sai bayan nikah zan dinga baka a baki" Haka ta zuba masa Abincin nan, yana ci yana zuba santi yana koɗata. Ya kammala ci, ya ce "dama wancan ba ci zai yi ba, ya ce lemo kawai zai sha, na gode sosai matata in sha Allah, bari in tafi" Hafsa ta marairaice ta ce. "Ni kar ka tafi yanzu, ban gaji da ganinka ba" "Allah sarki sweetheart, ni kai na bana son tafiya, ban gaji da ganinki ba" "Shikenan ma yi video call, kar kayi dare muje in raka ka mota" Khalil ya ce "A'a, bana son ki wahala, ki ce ina gaida Mamana" "Ni baka taɓa haɗani da Mummy na gaisheta ba" Ɗan dam yayi, sai kuma ya ce "Karki damu zan haɗaku" Yana nan tsaye, sai da ta shiga gida, sannan ya nufi in da motarsu take. Jiki a sanyaye ya shiga motar ya zauna. Abdul ya kalleshi ya ce "Baban soyayya, ka shanyani kana can kana soyewa, Allah yasa baka ƙone ba" Khalil ya Shafi gemunsa ya ce "Kamar kar in taho, ina son yarinyar nan" "Nima na ga alama, zan taya ku da Addua in sha Allah". Da haka Khalil ya ja motar, ya tafi kai Abdul gida. Washegari Monday, su Amina zasu koma makaranta, ta yi gugar uniform ɗinta, ta wanke jaka da takalminta, ta shirya litattafanta, tana ta kallon jakarta tana jin shauƙi da farincikin komawa makaranta, ta dinga tuna rayuwar da tayi a ƙauye, yadda ta dinga makaranta a wahale, wataran sai dai ta saci hanya ta je makaranta, idan ta dawo ta ci duka, amma nan duk da tarin ƙalubalen da take fuskanta, akwai Abinci, akwai wurin kwana mai kyau, gashi duk wani aiki da ake sakata, ba a sakata lokacin makarantarta. "Kai Allah ya saka maka da alkhairi" ta faɗa a fili, sai kuma ta tuna da abin da Alhaji Ahmad yayi mata, sai ta tura baki tana ƙunƙuni kamar tana gabansa, ta tashi ta tafi wurin Baba. Ganin fara'a a fuskar Amina ya sanya Baba yin murmushi ya ce "Uwata, murmushin me kike haka ne?" "Baba ka san gobe in Allah ya kaimu zamu koma makaranta, shine nake ta jin daɗi, na wanke uniform ɗina na goge, shi ne nake jin daɗi" Baba ya ɗan yi ajiyar zuciya, ya ce ina zuwa. Ya tashi ya shiga ɗakinsa ya fito da ƙatuwar leda, ya miƙawa Amina ya ce "Gashi in ji Alhaji Ahmad, jaka ce da takalmi ya ce a baki, kuma wai idan kinje makaranta ki je ki karɓa sabon kayan makaranta, Uwata ban taɓa zaton Alhaji Ahmad zai kyautata miki haka ba, bani da bakin yi masa godiya, sai fatan ya gama da duniya lafiya, Uwata ki same shi ki durƙusa har ƙasa ki yi masa godiya Amina" Maimakon Amina tayi murna, sai ta ɗan tura baki, dan ji tayi ma kamar ta ce bata so. "Uwata ya naga kin haɗe rai" "Ba komai Baba murna nake yi, Allah ya saka masa da alkhairi, na gode sosai, amma ai ni takalmi na da jakata da Uniform ɗina suna da kyau" "Ba sai ki adana abinki ba, kuma ya mini ƙorafin idan ya baki abu ba kya karɓa, wannan kuma kin yi daidai, ki cigaba da kula da mutuncinki" "To, In sha Allah Baba Na gode sosai" Ta miƙe da ledar a hannunta ta koma ciki, Hajara na ganin Amina da leda, ta fara washe baki, "Amina sayayya aka yo mana haka?" Ko kallonta Amina ba tayi ba, ta wuce ɗakinta. Zuwa tayi ta zauna ta bubbuɗe ledar, jaka ce mai tsadar gaske, da takalmi da safa, kai da ganinka san kaya ne masu matuƙar tsada. Fadila sai dubawa take taga Yazid a ajin, amma babu Yazid babu dalilinsa, har aka yi lectures ta farko aka gama, ba taga Yazid ya zo ba. Suka yi ta 10_12 ma, still Yazid bai zo ba, gashi tana lectures ɗin 2-4 za suyi presentation ɗin nan, amma Yazid bai zo ba, gashi presentation ɗin nan shi ne zai ɗau maki mafi yawa. Taje ta yo salla ta je Cafeteria ta ci Abinci, ta nufo aji.   A wuri ɗaya ta hango shi a zaune, ya sunkuyar da kansa, da alama wani abu ne mai muhimmanci ya ɗauke masa hankali, ba ta san ya aka yi murmushi ya suɓuce mata ba, ta nufi in da yake zaune "Kai dama zaka zo school ɗin nan, amma kayi missing ɗin har lectures biyu?" Tayi maganar ba tare da ta zauna ba, Yazid ya ɗago a hankali ya kalli Fadila, ya mayar da kansa ya cigaba da kallon wayarsa dake hannunsa. "Am talking to you" tayi maganar tana kallonsa. Ya ce "Ina jinki ai" "Kana jina Kai mini banza?" Cigaba da kallon wayarsa ya yi. Haushi ya kama Fadila, ta sa hannu ta zare wayar daga hannunsa, ko ɗaga kai bai ba balle ya kalleta. Duk da ƙaramar waya ce amma Alqura'ani ne a kai yake karantawa. Zama tayi a kusa da shi "Wai yau ma azumin maganar ka ke yi?". Kashingiɗa yayi da jikin bencin, ya ware mata idanunsa a kanta, still bai ce komai ba. Da sauri ta janye nata idanun, jin tsigar jikinta na tashi, ga wani gumi da bata san na menene ba yana tsatsafo mata a goshi, ta kasa tashi ta kasa komai, shi kuma ya cigaba da kallonta, kamar ya samu majigi. Samun kanta tayi da miƙewa tsaye, tana ƙoƙarin barin wurin, amma cikin shammata ya janyo hannunta wanda hakan ya tilasta mata zama jikinsu na daf da haɗewa har tana iya jin saukar numfashinsa a fuskarta, Allah yasa ajin babu mutane, kowa sabgar gabansa yake yi. Sosai jikinta yake rawa, kamar wadda ake yiwa gangi, ga idanun Yazid da suka dasa mata wani shocking da yake tsirga mata tun daga kanta har yatsun ƙafarta, yawun bakinta har wani bushewa ya yi. Bakinta ya dinga bi da kallo, ɗan madaidaici a kyakykyawar fuskarta, da ya ƙware a wurin iya tsiwa da masifa. "Bani wayata" ya furta yana sake ƙoƙarin sanya idonsa a nata, amma ta hana hakan, ta hanyar sunkuyar da kanta. "Bani mana" ya sake maimaitawa, amma ta kasa motsi, sai jujjuya idanunta da take yi. Hnnunsa ya sa ya zare wayarsa daga hannunta. Mafarkan da take da shine suka dinga dawo mata cikin ƙwaƙwalwarta, maganar Yusra ce ta dawo mata 'Wataran sai kin rungumeshi a zahiri' Firgigit ta dawo hayyacinta, daga duniyar da ta lula, har ta kasa gane mafarkan da ta saba yi ne, ko kuma zahiri ne, dan wani irin yanayi ta shiga wanda da ta kasa fassarawa kanta wane irin yanayi ne haka. Miƙewa tsaye tayi, ta bar wurin da sauri, tana ta sauke numfashi a jejjere. Yazid kuwa binta yayi da kallo, yana kallon yadda ta birkice a lokaci ɗaya, duk taurin kan Fadila, ba wuya ya sa ta shiga taitayinta. Fadila ta cigaba da rarraba idanu, tana jin yadda halin da ta shiga ya kasa barinta haryanzu. A hankali ɗalibai suka cigaba da dawowa ajin, saboda shiga lectures ɗin su ta ƙarshe, wadda daga ita kowa zai tafi gida, kuma wadda a ita ne, zasu gabatar da presentation ɗinsu. Lokaci na cika malamin ya shigo ajin, kasancewar mutum nai kiyaye lokaci, kowa ya nutsu ya shiga taitayinsa, kasancewar malamin ba shi da wasa Sam. Kowane 'yan group sun nutsu, sun haɗu wuri guda, suna tattauna yadda za su gudanar da presentation ɗin su, banda 'yan group ɗin su Fadila, ita tana nata wuri, Yazida ma haka, sauran 'yan group ɗin ma haka. Aka dinga kiran groups ɗaya bayan ɗaya, suna gabatar da presentation ɗinsu, duk karsashin group idan lecturer da 'yan bani na iyan aji suka fara suburbuɗo tambaya, duk karsashin 'yan group ɗin, sai sun karaya. Da haka aka zo kan group ɗin su Fadila, aka kira su, suka fito ɗaya bayan ɗaya, suka jeru a gaban aji, sai dai Yazid bai fito ba, sai da suka gama fita gaba ɗaya sannan Yazid ya fito, yana zuwa ya tsaya a kusa da Fadila, suna fuskantar 'yan aji. Ji tayi tana neman diriricewa, a hankali ya furta mata "Ki nutsu mana, you are facing the class" Suka fara gabatar da presentation, aka zo kan Wanda Fadila za tayi, gaba ɗaya ba ta da confidence, saboda a halin da Yazid ya sakata, sai dai yadda take zuba turancin ne zaka san ya zauna sosai a bakinta. Suka gama gudanar da presentation, aka zo fannin amsa tambayoyi, lecturer ya fara yi musu tambaya, Yazid ke da karsashin amsa tambayoyin, tun da shi ya yi Assignment ɗin, sai dai ba ya iya public speaking da harshen turancin yadda yakamata, a rubuce ne dai ba laifi, amma banda a baki. Yana ƙoƙarin bada amsar, sai larabci ya suɓuce masa, ya dinga haɗawa da hausa yana bayani. "Kai Malam, bafa ajin larabci bane, ba nahawu muke yi ba, da turanci zaka mana bayani" cewar wani ɗalibi. Yazid ƙoƙari yake ya kuma gudanar da bayanin, amma turancin yaƙi fita yadda yakamata. Ana haka, Amra ta kuma yankowa Yazid wata tambayar. Ƙoƙarin amsawa yake, gashi ya san amsar, amma bisa kuskure sai ya dinga haɗawa da larabci, babban abin da ya ƙonawa Fadila rai, bai wuce yadda wasu daga 'yan ajin ke masa dariya ba, ba ita ake yiwa dariyar ba amma abin ya ƙular da ita sosai. Shi dariyar da suke masa, bata dameshi ba, ganin turancin ya ƙi yiwuwa kawai ya juya harshe zuwa larabci, ya dinga zuba bayani, wanda ya tilastawa 'yan ajin yin shiru suna kallonsa, ba zaka taɓa cewa ya jii hausa ba. Fadila ce ta fara yi masa tafi, 'yan group ɗin ma suka ɗau tafi, lecturer kam zuba musu ido yayi yana kallon ikon Allah, ya miƙe tsaye ya ce "Kai Sheikh haka za muyi da kai, wa zai fassara mana me kace mu da bama jin larabci?" Yazid ya ce "Sir, ban iya turanci ba, kuma na ji sun ce ba sa so da Hausa". Lecturer ya dafa kafaɗar Yazid ya ce "Ka burgeni sosai, Allah ya ƙara hazaƙa, ina ɗan jin larabci kaɗan, na kuma fahimta, and you zaki zo mini da abin da kika fahimta a bayanin da yayi a next lectures" lecturer yayi maganar yana kallon Amra. Lecturer yayi nasiha sosai, da nuna musu kuskuren abin da suka yi, na son ƙure Yazid dan bai iya turanci ba. Fitar lecturer babu daɗewa, class rep ya fita gaban allo, ya dinga faɗa a kan abin da Amra da wasu 'yan ajin suka yiwa Yazid, duk da irin taimakon da yake musu, a kan koya musu wasu abubuwan da ya shige musu duhu. Amrah ta ce "Nifa bana son raini, ai naga Fadila ce ta fara yi masa dariya a ajin nan a kan bai iya turanci ba, amma ba wanda ya ce mata komai dan ana tsoron ta sai ni" "Kar ki ƙara saka sunana a shirmenki, ni ba sa'ar yinki bace wallahi" Fadila ta faɗa daga wurin da take tsaye, tana ƙoƙarin haɗa jakarta ta fice. Hayaniya ce ta nemi ɓallewa a ajin, Yazid kuwa tuni ya sulale yayi tafiyarsa. Saura ƙiris Fadila ta tsinke Amra da mari, da ƙyar aka lallaɓata aka sallameta ta tafi, dan Fadila ba ta fiye shiga harkar mutane ba, amma idan ama taɓata ta ƙware a masifa, bata ragawa kowa. Kusan ƙarefe goma saura na dare, Mummy ta shiga in da su Amina suke, ta ƙwanƙwasawa Hajara ƙofa, Hajara ta buɗe ta fito tana mutstsuka ido, alamun ta fara bacci. Hajiya Zainab ta kalli Hajara a yatsune ta ce "Ki dafawa baban su Fadila tea, ki ajiye masa a dining, zai fito ya sha" Hajara ta risuna ta amsa da to. Haka ta shiga kitchen, kamar tayi kuka, dan taji daɗin baccin da ta fara yi. Ta kammala dafa shayin, ta fita falo, ta tarar da Alhaji Ahmad a zaune a falon. Ta risuna ta ajiye masa shayin, ya miƙe tsaye, ba tare da ya kalli Hajara ba ya ce "Ajiye a nan, ki turo Amina ta kai mini falona" daga haka ya wuce ya barta saroro tana binsa da kallo. Hurry up and subsribe the VIP GROUP at affordable price. 08081012143 07063065680GABA DA GABANTA BY AISHA ADAM (AYSHERCOOL) 35 "Too wai meke faruwa a gidan nan ne?" Hajara ta faɗa a fili, sai da ta gama surutanta da mamaki, sannan ta tashi ta tafi kiran Amina" Amina na zaune a tsakiyar katifarta, ta baje litattafanta, tana ta aikin nata na karatu. Hajara ta ɗaga labulen ɗakin Amina, ta kalleta, ita lamarin Amina ya fara bata tsoro, kullum tana nace da littafi kamar masifa, har aiki idan tana yi, tana kallon littafi, saboda tsananin saka boko a ranta. Amina da bata son Hajara ta shigo ɗakin ba sai yanzu da ta ɗago kai, ta ganta a tsaye tana kallonta. "Lafiya kuwa?" Hajara ta ɗan geɓare baki ta ce "Maigidan nan ya ce ki kai masa shayi falonsa, yana son ganinki" "Ni kuma? Ba ke na jiyo Hajiya tana cewa ki dafa masa shayin ki kai masa ba?" "Na dafa masa, amma ya ce ki kai masa" Hajara ta faɗa a hasale. Haɗe rai Amina tayi tana ɗan tura baki, ganin Hajara ta zuba mata ido, tana nazartar action ɗinta ya sanya Amina ta ce "Ina shayin ya ke?" "Mhmm yana falo" "To zan kai masa, ina ga zai mini maganar tafiyar mu Abuja ne, wurin competition, ina ga makarantarmu sun masa magana" tayi maganar cike da son kawar da mugun tunani da mummunan zargi a zuciyar Hajara. Amina ta ɗan buɗe baki ta ce "Au Wai dagaske Habujar zaki?" Amina ta ce "Ai ban sani ba, sun ce zasu kira shi a waya ne su sanar masa, ina ga shi yasa ya ce in kai masa shayin, bari in je" Amina ta miƙe ta zura dogon hijjabi, a kan kayan da ke jikinta na bacci. Hajara tabi bayanta da kallo ta ce "Lallai yarinya, ni zaki rainawa hankali, zan zuba ido dai in ta bibiya" Amina ta ɗau kayan tea ɗin, ta tafi falon Daddy, tana fatan Allah yasa idon Hajiya Zainab biyu, kuma ya sanya tana ɗakin, yadda tana ajiye masa tea ɗin zata dawo ta cigaba da sabgarta, dan bata son wani abu ya sake haɗata da Daddy. Da sallama ta shiga falon, yana sanye da jallabiyya fara ƙal, hannunsa riƙe da remote. Ya amsa mata ba tare da ya waiwayo ya kalleta ba. Ta zo gabansa ta ajiye tea ɗin a kan center table. Ta juya zata tafi ta tsinkayi muryarsa yana faɗin "Sai yanzu kika ga damar zuwa?" Tsayawa tayi cak tana kallonsa, tayi masa shiru tana kallon gefe guda. "Zo nan" ya faɗa cikin command. Ta juyo ta dawo ta tsaya a gabansa tana kallon ƙasa. "Zaki saka kaina yayi ciwo, kin tsaya mini a ka kamar sa'anki" Ta nemi wuri a ƙasa ta zauna, tana cukuikuye hannunta a hijjabinta, kamar mara gaskiya. Ya ɗan kalleta ya kallia shayin ya ce "Haɗa mini tea" Ba musu ta matsa gaban teburin, ta fara haɗa tea, tana tunanin ina Hajiya Zainab take, a irin wannan lokacin da har Daddy ke samun damar keɓewa da ita? Zancen zucin da take, ya bata damar antaya sugar da yawa a cikin shayin. Sai da ta gama haɗa tea ɗin nan, sannan ya kalleta ya ce "Amma bani kika haɗawa ba ko?" Yayi Maganar yana tsareta da ido. Ta ɗago da sauri ta kalleshi. Ya ce "Eh mana, wannan kan ki kika haɗawa, wannan sukarin da kika zuba, idan na sha ai sai in rasa raina, kodayake dama haka kike so ko? Oya  Sake haɗa mini wani ki shanye wannan da kika cika sugan" A raunane ta ce "Ni na ƙoshi" "Ai kuwa sai kin sha, haɗa mini wani" Haka ta sake haɗa masa wani, ba tare da ta zuba sugar sosai ba, ta ajiye masa. Ta tsaya jiran ya bata umarnin tafiya. "Ki ɗauki shayin nan ki shanye na ce" "Wallahi na ƙoshi" tayi maganar kamar za tayi kuka. "Sai fa kin sha" Amina tayi shiru tana mamakin wannan takura haka. Ya cigaba da shan shayinsa, kamar ya manta da ita a wurin, can har ta fidda ran zai magana ya ce "Meyasa na bada abu a baki, dan kin raina ni kika dawo mini da shi ko? Kuma kika daina gaisheni, gani ga ki idan muka haɗu, sai kiyi fuska ki ƙi gaisheni, meye dalili?" Tuni ƙwalla ta taru a idon Amina, ta ce "Bakomai" "Akwai ko mai, sai kin gayamini dalili, ko mu kwana a nan tare" Ɗan waro idanunta tayi, amma ba ta iya cewa komai ba. "Wallahi idan na rufe ƙofar falon nan da mukulli, sai kin kwana a falon nan, kuma kin San halin Zainab ni ba ƙwatar ki zan yi ba a wurinta" Cikin marairaicwa Amina ta ce "Dan Allah kayi haƙuri, wallahi ban rainaka ba Daddy" "To menene idan ba raini ba" ya faɗa yana zuƙar tea hankalinsa kwance. "Ba kai ne ba" sai kuma tayi shiru, saboda kukan da ya ƙwace mata. Daddy ya ce "Ikon Allah, to gama kukan sai ki mini bayani, kafin ki gama ma na gama shan shayin nawa" Aikuwa Amina ta gyara zama, ta dinga kuka, sai da tayi mai isarta ba tare da Daddy ya ce tayi shiru ba, tana yi ta goge hawaye da hijjabinta. Ba tare da ya kalleta ba ya ce "Kinga ga tissue nan, ki dinga goge hawayen da majinar da ke ƙoƙarin zubowa, kar ki mini ƙazanta ina cin Abinci" aikuwa sai ta ƙaro sautin kukan nata, jin ya jefeta da kalmar ƙazanta. Ya ce "Cigaba da ɗaga murya, Allah yasa ta jiyo ki, ta zo ta tarar da ke kin saka mijinta a gaba kina kallonsa" Ba shiri Amina ta fara ƙoƙarin haɗiye kukan nata. Shi kuma ya dinga murmushin gefe ɗaya, yadda ba zata gani ba. Sai da ta gama kukan, sannan ya ce "Masha Allah, in kin gama ina jinki" "Ba kaine Kai mini gori ba, shi yasa na dawo maka da wayar ka" Dariya yayi ya ce "Subhanallah, Ohh ni Ahmad, to mai yasa kika daina gaishe ni" "Daina amsawa kayi, idan na gaisheka sai ka harareni" Sosai Alhaji Ahmad yayi dariya da jin abin da Aminar ta faɗa cike da wauta da ƙuruciya. "Ni Ahmad naga ta kaina, na yi miki gori nace me?" "Cewa kayi gidanka ba wurin tara maza bane, kuma ni Bakomai tsakanina da shi, ranar da ka ajiyeni a hanya ne, ya kawoni gida sai gaisawa da muke da shi shikenan" "Saboda na ce Kar ki sake kawo wani gidan nan shine kike jin haushina? Amina na fiki shekaru, hankali da kuma gwagwarmayar rayuwa, muddin kika haɗa karatunki da shirmen samarin zamanin nan, to ba zaki mayar da hankali ba, idan ki ka biyewa samarin zamani da soyayya karatunma sai ya gagareki, soyayya ba abin da ba ta sakawa. kuma ni idan kin gaisheni ba hararki nake ba, bana amsawa ne saboda ki fahimci kin mini laifi, ki bani haƙuri amma ki kayi mirsisi ashe ke nan fushi kike dani ne ko? Wace irin 'ya ce haka mai fushi da babanta har ta daina kula shi, ya bata abu ta mayar masa anya kuwa kina Baban da ni?" Amina tayi shiru ta sunkuyar da kai. "Shikenan, ni bari in sauko in baki haƙuri" Da sauri ta ce "A'a kayi haƙuri dan Allah kar ka bani haƙuri" "To tunda fushi kike, har da cewa na miki gori gara in bada haƙuri ai" "Kayi haƙuri dan Allah, bana fushi da kai" "To sai kuma me nayi miki?" "Kace mini ƙazama" ta faɗa har cikin ranta. "Yaushe kuma na ce miki ƙazama?" "Yanzu" ta faɗa tana tura baki. "Eh ai ƙazamar ce, kalli yadda kika ɓata hijjabinki da hawaye, kuma haka kike mana girki, kina mana ƙazanta, shi yasa Abincin yake daɗi ashe". "Mhmm ka daina ce mini ƙazama" "To ki daina goge hawaye da hijjabinki" Ya ɗan tsura mata ido, sannan ya ce "Jeki janyo drower can, wayarki na ciki, ki ɗauko ki haɗo mini da abin gwajin suga na" tamkar wata kurma haka ta tashi, taje ta ɗauko abin da ya sakata, ta dawo ta zauna, ya sauko daga kan kujerar ya zauna a kusa da ita, hakan ya sa ta sake takurewa. Ya fito da kayan gwajin, ya yi gwajin sugan nasa, ya kalleta ya ce "Kin gani sakamakon daina kula dani, suga na ya hau duk abin da kika ga dama, dafawa kike ki bani, suga na ya hau ya kai sha biyu da ɗigo uku" Ita dai ba tace masa komai ba, sai sunkuyar da kai, kamar mara gaskiya. A ranta ta ce 'Hakkin azababbiyar matarka ne ai bani ba, abin da aka ce in dafa ai shi zan dafa' Ya miƙa mata wayar ya ce "gata nan, lokaci lokaci, zan dinga karɓa ina dubawa" Ta Sanya hannu biyu ta karɓa ta ce "Na gode Allah ya saka da alkhairi, naga takalmi da jaka ma, Baba ya bani Allah ya ƙara buɗi" "Amin rigimammiya, mutanen nan ma da kika mini Maganana akan su an biya musu kuɗin shekara biyu, na bawa Maigidan fili ya gina kamar yadda kika nema" A gigice Amina ta kalleshi ta rasa me zata ce masa sai ta sake fashe masa da kuka. "Ke wai komai ma kuka kike masa, tashi ki tafi Allah ya bamu alheri" "Allah ya biyaka da Aljanna Daddy" Yayi murmushi ya ce 'Ameen, tare da ke da kika ankarar da ni nayi aikin alkhairi. To Yanzu mu shirya ko?" Yayi Maganar ƙasa-ƙasa. Ta ɗaga masa kai alamar eh. "Bana son ɗaga kai, amsa mini zaki" "Eh mun shirya" ta faɗa cikin jin kunyar abin da tayi. "To shikenan, tashi muje in rakaki bakin ƙofa" ta miƙe tsaye hannunta riƙe da kwalin wayarta. "Kun koma makaranta yau ko?" Tace "Eh Daddy. kayi magana da Baban kuwa a kan tafiyar?" "Kar ki damu, zamu yi maganar in sha Allah, ke dai ki cigaba da karatu" "Ina nan ina yi, ka dinga yi mini addu'a" "Sai kin biya tukuna, kawo abin sadaka, ai miki Adduar" dariya Amina tayi ta ce "Zan kawo, idan kai mini addu'ar na ci" "To shikenan, kije ki duba wayar, abin da baki gane a ciki ba, sai ki mini magana" "To Daddy na gode" ta juya ta fice, Daddy ya tsaya yana binta da kallo, harta ɓacewa ganinsa, sannan ya koma ciki, yana shafa gemunsa. Hajar kuwa tun da Amina ta tafi wurin Daddy take yi tana leƙa falo zuwa kitchen, dan taga dawowar Amina, amma shiru babu Amina babu dalilinta, ji take tamkar ta zama tururuwa ta rarrafa taje ɗakin Alhaji Ahmad, ta gano meke faruwa Amina ta zauna haka? Tun tana zuba ido taga dawowar Amina har ta gaji, ta tafi ɗakinta ta zauna tayi shiru tana tunani, tashi ta kuma yi ta leƙa ɗakin Amina, ta tarar da ita a tsakiyar katfarta tana kunna sabuwar waya. "Amina ashe kin dawo, naga kin daɗe daga kai shayi, ki kayi wannan zaman?" "Kai Hajara, ban gane me kike nufi ba, da na kai masa shayin fa suna tare da Hajiya, na ajiye musu na tafi baranda na cigaba da karatuna, me zai zaunar da ni kuma?" Sai kuma cikin borin kunya Hajara ta ce "Au, na zata wani laifin ki kayi ai, duk hankalina ya tashi, wannan sabuwar wayar fa" Amina ji tayi kamar ta zagi Hajara, amma idan ba ta bi Hajara a sannu ba, zata sanya kwaɓarta tayi ruwa, dan haka ta ce "A makaranta ne aka bamu, saboda mu dinga amfani da ita wurin karatu" "Allah sarki, lallai wannan makaranta taku ana ji daku, lallai da safe na shigo a bani in gani" Amina tayi murmushin yaƙe, ta cigaba da kunna wayarta, bayan Hajara ta fita Amina ta raka bayanta da harara, cike da jin haushin saka idon da take mata. Hafsa na cikin bargo ta ƙule, ta saka wayarta a silent, tare da rage mata haske, suna chatting da Khalil, sai su daɗe suna chatting basu san dare ya yi ba, ita kanta tana mamakin kanta yadda ta yi wani irin sabo da Khalil, wanda har ya kai idan Khalil baya son abu, har rawar jiki take ta daina, duk abin da ta san zata yi yayi farin ciki tana masa. Haka shima ɓangaren sa tattalata yake tamkar ɗanyen ƙwai a kan dutse, shima yana kaucewa duk wani abu da zai sanya ta ɓacin rai ko damuwa, yana matuƙar tausayinta, hakan ya sanya yake tattalinta yake gudun abin da zai ɓata mata rai ko tayi fushi. A Hanyar Yazid ta tahowa makaranta, suka haɗu da class Captain ɗinsu, ya ɗauko Yazid a babur ɗinsa, suna tafe yana bashi labarin faɗan da Amra da Fadila suka kusa yi jiya, a kan abin da Amran tayi masa. Yazid dai bece komai ba, sai ɗan murmushi da yayi, Captain ya cigaba da bashi haƙuri, a kan irin abubuwan da wasu daga cikin 'yan ajin suke masa. Zuwansu yayi dai-dai da tsayuwar motar Fadila. "Ahh Yazid ga Bestynka nan ta ƙaraso" "Wace kuma Besty na?" Yazid yayi maganar cikin ko in kula. "Fadila mana" Ta rufe motar ta ɗan tsaya tana jiran ƙarasowarsu. "Captain" ta faɗa tana ɗan murmushi. Captain ya ce "Na'am tsigai, sarkin tsiwa" "Kaga ka kiyayeni bana so" Yazid yaƙi ko kallon in da Fadila take. Ya yin da ita kuma take satar kallonsa, Captain ya ce "Bari in yi gaba ku gama ganawa, dama zan karɓo mana Assignment, sai kun taho" yayi gaba ya bar su a tsaye. Captain na barin wurin, Yazid shima ya yi tafiyarsa ya barta a wurin, gaba ɗaya sai taji babu daɗi shareta da ya yi, ko dai Kankiya ya kira shi ya yi masa warning ne a kanta, shi ya sanya ya daina kulata?. Ɗan taɓe baki tayi, ita ma ta nufi aji tana cigaba da zancen zuci. Sai yau Azima ta dawo daga hutu, suka rungume juna ita da Amina suna ta murna. "Azima shi ne kika ƙi dawowa sai yau?" "Ke bari, munje hutu da Mummy ne, sai jiya muka dawo" Amina ta ce "Masha Allah, ya Mummyn?" "Mummy na nan lafiya, ya Baba da mutanen gidanku marasa mutunci" Amina ta ɗan ɓata fuska ta ce "Meye haka?" "Ba dole in faɗa ba, mutuncin ne da su? Wallahi matar nan ta bani mamaki Amina, a gaskiya kina haƙuri sosai, Allah ya ƙara miki haƙuri" "To Azima idan ban yi haƙuri ba yaya zan yi? Tun da karatu nake son nayi" "Ke zan yiwa Mummy magana, wallahi da zaki yadda ki dawo gidanmu, ki daina wannan aikin, Mummy zata dinga biya miki kuɗin makaranta, meye dubu sittin Allah na tuba, Mummy zata biya miki" Waro ido Amina tayi ta ce "Azima dubu sittin kuma? Dubu sittin ne kuɗin makarantar?" "Au ke da baki sani ba? Dubu sittin ne fa kawai duk term, sai sauran abin da ba a rasa ba, Mummy tana da kuɗi sosai, ga shi Daddynmu ya mutu ya bar mana kuɗi, ni da Yaya Sagir da nake gaya miki, wallahi da zaki yadda Mummy cewa tayi zata ɗauke ki ki dawo gidanmu, ita tana sonki" Shiru Amina tayi tana tunani, Yanzu duk term naira dubu sittin Alhaji Ahmad yake biya mata na makaranta, kuma gashi ance na shekara ya biya mata, ga kuɗin litattafai da sauransu. "Ya naji kin yi shiru? Zaki yadda ki dawo gidanmu?" Firgigit Amina ta dawo daga tunanin da ta tafi, ta ce "Azima Baba ba zai yarda in nisa da shi ba, nima ba zan so hakan ba, amma naji daɗi da ƙauna da karamcin da Mummy take nuna mini, shi wannan aikin da nake na lokaci ne, watarana sai labari. Kuma in Allah ya kaimu next year fa zamu gama, da an gama wannan competition ɗin fa za'a fara yi mana lesson ɗin Jamb da na Waec da Neco, Kinga lokaci kaɗan ya rage mana". "Haka ne Amina, Allah yasa mu gama lafiya" "Ameen" Amina ta amsa. Har aka tashi Yazid bai yi gigin zuwa in da Fadila take ba, gaba ɗaya sai taji babu daɗi, dan a 'yan kwanakin ta saba da shi da nacinsa, ba tare da ta shirya hakan ba. Hajiya Zainab ta sha mamakin yadda Khalil ya iya daina shigowa cikin gidan, ko gaisheta yayi balle ya ci Abinci, duk dan saboda ta raba shi da wata 'yar matsiyata. Dan haka a fusace yau ta tafi ɗakin nasa, ta tarar yana zaune  yana dannan system, walpaper system ɗn, hoton hannunsa da na Hafsa ne sanye da zobunan da ya saya musu. "Sannu mara mutunci salamamme" A razane ya ɗago ya kalli Mummy. "Yanzu Khalil wuyanka har ya yi kaurin da dan nayi maka faɗa na hanaka kula wata matsiyaciyar yarinya zaka daina shiga harkata, ka daina shigowa cin abinci?". "Mummy ba haka bane kaw .... "Yi mini shiru, gaba kake da ni ko Khalil, ka kyauta ka cigaba kar ka fasa, wannan yarinyar ce dai ko, to na rabaka da ita har Abada. Idan kuma ka ƙi ji, ba zaka ƙi gania ba. Ta juya ta fice tana huci, ba ta jin zata iya yiwa Khalil sassauci a kan al'amarin nan sam. Khalil ya dafe kansa da yayi masa wani irin nauyi, da har yake barazanar yi masa ciwo, ya rasa Wannan wace irin ƙiyayya ce haka Mummy take yiwa talaka, meye aibun Hafsa banda talauci, kuma ai komai na Allah ne. Washegari ma a school, Yazid ya ƙi kula Fadil, ya cigaba da sabgoginsa, sun yi lectures na farko, sun samu break, Fadila ta kasa jurewa, ta tsinci kanta da tafiya wurin da yake a zaune, a can ƙarshen ajin. "Ustaz wurinka na zo" Ya ɗago ya kalleta "Waye kuma Ustaz?" "Kai mana" "Baki san suna na bane?" "Eh sunan naka ne bana riƙewa" Yazid ya gane ba zata iya kiranshi da sunansa bane a gabansa, amma dan rainin hankali ba zata faɗa ba. "Magana fa nake maka" "Ba fa kurma ne ni ba, ina jinki" "To ba zaka amsa ba" "Ki faɗi sunana mana idan so kike in kulaki" yayi maganar ba tare da ya kalli in da take ba. Share maganar tayi ta ce "Abu nake son ka koya mini dan Allah" "Ba zan koya ba" ya bata amsa direct. Ji tayi kamar ba taji daidai ba, dan haka ta ce "Me kace?" Ya waiwayo ya kalleta ya tsuke fuska ya ce "Ba zan koya ba nace, idan kin koyi faɗan sunana sai in koya miki" Nan da nan ya ga ɓacin rai ya bayyana a fuskarta, kawai ta juya ta bar wurin, ranat yana mata suya, 'laifina ne da nuna na damu da kai, shi yasa har ka yi mini wulaƙanci' ta faɗa a zuciyarta. Tana bada baya Yazid ya fara dariya ya furta "Yarinya ba wayo" yana ankare da ita har suka kammala lectures na biyu, sai cika take tana batsewa, taji zafin abin da ya yi mata sosai. Sai da ya daidaici lokacin da yafi sakata a kwana, ya hautsina mata lissafi, ya dawo daga salla, lokacin da ɗalibai suka ragu daga ajin, wasu suka tafi salla wasu cin abinci, ya lura ko sallar babu alamar ta je, ta Kwantar da kanta a kan benci. "Bestyna, what are you thinking about? Tashi muyi karatun ɗauko littafin muyi karatun" Sarai ta gane muryarsa, amma tayi masa banza, taƙi ɗagowa. "Common, ɗago mana" yayi maganar yana zama a kusa da ita. Da sauri ta tashi zaune, ta kuma matsawa ciki, tana haɗe rai. "Ɗauko littafin muyi karatun" "Kaga malam ka ƙyaleni bana so" ta faɗa tana jin kamar a lokacin ya ce ba zai koya mata ba. "Haba Ukty, kefa kika fara wasan nan, kika ce idan ina da zuciya kar in sake kula ki, kuma ina da zuciya a ƙirjina, tana aiki kuma, kawo hannunki ki taɓa kiji" yayi maganar kamar zai riƙo hannunta. "Wai meye haka ne, kar ka sake ka taɓa ni" "Ashe kina tsoro, kawo muyi lesson ɗin kin ji Bestyna" "Bana so, na gaya maka ka ƙyaleni zan maka rashin mutunci wallahi" "To ni rashin mutunci wanne ne baki yi mini ba, duk haddace in kin mini ba haushi nake ji ba, ni ɗanawa nayi yau, amma ki yi haƙuri muyi da wasa nake miki" Ɗauke kanta tayi, tana kallon gefe guda, irin yayi idan ya gaji ya tashi. "Baƙin gashi, fararen idanuwa, dogon hanci, bakin tsiwa, matsakaicin tsayi, fa tubarakallahu ahsanul khaliƙin, You Are beautiful" murguɗa baki tayi tana kuma ɗauke kai. "Shikenan, idan kin sakko kya kulani, ni na tafi gida, saurayinki ne zai shigo lectures yanzu, gara in fita in tafi, tun kan ya shigo ya dizgani a gaban mutane saboda ke". "Kar ka sake cewa saurayina, na gaya maka" "Saurayinki ne mana, idan ba saboda ke ba me nayi masa ya tsaneni, bai san ba wata alaƙace ta kirki tsakanina da ke ba, ki mini tsiwa lokacin da kike so, ki lallaɓani idan kina buƙatar wani abu a wurina, ko ba haka ba ne?" "Kai ka sani" "Dama ni na sani mana, ki kalli idona ki maimaita abin da kika faɗa in ba tsoro ba" Sake kifa kanta tayi, tai masa shiru, tana jinsa ya ɗau biro, yana mata rubutu a jikin hannunta, taƙi ko motsi, sai da taji alamar ya tashi ya tafi, sannan ta ɗaga hannun ta duba, da larabci ya yi mata rubutu, sai dai ba ta gane meya rubuta ɗin ba. Ɗaga kai tayi taga har ya kai ƙofa, a ranta ta ce 'A haka kamar baya magana, amma ya iya wulaƙancj kala-kala'. Khalil ya rasa yadda zai yi da ransa, gashi ya cinye satinsa biyu, amma babu wani daidaito a tsakaninsa da Mummy, balle ya sanya ran zata fahimce shi. Kusan ƙarfe goma na dare, yana kwance a kan gado, ya rungume pillow, yana ta zuba soyayya a waya shi da Hafsa. "Baby, ina ga haryanzu Abincin da kika mini, bai gama narkewa a cikina ba, har yanzu bana jin yunwa" "Ni dai ban yadda ba, idan ulcer ta kama mini kai, sai mun yi faɗa" "Allah Hafsa bana son cin abinci, ga kewar ki ta isheni zan koma wurin aiki" Ta Kwantar da muryarta ta ce "Eyya,  ai ba komai, ka kwantar da hankalinka, zamu dinga waya". "Ai ni nafi sonki a kusa da ni Babyna, ginin gidanki ya kusa kammala insha Allah, idan na je zan ɗauko miki video ki gani, idan da abin da bai miki ba sai a sauya" Hafsa ta ce "Wace ni in ce ga abin da bai mini ba, komai kai daidai ne, Allah ya yassare maka halal, ya tabattar mana da alkhairi" "Ameen my sweet, yadda gari yake da sanyin nan, ace kina kusa da ni, kin dafa mana tea, ina sha ina kallonki cike da so da ƙauna" Tayi dariya ta ce "Abin da ka hango kenan?" "Eh mana, da mun yi aure ba ruwaa da bargo, kin isheni" Ta ɗan tura baki ta ce "Zaka fara ko? To sai da safe" ya buɗe baki zai yi dariya, yayi tozali da Mummy a tsaye a kansa, wadda ganin bai shigo cin abincin dare ba, duk da faɗan da tayi masa ya sanya ta biyo shi ɗakinsa, ta zo ta tarar da shi yana waya da Hafsa. Mugun kallon da ke masa ne ya sanya shi, rikicewa ya katse wayar yana kallonta" AYSHERCOOL 08081012143GABA DA GABANTA BY AISHA ADAM AYSHERCOOL PAGE36 Cikin rikicewa da inda-inda Khalil ya ce "Mu..mmm...Mummy dan Allah ki tsaya ki ji" "Me zan tsaya in ji banda wanda na ji Khalil, ai naji komai ka saurari matakin da ni kuma zan ɗauka". "Innalillahi, Mummy dan Allah kar ki yiwa Hafsa komai, marainiya ce" "Eh marainiya ce, kai ne baitul mali ai, kai ne mai arziƙin ɗaukar nauyinta a ɗora maka wahala, kana nan kana gina mata gida ko? Sai ta shiga in gani, kaje ta dafa abu tayi barbaɗe barbaɗe ta baka kaci, zaka gamu dani" ta fice fuuu ta bar ɗakin. A sukwane Khalil ya bita, yana kiran sunanta. Ya cinmata a falo. "Mummy dan Allah kar a yiwa Hafsa wani abu, ni ki hukuntani, ba zata iya ɗaukar hukuncin da zaki mata ba" "Rufen baki Khalil, ni zaka mayar ƙaramar yarinya, wato har Asirin da suka yi maka ya fara tasiri a kanka ko? Matsa ka bani wuri kan in make ka" Ya haɗa hannayensa biyu cikin magiya ya ce "Dan Allah Mummy ko sau ɗaya ki saurareni, wallahi mun shaƙu Hafsa bata da wani aibu, dan Allah ko sau ɗaya ki saurareni" Shareshi tayi ta wuce ɗakinta, Khalil ya zauna a kan kujera ya dafe kansa, wani irin gumi ya tsatsafo masa a goshi, duk da a yanayi ake na sanyi. Amina da ke gefe tana kallon Tv tayi shiru, jikinta yayi sanyi tamkar ita ake yiwa faɗan, gaba ɗaya taji babu daɗi, Saboda Hajiya Zainab ta iya tijara. Ita Amina abin har mamaki ya bata, ɗanta ma ba ta ƙyaleshi ba, duk dan ya ce yana son 'yar talaka ake wannan dambarwar bala'in. Jiki a saɓule Khalil ya miƙe, ya bar falon yana tunanin meye mafita, bai taɓa yiwa Mummy turjiya a kan wani abu ba, amma a wannan karon zuciyarsa na raya masa ya tirje, tun da Aurensa da Hafsa bai saɓawa Addini da kuma Al'ada ba, gani yake idan ya fasa aurenta bai mata adalci ba, kuma bai san wani irin hali zata shiga ba kuma bai san hannun wa zata faɗa ba, babban abin daya ƙara tsaya masa shi ne, bai wataƙila idan ya rabu da ita halin da zata shiga na damuwa ya fi na baya, tun da dama shigarsa rayuwarta ne ya bata ƙwarin gwiwa sakewa da rage mata damuwar da take ciki. Washegari Daddy ya fito falo, ya tarar da Amina a zaune, tana jiran lokaci ya cika ta tafi makaranta "Ina kwana" Amina ta gaishe shi. "Lafiya ƙalau, yau ban hararekin ba ko?" Murmushi tayi tana sake janyo jakarta jikinta. "Har kin shirya tafiya makarantar?" "Eh jira nake lokaci ya cika" "Ok, school ɗin ku sunyi mini waya, a first term za a yi muku registration ɗin Jamb da SSCE ko?" Amina ta ce "Eh haka suka ce mana" "To ki ƙara dagewa, idan result ɗinki yayi kyau, hope baki manta da sirrinmu ba  ko?" Cikin murmushi Amina ta ce "Eh, ban manta ba, zan yi karatu sosai in sha Allah" Daddy ya ce "Good girl" hakan yayi daidai da fitowar Fadila, cikin shirin tafiya makaranta. Ba ta kawo komai a ranta ba, ta zauna, ta zuba Abinci ta fara ci. "Ina Mummynku ne?" Daddy ya tambayi Fadila. "Bacci take, ta ce kar wanda ya dameta" "Ok, nima fita zan yi yanzu". "To Daddy a dawo lafiya" Fadila ta faɗa tana shan tea. Da ido ya yiwa Amina alamar, ta biyo bayansa. Amina ta miƙe ta saɓa jakarta, tabi bayan Daddy. Sai da suka fito daga falon, sannan ya tsaya Amina ta ƙarasa in da yake, ya dubeta ya ce "Muje in ajiye ki a School ɗin, sai in wuce in da zani" Amina ta ce "Amma Ba wani wurin zaka ba? Kar ka makara fa, zan hau Napep" Yadda ya tsareta da ido ne, ya ɗan tsuke fuska ya sanya ta yin shiru, yayi gaba ta cigaba da bin bayansa. "To bari in je in gaida Baba" "Ki sauri" ya faɗa tare da nufar in da motocinsa suke. Amina ta isa wurin Baba, ta durƙusa har ƙasa ta gaishe shi. "Lafiya ƙalau Uwata, kin tashi lafiya?" "Lafiya ƙalau Baba, ya aikin" "Alhamdilillah, zaki tafin ne?" Amina ta ce "Eh, amma wai ya ce zai ajiyeni a makarantar" Cikin rashin fahimta Baba ya ce "Shi wa?" "Baban su Fadila" Baba ya ɗan yi shiru, saboda ya lura a 'yan kwanakin nan akwai wani ɓoyayyen abu tsakanin Alhaji Ahmad da Amina, yanzu bata tsoronsa kwata-kwata, ga wata shaƙuwa a tsakanin su. Ga yawan kyautata mata da yake yi, ya yita sayen abubuwa yana bawa Baban ya bata, tuna miyagun fatan da su Bala suka dinga yi a lokacin da ya sanar da su Amina zata taho birni karatu. Kan Baba ya ce komai, Alhaji Ahmad ya ƙaraso in da Baba yake da mota, ya sauke glashin motar, Baba ya taso da sauri, suka gaisa da Alhaji Ahmad. Ya ce "Zan sauke Amina a makaranta sannan in wuce" Baba yana matuƙar jin nauyin Alhaji Ahmad, mussaman duba da irin alfarmar da Ya yi masa a kan Amina, haka ya danne ya ce "To shikenan babu laifi, Allah ya saka maka da alkhairi" "Ahh kar ka damu babu komai". Amina ta zaga ta shiga mota, Daddy ya ja motar suka bar gidan. "Daddy a kashe Ac nan sanyi fa" Amina ta faɗa tana duunƙule jikinta saboda sanyi. Kwaikwayon muryarta ya yi ya ce "Ba za a kashe ba zafi nake ji" A ɗan shagwaɓe ta ce "Allah sanyi nake ji, mura zan yi idan baka kashe ba" "Mayar da ita ɗumi, ai kina kusa da wurin" yayi maganar yana mayar da hankali a kan tuƙinsa. Ta ce "Ai ban iya ba" "Ohh Ashe fa 'yar ƙauye ce" Ta ɗan zumɓura baki, tana kallonsa ta gefen ido. Miƙa hannunsa ya yi, ya canza zuwa ɗumi, tamkar zai taɓata, hakan yasa ta takure jikinta har da ɗan rintse ido. Yayi murmushi kawai sannan ya ce "Kin gane kan wayar taki kuwa?" "Eh na gane, wayar tana da kyau sosai, ga Camera mai kyau, duk nasa lambar ƙawayena da ta Baba a ciki, har what's app aka buɗe mini" "Waye ya buɗe miki?" ' "Ƙawata Azima" "Kar ki sake zuwa da wayar makaranta, kuma ban yadda ki saka lambar wani  namiji a ciki ba" Ta ce "Dama sau ɗaya naje da ita makarantar, ba zan sake ba, amma har lambar mazan ajinmu ma ba zan saka ba? Kuma an sani a wani group fa na makarantarmu gaba ɗaya". Daddy ya ce "To daga haka kar a ƙara, idan ba haka ba what's app ɗin ma zan hana" "Tom na gode sosai, zan kiyaye in sha Allah" "Kin sa lambar ƙawaye Amma kika kasa ko yi mini flashing a wayar taki, ko kuma da safe ki gaisheni a wayar, bayan har kuɗi na saka a layin, kuma da lambata a ciki" Amina ta zaro ido ta ce "Haka kurum, in kiraka ta ɗaga in ce mata me?" "Ita wa?" "Au, ba kowa" "Saifa kin faɗa, ita wa?" "A'a, haka kurum in faɗa in je ka ajiye ni, a titi" Kawai yayi dariya ya cigaba da tuƙi. A ƙofar makarantar ya ajiye ta, ya ce "In an tashi zan turo a ɗauko mini ke, ko in zo da kaina" Amina ta kalleshi ta ce "A ɗauko ni a kaini ina? Ina da kuɗin mota fa" Ya haɗe rai ya ce "Haka nace" "To Allah ya baka haƙuri, Allah ya kaimu a tashin" ta ƙarasa maganar tare da buɗe motar ta fice. Ƙarfe goma da rabi ma safe, sannan Mummy ta tashi daga bacci, tayi wanka ta karya, ta cigaba da tunanin ta ina zata ɓullowa lamarin Khalil, yadda zata rabashi da yarinyar nan. What's app ɗinta ta buɗe, ta duba group ɗin su, da suke ita da Hajiya Salma da Turai, tayi sallama. Cikin ikon Allah duk suna online, suka amsa mata, suka gagaisa tare da tambayar junansu yara da kasuwanci, Mummy ta tura musu saƙon Voice message. "Jama'a ku bani shawara yadda zan ɓullowa lamarin yaron nan, haryanzu fa yaƙi rabuwa da ita, jiya har naje ɗakinsa na tsaya a kansa yana waya da ita, bai san na zo ba, har gaya mata yake, wai zai yi mata video na gidanta na Abuja". Nan da Nan Hajiya Salma ta haɗa group Video call, "Lallai ma Zainab, to wani matakin kika ɗauka?" "Zage shi nayi tsaf, amma banga alamar zai saduda ba, bina yake kuma yi, wai zai yi mini bayani, na rasa mema yakamata in yi" Turai ta ce "Ke, ta bayan gida zaki ɓullowa lamarin, Khalil dai ɗanmu ne, ba zaki cigaba da zuba masa ido ba a mallake miki shi a banza ba" Mummy ta tari numfashinta ta hanyar cewa "Kamar kin san har da maganar tayi masa girki ya ci naji, gaba ɗaya jiya da ƙyar nayi bacci wallahi" Hajiya Salma ta ce "Kut kinga Zainab bamu ga ta zama ba, ba mun san in da yarinyar take ba, ai mu muka ganota a hanyar zuwa plaza, zuwa za muyi mu kasa mata warning, ko nemi gidansu muje har gidan nasu mu samu uwarta, mu musu wankin babban bargo, idan suna da zuciya zasu rabu da shi, kinga ko ya ƙi Allah ya haƙura" Mummy ta ce "Amma kamar ƙasƙanci ne, mu wanke ƙafa mu tafi gidan talakawa yawon yi musu warning, gaskiya Khalil ya gama da ni, wai 'yar masu awara a kan kwalta, wannan yaro duk matan garin nan" Hajiya Salma ta ce "Meye wani ƙasƙanci, biyan buƙata ai yafi dogon buri, da su mallake shi fa, da munyi nasarar raba su, ki nemo masa mata ya aura" Mummy ta ce "Haka za ayi, bari ƙarfe huɗu bayan sallar la'asar, mu haɗu ku rakani muje" Turai ya ce "Allah ya kaimu yammar" suka amsa da Amin. Ganin yau ƙarfe goma babu malamin da ya shigo, ya sanya Fadila tafiya Library, dan Captain ya sanar da cewa malamin ba zai samu shigowa ba, kuma ga exams na gabatowa. Ta nutsu sosai ta mayar da hankalinta kan littafin da ke gabanta, ba zato ba tsammani taji an ja kujerar da take ta baya, kamar zata faɗi, a razane ta ƙwala wani marayan ihu, saboda ta tsorata sosai da sosai. Sai da hankalin wasu daga cikin tsirarun ɗaliban da ke cikin libraryn ya dawo kansu, bai saki kujerar ba, ya leƙo fuskarta ta sama yana kallonta yana murmushi. Ta marairaice kamar zata yi kuka ta ce "Dan Allah ka sauke kujerar nan kar in faɗi" "Ba zan bari ki faɗo ba ai". "Dan Allah ka ajiye kujerar, bana so" "Haka kike shagwaɓaɓiya, faɗi sunana sai in saki kujerar" "Dan Allah ka bari, zan faɗo fa" Sake matso da fuskarsa yayi saitin tata ya ce "Sai kin ce Yazid tukuna" "To ajiyeni sai in faɗa" "Ni zaki yiwa wayo yarinya, faɗi ko in kai ki ƙasa a kan kujerar" yayi maganar yana sake jan kujerar baya. "Wayyo Allah Daddy, Yazid na faɗa ka ajiyeni dan Allah" "Wow, sake maimaitawa in ji" "Dan Allah ka bari" tayi maganar tana rirriƙe hannunsa, jin yadda yake kuma baya da kujerar. "Kar ki saka mutane su juyo suna kallonmu, ke zasu gane ni na da mask a fuskata, sake faɗa" A hankali ta ce "Ai na faɗa" "Ki ka ce me?" "Yazid" "To daga yau, kar ki sake zuwa ki tsaya a kaina, cikin tsiwa kina wani cewa Ustaz" "To naji, ajiye ni" Zuba mata ido yayi, yana kallon bakinta, yadda take motsashi a hankali cikin tsoro. A hankali ya mayar da kujerar yadda take. Dafe ƙirji tayi tana sauke ajiyar zuciya, saboda yadda ta tsorata. Kujerar gabanta ya ja ya zauna, yana kashe mata ido. Wata uwar harara ta watsa masa. "Da kika samu na saukeki shine ki ke hararata ko" wata harar ta kuma watsa masa tana ta sauke ajiyar zuciya. Jan littafin gabata yayi ya ce "Kawo mu gani, me kike karantawa" Janye littafin tayi ta ce "Ina ruwanka da abin da nake karantawa". "Hmm babu ruwana, me kika ce zan koya miki jiya?" Cikin tsiwa ta ce "Ai na ce maka na fasa, bana son koyarwar taka" "Aikuwa karki nuna kin sanni a exam hall" Hararsa tayi ta saka takalmanta zata tashi. Ya ce "Haba Besty, zauna muyi karatun mana, tun da kika shigo school ɗin nan nake biye da ke, kika je wurin Yusra, ki ka koma Aji, sannan ki taho nan" "Wallahi ka takura mini" Yazid yayi murmushi ya ce "To ya zan yi tun da bani da abokai, ana abota da ni ne saboda abin a za a mora wurina na karatu, ni kuma nafi son ayi abota da ni saboda Allah" "To ni ina ruwana da wannan bayanan naka?" Ɗan tsura mata idanu yayi yana nazartar yanayinta, a hankali ya furta "Happy birthday in advance" Waro idanunta tayi tana kallonsa, "Waye ya gaya maka birthday na?" Murmushi ya yi ya ce "Password ɗinki na System da kika saka na gane date of birth ɗinki, gobe in Allah ya kaimu shekarunki Ashirin da biyu, Happy birthday 'yar yarinya". Fadila ta ce "Allah ya hore maka saka ido, da bin ƙwaƙwƙwafi, kai dama ɗan sanda ka zama" Yayi murmushi ya ciro leda a aljihunsa, cikin fargaba ya miƙa mata. "Meye wannan?" A ɗan sanyaye ya ce "Karɓi ki gani, sai dai ban sani ba, ko kina karɓar abin da ya fito daga hannun talaka kamar ni ba, first gift as a brother, and at the same time friend" Ɗan taɓe baki tayi, ta karɓi ledar ta buɗe, ta fara ciro abin da yake ciki, turaren lailatul sahara da Bushra, da kuma wani abun hannu da zobensa, da gani dai ba mai tsada bane, amma taji kyautar ta kama zuciyarta. Ɗan murmushi ta yi ta ce "Kai ka mini kyauta ta farko wannan birthday, na gode sosai" "Da gaske Kin karɓi kyautar da nayi miki?x yayi Maganar da mamaki, dan bai taɓa zaton zata karɓa ba. Tayi murmushi ta ce "Gashi kuwa kana gani" ta ɓalle abin hannun ta saka, ta zura zoben. Ta ce "Na karɓi abin hannun Ustazu" tayi maganar tana dariya, tana kallon hannunta. Yazid yayi mata ƙuri da ido, yana kallon yadda take murmushi, da yake matuƙar burge shi, sai dai ya san cewa abu ne mawuyaci idan ya bayyana mata haƙiƙanin abin da yake zuciyarsa ta yarda da shi ba. Yanzun ma ya aka cika, shirin nasu baya ɗaukan lokaci, suke ɓatawa. "Ya ka zuba mini ido ne?" Ta miƙa masa greeting card ɗin da yake cikin ledar, wanda rubutun larabci ne a jiki ta ce "Fassara mini wannan" Ya kalleta ya ce 'Ki karanta mana" "Amma dai ka san ban iya ba" "Birthday wishes ne kawai" ta ce ok Ta jujjuya katin tana kallon adon da ke jikins, ta ɗago ido, taga yadda ya ƙureta da ido. "Wai kallon me kake mini ne? "Ba komai, lokacin salla yayi, muje muyi salla" ta jinjina kai ta miƙe, ta ɗau jakarta, da ledar da ya bata suka fita daga libraryn. Da yamma Fadila ta dawo gida, tana dawowa ta shiga falo ta watsar da jakarta a falo kamar yadda ta saba, ta shilla ɗakinta da gudu, saboda fitsarin da ya matseta. Daidai lokacin Mummy ta fito cikin shiri, zata je ta ɗauki su Hajiya Turai. Jakar Fadila da ta gani yashe a tsakar ɗakin ne ya sanya ta gane Fadilan ta dawo gida. Miƙa hannu tayi zata ɗaukewa Fadilan jakarta, taga leda a ƙasa. Ta ɗau ledar ta buɗe, sai taga turare guda biyu da kati a ciki. Sansana turaren tayi tana yamutsa fuska, tamkar wadda ta shaƙi warin bola. Fadila ta fito daga ɗakinta, dan zuwa ɗakin Mummy, amma taga Mummyn tsaye hannunta riƙe da ledar da Yazid ya bata. "Mummy fita zaki ne?" "Eh fita zan yi, me kike da wannan a jakarki?" Ta nunawa Fadila turarukan tana yatsune hanci. "Bani aka yi" Fadila ta bata amsa. "Waye ya baki wannan tarkacen, turare kamar na 'yan bori" Fadila ta miƙa hannu ta karɓa tare da faɗin "Wallahi turarukan da ƙamshi, wani ne ya bani" "Waye wani?" "Wani ɗan ajinmu ne?" "Meye haɗinki da shi da zai baki wannan tarkacen ki karɓa?" "Bani da wani haɗi da shi, muna mutunci ne kawai, and i can't reject it, ba zai ji daɗi ba, kuma bani kaɗai ya bawa ba" "Shikenan, kar dai ki sake ki shafa wannan turarukan ki shiga jama'a, kowa yaji wannan turaren ya san mai arha ne, wani wari suke kamar na ciyawa, ni zan ɗan fita zan je wata unguwa" "Ok Mummy, safe journey" "Thank you" ta amsata ta fice. Alhaji Ahmad bai tura ɗan aike ba, shi da kansa ya je makarantar ya ɗauko Amina, suna tafe suna hira, ya ajiyeta a ƙofar gida ya shiga da motar ciki, dan ko Baba bai san tare suka dawo ba. Gaba ɗaya hankalin Hafsa yana kan mutanen da take sallama, tana yi tana iza wutar awararta. Wata danƙareriyar mota ce ƙirar Highlander tayi parking a gefen inda Hafsa take. Sam hankalinta baya kan abin da yake wakana wajen abin da yake gabanta. "Ke!" Taji an yi shouting a kanta. Cikin ɗabi'arta ta ta miskilanci, ko ɗaga kanta ba ta yi ba, ta cigaba da sallamar mutane, dan ba ta kawo ma da ita ake ba, saboda yanayin yadda aka yi maganar cikin isa da gadara. "Ke da ke nake magana, nayi magana kika mini banaza" Jin an dunguri kanta ne ya sanya ta ɗaga kai, ta kalli Hajiya Turai dak zazzaro mata ido, amma ba ta ce uffan ba. "Wai ba da ke nake ba? Ko bayan talauci kuma naksashiya ce ba kya ji ne?" Cewar Hajiya Salma. Kamar ba za tayi Magana ba kuma sai ta ce "Me nayi miki ne?" Tayi maganar cikin rauni. "Uwarki ki ka yi mini? Ina magana kina jina dan iskanci kika shareni?" "Uwata ta gode" Hafsa ta sunkuyar da kai, tana fifita wuta. Saboda rashin girma, da iya duniyanci, Hajiya Turai ta saka ƙafa tayi fatali da awarar da Hafsa ta riga ta tsame, ta kuma yi ball da wadda take cikin bokiti tana soyawa. A gigice Hafsa ta miƙe tsaye ta kallesu "Baiwar lafiya,me nayi miki zaki zo wurin san'ata kina watsar mini da kaya? Ni ban sanku ba ban taɓa ganinku ba balle in ce ko wani laifin nayi muku" Hajiya Turai ta ce "Ashe ƙaramar fitsararriya ce, yanzu da na zubar da wannan tsiyar, ai gashi kin bani dukkan hankalinki, dana ɓarar da tsiyar da kuka dogara da ita, ba kece Hafsa ba? Kin samu yaro kin asirce shi, yana muku bauta, 'yar matsiyata ce, ni na zata ma wata haɗaɗiyar yarinya zan gani, kalleki kalli kayan kayan jikinki, Khalil ya miki kama da sa'an Aurenki?" Sai yanzu Hafsa ta gane ina suka dosa, kuma a kan me suke mata wannan tijarar, da tuni mutane suka fara taruwa suna kallon abin da ke faruwa. Hajiya Salma ta kalli Hafsa a wulaƙance ta ce "Ɗanmu ba tsarar aurenki bane, ki duba cikin kwararon matalauciyar unguwarku, ba zaki rasa Irinki ki aura ba, ko kuma 'ya'yan kwalta lalatattu irinki, da babu yarinyar kirkin da zata zo bakin titi tana kasa kaya, tana cakuɗeɗeniya da maza, ka ce ta kirki ce, ki nemi irinki daidai ke ki aura, Khalil ba sa'an yinki bane" Turai ta kalli wasu almajirai ta ce "Kai zo ku ƙarasa zubar mini da wannan kayan ƙazantar, zan biyaku, idan na karya jarin in ga uban da zai ɗorasu, matsiyata gayyar yunwa an samu mai kuɗi ana rawar jikin bin malamai a asirce shi aci dukiya" Hafsa zuba musu id tayi tana kallon ikon Allah, tana kallon yadda ake cigaba da yi mata watsi da kaya, bayan ta kwashi zagi da cin mutumci a bainar nasi, Hafsa a yau tayi dana sanin sanin Khalil da tayi, dan haka ta yunƙura tayi wani abu wanda daga shi, zata yanke alaƙar ta da Khalil. Ta ɗauko wayarta ta fara dannawa, zuciyarta na mata wani irin zafi, amma ta dake taƙi yin hawayen, ta shiga neman lambar Khalil. Hajiya Turai ta yiwa Hajiya Zainab alama da ta fito. Hajiya Zainab ta buɗe motar, ta fito ta nufo in da suke a tsaye da cincirindon mutane. Gaban Hafsa ya faɗi, dan ko ba a gaya mata ba, kammanin matar da ta gani da Khalil ta san mahaifiyarsa ce. Tuni ta turawa Khalil saƙo kamar haka "Please man, idan ban takuramaka ba, ka taimaka mini da dubu goma" Da saƙon ya isa wayar Khalil, yayi mamaki, dan ko da abu mai kamar wasa, bata taɓa roƙonsa abin ficika ba, amma yau tana neman dubu goma Bai yi tunanin komai ba, ya tura nata dubu talatin. Mummy ta ƙarewa Hafsa kallo, dan ta gano wani aibun nata, saboda ta ji daɗin cin mutuncinta, amma ba taga alamar wani aibu ba, bayan na talauci. "Ni ce uwar Khalil, na zo ne nan ne da mutanena, dan in sake ja miki kunne, muddin baki rabu da shi ba, yadda na saka aka watsar da wannan tsiyar da kuke kasawa ku dogar da shi, haka zan saka a rushe mini in da kuke zaune, saina tabattar da kun dauwama cikin tsiya. Wannan gayyar iskar da kike kasawa, da dudu kuɗinsa bai wuce kuɗin ruwan robar da Khalil yake sha a sati ba, da na sa aka watsar, kaɗan nayi miki, kin san waye Khalil kuwa? Kin san waye ubansa a ƙasar nan, kin masa asiri zaki mallake mini shi? To ahir ɗinki wallahi, kuma daga yau na saka almakashi na datse duk wata alaƙa dale tsakaninki da Khalil, saboda ba sa'an Aurenki bane, naji ya ce ke marainiya ce, sai ki jira idan ya buɗe orphanage Home, sai ki requesting ko zaki samu gurbi" Hajiya Salma ta ce "Talaka kenan, akwai ladabin dole, ga yadda ta sunkuyar da kai kamar ta Allah, irin wannan cinikin ne idan dare yayi suke tara maza su lamube su su basu kuɗi, banda haka ina wata awara zata riƙe mutu" "Khalil ya biyani kuɗin asarar da akayi mini, kuma daga haka insha Allah in dai ni 'yar halak ce, bani ba Khalil har abada, in sha Allah na rabu da shi" Hajiya Turai ta ce "Kar ma ki rabu da shi, kici ubanki ko ba dan Allah ba, ai karo da karo sai rago" DOMIN SHIGA VIP GROUP KU TUNTUƁENI TA WANNAN LAMBAR. AYSHERCOOL 08081012143GABA DA GABANTA BY AISHA ADAM (AYSHERCOOL) Page37 Hafsa tabi bayan su Hajiya Turai da kallo, da mamakin irin tsanar da ta gani ƙarara a idon Mummy. Jikinta a sanyaye tabi wurin da aka watsar mata da kaya da kallo, ga sauran mutane da suke tsaye a wurin, Mussaman majalisar mai shayin nan, da wanda suke jin haushinta bata kula su, da wanda take burgesu saboda kamewarta, wasu suka jajanta mata, abin takaicin shi ne yadda har su Hajiya Turai suka yi mata tijara suka gama baby wanda yayi yinƙurin dakatar da su ko basu haƙuri sai son jin ƙwaƙwaf. Daga irin zage-zagen da suka yi ne, wasu suka gane cewa mahaifiyar Khalil ce da jama'arta. A gaggauce Hafsa ta durƙusa, ta dinga tsince kayanta da aka baje su a wurin kamar abun banza, zuciyarta na wani irin raɗaɗi da zafi, ta dinga ƙoƙari ta danne hawayenta, mai shayi ya tayata tsince kayan, ya so saka baki, amma ganin su Hajiya Salma sun yi kama da manyan 'yan duniya ya sanya bai iya saka baki ba. Ya tsare mata abin hawa ta shiga, mai shayi ya ce "Ayi ta haƙuri Hafsa, haka rayuwa take" Ita dai ba ta ce masa komai ba, sai da taga mai Napep ɗin nan ya ja baburin, ya bar wurin, sannan ta fashe da wani irin kuka, mai ban tausayi da ratsa zuciya. "Yaushe zan samu sauƙin rayuwa ni Hafsa, daga wannan sai wannan, Astagfriullah" ta faɗa a hankali tana ƙanƙame jikinta, tana cigaba da raira kukanta, tana jin yadda zuciyarta tayi mata nauyi, shikenan Khalil ɗin da ta saka rai, ta fara samun afuwa a tare da shi, shima zai kauce, zata koma waccan duniyar da yayi ta ƙoƙarin fito da ita daga ciki, mai tarin damuwa da rashin gata. Kan su kai gida, tuni idanunta sun yi mitsi mitsi, sun yi jawur kamar wadda aka sawa teargas, ta sauko ta sallami mai Napep, ta kwashi kayan da wasu suka yi buɗu- buɗu da ƙasa, ta shigo da su ta ajiye a tsakar gida. Mama ta kalli kayan ta kalli Hafsa ta ce "Ke lafiya kuwa? Meye ya sameki wanan kayan ya aka yi suka yi kaca-kaca da ƙasa haka?" Hafsa na ƙoƙarin dannewa, amma ta kasa kawai ta nufi ɗaki da sauri, tana zuwa ta faɗa kan katifar Mama, ta fashe da wani irin kuka, jikinta har rawa yake yi. Mama ta biyo ta cikin tashin hankali, tana faɗin "Hafsa ki gaya mini, meyafaru wannan wane irin kuka ne kike yi, Ki gaya mini menene" Mama tayia maganar cikin matsananciyar damuwa tana ƙoƙarin ɗago Hafsa. Hafsa kasa magana tayi, kuma ta kasa yin shiru, nan da nan hankalin Mama ha ninka tashi, cikin rauni ta ce "Dan Allah ki gaya mini maiya faru, ko dai Najib ɗin ne dai?" Hafsa ta girgiza kai alamar a'a. "To Hafsa ki gaya mini menene, har bugun zuciyata ya sauya wallahi, dan Allah ki mini bayani" tayi maganar hawaye na cika idanunta. A birkice Hafsa ta tashi zaune, tana girgizawa Mama kai ta ce "Mama dan Allah kar kiyi kuka" "To Hafsa ya zan yi, kin shigo kina wannan uban kukan, ga kayan sana'arki duk ƙasa, dole hankalina ya tashi" Hafsa ta sunkuyar da kanta, wasu hawayen ma zubowa, ta saka hannunta ta share hawawnta, ta ɗan ɗago ta ce "Mama ina ga bani da sa'a a rayuwata" "Subhanallah, kamar yaya, Meyasa kike faɗan haka?" "Mama Khalil" ta faɗa tana sake fashewa da kuka. Cike da zaƙuwa sa son jin ƙarshen zancen, Mama ta ce "Me Khalil ɗin yayi miki?" Cikin kuka mai ƙuna zuciya, da dashewar murya, Hafsa ta ce "Mamansa ta zo ita da wasu mata inda nake sana'a, ta ce bani babu ɗanta, wai ni ba sa'ar aurensa ba ce ba, saboda ni talakace, suka ci mini mutunci a gaban mutane, suka zubar mini da kayan sana'ata. Ai kema Mama kin san ai ba dan kuɗinsa nake son sa ba ko?" Mama tayi shiru, ranta ya ɓaci, idan Hafsa na cikin damuwa, tana iya haɗiyeta taƙi faɗa, amma tabbas tun da ta kasa ɓoyewa Mama, ta faɗa mata kai tsaye, abin ya girmama. "Yanzu dan kawai kina 'yar talaka shi ne suka je suka yi miki Wannan cin mutuncin?" Hafsa ta ɗaga mata kai tana kuka. "Shikenan, share hawayenki, Allah ya kawo miki mafi alkhairi, ita kuma Allah ya ganar da ita, in dai Khalil ne ba shine autan maza ba ai" Hafsa ta faɗa jikin mama tana kuka, Mama ta rungumeta sosai tana rarrashinta, ganin Hafsa bata ganinta ya sanya ta lunshe idanunta ita ma, hawaye suka shiga kwararo mata, ita ta matsa Hafsa a kan ta yarda da Khalil, sai da ta yadda da shi tayi nisa a son sa wannan matsalar ta kunno kai, Mama ta share hawayenta ba tare da Hafsa ta gani ba ta ce "Ga ruwan wanka can na dafa miki, na kammla girkin dare, idan an yi sallar magariba, sai kiyi wanka ki zo ki ci Abincin dare. Hafsa jin Mama kawai take, amma Abincin nan ba ciyuwa zai yi ba a wurinta. Khalil kuwa ya dinga jerawa Hafsa waya, amma ko ɗaya bata ɗauka ba, ta share wayar, ƙarshe ma ta saka wayar a silent, ta jefata bayan katifarta. Daddy na zaune a kan kujera 3seater, Fadila na kusa dashi, tana ta 'yan ciye-ciyenta tana masa hira irin ta uba da ɗa. Amina kuma na ƙasa a zaune tana kallon tashar da suke kallo. Fadila ta ce "Ke ɗan jeki ɗakina, ki ɗauko mini wata leda a kan madubina" Amina ta tsani ke ɗin da Fadila kan kirata da shi, ko ita ko Mummy, amma ba yadda ta iya, haka ta tashi, ta nufi ɗakin Fadilan. Ta je ta ɗauko ledar ta kawo, ta miƙawa Fadila, Daddy ya ɗan ƙure Amina da ido, yana mata murmushi. Amina dai bata nuna ma ta san ita yake yiwa murmushin ba. Fadila ta ɗauko turarukan da Yazid ya bata ta ce "Daddy, sansana wannan turaren kaji, da ƙamshi?" Daddy ya ce "Wow, lailatul sahara, na so turaren nan sosai, ina kika samo shi?" "Wani ɗan ajinmu ne Yazid ya bani, as a birthday gift, but you, you even forget about it, you don't even wish me" tayi maganar cikin shagwaɓa. "Ohh my dear, ai naga birthday ɗin naki sai gobe in Allah ya kaimu zai cika, kuma ni banga kina mana organising komai ba". Fadila ta ce "Yusra zata yi mini cake, then just chill with you tonight, mu ci Abinci tare snap pictures together that's all, ba zan haɗa hayaniya ba" Ya ce "Hmm, alright Allah ya kaimu" "Ameen Daddy, amma me zaka bani as my birthday gift?" Ya ce "Mmmm, what do you want?" "Kome ka bani yayi" "To shikenan, Dubai or Umrah" Fadila ta ɗan zaro ido ta ce "Daddy Umrah, ina son komawa Saudiyya" "Fine, amma ke da Mummyn ki zaku je, idan kun yi hutun makaranta" "Alhamdilillah, Daddy na gode sosai, Much Love my Hero" tayi maganar tana rungume Daddy tana murmushi. Amina da ke gefe, ta kwaɓe baki, ganin yadda Fadila ke ta nan nan da babanta, tana zuba taɓara, amma ta iya zagewa ta wulaƙanta wani, ba tare da tunanin yadda take jin son babanta a ranta haka kowama yake ji ba. "Daddy, ka san Mummy cewa tayi wai turaren nan wari suke yi kar in shafa" Daddy ya ce "Aikuwa turaruka ne masu kyau" Fadila ta nuna masa hannunta ta ce"Kalli, har abin hannu ya bani, da turaren nan, Daddy baka ga ƙoƙarinsa ba sai dai Yaizd bai iya turanci ba, kaga yadda yake larabci kamar balarabe" "Dama ai haka lamarin ilimi yake, kuma turanci yare ne kawai" Hajara ce ta leƙo falon, ta ga Daddy zaune shi da Fadila suna hira suna kallo, Amina kuma ta kame a ƙasa ita ma kallon take yi. A ranta zuciyarta ta ce Lallai ma yarinyar nan, ina can ina aiki, kin zo kin zauna a cikin masu gida kina kallo A fili ta ce "Amina, ko zaki zo ki yanka mini alayahhu muyi mu kammala girkin dare kan Hajiya ta dawo?" Daddy ya ce "Kallo, take yi, kiyi aikin a hankali ba sai kin yi gaggawa ba, tun da ba yanzu za aci Abincin ba" Da ɗan mamaki Fadila ta ce "But Daddy, she's also a maid, ai ba kallo ta zo yi ba" "Yes i know, she's facing her SSCE,  yakamata tayi passing, kuma abin da take kalla is educative, bana son yin asarar kuɗin makarantar da nake biya" Jiki a saɓule, gwiwa a sace Hajara ta koma kitchen, tana masifa tare da mamakin yadda Amina ke abin da taga dama, da wasu abubuwa da ke faruwa, wanda ta kasa gane kan in da suka dosa. Fadila ta tashi tsaye ta ce "Daddy, zanje in ɗan yi karatu, exams is around the corner" "Ok Best of luck" "Thank you" ta nufi ɗakinta. Sai da ya tabattar Fadila ta bar falon, sannan ya ce "'yar Daddy" shiru Amina tayi ta cigaba da kallonta. "Amina am talking to you fa" a hankali ta waiwayo ta kalleshi. "Ya naga kin haɗe rai, any problem?" "Nothing" ta faɗa a taƙaice. "Oya kawo mini Apple, da ruwa" ta miƙe ta nufi kitchen, ta tarar Hajara ta cika tayi famm, tana aiki ita kaɗai. Tana ganin Amina ta ce "Yauwa, ga alayahun nan, kk ɗauka ki yanka" "Wai baki ji me Daddy ya ce ba? Kallo nake yi, kuma wallahi da nice ba zan takuraki sai kin yi aikin nan ba, duk ni zan abina, amma ke ba damar in ɗan huta sai ki sa mini ido, ke fa wuni kike a gida ni kuma ga makaranta ina zuwa haba. "Amina rashin kunya zaki mini?". "Ni ban miki rashin kunya ba, kece ba kya jan girmanki" Daga haka Amina ta ƙarasa gaban fridge, ta buɗe ta ɗauko Apple, ta ɗora a kan plate da wuƙa ta bar kitchen ɗin, ta bar Hajara da mamakin da tambayoyin da babu mai bata amsarsu. Ta kawo wa Daddy ta ajiye masa. "Yanka mini mana 'yar Daddy" Amina ta zauna ta yanka  masa ta miƙa masa, yasa hannu ya karɓa yana ci. Can Amina ta ce "Daddy, ya sugan naka ya sauka kuwa?". "Ban duba ba, naji daɗin jikina Yanzu sosai Alhamdilillah" "To Allah ya raƙa lafiya" "Ameen 'yar Daddy, anjima ki hau online muyi hira" Ta ɗan kalleshi ta ce "Karatun fa?" "Wai ke ba kya hutawa karatun nan ne? Ki dinga hutawa ranki" "Ai ba iya karatun boko nake ba, bana son haddata ta zube dole sai ina tilawa" Cike da girmamawa ya kalli Amina ya ce "Masha Allah, 'yar Daddy, kina nufin kina haddar Alqura'ani?" Ta jinjina masa kai alamar eh. "Kai, dole in san abin yi, ban goyi bayan haddar nan ta zube ba, kin haddace duka ne?" "A'a, ban haddace duka ba" Daddy ya ce "Matso nan kusa da ni muyi magana" Amina ta matsa kusa da ƙafafuwan Daddy, ya ajiye ɗan ƙaramin plate ɗin da ta zuba masa Apple a kai, a kusa da ita, sannan  ya ce "Na daɗe banga mutum mai ƙwazo kamarki ba, zanga abin da ya dace, yakamata in samo wanda zai cigaba da koya miki a gida ina biyansa" Amina ta washe baki ta ce "Ai ba sai ka kirawo wani ba, direbanka Zakiru malami ne, ka ce ya dinga koya mini, sai ka dinga biyansa shi" Daddy yayi murmushi ya ce "To shikenan, zan yi Magana da shi in sha Allah" "Na gode Daddynmu" Yayi murmushi ya ce "idan kin yi tilawa, ki dinga yiwa Daddynki Addu'a". "Me zan roƙa maka?". "Abubuwa da yawa, amma ba zan gaya miki ba, kan ki yayi ƙarami ba zai ɗauka ba" Hajara kuwa tana laɓe ta hanyar shigowa falon, tana hango Amina da Alhaji Ahmad, amma ba ta jin me suke cewa, bata iya hango Alhaji Ahmad, amma tana ganin Amina tana murmushi, Amina ta miƙe, ta ɗau ragowar plate ɗin da Alhaji Ahmad ya gama da shi, ta ɗan tsaya a kan Daddy tana sauraren abin da yake faɗa mata. Idan ba gizo idanun Hajara suke mata ba, kamar shagwaɓa Amina ke yiwa Daddy, shikuma ya kashingiɗa yana kallonta. "Na shiga uku ni Hajara, me ake aikatawa a gidan nan ne? Ita ma matar gidan uwar gantali, tana can yawo ana munafurtarta, kai amma wannan an yi tsohon banza, wannan 'yar tamilon 'yar zai tsaya tana masa barikanci yana kallo, yo ko ya aka yi ma ta samu wannan damar oho?" Amina ta nufi hanyar ƙofar kitchen, sai ga Hajiya Zainab ta turo ƙofar falon, sai da Amina ta ɗan razana, ta tsaya ta zubawa Hajiya Zainab ɗin ido. "Ke uban me kike kallo, sai kace mayya kin tsaya kin zubo mini ido, ko kin aike ni ne?" Amina ta girgiza kai, ta nufi barin falon. "Ki kawo mini ruwa, da exotic ƙishirwa ta isheni" tayi maganar tana ƙarasawa in da Daddy yake. Hajara na ganin Amina ta ce "Mmm su Amina manya, kina sha'aninki" ko kallon Hajara Amina ba ta yi ba, ta cigaba da sabgarta. Alhaji Ahmad ya ɗan ɗaga murya ya ce "Sweetheart kin dawo?" Mummy ta ce "Na dawo, kana gida kenan?" "Na dawo tun ɗazu, ban sameki ba masu aikinki sun ce mini ba kya nan" "Eh, fita ce ta sameni da gaggawa" Ya ce "Ok, sannu da zuwa". "Yauwa, Fadila ta dawo ne?" Ta faɗa tana zama a kusa da Daddy. Daddy ya ce "Ta dawo, yanzu ta gama yi mini mita, wai gobe in Allah ya kaimu birthday ɗinta, ban wishing ɗinta ba" Mummy ta ce "Ƙyaleta rigimammiya" Daddy ya ce "Nan ta nuna mini turare, wai an bata gift, amma ni ban bata komai ba" Mummy ta ce "Naji ta ce za'a yi mata girki, ayi hotuna tana ta lissafinta dai". Daddy ya ce "Na yi mata alƙawarin umara, zaku je ke da ita, maybe idan sun yi hutu" Mummy ta ce "Inyee 'yar gidan Daddy, to Allah ya kaimu, dama nima ina son zuwa, to Allah ya kaimu" "Wai ni Khalil ya koma ne?" Daddy yayi maganar da ɗan damuwa. A daidai nan Amina ta kawowa Hajiya Zainab ruwa da lemo. Hajiya Zainab ta ce "Mata da wannan yaron, wani halin rashin mutunci ya ɗaukar wa kansa, amma zan yi maganinsa" Daddy ya ce "No, wani abun yana damunsa ne, idan har yana gidan nan, ba zai ɗauke ƙafa daga shigowa gidan nan ba" Mummy ta ce "Ka rabu da shi kawai" ta mayar da idonta kan Amina ta ce, "Ki buɗe ki zubamini, kin zo kin tsaya a kanmu kina rarraba ido". Amina ta tsuke fuska, ta fara ƙoƙarin zuba wa Hajiya Zainab ruwa a kofin, ta zuba zata miƙa mata ruwan, Daddy ya kalli Amina ya kashe mata ido ɗaya. Aikuwa sai hannunta ya kama rawa, har ta zubawa Hajiya Zainab ruwa a jiki. "Ke mahaukaciya, ba kya gani ne? Ke wace irin dabba ce, kalli yadda kika zuba mini ruwa a jiki, ba kya gani ne?" Cikin rawar murya Amina ta ce "Kiyi haƙuri, ba da sani na bane" Dama Hajiya Zainab har yanzu a ƙule take, duk da sunje sun yiwa Hafsa rashin mutunci, amma bata huce ba, dan haka take ƙoƙarin ƙara hucewa a kan Amina, a hasale ta ce "Dalla ɓace ki bar gabana, dabba kawai" Hawaye ne suka cika idon Amina, amma Daddy ya shiga girgiza mata kai alamar kar tayi kuka. Duk yadda Mama tayi da Hafsa, a kan ta daure ta ci Abinci, ƙi tayi, tana sallar isha'i, ta kwanta, ta zubawa wayarta ido, tana kallon yadda kiran wayar Khalil da saƙonninsa ke shigowa babu ƙaƙƙautawa, amma bata ɗaga ko guda ba. Ƙarshe ta saka wayar a flight mode, ta shiga gallery, tana kallon hotunan Khalil da ke wayarta, da Videos ɗin da yake haɗa musu, na hotunansu shi da ita. Wata irin soyayyarsa ce take sake fizgarta, tana jinta wani iri iya awannin data kwashe daga fitarta zuwa wurin sana'a zuwa yanzu da ba suyi waya ba, ta san yana can cikin damuwar rashin ɗaga wayarsa da ba ta yi ba. Ta ƙanƙame wayar a ƙirjinta, ta toshe bakinta, ta cigaba da kuka, dan tun a yanzu ta fara jin kewarsa, tana matuƙar ƙaunar Khalil har cikin ranta. Fadila ce tsaye a gaban mudubi, sanye cikin doguwar rigar abaya, ta ɗan gyar fuskarta, ta ɗauki turaren wurin Yazid ta shafa, ta ɗaura abin hannun, sannan ta ɗauki wasu turarukan ta shafa, ta ɗauki jakarta ta jefa mukullin motarta a jaka, ta tafi ɗakin Mummy. Bata tarar da ita a falon ba, dan haka ta wuce ɗakin Daddy. A can ta tarar da su a falon Daddy, a tare ta gaishe su suka amsa. Daddy ya ce "Har kin shirya?" "Eh Daddy, and karku manta, tonight in Allah ya kaimu, za muyi party" Daddy ya ce "To Allah ya kaimu" Ta ce "Amin" ta ɗau jakarta ta fito falo, a falo ta haɗu da Amina, ta kalli Amina ta ce "Yauwa, idan kin dawo daga school, zan ɗan yi mini party na birthday na, dan haka a gyara ko ina, zamu zo ni da Yusra, za ayi decorations a falon nan" Amina ta ce "To, Allah ya kaimu" Fadila ta fice, ba tare da ta amsawa Amina ba. A ƙofar ajinsu taga Yazid, kamar me jiran wani abu. Tun daga nesa yake mata murmushi, har ta ƙaraso. Tana ƙarasowa ta tsaya tana kallonsa ta ce "Wa kake jira ne? Naga kana ta fara'a kamar an maka kyautar wani abu" "Ke kawai nake jira, in ga kwalliyar ranar birthday, kin yi kyau sosai". Ta ce "Ikon Allah, ba zaka daina sa ido ba ko?" "Ai ke kaɗai nake sawa ido, bayan ke bana sawa kowa" ba ta kuma cewa komai ba ta shiga aji. Yazid kuwa murmushi ya yi, ganin abin hannunta da ya bata, da kuma tashin ƙamshin turaren lailatul sahara a jikinta. Lectures ɗaya tayi attending, ta tafi gidansu Yusra, ita Yusra basu da lectures. Ta tarar Yusra ta gama haɗa mata cake ɗin ta da duk wani snacks da za tayi amfani da shi, suka rankaya tare zuwa gidansu Fadila. Kusan wuni suka yi, suna decorating ɗin falon, Amina na taimaka musu da wasu abubuwan, yayin da ta zuba ido tana ganin yadda suke gudanar da komai. Khalil ya kasa jurewa, ya shiga damuwa da tashin hankalin rashin sanin dalilin da ya sanya Hafsa bata ɗaukar wayarsa, dan haka da yamma ya shirya ya tafi wurin sana'arta, dan ya san a daidai wannan lokacin ba zai sameta a gida ba, ta fito sayar da awara. Sai dai tun daga nesa ya ga wurin nata ba kowa. Ya ƙarasa ya yi parking ɗin motar, ya sauko ya nufi wurin, ya shiga wurin mai shayi, suka gaisa da Khalil. Khalil ya ce "Hafsa ba ta shigo bane?" "Eh, ba ta zo ba yau, ai wasu mata ne suka zo wurin nan jiya, suka watsar mata da komai na kayan sana'arta, suka yi mata zagin tsamar nama suka tafi" A firgice Khalil ya ce "Tsaya, ban gane ba me tayi musu?" "Oho ina na sani, biyu ɗima-ɗima, ɗaya sirirya a wata ƙatuwar mota, haka suka zo suka yi rashin albarka suka tafi, dama da ganinsu kaga 'yan duniya, na rasa a in da Hafsa ke zuwa tana kwaso rigima, rannan sun yi da wannan ɗan iskan, jiya kuma da waɗa nan mata" Khalil dana fahimtar me mai shayi yake faɗa masa yai, ya juya da hanzari a koma wurin da motarsa take, ya shiga ya rufe, ya bar wurin. A bakin layin su Hafsa ya yi parking, ya sauka ya taka da ƙafafuwansa, zuwa ƙofar gidansu, ya samu wani yaro a ƙofar gidan, ya aika shi ya kira masa ita. A ƙalla ya shafe mintuna Ashirin a tsaye a ƙofar gidan bata fito ba, ba wai taƙi fitowa bane, dan ta muzguna masa, sai dai tunanin halin da su biyun ka iya shiga, ta daɗe tana kuka, da ƙyar Mama ta rarrasheta ta fito. Ko da ta fito, bata ƙarasa in da Khalil ya ke ba, a bakin soron gidansu ta tsaya. Kallo ɗaya ya yi mata yaga yadda ta rame, idanunta sun yi jawur alamun tayi kuka har ta gaji. Da sauri ya nufi bakin soron, ya tsaya cikin damuwa ya kalleta ya ce "Hafsa baki da lafiya ne? Ina ta kiran waya ba kya amsawa, kalli yadda duk kika fita hayyacinki, meke faruwa ne?" Duk yadda ta so dakewa, sai da hawaye suka zubo mata, ta miƙa masa wata babbar jaka, ta ajiye a gabansa, sannan ta kalleshi ta ce "Khalil, jiya na maka text, ka turo mini kuɗi, ka bani ninkin abin da na nema, na nemi kuɗin nan ne dan mayar da asarar da aka yi mini, na kayan sana'ata, Khalil daga rana mai kamar irin ta yau, ka sa a zuciyarka baka taɓa saɓnin wata mai kama da ni bama, balle tuna mun yi soyayya. Jiya mahaifiyarka ta zo ita da wasu, sun yi mini kashedin babu ni babu kai. Tabbas sun yi gaskiya, zaren ba kalar yadin bane, ni da kai bamu dace ba, kyautatawarka a garrni ta ruɗeni na fara sonka, ba tare da na kalli banbancin matsayinmu ba. Ga shi nan duk wani abu daka bani, na tataro na dawo maka da su, zoben nan ne kawai ba zan iya dawo maka da shi ba, saboda kana cikin mutane masu muhimmanci da suka shigo rayuwata, na san ba zan taɓa iya mantawa da kai ba, Na gode Khalil Allah ya haɗa kowa da rabonsa" ta ƙarasa maganar tana zubar da hawaye, ta juya ta shiga cikin soron. Cikin zafin nama Khalil ya bita, ya riƙota ya juyo da ita tana fuskantar sa. Kamar zai fashe da kuka ya ce "Haba Hafsa, ina duk alƙawarin da kika yi mini na kasancewa da ni, duk ƙalibalen da ka iya tasowa kuwa, dan Allah karki ce zaki rabu da ni ba, dan Allah kar ki mini haka, in dai Mummy ce zan yi mata bayani, zata fuskance ni kuma, dan Allah Hafsa, muna son junanmu karki yanke wannan hukuncin" "Bakin Alƙalami ya riga ya bushe Khalil, idan na ce bana sonka nayi maka ƙarya, amma duk wani abu da za ayi iyaye ba sa so ba zai taɓa yin albarka ba, banga alamar Mummy zata fahimceka har ta bari muyi aure ba, dan Allah Khalil kar ka sake shigowa rayuwata, Allah ya haɗa kowa da rabonsa" Ta zame hannunta daga cikin nasa da ya riƙe, ta shige cikin gidan tana kuka. Contact me for the VIP group AYSHERCOOL 08081012143GABA DA GABANTA BY AISHA ADAM AYSHERCOOL PAGE 38 Wani abu me mai nauyi ya tokarewa Khalil ƙirji, bai taɓa tunanin Mummy zata aikata abin da ta aikata ba, na zuwa ta ci mutuncin Hafsa a gaban mutane. Tamkar wanda aka zare wa lakar jiki, haka ya ja jikinsa ya buɗe motar, ya shiga ya zauna, ya kifa kansa a kan sitiyarin motar, ya rasa abin da yake masa daɗi, ya rasa ta ina zai ɓullowa wannan lamarin, gab ɗaya komai ya cakuɗe masa, ya shafe a ƙalla mintuna Ashirin a cikin motar ya kasa ko da kunna motar, balle ya ja. Ganin bashi da wata mafita a cikin wannan tsayuwar da yake yi, ya sanya ya kunna motar, ya fara tuƙi, sai dai jin jikinsa yake tamkar an zare masa dukkan wata laka dake jikinsa, da wani dishi dishi yake gani, da ƙyar yake iya jan motar, ya nufi gidansu Abdul. Shagon Abdul a rufe yake, alama Abdul ɗin baya nan, Khalil ba shi da kuzarin da zai kira Abdul, dan haka ya cigaba da zama a cikin motar ta sa yana kuma tuno maganganun da Hafsa tayi masa. Bai san iya adadin lokacin da ya kwashe a zaune a cikin motar nan ba, knocking ɗin glass ɗin motar da aka yi ne ya sanya shi dawowa play, har ya sauke glashin motar, Abdul ne a tsaye yana kallon Khalil "Ya aka yi baka kirani a waya ba, ka zauna a mota kana bacci?" Khalil baice komai ba, ya buɗe motar ya fito, Abdul ya wuce ya buɗe ƙofar shagon, Khalil ya shiga ya nemi wuri ya kwanta, ba tare da ya ce wa Abdul komai ba. Abdul ma bai takura shi sai yaji meke damunsa ba, ya ƙyaleshi. Fadila kuwa sai yamma suka gama shirin komai, suka zauna yin kwalliya, har su Hajiya Turai sun zo, Daddy maa da wuri ya dawo gida, sai dai Fadila ba taji daɗin rashin Khalil a wurin ba, ta yank Cake suka yi hotuna, zuwa magariba kowa ya watse. Hafsa kuwa bayan shigarta gida wani sabon kukan ta zauna tana cigaba da yi, Sai da Mama ta ga kukan ya yi yawa sannan ta sameta a ɗaki ta ce "Hafsa, wannan kukan da kike fa babu in da zai kai ki, kiyi haƙuri, kiyi Addu'a Allah ya zaɓa miki mafi alkhairi, ko kin auri Khalil tunda mahaifiyarsa ba ta ƙaunarki, ba zakiji daɗin zama da shi ba, kiyi haƙuri Allah ya musanya miki da mafi alkhairi" Hafsa ba ta cewa Mama komai ba, dan ita kaɗai ta san me take ji a ranta, a kan rabuwarta da Khalil, ta sani rabuwarsu ba yana nufin rayuwarta ta zo ƙarshe bane, amma samun wanda zai maye mata gurbin Khalil abunne mai wahala, ita ta riga ta gama yadda ba ta da sa'a a rayuwata, duk wani abin alkhairi da zai tunkarota, sai ya lalace. Can Mama ta nisa ta ce "Yanzu wace sana'ar kike ganin zamu koma yi? Bana son ki cigaba da fitar nan tunda na fauskanci babu alkhairi a hakan, kowa ya tashi sai ya sameki a can ya yi miki wulaƙanci a cikin mutane, yanzu dai bari zuwa jibi in Allah ya kaimu idan kin yi tunanin wani abun da zamu yi sai ki mini magana,tun da muna da Abinci. Jinjina kai kawai Hafsa tayi, ba tare da ta iya cewa komai ba. Har Khalil ya gama zamansa a ɗakin Abdul, bai cewa Abdul ɗin komai ba, sai bayan sallar magariba, sannan ya yi wa Abdul Sallama ya tafi gida. Ko da ya fito zai tafi gida, zuciyarsa ji yake kamar ya sake komawa gidansu Hafsaz ko zata sakko ta saurareshi, amma yadda yaga hawayen nan a idonta cikin damuwa ya ƙara tabattar masa da gaske take, ta bar shi. Haka ya shiga motarsa ya tafi gida. Ita kanta Fadila rashin walwalar Khalil ya fara damunta, kwata kwata ya daina shigowa cikin gidan, ko ba komai ko su haɗu suyi faɗa yana ɗebe mata kewa. Ta kalli Mummy da ke zaune tana cin cake, su Hajara kuma na gyara falon,. "Mummy, wai dan Allah haka za'a zubawa Yaya Khalil ido? Kinga fa ya daina shigowa cikin gidan nan sam, ko ma bashi da lafiya ne?" Mummy ta ce "Lafiyarsa ƙalau, duk a kan na raba shi da waccan yarinyar ne, yake fushi da wannan iskancin, na ɗau matakin ƙarshe da nake ganin ya dace, in shi ba zai rabu da ita ba, su dolensu su rabu da shi, idan har suna da zuciya" "Amma Mummy wane matakin kika ɗauka" Mummy ta yi murmushi ta ce "Ke ina ruwanki, ba dai nace miki na ɗau mataki ba" Fadila na shirin yi magana sai ga Khalil ya shigo falon, gaba ɗaya ya rame duk yayi wani iri. Fadila ta ce "Yauwa brother, na je ɗakinka babu adadi ina nemanka, yau birthday na duk an yi hotuna babu kai". Be kula Fadila ba ya ƙarasa in da Mummy ta ke, ya kalleta ya ce "Mummy, ban taɓa zaton zaki mini abin da kika yi ba, dan kawai na ce ina son 'yar talaka ba, yanzu Mummy meye laifin yarinyar da za'a wulaƙanta ta haka? Me tayi ita?" "Au Yanz zuwa kayi ka titsiyeni ko ka tuhumeni a kan wannan shegiyar yarinyar? To ka kyauta daidia nake da kai, zan ga ni da kai waye ya haifi wani" Kamar Khalil zai fashe da kuka ya ce "Mummy ba haka bane, Mummy da girmanki da mutuncinki yarinya ce fa ƙarama Hafsa, 'yar cikinki kuma sirikarki" Miƙewa Mummy ta yi ta ce "Zan tsinke ka da mari, ni zaka zo ka tsayaa kaina kana gaya mini maganar banza, ka kiyayeni Khalil, wallahi ka cigaba da bibiyar yarinyar nan, zan maka abin da tunaninka bai taɓa kawo wa zan maka ba, kuma idan ta cigaba da bibiyarka, wallahi saina ƙasƙanta ta na tozartata fiye da abin da nayi mata yanzu, idan yaso ka nemi wata uwar ka canza ni" Khalil ya girgiza kai ya ce "A'a Mummy, ke uwata ce, ba yadda za ayi in iya canzaki, ko in fifita wata a kanki, Mummy ina nuna miki illar abin da kika aikata ne, ita ma 'ya ce, uwa ce ta haifeta ya tata uwar zata ji da wannan abin da kika yi mata? Haba Mummy" "Lallai Khalil, wuyanka ya riƙa ya isa yanka, ka nuna mini ka kawo ƙarfi, gara da na farga na miƙe tsaye, kan kwaso mini wadda zata dinga juyaka, idan kaga na bari kayi aure, to matar da na zaɓa maka ce, tun da naga baka da hankali" Idonsa fal hawaye ya ce " Shikenan Mummy, kin yi nasara kin rabani da Hafsa, shikenan Mummy" "Kar ma ta rabu da kai, da ta cigaba da bibiyarka dai, da taga ƙaryar talauci, sakarai kawai" Ta wuce fuuuuuu ya bar falon. Khalil ya zauna ya dafe kansa, yana girgiza kan yana jin yadda zuciyarsa ke tafasa. Fadila ta zauna a kusa da Khalil ta ce "Brother, wai me Mummyn tayi maka ne?" Ya ɗago idanuna da suka yi jawurr, jijiyoyin kansa duk suka mimmiƙe suka kumbura, ya kalli Fadila ya ce "Yanzu fisabilillahi Fadila ya dace ace Mummy taje da ƙawayenta, sun ci mutuncin yarinyar mutane a gaban al'umma, suka watsar mata da kaya a cikin ƙasa, ita meye laifinta?" Fadila ta ɗan yi shiru sannan ta ce "Haka ne, gaskiya Mummy bata kyauta ba, amma kaima Yaya Khalil meye kaika, duk matan duniya ka nacewa wata mai awara, ai koma menene kaine ka janyo mata, tunda Mummy ta nuna bata so ai saika haƙura" Kalaman Fadila ƙara masa ɓacin rai suke, dan haka ya tashi, ya bar falon zuciyarsa babu daɗi. Sosai Amina taji tausayin Khalil ya kamata, mussaman ita wadda ake ce anje an ci mutuncin ta a gaban mutane. tana mamakin baƙar zuciya irin ta Hajiya Zainab, babu tausayi ko Allah a ranta, gani take kamar ita ta yiwa kanta arziki ba Allah ne ya bata ba. Fadila ɗan taɓe baki tayi, ta tashi ta bar falon, duk da Khalil ɗin ya bata tausayi, amma a ganinta matakin da Mummy ta ɗauka yayi daidai, dan Khalil yana da taurin kai wasu lokutan. Amina wasu lokutan mantawa ma take da wayar da Daddy ya bata, saboda bata son ta ɗauke mata hankali da ga kan karatunta sam. Da Asubar fari Khalil ya shirya kayansa, ya ɗauki motarsa ba tare da ya yiwa kowa sallama ba, ya fice daga gidan. Abdul yana zaune yana azkar, bayan idara da sallar asba, yana jiran gari yayi haske yayi wanka, ya ga wayar Khalil. Yasa hannu ya ɗaga wayar yana faɗin "Lafiya kake mini wannan kiran haka da sassafe?" "Ina ƙofar gidan ku, airport nake son ka kaini, jirgin Bakwai da rabi zanbi in koma Abuja" Mamakine ya kama Abdul, dan ba suyi wannan zancen da Khalil ba jiya, ya miƙe, ya saka hula ya ɗau wayarsa ya fita, aikuwa yaga motar Khalil. Ya rufe shagon nasa, sannan ya nufi wurin da motar Khalil ɗin take. Ya buɗe motar ya shiga, ya kalli Yadda fuskar Khalil duk ta kumbura, ga idanunsa mu duk sun kumbura sun yi ja, kamar wanda bai yi bacci ba. "Wai Khalil meke damunka ne? Meyasa zaka koma yau bayan kace mini sai next week zaka koma?" "Abdul, Hafsa ta rabu dani, ba zata aureni ba" ya faɗa tamkar zai fashe da kuka. Abdul ya ce "Subhanallah, saboda me?" Cikin damuwa Khalil ya ce "Abdul, could you imagine Mummy da kanta iya da ƙawayenta wai suka je suka yiwa Hafsa warning a kaina, suka watsar da kayan sana'arta a gaban mutane? Abdul waye ni ɗin ne? Me aka yi aka yi ni? Yanzu ya dace abin da Mummy tayi, girmanta ne yin hakan?" Abdul ya ce "A'a Khalil, yi haƙuri, Mummy uwa ce kar ɓacin rai ya sanya ka faɗi wata maganar a kanta" "Haba Abdul, ka duba lamarin nan dan Allah, yanzu dama da yaya na samu kan yarinyar nan, maimakon idan ma rabuwar ce, a bari mu rabu ta daɗin rai, in mata bayani mu rabu cikin mutunci, amma anje an ci mutuncinta, meye laifinta? Har Abada ba zata taɓa ganin mutuncin Mummy ba, na rasa dalilin da yasa Mummy ke biyewa wannan ƙawayen nata suna zigata tana abubuwan da basu dace ba, idan nayi yinƙurin gayamata Gaskiya, ta ƙare mini zagi ta nuna mini haryanzu bani da hankali, amma ka duba wannan lamari meye na Hafsa a ciki?" "Haka ne Khalil, bai kamata Mummy ta aikata hakan ba, amma hakan ba shi yake nufin ka faɗi abin da kake so a kanta ba, kayi haƙuri ka cigaba da yi mata addu'ar Allah ya ganar ita. Ita kuma Hafsa idan rabonka ce, Allah ya daidaita lamarin, ya tabbatar muku da alkhairi, idan kuma ba alkhairi bace, Allah ya haɗa kowa da rabonsa. Khalil ya sauke wata ajiyar zuciya ya ce "Baka san wani abu ba, cewa fa tayi wai bani ba zaɓar macen da nake so na aura, ita zata zaɓa mini, kuma wallahi na san duk wannan matan ne suka kitsa mata ta hau ta zauna, Mummy tana valueing maganar ƙawayenta fiye da kima" Abdul ya ce "Kayi haƙuri abokina, ka cigaba da yi mata Addu'a" Khalil ya ce "Shikenan, muje airport, kai sai ka dawo da motar, idan ka samu lokaci ka mayar musu da motar can gida" "To shikenan, Allah ya tsare" Khalil ya ja motar suka tafi. Kamar kullum, yau ma Amina ta kammala shirinta na makaranta, cikin gogaggun uniform ɗinta, ta saɓa jakarta a bayanta, ta fita wurin Baba, ta tsaya suka gaisa da Baba, Baba ya ce "Uwata, kuɗin makarantar da nake baki ba sa isarki ne?" Cikin rashin fahimta Amina ta ce "A'a Baba me ka gani?" "Alhaji Ahmad ne ya bani kuɗi, kusan dubu goma, wai idan zaki tafi makaranta, in dinga baki isasshen kuɗi, saboda ba kya tafiya da Abinci, yunwa na damunki a makaranta" Amina ta mariraice Fuska ta ce "Wallahi Baba ban ce masa wani abu aba, ranar da na wuni a makaranta ne a wurin lesson, yazo ya ɗaukeni na ce ba zan sake zuwa lesson ba, mun wuni a makaranta ina jin yunwa, amma wallahi Baba ni bance masa komai ba" Baba yayi ajiyar zuciya ya ce "To Uwata, ba zan fasa yi miki nasiha ba, ki iya kankina duk in da kika tsinci rayuwa, kar ki sakankance da mutumin nan ki jamana wata matsala a gidan nan" Amina ta ce "To Baba in sha Allah" "To ni yanzu wannan kuɗin zan baki dubu uku, idan sun ƙare sai ki kuma yi mini magana in baki wasu, amma bance kiyi ta kashe-kashen banza ba" "A'a Baba, dubu biyu ta isheni duka watan nan, ka sayawa Inno kayan shayi a aika mata, ita ma ta dinga cin mai daɗi kamar yadda muke ci a nan" Baba yayi murmushi ya ce "Uwata kenan, ke dai ki karɓa, ni na san abin da zan yi" Amina ta miƙe daga tsugunon da tayi, ta ce "Baba, bari in tafi, bani yadda ka saba bani, idan na dawo sai muyi maganar kar na makara" Baba ya saka hannu a aljihunsa, ya cirowa Amina naira ɗari uku ya bata, ta saka hannu biyu ta karɓa, tayi masa sallama ta fita. Tana ta sauri ta ƙarasa titi, ana ta wucewa da yaran masu kuɗi a cikin motoci zuwa makaranta, ba tsammani taji an kira sunanta. Ɗan tsawa tayi ta waiwaya, Bilal ta gani cikin suit baƙaƙe. Ya ƙaraso in da take yana faɗin "Amina, makaranta zaki tafi ne?" Amina ta ce "Eh, ina kwana?" "Lafiya ƙalau Alhamdilillah, ɗan jirani in shiga gida in ɗauko mota, in kai ki mana" Amina ta ce "A'a sauri nake, ka bari na gode" "Haba Amina, dan Allah ki tsaya in kai ki" "A'a ka bari wallahi na gode" Bilal ya ce "Gaskiya ban ji daɗi ba, to muje in rakaki titi" "A'a karka damu dan Allah, zan ƙarasa" Bilal bai saurreta ba, ya cigaba da binta, suna tafiya tare, gaba ɗaya hankalin Amina baya kan Bilal, sai surutu yake mata, ba tare da tana amsa masa ba. Sun ƙarasa titi tana jiran mota, ba tsammani sai ga motar Daddy ta zo wucewa, lokacin da ta fito daga gida ko tashi baiyi ba, amma har ya shirya ya fito, sai da ya zo daidai in da suke, sanan ya ɗan ja motar a hankali, yayi musu horn, dan Amina ta san ya ganta, sannan ya ja motar da sauri ya bar wurin. Sai da cikin Amina yayi ƙara, ba ta san hukuncin da Daddy zai yi mata ba, saboda yayi mata gargadi a kan Bilal. Sai da Bilal ya tabattar da ta hau mota, ya biya kuɗin, sannan ya juya ya koma. Yau Fadila ita da kanta taje wurin zaman Yazid, sai kallonta yake yana murmushi, ta miƙa masa wata 'yar ƙaramar jaka ta ce "Gashi nan, kayan birthday ne, na kawo maka" "Ohh ni Yazid, har da ni a cikin kayan, to Allah ya sanya abin da kika bani ɗin na iya ci" "Idan ma baka iya ba saika koya" Ya ce "To shikenan, zauna muyi wata Magana" Fadila ta nemi wuri ta zauna, ya ɗan dubeta ya ce "Da kika ƙara shekara a duniya, kuma kika kama hanyar komawa ga ubangijinki, wace Addu'ar ki ka yi?" Fadila ta ɗan taɓe baki ta ce "Wace Addu'ar kuma?" "Au ke baki Addu'a ba, sai iyayi" "Ba wani iyayi, family and friends sun yi wishing ɗina, that's all" Yazid ya ce "No, yakamata ki roƙi Allah gafara, ki yiwa kanki kyakkyawan fata a cikin abin da ya rage miki a rayuwarki, kiyi Addu'a a kan karatunki, da kuma fatan Allah ya kawo miki abokin rayuwa na gari, wanda yake sonki" Ta ɗan kalleshi ta ce "Waye abokin rayuwar?" "Miji mana, na gari mai sonki saboda Allah, ko da kuwa Kankiya ne" Haɗe rai ta yi, ta ce "Wai sau nawa zan gaya maka, kar ka sake haɗani da mutumin nan, bana son irin haka na gaya maka" Yazid ya ce "Ikon Allah, to ke haka ake yi? Ba Addu'a nayi miki ba, ai idan kana neman azaɓin Allah, barwa Allah komak ka ke, baka zaɓe-zaɓe" "Over my death body in auri wanan mutumin mara tunani" Da sauri Yazid ya ce "Subhanallah, Ukty malaminki ne fa" Ai tamkar da kankiyan take magana, ta ce "And so what? Ko na rasa mijin Aure ni ba ajinsa ba ce, yana rayuwa kamar wani bagidaje da bai san meya ke yi ba, a haka zan so shin?" Jikin Yazid yayi sanyi, Kankiya ma kenan, da ya na ɗaukar wanka, ina ga shi, da kayan sawarsa ma ba su fi a ƙirgasu ba. Har tayi shiru ta cigaba da mita, "Allah na tuba, ko a ƙafata a ka ɗaura mini shi ba sai na kwance shi na yar ba, kai mini wata Addu'ar banda Wannan, ni waima waye ya ce maka zan yi Aure ne? Da in yi Aure da kar in yi duk normal ne" Yazid yayi murmushi ya ce "A hakan da kike?" Ta ɗan kalleshi da mamaki ta ce "Kamar yaya a hakan da nake?" Ɗan taune lips ɗinsa na ƙasa ya yi ya ce "Bar zancen, amma kina buƙatar abokin rayuwa na gari, ai kin kai girman da kin zama mutum 'yar yarinya" "Haka nace maka?" "Ko baki faɗa ba yanayinki ya nuna Besty, anyway mu bar wannan maganar, Allah ya baki miji nagari, ko da Yazid ne" Da wani irin sauri ta kalli Yazid, tare da yamutsa fuska kamar wadda ya gayawa saƙon mutuwa ta ce "What? Wane Yazid ɗin?" Tayi maganar babu alamar wasa a tare da ita. "Kai bari kaji in gaya maka, tun wuri ka mayar da hankalinka, am still the Fadila you know, kawai naga rashin dacewar wulaƙancin da nake maka ne, ya sanya nake kulaka, kan ka yiwa kanka fatan zama mijina, Yakamata ka san waceceni, ba sa'arka ba ce ni, we are just friends, tun da abin da kake tunani kenan, friendship ɗin ma is over now, Fadila ba matar ire-iren mutane kamar baka ce". Yazid yayi shiru, bai taɓa zaton Fadila zata yi masa haka, ta bishi da wanan kausasan kalaman ba, tun ma bai kai ga furta cewar yana sonta ba, matuƙa kalamanta sun tsaya masa a zuciyarsa. Ita kuwa tana gama yanka masa wannan maganganun, ta tashi ta bar wurin da yake. Ya bita da idanuwa, yana jin zafi a ransa. Ko da yake maganganun Fadila suna bisa turba, ita ba sa'ar aurensa ba ce, matsayinsa da nata ba ɗaya bane ba, amma idan aka duba matakan addini, yana da duk wani qualities da za a aureshi domin su. Shiru yayi yana jin yadda duniyar ta yi masa zafi, yana ji a ransa dama bai yi mata wannan maganar ba, da wataƙila sun cigaba da gaisawa. Gaba ɗaya Ajin ta bari, ta tafi department ɗin su Yusra, tana zuwa ta tarar da malami a ajinsu Yusra, dan haka ta jira sai da suka kammala lectures, malamin ya fita, sannan ita kuma ta shiga ajin. Yusra ta kalli Fadila da ɗan mamaki a fuskarta ta ce "Girl ya dai? Na ganki rai a ɓace". Fadila ta zauna tana ɗan hura hanci. "Ke wai meye ne?" Yusra ta faɗa tana sake tattara hankalinta a kan Fadila. "Kin san wani abin takaici da raini?" "A'a sai kin faɗa" "Yazid fa sona yake" ta faɗa cike da takaici. "Au da da nake gaya miki baki yadda ba? Me yayi miki ne?" "Wai Allah ya bani miji nagari ko shine" Yusra ta kwashe da dariya ta ce "Gaskiya Fadila baki da wayo, ke ce baki da tunani wasu lokutan, idan ba sonki yake ba mai zai saka yayi ta bibiyarki har ya dinga taimaka miki, yayi ta miki abubuwan da zai burgeki" Fadila ta ɗan yi shiru ta ce "Lalli bani da hankali, kawai na ɗauki alaƙarmu ne a friendship, ni mai yasa mazan nan suka rainani, amma Yazid tsaurin idonsa ya kai in da ya kai, ina shi ina mace kamar ni?" "Kar ki cika baki malama, tun da ya fara bijirowa a mafarkanki da kika gaya mini, akwai alamar cigaba da tarayyarku ka iya sanyawa ki fara son shi, saboda gayen yana da kirki sosai" "Ashe kuwa da Mummy ta kwaɗani ta cinye, kin san a tashin hankalin da Yaya Khalil yake dan ya ce yana son mai awara, hmm naga wautar Yaya Khalil" Yusra ta ce "Ikon Allah, shi kuwa Yaya Khalil meya yi masa zafi?" "Oho masa, duk yadda suke da Mummy,tayi masa fata fata, ko cikin gida ba ya iya shigowa, ba kiga ko jiya bai shigo wurin birthday na ba. Ina gama alhakinki ne" "A'a kar ki ce haka Fadila, Allah ya zaɓa mana mafi alkhairi" "Amin dai, da nazo na gaya miki maganar nan har naji sanyi, ni wallahi tausayi yake bani ma, Kankiya ya sako shi a gaba da yawa a kaina, ni kuma bana son a lalata masa karatunsa saboda ni, amma shi ma Kankiya tara sh nake, idan ya kaini bango sai ya rasa aikinsa wallahi" "A'a Fadila ki bi a hankali dai" "Ai a hankalin nake bi, ke kin san da ba a hankalin nake bi ba, Kankiyan shi da koyarwa a jami'ar nan har Abada, banda ke babu wanda ya san abin da ke tsakanina da shi, sai Yazid, shi kuma wannan ko ban gaya masa abu ba, ganowa yake kamar aljani" Yusra ta ce "Do you know one Funny thing? Kin iya faɗar sunansa wallahi, har wata madda kike Yaziiiid" Tsaki Fadila tayi ta ce "Ke bana son wulaƙanci, bana son duk wani abu zai sake haɗani da shi, kowa yayi rayuwarsa kawai". Yusra ta ce "Shikenan, tunda kin huce yanzu a kan yadda kika zo mini" "Bari kawai ya ƙular da ni ne, da wani shegen takalminsa irin na danƙon nan, sai uban saka jallabiya kamar limamin harami" Yusra ta kwashe da dariya ta ce A'a kar ki zafafa dai" Fadila ta kai kusan twenty minutes tare da Yusra, sannan ta koma department ɗin su. Da idanun Yazid ta fara cin karo, kallo ɗaya zaka yi masa, ka gane jikinsa yayu sanyi, guntun tsaki tayi ta wuce wurin zamanta. Ƙarfe biyu daidai, aka tashi daga makaranta, Amina tayi sallama da 'yan ajinsu, ta fito gate. Wata uwar mota ta gani a bakin gate ɗin makarantar ta su a tsaye, da wasu 'yan sanda biyu a jikin motar. Bata kawo tunanin komai a ranta ba, ta cigaba da tafiya. Ji tayi kamar ana binta a baya, ta waiwaya taga 'yan Sandan sun biyota. Gabanta ne ya faɗi , tana sake dubwa taga wa suke bi. Ɗaya ɗan sandan ya ce "Amina ko?" Idanuwa waje Amina take binsu da kallo, tana tunanin meye haɗinta da 'yan sanda suka biyota makaranta. "You Are under Arrest!!!" AYSHERCOOL 08081012143GABA DA GABANTA             BY AISHA ADAM AYSHERCOOL PAGE 39 Ƙara waro manyan idanuwanta ta yi ta ce "Arrest for what ni Amina?" Tayi maganar bakinta na rawa. "Arrest by Alhaji Ahmad Dutse order" ɗaya ɗan sandan ya faɗa yana murmushi. Sai kuma tayi saroro tana binsu da kallo, dan ta kasa fahimtar kan lamarin gaba ɗaya. "Kinga Kwantar da hankalinki, baki gane ni ba ne?" Yayi maganar yana nuna kansa "Ni ban taɓa ganinka ba balle in gane ka" ta faɗa hawaye na taruwa a idonta. "Ranar da kuka zo gidan Alhaji Ahmad ke da shi, muna aiki a gate ɗin gidan, ai ni na ganeki shi ne ya ce mu zo mu ɗaukoki, ya aikemu ne ya ce mu biyo mu ɗauke ki" "Taɓ aikuwa ba zan biku ba, ku 'yan sanda abin yarda ne? Haka kawai ku sani a motar 'yan sanda kamar wata ɓarauniya, naga ai da kansa yake zuwa ya ɗaukeni wataran" Ɗan sandan ya kalli motar da suka zo da ita, helux ce me baƙin glass, ya sake dubanta ya ce "Lambar motar ta aiki ce, ba tamu ce ta 'yan sanda ba, ta Alhaji Ahmad ce, kuma ba sace ki za muyi ba" Amina dai cike da tsoro ta ce "Kunga, ku gaya masa mu haɗu a gida, amma ni ba zan hau motar 'yan sanda ba, kalli jikinku da kaki, kawai idan na shiga ku wuce dani prison" Ɗaya ɗan sandan dai mamakin ƙarfin hali, da kuma taurin kan Amina yake, ɗayan kuma sai lallaɓata yake. "Kinga bari in kira miki shi a waya" "Aiko shi zaka kira nan wurin ba zan hau mota da 'yan sanda ba" ta faɗa tana duba hanyar da zata bi ta gudu. Wayarsa ya ɗan danna, Sannan ya saka a kunnensa. "Yauwa barka dai yallaɓai, gamu a ƙofar makarantar, mun zo ɗaukanta, amma ta ce ba zata hau mota ɗaya da mu ba, infact ma bata yadda kai ka turo mu ba" Daddy ya ce "Na san a rina, bata wayar" Ɗan sandan ya kalleta ya ce "To kinga, ya ce a baki wayar kuyi magana" A ɗan tsorace ta kalleshi ta ce "To idan na karɓa nayi maganar, zaku barni na tafi?" "Eh, sai abin da ya ce dai" Kamar wadda ake miƙawa kashi, haka ta karɓi wayar, tana Addu'ar Allah ya sa ba tana Magana wani abin zai sameta ba, ko matsafa ne. "He..h....hello Daddy" "Mmwummm" shi ne abin da ya faɗa daga cikin wayar. Kamar mai tsoron magana ta ce "Daddy kana jina?" "Mmm" "Daddy dan Allah kayi magana, wasu ne wai zasu tafi da ni in jika" "Baki iya sallama ba sai Hello?" Ya faɗa yana gyara kwanciyarsa a kan kujerar 3seater. "Yi haƙuri a tsorace nake ne, 'yan sanda ne fa suka zo zasu tafi da ni" "Eh laifi kika yi, na turo su su kamo mini ke" Zaro ido tayi kamar tana gabansa ta ce "Laifi ni ɗin, me nayi da zaka haɗani da police?" "Sai sun kawoki zaki ji laifin da ki kayi, idan kuma kika cigaba da yi musu gardama, za su saka miki handcuff su sako mini ke a motar su kawoki". "Na shigesu ni Amina, 'yan fashi fa ake sawa wannan sarƙar, dan Allah kayi haƙuri" tayi maganar cikin shagwaɓa tana marairaicewa. "Oya, ban da gardama ki biyosu ni na turo su" Jiki a sanyaye ta ce "To" ta miƙawa ɗan sandan waya, ta bisu, suka buɗe mata mota, ta shiga suka ja suka tafi. Gaba ɗaya zatonta gidan da suke zasu tafi, amma taga sun sauya hanya. "Bayin Allah ya haka?" Ta faɗa tana waige waige. "Meyafaru?" Cewar ɗan sandan da ya haɗata da Daddy a waya. "Naga mun tafi wani wurin daban, ba Tudun yola zamu ba?" "Ba nan zamu ba, gidan da kuka je tare ya ce a kaiki" "Na shiga uku ni Amina" ta faɗa a hankali, tare da sallama cewar wani aikin zai kuma sakata yauma, gashi ta gaji matuƙa yau ɗin nan. Tana ta zancen zuci, har suka isa gidan, parking suka yi a cikin gidan, wurin ajiye motoci, Amina yau har da motocin da bata gani ba wacan karon ta gani yau, har mamakin yadda Daddy yake yi da motoci take. Suka buɗe mata ta fito, ta ɗaga kai ta kalli gidan sannan ta ce "To yana ina Daddyn?". "Ki shiga, yana ciki" "Ciki ina kenan?" Ɗan sandan ya fara ƙufula da surutunta da tambayoyi, amma ya daure ya ce "Hanyar da kuka shiga wancan karon, ita zaki bi. Cike da fargaba da salati, Amina ta nufi hanyar da suka bi tare suka shiga gidan a wancan karon. Babu kowa a makeken falon, sai dai ko ina fes da shi. Ko yana ina oho? Ta tambayi kanta da bawa kanta amsa. Wata siriryar hanya ta bi, zuwa falon da ya saka ta jera Abinci ranar da yayi baƙi. Ta tura ƙofar ta shiga, ya ɗago idonsa ya kalleta a cikin uniform ɗinta, riga da skirt sun mata kyau sosai, sai uwar jakarta ta goyo. Shi kuma yana sanye da yadi mai taro taro maroon, kansa babu hula, yana shan ruwa a kofi. Girmansa da kwarjininsa suka cika mata ido, ta ƙarasa cikin falon, ta durƙusa ta ce "Ina wuni?" "Ban ganshi ba" ya bata amsa. Ɗagowa tayi tana mamakin irin amsar da ya bata. Ya ɗan ɗage mata gira ya ce "Yes, ban ga yini ba, ko in ce yana gidan biki ko?" Amina ta sunkuyar da kai, saboda haka kawai take jin ta takura, wannan keɓewar tasu bata dace ba. "Na saka an kamo mini ke, saboda laifin da kika yi mini". "Laifi kuma?" Tayi maganar a ɗan raunane. "Eh laifi mana, ai ke ba kya daina laifi, na fuskanci kina da taurin kai" Amina tayi shiru tare da sunkuyar da kanta ƙasa, dan ita dai bata san laifin da tayi ɗin ba. "Me nace miki game da tsaya da wani, dan tsabar rashin ji kuma a titi, zaki tafi makaranta" Sai yanzu ta tuna, da safe ya gansu tare da Bilal, ta ɗago ta ce "Daddy tsaya ka ji nayi maka bayani" "A zaune nake ai, ba wani bayani da zaki yi mini, ba kya jin Magana ne kawai, kuma zan gayawa Malam Hassan ɗin abin da kike" Ta marairaice ta ce "Ka tsaya ka ji dan Allah, wallahi shi ne ya biyoni wai sai ya rakani, ai kaga ba zan kore shi ba, wulaƙanci babu kyau" Alhaji Ahmad ya gyara zamansa ya ce "Ni meye ya hana ki nemi in rakaki?" "Ni a wa? Ni dai dan Allah kayi haƙuri, ka sa a mayar da ni gida" "Aminatu ba kya ji sam, sai na ɗau mataki a kan abin da kika yi" "Wallahi Daddy ina ji, kayi haƙuri, ni ban san ya zan masa ba, amma zan gaya masa ka ce kar ya sake shiga harkata" Kan Alhaji Ahmad yayi magana, aka kira shi a waya, ya sa hannu ya ɗaga wayar, ya kai kunnensa. Ba ta jin me ake cewa daga cikin wayar, ta dai ji yana cewa "Jiki Alhamdilillah, ya yi sauƙi jinin ma ya sauka, shi ma sugarn nawa ya sauka sosai" Amina dai ta sake gyara zamanta, tana ɗan satar kallon Alhaji Ahmad. "Eh, da ina tunanin zan ɗan je wata ƙasar in ɗan huta, amma a yanzu na samu wata Cartoon me Sani nishaɗi" Dariya yake sosai a wayar, sannan yayi sallama da wanda suke wayar, ya ajiye, ya kalli Amina a ya ce "Oya, a ɗan sama mini abin da zan ci, kan ki tafi" Ɓata fuska Amina ta yi, ta ce "Dan Allah Daddy..." Sai kuma tayi shiru. "Ina jinki" ya faɗa yana danna wayarsa. "Kaga Baba bai san ina nan ba, kuma ni Hajara tabi ta saka mini ido, gani take wani abu ne a tsakanina da kai" "Wani abu kamar me?" "Ranar fa da ka ce in kai maka shayi na daɗe, bina ta dinga yi tana tambayata wai ya aka yi na daɗe, da ranar da ka ce ba zan tayata aiki ba, duk ta bi ta saka mini ido, ita ma ka dinga sakata aiki kar ta zata da wani abu a tsakanin mu" Dariya ta ga yana yi, ya ce "Akwai wani abu a tsakaninmu mana, tsoron me kike ji?" "Ni meye a tsakaninmu?" Ya ɗan yi murmushi ya ce "Kinga, yanzu dai tashi ki je kitchen, ki sama mini wani abun in ci" Ɗan tsuke fuska tayi, tana jin Daddy ya takurata. Daddy ya ɗan zuba mata ido ya ce "Ko in haƙura?" "A'a zan yi" ta faɗa a sanyaye. "Yauwa Cartoon ɗin Daddy, a taimakawa Daddy" "Cartoon kuma?" Ta faɗa tana ɗan tura baki. "Eh mana, tashi da sauri, dan ki kammala da wuri mu tafi gida" Amina ta ajiye jakarta, ta nufi kitchen,  sai da ta ɗan tsaya tana tunanin mai zata girka, wanda zai iya ci saboda ciwonsa. Ta cire ƙaramin hijjabinta ta rataye ɓalle rigar saman ta rataye, ya zama daga ita sai rigar uniform ta ciki, da skirt ɗinta, sai kuma hular hijjabin, kana ganin gashinta da ta ɗaure da ribbon. A nutse ta fara gudanar da aikinta, tamkar tana kitchen ɗin gidanta. Gaba ɗaya Yazid bai fahimci lectures ɗin yau ba, saboda yana cikin damuwa, yayi mamakin abin da Fadila ta gaya masa, bai taɓa tunanin jin wannan maganganun daga bakinta ba. 'banda abinka kai ma Yazid me ya aikeka, ina kai ina ina wannan yarinyar, suturar da take sawa kawai, ta isa ta nuna maka ruwa ba sa'an kwando bane' wata zuciyar ta tunasar da shi. Haka nan jiki babu ƙwari, ya ja jiki yaje yayi sallar azahar, daga nan ya wuce gida. Khalil kuwa tun da Allah ya sanya ya sauka a garin Abuja ƙarfe tara na safe, ya wuce gidan da yake zaune a can garin Abujan, ba im da ya kuma fita ya je, sala ce kawai take fito da shi daga gidan, ko Abinci ya kasa yin order ya ci, loka lokaci ya kan buɗe saƙonnin Hafsa da take turo masa a baya, da hotunanta ya zuba musu ido. Maganganunta ha dinga tunawa, da take jadadda masa na ya riƙeta da amana. Har ga Allah ya ci burin auren Hafsa ya zauna da iga saboda Allah, ya sama mata farinciki, amma Mummy ta ɓata komai, babu Wanda za aayi masa abin da Mummy ta yiwa su Hafsa ya iya haƙuri, sai dai idan ba shi da zuciya. Duk yadda Khalil ya so ya yi tunanin mafita kasawa ya yi, ƙarshe ma kansa ne ya fara ciwo, amma ya kasa yadda zai iya cigaba da rayuwa ba tare da yana cigaba da magana da Hafsa ba, ya ɗauki wayoyinsa duka ya kashe su, ya ajiye. Amina ta gama girki, sai aikin yanka salak da take yi, tana ta decoration ɗinsa a tray. Ji tayi kamar motsi a bayanta, ta juyo gaba ɗaya dan ganin meke motsi a bayanta, sai taga Daddy ne ke shigowa. Tsananin kunya ce ta kama Amina, saboda jikinta babu hijjabi, sai rigarta ta uniform 'yar ciki, kuma rigar ta kama jikinta sosai. Da sauri ta kai hannu tana kare ƙirjinta, ta juya da sauri, sai kuma ta tuna shi kansa skirt ɗin a matse yake, kuma tayi stock in ɗin rigar. Murmushi Daddy ya yi, ya nufi fridge ɗin kitchen ɗin, still Amina ta kasa sakewa, sai ɓoye ɓoye take. Muryar Daddy ta jiyo yana cewa "Me kike ɓoyewa ne? Ai ni ba ke nake kallo ba, na gaji da jirane na zo na ɗauki fruit ne, ina jin yunwa sosai". Kunya ce ta sake kama Amina, har ta kasa cigaba da abin da take yi, dan bata taɓa zaton jin hakan daga bakin Daddy ba. Ai bata gama tunanin ba ta ji shi a tsaye a bayanta, ji tayi tamkar ƙasa ta tsage ga shige dan jinta take a wani yanayi da ta kasa tantance wane irin yanayi ne haka. Gaba ɗaya ƙamshin turarensa ya cika mata hanci, idan tayi ƙwaƙwƙwaran motsi babu abin da zai hana jikinta ya haɗu da nashi. Miƙa hanunsa yayi, ya ɗauko wuƙa ɗaya a cikin jerin set ɗin wuƙaƙen, dake gefen Amina. "Calm down, ba taɓa ki zan yi ba, wuƙa zan ɗauka" ya faɗa a kunnenta a hankali. Ƙiri-ƙiri Amina ta kasa cigaba da aikin, saboda yadda Daddy ya hanata motsi. Ringing ɗin wayarsa ce ta cika kitchen ɗin, a tunanin Amina zai matsa ne, amma ga mamakinta sai taga bai matsa ba, ya ɗaga wayar ya sanya a kunnensa. "Hello Madam" ya faɗa yana kallon gashin Amina. "Kayi nisa ne" kasancewar Yana kusa da Amina, tana iya jin abin da ake cewa a wayar, jin muryar Hajiya Zainab a wayar ne ya sanya hantar cikin Amina kaɗawa. Daddy ya ce "Ya aka yi?" "Eh zan fita ne, idan ka dawo akwai Abinci a dining" Ya ɗan shafi gemunsa ya ce "Ba za'a jira in dawo ba?" "A'a sauri nake, ban san lokacin da zaka dawo ba" Atishawa ce ta ƙwacewa Amina, kan Daddy ya katse wayar, tana ƙarewa kuma ta ce "Alhamdilillah" sai kuma ta ɗan zaro ido, tuna waya Alhaji Ahmad ya ke. "Kai da waye ne naji kamar muryar mace" Daddy ya koma gefen Amina, ya ɗan kalli Amina sannan ya ce "Na je wurin Alhaji Sambo ne, ma'aikatansa ne" Hajiya Zainab ta ce "But it seems that you are so close to the lady that sneeze" "And who told you she is Lady? Sakatariyarsa ce ta shigo Office ɗin" "Take care" ta faɗa cikin isa ta katse wayar. Ya zubawa Amina ido, ta ɗan ɗago ta kalleshi, ta mayar da kanta ƙasa. "Kin sani ƙarya, Shi ne kika ƙaƙalo atishawa ki ka yi, dan ta san muna tare ko?" Amina ta ce "Ni ba ƙaƙalowa nayi ba, zuwa tayi" "Yanzu idan nace miki ƙazama ki ji haushi, a kan Abinci na kika yi atishawa ko?" "A'a, ai na kawar da kaina, kuma kai ne ka ke wurin shiyasa ban matsa ba" "Yarinya idan asirinki ya tonu a wurinta, kina bibiyar mijinta sorrynki Amintako" Amina ta ɗan tura baki ta ce "Ni mai zan yi da mijinta? Kuma ai bani na kawo kaina ba, kai kace a ɗauko ni" "A'a yarinya faɗi gaskiya dai, kina bibiyar dattijon mijinta, ba ruwana ni" "Taɓ, ni mai zan yi da tsoho? Ni yaro zan aura" "Haba?" Daddy ya faɗa yana kai ayaba bakinsa. Ta jinjina masa Kai. "Lallai kin samu kanki, da Allah bai sa kin auri Jarmai ba, dole ki faɗi haka" Waro idanunta Amina tayi ta ce "Daddy ina ka san Jarmai?" "Ina ruwanki matar yara, ƙarasa mini aikina, yunwa nake ji sosai fa" Ya juya ya bar kitchen ɗin. Mamaki ne ya cika Amina, ya aka yi Daddy ya san Jarmai. Ta tsaya ta saka rigarta ta uniform, da hijjabinta, ta dinga kai kayan Abinci tana kaiwa gaban Daddy tana ajiyewa. "Ƙarasa ladanki mana, ki zuba mini" Amina a ɗarare dai ta zuba masa shinkafa kaɗan, ta zuba masa ganye cikin plate. "Wow, kina kula da dattijon nan sosai, God bless you dear" Ita dai Amina ta takure, tana jiran ya gama, ya bata umarnin tafiya, dan ta gaji da zaman nan. "Matso muci tare" Amina ta girgiza masa Kai "Na ƙoshi" "Aikuwa ba zaki tafi gida ba, muna nan zuwa bayan sallar isha'i" Amina ta marairaice ta ce "Dan Allah Daddy kayi haƙuri, ban san me zan gaya wa Baba ba". "To matso mu ci Abinci" "Wallahi Daddy ban taɓa cin Abinci da wani a kwano ɗaya ba, ba zan iya ba" ta faɗa a rikice. "Aminatu kenan, wasa nake miki, wannan rikicewar taki ce ke sani dariya. Amaryar Jarmai" "Dan Allah Daddy a ina ka san Jarmai" "Ina ruwanki? Juya ki daina kallona kar in ƙware" ta juya masa baya, ta daina kallonsa kamar yadda ya buƙata. Tana juya baya ya dinga mata dariya ƙasa-ƙasa, gaba ɗaya ya rikita ta lokaci guda. " 'yar Daddy" ya kirata. Ta waiwayo ta ce "Na'am" "Abinci yayi daɗi, Daddy ya gode sosai, zo ki ci naki" "Daddy na ƙoshi, gida nake so na tafi" "Sai kin ci Abinci zamu tafi, tafiyarku Abuja saura 2weeks, dan haka kan nu tafi zaki je garinku" "Me zan yi a ƙauyen? Tsoro nake ji kar ina zuwa su Baffa Lawan su riƙeni suce saina Auri Jarmai" "Idan har ina raye, ba wanda ya isa aura miki wanda ba kya so, zaki je ne dan ki musu sallama, kinga zaki tafiya mai nisa ne, zan saka Zakiru ya kai ki ki musu kwana biyu a dawo mini da ke" "To kun yi maganar da Baba ne ya yadda da tafiyar?" "Ba ruwanki da wannan, nace ki bar wannan maganar a hannuna ai" Amina tayi murmushi ta ce "To Daddy, na gode Allah ya saka maka da alkhairi" "Ameen Meenalin Daddy, nima na gode sosai kina kula dani da lafiyata, duk da ƙalubalen da kike fuskanta a gidana, ki cigaba da haƙuri watarana sai labari kin ji" "To Daddy" "Yau, ci Abinci sai mu tafi gida, zanje in yi sallar la'asar, kwanukan kuma da komai ki bari za a gyara" Ta jinjina masa kai, shi kuma ya miƙe ya bar ɗakin. Ta zuba Abinci ta ci, ta kwashe kwanukan ta mayar kitchen, dama tana fashin salla, dan haka ta zauna zaman jiran dawowar Daddy. Alhaji Ahmad na shigowa, Amina ta tashi tsaye, tana ƙoƙarin ɗaukar jakarta. Daddy ya kalli fuskarta, ya ce "ya na ganki a tsayem" "Ba tafiya zamu yi ba?" "Ban gama abin da nake ba" ya faɗa yana kallon agogon hannunsa. Amina ta kwaɓe fuska ta ce "Haba Daddy, lokaci ya ƙure fa, huɗu fa" kallon yadda take maganar tsakani da Allah yake, wanda gaba ɗaya shagwaɓa take yi. "Let me see your bag" yayi maganar yana miƙa hannunsa. Fuskarta babu daɗi, ta miƙa masa jakarta. Ya karɓi jakar ya nufi wani ɗakin. Kwaɓe fuska Amina tayi, ta samu wuri ta zauna, gaba ɗaya ranta ya gama ɓaci, so take ta tafi gida duk ta gaji, kawai ta ji wata irin ƙwalla ta taru a idonta. Bai wani jima ba ya fito hannunsa ɗauke da jakar, ya nufo im in da take a zaune ta takure tana zumɓura baki. " 'yar Daddy, kin gaji ko?" Ta ɗaga masa kai. "To tashi mu tafi, am sorry" ya faɗa cikin sigar rarrashi. Ta tashi tsaye, ta ce "To Bani jakar" "A'a bari in riƙe miki muje" Amina ta ɗan kalleshi ta ce "A'a Daddy ai bai kamata ba" Daddy ya yi gaba yana faɗin "To me is normal" Amina ba ta da zaɓi sai na bin bayan Daddy. Bayan fitowarsu ma'aikatan gidan suka nufo su suna masa barka da fitowa. Gaba ɗaya sai ya sauya ya koma Alhaji Ahmad ɗinsa, kamar ba shi ne wanda ya gama zolayarta a ciki ba da suna su biyu. Ya kalli wani daga cikin ma'aikatan ya ce "A shiga a gyara kitchen da sauran abin da aka yi amfani da shi" "Ok sir" Alhaji Ahmad ya buɗe motar, ya saka jakar Amina a ciki, Sannan ya kalleta ya ce "Bismillah" Amina ta shiga ya rufe ƙofar, sannan ya zaga ya shiga motar shima. Amina ta jingina da jikin kujera ta ce "Washhh Allah" "Sorry kin gaji ko?" Jinjina masa kai kawai tayi, tana sake lumshe ido. "Daddy" ta kira sunansa. "Meenalin Daddy" ya amsa yana tuƙinsa cikin nutsuwa. "Meyasa ka bawa Baba kuɗi ya dinga bani, yana zargin ni na roƙeka fa" "Ai na gaya masa baki roƙeni ba, ni nayi niyya kawai na bayar nace ya dinga ƙara miki in zaki makaranta, bana son na baki ni da ke, na san ba zaki karɓa ba, kuma bana son wani zargi ya shiga, shi ya sanya na bashi, kuma ai ba kuɗi me mai yawa ba" "Amma meyasa ba ka bawa Hajara sai ni?" Tayi masa tambayar a bazata. Kallon Amina ya yi ya kawar da kai bai yi magana ba. "Daddy ka amsa mana" "Bana son yawan tambaya fa, matsayin Amina daban a wurina, ita ma matsayinta daban" Amina ta ce "To meye banbancin matsayin namu ne? Naga duk masu aiki ne a gidanka" "Ki ƙyaleni" ya faɗa ba tare da ya kalleta ba. "Dan Allah Daddy" "Kin raina ni ko? Ni kike titsiyewa hakam" Da sauri ta ce "A'a" "Baki san da wa kike tare ba ko? To idan nace bana son abu, bana so" "To Allah ya baka haƙuri Daddy, ba zan sake ba in sha Allah" "Good girl" Ga mamakin Amina, Yau Daddy bai ajiye ta a ƙofa ba, sai da yaje bakin gate ya fara horn. "Daddy bari in sauka mana" ta faɗa tana ɗaukar jakarta da taji ta ƙara nauyi" "A'a sai mun shiga nayi parking" yayi maganar yana horn. A ɗan rikice ta ce "Daddy kar Baba ya ganni, ko Hajiya fa". "Ki tanadi abin gaya musu" maganar ta sa tayi daidai da buɗe gate da Zakiru yayi maimakon Baba ya buɗe. Gaba ɗaya Amina ta rikice, sai dai ba taga Baba a harabar gidan ba, Alla Alla take yayi parking, ta fito kan wani a gidan ya ganta. Bayan Daddy yayi parking, cikin hanzari Amina ta fara ƙoƙarin buɗe motar, amma taji a rufe. Tana waiwayowa ta kalli Daddy, taga ya kashe motar yana dariya. "Daddy dan Allah ka buɗe, kar Hajiya ta ganmu" "Kamar kin san idan ta ganki  kece a ciki, ni ba ruwana" "To ka buɗe mini dan Allah" "To ka buɗe mini dan Allah" ya kwaikwayi muryarta da tuni ta samu rauni, kamar tayi kuka. Murmushi ya cigaba da yi yana kallonta, sai da yaga idanunta sun ciko da hawaye, sannan ya cire motar daga lock. Da sauri ta fita daga motar, tana ɗan leƙa wurin zaman Baba, ko zata hango shi a wurin. Daddy ya rufe motar ya ce "Ki nutsu, Baba baya nan wadda kike tsoron ma haka, ko kin manta muna tare ta mini waya?". Ajiyar zuciya tayi ta ce "Na manta ne, ina tsoron ta mayar da ni ƙauye in rasa karatuna, dan da na yi laifi sai a fara cewa za'a mayar da ni ƙauye". "Allah ya sa ta jiki, zaki yi mata bayani dalla-dalla" "Allah  yasa na sauka daga motarka, balle in faɗi wani abu ka saukeni a hanya, da wani abu zan faɗa" "Aminatu kin raina Daddy fa" "A'a ban raina Daddy ba, Daddy yana da kirki ne sosai, ba kamar..." Sai kuma tayi shiru. "Ba kamar wa ba? So kike muyi faɗa ko?" Ta girgiza masa kai alamar a'a. Hajara ce tayi turus a falo ganin Amina da Alhaji Ahmad tare, da alama tare suka shigo. "Idan ba kya son muyi faɗa, to ki kiyaye abin da zan yi fushi" "To na daina" Ya jinjina kai ya ce "Go and have rest, see you later" Baban abin da ya bawa Hajara mamaki shi ne, yadda ganinta bai sa sun farga sun daina hirar da suke ba, cike da wani yanayi da ta kasa fassarawa. Daddy ya nufi hanyar sashinsa, Hajara ta risuna tana "Barka da zuwa" ɗaga mata hannu kawai ya yi, fuskarsa a haɗe, kamar ba shi ne ya gama ƙarewa Amina kallo yana murmushi ba. Waiwayowa tayi ta kalli inda Amina take, Amina ta kalleta sama da ƙasa, ta nufi na su sashin, sai kuma ta tsaya ta kalli Hajara ta ce "Kiji ki ƙi ji, ki gani kuma ƙi gani, idan ki ka matsa kuma hmmm" sai tayi murmushi kawai ta wuce Hajara, ta barta a tsaye sororo tana kallon Amina. AYSHERCOOL 08081012143GABA DA GABANTA BY AISHA ADAM AYSHERCOOL AREWABOOKS AYSHERCOOL7724 WATPAD ayshercool 7724 https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=pfbid026t2vzuetnW2Fw4oD3AtFx8ssrmVz8MvDoQw62FEKNmt4Mc6YNC9ccxnCrk7CoCSNl&id=100089289690624 _Assalamu alaikum 'yan'uwa masu albarka_ _Muna roƙon arziƙi ku shiga wannan link ɗin ku yi mana sharhi kan labarin idan kun karanta, ku danna like sannan ku yi share ɗin shi, Allah Ya saka muku da alheri Ya ba ku tukuici da gidan Aljanna maɗaukakiya._ _SANARWA DAGA: GAMAYYAR MARUBUTAN JIHAR KANO (GAMJIK)_ *Dan Allah masu nema daga farko, ko wasu pages ɗin, su duba Watpad ayshercool7724 ko Arewabooks ayshercool7724, zaku samu daga farkon, aikin babu sauƙi, in yi typing, nayi share kuma ace na bayar daga farko* 40 Saroro baki buɗe, Hajara tabi Amina da kallon mamaki, gaba ɗaya gani take kamar ba Aminan da ta sani ba ce, wani ɓoyayyen abu take gani a kan fuskar Amina mai kama da ƙudurin da zata iya jurewa kowace irin barazana. Banda haka, ta yaya zata shigo falon matar gida tare da maigidan cikin wani yanayi da haryanzu ta rasa muhallin da zata saka shi. Soyayya ce kenan? Ta tambayi kanta. 'a'a ba zai taɓa yiwuwa ba, mutumin da yake aiki a wani gari daban gari mai cike da goggagun mata masu ji da kansu, mai ɗumbin dukiya mai tarin yawa, ta yaya zai ɓige da son 'yar cikinsa, 'yar cikin nasa kuma mai aiki 'yar ƙauye?. Sukuku haka Hajara ta bi hanyar da Amina tabi, tana tunanin yadda zata samo zaren labarin, ta gane a wani ma'auni zata ajiye alaƙar Amina da Alhaji Ahmad. Cike da tsananin gulma da take cin Hajara, ta bi Amina ɗakinta, ta tarar da Amina ta cire uniform ta ɗaura towel zata shiga wanka. Hajara ta kalli Amina tana ƙaƙalo murmushi ta ce "Wai nikam Amina, ban gane me kike ce mini ɗazu ba, naji kamar wata karin magana ki ka yi" Amina tayi murmushi ta ce "Idan baki gane ba, ki barshi a haka kawai" "Ba zaki mini bayani ba kenan, yau naga kin daɗe a makarantar" "Eh, ai kin san muna zama yin lesson, shi ya sanya" Hajara ta ce "Haka ne, tare kuka dawo da shi Alhajin kenan?" "Eh Hajara, tare muka dawo, yaje ya ɗauko ni daga makaranta ne, shikenan? Ina son zan shiga wanka" "To bari in baki wuri, Lallai Amina kin shigo gidan nan da ƙafar dama" Amina bata kuma saurarrta ba, ta shige banɗaki ta bar Hajara. Hajara ta riƙe haɓa tana sake jinjina kai, ga labari amma babu bakin bayarwa, dan ta san ko giyar karnuka ta sha, ba ta isa ta tunkari Hajiya Zainab da wata magana makamanciyar Wannan ba, dan ta san kome zai faru tare da ita zata kwaɓewa, to ta isa ma tayi wani yinƙuri na furta wani mummunan abu a kan maigida meye hujjarta?' A fili ta ce "Allah ma ya ƙara, ni tsorona Allah ya sa ba lalubeta yake yi ba, ita matar gida tana can gantali kamar 'yar akuya kullum tana tafe kamar iska" Ɓangaren Hafsa kuwa, ta rame tayi duhu, gaba ɗaya ta daina walwala, waccan rayuwar tata ta baya ta sake dawo mata sabuwa fil, cike da sabon salo mai ɗauke da ciwo irin na soyayya. Tun daga koke koken nan da tayi, take fama da ciwon kai, tayi ta ƙoƙarin kawar da tunani da damuwa da Khalil, amma abu ya gagara tun tana ɓoyewa kar Mama ta gane, har abu ya zo ya zarce mata da zaɓi mai zafin gaske. A hakan Mama ta gane, saboda ganin yawan kwanciyar da Hafsa take yi, ga rashin cin Abinci. Cikin dare Mama ta tashi, domin yin sallar dare, ama ta dinga jin sheshsheƙar kukan Hafsa, ta miƙa hannu zata yaye abin rufar Hafsa, amma taji jikinta zafi rau. "Hafsa meye haka? Meke damunki ne?" "Mama bakomai" "Kamar yaya babu komai, ji yadda jikinki yayi zafi, Hafsa kin ɗora kanki damuwa kina nema ki hallaka kanki, Hafsa ƙaddara ba zata samu bawa yayi tawakkali ba?" Hafsa ta ja jikinta da ƙyar ta zauna, ta ce "Mama ba laifina bane ba, kawai rashin lafiya nake yi" "Haba Hafsa, nifa na haifeki ba ke kika haifeni ba, na sani kin shaƙu da Khalil haryanzu kina son sa, amma ki cigaba da Addua, Allah ya kawo miki mafita, bana jin daɗin ganinki a wannan yanayin ko Abincin kirki ba kya ci, kuma ni baki gaya mini baki da lafiya ba" Hafsa dai tayi shiru, ba tace komai ba. "Tashi ki lallaɓa kiyo alwala, ki zo ko raka'a biyu kiyi, kiyi Addua Allah ya bamu mafita gaba ɗaya, ina da guntuwar gasara sai in dama miki kunu ki sha, sai in baki paracetamol" Cikin yanayi na jin jiki Hafsa ta ce "A'a Mama, dare yayi sosai, bari in sallar kawai" "A'a ba komai, bari in dama miki, yunƙura ki tashi" Hafsa ta yunƙura za ta tashi, ama jiri ya kwasheta ta koma luuuuu zata faɗi. Duk da Mama bata da cikakkiyar lafiya, haka ta yunƙura ta rungumo Hafsa, suka kusa faɗuwa. Cike da damuwa Mama ta ce "Hafsa har jikin naki ya kai haka?" "A'a Mama, jiri ne kawai ya ɗan ɗebe ni" Mama ta kama Hafsa ta zauna, sannan ta ce "Kinga zauna, bari in je in dama miki kunun, in baki maganin, zuwa in Allah ya kaimu sai mu tafi Asibiti". Hafsa ba ta ce komai ba, sai lumshe idanunta da ta yi, tana sake jin jikinta babu daɗi. Bayan sallar isha'i Amina tana ƙoƙarin buɗe jakarta ta ciro litattafanta, ta ci karo da tarin kayan ciye-ciye na biscuit da chocolate, da wani turare da kwalinsa kawai abin kallo ne, jan kwali ne kwalbar turaren ma ja ce, mai matuƙar ɗaukar hankali. Ta fesa turaren a hannunta ta sansana, wani irin sassanyan ƙamshi ne da turaren mai kwantar da hankali. Ko ba a gaya mata ba ta san turare ne mai tsada sosai. Murmushi Amina ta yi, tana sake jujjuya turaren da kallon tarkacen kayan ciye-ciyen. Wani murmushi Amina tayi, wanda ita kaɗai ta barwa kanta sanin ma'anar murmushin. Fadila kuwa a ɗakinta ta ci Abinci ita kaɗai, tayi wanka tana saka kayan bacci tana shafa mai, ta kalli turarukan wurin Yazid, ta zuba musu ido tana kallonsu tamkar Yazid ɗin take gani a wurin, tunani ta shiga yi a kan barkwancinsa, da yadda yake ta nuna mata kulawa daga fara shirin su zuwa yanzu, mutum ne mai haƙurin gaske da kawaici, ta tuno yanayin da ya shiga a lokacin da ta gaya masa tafi ƙarfin sa, har aka tashi jikinsa babu wani kuzari. Guntun tsaki tayi a fili tana tunanin sai me dan tayi masa warning a kan ya fita daga harkarta, ai ya san ruwa ba sa'an kwando bane, kuma kamar yadda Yusra ta gaya mata, sanyin halin Yazid da kyautatawarsa zata iya sawa ta fara son shi ba tare da shirya hakan ba, gara ma tun wuri ta raba gari da shi. Wayarta ce ta kawo haske, ta kalli in da wayar take taga message ne ya shigo, ta ɗaga wayar ta duba sai taga missed calls biyar, duk na Kankiya saboda wayar na silent bata san ya kira ba.  Ta duba saƙon ta ga roƙonta yake  wai yana son ta bashi dama ya zo gidansu. Dire wayar tai tana harar wayar tamkar ita ta turo mata saƙon, "Zan ɗau mataki a kanka, idan ya so ka yiwa Yazid ɗin abin da ka ga dama ku ta shafa" tayi maganar tana ƙoƙarin kauda wani abu mai kama da tausayi a ranta game da Yazid. Mummy ce ta faɗo ɗakin Fadila babu ko sallama fuskarta cike da damuwa. Fadila ta kalleta ta ce "Mummy ya dai?" "Kin yi waya da Khalil ne?" "Mummy wane Khalil kuma, wayar me zan yi da shi bayan yana gidan nan" Mummy ta ce "Khalil baya gidan nan, sai yanzu na farga, tun safe banga gilmawarasa ba, na duba babu motarsa, naje in tambayi wancan shashashan tsohon when last Khalil ya fita, amma na tarar baya nan, sai direban babanku ne ke buɗe gate ɗina, wai ya nemi iznin babnku ya tafi ƙauye, shi kuma bai san lokacin da Khalil ɗin ya bar gidan nan ba" Fadila cikin mamaki ta ce "Ikon Allah, to Mummy ki kira wayarsa mana" "Na kira taƙi shiga sam, gaba ɗaya hankalina ya ɗaga" "Ko ya koma wurin aiki ne?" Fadila ta sake tambaya. "To wa ya sani ne? Kuma sai ya koma wurin aiki bai mini sallama ba, yaya hakan zai yiwu, kar inje a sace mini ɗa a banza, sai sa na gaya wa babanku, ya samar muku da security, yawonmu haka a gari is not safe, duba sa matsayin da ya riƙe a ƙasar nan, amma ya ce mini no need, ai ga irnta nan" Fadila ta ɗanyi shiru sannan ta ce "Mummy, bana tunanin sace Yaya Khalil aka yi, wataƙila ya tafi wani wurin ne dan huce haushin abinda kika yi wa yarinyar da yake so" Cikin mamaki Hajiya Zainab ta ce "Kuma haka ne ko? Yanzu sai Khalil ya bar gidan nan ya tafi wani wurin ba tare da na sani ba saboda haka? Aikuwa idan haka ne da ya ci ubansa, sai na nuna masa nice uwarsa kuma dole ya bini" "Mummy kibi a hankali, kar garin neman gira a rasa ido" "Rabu dani da wata ido da gira, zan cigaba da bincikawa muddin na tabbatar haka ne idan bai yi wasa ba saina ci mutuncinsa". "Amma me Daddy ya ce?" "Rabu dani da Daddyn nan na ku, nayi masa Magana amma bai mayar da abin serious ba, wai Khalil ba yaro ne ƙarami ba, duk in da yaje zai dawo kar in damu kaina" "Mummy, gaskiya Daddy ya faɗa, ki kwantar da hankalinki zuwa Allah ya kaimu da safe mu ga yadda hali zai yi" Jinjina kai Mummy ta yi ta bar ɗakin Fadila, gaba ɗaya ta rasa nutsuwarta saboda rashin sanin halin da Khalil yake ciki, da kuma a ina yake, ta ɗora alhakin duk wannan abun a kan Hafsa, wadda take can tana fama da kanta. Da safe wajen ƙarfe tara na safe, Mama ta shirya ta dafawa Hafsa ruwan wanka, da ƙyar Hafsa ta rarrafa tayi wanka, kasa cin Abincin ma ta yi, Mama ta taimaka mata, ta shirya suka tafi Asibiti. Tashin farko teses kawai sun yi na dubu biyu aka rubutawa Hafsa, aka yi mata likita ya tabbatar da jininta ya hau, ga malaria mai zafi da ulcer. Mama ba tayi mamaki ba jin Hafsa tana da hawan jini, likitan ya ɗan nazarci fuskar Hafsa sannan ya ce "Ƙanwata meke damunki a 'yan shekarunki kika kamu da hawan jini, jininki ya hau fiye da yadda za a iya cewa ko zafin zazzaɓin ne ya sanya jinin ya hau" Hafsa ta sunkuyar da kanta, tana muza yatsunta na hannu. "Magana fa nake" ya sake maganar yana ɗan dukan teburin gabansa. Hawaye ne ya taru a idon Hafsa, Mama ta ce "Likita rabu da ita kawai, duk saboda ta rabu da wani saurayinta, shi ne ta saka kanta a uku, nayi nasihar nayi rarrashin amma ta saka abin a ranta" Likitan ya ce "Mahaifiyarta ce ke ko yayarta?" Mama ta ce " 'ya ta ce" Likitan ya ce "Ba abune mai sauƙi ba Hajiya, musamman ga mu mutanen wannan zamani, muna bawa soyayya muhimmanci sosai da sosai, dole zata shiga damuwa, saboda abun ba sauƙi amma kiyi haƙuri ki cigaba da Addu'a ko kina son Mama ta rasaki at your young age, ko ki kamu da ciwon zuciya?" Hafsa ta ce "A'a" "Tukuna ma, gaya mini sunansa, sannan maiyasa ya yaudareki?" "Ba yaudarata yayi ba" "Ok na gane, kin san kowane bawa, akwai rubutacciyar ƙaddararsa, kiyi haƙuri, ga magunguna nan da ruwa, zan riƙe ki a Asibitin nan tsawon kwanaki biyu, sai naga jikinki yayi kyau, jininki kuma ya sauka" Mama ta yiwa likitan godiya, da jin daɗin yadda ya nuna damuwarsa ga Hafsa, ta riƙe Hafsa suka fita ma'aikatan jinya suka basu gado, Mama taje ta biya kuɗin, da kuma sayo magunguna. "Baban Fadila nifa ban gane manufarka ba, yaya zan gaya maka ban san in da yaro yake ba, amma ko a jikinka" "To yaya zan miki ni? Khalil dai ba yaro bane ba ƙarami, da hankalinsa kuma ke da bakinki kika gaya mini abin da kika yi masa, dan haka yayi wani wurin ne, dan yaje ya ji da tension ɗin da kika saka masa" Cikin ɓacin rai ta ce "Kana nufin saboda na rabashi da 'yar matsiyata shi ya sanya zai bar gida ban san in da ya tafi ba? To wallahi ko zai mutu ba zai kawo mini jinin tsiya a matsayin sirika ba, zai ga yadda zan yi da shi, bai isa ba wallahi" Daddy ya ce "Dan haka sai ki daina tayar mini da hankali a kansa, matsla ce da kika kunnota ke zaki maganinta" "Au haka ma zaka ce?" "To me zance ni?" "Zaka ga me zaka cex" ta bar falon Daddy Fuuu ranta a ɓace. Amina har ta tafi makaranta Baba bai dawo ba, bata san ya aka yi ya tafi ƙauye ba sanarwa ba, bai gaya mata zai tafi ba suka haɗu da Safe tayi masa sallama zata makaranta, amma bai gaya mata cewar za shi ƙauye ba, sai da ta dawo daga makaranta. Tayi ta ƙoƙarin kiran wayarsa, amma wayar bata shiga, sai ta shiga damuwa tana fatan Allah ya sanya komai lafiya. Haka ta dawo daga makaranta tana sa ran ganin Baba, amma ta dawo ta tarar bai dawo ba. Sai wajen la'asar sannan Baba ya dawo, Amina ma bata san ya dawo ba, kawai ta fito da niyyar ta duba ko ya dawo ta tarar da shi yana salla. Murna ta dinga yi tana godewa Allah, da ya sanaya yana lafiya. Ta jira ya idar da sallar, yayi Adduoinsa sannan ya kalleta ya ce "Uwata ya makaranta?" "Lafiya lau Baba, amma baka gaya mini zaka tafi ƙauye ba, sai da na dawo nake ji jiya" Baba ya ce "Eh, tafiyar ce ba ta shiri ba, nayi ta ƙoƙarin ma in kira wayarki in haɗaki da babarki, amma wayar taƙi shigowa" Amina ta ɗan ɓata fuska ta ce "Kash, nima nayi ta ƙoƙarin kiranka amma ba ta shiga, Baba dan Allah ka saiwa Inno waya, in dinga jin muryarta" Baba yayi murmushi ya ce "ai na bayar a saya mata, har layi na bawa Saminu nace ya sai mata mai ɗan kyau wadda zata iya gane kanta" Amina tayi murmushi ta ce "Yauwa Baba, yaya ka baro su, ya kowa da kowa" Baba ya ce "Duk suna lafiya suna gaisheki, Sa'a an saka bikinta. Mun yi magana da Alhaji Ahmad, yayi mini maganar zuwanki birnin tarayya a kan harkar karatunki, da fari dai na ɗan yi jayayya amma daga baya ya mini bayani na amince, ina fatan zaki kula da kanki Amina, ki riƙe mutuncinki, ki tuna ke ba 'yar kowa bace, ki kula da tarbiyyar da muka baki" Washe baki Amina ta yi ta ce "Baba, ka amince inje ɗin?" "Eh uwata, na amince ina miki fatan alkhairi, sannan ya ce mini zaki gida kiga gida kuma kiyi musu sallama, saboda doguwar tafiya zaki yi" Hawayen farinciki suka cika idanun Amina, ta kalli Baba ta ce "In Allah ya yarda ba zan baka kunya ba Baba, zan kula da kaina, ka mini Addu'ar samun nasara" "Addu'a ai kullum cikinta nake, Allah ya yi miki albarka, ga kayayyaki can babarki ta haɗo wai in kawo miki" Cikin murna Amina ta nufi wurin kayan da Baba ya nuna mata, ta ɗau ledar Vivan, tana jin yadda take jin kewar Inno a ranta. Har zata fita daga ɗakin Baba ya ce "Yauwa na haɗu da wannan malamin naku na makarantar boko, na manta sunansa, ya cc in gaisheki" "Laa Malam Sunusi?" "Eh shi" "Allah sarki, ina amsawa, yauwa Baba a kawo Abinci ne, ko in dafa maka wani abun?" "A'a ba sai an kawo ba, nan da kika ganni a ƙoshe nake" Amina tayi murmushi ta juya ta bar ɗakin Baba. A falon gidan ta tarar da Hajiya Zainab tana kaiwa tana komowa a falon, da waya a hannuta kamar ka taɓata ta fashe sai cika take tana batsewa. Tana ganin Amina da leda ta ce "Ke!" Amina ta tsaya tare da kallon in da Hajiya Zainab take. Cikin kaushin murya ta ce "Daga ina kike?" "Naje wurin Baba ne ya dawo" Amina ta bata amsa. "Maza kije ki kira mini shi, dama shi nake jira" tayi maganar tana hura hanci. Sai da Amina ta ɗan tsaya tana kallon Hajiya Zainab, tana son gano dalilin da ya sanya take son ta kira mata Baba. "Ba zaki je bane kika tsaya kina kallona haka?" Amina ta ajiye ledar hannunta, ta juya ta fita, tun daga nesa Baba ya hangota ta nufo shi, fuskarta a haɗe, tsayaqa6 yayi yana jiran ƙarasowarta. "Uwata lafiya naga kin dawo?" "Matar gidan ce ta ce na kiraka" Baba ya ce "To, Allah ya sa ba wani laifin ki ka yi ba, ko ni nayi ba" "Nima ban san meye ya sa take nemanka ba" "To muje, koma meye sai na ji" Suka rankaya suka nufi falon. Suka shiga Baba yayi sallama, amma Hajiya Zainab tayi biris tana ta wani kumbura wuya kamar kasa. Ta ƙarewa Baba kallo a wulaƙance, irin kallon yake ƙonawa Amina rai. "Jiya da yaushe ka bar bakin gate ɗin nan?" Ta jefowa Baba tambayar. Cikin girmamawa ya ce "Sai goma na safe ranki ya daɗe?" "Kenan kana nan Khalil ya fita?" "Eh, nina buɗe masa ƙofa, bayan sallar Asuba ya ɗau mota, na buɗe masa ƙofa ya fita". "Wane irin mutum ne kai da zaka buɗe masa ƙofa ya fita bayan sallar Asuba, ina ya ce maka zai tafi?" "A'a Hajiya, bai gaya mini ba, ko gaisawa ba muyi ba ya fita" Wani uban tsaki ta ja, sannan ta ce "Kai dai banga amfaninka a zaman gadin nan ba, tayaya yaro zai fita bayan sallar Asuba, amma ka kasa tambayar ina zai tafi" Ikon Allah Amina ta tsaya tana kallo, aikin Baba buɗewa da rufewa to meye huruminsa na sanin in da wani zai je a gidan? "Yaya dai meke faruwa ne?" Suka jiyo muryar Alhaji Ahmad, da ya fito yana ta zuba ƙamshi cikin wani vowel baƙi. Ya kalli Baba Hassan da ke tsaye fuskarsa cikin damuwa, ya risunar da kai kamar mai neman gafara. "Malam Hassan, ka dawo ashe?" Baba ya ce "Eh na dawo ranka ya daɗe" Baba ya Kalli Mummy ya ce "Meke faruwa ne?" "Ka jiye mini wannan rainin hankalin mana, wai Khalil ya fita daga gidan bayan sallar Asuba amma ya kasa tambayarsa ina za shi ko ya sanar mana, ni na gaji da sokoncin wannan mutumin" "Sokonci kuma?" Amina ta tambaya rai a ɓace. Nunata Hajiya Zainab tayi ta ce "Idan ina magana kina saka mini baki, sai na ɗauke ki da mari, da ubanki nake magana, na faɗa sokwanci, sam bai san aikinsa ba, nace maka ka sallame shi ka samo mana masu gadi na hukuma, wannan ko wani abun ne zai faru ba sai dai ya same mu ba, ba uwar da zai iya tsinana mana ba" Ga mamakin Amina ta sai ta ji Alhaji Ahmad ya ce "My dear kiyi haƙuri, ki bi komai a hankali, sanin in da Khalil za shi ba alhakinsa bane ba, kuma yana iya ƙoƙarinsa, bai kamata ace kina tada jijiyoyin wuya haka ba" "Ba dole in tada jijiyoyin wuya ba, ka bar wannan mutumin a shiritarsa ɗana ya bar gida, gaskiya Allah amfana aikin da yayi haka, ya koma in da ya fito, na gaji". Baba ya risuna ya ce "Dan Allah Hajiya kiyi haƙuri, in Allah ya yadda hakan ba zata sake faruwa ba" Amina ta zata Alhaji Ahmad zai ɗau wani mataki, amma ya ɓige da lallaɓa Hajiya Zainab a kan tayi haƙuri. Wani mugun kallo Amina ta yiwa Alhaji Ahmad, idanunta suka cika da hawaye ta ɗau ledarta ta wurin Baba kawai ta bar falon, saboda yadda zuciyarta ke mata zafi zata iya zagin Hajiya Zainab. Alhaji Ahmad ya lura da yadda Amina ta ɗau zafi, amma ba damar yayi wani yinƙuri a lokacin, haka ya dinga rarrashin Hajiya Zainab, ya ce Baba ya koma bakin aikinsa. Baba kansa ba ya jin daɗin yadda Hajiya Zainab ke masa a wasu lokutan, amma ba yadda ya iya idan ya bar aiki makomar karatun Amina da kuma iyalinsa baki ɗaya yake tunani. Kan ya ƙarasa wurin gate ɗin, aka fara horn. Ya ƙarasa da sauri jikinsa na tsuma, ko Fadila ce ta dawo, kar ya yi wani laifin ya kuma jawa kansa wani cin mutuncin. Yana buɗewa yaga motar Khalil, ɗan tsayawa Baba yayi, yana kallon motar. Abdul yaje yayi parking ɗin motar ya fito ya nufo Baba, Baban ma nufarsa yayi ya ce "Malam Abdul, ya na ganka kai kaɗai ina Khalil ɗin?" Abdul ya ce "Ai Khalil ya koma wurin aiki ne, ya aikin Baba Hassan?" Baba ya ce "Alhamdilillah" "Mutanen gidan kuwa suna nan?" Baba ya ce "Eh ka shiga suna ciki" Abdul ya nufi cikin gidan. A falon ya tarar da Hajiya Zainab, tare da Daddy, yana ta aikin rarashinta a kan rashin sanin in da Khalil yake. Abdul ya shiga da sallama, Daddy ne kawai ya iya amsa masa. Ita Mummy ma sai yanzu ta tuna da Abdul, ƙila ya san in da Khalil ya tafi, amma ko ya sani ma ita bata da lambarsa balle ta kirashi ta tambaye shi, ko da yake ta san wataƙila Khalil ɗin ɗin yazo nema shima dan da ya san in da yake, ba zai biyo shi gida ba. Har ƙasa Abdul ya durƙusa ya gaishe su. Daddy ya amsa masa cikin sakin fusak Daddy ya amsa, ita kuwa Hajiya Mummy ba ta bi ta kan gaisuwarta sa ba. Abdul ya ce "Dama motar Khalil ce na dawo da ita gida" "Motar Khalil kuma? Ina shi Khalil ɗin ya kex Mummy ta faɗa tana zazzaro wa Abdul ido. Mamakine ya kama Abdul, ganin da alama ba su san ina Khalil ɗin ya tafi ba. "Mummy, wajen ƙarfe shida ya sameni a gida, ya ce in kai shi airport zai koma Abuja, sai in dawo da motarsa gida, naje wurin aiki ne shi ya sa ban dawo da ita ba". "Amma kai baka da mutunci, har ya haɗa baki da kai ya tattara kayansa ya koma aiki, ban san in da yake baka gaya mana ba sai yanzu, kasa hankalinmu duk ya tashi bamu san ina yake ba". "Wallahi Mummy ni ban san bai gaya muku ba, kawai... "Dalla rufe mini baki, ai duk wata ƙulla-ƙullar rashin gaskiya kaine kake bashi shawara, na san wataƙila kaine kake hure masa kunne, yaje ya gano wata 'yar talakawa ya maƙale wai ita yake so" Abdul ya sunkuyar da kai yayi shiru ya gaza cewa komai. Daddy ya kalli Abdul ya ce "My son, tashi ka tafi Allah yayi maka albarka, ka gaida maman naka" Abdul ya ce "To Daddy sai anjima" Sai da Abdul ya fita, sanan Daddy ya ce "Zainab wai meke damunki ne? Dan kawai ɗanki ya miki laifi sai ki dinga bin wanda ba su ji ba ba su gani ba da miyagun maganganu da cin mutunci?" "Au haka kace? Suwaye ma mutanen wa na yiwa ƙarya wancan sakaran tsohon da bai san aiinsa ba ko wannan yaron mai kama da maye ya liƙewa ɗana ya ƙi rabuwa da shi duk wata harkar ƙasƙanci shi ne yake nuna masa" Ran Daddy ya ɓaci, ya miƙe ya ce "Sai kiyi abin da kika ga dama ki ki cigaba kar ki fasa, idan kika kaini bango kin fi kowa sanin halina" Bayansa tabi da harara, ta tashi tai nata wuri. Fadila kuwa tun da taje makaranta, ba ta ga Yazid ba sai lokacin lectures kawai, da an yi yake ficewa daga ajin sai lokacin wata lectures ɗin, kuma ko da wasa bai yadda ya kalli in da zai ga Fadila ba, balle a samu kuskure ko ido su haɗa. Ita ma tayi nata ƙoƙari, wurin ganin ba ta ko nuna ta san da zamansa a ajin ba, ta cigaba da harkokint. Sai dai yin hakan taji ta takura kanta sosai da sosai, ko ba komai Yazid mutumin kirki ne, kuma ya taimaketa sosai a first semester, wanda garin taimakon nata ne har ya rasa wasu marks ɗin, amma hakan bai hana shi zama overaller ba! Bayan Daddy ya dawo daga sallar isha'i, ya tarar da Amina tana shirya Abincin dare, fuskarta babu walwala sam, idanunta duk sun ƙanƙance da alama tayi kuka. Dining ɗin ya ƙarasa yana murmushi "Meenali me aka dafa ne yau?" Banza ta yi masa ta cigaba da abin da take yi. "Ba kya jina ne?" "To ni me zance" ta faɗa bata ko kallon inda yake. "Amma magana fa nake miki" Idanunta da suka cika da hawaye ta ɗago tana kallonsa. "Ka zama mai kulawa da mutuntawa a gareni, ka ɗauki lamurana da muhimmanci amma a gabanka matarka take ciwa mahaifina mutunci, idan nayi magana ka ji haushina, ka san yadda nake ji a duk lokacin da iyalinka suka ci zarafin mahaifina a gabana? Kawai dan muna talakawa? Mu muka yiwa kanmu? Duk lalacewar uba uba ne, balle babu lalacewa a iyaye, ni kar ka sake nuna mini wata kulawa, babban abin da za a mini a rayuwata shi ne a girmama mahaifina ya fi mini duk wani tattali da kulawa" ikon Allah Alhaji Ahmad ya tsaya yana kallo, tuni idanunta suka yi jawur hawaye ya wanke mata fuska, ta bar falon ta bar shi a tsaye. (*Masu yi mini sharing, da masu Comment, ina gani kuma ina godiya Allah ya bar ƙauna. Haryanzu ƙofa a buɗe yake, ga masu buƙatar shiga VIP GROUP, domin samun posting kullum, ku garzayo kuyi payment*) AYSHERCOOL 08081012143GABA DA GABANTA BY AISHA ADAM AYSHERCOOL PAGE 41 Alhaji Ahmad ya shafi gemunsa, bai zaci Amina zata iya tsayawa ta yi masa tsiwa haka ba, amma ta wani fannin da gaskiyarta, ba bu wanda zai jure a dinga cin mutuncin iyayensa haka kurum, dan kawai talaka ne, amma ai ba shi yayi mata laifin ba. Amina kuwa ɗaki ta koma, ta zubar da hawaye sosai tayi kuak, ba zata iya ƙirga adadin yadda aka sakata kuka ba a gidan nan, iya cin mutuncin da ake mata baya damunta a kan wanda ake yiwa Baba. Komawa aiki ya gagari Khalil, daga masallaci sai gida, sai yaji yunwa zata kassara shi, sannan yake order Abinci ya ɗan ci kaɗan. Haka nan yaji yana son ya kunna wayar, yayi trying layin Hafsa. Da saƙonnin Mummy ya fara cin karo rututu, a kan ina ya tafi, bai sanar da ita ba? Message ɗaya ya iya yi mata reply ya ce 'ina wurin aiki' Ya lalubo lambar Hafsa, ya fara kira, cikin ikon Allah ya ji wayar ta shiga, tashi yayi zaune ya gyara zamansa, yana jiran ya jibta ɗaga wayar, amma har wayar ta kaste bata ɗaga ba. Ya kira ya kai sau biyar, amma bata ɗaga ba. Message ya tura mata kamar haka "Dan Allah Hafsa, ba dan ni ba ko sau ɗaya ki ɗaga wayata mana, magana nake so muyi" yana tura nata ya ajiye wayar ya dafe kansa. Mintuna kaɗan ya ji kira ya shigo wayarsa, da sauri ya miƙa hannu ya ɗauko wayar, a zatonsa Hafsa ce amma ya ga sunan Mummy, ya ɗaga wayar ya kai kunnensa tare da yin sallama. "Sannu Khalil, wato saboda mace ka zama ɗan kanka ko? Ka shirya ka koma aiki ban sani ba, saboda bani da amfani a wurinka, sai kawai ka aiko mini da motarka ko?" "Ba haka bane Mummy, bana jin daɗi ne, kuma na riga nayi booking ɗin jirgi shiyasa na san at that time babu lallai kin tashi" "Ai dole kaji babu daɗi, tunda na rabaka da waccan yarinyar mana, laila majnun baban soyayya, da ni kake zancen Khalil" ta katse wayarta. A saɓule ya ajiye wayar ya cigaba da riƙe kansa. Fadila kuwa zaune take a kan gadonta tayi tsuruu, gaba ɗaya mood ɗin da taga Yazid bai yi mata daɗi ba, haka nan ta ji ta damu, cikin ƙoƙarin kauda tunanin Yazid daga ranta, ya sanya ta ɗau wayarta ta fara game, ita a dole bata damu da Yazid ba. Alhamdilillah, Hafsa ta ɗan farfaɗo ba kamar lokacin da aka kaita Asibiti ba, an samu jinin ya ɗan sauka. Likita yayi ta mata nasiha, da rarrashinta a kan ata kwantar da hankalinta, ta miƙa lamuranta ga Allah, sannan ya sallamesu. Kusan duk kuɗin hannunsu ya ƙare, saboda zaman Asibiti, ga babu kayan Abinci. Hafsa ta ɗan ji daɗin jikinta, sai dai ta kasa mantawa da batun Khalil, babu abin da ya canza daga soyayyar da take yiwa Khalil ɗin. Kayan da Khalil ya bata ta tattara ta bashi bai karɓa ba,  a soron gidansu ya bar mata, dama tunu ta cire layin wayarta daga wayar da ya bata zuwa tsohuwar tata. Da suka dawo gida ta duba wayar, sai ta ga missed calls ɗin Khalil rututu a ciki, da tarin messages, ba dan ta so ba haka ta saka lambar Khalil a blacklist, tana jin kamar da zuciyarta ta haɗa ta saka a black list ɗin. Bayan Amina ta gama koke kokenta, kuma sai ta fara tunanin akan abin da ta yiwa Daddy, sai taga kamar bata kyauta ba, saboda ya kyautata mata har ƙarawa Baba albashi yayi ba tare da ko matar gidan ta sani ba, ita ma Baba da ya gaya mata ya gargaɗeta a kan kar wanda ta gayawa, dan Alhaji Ahmad ya ce masa ko Aminan kar ya gayawa, banda kyautatawa da yake mata a kai a kai da ƙoƙarin bata kariya a duk lokacin da aka yi ƙoƙarin cin mutuncinta, gaba ɗaya kuma sai jikinta yayi sanyi. Da magariba Hafsa na zaune, ta saka tuwon da Mama ta zuba mata, amma ta kasa ci, Mama sai hira take yi mata dan ta ɗebe mata kewa. Wayar Hafsa ce ta kawo haske alamar kira ya shigo, kasancewar wayar a silent take, Mama ta ɗauko wayar ta miƙawa Hafsa. Hafsa ta girgiza kai ta ce "Mama ƙyale wayar nan kawai" "A'a ai ba a yi haka ba" Mama ta ɗaga wayar tare da yin sallama. "Wa'alaikum salam, Mama ina wuni?" Mama ta kalli Hafsa jin muryar Khalil. "Lafiya lau Khalil, ya aiki?" Waro ido Hafsa ta yi jin Mama ta ambaci Khalil. "Aiki lafiya lau Mama, ina ta kiran Hafsa a waya bata ɗagawa, daga baya ma wayar bata shiga" Mama ta ce "Ai da yake ta ɗan yi rashin lafiya ne, ɗazu muka dawo daga Asibiti" Cikin damuwa Khalil ya ce "Subhanallah, ya jikin nata?" "Taji sauƙi Alhamdilillah, bari in bata wayar" Mama ta miƙawa Hafsa wayar, ta tashi ta bar ɗakin. Hafsa ta kalli sabuwar lambar, sannan ta saka wayar a kunnenta. "Assalamu alaikum, Hafsat" "Na'am" ta amsa a sanyaye. "Hafsa why? Meyasa laifin Mummy zai shafeni, ko mun rabu ai bai kamata ki yanke duk wata alaƙa da ni ba" Hafsa tayi shiri ba ta ce masa komai ba, sai ma jin kewarsa na damunta. "Hafsa kiyi magana mana" "To me zance?" "Shikenan, Yanzu ya jikin naki?" "Naji sauƙi" "Allah ya baki lafiya, gaba ɗaya ina cikin damuwa ko aiki na kasa yi, na kira ba kya ɗagawa daga baya ta daina shiga, sai sabon layi na saya na saka na kira sannan kika ɗaga, dan Allah Hafsa kiyi haƙuri abin da Mummy ta yi miki ya wuce, ina ta ƙoƙarin saita komai, in Allah ya yarda za mu yi Aure" Hafsa ta lumshe idanunta sannan ta buɗesu ta ce "Khalil" "Na'am Hafsa" "Duk abin da iyaye ba sa so aka aikata shi baya albarka, baya zuwa ko ina, dan Allah Khalil kayi haƙuri ka ƙyaleni, dole mu haƙura da juna" Khalil ya maraice ya ce "Dan Allah Hafsa... "Shhhhhh" ta katse shi. "Ko Mama ce ta ce na rabu da kai, idan har bata son alƙarmu zan rabu da kai har abada, Yakamata mu yiwa Mummy biyayya, dan Allah Khalil kar ka sake kirana, kayi haƙuri" "To ki tsaya kiji" ba ta jira mai zaice ba, ta kashea wayar, ta cire layin gaba ɗaya daga kan wayar. Ta haɗe kai da gwiwa tana ta ƙoƙarin mayar da hawaywnta amma ta kasa. Mama tayi sallama ta shigo ɗakin, ta zauna ta ce "Yaya kiran me yake miki?" "Haƙuri yake bani, wai mu koma kamar da" Mama ta girgiza kai ta ce "Ai hakan ba zai yiwu ba, tun da mahaifiyarsa bata so, Allah ya haɗa kowa da rabonsa na alkhairi" "Ameen" Hafsa ta amsa jiki a sanyaye. Khalil kuwa sakin wayar yayi a ƙasa, sai a Yanzu yaji wasu irin lafiyayyun hawaye suna zubo masa, bai taɓa zaton zai iya kuka a kan mace ba, babban abin da yasa yake jin zai iya taking kowane risk saboda Hafsa shi ne ya sani ba kowane namiji ne zai iya karɓar Hafsa da ƙaddararta ba, gashi so yake mata na fisabilillahi, ji yake a duniya banda uwar da ta haifeta babu wanda ya kai shi ya sonta da ƙaunarta. Daddare Amina zata kwanta bacci, ta dinga kallon wayarta, da sukan yi chatting da Daddy da daddare kafin tayi bacci, tayi ta masa shirme da shirirta yana biyeta. Sai dai yau ko saƙo ɗaya bai turo mata ba, ta duba what's app taga yana online. Sallama tayi masa, sai dai ya buɗe ya gani amma ya share, ga zauna shiru shiru amma bai mata reply ba. Ajiye wayar tayi cike da damuwa, tana sake ganin rashin kyautuwar abin da ta aikata wa Daddyn. Kwanaki biyu kenan, babu wanda ya nemi wani tsakanin Fadila da Yazid, a kwana na uku kuwa bai zo makarantar ba gaba ɗaya, gashi ana ta shirye shirye na fara exams, ana fa teses baya nan, abu kamar wasa har aka tafi kwana na uku baya zuwa makaranta, gashi shi ba wani aboki ne da shi ba, balle ta tambaya. "To ma ina ruwana da rashin zuwansa' ta tambayi kanta, ta cigaba da ƙoƙarin mantar da kanta batun Yazid. Amina kuwa nadamar abinda ta aikata ya addabeta ya hanata sukuni, ta kai ta kawo, idan taga Daddy ta gaishe shi, sai dai ya amsa sama-sama, alamar fushi yake da ita. Gashi ta rasa hanyar da zata bi wurin bashi haƙuri. Ranar asabar da safe, tana gyarawa Hajiya Zainab falo, ya shigo falon, Amina ta risuna ta gaishe shi. "Lafiya lau" ya amsa. Ya wuceta ya nufi bedroom ɗin Hajiya Zainab. A tsaye ya tarar da Hajiya Zainab, ta sanya skirt ɗin lace, tana kwalliya a gaban mudubi, ba ta saka rigar ba tukuna. Ya ɗan ƙare mata kallo sannan ya nufi in da take yana faɗin "Bainu ba kya tsufa" Ta ce "Hmm, ka fito kenan, ya ka kwana da jikin?" "Ba zan amsa ba, tun da baki kwana da ni ba, duk da kin san jikina babu daɗi". Hajiya Zainab ta waiwayo ta kalleshi ta ce "Sai kace wani ƙaramin yaro, da ban kwana da kai ɗinba, ba ga ka nan ras da kai ba, jikin yayi sauƙi". Ya ƙarasa bayanta ya tsaya, ya rungumeta ta baya, ya zagaya hannayensa a cikinta, tare da kwantar da kansa a kan kafaɗarta ya ce "Ko ba komai kasancewarki a kusa dani, zai sa naji daɗi" Ɗan ƙoƙarin ture hannunsa take ta ce "Kaima dai, ba magungunaka suna nan ba, ka sha ka kwanta kayi bacci, ko kaje Asibiti mana" "Duk ba wannan nake buƙata ba, ke ɗin dai, attention ɗinki, kulawarki da hirarki domin ɗebe mini kewa, musamman na ɗauki hutun shekara saboda in kasance da ku, duba da yanayin aikin ina daɗewa bama tare amma duk kinfi mayar da hankali a kan 'ya'yanki, business ɗinki da sauransu, ni ba kya kulawa da ni sosai, ina buƙatar kulawa nima" yayi maganar yana cigaba da ƙanƙameta yana shaƙar ƙamshin man da ta shafa. Ɗan tsuke fuska ta yi ta ce "Ahmad meye haka ne? Dan Allah Yakamata ka san yanzu ba da bace bafa, mun girma fa yanzu,da auren wuri muke yiwa yaranmu da yanzu muna da jikoki, yanzu jikinmu hutu yake buƙata ba wannan abin ba,  abin da aka yi a baya Allah ya amfana". Alhaji Ahmad ya sake ƙasa da muryarsa ya ce "Am not old for that, ban san me kike nufi da ni ba, ban yi girman da na wuce samun kulawa da tatali daga iyalina ba, Please kar muyi haka da ke" "Kaga dan Allah ka rabu da ni, unguwa zan fita ni" "Unguwa ƙarfe goma na safe, ke kenan kullum cikin fita da wadda na amince, da wadda ban amince ba? Dan Allah ki zauna a gida mu wuni tare yau" "A'a wallahi, fita ta tana da muhimmanci sosai, zan zaga shaguna na, daga nan zanje biki, classmate ɗinmu na auran 'ya" ta zame daga jikinsa tana ƙoƙarin ɗaukar rigar kayanta ta saka. "Haba Zee, shikenan let's have some fun before you go" yayi maganar yana kuma ƙoƙarin rungumota. Cikin tsawa ta ce "Wai meye haka ne, na ce maka bana so, dan Allah wai sai yaushe zaka girma, you don pass this level, haba dan Allah" Lumshe idanunsa yayi, ransa a ɓace, ya kalleta da idanunsa suka fara sauya launi, "Zainab, ki bini a hankali tura ta kai bango" "Da tura ta kai bango, saika rushe bangon ai, shikenan shekara da shekaru ana abu ɗaya, shekaru sun ja ma amma mutum bai san ya girma ba" Daddy bai kuma ce mata uffan ba, ya juya ya fice. Amina tana mopping a babban falo ya fito, kallo ɗaya tayi masa ta fuskanci akwai damuwa, amma bata da ikon magana, haka ya koma nasa sashin. Babu daɗewa Hajiya Zainab ma ta fito, ta sha uban ado sai ƙamshi take, hannunta riƙe da mukullin mota, sai yatsuna fuska take ta dubi Amina da take ƙarasa mopping ta ce "Idan an tashi girkin rana, ba sai an yi da ni ba,  dinner ayi abinci mara nauyi" Amina ta ɗan basar ta ce "Shikenan" dan a duniya idan da mutumin da ta tsana bai wuce Hajiya Zainab ba, saboda rashin mutunci da wulaƙancinta. Fadila ta zuba wa wayarta ido, tun da garin Allah ya wayez tayi salla tayi wanka a ɗakinta ta karya, ta koma kan gadonta ta naɗe take chatting tana game, gaba ɗaya ba ta jin daɗin komai, ta rasa meye yake mata daɗi, Khalil baya nan, ta saba ko baya nan sukan yi chatting amma yanzu taga last seen ɗinsa ya kai 3days,taga alamar kamar ita ma haushinta yake ji. Ta gaji da latsa wayar, ta ɗauko litattafanta ta fara karantawa, ta tsinci kanta da duba ire iren rubutun da Yazid kan yi mata a cikin littafi. Tayi ajiyar zuciya ta cigaba da karatun ta. Hajara yau naɗewa tayi taƙi yin aikin komai, wai mura ce take nuƙurƙusarta, dan haka ba zata iya aikin komai ba, ta barwa Amina aikin gida gaba ɗaya, sam hakan bai dami Amina ba, yadda zata ga Daddy ta bashi haƙuri ne ya dameta. Bayan girkin rana da tayi na duka gidan, ta koma ta ɗora faten wake da dankalin turawa saboda Alhaji Ahmad. Ta tsara masa abinci, sai dai ta shiga zullumin karta kai masa ya yi mata wulaƙanci, tun da fushi yake da ita. Ta fara zuba na Baba ta kai masa, sanan ta kaiwa Fadila nata ɗakinta, ta  tarar da Fadilan na toilet tana alwala, ta kalli yadda ta baza liatattafai a kan gado, kamar wata 'yar Nursery. Ta kalli wani rubutun larabci, da ke rubuce a wani littafi da yake a buɗe. Amina ta karanta larabcin, kasancewar Amina tana jin larabci kaɗan-kaɗan ya sanya ta fahimci rubutun na soyayya ne, daga ƙarshe ya rubuta sunansa Yazid. Ɗan shiru Amina tayi tana tunanin a ina ta san wannan sunan na Yazid, jin alamun buɗe ƙofar banɗakin ya sanya Amina saurin ficewa daga ɗakin. Amina, Tana fitowa taga fitar Alhaji Ahmad, ɗan dafe kanta tayi tana tunanin ina za shi haka bai ci Abinci ba, amma jin ana sallar azahar, ya sanya ta ce ko masallaci za shi. Ta koma ɗakinta tayi wanka, tayi sallar azahar ita ma, ta canza kaya ta gyara jikinta. Cikin sa'a da ta kuma fitowa, taga ya dawo, sai dai fuskar nan tasa babu annuri sam, ya wuce sashinsa. Da sauri ta koma Kitchen, ta haɗo kayan Abinci a tray, har da favorite fruits ɗin sa, ta nufi falonsa tana Addu'a. Sallama ta yi, amma ta ji shiru ba a amsa ba, tayi addu'a ta shiga, tana fatan Allah ya sa yana falon. Aikuwa ta hangoshi kwance a kan 3seater, idanunsa a rufe. Ta ƙarasa gabansa ta ajiye trayn a ƙasa. Ta miƙe ta kalli in da yake kwamce ta ce "Daddy"  ya buɗe idonsa ya kalleta. "Ga Abincin rana na kawo maka" ya jinjina mata kai ya mayar da idonsa ya rufe. Amina ta zauna a kan gwiwowinta a hankali ta fara magana "Daddy ka tashi ka ci Abincin" Ba tare da ya buɗe idonsa ba ya ce "Ki bar shi a wurin zan ci" A ɗan marairaice ta ce "Dan Allah ka tashi zaune" sake buɗe idomsa yayi, ya tsareta da ido wanda sai da ya sanya ta sunkuyar da kanta ƙasa. A hankali ya tashi zaune, ya kalli agogon hannunsa, ya fara shirin tashi tsaye, da sauri Amina ta ce "Daddy Abincin fa?" "Ki bar shi a nan, ranar Alhamis in Allah ya kaimu, ki shirya da wuri, Zakiru zai kai ki ƙauye" Kan ya tashi tsaye, Amina ta ƙarasa gabansa a kan gwiwowinta ta ce "Dan Allah Daddy, kayi haƙuri, na san ban kyauta ba kana fushi da ni, dan Allah kayi haƙuri" Kallonta yayi ya ce "Laifin me ki ka yi mini kike bani haƙuri?" "Daddy na maka laifi mana, baka cancanci in maka magana a yadda nayi maka ba, raina ne ya ɓaci sosai, amma ban kyauta ba, dan Allah kayi haƙuri ba zan sake ba" Ya ɗan girgiza kai ya ce "Hmmm" "Dan Allah kayi magana, duk na damu da laifin da nayi maka, kayi haƙuri" "Shikenan ya wuce" "Ka haƙura?" "Eh ya wuce" Ta ɗan marairaice fuska ta ce "kamar ba ka haƙura ba fa" Ba tare da ya kalleta ba ya ce "Meyasa kika ce haka?" "Haryanzu ranka a haɗe yake fa" "To ai bani da lafiya ne, amma nace miki ya wuce ai" Cikin damuwa ta kalleshi ta ce "Jikin ne haryanzu? Sannu Allah ya baka lafiya" Ya amsa da Amin. "To in zuba maka Abincin?" Ya jinjina mata kai. Ta zuba masa Abincin a plate ta saka cokali ta miƙa masa. Ya karɓa ya kalleta ya ce "Zauna a nan yayi maganar tare da nuna mata kusa da shi a kan kujera. Ɗan turus tayi tana ganin rashin dacewar hakan. Amma kasancewar shiri take nema, haka ta tashi ta zauna a kusa da shi. "Amina?". "Na'am Daddy" "Banji daɗin abin da ki ka yi mini ba, kema kina cikin masu mini kallon anfi ƙarfina a gidana ko? Duk abin da nake yi, ina da dalili ina ƙoƙarin baki kariya, bana son ki bar gidan nan karatunki ya samu matsala, amma saboda yadda nake da ke kika kalli tsabar idona ki gaya mini magana haka ko Amin? Da wani ne ya mini abin da kika mini saina hukunta shi, ko da kuwa matar gidan nan ce, amma shikenan. Idan kin dawo daga ƙauye upper week zaku tafi Abuja, before na so inje Abujan nima, in ga competitions ɗin naku, dan sun bani invitation as a special guest, amma I don't think zan samu zuwa" Hawaye ne ya cika idon Amina ta ce "Dan Allah Daddy kayi haƙuri, gaba ɗaya na san ban kyauta ba, amma ba Baba ba, ko kai na gani wani ya maka haka sai inda ƙarfina ya ƙare, Matarka da 'yarka sun tsani Baba, ban san me yayi musu ba, wallahi ko dukana za suyi ba zan damu ba a kan su ci mutuncin Baba, ina jin zafi a raina, amma dan Allah Daddy kayi haƙuri, ba zan sake ba" Ya kai lomar abinci bakinsa ya haɗiye, sannan ya ce "Ba komai ya wuce" "To amma naga haryanzu ka haɗe rai" "Abubuwa da yawa suna damuna, ga kuma yanayin jikina dan haka am not in mood, ai nace ya wuce" Cikin damuwa ta ce "Sannu Allah ya baka lafiya, Daddy kaje Asibiti" Ya ce "Zaki rakani?" Ta ɗaga masa kai alamar eh. Ya cigaba da cin abinci, can kuma ya ce "Yauwa, idan zaki tafi ƙauyen me kike ganin za a saya ki kai musu?" "A'a ba sai an sai musu komai ba" Amina ta faɗa tana ƙoƙarin zuba wa Daddy ruwa. "Idan zaki tafi ƙauye, me kike ganin ya dace a sai musu?" Ya kuma maimaitawa, hakan ya tabbatar mata he is serious. Ta ce "Lemo da ayaba" Ɗagowa yayi ya kalleta ya ce "Dubiya zaki je ko kai ziyara?" "Ziyara" "Kuma sai ki kai musu lemo da ayaba?" Amina ta tura baki ta ce "To ni me zance?" "Idan ina magana kina cewa ke me zaki ce, zamu ɓata" "A'a na daina, bana son mu kuma ɓatawa, in muka ɓata ba na jin daɗi" Murmushi ya yi ya ce "Are You serious?" Ta ɗaga masa kai alamar eh. "To shikenan, ki daina mini abin da zamu yi faɗa" "In Allah ya yarda na daina Daddy, amma zaka zo wurin taron namu na Abujan?" Daddy ya ce "Babu tabbas" "Dan Allah Daddy ka zo, ko ba ka haƙura ba haryanzu?" "Ai nace miki ya wuce" "To shikenan, na gode sosai, Baba da kansa yayi mini maganar zuwa Abujan, Allah ya biyaka da Aljanna Daddy, in Allah ya yadda ba zan baku kunya ba, zan yi abin da ya dace" Yayi murmushi ya ce "Allah ya sa, bayan sallar la'asar ki shirya, zaki rakani ganin likita" Ta miƙe tsaye ta ce "To, amma me zance wa Baba?" Ya miƙe ƙafafuwansa ya ce "Baba baya nan a lokacin" "Ina za shi?" Daddy ya yamutsa fuska ya ce "Tambayoyinki sun yi yawa" "To yi haƙuri, na tafi". Ya jinjina mata kai, tare da lumshe idanunsa" Ta juya da tray ɗin Abincin ta fita. A falo tayi kiciɓus da Hajara, Hajara ta dubeta ta ce "Amina daga ina haka?" "Kaiwa maigidan nan Abinci" Hajara ta waro ido waje ta ce "Ikon Allah, da kika kai masa kuma shi ne kika zauna kika jira ya gama kika fito da kwanukan, ni fa na zata ma ba kya nan, tun ɗazu nake falon nan ban ga gilmawarki ba" "Hajara, na kai masa na rana, sai ki kai masa na dare kema" tayi tsaki ta wuce, dan ta fara ƙuluwa da shegen sa idon da Hajara take yi mata. Amina na tsaye a gaban mudubi, ba wata kwalliya tayi ba, amma tayi kyau sosai, wata doguwar rigar abaya ta saka, wadda Babar Azima ta kuma aiko mata da ita, ta ɗan gyara fuskarta tayi tsaf da ita, ta riƙo wayarta a hannu ta fito falo. Ko da ta fito ta tarar da Daddy a tsaye yana jiran fitowarta. Kashe mata ido ɗaya yayi ya ce "You look beautiful in this outfit" Murmushi Amina tayi ta ce "Thank you Daddy" Hajara da ta daskare a wuri ɗaya, har ƙara leƙa fuskar Daddy take, dan ta sale tabattarwa kanta abin da take gani ba mafarki bane ba, babban abin da yake sake ɗaure mata kai, wanzuwarta a wurin ba ta sanyawa su bar abin da suke yi, bata ƙara tsinkewa da lamarin ba, sai da taga alamar fita zasu yi tare. Corridor dake cikin sashin Hajiya Zainab Hajara tabi, ta leƙa dan akwai taga da take kallon wurin parking space, aikuwa idanunta suka dake gane mata Alhaji Ahmad ya buɗewa Amina gaban motarsa ta shige, shima ya zagaya ya shiga ya kunna motar. Fita tayi da sauri ta nufi falo, taji tamkar taje ta kira Fadila ta ce ta zo taga cin amanar da akewa babarta, amma ta tuna Fadila ta tuna halinta na rashin mutunci, dan a 'yan kwanakin nan ta hanata zuwar mata ɗaki ma gaba ɗaya, Amina ce kawai ke kai mata Abinci idan na zata ci a dining ba, ko kuma gyara mata ɗaki. Fadila na kwance a kan gadonta kamar mai ciwo, tana chatting a Instagram tana taya wata riga, notification na what's app ya shigo wayarta. Komawa tayi what's app ɗin dan duba meke faruwa, saboda taga an yi maganganu da yawa a what's app group ɗin su na makaranta. Da saƙon Captain ta fara cin karo "Yau na haɗu da wani abokina wanda ya san Yazid, ya ce Yazid na Asibiti babu lafiya sosai, ku sa shi a adduoinku Please" "Innalillahi wa innalillahi raji'un" MASU BUƘATAR SHIGA VIP GROUP, KU TUNTUƁENI TA LAMBAR WAYATA AYSHERCOOL 08081012143GABA DA GABANTA BY AISHA ADAM AYSHERCOOL AFUWAN NOT EDITED 42 "Innalillahi wa innalillahi raji'un, shine abin da Fadila ta dinga maimaitawa, take taji jikinta ya hau rawa bugun zuciyarta ya ƙaru, tana daga kwance amma ta dinga jin kamar  jiri na kwasarta. Babu abin da ta hango sai lokacin da Yazid yayi wannan faɗuwar har ta kai shi Asibiti, da ƙyar aka iya ceto ransa. Da ƙyar taja jikinta ta tashi zaune, ta ciri lambar Captain daga what's app group ɗin, ta kirashi. Captain na ɗagawa yayi mata sallama "Assalamu alaikum" "Wa'alaikum salam, Captain Fadila ce" Captain ya ce "Ahh, babar yarinya ai na ɗauki muryarki" "Yauwa, naga posting ɗinka a group ne, meya sami Yazid ɗin ne? Kuma yana wani Asibitin?" Captain ya ce "A gaskiya ban sani ba, dan ke Yakamata mu yiwa wannan tambayar dan fi kowa kusanci da shi, wani abokina ne muka haɗu, muna hira har hirar ta kawo zancen Yazid ya ce mini ko ya sanshi a ina ne na manta, wai yaji ance an kwantar da shi a Asibiti babu lafiya" Fadila ta ɗan jaa numfashi ta ce "To dan Allah Captain ka ɗan bincika mana, sannan ka turo mini lambarsa" "Kaii Fadila, kina nufin baki da lambarsa?" Fadila ta ce "Kai dai ka bar wannan maganar, ka turo mini" "Shikenan ina zuwa" suka yi sallama, ta zauna tayi shiri tana cigaba da tunanin halin da Yazid ke ciki. Tana nan zaune Captain ya tura mata lambar Yazid, nan da nan tayi saving ta kirashi a wayar, amma wayar a kashe, duk da haka ba ta haƙura ba ta sake gwadawa, amma still a kashe bata shiga. Fadila ta ajiye wayar, tana jin tamkar ita ce bata da lafiyar, dan yana ɗaya daga abin da ya sanya ta fara tausayin Yazid har take sakar masa fuska, tunawa da irin yanayin da yake shiga saboda larurarasa. Ya bata tausyi matuƙa lokacin da ciwon ya tashi. "Wai ya saunan wannan kwalliyar ne?" Daddy yayi maganar yana kallon Amina. Murmushi Amina tayi ta ce "Ni ina yi wata kwalliya, kwalli kawai na saka da man leɓe" "Aikuwa gaki nan kin yi kyau sosai, ko mu tsaya wurin saurayin naki ne ya ga kwalliyar, Bilal yake kowa?" Amina ta ce "Ba fa saurayina bane, gaisawa kawai muke" "Au haba?" Daddy yayi maganar cikin sigar bugun cikinta. "Wallahi da gaske nake maka Daddy" "Hmm ke baki da saurayi ne?" "Samarina duk suna ƙauye, kuma na fara yin saurayi a birni, amma kace kar in kuma kawo maka kowa gida, ni yanzu ba ta samari nake ba, karatuna ne ya dameni" Daddy ya ce"Yauwa yarinyar albarka, your studies supposed to be your first priority, ki mayar da hankali idan mace tayi ilimi tafi daraja". "Haka ne, tun da Daddy ya tsaya mini, zan yi karatu sosai in Allah ya yarda" "Yauwa, idan kika gama karatun, da saurayin da mijin ni zan samo miki" "Kai dama ana haka?" "Eh mana za kuma ki gani" Amina tayi murmushi tana kawar da kai cike da jin kunya. Wani katafaren Asibiti suka isa, gini da tsarin Asibitin kamar ba Nigeria ba. Daddy yayi parking suka fito shi da Amina, duk in da suka ratsa manyan mutane ne sai gaisar da Daddy suke yi, alamu suka sake tabattarwa da Amina, ba ƙaramin mutum ne ba Daddy. Suna zuwa akaa yiwa Daddy iso zuwa wurn babban likitan mamallakin Asibitin, wani ba indiye. Yana ganin Daddy ya faɗaɗa faa'arsa alamu ya nuna dama sun daɗe da sanin juna. Amina ta gaishe shi da harshen turanci, ya amsa mata, sai da suka ɗan taɓa hira da Daddy, sannan Daddyn ya yi masa bayanin abin da yake damunsa. "Ai na gaya maka lafiyarka ƙalau, kwanciyar hankali kake buƙata ka cire damuwa ka samu isasshen hutu, sannan ka ƙara kulawa da abincin da zaka ci, shi ma sugan ya sauka, lafiyarka ƙalau" Daddy ya kalli Amina, ya ɗan marairaice fuska ya ce "Meenalin Daddy, kin ji abin da Doctor ya ce wai lafiyata ƙalau, kin yadda lafiyata ƙalau?" Amina tayi murmushi ta ce "Tun da Doctor ya faɗa haka ne mana, Allah dai ya ƙara lafiya da nisan kwanax Shima murmushin ya yi ya ce "To Amin, yanzu meye abin yi?" Likitan ya gyara zama ya ce "Abin yi dai shine ka kula da shawarwarin da na baka, sanannan ka dinga motsa jiki, ka rage cin daɗi, ka samu isashshen hutu, ka dinga abubuwan da zasu ɗebe maka kewa shikenan, ba zan rubuta maka magunguna da yawa ba" "To shikenan, na gode sosai, Allah ya sa mu dace" Amina ta ce "Shikenan, tsalle-tsalle da guje guje sun kama ka, idan naga kana yi ni video zan maka" tayi maganar tana dariya. "Ai tare zamu dinga tsalle-tsalle da gujegujen, sai kiji daɗin yin video" Haka suka cigaba da hirarsu cikin nishaɗi, likiya ya sallamesu, suka hau mota suka tafi. Suna tafe a hanya Daddy ya ce "Ko mu tsaya ki sha ice-cream?" Amina ta girgiza kai ta ce "A'a ni dai mu tafi gida, kar Baba ya dawo bana nan, idan ya tambayeni ina naje ban san me zance masa ba". "Aminatu, Baba ba zai ce komai ba, kuma har mu koma ba zai dawo ba, bari in sayo miki ice cream" Da sauri ta ce "A'a Daddy, kaga ba lafiya ce da kai ba, kuma ka bani chocolate da yawa ranar, ina da su kar ka wahalar da kanka" yi yayi kamar bai jita ba, yayi parking a bakin wani wurin sayar da kayan ƙwalam da maƙwalashe, ya sanya facemask ɗinsa, dan ɓatar da kama, ya fita daga motar. Amina dai kamar a kan ƙaya take, babban burinta kawai ta gansu a gida. Bai wani jima ba ya dawo da wata babbar leda, ya ajiye mata a kan cinyarta. Ta kalleshi ta kalli ledar za tayi magana ya ce "Shhh, kar in ji komai" Ta ɗan marairaice ta ce "Amma Daddy..." Ya ɗan tsuke fuska ya ce "Nace bana son jin komai fa" Amina ta gimtse maganar da take shirin yi, ta ɗan kalli Daddy tana murmushi. Shi ma murmushin ya yi mata sannan ya ɗora da cewa "Idan Allah ya kaimu Monday, zan aika a ɗaukeki a kaiki banki, su buɗe miki account, sannan yakamata ke ma ki yi sayayya abubuwa da zaki amfani da su saboda tafiyarku Abuja, musamman kayan sawa, dogayen rigunan nan naga kina san su sosai, kuma suna miki kyau, amma naga Atamfa ma tana miki kyau" "Daddy" "Yes" ya amsa tare da kallon wurin da take zaune. "Idan aka tambayeni waye yake bani wannan abubuwan me zance?" "Waye zai tanbayeki?" "Baba mana ko mutan gidan" "Mutanen gida babu wanda zai tambayeki ina kika samo kaya, Baba ma haka, na baki amsa and keep your mouth shut" haka Amina tayi shiru tana zancen zuci. Har zuwa bayan sallar magariba, Fadila na dakon wanda zai ce gashi yaje inda Yazid yake duba shi, sai ma ƙorafi da 'yan ajin suka dinga yi a kan cewa babu wanda ya san gidansu, kuma lambar wayarsa ba ta shiga sam. A layi Daddy ya sauke Amina, dan yana tunanin ko Hajiya Zainab ta dawo, Amina tayi mamakin rashin ganin Baba a bakin gate, a 'yan kwanakin nan tana mamakin in da Baban yake zuwa. Hajara dake Kitchen taga gilmawar Amina da leda, saura ƙiris ta yanke da wuƙa saboda son ganin ƙwaƙwaf, ta yasar da abin da take tabi bayan Amina tana ƙwala maga kira. "Amina! Amina!!" Amina ta tsaya ta waiwayo ta ce "Lafiya?" "A'a lafiya lau, ina kuka je ne haka ke da Alhajin, na ganki da uwar leda haka, ina kuka je?" Amina ta kalli Hajara rai a ɓace ta ce "Yana sashinsa, zaki iya zuwa ki tanbayeshi, zai fi baki amsa yadda yakamata" Hajara ta haɗe rai ta ce "Ke Amina, kar mini rashin kunya mana" "Hajara wace irin rashin kunya, da muka fita da mutumin nan kin san ina muka je, ana ta shirin tafiyarmu Abuja ne, kuma Yanzu tare kika ga mun dawo da zaki titsiyeni da wasu maganganu na daban" Hajara tana jinjina yadda Amina ta ƙware a iya rainin hankali, da sauya zance, amma ta basar ta biye mata ta hanyar cewa "Wannan ledar a makarantar aka baku kenan, bari in zo a kwanceta da ni" Banza Amina tayi mata tana tunanin yadda za tayi maganin Hajara da saka idonta. Abdul ya kira wayar Khalil har ya gaji, baya ɗaga wayar, har ya fara tunanin ko wani abun ne ya samu Khalil ɗin. Ba tsammani yaga kiran Khalil ya shigo wayarsa, ya ɗaga wayar yayi sallama, Khalil ya amsa sannan ya ɗora da cewa "Abdul yakake?" Abdul ya ce "Dalla ware, kawai ka kashe wayoyinka, na kiraka na kiraka ka ƙi ɗaga wayata". Khalil ya ce "Yi haƙuri, bani da lafiya ne" "Ya salam menene ya sameka?" Khalil yayi ajiyar zuciya sannan ya ce "Bari kawai Abdul, tun da na baro gida da ƙyar na samu Hafsa ta ɗaga wayata sau ɗaya, itama ashe babu lafiya, yarinyar nan ta tubure, da gaske take ba zata aureni ba" ya ƙarasa maganar cike da damuwa. Abdul ya ce "Dama banda abin ka Khalil, ka sawa ranka salama a kan yarinyar nan, mahaifiyarka bata so. Kuma dan shirme ka koma wurin aiki baka sanar a gida ba, sai da na mayar da motarka sannan suka sani, baka ga faɗan da Mummy tayi mini ba" "Abdul ba zaka gane bane, gaba ɗaya Mummy bata damu dani ba, ta tatarani ta watsar da ni, ko kiranta nayi na gaisheta sai dai mu ƙare babu daɗi tayi ta mini faɗax. "To ai haƙuri zaka yi, tun da ta nuna bata son abu kayi haƙuri da shi kawai" Khalil ya ɗan numfasa sannan ya ce "A zahiri na rabu da Hafsa, amma zuciyata ga kasa Abdul, ka san me ma Mummy ta ce? Wai ba zan zaɓi matar da zan aura ba sai wadda ta zaɓa mini" "Khalil, ni dai babu abin da zan iya ce maka, sai dai kayi haƙuri, iyayenmu ba zasu taɓa zaɓa mana abin da zai cutar da mu ba, sannan dolenka kayi haƙuri ka cigaba da yi mata biyayya, komai zai wuce in sha Allah" Khalil ya ce "Kaga ni ba wannan ba, dan Allah so nake kaje ka duba mini ita" "Khalil, ba zaka haƙura da batun Hafsa ba ko?" "Ba haka bane ba, ni dai dan Allah kaje ka duba mini ita" "Shikenan, naji zanje in Allah ya yarda" Khalil ya ce "Yauwa na gode sosai, dan Allah idan kaje ka haɗani da ita" Abdul ya ce "Shikenan, zanje in sha Allah". Sai wuraren ƙarfe tara na dare, sannan Hajiya Zainab ta dawo gida, ta sha hidima duk ta gaji, tayi wanka ta rama sallolin da bata samu yi ba, ta fito falo ta bawa Amina umarnin dafa mata indomie da tea ta kai mata sashin Daddy. Ganin tun da ta dawo Fadila bata fito ba, kuma rabon da ta ganta tun kan ta fita da ga leƙa taga tana bacci, ya sanya ta tafi ɗakin Fadila. "Autar ko nemana ma ba kya yi ko?" Fadila data mayar da hankali a kan litattafanta a zahiri, wanda a baɗini tunani ne fal ranta, ta ɗago ta kalli Mummy ta ce "Mummy kin dawo?" Mummy ta ce "Eh mana na dawo, amma ko kizo ki mini sannu da zuwa" Fadila ta ɗan yamutsa fuska ta ce "Mummy karatun exams nake ne, mun kusa farawa" "Amma dai dan kizo ki ganni kawai, shikenan Allah ya bada sa"a ya karatun?" "Alhamdilillah" "Fadila na so kin rakani wurin bikin nan, mates ɗinmu duk da yaransu wasu suka je, gwanin sha'awa ke kuwa ba kya son shiga mutane sam, sai kace daddawar sata kullum kina ƙule a ɗaki" "Mummy, ni kin san bana son abin hayaniya ne gaba ɗaya, gara in zauna a gida in karatuna" "Aishikenan, amma dai ai gara ki dinga shiga mutane, da haka ake sabawa, wai ni ya na ganki duk wani iri ne, meke damunki?" "Mummy me kika gani?" "Kamar ya me na gani, gaba ɗaya mood ɗinki ya canza yayi wani iri" Fadila ta ce "Kawai gajiya ce Mummy" "To ki dinga hutawa kanki dai, bari inje in ci Abinci" ta tashi ta tafi sashin Alhaji Ahmad, ta tarar da shi yana aiki a system. "Sannu da gida" ta faɗa tana zama a kusa da shi. "Yauwa sannu da zuwa ya hanya?" "Lafiya lau, ya jikina naka?" Ya ɗan kalleta ya ce "Ina ruwanki da ya jikina, da kika iya ficewarki kika barni" Tsuke fuska tayi ta ce "Zaka fara ko?, Yanzun da naje na dawo meye ya sameka nifa bana son neman rigima daga dawowata Yanzu" Girgiza kai kawai yai ya ce "Ba zaki camza ba Zainab" "Eh ba zan canza ba ɗin, yauwa ni dama ina son muyi magana, ina son ka ƙara mini jari ne" Banza yayi mata ya cigaba da aikinsa. "Sweetheart magana fa nake maka" tayi maganar tana kashe murya. Still bai kulata ba, ta sanya hannu ta saƙalo kafaɗarsa ta ce "Talk mana" Amina tayi sallama hannuta riƙe da kular Abinci da teaflask. Gabanta ne ya faɗi da taga Daddy tare da Hajiya Zainab, wani abu taji yana ƙoƙarin taso mata. Innalillahi wa innalillahi raji'un tai ta maimaitawa a ranta. Ta ajiye ta ce "Bari in kawo miki kofi da plate" tayi maganar muryarta har sarƙewa take yi, ta juya ta bar ɗakin. Murmushi Alhaji Ahmad ya yi, dan ya lura da halin da Amina ta shiga. "Wai ya naga kana murmushi ni kuma kaƙi kulani?" Ya ce "To ba ina jinki ba" "To kayi Magana" "Me kike son ince miki, wato bani da wani amfani a wurinki sai lokacin da kike buƙatar kuɗi ko wani abu a wurina ko?" "Haba dai, ba haka bane taimakawa zaka yi Please Baban Khalil" tayi maganar tana sake shigewa jikinsa. Amina ce ta kuma dawowa, yanzu ma kanta a ƙasa har da tuntuɓenta. Alhaji Ahmad na ganin haka ya rungumo Hajiya Zainab ya ce "Nawa kike so?" Gyar zama tayi tana murmushi cike da duniyanci ta ce "Ni ko million uku ce, wasu sarƙoƙi zan order da takalma" Ganin Amina taƙi kallonsu, kuma tana ƙoƙarin tashi ta tafi, ya sanya Daddy ya ce "Buɗe fridge ki bani coc" Kallon Daddy tayi da sauri, dan daga dokokinsa da aka saka masa an hana shi shan lemukan nan. Yana ganin ta kalleshi, ya kashe mata ido yana kuna rungume Hajiya Zainab, Amina bata san lokacin da ta watsa masa wata uwar harara, ta nufi fridge ɗin, maimakon ta ɗauko masa coc sai ta ɗauko masa ruwa. Daddy ya ce wa Hajiya Zainab "Zan duba inga nawa zan baki, amma ba wannan watan ba" "A'a gaskiya ni yanzu nake so" Ya ɗan tsuke fuska ya ce "Bafa na son rigima" Ko da Amina ta kawo ruwan dire masa tayi a wurin, ta fice daga falon, Ba tare da ta kuma ko kallonsu ba. Gaba ɗaya haka Amina ta dinga jin ranta babu daɗi, musamman da Amina ta lura da gayya yayi, dan ya bata haushi. "To ma ni ina ruwana" ta faɗa cike da basarwa. Abu kamar wasa Yazid ya kwashi kusan kwanaki bakwai bai zo makaranta ba, kuma babu wanda taji ya ce gashi ya san ga a halin da Yazid yake, ta san ba ƙaramin abu ne zai hana shi, zuwa makaranta ba, ta so tayi zancen da Yusra amma ta san halin Yusran, yanzun nan zata fara kawo mata wasu zantukan na banza da zasu ɓata mata rai. Gefe guda ga Kankiya ya addabi rayuwarta, ta so ta yiwa Mummy zancensa, but she knows what she can do, Mummy bata ɗaukar al'amura irin wannan da sauƙi, ba ta ƙi ta rufe kanta taje ta sameshi ta yi masa tatas ba a kan Fadilan, koma ta kunno masa wutar da ba zai iya kashewa ba, wanda ita kuma Fadila ba ta son hakan, dan haka ta sak duk lambobinsa a blacklist, yadda ba zai iya samun damar kiranta b, amma ya canza lamba ya cigab da uzzura mata. Gaba ɗaya Fadila a yanayin Activities ɗinta zaka gane cewar tana cikin damuwa, amma ta ƙi gayawa kowa meke damunta. Amina tana kallon saƙonnin Daddy, yana mata magana amma ta shareshi, dan haka kurum haushinsa take ji. Kamar yadda Khalil ya buƙata, Abdul ya je gidansu Hafsa domin dubata, sai dai ya tausaya mata, ta rame tayi zuru-zuru, suka gaisa cikin mutuntawa, Sannan ya ce "Dama Khalil ne ya ce in zo in duba masa ke, wayarki ta daina shiga gaba ɗaya" Hafsa ta ɗan yi shiru sannan ta ce "Yaya Abdul, dan Allah ka dinga gayawa Khalil gaskiya, ka nuna masa muhimmancin yiwa iyaye biyayya, mahaifiyarsa ta nuna ba ta son alaƙarmu, har wurin sana'ata suka ,o ita da wasu, a kan in rabu da shi mai zai sa ya cigaba da dagewa a kan lallai sai mun cigaba da alaƙa?" Abdul ya numfasa ya ce "Haka ne Hafsa, kuma nima kaina ina gaya masa, sai dai kiyi masa uzuri tun da na san Khalil ban taɓa ganin macen da Khalil ya nuna ya ce ga budurwarsa ba sai ke, duk da ana nuna ana son sa, a kanki ya fara cewa wannan mace ce da tayi mini nake son na aura, dan haka abin zai masa wuya rabuwa da ke lokaci ɗaya, shima yana can ba shi da lafiya, amma Hafsa ku cigaba da addu'a, idan da Alkhairi sai kiga kun yi auren" "Anya Yaya Abdul? Kamar yadda mahaifiyarsa ta faɗa ni ba tsarsr aurensa bace, haka ne ni ɗin ban dace da shi ba, ko ya aureni ba zanji daɗin zama cikin family ɗinsu ba" Abdul ya ce "Ai shi lamarin Allah, ba ruwansa da wani yana so wani baya so, idan ya ƙaddara abu zai yiwu sai ya yiwu, ki cigaba da Addu'a, Amma Khalil ma yana cikin wani hali, kiyi masa Addu'a" Jiki a sanyaye ta ce "Allah sarki Khalil, mutumin kirki ne zan cigaba da yi masa da Addu'a". Abdul ya ce "Bari in kirashi ku gaisa" tayi saurin girgiza masa kai ta ce "A'a na samu nutsuwa kwana biyu, idan muka yi waya zan kuma shiga damuwa" tayi maganar idonta fal hawaye. Wani irin tausayin su ne ya kama Abdul, sun shaƙu da juna, Mummyn Khalil ba ta da tausayi kanta kawai ta sani. Abdul ya cigaba da rarrashin Hafsa, ya shiga har gida ya gaida Maman Hafsa, yayi musu alheri sai dai da ƙyar ya samu suka karɓa ya tafi. Amina tana ta shirya kayanta da wuri, saboda tana ɗokin zuwa ganin gida, ranar Litinin da safe, bayan Daddy ya idar da sallar asuba bai dawo gida ba sai ƙarfe shida saura, saboda ya tabattar a wannan lokacin zai ga Amina, tana aikin gida saboda zata tafi makaranta. Aikuwa yana zuwa ya tarar da ita da duku-dukun nan tan mopping a falo. Wutar falon aka kashe, hakan ya sanya ɗakin ya gauraye da duhu, da sauri ta waiwaya dan ganin meke faruwa. Taku taji ana tunkaro in da take, sai dai ko ba a gaya mata ba, ƙamshin turarensa ya sanar mata da shi ne. Sai da ya zo in da take sannan murya ƙasa-ƙasa ya ce "Good morning" Shiru tayi taƙi Magana. "Am talking fa, kuma kina jina" Cikin basarwa da shagwaɓa ta ce "To meye yasa zaka tsorata ni?" "Saboda abin tsoron baya baki wahala ko? Wai me nayi miki ne kike wani fushi da cin magani?" "Ni ba fushi nake ba" Yayi murmushi, ya sake sunkuyowa daidai tsawonta har tana jin numfashinsa a wuyanta ya ce "Faɗi gaskiya dai, idan ba fushi kike ba, meye na ignoring messages ɗina, ko dai ko dai?" "Ko dai me?" Ta faɗa a tsorace saboda yadda jikinta yayi sanyi. "You are jealous dear, stop pretending" Kunna wutar lantarkin falon da aka yi ne, ya sanya su ɗagowa. DOMIN SAMUN POSTING KULLUM GARZAYO KI BIYA KUƊIN VIP, KU TUNTUƁENI TA KAN LAMBAR WAYATA AYSHERCOOL 08081012143.GABA DA GABANTA BY AISHA ADAM AYSHERCOOL AREWABOOKS AYSHERCOOL7724 WATPAD AYSHERCOOL7724 43 Gaba ɗaya suka waiwaya dan ganin waye haka? Gaba ɗaya hankalin Amina ya riga ya gama tashi, Hajara ce a tsaye a wurin makunnin ƙwan, ganin duk suna zuba mata ido kuma sai ta hau kame-kame tana faɗin "Amm.... Ban san.." Ɗauke kai Daddy yayi daga kallon in da Hajara take, ya mayar kan Amina ya yi ƙasa da muryarsa ya ce "Karki manta anjima zan aiko a kai ki banki, a buɗe miki account" Noƙe faɗa tayi ta ɗan tura baki ta ce "Ni ba zani ba" "Me kika ce?" "Bakomai" ta faɗa taka sake tura baki. Murmushi ya yi ya wuce sashinsa, Amina ta cigaba da mopping ɗin ta suka mayar da Hajar daidai da kujerun da suke falon. Gaba ɗaya Hajara rasa abin yi tayi, a baya tunane tunanenta sun fi karkata ga zargi, amma a yau ta sake tabattar da abin da ke tsakanin Alhaji Ahmad da Amina wata alaƙa ce mai ƙarfi da girman gaske, wadda da alama alaƙar tayi ƙarfi sosai da sosai. Kamar yadda Daddy ya ce, da kansa yaje makarantar su Amina, bayan an tashi sukaje banki, aka yi mata duk abinda yakamata, ya saka kuɗi a ciki naira dubu ɗari biyu. Mamaki ne ya cika Amina ta ce "Daddy wannan maƙudan kuɗin me zan yi da su, idan Baba ya gane fa?" Daddy ya ce "Ta yaya Baba zai gane, sai dai idan kece zaki gaya masa, kuma ai ba wasu kuɗi ne masu yawa ba, Zakiru zai kai ki ki sayi duk abin da kike so, ban fiye son shiga wurare bane saboda identity ɗina, ba dan ke ba wurare da yawa ba zan iya zuwansu ni kaɗai ba, kuma ni bana son a takura rayuta duk in da zaka sai da masu baka kariya" "Amma meyasa baka so a ganka? Kar a ganmu tare aje a gayawa Maman su Khalil ko?" Ya ce "Eh, kin san bana son ɓacin ranta da damuwarta" "Eh amma ni kana son ganin nawa" tayi maganar da iya gaskiyarta. "Mhmm, me yasa kike haɗa kanki da ita? Ita matata ce ke kuma" Sai yayi shiru. A ƙule Amina ta ce "Eh ita matarka ce, ni kuma 'yar aiki ba talaka mara galihu" "Yauwa Ashe kin sani, amma ni bance miki talaka mara galihu ba" yayi maganar da salon ya sake kunna Amina. Aikuwa ta kai ƙololuwa dan taji haushi ba kaɗan ba. "Banda rigima irin taki, ina na taɓa ganin wannan ƙarfin hali in ba a wurinki ba, nace kina son mijinta kince me zaki da tsoho". Cikin tsiwa ta ce "Allah ya kiyaye in yi kishi da wannan matar, ta kasheni da bala'i wadda ba ta san darajar ɗan Adam ba" "Zaki fara ko? Ban gaya miki bana so ki dinga duk wata magana da zata shafi matata ba". Amina ta ce "Amma ai kai ka fara bani ba, wallahi Daddy seriously yakamata ka kula sosai, Allah ya baka dukiyar da zaka amfanar da al'umma, amma an gindayeta wuri ɗaya daga ita sai iyalanta, duk wanda ya raɓoka zai mora an dinga yi masa gori kenan da kallon banza, wallahi idan baka gina lahirarka ba daga ranar da ka mutu, wanan dukiyar aka raba musu, su sadaka ma Allah ya kai ladan kabarinka sai wanda ya dubi Allah. Na san naganganuna sun yi tsauri da yawa, amma dan Allah kayi haƙuri Daddy, wallahi gaskiya nake gaya maka. Dan Allah yanzu dan Allah ya baku arziki ya dace aje aci mutuncin 'yar mutane dan Khalil ya ce yana sonta, ba a gabana aka yi ba, amma yadda ya zo yana faɗar zancen naji zafi sosai saboda nima tsatson talaka ce, da na motsa a gidan nan sai kyara da gori, wallahi Daddy kaf mutanen da ke aiki a cikin gidanka suna yi ne dan basu da wata sana'ar da zasu samu su rufawa kansu asiri, ban da haka mai zai sa ka zauna a gabanka ana kiran mahaifinka nusari, soko da sauran miyagun maganganu?" Ta ƙarasa maganar hawaye mai ƙarfi suka ƙwace mata. Ba ƙaramin tasiri maganganun Amina suka yi a zuciyarsa ba, duk da ba wata babba bace ba, amna wasu lokutan tana da matukar hangen nesa da son faɗar gaskiya. Yana jinta tana kukan Amma bai rarrasheta ba kuma bai ce mata komaia ba, har tayi ta gama tayi shiru. Wasa² rashin sanin halin da Yazid yake ciki ya addabi Fadila, tun tana dannewa har ta kasa ya kai ga ta kira Yusra a waya. Ta zayyanewa Yusra duk abin da ke faruwa. Yusra ta ce "To ni yanzu da kika kirani me kike so in yi miki? Da kina da lambarsa ne ma sai a kirashi, ko kuma ki tanbaya a 'yan ajinku ko akwai mai lambarsa" Cikin damuwa ta ce "An bani lambar na kira baya shiga" "Wai to meye duk kika bi kika ɗaga hankalinki?" Fadila ta ce "Haba Yusra, kamar ba a gabanki kinga halin da yake shiga idan ba shi da lafiya ba, ko da yake ke lokacin da kika zo ya farfaɗo, ni da muka kaishi Asibiti ban zaci zai rayu ba, yau fa ina miki maganar yafi sati baya zuwa school, aikuwa duk abin da zai san ya yaƙi zuwa makaranta ba ƙaramin abu bane ba" "Na gane, yanzu dai ki kwantar da hankalinki, ki cigaba da Addu'a Allah ya sa yana lafiya, da an san ko unguwarsu ne ma da anje an tambayi in da gidansu yake" Fadila ta ce "Ni banji wanda yace ya san unguwarsu ba, shikenan dai sai anjima" ta ajiye wayar tare da dafe goshinta, gaba ɗaya tana cikin zullumi. Khalil dauriya kawai yake yi, ko yaje zuwa wurin aiki sai dai baya iya wani abin kirki, lamarin Hafsa ha tsaya masa a rai nesa ba kusa ba, yana matuƙar sonta da tausayinta, baya son ta faɗa hannun wanda bai san ƙaddara ba, tsananin yardar da tayi da shi ne ya sanya ta gaya masa wani babban sirri na rayuwarta, da baga gayawa kowa ba sai shi, yanzu gashi Mummy ta shiga ta fita, yanzu da wani ta gayawa wannan sirrin ba shi ba, ha zamana kuma bai aureta ba, shikenan haka zai ta kallonta da abin koma yayi ta yaɗawa a gari. Duk shirin da Amina take yi na zuwa ƙauye, da hidmar da take tayi da kuɗi babu wanda ya tambaye ta ina ta samu kuɗi, hatta wayar hannunta da aka wayi gari aka ganta da ita, Hajiya Zainab bata tuhumeta a ina ta samo ba, sai tsananin saka idanu da take fuskanta daga wurin Hajara. Ita kuwa Fadila abin da ya dameta daban dan baka ba ta Amina take yi ba, dan idan ta ga dama sai ta wuni a ɗaki bata fito ba balle su haɗu. Musamman da aka tashi daga makaranta, Amina ta tafi gidansu Azima, mamansu ta sa aka kaita wurin masu gyaran kai, aka wanke kan aka yi mata kitso ƙanana masu kyau, aka yi mata lalle ja da baƙi, sai bayan la'asar ta dawo daga gidansu Azima. 'yan kwanakin nan Daddy ya auri zaman falo, saboda kawai ha dinga ganin Amina, yana zaune shi da Hajiya Zainab Amina ta shigo gaba ɗaya ya mayar da hankalinsa kan Aminar, ba tare da Hajiya Zainab ta lura ba. Amina na zuwa ɗakinta ta ajiye jakar makaranta, ta tsaya a gaban mudubi tana kallon kyan da kitson kanta yayi. Wayarta dake kan mudubi ce tayi vibrating. Ta janyo wayar ta duba, sai taga saƙon Daddy ne "Lalle yayi kyau sosai, ki shirya mana dinner a dining yau, ina son zan sake gani" Murmushi Amina tayi tana sake kallon lallen, tare da mamakin ya aka yi harya ga lallen nan. Emojin murmushi ta tura masa tare da saƙo kamar haka "Ya aka yi har kaga lallen nan?" "I watch everything about you, dan haka ba abin mamaki bane, zan jira a dining ki kawo Abincin dare in kuma gani" Tana daga tsaye sai murmushi take tana bashi amsa, ta tura masa "A gajiye nake, Hajara ce zata shirya dining" "Kin mai da ni kamar wani kakanki ko? Idan baki zo ba ba ke ba zuwa ƙauye, and i mean it" Ɗan kwaɓe fuska tayi ta masa reply da "Tuba nake ranka ya daɗe, ba zan iya ɗaukar wannan hukuncin ba, zan zo in sha Allah" Murmushi ne ya suɓuce masa da ganin abin da Amina ta rubuta masa. "Ba zan haƙura ba, a haɗa mini fruit salad" Tayi masa reply da "An gama as you wish" "Wai dariyar me kake tayi ne kai kaɗai, ka tattara hankalinka a kan waya gaba ɗaya?" Daddy ya ɗago ido ya kalli Hajiya Zainab ya ce "Ke ma ba taki wayar ce a hannunki ba, hira nake da mutane na" Ta haɗe rai ta ce "Mutanenka suwa kenan?" "Nika ɗai nake rayuwa a duniyar ne, babu abokai da 'yan uwa da zan hira da su in murmushi?" Yayi maganar ransa a haɗe, tuna tana lallaɓa shi dan ta karɓi kuɗi a hannunsa ne ya sanya ta bar zancen ta sauya akalar zancen zuwa wani. "Baban Fadila anya Khalil yana da hankali kuwa?" Cikin rashin fahimta Daddy ya ce "Kamar yaya kenan?" Ta ɗanyi ƙwafa sannan ta ce "Ko kiran wayata fa ba yayi, fushi yake da ni kenan?" "I don't know, bana ce ba, ya kan gaisheni ni dai ta chat" "Lallai Khalil, aikuwa zan nuna masa nice uwarsa, a kan yarinyar talakawa zai ɗau fushi da ni?" Daddy ya ce "Idan yana sonta ki ƙyaleshi mana, Khalil fa ba yaro bane ya mallaki hankalinsa, he knows what is right for him, ki ƙyale yara su zaɓi abin da ya dace da rayuwarsu" A fusace ta ce "Over my dead body, yarinyar fa a bakin titi take sayar da kayan shirme, ai ba kimar gidan nan bace kaje nemawa ɗanka aure gidan matsiyata, Allah ya suttura, haryanzu Khalil bai san me ya dace da shi ba, dan haka ni zan zaɓa masa mace 'yar gidan daraja ya aura" Daddy ya ɗan gyaɗa kai sanan ya ce "Ba kya ganin hakan zan haifar masa da matsala? Karki aura masa 'yar mutane ya wahalar da ita, tun da ba shi ya ce yana so ba" "Shi ya isa ya tsallake umarni na? Yaje ya yi ta fushin kar ya fasa, zan maganinsa ne" Daddy dai be kuma cewa komai ba, ya cigaba da taɓa wayarsa. Kamar yadda Daddy ya gaya wa Amina, yana dawowa daga sallar isha'i ya nufi dining yayi zamansa, yana jiran Amina. Sai dai ko da Amina ta kammala girkin, ta shiga tayi sallar isha'i, Hajara ta je ta fara shirya kayan Abinci. Ba tare da ya kalli Hajara ba ya ce "Turo mini Amina ta ƙarasa kawo Abincin" "To" ta amsa gwiwa a saɓule. Ta tarar da Amina a Kitchen, ta zuba ruwa tana sha, "Alhaji ya ce ki ƙarasa kai sauran Abincin" "Ban da abu irin naki dama Hajara, ni da ki ka barwa girki nayi ai sai ki bari in ƙarasa ladana, amma na zo na tarar kin fara kaiwa" ta wuce ta ɗauki plates, da jug ɗin da ta yi fruit salad ta fice. Hajara tayi ƙwafa ta ce "Ayi dai mu gani, Allah ya tona muku asiri muga ƙaryar iskanci" Cikin sa'a Amina ta tarar Hajiya Zainab da Fadila ba su fito cin abincin ba, sai shi ka ɗai a dining. "Kana ta kallona idan na faɗi fa?" Amina tayi maganar tana jere plates ɗin hannunta. "Nace ki kawo Abinci in kuma ganin lalle, amma kika turo wata ko?" Amina ta girgiza kai ta ce "Bani na turota ba" Ya ce "Well, mu ga lallen" Ta ɗago masa dogayen yatsunta, da suka lalle baƙi da ja. "Wow Masha Allah, a yiwa lallen nan kuɗi zan saya" Ta ce "Ai an riga an biya mai lallen, Babar ƙawata ce ta biya" "Na san an biyata, wani biyan zan yi ai na musamman" "Ni dai a'a ka daina bani kuɗi haka" Muryar Hajiya Zainab suka jiyo tana waya, nan da nan Amina ta nutsu ta fara ƙoƙarin barin wurin, Da kallo Daddy ya raka Amina, yana jin ba daɗi zuwan Hajiya Zainab ta katse musu hira. "Nifa gaba ɗaya na kasa gane kan yaran nan, kowanne da salon tsirfar da ya tsira, shi wancan yayi zuciya ya bar gida ya daina kula kowa, ita wannan ta tsiri zaman ɗaki, da rashin walwala na tambayeta wai pressure ne na karatu wannan wane irin abu ne?" Daddy ya ce "Wani abu na damunta ne?" "Yo ni ina na san mata, 'yar ganin dama, koma wani abu na damunta sai ta ga dama ai zan sani" Alhaji Ahmad ya miƙe ya ce "Ba zai yiwu wani abu na damunta, kuma a zura mata ido ba. Ɗakin Fadila ya nufa, yayi knocking sannan ya shiga, tana zaune a kan Carfet ɗin ɗakinta, hannunta riƙe da littafi tana kallo. Alhaji Ahmad ya ƙarasa yana faɗin "Autana, karatun kike yi haka?" "Eh Daddy" ta faɗa a sanyaye. Shi kansa ya karanto damuwa a tatare da Fadilan, duk da gwnaace wurin iya tsiwa da surutu idan ta ga dam, but her silent part dominate the other side of her. "Amma ya ban ganki a dining wurin Dinner ba?" Tayi murmushi ta ce "Bakomai Daddy, kawai ina son yin karatuna a cikin nutsuwa ne, da kuma cin abincin nikaɗai kar wani abu ya ɗauke mini hankali" Daddy ya ce "No, i want see you by my side, ta so muje in tabattar kin ci Abinci, sai ki zo ki cigaba da karatunki kinji sweetheart" Tamkar ƙaramar yarinya, haka Daddy ya lallaɓota suka fito, ya riƙo hannunta zuwa dining yana yi mata hira. Mummy ta kallesu ta ɗan yatsuna fuska ta ce "Eh, da yake babanki ne ai gashi nan kin fito, ni da kika raina ce mini ki kayi in ƙyaleki ai" Daddy ya ce "Please Madam, karki damar mini baby" yayi maganar yana zaunar da Fadila a kan kujera. "Ka mayar da ita cikinka, ƙarewar Baby ma" "Eh ba ruwanki da mu" Alhaji Ahmad yana matuƙar ɗaukar al'amuran Fadila da muhimmanci, dan wasu lokutan bai fiye damuwa da Khalil kamar yadda ya damu da ita ba, yake gudun abin da zai ɓata mata rai ba. Sosai ya dinga ƙaƙalo hirarraki yana yi mata, a haka har ta ɗan saki jiki ta ci Abinci sosai, har zuciyarta ta fara raya mata ko ta gaya wa Daddy, abin da ke faruwa amma kawai ta share, ta kamala cin abincin ta tafi  ɗakinta. Rana bata ƙarya sai dai uwar ɗiya ta ji kunya, yau ne Amina zata je garinsu, tun bayan watanni tara da ta shafe bata garin nasu duk da ba rabuwar daɗi aka yi ba, kuma bata san wane irin karɓa za suyi mata ba, hakan bai hanata yin murna da farin ciki ba, na zuwa ganin gida da zata yi, musamman ganin Inno, da shi ne babbar damuwarta. Da Asubar fari, ta ɗau akwatinta ta kai jikin motar da za su yi tafiyar a ciki, ta tsaya suna gaisawa da Zakiru, Zakirun hana tsokanarta "Ke fa yau kamar salla take a wurinki, zaki je gida" "Zakiru waya ƙi gida, kowa ya bar gida ai ba bisa son ransa bane ba, gida akwai daɗi sosai" Zakiru ya ce "Haka ne, Alhaji yayi mini maganar zan cigaba da koya miki karatu yana biyana, yaushe zamu fara ne?" "Ehh, nima mun yi maganar da shi, ka bari in dawo daga ƙauye, sai mu sanya lokaci, yadda ba zai shafi aikin da muke ba, kar ya zama abin magana". Zakiru kamar Amina ta taɓo masa in da yake masa ƙaiƙayi ya ce "Ke dai bari, wannan gida Allah ya nuna mana iyakar wannan mata, ke dai kije ki shirya da wuri, yanzun nan mu kama hanya" Gyaran murya suka ji a bayansu, Zakiru ya ɗa rikice yan risunawa ya gayar da Alhaji Ahmad. "Bamu wuri" Daddy ya faɗa ransa a haɗe, Zakiru ya bar wurin, Amina ta tsaya tana kallonsa. "Can't you greet me?" Yayi maganar yana tsareta da ido. Ta ce "To ai gani nayi ka haɗe rai" "Ba dole in haɗe rai ba, kawai kin zo nan kina ta zuba da wani" "Daddy Akwatina fa kawai na kawo ya saka a mota" "Eh daga nan kuma kika tsaya surutu ba, kin gama shiryawar ne?" Ta ɗan gyaɗa kai ta ce "Eh, na shirya kaya kawai zan saka" Ya ɗan tsareta da ido sannan ya ce "Ki kula sosai, zan dinga kiranki a waya in ji idan kun sauka" "To in sha Allah" tayi maganar tana kallon ƙasa. "Yauwa, banda yawo idan kin je ki zamanki a gida idan ba in da ya zama dole ba, bana son yawo ki zamanki a gida kin ji" Ta ɗaga masa kai alamar eh. "Talk" "To Daddy" ta faɗa a shagwaɓe. "Idan ma kika tafi yawo, za a gaya mini kuma zan haɗu da ke, maza kije ki ƙarasa shiryawa kiyi breakfast, kuzo ku tafi" Amina ta jinjina kai, ta wuce ciki. Cikin lokaci ƙalilan, ta kammala kintsawa, ta karya tana ta murna, Hajara ta rakota, har suka fito Hajiya Zainab bata tashi ba, dama lokacin tashinta bai yi ba. A kan baranda suka tarar da Daddy, yana tsaye yana danna waya, Baba kuma yana gefensa a tsaye. Murmushi Amina ta yiwa Baba ta ce "Baba tare zamu tafi?" Baba ya girgiza kai ya ce  "Ai ni naje na kuma komawa, ke kaɗai zaki tafi" Tare da Daddy suka rakata har mota, cikin ƙasa da murya Daddy ya ce "Saura kije ki saki baki, kiyi ta hira da shi a mota" ba ta ce komai ba tayi shiru. Ya ce "Safe journey" Ta amsa masa da "Thank you" Amina ta shiga mota, tana ɗaga musu hannu, suka tafi. Gaba ɗaya Fadila damuwa ta fara shafar karatunta, saboda rashin sanin a wani hali Yazid yake, saboda tana matuƙar tausayin halin da yake shiga idan ba shi da lafiya. Da ko ba komai da yana nan yana takura mata, ajiyar zuciya ta ɗan sauke tana kallon agogon hannunta, ranar Litinin zasu fara jarrabawa, amma babu Yazid babu dalilinsa. Saura mintuna goma lokaci ya cika malamin da suke da shi ya shigo, babu zato babu tsammani ta ji aji ya kaure da hayaniya. Babson ne da Captain, tare da Yazid a tsakiyarsu, Captain ya riƙo side ɗin Yazid na hagu, Yazid yana takawa a hankali yana murmushi. Ba ƙaramin faɗuwa gaban Fadila yayi ba, Yazid ya rame fiye da tunani, ga wani irin haske gauuu da yayi, sai sajensa da ya ƙara yawa. Kana ganinsa ka san yaji jiki, koma yana kan sha, amma kasancewar ya zame masa jiki murmushi ne kwance a fuskarsa. Mutanan ajin ne suka fara yi masa sannu, suna masa ya jiki, sai gaisawa da mutane yake, yana musabaha da mazan. Fadila ta zuba masa ido, sai dai ta kasa ko motsawa daga in da take, sai dai ƙasan zuciyarta da take murna kasancewar babu wani babban abu da ya same shi. Kankiya ne dama zai shigo ajin, ya shigo ajin fuskarsa a haɗe ransa babu annuri sam, hakan baya rasa nasaba da canza lamba da yayi ya kira Fadila, tayi masa wankin babban bargo ta ci mutuncinsa. Ya shigo yana ta muzurai, da hura hanci, da fari bai lura da Yazid da ke zaune a ajin ba, sai daga baya bayan ya yi rubutu a kan board ya juyo. Ya sauke idonsa a kan Yazid, sake haɗe rai yayi ya kalli  ce "Me kake yi a class ɗina?" Yazid yayi shiru bai ce komai ba. "Zo ka fita ka bar mini aji, dan baka da mutunci shi ne zaka zo ka zauna mini a aji, zo ka bar mini aji, kuma ka sa a ranka ba zaka zana jarrabawata ba, come and leave my class usless" Kalmar usless ɗin nan ba ƙaramin ƙonawa Fadila rai tayi ba, ji tayi kamar ta zagi Kankiya. Captain ya ce "Sir kayi haƙuri ba shi da lafiya ne, yau ya dawo" "Shut up! Nace ka sa mini baki ne? Ai ya riga ya san na hana shi zama a ajina, tashi ka bar mini ajina" Yazid ya ja jikinsa a hankali, ya tashi tsaye, sai da ya tashi Fadila ta lura da Cannula a hannunsa, a hankali yake jan ƙafarsa, tare da dafe gefen cikinsa ya fice daga ajin. Kankiya yayi tsaki ya ce "Nonsense" Miƙewa Fadila ma tayi, ta ɗau jakarta ta nufi hanyar fita, tana jin Kankiya na kiranta amma tayi masa banza ta bar ajin da sauri. Hajiya Zainab ce ta shigo ɗakin Daddy tana masifa "Wai ni ina wannan sakaran direban naka ya tafi? Tun ɗazu nake nemansa, yazo ya karɓo mini saƙo a wurin Hajiya Salma. Cikin ko in kula Daddy ya ce "Na aike shi ne" "Zuwa ina? Jiransa nake yi ni akwai in da zani" "To ke ki ɗauki mota kije ki karɓo da kanki mana, ko ta yi miki aike" "Haba Baban Khalil, ina gaya maka uzurina kana gaya mini wani abu daban, dan Allah ka kirashi ya zo ya je mini aiken nan" Alhaji Ahmad ya tashi zaune ya ce "Na aiki Zakiru Shanono, zai kai Amina gidansu" "I don't get you, and what does that mean? Meyasa zaka aike shi ya kaita ƙauye, a matsayinta na wa?" "Mahaifinta ya nemi hakan, dan ba zai yiwu ya bar yarinya ita kaɗai ta tafi ba" Rai a ɓace ya ce "I don't care, me yasa zaka yanke wannan hukuncin ba tare da na sani ba, 'yar aiki tafi aikin gidana muhimmanci kenan? Ubanta ya kaita mana, yanzu waye zai je mini aiken nawa?" Miƙewa tsaye Daddy yayi ya ce "Zainab, ba Khalil bane da Ahmad kike Magana, duk wanda yake aiki a ƙarƙashina yana da damar ya nemi alfarma a wurina nayi masa" ya fice ya bar mata ɗakin. MASU BUƘATAR SHIGA VIP GROUP, SUNA IYA TUNTUƁATA A KAN LAMBAR WAYATA DA KE ƘASA, DOMIN SU BIYA A SAKA SU AYSHERCOOL 08081012143GABA DA GABANTA AISHA ADAM AYSHERCOOL 44 Ganin Alhaji Ahmad ma ya ɗau zafi sosai, ya sanyata saurin saukowa daga nata fushin, dan da wuya yayi fushi amma idan yayi fushi wahalar sha'ani ne da shi fiye da tunani. Dan haka ta ce "Naji shikenan ya wuce, na haƙura da saƙon na san yadda zan yi" Bedroom ɗinsa ya wuce ya barta, tabi bayansa tana cigaba da lallaɓa shi, amma ya shareta ya ƙi saurarta. Ba ƙaramin yarfa Kankiya Fadila tayi ba, ganin yadda yake muzurai ake tsoronsa amma Fadila ta yarfa shi a gaban ɗalibai, hakan ba ƙaramin ɓata masa rai yayi ba, kuma hakan ya jefa zargi a zukatan ɗaliban, mai zai sa Fadila ta tsinka malamin haka duk da yadda ake tsoronsa. "Yazid, Yazid" tsayawa yayi ya waiwaya da jin muryarta a cikin dodon kunnuwansa. Ta ƙarasa in da yake da sauri, bai ƙosa ba ya jira har ta cin masa. Cikin damuwa ta ce "Sannu, ya jikin naka? Ashe baka da lafiya?" "Eh, amma da sauƙi sosai Alhamdilillah" "Wai meya sameka ne?" "Rashin lafiya ne" ya bata amsa. "Wane irin rashin lafiya?" Ta kuma tambayarsa cikin kulawa. "An mini aikin appendix ne, sai kuma asma da ta dameni shikenan amma da sauƙi sosai" "To yanzu ina zaka daga nan?" "Gida zan tafi" "Ok, to muje in sauke ka" Da sauri ya girgiza mata kai ya ce "A'a ki bari na gode zan tafi" "Ba ka ganin a yadda kake tafiya, kazo muje in sauke ka" "Na gode, amma ba zan hau motarki ba, ban kai in hau mota irin wannan ba, ba ta dace da hawan talaka kamata ba" daga haka ya juya yana tafiya a hankali. Tsayawa tayi tana cigaba da kallon yadda yake tafiya a hankali, har ya ɓacewa ganinta. Tafe suke suna hira jefi jefi ita da Zakiru, yana bata labarin yanayin zamantakewar gidan kafin zuwanta. "Ai nake gaya miki, ko 'yan uwan maigidan nan duk zumuncinsu sun haƙura sun daina zuwa, sun zuba masa ido, shi kansa sai lokaci lokaci yake zuwa, dama bata yadda yaranta suje ba, kuma fa 'yan gari ɗaya ne, saboda azabar baƙin halinta, duk son sa da yayi taimako sai dai yayi bata sani ba. Ai matar nan bana zaton tana son taga Annabi" Amina ta ce "A'a karka ce haka, amma ina mamakin ita ko nata 'yan uwan basa zuwa sai ƙawaye" "To ina taga wasu 'yan uwa ma, sukan zo wasu lokutan suna ba wani kallon arziki take musu ba, amma a hakan tana jidar kaya ta bani in kaiwa wasu daga 'yan uwanta, ai ita idan kika ga tana rawar kai tana nan nan da kai, to mai kuɗi ne kai, duk ta kanainaye maigidan baya jin maganar kowa sai tata, ai har gara yanzu a kan da, sanyinsa yayi yawa, sai ya fito cikin mutane ya fito yana taƙama baki Ga yadda ake girmama shi a waje ba, amma a gidansa ba shi da kataɓus ga shegen son 'ya'ya kamar masifa, waccan tsigalaliyar 'yar ta sa idan ta zauna tana taɓara abin takaici, gata halinta ɗaya da uwarta na rashin mutunci, ba kunya idan nayi kuskure take ƙare mini zagi, ai Alhaji Ahmad yayi ta kowane fanni amma a gidansa dai damisar kwali ne" "Zakiru ya isheka haka, wasa yayi wasa banda tsikarin uwar miji da taɓarya" tayi maganar ranta a haɗe. Zakiru ya ce "Kamar yaya kenan?" "Ina ruwanka da abin da ke faruwa a gidansa kake ce masa damisar kwali, kai waya san yadda taka matar ke juyaka, ya isheka bana son wannan hirar" Zakiru ya yi murmushi ya ce "Allah ya baki haƙuri, tuba nake" Amina ta basar da shi ta haɗe rai. Message ɗin Daddy ne ya shigo wayarta. "Yaya hanya, kun isa kuwa?" Tayi masa reply "A'a muna hanya" "Ina fatan ba kya jin yunwa, idan kina jin yunwa ya tsaya ki ci Abinci" "Ka manta na karya kafin mu tafi, mun shiga Shanono, mun kusa gida in sha Allah" "Ok, to Alhamdilillah, ki gaishe su" "Thank you, za su ji" ta ɗan yi murmushi ta ajiye wayar. Hajiya Zainab ce zaune a ɗakinta tana waya da Hajiya Salma "Dan Allah Salma ki ƙara haƙuri, kwanan nan duk na kasa gane kan babansu Khalil, ya ce zai bani kuɗin amma sai wasa yake mini da hankali, da abu ya ɗan haɗamu sai ya hau fushi, a yadda yake ɗin nan idan na matsa, zai iya hana kuɗin nan, kuma ni kinga na tattare kuɗin hannuna na yi order kaya, kuma ba zai yiwu in kwashe sauran kuɗin hannuna in baki ba, saboda suma juyasu nake". Hajiya Salma ta ce "Ni yanzu ya zan yi? Turai ta bani aron million biyu, dama na wajenki nake jira da million bakwai coustom suka ce zan bayar a sakar mini kayana, da ƙyar suka bari a 5million, kuma kinga Alhaji  kwanan nan ya ƙara mini jari ya ce ba zan samu ba" "Kiyi haƙuri, zan cigaba da lallaɓa shi saina karɓa zan baki in Allah ya yarda, kuma ina ga zan je Abuja a satin nan in Allah ya yarda" "Too, Zainab me zaki yi a Abuja kuma?" Hajiya Zainab ta ce "Wurin yaron nan Khalil mana, gaba ɗaya ya ɗauki gaba da ni, ubansa kawai yake tuntuɓa, ba ruwansa dani" "Kaii yaran zamanin nan, anya ba asiri suka yi masa ba, duk yadda Khalil yake miki biyayya, amma yanzu a kan wannan yarinyar ya daina shiga harkarki" "Bari kawai Hajiya Salma, bana son babansa ya gano actual abin da nayi masa, kin san halinsa a kan 'ya'yansa, gaba ɗaya ina cikin damuwa dole in je Abuja" "Ke Zainab, ai ba a yiwa yaran zamanin nan haka, ba ke yakamata kije ba, ki kai yarinyar wurin malamai, idan ma wani abun suka masa a karya shi, sannan ki nemo masa wata matar, akwai 'yar ƙanwata  Hajiya Badi'a ai kin santa Kursum ki haɗa shi da ita kawai" "Kin kawo shawara haka za ayi, zai ga tsiya" "Ai kawai ba sai kinje ba, sai bayan an kai kuɗi da komai, ki ce masa ya zo ga mata shine zaki hukunta shi ki nuna masa ke uwace" Hajiya Zainab ta ce "Hakan ma yayi, na gode sosai Salma, zan zo gidanma da kaina mu ƙarasa tattaunawa" "To shikenan, sai Allah ya kawoki" suka yi Sallama Hajiya Zainab na jin ta gamsu da shawarar da Hajiya Salma ta bata. Amina tayi ta kwatantawa Zakiru hanya har ƙofar gidansu, suna parking ta buɗe motar ta tafi da gudu cikin gida, wasu daga yaran su Kawu Bala suna ƙofar gida suka bi motar da aka kawo Amina da kallo, dan ɗaya ce daga irin jibga jibgan motocin da Alhaji Ahmad yake hawa ne aka kawota. "Inno! Inno!" Amina ta dinga ƙwalawa Innon kira. Inno ta saki ƙwaryar hannunta, ta buɗe hannayenta Amina ta zo ta rungumeta, Inno ta ƙanƙame Amina kamar zata mayar da ita ciki, Amina kuwa kuka ta fara yi tana jin tsananin kewar Inno. "Amina, Amina na rasa mema zance" "Inno, yaushe rabon da in ganki?" Inno ta ce "Yau ai gashi kin ganni" Tuni wasu daga cikin yara har da 'yan matasa na maƙotansu, suka cika tsakar gidan suna kallon Amina. Suka shiga ɗakin Inno, Amina sai sake ƙanƙame Inno take yi. "Amina ya gida ya karatun bokon?" "Karatu lafiya lau Inno" Inno ta riƙe haɓa ta ce "Ohh, Amina buri ya cika ana can ana boko" "Inno kenan, ai zaki ga ribar boko in Allah ya yarda, bari in yiwa Zakiru magana ya shigo ku gaisa" Inno ta ce "Waye shi kuma?" "Direban gidan da nake aiki ne" "Au ai na zata siriki ne" Dariya Amina tayi ta ce "Ba wani siriki" Amina taje ta kira Zakiru, ya shigo gidansu Amina, suka gaisa da Inno, daga nan suka ɓige da hira kasancewar Inno ta san garinsu Zakiru yayarta tana aure a can. Mutane sai shigowa suke suna sun zo yiwa Amina sannu da zuwa, nan kuwa gulma suke zuwa yi, suna ta maganganun Amina ta zama ƙatuwa, gashi ta yi fresh ta zama 'yar gayu, ga uwar waya a hannunta. Zakiru ya kalli Amina ya ce "Amina ko zaki haɗani da wanda zasu tayani kwaso kayan da ke motar" Amina ta miƙe tana faɗin "Ai ko nima sai in ɗauka" Ya kalleta ya ce "Ki ɗauki me? Zo muje ki gani fa" Amina tabi bayan zakiru zuwa mota. Ya saka hannu ya buɗe mata boot, waro ido tayi ta buɗe baki da tayi tozali da abin da ke cikin Boot ɗin. Kayan Abinci ne kamar za a buɗe kanti, ta kalli Zakiru ta ce "Zakiru, wannan fa?" "Aike Amina kin ciri tuta a gidan nan, shekaranjiya ya saka na ɗau motar nan muke je da shi muka sayo, jiya da daddare ya ce mini a wannan motar zamu tafi, kar in bari ki san da kayan" "Na shigesu ni Amina, Zakiru kalli uban kayan fa" "Ke ki gode Allah, Allah ne ya baki, da waccan matar ta sani ba zata bari a baki ba" Amina ta ce "Zakiru kaima ka ɗiba" "A'a nima ya sallameni, bari in kira wasu su tayani" Haka aka dinga kwasar kaya ana shiga da su gidan su Amina, nan da nan sai ga matan su Baffa Lawan da yaransu sun cika gidan suma. Sai da Zakiru ya tabattar da an gama kwashe kayan an shiga da su, yayi musu sallama ya ajiye musu bandir kuɗi ya ce in ji Alhaji Ahmad. Gaba ɗaya Mamaki ya gama kashe Amina, amma ta basar kamar bata wani damu ba. "Ohh Amina, kalli yadda kika koma, lallai yanzu kin wuce ajin Jarmai, birni ya karɓeki" Cewar Amaryar Kawu Bala. Suka yi ta yaba Amina, suna son jin ƙwaƙwaf, ance musu gidan da Baba yake aiki a nan Amina ma take yi, amma shi tun da yake bai taɓa zuwa da wanan kayan ba, kuma ba a taɓa kawoshi a irin wannan mota ba sai Amina. Suna ta son su tanbaya suyi tsegumi, amma Amina ta haɗe rai ta haye Gadon Inno tana latsa wayarta, dan ba zata manta wulaƙanci da rashin mutuncin da suka dinga mata ba a baya. Gaba ɗaya Fadila ji daɗin reaction ɗin da Yazid yayi ba, ji tayi gaba ɗaya bata son zaman makarantar, dan haka ta ɗauki motarta ta wuce gida. Zuwa azahar sai ga su Baffa Lawan, an je har Gona an sanar da su, ga Amina can an kawota a wata ƙatuwar mota daga birni. Basu ƙara tsinkewa da lamarin ba, sai da suka ɓangaren su Amina, suka tarar da uban kayan Abinci fal tsakar gida, cikin ɗaki kuma kayan sawa ne da kayan ciye-ciyen da Daddy ya saiwa Amina. "Ke ina Aminar take, wanann kayan kuma na menene?" Cewar Baffa lawan yana shafa buhun shinkafa. Inno ta ce "Bismillah Baffa ku shigo" "Ba zamu shigo ɗin ba, ina Hassan ɗin ma tukuna?" Inno ta fito tare da faɗin "Ai ita kaɗai ta dawo ban da shi, shi ya zazzo a 'yan kwanakin nan" Bala ya ce "Ina Aminar ne?" "Tana ɗaki" "Eh lallai, rashin tarbiyyar ta ta har ta kai ta kasa fitowa ta gaishe mu?" Inno ta ce "A'a ba haka bane ba, ke Amina fito mana" banda Inno ta saka baki babu abin da zai sanya Amina ta fito. Gaba ɗaya suka bi ƙofar ɗakin Inno da kallo, Amina ta yi ƙiba, fatarta ta ƙara haske. "Ina wuninku" Kawu Bala ya riƙe baki ya ce "Ba shakka, yanzu dama irin wannan rayuwar Hassan ya zaɓi kiyi, shi ya sanya ya tattaraki ya kai ki birni? Ko in ce kuka haɗa baki kika gudu, yawon ta zubar ai shikenan gaki ga duniyar nan, kin ƙi sunnar ma'aiki kin shiga duniya bin yaran yahudawa" "Kawu Bala, Tazubar kuma?" "Eh yawon ta zubar mana, idan ba haka ba wani irin aiki ne kike yi haka da kika samo wannan kayan, tun da uban naki yake aikin a birni ya taɓa zuwa da makamancin haka ne?" Ran Amina yayi bala'in ɓaci, kawai ta tashi ta bar musu tsakar gidan, dan idan ta cigaba da zama zata iya rama cin zarafin da suke mata. "Ka gani ko Yaya Bala, wai mu muke mata magana ta tashi ta tafi, idan ba bariki ba mai zai kawo haka?" Ita dai Inno tayi mus shiru, suka gama cin mutuncinsu suka tafi. Inno ta koma ta samu Amina a ɗaki ta ce "Amina kiyi haƙuri, wallahi tun da kika tafi suke surutai da ƙanann maganganu" Amina ta ce "Aikuwa sai sai suyi, dan bani da lokacinsu, na gaba ya riga yayi gaba, kuma Inno a ɗibar musu wani daga kayan Abincin nan a basu, aniyarsu ta bisu" Da yamma Amina ta shirya, ta tafi sada zumunci wurin sauran 'yan uwa, kowa sai son ya ganta yake yi, masu ƙananan maganganu kuma suka cigaba da yi. Su Bala kuwa da aka ɗebi kayan Abinci aka basu, lumi suka karɓe duk da suna iƙrarin kayan haram ne. Da daddare Amina da Inno suna tare, Amina tayi musu girkin dare, suna ta hira Inno na bata labarin abubuwan da suka faru bayan tafiyarta, haka ita ma Amina ta dinga bawa Inno labarin birni makaranta da yanayin rayuwar mutanen birni. "Gaskiya Inno an mana nisa, cigaba yana birni, in Allah ya yarda a dalilin karatun nan nawa sai garin nan ya samu cigaba na gaske" "To Allah ya sa, amma da fari nima naso kiyi aurenki duk da ba Jarmai na ke so ki aura ba, amma yadda na ganki ɗin nan naji daɗi sosai, kin san bayan tafiyarki Jarmai mata biyu ya aura ya saka" Amina ta ce "Allah ya rufa mini asiri, da tuni nima ina ciki" Wayar Amina ce ta fara vibrating tana kawo haske, ganin sunan Daddy ya sanya ta kalli Inno ta ce "Ina zuwa" Ta miƙe ta bar ɗakin ta koma wani, ta zauna sannan ta amsa wayar tare da yin sallama. Sai da yayi ajiyar zuciya sannan ya amsa ya ɗora da cewa "Da ba zaki ɗaga bane?" "Wace ni in ƙi ɗaga wayarka, ina tare da Inno ne ina cin abinci" "Ok, nayi zaton kin yi bacci ai" "Ai dare bai yi ba sosai" Daddy ya gyara kwanciyarsa Sannan ya ɗora da cewar "Ina fatan kin ci kin ƙoshi" "Na ƙoshi sosai ma, gani ga Inno muka ci fa, nayi kewarta sosai" Yayi murmushi ya ce "That's good, ni kuma na kasa cin Abincin" Ɗan waro idonta tayi ta ce "Me yasa?" "Ba a bani wanda nake so ba, fruit kawai naci na kwanta" Cikin damuwa da tausayawa Amina ta ce "Meyasa baka sa an dafa maka wanda kake so ba? Kar ka kwana da yunwa fa" Ya shafi cikinsa ya ce "Abincin ne bana jin daɗinsa idan bana ki ba, na san da kina nan zaki dafa mini abin da nake so" "Kar ka kwana da yunwa kaji Daddy, dan Allah ka ci wani abu" "To me zanci, kar ki damu zan kwana haka ba wata damuwa" Noƙe kafaɗa tayi ta ce "Ni ban yarda ba" Dariya yayi ya ce "Rigima ko?" "Allah da ina gida da komai dare saina dafa maka Abinci, me zai sa a bar mai nemowa ya kwana da yunwa, rashin kyautawar yayi yawa" Har cikin ransa yaji daɗin abin da ta faɗa, na nuna damuwa da shi sosai. "Ai nace karki damu, na ƙoshi na sha fruit sosai da cock" "Cock kuma?" Ta faɗa da ɗan ƙarfi. "Eh Cock" ya bata amsa. "Daddy ba a hanaka sha ba?" "To ya zan yi idan ban sha ba?" "Daddy baka kiyaye lafiyarka sai wani abu ya sameka, daga tafiyata ka cigaba da ciye-ciye ko" Sosai ta bashi dariya ya ce "Da wasa nake yi, ban sha ba" "Har naji daɗi na zata ka sha" "Mhmm ban sha ba Meenali" Amina ta ɗan numfasa ta ce "Daddy" "Mmm" Ta ɗan tura baki ta ce "Ka amsa mana" "Na amsa ai" yayi maganar yana murmushi. Ta ce "Kace Na'am Meenali" Dariya yayi ya ce "Kina son sunan kenan?" "Eh mana, idan ka faɗa sai in jini kamar wata irin babbar 'yar gayun nan, nan kuwa 'yar ƙauye ce" Ba ƙaramin dariya ta bawa Daddyn ba, "Allah ya shirya mini ke" Ta sake nutsuwa ta ce "Daddy, kayan daka saya muka taho da....." "Shhhhhh" ya katseta. "Daddy ka tsaya ka ji me zance" "Keep quiet" yayi maganar cikin bada umarni. "Daddy dan Allah ka bari nayi magana" "I say keep quiet" Ta sake marairaicewa ta ce "Dan Allah Daddy" "Amina i said you should keep quiet, tun da ba kya ji saida safe" Da sauri ta ce "Yi haƙuri dan Allah nayi shiru" "Idan nace bana son abu just leave it immediately" "To in sha Allah" "Yauwa ko ke fa, i hope dai baki fita ko ina ba?" Amina ta ɗan sosa kai ta ce "In gaya maka gaskiya?". "Kin fita kenan?" "A'a ai ban yi nisa ba, gidan 'yan uwanmu naje, kaga ba zan daɗe ba zan dawo" "Meyasa baki gayamini ba" "To kayi haƙuri" Cikin kwaikwayonta ya ce "To kayi haƙuri, mara ji kawai, kije ki kwanta sai Allah ya kaimu da safe kuma" "To Daddy, ko in hau Online" "A'a hutawa zaki yi, kun sha tafiya, ki gaida Mutanen gidan" Amina ji tayi bata son ta katse wayar, amma ta maze ta ce "To, Allah ya tashemu lafiya, don't forget to recite Suratul mulk before you sleep, zan kawo maka Abinci a mafarki" tayi maganar tana dariya. "Meenalin Daddy, my joy giver zan karanta in sha Allah bye bye" ya kashe wayar, dan shima idan ya biye mata ba zai katse kiran ba. Ya lumshe idanunsa tare da ɗora wayar a kan ƙirjinsa yana murmushi. Ɗaki Amina ta koma, ta tarar Inno na shirin kwanciya. "Inno har kin gama cin abincin?" Inno ta ce "To yaya zan yi idan ban ci na tashi ba, kin je kin shantake kin shanyani, wai ma da wa kike wayar ne?" Amina ta ɗan sosa kai ta ce "'yan ajinmu ne fa" Inno ta gyaɗa kai ta ce lallai kam. Fadila na zaune a babban falo, tana shan tea tana kallon wani Indiyan series, Mummy ta fito falon ita ma. "Au baki bacci ba dama?" Fadila ta ce "Eh Mummy, na kasa baccin ne" Mummy ta zauna a kusa da Fadila ta ce "Ke, wata shwara Hajiya Salma ta bani a kan Khalil, kuma ina ga hakan zan yi, dan in nuna masa kuskurensa" "Shawarar me kenan?" "Ai da Abujan zanje in ga halin da yake ciki, ya ɗau gaba dani ko gaisheni baya yi sai ya ga dama, shi ne Salma ta ce in rabu da shi, kawai in nema masa aure sai dai in ce ya dawo ga mata" Fadila ta kalli Mummy ta ce "Kuma kina ganin hakan mai yiwuwa ne?" "Me zai hana shi yiwuwa? Hakan ne kawai zai sanya in yi maganinsa, kuma in raba shi da waccan yarinyar da ya ɗora ransa a kanta". "Gaskiya bai kyauta ba sam, nima ko magana nayi masa sai ya ga dama yake kulawa, amma kar ki aura masa wadda baya so ya wahalar da 'yar mutane a banza, kin san halinsa". "Shi ya isa, zan nemo masa yarinyar wadda ta dace da shi, ba wannan shiriritar gayyar tsiyar da ya kwaso ba" Fadila ta ce "Shikenan, Allah ya sa a dace". Hajiya Zainab ta amsa da "Ameen" Ɓangaren Hafsa kuwa, sayar da ƙosai suka koma yi a cikin gida, da kayan su maggi da kayan kaɗin miya, Hafsa tayi iya ƙorainta ta cire Khalil daga ranta, amma abun ya gagara, a zahiri ta cigaba da sabgoginta, tare da nuna komai ya wuce, sai dai walwalarta ta ragu sosai tana ta dannewa dan kar Mama ta gane tana cikin damuwa, sai dai ita kanta Maman ta damu sosai da rabuwar ta su. Har zuwa wannan lokacin, Hafsa ba ta daina ɓuya tayi kuka ba, saboda ba ƙaramin so take yiwa Khalil ba. Dan har a yanzu wasu lokutan ji take yi tamkar ta mayar da layinta ta kirashi, amma sai ta fasa ta cigaba da danne abin a zuciyarta, tare da miƙa lamuranta ga Allah. Washegari jama'a basu fasa cigaba da zuwa ganin Amina ba tare da yi mata sannu da zuwa ba, wajen ƙarfe goma na safe tayi wanka ta kintsa, ta cewa Inno zata je makarantar bokonsu, ta gayar da malamanta na makaranta. Inno ta amince, Amina ta shirya ta tafi makarantar. Malamanta sun ji daɗin ganinta, Malam Sunusi ya ce "Amina, sai wayar gari muka yi muka samu labarin wai kin gudu, kwatsam na haɗu da mahaifinki a kasuwa ya ce ai kina can wurinsa a birni" Amina ta ce "Wallahi Sir a lokacin nan bani da wani zaɓi da ya wuce in gudu wurin mahaifina, Auren dole 'yan uwan babana za suyi mini a lalata mini karatuna, ni kaina ba a son raina na tafi ba, amma ina can wurin Babana" "To Masha Allah, ya karatun naki, yace mini kin cigaba da karatunki" "Eh sir na cigaba, ni shekara mai kamawa in Allah ya yarda zan gama Sakandire" Nan malaman suka yi ta saka mata albarka tare da yi mata fatan sa'a da nasara. 'yan ajinsu duk babu, wasu sun yi Aure wanda Allah ya taimake su kuma sun cigaba da karatun. Sai wajen azahar Amina ta baro makarantar, ta nufi gida, sannu a hankali take tafiyarta sam bat jin zafin ranar nan, duk da akwai nisa a tsakaninsu da makarantar, amma bata damu ta hau abin hawa ba, a ƙafa ta tafi tana tafe tana tunanin abubuwan da suka faru a baya. Sautin ƙarar wani akwalan babur ne ya cika mata kunne, tana ƙoƙarin kaucewa babur ɗin amma burki ya ƙwacewa mai baburin ji kake gauuuu!! AYSHERCOOL 08081012143GABA DA GABANTA              BY AISHA ADAM AYSHERCOOL 45 Gafe Amina tayi da sauri, shi kuma ya daki bishiya, ya kusa hantsilawa, Allah ya taimake shi bai faɗi ba, ya saki baki ya bi Amina galala da kallo "Amina" ya faɗa cikin mamaki. Haɗe rai Amina tayi ta ce "Wannan wane irin abu ne, da ka bugeni fa shikenan ka cuce ni?" "Haba Amina, ai kya bari mu gaisa, dama da gaske kin dawo garin nan, Allah mai iko" "Kaga Jarmai, babu ruwanka dani dan Allah, ka fita daga harkata" "Haba Amina, ki tsaya muyi magana mana" Wata uwar harara Amina ta watsa masa ta ce "Muyi magana kace mini me? Da ka nemi jefa rayuwata cikin masifa" "Amina ai shi masoyai ba zai taɓa zama maƙiyi ba" "Can da yawarka, ai ni ban taɓa sonka ba, kuma ba zan ba ka fita daga harkata na gaya maka". Ta juya ta cigaba da tafiya, hawa baburinsa yayi ya cigaba da binta, amma tayi masa banza kamar da dutse yake ba da ita ba, a haka har suka iso cikin gari, sai da ya bita har gida, amma ko ɗaga kai bata kuma yi ba, balle ya sanya ran zata saurareshi. A tsakar gida ta tarar da Inno tayi alwalar sallar azahar. "Amina ina kika tsaya haka kin daɗe?" "Ina makaranta, na tsaya wurin su Malam Sunusi na taho hanya wannan Jarman ya kusa bugeni da babur har ƙofar gidan nan ya biyoni yana mini magana, wai in saurareshi" Inno ta jinjina kai ta ce "Lallai Jarmai ba shi da kunya, kinga yadda ya dinga yiwa su Baffa Bala zarya, yana neman ya kai su ƙara, suka ce ya bari idan aka ganki zasu ba shi ke, ya ce ko kyauta suka bashi ke ba zai karɓa ba, wai kin tafi yawon duniya" Amina t girgiza kai ta ce "Allah ya rabani yawon duniya, yaje aniyarsa ta  bishi" "Kije kiyi salla, ki zo ki ɗibi Abinci, nayi waya da babanki a kan kayan nan da aka kawo, ya kira wayarki amma kin barta a gida, ya ce a ɗebarwa maƙota ma" Amina ta ce "Na manta da wayar ne, a ɗebar musun, bari in yi salla" "Aikuwa ana ta kiranki a wayar, ni dai ban iya ɗagawa ba haka na barta" Amina ta ce "Idan nayi sallar na duba waɗanda suka kirani, na san ba zai wuce Daddy ba". Tun ranar da Kankiya ya kori Yazid daga aji, bai kuma zuwa ba, Fadila dai ta gaji ta sake kiran wayarsa, cikin sa'a taji ta shiga, sai da ta kusa katsewa sannan ya ɗaga kiran. "Assalamu alaikum" Ta amsa da "Wa'alaikum salam warahmatullah, Yazid" "Na'am" ya amsa yayi shiru. "Kana jina?" "Eh ina ji" "Fadila ce" "Na gane, ina jinki" taji haushin amsar da ya bata, amma ta basar ta ce "Ya jiki?" Ya ce "Jiki Alhamdilillah, da sauƙi sosai" "Naga baka kuma zuwa school ba tun ranar, shine na yi zaton ko jikin ne haryanzu". "Hmm in zo saurayinki ya kuma korata, jikin ne ban gama warkewa ba, wurin da aka mini aikin yana ciwo, likita ya ce in zauna a gida, ina ga sai lokacin exams zan shigo" "To Allah ya baka lafiya, tun lokacin da ka daina zuwa na sanarwa HOD in sha Allah duk zaka yi exams ɗinka ba wata matsala" Yazid ya ce "Masha Allah, na gode sosai" "Amma ka bani direction ɗin gidanku, ko Asibitin da kake, zan zo in dubaka" "No, unguwarmu ta talakawa ce sosai, idan kika ce zaki zo, motarki zata iya ɓaci, kuma ba zan so in wahalar da ke ba, na gode sosai" Jiki a sanyaye ta ce "Ba damuwa ka gaya mini in zo" Ya girgiza kai ya ce "Kar ki damu, hakan ma na gode sosai, sai anjima" ya katse kiran. Ta sauke wayar daga hannunta tana bin wayar da kallo. Haryanzu Khalil yana fama da ciwon kai mai zafi, duk da yana ta ƙoƙarin danne damuwar da yake ciki, amma kallon hotunan Hafsa da duba previous chats ɗinsu ya zame masa kamar ibada, idan bai yi ba baya jin daɗi, gaba ɗaya ya rame sosai. Gidansa da yake ta ɗoki yana ginawa, yana ƙaƙale gaba ɗaya ya dakatar da ginin, dan ji yake idan ba Hafsa ba babua wadda zai iya sanyawa a cikin wannan gidan. Bayan sallar la'asar yaga missed video call ɗin Fadila. Kiranta yayi dan yaji dalilin kiran nasa da take yi. Ya ci sa'a tana Online, ta ɗaga wayar. Ɗan zuba masa ido tayi, cikin damuwa ta ce "Yaya Khalil baka da lafiya ne?" "Lafiyata ƙalau menene?" Ta ɗan rausayar da kai ta ce "Yaya Khalil me nayi maka ne?" "Kamar yaya?" "Naga idan nayi maka magana sai ka ga dama kake amsawa, ko a waya baka kirana" Ya ɗan ɓata fuska ya ce "Ayyuka ne suka yi mini yawa sosai" "Na sani, ba wani aiki da yayi maka yawa, ka rame fiye da yadda kake tunani, duk wanda ya ganka ya san kana cikin damuwa ne. Dama na kira in gaya maka ne, Mummy tana nan tana fushi da kai, wai kana gaba da ita, Hajiya Salma ta bata shawarar ta aura maka wata yarinyar, tun da haka ka zaɓa gara ka san abin yi" Zaro ido yayi ya ce "Ban gane ba, kamar yaya a aura mini wata yarinyar, idan bana sonta fa?x" "Nima ban sani ba, haka kawai Mummy ta gaya mini, gara ka dinga kiran Mummy kana gaisheta" "Fadila ya ake so in yi da rayuwata? Yaya za ayi in gaba da Mummy, duk lokacin da na kirata sai ta mini faɗa ta ƙare mini zagi a kan Hafsa, ita kanta yarinyar mutuncina ya zube a idonta, ace uwata taje ta sameta ta ci mutuncinta wai ta rabu da ni, wanene ni ɗin? Kuma yanzu haka bama tare, yarinyar ce ta ƙarfafa mink gwiwa a kan mu rabu da juna, tun da Mummy bata so, amma gaskiya idan Mummy ta aura mini wata daban wadda bana so bata kyauta mini ba" Fadila ta ce "To ni dai ban gaya maka dan ka tashi hankalinka ba, na gaya maka ne kawai dan ka san abin da kake ciki" Ya jinjina kai tare da fesar iska daga bakinsa ya ce "Shikenan, na gode sosai" yayi disconnecting ɗin kiran, ya cillar da wayar gefe, ya dinga murza goshinsa, yana mamakin yadda Mummy ke biye shawarar ƙawayenta fiye da komai. Sai da Amina ta idar da sallar azahar, sannan ta turawa Daddy saƙo "Can i call you?" Kusan mintuna goma da tura masa saƙon, Daddy ya kirata. Wani nishaɗi ne ya ratsa Amina, ganin kiran Daddy ta ɗaga wayar tare da faɗin "Ina wuni?" "Kin dawo kenan?" "Eh, amma makarantarmu naje na gaida malamaina, ba wani wurin naje ba" "Kin dai fitan, baki gaya mini ba" ya faɗa yana kwance agogon hannunsa. "Kayi haƙuri, zan dinga tambayarka" "Well, ya gidan ya kowa da kowa?" "Kowa lafiya lau, ka san wani abu?" "A'a, sai kin faɗa" "Jarmai fa na haɗu da shi a hanya ya biyoni" ɗan tsuke fuska Daddy yayi, amma ya ce "Wow, kin haɗu da tsohon zuma kenan?" "Allah ya kiyaye, ka san yadda na tsani mutumin nan, Allah dai ya taimakeni, bayan tafiyata mata biyu ya aura ya saka" Daddy ya girgiza kai ya ce "Kashh bai kyauta ba gaskiya, to ke yanzu idan ba kya son Jarmai wa zaki aura?" "Kai fa kace ba zan yi soyayya Yanzu ba" Kawai Daddy ya fara dariya, ita ma ta biye masa suna dariyar tare. "Meenalin Daddy, am missing you gaskiya, da wurin zan tura a dawo mini da ke, ina son ganinki sosai" "Wallahi Daddy nima ina son in ganka, kuma ka kusa komawa aiki ko?" "Eh Meenal, hutuna ya kusa ƙarewa" Ta ɗan langaɓar da kai ta ce "Shikenan idan ka tafi na daina ganinka sai a waya?" "Will you miss me?" Yayi maganar yana ƙasa da muryarsa. "Zan yi mana sosai" "Ai zamu dinga waya, kin san kina dawowa zaku yi tafiyar nan, ki cigaba da karatunki kin ji" "To Daddy amma daia zaka zo Abujan?". "Babu tabbas, zan tura Khalil dai lokacin zai yi clashing da time ɗin aikina" Ai sai Amina ta fara kuka tana diddira ƙafa "Daddy ba fa haka muka yi da kai ba, ni dai dan Allah ka zo, ko in fasa zuwan" Daddy ya ɗan buɗe baki ya ce "Ki fasa zuwan, da kuwa munyi faɗa da ke" "To dan Allah ka zo" shiru yayi yana sauraren yadda take masa shagwaɓa, ya lumshe idanunsa yana shafa ƙirjinsa, ya ɗan jaa numfashi ya ce "Meenal" "Na'am" "Bana son rigima, ki cigaba da karatunki, zan turo a ɗaukeki jibi in sha Allah" "Daddy" "Shhhhhh, maza kiyi abin da nace" Ta rausayar da kai ta ce "To shikenan" Ya ce "Yauwa Meenalina" "To daddare zaka kirani?" "Dare lokacin matata ne, sai da safe kuma in Allah ya kaimu" shiru tayi ba tayi magana ba. "Hello, kina jina?" "Eh, ina jinka" tayi maganar tana jin haushin amsar da ya bata ɗazu. "Za muyi Video call da safe in sha Allah, ina son in ganki" "Da safe aiki zan yiwa Inno" Sai da dariya ta kusa ƙwacewa Daddy, ya ce "Idan kin gama aikin zan kiraki, ki ce ina gaisheta" daga haka ya katse kiran. Ajiye wayar Amina tayi, tana hararar wayar. Amina ta sada zumunci sosai a ƙauye, wasu ta burgesu matuƙa da suka ganta, wasu kuma ƙanan maganganu suka cigaba da yi a kanta. Babu kunya babu tsoron Allah, Jarmai ya cigaba da sintiri a wurin Amina, bayan ba irin cin mutuncin da ƙagen da bai yiwa Aminan ba, bayan barinta ƙauyen. Kwanan Amina huɗu ta fara haɗa kayanta, ji take kamar karta tafi, tun ana ya gobe zata tafi, Daddy yake kiranta a waya, yana jadadda mata ta shirya da wuri, zai aiko a tafi da ita. Ƙarfe sha ɗaya na safe, Amina ta gama shirinta, yaran Baffa Lawan suka shigo gidan wai ga 'yan sanda nan, Amina ta zo. Inno ta dafe ƙirji ta ce "'yan sanda kuma, meye haɗinmu da 'yan sanda?" Amina ta ce "Bari in leƙa in gani" Amina ta saka takalmanta, ta leƙa waje, motoci uku ta gani, da kuma 'yan sanda suna kaiwa suna komowa a ƙofar gidan, yara da matasa suka tsatstsaya suna kallo. Baƙin glashin wata mota aka sauke, saiga Alhaji Ahmad a ciki a zaun, yana sanye da baƙin glass, da dark blue ɗin shadda ba ƙaramin kyau yayi ba. Buɗe baki Amina tayi da mamaki ta ce "Daddy" Alama yayi mata da hannu, tazo. Ƙarasasa Amina tayi gaban motar tana masa murmushi. "Daddy dama kai zaka zo ka ɗaukeni?" "Eh mana ba gani ba, i hope kin gama shiryawa?" "Na shirya, amma zaka zo ku gaisa da Inno ko?" Daddy ya ce "Eh mana, je ki mini iso" "Amma baka gaya mini zaka zo ba, da na maka girki" "Kar ki damu, jeki mini iso mu gaisa" Da sauri Amina ta nufi cikin gidan tana kiran Inno. "Ke lafiya, meya kawo 'yan sanda?" Cikin washe baki Amina ta ce "Inno Alhaji Ahmad ne fa, zai zo ku gaisa" Amina bata tsaya ƙarasa yiwa Inno bayani ba, ta ɗauko uwar tabarma, ta shimfiɗa a tsakar gidan, ta ce "Inno ki sako mayafinki bari in ce ya shigo". Tare da Amina suka jero suka shigo, ya samu wuri ya zauna a kan tabarma, Inno ta fito suka gaisa, ta shiga jero masa godiya, amma ya ce ba komai karta damu, ya zo tafiya da Amina ne, saboda makaranta. Inno ta zubo man shanu fal da fura ta bawa Alhaji Ahmad, ya karɓa tare da yi mata godiya. Amina ta kai Akwatinta mota, Inno ta rakota har ƙofar gida, a nan suka iske su Bala. Amina ta ce "Daddy, ga 'yan uwan mahaifina nan, ga Baffa Lawan da Baffa Bala" Ta kalli su Bala ta ce "Baffa, ga Alhaji Ahmad, wanda muke zaune a gidansa ni da Baba. Saboda tsananin kwarjini Alhaji Ahmad, haka suka zube jiki na rasa suka gaishe shi, ya amsa musu yayi musu alheri, sai dai sai da Amina tayi kuka da taga zata tafi ta bar Inno. A motar da Alhaji Ahmad ya ke Amina ta shiga, yara suka taru suna ɗaga musu hannu suka bar ƙauyen. "Daddy, wai yana ganka da 'yan sanda kamar zaka kama mai laifi?" "Saboda tsaro, ai a ƙa'ida ina yawo da su saboda tsaron lafiyata, yanzunma dan doguwar tafiya zan yi ne, amma Allah ne ke karewa ai" Ta ɗan kalli Daddy ta ce "Mmn kayan nan sun maka kyau, kamar wani ango sai ƙamshin turare kake" Daddy ya gyara hular kansa ya kalleta ya ce "Kamar wani ango ko? Zaki maimaita a gabanta" Amina ta tsuke fuska ta ce "Ita wa?" "Lovely Zeena" Ta ɗan taɓe baki ta ce "Lovely manya" "Ke, kin fiye tsaurin ido fa, wai me matata tayi miki ne kike kishi da ita?, gaya mini gaskiya what is in your mind about her husband?" Yayi maganar muryarsa can ƙasa. Amina ta kalleshi ta ce "Like?" "Nothing" daga nan yaja bakinsa yayi shiru. Ko da suka isa cikin garin Kano, maimakon su wuce gida, guest house ɗinsa suka wuce. Amina ta kasa yin shiru ta ce "Daddy ya na ganmu a nan kuma, ba gida zamu wuce ba?" "Eh ba gida zamu wuce ba" yayi maganar ransa a haɗe dan kar ta sake yi masa wata tambayar. Gaba ɗaya ba haka ta so ba, da aka yi parking ma bai ce ta sauko ba, dan kanta ta sauko tabi bayansa. Sai da suka je tsakiyar falon gidan, sannan ya kalleta ya ce "Ki shiga wancan ɗakin, kiyi sallolinki, za a kawo miki Abinci ki huta da la'asar Zakiru zai zo ya kai ki gida" Jiki a sanyaye ta ce to, dan ita duk ba haka ta so ba. Ta ware mayafinta ta yafa sosai, tayi sallar azahar, tayi adduointa, ta kira Inno ta sanar mata sun sauka, yanzu zasu ƙarasa gida, sun ɗan jima suna waya sannan Amina ta kashe wayar. Ajiye mayafinta tayi a kan gadon dake ɗakin, ta tafi gaban mudubi tana duba fuskarta, ta kwance ɗan kwalin kanta tana sake gyara shi, kawai aka turo ƙofa, tsayawa yayi a bakin ƙofar yana ƙare mata kallo, gaba ɗaya sai ta ɗan rikice, gashi tayi nesa da mayafinta da ke kan gado. Lumshe idanunsa yayi ya buɗe, kamar wanda aka yiwa dole ya ce "Zo ki karɓa" yayi maganar yana miƙo mata leda. Kasa motsi tayi daga in da take tsaye, saboda kunya da ta gama mamayeta. "Meenal, am talking fa" Sunkuyar da kanta tayi ƙasa, ta fara tafiya a hankali, tana jin yadda idanunsa ke yawo a jikinta, ta ƙarasa in da yake tsaye ba tare da kalleshi ba. "Menene? Ya naga kina sunkuyar da kai meyafaru" Yayi maganar tamkar bai san meya sanyata cikin ɗari-ɗari ba. "Babu komai" ta faɗa ba tare da ta kalleshi ba. "Ga Abinci nan, da kin yi sallar la'asar kije haraba Zakiru na jiranki, ni zan tafi yanzu, zanje wani wuri" Ta karɓi ledar hannunsa ta ce "Na gode" Kamar yadda ya gaya mata, bayan sallar la'asar ta tarar da Zakiru a harabar gidan yazo ɗaukarta, ita har mamaki ma take yi, Daddy baya tsoron ko Zakirun ya gayawa Hajiya Zainab cewar suna yawo tare, har gidansa ya kai ta. Zakiru bai nuna mata komai ba, sai tambayarta ya ta baro mutan gida, a haka har suka isa gida. Baba na ganinsu ya taso da murnarsa zuwa wurin motar, Amina ta fito tana masa murmushi tare da gaishe shi. Ya amsa mata cikin sakin fuska ya ce "Ya hanya, ya babar taki?" Amina ta ce "Lafiya lau Baba, kamar kar in dawo gida da daɗi" Baba yayi murmushi ya ce "To ko zaki koma ne?" "Ai Baba ba dan wannan tafiyar ta makarantar mu ba, da ba zan dawo yanzu ba" "To shikenan, maza shiga ciki ki samu ki huta" Amina ta juya ta ɗau Akwatinta da Zakiru ya fito mata da ita, Baba sai sannu yake masa, Amina ta ja Akwatinta zuwa cikin gidan. A falo ta tarar da Hajiya Zainab da ƙawayenta su Turai, sun ci Abinci duk sun bar kwanukan. Amina ta ce "Ina wuninku?" A yamutse suka amsa mata, dan Hajiya Zainab bata amsa ba, sai ma kallonta da tayi ta ce "Zo ki kwashe kwanukan nan" Mamakine ya kama Amina, Hajiya Zainab dai ba makauniya ba ce ba, taga Akwati a hannunta yanzu ta dawo, amma saboda tsabar son ta wulaƙantata wai ta zo ta kwashe kwanuka. "Ko ba zaki zo bane, kika cake a wurin kina kallona?" Amina ta jingine Akwatin, ta zo tsakiyar falon, ta kwashe kwanukan ta kai Kitchen, ta zo kuma kwashe sauran, Mummy ta kuma kallonta ta ce "Idan kin gama, na fito da labulaye na barsu a kan gado, zaca cire na part ɗina gaba ɗaya a sanya wannan, Carfet ɗin bedroom ɗina ma, zaa a canza wani, wannan fita da shi za ai, Zakiru ya kai shi Car wash. Amina kawai ta jinjina kai ta tashi, ta kai kwanukan ta dawo ta ja Akwatinta. Hajara ce ta fito daga ɗakinta, sanye da hijjabi alama salla tayi, ta washe baki tana faɗin "Amina ashe kin dawo ya hanya?" "Lafiya lau Hajara, ya aikin?" Hajara ta kwaɓe fuska ta ce "Aiki gashi nan, kin tafi kin barni, matar gidan nan da alama akwai abin da yake damunta, kullum cikin sauke mini kwandon bala'i take, da na motsa sai hantara, haka ita ma 'yar ta ta, kai wanan masifa ni Hajara wanan mutane kamar gadonta suka yi" Amina ta ɗan taɓa baki ta ce "To Allah ya kyauta". Hajiya Turai ce ta kalli Hajiya Zainab ta ce "Ita kuma wannan 'yar aikin taki daga ina na ganta da uwar akwati?" "Wai nan ƙauye ta je" Turai ta ce "Ni fa gani nayi tana wani ƙara kyau" "Ke ni bar ni da zancen banza, Hajiya Salma, ya batun yarinyar nan da kika ce in haɗata da Khalil, da wuri zan duk abin da ya dace, kan ya lallaɓa ya koma wurin waccan shahshashar ban sani ba" Hajiya Salma ta ce "Karki damu duk ranar da kika shirya, ki zo muje kiga yarinyar" "Allah ya kaimu jibi, zan zo muje" Amina ta shiga aikin canza labulaye, kamar yadda Hajiya Zainab ta umarce ta, Amina ba ta gama aikin nan ba sai bayan sallar isha'i, gaba ɗaya ta gaji. Kasancewar tafiyarsu ta ƙarato, ya sanya Amina ta duƙufa cigaba da bitar karatun da tayi, ana sallar isha'i, ta shige ɗakinta, hatta Abinci a ɗakinta ta ci. Wajen sha ɗayan dare ta ga kiran Daddy, ta ɗaga ta saka wayar a handsfree taƙi magana. A hankali ya ce "Meenalin Daddy" "Na'am" "Au na zaki kulani ba, ki ka ɗaga wayata ki ka yi shiru?" "Ai kaima watarn haka kake mini" "To naji, zan samu tea?" Amina ta ɗan tura baki ta ce "Ni gaskiya a gajiye nake, daga dawowata aka sani canza labulaye da Carfet, da nayi niyyar ko girki na yi maka, amma ko akwatina ban ajiye ba aka sani aiki" "Waye ya saki aikin?" "Ai kai ma ka sani" "To shikenan naji, da safe idan Allah ya kaimu, ki mini girki kin ji Meenalina, am missing your delicious food, kuma kinga kin fi kowa sanin Abincin da ya dace da ni" Ta yi wani murmushi kamar tana gabansa ta ce "I Will in sha Allah" "Ranar Wednesday zaku tafi, so ki cigaba da shiri, idan da wani abu da kike buƙata ki sanar da ni" "Eh, abu ɗaya nake so" Cikin zaƙuwa ya ce "What it is?" "Your presence their" tayi maganar a shagwaɓe. "Rigimar ce ko, sai da safe" ya kashe wayar. Ajiye wayar tayi tana cigaba da mita, ta mayar da hankali ga karatunta. Cikin rashin samun mafita, da rashin karsashi Khalil ya kira Mummy a waya, sai da ta kusa katsewa sannan ya samu ga ɗaga. "Yau ka ga dama ka neme ni kenan?" Yaji muryarta maimakon ko gaisawa ta bari suyi. A saɓule ya ce "A'a ba haka bane, bani da lafiya ne" "Eh, ko ba baka da lafiya ba? Kana fama da ciwon so ko, gubar Asirin da suka zuba suka baka a Abinci bata sake ka ba, to ka sani in kai sun shanye ka ni basu shanye ni ba". "Mummy dan Allah duk a bar wannan maganar, ni kiranki nayi na gaisheki" "Ka riƙe gaisuwarka bana so, jibi in Allah ya kaimu zanje naga iyayen yarinyar da na zaɓa maka, next za a kai kuɗin Aurenka da ita" "Innalillahi wa innalillahi raji'un, dan Allah Mummy kar ki mini haka" "Ai tuni ma an riga an yi, idan ka ga dama kayi mini biyayya, idan ba ka ga dama ba kabi 'yar matsiyata mai awara a hanya!! AYSHERCOOL 08081012143GABA DA GABANTA BY AISHA ADAM AYSHERCOOL 46 Baki na rawa Khalil ya ce "Dan girman Allah Mummy ki tsaya ki ji" "Ubanka zan ji, rufan baki zaka gane kurenka" Ta kashe wayar, Khalil ya dafe kansa yana jin wasu zafafan hawaye suna zubo masa, ba tausayin kansa yake ji ba, tausayin Hafsa ya fi cika masa zuciya, saboda bai san wane irin mutum Allah zai haɗa Hafsa da shi ba. Kankiya ne zaune a office ɗinsa tare da wasu abokan aikinsa, suna ta hayaniya da surutu. Suka ɗan tsagaita Kankiya ya ce "Wallahi baku ga rashin mutuncin da yarinyar nan tayi mini ba, duk yadda ɗalibai ke shakkata amma ta yarfa ni yarinyar nan, wallahi ban da ina sonta da saina wahalar da ita wallahi" "To kai Kankiya, ya aka yi ka bari har ta rainaka haka ne?" Kankiya ya ɗan taune leɓensa na ƙasa ya ce "Bari kawai TJ, ni ban taɓa ganin yarinyar da na nuna ina so ba, sai ita, amma sai wulaƙantani take yi, ta tsaya tana saurar wani sakaran yaro, dan ina sonta ne, ba yadda zan iya da ita, kuma da alama babanta mai faɗa aji ne, shi Wannan Yaron zan wulaƙanta in ga ta tsiya" TJ ya ce "Ka bari sai exams, kai ta gara shi, kana dawo da shi" "Ai ba sai ka faɗa ba, nace no Attendence no exams, kuma na hana shi zama a ajina, naga idan na taɓa shi tana jin haushi" Suka cigaba da tattaunawa a kan Yadda Kankiya zai yi da Yazid. Kamar yadda Daddy ya buƙata, da sassafe kan Amina ta tafi makaranta, tayi girki, ta je ta shirya a dining. Ta koma ɗakinta ta tura masa saƙo "Na gama Abinci, ka fito in ganka kan in tafi" Yana zaune ya idar da azkar, yana duba muhimman saƙonni a wayarsa, saƙonta ya shigo ta what's app. Murmushi yayi ya kirata video call, tana tsaye ɗaure da towel, tana jira ko zata ga saƙon Daddy kan ta shiga wanka, sai ga video call ya kirata, bisa rashin sani tayi zaton Voice call ne, kawai ta ɗaga kiran. Da fari bata lura ba, ta ajiye wayar tana neman comb, tana ta hello. Sai da ta ɗago ta ga kyakkyawar fuskarsa ta bayyana a kan screen ɗin wayarta. Wata 'yar ƙara ta saki ta cilla wayar kan gado, tare da dafe ƙirjinta, gaba ɗaya ba ta sa Video call ne ba ta ɗaga kiran, ya ganta babu mayafi yanzu kuma ya ganta daga ita sai towel. Wani Irin haushi ne ya kama Amina, gaba ɗaya taji wata irin kunya da haushin kanta sun kamata, tare da zargin kanta mai yasa bata duba ba ta ɗaga, yanzu ma sai ya yi zaton ko tana sane ta ɗaga kiran. Jiki a sanyaye haka tayi wanka, ta fito ta shafa mai ta saka uniform, ko karyawa ba tayi ba, ta ɗau jakarta, ƙarfe bakwai da kwata ta lallaɓa ta fice, tana fatan kar su haɗu. Sai dai tana fitowa ta ganshi a kan kujerar da ke facing ɗin ƙofar da zata fito, ya zubawa ƙofar ido. Ji tayi tamkar ta koma ciki da gudu, amma ya riga ya ganta, ta fito kanta sunkuye, ko ɗago kai ta kasa yi balle ta kalleshi, ta dinga jin tamkar ƙasa ta tsage ta shige ciki. Kanta a ƙasa haka ta ce masa ina kwana, amma ya ƙi amsawa ya cigaba da kallonta. Har ta kai ƙofa ya ce "Amina" ta tsaya cak bata waiwayo ba. "Zo" yayi maganar fuskarsa babu wasa. Ta juyo ta dawo kanta a ƙasa, ta zo gabansa ta durƙusa. Yayi ƙasa da muryarsa ya ce "Mun yi faɗa ne?" Ta girgiza masa kai. "To ba faɗa meye yasa kike sunkuyar da kai ko kulani baki ba?" "Ai na gaisheka baka amsa ba" "Banji bane, kince in zo ki ganni, kuma na fito baki kulani ba" Amina ta ɗan yi Jimm ta ce "Dama ba komai" Fadila ce ta fito, hannuta riƙe da mukullan motarta, da kuma jakarta. "Daddy good morning" Cikin sakin fuska ya ce "Morning dirling, how are you?" Ta kalli in da Amina ke durƙuhe a gaban Daddy, ba ta kawo komai a ranta ba ta ce "Daddy bari in karya in wuce school" Ya ce "Ok, yaushe za kuyi hutu ne, a fara shirin tafiyarku ke da Mummynki?" "In the next couples of week in sha Allah" "Shikenan, Allah ya taumaka ya bada sa'a" "Amin Daddy" ta nufi dining domin ta karya. Ya kalli in da Amina ta sunkuyar da kai ya ce "You can go" Amina ta miƙe ba tare da ta ɗago ta kalleshi ba, ta juya ta bar falon. Amina ta fara zuwa suka gaisa da Baba sannan ta tafi makaranta, da aka tashi sai da ta biya gidansu Azima, ta haɗa Maman Azima da Inno a wayar Ammin Azima suka gaisa, ta bawa Ammin Azima tsarabar. Ammin Azima ta na matuƙar son Amina, jin ta take tamkar 'yar da ta haifa, sai la'asar sannan Amin ta tafi gida. Sai da Baba ya yambayeta a ina ta tsaya, ta gaya masa taje gidansu Azima ne ta kaiwa Mamanta tsarabar da Inno ta bayar a kaimata. Wasa-wasa aka shiga wasan ɓuya tsakanin Amina da Alhaji Ahmad, in dai ta san zata ganshi, ba ta fitowa kuma ta kashe wayarta gaba ɗaya, dan karma ya kirata. Hajiya Zainab tare da Turai da Salma, suka shirya suka je gidan ƙanwar Hajiya Salma, wato Hajiya Badi'a. Gida ne na alfarama, kai da ganin gidan ka san suna da abin hannunsu, Mummy ta washe baki, dan irin mutanen da take son su haɗa zuriya kenan, bata fatan talakawa su raɓi zuriyarta sam. A katafaren falon Hajiya Badi'a tasa aka sauke su, ba laifi ta karɓesu cikin mutuntawa, dama sun san juna Hajiya Zainab da Hajiya Badi'a, su kan haɗu a sha'anin Hajiya Salma, amma ba ta taɓa sanin tana da 'ya mace ba. A lokacin Hajiya Salma ta yiwa Mummy bayanin cewa, Kursum ba ta gari ne tana karatu a ƙasar waje, shi ya sanya bata santa ba. Sun taɓa hira sosai, sannan Hajiya Badi'a ta kira Kursum dan su gaisa. Duk ramar Fadila Kursum ta fita, ga ta da wani irin haske gauuu babu kyan gani, kai da ka gani ka san ba farinta bane, tayi fixing nails ta musu fenti, haka ta fito soƙai-soƙai kamar raƙumar dawa. Cikin iyayi ta ɗan lanƙwasa ta ce "Ina wuninku?" Suka amsa mata da lafiya ƙalau. Ta kalli Hajiya Salma ta ce "Mummy, yau nace zan zo gidanki" "Ba wani nan, dan kin ganni ne shi ne zaki wani ce yau zaki zo gidana" Nan suka gabatar mata da Hajiya Zainab, da abin da suke buƙata, har muƙaman Alhaji Ahmad sai da aka gayamata, suka nuna mata hoton Khalil. Ba kunya a gabansu ta ce musu ta amince, da ma duk samarin nata ba wani tsayayye sai watsatstsu, ga Khalil ya haɗu ta ko'ina, a nan Hajiya Zainab ta tabattarwa da Hajiya Badi'a cewar kan su tafi umara, ko da zarar sun dawo, za a kawo kuɗin Aure. Kursum ta ce "To amma shi yaushe zai zo?" Hajiya Zainab ta ce "Kar ki damu, da zarar ya shigo Kano, zai zo ku gaisa" Hajiya Salma ta ce "Kaga mara kunya tambaya ma kike yaushe zai zo ko?" Kursum ta tashi tana murmushi ta bar falon gaba ɗaya. Makarantar su Amina suna ta preparing ɗinsu a kan tafiyarsu, suna ta gaya musu ƙa'idojin da zasu kiyaye, da jadadda musu ranar tafiya kar wanda ya makara. An tashi daga makaranta, Amina na tafe da ita da Azima, wata Perfect ta sanar da Amina ana nemanta a Office ɗin director. Ba tayi tunanin komai ba, ta cewa Azima ta jirta ta je ta dawo, sai dai tana shiga da Daddy ta fara tozali, idonsa cikin nata, tayi saurin ɗauke idonta ga sunkuyar da kai ƙasa. Ta ƙarasa ciki, ta gaida director ta gaida Daddy ya amsa mata yana kallonta. Director ya ce "Amina, an zo musamman ana kafa mana dokoki a kanki, mu kula da ke sosai". Amina dai ta sunkuyar da kai tana wasa da yatsun hannunta. Daddy ya ce "Idan kun isa can Abuja, in kun sauka, za a tura direba ya ɗuke ki sai lokacin da zaku fara competition ɗin za a dinga kai ki, ba zaki zauna a hotel ba" Ta jinjina masa kai kawai. "Shikenan tashi mu tafi gida" ta miƙe ta bar Office ɗin, Daddy yayi sallama da director, ya bi bayan Amina. Azima kuwa da ta gaji da jira, sai tayi tafiyarta, saboda kwanan nan kusan kullum cikin kiran su Amina ake, saboda tafiyar da za suyi. Daddy ya ƙaraso ya buɗe motar, ta shiga shi ma ya zaga ya shiga. Gaba ɗaya ta zama wata iri, kamar ba ita ce take masa surutu kala-kala ba, ta koma kamar wata baƙuwa ta kasa sakin jikinta, ko haɗa ido taƙi bari su yi. "Kin gama guje-gujen?" Ta girgiza kai. "Yi magana mana" tayi shiru ba tace komai ba. Murmushi ya yi ya ce "kawai kiji kamar babu abin da ya faru, banga komai ba ki manta" wata Kunya ce ta sake kama Amina, ya dai ganta da towel ɗin kenan?. 'yanzu gaya mini me kike buƙata, mai zan saya miki?" Zumɓura baki tayi ta ce "Ni bana son komai" "Meyasa?" "Bayan kace ba zaka ba" "To ai Khalil zai je, zai wakilceni" "Ni Khalil ɗin da baya kulani, ni kai nake son ka zo" Ya ɗan shafi gemunsa, wanda hakan ya zamo kamar ɗabi'arsa ya ce "Ni wurin aiki zan koma, idan Khalil ɗin ma ya zo ai duk ɗaya ne" Ɗauke kanta tayi tana tura baki, ita ba haka take so ba. Ɗan leƙa fuskarta yayi ya ce "Meenali na" "Ba wata Meenalinka" Yayi murmushi ya ce "Tawa ce mana" "Amma na roƙi abu ka ƙi yi mini" tayi maganar tana masa wani irin kallo, da yake kai wa zuciyar Alhaji Ahmad wasu irin saƙonni. "Ke idan baki yi rigima ba ba kya jin daɗi ne?" "Kaifa kace in dinga tambayarka abin da nake so" "To ai duk cikin abin da kike tambaya wannan ne kawai ba zai yiwu ba" Ta ce "Ai shikenan" tayi maganar tana sake ƙanƙame jakarta, tana kallon titi. "Meenal, idan kunje ki kula da kanki sosai, ban da yawo, banda rashin ji, ki yi ta Addu'a Allah ya baku nasara, ya sa a samu abin da aka je nema" "Amin, zan kiyaye idan Allah ya yarda" "Yauwa Meenalina, yau zan samu Coffee ɗin dare?" Ta ce "To, amma a dining zan ajiye maka, ka fito ka sha, ni bana son abinda zai haɗani da ita, kuma ni gaskiya tsoro nake ji, kullum in dinga zuwa falonka, ga Hajara ta saka mini ido, kuma idan matarka ma ta ga ina yawan zuwa wurinka ta ritsani ni me zance mata?" Sai da ya bari ta gama wassafa bayananta sannan ya kuma cewa "Can i get a Coffee tonight?" A duk lokacin da yayi irin wannan, ta san yana son tabattar mata he is serious. Jinjina masa kai tayi alamar eh, ya cigaba da tuƙinsa sannan ya ɗan nisa ya ce "Idan na baki umarni, ko na nemi abu a wurinki, bana buƙatar ki kawo mini ko wane irin excuse, ina fatan kin gane?" "Eh na gane, kayi haƙuri" bai ce mata komai ba suka cigaba da tafiya. Gaba ɗaya a wannan karon karatun jarrabawa ba ya yiwa Fadila daɗi sam, dan abubuwa da yawa idan Yazid ya koya mata tafi ganewa kuma ta riƙe, amma wannan karon ita kaɗai take karatunta, gashi wayar ta sa ma taƙi shiga gaba ɗaya, kullum sai a ce mata tana rufe. Tana matuƙar tausayinsa da jin damuwar rashin zuwansa makaranta, amma babu wanda ta gayawa, ciki har da Yusra, dan ita bata son Yadda Yusra ke ƙoƙarin nuna mata cewar tana son Yazid. Yau kamar Hajiya Zainab ta san Alhaji Ahmad ya shirya ganin Amina, taƙi yafiya ta je ta kwanta, ta saka shi a gaba a kan lallai sai ya bata kuɗin da ta nema a wurinsa na zata ƙara jari, shima kuma kamar ya san da wata a ƙasa sai ja mata rai yake, ya ce yau ya ce sai gobe, ba kuma dan ba shi da su ba, sai dai ya ce a cikin satin zai bata, sannan hankalinta ya kwanta, ta amince ta sako masa wata hirar kuma. "Baban Khalil, yau na yiwa Khalil mata" Daddy ya ce "To, Mata a ina kenan?" " 'yar ƙanwar hajiya Salma ce, yarinyar nutsatsiya da ita, na yaba da ita sosai ga ta 'yar babban gida" Ya ɗan kalleta sannan ya ce" Shi Khalil ɗin ya amince da hakan ne?" "Ai kamar punishing ɗin sa zan a kan abin da yayi mini, kuma na san ba zai ƙi ba zai so ta ya manta za waccan yarinyar" Ya ɗan ɗage kafaɗa ya ce "Ok, shikenan, Allah ya tabattar da Alkhairi" Ta gyara zamanta ta ce "Amin, amma nan kusa nake son a kai kuɗin aure, ko kan mu tafi umarar nan ne" Daddy ya ce "No, akwai wani abu da nake yi, sai na kammala zuwa idan kun dawo daga umarar, zan ga uban yarinyar tukuna" To shikenan na gode sosai. Tayi maganar tana murmushi, ita dai idan har kaga walwala a fuskarta, to an biyewa ra'ayinta ne, ko da kuwa son zuciya ne. Suna nan zaune suna hira, Amina tayi sallama ta kai masa tea. Hajiya Zainab ta kalleta a wulaƙance ta ce "Waye ya saki wannan aikin, an ce miki muna buƙata ne?" Daddy ya yi saurin cewa "Ni nayi musu Magana ɗazu, na ce a kawo mini tea, zan yi aiki da daddaren nan" "Ok ban sani bane" tayi maganar ba tare da zurafafa bincike ba. Amina dai ta ajiye kayan shayi tayi waje abinta, taji daɗin tarar da Hajiya Zainab da tayi, ba damar Daddy ya tsareta ya hanata tafiya. Ana ya gobe su Amina za su yi tafiya, Baba ya kira Amina, ya zaunar da ita ya dinga yi mata nasiha mai shiga jiki sosai. "Uwata, kinga ni dai zuwanki birni na barki ne dan ki samu ki cika burinki, na yin karatu, bani da burin da ya wuce ki samu ingantaccen ilimi, ki samu miji nagari, kin san ɗauki ba daɗi da kuma irin miyagun alkaba'in da aka dinga janyo mana, duk saboda na goyi bayan ki zauna da ni a nan kiyi karatu, dan Allah Amina kar ki bani kunya, kinga in da zaki tafin nan, baki da kowa sai Allah, dan Allah ki mayar da hankalinki, ki nutsu kiyi abin da kika je yi, ki riƙe mutuncinki, ba danni ba ba dan halina ba ki kula da kanki Amina, ki kula da mutuncinki, kije lafiya ki dawo lafiya, dan Allah kar ki watasa mini ƙasa a ido". Gaba ɗaya jikin Amina yayi sanyi, ta ce "In Allah ya yarda Baba, ba zan baka kunya ba, ba zan aikata duk wani abu da ya saɓawa abin da ka ɗorani a kai ba in sha Allah" "To madalla, Allah ya bada nasara, Allah ya kiyaye ku, Allah ya kaiku lafiya ya dawo da ku lafiya, ya bada abin da aka je nema, da salularki zaki tafi ko?" "Eh Baba, sunce zamu iya zuwa da ita" Baba ya ce "Yauwa, na dinga kiranki, in ji abin da ake ciki, zan so in rakaki ko makarantar ne, amma kin san idan nayi yinƙurin hakan, mutan gidan za su kya cewa nayi laifi" Amina ta ɗan gyaɗa kai ta ce "Zan so ka rakani Baba, amma bakomai Allah ya nuna mini ranar da zan rabaka da aikin nan, mu ci gashin kanmu" Baba yayi murmushi ya ce "Amin uwata" Sosai nasihar Baba ta ratsa Amina sosai, ta koma cikin gida, gefe ɗaya tana murna za tayi doguwar tafiya ta bar Kano a karo na farko a rayuwarta, wani sashin na zuciyarta tana fargabar ba ta san yadda tafiyar da competitions ɗin su zasu kasance ba. Amina tayi ta saka ido, ko Daddy zai yi mata sallama ko su haɗu amma bai nemeta ba, gaba ɗaya sai taji babu daɗi hakan, har ta shirya da sassafe cikin goggagun uniform ɗinta, tayi kyau sosai, amma Daddy bai fito ba, a wannan karon Hajara ce ta kai mata Akwati har gaban mota, Fadila na kallonsu suna ta shirin tafiya, amma ko kallo ba su isheta ba. Baba yayi ta yi mata nasiha da Addu'a. A wannan karon ma, Zakiru ne ya kai ta har makaranta, tuni an fito da zungureriyar motar makarantar su, sauran ɗaliban da ba da su za a je ba suka fito harabar makarantar ana kallonsu, ana ɗaga musu hannu, su Amina suka ɗuru a motar makaranta, suka kama hanya. KU BIYONI BABBAN BIRNIN TARAYYA DOMIN JIN YADDA ZATA KAYA. AYSHERCOOL 08081012143GABA DA GABANTA BY AISHA ADAM AYSHERCOOL 47 Hausawa suka ce tafiya mabuɗin Ilimi, Amina ta ga abubuwa da dama, wanda tun da take bata taɓa barin garin Kano ba, amma sai gata a hanyar babban birnin tarayya Nigeria wato Abuja, suna tafe a hanya ana tsayawa masu uzuri su yi da cin abinci, Baba yana ta kiranta a kai a kai yaji ya hanya, haka ma Ammin Azima tana kiranta, sai kuma ita da take kiran Inno, sai dai sam Daddy bai kirata ko sau ɗaya ba. Sai Azahar su Amina suka sauka garin Abuja, a wani katafaren hotel da aka kama saboda saukar ɗaliban, Amina ɗakin da aka ajiyesu su uku ne a ciki. Amina taji shiru, Daddy ya ce mata za a zo a tafi da ita gidan Abokinshi in da zata zauna, amma taji shiru, ita ba rashin tafiya da ita gidan abokin nashi ne ya dameta ba, rashin jin ɗuriyar Daddyna ne ya dameta. Har zuwa dare bai kirata ba, dan haka ita tayi kasadar kiransa, domin jin ko lafiya. Sai da ta kusa tsinkewa sannan ya ɗaga wayar, cikin kamilalliyar muryarsa ya yi mata sallama. Ji tayi kamar ta kashe wayar, dama yana nan normal amma yaƙi kiranta yaji ko sun sauka lafiya. Muryarsa ta ji ya ce "Yaya kuma ki ka yi shiru? Akwai damuwa ne?" Wani haushin ne ya sake kamata, wasu lokutan Daddy akwai iya kunna mutum. "Bakomai" ta bashi amsa a taƙaice. Ta kasa kuma cewa komai, shi ma kuma bai sake cewar ba duk suka yi shiru, ƙarshe Amina ta gaji ta kashe wayar ta ajiye. Jin ta kashe wayar ya sanya Daddy sauke wayar daga kunnensa, ya bi wayar da kallo yana murmushi, ya ɗan kashingiɗa ya ce "Meenal kenan, dole ki saba da shiga damuwa a duk lokacin da kika mini laifi, na fuskanci wannan shi ne hukuncin da ba kya so" Ya sake ɗaukar wayar, ya shiga gallery lock ɗinsa, in da yake adana hotuna, yana kallon hotunan ta, wasu hotunan shi ne yayi mata su, wasu kuma shi ya saka ta tura masa, ya dinga kallon hotunan yana murmushi, ya tsaya a kan wani hotonta da take sanye da uniform, ta goya jakarta tana murmushi, ƙuruciyarta ta fito sosai musamman yadda ta riƙe hannun jakar bayan ta goya jakar. Ɗora wayar yayi a kan ƙirjinsa, yana jin wani al'amari yana fuzgarsa a game da Aminan. A yau ne su Fadila zasu fara jarrabawar second semester, sai dai ta kasa zaune ta kasa tsaye, saboda rashin ganin zuwan Yazid, haka nan taji hankalinta ya tashi, bata son ya rasa jarrabawar nan. Kan ta shiga ajin ta samu wuri ta tsaya, ta kira shi a waya, sai dai wayar tayi ringing bai ɗaga ba. Haka ta shiga ajin ta zauna, aka farra jarrabawa, amma babu Yazid babu dalilinsa gaba ɗaya sai ta kasa nutsuwa ta kasa rubutun jarrabawar, ji take ina ma zata iya yi masa jarrabawar bata manta taimakon da yayi mata a baya ba. Jin ɗaya daga cikin invigilator ya ce "Sheikh sai yanzu?" Ya sanya Fadila ɗagowa da sauri. Kasancewar har da TJ abokin Kankiya, a malaman da suke invigilating ne ya sanya ya dakawa Yazid tsawa ya ce "Get out, saboda ba ka san darajar jarrabawar ba, shine sai yanzu zaka zo jarrabawa, ka yi asararta kuwa, gobe idan kana so ka zo da wuri" Ɗaya malamin ya ce "A'a yi haƙuri, na san ba zai makara intentionally ba, ya aka yi ka makara Sheikh" Kasancewar malamin sukan haɗa jam'i da Yazid a masallacin makaranta, ya sanya ya san shi. Yazid ya ɗan yi murmushi ya ce "Afuwan Sir, na biya Asibiti ne an yi mini dressing, idan na makara ba za su yi mini ba" Malamin ya ce "Meya sameka ake maka dressing?" Yazid ya ɗan juya ya ɗagawa malamin rigarsa, sai ga plasta da aka saka a rufe masa wurin da aka yi masa aiki ya ce "An mini aiki ne, har sau biyu a wurin, ina zuwa ana wankewa duk bayan kwana uku" Fadila kuwa sai leƙawa take kamar ita yake nunawa. Cikin tausayawa malamin ya yiwa Yazid sannu, tare da bashi wurin zama, ya bashi booklet ya kai masa question paper da Attendence har wurin zamansa duk yayi, ya yiwa malamin godiya, ya fara jarrabawar sa. Sai da Fadila taga Yazid ya nutsu ya fara jarrabawa, sannan hankalinta ya kwanta, ta cigaba da tata jarrabawar, sai kuma ta tuna ai akwai abubuwa da yawa da aka yi baya nan, da yaya zai yi jarrabawar? A take ta tuna gwanancewa irin ta Yazid, ba abune mai wahala a wurinsa ba ya cinye jarrabawar ba. Sai da tayi wannan tunanin, ta samu cikakkiyar nutsuwar cigaba da rubuta jarrabawata cikin nutsuwa. Suna nan suna jarrabawa, Kankiya ya shigo yana zazzagaya su, yana wani muzurai da zare da ido, ya zo kan Fadila ya tsaya, yana kallon abin da take rubutawa, haushi ne ya kama Fadila, dan ko san ganin Kankiya bata yi, ta janye takardarta ta ajiye biron tare da haɗe rai. Yayi ƙasa ƙasa da murya ya ce "Ina son ganinki yau, idan kun gama jarrabawa" Ɗagowa tayi ta kalleshi ta ce "Ba zan zo ba" "Kin san me rashin zuwan naki yake nufi kuwa?" "Ban damu ba, kaje kayi duk abin da kaga zaka iya yi". Yayi murmushi ya ce "Kar in ɗau matakin da zuciyarki ba zata iya ɗauka ba" "Nace kaje kayi duk abin da ka ga dama, kuma ka matsa daga kaina kan in yi Magana da ƙarfi in janyo hankalin mutane kanmu" Ganin da gaske take zata aikata abin da ta ce, ya sanya shi yin gaba, yaje ya tsaya a kan Yazid ma, ya ƙure shi da ido, amma Yazid bai ko ɗago kansa ba, balle ya kalleshi, ya cigaba da rubutunsa. Yau ma bayan kammala jarrabawar, Fadila sai da ta tsaya jiran Yazid, ya fito yana takwa a hankali kamar wank basarake, nan kuwa cuta ce ta sanya shi hakan, 'yan ajin suka yi ta masa sannu. Sai da ta bari ya ƙaraso in da take tsaye sannan ta ce "Sannu ya jiki?" Fuskarsa babu yabo ba fallasa ya ce "Da sauƙi Alhamdilillah" Cike da tausayawa ta ce "Allah ya ƙara lafiya, amma kana jin sauƙi ko?" Ya kalli cikin nasa sannan ya ce "Eh da sauƙi sosai, gashi ina iya tafiya sosai, kuma har nayi exams ma" "Haka ne, amma nace naji kace sau biyu ana maka aikin, ko ka zo muje Asibitin nan da na kai ka ranar, su dubaka idan da wani sai suyi maka" Ɗan ƙureta da ido yayi sannan ya ce "Kar ki damu, Asbitinmu na talakawa ma suna kula dani, na gode sosai" daga haka bai kuma cewa komai ba ya tafi. Gaba ɗaya gani take kamar Yazid ya canza daga yadda ta san shi a baya. Kafin fara gudanar da competitions ɗin da aka kai su Amina Abuja dominsa, aka ɗaukesu a motar makaranta zuwa wuraren shaƙatawa daban-daban, da buɗe ido. Amina tana ta rehasal na abubuwan da zasu gudanar a wurin competitions, malamnsu na ta ƙara dagewa wurin tabattar da sun iya komai, saboda an gayyaci manyan mutane sosai. Ranar farko da debate suka fara, Amina tayi rawar gani, ta burge da yawa daga cikin mutanen da suka je wurin, tayi ƙoƙari sosai da sosai tayi abin da ake so, tana da confidence ga kuma demonstrating na abin da take faɗa, wanda yake nuna kai tsaye daga zuciyarta take debate ɗin, a wannan karon makarantar su Amina ta samu nasara a kan Makarantar da suka kara tare, da maki mai tazarar gaske. Sai azahar aka kammala na ranar, aka yi ta kaɗe kaɗe da raye-raye dan nishaɗantar da ɗaliban da kuma mahalarta taron. Bayan su Amina sun koma masaukinsu, malamansu suna ta jinjinawa ƙoƙarinta, tare da sake ƙarfafa musu gwiwa. Bayan sun koma ɗakin da suke, Amina tayi wanka tayi salla, ta nemi wuri ta kwanta, saboda ba yunwa take ji ba. Knocking ɗin ƙofar ɗakinsu aka yi, Amina ta tashi ta buɗe, wata malamarsu da suka zo tare ta gani a tsaye, ta kalli Amina ta ce "Ki ɗauko kayanki ki zo" Cikin rashin fahimta Amina ta ce "Ina zani?" "Ki ɗauko kizo, dai ki gani" Amina ta koma ɗakin, ta shiga tattara kayanta, wanda suke ɗakin suna ta tambayarta ina zata je, amma ta ce musu ita ma ba ta sani ba, ta ja akwatin ta futa ta bi bayan malamar. A harabar hotel ɗin suka tarar da malaman makarantarsu, "Yauwa Amina, kin ɗauko komai naki ko?" Cewar Sir Patrick. Amina ta ce masa "Eh" "Mun yi waya da director, dama kan mu taho an ce mana idan mun zo za a zo a ɗauke ki" Sai a yanzu Amina ta tuna batun zama a gidan abokin Daddy, ta gyaɗa cike da gamsuwa da bayanin da malamin yayi mata. Wata mota ce haɗaɗɗiya, mai baƙin glass tayi parking a gabansu, direban ya fito ya ɗau Akwatin ya saka a boot ɗin motar, ya buɗe mata ta shiga, tana ɗagawa malaman nasu hannu har suka bar harabar hotel ɗin, Amina ta gaida direban da harshen turanci, kasancewar shi ba bahaushe bane ba. Amina a ranta ta jin jina cewar da alama shima abokin Daddyn babban mutum ne kamarsa. Wata unguwa suka shiga, mai ɗauke da wasu irin haɗaɗɗun gidaje, kamar ba hannu ne ya ƙerasu ba, layin da suka shiga kuwa ko ina security ne suke kaiwa suna komowa, da wasu irin murguza murguzan karnuka, masu ban tsoro da suke sintiri a layin. Bata gama mamakin gidaje da karnuka ba, direban ya tsaya a bakin wani ƙaton gate, ya shiga da motar cikin gidan, yayi parking a tsakanin wasu manyan motoci dake harabar gidan. Harabar gidan kawai ba ƙaramin tafiya tayi da Amina ba, saboda yadda aka ƙawata shi, sai dai cikin gidanma akwai irin wannan karnukan, hakan ya sa taja ta tsaya a wuri ɗaya tana rarraba ido. Direban ne yayi mata jagora zuwa cikin gidan, zuba ido Amina take taga mutan gidan amma taga bata ga alamar kowa ba. Direban ya kalleta ya ce ta tsaya a nan ta jirashi, yana barin wurin tsoro ya kama Amina, ganin babu alamar motsin kowa. Bai daɗe ba ya dawo ya ce ta biyo shi. Amina ta kasa jurewa ta ce "Wai kuwa akwai mutane a gidan nan?" Ya ce "Eh, muje ki gani wurin mutanen zan kai ki" ya karɓi trolleynta, Amina dai cikin zuciyarta Addu'a ta fara yi, saboda abin ya fara bata tsoro. Wani falo ya buɗe suka shiga, wani irin sanyin AC ya daki Amina, ta tsaya tana kallon ikon Allah, wata uwar Tv dake falon kusan rabin bango, komai na falon na musamman ne. Direban ya kalli Amina ya ce ta ƙarasa . Ta kalleshi da mamaki ta ce "In ƙarasa ina? Ina mutanen gidan?". Wata kujera ya nuna mata, bata hango waye a kai, bai jira me zata ce ba ya juya ya fice. Gyaran murya yayi ya ce "Ƙaraso mana, ba a yanka mutane a gidan" Waro ido tayi jin muryar Alhaji Ahmad. Da ɗan ƙarfi ta ce "Daddy" "Na'am Meenali" washe baki tayi tare da mamakin ganinsa. Shima murmushin yayi mata ya ce "Ƙaraso mana" Ƙarasawa tayi ta zauna a kusa da shi, kamar yadda yayi mata nuni. "Daddy dama zaka zo?" "Eh mana gani na zo, saboda Meenalina ta ji daɗi" Ta ɗan tsuke fuska ta ce "Amma shi ne Daddy ko ka kirani kaji ya hanya, nayi ta kiranka baka ɗagawa?" "Kin manta da kin mini laifi kenan?" "Laifin me nayi kuma? Tayi maganar a marairaice. "Nace ki kawo mini tea, nace kar ki kawo mini saina kiraki ina son muyi magana, amma kika daidaici ina tare da Madam kika kawo mini kika yi tafiyarki" Cikin shagwaɓa ta ce "Kuma wannan har ya kai laifin da zai sa ka ƙi kiran wayata kaji ya nake nayi tafiya mai nisa?" Yayi murmushi ya ce "Har kuka sauka ina kiran malamanku ina jin halin da kuke ciki, ke punishing ɗinki nake da missing ɗina, na san shine punishment ɗin da ba kya so" "Ba wani missing ɗinka da nake, kawai dai banji daɗi bane" Ya ɗan ƙura mata ido ya ce "Wannan murnar da kike yi fa dan kin ganni" shiru tayi tana ɗan motsa baki. "Daddy nan ne gidan abokin naka?" Tayi maganar tana kallon falon. "Gidana dai" ya bata amsa. "Kai da waye a gidan to?" Tayi maganar tana waige waige. "Ni da mata ta" ya bata amsa. Ta ɗan waro ta tashi ta koma kujerar kusa da shi ta zauna. "Ya kika tashi" "Idan ta zo ta ganni a zaune a kusa da kai Allah kaɗai ya san iya zagin da zata yi mini, ni da na san ba gidan abokin naka zan zauna ba, da ba zan zo ba dan na san aiki zata yi ta sakani a nan ɗinma na zan huta ba" "Da wasa nake miki, nikaɗai ne ba tare muke ba" Amina ta ɗan yi Jimm sannan ta ce "To yaushe zaka kaini gidan abokin naka?" "A'a a nan zaki zauna" ƙwalalo idanuwanta waje ta yi ta ce "Wai mu zauna mu biyu kawai a gidan nan?" "Eh" ya bata amsa kansa tsaye. Ɗan saroro tayi tare da jin nauyin yi masa nuni da rashin dacewar hakan. Ta zura masa ido tana kallonsa, tana saƙe-saƙe a zuciyarta na yadda zata kawo uzurin da zai sa yasa a mayar da ita in da aka ɗaukota. "Ya dai, akwai damuwa ne?" Yayi maganar yana nazartar yanayin da ta shiga. Ya miƙe tsaye ya ce "Muje in nuna miki in da zaki zauna" ya ƙarasa ya janyo Akwatinta, yayi gaba ta bishi a baya a tsorace. Wani ɗan madaidaicin bedroom ne, mai matuƙar kyau da ban sha'awa, ya kalleta ya ce "Nan yayi miki ko in canza miki ɗaki?" "Yayi, amma ina jin tsoro ko zaka saka a mayar da ni can wurin 'yan makarantarmu?" "A nan zaki zauna, kuma da rana tsakar nan me zai kama ki, idan kin huta ki zo ki ci Abinci" yana gama yi mata bayani ya fice ya bata wuri. Duk da zullumin da take ciki, bai hanata ƙarewa ɗakin kallo ba, tare da jinjina kuɗin da Alhaji Ahmad yake da shi, sai dai da tuna al'umma basa amfana da wannan tarin dukiyar duk sai taji babu daɗi. Gaban mudubin dake ɗakin taje, taga wata magazine, ta ɗauka ta fara dubawa, babban abin da ya bata mamaki shi ne ganin Alhaji Ahmad ya taɓa riƙe minister, a tattaunawar da aka yi da shi. Jinjina kai tayi, gaba ɗaya yadda ya saki jiki da ita, har wasu lokutan take wuce makiɗi da rawa ne yake bata mamaki, idan kuwa hakane gaba ɗaya bashi da girman kai, haka ta nustu ta cigaba da dudduba jaridar, sai da ta kammala tsaf ta ajiye. Gaba ɗaya ta gaji da zaman ɗakin, jin ana kiran sallar la'asar ne ya sa ta shiga banɗakin da ke cikin ɗakin tayi alwala, ta dawo tayi salla a kan Carfet ɗin da ke ɗakin. Ta idar da salla da Adduointa, sai kuma ta ji duk zaman shirun ya isheta, tashi tayi ta bi hanyar da Daddy ya bi da ita, ta koma wannan ƙaton falon, amma baya nan sai TV dake tayi ita kaɗai. Hakan bata damar sake tsayawa ta kalli abubuwa yadda take so a falon, a hankali kuma ta cigaba da leƙe leƙe tana cigaba da kallon ikon Allah, gidan ba ƙaramin kyau ne da shi ba. Tuni ta manta da fargabar da take ciki, ta cigaba da buɗe wurare tana leƙawa. Faluka sun kai uku wanda ta gani, kowanne da kalarsa. Babu zato ba tsammani ta buɗe wata ƙofa, wani ƙaton ɗaki ne da makeken gado ɗakin shima nasa kalar tsarin daban. Daddy ne zaune ya saka laptop a gaba, yana nazartar wani abu, daga shi sai dogon wando da vest. Da sauri ta saki ƙofar ta juya zata arta da gudu. "Amina zo nan" taji muryarsa. Tsayawa tayi a waje, amma ta kasa dawowa. "Karki bari in taso, ki zo nace" ya faɗa a ɗan kausashe. Kamar munafuka haka ta shiho kanta a ƙasa. "Me kike nema ne?" Yayi maganar da dukkanin attention ɗin sa a kanta. "Bakomai" "Ki gaya mini menene?" Ba tare da ta kalleshi ba ta ce "Bakomai". "Kin ci Abincin ne?" "A'a na ƙoshi" gaba ɗaya ya lura a tsorace take. "Ko kin gaji da zaman ke kaɗai ne?" Ta ɗaga masa kai da sauri. "Ok, taho ki zauna a nan muyi hira" Ta girgiza kai ta ce "A'a, zan koma ɗakina" "Kamar a takure kike, bari in zo muje a kaimu yawo, zaki?" Ta ɗaga masa kai da sauri. Ya miƙe ya zura riga, ya sanya facemask da hula, ita dai tana gefe tana kauda kai gefe. Kasancewar sanye take da hijjabi, ya sanya suka fita. Yadda ake ta giramama Daddy abin har mamaki yake bata, ba a masa wannan girmamawar a Kano. Suka shiga bayan mota ita da shi, direba ya ja su suka fita. Suna tafe yana mata hira yana nuna mata gari, har ya samu ta saki jikinta, ya saka aka kaisu wuraren shaƙatawa, Amina har da hawa liluka tayi ta nuna halin ƙuruciya da yarinta, Daddy bai hanata ba, sai da ya tabbatar da ta samu nutsuwa ta saki jikinta, sannan suka koma wancan gidan. Da daddare bai tsareta da doguwar hira ba, ya bata umarnin tafiya ta kwanta, shima ya tafi nasa wuri,Amina bata da tabbacin a in da ya kwana, ko a gidan ne ko ba a gidan bane ba bata sani ba, kawai dai ya saka ta shiga ɗakin ta kulle ta ciki sannan ya tafi. Da ƙyar Amina ta iya bacci, saboda tsoron da take ji, haka ta kwana da hasken ƙwan lantarki saboda tsoron da take ji. Bata kuma ganin Daddy ba sai washegari ƙarfe tara na safe, ya kirata a waya ya ce ta fito ta karya. Dama a shirye take ta daɗe da tashi, ta saka hijjabi ta fito falon, "Good morning" ta gaishe shi cikin girmamawa. "Morning, kin tashi lafiya?" Ta amsa da "Lafiya lau Alhamdilillah" Ta kalli kayan tea da flask ɗin Abinci da ke gaban Daddy, ta kalleshi ta ce "Waye yayi girki?" "Kawo mana nasa aka yi, serve us" Ta haɗa musu tea, ta zubawa kowa nasa, ta miƙa masa nasa ta ɗau nata ta koma bayan kujera, ita ba zata ci Abinci a gabansa ba. Murmushi kawai yayi, ya yi Bismillah ya fara cin Abincinsa. Sai da ta gama cin nata, ta tashi ta haɗe kwanukan wuri guda. Kamar an tsikareta ta ce "Yauwa, Daddy dama kai minister ne?" Ya ce "In ji wa?" "A ɗakina na gani, ashe ka taɓa riƙe minister" Ya girgiza kai ya ce "Bani bane gaskiya, wa zai bawa talaka almajiri Minister a Nigeria?" "Waye talakan?" Tayi maganar seriously. "Ni mana" "Taɓ, Ashe mu sai dai a ce mana faƙirai, kalli gidajenka da motocinka, amma kake cewa kanka talaka wallahi Daddy ka dinga cewa Alhamdilillah" "To Anty Meenal" "Anty kuma?" "Eh mana, gashi kin sani a gaba kina mini faɗa a kan zancen da ban san shi ba, ban san a ina kika samo wannan labarin ba" "Bari in ɗauko maka jaridar ka gani" ta tashi ta tafi ɗakin da ta kwana. Murmushi kawai yayi ya girgiza kai. Ta dawo riƙe da jaridar, ta buɗo shafin da ta karanta hirar da aka yi da shi da kuma hotonsa ta ce "Kaga fa" Ha kalli jaridar ya ce "Ikon Allah, me kama dani" "Baga sunanka a nan ba, Ahmad Musa dutse gaka nan a zaune" "Wane sunan kika ce?" Ba tare da tayi tunanin komai ba ta ke nuna masa "Gashi Ahmad Musa dutse, gaka nan kaine fa a jiki" Yayi murmushi ya ce "Wow, sake faɗar Ahmad ɗin in ji" Kallonsa tayi a shagwaɓe ta ce "Daddy ni gaba ɗaya ka mayar da ni wata 'yar yarinya" "To meye idan ba 'yar yarinyar ba? Sai sha ɗaya zaku fara event ɗin yau ko?" "Eh, zaka je ne?" "Ya na iya, saboda ke ai na zo garin nan" "Yauwa Daddyna na gode, zan fi samun confidence idan muna tare". A yau su Fadila zasu zana jarrabawar Kankiya, gaba ɗaya a tsorace take, Saboda warning ɗin da Kankiya ya yi mata, saboda ta ƙi zuwa kiran da ya yi mata. Ƙarfe takwas na safe tuni ɗaliban sun gama settling a aji, sun mayar da hankali wurin rubuta jarrabawarsu ciki har da Yazid. Wajen ƙarfe tara da rabi, Kankiya ya yi dirar mikiya a ajin, kai tsaye Ya dubi Yazid cikin son ya tozarta shi ya ce "Me kake yi a zaman jarrabawata na yau, tashi ka fita ka bar mini aji, ai na gaya maka no 75percent attendance no exams come and leave you have automatical carry over" Malamin nan dai na jiya ne yau ma tare da TJ suke invigilating. "Kankiya ina roƙa masa alfarma, yaron nan ba shi da lafiya ne dan Allah a bar shi yayi jarrabawar nan na roƙa masa arziƙi" Kankiya ya ce "A'a ba zai zana jarrabawar nan ba, ya tashi ya fita" Yazid ya kalli Sir Kankiya ya ce "I never miss your attendance sir" "Ni kake gayawa You never miss my attendance, ƙarya zan yi maka, ka kalli tsabar idona ka ƙaryatani, ga Attendence sheet ɗin a hannuna" "Sir ba ƙartayaka nake ba, ina da Attendence ɗin ka full" Ganin Yadda Kankiya ya harzuƙa, ya sanya malam Sani cewa ya ɗauko Attendence ɗin a duba" Kankiya ya ɗauko takardar Attendence, yana ta kumfar baki, sai dai ko da aka duba lambar Yazid he never missed it. Mamakine ya cika Kankiya, saboda yadda yake tsaurarawa wurin yin attendance, kuma ya san Yazid baya zuwa ajin, amma complete Yazid yana da Attendence. Lumshe ido Fadila tayi tana murmushi. Abin da Kankiya bai sani ba shine, tun lokacin da Yazid yayi ta sintirin zuwa ya amsa kiran da Kankiya yake masa baya samunsa, har sakatariyar Kankiya sai da ta fara jin tausayin Yazid, bayan Kankiya ya hana shi shiga aji, Fadila ta je wurin Sakatariyar Kankiya, ta bawa sakatariyar kuɗi ta ce tana son idan Kankiya baya Office, ta dinga duba Attendence ɗin 'yan ajinsu tana yiwa Yazid. Aikuwa sakatariya ta amshe kuɗi, ta dinga yiwa Yazid attendance ba tare da sanin Kankiya ba. A lokacin ba su samu saɓani da Yazid ba, tayi ta kwantar masa da hankali a kan babu abin da zai hana yayi jarrabawar Kankiya, za a dinga yi masa Attendence, amma bata gaya masa me tayi ba, shi dai yaje ya cigaba da Addu'a ne, kuma ya yarda Allah ya karɓa. Abun ba ƙaramin ɗaurewa Kankiya kai yayi ba, haka ya haƙura da batun hana Yazid jarrabawa. Sai dai duk da hakan bai haƙura ba, ya cigaba da neman hanyar da zai soke jarrabawar Yazid. Yazid hamdala ya dinga yi a ransa, ya kammala jarrabawarsa, ya tashi zai je yayi submitting, bironsa ya faɗi ƙasa, ya durƙua ya ɗau biro kawai TJ ya ce "Kai me kake yi haka?" Ya nuna masa biro ya ɗauka, TJ yana zuwa ya duƙunƙuna takardar Yazid yayi jifa da ita. (WHAT DO YOU THINK GUYS, ZAMAN DADDY DA AMINA A GIDA ƊAYA SU BIYU IS IT SAFE? GA KANKIYA GA FADILA GA KUMA YAZID DA KANKIYA KE SON GANIN YA KAI SHI ƘASA, AYI HASASHE LAFIYA SANAN AYI HUTUN ƘARSREN MAKO LAFIYA) AYSHERCOOL 08081012143LITTAFINA NA KUƊI NE, ₦500 TA WANNAN ACCOUNT ƊIN 0009450228 AISHA ADAM JAIZ BANK KO KU DUBA AREWABOOKS. Har Amina zata rufe flask ɗin ta juya, ta kuma tsayawa tana kallon naman, sam bata kawo Hajiya Zainab ce ta dafa ba, ta zaci Hajara ce ta tashi ta kammala aiki da wuri ko akwai in da take son zuwa. Amina ta ɗauki spoon, ta ɗan ɗiba ta saka a bakinta. Ya ji spices sai ƙamshi yake, duk da akwai wani ɗan ɗaci da tayi zaton kawai bakinta ne. Amina ta sake ɗiba ta ci, taji yayi mata daɗi sosai da sosai. Jan kujera tayi ta zauna, ta dinga tsamar naman nan tana ci, kan kace meye wannan ta ci ya kai rabi. Hajiya Zainab kuwa sai lallaɓa Daddy take yi, tana yi masa kwarkwasar da sai zai bata kuɗi yake ganinta. Ta sha uwar kwalliya, sai ƙamshi take tayi masa jagora zuwa falo, sai hira take yi masa. Turus tayi lokacin da suka ƙaraso dining, taga Amina zaune da spoon a hannunta tana cin naman da ta tanada saboda Alhaji Ahmad. "Ke, wani irin wulaƙanci ne wannan da rainin hankali, na girka wa Mijina abun ki zo ki zauna kina ci?" Ɗan saroro Amina tayi sannan ta ce "Dan Allah kiyi haƙuri, wallahi ban zaci ke kika dafa masa ba, nayi zaton Hajara ce...... "Ko kuma uwar Hajara ba, saboda tsabar rashin mutunci ko Hajarar ce ta dafa ba kya bari a baki iznin ci ba, zaki zauna na yiwa mijina girki ki cinye" Amina ta ce "Ya salam, amma nace kiyi haƙuri ni wallahi ban san ke kika girka ba, saboda ban taɓa ganin kin yi ba, raina ne ya biya amma ba damuwa ai sai na girka masa wani". A cikin tsananin fushi Hajiya Zainab ta kalli Daddy ta ce "Wallahi tun wuri ka taka wa Yarinyar nan burki, wannan wane irin iskanci ne da rashin mutunci,? Yaya za ayi na dafa abu saboda kai ta zauna ta na ci, yanzu nayi magana ace na fiye kishi da neman rigima ita kuma wannan me tayi?" Daddy ya kalli Amina ya ce "Meenal, meyasa ki ka ci bayan kin san ba ke kika ajiye ba, kin san fa bana son neman magana" "Wallahi Daddy ban san naka ne ta ajiye maka ba, ji nayi ina son ci shiyasa" "Eh tunda gaki mayya ba, dangin mayu kinga nama idan baki ci ba mutuwa zaki yi". Amina ta ce "Ni ba mayya bace, danginmu kuma babu mayu, dan hak.... Ba ta ƙarasa ba Daddy ya ce "Ya isa haka, ki bata haƙuri kawai a wuce wurin" "Amma Daddy tunda kuka fito fa nake bata haƙuri, me kuma take so nace mata?" A ɗan hasale ya ce "Ki bata haƙuri nace, bana son gardama" Amina ta sunkuyar da kanta ta ce "Dan Allah kiyi haƙuri, ban san ke kika girka ba" Daɗi ne ya kama Hajiya Zainab, ganin yadda Daddy ya fara acting, ya sanya taji a ranta ai maganinta ya fara ciksa, dan ma bai ci wannan naman ba, in da Allah ya taimaketa akwai sauran maganin. Ta haɗe rai ta ce "Gaskiya dai ka sake ja mata kunne, kar ta sake yi mini irin haka, idan kuma ta kuma komai nayi mata ita ta saya" Daddy ya ce "Kiyi haƙuri, ba zata sake ba in Sha Allah, kuma in dai nine kar ki damu, na karya haka na gode sosai da kulawa" Amina kuwa miƙewa tayi, ranta babu daɗi garin ta bar wurin, ta kifar da sauran naman ya zube a ƙasa. Daddy ya kalleta ya ce "Ina zaki? Ba zaki zauna ki karya ba?" Hajiya Zainab ta ce "No, bana buƙatarta a nan, daga ni sai kai nake son muyi breakfast, ta samo dai abu ta gyara wannan abin da ta zubar" ko sauraransu Amina ba tayi ba, tai musu banza tayi tafiyarta. Ɗaki ta koma ta nemi wuri ta kwanta, taji yadda naman da taci yake taso mata, ga shi taji kamar tana ƙaurin hayaƙin nan da ta fito ta tarar ya turnuƙe falo. Guntun tsaki ta ja ta na juyi a kan gadonta, daga bisani wani irin bacci yayi awon gaba da ita. A cikin baccin nata ne, taji yadda cikinta yake murɗawa, ta farka ta tashi zaune, abu kamar wasa cikinta ya dinga murɗawa, ta dinga juyi a kan gadon nan, daga baya kuma sai amai. Tun tana iya tashi daga kan gadon ta tafi toilet, har ta nemi wuri ta zauna a toilet ɗin, ta dinga kwara aman nan ba ƙaƙƙautawa, duk ta fita hayyacinta kamar wadda tayi cholera. Babban abin da ya bata haushi bai wuce yadda Daddy ko ya leƙo yayi mata sallama kan ya fita ba, alhalin idan yana wurinta, sai ya je yaga Hajiya Zainab koda kuwa zata ci masa mutunci ne. Bayan fitar Daddy, Hajiya Zainab ta ɗau waya take bawa su Turai labarin abin da ya faru a group. Suka tayata murna saboda alamu ya nuna kamar maganin ya fara aiki, amma Hajiya Turai ta ce "A gaskiya naji haushin cin naman nan da wannan shegiyar 'yar tayi, Allah ya sa shi ne ajalinta" Salma ta ce "Amin dai, sai ki sake dafa masa wani, amma ki tabattar daga ke sai shi a ɗaki, ki bashi ya ci". "Haka za ayi, na fara na turaren nan ma, ni na naman na damu ya ci, kuma shi yafi son kifi fa a kan nama, saboda hawan jini" Turai ta ce "Haka nan zaki lallaɓa shi, sai yaci, mu dai fatanmu buƙatar mu ta biya" Ta ce "Haka ne, in Allah ya yarda zan duk mai yiwuwa, naga na bashi ya ci, sonake naga ya kori Yarinyar nan korar wulaƙanci a gidan nan" "Kar ki da mu, ke dai ki civaba6da gwada maganin" suka cigaba da zigata da baga shawarwarin yadda zata ɓullowa al'amuran. Khalil kuwa ya dage sai shiri yake, yana narka kuɗi a gininsa, kamar wanda zai auro 'yar wani gwamna ko sarki, sannan yana turawa Hajiya Maryam kuɗi domin yi masa sayayar kayan lefe. Sunata cigaba da tsara yadda biki zai kasance. Abdul ya ga yakamata ya sanar da Khalil batun soyayyarsa da Yusra, kar ya zo yaji a wani wurin yaji babu daɗi. Dan haka bayan sun gama hirar yadda abubuwa zasu kasance a bikin Khalil, sai Abdul ya fara sako masa nasa zancen ta hanyar cewa "Malam nima fa na kusa kai kuɗin Auren nan". Khalil ya ce "Are You serious?" "Da gaske nake maka" "Amma gayen nan baka da kirki, amma baka taɓa gaya mini ba, ko ka haɗani da ita mu gaisa ba" Abdul ya ce "Ai ba wata bace a nesa, ta gida ce" "Ok, wacece?" Abdul ya ɗan yi shiru sannan ya ce "Yusra ce, ƙawar Fadila". Khalil ya ce "Ohhh Allah, Allah mai yadda ya so, lallai zaka sha iyayi da rawar kai, ka rasa Fadila amma kusan halinsu ɗaya Allah ya baka wuyanka ɗauka" "Amin na gode da fatan alkhairi" "Ahh haba bakomai, amma gaskiya ku bari a fara nawa sai ayi naku" Abdul ya ce "Saboda wayo, to ban yadda ba" Gaba ɗaya Abdul bai yi zaton Khalil zai ɗau abin so simple haka ba, a zatonsa zai nuna bai ji daɗi ba, saboda a baya ƙanwarsa ya nuna yana so. Yazid kuwa ya kuma haɗuwa da Fadila a makaranta, sai dai fuskar nam babu yabo ba fallasa, da fara'arsa ya ƙarasa gareta yana mata murmushi. "Alhamdilillah, naji daɗi da ban ganki kina kuka ba, amma ya aka yi kwana biyu baki shigo school ba?" Yayi maganar yana ƙoƙarin zama, amma ta matsa gefe dan bata son yadda jikinta ke rawa da sun samu kusanci. Fasa zaman yayi ya ce "Ohhhh sorry, ina fatan yanzu kin watstsake?" Ta ɗan gyaɗa kai ta ce "Yes Alhamdilillah" "Tsarki ya tabatta ga Allah, mun gode masa bisa ni'inominsa da jarabbwowinsa. Kin san ita rayuwa sai ana yi ana taɓa ɗan Adam yake sake samun kusanci ga mahaliccinsa, kuka ba mafita bane ba sam, Addu'a da miƙa lamari ga Allah su ne mafita kin ji?" Kallonsa tayi amma bata amsa ba. "Ya kika yi shiru?" "Ina jinka ai" Ya ce "Alright, yauwa dan Allah ina sake godiya da alherin da aka yi minina gidanku" "Kaga bakomai kar ka damu kawai" ta katse shi. Bai sake cewa komai ba ya bar wurin, ita ji tayi ma gaba ɗaya ta tsani zaman ajin, dan haka ta tashi ta ɗau jakarta ta fice. Yusra ta kira a waya, Yusra ta sanar mata tana common room, dan haka ta wuce ta je ta tarar da ita a can. Ta je ta samu Yusra a can, tana zuwa ta zauna ba tare da ta ce mata komai ba. Yusra ta kalleta a nutse ta ce "Beb, meke faruwa ke ba a rasaki da damuwa menene?" Kaar za tayi kuka ta ce "Komai ma Yusra, gaba ɗaya gidanmu babu daɗi, wannan yarinyar ta ɓata mana jin daɗin rayuwa, ko kin san Mummy sai da ta bar gida kwana huɗu ba wanda ya san in da take" "Subhanallah, amma dai an ganta ko, ai ni baki gaya mini ba" "Ta dawo jiya, baƙin ciki da ɓacin ran da Daddy yake sakata ne ya ta tafi, ba wanda ya san ina taje sai jiya ta dawo, Yarinyar nan munafuka ce, last week tunda na zo school ɗin nan nake kuka, baki ji cin kashin da take yiwa Mummy ba, kuma Daddy yana goya mata baya, da aka tashi daga school yazid ya kaini gida, saboda munafurci ta bashi abu ni ban san me ta bashi ba yake ta ayi mata godiya, da ni na bashi ba lallai ya karɓa" Yusra ta ce "Au kun shirya da Yazid ɗin ne?" "Ke oho masa, ni ba shi ya dameni ba, Yaya Khalil fa ko a jikinsa abin da Daddy yayi wa Mummy, yama koma wurin ta ita da Daddy, duk yadda zan gaya miki ba zaki gane yadda gidanmu ya tarwatse ba" "No, ki daina faɗar haka, gidanku ba zai taɓa tarwatsewa ba, kuma komai zaa wuce da yardar Allah" Fadila ta ce "Allah ya sa, ni ji nake dama muna da wasu 'yan uwa da muke zuwa gidansu, da can zan koma ba zan iya jure wannan tashin hankalin ba" "Fadila Addu'a ita ce mafita a kan komai, dan haka ki miƙa lamuranki ga Allah, ki manta da komai" Fadila ta nemi wuri ta kwanta a cinyar Yusra, tana ganin Yusra ba zata gane halin da take ciki ba. Amina ba ƙaramin ƙulewa tayi ba da Daddy bai shigo ba, ta sha wahala sosai da ƙyar aman da take ya tsaya. Wajen azahar taji ana bubbuga ƙofar bedroom ɗinta, da ƙyar ta taso ta buɗe. Sai taga Hajara a tsaye. Hajara ta ce "Naga gaba ɗaya banga kin fito ba, shine nace bari na zo na duba ko lafiya". Amina ta ce "Wallahi Hajara bana jin daɗi ne, dan Allah ida da gasarar kunu, ki damo mini ki kawon in samu na sha" "Subhanallah, Allah ya sauwaƙe kina ɗaki baki fito ba shiyasa ba wanda ya sani, bari na kawo miki" Amina ta ce "Yauwa na gode" ta koma taje ta kwanta. Mintuna talatin da ɗoriya, sai ga Hajara ta dawo, ta kawowa Amina kunu, ta karɓa tayi mata godiya, ta zauna ta sha kunun sosai dan tana ji yunwa, amma bayan ta gama sha, tana tuna naman nam da ta ci, taji cikinta ya kuma hautsinawa taje ta amayar da shi. Amina ta ce "Na shiga uku ni Amina, anya wannan naman da arziƙi ne, naje na ciyo wa kaina masifa da kaina" Haka ta wuni tana malelekuwa, da kyar aman ya tsaya. Duk ta fita hayyacinta. Wajen ƙarfe shida da rabi, tana kwance bacci ya ɗauketa, taji ƙamshin turaren Daddy. Ta buɗe idonta a hankali ta ganshi zaune a kusa da ita yana shafa kanta. Kallo ɗaya tayi masa ta ture hannunsa, ta juya masa baya. "Meenal lafiya kuwa?" Amina ta ce "Ni ka ƙyaleni" Ya kwantar da murya ya ce "Haba 'yar babyna, nine fa Daddy ne" "Ba wata 'yar babynka, da ka mini wulaƙanci a gaban matarka, ka goya mata baya dan an dafa maka abu na ci, har da wani yi mini faɗa naman ma da naci ya kusa kasheni, kuma wai wunin yau ko ka leƙo ka ganni, bayan idan kana wurina ko zata maka wulaƙanci ita kana leƙawa ka ganta wuni nayi ina ciwon ciki amma banga ka zo in da nake ba" Cikin rarrashi ya ce "Haba Meenal, ya zan bata rashin gaskiya bayan kin san kin yi laifi, zata dinga ganin bana yi mata adalci. Wallahi ina ƙoƙari Amina idan na biyewa son zuciyata ba zan muku adalci ba, saboda na san ina miki son da ni kaina yake bani mamaki. Kuma naje mun yi maganar auren Fadila ne da iyayen wannan yaron, ban zaci zan daɗe haka ba, amma dan Allah kiyi haƙuri" banza tayi masa tana cigaba da zumɓura baki. "Babyna, ko in tsuguna ne? In dai hakan zai saki farinciki sai na durƙusa na baki haƙuri, dan Allah ki daina fushin nan wallahi ni kaina wunin yau babu daɗi nayi shi, nayi missing ɗinki abubuwane suka sha kaina dayawa, amma am sorry Dear" Ya ƙarasa maganar yana juyo da ita ta fuskance shi. Saboda tsabar shagwaɓa sai ta hau kuka har da hawaye, tana tura baki, Daddy kuwa ya lalace a wurin rarrashinta, yana share mata hawaye. Sai da ta ɗan samu nutsuwa sannan ya ce "Yauwa Meenalin Daddy, ko ke fa saura kuma ki yi mini murmushi zuciyata ta samu nutsuwa" Ta noƙe masa kafaɗa. "Please Baby" Ta ce "Ina da sharaɗi" "Wane sharaɗin ne?" "Gaskiya kar ka sake ka ci nama a kwanakin nan, ka san dai kana kan dokokin likita ko?" "In dai wannan ne, shikenan ba zan ci ba i promise, yi murmushin na gani" Murmushin tayi tana share sauran hawayen fuskarta. Murmushin shima yayi ya ce "To yanzu me zaki ci?" "Gasashen Kifi nake so, manyan nan mai miya" "To shikenan, amma taso muje ki ɗan tattaka, ko kya ji dadin jikin ki". Ta ce "Ni ba tattakawa zan yi ba, ban yi wanka ba, duk jikina ciwo yake mini saboda ciwon ciki" Daddy ya miƙe, ya cire babbar riga, ya saka Amina gaba zuwa toilet. Har mai shi ya shafa mata, ya taimaka mata ta sanya wasu kayan, ya kalleta ya ce "Ko muje Asibiti dai, naga jikinki yayi weak?" "Ai ya daina yi mini ciwon, ka sayo mini kifin kawai" "To shikenan, kwanta ki huta yanzu zan dawo" Ta ce "To a dawo lafiya" Ya jinjina mata kai ya fice, yan fita falo ya haɗu a Hajiya Zainab, ta kalleshi ta ce "Dama kana gidan nan tun ɗazu? Nifa bana son munafunci, amma dai ka san yau a wurina kake ko?" Alhaji Ahmad ya ce "Haba Zainab, dan ina wurinki shikenan ba zan leƙa in ga ya take ya ta kwana ba? Yarinyar nan tunda na fita ashe bata da lafiya, hakkinta a kaina yake dole naje naga jikinta" Cikin ɓacin rai ta ce "dole ko? Yayi maka kyau" ta wuce fuuuu ta bar shi a wurin. Da fari ji yayi kamar ya bita, da ya tuna Amina ko Abinci bata ci ba wunin yau, kawai sai ya fice ya tafi saya mata kifinta da ta nema. Hajiya Zainab iya ƙuluwa ta ƙulu, amma ta danne saboda ta sake dafa wani namn, so take ya ci. Amina kuma zaman ɗakin ne ya gundureta, ta ɗan ji daɗin jikinta, dan haka ta fito da niyyar zuwa kitchen, ta dafa tea idan Daddy ya kawo mata kifin, ta samu abin haɗawa. Sai dai kamar ɗazu da safe, yanzu ma falon warin wannan hayaƙin yake yi. Da sauri ta ƙarasa kitchen, saboda jin yadda tari ya fara taso mata. A gurguje ta dafa tea ɗin, ta koma ɗakinta tana tsaki, saboda ita bata ga amfanin wannan hayaƙin ba, bata san ta ina yake shigowa falon ba, dan sam bata yi zaton Hajiya Zainab ke kunna shi ba. Da magariba Daddy ya dawo da kifin Amina, ta dinga murna da ganin kifin nan, ya zauna ya sata a gaba ta ci sosai sannan ya ce "Alhamdilillah, tun da kin samu kin ci kifin sosai, Allah ya baki lafiya, gobe in Allah ya kaimu nake son muje mu yiwa 'yan uwa bangajiya, har Shanono nake son muke, jibi in Allah ya kaimu kuma, zamu je Dutse ta can zamu tashi". Murmushin fuskarta ne ya ƙaru cikin murna ta ce "Amma naji daɗi sosai, Allah ya kaimu da rai da lafiya" "Amin ya rabb, bari na tashi naje wurin Yayarki" Ta gyaɗa kai ta ce "Ok, shikenan kace ina gaisheta" "To zata ji" ya tashi ya tafi. Ta ji daɗin jikinta mussaman yanzu da ta samu ta ci wani abin ya zauna a cikinta. Tashi tayi ta duba littafinta da take rubutun Alqur'ani a ciki, ta sanya hijjabinta ta ɗau biro ta zauna, tana karantawa a hankali tana rubutawa. Ba dan Hajiya Zainab ta so ba, ta saki fuskarta, bayan Daddyn ya rarrasheta a kan Amina ce bata jin daɗi. Ta kawo masa abinci tare da wani farfesun naman, ya kalli naman ya ce "Naman nan a bar shi, zuba mini Abincin kawai" Ta kalleshi ta ce "Saboda me?" "Likita ya hanani cin jan nama, saboda shekaru da yanayin jikina" Ta ɗan rausayar da murya ta ce "Amma sai da ka bari na dafa zaka ce ba zaka ci ba, dan Allah ko kaɗan ka ci mana" ganin duk ta damu ta ɓata fuska, ya sanya ya ɗau fork ya ɗebo naman, murmushi yayi kan ya kai bakinsa, ya tuna da tare za su ci Abinci da Amina, zai fara cin Abinci ƙura masa ido za tayi sai taji yayi Bismillah, idan kuwa bai yi ba sa ta riƙe masa hannu tana haɗe rai kamar wani ɗanta. A hankali yayi Bismillah, ya kai yanka ɗaya bakinsa, sai ya tuna alƙawari yayi wa Amina ba zai ci ba, dan haka ya ce ya ishe shi. Kissar duniya da rarrashi ba wanda Hajiya Zainab ba tayi ba, amma ya ce ba zai ƙara ba ya ƙoshi. Ji tayi kamar ta tsinke shi da mari ta huta, amma ta shareshi. Abu ɗaya ne ya ɗan faranta mata rai, shine maganar da yayi mata na cewa iyayen Salim sun zo ya haɗu da su, sun ce zasu kawo kuɗin Aure da zarar ya dawo, shi kuma ya ce ya basu, sannan zai cigaba da saurarensu. Wannan maganar ce ta ɗan faranta mata rai, amma duk da haka ta shareshi, saboda rashin cin naman nan ba ƙaramin ƙuluwa tayi ba. Da daddare har sun kwanta, yake gaya mata cewar gobe in Allah ya kaimu zasu fita shi da Amina, jibi kuma za suje Dutse daga nan zasu bar ƙasar kwanaki goma ma kawa za suyi su dawo. Sai da Daddy ya gwammace bai yi nata zancen ba, saboda azabar bala'in da ta dinga yi masa a ka, tamkar zata dake shi. Ƙarshe sai juya mata baya yayi, tayi mai isarta ƙasan zuciyarta kuma tana Mamakin yadda aka yi maganin bai fara aiki yadda take so ba. Hajiya Zainab tana can tana bacci, Daddy ya lallaɓa ya tafi wurin Amina, dama ranar girkinta ne, yayi wanka ya shirya ko karyawa ba suyi ba, ya ɗauketa suka fice. Ɗaya gidan nasa suka tafi, ta haɗa musu breakfast, bayan sun kammala suka sake shiri a tsanake suka fita. Gidan Ammi suka fara zuwa, Ammi tayi murna da ganin Amina, ta yi ƙiba sosai ta ƙara kyau. Amina ta hau yiwa Ammi mitar, ita bata dawo ba, Azima ma bata je ba. Ammi ta ce "Ai bai kamata mu dinga yi miki zarya a wannan ƙadamin ba, ita ma nan suka shirya da 'yan ajinku da zasu je miki, nace kar suje tukuna kar wannan abokiyar zaman naki ta tsinkaki a gabansu" Amina ta ce "Ni da yake ma bata tata nake yi ba, idan tayi mini ba raga mata zan yi ba, kullum ni ba mai zuwa wurina, ita Azima ai da ko ita sai ta dinga zuwar mini". Azima ta ce "Ni rabani da zuwa gidan matar aure, ta koreni ta ce mini mijinta ya dawo" Bata wani jima ba, Daddy ya kirata ya ce ta zo suna da wurin zuwa sosai, haka tayi sallama da Ammi da Azima suka tafi. Daddy gidajen wasu daga abokansa na Kano, ya kai Amin suka gaggaisa da iyalansu, tare da yi musu bangajiyar zuwa walimar bikinsu. Amina tayi mamakin yadda Daddy yake da jama'a, amma babu mai iya takawa gidansa saboda masifar matarsa. Sai azahar suka ɗauki hanyar Shanono, Amina sai daɗi take ji, kamar yau zata fara zuwa garin. Inno da bata san da zuwansu ba, ta rasa ina zata ajiyesu dan daɗi, nan da nan aka yiwa Baba waya aka ce Amina ta zo, Baba ya rufe shago ya nufo gida cike da ɗokin son ganin tilon 'yar ta shi. Abin kunya sai ga su Baffa Bala, sun biyo sahun masu zuwa su gaida mijin Amina, kamar ba iyaye ba sai gasu suma. Sai a yau Amina taga sabon gidan da aka sayawa su Baba, manyan gidaje biyu ne aka saya aka haɗesu, aka ƙawata su, ga aiken kayan Abinci da Daddyn yake yi musu. Ba ƙaramin kima Daddyn ya daɗa a wurin Amina ba, ita a rayuwarta duk wanda yake son iyayenta to ya samu zuciyarta. Aikuwa duk wanda ya zo akwai alherin da Daddy zai yi masa, Amina ta sake sosai a gida tare da Inno da Baba, suka yi ta hirar yaushe gamo. Bayan sallar la'asar suka nufo cikin garin Kano. Hajiya Zainab kuwa bayan ta farka ta nemi Alhaji Ahmad ta rasa, ta kira wayarsa ya sanar mata yayi sammako sun fita da Amina. Haka ta dinga zage-zage ita kaɗai a gida, ta zari mayafi ta tafi gidan Hajiya Turai, suka sake tattaunawa a kan batun magungunan wurin malamin, aka tambayeshi ko za a iya amfani da maganin a kifi, ya ce musu a'a lallai a Nama ake so. Har ta dawo da yamma su Amina basu dawo ba, ta zauna a falo ta kasa tsare tana jiran taga ta ina zasu shigo. Aikuwa tana nan zaune, sai gashi sun dawo, Daddy na riƙe da jakar Amina, Zakiru kuma ya shigo da kayan tsaraba, da suka zo da su daga ƙauye. Ba kunya ba mutunci haka Hajiya Zainab ta cigaba da tsigale masa a gaban kowa. Amina tafiyarta tayi ta bar su, dan ta lura ita dai Hajiya Zainab idan har za a biye mata kullum sai an yi tashin hankali da ita. Amina bata san yadda suka ƙare ba, dan tana zuwa sashen ta rage kayan jikinta tayi, ta shiga tayi wanka tayi alwala ta zo ta tada salla. Bayan ta idar Daddy ya shigo, sai dai yanayinsa ya nuna mata yana cikin damuwa, kuma ta san Hajiya Zainab ce ta kunno shi. Ya zauna yayi shiru ya rasa abin da yake masa daɗi, Amina ta ninke abin sallar, ta je ta zauna a kusa da shi, ta rungumo kansa jikinta, tana ɗan shafa bayansa cikin sigar rarrashi ta fara magana "Sweetheart, ni da yaranka da duk masoyanka muna buƙatar ranka da lafiyarka, dan Allah kar ka cutar mana da kanka, saboda wata damuwa da zaka iya ajyeta a gefe muyi rayuwarmu. Damuwarka na jefa ni cikin damuwa nima duk sai na rasa meyake mini daɗi, kayi haƙuri ka ji?" Da fari ji yake kamar zuciyarsa zata tsaga ƙirjinsa ta faso, amma kalaman Amina suka dinga kwantar masa da hankali, sai da taga ya ɗan nutsu, sannan ta ƙyaleshi yaje yayi salla, ya nemi wuri ya kwanta. Washegari yayi shahada ya je wurin Hajiya Zainab yi mata sallama saboda doguwar tafiya da za suyi, tana fara zage zagenta, ya fice ya tafi ya barta. Ko da suka Dutse, danginsa tamkar zasu goya Amina, Amina gata da saurin sabo, ga ungo uban kayan zaƙi na gararta da aka kai musu kawai sai santi suke. Wasun su har suna ita wannan da ake gani ga karkara ce har da abin arziƙi na gara, uwar mulki kuwa ko barbaɗen gishiri ba ai kai mata ba. Amina ta yadda Alhaji Ahmad ɗan gata ne, kuma ɗan dangi gaba da baya, amma saboda tsabar son zuciya na Hajiya Zainab ta sa ya watsar da kowa sai ita. A family house ɗin su Daddy suka kwana, ya ɗauko mata hotuna yana nuna mata hotunan iyayensaa da 'yan uwansa da ya rasa, sai da ya zub da hawaye, saboda iyaye wasu duraku ne masu girman gaske a rayuwar kowane ɗan Adam. Washegari da Azahar, aka kai su Alhaji Ahmad airport, inda jirginsu ya ɗaga zuwa Dubai. Alhaji Ahmad ya samu isashshen lokacin hutawa, da nuna wa 'yar babyn amaryarsa kulawa da soyayya sosai da sosai, ya ɗan samu releif daga yawan hayaniya da tashin hankali da yake fuskanta na Hajiya Zainab. Amina lallaɓa abinta take, ta mayar da shi kamar yaro dai-dai da shekarunta. Ya dinga yawo da ita wuraren shaƙatawa daban daban yana kashe mata kuɗi. Hajiya Zainab saboda azabar baƙin ciki da kishi, gaba ɗaya ta manta bata gayawa Fadila batun maganar aurenta ba, sai ma shirin sake komawa nijar da suke yi a karo na biyu, dan yin wani asirin tunda wannan bai yiwu ba. Sai da taje tana yiwa Fadila sallama, tana sanar mata in da zata tafi ne, Fadila ta ce "Mummy, me kuma zaki je yi a nijar? Muda bamu da kowa a can?" Mummy ta ce "Sirikarki zamu raka, zamu je harkar wani business ne" Cikin mamaki Fadila ta ce "Sirikata kuma? Wacece sirikata?" Mummy tayi murmushi ta ce "Hajiya Salma mana, ni mana manta ban gaya miki ba fa, iyayen Salim sun zo sun yi magana da babanki, ya ce ya basu kuɗi kawai zasu kawo a saka rana". Saroro Fadila tayi tana kallon Hajiya Zainab, ta ce "Mummy yaya za a ba dani ga mutumin da duk abin nan da ake yi ko ganinsa ban taɓa yi ba" Mummy ta dafa kafaɗar Amina ta ce "kar ki damu, an tura masa lambarki, za kuyi magana, ai na san ba zaki bani kunya ba, shi ya ce kin masa ai, bari in tafi kar suyi ta jirana, idan na samu dawowa a yau shikenan, idan ban samu ba, sai dai mun yi waya" ta ɗau jakarta ta nufi hanyar fita, ta bar Fadla da wani yanayi da ta kasa gane kanta, takaici ne ko mamaki. Amina tana cikin bacci, tayi mafarkin wata baƙar mage, ta biyota, tana ta gudu tana kiran sunan Allah, amma duk da haka magen tayi tsalle ta kafa haƙoranta a cikin Amina. "Innalillahi wa innalillahi raji'un, Daddy ka taimakeni" Daddy da yake banɗaki yana wanka, kansa yayi wata irin sarawa, sai da ya dafa bango, da ƙyar ya iya lalubar towel ya ɗaura ya fito. A gigice ya ƙarasa gadon da Amina take, wanda gaba ɗaya ya wanke da jini, ga jikinta sai rawa yake, kan ya ƙarasa in da take yaji jiri yana neman kayar da shi. WANDA KUKE FITAR MINI DA BOOK, NA GODE SOSAI 🙏 ALLAH YA NA KALLONMU DUKA, DAN BA MUYI HAKA DA KU BA. AYSHERCOOL 08081012143GAB DA GABANTA BY AISHA ADAM AYSHERCOOL 48 Kallon in da TJ yayi jifa da takardar Yazid da ya duƙunƙune Yazid yayi, yana tunanin laifin me ya yiwa TJ haka. Tj ya kalli Yazid ya ce ya fita ya bar ajin. Miƙewa Fadila tayi, ta yi submitting ɗin takardarta, ta ɗauko ta Yazid da aka jefar, ta warware takardar, taje ta ajiye a wurin da ake submitting. "Ke! Meye haka kika yi?" Tj yayi maganar yana tsareta da ido. "Yazid bai yi laifin komai ba, ban ga dalilin da zai sanya a yar masa da takarda ba" Ƙarasowa TJ yayi ya sake ɗaukar takardar Yazid ya jefar. Yazid bai ce uffan ba, ya fice daga ajin, takardar Fadila ta sake ɗauka tabi bayan Yazid da sauri. "Yazid" ta ƙwala masa kira, ya tsaya ya waiwayo yana kallonta, karon farko tun sanin ta da Yazid da taga ɓacin rai kwance a kyakkyawar fuskarsa da kullum cikin murmushi ya ke, ko da an yi masa abu da bai yi masa daɗi ba, murmushin nan baya barin fuskarsa, ko ya haɗe rai ba ya ɗaukar lokaci yake sakin fuskarsa. Amma a wannan karon har idanunsa sun yi jawur, jijiyoyin kansa sun ɗaga ɓacin rai ya bayyana sosai a fuskarsa, sai da Fadila ta tsorata da ganinsa a haka. Jiki a sanyaye ta ce "Ka zo muje wurin HOD ka gaya masa, na san zai yi wani abu a kai". Yazid ya girgiza mata kai ya ce "No need" ya juya zai tafi. Carf ta riƙo hannunsa, ya waiwayo da sauri ya kalleta "Dan Allah ka zo muje, na san Sir TJ yana sane yayi maka wannan abun duk bakinsu ɗaya da Kankiya, dan Allah ka zo muje a san yadda za ayi". Ya zame hannunsa daga nata ya ce "Kar ki damu, na barwa Allah" yayi maganar yana jan numfashi, alama numfashin ya fara yi masa gardama a sakamakon ɓacin ran da ya shiga. 'yan ajinsu da suka fito suka dinga kumfar baki a kan abin da aka yiwa Yazid, suka ƙaraso in da su Fadila ke tsaye suna ziga Yazid ya kai ƙarar abin da aka yi masa. Da ƙyar da rarrashi Fadila ta shawo kansa ya amince, suka je wurin HOD, sai dai baya nan sai mataimakinsa, ko da suka gaya masa abin da ya faru, sai ya goyi bayan su Kankiya, wai ai ba za su yiwa Yazid ƙarya ba, meyasa duk ajin ba a yiwa kowa haka ba sai shi, yayi misbehaving a wurin exams. Kankiya kuwa ya ce ta shafi duka 'yan ajin saboda ƙarsrsa da suka kai a kan abin da aka yiwa Yazid. Ran Yazid ya ɓaci iya ɓaci, duk dakiyar zuciyarsa sai da wata ƙwallar baƙinciki ta taru a idonsa, nan da nan ya fara tari, Asma na neman ta tashi. Fadila ta sake gigicewa, ta samo kujera ta bashi ya zauna, ta ɗauko handout tana masa fifita. Alhaji Ahmad ya shirya tsaf domin tafiya wurin event ɗin su Amina, ita ma ta fito cikin uniform ɗinta, sai wata jaka da ta zuba wasu kayan a ciki ta ratayo. Tana ganin Daddy tayi murmushi ta ce "Inyee minister an sha kyau" Ɗan buɗe baki ya ce "Meenal kin raina ni da yawa, ko Zainab idan na haɗe rai nutsuwa ta ke yi, amma naga alama ke kuka zan yi be dameki ba, kin mayar da ni kamar wani kakanki" "Dan kawai nace kyau?" "Dame kika kirani?" Dariya tayi ta ce "Minister mana" Ya ɗan yi murmushi ya ce "Wanan lokacin ya wuce, yanzu ba harkar siyasa nake ba, kasuwanci nake yi, dan haka ni ba Minister bane" Amina ta ce "Gaskiya ka cigaba da siyasa, saboda zan tsaya takara fa, sanata zan zama" Sosai Daddy yake dariya ya ce "To Allah ya taimaka, zamu iya tafiya?" "Eh mu tafi, yauwa idan muka je, yau za muyi debate zagaye na biyu, da wasu 'yan makaranta kayi ta mini Addu'a, idan nayi ƙoƙari ka tafa mini sosai yadda zan jiyo, in samu ƙwarin gwiwa" "Wancan da ki kayi bana nan ai kin ci, ba abin da tafin zai ƙara miki" Haɗe rai ta yi ta ce "Ba zaka tafa mini ba kenan?" "Ke idan mutum ya biyewa rigimarki, sai ayi ta ɓata lokaci, oya let's go" Kan Amina ta sake Magana, wayarsa ta fara ringing. "Sweet daughter" ya furta a hankali da yaga sunan Fadila a kan screen ɗin wayarsa. "Hello sweetheart" "Hello Daddy kana jina?" "Eh ina jinki, amma ya na jiki kamar a  ruɗe?" "Daddy akwai matsala" Ya ce "Subhanallah, nutsu Fadila menene yi mini bayani" Nan Fadila ta warware wa Daddy komai. Amina maimaita sunan Yazid tayi a cikin zuciyarta, Fadila na yawan zancensa. "Fadila meyasa baki mini wannan bayanin ba tuntuni sai yanzu? Meyasa ki ka yi shiru, ban turaki makaranta dan wani malami ya takura miki ba, ki gaya mini idan da wani abu da yayi miki?" "Ni Daddy babu abin da yayi mini, Issue ɗin Yazid nake so ayi clearing dan Allah, idan aka ɓata masa jarrabawa ba ayi masa adalci ba" "Shikenan nutsu, kin tabattar babu wani laifi da yayi, kar ki saka in yi magana idan kin san mai laifinsa ne" "Wallahi Daddy bai yi laifin komai ba, ai nayi maka bayani" "Shikenan, bani 5minutes" Amina a ranta ta ce 'Taɓ dama kin san abin da ya dace da wanda bai dace ba?' Fadila tana nan tana zaman jiran Daddy ya kirata, sai sannu take jerawa Yazid, shi kam Yazid yayi shiru bai cewa komai, sai taron ɗalibai 'yan ajinsu dake tsaye a wajen suna mayar da yadda aka yi. HOD ɗin su suka gani ya tunkaro in da suke, da shi da wasu malamai guda biyu. Yana zuwa ya kallesu a ɗan rikice ya ce "Wacce Fadila?" "Gani" "Ke ban da abinki, idan kina da wata Matsala ba sai kizo ki mini bayani ba a san yadda za ayi, amma kawai kina nema ki kunno mana wuta daga sama haka ake yi, ina shi wanda aka krɓarwa takarda?" Yazid ya sauk mask ɗin fuskarsa ya ce "Gani sir" HOD ya kalleshi ya ce "Yazid kai ne?" "Eh nine sir" HOD ya kalli malaman da suka zo tare ya ce "Baku gane wannan yaron ba? Ya taɓa jan sallar juma'a ranar da Imam bai zo ba, Yazid ya aka yi wannan matsalar ta faru, ya aka yi aka kamaka da satar amsa" "Wallahi sir ban saci amsa ba, ga class mate ɗina nan a tambaya aji?" "Wallahi Sir ka san Yazid ba zai yi satar amsa ba, the overaller of the year, ka sani sir" cewar Captain. HOD ya ce "Naji, kuje za a san abin yi, ke Fadila da kai malam Yazid ku shigo na kira Kankiyar a waya ai" Captain ya ce "Allah ya ƙara maka lafiya Baba HOD, Allah ya tsare mana kai, wallahi mun yarda in dai Yazid na da laifi a hukunta shi". "shikenan, kuje za a kula da komai in sha Allah" Bayan sun shiga Ofishin HOD, Vice ɗinsa sai masifa yake yi, a kan dan me za a goya musu baya, su kai ƙarar malami?. HOD ya ce "Daga sama aka bada umarnin faɗaɗa bincike, dan haka sai ka ja bakinka kayi shiru". Fadila da kanta ta janyowa Yazid kujera, ta goge masa ya zauna a hankali. Ɗaya malamin ya ce "Shi bashi da hannu ne?" Fadila ta ce "Ba shi da lafiya ne" "Meya same shi ga mutum garau da shi?" "An masa aiki ne, kuma yana da Asma, baya son ƙura" "Lallai kam" Shi dai Yazid babu abin da ya iya cewa. Kankiya da yaga kiran HOD, ya gama tsara ƙarairayin da za suyi shi da TJ, bai zaci abin ya girmama ba, sai da ya tarar da Exam officer da student affairs ga kuma Yazid da Fadila, a take ya sha jinin jikinsa. Gaba ma she akwai gabanta. Suka nemi wuri suka zauna, nan aka shiga bin diddigin abubuwan da ya faru, da har ya sanya aka yi waya daga sama a kan case ɗin. Nan Fadila ta warware komai, hatta chats ɗin su da Kankiya, da yadda yake takura mata da waya, da warning a kan Yazid, sai data nuna musu da wasu daga recordings ɗin wayar da suke yi. Shi kansa Kankiya sai a lokacin ya san waye mahaifin Fadila, Yazid kansa yayi sanyi da jin Fadila 'yar waye, bai taɓa zaton hakan ba, kawai dai ya zata 'yar masu kuɗi ce, amma mutumin da ya taɓa riƙe ministan albarkatun ƙasa, kuma sananne bai zai gaza sanun kowace irin alfarma yake nema a ƙasa ba. Aka koma ɓangaren Kankiya ko yana da abin cewa, da kuma TJ ya bada hujjar cewa Yazid ya saci amsa, amma kowanne ya gaza kare kansa. Nan aka ce sallami su Fadila, amma Fadila ta ce ya batun jarrabawar Yazid? Ta fito da takrdarsa da aka duƙunƙuna, EO ya karɓa ya ce su tafi an sallamesu. HOD ya ce "Dan Allah dan gaba idan abu irin wannan ya faru, kan a gayawa father a fara zuwa a samemu muyi maganin abin, ba sai an kunno mana wuta daga sama ba" Murmushi kawai Fadila tayi. Yazid ya kalli malaman ya ce "Sir na gode sosai da sosai, Allah ya saka muku da Alkhairi ya biyaku da aljanna" Student affairs ya ce "Kar ka damu, Allah yayi muku albarka" Suka amsa da Amin. Yazid ya fito yana ta jera ajiyar zuciya, yana godewa Allah yadda yake tsallakar da shi tarko da sharrin mutane daban daban. Fadila ta kalleshi ta ce "Nayi farinciki da Allah ya sanya wahalarka ta semester nan bata tafi a banza ba, Allah ya ƙara kiyayewa" "Amin, na yaba da namijin ƙoƙarin da kika yi a kan ganin ba aci mutuncina ba" "Kar ka damu, idan na bari aka tozarta ka kamar ni aka yiwa, kuma koma menene ai a kan gaskiyarka ne, bari in kira Daddy in yi masa godiya" Yazid ya jinjina mata kai. Ta ciro wayarta ta kira Daddy. "Hello yaya aka yi, komai ya daidaita ko kuwa?" Ta faɗaɗa murmushinta ta ce "Daddy komai yayi daidai, an kiramu an warware komai, muna godiya Allah ya saka da alheri" "Amin, sannan idan na dawo gari zan zo makarantar ta ku, dole ayi miki tsakani da wannan malamin, ba zan lamunci irin haka ba, kuma daga yau kar ki sake ɓoye abu makamancin wannan" "To Daddy in sha Allah, mun gode sosai" "Never mind sweetheart, ayi karatu da kyau Allah ya bada sa'a" "Amin Daddy" Ta mayar da dubanta kan Yazid ta ce "To yaya, muje in sauke ka ne?" "A'a, ina jiran Sir Kankiya ya fito ne, zan bashi saƙo" "Saƙon me?" "Ki jira zaki gani" "Ko mu samu wuri ka zauna, saboda jikinka?" "A'a bakomai, zan iya tsayawa" Ba su wani ɗau lokaci ba, sai ga Kankiya ya fito fuskarsa babu annuri, ga wani gumi a goshinsa shi da TJ, aka yi sa'a kuwa su biyu ne kawai suka fito. Yazid ya tari Kankiya ya ce "Sir kayi haƙuri a kan abin da ya faru, ni da a son raina ne, ba zan taɓa yin abin da zai ja maka ɓacin suna ba, sai dai ka sani duk wata halittar ubangiji da ke doron duniya duk talaucinta muninta, kayanta ko arzikinta, ko da kafiri ne Allah yana son halittarsa, ba kuma zai bar zalunci ba, ka tsangwameni ka takurawa rayuwata duk saboda Fadila. Dan Allah Sir idan har kana son Fadila da gaske kaje gidansu ka sami mahaifinta, ka cireni daga wanda ke barazana ga soyayyar ka, ni kawai na ɗauketa a matsayin'yar uwata da muke aji ɗaya. Fadila tana da komai na gata da jin daɗin rayuwa, Amma Bani da komai sai Allah sai karatuna, idan ka durƙusar da ilimina ka durƙusar da rayuwata baki ɗaya, in dai yanke alaƙata da Fadila zai sama maka nutsuwa na yanke duk wata alƙata da ita, zan mayar da hankalina a kan abin da ya kawoni, amma ka dubi Allah ka tausayawa maraya, ka bar ni in samu ilimin da na zo nema cikin kwanciyar hankali" yayi maganar tare da haɗa hannayensa biyu alamar magiya. Daga haka ya juya ya fara tafiya, Fadila ji tayi kamar ta shaƙe Kankiya ta huta. Jikin Fadila yayi sanyi, tabi bayan Yazid da kallo, ga wani irin tausayinsa da ya mamaye zuciyarta, ta mayar da kallonta ga Kankiya da ya ƙame a wurin, tayi masa wani mugun kallo ta bar wurin, a can harabar ajinsu suka tarar da ɗalibai a tsaye suna jiran su ji yadda ta kaya game da jarrabawar Yazid. Yazid ya basu tabbacin cewa komai ya daidaita, na suka dinga yi masa son barka, tare da cewa Fadila ta cika ƙawa ta gari. Sai dai bai tsaya wani abu ya kuma haɗashi da Fadilan ba ya bar Wurin. Debate ɗin yau babu Amina a ciki, sai dai a quiz tayi participating, shima cikin ikon Allah makarantarsu Amina tayi nasa zuwa mataki na gaba. Daddy har mamakin ƙwaƙwalwar Amina yake yi, ta burgeshi matuƙa gaya, a ransa yake jin ko nawa ne zai kashe ya kaita ko ina ne a faɗin duniya tayi karatu, ba zai taɓa barin wannan ƙwazo nata ya tafi a banza ba. Ana tashi daga quiz ɗin wurin Daddy ta nufa, kan ta ƙaraso ya fara tafa mata, sai da ta rufe fuskarta tana murmushi. "Gaskiya kin birgeni, ban san yadda zan misalta miki fatincikin da na shiga ba, Allah ya ƙara hazaƙa Allah ya baku nasara" "Amin Daddy, duk wata nasara dana samu a harkar karatuna, ba zan taɓa mantawa da gudumuwarka ba, Allah ya biya maka buƙatunka na alkhairi ya kula da zuriyarka, sai da na zubda hawaye a lokacin da naji nawa kake kashewa a kan harkar karatuna, bani da bakin.... "Ya isa haka, zo mu tafi ai kun gama" ya katseta ba tare da ta gama maganar ba. "Wai Daddy duk lokacin da ka yi mini abu ba zaka barni nayi maka godiya ba, bana jin daɗin hana. Ƙiri ƙiri ya basar da zancen ya ce "mu tafi ko" ba yadda ta iya haka tayi shiru ta fito suka tafi. Gaba ɗaya jiki babu ƙwari haka Fadila ta koma gida, haka nan ta rasa abun da yake mata daɗi. Ba dan tana jin daɗin komai ba, tayi wanka ta ci Abinci ta fara karatunta. Wajen ƙarfe biyar na yamma sai ga Mummy ta dawo, ta tarar da Fadila tana zaune tana duba litafinta. "Ashe kin dawo" Fadila ta ce "Eh na dawo, ai exams muke a school" "Yayi kyau, ke Albishirinki?" Fadila ta ɗan kallk Mummy sannan ta ce "Mummy duk wannan fara'ar ta mecece?" "Ke dai ki amsa mana, ai dole kiga farinciki a fuskata" Fadila ta rufe littafin, ta tattara dukkan nutsuwarta a kan Mummy ta ce "Goro" "Ina kyautata zaton, na kusa yin sirukai very soon, na yiwa Daddynku maganar Kursum, ya ce mini in bari mu dawo daga umara, zai zauna da mahaifinta, and finally ɗa gidan Hajiya Salma yana iya dawowa a kowane lokaci, dan yana ta bada saƙon gaisuwa a baki, da ya takura ma a bashi lambarki amma ta hana, ta ce kar ya ɗauke miki hankali kina karatu ne yanzu, ya bari ya dawo tukuna, dan har ta yiwa mahaifinsa magana" Fadila gaba ɗaya zancen bai mata ba, ta ce "Ohhh my Goodness, yanzu a kan wannn maganar ne kike ta wannan murnar for God sake, Mummy ko ganinsa fa ban taɓa yi ba, har ya yiwa babansa magana, dan Allah a ajiye wannan maganar aside" Ɗan tsuke fuska Hajiya Zainab ta yi ta ce "Ban gane a ajiye maganar nan aside ba, am trying to make your tomorrow better ke da ɗan uwanki, yadda ko bayan ba ranmu na san na kafaku abokan rayuwarku ba zasu zame muku liability ba, ba ruwansu da abin da kuka mallaka, ta nuna mini hoton yaron ba shi da wani aibu, kuma already yana da sana'arsa a can in da yake karatu, idan kun yi aure can zaku tafi gaba ɗaya" Tura baki Fadila tayi ta ce 'Ni gaskiya Mummy am not going anywhere, karatuna fa?" "To karatun dama ba a waje muke yi burin kiyi ba, amma mahaifinki ya hana ba yanzu ga dama ta samu, ba sai kije ki cigaba da karatun a can ba" Sake tura baki Fadila tayi tana noƙe kafaɗa, dan tun bata ga gayen ba taji lamarin bai yi mata ba sam. Mummy ta kwantar da murya ta ce "Haba autar, am sure you will like that guy, yaron yana da hankali ba zaki shiga wahala ba zaki huta sosai, Please don't disappoint your mum, na san type ɗin mijin da kike so, I know you are classic that's why I chose him for you" Fadila ta tashi tsaye ta ɗau littafinta ta ce "Mummy, we should discuss it later, let me first concentrate on this one" tayi maganar tana nuna wa Mummy littafin hannunta. "Ok dear, good luck" Fadila ta amsa da thank you ta bar wurin. "Minister" Amina ta faɗa tana leƙa fuskar Daddy, dan taga reaction ɗinsa. Shareta yayi ya cigaba da kallon tagar mota. "Minister am talking fa" "Kinga ki kiyayeni tom" Murmushi tayi ta ce "Ka san me nake sha'awar ci kuwa?" "A'a, ki faɗi ko meye kan mu isa gida sai mu tsaya a nema a hanya" "A'a ni ba na sayarwa ba, wainar fulawa zan soya in ci" Ya waiwayo ya kalleta ya ce "Ina kika ga kayan wainar fulawa a gidan?" "Ban gansu ba amma sai a nemo" Daddy ya ɗan ƙura mata ido ya ce "Ni ne zan nemo"? "A'a ni na isa in ce haka, wace ni ranka ya daɗe, dan Allah ka saka a samo mini kayan yi, ni zan yi da kaina" "Sai dai a ajiye ki, ke kije ki nemo" "Idan na ɓata fa, ko wanan karnukan suka cinyeni a hanya" Ya kasingiɗa da jikin seat ya ce "Da na huta kwana biyu, da yawan surutunki da rigimar tsiya" Ta ɗan marairaice ta ce "Kenan takura maka nake" "Eh to ba nace ba, surutunki bai fiye takura mini ba, kamar gaddama da rigimar rashin dalili" "To ka saka a mayar da ni in da ka ɗauko ni tun da haka ne" "As you wish, bari in yiwa direban magana ya sauke ki sai in ɗoraki a babur ki tafi" Kwaɓe fuska tayi zata yi kuka ta ce "Au yanzu da gaske takura maka nake yi, kuma sai ka mayar da ni?" Dariya yayi ya ce "Ji mini yarinya da rikicin gangan, ke fa kika ce na mayar da ke in da na sa aka ɗauko ki" "To ni ba in da zan koma" ta faɗa tana haɗe rai tare da gyara zamanta. "Haba Meenalin, meye na fushin kuma? Za a nemo kayan wainar fulawa idan ma cewa ki kayi in soya miki, sai in ɗaura zani in soya miki" Dariya ce ta ƙwace mata ba tare da ta shirya hakan ba, ta ce "Wa yaga Daddy na soya wainar fulawa, da sai na maka hoto a haka" Dariyar ta ta kawai yake kallo, gwanin burgewa kamar kar ta daina. Ya gyara zamansa ya ce "Kin san gidan ne tun da ba zama nake a cikinsa ba, ba bu kayan masarufi a ciki, tun lokacin da na riƙe muƙami a gwamnatin baya aka bani shi, idan ba na shigo Abuja ba bana zama a cikin sa, na cewa Khalil ya zauna a ciki, ya ce yayi masa nisa da wurin aikinsa, sai mun zo hutu kawai muke zama". "Gidan me kyau kuwa, to a can Lagos ɗin ma kana da gida?" Ya ɗaga mata gira alamar eh. "Mmm lallai Daddy, kana jin daɗinka, ka dinga sawa ana Abincin sadaka kana rabawa mabuƙata, ka godewa Allah, Allah bai jarrabeka da tashin hankalin rashin muhalli ba" tayi maganar tana duba wayarta, ba da wani serious tayi maganar ba, amma maganar yaji ta shigeshi sosai. Har ta manta da tayi maganar sai kuma ta ɗora da cewa "Annabi Sallallahu alaihi Wasallam ya ce 'Dukiyar me bayarwa bata taɓa tawaya saboda yana bayarwa. Ka lura a duk lokacin da ka yayewa wani damuwa, sai kafi wanda ka yiwan shiga farinciki, kyauta akwai daɗi, ka bawa mutum abu kaga yana murna, saifa ka gama shekarunka kana salla ba a karɓa, amma cikin rahamar ubangiji a sanadiyyar faranta ran bawansa ɗaya, sai ya yafe maka, ai shi Allah gafuru rahim ne" "Haka ne sayyadata, shi yasa bana manta lokacin da kika mini kyautar fura da Nono da zan yi tafiya, tun daga lokacin kika ƙara kima a idona" Tayi murmushi ta ce "Allah ya ƙara arziki, ka ci kaita bayarwa" "Ameen ya Allah" "Daddy na ji kace Khalil a garin nan yake aiki, ba zaka je ka ganshi ba, naga ha daɗe bai je gida ba" "Aikuwa Yakamata in je ɗin, dan ya daɗe yana magiyar in je in ga gininsa, amma Allah bai sa na shigo Abuja ba, bari in kira wayarsa in ji, idan yana nan anjima sai in je" Amina ta gyaɗa kai, Daddy kuma ya nemi wayar Khalil ya kira. Sai da ga kusa yankewa sannan ya ɗaga, cikin numfarfashi yayi sallama. "Khalil, lafiya kuwa naji kana numfashi da kyar?" "Lafiya lau Daddy, bana jin daɗi ne kawai" "Subhanallah, meke damunka?" "Nima ban sani ba, ji nake dai kamar zuciyata ce take ciwo, bana iya numfashi sosai" A rikice Daddy ya ce "Kana wane Asibitin?" "Ina quarters ni banje Asibiti ba" Daddy ya katse kiran yana mita "Wannan wane irin shahsahnci ne, ya zauna a gida yana fama da ciwo, yi sauri muje mu ajiyeta, mu wuce can wurin Khalil ɗin" yayi maganar cikin damuwa. "Daddy ka kwantar da hankalinka, Allah ya bashi lafiya, ni ka sani a napep a kaini gidan" Ya girgiza kai ya ce "No, muje a kai ki tukuna" Amina ta ɗan ƙura masa ido sannan a ranta ta ce "let me see if I can do something, Hajiya Zainab Gaba akwai gabanta" AYSHERCOOL 0808102143GABA DA GABANTA                BY AISHA ADAM AYSHERCOOL 49 Sake kallon Daddy Amina tayi, taga yadda damuwa ta mamaye ilahirin annurin da yake ci da, ta ɗan yi ƙasa da muryarta ta kira sunansa "Daddy" Ya waiwayo ya kalleta, ba tare da ya amsa mata ba. "Dan Allah ka kwantar da hankalinka, in sha Allah yana nan lafiya, naga duk ka shiga damuwa" Ya ɗan sake kallonta ya ce "Yanzu har damuwa ta bayyana a fuskata?" "Eh mana, ga damuwa nan kwance a fuskarka ina gani" Ya ɗan shafi fuskarsa ya ce "Dole in damu, yanzu kamar Khalil da girmansa da komai, ba shi da lafiya amma ya kasa zuwa Asibiti, kuma ya ƙi gayawa kowa haka ake yi, idan ya cutar da rayuwarsa fa, wannan ai shirme ne" "Haka ne, amma ka kwantar da hankalinka, ka fara jin ta bakinsa kafin ka yanke masa hukunci, ka bi komai a hankali ka gano kan rashin lafiyar ta sa, akwai malaminmu da ya gaya mana, akwai cututtukan da sukan faru da basu da alaƙa da magani, nutsuwa da kwanciyar hankali kawai mara lafiyan yake buƙata" Daddy ya gyɗa kai ya ce "Haka ne" "Yauwa dan haka dan Allah ka kwantar da hankalinka, idan kaje kar kayi masa faɗa, sannan kuma ka ɓoye wannan damuwar da ke fuskarsa kar ka sa ya karaya, kuma kaga kai ma baka da cikakkiyar lafiya" Kallon Amina yake yi, 'yar ƙarama sai hikima, tana ta ƙoƙarin taga ta kawar da tasa damuwar. Ya ɗan ja numfashi ya sauke ya ce "To shikenan, na gode sosai" Hakan yayi daidai da tsayuwar motar a ƙofar gidansa, har zata sauka ya ce "Ki rubuta duk abin da kike buƙata, ki bawa Joseph, zai sayo miki" "To wanne ne Joseph ɗin?" "Dogon mai suma" Amina ta jinjina kai ta fice daga motar. Kai tsaye quarters ɗin Khalil yake su Daddy suka nufa, suna zuwa Daddy ya tarar da wani abokin aikin Khalil ɗin tare da shi. Khalil ya rame yayi baƙi, cikin girmamawa abokin Khalil ɗin ya gaida Daddy, Daddy ya amsa masa sannan ya mayar da dubansa kan Khalil ya ce "ya aka yi ka zauna haka ba ka je Asibiti ba?" "Daddy naje, idan na sha maganin bana jin komai, shi ya sa na daina zuwa" A fusace Daddy ya kalleshi ya ce "Kuma saboda shirme, da rashin sanin ciwon kai ka kasa kirana ko mahaifiyarka ka sanar mana, kawai kayi zamanka kana fama da ciwo, da sa dai ace mini in zo in ɗau gawarka? To idan kai baka buƙatar rayuwarka ni ina buƙata, ku kenan ku biyu Allah ya bani ka zana kana wasa da lafiyarka, tashi mu tafi ni muje Asibiti" Khalil wani irin jiri yake fama, da ƙyar ya iya miƙewa tsaye, ƙarshe sai sa shi aka yi a mota, suka tafi Asibiti. Suna zuwa aka yi masa gwaje-gwaje aka tabattar da jininsa ne yayi ƙasa sosai Hypotension, haka sugansa ma saboda rashin cin abinci. Nan da nan likitoci suka yi ta kai kawo a kan Khalil, ana saka masa ruwa da allurai, sai ga shi ya ɗan farfaɗo har yana iya zama da kansa, Daddy da kansa yaje ya nemowa Khalil Abinci, ya zauna ya sa shi a gaba, yana zare masa ido ya ci, kamar wani ƙaramin yaro (Iyaye masu daɗi, Allah ya ƙarawa iyayenmu lafiya da nisan kwana, wanda suka rasu kuma Allah ya yi musu rahama) Sai da ya tabbatar Khalil ya ƙoshi, har ya iya shiga banɗaki yayi alwala ya dawo ya yi salla. Daddy ya cigaba da yi masa faɗa. "Ni ban san ma dalilin da yasa ko gida da kake zuwa ƙarshen wata ka daina ba? Gaba ɗaya ka ɗauko wasu sabbin ɗabi'u, nema ma kake ka cire kanka daga cikinmu, mahaifiyarka na ta complain a kan ko kiranta baka yi a waya" Kamar Khalil zai kuka ya ce "Daddy ya zan yi, ko na kirata a waya sai ta nemo abin da za tayi mini faɗa, ta rabani da yarinyar da nake so, wai yanzu wata zata aura mini" "To sai me, a kan hakan kake nema ka kashe kanka? Ba zaka yi mata biyayya ba, naga dai ba zata zaɓi abin da zai cutar da kai ba" Shiru Khalil yayi Daddy ya cugaba da banbanminsa, dama ya san Daddyn ba zai goyi bayansa ba, duk abin da Mummy ta shirya masa shi kawai yake aiwatarwa. Sai bayan sha ɗayan dare aka sallami Khalil, a kan sharaɗin, zai koma washegari ya sake ganin likita. Daddy bai koma gida ba sai sha biyu saura na dare, abin mamaki yana zuwa ya tarar da Amina a falo ba tayi bacci ba tana jiranshi. Da sauri ta tashi tana masa sannu da zuwa. "Ya aka yi baki kwanta ba?" "Ai kona kwanta ba zan iya bacci ba, baka dawo ba kuma ban san a wane hali Khalil ɗin yake ba, nayi ta ƙoƙarin kiranka a waya, amma bani da network gaba ɗaya" "Jikinsa da sauƙi sosai, na mayar da shi gida ma sun sallemshi daga Asibitin". "Allah ya bashi lafiya, kaje ka kintsa ka zo ga Abinci na maka" Ya kalli inda ta nuna masa fulasan abinci ya ce "A ina aka samu Abinci?" Ta ce "Sautun kayan wainar fulawata nayi da kuma abin da zan dafa maka, ga tuwon Alkama nan da miyar kuɓewa sai kuma Coffee, sai kuma Fruit ka ci duk wanda kake so" Lumshe ido yayi, Amina duk ta gama sanin abubuwan da yake so, da kuma lokacin da yake son su. Ya ɗan buɗe idonsa ya ce "Me zance miki ne Meenalina? Allah ya saka miki da alkhairi, idan kin yi Aure ya baki ikon yiwa mijinki biyayya" "Yaushe zan yi Auren bayan ka hanani yin saurayi" Murmushi yayi yayi gaba, dan baya son ta ƙaƙalo rigima, ya shiga ɗakinsa yayi wanka ya canza kaya, ya fito ya sake tarar da ita a zaune tana jiransa. Sai dai kallo ɗaya tayi masa ta ɗauke kanta, kasancewar dogon wando ne a jikinsa sai shirt baƙa. Yana ankare da ita amma ya basar ya kunna Tv sannan ya zauna ya ce "Yauwa serve me" Kamar mara gaskiya haka ta sunkuyar da kai tana zuba masa Abincin, cikin son kawar mata da yanayin da ta shiga, ya fara bata labarin irin sakarcin da Khalil ya yi. Ta kalleshi ta ce "Yanzu ba shi da lafiyan kayi masa faɗa?" "Ba dole in masa ba, kin ga yadda yaron nan ya koma kuwa?" "Hmm, to ka tambaye shi meyake damunsa?" "Shiritarsa ce dai, wai babarsa ta hana shi auren wata wadda zata aura masa daban" "Eh ai da gaskiyarsa, gaskiya yakamata kayi wani abu a kai" Ya ce "Me zan yi a kai?" "Ka duba abin da yake so kayi masa idan har bai saɓawa Shari'a ba, ba ita kaɗai take da haƙƙi a kansa ba, yakamata a ce...." Kan ta ƙarasa maganar ya ce " Ɗan ki ne ko ɗanta? Ta fiki sanin ne ya dace shi, haryanzu yaro ne bai san meye ya dace da shi ba" Sak Amina tayi tare da yin shiru, ba ƙaramin ɓata mata rai maganar ta sa tayi ba, ta ɗan jinjina kai ta ce "Haka ne, ɗanku ne bai kamata in dinga shishshigi a kan abin da bai shafeni ba, amma idan ka cigaba a haka watarana zaka ga abin da ba ka so a gidanka" ta tashi fuskarta ɗauke da ɓacin rai ta bar falon. Dan haushi tana zuwa ɗakinta, ta haye gado, ta ja bargo tana jin yadda zuciyarta tayi mata babu daɗi da abin da Daddy yayi mata. Sam bacci ya kasa ziyartar idanunta, tana ta saƙawa da warwarewa, ji tayi an turo ƙofar ɗakin, sake dunƙulewa tayi cikin tsoro, dan bata san waye ya shigo ba. A hankali ya tako ya ƙaraso gaban gadon, ya sanya hannu zai janye bargon, ta riƙe bargon gam tare da sakin ihu, da sai da ta ɗan razana shi. "Ke lafiyarki kuwa?" "Meyasa zaka zo mini ɗaki yanzu ka yaye mini bargo, ka san a halin da nake?" Tayi maganar da iya gaskiyarta. Ya ce "Haka ne, ban kyauta ba, tashi muyi magana". "Ni ba wata magana da zamu yi, bacci zan yi". "Idan baki tashi ba zan yaye bargon, and I mean it" Buɗe ido tayi ta ce "To ɗauko mini hijjabina gashi can a ninke" Kallonta yai ya ce "Are You commanding me?" "Idan baka ɗauko mini na saka ba, zan yi kwanciyata" "Ok shikenan, bari in yaye bargon in ɗauko ki" "Wayyo Allah Babana, dan Allah ka bari" Juya mata baya yayi, yayi murmushi ya ɗauko mata hijjabin ya bata. Ta ziro hannu ta karɓa sannan ta ce "Ka juya to in saka hijjabin" tayi maganar a shagwaɓe. Ya juya mata baya domin ta saka, sai dai abin da bata sani ba shi ne, yana kallonta ta jikin mudubin ɗakin, har ta gama saka hijjabin a kan kayan baccinta. "In juyo kin gama?" "Eh" Ya juyo ya ƙaraso gefen gadon zauna, ita kuma ta sake matsawa baya, ya share ya ɗora da maganarsa "Ɗazu kina mini magana a kan Khalil, na katseki, kuma akwai buƙatar in jira ki gama bayanin" "A a Ni da ba ɗana ba, me zai sa in yi shishshigi ba ruwana na tsaya matsayina na 'yar aiki" "Look Amina, am serious, na san ban kyauta ba kiyi haƙuri, amma ni ina tunanin duk abin da mahaifiyarsa ta yanke a kansa ai daidai ne" Amina ta ɗan yi Jimm sannan ta ce "Daddy meyasa kai da iyalanka kuke gudun talaka ne? Ko ka tambayi mahaifiyarsa meyasa bata son yarinyar da yake so? Maybe na san ka sani, saboda basu da ƙarfi ne, meye aibun dan ya aureta? A sanadiyar son ka kyautata mini, ka saiwa iyayena kayan Abinci masu yawa muka tafi da su ƙauye, maƙotanmu da 'yan uwanmu sun amfana da Abincin nan sosai, Allah kaɗai ya san iya mutanen da ka samu ladansu, ko iya wannan idan ya duba ya karɓa maka a ayyukanka sai ya yafe maka. Daddy ina maka kwaɗayin al'umma su amfana da dukiyarka, ita yarinyar ance awara take sayarwa, idan ya aureta ya mayar da ita makaranta kamar yadda ka mayar dani makaranta bai taimaketa ba? Atleast zai taimaki iyayenta ma, ko ba komai an rage yawan talauci. Kuma ka san wani abu Daddy, a yadda basu shi ɗin nan, abu ne mawuyaci ta kasa yi masa biyayya, saboda ta san ita wacece, amna idan ya auri wadda suke level ɗaya tan da kuɗi yana da su, is hardly ta bishi yadda yakamata. Dan Allah Daddy ku daina ƙyamar talaka muma 'ya'ya ne, kaine jagora a gidanka da iyalanka damu duk a ƙarƙashinka suke, abin da kace dole abi, ni nafi jin tausayin yarinyar har fa wurin awarar matarka taje ta ci mata mutunci a gaban mutane, abin fa babu daɗi Daddy, akwai zafi a zuciya a wulaƙantaka dan baka da shi, kar Allah ya jarrabeku fa". "Da gaske Zainab taje ta ci mutuncin 'yar mutane?" "To ni dai ba a gabana aka yi ba, amna Khalil naji yana gaya wa Fadila" Yayi ajiyar zuciya ya ce "Na gode sosai Meenal, Ki kwanta kiyi bacci, sai Allah ya kaimu safe zamu cigaba da Magana" "Allah ya tashemu lafiya" Ya amsa da Amin, ya tashi yana cigaba da lissafa maganganun Amina, ya bar ɗakin. Tabi bayansa da kallo, sai da ya fita ta ce "Ya ubangiji Allah ka cika mini burina, ka ɗorani a kan bawan nan naka, Allah ka amfanar da mabuƙata a cikin dukiyarsa". Fadila kuwa ta ɓangare ɗaya taji daɗin yadda Allah ya sanya Yazid ya tsallake tarkon Kankiya, amma ta rasa dalilin da ya sanya ta damu matuƙa da jin batunsa na ya rabu da ita, gashi suna da interval daga waccan jarrabawar zuwa wata, ko ta ɗauki waya da niyyar ta kira shi, sai ta kasa tana tunanin idan ta kira shi me zata ce masa. Ɓangare guda kuma rashin Amina ma a gidan na ƙara ɓata mata rai, gab ɗaya tafi son aikin Amina a kan Hajar, Amina komai ka sakata ba ƙyuya babu komai, wani abun ma baka sakata ba zata ta yi maka shi idan ta ga dama. Hakan ya sa komai Hajara tayi mata sai ta gwale ta, ko tayi ta hantarar ta, ko wurin Mummy bata fiye zuwa ba, saboda da taje Mummy take sako mata zancen ɗan gidan Hajiya Salma, ita kuwa ko zancen ba ta son ji, balle ta ganshi har ayi wata maganar Aure. Da safe Amina ta fito, ta na ɗan gyare-gyare, Kitchen ta shiga ta duba sauran kayan Abincin, cikin nutsuwa ta fara aikin girkinta, tayi ta kammala, ta koma ɗaki tayi zamanta tana danna wayarta, sai takwas na safe sannan ta sake fitowa. Jinta tayi wani iri cikinta duk babu daɗi, ga tashin zuciya da yake damunta. Yau cikin suit ya fito baƙaƙe, ɗan ƙura masa ido tayi, ba zaka taɓa cewa ya haifi wannan 'ya'yan ba. "Meye kike kallona haka?" Ɗauke kanta tayi tana murmushi ta ce "Kwalliyar zan saya, ta tafi da ni sosai" Ya ƙarasa ya zauna a kusa da ita ya ce "Nawa kika saya?" Ta ɗan sake ƙare masa kallo daga sama har ƙasa ta ce "Eh to, na sayeta da delicious food" "Saboda kin mayar da ni acici ko?" Dariya tayi ta ce "Ahh babu laifi kam, Minister akwai karrama ciki" Yayi murmushi ya ce "Aifa shikenan, ni kin riga kin gama rainani, kina ganin haƙorana ko?" Ya ɗan lumshe idanunta ta buɗesu a kansa ta ce "Ba rainaka nayi ba, ina jin daɗin in tsokane ka in ga kana irin wannan murmushin" Murmushin ya kuma yi ya ce "To zan daina, ki dinga biyana sai in miki murmushin" yayi maganar yana kallonta, yana jin tamkar ya furta abin da yake masa nauyi a zuciyarsa game da ita. "Me za mu yi order ne? Ni zan fita in koma wurin Khalil duk da mun yi magana ya ce jikinsa da sauƙi" "Ga breakfast nan nayi, ga bread an sayo, ka zauna ka karya mana" "Masha Allah, Allah ya yi miki albarka, sauko mu karya" Ta ɗan yamutsa fuska ta ce "Ka ci kawai, ni naci anjima" Cikin kulawa ya ce "Ya dai, naga kina yamutsa fuska?" "Cikina ne yake ciwo da ƙirjina" Nan da nan ya rikice "garin yaya? Kuma meyasa baki gayamini ba? Kema kina wasa da lafiyarki ko? Tashi ki sako hijjabi muje Asibiti" Ita mamaki ma abin ya bata, "Ba fa wani abin damuwa bane ba, jiya wani yaji suka sayo mini mai zafi, na ci wainar fulawa da shi, shi ne yake damuna kuma na sha anti acid" "Are you sure?" "Da gaske nake, ba gani garau kana gani ba" "Idan kin san da matsala mu tafi Asibiti" "Daddy babu wata matsala fa, ka kwantar da hankali ina lafiya sosai" "Ba zan so wani abu ya sami lafiyarki ba, ni wa zai kula da ni?" Ganin yadda yayi maganar yana tsareta da idanunsa ya sanya ta kawar da kanta gefe. "Meenal" ya kira sunanta. Ta ɗaga ido ta kalleshi. "Keep looking at me, akwai wani abu mai tasiri a gareni da yake fitowa daga idanunki" Jan idanuwan nata tayi ta lunshe, ta sake buɗe su ta ce "Daddy, kaje wurin Khalil please" "Ai kuma na fasa, sai naga ya naki jikin tukuna" "Kar ka biye mini, na gama duk ayyukana, kaya kawai zan saka, sai ka saka a kaini". "Na san abokin nan nasa da na tarar da su tare, zai kai shi Asibiti, shirya mu tafi kawai" "A'a Daddy, ya fini buƙatarka" "Ki shirya mu tafi" ya maimaita mata yana tsuke fuska. Miƙewa tayi ta wuce ɗakinta, ta shiryo tsaf sannan ta sake fitowa, hannunta riƙe da kwalbar turaren da ya taɓa bata tana ɗan ɓata fuska. Ya dubeta ya ce "Ya dai?" "Turare na ne ya ƙare" "Shikenan kin huta" "Na huta kuma, wai haka zan tafi babu turare" "Eh mana haka shi ne dai-dai" sai ta sake ɓata fuska, ta tsaya tana kallonsa. Ya ce "Ya dai mu tafi mana" "Ni ba zan tafi ina wari ba" "Waye ya ce kina wari, ba kin yi wanka ba?" "To idan nayi gumi fa?" Ta faɗa tana sake tura baki gaba. Ya girgiza kai ya ce "Shikenan, kije ɗakina ki shafa nawa" Ta juya ta nufi ɗakinsa, sai dai yadda ya tashi daga bacci, haka ya ɗan gyara gadon, sam bai gyaru ba, ga kayansa nan na bacci da ya fito daga wankan a kan gadon a ajiye, kan mudubinsa ma da ya yi kwalliya a nan ya bar komai har da wani comb da brush, da mayuka kala kala, ta tsaya ta fara da gyara masa gadon, ta kwashe kayan da ya fito da su daga wanka, ta ajiye su a toilet, ta fito ta gyara masa kan madubin, wani mai ta gani a tube, ta ɗauka tana dubawa man da ake shafawa gemu ne, dan ya ƙara taushi. Dariya Amina tayi, ta ce "Su Daddy an girma amma ba a daina gayu ba" ta gama taɓe taɓenta, ta ɗaukar masa turarr ta dinga ɓarnarsa, har da fesawa a jikin jakarta. Sai da ta gama rashin jinta sannan ta fito. Tana buɗe ƙofar ɗakin ya san ta yi masa aika aikar turaren, saboda yadda falon ya gauraye da ƙamshi. Ta nufo shi tana "Mu tafi Daddy" "A ina da ina kika fesa turaren nan ne?" Ta ɗan yi shiru sannan ta ce "Tsakani da Allah, kawai fesawa nayi" "Ai na san fesawar kawai kika yi, kin san tsadar turaren nan kuwa? Ai shikenan Meenal, idan ya ƙare sai ki sai mini wani" Dariya tayi ta ce "Duk in da naji ƙamshin turaren nan na san kaine a wurin" bai ce mata komai ba sai murmushi, ya tashi tsaye yana gyara zaman suit ɗinsa, ta kalli dogon gemunsa da yake ta ƙyalli, kamar wadda mintsuna ta ce "Daddy, kana shafa mai a gemunka dama?" Nufota yayi gadan gadan, har sai da yaje daf da ita, ta tsaya cak tana wulƙita idanu, ya sunkuyo daidai fuskarta ya ce "Duba da kanki ki gani" Duk da irin sassanyan ƙamshin turaren da take shi yake yi, amma sai taji wanda yake tashi a jikinsa na musamman ne, ta zama kamar gunki tana kawar da kai. "Silly girl, da bana taje shi ina shafa masa mai da bai burgeki ba" da sauri ta ɗago ta kalleshi, ya kashe mata ido ɗaya, yayi gaba, ajiyar zuciya ta yi, tabi bayansa da sauri. Suna tafe a mota, cikin rarrashi tana kuma yi masa nasiha a kan ya duba lamarin Khalil, amma yayi mata shiru sai zuba take. 'Daddy ka ƙi cewa komai fa" "Ina jinki ai" "Maganar tawa ba ta da muhimmanci kenan?" "Ai ke hirar taki ce, wata ina ganewa wata kuma shirirtarki kawai ki ke yi" A ranta ta ce 'Ai ba zan yi fushi ba, sai burina ya cika' "To shikenan, ai wannan hirar ba ta shirita ba ce ba, a duba lamarin nan ranka ya daɗe, wasu lokutan ana ɗaukar soyayya wata aba ta shirita musamman ma gamu 'yan zamani, amma soyayya da daɗi aba ce mai tsayawa a rai" Waiwayowa ya yi ya kalleta ya ce "Kin taɓa yi ne?" "A'a ji nayi nima ana faɗa ai, kuma ina ji in ana karantawa a littafi, ai kai ka taɓa yi da daɗi ko?" Kafin ya yi mata magana, wayarsa ta fara ringing ya kalli Amina ya ce "Remain silent, Gimbiya na kirana" Wani haushi ne ya kama Amina, ta ce "Idan ka ɗaga sai nayi magana" tayi maganar very serious. Kallonta yayi yaga da gaske take. "Ina magana kike cewa sai kin yi magana?" shi ma yayi maganar so serious. Ta mayar da kanta ga kallon window, ya ɗaga wayar ya sa a kunnensa. "Hello dear, kin tashi ne?" Amina na iya jiyo muryar Hajiya Zainab ta ce "Na tashi, ya kake ya aikin?" "Alhamdilillah, ya Fadila kodayake mun yi waya da ita". "Haka ne tana lafiya, sun kusa gama exams ma" "Masha Allah, kina lafiya dai ko?" "Lafiya lau dear, visa mu ta fito fa, ba zaka dawo muyi sallama ba, da Fadila sun gama exams zamu tafi" "Ohh, yakamata in dawo in ganki muyi sallama kuwa, dole in tsayar da komai in dawo in ki my dear" Amina ce ta jiyo ta kalleshi a fusace, gane yinƙurinta da yayi na zata yi Magana, ya sanya cikin hanzari ya janyota jikinsa, ya toshe mata baki. Ware baki tayi zata yi masa ihu, amma ya kuma danneta a jikinsa, ya toshe mata baki, ta kasa motsi. Wani Irin Bugu zuciyarsu take a tare, Hajiya Zainab na yi masa magana amma ya kasa amsa mata, saboda halin da suka shiga baki ɗaya. (TOFA AKWAI JAGWAL FA🤣🤣🤣) AYSHERCOOL 08081012143GABA DA GABANTA                 NA AISHA ADAM AYSHERCOOL 50 Lamo Amina tayi a jikinsa, tana cigaba da jin yadda zuciyoyinsu ke bugawa, shiru yayi ya kasa magana, yana sauraren Hajiya Zainab. "Hello, ya naji kayi shiru, kana jina kuwa?" Da ƙyar ya iya harhaɗo kalaman da zai yi Magana da su ya ce "Lafiya lau" "Amma ya naji muryarka ta sauya, ko akwai wani abu ne?" "Bakomai, mu cigaba da magana ina jinki" Ta ce "Nifa so nake da zarar mun dawo daga umara, kaje kayi maganar auren Khalil, dan ba zan bari ya auro  mini ƙasƙantacciya a cikin zuri'ata ba" "My zee, a bar wannan maganar zuwa ku dawo ɗin, sai muga yadda za ayi" "To zaka zo ɗin kan mu tafi?" "Gani nan dai, idan na samu chance zan dawo kan ku tafi in sha Allah" "Shikenan, Allah ya sa ka zo na fara kewarka, zaman nan da kayi ka daɗe a gida, naji ina missing ɗinka" Yayi murmushi ya ce "Bayan nace ki biyoni nan kin ƙi, kuma ma ai guduna kike kince na tsufa" Dariya Hajiya Zainab tayi ta ce "Kai da ba zaka canza ba ko? Ko zaka dawo ne, am just missing You" "Idan kika ce in dawo sai in dawo ai" Mutsu mustu Amina ta dinga yi, tana son ƙwacewa dan hirar ta su tafi ƙarfin kunnenta, kuma ga hirar ta su wani irin baƙin ciki ta jefata a ciki, gaba ɗaya Amina ta rasa ƙwarin jikinta, dan ba ƙaramin riƙo yayi mata. Kawai ta ware haƙoranta ta gasa masa cizo a hannunsa da ya toshe mata baki. Rintse idanunsa yayi, saboda yadda zafin cizon ya ratsa shi, amma ya sake riƙeta yana, fesar da iskar bakinsa. Hajiya Zainab ta ce "To ni dai ya maganar kuɗin, haryanzu baka turo mini ba" Ya buɗe idonsa ya ce "Anjima zan saka miki in sha Allah" "Wayyo Allah, na gode sweetheart, sai na jika" Shi dai direba duk da ba jin hausa yake ba, mamakin Boss ɗin nasa yake yi, ya san shi mutum ne ba mai son hayaniya ba, mai matuƙar tsare gida, sai dai rana tsaka ya ganshi da wata 'ya da bai san alaƙarsu ba sai biye mata yake. A hankali ya ajiye wayar, ya kalli Amina, da tayi wuƙi wuƙi kamar an kwashewa karya 'ya'ya. Ya cire hannunsa daga bakinta, aikuwa da sauri ta tashi zaune daga jikinsa tana ɓata rai. Ya kalleta ya ce "Meyasa kika cijeni?" Hararsa tayi ta ce "To waye ya ce ka rungumeni?" "Ba rungumeki ne ya sa kika cijeni ba, kishina kike saboda ina waya da matata, haushin hakan ha saki cizo na" "Ni ina ruwana da wayarku?" "Meenal" ya kira sunanta. Ta ɗago idonta ta kalleshi ya ce "Meyasa kike kishina, kina sona ne?" Yayi maganar yana ƙura mata ido. Hararsa tayi ta ce "Allah ya kiyaye, me zan yi da tsoho?" "Tsoho yana da abin da zai yi da ke, kuma na kuma ganin ina waya da mata ta, kina haɗe rai za kiga abin da zan miki" Haɗe rai tayi, ta kawar da kanta gefe, idanunta har sun yi ja, tana ta ƙoƙarin basarwa amma ta nemi ta kasa. Har suka isa wurin da zasu ajiyeta, ba wanda ya kuma cewa kowa komai, sai da zata sauka sannan ya ce "Ki kula zanje in ga Khalil in dawo" "Kar ma ka dawo" ta faɗa cikin ƙunƙuni. "Kar ma na dawo ko Meenal? Na gode" ba tayi zaton zai ji ba. "Yi haƙuri ba haka nace ba" "Idan ma hakan kika ce, yaya zan yi da ke?" Sai da ta sauka suka tafi, taga bai dace ta gaya masa haka ba, "Am sorry' ta furta a hankali ta nufi cikin hall ɗin. Ko da Daddy ya kira Khalil, Khalil ya sanar masa yana gida, yaje ya ɗauke shi ya mayar da shi Asibiti, sai dai an samu cigaba sosai da sosai, jikin Khalil yayi sauƙi sai dai fuskarsa babu walwala sam. Maganganun Amina ne suka dinga dawowa Daddy, ya ɗan ƙura wa Khalil ido sannan ya ce "Khalil" "Na'am Daddy" "Gaba ɗaya baka walwala, ka gaya mini meke damunka ne?" "Bakomai Daddy, yanayin jikina ne kawai da bana jin daɗi, amma na ji sauƙi sosai Alhamdilillah" "Khalil, ina son ka dinga sawa ranka salama a kan komai, ba kowane lokaci ne muke samun abin da muke so ba, wasu lokutan sai mun gama saka ranmu a kan abu, kawai sai Allah ya musanya mana da mafi allhairinsa, dan haka ka koyi bawa zuciyarka haƙuri a duk lokacin da ka rasa wani abu" Khalil ya jinjina masa kai alamar to, a ƙasan zuciyarsa kuwa damuwa ce fal, baya son Hafsa ta auri wani ba shi ba, ji yake ko ya roƙi Abdul ya aureta, idan ya so sai ya yi masa bayinin abin da ya faru da ita, ya san Abdul mutumin kirki ne, ya san ƙaddara ba zai cutar sa Hafsa ba, amma sai yayi tunanin idan shi ko kuma Hafsan wani daga cikinsu bai amince ba fa? Haka yayi shiru ya cigaba da laluben menene mafita. Tun da al'amarin nan na ranar exams ɗin Kankiya ya faru, sai yau suka sake komawa makaranta domin suna da exams, a aji ta tarar da Yazid, amma sai taga ya yi mata kwarjini sosai da sosai, ba tare da tunanin komai ba ta isa wurin da yake. "Sannu ya jiki kuma?" Ya ɗaga kansa ya kalleta ya ce "'Jiki Alhamdilillah, na ji sauƙi" "Kaji sauƙi, ko kuma ka warke?" "Da sauƙi dai" ya bata amsa yana ɗauke kansa daa gareta, saboda wani abu da yake fuzgarsa game da ita, idan har zai yi tozali da ita sai ya nemi ya rasa nutsuwarsa, yana matuƙar jinta a ransa, amma idan har ya na son ya zauna lafiya a makarantar nan, ya zama wajibi ya nisanceta, idan ba haka ba zai ta shan wahala ne a banza. Ta ɗan jingina da jikin bencin da yake ta ce "Wannan karon da baka zuwa, akwai abubuwa da yawa da ban iya ba, kawai dai nayi karatu ne ina fatan Allah ya sa na tsallake". "Just feel like you never knew me before, ki fuskanci karatun zaki iya ko babu ni" "Kamar yaya kenan, ni bana gane irin wannan hausar da ake yi a dunƙule" "Fadila, kar ki saka a kuma jefar mini da takarda, na riga na sanarwa da Kankiya babu ni babu ke, ban sani ba ko bayan Kankiya akwai wani malamin ma da yake sonki, kar yawan ganinmi tare ya kuma janyo mini wata matsalar, idan na rasa karatuna komai nawa zai koma baya ne" Jiki a sanyaye ta ce "You mean i should leave?" Ya jinjina mata kai. Miƙewa tayi tsam ta bar wurin, ji yayi kamar ya kirata, yana missing ɗinta sosai, daure zuciyarsa kawai yake yi, amma babu yadda ya iya, tun da ruwa ba sa'an kwando bane ba. Ɓangaren Hafsa kuwa, Mama jiki na nema ya kuna rikicewa, saboda ganin halin da Hafsa ke ciki, duk da Hafsan na ƙoƙarin ɓoyewa, amma Mama ta kan gane wasu lokutan idan tayi kuka, wasu lokutan kuwa sai cikin dare take jin sheshsheƙar Hafsan tana kuka, Mama bata ga laifin Hafsa ba, saboda ta daɗe ba taga mutumin da Hafsan ta bawa yarda ɗari bisa ɗari kamar Khalil ba, zata iya wuni ba ta zauna ta yi hira sosai da Mama ba, sai abin da ba a rasa ba, saboda ɗabi'arta ce haka, amma da zarar Khalil ya kirata a waya, sai dai Maman ta dinga jiyo dariyarta, yana bi da ita a yadda take da halinta, yayi faɗi tashi sosai kan ya samu kanta. Hafsa na iya ƙoƙarinta, dan kar Mama ta gane, amma yanayin ya kasa ɓoyuwa baki ɗaya, lokaci loka idan suka zauna, Mama na yiwa Hafsan nasiha, gami da rarrashinta, da bata shawarar ta dage da Addu'a. Sai dai ita ma Maman dakewa kawai take yi, har zuciyarta tana son Auren Hafsa sa Khalil, tana jin yaron a ranta, yadda yake girmamata da yadda yake bawa Hafsan kulwa daa hausawa sun ce mai ɗa wawa, ya siye zuciyar Mama da soyayyar da yake wa 'yar ta, sai dai mahaifiyar Khalil ta rushe burin da suke da shi na son kasancewa da juna. Khalil na kwance a gadon asibiti, ana cigaba da ƙara masa ruwa, Daddy kuma ya yi masa sallama ya tafi, ya rintse idanunsa, babu abin da yake hangowa, sai Hafsa a kusa da shi, ko muryarta yana ƙishirwar ya ji, zuciyarsa ta dinga raya masa ya koma Kano, ko ya samu ya ganta, amma yana matuƙar jin nauyin Maman Hafsa bisa ga abin da Mummy tayi musu, baya jin ko ido zai iya haɗawa da ita, ga furucin Hafsan ita ma da tayi. Lumshe idanunsa yayi, yana tariyo al'amuran masu wuyat gushewa a zukatan masoya da ya faru tsakaninsa da Hafsan, abubuwan da suke burgeshi da ita, na kamewarta, miskilancinta murushinta da yawan tsokanarsa da ta kan yi, uwa uba kyauta da bashi Adduoi na tsari, da jaddada masa ya riƙe Addu'a. "Am missing You so badly Hafsa" ya furta yana jan numfashi da ƙyar. Babban abin da yake tsoro shi ne, kar ya koma Kano yaje gidansu Hafsan, wani ya gayawa Mummy ya ƙara janyo masa wani tashin hankalin. Ya dafe kansa da yake yi masa wani irin ciwo kamar zai tsage. Hafsa tana tsakar gida tana ta shara, Mama tayi baƙuwa wata maƙociyarsu da take layinsu Alawiyya, ta shigo sayen kuka da maggi ta tsaya tana ta zuba. "Ni kuwa Maman Hafsa ina sirikinmu ne?" Cikin rashin fahimta Mama ta ce "Wane sirikin kenan?" "Wannan ɗin nan da yake zuwa wurin Hafsa mana mai mota, muna ta jira muji abin arziki ace ya fito, kar dai ace irin samarin shahon nan ne?" Mama ta ce "A a, baya gari ne ba a nan yake nema ba" Alawiyya ta ce "Au, ai na zata shima guduwa yayi, kin san samarin nan na zamani, da ance su fito suke guduwa dama wasu 'yan rage dare ne, ina tayi muku murna wallahi, Allah ya tabattar da Alkhairi". Mama ta amsa da"Ameen" Maimakon Alawiyya ta tafi, sai ga ɗora da cewa "Wallahi ku yi ta addu'a, Allah ya riƙe musu shi kuna kwa huta, kin san halin mufuncin 'yan unguwar nan, za a iya zagewa aje ace masa 'yar mace ce ba ta da uba, ba a taɓa ganin wani naku ya zo ba. Kwanaki zancen nan yayi ta yawo a unguwa, wani babban mutum ya saka direbansa ya biyota ya ga gidans, kan ya zo ya sa aka ɗan yi masa bincike a kanku, saboda Aurenta zai yi, amma aka samu munafukan da suka gaya masa wannan Magana, na san babu lallai ku san an yi, amma zance ya cika gari" Mama ta ce "Aishikenan kowa yayi na gari kansa" Alawiyya ta gama soki burutsunta ta fita. Hafsa ta duƙufa tana wanke-wanke, hawaye na ɗiga cikin ruwan wanke wankeen nata, tayi zurfi a cikin tunani, kawai taji an dafa kafaɗarta, ta ɗago ta kalli Mama da ke tsaye a kanta. Mama ta durƙuso ta dafa ta ta ce "Dan Allah, ba danni ba Hafsa ki kwantar da hankalinki, ki daina wannan kukan, duk abin da yake rabonki ne, duk surutun mutane sai Allah ya kawo miki shi, kuma a jikina ina ji cewar Addu'ata ta karɓu a wurin ubangiji komai zai zo ƙarshe" ta gyaɗawa Mama kai tana ƙoƙarin cigaba da wanke kwanukan. "Dan Allah ki daina kin ji Hafsana" mama tayi maganar a sigar rarrashi. "Na daina Mama" "Yauwa, Allah yayi miki albarka ya yanke mana wannan wahalar haka" "Amin Mama" a gaggauce Hafsa ta gama wanke kwanukan, ta gyara wurin ta nufi banɗaki, ta shiga ta kulle ƙofar tayi kukanta mai isarta, sannan ta wanke fuskarta ta fito. Sam Amina ba ta san Daddy ya zo ba, a wannan karon ma sun yi nasara, makarantarsu taje semi final both a debate da Quiz, sai murna suke yi ɗaukacin ɗaliban da malamansu. Kamar yadda aka tsara aka yiwa su Amina shigar fulani na shuɗin saƙi, da kwalliya, wasu kuma shigar hausawa, suka fito suka yi presentation a kan Al'adu na fulani da Hausawa, da abubuwan burgewa game da Al'adun nasu. Ciki har da rawa irin ta Fulani. Wani daga cikin manyan baƙin da aka gayyato, wani Christian mai babban muƙami, ya tashi yayi musu tafi tare da jawabin jinjina ga matasan yaran, har yake cewa Amina zai zo Kano a bashi Auren ba fulatana" Cikin murmushi Amina ta ce "Zamu  baka, bayan Auren bafaulatana har da saniya zamu haɗa maka, Auratayya da abota a tsakanin mabanbantan ƙabilu na ƙara kawo ƙauna da zaman lafiya da kuma cigaban tattalin arzikin ƙasa" tafi aka sake ɗauka a hall ɗin, Amina ta burge mutane sosai da sosai ba ga da tsoro sam idan ta fito gaban mutane, akwai confidence ga iya Magana gata kuma da barkwanci. Mutumin ya ce "Na ji daɗin wannan karamci na Hausa Fulani, kuma ina fatan zan kawo ziyara garin Kano domin tabattar da abin da kuka yi mana presenting game da ƙabilarku, sai dak kafin in zo Kano a bani mata da saniya, na bawa wannan yaran da suka yi presenting ethnic groups ɗinsu naira dubu ɗari biyar kowannen su, ita kuma wadda ta ce zasu bani kyautar mata da saniya, na ƙara mata naira dubu ɗari biyu a kai, sannan akwai kyautuka na musamman ga makarantar da tayi nasara, zan bada kuɗin a ranar da za a rufe ceremony. Nan aka yi ta tafi ana shewa, aka shiga kaɗe kaɗe da raye-raye a hall ɗin, kamar yadda aka saba a duk lokacin da aka kammala presentations ɗin ranar. Wannan mutumin na ɗazu ne da ya basu kuɗi, ya sa aka kira masa Amina ya tsareta da surutai. Suna cikin magana ne taga Joseph ya nufo su, Amina ta kalli mutumin ta ce "An zo ɗaukata, zan tafi" Ya ce "Shikenan sai mun haɗu gobe" Ta jinjina masa kai, ta cewa Joseph tana zuwa, taje ta ɗauko jakarta, ta ɗora after dress a kan kayan, tabi Joseph suka fice daga hall ɗin. Ta tambayi Joseph yaushe suka zo?. "Ai tun kan ku gama Quiz muka zo tare da Oga". "Amina ta ce Amma ya aka yi ban ganku ba?" "Eh ai yau ba a wurin baƙi na musamman ya zauna ba" ta gyaɗa kai, suka ƙaraso wurin mota. Ko da ta buɗe bayan motar ta shiga, fuskar Daddy sam babua annuri, ya haɗe rai tamau bata taɓa ganin ya ɓata fuska haka ba sai yau. "Daddy lafiya kuwa?" Tayi maganar cikin fargaba. Banza yayi mata ya kawar da kansa. Ba ta haƙura ba ta kuma cewa "Ko wani abu ne ya samu Khalil?" Still ya kuma yi mata shiru, Amina tayi shiru da bakinta, har suka ke gida bai ce mata komai ba, bayan sun shiga cikin gidan kasa jurewa tayi, tabi bayansa tana masa Magana. "Daddy dan Allah idan laifi nayi maka ka gaya mini mana, ko wani abin ne ya faru?" Tsayawa yayi cak ya kalleta, sai da hantar cikinta ta kaɗa, ta tsaya tana kallonsa. Duk da tazarar da ke tsakaninsu, haka ya sanya hannu ya janyota, ya fara ƙoƙarin cire after dress ɗin da ke jikinta. Kwanakin nan ta kasa gane kan Daddy gaba ɗaya, yana tsiro mata da wasu ɗabi u da bata san shi da su ba, a baya ba ruwansa da ko kai hannu kusa da ita, amma yanzu ta kasa gane kansa. Riƙe rigar tayi tana faɗin "Daddy meye haka?" Idonsa jawur, ya cigaba da ƙoƙarin cire rigar jikinta. Riƙe rigar tayi tana ihu, amma yafi ƙarfinta, sai da ya cire after dress ɗin kan kayanta, ya rage sai kayan saƙin fulanin da tayi presentation da su a jikinta. "Daddy meye haka ne?" "Shut up!" Ya daka mata tsawa, sai da ta razana. "Ke baki ji kunyar kanki ba? Kalli kayan da suke jikinki, da su kika fita gaban mutane kina rawa kina da hankali kuwa?" "Amma Daddy ai kayan basu matsani ba" "Basu matse ki ba ko? That's good for you" Ya juya yana huci, ya bar ta a tsaye a falon. Amina sai murna ta koma ciki, tana murna ta samu kuɗi masu yawa, tana son ta gayawa Daddy ya tayata murna, amma yayi fushi bata taɓa zaton ya iya fushi haka ba sai yau. Ɗakinta ta wuce, tayi wanka ta canza kaya, yunwa take ji sosai, ta fito falon ta tarar da Daddy a zaune, ya lumshe idonsa yayi shiru. "Daddy me zan girka maka?" "Na ƙoshi" ya bata amsa a taƙaice. "Dan Allah Daddy kayi haƙuri, na san nayi kuskure, ba zan sake ba in Sha Allah" Tashi yayi ya barta a wurin ba tare da yace mata komai ba. Jiki a sanyaye ta tafi Kitchen, ta tarar da kayan Abinci an sayo an ajiye, ta dafa indomie, amma ta kasa ci jinta take kamar ba ita ba komai ma baya mata daɗi, ta ɗau wayarta ta kira Daddy, amma ya ƙi ɗagawa, ta tura masa saƙonni na ban haƙuri, amma yaƙi tankawa. "Daddy am sorry, kayi haƙuri mana" ta furta maganar lokacin da take sake tura masa wani saƙon. Bata gaza ba, ta kuma fita falon, ta hango ƙofar ɗakinsa a buɗe. Cike da fargaba ta nufi ƙofar ɗakin, ta leƙa amma ba ya ciki. Dawowa tayi falo ta zauna tayi tagumi, abin duniya ya isheta, shi haka yake idan yayi fushi, abin nasa babu sauƙi sam, bata taɓa zaton ya iya fushi haka ba. Kamar yadda Alhaji Ahmad ya yiwa Hajiya Zainab alƙawari, ya tura mata kuɗin da ta nema a wurinsa, kuma ya bata, da taga alert jiki na rawa ta kira Hajiya Salma a waya ga sanar nata kuɗin nan sun samu, suka yi ta murna tare, Hajiya Salma ta tura mata account number ta tura mata kuɗin nan. Ta kira Mummy a waya tana cigaba yi mata godiya, daga nan kuma suka faɗa hirar batun Khalil. Hajiya Zainab ta ce "Ai karki damu, na yiwa babansa magana muna dawowa daga umara, babansa zai je nema masa auren Kursum, ai yarinyar tayi na yaba da ita" Hajiya Salma ta ce "Alhamdilillah, kuma a lokacin ma na san Bashir zai dawo, sai su haɗu da Fadila ma" "Aikuwa da faɗuwa ta zo daidai da zama, duk sai a haɗa ayi maganar a wuce wurin, kin san halin Fadilan ma ita idan na biye mata yin auren a yanzu ma baya gabanta, gara tun wuri kan tayi mini irin ta ɗan uwanta, ta kwaso mini gayyar tsiya ko da ba halinsu ɗaya ba ita da Khalil, in nema mata miji da kaina, na san ba zata ƙi ba ita 'yar I don't care ce" "To shikenan, Allah ya daidaita mana kansu, kawai da kun dawo a fara magana, sai mu ɗaufa azamar biki" Suka yi dariya, Hajiya Salma ta ƙara yiwa Hajiya Zainab godiya, sannan suka yi sallama. Duk wani abu da Amina za tayi ta bawa Alhaji Ahmad haƙuri, ya shareta ya ƙi kulata, har girki tayi masa amma ya ƙi ci, ya cigaba da sabgoginsa. Kasancewar washegari lahadi ace, babu wani event da za suyi ranar, aka ce kowa ya huta ranar. Abu kamar wasa Amina ko Abinci ba ta iya ci, sai aikin kuka, gaba ɗaya taji haushin kanta take ji, duk abin da tayi masa na rashin kunya da cizo bai fushi da ita haka ba sai a kan tayi rawa a gaban mutane, ita na ta wanni fannin taga rashin dacewar hakan, amma rawar ba ta rashin kunya ba ce, kuma ko ina na jikinta a rufe yake, amma ya ɗau wannan fushi haka. Wunin ranar lahadin nan, bai wuni a gidan nan ba, sai dare bayan ƙarfe tara ya daw gida. Amina ta riga tayi wani irin mugun sabo da shi, hakan ne ya sanya ta ƙara shiga damuwar rashin kulata da yake yi. A falo ya tarar da ita taci kukanta ta godewa Allah, yana shigowa ta miƙe tana masa sannu da zuwa. Da kai kawai ya amsa mata ya wuce ɗakinsa. Binsa tayi ɗakin tana kiran sunansa. Sai da ya shiga ɗakin sannan ya tsaya ya kalleta ya ce "Lafiya?" "Daddy dan Allah kayi haƙuri, ka daina fushi da ni" Maimakon ya bata amsa sai ya ce "Bani wuri zan cire kaya" Ta ce "To ka haƙura?" Bai kulata ba ya fara cire kayan jikinsa. Juyawa tayi ta bar masa ɗakin tana share hawaye, tana fita ya bi ƙofar da ido, ya shafa ƙirjinsa a hankali ya ce "Am sorry meenalina, ba yadda na iya dole in hukunta ki, yadda gobe ba zaki sake ba, am not punishing only you, but together with my soul am missing you" ya ƙarasa maganar kamar tana gabansa. Wankansa yayi ya fito, ya koma falo ya tarar da ba ta gaza ba ta kuma yi masa wani girkin. Ya zauna ya kwashi girkinsa tukuna, sannan ya nufi ɗakinta, har ta kashe fitila, ya sa hannu ya kunna fitilar. Tana zaune a kan gado tayi shiruu alamar tayi kuka ta gaji. Ya nufi in da take zaune a kan gado, yana zuwa ta juya masa baya tana haɗe rai. "Dan kin samu na biyoki zan rarrashi shi ne zaki ja mini aji?" Sai ta fashe masa da kuka. "Shikenan ya isa, is ok let's talk juyo kiji?" Noƙe kafaɗa tayi ta ƙi kallonsa. "Ni zaki jawa aji dan kin samu na sauko?" "Amma ba nayi ta baka haƙuri ba ka ƙi haƙura, kayi ta sakani kuka ko Abinci bana iya ci" tayi maganar wasu hawayen na zuba daga idonta. "Inyee Meenalin ba, tana son Daddy ashe, har kin yi missing ɗina haka?" Murguɗa masa baki tayi tana goge hawaye. Dariya yayi yana girgiza kai ya ce "Meenal, dole in yi fushi da ke, kin je kin yi rawa a gaban mutane a haka, kuma wani ƙaton banza ya keɓe da kw kuna hira, naji babu daɗi saura ƙiris na zane ki ma, kuma kuɗin da ya baki ba zaki karɓa ba" Ta kalleshi ta ce "Meyasa?" "Saboda haka nace" tayi shiru tare da sunkuyar da kai. Ya ce "Tashi muje in baki Abinci" Ta ce "Ni na ƙoshi" "Kika ƙoshi da me? Oya tashi muje" Ta noƙe kafaɗa ta ce "Ni sai dai ka kawo mini nan in ci" "Ni zaki aika, kuma ki sa aiki?" "Eh ramawa zan yi, ka dinga sani kuka duk haƙurin da na baka" "Ai shikenan ya wuce, muje in nuna miki wani abu" Ta kalleshi ta ce "A ina?" Ya ce "Muje ki gani" Ta sauko daga kan gadon, shima ya miƙe suka fice daga ɗakin. Yau Litinin a yau su Amina zasu yi karawar kusa da ta ƙarshe a gasar Quiz, wadda kusan ita ke jan ragamar makarantarsu gaba ɗaya. Ko da Alhaji Ahmad ya fito falo, kallo ɗaya ya yi mata jikinsa yayi sanyi, saboda yadda fuskarta da idanunta suka kumbura, alamar ta daɗe tana kuka sosai. Ya dafe goshinsa yana sake ɗora zargin komai a kansa, ya tunkari in da take, ya zauna kusa da ita, ya sauke mata tagumin da tayi, ta ɗago jajayen idanuwanta ta kalleshi. "Dan Allah Amina, ki sassauta wannan kukan haka kin ga cikin mutane zamu shiga, kar ki wani abu da zai janyo hankalin mutane har a fuskanci abin da ya faru, kar mutuncina ya zube a idon mutane". Wasu irin hawaye ne masu ƙona zuciya, suka zubo daga idonta, ta kalleshi da kumburarrun idanunta ta ce  "Kai mutuncinka ne ya dameka ko? Nawa kuma ko oho, na gode sosai" 😳🙄JAMA'A MEKE GOING NE, NIFA BAN GANE BA" AYSHERCOOL 08081012143 VIP GROUP, KAR KUGA KUN BIYA KUƊI, NA CIGABA DA GANIN POSTING ƊIN VIP A GROUPS ZAN DAINA MUKU POSTING KULLUM, AND I MEAN IT🤨GABA DA GABANTA BY AISHA ADAM AYSHERCOOL 51 Sosai daa gaske Amina ta sake fashewa da kuka, jikinta har rawa yake yi, saboda yadda take kukan. Cikin kwantar da murya Daddy ya ce "Amina, i feel your pain, na fiki shiga damuwa da tashin hankali a kan abin da ya faru, amma dan Allah ki tsaya ki fahimceni, wannan abu ne da ya faru tsakanin ni da ke, babu wanda ya sani, ba wanda ya san muna tare ma, dan Allah ki rufa mana wannan Asirin, ki kwantar da hankalinki, babu wanda zai gane" Cikin kuka ta ce "Ni dai ba ka yi mini adalci ba, ka cutar da ni, duk da irin tarin nasihar da Baba yayi mini kan nayi tafiyar nan, Wannan shi ne sakamakon da zan masa?" Tayi maganar tana shesheƙar kuka. Miƙa hannu ya yi yana ƙoƙarin janyota jikinsa, amma ta ja da baya. "Shikenan, dan Allah kiyi haƙuri ai na baki haƙuri, kuskure ne ya riga ya faru, kiyi haƙuri ki daina wannan kukan, ki zo mu tafi lokaci yana ƙurewa" "Ni ba in da zani, ba zani makarantar ba, na fasa duk competitions ɗin tun da a kansu koma menene ha faru da ni, ni gidan zan koma ba zan sake kwana a garin nan ba" Gaba ɗaya Daddy ya rasa abin da yake masa daɗi, gaba ɗaya Amina ta birkice masa ta caza masa kai. "Amina so kike kiga ina kuka nima? Wa zai rarrashi wani kenan? Dan girman Allah kiyi haƙuri, ki zo muje ko quiz ɗin ku gama sai na san abin yi" "Ni ba in da zani na gaya maka, na riga na haɗa kayana kawai ka sakani a mota mu tafi" "Meenal ko durƙusa miki zan yi a kan gwiwata ne? Dan Allah ki mini Wannan alfarnar, ko ita kaɗaice alfarmar da ta rage zaki iya yi mini a rayuwata" Da ƙyar da siɗin goshi, da rarrashi da kwantar da murya, Daddy ya sanyata ta shirya, suka tafi wurin competition. Sai dai abin yayi affecting ɗin ta, gaba ɗaya bata da karsashi a wannan karon, babu ƙwarin gwiwa, sai shirme take yi, lokaci lokaci hawaye na cika idanunta. Gaba ɗaya ta kasa mayar da hankali, har ɗaya makarantar na neman yin galaba a kansu. Gaba ɗaya Daddy ya rasa ina za zai saka ransa, wannan babar dama ce ga Amina da zata taimaki karatunta, ta samu damarmaki, amma tana neman tayi wasa da damar. Aka tafi hutun mintuna goma sha biyar, hakan ya bawa Daddy damar janta gefe, ya cigaba da aikin rarrashi, kamar wanda aka tafi aka bar shi da 'yar yaye. Mutumin nan ne da yayi musu alƙawarin kuɗi, ya nufo su yana kallon Amina da take zubar da hawaye Daddy na mata Magana ƙasa ƙasa. "Yarinyar fulani, meke damunki ne? Haba our champion of the year, ya kike nema ki bamu kunya ne?" Wani irin haushin mutumin ne ya kama Daddy, yaji tamkar ya tashi ya make shi ya huta. Amina dai kallo ɗaya ta yiwa mutumin ta sunkuyar da kai tayi shiru. Ganin ba su kula shi ba ya sanya ya kalli Daddy ya ce "Ko kaine babanta?" Ya amsa masa da "Eh ni ne" "Amma ya aka yi ba kwa kama sam? Yarinyarka ta burgeni sosai da ina da ɗa da na nema masa aurenta" yayi maganar cikin sigar wasa. Daddy bai tanka masa ba, ya ja hannun Amina zuwa wani wurin daban. Ya dinga share mata hawaye, yana cigaba da kwantar da hankali, tare da yi mata alƙawarurruka daban daban, Allah ya ɗora shi a kanta, da ta koma tayi abin arziki, makarantarsu tayi nasara zuwa zagaye na ƙarshe wanda a nan za a fitar da gwani. Su kansu malaman makarantar su Amina, da sauran ɗaliban wasu makarantun ma da suka saba da juna a wurin, suka dinga tambayar ta meke damunta, amma ta ce musu babu komai, sai haƙura suka yi suka ƙyaleta. Da aka zo tafiya ma, ta tuburewa Daddy cewar ita ya barta cikin 'yan makarantarsu, ya kawo mata kayanta ba zata sake kwana da shi a gida ɗaya ba, nan ma sun shafe tsawon lokaci suna fafatawa sannan ta amince ta bi shi gida. Hatta girki da take musu ta daina, sai dai yayi order Abinci, ya zo ya zauna ya yi ta aikin rarrashi yana bata, gaba ɗaya damuwar da Amina take ciki ya fara shafarsa. Khalil ya warke, har ya ce zai zo ya kaiwa Daddyn ziyara, Daddy ya ce masa ba sai ya zo ba, shima barin Abuja zai yi, ya wuce Lagos. Tun Amina na share Daddy, tana ta yi masa wulaƙanci, shi kuma yana binta yana lallaɓata, har ya fara bata tausayi, kullum cikin bata haƙuri yake, yana kuma ƙoƙarin kwantar mata da hankali, da ta motsa cikin rawar jiki zai fara tambayarta me take buƙata me zai yi mata, gashi ba kowane Abinci yake iya ci ba, dan haka ta lura galibi Fruit kawai yake ci. Fadila ce zaune, a ɗakin Yusra tana ta jujjuya yadda za ta yiwa Yusra bayani ba tare da ta yi mata wata fassara ta daban ba. "Girl, ya ne? Kin zo kin sani a gaba kina kallona, kin ƙi magana" Fadila ta ce "Girl ba zaki gane ba" "Zan gane, yi mini bayani mana" "Kin san abin da ya faru kuwa ranar da muka yi exams ɗin Kankiya kuwa?" Yusra ta ce "A'a baki gaya mini ba" Nan Fadila ta bata labarin abin da ya faru, da duk yadda suka yi. Yusra ta ce "Ikon Allah, ai tun farko yakamata ki ɗau wannan matakin, ba sai da lamarin yayi tsami haka ba" "Bari kawai, bana son in yi wani abu ne da zai sa Kankiya ya rasa aikinsa, yanzun ma dan ta ƙure ne, bana son wani abu ya sami Yazid saboda ni, ƙiri ƙiri suka haɗa kai da abokinsa Tj suka nemi su ci zarafinsa fa" "To Allah ya kyauta" Fadila ta ɗan yi shiru sannan ta ce "Kin san wani abu Yusra?" "A'a sai kin faɗa" "Yazid ya yi fushi, ya daina shiga harkata baya son duk wani abu da zai sake haɗani da shi" Yusra ta gyara zamanta sannan ta ce "Ai dama abin da kika yi masa baki kyauta ba, na gaya miki kika ƙi yarda" Fadila ta ce "Kinga ni fa ba wannan ne ya dameni ba, Yusra ni ba son Yazid nake ba so nake na taimaka masa" "Ki taimaka masa kamar yaya kenan?" "Yusra, Yazid ya faɗi wasu abubuwa da na fuskanci yana buƙatar taimako, tun a farko na fuskanci ba shi da shi, kuma ya gaya wa Kankiya cewa, ni ina da komai shi ba shi da komai sai Allah da karatunsa. Ina son sanin idan da abin da zai taimake shi da shi in taimaka masa" Yusra tayi murmushi ta ce "To yanzu ke Fadila ai kin riga kin ɓata lamarin, maganganun da kika gaya masa dole ya ji babu daɗi ga wulaƙanta shi da aka nemi ayi duk dan saboda ke, dole yayi ƙoƙarin nesanta kansa da ke." "Girl, Yazid he is simple minded, kawai ina son in taimakawa rayuwarsa, amma zai yi wahala ya yadda he is avoiding me, ko lokacin da muke shiri da ƙyar yake karɓar abu a hannuna" "Girl, yanzu duk wani abu dole ki bari a koma school, idan aka koma sai mu san ta yaya zamu ɓullowa lamarin, muyi bincike a kan sa, sai kiga ta ina zaki ɓullo masa" Tayi ajiyar zuciya ta ce "Shikenan, Allah yasa ya amince da taimakon, dan Yazid da alama yana da taurin gaske sosai" Yusra tayi murmushi daidai lokacin da take miƙa hannu kan wayarta da ke vibrating. Ta ɗaga wayar ta saka a kunnenta tare da yin sallama. "Salamu Alaikum, Yaya Abdul brk da rana" "Barka dai, kin tashi ko kuma ni na tasheki?" Murmushi ta yi ta ce "Haba dai, rana fa tayi na tashi tun ɗazu" Ya ce "Hmm ai ke 'yar hutu ce, yaya zan samu Cake ɗin anjima?" "Eh zaka samu in Sha Allah, guda ɗari ko?" "Eh ɗari, gudunmawa zan bawa abokina za mu yi reception gobe in Allah ya kaimu, zai yi Aure" Yusra ta ce "Ma sha Allah, Allah Ya sanya alkhairi, saura naku kai da Yaya Khalil Allah ya nuna mana" Abdul ya yi murmushi ya ce "Sai dai Khalil, tun da yana da budurwa ni ko budurwar bani da ita, yanzu reception ɗin nan kowa zai je da budurwarsa ni sai dai in je ni kaɗai, ki samo mini hayar budurwar da zata rakani in biya" yayi maganar cikin zolaya. Sosai Yusra take dariya, ta ce "Hayar budurwa kuma?" "Eh mana Kodayake ba sai naje da nisa ba, ai gaki sai ki rakani kawai, gani ga ki ga cake ɗinmu" "Yaya Abdul kana da abin dariya, sai muyi ciniki ka biyani in raka ka ai, bari in je in fara aikin dan in gama da wuri" "To shikenan, ki sako mini account number in tura kuɗin" "Yaya Abdul ai kai ne, ka saka kuɗin 50, kawai" Abdul ya ce "No, Ana Yaya sama Yaya ƙasa zan karya jari, no sako account kawai" "Ko ka saka na 100 kana da gyara guda 50" Sai da ta lura Fadila ta fara ƙosawa da wayar, sannan ta yi masa sallama. Fadila ta ce "Wai da wa kike waya haka ne?" Yusra ta ce "Yaya Abdul ne, yayi mini magana ta IG jiya, wai yana son cake" Fadila ta yamutsa fuska ta ce "Shi ne kuke ta wannan surutun, ni surutun gayen nan ba ƙaramin haushi yake bani ba, yai ta surutu ba wani class" "Shi Yazid baya surutu kike saurarsa" "Amma ai Yazid gently yake surutu, kuma ba ko yaushe yake yi ba" Yusra ta ce "Allah Fadila, kice he is so classic?" Fadila ta haɗe rai ta ce "Yusra ba wannan maganar muke ba fa, alaƙata da Yazid daban" "Shikenan naji, yi haƙuri zo muje ki tayani muyi cake ɗin tare?" Fadila ta miƙe ta ce "Allah ya kiyaye" ta ɗau jakarta ta fice. Ranar da su Amina za suyi zagayen ƙarshe na completions, ta shirya ta fito falo, amma taga Daddy bai fito ba, gashi lokaci na nema ya ƙure. Cike da tsoro ta tunkari ƙofar ɗakinsa ta tsaya tana knocking. "Come in" shi ne abin da taji ya faɗa. Kamar kar ta shiga, sai kuma ta murɗa ƙofar ta shiga da sallama. Yana zaune a bakin gado, idanunsa sun ɗan yi ja, ta dube shi ta ce "Naga haryanzu baka fito ba, kuma lokaci yana ƙurewa". Ya ce "Bana jin daɗi ne, kije Joseph zai kai ki, sai dai dan Allah Amina ki kula sosai, dan Allah kar ki je kiyi wani abu da bai dace ba, ko ki tsaya kula wannan mutumin". Ba ta ce masa komai ba, ta rufe masa ƙofarsa ta tafi. Duk abin da bawa ya sanya a gaba, cikin ikon Allah idan har yana miƙa lamuransa ga Allah, idan har da rabo sai ya yi nasara. Abu kamar wasa Amina ta ɗaukarwa makarantarsu gwarzuwar shekara, da maki mai tazara a tsakaninta da abokan karawarta, a cikin ƙwarin yaran da sai da aka tace sannan aka ɗebo su. Yayin da makarantar ta su ta zo ta biyu, a debate da suka yi. Makarantarsu sun yi murna nara misaltuwa, aka sanar da cewa jibi za ayi ceremony na karrama waɗanda suka yi nasara, ayi walima washegari kuma kowa ya tafi. Tun a mota Amina taji tana missing ɗin Daddy, da yanzu yana nan ya biye mata suna murna tare a mota. Suna zuwa gida tayi clashing da wani mutum sanye da lapcort, da box a hannunsa ya fita. Tana shiga falon taga Daddy a zaune, gefensa da magunguna, murmushi yayi mata yana faɗin "Congratulations Meenalina, am proud of you" Fuskarta Babu yabo babu fallasa ta ce "Thank you, amma yaa aka yi ka sani? Naga baka je ba" "Na kalla live, ai ana haskawa a wata tasha" yayi maganar yana nuna TV Ta ɗan jinjina kai ta wuce shi, dan haryanzu tana jin haushinsa. Babban abin da ya sanya ta ɗan damu shi ne yadda ko salla baya fita Masallaci. Ko falo bata sake ganin ya fito ba tun da ta dawo, basarwa tayi ta fara haɗa kayanta, saboda sun kusa komawa gida, amma ta kasa basarwa tayi ta tunanin halin da yake ciki. Khalil jikinsa yayi sauƙi sosai, sai rama da yayi, har ya koma ya cigaba da zuwa wurin aikinsa, sai dai ya kasa fidda rai a kan samun Hafsa. Yana son zuwa gida, amma ya san yana zuwa Mummy babu abin da zata yi masa sai wancan zancen da baya so, na batun yi masa aure da wata daban. Haka nan ya daure yake kiran Mummy a waya gaisheta, amma wani lokacin sai ta ƙi ɗaga wayar, wani lokacin kuma ta ɗaga ta amsa masa ciki ciki. Ƙarfe huɗu, Abdul ya isa gidan su Yusra, a lokacin ta gama yi masa aikinsa na cake gaba ɗaya. Ya kirata a waya, ya sanar da ita yana waje yana jiranta. Maimakon ya ga ta fito da kayan Cake ɗin sai ya ganta ita kaɗai. Ta ƙaraso suka gaisa, ya ce "Chef ina kayan?" Yusra ta ce "Baka taɓa zuwa gidanmu ba, sai yau da taka ta kawoka, dan haka ka shigo ka ci Abinci" Abdul ya yi murmushi ya ce "Banda abinki Abinci da la'asar ɗin nan, a ƙoshe nake ai" Ta ɗan ɓata fuska ta ce "Aikuwa na ajiye maka Abinci, idan baka ci ba ba zan baka cake ɗin ba" "Ayi haƙuri next time idan na zo zan ci" "Naƙi wayon, Abincin fa da daɗi dan Allah ka shigo Yaya Abdul" tayi maganar cikin magiya. Yadda ta kwantar da kaine ya ga babu daɗi ya ce mata a a. Tayi masa jagora zuwa cikin gidansu, babu laifi gidansu me kyau ne sosai, suma suna da rufin Asiri sosai. Ta gabatar masa da Abinci da abin sha, da fari niyyarsa ya ɗan sa albarka ya tashi ya tafi, amma yaji Abincin ya ratsa shi sosai yayi daɗi. "Yaya Abdul da ɗazu ka zo da kun haɗu da Fadila, muna tare ɗazu" Jiki a sanyaye Abdul ya ce "Ai ko mun haɗu babu lallai ta kulani, Fadila tafi ƙarfina ba zata aureni ba, na ma haƙura gaba ɗaya" "Mhmm kamar yadda na haƙura da Yaya Khalil, girl tayi iya ƙoƙarinta a kan ya soni amma ya ƙi, ban sani ba ko ina da wani hali da ban cancanci a so ni saboda shi ba" Abdul a ransa ya ce 'Khalil baya son ramammiyar mace ne' A zahiri kuma ya ce "Kar ki ce haka, kina da kirki sosai Yusra, baki da wani aibu, sai dai kin sa zuciya kowacw da irin abin da take muradi, dan Allah ki daina wannan tunanin, ki cigaba da Addu'a, Allah zai kawo miki wanda ya fi shi alkhairi in sha Allah" Tayi murmushi ta ce "Haka ne Yaya Abdul, na gode sosai, naji kace sauri kake, muje mota in kawo maka saƙon" Ya miƙe ya fita, ita kuma ta koma ciki ta ɗauko masa kwalin cake ɗin. A wajen motarsa ta tarar da shi, ta bashi kwalin. Ya karɓa ya buɗe sai ƙamshi Cake ɗin yake, sai dai yafi guda ɗari. Ya kalleta ya ce "Allah ya yi miki albarka, ya baki miji nagari, na gode sosai" "Bakomai, a sha biki lafiya Allah ya kawo na abokan ango" Dariya yayi ya cigaba da yi mata godiya, sannan ya tafi. Tana komawa ɗakinta taga alert ɗin 10k, daga Abdul. Kiransa tayi a waya, domin jin na menene bayan ya riga yayi payment ɗin kuɗin Cake. "Ai na san ba iya na kuɗina kika bani ba, kuma ga girki na kwasa, kiyi haƙuri ita kenan da ni, da na ƙara miki Abinci yayi daɗi sosai" A ɗan shagwaɓe ta ce 'Haba Yaya Abdul, dan na baka abu kuma sai ka bani kuɗi, gaskiya ban ji daɗi ba, ina da kuɗi a account ɗina fa" "Na san kina da su Yusra, kuma ba wai biyanki zan yi ba, naji daɗi ne sosai ƙanwata, sai dai kuma idan rainawa kika yi" "Ba rainawa nayi ba, amma ina laifin ko 2k, kace ita kenan da kai, kuma sai ka bani, Cake ɗin da bai wuce in maka kyauta ba". "Ai hakan ma na gode sosai, na san ban biya kuɗin cake ɗin ba, Allah ya ƙara ƙwarin hannu" "Amin yayana, na gode" ya kashe wayar yana yaba karamcin Yusra. Alhaji Ahmad na zaune a gaban mudubi, ya ga an murɗa ƙofar ɗakinsa, Amina ya gani ta shigo da tray ɗin Abinci. Zuba mata ido yayi har ta ajiye, ta nufi in da yake zaune, ta kalli magungunan da yake gabansa, ta ɗauka ta dudduba wanda zai sha a lokacin. Ta dinga ɓallo masa ɗaya bayan ɗaya, tare da zuba masa ruwa tana ba shi. ya dinga karɓa yana sha har ya gama sha. Ba tare da ta kalleshi ba ta ce "Ya jikin naka?" "Da sauƙi Meenal, kin daina fushin da ni?" "Kona daina fushi da kai, ko ban daina ba, ba zan iya jure ganinka babu lafiya ba, na damu sosai da sosai, naga kamar maganin zazzaɓi ne da hawan jini ko?" Ya ɗan yamutsa fuska ya ce "Zazzɓi ne ya dameni, sai kuma jinina da ya ɗan hau" "I hope bani ce silar hawan jinin ba?" Tayi maganar tana kallonsa. "To Meenali me zance? Ina cikin damuwa sosai, abin da ya faru ya dameni sosai, kuma kema kin ƙi saurarata, ina ga na fiki damuwa da abin da ya faru, ba yadda na iya ƙaddara ta riga fata, amma ina sake baki haƙuri". Amina ta kwaɓe fuska ta ce "Amma ni ya zan yi idan Baba ya sani? Duk irin nasihar da yayi mini, naci amanarsa" "A'a Meenal, ai ba zai gane ba, sai dai in ke zaki faɗa masa, dan Allah Meenali kar ki gayawa kowa, this is our secret kar wani ya sani" Ɗan tura baki tayi ta ce "Ga Abinci ka zo ka ci" "I have no appetite, and bana son ganin fuskarki da fushi" "Mu bar wannan maganar ka daure ka ci Abincin ko babu yawa" Ta zubo masa ta dawo gabansa, ta ɗora masa a kan mudubi. Ya ɗage hannun rigarsa na dama ya nuna mata ya ce "Hannuna da Cannula zafi yake mini, sai dai ki bani a baki" Ta waro ido ta ce "A baki kuma?" "Eh mana, help me please" "Ni gaskiya.." Ya kasteta ta hanyar cewa "Please, idan ba haka ba ba zan iya ci ba". "Ni da na zo competition, na ɓige da kula da mijin wata" ta faɗa tana zumɓura baki. Ya ɗan yi murmushi ya ce "Ko kin kamu da son mijin wata ba" wata uwar harara tayi masa, ta kawar da kai shi kuma ya cigaba da kallonta yana dariya. Ta ciko cokali ta kai bakinsa ta ce "To ka buɗe bakin" "Amina ya zan yi iya cinye wannan lomar ta mini yawa ai" "Wallahi Daddy iyayinka yayi yawa" ta rage ta miƙa masa. Ci yake yana kallonta, cike da tsananin soyayyarta da ya gama mamaye zuciyarsa. Bai ci da yawa ba, ya ce mata ya ƙoshi. Da ƙyar ta takura masa ya ƙara Abincin, sai dai lokacin da take ƙoƙarin kwashe kayan ta tafi ya miƙe yaje ya kulle ƙofa ya saka key, ya ce "Baki gama aikin ba da saura, bani da lafiya bai kamata ki tafi ba, i still need you by my side, ko da wani abu da zaki taimaka mini" Saroro Amina ta kalleshi ta ce "In taimaka maka da me? Ban gane me kake nufi ba" Ya ɗan ƙare mata kallo sanan ya ce "What i mean is that, a nan zamu kwana tare" Waro masa idanuwanta tayi gaba ɗaya, tana son tayi magana, amma ya karɓe kwanukan hannunta, ya ɗagata cak zuwa kan gadonsa. "Daddy wai meye haka ne? Me kake nufi da ni ne" tayi maganar cikin ɗaga murya. Yatsan sa ya ɗora a kan lips ɗinsa ya ce "Shhhhhh" ya kwantar da ita ya rufa mata bargo. Tashi tayi zaune fuskarta duk hawaye, zata yi Magana, amma taga ya jefa mukullin a aljihunsa ya tayar da salla. A yau ake gabatar da walimar karrama ɗalibai da makarantun da suka yi nasara, a cimpetitons ɗin da aka yi, aka karrama su Amina, ta samu kyaututtuka da dama na nasarar sa tayi, aka yi musu hotuna sosai aka ci aka sha. Shi kansa Daddy ya bayar da kyaututtuka ga makarantu da kuma ɗaliban da suka yi nasara. Aka yi aka gama ya ɗauko 'yar shilarsa suka tafi gida, bakinta har kunne sai murna take, tana ta Alla Alla su ƙarasa gida ta saka wayarta a caji, ta kira Baba ta fara labarta masa abubuwan da suka gudana sa irin kyaututtukan da ta samo. Sai dai bata lissafi da kuɗin da wancan mutumin ya basu, dan Daddy ya ce ba zata karɓa ba, dama ba ita aka danƙawa ba malamansu ne. Suna komawa gida, ta hau shirin kayanta, dan ance musu da wuri zasu nufi Kano. Tayi wanka ta cire uniform ɗin ta, ko wanke su ta ce ba za tayi ba sai taje gida, tana ɗaure da towel da vest, tana sake kallon wasu daga cikin kyaututtukan da aka bata, dan wasu suna hannun malamansu, ance sai sunje Kano can ma za a shirya wata walimar a kuma basu kyautukan a gaban sauran ɗalibai da iyayen da basu samu halartar wannan taron na Abuja ba. Babban abin da ya ƙara saka Amina, jinta on top shi ne yadda har 'yan jaridu suke rige rigen tattaunawa da ita, da bayyana irin farin cikin da take ciki. Ta ce "Ohh ni Amina, Allah mai yadda ya so, ni ake nunawa a Tv, Allah ka ƙaro mini nasarori" Buɗe ƙofar ɗakinta yayi, kansa tsaye ya shigo yana kallonta. Take ta sha jinin jikinta ta zuba masa ido, ya zauna a kusa da ita, yana kallon manyan text books ɗin da ke gabanta ya ce "Lallai baki karatu a banza ba, kodayake ni kusan riba biyu na ci, a sanadin karatun competition ɗin nan naki, a nan muka fara shaƙuwa ko Meenali na?" Yayi maganar yana ɗan jan gashinta kaɗan. Matsawa tayi gefe, tana kuma tattara kayanta a cikin Akwati. Ya kalli Akwatinta ya ce "Wannan kayan na menene?" Sai a yanzu ta samu damar yin magana ta ce "Na tafiya mana, gobe in Allah ya kaimu da wuri zamu tafi ai" Ya riƙo towel ɗin jikinta ya ce "Ku tafi ina?" Riƙe towel ɗin ita ma tayi ta ce "Kano mana" "Ke da wa?" ya sake tambayarta "A'a, 'yan makarantarmu mana da muka zo, ai an gama competition ɗin" "You are not going anywhere" ya faɗa sounding very serious, yana mata numfashi a wuya. A ɗan tsorace ta kalleshi ta ce "Saboda me?" "Ba zaki koma ba, Lagos zamu tafi daga nan can wurn aikina, sai su Fadila sun tafi Umara, zaki koma" Tamkar Fadila ta ɗora hannu a ka tayi ihu haka ta ji. "Amma idan kayi mini haka baka mini adalci ba, yaya Baba zai ji idan aka koma ban koma gida ba?" Ya ce "Am seizing your Phone ai, dan karma ki ɓata mini shiri, zan gaya masa baku gama ba. Idan kika tafi gida waye maganin damuwata?" "Amma dai ka san zaman da muke yi ni da kai bai dace ba ko?" "Na sani mana" yayi maganar yana mata murmushi. "Au ka sani ko, na shigesu ni Amina, da na san haka ne da ba zan zo abin nan ba, kawai sai kayi ta yawo dani a gari kamar wata karuwa, wai ka kaini Lagos daga nan Abuja? Baka kyauta mini ba" Tayi maganar tana kuka wiwi. Ya ɗago haɓarta ya ce "Kike kiran kanki karuwa?" "To meye marabata da karuwar?" "Ai ba damuwa tunda ba karuwar kowa bace, karuwar Ahmad ce kawai" ya ƙarasa maganar yana kissing ɗin ta. 🫣 DADDY DAMA HAKA KAKE BA RUWANA FOLLOW ME ON AREWABOOKS@ ayshercool7724 08081012143GABA DA GABANTA                BY AISHA ADAM AYSHERCOOL 52 Wani irin haushi ne ya mamaye Amina, ta rasa me zata yi masa ta huce, gaba ɗaya bai ɗauki abin da take faɗa serious ba. A hankali ya cire bakinsa daga nata, ta sa hannu tana goge bakinta. Murmushi yayi ya ce "Ƙyanƙyamina kuma kike yi?" Banza tayi da shi tana share hawayen fuskarta. "Ki shirya, anjima zamu je yawo tare, muyi celebrating ɗin masarar da kika samu tare, am enough for you dear" A ƙufule ta ce "Ni ba in da zani" "Shikenan kin huta, gara tun wuri ki saki ranki, jibi in Allah ya kaimu Lagos zamu tafi" "To walimar da za muyi a Kano fa ta makarantarmu?" "Babu ke a ciki, ai na gaya miki am enough for you, tare za mu yi namu shagalin" ya ɗora hannunsa a kan cikinta ya ce "Ya naga kamar babu alamar akwai Abinci a ciki?" Ture hannunsa tayi, ta matsa gefe ta sha kunu. Ya miƙe yana kallonta, yana jin kamar ya kwashe da dariya ya ce "In ki gama kumburin kar ki fashe please, ki kwanta ki ɗan yi bacci, anjima zuwa la'asar sai kiyi wanka, ki shirya mu tafi, wankan ma idan ba zaki ba zan zo in miki da kaina" A sangarce ta sake sakin wani kukan, kamar wata 'yar goye. "Wow, you look so beautiful, i like this your dramatic scenes, this is the version of me you don't know before, gara ma tun wuri ki saba" ya fice yana mata dariya. Ita kuwa ta cigaba da kuka, tana kewar Kano da Baba sosai, ta gaji da kukan ta yi bacci a wurin. Sai da la'asar ɗin kuwa ta farka, tayi alwala tayi salla, ta gyara gadonta tayi zamanta a ɗakin, tana tunani daban daban a ranta. "My cartoon kin shirya kuwa?" Taji maganar Daddy unexpected a ɗakin. "Ni ban shirya ba, dan Allah Daddy ka bari in koma gida, ni na gaji da zaman nan bana so" tayi maganar cikin magiya. Yaje ya zauna a kusa da ita ya ce "Meyasa ki ka takura sai kin tafi ne?" "Ni na gaji da zaman nan, kawai gida nake son na tafi" "Kin gaji da zama dani ko?" Ba kunya ba kara ta ce eh. Ya ce "That's good, kin kyauta ni kuma ina son zama da ke, dan haka sai na gama hutawa da ke zaki koma gida" idonta ya cicciko da hawaye tana kallonsa. "Idan kika yi mini kuka, zaki ƙara tsawon zaman da za muyi tare, gara tun wuri ki mayar da shi" Ta saka hannu ta toshe bakinta, dan kar tayi kuka. Ya kwantar da kansa a kan cinyarta, yana cigaba da binta da kallo, ita kuma ta ɗauke kai ta ƙi kallonsa. Ya saka hannu ya juyo da fuskarta, ya ce "Kina son tafiya?" Ta ɗaga masa kai. "Idan kina son tafiya, dole ki dinga bin umarnina, adadin yadda kike mini biyayya shi zai kusanto da komawarki gida" "Ai ina maka biyayya" Ya ce "Kuma kina mini tsiwa ba, da taurin kai ba" "A'a na daina" tayi maganar seriously. 'A baki ba, amma na san zaki cigaba ai" "Allah Daddy na daina" "Kina sane kike yi mini kenan, dan kin raina ni ko?" "A'a ban rainaka ba" Ya lumshe idanunsa, ya kamo hannunta ya ɗora a kan gemunsa, Sannan ya ce "Bana jin daɗin ganin kin je school kin dawo, a zo a saka ki aiki, ko kuma in ga ana gaya miki maganar da zata ɓata miki rai, a duk lokacin da na ganki a cikin damuwa bana jin daɗi" Kamar ba yanzu ya gama yi mata kashedi ba cikin tsiwar ta ce "Eh amma ai kana gani ake mini baka cewa komai, ake mini duk abin da ake minin" Daddy ya ce "Meenal ba zaki canza ba, Allahn da yayi ki bakinki baya shiru, kamar ba yanzu muka gama yarjejeniya da ke ba" "Au na manta Yi haƙuri" "Da anyi magana ki fara ayi haƙuri, matar tawa zan cewa dan me dan ta miki wani abu?, ba 'yar aikinta ce ba ke" ture kansa tayi daga kan cinyarta ta naɗe ƙafafuwanta, tana hararsa. Dariya yake yi sosai, yana son ya ga ya kunna Amina, tana wannan kumbure kumburen, mussman yadda kishinta baya ɓuya sam. "Ki cigaba da rashin ji, muna nan da ke like for 6months, in kin daina tsiwa sai ki koma gida, tashi ki shirya mu tafi kar muyi yamma, kinga bamu ci abinci ba" Tayi masa ƙuri da ido, tana kallonsa cike da ƙuruciya. Ya ce "Shikenan, bari in zo in shiryaki, sai munfi sauri" da sauri ta tashi tsaye ta ce "A'a zan shirya da kaina, ka tafi zan fito" "Ni kike kora?" Ta ɗan rausayar da kai ta ce "A'a ni na isa??" Ya fice yana mata dariya. Wajen ƙarfe biyar saura, sannan Amina ta fito cikin shiri, yana zaune a falo yana jiranta, ta gama nuƙu_nuƙunta da ɓaga lokacinta sannan ta fito. Ya ɗan tsura mata idanu, ya ga tayi masa kyau sosai, ta ƙara girma. "Me kuma nayi naga kana kallona?" "Sai kin yi wani abu zan kalleki, kyau kika yi mini sosai" Ɗan murmushi ta yi ta ce "To turare fa?" "Ba zaki shafa mini turare ba, idan mun fita zan sai miki naki" "To kai kana ƙamshi ni bana yi" "Zaki fara ko?, Dama idan kin saka turaren aini yakamata naji ƙamshin ba wani ba, tun da Karuwar ta wace nikaɗai" yayi maganar yana dariya. Haɗe rai tayi ta kalleshi ta ce "Nice karuwa?" "Kefa kika fara faɗa bani ba" haɗe rai ta yi,  ta sha kunu ta kawar da kanta gefe. "Meye na fushin kuma my cartoon, zo kiji" yayi maganar yana jan hannunta, ta fizge hannunta ta naɗe shi a ƙirjinta. Ɗagata yayi yana juyi da ita a tsakar falon, yana cewa "Smile mana" Ta rirriƙe shi ta ce "Zan faɗi fa" A haka ya fito da ita, sai da suka kusa zuwa harabar gidan, sannan ya sauketa ya riƙe hannunta, zuwa mota. Da kansa yake tuƙin, ya saka hannuna ya riƙe hannunta ɗaya, suna tafe yana mata hira, har ya samu ta ɗan sake daga fushin da take yi. "Yauwa Daddy ya jikin Khalil kuwa?" "Khalil ya warke, ya koma aikinsa ma" Ta ɗan kalleshi ta ce "To ya batun Auren nasa?" Shima kallonta ya ɗan yi ya ce"Yana nan, mamansa zata yi masa aure da, idan suka daw daga umara zan je in gana da mahaifin yarinyar" "Wai dama ana yiwa namiji Auren dole ne? Auren nan fa zai iya shafar rayuwarsa gaba ɗaya, tayaya mutum zai rayuwar aure da wanda baya so, ita kanta wadda za a aura masan za a saka rayuwarta a Matsala". "Ki bari idan muka koma gida, sai ki gaya wa Zeena tun da ita ce mamansa ita ta yanke hukuncin" Gyara zamanta tayi ta ce "Da ita matar taka, da Khalil ɗin duk a ƙarƙashin ikon ka suke, dan haka kai yakamta ka tsaya ka yiwa kowa adalci ya samu abin da yake so. Wai shikenan a rayuwar anan talaka abin gudu ne? Haba Daddy". "Naji, yanzu dai ki bar wannan maganar muyi wani lokacin, ki bari muje mu gama abin da ya fito da mu" Ta ce "Ok, shikenan". Ya cigaba da tuƙinsa. Yusra tana kwance tana waya, tana ta dariya saboda yadda Abdul ke ta koɗa yadda Cake ɗin nan da Abinci yayi daɗi, da yadda abokansa suka yi ta santi suma. "Kai Yaya Abdul, ka daina zigani, kaina zai fashe fa" "Ba ziga bace ƙanwata, ai ke ƙarshe wurin iya girki, mijinki ya huta" "Kaima ƙarshe ne wurin kirki, ko Abincin bai yi daɗi ba ma dai, gashi ka ɓoye mini kana ta santi" "Kar ji da wai, abinci yayi fiye da tunaninki, ina ga zan biya in yi joining classes ɗinki, naga kina tallan su a IG, zan joining ina son in ƙware a iya girki kan in yi aure, in dinga taya matata aiki" Yusra ta ce "Matarka ta huta Yayana ga ka da sauƙin kai, ga barkwanci, ai kai naka class ɗin special za ayi maka" "To shikenan, zaki fixing mini date in zo a koya mini, sai dai ɗalibin naki baya ja sosai, sai kin yi dagaske sai kin haɗa sa haƙuri. Wataƙila ma sai kin haɗa da bulala tukuna" Garin dariya sai da ta tashi zaune ta ce "'yar Ƙarama da ni, a ga na saka ƙato a gaba da bulala, abin ai ba kanta" Yayi murmushi ya ce "To ai malama da ɗalibi ne, duk hukuncin da ta yanke daidai ne" "Yayana kenan, Allah ya kawo bikinka, ni zan sponsoring duk Abincin da za aci" Yana zaune a kan gadonsa, ya ɗan yi shiru yana tunani. "Hello Yaya Abdul, kana jina?" Yayi ajiyar zuciya ya ce "Ina jinki Ƙanwata" "Shikenan sai anjima, kar in takura maka" Abdul ya ce "No, baki takura mini ba, ina jin daɗin hirar taki ai, me zaki fara koya mini a girkin?" "Dafa shayi" ta faɗa tana dariya. Shima dariyar yayi ya ce "Dafa shayi ƙanwata, ai ko da muna school na iya dafa shayi, kar a kaini playgroup a makarantar taki, a ƙalla zan kai primary 2 a iya girki ai" Sun daɗe suna waya, barkwancin Abdul ba ƙaramin burgeta yake ba, yayin da shi kuma girmamawarta da karamcinta yake burgeshi. Alhaji Ahmad kuwa da Amina, wurin cin abinci suka fara zuwa, suka ci, sannan ya kaita wurin shan ice cream, ya zaga da ita wurin liluka, ta dinga hawa tana nishaɗi, taji daɗin fitar sosai, gaba ɗaya ta manta da damuwowin da take ciki. Shi kuma ya dinga kallonta yana nishadi shima, yaji daɗin yadda ta sake, harta ke ta fara'a tana kalle kalle da wasanninta, sai da ya fuskanci ta gaji dan kanta, sannan ya ɗauke ta zuwa wurin sayar da kaya. A cikin botques ɗin ya dinga zagayawa da ita, ya ce ta ɗauki duk abin da take so, amma yaga kamar tana tsoro. Ya dubeta ya ce "Look, ki zage ki zaɓi duk abin da kike so, waɗan da zaki dinga kwaliya da su. Sanan akwai wurin atamfofi ma sai ki zaɓa in bayar a ɗinka miki, ki dinga mini Kwalliya, ta safe daban ta yamma daban ta other room daban". "Kai ka san shi, shi other room ɗin" "Eh dama ni na san shi mana, kema kin san shi ai" gaba tayi ta bar shi a baya, ya biyota shima ya sai abubuwan da yake buƙata sanan suka wuce gida. Wannan yawon da suka yi, duk ta gaji, ana yin sallar isha'i, ta nemi wuri ta kwanta. Gaba ɗaya Hajara ba ta gane Amina ba ƙaramin rana take da shi a gidan nan ba, sai da tayi tafiyar nan, aiki kamar zai kasheta san bata da hutu, tayi aikin gida tayi na Hajiya Zainab, sannan tayi na Fadila kuma abin takaicin ma idan tayi ba sannu ko san barka, sai wulaƙanci da cin zarafi da uwar kyara kamar wadda suka sayo baiwa. Baba Hassan kuwa yana ta dako da lissafin ranar dawowar Amina, ya samu kiran wayar Alhaji Ahmad, jiki na rawa Baba Hassan ya ɗaga wayar yayi sallama tare da risunawa yana gayar da Alhaji Ahmad, Kamar yana gabansa. "Malam Hassan, dama nace game da batun Amina ne" Baba ya ƙara nustuwa ya ce "To meyafaru da ita?" "Eh, ba wani abu bane ba, nayi magana da malamansu ne, basu gama abin da suke yi ba, dan haka akwai yiwuwar su ƙara lokaci kan su dawo" Jikin Baba ya ɗan yi sanyi, amma ya maze ya ce "To shikenan, babu laifi, amma bana samunta a waya, sun gaya maka tana dai lafiya ko?" Daddy ya ce "Tana lafiya lau, sun haɗani mun yi magana har wurin taron nasu naje, wayarce ta samu matsala". Baba ya ce "To babu laifi, Allah ya dawo da su lafiya". Daddy ya amsa da Amin. Washegari, Kamar yadda da Daddy ya faɗa, ba tayi zaton da gaske bane ba, da daddy yake gaya mata ta shirya da wuri, tara da rabi jirginsu na Lagos zai tashi, ta ɗauka da wasa yake mata, ba ta yi zaton tafiya Lagos ɗin nan da gaske yake ba, dan haka ta shantake ta na baccinta. A lokacin da ya gama shirinsa ƙarfe tara yaje ɗakinta, tana dunƙule a bargo, tana bacci. "Meenali, mu da zamu tafi 10 amma kina nan kina bacci?" Ya saka hannu ya janye bargon, ta buɗe idonta a hankali. Haushi ya kama shi, ya ɗagata zaune ya dubeta ya ce "Ban gaya miki zamuyi tafiya ba?" Ta ɗan mruje idanunta ta ce "Nifa na zata da wasa kake mini" "Nine nake miki wasan? Oya tashi ki saka kaya" "Daddy ban fa yi wanka ba". "Idan mun je can kya yi" haka ya azalzaleta, ta shirya ba ta koyi wanka ba, ya tattara mata sauran kayanta a Akwatinta suka fito, Joseph ya ɗauke su zuwa airport. Duk da Amina bata taɓa hawa jirgi ba, amma ta kasa farinciki a lokacin da ya zamana wannan ne karonta na farko da ta hau jirgi, saboda tarin damuwar da take ciki. Shi kansa Daddy ya lura da yadda gaba ɗaya jikinta yake a sanyaye, amma bai matsa sai ya tanka mata ba, saboda karata dame shi da rigima, dan da alama ƙiris take jira. 'Meenalina, nan gaba zaki gane gata nake miki, a duk wannan abun da nake yi' yayi maganar a cikin ransa. Kasa jurewa ya yai, ya ce "Meenalina ya ne?" Ta girgiza masa kai alamar bakomai. Ya matso da ita jikinsa, ya riƙo hannunsa a nata, yana matsa yatsun hannunta a hankali, tayi lamo a kan kafaɗarsa ba tare da wani ya tankawa wani ba. Su kuwa malamansu da sauran ɗaliban da suka zo tare, tuni suka shirya a ranar suka nufo Kano, Amina tana ta tunani a ranta, da tuni har da ita amma an mata fin ƙarfi babu yadda ta iya. Bata taɓa zaton Daddy babban mutum ne haka ba, sai da suka sauka a Lagos, yadda ake girmamashi, ana risuna masa abin har mamaki ya bata, ashe normal yake rayuwarsa a Kano, kamar ba shi da wata damuwa. Ko a garin Abuja ba taga ana masa haka ba sai da yazo Lagos. Aka zo aka ɗauke su daga airport zuwa residents ɗinsa na Lagos, wani irin gida ne na alfarma, kai baka ce za a mutu ba. A wani irin katafaren bedroom suka yi birki, in da suka tarar an ajiye musu kayansu da suka zo da su. Daddy ya nemi wuri ya zauna a gefen gado, yana cire neck tie ɗinsa. Ƙarshen gadon ta samu ta zauna ita ma, sannan ta ce "Ni ina nawa ɗakin, a ina zan zauna?" "A nan babu wannan, we are sharing the same bedroom, the same bed and pillow together" Cikin rashin fahimta ta ce "Saboda me? Naga kamar gidan da ɗakuna ai, meyasa zamu zauna a bedroom ɗaya" "Saboda gidana ne, kuma dokata ce haka nake son ayi" Ta ɗan ɓata fuska ta ce "Ai dama bance gidana ne ba, amma ni gaskiya ba zan zauna ɗaki ɗaya da kai ba" Ya miƙe tsaye ya ce "Kinga kenan a maimakon kwanakin da zaki yi tare da ni, ki cigaba da gardama da taurin kai, su zama watanni". Jan bakinta tayi tai shiru. "Idan kin huta ga toilet nan, ki shiga kiyi wankan, a cikin wardrobe ɗin nan akwai towel" A ɗan shagwaɓe ta ce "Ai na fa sa yin wankan" "A haka zaki zauna?" "Eh, idan ka fita nayi" Ya ce "As you wish" Ya zagaya bayanta, ya kwanta a kan makeken gadon, yana lumshe ido. A ranta tayi ta tunanin ko iya adadin yaushe zata kwashe a gidan nan oho. Fadila suna ta shirin tafiya umara, amma gaba ɗaya hankalinta na kan yadda zata samo Yazid. Tana falo tana kallo, Hajara na kaiwa tana komowa tana gyarawa, Hajiya Zainab na gefenta da system a kan cinyarta. "Fadila kinga yaron nan ko?" Ko ba ayi wa Fadila dogon bayani ba, ta san maganar ba zata wuce a kan Khalil ba. "Mummy what again?" "Muna ta shirye shirye zamu yi tafiyar nan, amma dan wulaƙanci ko ya zo garin nan, gaba ɗaya yama ɗauke ƙafarsa daga zuwa" "Amma ai kamar bai san zamu yi tafiya ba fa" "Au baki gaya masa ba?" Fadila ta ce "Ina nake ganinsa online balle na gaya masa, ba fa kulani yake yi ba" Ta ɗan jinjina kai ta ce "Anya Fadila yarinyar nan ba Asiri suka yiwa Khalil ba? Duk nacin Khalil da gida, amma shi ne ya shafe wannan lokaci bai ko waiwayo mu ba, ya nesanta kansa da mu?" "I don't know" Hajiya Zainab ta ɗauki wayarta da ke gefenta, ta nemo lambar Khalil. Sai da ta kusa katsewa sannan ya ɗaga tare da yin sallama. "Anya Khalil kana son ka gama da duniya lafiya kuwa?" Gaban Khalil ya faɗi ya ce "Subhanallah, Mummy me ya kawo wannan maganar kuma?" "Ban sani ba, shikenan ka daina zuwa gida kenan? Ga tafiya za muyi umara, babu ma alamar zaka zo gidan nan balle muyi sallama ko Khalil, duk saboda masu awara sun yi tsafi sun baka ka ci" Khalil ya fesar da wata iska, ya ce "Mummy, dan Allah kiyi haƙuri, ban san zaku yi tafiya ba wallahi, rashin lafiya nayi na sha wahala, sai da Daddy ya zo ya kaini Asibiti" Ɗan shiru tayi sannan ta ce "Ban gane ya zo ya kai ka Asibiti ba, shi da yake Lagos kana Abuja, ya aka yi ya je ya kai ka Asibiti?" "Mun yi waya da shi ne, ya ce mini ya shigo Abuja, shi ne yaje in da nake, sai da aka yi tayi mini ƙarin ruwa da allurai" "Eh lallai, har ka gayawa mahaifinka baka da lafiya, amma ni ban sani ba, duk dan saboda masu awara ko?" Fadila ta fara tausayin ɗan uwanta, Mummy akwai nanata zance, abu baya wucewa a wurinta, ta saka Khalil a gaba da zancen nan. Nan ma ta ƙare masa ta tas ta kashe wayarta. Tun Amina na zaman ɗari ɗari da Alhaji Ahmad, a hankali har ta saki jiki da shi, ko girki tayi ba zata ci ba sai ya dawo, gashi tana ta kula da Abincinsa, cikin ikon Allah sugansa ya sauka zuwa normal range, ga exercise da yake yi a gida, gaba ɗaya Amina ta mayar da shi kamar dai-dai da shekarunta, har tseren keke suke yi tare a gidan. Babu yadda za ayi ka zo gidan kace ba matarsa bace ba. Shima yana ƙoƙarin faranta mata, yana kaita wurare daban daban na buɗe ido da sanya nishaɗi, idan yana gida tare suke gabatar da wasu ayyukan. Tana kwance a kan gado tana cin cheese, duk ta ɓata gadon da cheese, ya bata wayarsa tana game, shi kuma yana gefe ya saka system har biyu a gaba, ya dannan wannan ya koma ya danna waccan, ga ruwa da lemo mai sanyi a kusa da shi yana ta aikinsa. "Daddy" "Na'am" ya amsa mata. "Wai dan Allah aikin me kake yi ne? Ranar kace mini sayar da kuɗi ka ke yi, Yanzu kullum kana ce mini kaje wurin aiki, amma ban san aikin da kake yi ba" Ya ɗan waiwayo ya kalleta yana murmushi ya ce "Ai nace miki sayar da kuɗi nake" "Ai ba a sayar da kuɗi" "A na yi mana" ya bata amsa. Ɗan matsawa tayi, tana leƙa computer da ke gabansa, ɗaya calculation yake yi da ita, ɗaya kuma kamar zane yake yi, ba ta gama fahimta ba. "To wai wannan ɗin meye kake yi?" "Meenal, sai ɓatar da ni da kike yi fa, ni da na sani ma ɗakin karatuna na tafi" Ta ce "Au nan ma kana da ɗakin karatu, aikuwa da sai na bika" "Ki zauna ki cigaba da game ɗinki" Ta noƙe kafaɗa ta ce "Ni na gaji da game ɗin, i just wanna disturb you" "Ina aikin zaki disturbing ɗina?" "Eh, ni ka ajiye aikin ka kulani" tayi maganar a shagwaɓe tana jan hancinsa. Murmushi ya cigaba da yi, yana aikinsa. Ta koma ɗaukar cheese tana saka masa a baki, duk cikin son ta addaba masa ta hana shi aikin da yake yi. Wayarsa ce take ringing a jikinta, ta duba ta ga hayatee da emojis na luv, ta san Hajiya Zainab ce, amma ta basar ta ajiye wayar. "Miƙo mini wayar mana" Ta saka idonta a nasa ta ce "Na hana" "Meyasa?" "Tun ɗazu nake maka Magana ka ƙi kulani, amma tana bugo waya shi ne zaka ɗauka, ban bayarwa" tayi maganar tana haɗe rai. "Bani wayata, bana son ɓacin ran matata" Kicin kicin tayi da rai, ta hana shi wayar. "Allah ya shiryi cartoon da rigima da tsagwaron kishi, idan muka koma gida ya zaki yi ne?" Tayi shiru tana kallonsa ta gefen ido. Wayar tayi ringing ta gaji ta katse. Hamma ta fara yi ta kalleshi ta ce "Tun da ba zaka gaya mini aikin da kake ba, ka zo ka rarrasheni bacci nake ji" Girgiza kai kawai yayi, ya kashe system ɗin, aikin da yake yi ɗin ne a yanzu bata so, shine take ta ƙaƙalo abubuwa. Ya nemi wuri ya kwanta, ita kuma ta kwanta a jikinsa, ya rufe su da bargo, daga nan ya fara gaya mata aikin da yake yi. "Akwai wani abokin mahaifina, babban ɗan siyasa ne, a zamanin wancan shugaban ƙasan na hannun daman shugaban ƙasar ne, dan kusan shuhaban ƙasar yaronsa ne. Bayan an yi Election yaron nasa ya ci zaɓe, ni kuma a lokacin ina da master's a kan Civil engeenering, nayi aiki da kamfanoni daban daban na Chinese da 'yan Turkiyya. Abokin mahaifina ya sanya aka yi mini ministern ayyuka. Na fuskanci ƙalubale daban daban, kasancewar ana ganin akwai waɗanda suka fini cancanta, kuma ni ba ɗan siyasa bane ba, ga ƙananan shekaru a wannan lokacin. Ina iya ƙoƙarin tsare gaskiya, a kan aikina nan ma ya nemi ya janyo mini matsala, saboda bana karɓa ko bayar da cin hanci. Na samu abokin mahaifina da nake masa kallon uba, nace masa ina son yin resigning ni wannan mulkin ya isheni, amma ya ce mini bai lamunce ba. Babban abin da ya ƙara tsolewa masu adawa dani ido, shi ne yadda na samu kusanci da shugaban ƙasa sosai, yana ji dani dan a lokacin ya kusa haifata, amma sai ya tsallake manyan carbinet ɗinsa yayi shawara yayi dani. Abu kamar wasa, bayan suka da nake fuskanta, har aka fara nema a taɓa lafiyata ta hanyar yi mini barazana daban daban, a haka da ƙyar muka shekara takwas. Duk da wannan ƙalubale, mutane suna sona sosai da sosai, har wasu sun yi zaton ko zan tsaya takara, amma nace ba zan iya ba. Muna barin mulki, nace ba abin da zai sake mayar da ni harkar siyasa ba zan iya ba. Na koma na samar da kamfanina na A.M dutse construction limited. Nake kwangila. Cikin ikon Allah kamar wasa kamfanina ya karɓu, nake samun ayyuka ta ko ina, har gwamnati ina yiwa ayyuka. Khalil ma irin karatuna yayi, na so ya karɓi harkokina ni in samu in huta, amma na lura irin halina ne da shi, baya son dogara da kowa, ya ce shi nasa aikin yake so, shi ne na samar masa aiki a Abuja, amma shima yana nan yana ƙoƙarin buɗe nasa kamfanin, ina son in taimaka sa ya buɗe, ya haɗa kai shi da wannan abokin nasa, su tafiyar da kamfanin, ina son Yaron yana da nustuwa sosai" Amina tayi ajiyar zuciya ta ce "Allah ya sa wannan matar taka ta bari, with due respect sir, kayi haƙuri da abin da zai fito daga bakina a kan matarka, wallahi matarka ta fiye son kanta da yawa, idan baka yi da gaske ba ka amfani dukiyarka a duniya ba zaka amfaneta a lahira ba. Gaba ɗaya ka sakar mata ragamar gidanka ba irinta ake sakarwa ragamar gida ba. Ita duk wanda zai raɓoka ya ci arziki bata so, duk wannan tarin dukiyar ya zata yi da ita idan ba ta bari anci ba?" Shiru Daddy ya yi, ya janye Amina daga jikinsa ya juya mata baya. FOLLOW ME ON WATPAD @ ayshercool7724 08081012143GABA DA GABANTA               NA AISHA ADAM AYSHERCOOL Arewabooks@ ayshercool7724 Watpad Ayshercool7724 53 Ba tayi fushi ba, ta koma bayansa ta kwantar da kanta a kafaɗarsa, ta saƙalo hannunta a ƙirjinsa, cikin sanyin murya ta cigaba da yi masa magana. "Daddy, na san wataƙila maganganuna su yi maka tsauri, amma ban gaya maka domin cutar da zuciyarka ba, so nake ka duba lamarin nan. Tun da na fara aiki a gidanka sau ɗaya naga kaje garinku, Shima ɗaurin Aure kaje, sannan kuma sau ɗaya kacal na taɓa ganin 'yan uwanka sun zo gidanka, anya kuwa Daddy rayuwa zata tafi a haka?. Ko da iyayenka basa raye, 'yan uwansu da abokan mu'amalarsu yakamata ace suna zuwa inda kake, amma kullum ba mai zuwa wurinku ba kuma kwa zuwa wurin kowa, baƙi sai wanda aka zaɓa ake karramawa hakan ba daidai bane ba, dukiyar da ake taƙama da ita lokaci ɗaya Allah na iya durƙusar da ita ba fata nake maka ba, amma dan Allah kayi haƙuri idan maganganuna sun ɓata maka rai" Daddy bai ko yi motsi ba, balle ya tanka maganganun da tayi masa. Yayi shiru yana sauraren yadda take wasa da gemunsa, tana masa magana kamar wata babba har bacci ya kwasheta. Jin alamar tayi bacci ne, ya sanya ya tashi zaune ya zame ta daga jikinsa, ya kwantar da ita, ya  ya dafe kansa yayi shiru, yana ta lissafa maganganun Amina. Ya waiwaya ya kalli yadda take baccinta hankali kwance, ya dafe kansa yana jin yadda yake masa wani irin zafi. Yayi shiru ya dinga tunanin wasu abubuwa da yakamata ace tun tuni ya farga ya tuna, ba sai yanzu ba. Wasa wasa bacci ya gagareshi, yayi ta zazzagawa a ɗakin, ƙarshe ya haƙura ya nemi wuri ya kwanta. Ya kwanta babu daɗewa, Amina ta tashi ta kalli in da yake kwance, ya lumshe idanunsa, tamkar me baccin gaske. Ta sauka daga kan gado, ta tafi banɗaki, ta yo alwala ta zo ta tayar da salla. Har ta kammala sallolinta, da tilawar Alqur'ani, yana kallonta, tayi adduointa ta shafa, sannan ta tashi ta koma kan gadon, ta ɗora hannunta a goshinsa ta dinga karanto masa adduoin kwanciya bacci, sai da ta gama sannan ta ja bargo ta rufe shi, ta nemi wuri ta kwanta abinta. Duk abin da take yi, har ta gama duk idanunsa biyu yana kallonta, yaji ta ƙara kima sosai a idonsa. "Mummy nifa gaskiya na fara gajiya, haryanzu wai yarinyar nan ba zasu dawo ba, nafi jin daɗin aikinta a kan na wannan sokuwar" Fadila tayi maganar cikin mita. Mummy ta ce "Wallahi bake kaɗai ba, wannan Hajarar shegen lalacin tsiya, wai ni ba kwana goma aka ce za su yi ba, yau kusan kwanaki ashirin shiru?" Fadila ta yamutsa fuska ta ce "Ni da tana nan, da ta haɗa mini kayan nan, Abinci babu wani daɗin kirki, gyaran ɗakina idan wannan ce tayi na zo saina ga datti, ga gandar tsiya ni sai da ta tafi ma, sannan na lura ashe kusan duk ita take aikin gidan nan" "Ni kaina na gaji da wannan abun, dole a rage wani abu a kuɗin aikin babanta, tun da ba tayi aiki ba a wannan kwanakin" Fadila ta ja ɗan ƙaramin tsaki, dan gaba ɗaya wannan tafiyar ta Amina ba ƙaramin haushi ta bata ba. Da safe kamar yadda Amina ta saba, ta shirya musu abin karin kumallo, sai da ta kammala ta koma ɗaki, ta tarar Daddy har yayi wanka ya saka kaya. "Good morning" ta gaishe shi. Murmushi yayi mata mai kama da na yaƙe ya ce "Morning dear, kin tashi lafiya?" "Lafiya lau Alhamdilillah, your breakfast is ready" Ya jinjina mata kai ya ce "Gani nan zuwa" ta juya ta bar shi a ɗakin ya ƙarasa shiryawa. Gaba ɗaya cin abincin kawai yake yi, amma kamar akwai wani abu da yake damunsa, gaba ɗaya yau baya walwala balle yayi ta tsokanarta kamar yadda ya saba yi, ya koma mata Alhaji Ahmad ɗin sa sak. Duk da kwarjinin da ya yi mata, hakan bai hana ta dakewa ba, ta ɗan taɓa hannunsa. Ya ɗago kai ya kalleta. Ta ɗan marairace ta ce "Daddy, gaba ɗaya ka sauya meke faruwa ne?" Ya girgiza mata kai alamar bakomai. "Dan Allah Daddy idan duk a kan maganar jiya ne, kayi haƙuri ba zan sake yi maka ba" Ya girgiza kai ya ce "No ba a kanta bane" "Ba a kanta bane amma naga tun da nayi maka maganar mood ɗinka ya canza?" Ajiye cokalin hannunsa yayi ya tashi, ya ce "Bakomai fa, sai na dawo" bai tsaya jiran abin da zata ce ba, kawai ya tashi fice daga falon. Shiru tayi tana ta ƙoƙarin tayi tunani a kan, ko tayi wani abu da zai ɓata masa rai, amma ta kasa tuna komai. Hajiya Zainab ce tare da manyan aminanta a falon da ke sashenta, sun zo domin su yi mata sallama, saboda tafiya da za tayi umara, sai shewa suke sun hirarrakin su. Hajiya Turai ce ta ce "Ni kuwa Zainab ina wannan 'yar aikin naki me shegiya rawar kan tsiya?" "Tana Abuja, sun je competition na makarantar da take zuwa" Waro ido Hajiya Salma tayi ta ce "Ban gane ba wace makarantar ce haka?" "Makaranta da take zuwa mana, ai tana mana aiki ne babansu Khalil yana biya mata kuɗin makaranta" Turai ta ce "Amma wannan cimpetiton ɗin ba na makarantun kuɗi ne kawai ba" "Eh private ce makarantar da take yi" Turai ta ce "A gaishe ki Zainab lalai kin yi lausi, ni mai zai sa ma na bari a kawo mini 'yar aiki da ta je makaranta, balle ta zauna mini a gida ana biya mata makarantar kuɗi, kin san 'yan ƙauyen nan idan suka kile basu iya iskanci ba" "Ke ni rabu da ni, ni wannan yar baya gabana, a shekarar nan zata koma ƙauyensu, da zarar ta gama WAec ni yanzu makomar yarana ce ta dameni. Ni yanzu babban fatana shi ne muje mu dawo daga tafiyar nan, a fara maganar Auren Khalil, Hajiya Salma ki yiwa Baban Bashir magana ma, idan Bashir ɗin ya dawo kan mu dawo daga umara shikenan, sa haɗu su gana, idan ma bai dawo ba, babu komai ya nemawa Bashir ɗin Auren Fadila zan ba shi, bani da case da ita" Hajiya Salma ta ce "Ahh wannan ai babban albishir ne, aikuwa zan gayawa baban nasa, ni ina ga wataƙila ma ba sai ya zo ba, ayi abin da za ayi a tura masa matarsa kawai" Hajiya Zainab ta ce "A'a, ai idan an yi auren bar mini ita zai a Nigeria sai ta kammala Makarantar ta tukuna, zan aurar da ita yanzu ne, dan kar azo a samu wata matsala, ta yi mini irin ta Khalil" Turai ta ce "Gaskiya ne, wanan ma dubara ce, Allah ya haɗa kansu baki ɗaya mu sha biki, bikin 'ya'yan gata" Hajiya Zainab tayi wata dariya ta ce "Bari kawai, ai za aga biki ba muna biki ba, za a warwasa" suka cigaba da dariya suna hira. Bayan dawowar Daddy ma bata sauya zani ba, still baya wata walwala, duk yanayinsa babu daɗi, ko hirar ma da yake yiwa Amina bai saurareta ba. Aikuwa ta saka shi a gaba tana masa kuka. A ɗan rikice ya ce "Meenali, menene?" "To ba kaine ba, ni ban san me nayi maka ba, ka ƙi kulani, nace kayi haƙuri amma duk ka ƙi saurarata ni ya zan yi?" "Haba Meenal, ba haka bane ba, ai baki mini laifin komai ba, tsakanina da ke sai san barka, wani abu ne yake ɗan damuna kawai, amma ki kwantar da hankalinki" "Ni hankalina ba zai kwanta ba, idan ina ganinka a haka" Ya sa hannu yana share mata hawayen fuskarta ya ce "Ki daina kukan nan bana so, a cikin satin nan su Fadila za suyi tafiyar nan, da zarar sun tafi muma zamu koma, ko dan saboda Jamb ɗinki" Cikin murna ta ce "Da gaske? Kai amma naji daɗi sosai, Allah ya kaimu, ina son naje na ga Baba dama, amma idan mun koma zaka bani wayata?" Ya jinjin mata kai ya ce "Eh, zan baki abarki" "Godiya nake yallaɓai, dan Allah kome yake damunka ka barwa Allah, ka daina damuwa kaji?" "Na ji Meenalina, na dai na in sha Allah" Amina ta yi murmushi ta ce "Yauwa ko kaifa, idan kana cikin fara'a na fi jin daɗi" Shima murmushin yayi mata, yana cigaba da kallon kyakkyawar fuskarta. Wayarsa ce ta fara ringing, ya ɗauko ya ɗaga wayar ya saka a kunnensa yayi sallama. Amsa masa tayi sanan ta ɗora da cewa "Baban Khalil, zaka samu damar dawowa kuwa muyi sallama?" Ya kalli Amina da ke kwance a jikinsa, sannan ya ce "Ba zan samu zuwa ba gaskiya, ayyuka sun yi mini yawa sosai" Hajiya Zainab ta ce "To shikenan, wai ni kayi waya da makarantarsu yarinyar nan kuwa, an ce kwanaki goma amma haryanzu shiru, ni gashi zan yi tafiya, bana son in tafi in bar wannan mara kan gadon a gidana ita kaɗai" Ya shafi gashin Amina da hannunsa ɗaya ya ce "Mun yi waya da malaman makarantar ta su, sun ce a satin nan zasu dawo, wasu dalilai ne ya sanya basu dawo da wuri ba" "To amma gaskiya zaka rage kuɗi a cikin kuɗin aikin babanta, wannan watan kenan ma babu uban aiki tayi, gaba ɗaya gidan nan ya ƙi fasali saboda bata nan. Zan bar sallahun ayyukana a wurin waccan Hajarar idan ta dawo ta sanar mata". Daddy ya ce "Shikenan" Ta ce "Yauwa, kuma ni gaskiyar magana, kuɗin makarantar da kake biya mata ya fi ƙarfin aikin da take yi a cikin gidan nan, dan haka ka sauya mata wata makarantar mai arha, ga ta gwamnati nan, ka biya mata abin daya samu sauran a dinga bata abinta a hannunta, idan tayi cikaken aiki ta samu kuɗinta, idan ba tayi ba kuma ta karɓi na iya kuɗinta, dan wannan makarantar ba ta dace da irinta ba, idan kuma wannan makarantar take so ubanta ya biya mata" Amina ta kalleshi ido cikin ido, tana jin zafin maganganun da Hajiya Zainab ke yi, idanuwanta suka ciko da hawaye. Girgiza mata kai ya shiga yi, ya ƙara rungumeta a jikinsa, yana shafa bayanta da sigar rarrashi. Ya ce "Shikenan za a duba, idan na dawo gida, kuma kuka dawo sai muyi magana". "Yauwa, saura kuma abu ɗaya, magana mai daɗi" "Ok ina jinki" "Fadila ta samu miji fa" Daddy ya ce "A ina?" "Ɗan gidan Hajiya Salma Bashir, shi ne yake sonta, idan Allah ya kaimu muka dawo, da maganar aurenta da na Khalil duk za a haɗa" "Ma sha Allah, Allah Ya sanya albarka, zan yi bincike a kan lamarin" "Wane irin bincike kuma, Bashir ɗin ai ɗan Hajiya Salma ne, ba shi da wata matsala, mahaifinsa zai zo da kansa kuyi magana" "Shikenan, yadda kike so haka za ayi ranki ya daɗe" "Hmm, na so in ganka muyi sallama, anyway stay safe, sai anjima" Ya ce "Ok Allah ya bamu alkhairi" Yana ajiye wayar Amina ta saki kukan da ya maƙale mata, ta tashi daga jikinsa. "Am sorry dan Allah Amina ki rage yawan kukan nan, ke ba kya tsoron kanki ma ya dinga ciwo" A hasale ta ce "To yayi ciwon mana, ina ruwanka ne? Kana jin ai abin da matarka ke cewa, ka mayar da ni makarantar gwamnati, tun da ina 'yar talaka babu ni babu jin daɗi sai wahala, ga kwantai aiki kuma ta bar mini in koma in yi mata. Duk bautar da mahaifina yayi a gidanka tsawon shekaru ba shi da kima a idon matar nan" Gaba ɗaya Daddy ya rasa abin da yake masa daɗi. "Meenal, yanzu kinga na cireki daga makarantar? Ko kuwa kinga na majar da ke makatantar gwamnatin?" "Amma ai a gabana ka amsa mata, kuma ita a gurinka ai bata laifi, komai ta ce tana so sai ka yi mata, shikenan a gidanka da wurin iyalanka talaka ba shi da amfani sai na ya yi muku bauta? Gaskiya na gaji" ta fashe da kuka tana sheshsheƙa. Ya lura da ta ƙulu sosai da sosai, dan haka ya miƙe tsaye ya ɗauketa, ya ɗorata a kan kujera 3seater, ya zauna a kusa da ita, ya riƙe hannunta, yana matsawa a hankali. "Meenal, kin san ba zan taɓa yin abin da zan cutar da ke ba, so kike na biye mata asirnmu ya tonu ne? Ta tayar mini da hankali ta tayar miki da naki?" "Ni ina ruwana idan asirin ya tonu, iykaci na san ƙauyenmu zan koma, laifin da bai kai wannan ba ta mini gori ta ce zan koma ƙauyenmu ina ga wannan?" Ya haɗe rai ya ce "Ya haka ne? Ina rarrashinki kina sake botsarewa, Zainab fa matata ce, kuma uwar 'ya'yana so kike na dinga ɓata mata rai saboda ke, meyasa ba zaki bari mubi komai a sannu ba?" "Eh ko ba matarka ba, ita matarka ce mana, ni kuma karuwarka ko, mara daraja da 'yanci, na gode ba laifin kowa bane laifina ne da na biye maka" Daddy ya dafe Kai ya ce "Innalillahi wa innalillahi raji'un, meyasa zaki canza mini fassara ne?" Tayi masa shiru ta cigaba da kuka, kamar ance mata Inno ta mutu. Takaici ne ya ishe shi, ya tashi ya bar mata wurin gaba ɗaya. A daren ranar kwana suka yi, babu wanda ya tanka wani, bai ma shiga ɗakin ba, sai da ya tabattar da tayi bacci, sannan ya shiga ya kwanta. Da safe kuwa har ya fita ba ta tashi ba, balle tayi masa abin breakfast, dan haushinsa take ji, sai da rana ne kan ya dawo ta yi masa girki. Kwanaki uku babu wanda ya nemi ɗan uwansa, duk da kowannensu abin yana damunsa, amma Daddy yan ganin shi ta yiwa laifi yakamata ta bashi haƙuri, ita ma kuma tana ganin shi ne yayi mata laifi da yake biyewa matarsa da ke neman taci zarafinta. Da daddare ya sameta a ɗaki, har ta kwanta, sai da ya hau gadon sannan ya ce mata "Ki shirya, gobe in Allah ya kaimu da yamma, zaki koma Kano, jirgin ƙarfe biyar" Zumbur ta tashi zaune tana faɗin "Alhamdilillah" ta sauka daga kan gadon da sauri, ta kunna fitilar ɗakin, ta sauke sabuwar Akwatin da ya sai mata, wadda ta fi ta ta, ta da girma. Ta buɗe wardrobe ta shiga haɗa kayanta. Ta shiga toilet ta kwaso underwars ɗin ta, ta zo duk ta haɗa komai a daren, yana kallonta bai ce mata komai ba, tayi ta gama sannan ta kashe fitilar ta dawo ta kwanta. Girgiza kai kawai ya yi, bece komai ba. Washegari kamar tayi janyo la'asar, dan tun azahar ta kammala shirinta, ta fito da Akwatin falo, ta zauna tana kallon agogo tana jiran la'asar tayi. Daddy kuwa kallonta kawai yake, yana sake jinjina tsagwaron ƙuruciya irin na Meenalinsa. Bayan sallar la'asar, direba ya kira Daddy a waya ya ce ya shirya zai kai Amina airport. Daddy ya yi masa umarni da ya zo ya ɗauki Akwatin Amina ya kai mota. Amina kuwa ji take kamar ta taka rawa. Daddy ya kalleta ya ce "Shikenan hankalinki zai kwanta ko?" Ta ce "Eh" "Shikenan yayi kyau, Allah ya tsare ki gayar da mutan gidan" "Yauwa za suji" tayi gaba cikin sauri ta shige motar, dan kar ma ya ce a fasa tafiyar. Yana nan tsaye har motar ta tashi, suka bar gidan. Daddy ya ɗan lumshe idanunsa ya ce "I will miss you dear, ina fatan kema kiyi kewata Meenalina" Amina jin ta take tamkar ta shekara bata garin Kano, abin mamaki da ta sauka, already Zakiru na filin jirgin yana jiranta. Suka gaisa da Zakiru, suna tafe yana tsokanarta ya ce "Amina kinga yadda ki kayi ƙiba kuwa, me suke bakuna can Abujan kika zama haka ne?" Murmushi kawai tayi ta ce "Shinkafa mana" "Eh ba shakka kam, shinkafa da kayan daɗi dai, ke baki ga yadda ki ka ƙara ƙiba ba masha Allah, kin ƙada haske sosai" Ita dai ba tace masa komai ba, sai murmushi amma ita kanta ta san tayi ƙiba sosai daga tafiyarsu zuwa yanzu. Kasancewar Baba ma ya san yau zata dawo kamar yadda Daddy ya gaya masa, ya sanya ya kasa zaune ya kasa tsaye, yana dakon ganin tilon 'yar ta sa, kamar yayi tsuntsuwa ya je ya taho da ita. Yana jin horn ɗin mota, ya tashi da sauri, ya leƙa ta ƙofa yaga motar gidna ce, a gaggauce ya buɗe gate ɗin, Zakiru ya shigo da mota, ai kuwa da sauri ya bi bayan motar. Zakiru na tsayawa, Amina ta buɗe motar ta fito, ta nufi wurin da Baba yake. "Uwata sannu da zuwa" Amina ta washe baki, tana jin wani irin farinciki, ganinta ga ta ga Baba, tayi kewarsa ba kaɗan ba. "Babana, sannu da gida Baba na sameka lafiya?" "Lafiya lau uwata, ya hanya kun shawo hanya ko?" Amina ba ta sani ba, ko ya san a jirgi a ta dawo ba, ta maze ta ce "Hanya lafiya lau Alhamdilillah" "To ma sha Allah, an sanar mini cewa kin yi nasara a tafiyar da kika yi, ubangiji Allah ya sanya albarka, ya sa an fara kenan" "Amin Baba na gode" Baba ya ce "Maza ki shige ciki, ki samu ki huta, duk da yanzun nan za ayi magariba, ki samu ki ɗan huta". "To Baba" Zakiru ya ɗauko mata akwatinta, ya rakata har cikin gidan. Hajara na ganin Amina ta washe baki "Amina, dama yau zaki dawo babu labari, sannu da zuwa" "Yauwa, ya gida ya aiki?" Hajara ta ɗan ɓata fuska ta ce "Gida gashi nan yadda kika bar shi, aiki kuwa kamar ha kasheni. Amina ke da aka ce zaki kwana goma kece ki ka yi kusan wata guda" Amina ta ce "Ai ita dama tafiya kan kayi kai ke da ita, bayan kayi kuwa ita ke da kai" Hajara ta ce "Haka ne, ya hanya?" "Hanya Alhamdilillah, ina mutanen gidan?" "Jiya da daddare jirginsu ya ɗaga, 'yan bala'i daga tafiyarsu har na ɗan murmuro mutanen nan basu da kirki, sai baƙar zuciya da cin zarafi a ransu". Amina ta ce "Hajara kena, bari in shiga in ɗan huta" Har Amina ta ja Akwatinta, Hajara ta lura ai Akwatin ba wadda tayi tafiya da ita bace ba, wannan tafi girma da kyau. "Amina, wannan galleliyar Akwatin fa?" "Bamu aka yi" Amina ta amsa mata ba tare da ta juyo ba, ta shige sashensu. Tun da Amina ta tafi, Daddy yake jin gidan ya yi masa babu daɗi, gaba ɗaya gidan ya yi masa girma, tun baya fi awani da tafiya ba, gaba ɗaya ya ji kewarta ta dame shi. Bai ƙara tsinkewa da lamarin ba, sai da dare yayi zai kwanta, da tana nan ta san zai yi aiki da daddare, zata ajiye masa abin motsa baki, ko kuma ta hana shi aikin cikin nutsuwa, tayi ta takura masa. Kasa yin aikin yayi, ya nemi wuri ya kwanta, sai dai nan ma bacci ya gagareshi, yayi ta kallon empty space ɗin gadon, ya janyo pillonta, wanda da suka yi faɗa ta daina kwana a jikinsa sai a kan pilon, ya rungume a jikinsa yana faɗin "I miss you Meenalina" Ɓangaren Amina ma, tana tunanin Daddyn, amma bata bari tunanin nasa ya hanata sabgoginta ba, sai da ta zo kwanciya ita ma, ta fara tuna irin rayuwar da suka yi tare a ɗan wannan lokacin, yadda yake bata kulawa da taraiyarta. Rayuwa suka yi mai ɗauke da tarihin da abune mawuyaci zukata su iya mantawa da shi. Sai a lokacin kewarsa ita ma ta addabi ruhinta, har ta kasa bacci tayi ta juye-juye, ba tayi zaton haka tayi mugun sabo da shi ba sai yau. A hankali ta furta sunansa "Daddy" ta cigaba da jiyinta, bacci ɓarawone ya saceta ba tare da ya sani ba, a baccin ma banda mafarkin gasu tare babu abin da take yi. Saboda tsabar ƙawazucin makaranta, a washegari Amina ta shirya, zata makaranta. Hajata ta ce "Ke Amina daga dawowarki har zaki makaranta?" "To idan ban je makaranta ba, zaman me zan yi?" "To aikuwa Hajiya ta bar tulin aiki, da zaki yi mata kan ta dawo" Amina ta ce "Matsalarta ce" ta saɓa jakarta tayi waje, shi kansa Baba bai yi zaton zata je makaranta a yau ba, amma tayi masa baynin an wuceta a wasu abubuwa da yawa a makarantar. "Yan ajinsu murna suka dinga yi suna shewa, da suka ga Amina ta dawo, dan ko bakomai Amina akwai surutu da abin dariya, kusan kowa ya santa, nan malamai da ɗalibai suka dinga yi mata murnar nasarar da ta samu. Duk da ta sha tambaya a wurin wasu, na rashin dawowarta tare da sauran ɗalibai, amma ta dinga waskewa tambayoyin nasu. Abu kamar wasa, Amina damuwa ta isheta, tana missing ɗin Daddy sosai da sosai, gashi wayarta tana hannunsa, balle ta kira shi a waya taji ya yake. Amina har gidansu Azima taje, Maman Azima tayi ta mitar ta kira wayar Amina amma ba ta shiga, ta yi mata ƙaryar wayar ta lalace. Ranar taje gidan mai lallen Ammin Azima ta zo, ita ma aka yi mata sannan ta tafi gida. Kusan sati guda da dawowarta, Amina duk sai da ta yiwa gidan kwalema, ta gyara ko ina. Saura sati ɗaya Amina ta zana Jamb, ta dage tana ta karatu, wuni take a makaranta sai yamma ta dawo, saboda ta samu isashshen lokaci tayi karatu yadda yakamata. Ta dawo da yamma, tana shiga falon ta ɗan yi shiru tana nazari. Hajara ta ce "Lafiya naga kin tsaya a nan?" "Hajara Daddy ya dawo ko?" "Me kika gani?" "Ƙamshinsa naji" "Ke Amina, wane irin ƙamshinsa kuma?" Amina ta ce "Ƙamshin turarensa nake nufi" "Ke yanzu saboda salo har kin wani san ƙamshin turarensa?" Kai tsaye Amina ta nufi sashin Daddy. "Ke Amina ina zaki?" Amina bata tsaya ba, ta wuce sashinsa. Yana gaban wata cupboard da litatafansa ke ciki, yana duba wani littafi ta tafi da gudu ta rungumeshi ta baya. Ta ce "Oyoyo Daddy saukar yaushe?" Ya juyo da ita suna fuskantar juna ya ce "Kamar gaske, murna kike kin ganni bayan kin taho kin barni" "Wallahi Daddy nayi missing ɗinka sosai, ya aka yi ka dawo? Na san saboda ni ka dawo ko?" Ya ce "Ni ba saboda ke na dawo ba, wani aiki na dawo yi" "Ba wani nan, saboda ni ka dawo mana" tayi maganar a shagwaɓe. Murmushi yayi ya ce "Ya school ɗin?" "School Alhamdilillah, mun kusa jamb" "Ma sha Allah, yayi kyau" Kamar yadda yake mata ita ma ta ɗora hannu a cikinsa ta ce "Ka ci Abinci ko in je in dafa maka" "A ƙoshe nake, ai ban daɗe da sauka ba" Sake rungumeshi ta yi ta ce "Nayi missing ɗinka sosai" Shima rungumeta yayi sosai a jikinsa, yayi zaton idan ya dawo, zata cigaba da fushin nan, amma kamar ba suyi faɗa ba tana ta murnar ganinsa. Amina ta koma ɗakinta, a gurguje tayi wanka ta sauya kaya, ta koma wurin Daddy. Hira suke yi sosai shi da ita, ya kama hanunta yana kallon lallenta ya ce "Saboda ni aka yi shi ko kuwa?" "Tun da Allah ya kawoka ai shikenan ya zama naka" tayi maganar tana murmushi. Ya kai hannun hancinsa yana sansanawa, "Waye ya yi miki?" "Gidansu Azima naje, na tarar ana yi musu nima aka yi mini" "Yawo kike ko?" Ta tura baki ta ce "Ni ba yawo nake yi ba, gidansu Azima ne fa" Hannunsa ɗaya ya kai kan leɓenta yana ja a hankali, hannunsa ɗaya kuma riƙe da hannunta, hannun nata ta miƙa ita ma tana ja masa gemu tana murmushi. "Nayi missing ƙiriniyarki sosai da sosai" Murmushi tayi tana lumeshe ido, ta buɗe tana kallonsa. Hajara ce tayi sallama, kan su farga ta bankaɗo sai ganinta suka yi a tsakiyar falon, tayi turus tana bin su da ido. AYSHERCOOL 08081012143GABA DA GABANTA NA AISHA ADAM AYSHERCOOL Watpad@ ayshercool7724 Arewabooks@ ayshercool 7724 54 Haɗe rai Daddy yayi, ba tare da ya saki hannun Amina ba ya ke kallon Hajara. Gaba ɗaya Hajara ta diririce, da ganin abin da ba tayi tsammani ba, ga kuma irin kallon da Daddy yake mata da ta kasa gan ma'anarsa. "Lafiya?" Ya tambayeta a kausashe. "Mmm.amm.... Eh dama Zakiru ne ya ce a gaya maka wai baƙinka, sun iso ya kira wayarka baka ɗaga ba" Daddy ya ce "Na ji, amma daga yau kar ki sake zuwa sashen nan, idan ya kama dole sai kin zo, kiyi sallama idan na miki izini sai ki shigo" "To..toto in Allah ya yarda" ta juya zata fita, tana sake waiwayowa tana kallonsu, amma babu wanda yayi aniyar daina abin da yake a cikinsu. Kusan da gudu ta ƙarasa ɓangaren su, ta dafe ƙirji ta ce "Na shiga uku ni Hajara, iskanci a cikin gida da yammacin Allah, kuma da maigida? Lallai Amina masifa ce ke, ubangiji Allah ka tona musu Asiri, kaga tsohon nan tsohon banza dan girman Allah. Ni yanzu da wa zan tattauna wannan zancen ne? Uhmm babu ruwana 'yan gidan ba amana ce da su ba, Zakiru ba shiri muke ba, kuma yana da kusanci da Alhaji, idan na faɗa cewa za ayi ƙarya nake, dama ban isa in tunkari wannan matar mai fuskar shanu ba, in ce zan gaya mata, sai ta kasheni ai". A ɗan tsorace Amina ta ce"Daddy, ni fa gaskiya ina jin tsoron kar Hajara ta tona mana asiri, dama tun a baya tana yawan saka mini ido, balle yanzu da ta zo ta ganmu a haka" "Karki damu da ita please, a wurin wa zata tona mana Asirin, she can't do anything, i will intimidate her to keep quiet, ba abin da zata iya yi" Amina tayi ajiyar zuciya ta ce "Shikenan, suwaye baƙin naka ne? Nan zasu shigo?" Ya ce "A'a, suna wancan gidan nawa, wasu mutane ne, za'a ginawa Asibiti, zamuyi magana, nace musu mu haɗu a can" "Ok to shikenan, amma dai zaka canzaa kaya ko?" Tayi maganar tana kallon kayan jikinsa. Shima ya kalli kayan sannan ya ce "Me wannan ɗin suka yi?". "Ni dai a canza wannan kayan, bana son ka fita da su" "To shikenan, muje ki zaɓa mini wasu" suka miƙe tare, tana gaba yana binta a baya, suka isa bedroom ɗin sa, ta ɗauko masa wasu kayan ya sauya, ta rakoshi har falo. Kan ya fita ta ce "Me kake so a girka maka da daddare, Coffee ko Fruit?" "Duk abin da kika dafa ina so" "To shikenan a dawo lafiya" "Allah ya sa dear" yayi gaba. Amina na hangen Hajara a Kitchen, amma ta basar ta wuce ɗakinta, bata sake fitowa ba, sai da aka yi sallar magariba, shi ma ta shiga Kitchen ne domin yiwa Daddy girki. Hajara sai bin Amina take da kallo, tana son ta yi Magana, amma taga ba fuska Amina ta haɗe girar sama da ta ƙasa ta sha kunu, aikin gabanta kawai take yi.    Kasancewar baya cin abinci mai nauyi da daddare, ya sanya ta girka masa jallop sphagetti, ta sha kayan ganye sosai da kifi, dan bata fiye barinsa ya ci nama sosai ba, ko tea zata ba shi, sai dai ta zuba masa zuma a maimakon suga, fafur ta hana shi shan lemukan gwangwani, sai wanda ta haɗa masa da kanta, cikin ikon Allah, ba a kuma cewa sugansa ya hau ba. Hajara ba abin da take yi a Kitchen ɗin, amma sai kaiwa take tana komowa taga iya gudun ruwan Amina. Bayan sallar isha'i, Alhaji Ahmad ya dawo gida. Amina ta sha wanka cikin riga da skirt na atamfa, ta ɗaura ɗan kwalinta, ta shiga Kitchen ta jera Abinci a kan tray, ta nufi sashinsa, cikin sanɗa Hajara ta bita har falo, taga Amina ta shige sashin Daddy. Ta sake riƙe baki ta ce 'Abin da nake zargi dai ya tabbata, amma Amina sheɗaniya ce, yarinya ƙarama haka, amma kalli tana lalacewa da maigida, amma Hajiya Zainab duk wayon nan nata ya zama na banza, sun mayar da ita albasa. To amma ya aka yi suka yi wannan shaƙuwar, naga dai ita bata gari shima haka? Kuma dai da Hajiya Zainab tana nan abin nasu bai kai haka ba, ko dai a wani wurin suke haɗuwa tun a baya, taɓ Allah ya nuna mana ranar tonon asiri mu sha kallo". Tun da ta shigo yake binta da kallo, tayi kyau sosai, kayan sun karɓi jikinta yadda yakamata. Ta ajiye kayan a ƙasa, ta nufi in da yae ta zauna a kusa da shi ta ce "Sannu da zuwa, ya baƙin naka?" "Baƙi lafiya lau, har sun tafi ma" "To kun daidaita ɗin da su?" "Eh mun daidai ta, har sun bada 70% na kuɗin, idan aka kammala zasu bayar da sauran" Ta ce "Alhamdilillah, Allah ya yi jagora, ya sanya a yi a sa'a" "Ameen Meenalina, naga sai wani ƙara kyau kike, meye sirrin ne?" Kamar za tayi kuka ta ce "Wane kyau Daddy, karatu ya sakani a gaba, ko isashshen bacci bana yi, ina son na samu maki sosai a jamb ɗina" Ya gyara zamansa tare da matso da ita kusa da shi ya ce "Zaki yi nasara in sha Allah, ba na jinki, idan har ɓangaren himma ne, Allah ya bada sa'a i will make sure na cika alƙawarin da nayi, na cigaban karatunki" Ta ɗan kalleshi ta ce "Ka fasa cireni daga makarantar da nake? Dan ni a ɗar ɗar nake, na san a kowane lokaci ana iya sauya mini makaranta" Girgiza kai ya yi ya ce "Please, mu bar wannan maganar, bana son abin da zai rusa mini farinciki ki saka mu fara faɗa, mu fara cin Abinci tukuna" Ya miƙe tsaye, ita ma ya miƙar da ita, suka nufi wurin Abincin. Ta zuba musu a plate ɗaya, da kansa ya dinga a baki, yana ci yana mata santi, yana sake koɗata a kan iya girki. Amina kuwa sai ji take yana fasa mata kai, tana jin daɗin yadda yake yaba mata. Sai da ya tabattar ta ƙoshi, ya kashe wutar falon, sai hasken TV suka cigaba da hira, yana mata hirara aikinsa, nasarori da ƙalubale, suna nan zaune har kusan goma na dare, a lokacin ta haɗa masa Coffee ta hau cinyarsa ta zauna, ta saka cokali tana ɗebo coffeen ta hura da bakinta, yayi sanyi sannan ta bashi a baki. Alhaji Ahmad jinsa yake tamkar yanzu yake kan ganiyarsa ta matashi, gaba ɗaya kasancewarsa da Amina, ya sanya ya dinga jinsa na musamman, duk da tarin ƙuruciyarta da wautarta wasu lokutan, amma Amina tana da baiwa da hikimomi daban daban. Sai da ya shanye tsaf, sannan ta ɗau tissue ta goge masa baki, ta ce "Alhamdilillah, mun ci mun ƙoshi, sai mu ɗan jira ya faɗa maka, sai kaje ka kwnata nima na je na ɗan yi karatu na kwanta. "Kije ki kwanta a ina?" Ya tambayeta. "Ɗakina mana" "You are not going anywhere, muna nan a tare" yayi maganar yana kwantar da ita a jikinsa. "Daddy mun fa dawo gida, idan aka ankare fa akwai hatsari a yin hakan, kayi haƙuri Please" "Babu wani hatsari, kefa kika ce saboda ke na dawo, naji na yadda saboda ke na dawo, kuma sai ki tafi ki barni, impossible" "Idan an yi magana ka ce mini rigimammiya, yanzu waye me rigimar tsakanin ni da kai?" Yayi dariya ya ce "Ke kika koya mini, da rigima da rikicin gangan, ƙaƙalo faɗa ba dalili" Ta ɗan tura baki ta ce "Duk ni ɗin?" "Eh mana, oya tashi muje mu kwanta" Amina ta ce "Naji, amma bari na fita da kwanukan nan, na canza kaya" "Na ƙi wayon, bar kwanukan a nan" ya tashi tsaye da ita a jikinsa, ya kashe socket ɗin TV, suka wuce bedroom ɗin sa. Alhaji Ahmad ko kunyar Amina baya ji, Kodayake ya riga ya sanya ta saba da shi, tun a lokacin suna tare, he make her feel free with him, so he enjoys the night with her, making her more comfortable with him. Bayan sallar Asuba, bata kwanta ba, domin zata makaranta, bayan Daddy ya koma bacci, ta sauka daga kan gadon, ta nufi sashin su. Tana zuwa babu ɓata lokaci, tayi wanka ta fito Kitchen, dan tabattar da ta kai masa Abinci kan ta tafi makaranta. Hajara tana ta yanka doya zata fara soyawa. "Hajara ina kwana" Amina ta gaisheta a lokacin da ta shiga Kitchen ɗin. Cikin mamaki da kallon tuhuma, Hajara a ta ke bin Amina da kallo. "Hajara lafiya naga kina kallona a haka, kamar na canza miki?" "Kin canza mana Amina, a ina kika kwana jiya da daddare?" Ras! Gaban Amina ya faɗi, amma da yake idonta ya riga ya buɗe ta dubi Hajara ta ce "A ɗakina mana" "Amina kiji tsoron Allah, ki tausayawa kan ki, ki tausayawa dattijon nan mahaifinki, mutumin nan fa ba zai aureki ba, kawai yana amfani da ke ne da ƙuriciyarki dan cinma muradinsa, mahaifinki ya kawo ki kiyi karatu, amma kike biyewa mai gidan nan kike bashi kanki? Wallahi Amina idan baki nutsu ba, zan samu Malam Hassan in gaya masa abin da kike yi, idan kika ja masa abin kunya ba ki yiwa kanki adalci ba". Jikin Amina ne yayi sanyi da maganganun Hajara, mussman maganar Baba, da kuma irin ɗauki ba daɗin da aka sha da su Kawu Bala, tabbas idan Baba ya san abin da take aikatawa, bata san ina zata saka kanta ba, kunyarsa ma kawai ta isheta, su Baffa Lawan kuwa za suyi musu dariya ne, ga uwa uba Inno. Amma saboda tsabar iya gwanancewa a iya rainin hankali Amina ta sake kallon Hajara ta ce "Ke ya aka yi kika san cewa bashi kaina nake yi?" "Amina karki raina mini hankali, meye a tsakaninki da shi? Ko kin manta a yanayin da na ganku jiya, yau kuma ƙarewa a sashimsa kika kwana" "Meye shaidarki a kan hakan?" Saroro Hajara tayi tana cigaba da mamakin sauyawar Amina. Amina ta nisa ta ce "Ki Ƙaddara ma na kwana a ɗakinsa, hakan na nufin bibiyarmu kike kina saka mana ido ko? To bari kiji na gaya miki, ki sakawa zuciyarki kamar baki ga komai ba, ko kya samu ki cigaba da harkokin ki cikin nutsuwa. Idan kina da wata hanyar ta samun kuɗi, zaki iya zuwa ki tona mana asiri, idan kuma baki da wata hanyar kina iya rufe bakinki, mu cigaba da harkokinmu, idan kuwa kika cigaba da bibiyata da saka mini ido, to tabbas zan saka ya sallameki daga gidan nan, idan kuma kika kuskura ya san cewa zaki tona mana asiri, wannan shi zai ɗau mataki a kanki da kansa bani ba, ki saka wannan a ranki". Amina ba ta saurari me Hajara za ta ce ba, tayi abin da ya kawota ta bar kitchen ɗin. Hajara ta daɗe a tsaye tana mamaki, sai da doyar da ta zuba a mai ta fara ƙauri, sannan ta farga ta cigaba da aikinta, jikinta har tsuma yake yi, mussman da ta tuna idan ta bar gidan nan, bata da wani aikin yi, to a ina ma zata dinga samun abinci mai kyau tana ci?. Sai da ta gama shirinta tsaf cikin uniform, sannan ta kai masa duk abin da zai buƙata falonsa, ta shiga bedroom ɗinsa, domin ta ganshi kafin ta tafi. Ta ɗan ƙare masa kallo, sannan ta ɗan ja hancinsa, caraf ya riƙe mata hannu. Dariya tayi ta ce "Idonka biyu dama?" Ya ɗaga mata gira yana murmushi, ba tare da ya buɗe idonsa ba. Ta ce "Ina kwana Babban mutum" Bai amsa ba, yayi kissing ɗin hannunta da ya riƙe. "Ka sakar mini hannuna, kar in makara fa" Sai yanzu ya buɗe idonsa ya yinƙura ya ce "Jirani na zo na kai ki" Tayi saurin dafa shi ta ce "No, ka kwanta kayi baccinka, Zakiru zai kaini" "Ok" "Daddy wai yaushe zaka bani wayata ne tun da mun dawo" "In kin dawo, ki tuna mini zan baki, and na aika an karɓo miki gifts ɗinki, da suke makarantarku, suma idan kin dawo duk zan nuna miki, sai a nunawa Malam Hassan, kin samu kuɗi masu yawa sosai Meenal, Allah ya ƙaro ɗumbin nasara" Murmushi tayi masa ta ce "Amin Daddy, amma komai na samu kai ne tsanin nasarata, ba zan manta wannan ba, Allah ya ƙara buɗi, Allah ya sa kafi haka, ya sanya ka gama da duniya lafiya, na gode ƙwarai dagaske" Yadda tayi maganar harda ƙwalla a idonta, ya sa jikinsa yayi sanyi. "You deserve more than this from me Meenalina, you mean a lot to me. Yanzu nawa zan baki na makaranta" "7 thousand" ta faɗa tana dariya. "7thousand ɗin sun isheki" Ta jinjina masa kai. Ya ce taje ta buɗe drower, ta kusa da kayansa ta ɗauka, ya nuna mata in da mukulli yake. Da ta buɗe ta sha mamaki, kuɗi ne zunzurutunsu a ciki. Ta ɗebi dubu bakwai ta ajiya masa mukullin. "Kin dai tabattar sun isheki ko?" Ta ɗaga masa kai, alamar eh. Sannan ga ɗora da cewa "Na gode sosai, dama dubu biyu nake so, dubu biyar kyautar ta zan yi". "Idan Baba zaki bawa, karki damu, zan bashi, ki riƙe wannan kiyi amfani da shi" "To ni idan na riƙe me zan da su? Sadaka zan yi mana da su" "Funny you, shikenan a dawo lafiya, Allah ya karɓa mana" Ta ce "Amin". Kitchen ta koma, in da ta bar Hajara tana iyo, a tekun mamaki. Kamar babu wani abu da ya faru Amina ta ce "Hajara ungo" Hajara ta waiwayo ta kalleta, ta kalli kuɗin da ta miƙo mata ta ce "Na menene wannan?" "To ki karɓa mana" Hajara ta karɓa, ta duba dubu biyar ne cif "Me za ayi da su?" "Naga wata yayi nisa ne, ba ayi albashi ba, ki riƙe ko wani abun ki saya ki aikawa yaranki" Hajara ta dinga yi mata godiya, kamar ta durƙusa. "Hajara dubu biyar ce fa, karki damu sai na dawo" Hajara ta dinga kwarara mata addu'a, sai da Amin ta fice Hajara ta jujjuya kuɗin ta ce "Wato ta karɓo kuɗin aikinta na jiya, harda bani kasona a ciki, kenan yarinyar nan kwaɗayin kuɗi ne ya sanya ta yarda ta bada kanta? Kai amma wannan mutumin tsohon banza ne. Allah ya sa ta cigaba da bani karɓa zan yi. Abu kamar wasa, shaƙuwa mai ƙarfi ta fara shiga tsakanin Abdul da Yusra, dan har mahaifiyarta ta san shi, ta gabatar mata da shi a matsayin abokin Khalil. Abdul da ya samu 'yan kuɗinsa, sai yaje ya yi mata sayayya ya kai mata, Yusra duk da itama gwana ce wurin iya tsiwa, amma tana matuƙar girmama Abdul da jin nauyin sa, gashi abu kamar wasa, ya fara jin strong feelings a kanta, amma yana tsoron yadda zai gaya mata, kar ta ce bata son shi kamar yadda Fadila tayi, kuma yana gudun Khalil yaji haushi, baya son abotarsu ta samu matsala sam. Yanzu ma waya suka gama, sun shafe kusan mintuna arab'in suna waya, sannan suka yi sallama. Bayan sun yi sallama ne ya kira Khalil a waya. Khalil ya ɗaga yayi  masa sallama. Abdul ya amsa ya ce "Kai wai ba zaka dawo garin nan ba, kaje ka shantake a Lagos?" "Abdul, bana son dawowa ne, mussman idan na tuna ba zan ga Hafsa ba, na san ko naje ba zata saurareni ba" "Khalil, meyasa baka da tawakalli ne? Dan ba zaka samu Hafsa ba ba zaka zo kaga iyayenka ba, ga kuma ni abokinka duk bamu da amfani ko?" Khalil ya ɗan ja numfashi ya ce "Ba haka bane, zan shigo idan su Mummy suka dawo daga umara, yanzu dai wata alfarma nake nema a wurinka" Abdul ya ce "Wace alfarmar kenan?" "Dan Allah Abdul zaka auri Hafsa?!" "What! In auri Hafsa kamar yaya?" "Kayi mamaki ko? Babu wanda zai iya yi mini wannan taimakon sai kai Abdul, dan Allah kar kace mini a'a" Cikin rikicewa Abdul ya ce "Amma ya za ayi ai haka? Ita Hafsan ba zaka tursasata ba, idan bata sona fa?" "Ba zata ƙi ba, sai dai idan kai ne ba zaka yadda ba, dan Allah Abdul" Abdul ya ce "Shikenan naji, ka bari idan ka dawo sai muyi maganar" Khalil ya ɗanyi murmushin yaƙe ya ce "Yauwa Abdul, na gode sosai zan dawo in Allah ya yarda" suka yi sallama suka kashe wayar. Jikin Abdul yayi sanyi sosai, yaso ya yiwa Khalil maganar Yusra, amma Khalil ya zo masa da wani sabon abu daban, gaba ɗaya sai lissafinsa ya ƙwace. Amina ce a ajinsu, ta kifa kanta a kan benci, tana ta baccinta. Azima ta daki bayanta ta ce "Ke ki tashi, tun ɗazu kike bacci a aji, wai ba kya bacci ne?" Amina ta ɗago a fusace ta ce "Ban sani ba, kawai kin kama kin tasheni" "An tasheki ɗin, kika kuma kwanciya sai na tasheki" "Ke gaba ɗaya wasu lokutan sai a hankali kike" Azima ta ce "Eh naji, kince mini mutanen gidanku basa nan, balle in ce sune suka hanaki bacci suka saka ki aiki" Amina ta yi miƙa ta ce "Ba zaki gane ba" "Ai dama ba zan gane ɗin ba, idan an tashi zamu je muyi printing ɗin Slip na Jamb ko?" Amina ta ce "Ke ba zani ba, sai Allah ya kaimu da yamma" "Kai, meyasa?" "Saboda ɗaya baban nawa ya dawo, zanje gida nayi masa girki" "Kai Amina kina ji da Daddyn nan sosai" "Shima yana ji da ni ne, kuma kinga ba kowane Abinci yake ci ba, akwai Abincin da ake bashi saboda ciwonsa" Azima ta ce "Gaskiya ne, Allah ya bashi lafiya" "Amin" daga nan Azima ta ɗauko littafi, Amina ta koya mata wasu abubuwan, har aka tashi. Da rana bayan dawowar Amina daga makaranta, ta shirya ta sha kwalliya, tana jiran dawowar Daddy sai kace matar gidan. Da ya dawo, dai tarairayarsa take tana nan nan da shi, kasancewar rana ce sosai, Hajara tana can sashensu, Amina suka zauna a babban falo suka ci Abinci, Daddy ya ce idan aka yi sallar la'asar zai kaita tayi printing slip ɗin. Amina babu kunya tayi ɗare ɗare a kan cinyar Daddy, yana biyewa shirirtarta. Hajara kuwa da munafurci ke cigaba da cinta, ta leƙa ɗakin Amina taga bata nan, dan haka ta fito falo, dan ta lelleƙa ta ga ko yanzun ma suna tare. Sai dai a wannan karon ma ta kuma katarin ganin Alhaji Ahmad da Amina tare, ya sanya ƙarshen chocolate a bakinsa, ita ma ta sanya ɗaya ƙarshen a bakinta, suna ci a hankali tana kallon idonsa tana murmushi. Cak Hajara ta tsaya, ta dafe bakinta, kuma taƙi tafiya ta tsaya ganin ƙwal uwar daka. Aikuwa suna cin Chocolate ɗin, suna zuwa tsakiya ya haɗe da bakin Amina yana murmushi. A hankali Hajara ta koma, saboda a wannan karon bata san matakin da zai iya ɗauka a kanta ba idan ya ganta, ji tayi ina ma da hanyar da zata silale taje ta gayawa Baba ya zo ya gani da idonsa, amma sai ta tuna gargaɗi da kashedin da Amina tayi mata ɗazu da Safe. Bayan sallar la'asar, Daddy yau ɗau Amina a mota, ya sanarwa da Baba cewar zai kaita su cire slip ɗin jarrabawa. Bayan sun dawo, Daddy ya danƙawa Amina tarin kayan karatun da ta samu na kyaututtuka a wurin competition, sai kuma kuɗinta ya ce ba zai bata ba, sai dai ta faɗi abin da za ayi mata da su. Ta ce "Ina son ka ɗauki dubu ɗari biyu, a kaiwa Inno dubu hamsin, Hajara da Zakiru a basu dubu ashirin, sauran idan zasu isa a saiwa Baba gida a bashi jari" Daddy yayi murmushi ya ce "To ai duk kin rabar da kuɗin, kuɗin naki baza su a rabar haka ba sannan a saiwa Baba gidan ba, amma zan san abin da zan yi. Sannan ni kuma ki bar kuɗinki Amina ni yakamata na baki bake zaki bani ba" "Saboda ka raina ko?" Tayi maganar tana haɗe rai. "Ni na isa in raina? Ban raina ba" "To ni dai a raba kamar yadda nace, sauran ko jarin a fara bawa Baba, so nake ya tsaya da ƙafarsa in raba shi da wannan aikin da yake" "Yadda kike so haka za ayi ranki ya daɗe" murmushi tayi tana ɓoye fuska saboda maganar ta sa ta bata dariya. Babban abin da ya ƙara sanya Amina farinciki, shi ne sauya mata wayar da yayi zuwa wata haɗaɗɗiyar Samsung. Amina tayi wani uban tsalle ta rungume shi tana shafa bayansa tana murmushi. Kusan sati biyu, Daddy ya ƙi komawa wurin aikinsa, ya mayar da Amina tamkar matarsa, idan ka zo sai kayi zaton ita ce matar gidan. Wasu lokutan ida suka bushi iska, idan aka tashi daga makaranta, sai su tafi ɗaya gidan nasa, su wuni a tare sannan su koma gida. Hakan ya ƙara musu tsananin kusanci da soyayyar juna. Yau suna ɗaya gidan nasa, Kasancewar Asabar ce, ta sanya ta yiwa Baba ƙarya ta tafi wurin Daddy a ɗaya gidan nasa. Sai dai yau ɗin sai cika take tana batsewa, tun bayan jin cewar su Hajiya Zainab zasu dawo. "Meenalina, dan Allah ki daina fushin nan" "Ba dole nayi fushi ba, nasan idan ta dawo tsakanina da kai sai dai kallo, ba kulani zaka dinga yi ba" Alhaji Ahmad ya ce "Haba Babyna, ya za ayi na ƙi kulaki, kin san matsayinki a zuciyar nan tawa kuwa?" "Idan matarka tana nan, matsayina mai aikinta, ita da take matarka uwar 'ya'yanka" "Dan Allah kar ki fara Amina, na san yadda zan tsara mana rayuwar da zamu yi ko bayan ta dawo, ni kaina ba zan iya haƙura da ke ba!!! (Sai da ku fans ɗina, ina yinku kamar yadda kuke yina kuke ƙaunar rubutuna💞💕) AYSHERCOOL 08081012143GABA DA GABANTA                NA AISHA ADAM AYSHERCOOL Arewabooks ayshercool7724 Watpad ayshercool7724 55 Hararsa tayi, taji tamkar ta yi masa tsaki, saboda haushin da ya mamaye ilahirin zuciyarta. Ya kwantar da kai ya cigaba da rarrashinta, yana bata baki a kan zai san yadda komai zai tafi daidai ba tare da wata matsala ba.   Amina dai kawai jinsa take, ba tare da ta gamsu da maganganunsa ba, dan yadda yake nunawa a kan Hajiya Zainab, tamkar tsoronta yake ji ma. Bayan sun koma gida, Amina taje ta samu Baba, ya na zaune yana jin radiyo. Amina ta kalleshi cike da ƙauna ta ce "Baba sarkin radio" Yayi murmushi ya ce "Bari uwata, ai dole mutum ya saurari radio, domin ka san halin da duniya take ciki, kuma kinga mu da ba muyi karatun boko ba, radion nan makaranta ce a garemu" Amina ta jinjina kai ta ce "Haka ne, Baba magana nake son muyi da kai" "To uwata bari in kashe radion" Ya kashe radion ya bata hankalinsa yana saurarenta. "Baba kaga sakamakon nasarar nan da nayi, na samu kuɗi masu yawa, bayan kayan karatu da na samu" Baba ya jinjina kai ya cigaba da sauraron ta. "To dama kuɗin suna wurin Daddy, sai muka yi magana kaga Hajara da Zakiru duk tare muke aiki da su, nace a basu wani abu a ciki. Shi ma Daddyn duk da yana da kuɗi ai kaga yana ɗawainiya da mu, ko babu yawa shi ma a bashi wani abu" sai kuma ta yi shiri dan taga reaction ɗin Baba. Baba ya ce "Cigaba ina jinki" "Yauwa, to da nace sauran kuɗin, a sai mana gida a ƙauye mu baro cikin gidan yawan nan, sannan a baka jari, amma Daddy ya ce mini ba zasu isa ba, sai na ce ko a je ƙauye a mayarwa da Jarmai kuɗinsa, ya dawo mana da gonarmu, sauran kuɗin a biya ayi mana noma ko?" Baba yayi murmushi irin na su na manya ya ce "To uwata, na ji amma batun aje ƙauye a mayarwa da Jarmai kuɗi ya bada gona bai taso ba, abu wurin shekara guda. Ni ba zan hanaki yin alkhairi ba, kuma kuɗi naki ne, abin da kika yi na kyauta da sadaka daidai ne, sauran ki bayar a saya miki gona, in an tashi a sayar in haɗa da abin da nake da shi ayi miki kayan ɗaki" "Kayan ɗaki kuma Baba?" Ya ce "Eh mana" "Baba Allah zai kawo wasu, yanzu wannan ma ai babu wanda ya san za a samu, dan Allah Baba ni gonarka nake son ta dawo" "A'a sai dai a saya miki gona, ai ni yanzu babu abin da wata gona zata yi mini" Amina ta marairaice ta ce "Baba, baka san yadda nake ji a zuciyata zaman aikin gadin nan da kake, ana wulaƙanta mini kai ba, idan aka sai gona, aka noma abin da aka samu so nake ko kiwo sai a zuba maka, ka koma gida ka huta, Baba bana son aikin gadin nan, ni fa ba dan mutanen da na lissafo suma sun cancanci su samu wani abu a kuɗin ba, da duka zan bayar a sai mana gida. Ko kayi jari ka sauya sana'a Baba" "Allah sarki uwata, Allah yayi miki albarka, komai lokaci ne kinji, ki daina damuwa, watarana sai labari. Ni dai fatana ki kula da kanki, idan lokaci yayi watarana dole na bar gadi, lokacin kin kawo ƙarfi sosai, sai na koma gefe na huta" "To ai yanzu ma ina da ƙarfi" Yai murmushi ya ce "A'a da saura" Ƙarshe dai suka daddale a kan, za a sai kayan Abinci a kai gida, a sai kiwo a zuba. Amina ta samu Daddy da maganar yadda suka yi da Baba, ya ce mata shikenan babu damuwa. Daddy ya samu Baba suka kuma tattaunawa da Baba, ba tare da Amina ta sani ba. Mamaki ne ya cika Inno, ganin uban tarin kayan Abincin da aka kuma aiko musu da maƙudan kuɗi daga birni, a wai Amina ce ta aiko da su, a sanadin karatun boko ta same su. Baƙi ciki da hassada suka cika zuciyar su Baffa Lawan, duk da idan an aiko da kayan har da su ake ɗibarwa, su karɓe su koma gefe suna ƙananun maganganu. Yau ya kama su Fadila zasu dawo, bayan shafe kusan wata guda a ƙasa mai tsarki, kuma ya kama Asabar ce ranar dawowar ta su. Tun safe Amina da Hajara suke ta faman aiki, yayin da Hajara a ranta take son ganin ya zata kaya, alƙar Amina da Alhaji Ahmad zata ɗore ko kuwa Asirinsu zai tonu a wurin matar gidan. Daren jiya kuwa Amina kusan kwana suka yi, suna rigima da Daddy duk a kan dawowar Hajiya Zainab, saboda ta san da ta dawo zata ɗora daga in da ta tsaya wurin wulaƙanci, da cin mutunci kamar yadda ta saba ita da Fadila. Da magariba, Daddy da kansa ya tafi airport ɗaukosu, Fadila na ganinsa ta rungume shi tana murna, kamar ta shekara bata ganshi ba. Ya kalli Hajiya Zainab ya ce "Sweetheart ya hanya?" "Alhamdilillah, ashe kana gari na zata direba ne zai zo ya ɗaukemu" Ya ce "Eh na shigo gari jiya" yayi maganar a taƙaice. Ai tun a mota, ta fara buge-bugen waya, tana sanarwa su Hajiya Turai sun sauka yanzun nan, gasu a hanyar gida. Bayan ta gama wayar Daddy ya ce "Haba Madam, daga dawowarki ko gida baki je ba kin fara kiran waya, ai kya bari muje gidan ku huta, in ganku sosai da sosai, tunda mun kwana biyu bama tare" "Lallai ma kai ɗin nan, kai da wataran sai ka shafe wata uku baka ganmu ba, bamu ganka ba, shi ne yanzu kake wani ga zance ga magana. Kuma idan ban gaya musu ba suwa zan gayawa, ai gara sun san mun sauka lafiya hankalinsu ya kwanta" girgiza kai yayi, ya cigaba da tuƙi, ita kuma ta cigaba da mita. Ko da suka isa gida, tare suka shiga falo, Zakiru tare da Baba ya biyo su da Akwatunansu. Hajara na ganin Hajiya Zainab, ta washe baki ta risuna tana gaisheta, sai dai kamar yadda ta saba a wulaƙance haka ta amsa mata gaisuwar, irin wanzuwarta a wurin da rashinsa duk ɗaya a wurinta, take Hajara ta haɗiye murmushinta a ranta ta ce "Shegiyar mata, ai Allah ya ƙara ma abin da mijinki yake yi, mai baƙin hali kawai". Ai kan sallar isha'i, tuni su Hajiya Turai, da wasu daga ƙwayenta suka cika gidan, suka dinga hayaniya, kamar ba a lokacin ta dawo ba. Ita dai tunda Amina ta fito ta gaishesu,taga Hajiya Zainab tayi mata kallon banza, ba ta sake komawa ta kansu ba, ta koma ɗakinta tayi zamanta, Sai Hajara ce ta kai musu Abinci. Gaba ɗaya hayaniyar ta ishi Fadila, ta wuce ɗakinta ta rufe ƙofa, domin ta samu nutsuwa, Alhaji Ahmad kansa sai bar musu gidan yayi, kamar ana taron biki. Tun a daren ta fara kwance abin da ta zo da shi, ta hau yi musu rabo. Alhaji Ahmad kuwa, bayan ya fita yayi sallar isha'i, Amina ya kira a waya, suka daɗe suna waya sai da ta tabattar masa da sun tafi, sannan ya dawo gidan. Ko da ya dawo gidan, yana son sun ɗan yi hira, Hajiya Zainab ta ce ita a gajiye take bacci take ji. Washegari sai bayan sallar Azahar sannan Fadila ta sanarwa da Yusra cewar sun dawo, Yusra tayi ta murna, ta ce anjima zata zo ta ganta. Ganin da Hajara tayi kamar Amina na cikin damuwa, ya sanya ta dinga murna a ranta tana cewa Allah ya ƙara. Bayan Amina ta bata kuɗi masu yawa kan dawowar Hajiya Zainab. Abdul yana ta son ya gaya wa Yusra yana sonta, amma ya kasa bai san ya zata ɗauki abun ba, kasancewar Khalil take so a farko, kuma shima a baya Ƙawarta Fadila yake so, bai san ya zata karɓi abin ba, ga kuma Khalil da yake ƙoƙarin bijiro masa da wani abu daban. Washegari kamar yadda Yusra ta alƙawarta, taje gidansu Fadila domin ta ganta. Da Amina ta fara karo a falo, Amina na ganinta tayi murmushi ta ce "Chef Yusy" Yusra ta ɗan kalleta ta ce "Fadila tana nan ne?" "Eh tana nan, ina son zan shiga classes ɗin ki na girki ya za ayi?" Yusra tayi murmushi ta ce "Sai kin zo" "To amma nawa zaki rage mini, kinga ni bani da kuɗi sosai" Yusra ta ce "Duk kuɗin da kika samu? Naji ance kin yi nasara a cimpetiton da ake duk shekara a Abuja, amma baki yi mana ko walima ba" Amina ta ce "Ai ma idan nace kuzo, na san ba zuwa za kuyi ba, ni irin cake ɗin da ki ke yi nake son na iya, mun taɓa oreder sa da 'yan ajinmu yana mini daɗi sosai" "In dai Cake ne, idan na fara classes ɗin, ki zo na koya miki kyauta, idan na koma gida zan bayar a kawo miki". "Dan Allah dagaske?" Yusra ta jinjina mata kai. "Kaii amma naji daɗi wallahi, Allah ya saka da alheri, aikuwa zan zo, idan kina so nima sai in koya miki abincin gargajiya, irin su dambu, Alkubus, tuwo kala kala, normal tuwo da na masu kamar ciwon sugar, har da su gurasa fa na iya su sinasir da sauransu" ɗan shiru Yusra tayi tana nazartar Amina ta ce "Dagaske duk kin iya wannan girke-girken?" "Wallahi duk na iya, Inno ta koya mini girke-girke, har su yadda ake haɗa kwaɗon salak, kwaɗon rama da abubuwa kin san sun fi lafiya" "Gaskiya ne, ko zamu shirya wani business tare ne? Muyi join classes, ki dinga koyar da Abincin gargajiya" Cikin sauri Amina ta ce "Eh zan iya wallahi" Hajiya Zainab ta fito tana faɗin muryar wa nake ji ne haka?" "Nice Mummy, na zo Amina ta tsareni da surutu, ina ga ma zamu fara join class tare, tun da na ga ta iya girkin gargajiya" Haɗe rai Mummy tayi ta ce "Ke da wa? Sai ki ɗau wannan ƙazamar a cikin harkar sana'arki, wa zai mini aikin gidan nawa, shareta dan Allah ya gidan naku ya Mummynki?" "Tana nan lafiya Mummy, ya hanya?" "Lafiya lau, Fadilan tana ɗakinta. Ke kum wuce kije kiyi mini abin d ana saka ki, sai shegen surutun tsiya duk wanda ya zo ki tsareshi da surutan banza" Amina ta juya rai a ɓace, ta bar falon. Saura kwanaki uku kacal su Amina su fara WAEC, gaba ɗaya a gajiye take, Hajiya Zainab ta tsiro da sabbin salo na muzguna mata saboda taga jarrabawa take fuskanta, tayi ta sakata aiki ta hanata sakat balle tayi karatu, sai dai ta bi dare tayi karatun. Yau da aka tashi daga makaranta, gidan Daddy ta wuce, domin ta zauna ta huta da yamm sai ta koma gida. Sai dai tana zuwa ta tarar da Daddy a gidan. Yayi mamakin ganinta, mussman yadda ya ganta a gajiye. "Babyna lafiya kuwa?" A gajiye ta ce "A gajiye nake ne, zuwa nayi na huta na san da naje gida, matarka ba zata bari in huta ba, za tai ta sakani aiki, ni kuma a gajiye nake hutu nake so, jarrabawa zamu fara" Cikin matuƙar tausayinta ya miƙe ya janyota jikinsa yana mata sannu. Ta lumshe idanunta ya zare mata hijjabin jikinta, yana ɗan matsa mata jikinta a hankali. "Da na sani na zo na ɗauko ki daga makarantar, ni gani nayi ma kina ramewa" "Ba dole in rame ba, wannan matar ta sakani a gaba, kullum cikin zagi da hantara" "Am sorry on behalf of her, bari in kawo miki ruwa" ya tashi ya ɗauko mata ruwa, ya kawo ya bata ta sha, yayi mata order Abinci. Kusan tun da Hajiya Zainab ta dawo, basu sake samun damar haɗuwa ba sai yau. Ta nemi wuri ta kwanta cike da gajiya da rashin bacci da ya sanya mata ciwon kai. Daddy ya duƙufa Sosai, yana ta aiki a system, Amina ta ce "Daddy aikin me kake yi ne?" "Lissafi nake, a cikin Azumi zan fitar da Zakka in Sha Allah" "Mhmm dama kana bada zakka?" "A'a wannan karon zan fara" yayi maganar yana hararata Tayi murmushi ta ce "Wa zaka bawa?" Ya ɗan nisa ya ce "Mai rabo" Amina ta ɗan nisa ta ce "Ina son dan Allah a taimakawa 'yan garinmu da wani abu daga cikin zakkar, muna da mabuƙata sosai" "Shikenan, za a duba in sha Allah Meenalina" "Godiya muke, Allah ya ƙara arziki" "Amin Sweetheart, jibi in Allah ya kaimu zan koma" Ta ɗan zabura ta ce "Haba dai?" Ya jinjina kai ya ce "Eh" Kamar tayi kuka ta ce "Daddy why?" Ya riƙo hannunta ha ce "Meenalina, am so much addicted to your care. Idan ina cigaba da ganinki, asirnmu zai iya tonuwa, sannan bana jin daɗin yadda wasu abubuwan suke gudana, alhalin ba zan iya baki kariya ba. Idan na koma na yi nesa da ke, maybe zan fi samun nutsuwa iyakaci dai zan yi matsananciyar kewarki". Shiru Amina tayi, amma kusa maganar Daddy haka take, idan suna cigaba da ganin juna, kusancinsu sake ƙaruwa yake yi, kuma a kowane irin lokaci, Asirnsu yana iya tonuwa, dan a dawowar Hajiya Zainab, da taƙi yadda su haɗu, har Kitchen ya bita. "Maganarka haka take Daddy, Allah ya zaɓa mana abin da yafi alkhairi, nima ba zan so asirnmu ya tonu ba, amma kar ka manta alƙawarrukan da ka yi mini" "In sha Allah ba zan manta ba, zan yi Kamar yadda nayi alƙawarin, zan san hanyar da zan sama mana, kiyi karatu da kyau my love" yayi maganar yana rungumeta yana jin yadda yayi kewarta sosai. Suna tare har Yamma liƙis, sannan ya kai ta gida ya ajiyeta a bakin layi, ya wuce. Da daddare Hajiya Zainab tana ta hira da ƙawayenta a waya, Daddy yana gefe yana cigaba da lissafinsa, gefe guda kuma kewar Amina tana damunsa, duk baya walwala. Hakan bai damu Hajiya Zainab ba, ganin yana lissafin kuɗi ya sanya ta matsa kusa da shi ta ce "My dear ya batun zuwa nema wa Khalil aure ne?" "Ki ɗan bani lokaci tukuna" yayi maganar ba tare da ya kalleta ba. "Amma  kai fa kace idan mun dawo zaka nema masa" Daddy ya ce "Yanzu abubuwa sun yi mini yawa, ki ɗaga mini ƙafa sai na koma na dawo tukuna" A ɗan hasale ta ce "Amma dai ka san na riga nayi maganar da uwar yarinyar ko?" "Kinga idan ba zaki jira kamar yadda nace ba, ki je ki nema masa auren da kan ki" "Ta yaya ma e zata nemi aure, wannan ai sai su zata ko ƙarya nake yi?" Shiru yayi bai ce mata komai ba. Ta sake kallonsa ta ce "Wai lissafin me kake ta yi haka ne?" "Kuɗin na Zakka ne" ya bata amsa. Murmushi tayi ta ce "Wow, ashe fa lokaci ya kusa, zan yi magana da Turai, a san abin yi a bayar a gidauniyarta" "A'a wannan karon, da kaina za bawa waɗanda suka dace" ya bata amsa kai tsaye. "Kamar yaya, ni ba wanda suka dace ɗin nake bawa ba?" "Wannan karon haka na ga dama" Gaba ɗaya tunda ta dawo, ta kasa gane kan Alhaji Ahmad, gaba ɗaya ya canza, sai wasu muzurai yake yi mata, duk maganar da tayi masa, sai yayi fushi ya hayayyaƙo mata abin da ba yayi mata. "Wai ni Ahmad me kake nufi da ni ne? Babu damar nayi Magana sai ka hauni da masifa, kana wani cika kana batsewa me nayi maka ne? To bari na gaya maka, kuɗin zakkar nan ba wanda za a bawa wallahi, ga in da aka saba bayarwa duk shekara, kawai wannan karon kace ba haka ba". Bai ce mata uffan ba, ya tashi ya bar mata wajen. Hajiya Zainab ta sako shi a gaba da tijara kala kala, ta yau daban ta gobe daban, ta tsiri salo salo na rashin mutunci. Hakan ya ƙara rura wutar sanya shi ya koma ya bar mata gidan. Amina ta makaranta, ya biya yayi mata sallama ya tafi, aikuwa sai da tayi kuka. Abin da ya faru tsakanin Hajiya Zainab da Alhaji Ahmad, ba ƙaramin ɗaga mata hankali yayi ba, tsawon shekarun da suka shafe a tare, bai taɓa mata abu makamancin haka ba, ya kan yi fushi wasu lokutan, amma ko tayi laifin shi me yake bata haƙuri. Duk abin da ta ce ayi shi yake yi, amma a wannan karon, gaba ɗaya ya sauya mata, sai wani ji da kai yake yana hura hanci. Da fari tayi tunanin ta gaya wa su Hajiya Turai, amma sai taga yin hakan kamar ta faɗo ne da nuna gazawa, ace kamar ita miji ya yiwa wulaƙanci, dan haka ta ƙudurce zata ɗau mataki da kanta. A yau ne su Fadila suka koma makaranta suma, domin cigaba da karatun sabon zango. A wannan karon ma, da result ya fito babu mai grade ɗin Yazid, shi da wani ɗan level 4 duk department ɗin babu mai grade ɗin su. A wannan karon ranar da aka dawo makaranta, ranar Yazid ya dawo shi ma, sai dai yayi ƙalau da shi ya ƙara haske ya ƙara kyau. Tun kallon farko da yayi mata, lokacin da ya shigo ajin, ya hanzarin kawar da kansa, a ransa yake faɗin "Tubarkallah, masha Allah". Tayi masa kyau sosai da sosai. Babu wanda ya kula wani, ƙarewa Yazid yi kamar babu wata alaƙa da ta taɓa shiga tsakaninsa da ita. Kusan wata guda kenan an shiga na biyu, da komawar Daddy Lagos, Amma duk da yadda Amina ta mayar da hankali a kan karatunta, amma tana jin kewar Alhaji Ahmad sosai da sosai. Sai dai kusan kullum cikin waya suke. Yana cigaba da kwantar mata da hankali yana rarrashinta. Ya zo gari sau ɗaya cikin Azumi suka haɗu da Amina, ba tare da kowa ya sani ba, sai guards ɗinsa na ɗayan gidan. Kwanansa biyu idan Amina ta tashi daga makaranta sai ta tafi wurinsa,tayi masa girkin abin shan ruwa, sai bayan an sha ruwa ta tafi gida, sai ta yiwa Baba ƙaryar cewa tana gidansu Azima. Kafin Daddy ya koma, ya tura mata kuɗi masu yawa a account ya ce ta sai kayan salla. Hajiya Zainab ta sha mamakin rashin nemanta da Alhaji Ahmad bai yi ba, tun da ya tafi ko flashing bai yi mata ba, sai dai ya kira Fadila. Ita ma kuma Hajiya Zainab girman kai ya hanata kiran sa a waya. Shiru² bai dawo ba ba suyi waya ba, balle su sake tattaunawa a kan Auren Khalil. Tuni Amina kuma sun riga sun gama Waec, Neco suke facing, ana ta yi musu lesson a makaranta. Yau Asabar ce amma zata shiga makaranta, suyi karatu. Har ta fito falo, Hajiya Zainab ta dubeta ta ce "Ina zaki?" Amina ta ce "Makaranta ne ake nemanmu, muna ta shirin fara jarrabawa" "Babu in da zaki, baƙi zan yi girki zaki yi mini" Haushi ne ya kama Amina ta kalli Hajiya Zainab ta ce "Wallahi bana jin daɗi, kuma zuwana makaranta yana da muhimmanci". "Ke ta shafa, na gaya miki aiki zaki yi mini, idan kika fita kuma zaki ga abin da zan miki" ta wuce ɗakinta ta bar Amina a falon. Tana shigewa sashenta, Amina ma ta sa kai tayi ficewarta. Dan yanzu kawai tana ɗagawa Hajiya Zainab ƙafa me, amma ta fara ƙulewa. Kuma bata tsoronta. Baba baya nan yaje ƙauye, tun da aka yi Azumi bai je ba, har salla aike kawai ya yi musu, dan haka a Wannan karon ya samu damar zuwa. Amina tayi tafiyarta makaranta. Ba tare da sake bi ta kan umarnin Hajiya Zainab ba. Fadila tana ganin Yazid, amma yadda baya kulata, haka ita ma ba kulashin take ba, duk da hakan yana damunta kuma tana da burin taimaka masa kamar yadda tayi niyya da farko. Hankali kwance Amina ta dawo gidan, kamar ta dawo gidan ubanta. Kasancewar ba kowa a falon, ta wuce sashinsu, ta yi wanka ta nemi wuri ta kwanta, dan kwanan nan ta kasa gane kanta. Ta so tabi Baba ƙauye, ko ta ɗan sarara da masifar Hajiya Zainab, amma ba zai yiwu ba, saboda wannan jarrabawar da take gabanta. "Amina" Hajara ta kira sunanta lokacin da ta shiga ɗakin. Amina ta ɗaga kai ta kalleta ba tare da ta ce mata komai ba. "Ki zo Hajiya na kiranki" Amina tayi tsaki sannan ta ce "Ina zuwa" Ta miƙe a hankali, tana jin yadda mararta ke ƙullewa tana saki, wanda alama ce ta a kowane lokaci tana iya ganin period. Ko gezau ba tayi ba, da tayi arba da idon Hajiya Zainab da ke jifanta da wani irin mugun kallo, ga Fadila ita ma a tsaye a falo. Ta ƙarasa in da suke tana ɗan yamutsa fuska ta ce "Gani" "Ke! Me nace miki ɗazu da zaki fita?" Hajiya Zainab tayi tambayar kamar ta mari Amina. "Ai da kika sakani aikin na baki uzurina, baki taɓa sakani aiki na ƙi yi miki ba, komai wahalarsa komai gajiyar da nayi ba, a karo ɗaya dai ai ya kyautu kiyi mini uzuri". "Ke! Ni kike gayawa haka? 'yar ƙauye matsiyaciya, ni zan saka ki aiki ki fice ki ƙi yi mini, sai ka ce kina gidan ubanki, to tattara kayanki zaki yi ki bi matsiyacin ubanki da be koya miki tarbiyya ba in da kika fito, tun da baki da mutunci baki iya cin arziki ba,. Shashasha 'yar talakawa" Cikin dakewa Amina ta ce "Ina Arzikin yake, ai ban ganshi ba, kuma kar ki sake zagar mini uba, dan ya bani tarbiyyar da kika gaza bawa naki 'ya'yan. Buɗe baki Hajiya Zainab tayi, ta kasa magana, ita tsoro da mamakine ma suka cikata. Fadila ta rikice ta ce "Ke Mummyn kike gayawa haka? Ba 'yar matsiyatan ba ce ke? To wallahi sai kin bar gidan nan" Hajiya Zainab ta ce "Gaskiya ne, da aka ce ɗan ƙauye bai iya samun wuri ba, ke jeki watso mini kayanta ta zo ta bar mini gida" "Idan kin mutu ayi miki gammo, ki ɗora gidan a ka ki tafi kabari da shi. Haba tunda na zo gidan nan nake muku bauta, amma kullum cikin zagina kuke da cin mutunci, idan na tafi ki samu kofin ruwa ki haɗiye gidan. Kuma Allah ya isan Babana cin mutuncin da kuke masa ba yau ba gobe. Zan bar miki gidanki amma zaki ga abinda baki tsammani ba, saboda zan tabattar miki GABA DA GABANTA, kuma maganin biri karen maguzawa" Amina tayi maganar rai a ɓace, da alama ta daɗe tana jiran Irin wannan damar. Ta juya zata bar falon, Fadila ta saka hannu ta fizo Amina a hasale, da niyyar ta kwaɗa mata mari, amma kasancewar jikin Amina  babu ƙwari ya sanya ta faɗi, kanta ya bugu da Centre table. Ba zafin buguwar da tayi ne ya ɗaga mata hankali ba, wani irin ƙullewa da mararta tayi ne, ta sanya ta zuba wani uban ihu ta rintse idanunta. Saroro Hajiya Zainab da Fadila suka yi, ganin Jini yana gangarowa daga jikin Amina ya fara gudu a tsakar falon!!! AYSHERCOOL 08081012143GABA DA GABANTA NA AISHA ADAM AYSHERCOOL Watpad@ ayshercool7724 Arewabooks@ ayshercool7724 56 Wani irin gumi ne yake tsatstsafowa daga goshin Amina, duk da yadda sanyin Ac ya bawa ɗakin sanyi. Ta riƙe cikinta tana jujjuya kanta, saboda yadda take jin wani abu yana dunƙulewa a cikin mararta. Ita kanta tayi mamakin yadda jini yake fita daga jikinta, dan bata taɓa period a haka ba. "Ke Hajara!" Mummy ta kwaɗawa Hajara kira. Da sauri Hajara ta fito, sai dai tayi turus da ganin halin da Amina ke ciki. Cikin ƙyama Hajiya Zainab ta ce "Janye mini ita daga nan, karta cigaba da ɓata mini wuri ki zo ki gyaran Wannan ƙazantar da tayi" A rikice Fadila ta ce "Mummy, kalli fa yadda take zubar da jini, anya ba za a kai ta Asibiti ba, kar fa wani abu ya sameta" A hasale ta ce "To ya sameta ɗin mana, ina ruwana ba yanzu a gabanki ta gama ci mini mutunci ba, ko sharafa take zata mutu sai ta bar mini gidana yau. Ke ba zaki janye mini ita bane!" Ta yiwa Hajara maganar cikin tsawa. Hajara taje kan Amina, zata ɗagata amma ta kasa, Amina ta riƙe hannun Hajara hawaye na zubowa daga idonta. "Hajara zan mutu, wani abu na yawo a marata, dan Allah ki taimaka mini, ki kira mini Baba kar in mutu in nemi yafiyarsa kar in mutu" Hajara ta ce "Daure ki tashi, kinga kina ɓata wurin" "Ba zan iya ba Hajara, cikina ciwo yake mini, wani abu ne ya dunƙule a ciki" "Daure dai ki tashi, na rakaki ki gyara jikinki" Amina ta yunƙura ta tashi, amma jinin ya cigaba da zubowa, Amina ta kuma durƙushewa, tana jujjuya kai. "Mummy this is serious fa, you have to do something, duk abin da ya sameta fa ni za ace, ni ban taɓa ganin period ya yiwa mutum haka ba, dan Allah kiyi wani abu a kai" "Ni me zan mata, ba abin da zan yi mata, koma menene ya lafa mata ta kwashi kayanta ta bar gidan nan, idan ma pretending take yi, ta gama ta bar mini gida" "Mummy ba pretending bane, tayaya mutum zai dinga zubar da jini haka, bari na kira Doctor Aliyu ya zo ya dubata, kan wani abu ya sameta kar jininta ya ƙare ta mutu" Sai kuma jikin Hajiya Zainab yayi sanyi, dan ita ma jinin ya bata tsoro. Ta ce "Shikenan, ki kirashin" Da ƙyar Hajara ta iya kai Amina ɗaki, ta shiga banɗaki, ta cire kayan jikinta, sai dai abin da ya ƙara tsoratar sa ita bai wuce yadda jinin yake zuba da guda-guda ba. Amina ta waro ido tana tunanin wani irin ciwo ne haka yake damunta. Ta kalli mudubin da yake banɗakinta, taga yadda gefen goshinta ya kumbura, saboda buguwar da tayi, wurn sai zafi yake yi mata, ga kanta da yake mata ciwo dama tun kan hakan ta faru. Ji tayi jiri ya fara ɗibarta, dan haka ta nemi wuri ta zauna, tana addu'a a zuciyarta Allah ya sa ba wani mugun ciwon ne yakamata ba. Tunani ta dinga yi, tunda Hajiya Zainab ta koreta, ta tafi gidansu Azima tayi zamanta, zuwa lokacin da zata kammala Neco, ko ta zauna a gidan Alhaji Ahmad, ta ƙarasa jarrabawarta, kuma ta kanainaye shi ta hana shi zuwa inda Hajiya Zainab ɗin hake. Duk da halin ciwon da take ci, sai da tayi ƙwafa ta ce "Zaki ga tsiya, zaki ga matsiyaciya 'yar ƙauye kuma 'yar talakawa, idan takenki rashin mutunci, da kuma wulaƙanta ɗan Adam, zan nuna miki gaba da gabanta, zan rama abin da kike mini ni da mahaifina hankali kwance, da ni kike zancen". Jiki babu ƙwari, ta wanke jikinta, ta fito tana bin bango, ta shiga ɗaki ta saka pad, ta saka wata rigar ta nemi wuri ta kwanta, saboda a zaune ma jirin take ji. Hajara taje ta zage, ta gyara wurin da Amina ta ɓata da jini, Hajara ta fara zargin wannan jinin kuwa ba ɓari Amina tayi ba. 'Innalillahi wa innalillahi raji'un, idan haka ne yarinyar nan ya babanta zai ji? Gaskiya wannan lamari akwai matsala, da rabon asiri zai tonu. Da Hajara ta fara jin tausayin Amina saboda yarintarta kuma ɓari ba abu ne mai sauƙi ba. Wata zuciyar ta ce "Shegiya ai Allah ya ƙara mata, ba dai ta san ta liƙe wa namiji ba, ga sakamako nan ai" Fadila ta kira doctor Aliyu a waya, ta sanar masa, ya ce mata baya kusa, amma da zarar ya dawo zai ƙaraso. Hajiya Zainab ji take kamar a kanta Amina take, saboda rashin kunyar da tayi mata, so take ta koreta a ƙasƙance cikin wulaƙanci da tozarci. Amina kuwa abu cigaba yayi, babu sassauci sam, tun da take ciwon mararta idan za tayi al'ada, ba ta taɓa wanda ya gigita kamar wannan ba, kuma haryanzu jinin bai daina zuba sosai ba. Juyi kawai take yi a kan katifar, tana taune leɓenta na ƙasa, ƙarshe ta kasa jurewa ta fashe da kuka, sai juyi take tana kuka. Bayan Fadila ta gama wayar, ta dawo falo ta tarar da Hajara tana kunna turaren wuta, saboda ya ɗauke ƙarnin jinin da Amina ta zubar. Cikin damuwa Fadila ta ce wa Hajara "Nace ya jikinta, tana cikin hayyacinta dai ko? Kuma jinin ya daina zuba?" Saboda gaba ɗaya Fadila gani take, wannan faɗuwar da Amina ta yi ne ya haddassa mata wannan zubar jinin. Hajara ta ce "Wallahi ban sani ba, bari naje na gani amma" ta tafi sashinsu dan duba Amina. Ta tarar da ita, tayi ruf da ciki sai kuka take, tana kiran sunan Allah, tare da kiran Wayyo Allah Babana zan mutu, Daddy cikina". "Au ke dan jaraba kina cikin wannan halin, amma kina kiransa bayan shi ya jefa ki a wannan halin, ko ince kika biye masa" Hajara ta faɗa cikin jin haushin yadda Amina ke kiran Daddy. Amina ba ta gane me Hajara take cewa ba, ta cigaba da kukanta. Hajara ta taɓe baki ta ce "Jinin ya daina zuba kokuwa" nan Amina tayi shiru ta cigaba da kukanta. Ganin Amina bata da niyyar kulata, ya sanya ta koma falon ta samu Fadila ta ce mata "Gaskiya dai tana cikin ciwo sosai, nayi mata magana ma bata kulani ba sai kuka take yi" "Na shiga uku, amma dai tana numfashi ko?" Hajara a ranta ta ce 'Eh ashe kina tsoro dai" amma a zahiri ta ce "Ai har kuka take yi, tana numfashi" "Ok shikenan na gode" Fadila haka halayyarta take, duk rashin mutuncinta bata son taga mutum ba shi da lafiya duk sai ta shiga damuwa da tashin hankali. Hajiya Zainab kuwa ko a jikinta, ta cigaba da sabgoginta. Fadila kuwa ta kasa zaune ta kasa tsaye, ta dinga kiran Doctor Aliyu a waya, hanklinta bai kwanta ba sai da ya zo. Yana zuwa ta saka Hajara ta kamo Amina, ta fito da ita falo. Ya ɗan ƙarewa Amina kallo sannan ya ɗan yi mata tambayoyi. Hajiya Zainab ta fito falon ta na jiran me Doctor Aliyu zai ce, ya gama ta bawa Amina kuɗin mota ta tafi ta bata wuri. Doctor Aliyu ya ce "Gaskiya ta ɗan galabaita, jikinta yayi weak sosai, zan bata magunguna nayi mata allurai, zan rubuta mata scanic, da test taje tayi, gobe in Allah ya kaimu da safe zan dawo sai in duba". Hajiya Zainab ta ce "Ban gane scanic ba, na meye scanic ɗin? Meya haɗata da scanic kuma?" Doctor Aliyu ya ce "Ai dole ayi mata scaninc, aga musababbin zubar jinin, kin san akwai cututtuka da yawa da sukan kama mahaifa, dole a gano meye musababbin zubar jinin haka" 'Kaga ni ba wannan ne a gabana ba, kayi mata abin da zaka yi mata, kuɗin mota zan bata ta tafi garinsu ta bar mini gida". Doctor Aliyi ya kalleta ya ce "A wannan yammancin? Baki ga yadda jikinta yayi bane? Idan wani abu ya sameta a hanya fa? Kamata yayi fa tun a lokacin ku kaita Asibiti, ta kwana a can bai kamata ma a barta a gida ba, kiyi haƙuri a gano meke damuntax Amina ba ta ce komai ba, sai lumshe ido da tayi, a ranta ta ce "Ji Azzaluma, kamar ba ke da 'yar ki ne ya sanya koma menene ya faru da ni ba, ai wallahi ba in da zanje sai na warke' Fadila ta kwantar da murya ta ce "Mummy, tun da likita ne yayi suggesting ɗin ya zauna, kiyi haƙuri a fara gano matsalar tukuna" Da ƙyar ta haƙura ta ƙyale Amina, yayi wa Amina allurai, ya bata magunguna ta sha, nan da nan wani wahalalalen bacci yayi awon gaba da ita. Da magariba, Hajara ta taro napep ta saka Amina suka tafi yin scanic ɗin, Amina da kuɗi a wurinta ta biya kuɗin, da ɗaya test ɗin ya rubuta duk aka yi mata. Baya biye son sanin meye a test ɗin ba, suka karɓo result suka dawo gida. Da daddare tana jin ringing ɗin wayarta, ta san kuma Daddy ne yake kiranta, amma ta ƙi ɗagawa dan data ɗaga zai gane bata da lafiya ya tashi hankalinsa. Shi kuwa Daddy jikinsa ne ya dinga bashi kamar akwai wani abu na faruwa mara daɗi, shi ne yake ta kiran Amina, amma bata ɗaga ba. Sai ya koma ya nemi Fadila a waya, ta ɗaga kiran suka gaisa. Ya tambayeta ba dai wata matsala a gidan komai lafiya? Sai da gabanta ya faɗi, amma ta ce masa ba matsala ba komai. Da daddare da ƙyar Amina ta iya cin Abinci, duk jikinta babu ƙwari kuma ba ta daina zubar da jinin ba, sai dai ba yawa kamar da haka yake zuba. Wurin ƙarfe goma na safe, Doctor Aliyu ya zo, Hajara taje ta kira Amina, ta kira Fadila. Doctor ya karɓi tes da scanic, ya duba ya kalli Amina da ta ɗashe, ya maida idonsa kan Fadila ya ce "Kira mini Hajiyar" "Ba dai wata matsalar ce ba ko Doctor?" "Eh ba matsala, kije ki kirawo ta dai" Amina ta kalli Doctor Aliyu jiki a sanyaye ta ce "Doctor ba dai wani abu ne ya sameni ba ko?" Ya ce "Eh kar ki damu". Ya shafe kusan mintuna Ashirin yana jira, sai gata ta fito, ta falon ta zo ta samu wuri ta zauna. "Hajiya ina kwana?" "Lafiya lau doctor, ya gida ya aiki?" "Alhamdilillah ya mai jiki?" "Gata nan ka tambayeta mana" ya ɗan girgiza kai ya ce "To, sakamakon dai jininta yayi ƙasa gaskiya, sai dai akwai buƙatar a yi mata ƙarin ruwa da magunguna in Allah ya yarda komai zai zama normal, sannan sacanic ɗinta ya nuna, ɓari ne tayi kuma akwai saura, sai an yi wankin ciki" Hajiya Zainab ta kalleshi kamar tana kallon soko ta ce "Ban gane ɓari ba, me ta ɓarar ne?" "Hajiya ɓari dai na ciki, wata biyu da kwana Ashirin da huɗu" Ras! Gaban Amina ya faɗi, amma ta dake ba ta nuna girgizar a fili ba. "Kana nufin cikin shege kenan?" Doctor Aliyu ya ya ce "Bana ce ba, tun da ban san a yadda aka same shi ba" Tafa hannu ta shiga yi tana salati, tana kallon Amina, Fadila kuwa tamkar an dasata haka tayi saroro tana kallon Amina, tana mamakin me Amina ta sani har taje tayi ciki, ko ita da take kusan shekaru Ashirin da huɗu ba tayi Aure ba, bata yi abin da Amina tayi ba. "Wallahi ba a gidana ba, idan ranki ne yake fita yana dawowa sai kin bar mini gida a yanzun nan ba sai anjima ba. Daga ɗakkoki cin arziki kizo ki ɓata mini sunan zuri'a, dama ba makaranta kike zuwa ba yawon iskanci kike?, wallahi tashi sai kin bar mini gida". Doctor Aliyu dai sallama yayi musu, ya kwashi kayansa ya tafi, tare da ba su shawarar su kaita Asibiti. Cikin hargowa da hayagaga Hajiya Zainab ke masifa "Tashi sai kin bar mini gida wallahi, Munafuka 'yar iska" Amina ta lumshe idanunta tana jin zafin maganganun Hajiya Zainab, da yadda suke sukarta a zuciyarta. "Ki tashi ki tafi gidan ubanki nace" Amina ta ce "Ko baki koreni ba zan tafi, amma akwai buƙatar ki san wake da alhakinsa" "Ina ruwana da ko na ubanwaye? Lokacin da ki ka kai kanki na sani ne? Tashi wallahi sai kin bar mini gidana a yanzun nan, tashi kije ki haɗo tsummokaranki ki fita, lumbu lumbu wutar ƙaiƙayi, kin ƙunso masifa da abin kunya zaki zauna mini a gida, gara da Allah ya toni asirinki ai" Amina ta miƙe a hankali ta tafi sashinsu, Hajiya Zainab ta cigaba da yaɓa mata maganganu marasa daɗin ji. Ita dai Fadila kasa magana tayi, gaba ɗaya jikinta yayi sanyi. Amina na zuwa ɗaki, ta rufe ƙofar ɗakinta, ta kira Daddy a waya ta sanar masa da abin da yake faruwa. Hajiya Zainab kuwa sashinta ta koma tana bala'i, tana cigaba da kwashewa Amina albarka. Kiran Alhaji Ahmad ta gani, kamar ta share shi, saboda tunda ya sa ƙafa ya tafi, bai sake bi ta kanta ba. Ta ɗaga wayar ta kara a kunneta tana ta huci ba tare da tayi magana ba. "Lafiya dai ina magana kika yi shiru?" "Ehh, dole ka tambayeni mana, tunda sai yau ka ga damar kirana tun da ka tafi" Cikin hikima da son bugun cikinta ya ce Ya ce "Wait, huncin me kike yi haka ne?" "Ba dole nayi huci ba, ka san yar iskar yarinyar nan, 'yar gidan wannan mutumin banzan, yawo take yi?" "Yawo kamar yaya?" "Jiya na sakata aiki, tayi mini rashin kunya, daga Fadila ta ture ta ta faɗi, shikenan jini ya ɓalle ashe cikine da ita har wata biyu" Daddy ya ce "Subhanallah, ita Fadila waye ya aiketa, da da ƙarar kwana fa ta janyowa kanta wata matsalar?" Ta ce "Ai gara da hakan ta faru, Allah ya tona mata Asiri, da tuni yadda ta ƙunso abin tsiyarta haka zata raine shi a gidana, to a yau zan bata kuɗin mota tabi ubanta in da suka fito" Alhaji Ahmad ya ce "No, ba za ayi haka ba, tun da mahaifinta baya nan bai kamata ayi masa haka ba, idan aka yi haka ba ai masa adalci ba, ki bari in dawo gidan muga abin da yakamata ayi" "Ban gane me kake nufi ba, ka dawo kayi me, wallahi sai ta bar mini gida, ina ruwana da babanta ba zai ji daɗi na, ta san da hakan ba ta tausaya masa ba taje take iskanci" Daddy ya ji zafin maganganun Hajiya Zainab, amma ya dake ya ce "Zainab, nima uba ne, kuma na haifa idan wannan tsautsayin ya faru a kan tawa 'yar aka yi mini haka, ba ayi mini adalci ba, ki bari zan zo gidan da kaina" "Allah ya sauwwaƙe ya faru a kan 'yata, sai dai a kan irinta ga rashin gata ga rashin tarbiyya da watsewa" Gaba ɗaya ya kasa controlling ɗin Hajiya Zainab. Ƙarshe sai katse kiran yayi ya kira Amina a waya. Ta ɗaga wayar tasa tana ta ƙoƙarin haɗa kayanta. "Meenal, kina jina kiyi haƙuri ki bar mata gidan, kar ta illata mini ke, ki jira a waje, zan aiko a ɗauke ki, kije can gida ki jirani, zan dawo anjima in sha Allah, komai dare zan kai ki Asibiti, ki kwantar da hankalinki kin ji Dearna, komai zai tafi daidai, amma dan Allah karki gayawa kowa komai" A taƙaice Amina ta ce "Shikenan" hargowar Hajiya Zainab ta cigaba da jiyowa, tana tunkaro ɗakinta. Dan haka ta miƙe, tana jin jiri ta saka hijjabinta, ta ɗau wayarta da jakarta ta nufo hanyar fita tana dafa bango. A corridor suka haɗu da Hajiya Zainab, ta kalli Amina a wulaƙance ta ce "Ina zaki je ki bar mini kayanki, ki wuce ki kwaso tarkacenki ba zaki bar mini dauɗa da ƙazanta a gida ba, Allah wadaran halinki" Amina ta kalleta ta ce "Ki daina zaƙewa a kan abin da baki sani ba, kar ki zo kiji kunya, wataƙila abin da kike kira da ƙazantar yana da alaƙa da gidanki, ma'aikatanki ko kuma wani makusancinki. Yanzu idan na kai ƙararku a kan sanadin salwantar cikina ko da yake na gaba da alfatiha ne, sai an bi mini hakkina saboda kun taka doka" "Ke kina da arziki ko madafar da zakiyi jayayya da ni, matsiyaciya kamarki me kike da shi me kika bawa wani ajiya. Karki fasa kaimu ƙarar, kuma can kije ki nemi wanda yake da alaƙa da abin kunyarki bani ba, fisararriya, ni banda kar inje ki mace mini, da saina tuburbuɗa miki jikinki kan ki bar gidan nan, karuwa kawai" "Na gode, sai dai ki sani kamar yadda na bar kayana a gidan nan, ina nan dawowa tare da wanda yake da alaƙa da cikin, Ɗanki ko kuma wanda baki zata ba, kuma dole ki karɓemu tun da mai faruwa ta riga ta faru" "Ƙarya kike yi, ni ban haifi ɗan iska ba, babu abin da ɗana zai yi dake ƙazama kamarki, fice ki bar mini gida munafuka" Amina ta bi hanyar falo, ta fice. Tausayin Amina ya kama Hajara, taji kamar ta bi bayanta, dan bata san ina zata je ba. Amma taji tsoron kar daga nan Hajiya Zainab ta ce ita ma ta bita. Tana zuwa ƙarshen layin, bata wani daɗe ba, mai ɗaukarta ta ya zo, ya ɗauketa ya kai ta can gidan Alhaji Ahmad. Sai wajen ƙarfe shida Alhaji Ahmad ya dawo gida, gaba ɗaya a ruɗe yake cikin tashin hankali ya isa gidan nasa. A bedroom ɗin da suka saba zama ya tarar da Amina a kwance. Da sauri ya ƙarasa gaban gadon yana kiran sunanta. Ya ɗagota jikinsa, fuskarta duk ta ɗashe tayi wani iri. Nan da nan ya ɗauketa suka tafi Asibiti, Asibitin da ta taɓa rakashi, yaga likita. Suka sake duba Amina, suka tabattar masa cikin ya riga ya lalace, zasu bata magani sauran ma ya ƙarasa fita, idan bai yi ba kuma sai sun mata wankin ciki. Amina ta sha wahala sosai a kan ɓarin nan, suka dinga sakamata ruwa da allurai. Tana kwance a kan gadon marasa lafiya, ga ruwa a saƙale, Daddy na kusa da ita a kan kujera, ya riƙe hannunta a nasa. A hankali ta buɗe ido, ta farka daga nanauyan baccin da tayi. Ta kalleshi ta ce "Daddy baka tafi ba?" "Eh Meenal, idan na tafi wa zai kula mini da ke?" "Daddy na sha wahala sosai" "Na gani Meenalina, Allah ya ƙara miki sauƙi, ina fatan yanzu ba kya jin ciwon komai?" "Bana jin ciwo yanzu, jikina ne ba ƙwari sosai" Daddy ya ce "Bari in ɗagaki in baki Abinci" Tayi murmushi ta ce "Zan iya tashi ai" "No bari in taimaka miki" ya ɗagota zaune, ya jinginar da ita, ya zauna ya dinga bata Abinci da kansa. Ƙarshe dai shi ya kwana da Amina a Asibiti. Wajen sha ɗaya saura, aka sallamosu da ga Asibiti, jikinta yai sauƙi sosai jinin ya tsaya sai abin da ba a rasa ba. Bai wuce da ita ko ina ba, sai gidansa. Hajara ce ta fara ganinsu, sun dawo tare, Hajara ta ce "Lallai yau mutumin nan ya shirya bala'i a gidan nan" Amina ta zauna a falo, ya ce mata yana zuwa, Hajara kuma ta shigo tana yiwa Amina sannu, tana son tambayarta ya aka yi amma taga Amina ta tsuke fuska. A ɗaki ya tarar da Hajiya Zainab, tana ta shirin fita yawonta. Ta kalleshi ta ce "Daga ina haka?" Bai amsa mata ba ya ce "Zainab bance miki karki kori yarinyar nan ba?" Ta kalleshi ta ce "Na koreta ɗin, nawane kuɗin ubanta a cikin kuɗin daka haɗa ka gina gidan, me zata zauna tayi mini?" Ya ce "Tun da gina ne, na dawo da ita, ba zata bar gidan nan ba sai mahaifinta ya zo, zan danƙa masa 'yar sa" Hajiya Zainab ta daki mudubi ta ce "Wallahi ba a gidana ba, kaje can ku haɗu a titi ya karɓi 'yar ta sa" Ta yi waje ta fice daga ɗakin. Bayanta ya bi yana kiran sunanta, bata saurareshi ba, ta ƙarasa falo. Ta sha mamakin ganin Amina a falon. "Ke bance ki bar mini gida ba? Meya dawo da ke?" Amina tayi shiru tana binta da ido. "Zainab ki nutsu ki bi komai a hankali dan Allah" "Ba zan bi koman a hankali ba, wannan mara mutuncin da jiya kamar zata dokeni, Wallahi sai ta fita" tayi maganar cikin tsawa. Jin hayaniya ya sanya Fadila fitowa, ta tsaya tayi saroro tana ganin ikon Allah. Ta sake kallon Daddy ya tareta daga kaiwa ga Amina ta ce "Wai Ahmad, meye alaƙarka da uban yarinyar ne? Ba fa zata zauna mini a gida da najasa ba, tayi ɓarin shege nan gaba haihuwa za tayi, wallahi sai ta fita" "Ba zata fita ba, babu in da zata je?" Yayi Maganar cikin fushi. "Saboda me zata zauna mini a gida?" "Saboda ba a waje tayi cikin ba, yana da alaƙa da gidan nan, dan haka ba zai yiwu wannan abu ya faru ba sannan a tura masa 'yar sa a haka ba, idan aka yi haka ba ayi masa adalci ba, gara komai zai faru ya faru" Ɗan saroro tayi tana kallonsa ta yi ƙasa da muryarta ta ce "What do you mean?" Ya ɗan yi shiru sannan ya ce "Am responsible of it" Ƙara Fadila ta saki, saboda jin maganar ta diro ta in da ba ta zata ba, gaba ɗaya suka waiwaya, dan basu san ta shigo falon ba. AYSHERCOOL 08081012143GABA DA GABANTA NA AISHA ADAM AYSHERCOOL Follow my Arewabooks account through this link. https://arewabooks.com/u/ayshercool7724 57 Cikin tsawa Daddy ya kalli Fadila ya ce "Get out from here" Saboda gaba ɗaya bai san Fadila tana falon ba. Jiki na rawa ta juya ta bar falon, tana jin tamkar mafarki take yi, tana tantamar anya kuwa Daddy ya san meyake faɗa?. Tsatstare Alhaji Ahmad Mummy tayi da ido, ita bata motsa ba kuma ba ta ce masa komai ba. Shi ma kallon nata yake yi, domin yaga wani mataki zata ɗauka. "Zainab" ya kira sunanta, ba ta bari ya faɗi wani abu ta ɗaga masa hannu ta dakatar da shi, ta kalli ƙwayar idonsa ta ce "Ahmad, ka bari in gama nazartar ka ko Allah zai sa in gano wace irin ƙwaya ka fara sha mana, ko kuma in ce giya ka san abin da kake gaya mini kuwa?" "Na sani, bani da wani da zaɓi da ya wuce na gaya mikin, cigaba da ɓoyewar ba shi da amfani" "Lallai ka riƙa wuyanka ya isa yanka, kai saboda rashin kunya sa rashin sanin darajar kai ka tsaya a gaban ka kalli tsabar idona kake gaya mini ka yiwa mai aikin gidana ciki?" "Idan na ɓoye miki, ai ba zan ɓoyewa Allah ba" "Ta tabbata kenan kai ne ka yi mata cikin?" Tayi maganar tana nuna Amina, da ke bayan Daddy a tsaye. Alhaji Ahmad ya daidaita tsayuwarsa ya ce "Dan Allah Ki tsaya ki fahimceni, kuma ki mini adalci kafin ki yanke mini hukunci". "Rufe mini baki munafuki, mara mutunci ni zaka tonawa asiri ka ciwa mutunci a idon duniya? Ka haɗa jiki da wannan kucakar ƙazama jahila 'yar ƙauye ka dawo ka haɗa jiki da ni Ahmad?. Ashe shiya sa kake ta nan nan da ita, na kaɗa na raya ka canza mata makaranta kaƙi, ka dinga tsiro mini da rashin mutunci da wulaƙanci kala kala, ashe wannan 'yar abar ka samu ka liƙewa kake bibiya" Amina dai ta kashingiɗa tayi shiru da ita, jin Hajiya Zainab ta kirata da 'yar aba ne ya sanyata yin murmushi a ranta ta ce 'Lallai 'yar aba ta baki mamaki ai GABA DA GABANTA'. Fadila da bata riga ta gama barin falon gaba ɗaya ba, ta zube a ƙasa ta toshe bakinta tana kuka, wannan wane irin abu ne Daddy ya janyo musu, su basu ɗauko masa magana ba sai shi da girmansa da komai zai yi mus haka?. Ya kalli Mummy ya ce "Zainab ko me zaki kirani da shi, ba zan ji haushinki ba, amma ki bari nayi miki bayanin komai" Cikin tsabar bala'i ta ce "Kai har akwai wani bayni da zai fito daga bakinka in tsaya in saurara? Me zaka gaya mini munafukin Allah wata'ala, wallahi kaji kunya Ahmad, 'yar wannan yarinyar 'yar aikin gidanka, ina ka baro manya manyan karuwan da ke tsakanin Lagos da Abuja da kake zuwa, manyan karuwai da suk ji da kansu, da ka gaza nemansu yadda zanniya gogawa da kowace 'yar bariki kake bi, amma saboda tsabar rashin ta ido irin naka ka rasa wadda zaka bi sai wannan" Ta mayar da idonta kan Amina ta ce Tsinanniya munafuka, dama shi ne wanda yake da alaƙa da cikin ko? Zan nuna miki ƙarshen iskanci da alama baki san wacece ni ba, sai na yi miki abin da ke da ƙara ganin wani ɗa namiji ya burgeki balle ki bibiyeshi har abada, ai ƙaryar iskanci kike yi, zaki san mijina kika bi. Wallahi saina yi miki illar da ko a bola aka yasar da ke ba zaki moru ba". Ƙarar buɗe ƙofar da aka yi ne, ya sanya suka waiwaya suga mai shigowa. Baba ne ya shigo sanye da ash ɗin yadi,yayi kyau sosai, ya shigo bakinsa ɗauke da sallama. "Dakata a nan! Kar ka kuskura ka shigo mini falo, tsohon banza da na wofi. Ashe haɗa kai kayi da 'yarka ka kawota karuwanci gidana take bin mijina wallahi sai nayi maganinku" A fusace Amina ta yinƙura za tayi magana, amma Daddy ya dakatar da ita, ya kalli Baba da jikinsa yayi sanyi ya ce "Malam Hassan ƙaraso mana" "Wallahi ya shigo mini falo, sai nayi masa lahani ya fita ya bar mini gida, kan nayi masa illa" "Zainab wai meye haka ne?" "Ban sani ba, ai ka taro bala'i da masifan da ba zaka iya tarewa ba, son zuciyarka da budurwar zuciyarka sun ranto maka abin da ba ka da yadda zaka biya" ta faɗa tana kumfar baki cikin bala'i. Amina ba ta taɓa zaton bala'in Hajiya Zainab ya kai har haka ba sai yau. Baba dai ya takure a jikin ƙofa, yana kallonsu, Amina kuwa duk ta sha jinin jikinta ta sunkuyar da kanta ƙasa. Wasu dattijai ne suma suka yi sallama a falon. Daddy ya amsa musu, ya na musu sannu da zuwa. Hakan ya bawa Baba damar biyo bayansu ya shigo shima, saboda yadda yaga alamar jikin Hajiya Zainab yayi sanyi da ganin wannan mutanen. Ɗaya daga dattijan ya bisu da kallo, ya ce "Lafiya tsayuwar me kuke yi haka ne? Kai kuma ka taso mu babu shiri" yayi maganar yana kallon Alhaji Ahmad. Amina da ke gefe a zaune a kan Carfet ta ce musu "Ina kwananku?" Suka amsa mata cikin sakin fuska. Daddy ya ce "Eh na kira ku ne, domin a samu a warware matsalar da nayi muku bayani tun a waya." Dattijon ya kalli Hajiya Zainab ya ce "To ki zauna mana, ayi maganar da za ayi" "Wace magana za ayi, ai babu wani abu da wani zai gaya mini a kan abin Kunyar da Allah wadai ɗin da ya aikata" tayi maganar babu girmamawa "Ki zauna dai nace" dattijon ya maimaita mata. Tana wani irin huci ta nemi wuri ta zauna a kan kujera ɗaya. Ɗaya dattijon da tun da suka shigo bai yi Magana ba sai yanzu, ya ce "To muna jinka" Alhaji Ahmad cikin jin nauyi ya kalli Baba  ya ce "Kan nace komai, zan fara da baka haƙuri, a bisa abin da ya faru, na saɓa alƙawari da nayi, amma dan Allah ina neman afuwarka. Ina son zan sanar da abin da ya faru a yanzu kuma Kawu na kiraku ne saboda kune shaida, kuma ga waliyina kuma ga nata na kiraku ne dan kuma ku zama shaida". Ya mayar da idonsa kan Hajiya Zainab, da take ta huci tamkar zata kama da wuta ya ce "Zainab, ina son ki zama mai adalci a duk abin da zan faɗa a yanzu". MONTHS BACK. Bayan malam Hassan ya nemi alfarma a wurin Alhaji Ahmad, na son ya kawo Amina gidan, tayi aiki a dinga biya mata kuɗin makaranta, saboda yana da burin tayi karatu. Alhaji Ahmad ya amince. Akwai wani ɗan garinsu shi ne mamallakin  makarantar Bright future science Academy. Ya yi masa magana, a kan zai kai Amina, yayi masa lissafin duk abin da ake buƙata. Haka kuwa aka yi, aka lissfa masa komai kuɗi kusan har dubu ɗari talatin da wani abu ya biya, ya sanar da Khalil cewa idan ya dawo ya kai Amina makaranta. Bayan Alhaji Ahmad ya koma wurin aiki, ya ma manta da batun an kai Amina makaranta, director ya kira shi a waya. Bayan sun gaisa a waya ne, Director yake ta koɗa masa irin ƙoƙarin da Amina take da shi, da yadda ta basu mamaki a lokacin da aka kawota. Daddy ya ji daɗin cewa yarinyar tana da mayar da hankali sosai, dan haka ya cewa Director yayi masa bill ɗin school fees ɗinta na shekara ya biya, saboda yana son yaga yaro na mayar da hankali a kan harkar karatu. Lokacin da Daddy ya dawo gida, Baba ya dinga yi masa godiya. Ya sa Amina na tayi masa godiya. Amina ita ma har ƙasa ta duƙa ita ma tana yi masa godiya. A dawowar da yayi ya fuskanci Amina 'yar drama ce, ga shegen surutun tsiya kamar radio ko gajiya ba ta yi, amma duk lokacin da zai ganta, zai ganta ne da littafinta a hannu, tana aikinta tana duba littafinta. Abin da ya lura da shi shi ne, a duk lokacin da ta gaishe shi, ya ja mata aji kan ya amsa, sai ta ɗan yamutsa fuska tana tura baki. Abun ya kan bashi dariya wasu lokutan, sai dai ba yayi a gabanta. Ya kan so ya yaba mata saboda yadda ake gaya masa jajircewarta a makaranta, amma sai ya ga to ina ruwansa ma da ita, dan haka ya shareta. Abubuwan Amina na burgeshi wasu lokutan, mussman idan ya zo wucewa ta falo, ya ga suna kallo ita da Hajara, tana yiwa Hajara bayni abin da ake yi a film ɗin idan bana hausa bane ba. Babban abin da ya lura da shi game da ita, shi ne riƙon addininta da kuma dagewa a kan abubuwan da ta saka a gaba, ga uwa uba yadda ƙaunrta ga mahaifinta a baiyane take, tana matuƙar nunawa Baba kulawa. Akwai ranar da zai fita, ya daɗe a mota yana kallonsu, ta zaune tana yankewa Baban farce da kanta, duk da baya iya jiyo me take gaya wa Baban, amma ya fuskanci hirar ƙuruciya take masa yana murmushi. Ranar da yazo ya tarar Hajiya Zainab ta ci mutuncin Baba, wanda hakan ya sanya Amina kuka sai yaji babu daɗi sam. Ya sami Hajiya Zainab a ɗaki,, cikin hikima ya ce "Dear me Malam Hassan yayi miki ne kike masa wannan faɗan?" "Ai ni ban san ma me zance maka ba, nayi nayi da kai ka canza mana mutumin nan ka ƙi, shikenan kullum cikin yiwa mutane shirme" Daddy ya ce "Na ji, amma dan Allah a dinga sassauta masa kinga babb ne, kuma a gaban yarinyar sa ba zata ji daɗi ba, ba zata dinga ganin girmanki ba, kin san iyaye abu ne masu muhimmanci a rayuwar mutum" "Ban gane ba me kake nufi da ba zata ji daɗi ba!" Tayi masa maganar cikin tuhuma. "Babu abin da nake nufi, nufina ɗaya dai ki daina wulaƙanta mahaifinta a gabanta" "Wallahi muddin ba zai daina yi mini shirme ba, nima na zan fasa ba, idan ba zasu iya ba su bar mini gida" girgiza kai kawai yayi ya ƙyaleta, dan idan ya biye mata, sai suyi faɗa. Kwanaki biyu a tsakani, Amina ta gaisheshi ya ƙi amsawa, tana yin gaba yaji ta ce 'Aikuwa ba zan sake gaisheka ba' Bata san maganar ta fito fili ba, amma ya ji ta kawai yayi murmushi ya ƙyaleta. Ba a rufa sati ba, Hajiya Zainab ta sake yiwa Baba wani saukalen rashin mutunci. Har cikin ransa ya ji zafin yadda ya kuma ganin Amina tana kuka, ya fita da safe, ya dawo da yamma, ya tarar da ita a haraba tana karatu, amma idanunta sun yi ja sosai, alamun tayi kuka har ta gaji. Har ya zo ya gifta ta, ya ji ta ce 'Daddy sannu da zuwa" Maimaita Daddy yayi, saboda tun da suke bai taɓa jin ta kira shi da kowane irin suna ba, ranar da ya kamata tana gulmarsa da sassafe a falo, tana yiwa  Hajara kwatance yana ji tana ce mata  maigidan nan, wannan farin mutumin mai gemu, ya fiye iyayi, wai idan a ka kai Abinci dining, sai ya buɗe yana kallon Abincin kamar an ba shi guba, cikin kwaikwayon muryarsa ta ce "A small portion of it" wai dankali za a ɗan zuba masa kamar wani ɗan yaye, kai wannan da saurayi ne za a ga tsari. Wai idan aka kai masa Abinci a flask da safe, wai ba zaki kuma kawo masa shi da rana ba ji fi'ili" Sai da ya ƙunshe baki yana dariya, kasancewar basu san ya fito ba. Amma yau sai gashi ta kira shi da Daddy, har ta manta da tayi masa sannu da zuwa, taji ya amsa da yauwwa ya wuce. Tun daga ranar idan har Amina zata gaisheshi, sai ta ce masa Daddy, shi dai haka nan take burgeshi. Ba in da ta sake burgeshi, sai yadda ta dinga ba shi Abinci da sasafe kan ya fita, idan bai samu damar ci ba, ta bashi ya tafi da shi wurin aiki.   Babban abin da ya lura da shi shine, ita yarinya ce mai son kyautatawa mutane. Daga alkhairan da tayi masa, bai manta lokacin da zai tafi Jigawa ba, ta haɗa masa guzuri wai ko zai ji yunwa a hanya, abin ya daɗe yana bashi mamaki. Danginsa sun yi farinciki da ganinsa, saboda rabonsa da su har sun manta, shima sun san albarkacin ɗaurin Auren da za ayi ne ya zo. Ƙannnen mahaifin Daddy suka saka shi a gaba, suka dinga yi masa faɗa, faɗan dai an saba yi masa shi, a kan rashin zumunci sannan kuma shi babu wanda ha isa ya je gidansa, saboda wulaƙanci na matarsa. Ba abin da Daddy yake yi sai basu haƙuri. Cikin family House ɗinsu ya shiga, cousins ɗinsa mata suka sako shi a gaba, wasu na tsokanarsa wata sabon gani, wasu na masa mitar rashin zumunci. Shi kansa a wani irin nishaɗi ya tsinci kansa, saboda ba abin da ya kai zumunci daɗi. "Engineer wai kuwa an gaya maka mun zo gidanka kwanaki?" Cewar matar ƙaninsa Hauwa. Cikin mamaki Daddy ya kalleta ya ce "Yaushe?" Ta ce "Wallahi mun je, ai mun san babu lallai Hakima ta gaya maka, ni da su Fauziyya mu kusan huɗu, mun zo Kano ka san nan Kano a ka kai 'yar Yayana muka je gidanka, baka nan, muka haɗu da wata yarinya mai aiki, baka ga yadda ta karrama mu ba, da Abinci da kirki amma matar gidan nan na dawowa ba ka ga kallon banza ba da tayi mana, na san yarinyar nan ta sha masifa bayan tafiyarmu, dan ba kaga kallon banza da tayi mata ba" Daddy ya ce "Ikon Allah,Ni kuwa wace yarinya ce haka?" "A gidan dai take aiki, wata mai ɗan ƙaramin baki, tana da ɗan jiki dai, na manta sunanta yarinyar ta karrama mu wallahi sosai da sosai" "Amina" ya furta a hankali ba tare da kowa ya ji ba. Wata gwaggonsa da ke gefe tana jin hirar ta su ta ce "To ko ita zamu aura masa ne, mu samu wurin zuwa ko ma samu mu dinga ganinsa?" Tayi maganar cikin sigar wasa. Daddy ya zaro ido ya ce "Rufa mini asiri, yarinya ce ƙarama fa, bata fi shekara sha shida ba" "Yo to meye, ba aure bane ba?" "A'a kar ki haɗani da Zainab, aini babu agender na sake ƙara aure ta isheni" Gwaggo ta ce "Tafi can, kana zaune mace ta shanye ka, me ake da hali irin na matarka, duk wannan dukiyar taka ko a dangi ka kasa neman wata ka ƙara, dan baƙin ciki ta kanainaye komai ita da 'ya'yanta muguwa" Daddy ya ce "Allah ya baki haƙuri" "Rufe mini baki, ba wani Allah ya ani haƙuri" suka yi ta yiwa Daddy mita, shi dai haƙuri kawai yake ta basu. Yayi musu alkhairi sosai, sannan da yamma ya nufo gida. Kan ya tafi gida, Hauwa ta bawa Daddy turare da nama fal da kaskon turaren wuta, da wasu kayan da aka raba na biki, ta ce ya kaiwa Amina ya ce suna gaisheta. Daddy ya ce 'Hauwa banda neman rigima, ki bani abu na bawa 'yar aiki baki bawa matar gida ba?" "Engeener ita matar gidan da wa ta damu? Ai ni wannan yarinya na sani mai kirki" Haka Daddy ya karɓi kayan, ya yi musu sallama, ya tafi gida. Ko da ya dawo gida Hajiya Zainab bata nan, Fadila kuma tana makaranta. Ya shiga sashen sa yayi wanka, yayi salla, ya fito dining ya ci Abinci. Ya gama ci yana ƙoƙarin barin falo, Amina ta fito da bokiti da mopper, zata gyara falon. "Daddy ina wuni" "Lafiya lau, biyoni mota zan baki saƙo" sai da ta ɗan yi sororo, sannan ta bi shi tana tunanin wani irin saƙo ne haka? Ya ɗan kallta ya ce "Meye ma sunanki?" "Amina Hassan Shanono" shi da ya tambayi sunanta har da ƙara masa da sunan mahaifinta da garinsu. Wata babbar leda ya bata Sannan ya ce "Gashi, baƙin da suka zo rannan ne, suka bani kayan biki suka ce a baki" "Wane baƙin?" "Matan da suka zo su huɗu, ki ka yi musu girki" Ta yi murmushi ta ce "Au, na tuna masu yara ko?" Ya gyaɗa mata kai ya ce "Sunce a baki" Ta saka hannu biyu ta karɓa ta ce "Na gode sosai, Allah ya saka da alheri" Kai tsaye daga wurinsa Wurin Baba ta wuce, taje ta nuna masa. Ya ce an gode madalla, ta ɗebar masa sauran taje suka yi ta ci ita da Hajara. Ta bata abin da zata bata ta ajiye sauran. Watarana cikin Daddy yana bacci, ya farka jikinsa babu daɗi, ƙafafuwansa sun yi zafi kamar wuta, sun samu saɓani da Zainab ranar, saboda shegen yawonta dan ko Abincin dare bai ci ba ya kwanta. Cikinsa da ƙaffauwansa kamar ana hura wuta, ya duba sugarnsa ya ga ya hau, ga kansa yana masa ciwo. Hannu ya kai ya tattaɓata, ya samu ta farka da ƙyar, ta kalleshi ta ce "Ya dai?" Ya ce "Bana jin daɗi ne, jikina zafi yake mini, na duba sugana ya hau" "To Allah ya sawwaƙe, ka sha maganinka Allah ya sawwaƙe" daga haka ta juya ta cigaba da baccinta. Ya taso ya fito falo, yana zazzagawa saboda yadda jikinsa yayi nauyi, yana nan tsaye yaga Amina ta buɗe ƙofar sashensu ta fito kamar aljana. Ta dinga tunkaro in da yake tsaye, kasancewar babu haske a falon, bata sani ba, har sai da suka yi karo, za tayi ihu ya rufe mata baki. Tun daga wannan ranar, da ta sama masa ruwa ya sanya ƙafafuwan sa, wata irin shaƙuwa ta fara shiga tsakaninsu. Abu kamar wasa, ƙaramar magana na neman zama Babba, Alhaji Ahmad ko wuni yayi bai ga Amina, sai yaji duk babu daɗi, idan ya ganta kuwa ko bata kula shi, gaba ɗaya nishaɗi take saka shi.   Kasancewar Daddy hutun ƙarshen shekara ya zo, yana shafe a ƙalla watanni uku a gida, dan haka yadda Amina ke kula da Abincinsa, da kirkinta a gareshi, ya sanya suka samu kusanci sosai. Watarana Daddy ya dawo, ya tarar da Amina tare da Baba, tana ganin ya zo wurin, ta tashi ta bar wurin ta bar shi ita da Baba. Alhaji Ahmad ya zauna a kusa da Baba, abin da Baban bai taɓa ganin yayi ba. Suka gaisa. Alhaji Ahmad ya ce "Malam Hassan, na yaba da yadda malaman su Amina suke ta yaba mata, naji daɗin mayar da hankali da take sosai". Malam Hassan ya ce "Ai bani da bakin yi maka godiya Alhaji, Allah ya saka maka da alkhairi ban taɓa zaton burin Amina zai cika" "Wane burin kenan?" "Burin yin karatun boko mana, mu garinmu ba su damu da shi ba, ina nan 'yan uwana Aure suka so suyi mata da wani dattijo, ta biyoni nan, da baka karɓe ta ba ban san ya zan yi ba" "Aure kuma, karatun nata fa?" "Ai basu damu da shi ba, ita ma ɗin da take yi, gani suke yi, tamkar wani zunubi ne barinta da nake tana karatun nan" Alhaji Ahmad ya ce "Amina tana da ƙwaƙwalwa, Yakamata a bata dama ta cigaba da karatunta har gaba da Sakandire" Baba ya ɗan yi shiru ya ce "Ashsha, wannan ɗin ma na gode, idan na samu dama ta cigaba da karatun, idan ban samu ba, da ta gama na sakandiren ta samu miji sai na yi mata aure, duk danginmu babu wanda 'yar sa ta yi karatu haka, idan na barta sai ya zama abin magana, yanzun ma suna ta surutu a kan zamanta a nan" Daddy ya ɗan yi shiru ya ce "Haka ne, Allah ya zaɓa abin da yafi alkhairi" "Ameen yallaɓai, Allah ya saka da alheri" "Bakomai Malam Hassan" Daddy kuwa tuni ya yiwa Amina alƙawarin cigaba da karatu, tun bayan da ya fuskanci tana so. Wasa wasa, Alhaji Ahmad ya kasa gane me yake ji a game da Amina, a hankali ya cigaba da ƙoƙarin samun kusanci da Amina sosai, ya tsiri sawa a kai masa ita gidansa, dan kawai ya samu nishaɗi daga shirmenta. A haka yayi galaba ta fara shaƙuwa da shi, shi kuma suna ƙara shaƙuwa yana cigaba da shiga damuwa a kan Amina. Da fari Daddy 'ya ya ɗau Amina, ita ma ta ke masa kallon uba, amma daga baya ha kasa gane wane feelings yake da ita a kanta, ya kan samu wata nutsuwa ta mussman idan yana tare da ita. Ranar da ya sauketa a hanya kuwa, a kan tayi maganar Hajiya Zainab, ji yayi tamkar ya sauka ya bita su tafi tare, amma yayi hakan ne dan kar alaƙar da kw tsakaninsu ya sanya ta ce zata raina uwar ɗakin nata, dan ba zai iya bari ta koreta daga gidan nan ba. Sannu a hankali ya dinga tafiya a motar, har zuwa lokacin da ta hau motar Bilal, tun da ta shiga motar Bilal yaji wani irin haushi da kishi ya mamaye masa zuciya. Kwana biyu a tsakani, yaga Bilala a gidan, ya je wurin Baba suna gaisawa, hakanan hankalinsa ya tashi yaji yana son sanin meye alaƙar dale tsakaninsa da Amina da har zai zo wurin Baba. Haka nan Alhaji Ahmad ya kasa zane ya kasa tsaye, ya rasa wanda zai tunkara da maganar. Ya samu wani abokinsa, Alhaji Sambo ya gaya masa komai. Dariya Alhaji Sambo ya dinga yi masa ya ce "Lallai kana son kunna wuta a gidanka Ahmad" "Ban fahimce ka ba me kake nufi?" "Au tanbayata ma kake yi? Son yarinyar nan kake malam" Daddy ya dafe ƙirji ya ce "Haba dai, yanzu ya zanyi?" Alhaji Sambo ya ce "Ka yarda son nata kake ko kuwa?" Daddy ya ɗanyi shiru sannan ya ce "Na yadda da maganar ka, dan bana jin zan iya yarda ta bar gidana, saboda yadda take kula dani, amma na rasa abin yi, ga wani yaro a maƙotana da ya sarƙi zuwa wurin mahaifinta na san bai wuce ya ce Aurenta zai yi ba" "Ka shirya facing ɗin kowane Challage dan ta zama taka?" "Kamar dai haka nake ji a jikina" "Ka fara nemo soyayyarta, sai in gaya maka abu na biyu da za mu yi" Daddy ya waro ido ya ce "Ta yaya ni Ahmad, Sambo ba ta fi shekaru sha shida ba fa, kalleni sai inje in ce ina sonta?" Alhaji Sambo ya ce "Kai dalla ware, ranar biyan buƙata rai ba a bakin komai yake ba. Sweet sixteen kenan ake gaya maka, ita kaɗai ta isa maganin damuwarka, ita waccan matar taka ba ta saka shirme a gaba ba, malam Allah ne ya baka dama kawai kayi abin da ya dace fara samun soyayarta dan ba za ayi mata dole ba" Daddy ya goge gumin goshinsa ya ce "Ni Ahmad ta ina zan fara wannan taɓarar, na kalli yarinyar da take mini kallon uba nace ina sonta?" AYSHERCOOL 08081012143GABA DA GABANTA BY AISHA ADAM 58 Haka suka yi sallama da Alhaji Sambo, Daddy ya koma gida yana cigaba da saƙe saƙen yadda zai ɓullowa lamarin yi wa Amina bayanin abin da yake buƙata, dan yarinta Amina akwai ƙuruciya, ya samu ta karɓi batun ma ya san sai ya sha gwagwarmaya. Ya cigaba da ƙoƙarin samun kusanci da ita, tare da kyautata mata, yana yi yana lissafin yadda zai yi ya sanar mata da abin da yake zuciyarsa dan ganin abin yake banbarakwai. Mussaman ya aika aka ɗauko masa ita aka kai masa ita gidansa, ya sakata tayi masa girki, har Kitchen ɗin yaje ya tsaya yana kallonta, amma ya kasa ce mata komai. Sai da ta kawo masa Abincin, ya fara ci yana ta yi mata santi tana murmushi, ya numfasa ya ɗan tsura nata ido sannan ya ce "Sweetheart Abincin nan yayi daɗi fiye da yadda kike zato, kullum girkinki ƙara daɗi yake" Waro ido waje tayi ta ce "Sweetheart kuma?" Ya ce "Eh mana, ai normal ne, ina gayawa mutane na mussaman a wurina, ina gayawa matata da 'ya'yana, kema kuma ta musamman ce" "To aini 'yar aiki ce" ta faɗa tana ɗan tsuke fuska. "Meenalina, ina son na mayar da ke ƙarƙashin inuwata yadda zan baki kulawa yadda yakamata" yayi mata maganar cikin nutsuwa yana kallon fuskarta "Nifa bana gane magana a dunƙule" Yayi murmushi ya ce "Ina son ki zama tawa, ki zama cikin kulawata da kariyata" "In zama taka sai kace wata baiwa, ba zamanin bayi ne ake wannan ba" Amina kenan duk wani abun serious, sai ta kawo shirmenta a ciki. "Meenal" "Na'am Daddy" "Zaki iya aurena?" Da hankalinta rabi na kansa rabi kuma na kan Tv, dai taji maganar tasa kamar daga cikin tv ta fito, tayi masa ƙuri da ido. Ya jinjina mata kai ya ce "Yes, i mean it, zaki iya aurena?" "Taɓ Daddy ka daina wanan wasan dan Allah" "Kalli idona, ba wasa nake ba, ina son na cigaba da samun kulawa daga gareki. Ki kalli abin da na zo miki da shi a mahanga ta addini, ba a mahangar Al'ada ba, addininmu bai hana hakan ba, amma kiyi tunani a kai, zaki iya aurena?" Tura baki tayi ta ce "Ni ba zan auri tsoho ba" Yayi murmushi ya ce "Jarmai kike so kenan?" "Allah ya kiyaye, Jarmai fa ƙazami ne, gashi masifaffe, ga auri sakin tsiya, gidansa yaransa sun fi Ashirin, ya haɗa kai da su Baffa Lawan, suka sayi gonar Baba da arha, ni bana sonsa". "To Bilal kike so?" "To ai ni ban san me ake ji idan ana son mutum ba, Nifa ba soyayya muke da Bilal ɗin bama, kawai mutunci muke yake zuwa gaida Baba". "Is ok, ina nan ina sauraren amsarki, ba zan takura miki ba, na gaya miki abin da ke zuciyata ne, idan ba kya sona, bakomai zan yi haƙuri in tayaki samun wanda kike so ɗin kinji Meenalina, amma dai Daddy yana son Meenalinsa Sosai, idan Meenal ta auri Daddy zai ririta ta ya bata dukkan kulawar da take buƙata". Amina ji tayi kamar ƙasa ta tsage ta shige dan kunya, ita wannan abu jinsa take kamar daga sama an yiwa wada ƙwace. Ganin duk ta takura da maganganunsa, ya sanya ya ce ta tashi ya sauketa a gida. Ba musu ta ɗau jakarta tayi waje. Suna tafe a mota, taƙi kallon in da yake sai kawar da kai take yi, saboda nauyinsa da take ji. "Meenal" "Na'am" ta amsa ba tare da ta waiwayo ba. "Kalleni mana" taƙi waiwayowa ta kalleshi. Ya ce "kar ki je ki saka maganar nan a ranki ki ƙi sakewa kinji, ba zan takura miki a kan abin da ba kya so ba kinji sweetyna" A ranta ta ce "Innalillahi, me Daddy ya zama ne?" Haka yayi ta surutunsa, ita dai ba ta ce masa komai ba suka cigaba da tafiya. A bakin layin ya ajiyeta, ya ce "Maza daga nan ki wuce gida, kije ki samu ki huta, sai mun yi waya" kai kawai ta ɗaga masa, ta fice daga motar da sauri, ta shiga layin. Daga nan Kai tsaye wurin Alhaji Sambo ya wuce, ya gaya masa yadda suka yi Amina, Alhaji Sambo ya ce "Shawarar da zan baka ita ce, ka cigaba da lallaɓata sannu a hankali, tunda yarinya ce ƙarama, kar ka nuna zaka yi mata dole, komai zai zo da sauƙi in sha Allah". Daddy ya ce "Allah ya amince, ina fatan ta amince ɗin, kamar tana sona shirirtarta ce ta dameta shiyasa ba ta gane hakan ba". Alhaji Sambo yayi dariya ya ce "Ai shirirtar kake yiwa, kawai ka cigaba da wasanka, sai dai kayi taka tsantsan kar wannan masifaffiyar matar taka ta sani, dan wallahi ta sani yarinyar ta shiga uku ne". "Ai ba zan bari ta sani ba, ina sane da duk abin da nake yi". Alhaji Sambo ya cigaba da ba shi shawarwari, daga bisani suka yi sallama. Ko da taje gida ɗakinta ta wuce, tana tunani tana jujjuya maganar da Daddy yayi mata, ita kaɗai ma a ɗakin sai kunya take ji, tana sake jin abun wani iri. Da daddare ta gama shirinta, ta zauna ta ɗauko littafinta tana karatu, kawai sai taga wayarta tana ringing, ta duba taga Daddy ne, taƙi ɗagawa ta zubawa wayar ido. Ya kirata ya kai sau uku, amma taƙi amsa wayar. Saƙonsa ne ya shigo wayar "Meenali meyasa ba kya ɗaga wayata?" "Bakomai" ta tura masa dan shirme. "Wai duk a kan maganar nan ne, dan Allah ki saki ranki, ki ɗaga wayar muyi magana". Yana tura mata saƙon ya kuma kiranta a waya, jiki na rawa ta ɗaga, ji take kamar a gabansa take kunya na sake ratsata. "Duk dan nace ina sonki shi ne kika ƙi amsa mini waya?" Tayi shiru. "Meenal, ke ma'abociyar ilimin addini ce, abin da na nema a wurinki, bai saɓawa addini ba, ki kalleshi a ma'aunin Addini ba al'ada ba, kin ji, ni dai fatana ki saurari zuciyarki ki gani idan zaki iya aurena ki zauna da ni, amma idan da wanda kike so ba zan takura miki kinji" "To" "Yauwa, na san wataƙila yanzu kina karatu ne, ayi karatu lafiya" ko sallama ba ta yi masa ba ta kashe wayar gaba ɗaya. Babu wanda ta gayawa abin da ya faru, da abin da Daddy ya ce mata. Sai dai duk abin da zai haɗa su kauce masa take yi, ta koma shiryawa da uwar safiya ta tafi makaranta, idan ta dawo kuwa ba zata bari su haɗu ba, ta wuni a ɗaki. Ta daina kunna wayarta gaba ɗaya, dan karma ya kirata ya sameta. Ranar wata juma'a, bayan ta dawo daga makaranta, Hajiya Zainab ta tafi yawon bikinta, Fadila kuma na makaranta. zaton Amina Daddy ma baya gida, dan haka ta fito falo tana cin kantu a leda, tana goge goge, ba tsammani ta juya ta ganshi a tsaye yana kallonta. Gaba ɗaya ta rikice ta na neman wurin ɓuya, kamar wadda ta yada zani a gaban siriki. Yayi murmushi yayi mata alamar ta zo. Ji tayi kamar kar taje, sai kuma taga idan tayi hakan baya kyauta ba, dan haka tabi bayansa. Bai tsaya a ko ina ba sai a tsakiyar falonsa. Ya kalleta ya ce "''yar Babyna, laifin me nayi miki kuma kike guduna, kika dai na amsa wayata?" Tayi shiru tana wasa da ledar hannunta. Ya miƙa mata tafin hannunsa ya ce "Ɗan sanmini abin da kike cin" Ba musu ta miƙa masa ledar kantun. Ya ce "Zaki bani abin hannunki amma kina guduna ko, dan Allah ki bar wayarki a kunne muyi magana da daddare kinji?" Ta amsa da to, ya ce "You can go, ko in zo in tayaki aikin ne" Ta girgiza masa kai alamar a'a. "Hmm to shikenan, sai munyi wayar, jeki ki cigaba da aikin ki" ita dai ba tace masa ƙala ba ta bar falon. Da daddare da Daddyn ya kirata ma dai, shirun tayi masa yayita kiɗansa yana rawarsa, bata iya ce masa komai, sai ya gama wayar ta ajiye tana dariya. Suna daf da fara jarrabawa, ta shirya zata tafi makaranta, ta fito falo ta tarar da Baba a durƙushe a gaban Hajiya Zainab, sai banbamin bala'i take yi masa. Cak Amina ta tsaya ta rasa abin da za tayi ko ta ce, ta in da ta shiga ba ta nan take fita ba, tana ta ci masa mutunci, Amina ba ta san laifin da Baba yayi mata ba, sai da tayi ta gama ta sallmeshi, sannan Amina tabi bayan Baba. Cikin sauri ta ƙarasa ta cimmasa "Baba" ya tsaya ya waiwayo ya kalli Amina. Ƙwalla ta gani kwance a idon Baba, ya dake ya ce "Makarantar zaki ne?" "Baba me kayi mata take maka wannan rashin mutunci da sassafe" Baba ya ce "Kar ki damu, Kina da kuɗin makaranta ko na baki?" Hawaye Amina ta fara yi, wani irin tausayin Baba ya sake kamata. Saura ƙiris hawayen idonsa ya zubo, amma ya dake ya ce "Yi maza ki tafi kar ki makara" Haka Amina ta tafi makaranta tana kuka, gaba ɗaya haka taje makarantar bata walwala. Azima tai ta tambayarta meke damunta, amma taƙi gayamata sai kukanta kawai take. Da aka tashi daga makaranta, sun fito zasu tafi, Amina ta ce "Azima kinga sabon dabino, muje na sayawa Baba yana son sabon dabino sosai" Azima ta raka Amina, suka sai dabino, Azima ba ƙaramin burgeta Amina take ba, saboda alaƙarta da Babanta, dan ita nata mahaifin ya daɗe da rasuwa. Amina ta kalli Azima ta ce "Azima wannan dabinon sai dai kiyi haƙuri, na Baba ne, dan haka ni da ke ba mai ci" Azima tayi murmushi, ta ce "Ai nima mai saya ce in baki ki kai wa Baba. Amina ina fatan ubangiji Allah ya baki miji nagari a garin nan, wanda zai riƙeki amana ya raba Baba da wannan aiki a ƙarƙashin mutanen gidan nan naku marasa mutunci" Shiru Amina tayi tana nazartar maganganun Azima, kamar ta tunatar da ita wani abu mai matuƙar muhimmanci, da sauri Amina ta ce "Azima na gode, sai Allah ya kaimu gobe" ta nufi titi tana cigaba da juya maganar Azima a ranta. Baba yayi murna da dabinon da Amina ta kawo masa, Yayi ta yi mata addu'a. Amina da taje ɗakinta, tayi salla ta dinga tunanin maganar Azima, Allah ya bata miji nagari wanda zai raba Baba da aikin gadi. "What if na Auri Alhaji Ahmad, kenan Allah ma ya riga ya bani ban ankare ba" tayi maganar tana murmushi. Amina ta wuni ta na nazarin maganar Azima. Kamar kullum da daddare, Amina na tsaka da karatu, Daddy ya kirata, yau ba jan aji ta ɗaga wayar. "Hello 'yar Babyna" "Daddyna" ita kanta da ta faɗi hakan sai da kunya ta kama ta. "Wow, amma naji daɗi sosai, ya school ɗin 'yar Babyna?" "Alhamdilillah, ya aiki?" "Aiki kam akwai shi, kin bani aikin tunaninki Sweetheart, ina cikin damuwa, duk na rame". Cikin kulawa ta ce "Daddy damuwar me kuma?" "Kin ƙi bani amsa zaki aureni, kince ba kya sona" Amina ta ce "Ka tambayi Baba duk abin da yace maka shikenan" "Kina nufin idan Baba ya amince zaki aureni?" A kunyace ta ce "Mmm, amma kar kace masa ni nace ka tambayeshi" Wani lumshe ido yayi yana murmushi ya ce "Thank you Meenalina, idan har Baba ya amince na aureki, zan baki farinciki da kulawa iya yina" "Hmm sai anjima" "Au ba zaki tsaya muyi hirar ba, a haka za mu yi auren Babyn, Ahmad yana sonki sosai fa" Kashe wayar Amina tayi, ta dafe ƙirji tana murmushi ta ce "Daddy dama haka kake? Sai kunya yake bani, innalillahi wa yaga na auri Daddy". Ta shiga what's app ɗinta, ta duba hotunansa da yake turo mata. "Wayyo Allah na, masha Allah Daddy fa yana da kyau, ga shi da gemu ga gayu. Yana aura ta zan saka Baba ya bar aikin gadi a gidan nan, kuma duk wani mai rabo sai yaci arziƙin da ake wulaƙanta mu a kansa, wayyo zuciyata". Tayi maganar tana tsalle a kan katifarta Daddy kuwa jinsa yake tamkar ya taka rawa, saboda tsabar farinciki da jin daɗi, washegari da safe Alhaji Ahmad ya koma wurin Alhaji Sambo, ya sanar masa. Alhaji Sambo ya ce "Alhamdilillah, yanzu abin da ya rage kan ka tambayi mahaifin nata aurenta, zan fara zuwa garinsu, nayi maka bincike a kansu tukuna dan ko ba komai yakamta ka san wa zaka aura, Daddy ya ce hakane. Alhaji Sambo da kansa ya je Shanono, yin bincike a kan dangin su Amina, ya samu kyawawan bayanai a kan mahaifinta, sai dai sai da aka gaya masa batun guduwa da Amina tayi daga garin za ayi mata aure. Da Alhaji Sambo ya dawo wa da Alhaji Ahmad da sakamakon binciken sa, Alhaji Ahmad ya ce Bakomai, da ta gudun ai wurin Baba ta taho nan gidansa, hakan ya ƙara bawa Alhaji Ahmad ƙwarin gwiwar zuwa ya tunkari Baba Hassan. Malam Hassan yayi mamakin ganin Alhaji Ahmad a ɗakinsa na gadi. Suka gaisa da Baba, gaba ɗaya jikin Baba yayi sanyi, saboda tsananin mamaki har tsoro yake kar wani laifin yayi. Alhaji Ahmad ya duni Baba cikin nutsuwa ya ce "Malam Hassan, na san zaka yi mamakin ganina a daidai wannan lokaci, sai dai na zo ne domin wata muhimmiyar magana sosai da sosai, amma ina son ka kalli maganata a mahangar  addini, wata alfarma na zo nema a wurinka, ban sani ba ko zaka iya yi mini" Baba ya ɗan yi shiru yana tunanin wace irin alfarma ce haka, ya numfasa ya ce "In dai bata fi ƙarfina ba, kuma bai saɓawa addini ba in Allah ya yarda zan maka" Alhaji Ahmad ya ce "Masha Allah, abu ne na alkhairi, da nake saka ran ya zame mana alkhairi a tsakaninmu. Malam Hassan ba wata alfarma ba ce ba, Auren Amina nake son ka bani, ina son zan aureta idan ka amince" Jimmm Baba yayi, yaji maganar daga sama, wani banbarakwai. "Malam Hassan, ba takura maka zan yi kayi mini abin da baka yi niyya ba, ba takura muku zanyi ba, idan kana ganin babau damuwa ina son ka bani aurenta, ta zama a ƙarƙashin kulawata" Baba yayi shiru sannan ya ce "Amma Yallaɓai, wannan lamari da ka zo da shi yayi girma da yawa, al'umma za suyi mana kallon butulallu, daga zuwa cin arziƙi, shikenan kuma sai ka auri 'ya ta" "Malam Hassan kar ka damu da wannan, ai addininmu bai hana ba, idan kana ganin babu damuwa ina neman wannan alfarmar, amma zan baka dama kayi shawara tukuna" Malam Hassan ya ce "To shikenan, Allah ya wuce mana gaba". Bayan kwana da biyu da yin maganar, Baba ya dage yana Addu'a a kan lamarin, baya son yayi jayayya a kan lamarin, saboda ya lura da tun kan Alhaji Ahmad ya gaya masa, Ya lura da yadda kusancin Alhaji Ahmad da Amina yayi yawa. Dan gaba ɗaya ta daina jin nauyinsa,  ƙarewa ita ma Daddy take ce masa, baya son ya zaƙe ya zo yaji kunya daga baya. Amina ta kai masa Abincin dare, ya tsayar da ita, ya ce "Uwata magana za muyi" Ta ce "To Baba". "Maigidan nan ya zo mini da wani zance na cewar wai yana sonki, zai aureki, duk da dai alamu sun nuna kun gama fahimtar juna kan maganar ta iso gareni" Nan Amina ta tubure a kan cewar ita bata san zancen ba. Baba yayi murmushi ya ce "Hmm koma dai mene, ki je kiyi ta addu'a, sannan idan kina son mutumin nan zaki aureshi, ki aure shi saboda Allah ba wani abu ba, kuma abu na gaba ina jinjina yadda zaki da iyalansa, sannan kuma ga batun karatunki bana son karatunki ya tsaya". "Ai ya ce saina gama karatu x Baba ya ce "Kuma ki ka ce baki san zancen ba" da sauri Amina ta shiga taitayinta, ta tuno katoɓarar da tayi. Baba ya ce "Tashi kije, ki cigaba da Addu'ax Amina ta tashi ta tafi. Baba ya duƙufa yana ta Addu'a a kan lamarin, saboda ya lura da yadda ita kanta Amina ke da rawar kai, kuma ya fuskanci tana son Alhaji Ahmad ɗin. Alhaji Ahmad kuwa ya cigaba da lallaɓa Amina, yana kyautata mata tare da yi mata alwashin bata kulawa idan sun yi aure. Baba ya bawa Alhaji Ahmad damar ya je garinsu ya nemi auren Amina a wurin su Kawu Bala. Ahmad ya je ya sami 'yan uwan mahaifinsa, ya sanar musu da yana son suje Kano Shanono su nema masa aure. Familyn Alhaji Ahmad sun yi farinciki da jin cewa zai yi aure, dan kusan duk a ciki suke da Hajiya Zainab, da yadda ta kainanaye Musu ɗan uwa, ta hana shi sakat ta rabasu da shi. Be gaya musu wa zai aura ba, kawai ya ce su je su nema masa Aure. Za'a ɗaura masa aure yanzu, amma tariya sai bayan shekara ɗaya zata tare. AYSHERCOOL 08081012143GABA DA GABANTA NA AISHA ADAM (AYSHERCOOL) 59 Ba tare da Amina ta sani ba, Baba ya bawa Alhaji damar zuwa ya nemi auren Amina a wurin yayyensa su Kawu Bala. Dangin Alhaji Ahmad da suka ji batun zai yi aure, amma tariya sai bayan shekara guda, suka dinga murna kamar su zuba ruwa a ƙasa su sha, a dangin nasa ba kowane ya san zai yi auren bama, sannan bai yadda sun san wa zai aura ba, kawai ya ce wa 'yan uwansa za aje nema masa Aure a Shanono. Lokacin da suka je wa su Kawu Bala da maganar, suka dinga kushe Amina, da faɗar miyagun maganganu a kanta, 'yan uwan Alhaji Ahmad suka ce babu ruwansu shi ya ce yaji ya gani. Baƙin ciki da hassada kamar Ya kashe su Baffa Lawan, saboda su so su kayi Amina ta dawo a ƙasƙance cikin tozarci. Suka bada maƙudan kuɗi, a matsayin kuɗin Auren Amina, aka sanya sati biyu kacal zasu dawo a ɗaura Aure. Amina bata san budurin da ake yi ba, tana can tana jarrabawa. Ranar wata juma'a, Daddy da jama'arsa suka tafi Shanono, Baba ya ce wa Amina zai je ƙauye, bata san me zai je yi ba, tayi masa Allah ya tsare, lokacin suna jarrabawa kuma sun daf da yin wannan tafiyar. Har aka je Shanono aka ɗauro mata aure, bata san an yi ba. Tun da aka ɗaura auren nan Alhaji Ahmad yake jinsa kamar a wata sabuwar duniyar yake jinsa, sai dai da yaga Hajiya Zainab sai gabansa ya faɗi. Da ya dawo daga ɗaurin Aure ya tarar da ita tana mopping, ji yayi kamar ya karɓa yayi mata. "Amaryata" ya faɗa lokacin da ya zo kusa da ita. Waige waige ta shiga yi, dan kar ta je wani yaji me ya ce. Ta ce "Ni dai kar ka janyo mini tashin hankali, a falo fa muke" Murmushi yayi, ya wuce yana jin nishadi na ratsa shi. Baba bayan ya dawo, ya kira Amina a waya, ta zo ta same shi, ta kasa gane me take gani a fuskar Baba, farinciki ko kuma damuwa. "Uwata" ya kira sunanta. "Na'am Baba" "Kowane abin halitta da kika gani a doron duniya, tun kan Allah ya samar da shi ya tsara masa abin da zai same shi, me kyau da akasin haka. Ranar juma'a, an ɗaura miki aure ke da Alhaji Ahmad". Waro ido tayi ta dafe ƙirji ta ce "Baba aure kuma? Dama yanzu za ayi auren?" "Eh, shi ya buƙaci hakan, idan kin gama jarrabawa, zaki je ƙauye za kuyi wuninku na mata, amma ya tabattar mini da ba zaki tare ba sai Allah ya sa kin gama karatunki" Ai sai Amina ta fashe da kuka. "Kefa kika nuna mini kina so, meye na kuka kuma? Ni dai fatana ki tsare mutuncinki yanzu da da akwai banbanci, yanzu kina da Aure saɓanin da. Sanan ki rage wannan rawar kan naki, kuma ki kula da kanki, kinga dai baki tare ba sai Allah ya sa kin kammala karatunki, to ki kula ki jira ki tare, kin san dai me nake nufi. Sannan ki duƙufa da Addu'a, dan na san wannan auren naki ko a yanzu ko a gaba, zai zo da tangarɗa". Ai gaba ɗaya daina gane Abin da Baba yake faɗa tayi, ya gama gaya mata abin da zai gaya mata, ita babban abin da take hangowa idan an tashi graduation shagalin da za ayi ba zata sake ba sosai saboda tana da Aure. Jiki a sanyaye kamar wadda aka bawa saƙon mutuwa, haka ta tafi ɗakinta, ta rufe ƙofa ga zauna ta dinga kuka, sai da tayi mai isarta, sannan ta tashi saboda kiran salla tayi alwala. A Kitchen haka Hajara ta addaba mata a kan meya sameta a fuska, fuskar ta kumbura, amma tace mata bakomai. Da suka gama girki ma, ɗakin ta koma tayi zuguum, ko Abinci ta kasa ci. Wayarta ce ta fara ringing a kusa da ita, cikin ƙwarin gwiwa ta ɗaga wayar, za ta yiwa Daddy tsiwa, saboda ya sa an ɗaura mata aure ba da saninta ba, amma ajiyar zuciya da yayi ta wayar, kawai taji bakinta ya mutu. "Sweetheart ba magana?" Tayi shiru taƙi cewa uffan. "Magana fa nake yi, ko mulkin ne ya motsa?" Kawai ta fashe da kuka iya ƙarfinta. A rikice ya ce "Subhanallah, Amina menene?" Ta katse wayar ta ajiye, ta cigaba da kuka. Tana kallo ya cigaba da kiran wayar, amma ta share shi. Washegari tana shirin makaranta, yana cigaba da rangaɗa mata waya, amma taƙi ɗagawa. "Idan ba zaki ɗaga wayar ba, idan an tasheku daga school, ki jirani zan zo na ɗaukeki, sai muyi magana amma kin tayar mini da hankali Meenali" tana gama karanta saƙon ta murguɗa baki, ta ajiye wayar tayi ficewarta. A makaranta ma gaba ɗaya ranar bata walwala, ana tashi daga makaranta ta cewa Azimi gidansu zata bita. Azima bata takurata sai taji meke damunta ba, suka tafi gidansu Azima tare. Kamar kullum, Ammi na ganinsu tare, kamar ta goya Amina. Ta karɓi Amina cikin sakin fuska, amma taga fuskar Amina a haɗe. cikin damuwa Ammi ta ce "Aminatu, mene? Na ganki duk wani iri". Ai kamar jira take yi, ta fashe wa Ammi da kuka. Ammi ta rungumeta tana rarrasinta, sai da ta samu ta tsagaita da kukan, sannan ta kalleta ta ce "Gaya mini, menene?" "Ammi Aure aka yi mini" ta faɗa tana fashewa da wani kukan. Azima ta ce "Aure kuma?" Ammi ma abin ya ɗaure mata kai, ta ce "Yi mini bayani Amina, shi Baban ne ya yi miki auren ko kuwa kamr yaya an miki aure?" Amina ta zauna ta warwarewa Ammi komai, har zuwa ɗaura mata aure da aka yi. Maimakon Ammi ta ɗaga hankalinta ita ma, sai kawai tayi murmushi. Azima ta ce "Taɓɗijan, dama duk wannan Daddy da Meenal ɗin da ake sonki yake, amma dai anji kunya raƙumi ya shanye ruwan 'yan tsaki" Ammi ta ce "Ubanki ke dai raƙumin fitsararriya, ni kaina da zan samu wani dattijon arziƙin kamarsa dana aura masa ke. Tashi ki bani wuri ma zan yi Magana" "Ammi kiyi haƙuri" Azima tayi maganar cikin shagwaɓa. "Zaki tashi ko sai ni na tashi" Azima ta tashi sum sum ta bar wurin, tana ta mamakin yadda wannan lamarin ya kasance. Ammi ta sake matsawa kusa da Amina ta ce "Kina jina ko Amina? Ita rayuwar duniya a duk lokacin da kace wani bai isa ba, sai Allah ya nuna maka kaine baka isa ba, ki duba wulaƙanci da cin zarafin da matar gidan ke yi miki ke da mahaifinki, amma da yake Allah sannu a hankali yake hukunta bayinsa sai ya ƙaddara aure a tsakaninki da mijinta. Da farko abin da zan gaya miki shi ne kiji tsoron Allah, ki saka a ranki kema wata dama ce Allah ya ara miki, idan kin yi amfani da ita yadda ta dace, ki rabauta, akasin haka kema zaki ga abin da ba kya so. Meye a ciki Allah ne ya kashe ya baki, meye aibunsa, Allah ne ya kawo lokacin da zaku huta, dan haka karki damu, kiyi ta addu'a sannan zan yi iya ƙoƙarina in ga kin yi abin da ya dace a gidan mijinki. Yanzu ta san an yi auren?" Amina ta ce "A'a, wai sai mun gama makaranta zai gaya mata sai na tare" "Ahh to babu laifi, babban abin da nake so da ke shine, ki kula da kanki kinga yanzu kina da aure, banda biyewa su Azmia saboda yanzu ke da su ba ɗaya bane ba" Ammi ta zage sosai ta dinga yi mata nasihohi. Amina dai jin Ammi kawai take yi, amma gaba ɗaya ta rasa in da zata saka kanta, a kan Aurenta da Daddy yayi da gaggawa haka. Ammai ta ce "Idan kun kammala jarrabawar, kan ki tafi ki zo nan, a gyara miki kai, a yi lalle" Amina ta jinajina mata kai, sai Yamm sannan Ammi ta saka direba ya kai Amina gida. Gaba ɗaya jinta take kamar ba ita ba, wai an ɗaura mata aure, ta zama matar Daddy, gani take tamkar mafarki. Gaba ɗaya ta nemi kuzarinta ta rasa, da daddare ta fita kaiwa Baba Abinci, ta hangi Daddy a dining, suna cin Abincin dare, ya ƙura mata ido ba tare da kowa ya lura ita yake kallo ba. Zumɓura masa baki tayi ta wuce, da ta lura iya yake kallo, murmushi kawai yayi mata, ita kuma ta fice daga falon. Da ta kaiwa Baba Abincin ma, nasihohi ya cigaba da yi mata, a kan ta kula da kanta, tun da yanzu tana da aure, kuma ta tsare mutuncinta sannan ta cigaba da Addu'a, Allah ya sassauta abin da ka iya biyo baya, idan har iyalansa suka san meyafaru. Bayan Amina ta dawo daga wurin Baba, ta tarar da dining kaca kaca, ko arziƙin haɗe kwanukan da suka ci Abinci ba suyi ba. Tsaki tayi, ta wuce dining ɗin, ta tattare kwanukan, ta gyara wurin tsaf. Ta wuce sashinsu, ta tattara kwanukan da aka ci Abincin faren tana wankewa, sai ga Hajara ta shigo Kitchen ɗin. "Yauwa Amina, ance ki kaiwa maigidan nan shayin dare, da kayan marmari" shiru Amina tayi mata ta cigaba da aikinta. "Amina magana fa nake miki" 'Ai naji ko" Amina ta faɗa a hasale. Ta gama abin da take sannan ta dafa shayin da Fruit ta kai masa, tun da tayi sallama yake binta da ido, a ƙasan maƙoshinsa ya amsa mata. Ba ta ce masa uffan ba, ta ƙarasa ta ajiye masa, ta juya zata tafi. "Amina" ya kira sunanta kai tsaye yau ba karantawa, sai taji wani dammm babu daɗi, ta juyo ta dawo tana tura baki, ta tsaya masa a ka. "Sai kaina yayi ciwo, kika tsaya mini a ka?" Neman wuri tayi ta zauna a ƙasa, saukowa ya yi ya zauna a kusa da ita ya ce " 'yar Babyna me nayi miki ne? Na ce miki zanje school ɗauko ki, kika yi tafiyarki, kin daina mini magana me yayi zafi?" "Daddy shi ne kuka haɗa kai da Baba ka aureni, ba cewa aka yi sai na gama makaranta ba, amma Baba ya ce wai an ɗaura mana aure" ta ƙarasa maganar tana fashewa da kuka. Murmushi yayi, bai zaci Baba ya gaya mata ba, ya so sai taje ƙauye ta ji. "To meye a ciki? Shine dalilin fushin dama? Bana son in zauna zaman jira wani ya zo ya canza miki ra'ayi, kiyi haƙuri ki daina kuka. Zan saka Zakiru ya kai ki. Ai ba abin damuwa bane ba, kema sai hankalinki yafi kwanciya kina ganin mijinki ko sweetyna?" Tura baki tayi alamar baya gamsu da maganganunsa ba. "Ki kwnatar da hankalinki, ba wani abu ai, na ƙara miki kuɗi a account ɗin ki idan da akwai abin da kike buƙata" Yayi ta janta da hira, har ta ɗan sake, sukayi sallama ta tafi. Kamar yadda Ammin Azima ta umarceta, ta je aka yi mata gyaran kai, aka yi mata lalle tayi kyau tayi shar da ita. A tsakanin kwanaki ukun nan, Ammi ta sanya aka yiwa Amina ɗinkuna masu kyan gaske, tayi mata sayayyar kaya masu kyau, Azima sai tsokanarta take yi, ita kuma da tuna Azima ita free take amma ita an yi mata aure, sai ta hau kuka. Zakiru ne ya kai Amina ƙauye, tare da wannan uban kayan Abinci da bata san da su ba, mutane suka dinga zuwa ganinta, saboda yadda tayi kyau ana ta mamakin yadda ko ranar ɗaurin Aure babu wanda ya ga angon nata. Ranar wunin biki kuwa, sai ga Maman Azima tare da Azimar sun zo, Amina bata taɓa zaton zasu zo mata b, tayi ta murna tana jin daɗi. Tun da ake biki a ƙauyen, ba a taɓa yin bikin da aka ci aka sha kamar bikin Amina ba, kowa sai mamaki yake yana tambayar wai waye mijin da ta aura ne?. A wannan zuwan da tayi ne, har ta haɗu da Jarmai ya biyota. Inno ma ta yiwa Amina nasiha sosai da sosai, mussaman da ta san halin Aminan da rawar kai wasu lokutan. Bayan biki da kwana biyu, Alhaji Ahmad ya zo da kansa ya ɗau Amina. Ya yiwa Inno alheri, Amina har da Kuka kamar kar ta tafi, har ya gaisa da su Baffa Lawan a ƙofar gida, basu san waye ba, dan basu kawo babban mutum kamar wannan zai iya auren Amina ba. Kasancewar har da tawagar da suke take masa baya ya zo, kuma ta gabatar da shi a matsayin mutumin da suke aiki a gidansa ita da Baba. Suna tafe a hanya tana kuka, maimakon Daddy ya rarrasheta sai ya hau tsokanarta "Inyee yarinya tana kukan daɗi ta auri ɗan beauty" ta sake ƙaro volume ɗin kukan, tana sheshsheƙa. Sai da ya ga da gaske take, sannan ya miƙa hannu zai goge mata hawayen, amma ta ture hannunsa, ta matsa gefe wai kar ya taɓa ta. Shi abin ma dariya ya bashi, Hajiya Zainab ta kirashi ya ɗauka, nan ma ta haɗe rai. Ya gama wayarsa ya  kalleta ya ce "Daɗinta ina da wadda zan taɓa idan naje gida" yayi maganar yana dariya. Shiru tayi masa, ta juya gaba ɗaya tana kallon window, dan taji haushin abin da ya ce ɗin. Har suka koma gida, yana tsokanarta yana sakata kuka, shi kuma yana saka shi nishaɗi. Daddy yayi farinciki da kasancewa Amina ta zama matarsa, amma yana fargabar cakwakiyar da ka iya biyo baya idan Hajiya Zainab ta sani. Kansa tsaye yake zuwa ya ɗauketa ya kaita gidansa, tayi masa girki da ɗan abinda ba a rasa ba, a haka suka cigaba da sabawa. Watarana tayi girkin rana ta jera a dining, lokacin bai daɗe da warkewa daga rashin lafiya ba, Amina taga ya miƙawa Hajiya Zainab ta zuba masa coc a kofi. Ya saci kallon in da Amina take, yaga ta zazzaro masa ido, tana son tayi magana, yayi murmushi ya kafa kai ya shanye kayansa. Ta tura masa saƙo a waya "Ba zan sake raka ka Asibiti ba, shi ne kake shan coc ko?" Replying ya yi mata da "Meyasa baki hanani sha ba, bayan a gabanki na sha" Ta ɗaga ido ta sake kallonsa, ya kashe mata ido ɗaya. "Ba zan sake cewa ka daina cin abin da aka hanaka ba, har da lumshe ido ko Daddy?" Yayi mata reply da "Matata ce fa ta bani, sai in ce mata bana sha?" Tana ganin abin da yayi mata reply, suka haɗa ido ta galla masa harara, ta bar falon. Ya gyara zamansa a zuciyarsa ya ce "I wish tare muke cin abincin nan Babyna, amma lokaci ne". A haka lokacin tafiyarta Abuja yayi, tayi ta roƙonsa a kan yaje wurin competition ɗin amma ya ce mata ba shi da lokaci, zai saka a ɗauketa a kaita gidan abokinsa dan matarsa ba zata zauna a Hotel ba. Sai dai kuma kwatsam sai ta ganshi a Abuja. Amina tayi murna sosai da ganinsa a garin Abuja. Kaɗaicewarsu tare a gida ɗaya, ya sanya wasu lokutan Daddy kan yi ƙoƙarin kai hannunsa jikinta, abin da ya sanya suke yin faɗa kenan, duk shirin da suke da hakan ta faru, sai ta haɗe rai su yi faɗa. Ranar da Amina tayi rawa da shigar fulani a wurin taronsu, abin ba ƙaramin ɓatawa Daddy rai yayi ba, dan ji yayi tamkar ya ɗauketa su koma Kano kar ta cigaba da competition ɗin. Amina tayi ta binsa tana bashi haƙuri, amma yayi mirsisi yaƙi haƙura, bata taɓa zaton zai iya fushi haka ba, dan sai da ta fara sarewa da bashi haƙurin, sannan ya sauko, dan ta koma koke koke ganin yaƙi haƙura. Ya je ya sameta a ɗakinta, ta ci uban kuka, ga shi babu alamar ta ci Abinci, sai ya zauna shi kuma hau rarrashi. "Meenal zuciyata ba zata yi mini daɗi ba, dole nayi fushi, matata a gaban wasu ƙarti babu mayafi kina rawa, kuma har wani ya dinga yi miki wasa ya zuciyata za tayi min daɗi?" "To ai ba wanda ya san ni matar aure ce" "Dan ba wanda ya san ke matar aure ce shiya sa kike rawa a gaban maza, to shikenan naga alamar kema haryanzu baki san ke ɗin matar aure bace ba, zo muje kiga wani abu" Ta ce "Me zan gani?" "Idan mun je kya gani" ya bata amsa. Ta sauko daga kan gadon, ya riƙe hannunta suka fice daga ɗakinta, zuwa nasa. Ko da suka shiga ɗakin nasa, sai taga duhu babu haske, ta ce "ya ɗakin ba fitila" Ya ce "Mmm yanzu zan kunna" bai kunna ɗin ba, taji ya mayar da ƙofa ya rufe, za tayi magana kawai taji yayi sama da ita. "Daddy meye haka? Nifa tsoro nake ji?" "Shhh meye yake baki tsoron? Bayan muna tare" Ya zaunar da ita a kan gadonsa, ya kunna fitilarsa sai ƙifta idanuwa take. Yayi murmushi ya zauna a kusa da ita. Gaba ɗaya duk sai ta takura, ya sanya hannu ya zare hijjabin jikinta, tana sanye da riga da wando na bacci, pink masu jikin bargo, kanta babu ɗan kwali, tayi parking ɗin gashinta. Haɗe jiinta tayi, tana sunkuyar da kai, dan sai ta kasa magana. Ya miƙa hannu kan side bed ɗinsa, ya ɗauko wani ɗan ƙaramin Chocolate cake, an rubuta Mrs Ahmad, a jiki. "Zo muci cake ɗin soyayya" dariya abin ya bata wai cake ɗin soyayya. Ya sa wuƙa ya yanka shi yana bata a baki, ya saka mata wuƙar a hannunta ya ce "Nima bani" Ita ma ta yanko ta saka a nasa bakin, ƙarshe cake ɗin nan da shi suka yi abincin dare, ya bata ruwa ta sha, ta fara laluben hijjabinta, ya kalleta ya ce "Me kike nema?" "Hijjabina mana, zanje na kwanta". "Ai kin zo kenan" Ta ɗan kalleshi ta ce "Saboda me?" Ya kashe fitilar wayarsa ya ce "Saboda haka nake so" Gaba ɗaya Amina kanta bai taɓa kawo mata Daddyn zai mata abin da yake yi mata a yanzu ba. A very deep and hot romance yake mata, hakan ya tuna masa baya. Gaba ɗaya Amina ta birkice, ta ɗaga masa hankali, ta dinga kuka tana masa ihu, tashi yayi ya kunna fitilar wayarsa ya haskata kawai ya zuba mata ido, idanunta har sun yi Ja, saboda kuka. "Amina me nayi miki ne kike mini wanan kukan?" Haushi ne yakamata, tambayarta ma yake me yayi mata, saboda tsabar ya raina mata hankali. "Ni ka tashi ka buɗe mini ƙofa in tafi" Shi kansa Daddy haushin ne ya kama shi, kawai yayi tsaki yai kwanciyarsa ya ƙyaleta. Ya ɗauka lamarin Aminan na ƙare ne, amma ya ga she's so much serious about it, bai san lokacin da ta gama koke koken tayi bacci ba. Da Asuba yana fita salla, ta fice daga ɗakin ta koma nata. Bayan ya dawo daga sallar ne ya nemeta ya rasa. Bai sake fitowa ba sai da gari yayi haske, ya tarar da ita a falo, idonta duk ya kumbura. A ransa ya ce 'Yarinyar nan tana da hankali kuwa? Ko haryanzu bata yadda aurenta nayi ba?" Ya ƙarasa wurin da take ya zauna, ya dinga aikin rarrashi, da ƙyar ta haƙura har taje Quiz ɗin ranar, sai dai ta kasa sakin jiki tayi wani abun arziƙi. Ta daina kulashi gaba ɗaya ta daina saurarsa, sai ranar da taga likita ya zo har gida ya duba shi, sannan ta koma wurinsa ta bashi Abinci da magani. Sai dai daga wurin bashi Abincinma, ya kuma riƙeta ta kwana a ɗakinsa, ya maimaita mata abin da ya mata a qan, amma Still Amina ta kuma yi masa kamar yadda tayi masa wancan karon. Aikuwa ta tubure masa a kan lallai ita sai ya mayar da ita gida tun da. Ba zai daina yi mata abin da ba ta so ba. Daddy ya barwa ransa cewar da Amina zai koma Lagos, ba zata koma Kano ba, saboda shirmenta yayi yawa. Ya ƙwace mata wayarta, sannan ya sanar mata da cewa da ita zai tafi Lagos, ta dinga kuka wai saboda ya mayar da ita karuwa, bai tare da ita ba amma yana yawo da ita a gari. "Karuwa ko, zaki ga karuwa ganin idonki, kuma kan ki tare ɗin saina tabattar da kin san kina ɗauke da aurena a kanki, fitsararriya, tashi ki shirya ki rakani unguwa, idan kuma ba haka ba.... Kin san sauran" Suna tafe a hanya yana waya da Hajiya Zainab, sai da Amina taso tayi abin da zai sa Hajiya Zainab ta san suna tare, saboda kishin tsiya. Bayan ya gama wayar ya kalleta ya ce "Amma fa baki da kunya, ke ina ruwanki da ni ne? Ina waya da matata kike jin haushi, ke da kike mini ihu, kike cewa ina yawo da ke kamar karuwa, meye na jin haushi dan nayi waya da matata abar ƙaunata, ai ke 'yar aikinta ce kawai dan haka ki daina kishin mijinta" Fuska duk hawaye ta ce "Ba zan daina ba, ai nima matarka ce" Dariya yayi ya ce "A'a 'yar aikin matata dai, kuma karuwata. Am missing my zee so much" Wani dunƙulallen baƙin ciki ne ya tokarewa Amina a ƙirjinta. A fusace ta ce "To daga nan ka tashi ka bita can Saudiya mana, kuma muna komawa gida sai na faɗa mata aure mukayi, komai zai faru ya faru" "Yarinya kina gayamata ƙauye zaki koma, dan cewa zan yi ban san zancen ba" Amina ta kumbura fuska tayi fam, kamar zata fashe, dan ƙarin abin takaici ya ɗauko wayarsa yana mata video. Ajiye wayar yayi ya matsa kusa da ita ya riƙo hannunta ya ce "Karuwar Ahmad" "Ni ba karuwa ba ce wallahi, matarka ce" ta faɗa cikin tsiwa. Dariya yayi ya ce "Akwai ki da ƙarfin hali yarinya. Meenalina kin gama mallake zuciyata, ƙiris ya rage miki, kuma sai wasa kike da damar, ina ga so kike na ƙara wani auren ko?" Kallonsa tayi da sauri ta ce "Wallahi ka ƙara aure ba zan zauna ba" "Idan ba kya son na ƙara aure, ki daina taurin kai da gardama, ki dinga yin yarda da abin da nake so" shiru tayi ta ƙwace hannunta daga nasa. Wani katafaren gida suka isa, mai ɗan karen kyau. Waya Daddy ta ɗauko, ya kara a kunnensa ya ce "Eh gamu mun iso" Babu daɗewa wani mutum da zai yi sa'an Daddy, ne ya fito yana ganinsu ya faɗaɗa murmushinsa ya ƙarasa "Suka gaisa da Alhaji Ahmad" Amina ta gaishe shi. Ya amsa cikin fara'a yana faɗin "Sannu amarya ba kya laifi" ta sunkuyar da kai saboda ita kunya ce ma ta kamata. Suka shiga katafaren falon gidan, suka zauna, suka cigaba da gaisawa. "Sweetheart, ga Engineer Abubakar Salihu Dutse, abokina ne tare muka yi karatu, yanzu shi ne ƙaramin ministern shiga da fice na ƙasa" Kasancewar a kusa da shi take zaune, tayi ƙasa da muryarta ta ce "To shi ne zaka ce mini sweetheart a gaban mutane?" Murmushi Engeener Abubakar yayi, ganin yadda tayi ƙasa da murya tana yiwa Alhaji Ahmad raɗa. Wata hamshaƙiyar mata ce ta fito, fara tas da ita sai zuba ƙamshi take. "Manya baƙi, yau a gidan namu?" Daddy yayi murmushi ya ce "Uwargida sarautar mata" "Na'am ya gida ya iyali?" Daddy ya ce "Alhamdilillah" ta ɗan ƙurawa Amina ido sannan ta ce "Wannan ce amaryar ta mu?" Daddy ya ce "Eh ita ce, na kawota hargida" Amina ta kalli matar ta ce "Ina wuni?" Matar ta ƙurawa Amina ido a ranta ya ce 'Lallai watan ƙarshen Zainab ya kama, ya so cin mutuncinta tun da ya auri wannan 'yar yarinyar, bari in yi amfani da wannan damar in ɗora yarinyar nan a hanya ko ba komai na rama abin da Zainb tayi mini ta hanyar wannan yarinyar. AYSHERCOOL 08081012143GABA DA GABANTA             NA AISHA ADAM AYSHERCOOL 60 Sai da Amina ta sake gaida matar, sannan matar ta farga ta amsa mata cikin sakin fuska. Ta kalli Alhaji Ahmad ta ce "Engineer, a ina ka samo wannan 'yar caras ɗin ka aureta?" Daddy ya kalli Amina yayi murmushi ya ce "Haɗin Allah mana" Matar ta ce "Ba shakka, Tubarkallah 'yar kyakkyawa da ita, ya sunanki" "Sunana Amina" "Masha Allah, bari mu zo mu baku wuri, mu mu wuce daga muyi hira da amarya, Blessing" ta Ware murya tana kiran 'yar aikinta. Wata matashiyar yarinya ce ta fito, ta kalleta ta ce "Rakata bedroom ɗina" ta mayar da idonta kan Amina ta ce "Amina bita kinji, ina zuwa" Amina ta tashi ta bi blessing, Daddy ya bisu da kallo har suka shige. "Kai Engeener sai kace za a sace maka ita" Alhaji Abubakar yayi maganar cikin zolaya. Matarsa Hajiya Maryam tayi murmushi ita ma ta ce "Ashe dai kaima ka lura, wannan ƙauna haka Engineer" Dariya Daddy yayi ya ce "Hajjaju ni dai gata nan, a ɗan koya mata duk abin da ya sawwaƙa, na san ba a rasa abin gaya mata ba" Hajiya Maryam ta miƙe ta ce "Kar ka damu, bari in saka a kawo muku Abinci" ta wuce tabi hanyar da su Amina suka bi. Amina na zaune a kan Carfet ɗin ɗakin, ga ruwa da lemo a gabanta da blessing ta kawo mata. "A'a Amina ya kika zauna a ƙasa kuma, ga bakin gado nan dan Allah tashi ki zauna" Amina ta ce "A'a bakomai anty, nan ɗinma yayi" "A'a tashi maza dan Allah" ta saka Amina ta koma gefen gado ta zauna, ta janyo kujerar gaban mudubi ta zauna a gaban Amina, sannan ta ce "Amina 'yar wani gari ce ke?" "A kano nake, ƙaramar hukumar Shanono" "Masha Allah, amma naji kamar maigidan nan ya ce baki tare ba, kuma na ganku tare da shi Engineer" "Eh, na zo competition ne, shi ne ya zo shima" Cikin salo na wanda suka kwana biyu a duniya, Hajiya Maryam ta ce "ok a kina gidanku kenan a zaune?" "A'a, a gidansa nake, aiki nake a gidan ina karatu, mukayi aure sai na gama ya ce zan tare" A ranta ta ce "Kan uba, wato idan ka ɗauki kanka a wani, idan Allah ya tashi nuna maka kai ba kowa bane, sai an tausaya maka, duk jiji da kai da izzar Hajiya Zainab ashe 'yar aikinta maigidan ya aura bata sani ba, duk bala'in nata da shegen bin diddigin amma bata iya ganewa ba, lallai watan girbar abin da ta shuka ne ya tsaya, a halin yanzu sai abin da ta gani" Hajiya Maryam ta ce "Masha Allah, a nan ɗin tare kuke a wuri ɗaya da shi kenan" Amina ta ce "Eh" "Ahhh to ai ni yanzu kin zama ƙawata, hira zamuyi sosai" Amina ta ɗan waro ido tana kallon Hajiya Maryam, saboda ta san Hajiya Maryam ɗin ta haifeta. "Ya kika zaro ido ne? Matar abokin mijinki ce ni fa, ai shikenan mun zama ƙawaye, hira za muyi irin ta manya, ki daina wani sinne kai ni ba kunyarki zan ji ba" Amina dai ta sunkuyar da kai, tana wasa da hannun jakarta. "Kinga Amina kalleni nan" Amina ta ɗan ɗaga kai ta kalleta. "Ba wai ina son in ɓata zamanki a gidan aurenki ke da abokiyar zamanki bane ba, a'a ina son na ankarar da ke damar da Allah ya baki ne. Ai kin yi aiki a ƙarƙashin ta, kin san halinta na ƙwarewa a cin mutunci da wulaƙanta ɗan Adam ko bata yi miki?" Amina ta ce "Tana yi mini" "Yauwa, ki sa ranki Allah ne ya baki dama ki rama, ba wai ina nufin kiyi fito na fito da ita ba no, ki ƙwace abin da kuka haɗu ku kayi tarayya a kai, wato mijinku. Kin ga Mijina abokin mijinki ne, tare suka taso, 'yan gari ɗaya ne, sai dai mijinki gidansu suna da wadata nawa mijin kuma talakawa ne, Engineer Ahmad ya bamu gudunmawa sosai a rayuwa, tun kan yayi aure lokacin mu munyi aure, na kusa haihuwa amma mijina ba shi da kuɗin sayan kayan jarirai, hatta hakikar da aka yankawa 'yata ta fari Engineer ne yayi, mutum ne managarci mai halaye na gari. Tun da ya auri Hajiya Zainab, ya fara tara abin duniya ta sauya shi, baya jin maganar kowa sai tata, gashi azabtar da shi take yi, amma baya iya saurara kowa sai ita, ta raba shi da kowa nasa daga ita sai yaranta da ƙawayenta. Da tana hulɗa da ni, tunda duk garinmu ɗaya, muka haɗu a wani biki, take nunawa ƙawayenta ni, wai ni matar yaron mijinta ce, bamu da komai sai mijinta yayi mana. Ban ɗau abin serious ba, duk da naji haushi, ta haifi Fadila naje mata barka, ƙiri ƙiri ta nuna ba zata iya cigaba da hulɗa da ni ba a gaban mutane, rigar da na saya na kai mata mace a sakawa jaririya, ta ce Allah ya kiyaye ta saawa 'yarta wannan rigar, wannan riga ai sai dai irin 'ya'yana a gaban mutane, ina zan manta wannan?" Amina ta jinjina kai tare da jinjinawa rashin mutunci irin na Hajiya Zainab ta ce "Gaskiya ba zaki manta ba" "Ke dai bari, da nayi haƙur9 gashi komai ya wuce, ko da mijina bai kai nata kuɗi ba, kuma shi ɗin dai shi ne silar samun mijina wannan matsayin gani a cikin rufin Asiri da take ganin har abada ba zan samu ba. Shiyasa nake gaya miki, dama ce Allah ya baki, kuma jihadi zaki yi, danginsa mutane masu matuƙar son nasu, ga zumunci, amma sai da ta shiga ta fita ta sanya ya zamana babu wanda yake iya raɓar gidansa, idan kuwa kaje ƙarshe ka fito da ɓacin rai. Dan haka yanzu abin da nake so da ke, tun da har Allah ya sanya kuna tare ke da shi, ki yi ƙoƙari kiyi amfani da wannan damar, wajen shawo kansa ki nusar da shi illar watsi da zumunci, sannan ki nusar da shi illar abin da ya ke yi, amma ki sani hakn ba zai samu ba sai kin mallake shi a hannunki kamar yadda tayi a baya, amma ke kibi hanyar da ta dace wurin mallakar ta sa, wato biyayya da kuma Addu'a. Na san Engineer farin sani, mutum ne shi mai haƙuri, haƙuri na gaske makuwa, ga sauƙin kai da son mutane, kinga tun da Allah ya sanya duk cikin matan da ke kai kawo a kamfaninsa da manyan matan da ke Kano, Lagos da Abuja da sauran garuruwan da yake zuwa, babu wadda ya gani tayi masa ya aura sai kez to ki tabattar da ba ƙaramin so yake miki ba, dan haka biyayya duk abin da yake so bi shi ki fi shi son abun, in dai bai saɓa wa Addini da al'ada ba, ko kuma ki ga akwai cutarwa a ciki ba, zai zama naki ki jiya abinki yadda kike so" Amina ta ɗan kalli Hajiya Maryam, da mamakin maganarta ta ƙarshe, ta yaya zata juya Daddy wai yadda take so. Hajiya Maryam ta ce "Eh mana, ke ba kya karanta litatafan hausa ne?" Amina ta ce "Da ina yi, amma ya ƙwace mini waya" "Me ki ka yi ya ƙwace wayar?" Cikin wauta Amina ta ce "Faɗa muka yi" "Au kika zauna ku kayi faɗa har ya ƙwace miki waya, baki yi masa kissa kin karɓo ba? Ke baki karanta littafin Wata kissar sai mata ba ne? Baki ga yadda jarumar littafin ta yiwa mijinta ba" Amina ta ce "Ban karanta ba" "Karɓo wayarsa a tura miki, bari a kawo miki Abinci ki ci, ke dole mu yi zama na musamman da ke, akwai karatukan da yakamata nayi miki, karɓo wayar ta sa". Amina ta tashi ta koma falon, ta tarar da Daddy sun sakankance suna ta hira shi da Alhaji Abubakar. Yana ganinta ya mayar da hankalinsa kanta, taje ta zauna a kusa da shi, ya kalleta ya ce "Ya dai in zo ne?" "A'a waya zaka bani aro" "Nawa zaki biya?" Murmushi tayi ta ce "Yi mata kuɗi" Shima murmushin yayi, ya ajiye mata wayoyinsa uku, ya ce "Wacce zan ara mikin?" Ta saka hannu ta ɗau guda ɗaya, ta tashi ta koma. Alhaji Abubakar ya ce "Kai malam, gaskiya yarinyar nan tayi gaba da zuciyarka da yawa" "Bari kawai nake gaya maka, har mamakin kaina nake yi, Yarinyar ce akwai shiga rai sosai" Hajiya Maryam ta saka Amina a gaba, ta dinga koya mata abubuwa, da bata shawarwari, ta saka aka kawo mata Abinci. Tun la'asar suka je gidan, amma sai gasu har bayan goma na dare, suna gidan, Amina ta ƙaru da Hajiya Maryam sosai da sosai, ta rubuta mata lambar wayarta ta ce idan ta samu lokaci ta kirata a waya zasu dinga tattaunawa. Sannan ta buɗe jakar Amina ta saka mata wata leda a ciki ta ce "Gashi nan, wannan kyauta ce tsakanina da ke, kar ma ki bari ya san wannan, kayan gyara aure ne, waɗan nan na ledar kuma bakomai idan kin bari ya sani" Amina ta ce "Nagode sosai Anty, Allah ya saka da alheri ya sa ki fi haka" "Bakomai Amina, Allah ya baku zaman lafiya ya sanya tsohuwar gida ce, Allah ya sa ki riƙe mana shi amana kamar yadda muke tsammani daga gareki, dan Allah kiyi amfani da maganganun da muka yi da ke" "To in sha Allah Anty, na gode" "Bakomai kar ki damu, duk abin da ya shige miki duhu, ki kirani ki tambayeni" Ta rako Amina har falo, suka fita tare da su Daddy, har harabar gidan Joseph ya fito da motarsu. Daddy ya ce "Hajajju a bani matata haka mu tafi" Hajiya Maryam ta ce "Ni zuwan nan yayi mini kaɗan, zan zo ma dai da kaina kan ku tafi Lagos ɗin, ban gama da ita ba" "To yanzu dai ban kayata mu tafi, kar ta fara mura wannan gidan naku mai sanyi" Hajiya Maryam ta ce "Lallai mutumin nan ka samu kanka wallahi, sai na gaya wa Uwargida" "Sai kin dawo". Daddy ya ce "Meenalina, ki yiwa abokina godiya, ya saka miki dubu ɗari a account, ya ce kya sai turare" Amina ta ce "Kai har dubu ɗari kuma, ai dubu ɗari tayi yawa a sai turare" Gaba ɗaya suka kwashe da dariya, Hajiya Maryam ta ce "kar ki damu, ku gaida gida kar kiyi mura ace a gidana kika kwasa" Amina dai ta yi masa godiya, sannan Daddy ya buɗe mata mota ta shiga, shima ya zagaya ya shiga, suna ɗaga musu hannu suka tafi. Suna tafe a hanya ta kashingiɗa da jikin Daddy, kasancewar ta san password ɗin wayarsa, ta buɗe wayar ta fara karanta littafin Wata kissar sai mata. Koda suka isa gida, ta san ba wani abu zata yiwa Daddy ba, ta nemi wuri ta cigaba da karatun littafinta. "Wai ke ba zaki kula dani ba kin saka waya a gaba?" "Daddy kamar wani Baby, me zan maka naga a ƙoshe kake fa" Miƙa mata hannu yayi ya ce "To Bani wayata, tun da ta fini muhimmanci" Ɓoye wayar tayi a bayanta tana tura baki. Ɗagata yayi cak zai karɓe wayar, ta hau ɓoyeta, cakulkuli yayi mata, ba shiri ta saki wayar tana dariya. Ya ɗau wayar yana cewa "Me kike a wayar ne?" "Wani littafi fa aka tura mini nake karantawa, dan Allah ka bani" Yayi murmushi ya miƙa mata wayar ya ce "Shikenan, idan kin gama kije ki kwanta, ni bacci nake ji" Ta ce "Shikenan, goodnight" "Yau ba zaki tayani kwana ba?" Ta noƙe masa kafaɗa, ya ce "Ai shikenan, have a sweet dream, i love you" yayi maganar yana kissing ɗin goshinta, Amina har cikin ranta take jin daɗi idan ya ce yana sonta, amma ita ba ta iya gaya masa. Ya tafi ɗakinsa yaje ya kwanta. Amina ta gyara kwanciyarta a kan kujera, ta cigaba da karatun littafin nan. Sai da kammala tayi wata irin ajiyar zuciya, ta duba agogo ƙarfe ɗaya na dare, ta tashi ta tafi ɗakinta, tayi alwala tayi nafilfili, ta karanta Alqur'ani tare da yin Adduoi, ta nufi ka gadonta. Abin da ta karanta a cikin littafin da maganganun Anty Maryam take ta jujjuya a ranta. A fili ta furta lallai Mufeeda jaruma ce, kuma tayi rawar gani, wayyo Allah ina ma zan iya yiwa Daddy abin da Mufeeda take yi. Ni da Daddyna ma mai sauƙin kai ne, ba kamar mijin Mufeeda ba, kuma fa shekarunumu ɗaya da ita, kai to ya aka yi ita bata jin kunyar mijinta, kai wallahi kunya nake ji, amma kuma ai Anty Maryam ta ce idan ina son na mallakeshi sai na dinga yi masa biyayya. Idan fa ina yi masa kalaman soyayya zai ji daɗi, wayyo Allah ta ina zan fara kunya nake ji wallahi. Amma in sha Allah zan yi ta ƙoƙari in ga ya aurawa Khalil yarinyar da aka je aka ciwa mutunci,ai sai na rama wulaƙancin da aka yi mana ni da Baba" haka tayi ta saƙe saƙenta, har tayi bacci. Cikin baccin ta ji an ɗagata zaune, "Dama na sani, ba lallai kin yi bacci da wuri ba, har naje na dawo daga sallar Asuba amma baki tashi ba" Daddy yayi maganar yana mita. "Wai har Asuba tayi ne? Yanzu fa na kwanta" "Tashi ko inje in tsomaki a ruwa". Sai da yaga ta shiga toilet, sannan ya tashi ya bar ɗakin. Wunin ranar kallon Daddy take, tana son ko sau ɗaya ta gaya masa wata kalma ta soyayya, amma ta kasa kunyarsa take ji, gashi da ta kalleshi sai su haɗa ido, har sai da ya magantu ya ce "Wai me kike son faɗa ne?" Ta girgiza masa kai ta ce bakomai. Yana ta shirin tafiyarsu Lagos, ranar da zasu tafi da Safe, Hajiya Maryam ta zo. Amina taji daɗi sosai da sosai, sai dai tayi farinciki na ganin Amina tsaf da ita, daga ita har gidanta ba datti. Amina tayi murna da zuwan Hajiya Maryam, lokacin Daddy baya nan. Hajiya Maryam ta ce "Allah yayi dai nazo, Jiya Baby ya ce mini yau da daddare zaku tafi" Waro ido Amina tayi ta ce "Wace Babyn?" Hajiya Maryam tayi dariya ta ce "Mijina mana" "Shi ne Babyn" Amina ta faɗa tana ganin kamar abun ba tsari. Hajiya Maryam ta ce "Ke ba kin tsaya ba, baki karanta littafin ba?" "Na karanta, tun ranar" "To meye feedback? Kin fara jarrabawa?" Amina kamar za tayi kuka ta ce "Ni wallahi kunya nake ji" "Ke ƙaniyarki ke da kunyar, ana nuna miki Annabi kina rintse ido" Amina dai tayi jimmm. Hajiya Maryam ta cigaba da yiwa Amina lecture, ta bata wasu irin manyan kwalaban turare, na humra da 'yan ɗuri masu kyau da tsadar gaske. Ta ce "Idan kinji daɗin turaren nan, in ya ƙare kice ya sai wasu, ni ke sayarwa" "Wannan kuma, gasu nan sune Auren, ba a zama haka, kiyi duk abin da nace miki, sannan kiyi biyayya. Saura muyi waya kice mini baki yi ba" Amina ita kunya ce ma ta isheta, ita wannan matar bata jin kunya sam, har da gwada mata yadda zata dinga yiwa Daddyn magana da kwarkwasa take yi. Hajiya Maryam ta tafi ba daɗewa, Daddy ya dawo. Ta sanar masa da batun zuwan Hajiya Maryam, ya ce Aikuwa zai kira Hajiya Maryam yayi mata godiya. Ƙarfe shida na yammaci, Jirginsu ya ɗaga zuwa Lagos, suna cikin jirgi Amina na saƙawa da warwarewa. Ta raya a zuciyarta a Lagos ɗin nan, zata dage ko sau ɗaya ta ce tana son sa taga ya zai ji. Koda suka sauka a Lagos, Daddy ya ce a ɗaki ɗaya zasu dinga kwana, Amina ta tashi hankalinta, amma take ta ƙoƙarin dannewa, saboda kar ta ɓata masa rai, kuma Anty Maryam ta ce ta daina yi masa musu da jayayayya. Daddy yana kwance yana waya da Khalil, Amina ta shirya musu kayansu a wardrobe, ta sanya kayanta na bacci, ta shafa turarenta na wurin Anty Maryam, ita kanta ta yaba da ƙamshin turaren Hajiya Maryam. Ta gama abinda take, ta raɓa ta hau kan gadon, ta koma ƙarshen gadon ta kwanta. A hankali ya mirgina kusa da ita, ya cigaba da wayar sa. Ya kammala wayar tare da zuba mata ido. Ta kai hannunta hancinsa ta ce "Kaji turaren nan da ƙamshi?" "Tun da kika shafa nake jin ƙamshinsa, a ina aka samo mana?" "Anty Maryam ce ta bani" "Lallai ta kyauta, na yaba sosai matso inji ƙamshin sosai" Yayi maganar yana kamo hannunta cikin nasa ya ce " 'yar Babyna?" "Na'am Baby" "Meenal, you call me Baby?" "Eh mana, ko ba ka so?" "Ina so mana, saura kice kina sona kuma" A ranta ta ce "Laa dama yana son nace masa ina son sa' Tashi tayi zaune, ta kai bakinta kunnensa ta ce "ان احبك" Murmushi yayi ya ce "Alhamdilillah, abin da nake son ji kenan?" Karatun da Daddy ya fara karanta mata ne, ta kasa ganewa, ta so yi masa gardama amma ta tuna abin da Hajiya Maryam ta gaya mata. Ƙarshe dai a ranar aka rantsar da Amina, daga gigin ƙuruciyar da yake damunta, ya tabbatar da ita a matsayin matar da ya biya sadaki ya auro. Bai yi zaton Amina ba zata yi masa tijara ba. Duk wannan bakin da tsiwar, da zaƙalƙalewar tayi tsit. Sai share hawaye da take yi. Ba abinda take sai bin umarnin duk abin da , bayan ya taimaka mata tayi wanka ta dawo ta kwanta, ta toshe baki a cikin bargo tana kuka. Daddy ya zauna a kusa da ita, ya cirota daga bargon ya ɗan dubeta ya ce "Me kuma ya faru? Haba Babyna" Ta sake fashewa da kuka, yayi ta rarrashinta sannan ta ce "Bafa haka muka yi da Baba ba, ni yanzu me zance masa?" "Haba Meenal, yanzu idan ba ke zaki je ki gayawa Baban abin da ya faru ba, ya za ayi ya sani? Dan Allah kiyi haƙuri kuma kiyi shiru da bakinki, kin sai dai Allah ya tsinewa mai tona asirin aurensa". "Amma Daddy, ka san ban tare ba ai, kuma Baba... Bata ƙarasa ba ta cigaba da kuka. " To kiyi haƙuri dan Allah, karki gayawa kowa kin ji Sweetheart, wannan ma sirrinmu ne da bai kamata kowa yaji ba, namu ne mu biyu kawai da zai shiga kundin tarihin rayuwar mu" haka yayi ta lallaɓata, yana kwantar mata da hankali, har ta haƙura. Suka cigaba da rayuwarsu, Amina na cigaba da lallaɓa shi ya shiga lamarin auren Khalil, kuma ya dinga zumunci da danginsa, tana yi masa nasiha dai. Sai dai abin da yake haɗata da Daddyn, shi ne yadda yayi kunnen uwar shegu da batun Amina bata tare da shi ba, ya cigaba da rayuwar aurensa da ita. Amina da fari tana yi masa biyayya, daga baya kuwa taga bata kyautawa Baba ba, gashi 'yan makarantarsu tuni sun koma gida, amma banda ita, ida Baba ya samu labari bata san ya zata ji ba. Dan haka ta uzzura wa Daddy, a kan ita sai ta koma gida, ta sashi a gaba kukan safe daban na dare daban, ya gaji ya biya mata kuɗin jirgi ta koma Kano. Sai dai tun da ta dawo Kano, ta koma gida, ta fara zazzaɓi da ciwon mara, amma ta basar ta cigaba da sabgoginta. Tunda taje gidansu Azima, Ammi take kallonta, dan Azima ta sanar da ita 'yan makarantarsu sun dawo amma banda Amina, gaba ɗaya yanayin Amina ya nuna alamun ciki a tare da ita. Sati guda Amina ta sake komawa gidansu Azima, Ammi tana jinta suna faɗa da Azima, Amina tana cewa bata son ko ganin shinkafa balle ta ci. Daddy kuwa kasa jurewa yayi, saboda sabon da suka yi da Amina, dan haka ya shirya ya dawo Kano, suka cigaba da rayuwarsu tare, cikin soyayya da kulawa. uwa lokacin da Hajiya Zainab ta dawo. Lokacin da Amina ta kirashi a waya sanar masa ga abinda ya faru, hankalinsa ya tashi sosai, bai so cikin Amina ya zube ba, saboda yana daga cikin abin da yake ƙauna a rayuwarsa 'ya'ya, tonuwar Asirinsa sam baya gabansa a kan ɓarin da Amina tayi, hankalinsa ya tashi sosai da yaji batun Hajiya Zainab zata kori Amina. Hankalinsa ya tashi sosai, da ya dawo yaga Amina, ya ɗauke ta ya kaita Asibiti, sai zuba shagwaɓa take son ranta. "Meenalina, Allah ya kawo mai amfani, naji ba daɗi sosai ance mini biyu ne ma" "Ni baka ta lafiyata sai ka rasa 'ya'ya ko, Daddy na sha wahala sosai" "Am sorry Meenalina, ina zan so lafiyarki ta taɓu, Allah ya bamu masu amfani" Bayan nan ya kira Baba a waya, a kan akwai buƙatar ya dawo gida akwai magana, ya kira kawunnansa da suka ɗauro masa aure. Shine wannan zaman da suke yi yanzu, domin a warwarewa Hajiya Zainab zare da abawa. Alhaji Ahmad ya kalli in da Hajiya Zainab ke zaune ya ce "Zainab ina mai baki haƙuri, a kan abin da zan gaya miki yanzu, ban yi domin naci zarafinki ba. Na auri Amina 'yar wajen Malam Hassan watannin baya, kuma na ɓoye miki ne zuwa lokacin da Allah zai sa ta tare na sanar miki, sai dai kana nasa Allah yana nasa, Allah yayi yanzu lamarin zai bayyana, dan haka Aure muka yi da ita!!! AYSHERCOOL 08081012143GABA DA GABANTA NA AISHA ADAM AYSHERCOOL 61 Kawun Alhaji Ahmad, da suke kira da Baba Mamman, yayi gyaran murya ya ce "Haka ne, mune muka je muka nemawa Ahmada Aure, kuma aka ɗauro masa aure, amma batun a sanar miki da auren, wannan shi ke da alhakin yi, mai faruwa dai ta riga ta faru, abin da ya rage kiyi haƙuri ki karɓi ƙaddara, ita ce cikar kowanne musulmi" Bai ida ba Hajiya Zainab ta miƙe tsaye, fuskarta babu alamar rahama ko sassauci, ta kalli Alhaji Ahmad ta ce "Kayi abin da kake so, nima ka jirayi me zan yi, ka san kayi kaɗan kayi tsararo kayi mini Wannan haukan, wallahi baka isa ba, ko ni ko kai ina nan a Zainab ɗina da ka sanni, zaka ga ƙarshen rashin mutunci, kun goyawa ɗanku baya, ya wulaƙantani ya tozartani ko, mu zuba ni da ku shege ka fasa. Kai kuma tsohon banza munafuki annamimi, zaka ga abin da zan muku, a tarihin zuriyarku nan gaba wani ba zai ƙara marmarin yin cin amana ba, mutumin banza maha'inci" "Kar ki sake zagar mini uba" Cikin tsawa Baba ya ce "Amina, ki mini shiru da bakinki" "Ta dai cigaba, ni haryanzu wannan abar, ba ta kai na kalleta a matsayin kishiya ba ko da kuwa kucakar kishiya, dukkaninku zaku ga abin da zan yi" Ta juya ranta na mata zafi, ta bar falon. Baba Mamman ya ce "Ka gani ko Ahmad, abin da muke ta nuna maka kenan, da ka sani ka sanar da ita tun da fari" Kamar Daddy zai kuka ya ce "Haba Baba, ka san komai ka san halinta, idan har ta san ina neman aure, wallahi ba zata bari ba, ka san abubuwan da suka faru a baya ai" Baba Mamman ya kalli Amina ya ce "Amina tashi kiyi tafiyarki kin ji" ba Musu Amina ta tashi, ta nufi sashinsu. Hajara ta gani a tsaye, da alama taji duk abin da aka yi, Amina ta kalleta ta ce "To Hajara, sai ki daina yi mini kallon mutuniyar banza, naje ina kwana ɗaki ɗaya da maigida, har kina zargin ina baki kuɗi ne dan kar ki tona mini asiri, yau kinji abin da ake ciki, mijina ne, kuɗi da nake baki kuma kyautatawa ce, saboda idan na samu sonake kowa ma ya samu, ki daina yiwa mutum hukunci da abinda kika gani kawai a zahiri" Hajara dai tayi tsuru tsuru, tana jinnkna al'amarin da matuƙar mamakin yadda abubuwa suka wakana haka a ɓoye, hankalin Hajiya Zainab na kan kar ɗanta ya auro mata mai awara, ita kuma an aure mata miji, auren cin amana 'yar aikinta. Alhaji Ahmad ya ce "Baba Mamman yanzu ba yadda za ayi ku ɗan yi mata nasiha ko zata ji?" Baba Sagir ya ce "Kana gani fa a gabanka ta wulaƙantamu, muna magana ta tashi tayi zage-zage ta wuce, ai wannan kuma aikinka ne, mu kaga yanzu ma tafiya za muyi, Allah ya baka ikon haɗa kansu". Alhaji Ahmad ya lura da yadda jikin Baba duk yayi sanyi. Ya ce "Bari muje ɗaya gidan nawa, ku ci Abinci kuyi salla tukuna" suka ce su ba zasu zauna ba, tafiya za suyi, suka yi ta bawa Baba haƙuri a kan irin cin mutuncin da Hajiya Zainab tayi masa. Ya ce "Kar ku damu, ai idan da sabo ni na saba" Daddy ya saka Zakiru ya mayar da su Baba Sagir Dutse, ya kawo alheri yayi musu. Ya koma wurin Baba da duk jikinsa yayi sanyi,  "Malam Hassan, na san nayi maka laifi na saɓa yarjejeniyar mu, amma dan Allah dan Annabi kayi haƙuri, na san ban kyauta ba amma kayi haƙuri dan Allah, kuma wallahi ba laifin Amina bane ba, bata da laifi ina dai bak haƙuri" Cikin dattaku Baba ya ce "A'a bakomai, ai a yanzu kai ke da iko da ita, ni tunani nake yadda Amina zata zauna da kai a gidan nan, a wannan yanayin" "A'a Baba, babu damuwa komai zai zama daidai in Allah ya yarda, yanzu zan saka a mayar da kai Shanono, zan zo da kaina" "Amma ina jin tsoron kar wani abu ya sameta" Daddy ya ce "Ba abin da zai sameta in Allah ya yarda" Baba ya ce "To amma aikina fa?" Daddy ya lura da tsoron tafiya yake ya bar Amina. Daddy yayi ta kwantar masa da hankali, shima ya saka a kaishi gida. Hajiya Zainab kuwa sintiri ta dinga yi a ɗakinta, ji take kamar wuta ce take ci a ƙirjinta, wa zata tunkara da wannan maganar abin kunya da tozarcin da mijinta yayi mata. Gaba ɗaya kanta ya toshe ta rasa wani kalar abu za ta yiwa Alhaji Ahmad da Amina ta huce wannan mummunan baƙin cikin da suka ƙunsa mata, gaba ɗaya kanta ya kulle. Fadila kuwa da a kunnenta Daddy ya furta cikin Amina nasa ne, kuma ba ta kai ga barin falon ba, taji wai auren Amina ya yi, ta koma ɗakinta da gudu, ta faɗa kan gadonta ta fashe da kuka, Daddy ya gama da su ya tozarta su, ba wanda take tausayi irin Mummy, ta san yadda bata ƙaunar kishiya, amma Daddy ya rafka mata wannan wulaƙanci, ta san Mummy ba zata iya jurewa ba, ashe dan ya samu ya sake ne ya sanya ha tura su umara. Take taji wani matsanancin haushin mahaifinta ya kamata, dan ta san Abune mai wuya Mummy ta iya jure wannan abu da yayi mata. Duk da tarin fargabar da ke cikin zuciyarsa, haka ya dake ya tunkari ɗakin Hajiya Zainab, yana shiga ya tarar da ita zaune a gefen gado, tayi jifa da ɗankwalin kanta, sai nishi take yi kamar wadda take naƙuda. Ya ƙarasa ya zauna a kusa da ita, ya gyara zamansa zai yi Magana, amma cikin ƙaraji ta ce "Ahmad bana son jin komai daga bakinka, kai har kana da ƙwarin gwiwar da zaka tunkari inda nake har ka sanya idonka a nawa zaka yi mini magana? Tsohon munafuki mara imani, Ahmad banda idan auren ne ka auro mini mace da zan goga da ita, amma ka auri ƙasƙantacciya 'yar aikina saboda azzalumi ne kai" "Zainab ban zalunceki ba, kuma koma menene kece kika janyo shi, kece kika bani dama kika buɗe mini ƙofar aikata koma meye, kuma ki sassauta kalaman da kike amfani da su a kaina, aure nayi ba zina ba! Kuma adddini bai haramta mini yin hakan ba, Zainab da na biye ta taki da yanzu ina nan ina biye biyen matan banza a kwararo. Zainab kusan shekaru talatin muna tare, kina garani yadda kike so, tun a baya na so in ƙara aure amma sai ki uwa ki makarɓiya ki hana, ki soke abun, kika dinga bin diddigina da kishin tsiya da saka ido, amma baki san ki kula dani ba, ƙawayenki sun fini a wurinki. Zainab yaushe rabonki da shimfiɗata a matsayinki na matata, idan nayi magana sai ki ce mini wai na girmi haka, ta yaya? Bayan kinfi kowa sanin ba haka bane, ko kin manta a baya lokacin da sai na biyaki zaki zo in da nake, duk kin manta wannan ashe ban yi haƙuri da ke ba. Buƙatuna Abincina, da makamancinsu duk sai dai masu aiki suyi mini, da masu tsafta sa akasin haka, na nemi ki bini wurin aikin kika ƙi saboda ƙawayenki, shikenan ni ban san ciwon kaina ba, ba zan yi farinciki ba sai abin da kike so, wace irin zuciya ce da ke haka mara adalci, ki...... "Dalla rufe mini baki, wannan bai isa ya zama dalilin da zaka auro wannan matsiyaciyar yarinyar ba, duk ina matan da suka amsa sunansu mata a garin nan, ba wadda zaka aura sai ita? Talaka 'yar ƙauye da ta zo cin arziƙi" "Duk a matan garin nan, babu wadda tayi mini sai ita, ban haifeta ba ban aureta ba amma tana mini biyayya, ta na zaɓar farincikima a kan nata, ita kuwa zuciya tana son mai kyautata mata, na zo da niyyar in rarrasheki, in baki baki, amma tunda haka ne abin, kiyi abin da kike so, amma ki sani wallahi muddin wani abu ya samu matata, Sabo da kaza baya hana a yankata, sai na ɗau mataki a kanki kuma ki jawa Fadila kunne, ba ruwanta da matata, dan kune silar ɓarim da tayi" yana gama yi mata kashedin ya fice daga bedroom ɗin. Zama tayi dirshen a ƙasa, ta ɗora hannu a ka tana "Wayyo Allah na na shiga uku, na lalace Ahmad ni zaka wulaƙanta har ka fara nuna ta fini, wannan kucakar ƙazama 'yar talakawa, wallahi sai nayi maganinka sai kayi dana sanin abin da kayi mini. Fadila kuwa kasa jurewa tayi, ta tashi ta nufi ɗakin Mummy, ta ɗan tsaya a ƙofar bedroom ɗinta, taji alamar Daddy baya ciki, sai surutan Mummy, ta shiga ɗakik da sallama. Tausayin Mummy ya kamata, ganin yadda tayi zaman dirshen a tsakar ɗaki tana kuna, lokaci ɗaya har ta fita hayyacinta. Fadila ta ƙarasa gabanta, ta zauna ta dafa kafaɗarta ta ce "Haba Mummy, ya da saurin karaya haka? Ban sanki da haka ba dan Allah ki kwantar da hankalinki" Hajiya Zainab ta ɗago jajayen idanuwanta ta kalli Fadila ta ce "Fadila kinga abin da mahaifinki yayi mini ko?" "Na gani Mummy, amma dan Allah kiyi haƙuri ki danne zuciyarki ki daina kukan nan, kar a ga gazawarki" "Nayi ƙoƙarin yin hakan, amma na kasa dole na nunawa mahaifinku kuskurensa a kan abin da yayi mini, sai na sanya yayi dana sanin abin da ya aikata, Fadila yayi aure wata uku ban sani ba yanzu ban da wannan tsautsayin ya gifta sai dai na tsinci Yarinyar zata haihu a lokacin ne zan san ya aureta, 'yar aikin fa Fadila. Meye abin so sa burgewa a tare da ita?" "Dan Allah Mummy, ki daina wannan kukan, bari naji na samo miki wani abu ki ɗan ci ki kwanta ki huta, amma yarinyar nan ko da me take yawo sai ta bar gidan nan" Mummy ta yiwa Fadila wani irin kallo mai cike da takaici ta ce "Ni da ya bani saƙon cewar, in sanar da ke bake ba matarsa idan kika kuma yi mata wani abu, zai ɗau mataki a kan ki" Waro ido Fadila tayi ta ce "Daddyn?" "Zan yi miki ƙarya ne?" Fadila ta ce "Innalillahi wa innalillahi raji'un, 'yar aiki ta zame mana annoba". "Ta zamewa kanta dai, ai aljani bai san wuta ba sai ya taka, shiyasa ba kunya ba tsoro ta kalli tsabar idona take gaya mini Gaba ma akwai gabanta, to nima zan gwada mata aljani bai san wuta ba, sai ya taka ta" Amina kuwa tana kwance a kan katifar ɗakinta, saboda haryanzu jikinta babu ƙwari, sai ga kiran Anty Maryam a wayarta. Amina ta ɗaga tana gaisheta. "Ke Amina yaya ake ciki, Baby ya ce mini wai Hajiya Zainab ta san batun aurenku ya maganar take, tun jiya nake kiran wayarki bata shiga". "Eh Anty Maryam, ta sani ɗazun nan Babana da su Baba mamman suka tafi, sun zo an yi mata bayani, sai masifa take da kumfar baki wai zan gani" "Ba wani nan, bawa bai isa ya yiwa kowa komai ba face abin da Allah ya ƙaddara masa". Amina ta ce "Haka ne, shiyasa ma ni ban tsorata ba, tunda ina Addu'a" "Yauwa, ki cigaba da Addu'a ki kuma cigaba da kula da shi, ba abin da ta isa tayi miki" "Haka ne Anty Maryam" "Yauwa, aure ai ba aibu bane, tun da Allah ya ce ayi, ita ba a auren aka aureta, tun yana ƙoƙarin ƙara auren tana hanawa har ya haƙura saboda tijararta, ni kain nan da kike ji da gani, mu uku ne a wurin mijinmu" Amina ta zare ido ta ce "Ku uku?" "Ƙwarai da gaske mu uku, amma mijina yana mutuntani, yana bani girmana a matsayina na Uwargida da aka yi gwagwarmaya tare, kuma gaba ɗaya matan nasa nima girmamani ske yi, abin da nake so shi ake yi, amma nima sai na dubi zatin Allah bana goyon bayan ya cutar da 'yar kowa, nima na kai 'ya'ya ɗaki, kuma ƙannena suna gidan wasu, duk wadda aka wulaƙanta a gidan miji ni aka yiwa, dan haka ban yarda in wulaƙanta 'yar kowa ba dan mijina yana jin maganata. Kuma tsantsar haƙuri da biyayya ce ta sanya yake bani wannan girman. Dan haka ki zauna da shi saboda Allah, idan taga zata zauna da shi shikenan, idan haukan zata cigaba da yi ba ruwan ki da ita, kuma kar ki yadda ki ƙasƙantar da kanki, matsayinku ɗaya yanzu duk matansa ne" Amina tayi ajiyar zuciya ta ce "Hakane na gode sosai Antyna" Suka yi sallama, Amina ta ajiye wayar, gaba ɗaya ji tayi gidan ya isheta, so take ta tafi ko gidansu Azima ne ta ɗan sarara. Baba kuwa har aka kai shi Shanono cikin ɗar-ɗar yake. Bai san meka iya biyo bayan tahowarsa ya baro Amina ba, ya sna halin Amina a tsaye take, a baya ma yana tausarta ne yana ja mata kunne, balle kuma yanzu da ta san karanta ya kai tsaiko a gidan, ba zata lamunci a cigaba da wulaƙanta ta ba. Tun da ya koma Inno ta fuskanci yana cikin damuwa, amma yaƙi ce mata komai, har sai da ta gaji, ta magantu ta ce "Nifa ba ka ce mini komai ba" "A kan me fa?" "Kace an maka kiran gaggawa can wurin aikin naka, ka dawo gida fuskarka babu daɗi, kuma baka ce mini komai ba, ko wani abu ne ya samu Yarinyar?" Baba ya ce "Eh to kusan hakan, ɓari tayi" Zabura Inno tayi ta ce "Wane irin ɓari kuma?" Baba ya ce "Wane irin ɓari mata suke yi? Na ciki mana" "A ina Amina ta samu cikin har tayi ɓarinsa" tayi maganar jikinta na rawa. "A'a ke kin ji ki wata tambaya, a wurin mijinta mana" "Malam to ai bata tare ba" "To, kin san halin Mutanen na zamani, can in da ta tafi birnin tarayya a can suka tare, ni godiyar da nake yiwa Allah shi ne, da ban zafafa a kan maganar auren nan ba, na barwa Allah zaɓinsa aka yi, da ko ba ayi ba idan da rabon zuwan abin cikinta duniya sai ya zo" "Malam kaga irinta ko, ayi wa yarinya aure tunda wuri kaƙi kai sai tayi boko, ai gashi nan" Baba ya ce "Ikon Allah, to ai da auren nata dai yanzu ko, a irin tarbiyya da addu'a da muke yiwa Amina ni na san ba zata bani kunya ba, kuma ba albarkacin bokon ta samu mijin da yake ta ɗawainiya da mu ba, har na da na kusa da mu ba? Banda wanda ita ma take aikowa ba, Ai ki gode Allah boko ta yi mana rana. Ni babban abin da ya dameni, yadda matar gidan ta tashi hankalinta, dan kin san bata san an yi auren ba, ina tsoron kar tayi wa uwata wani abu" A rikice Inno ta ce "Malam kuma ka taho ka barota a can? Idan ta yi mata wani abun fa, da ka sani ka taho da ita" "Mijinta ya fimi iko da ita, dan haka ba yadda za ayi na ɗaukota, na gaya miki ne dan mu haɗu mu cigaba da yi mata addu'a, kiyi haƙuri ki kwantar da hankalinki ba abin da zai faru sai ikon Allah, in sha Allah" yayi ta kwantarwa da Inno hankali. Amina na nan kwance, mararta na cigaba da ciwo, kaɗan kaɗan, Daddy ya shigo ɗakinta, karo na farko da ya taɓa shiga ɗakinta na aiki. Ya ƙarasa ya zauna a kusa da ita, ta tashi zaune ita ma, ba tare da tayi magana ba. "Sannu my dear, ya jikin?" Ta ɗan yamutsa fuska kaɗan sannan ta ce "Da sauƙi" "Yanzu me zaki ci, naje na samo miki?" "Bakomai, kawai ka kaini gidan Ammi na ɗan huta, ko zuwa dare ne sai ka ɗauko ni" Ya ɗan gyara zamansa yana kallonta ya ce "Amina dole azo ayi batun tariyar nan, kiyi exms ɗin nan a gidanki, kawai zan saka a sake gyara miki wancan gidan nawa, idan kuma wani kike so sai a saya" Amina a ranta ta ce 'Anyi ba ayi ba kenan, ai sai Hajiya Zainab ta san bata da wayo tukuna. Ta ɓata fuska ta ce "Ni gaskiya ka barni a nan, haka kurum taje ta yi mini wani abu a can gidan, gida nika ɗai" "A'a Meenal, akwai ma'aikata ai a gidan bana son rigima ne, gara na rabaku" Ta noƙe kafaɗa ta ce "Kawai ka barni a gida, daga ni sai ƙarti suna gadina, a'a gaskiya gara ina nan ɗin, ko wani abun zata yi mini, ai da mutane a gidan nan, balle ba abin da zata yi mini ma, kawai sai na zauna a ɓangaren ka, ni ba ruwana da ita ai" "Anya kuwa Meenali kin tabatta?" Ta jinjina masa kai. Ta ce "Sai kuma.." "Sai kuma me?" "Sai kuma nima gaskiya kayi mini walima, a san aure muka yi, tunda ba kowa ya san hakan ba, idan na gama Neco sai ayi walimar gama makarantata da tariya" Daddy ya ce "Sai me kuma?" Ta kai hannunta fuskarsa ta ce "Sai kuma a maye mini gurbin wannan damuwar da sakin fuska" "Meenal, dole na shiga damuwa, ban so al'amarin nan ya zo a haka ba" "Kayi haƙuri, ka kwantar da hankalinka komai na Allah ne, kuma daga gareni ba zaka samu wata matsala ba in Allah ya yarda. Allah ya baka ikon yin adalci a tsakaninmu, amma dan Allah ka daina wannan damuwar" Ya ɗan numfasa ya ce "Haka ne, Amen zamu je in kai ki gidan su Aziman ne yanzu?" "A'a na fasa, ka samu ka ci Abinci ka huta, kar jininka ya hau dan Allah" "Shikenan, amma ya kike jin jikina naki ba wata matsala ko zamu koma?" "A'a babu wata mata, naji sauƙi sosai" "Shikenan bari in tashi, idan da wani abu sai ki kirani kawai a waya" "To Babyna" ta amsa tana lumshe masa ido. Murmushi yayi sannan ya tashi ya fita daga ɗakin. Hajara sai sake jinjina lamarin take. Fadila da ƙyar ta iya rarrashin Mummy, ta nemi wuri ta kwanta, ita kuma ta koma ɗakinta, tana cigaba da tunanin wace shawara zata bawa Mummy. Ita kanta ta dasa a wani muhallin da zata ajiye abin da Daddy ya aikata. Wasu hawayen takaici suka shiga zubo mata, saboda ita kanta a ganinta wulaƙanci ne da cin zarafi ga mahaifiyarsu. Wayarta ta ɗauko tana kuka ta kira Khalil a waya, tayi sa'a wayar na fara ringing ya ɗaga, yayi mata sallama. Kasa Magana Fadila tayi sai uban kuka da ta fashe da shi. A rikice Khalil ya ce "Fadila menene? Meyafaru?" "Daddy ne Khalil" "Me ya sami Daddyn?" Ta share hawaywnta ta ce "Khalil Daddy ne yayi aure" Khalil yayi tsaki ya ce "Shine zaki ɗaga mini hankali, wallahi na zata wani abin ne ya same shi" "Khalil, baka yi tunanin wani hali Mummy zata shiga ba? Ka san wa ya aura ne? 'yar aikin nan Amina 'yar gidan mai gadi fa, could you imagine?" Khalil ya ce "To kuma shine kike wannan kukan kamar ance Daddy ya mutu? Ni duk kin tayar mini da hankali" Fadila ta ce "Khalil, baka damu da halin da Mummy zata shiga ba ne? 'yar aikinta fa ya aura?" "Fadila aure fa kika ce, Aure yayi ba wani abu ba dan Allah karki tayar mata da hankali da wannan kukan da kike yi" "Amma Khalil ka bani mamaki fa, ka manta yadda Mummy bata son kishiya? Wato ko a jikinka ko?" "Ba haka bane ba Fadila, yanzu ace mahaifinmu ya nemi 'yar wani a waje fa? Na san zuciyar Mummy babu daɗi, na san ba a kyauta mata ba, amma kamata yayi ki kwantar mata da hankali, ba ki zauna kina kuka ba, ta sake shiga cikin damuwa ba. In Allah ya yarda zan shigo a satin nan, amma karki bari Mummy ta ce zata yi wani abu da zai janyo mata dana sani a nan gaba" Gaba ɗaya haushi ne ya kama Fadila, saboda gaba ɗaya ji tayi kamar Khalil bai damu ba sam. Kashe wayar tayi, ta ajiye, ta fito domin ta koma wurin Mummy. Tana fitowa falo ta ga Amina ma ta fito, tana ta share share, tana gyara falo. "Ke!" Fadila ta dakawa Amina tsawa. Amina ta ɗago kai ta kalli Fadila. "Baƙar munafuka algunguma, saboda munafurci shine ki auri mahaifina kinga kuɗi jiki na rawa kika shiga kika fita kika aureshi, to wallahi kin kawo kanki kabarinki, sai kin bar gidan nan da ƙafarki, baƙauyiya dabba kawai mayyar abin duniya". "Fadila kenan, duk abin da zaki gaya mini, ma riga na gama da ke, tun da na haɗa shimfiɗa da babanki. Daga ke har mahaifiyar ki zan baku shawara, ba ruwanku da ni, kuyi rayuwarku nayi tawa mu zauna lafiya, idan ba haka ba yanzu na fara baku mamaki, a cikin gidan nan ku kiyayeni!!! AYSHERCOOL 08081012143GABA DA GABANTA NA AISHA ADAM AYSHERCOOL 62 Murus bakin Fadila ya mutu, ba abin da take sai bin Amin da kallo, ga kalaman na Amina ba ƙaramin baƙantawa Fadila rai suka yi ba, wai har ita Daddy zai ce a yiwa warning a kan wannan Yarinyar da take yiwa kallon ƙasƙanci. Amina ta bata mamaki ƙwarai da gaske. Amina kuwa ta cigaba da aikinta, ta share Fadila da ke tsaye tana binta da ido. Kasa jurewa Hajiya Zainab tayi, ta ɗau wayarta ta kira Hajiya Salma, har ta kusa katsewa Hajiya Salma ta ɗaga, suka gaisa Hajiya Salma ta ce "Ya naji muryar taki ƙasa-ƙasa ko baki da lafiya ne?" "Hajiya Salma ba gara ace kwance nake ba lafiya ba, idan likita ya dubani wataƙila na warke ba, a kan masifar da nake ciki a yanzu" "Innalillahi wa innalillahi raji'un, meyafaru ne?" "Hajiya Salma na ƙara yadda, namiji ƙanin ajali ne, tsawon shekarun da muka yi tare, a wannan karon ya gwada mini halin nasu" "Zainab, dan Allah ki warware mini ki daina yi mini magana kwan gaba kwan baya, me yayi miki?" Ta  ɗan numfasa sannan ta ce "Aure yayi" "Shi wa?" "Ahmad mana Salma, aure yayi ban sani ba yau watanni kusan uku da ɗaura masa aure, sai jiya Allah ya toni asirinsa, kin san abin baƙin ciki kin san wa ya aura?" "Bala'i, wace 'yar hau ɗin mai tsautsayin masifar ya aura?" "Salma 'yar aikina, 'yar wurin maigadi" "Laila ha illalahu Muhammad Rasulullah Sallallahu alaihi Wasallam, dan Allah Zainab kice mini da wasa kike yi mana" Cikin karaya Hajiya Zainab ta ce "Na taɓa yi miki irin wannan wasan ne?" "Innalillahi wa innalillahi raji'un, amma Ahmad ya cika mara mutunci, shi duk matan duniya ya rasa wadda zai aura sai wannan? Amma Zainab kina me har alaƙa ta shiga tsakaninsu suka yi aure baki sani ba" "Hmm, Salma munafuncin ɗa namiji ya wuce lissafinki da tunaninki, ko da wasa bai taɓa nuna wata alama na yana son Yarinyar nan ba, Rashin kunya tayi mini, Fadila ta tureta ta faɗi sai jini ya ɓalle, na kira Doctor Aliyu aka dubata sai ga ciki, na kira shi nace zan koreta ya ce in jira ya dawo, ashe wai ya aureta wata Uku kenan, wai idan ta gama jarrabawa zata tare, sannan ya gaya mini, Ashe abin competition da ta tafi Abuja suna tare, Salma na rasa yadda zan yi da raina, ji nake tamkar na balbala fetur na ƙonemu duka a gidan, kaina ya toshe na rasa mafita". Hajiya Salma ta ce "Ki kwantar da hankalinki, ai ba zamu so kiyi abin da za ayi mutuwar kasko ba, ubansu zamu ci sai ta fita ta bar gidan nan ko tsirara ne, shi kuma zai gane bashi da wayo, zan yiwa Turai magana zamu zo" "To shikenan Salma, sai anjima" "Dan Allah ki kwantar da hankalinki, kar kiyi musu wani abu da zaki illatasu, abu ya kwaɓe miki, ki bari dai mu zo" "In Sha Allah, ba abin da zan yi sai kun zo ɗin" suka yi sallama ta kashe wayar. Amina jin ta ɗan ji sauƙi ya sanya, ta ware ta cigaba da aikinta, amma hankalinta na kan Daddy, tunda ya fita bai dawo ba, ta san yana tsoron dawowa saboda Hajiya Zainab zata rikita masa lissafi. 'Aikuwa ba zan abri hakan ta faru ba, idan ita bata son sa ni ina so, ba zata katse mini walwalarsa ba, wadda ita ce tsanin farinciki na ba' Kitchen ta shiga tana gaganiyar ɗora Abinci, Hajara ta shigo Kitchen ɗin tana ganin Amina, da sauri ta ce "Amina ai kinfi ƙarfin wannan aikin yanzu, ga baki da lafiya ga shi kin zama matar gida, ai wannan aikin sa mu". Amina tayi murmushi ta ce "Ni ɗin wace da ba zan aiki ba, in naɗe sai dai ayi mini komai, ladan da zan samu fa. Manta kawai zan yi aikina, kya tayani da abin da ba a rasa ba". Hajara ta ce "A'a Amina, idan Allah ya ce ka huta ai sai ka huta, ke ina ke ina wannan aikin yanzu, yanzu fa daidai kike da masu gida, ke ma matar gidan ce, dan kije ki huta nayi aikina" "Hmm, lallai Hajara gani kike da wasa nake" Amina ta cigaba da ayyukanta. Sai da ta kammala, Hajara na tayata suna hira, amma Amina ba ta bari Hajara tayi mata tambayar rainin hankali ba, ko bin diddigin taji yadda abubuwa suka gudana ba. Ƙarfe takwas na dare, Amina ta gama komai ta cewa Hajara, ta je ta sanarwa da su Hajiha Zainab, an gama girki su fito suyi dinner. Ita kuma ta wuce ɗakinta, ta ɗau waya ta kira Daddy. Yanayin yadda ya amsa wayar kawai, ya isa ya nuna maka yana cikin damuwa. "Hello My dear kana ina ne?" A ɗan rikice ya ce "Lafiya, wani abin ne yafaru? Ko wani abun tayi miki?" "A'a ni ba abin da tayi mini" "To jikin ne?" "A'a fa duk ka kwantar da hankalinka, naga haryanzu baka dawo bane ba, nayi maka girki ka dawo kaci Abinci ka kwanta ka huta mana" Yayi ajiyar zuciya ya ce "Zan dawo in sha Allah" "Yauwa dan Allah ka dawo yanzu kaji My" "Shikenan Meenali, gani nan" ta katse kiran, ta ajiye wayar ta shiga wanka. Hajara kuwa koda taje ta sanar da Fadila an gama girki, wata irin tsawa ta daka mata, ta koreta daga ɗakinta, saboda shirme kuma, sai ta tafi ɗakin Hajiya Zainab, wai ko ita zata ci. Wata ashariya da Hajiya Zainab ta bankawa Hajara, bayan ta gama sanar mata da batun an gama abinci, sai da Hajara ta rikice. "Munafuka kema kin san komai, dake aka haɗa kai, ki ƙulle kayanki sai kin bar mini gida kema, gayyar tsiya gayya jaraba matsiyatan banza da na wofi, zaki fita ki bar mini ɗaki ko saina taka wuyanki, algungumai zuriyar tsiya" sum sum Hajara ta baro ɗakin Hajiya Zainab, ta tafi wurin Amina. Ta tarar da Amina a zaune, tana ta shafa turare. Amina ta kalli Hajara da take kamar a razanae ta ce 'Lafiya kuwa?" "Sunce ba sa ci, ni wata uwar ashar da aka yi mini, tunda nake ban taɓa jin irinta ba, dama ace mini matsiyaciya na saba, amma wannan ashar tayi mini zafi, wai kuma nima ta koreni barin gidan nan zan yi" Hajara ta ƙarasa maganar kamar tayi kuka. Amina ta ɗan jinjina kai ta ce "Kiyi haƙuri, ba in da zaki in sha Allah" Da ta gama shirinta ta windown kitchen taje ta leƙa, taga Alhaji Ahmad ya dawo. Ta shirya ta tafi sashinsa, da kayan Abincinsa na dare. Da sallama ta shiga, ya amsa mata yana zaune yayi shiru, alama yana cikin damuwa. Ta zauna a kusa da shi ta ce "Sannu da zuwa" "Yauwa Meenal, ya jikin?" "Jiki Alhamdilillah na warware, ga abinci nayi ta so ka ci" Daddy ya kalleta ya ce "Baki da lafiya kika yi girki?" "Idan ban yi ba kai me zaka ci, me mutanen gidan za su ci? Naji sauƙin jikina ne, ta so ka ci" "Meenal bar abincin nan kawai" Ta marairaice ta ce "Dan Allah ka ci, ga yunwa ga damuwa da wanne zaka ji" Ganin duk ta damu ya sanya shi haƙura, ya ci Abincin da kanta ta dinga ba shi tana yi masa hira, har ya ɗan saki ransa. "Daddy, nayi girki naga mutan gidan sun ƙi ci, duk da na san haushina suke ji, amma ni ba zan daina ayyukan da nake na gidan nan ba, daga girki gyaran part ɗinka kan na tare, gyaran ko ina ma, sashensu ne kawai Hajara ta dinga gyara musu, kuma ni zan zauna da su tsakani da Allah babu ruwana da su, ni dai fatana kawai Allah ya baka ikon yi mana adalci" Yayi ajiyar zuciya ya ce "Meenal kenan, naji daɗin maganarki Allah ya dafa mana" Ta amsa da "Amin" sai da ya gama ci, ta tashi tana masa sallama ya ce "Ba zaki kwana a nan ba?" "Saboda me zan kwana a nan?" "Ba zaki buƙaci wani abun ba? kije ki kwana ke kaɗai keda baki da lafiya" "Ba abin da zai faru da ni in sha Allah, good night" tayi kissing ɗin lips ɗinsa. Bayan tafiyar Amina, ya sake komawa wurin Hajiya Zainab, saboda yana matuƙar jin tausayinta, ya san kishi shi ne weak point ɗinta, bata ƙaunar taga wata ta raɓe shi, amma lokaci guda ya shammaceta haka. Ko da ya tura ƙofar ɗakin, a zaune ya tarar da ita a kan gado, tayi uban tagumi. A hankali ya ƙarasa in da take, ya zauna a kusa da ita, ya janyota jikinsa amma kamar ya haɗata da wuta, a fusace ta fizge ta ja gefe. "Wallahi Ahmad ka kuma gangancin taɓani, sai na illataka kai saboda tsabar rashin mutunci da rashin kunya har kana da ƙwarin gwiwar tunkarar in da nake ka haɗa jikinka da nawa, kaje ka ƙarata a wurin waccan 'yar matsiyatar" Daddy ya ce "Calm down please, Zainab duk abu kece matata ta fari, kuma ba zan so duk wani abu da zai tarwatsa kan iyalina ba, dan Allah ki kwantar da hankalinki, ki fuskance ni. Rana ɗaya gaba ɗaya kin fita hayyacinki ki rame lokaci guda" "Kaga bana son wannan soki burutusn naka, ji nake kamar zuciyata ta fashe, na tsaneka Ahmad bana ƙaunarka ko son ganinka bana yi, na tsani mai sonka ma dalla tashi ka fita ka bar mini ɗaki". "Na ji ba kya sona, ba komai ni ina sonki, amma kiyi haƙuri ba zan fasa baki haƙuri ba, naji na yi miki laifi na karɓa amma ina neman Afuwa, dan Allah kiyi haƙuri ki samu ko Abinci kici" "Wallahi Ahmad kai ba ƙaramin munafuki bane ba, da can da in ci Abinci da na mutu ba ruwanka, sai yanzu zaka wani lallaɓani wai naci Abinci, ni zaka yiwa fuska biyu saboda rashin tsoron Allah?" Munanan kalaman da Zainab ke amfani da su a kansa, ba ƙaramin ciwo suke masa ba, yana ta dannewa yana cigaba da rarrashinta amma sai cigaba take da gasa masa su yadda take so. Bai sake ce mata komai ba, ya tashi ya bar mata ɗakin. Wayewar garin Allah, Amina ta saka a ka fitar da Abincin daren jiya da basu ji ba, aka bayar, tayi girkin safe ta ajiye musu, sannan ta je ta kaiwa Daddy nasa. Ganinta da uniform ya sa Daddy ya ce "Baby har zaki iya zuwa makaranta?" "Eh mana, yau zamu fara exams fa, ga Abinci nan ka karya, idan an tashi ina gidan su Azima, da magariba sai ka ɗaukeni" "Ok shikenan, hakan ma yayi, a dawo lafiya, Allah ya bada sa'a, in sha Allah yau zan cika miki alƙawarin abin da kika yi ta nacin nan a kansa" Waro idanuwanta tayi waje ta ce "Da gaske Daddy?" Ya jinjina mata kai. Jikinsa ta faɗa tana murna ta ce "Allah ya biyaka da Aljanna my love, kai mutum nagari Allah ya ƙara wadata da arziƙi Hubby" Murmushi yayi ya rungumeta Sosai ya ce "Amin Meenalina, kema Allah ya saka miki da alkhairi da ankarar da ni abubuwa masu muhimmanci. Allah ya kawo mana wasu twins ɗin da kin gama exams Baby" Rufe fuska ta shiga yi, saboda kunya da ta kamata. "Ba zaki ce Amin ba" Ɓoye fuskarta tayi a ƙirjinsa ta ce "Ni kunya nake ji" Dariya ta bashi ya ce "Kunya kuma, madam kice Amin kawai". "Na faɗa a zuciyata ai" Yayi murmushi ya ce "Zo ki tafi kar ki makara, ba dan wancan uzurin ba, da ni zan kai ki, ki tafi da magungunan ki ki samu ki sha. Allah ya kiyaye hanya" "Amin Dear na" ta tashi daga jikinsa ta fice tana ɗaga masa hannu. A yadda Fadila take jinta, da halin da Mummy take ciki, bata ji zata iya zuwa makaranta ba. Kafin Daddy ya fita, sai da ya kuma leƙawa wurin Hajiya Zainab, ta sake ƙare masa zagi da cin mutunci, ya fita ransa babu daɗi sam. Ƙarfe tara, Fadila yunwa ta gallabeta taje dining ta tarar da Abinci, ta karya, ta kuma komawa wurin Mummy tana cigaba da bata haƙuri. Da ƙyar ta ɗan ci Abinci kaɗan, Fadila ta koma nata ɗakin. Ƙarfe goma na safiya, su Hajiya Turai suka iso gidan, gaba ɗaya yadda suka zo gidan kamar masu shirin zuwa ya ƙi. Har bedroom suka iske Hajiya Zainab, duk tayi wani iri. Hajiya Turai ta ce "Zainab, gaskiya kinyi sake, ke kuwa kina me wannan ɗanyen aikin ya faru a gidanki? Idan ban manta ba kwanaki na ja miki kunne a kan wannan Yarinyar, amna ki ka yi biris da ni, kika nuna mini ba abinda zai iya, ga shi kwaikwaya miki rashin mutunci da rashin daraja, amma Allah wadaran halin Alhaji Ahmad, wannan ai ba budurwar zuciya bace sai dai ace bunsurar zuciya ce da shi. Wato a baya ya buga ya buga, kin toshe bai samu kafa ba, shi ne ya ɓullo miki ta bayan gida, kai maza sai Allah" Hajiya Salmanta ce "Uhumm ai ni gaba ɗaya kaina yama kulle, na rasa abin yi, namiji ƙanin ajali, buhun ƙaya kenan, mugu ɗan masara ana kayanka kana kayan gemu" Hajiya Zainab ta rausayar da kai ta ce "Ban taɓa zaton Ahmad zai yi mini haka ba, na rasa mema zan sam na huce, tun jiya nake zaginsa amma zuciyata ta ƙi samun salama" Turai ta ce "Ina ita munafukar Yarinyar take?" "Ina na san musu, ni tun jiya ban kuma fita ko falo ba" "Au barinta kika yi ta kwanar miki a gida? Baki ci ubanta kin korata ba" "Hajiya Salma, al'amarin nan ya zo mini a bazata, Yarinyar nan fa a tsaye take, bata da mutunci ko kaɗan ban gane hakan ba, sai da wannan abun ya faru. Kin san mutumin nan har warning yake mini, wai in gayawa Fadila ni da ita ba ruwanmu da matarsa, Yarinyar nan idan ban bi a sannu ba ƙarshe ni ta koreni daga gidan, dan da biyu ta aure shi, dan ta rama abin da nake wa ubanta" Turai ta ce "Ke Auzibillahi wane irin ta koreki daga gidan, ai sai dai ita ta fita ta bar shi, nijar zamu tafi wurin malamai dan ubanta sai bi daji tsirara tana hauka" Hajiya Zainab ta ce "Hauka kuma, ni ba ruwana, kawai ta bar mini gida, yayi mata korar wulaƙanci" Hajiya Salma ta ce "Ke dalla can banza kawai, idan ya saketa daga baya suka kuma jonewa fa, ta haukace ta bi bola kawai. Kuma ki buɗe masa wuta da rashin mutunci da tashin hankali, ki hana shi kwanciyar hankalin da zai zauna ya ji daɗin Auren, ki buɗe masa wuta ba sani ba sabo" Haka suka cigaba da hure mata kunne, da ɗorata akan keken ɓera. Amina kuwa tana gidan su Azima, suna falo sun ci Abinci suna hira, Daddy ya kirata yake tambayarta, ta sha maganinta kuwa? Ta ce masa yanzu zata sha, bayan ta ajiye wayar, ta duba jakarta ta ɗauko ledar maganin. Ammi ta ce "Baki da lafiya ne?" "Eh amma na warke?" "Mhmm meya sameki haka ne?" Shiru Amina tayi ta fara kame-kame, ɗaya bayan ɗaya Ammi tabi magaungunan da kallo, ta kalli Amina ta ce "Idan kin sha maganin ki sameni a ɗakina" Amina ta amsa da to. Kamar yadda Ammi ta umarceta, haka taje ta sameta a bedroom ɗinta. Ammi ta kalli Amina sannan ta ce "Amina, maganin meye wannan, ki gaya mini gaskiya meye ya faru?" Amina ta ce "Bakomai, ai na warke zazzaɓi nake yi" Ammi ta ce "Amina, 'ya na ɗaukeki, garin yaya haka ta faru bayan baki tare ba" Amina a ranta ta ce "Na shiga uku da wannan tereren bankaɗar, kowa sai ya san halin da nake ciki, ya aka yi Ammi ta gane wani abu?' "magana fa nake Amina" "Ammi ai ban gane a kan me kike magana ba" "Laaa kun ga 'ya zata raina mini hankali? Meya haɗaki da maganin ƙarin jini na masu ciki" A zuciyarta ta sake cewa "Wayyo Allah na shiga uku ni Amina' A fili kuma cikin jin kunya ta ce "Ammi ai ya zube' "Garin yaya? Ya aka yi haka ta faru Amina? Ke ba kya gudun ayi miki mummunar fahimta tunda ba kowa ya san kun yi aure ba, kuma uwargidanki ta sani ki shiga uku? Tun da ba kirki ne da ita ba". "Ai yanzu ta sani" "Kamar yaya?" Nan Amina ta gaya wa Ammi komai, Ammi tayi salati tana mamakin yadda abubuwa suka gudana. Ammi ta numfasa ta yi ta yiwa Amina faɗa a kan gangancin da tayi, saboda ba kowa ya san sun yi aure ba. Ita dai Amina tayi shiru ba ta kuma tofawa ba. Kamar yadda su Hajiya Turai suka ɗora Hajiya Zainab a kan keke ɓera, ta cigaba da zuba wa Alhaji Ahmad rashin mutunci daban-daban. Amina dai ta mayar da hankali, a kan jarrabawar ta, tana cigaba da kula Alhaji Ahmad. Tun yana lallaɓa Hajiya Zainab yana bi ta kanta, har ya watsar da ita, ya cigaba da sabgoginsa. Yayi mata maganar tariyar Amina, ya tambayeta a wani ɓangaren take son zama a gidan, amma tayi masa banza sai cin mutuncinsa da tayi ma. Amina kuwa tana tuntuɓar Ammi, da Hajiya Maryam, a kan shirye-shiryen walimarta na tariya da kammala makarantarta. Alhaji Ahmad ya tambayi Amina, furnitures ɗin da zai canza mata. Amina ta ce "Ni ka bar mini na sashin naka sun isheni" "A'a, sabuwar amarya a baki tsoffin furnitures" "Ba wata sabuwar amarya' "Sabuwace mana" yayi maganar yana murmushi. "Daddy, ni dai ka bari ko babu yawa Baba ya sai mini ba sai ka saya ba" "Saboda me ba zan saya miki ba? Duka furnitures ɗin gidan ma sauyawa zan yi, dan haka ba ruwanki, ba alhakin Baba bane ba, na bawa Hajiya Maryam kuɗin kayan lefenki" "Wayyo daɗi, duka ni kaɗai, Kana ji da ni Daddy" "Ba dole na ji da ke ba 'yar Babyna" suka Cigaba da hirarsu, cikin soyayya da kulawa. Hatta Fadila sai ta ga dama take gaida Daddy, saboda haushinsa take ji, ya jefa Mummy cikin halin damuwa. Amina rayuwarta take yi a gidan hankali kwance, ko shiga sabgarsu bata yi, sai dai wasu lokutan Hajiya Zainab idan suka haɗu ta kan ci mata mutunci. Amina sai dai ta ce "Ni ba zan biye miki ayi ɓarin mutunci ba, ko bance miki komai na riga na gama da ke, zagi da cin mutuncin da zaki yi mini, ba zai canza komai ba. Dan haka ki cigaba kar ki fasa, kece a wahale bani ba. Kuma zan cigaba da baki mamaki a gidan nan ta in da baki zata ba, su kansu 'ya'yan da kike taƙama da su, idan har baki canza hali ba, suma sai na rabaki da su, saboda wautarki" Hajiya Zainab ji take kamar ta kashe Amina ta huta da baƙin ciki. Yazid ya lura da mood ɗin Fadila a 'yan kwanakin nan, bata walwala ku san kullum yanayinta babu daɗi, hakan ya sanya yake jin shima babu daɗi a ransa, sai dai ba ya jin zai iya zuwa ya tunkareta yaji damuwarta. Hajiya Zainab na zaune a falo, tana shan shayi, gaba ɗaya bakinta babu daɗi, abu mai ruwa-ruwa kawai take iya sha, a cikin abin da bai fi sati biyu ba gaba ɗaya ta zabge, ta fita hayyacinta. Alhaji Ahmad ya fito daga sashinsa, Amina na binsa a baya, kallo ɗaya tayi musu ta kawar da kanta taji kamar ta ɗora hannu a ka ta zabga ihu, Yarinyar da sai dai ta bata umarni a da, ta ci mutuncin ta son ranta, wai ita ce yau ta aure mata miji, da alama ma hankalinsa a kwance yake. Suka ƙarasa falon, Daddy ya zauna, Amina ta zauna a kusa da shi. Ta kalli Hajiya Zainab ta ce "Hajiya ina kwana?" "Ya kwana a ɗakin uwarki" ta bawa Amina amsa. Amina murmushi tayi ta ce "Na gode" "Zainab, ba zaki taɓa canzawa ba ko? Yarinyar nan na ƙoƙarin mutunta ki, amma sai zubar da mutuncinki kike yi, ai shikenan dama ina son sanar da ke, in Allah ya yarda jibi, za a fita da furnitures ɗin gidan nan gaba ɗaya. Zan zuba sababbi sannan akwai walima na tariya da kammala makarantar Amina. Zata zauna ne a part ɗina shine nata ɓangaren. Sannan sai kuma maganar raba kwana". Tamkar saukar wuta haka ta dinga jin zubar maganganunsa a zuciyarta, ko kunya baya ji. "Ban gane zata tare a ɓangaren ka ba, idan har kana son zaman lafiya, ka kaita duk in da kake so ka ajiyeta, amma banda gidana". Daddy ya ce "Ba zan raba kan iyalina ba, a nan zata zauna, kuma kamar yadda na tambaye ki da farko, kina son part ɗinki ko in canza miki, baki zaɓa ba, dan haka Amina zata tare a sashena" Miƙewa tayi a zafafe ta ce "Baka isa ba, kayi kaɗan wallahi sai ta bar gidan nan ka kaita koma ina ne, amma ba gidana ba" "Ba shawararki nake nema ba, hukunci ne da na yanke, lokacin da nake binki ina lallaɓaki wata ƙila da kin kawo wannan maganar, da nayi amfani da ita, amma yanzu lokaci ya ƙure, a komai ke nake fara bawa dama kan ita, amma sai ki sake da taki damar. Ina son idan wanda zai auri Fadila sun shirya, su zo su sameni muyi magana da su. Zan tsayar da lokaci, dai dai da lokacin auren Khalil. Na kai masa kuɗin aure, na tsayar da watanni biyu kacal". "Ka tsayarwa da Khalil aure ban sani ba, wai me ka mayar da ni ne? Wai wace yarinyar ce ma tukuna, naga dai ita baban Kursum ɗin baya gari?". "Yarinyar da kika je ki ka ciwa mutunci a gaban jama'a, saboda ɗanki yana sonta. Nayi bincike bata da wani aibu. Bai kamata mu dinga tursasawa yaranmu saboda son zuciya ba. Ita dai Fadilan idan tana son wancan ɗin, su zo muyi magana. Na gama da maganar Khalil yarinyar da yake so zan aura masa, ba wadda kike so ba, tunda bake zaki zauna masa da ita!!! AYSHERCOOL 08081012142GABA DA GABANTA              NA AISHA ADAM AYSHERCOOL 63 "Ahmad me kake nufi da ni ne? Ahmad so kake ka haukata ni? A kan me zaka aurawa Khalil 'yar matsiyata. Wato kai ka auri 'yar matsiyata shine zaka aurawa ɗana, wallahi baka isa ba Ahmad, ba zaka mayar da ni mahaukaciya ba" tayi maganar bayan ta ci kwalar Alhaji Ahmad. Buɗe baki Amina tayi, tana binsu da kallo. Ƙwayar idonta ya kalla, wadda babu abin da yake gani a ciki, sai zallar tashin hankali da masifa, duk sun ƙanƙance, sun yi ja sai huci take hawaye na zuba daga idonta. A hankali ya sanya hannunsa, yana ƙoƙarin ɓanɓare hannunta daga kwalarsa, amma ta riƙe shi gam, sai huci take tana cigaba da masifa, idanunta kamar zasu yo waje, dan azabar baƙin ciki. "Ki cikani, kar ki mini illa, wuyana yana zafi" "Ba zan sake ka na Ahmad, sai ka gaya mini dalilin da ya sanya zaka kaiwa ɗana kuɗin Aure gidan matsiyata, saboda ka tozatarni, bayan wanda kayi mini" "Ai na gaya miki dalilin, saboda kin san ni mutum ne mai son abin da 'ya'yana suke so" Cikin ƙaraji ta ce "Ƙarya kake yi, wallahi ƙarya kake, ba ka son su, kuma 'ya'yana ne ba naka ba" Yayi murmushi ya ce "Ai ba da su kika zo ba, kuma bake kaɗai kika same su ba, dan haka ba a canzawa tuwo suna" ya ƙarasa maganar bayan yayi amfani da ƙarfi wurin cire hannunta daga wuyan rigarsa. Da ƙarfi ya danƙi hannunta, ta jata zuwa sashinsa, sai turjewa take tana gaya masa duk maganar da ta zo bakinta, ta ƙazafi da rashin daɗi . Amina ɗan taɓe baki tayi, tana sake jinjina jaraba irin ta Hajiya Zainab. A bedroom ɗinsa yayi birki, ya haɗa hannayenta, ya riƙe su da hannunsa ɗaya, ta yadda ba zata iya ƙwacewa ba. "Zainab, nine munafuki azzalumi ko, ko kunya ba kya ji kike irin wannan maganar, kike nuna ban isa ba a gaban kishiyar ki, ke baki san raini zai janyo miki ba" "Kar ka sake cewa kishiyata, nafi ƙarfin kishi da wannan 'yar matsiyatan, kuma sakina zaka yi, kuma wallahi baka isa ka aurawa ɗana 'yar matsiyata ba kamar yadda kayi" "Kin makara ai, na riga na gama magana, amma yakamata ki sake tunani a kan abin da kike yi, hakan ba mafita bace, ƙaddara ta riga fata, kiyi haƙuri ki zauna mu cigaba da rayuwarmu, ina sonki Zainab, ban ƙara aure dan in wulaƙanta ki ba" Jarumin namiji baya saki Zainab, da zan sake ki tun a abubuwan da kika yi mini a baya, da tuni na rabu da ke, sai dai na lura ke mace ce mai mantuwar gaske, ba kya duba gaba, ko tuna baya abinda ya zo miki shi kawai kike yi, dan Allah ki daina ki nutsu ki kwantar da hankalinki, ni ba zan wulaƙanta ki ba, kece uwar 'ya'yana kuma matata ta fari, matsayinki na nan daram bai sauya a zuciyata, amma meyasa kike so ki fitine ni, ki fitini kanki, a kan abin da nuna jarumtar ki zai ninka darajarki a idona" "Jarumta kace, to Allah ya tsinewa jarumtar, ka cikani malam". Hannunsa ɗayan, ya sanya yana shafo gefen wuyanta, yayi murmushi ya ce "Am missing You so badly, kece sila koma menene, kece kika bada ƙofa" gaba ɗaya Alhaji Ahmad ya gama raina mata hankali. Ƙoƙari yake ya rungumeta ya rarrasheta, amma fafur taƙi ta dinga kuka tana ci masa mutunci, ba shiri ya rabu da ita ya fice. Sashin su Amina ya tafi, ya shiga ɗakinta yayi mata sallama, saboda cigaba da shirye-shiryen tariyarta. Sai dai ya tarar Amina ta cika tayi fam, tana danna wayarta. "Meenal, zan tafi in sha Allah zuwa la'asar zan dawo" "A dawo lafiya" ta faɗa ba tare da ta kalleshi ba. "Ya dai naga kin haɗe rai?" "Bakomai" ta bashi amsa. "Ban gane babu komai ba, amma ai ba haka muka tashi da ke ba yau, ko na yi miki wani abun ne?" Aikuwa kamar ya taɓo mata in da yake mata ƙaiƙayi ta ce "Ba kaine ka biya kaje ka daɗe ba, bayan kuma magana muke ba" Ɗan buɗe baki yayi cikin mamaki ya ce "Meenalina, haka za muyi da ke?" Tura baki tayi tana hararsa. Ya ɗan rausayar da murya ya ce "Shikenan, tunda ke ma ɓata mini rai zaki yi, bari da an kammala walimar na tattara na koma Lagos, tunda haka kuke so" ya yunƙura zai tashi, ta riƙe hannunsa cikin nata. "Dan Allah kayi haƙuri, kawai ji nayi ina jin haushi, amma ba zan sake ba, kar ka tafi Lagos ka barmu" "A'a komawa Lagos ya zama dole ai, tunda ba kwa son ganina, so kike hawan jinin ya ƙarasa ni" Da sauri ta girgiza kai ta ce "A'a wallahi muna sonka, dan Allah ka daina faɗar haka na daina kaji" "Is ok, sai na dawo" "Safe journey ranka ya daɗe, Allah ya tsare mana kai, ya kiyayeka a duk in da kake" "Amin Sweetheart, kiss me before I leave" Kissing ɗinsa tayi, sannan ta tashi ta raka shi, har mota ya tafi. Duk wannan abin da ake, Fadila bata sani ba, tana makaranta. Kasancewar Amina yau bata da exams, ya sanya take gida, kusan kullum sai Baba ya kirata ya ji ya take. Kullum idan taje makaranta tayi exams, gidansu Azima take wucewa, Ammi na kaita wurin wata mata 'yar Chadi tana mata gyaran jiki. Jikinta yayi kyau sosai gwanin sha'awa. Ta gama gyare-gyaren da zata yi a ɗakinta, ta fito falo ba tsammani taga su Hajiya Turai a zazzaune, Hajiya Zainab na gefe idanun nan jawur kamar an hura wuta. Da fari sai da gaban Amina ya faɗi, amma ta maze ta ratsesu ta nufi Tv stand, ta ɗauki abin da zata ɗauka. Hajiya Salma ta ce "Ga munafukar nan, algunguma tazo birni ta sha jar miya, ji yadda tayi ƙalau har da aure mai gida, shashasha mai kama da bulugari" Amina ta yi murmushi ta ce "Wallahi nafi ƙarfin a kirani da mai kama da bulugari, sake kalla dai da kyau, ai wani kaya sai amale" Hajiya Turai ta tafa hannuwa ta ce "Innalillahi wa innalillahi raji'un, haka kike zaune Zainab, baki kamata kin naɗa mata duka kin ɓata kamanni ba?" Kamar Amina ta sharesu taji abin da ta zo yi ta bar musu falon,  amma taji cin mutunci yayi yawa, dan haka ta ce bari ta haɗasu tayi maganinsu. Ta kallesu ta ce "Nifa bani da laifi a wannan abun, bani nace ya aureni ba. Wataƙila da kuna bata shawarar da ta dace, da mijinta bai aureni ba, wa zai ƙi auren mutumi Kamar Alhaji Ahmad, mutum nagartacce gashi tubarkallah mai kyau, ni ban auri mijinta dan in wulaƙanta ta ba, duk wutar ɗaukar fansar cin mutuncin da take mini ni da ubana na cigaba da ruruwa a zuciyata. Amma ki sani idan kika cigaba da cin zarafi na, zan rama abinda kike mini cikin kwanciyar hankali. Kuma ina fatan ki cigaba da hawa keken ɓeran da suke ɗoraki a kai, ki cigaba da treating ɗin mijinmu kamar yadda kike yi yanzu, ni kuma haka na ƙara bani damar mallakar sa. Ki sani daga lokacin da kika yi yinƙurin kai hannunki jikina da niyyar ki dakeni, tamkar kina wasa da igiyar aurenki ne, dan a yadda yake ɗin nan, duk abin da zai masa shamaki da kasancewa da ni zai iya maganinsa, ni kuma ba zan so kashewa uwarɗakina aurenta ba. Allah ne ya bani mijin mashiririciya na aure" Gaba ɗaya sai suka ƙame a wurin, aka rasa mai bakin magana. "Zainab abinda kike ciki kenan a cikin gidan nan?" "Gashi kuna gani da idonku" Hajiya Salma ta ce "Lalli yarinya ta samu wuri, yanzu ni dai ki san ƙaryar da za a yiwa iyayen Kursum, dan sun saka rai sosai da sosai. Sannan a satin nan zan yiwa Baban Salim magana, azo ayi maganar auren su Fadila tun kan ita ma yayi sadakarta kamar yadda ya yiwa Khalil" "Salma kaina ya kulle, ƙwaƙwalwata na saƙa mini miyagun tunani a kan Yarinyar nan, dole na shirya mu tafi Nijar ɗin nan, rashin lafiyar nan dake damuna ya sanya bance ayi tafiyar ba, ina fama da tsananin ciwon kai" "Hmm ai a haka baƙin ciki zai kasheki, jajigewa zaki yi, ki saka rana mu tafi Nijar, kuma karki kuskura ki ɗaga masa ƙafa, ki tayar masa da hankali ki hana shi nutsuwa" Suka yi ta zigata da rashin mutunci kala kala. Khalil yana jin yadda yayi kewar Kano sosai da sosai, yana tafe yana kalle-kalle, yana tuna soyayyar sa da Hafsa, da yadda yayi matuƙar kewarta. Da Azahar ya isa gida, sai dai Zakiru ne ya buɗe masa ƙofa saɓanin malam Hassan, bai damu ya tambaya ba, ya bawa Zakiru jakarsa shi kuma ya shiga cikin gidan. Kai tsaye sashin Mummy ya nufa, sai dai kallo ɗaya yayi mata, ya shiga damuwa, saboda tsananin ramar da tayi. "Mummy baki da lafiya ne?" Yayi maganar ba tare da yayi ko sallama ba, saboda yadda ya firgita. Ɗagowa tayi ta kalleshi, da sauri ya ƙaraso inda Mummy ta ke, yana ƙoƙarin zama a kusa da ita cikin kulawa da tausayawa. "Idan ka zauna mini a nan, sai na zabga maka mari" Cikin Mamaki Khalil ya ce "Mummy meyafaru ne?". "Ni kake tambaya, ubanka ya auri 'yar matsiyata ya kawo mini cikin gida, shi ne kai kuma kuka haɗa kai kaima zaka auri 'yar matsiyata, ka tashi ka bani wuri, kaje ayi maka aure, amma ba da yawuna ba" "Wallahi Mummy ban gane me kike nufi ba, dan Allah meyafaru ne?" "Ni zaka rainawa hankali, tashi ka fita ka bar mini ɗaki, tashi bana son ganinka. Saboda mace Khalil tun da ka sanya ƙafa ka bar gidan nan, baka sake waiwayowa ba sai yanzu, ka kyauta, kaje kai da uban naka kuyi duk abin da kuka ga dama, ku kasheni ku huta". "Mummy..... Ta katse shi ga hanyar cewa "Ka tashi ka bar mini ɗaki na gaya maka". Jiki a saɓule, Khalil ya tashi ya fita, amma sam bai gane a kan me take wannan maganganun ba, ya kasa gane ina maganar ta ta ta dosa. Lokacin da ya fito, Amina nata shirya Abinci a dining. Kallo ɗaya Amina tayi masa, ta gano ya fuskanci matsala a wurin Hajiya Zainab, gaba ɗaya jikinsa a saɓule. "Khalil ashe ka dawo?" Khalil ya waiwaya ya kalli inda Amina take ya ɗan kawar da kansa ya ce "Yauwa". "Ka dawo a dai-dai, mun gama abinci". Dama Khalil yunwa yake ji, ya ce "Ok bari ina zuwa". Ta cigaba da sabgoginta, Khalil ya dawo ya zauna ya fara cin Abinci, ya kammala ci, yana ta ƙoƙarin neman layin Abdul. Amina ta sake fitowa ta zauna a kujerar da ke facing ɗin ta Khalil ta ce "wannan lokacin ka daɗe sosai ba ka zo gida ba" "Eh aiki ne yayi mini yawa" "Ban sani ba ko kun yi wata maganar da Daddy, amma zan so ace nice wadda zan fara yi maka wani albishir. Duk da ban sani ba ko kaima kana jin haushina". Khalil ya ce "Meyasa zan ji haushinki me kika yi mini?" Ta ce "Shikenan, mu bar wannan maganar, Daddy ya kai maka kuɗin aure 4days back" Khalil ya ɗan yi saroro ya ce "Kuɗin aure kuma?" "Eh, an kai maka kuɗin aure gidan su Hafsa" "Ya aka yi kika san Hafsa?" "Ba abin mamaki bane, ina tayaka murna" Cikin mamaki da farinciki Khalil ya ce "Ya aka yi Daddy ya san da batun Hafsa? Amma dan Allah da gaske kike yi?" "Idan baka yarda ba, in ya dawo ka tambayeshi" Khalil ya ce "Subhanallah, ji nake kamar ina mafarki fa". "Ke wace irin daƙiƙiya ce, kin bi uba kin dawo wurin ɗa, meye haɗinki da Khalil kuma?" Cewar Fadila da dawowarta kenan, ta tarar da Amina da Khalil. Khalil ya ce "Wace irin magana ce kike yi haka Fadila? Magana kawai muke yi" A fusace Fadila ta ce "Kai dai ban san meke damunka ba, Yarinyar da ta aure mana uba, ta jefa mahaifiyarmu a cikin halin ƙunci da damuwa, ta tafiyar da sashin farincikinmu ita ce har kake da damar zama kayi magana da ita?" "Yaushe na fara wasa dake, da har kike gaya mini maganar da kika ga dama, shi Daddyn da ya aureta ba shi ya ga zai iya ba?meye abin wani tayar da jijiyar wuya, ni banga abin ɗaga hankali ba". Cikin mamaki Fadila ta ce "Au haka ma zaka ce?" Amina ta katse zancen ta hanyar cewa "Idan kayi confirming ina jiran tukuicin albishir" Murmushi Khalil yayi ya ce "To shikenan". Amina a ranta ta ce 'Wato su dai maza duk in da suke halinsu ɗaya ne, wato yana goyon bayan abin da mahaifinsa yayi, shi bai ga aibunsa ba. Lallai na samu damar da zan ɗanɗanawa Hajiya Zainab abin da ta ɗanɗanawa dangin Alhaji Ahmad, idan ta cigaba da wannan shirmen to tabbas 'ya'yan ma duk sai na ƙwace su, ai GABA DA GABANTA!". Khalil na fita kai tsaye gidan su Abdul ya wuce. Abdul yayi mamakin ganin Khalil. "Kai mutumina, saukar yaushe babu ko kiran waya, angon Hafsatu bada kanka a sare". Khalil ya kalleshi da mamaki ya ce "Au kaima ka san wannan zancen wai dan Allah da gaske ne ko wasa?" "Ban gane ba, kana nufin baka sani ba?" "Wallahi ban sani ba, ni ɗazu na dawo, Mummy na ta yi mini faɗa, ni ban gane a kan me take faɗan ba, sai kuma waccan Yarinyar da aka ce Daddy ya aura, 'yar Malam Hassan, take gaya mini" Abdul ya ce "Au, ni bama muyi zancen ba, Yusra ta gaya mini wai Daddy yayi aure". Khalil ya ce "Kai nifa ya gaya mini, na sani lokacin ina Abuja nayi rashin lafiya, har dubani suka zo yi tare, Daddy ya gaya mini yayi aure, ya gaya mini ita ya aura" Abdul ya waro ido ya ce "Amma ya aka yi kai shiru ba wanda ka gayawa?" "To Abdul me zance? Shi Daddy ai ya san dai-da ya san meye ya dace da shi, ni banga dalilin da ya sanya Mummy zata ɗaga hankalinta haka ba. Amma dan Allah Abdul ya aka yi ka san zancen kai kuɗin nan, kaina ya kulle meke faruwa ne?" Abdul ya ce "Nutsu na yi maka bayani" Khalil ya gyara zamansa, ya tattara hankalinsa a kan Abdul. Abdul ya ce "Daddy ne ya zo har inda nake, yayi mini tambayoyi a kan alaƙarka da Hafsa da abubuwan da suka faru a tsakanin ku, lokacin kayi mini zancen wai na auri Hafsa, Daddy ya ce kar na ɓoye masa komai. Na gaya masa komai. A nan yake gaya mini cewar yayi mamakin rashin gaya masa da baka yi ba, sai Amina ce ta gaya masa, nayi mamaki da naji ya ce Amina ce ta gaya masa, so ban dai matsa sai na ji ba. Bayan 'yan kwanaki ya kirani, ya sanar da ni cewar yayi binciken da yakamata a kan Hafsa, yaje wurin dangin mahaifinta sun tsaya yi masa wasa da hankali. Abin ban tausayi limamin unguwar su ne ya karɓi kuɗin auren nata, bayan sun gama ɓatata a wurin Daddy, Daddy ya kuma yi mini bayani, na gaya masa abinda na sani a kanta, ya koma wurin Mamansu, ta gaya masa irin zaman da suka yi da dangin mahaifinta, shi ne yaje suka yi magana da liman ya bashi kuɗin Auren, babban abin da Daddy ya sake burgeni da shi, shi ne ya ɗauke musu kayan ɗaki, ya ce 'yar sa ce". Wata irin nannauyar ajiyar zuciya Khalil ya sauke, ya ce "Abdul meyasa baka gaya mini ba?" "To ai lokacin ana ta turka-turka, abun bai tabatta ba tukuna, yanzu da ya tabatta ba gashi ka ji ba" "Abdul, tashi muje ka rakani gidansu Hafsa" Abdul ya ce "A wannan uwar ranar, ka bari dai yamma tayi". Sujudu shukur Khalil yayi a wurin, sai sauke ajiyar zuciya yake, kamar wanda aka biyawa bashi. Abdul ya ce "Lallai mutumina ka shiga da yawa" Khalil ya ce "Abdul, ba zaka gane ba, nikaɗai na san me nake ji" "Naga alama, dan haka yakamata kaje ka yiwa Daddy godiya" "Wannan dolene Abdul, amma dai yanzu ina nan sai naje naga Hafsa tukuna, na rasa me zan yi dan murna". "Godiya zaka yi ta yiwa Allah kawai". Fadila kuwa wurin Mummy ta wuce, tana cigaba da mitar abin da Khalil yayi. Mummy ta ce "Ai ba tun yanzu ba, na gane Cewar Khalil bayan ubansa yake bi, da ni suke zancen, daga shi har shi, duk sai nayi maganinsu wallahi". "Mummy ni dai dan Allah ki kwantar da hankalinki, ki samu ki daina wannan damuwar, dubi duk kin rame kamar ba ke ba" "Hmm Fadila kenan, bana fatan Allah ya gwada miki abin da nake ji a zuciyata, ke dai kawai ki cigaba da Addu'a". "Haka ne Mummy, amma dan Allah ki dinga ragewa, bana jin daɗin ganin fuskarki a haka" Tayi murmushi mai ciwo ta ce "Shikenan na daina" Abdul ya hana Khalil tafiya wurin Hafsa, sai wajen biyar na yamma. Ya saka kayan Abdul dan baya son komawa gida a samu wata matsalar, wata dakakkiyar shadda sky blue ta Abdul ya saka da hula, yayi kyau sosai da sosai. Hafsa na tsakar gida, ta gama girkin dare, tana yiwa Mama da ke ƙulla kuka hira. Yaro ne yayi sallama ya gaida Mama ya ce "Wai Hafsa taje in ji Khalil" Wani uban tsalle Hafsa tayi ta ce "Mama Khalil" Mama tayi murmushi ta girgiza kai ta ce "Eh Khalil" Gaba ɗaya Hafsa sai ta manta da batun kunya, da ma tsaf take tayi wankanta. A gurguje ta canza kaya ta zari mayafi tayi waje. Yana tsaye a ƙofar gidansu, ya zuba mata ido, ita ma kallon nasa take yi gani suke tamkar a mafarki komai yake faruwa. Kawai Hafsa ta fashe da kuka. Shi ma Khalil ji yayi kamar ya tayata kukan, amma ya dake ya ce "Da abin da zaki karɓeni kenan? Kuka kuma Hafsat" Sake ƙaro sautin kukan tayi, har da sheshsheƙa. "Shikenan, ya isa haka ƙaraso" ta ƙarasa suka zauna a dakalin gidansu. "Babyna kinga ikon Allah ko?" Kasa Magana Hafsa tayi, sai kuka da ta cigaba da yi. "Dan Allah ki daina kukan nan haka, ki so kike nima nayi?" Ta girgiza masa kai alamar a'a. "To ki daina muyi magana" Ta share hawayenta, ta kalleshi ta ce "Ina wuni" Yayi murmushi ya amsa mata ya ce "Ya kewata?" "Daina tuna mini, tsawon lokacin nan kawai dai gani nan ne dai, amma ban san yadda zan misalta maka halin da na shiga ba" "My dear, baki ga yadda na rame ba? Rashin lafiya nayi sosai har da zuwa Asibiti, na kira lambarki ba adadi, kin daina ɗaukar wayata. Anyway yanzu dai komai ya wuce sai godiyar Allah, ina mai kuma sake baki haƙuri a kan abubuwan da suka faru". "Bakomai ai ya wuce, tun da Daddy ya ce mini ba wata matsala, Mahaifinka mutumin kirki ne, duk da yadda dangin ubana suka dinga ɓata ni a wurinsa amma hakan bai hana ya amince ka aureni ba, bani da bakin yi masa godiya Allah ya sa ya gama da duniya lafiya, bani da bakin yi masa godiya" "Karki damu, kema kin zama 'yar sa" "Haka ne, amma Mummy kuwa ta amince?" Khalil ya ce "Ta amince mana, ai shi ya sanya Daddyn ma ya bada goyon baya, Allah ya sanya mana albarka, inye amarya ba kya laifi" rufe fuskarta tayi da hannayenta tana murmushi. Hira suka sha ta soyayya, da kewar juna. Sai da aka yi kiran sallar magariba, sannan Abdul ya zo ya ce "To tsuntsun soyayya, ai sai ka tashi mu tafi a barta ta huta" Hafsa ta ce "Laa Yaya Abdul, dama tare kuke?" "Eh tare muke mana, ya barni a cikin mota a kan layi ya manta dani, tsawon awanni". Murmushi suka yi, Khalil ya ce zasu je su yi salla, su dawo su gaida Mama. Haka kuwa aka yi, bayan sun yi sallar Magariba, suka koma gidan su Hafsa. Mama ta rasa in da zata saka ranta da daɗi, ta dinga kwarara musu addu'a, ta bawa Daddy labarin abin da dangin mahaifin Hafsa suka ce wa Daddy, wai yawon banza take bata kwaɓarta har cin kwalar maza take ba mutunci ne da ita ba. Amma Daddy ya ce bakomai su karɓi kuɗin auren, amma suka ce ba zasu karɓa ba, mahaifiyarta ba ta ganinsu da mutunci. Da yadda Daddy ya dawo wurin limamin unguwarsu, ya bada kuɗin auren Hafsa. Mama ta dinga zabga masa godiya, sai da kunya ta kama Khalil. Khalil ya ce "Bakomai Mama, ubangiji Allah ya nuna mana lokacin". Wasa-wasa har Abincin dare Su Khalil suka ci a gidansu Hafsa, kamar zasu cinye juna shi da Hafsa. Abdul ne yayi musu sallama, dan Khalil ya zo su tafi. A soro suka tsaya, yana sallama da Hafsa ya ce "Amaryata, ya batun shirye-shiryen da za muyi ne?" "Kaje gida ka huta, idan ka dawo mayi magana" "To shikenan, ina fatan yanzu zaki ɗauko wayarki ki kunna, ko wata zamu saya?" Ta ce "A'a tana nan" Khalil ya ce "Shine ko kirani a waya, ki gaya mini an kawo kuɗin" Ta ce "Yanzu ba ka shi ka sani ba, kaje kar Yaya Abdul ya gaji, ka tsayar da shi da yawa" "Shikenan ƙanwar Yaya Abdul, sai da safe za muyi waya" Tayi murmushi ta ce to shikenan. Suka yi sallama, su Khalil suka tafi, suna tafe a hanya Khalil jinsa yake kamar an ɗaura auren, yadda abubuwa suka dinga tafiya kamar ya shirya su. Lallai Addu'a bata faɗuwa ƙasa banza. Abdul ya dinga yi masa mita ya tsayar da shi, Khalil yana ba zai gane ba, yana son ya sanar da shi batun Yusra, amma yaji nauyin hakan. Khalil na zuwa gida ya ga motar Daddy, alamar yana gida, sai da ya kuma tambayar Zakiru, ya tabattar masa da Daddyn yana gida. Ya duba agogon wayarsa, ya ga ƙarfe goma saura na dare. Ko da yayi parking, ya fito kai tsaye sashin Daddy ya wuce. Da sallama ya shiga falon, Daddy ya amsa masa, yana zaune shi da Amina tana zuba masa shirme yana murmushi. Khalil na shigowa ya tafi da gudu ya rungume Daddy. Murmushi Daddyn yayi shima ya rungume shi. "Daddy na gode, na gode Allah ya biyaka da gidan aljanna, naji abin da kayi mini, ka sai mini kima a idon sirikaina, na gode Daddy". "Bakomai Khalil, ina fatan daga yanzu ka daina rashin lafiya tun da ka samu abin da ka ke so?" "Na daina Daddy, ina sonta sosai Daddy, ina tausayinta. Ban yi zaton zaka nema mini aurenta ba" Ita kanta Amina murmushi take yi, dan ita Hafsa tafi jiyewa Daɗi, koba komai ita ma ta dandali arziƙi ta huta. Daddy ya ce "Amina zaka yiwa godiya, ita ta sanar mini da halin sa ake ciki, amma mai ya sa tun farkon lamarin baka sanar mini ba?" Amina ta ɗan zabura ta ce "Daddy ya gaya maka fa, kace sai Hajiya ta amince" Dadyy ya ce "Shigar masa zaki kenan? Shikenan dai, Amina ce ta dinga shiga tana fita, a kan lallai ka samu abin da kake so. Naji tausayin yarinyar sosai bayan naji labarin abin da ya faru, daga ita sai mahaifiyarta suke fama da rayuwa, Amina ta saka pressure har Allah ya sanya dai aka kai kuɗin Auren" Khalil ya ce "Aikuwa a bakinta na fara jin maganar, na zata ma da wasa take mini. Na Gode ubangiji Allah ya saka miki da alkhairi, yadda kika yi silar farinciki da yayewar damuwata ni da Hafsa" Amina ta ce "Ai bakomai, ba abin damuwa bane, Allah ya sanya alkhairi, sai azo a fara shiri, lefe za ayi na gani na faɗa, dama Daddy ya ce "zai yi furnitures, kai kuma sai kayi lefe ni kuma zan yi kayan Kitchen" tayi maganar tana dariya. Daddy ya ce "A wurin wa zaki samu kuɗin kayan Kitchen ɗin?" "A wurin Daddy mana, Allah dai ya ƙara arziƙi ranka ya daɗe" Amina tayi maganar tana jinjina masa da hannunta. "Wallahi idan ina raye ba a isa an yi auren nan ba, idan kuwa ka dage sai kayi ba da yawuna ba sai dai ka nemi wata uwar Khalil. Shashasha mara zuciya ko kallon abin da ubanka yayi mini baka yi, ke kuma munafuka kin aure mini miji, shine kika saka ya aurawa ɗana 'yar matsiyata irinki ko, ai ina tsaye ina jinku, idan har ni na haifeka Khalil ban lamunci auren nan ba ba da yawuna ba". AYSHERCOOL 08081012143GABA DA GABANTA NA AISHA ADAM AYSHERCOOL 64 Gaba ɗaya jikin Khalil yayi sanyi, ya waiwaya yana kallon Hajiya Zainab. Daddy ya ce "Wannan aure babu abin da zai hana shi yiwuwa, babu biyayya ga abin halitta, wurin saɓawa mahalicci, auren Khalil yana kan tsari da koyarwa ta Addinin Musulunci, dan haka babu gudu ba ja da baya ba abin da zai hana wannan auren muddin ina raye". "Wallahi baka isa ba, ba za ayi shi ba, idan har aka yi auren nan ba da yawuna ba kuma sai dai ya nemi wata uwar bani ba" Amina ta jinjina kai ta ce "Taɓ" Mummy ta mayar da kallonta kan Amina ta ce "Ke kuma baƙar algunguma tashi ki bar wurin nan, ina magana da mijina da ɗana" Hararta Amina tayi, ta murguɗa baki, ya cigaba da kaɗa ƙafa. Daddy ya kalli Khalil ya ce "Khalil, tashi kaje ba abin da zai hana aurenka albarka da yardar Allah" Jiki a sanyaye Khalil ya tashi ya bar falon. Ya kalli Amina ya ce "Meenalina, kije ki kwanta kinga dare yayi" Amina ta miƙe tsaye ta ce "Ok, sai da safe ma ƙarasa maganar kenan?" Ya ce "Eh, but i hope baki ji haushi ba?" "No ba damuwa, good night dear" Ya kashe mata ido ɗaya, tayi gaba tana wani rausayawa kamar ana mata kiɗa, Alhaji Ahmad ya bita da kallo, wanda hakan ya fusata Hajiya Zainab ainun. "Wallahi Ahmad kaji kunya, 'yar tatsitsiyar a bar nan kake bi da kallo, 'yar cikinka Allah wadaran halinka wallahi". "Kema da zaki yi mini hakan kallonki zan yi, ke kika watsar kika daina, dan na samo mai yi mini ai ba laifi bane, ke a wurinki na tsufa ko? To ita a wurinta ban tsufa ba, ina sake gargaɗinki a kan wannan ɗaga hankalin naki da kike yi, kuma auren Khalil yana nan babu fashi, sannan Fadila idan har iyayen wancan yaron ba su zo ba, ita ma zan yi abin da ya dace a kanta". Ji take kamar ta shaƙe shi ta huta da baƙincikin da yake ta dan ƙara mata sinƙi-sinƙi. "Mu zuba ni da kai Ahmad, shege ka fasa" "Daga ni har ke babu shege duk 'yan halak ne" Ko a mafarki idan aka ce Alhaji Ahmad zai yi mata haka, zata ƙaryata ɗari bisa ɗari, amma ɗan tahalikin nan ya rufe ido yana ta surfa mata rashin mutunci yadda yake so. Malam Khalil kuwa ɗakinsa ya wuce, yayi sallar isha'i, dama cikinsa a cike yake, ya ɗau wayarsa ya haye gado, ya kira lambar Hafsa, cikin ikon Allah yana kiranta ta ɗaga, suka cigaba da yin wayarsu cikin soyayya da kewar juna. Amma ƙasan zuciyarsa yana jinjina masa yiwuwar abin nan, bayan Mummy ta riga ta nuna bata so. Shirye shirye suka yi nisa. Daddy ya canza furnitures ɗin gidan, amma banda na Hajiya Zainab, saboda ta ce ba ta so ya riƙe tsiyarsa. Zakka kuwa da ya fitar, 'yan dangin Amina wasu sun samu, nasa dangin ma haka, da kuma 'yan unguwa. Tuni ya bugo invitation na gayyata walimar kammala karatuk Sakandire, da tariyar Amina, ya bawa Amina nata, saboda neman rigima ya kaiwa Hajiya Zainab ma. Aikuwa ta yayyaga ta watsa masa abin sa a jikinsa, bai damu ba ya ce "Zainab, duk wannan lallaɓakin da nake, dan nayi miki adalci ne, amma tun da haka kika zaɓa shikenan. Dama kuɗin da kika karɓa a wurina, ki riƙe su, sune na faɗar kishiya da zan baki. Ko kallonsa ba tayi ba, ta shareshi. Amina kamar sabuwar amarya, tayi kyau sosai tayi shar da ita, har ƙauye taje ta kai musu invitation na tariya da walima. Daddy ya so ya saiwa Baba gida a birni, amma ya ce ba zai iya barin ƙauye cikin danginsa ba ya koma birni gaba ɗaya ba, dan haka a nan ƙauye aka saiwa Baba gida, suna ta shirin tashi da zarar an kammala tariyar Amina. Ya saiwa Baba rumfar kasuwa, ya bashi jari ya zuba kayan awon Abinci. Amina kuma kuɗaɗenta da ta samo, da kuɗin Aurenta da sadaki, Daddy ya cika aka saya mata ƙatuwar gona a ƙauye. Baƙi ciki kamar ya kashe su Kawu Bala, duk da suna cin arziƙin su Aminan, ba su taɓa zaton babban mutum ne mai kuɗi ya auri Amina ba. Ƙarin baƙin ciki sai da Amina ta kai invitation, yadda ta yi ƙiba, kwananta ɗaya washegari aka kawo mata kayan lefe. Kaya na gani na faɗa, da ba a taɓa makamancinsa a garin ba, Hajiya Maryam ta saiwa Amina kaya na alfarma. Ammi da su aka karɓi lefen Amina, aka ce walima da tariya kwana goma. Mutane suka dinga sintirin zuwa ganin kayan lefe, kwanan Amina uku, Ammi ta ce Lallai ta koma Kano, saboda a cigaba da yi mata gyaran jiki. Da ta koma Kano, gidan su Azima ta tafi, Ammi ta ce sai ranar tariya zata koma gidan. Khalil gaba ɗaya zaman gidan baya masa daɗi, dan haka a wurin Abdul yake wuni, da yamma ya tafi wurin Hafsa sai dare ya koma gida. Dangin Alhaji Ahmad, da suka sami labarin 'yar aikin Hajiya Amina ya aura, kamar su zuba ruwa a ƙasa su sha, mussaman ma su Anty Fauziyya da suka je gidansa, Amina ta karrama su. Alhaji Ahmad yayi ɓarin kuɗi a shirin walimar Amina kamar babu gobe, da ta ce za ayi kaza zai ɗau kuɗin ya bayar, danginsa da abokanansa suka dinga ba ta gudunmawa. Hajiya Maryam taji daɗin haɗuwa da Ammin Azima, dan a nan ne ma Hajiya Maryam take sake bata labarin halin rashin mutunci na Hajiya Zainab. Duk baƙin da suka zo, a ɗayan gidan Daddy suke sauka, Abinci kala kala haka aka dinga shiga ana fita da shi. Har gida Yusra taje ta samu Fadila, dan yi tayi kamar bata san meyafaru ba, sai da ita Fadilan dan kanta ta sanar mata da abin da ya faru, dan suna gida amma basu san zancen ya yaɗu a gari ba, mussaman Kasancewar sa sanannan mutum. Fadila na ganin Yusra ta rungumeta tana kuka, Cikin rarrashi Yusra ta ce "Haba girl, kiyi haƙuri mana ki danne zuciyarki" Fadila ta share hawayenta ta ce "Yusra ba zaki gane halin da nake ciki ba, Yusra 'yar aikin Mummy fa Daddy fa ya aura, kinga wulaƙancin da suke yiwa Mummy, kullum cikin kuka da damuwa take, gashi ya kaiwa Khalil kuɗin aure gidan su wata yarinya talakawa masu awara a titi, gaba ɗaya ta ɓata mana farinciki" Yusra cikin rarrashi ta share wa Fadila hawayenta, sannan ta ce "kiyi haƙuri, zaku iya maintaning farincikinku, ku amayar da komai ba komai ba, idan kuka yi kamar baku san da zamanta a gidan nan ba, Mummy ta ciresu daga ranta gaba ɗaya" "Haba Yusra, tsawon shekaru suna tare da mijinta, rana ɗaya yarinya ƙarama ta ƙwace mata shi, dole ta damu" "Haka ne Fadila, amma idan ta cigaba da damuwa zata iya haɗuwa da wata larurar" Yusra ta cigaba da kwantar mata da hankali, ta ce suje su duba Mummy, suka tarar da Mummy tana bacci. Ita ma Yusra taso sanar da ita batun alaƙarta da Abdul, amma ta yi shiru saboda halin da ta tarar da ita a ciki. Dangin Baba daga Dutse suka zo, haka 'yan uwan su Amina daga ƙauye, Daddy ko a jikinsa wai dan ya auri yarinya ƙarama yana gayyatar mutane walimar kammala karatu da tariyar matarsa. Rana bata ƙarya, sai dai uwar ɗiya taji kunya. Hall yayi hall yayi kyau sosai. Amina ta sha kwalliya tayi kyau har ta gaji da haɗuwa. Amina sai murna take yi, ganin yadda mutane suka taru duk domin ita. Ga ƙawaywnta na ƙauye, ga na birni 'yan makarantarsu, ga dangin Daddy, ga matan abokansa duk a wurin. Aikuwa sun tara mata kuɗi matan manyan nan. Tun ƙarfe takwas ake abu ɗaya sai sha ɗaya na dare sannan aka tashi. Su Ammi suka ɗauke Amina sai kuma gobe wurin kai amarya. 'yan garin su Amina da suka zo, sun sha mamaki a kan gidan da aka sauke su kawai, balle Abincin da aka dinga shiga ana fita da shi. Inno ma tazo, sai dai ba taje wurin walimar Amina ba. Hajiya Zainab ji take kamar zuciyarta zata buga ta mutu ta huta da tsananin baƙin ciki da damuwa. Da yamma Ammi ta saka Amina ta shirya, aka yi mata light makeup, sai zuba ƙamshin turaren Hajiya Maryam take yi. Mota mota aka dinga caikawa da 'yan garinsu Amina, da 'yan Dutse zuwa gidan Alhaji Ahmad. Suka shiga suka dinga rafsa guɗa, dangin Alhaji Ahmad suka dinga cewa ko anƙi ko an so yanzu dole su zo gidan ɗan uwansu. Hajiya Turai ta ce "Ji matsiyatan 'yan uwanta wasu gajiyayyu da su, duk a komaɗe kamar 'yan gudun hijira, munafukai talakawan banza" Suka dinga santin sashin Amina, komai yaji, yayi kyau sosai da sosai. Suka dinga Addu'a da sanya albarka. Sai da suka fito falo, Anty Fauziyya ta dinga "Allah ya kawo alkadarin baƙar daga, ko anƙi ko an so dole muzo gidan ɗan uwanmu. Engineer ai sai yanzu yayi dacen yin aure wallahi, auren haɗi ya zame masa bala'i". Hajiya Salma ta ce "Ke ki kiyayi kanki, Karki kuskura ki kuma yin gigin cin mutuncin matar gida" "Matar gidan banza, ai Allah ne ya kawo karshen mulkin mallakar da kika dinga yi tsawon shekaru. An samu wuri an miƙe ƙafa an manta tushe". Wuri ya kaure da hayaniya, da ƙyar manyan ciki suka tsawatar, sai wajen ƙarfe goma na dare, kowa ya watse, sannan Hajiya Zainab da Hajiya Maryam suka fara kai Amina danginta da dangin Daddy suka yi nata nasiha sosai, sannan suka kai Amina gidan Alhaji Ahmad. Hajiya Zainab na ganin Hajiya Maryam tayi sak, ta bita da kallo. Suka ƙarasa falon suka zauna tare da Amina, ta ce "Ya naga kamar kinyi manakin ganina Uwargida? Kwana da yawa, an naɗamu wakilcin kawo miki ƙanwarki, muna fatan Allah ya baku zaman lafiya" Hajiya Zainab ta ce "Da ke aka haɗa munafuncin auro mini 'yar aikina ko?" Hajiya Maryam tayi murmushi ta ce "Ni ba ruwana, sai dai kin san hausawa sun ce komai girman gona akwai kunyar ƙarshe. Allah ne ya kawo lokaci" Turai ta ce "Hmm, gayyar tsiyar banza da na wofi, zata gani ba dai ta shirya kishi da manyan mata ba, gata nan ga gidan ai" Ammi ta ce "Ai da sunan Allah muka shigo, dan haka ba abin da zai faru da izinin Allah. Ke Amina tashi muje" Suka tashi suka wuce da Amina sashin Daddy, wurin yayi kyau sosai, an jere mata kayan lefenta a bedroom ɗin, komai yayi kyau sosai da sosai. Suka zaunar da Amina suka yi ta mata nasiha, da gaya mata abin da ba a rasa ba, suka kira Daddy a waya dan suna son tafiya, Daddy ya ce su tafi bakomai yana cikin gidan. Suka fita suka tafi, su Hajiya Turai ma sun bar gidan, saboda dare ya fara yi. Duk wannan wunin budurin da aka yi, Fadila bata zauna a gidan ba, saboda kar ma taga tashin hankali. Daddy ya shigo, hannunsa da ledoji, ya fara nufar sashin Hajiya Zainab, amma ya tarar ta rufe da mukulli, juyawa yayi ya koma sashin Amina. Tana kashingiɗe a kan gadon, tana danna wayarta. Ya kalleta tare da yin murmushi, ya ce "Fitsararriyar amarya, maimakon ma ki jira na zo na buɗe fuskar taki, shine kika yi kwanciyar ki ko?" Ya ƙarasa maganar yana zama a kusa da ita, tare da ja mata hanci. Dariya tayi ta tashi zaune ta ce "Wace fuskar zaka buɗe? Mhmm me ka sayo mini?" "Mutuniyarki da madara" Amina ta ce "Wayyo daɗi" "Allah ya shirya wannan amaryar" Amin ta faɗa tana dariya. Daddy ya tashi ya cire babbar rigarsa, ya wuce banɗaki, ya yi alwala, ya fito ya kalli Amina ya ce "Je kiyo alwala muyi salla" Amina ta ce "Da muna Lagos ba ka mini wayo munyi ba". Daddy ya ce "Yanzu kuma a Kano muke ai, kuma satar hanya muka yi wancan karon, yanzu ma sai mu kuma yi" A tare suka yi dariya, Amina ta tashi taje ta yi alwala, ta dawo suka yi salla, yayi musu Addu'a sosai, sannan ya kalleta ya ce "Yanzu wanda bai sani ba ma ya sani, duniya ta shaida ke matata ce" "Da basu sheda ba kenan?" "Da karuwa ce yanzu kuma matata" yayi maganar yana dariya cikin tsokana. Amina ta ce "Hmm zan rama ne" Ya ce "Mmmmm, Meenal uwar daru da rikicin tsiya" ya dinga tuna mata tsiyatakun da ta dinga yi masa. "Kaga miƙo mini kazata in ci" "Innalillahi wai wace irin amarya ce wannan ne?" Tayi dariya ta ce "Irin wadda ka aura ka gama yawo da ita a gari, sai ka dawo kuma ka tuba" hirarsu suke cikin nishaɗi da kwanciyar hankali. Ya dinga bata kazar nan a baki tana cinye kayarta, har sai da ta ƙoshi. Ya kalleta ya ce "Yanzu ki shirya muje in rarrasheki kiyi bacci" Noƙe masa kafaɗa tayi, tana tura baki. Murmushi yayi, ya ɗagata cak zuwa kan makeken gadon ya rungumeta yana rage mata kayan jikinta ya ce "Ba kya son Allah ya bamu wasu twins ɗin? Ina son yara sosai Meenalina, ina fatan Allah ya bamu masu albarka da jin ƙai" Ɗan lumshe ido tayi ta ce "Daddy ciki da raino akwai wahala, ina jin tsoro sosai" "Allah zai sauƙaƙa miki, yayi maganar yana shafa ƙananan kitson da yake kanta. (Sai suka kashe fitila, ni kuma banga komai ba 🚶🚶🚶) Washegari tun sassafe, Ammi tayi musu aiken Abinci, Amina Kamar wata sabuwar Amarya haka ake ta wani ji da ita, mussaman dangin Daddy. Da wuri ta tashi suka karya tare, Daddy ya fita saboda baƙi sun fara zuwa. Sai da ya fara zuwa wurin Hajiya Zainab, amma still ƙofarta a rufe. 'yan garinsu Amina suka zo suka yiwa Amina Sallama, ciki har da Inno, Inno a ranta ta dinga yaba gidan Amina tana faɗin lallai boko tayi rana. Inno ta yiwa Amina nasiha sosai da sosai, tare da jan kunne a kan riƙe addu'a. Daga nan mota ta kwashe su, zuwa Shanono. Tafiyar Inno sai da Amina tayi kuka, kamar lokacin ta fara rabuwa da ita. Babban abin da ya bawa Amina mamaki, wanda bata san da shi ba, shi ne kayan gara da Baba yayi mata, kayan abinci dai-dai ƙarfinsa, ya ce yadda aka ɗauke masa kayan ɗaki, bai kamata ya zauna ba kataɓus ba, dan haka ya yiwa Amina gara. Dangin Daddy, suka yi ta jinjina karamci na danginsu Amina, a nan suka sake suna hira, a hirar ta su Amina taji labarin Auren Alhaji Ahmad da Hajiya Zainab. WANENE ALHAJI AHMAD MUSA DUTSE??? Alhaji Ahmad, haifaffen garin Dutse ne, familynsu sanannu ne a unguwarsu, kasancewar suna da rufin Asiri sosai, kasancewarsu 'yan kasuwa. Kusan su suka mamaye unguwarsu gaba ɗaya, ba yadda za ayi ka shiga layi ka fita, babu danginsu. Mahaifin Alhaji Ahmad, sananne ne sosai, yana ta'ammalli da 'yan siyasa da manyan 'yan kasuwa. Matansa biyu, mahaifiyar Alhaji Ahmad Hajiya Bilki, sai kuma amaryarsa Hajiya Sadiya. Hajiya Biliki bata samu haihuwa da wuri ba, sai bayan da ya auro Hajiya Sadiya tayi haihuwa uku mata. Duk yaran da Hajiya Sadiya ta haifa ba zaka taɓa cewa bana Hajiya Biliki bane ba, saboda yadda ta riƙesu, daga baya cikin ikon Allah ta haifi ɗa namiji aka saka masa suna Ahmad. An yi shagali sosai da sosai bayan haihuwar sa, haihuwar da tayi bai hanata cigaba da rainon yaran Hajiya Sadiya ba. Kowa yana girmama Hajiya Bilki, ciki har da Hajiya Sadiya da yaranta, saboda karamcinta da kyautatawarta. Daga baya Hajiya Bilki ta dinga ɓari, a haka dai bata kuma samu ta haihu ba, sai Hajiya Sadiya da ta haifi yara shida maza da mata. Sai dai ita ma Hajiya Sadiya tana ji da Ahmad, kamar babu wani ɗa a gidan sai shi. Bayan sun girma, duk suna ta karatu, 'yan uwan Ahmad maza suka nuna su sun fi son kasuwanci a kan karatu, shi kuma Ahmad ya ce karatu yake so, mahaifinsu ya goya masa baya yake ta karatunsa. Familynsu suna da matuƙar haɗin kai da ƙaunar juna, suna son junansu kuma manyansu a tsaye suke a kansu, dan haka da wuya kaga wata ɓaraka a tare da su. Kasancewar mahaifin su Alhaji Ahmad mutum ne mai kyauta, hakan ya sanya gidansa baya rabo da jama'a, ai ta shiga ana fita. A jikin gidansu, akwai gidan wani mutum Malam Habu mai itace, yaransa na yawan shigowa gidan su Ahmad, duk da malam Habu ba shi da wani ƙarfi, amma sai auri saki, a haka ya auro wata salihar mata, haihuwarta ɗaya amma azabar yunwa da masifar matansa kusan ita ta haɗu ta kashe ta, ta bar 'yar yarinyarta mai shekaru takwas a duniya Zainab. Ta tashi a tsakanin matan uba, ba kulawa sai azabar wahala, idan ta samu dama sai ta fita tafi wurin babarsu Ahmad wadda suke cewa Gwaggo, Gwaggo ta bata Abinci, idan bata da lafiya Gwaggo ce ke sawa a kaita Asibiti, harkar makarantarta duk ita ce. A lokacin da Ahmad ya cika shekaru Ashirin da ɗaya, yana shirin tafiya service, ita kuma Zainab na da shekaru goma sha huɗu, tana tsakiyar azabar matan uba, Gwaggo ta zaunar da Ahmad ta ce tana neman alfarmar ya auri Zainab, ko dan ya rabata da wahalar da take ciki. shi a rayuwarsa ko budurwa ba shi da ita, amma sama ta ka Gwaggo ta zo masa da wani batu mai nauyin da ba zai iya cewa a'a ba, dan haka ya amince. Tayi murna sosai tayi ta saka masa albarka. Ko da Gwaggo ta tuntuɓi Zainab a kan lamarin sai ta amince, dan Ahmad ya daɗe yana burgeta, duk gidansu babu mai kyansa, gashi ɗan gayu ɗan masu kuɗi. Ganin duk sun amince ya sanya Gwaggo ta yiwa mahaifinsu Ahmad magana, shima ya amince. Sai dai mahaifin Zainab ya ce shi ba shi da kuɗin da zai yi mata kayan gado, Gwaggo ta ce zata yi mata. Haka aka yi bikin nan, Ahmad na da shekaru ashirin da ɗaya, ita kuma shekaru goma sha huɗu. A cikin unguwar Mahaifin su Ahmad ya bashi gidan da zasu zauna, a lokacin ba shi da wata sana'a, karatunsa ya saka a gaba, saboda haka komai daga gida ake aika musu da shi, a ka tura shi Naija state service. Komai daga gidansu Ahmad ake kai mata, Gwaggo ta saka a canza mata makarata ta cigaba da zuwa. Bayan aurensu Ahmad ya fuskanci Zainab ba ta da kunya ko kaɗan, Shegiyar tsiwa ce da ita, amma yayi haƙuri saboda kullum Gwaggo cikin ja masa kunne take. "Ahmad Zainab amanat ce, idan kaci amana amanar mahaifiyarka kaci, kaga marainiya ce, idan ka zalunceta Allah zai saka mata" hakan ya sanya ya dage duk abin da Zainab take so shi yake yi mata. A haka ya gama service, ya kan gayawa Abokinsa Abubakar abin da Zainab take masa na rashin kunya, kasancewar shi Abubakar ya riga shi aure, amma yayi ta bashi baki yana bashi haƙuri. Anyi aurensu babu daɗewa, mahaifinsu Ahmad ya rasu, aikuwa sun girgiza ba su kaɗai ba har mutanen unguwa, da sauran iyalinsu. Kowa yafi tausayawa Ahmad, kasancewar sa ɗan gaban goshin Alhaji Musa. Bayan sadakar bakwai, ya koma garin da yake bautar ƙasa. Bayan mahaifinsu yayi arba'in, aka raba musu gado, aikuwa sun sami dukiya kamar kamar me, ya samu dukiya mai yawa, Zainab sai buɗa hanci ake. Duk da rashin kunya na Zainab, amma tana girmama Gwaggo sosai da sosai. Ahmad ya dawo ba daɗewa, ya nemi ya cigaba da karatu, ya samu admission a BUK, ya ce yana son ya tafi karatu. A wannan lokacin Zainab ta samu cikin ta na fari, lokacin ko Sakandire bata kammala ba. Kasancewar Ahmad ya samu rumfuna a kasuwannin Kano, ya sanya ya haɗa karatunsa da kasuwanci a Kano. Bayan ta haihu ta haifi namiji, Ahmad ya sakawa yaron sunan mahaifin Hajiya Sadiya Ibrahim ake kiransa da Khalil. Tun bayan da Zainab ta haihu, ta fara tsiro da rashin mutunci iri iri, ko gidanta bata son aje, dama 'yan gidansu wulaƙantasu take yi son ranta. Tana gama Sakandire, tabi Ahmad Kano, in da ya sai musu gida a can suka zauna. Zuwanta Kano ya sanya ta sake kilewa, ta fara tsiro masa da rashin mutunci, tun bayan haɗuwarta da su Hajiya Turai da Salma. Suka dinga hure mata kunne, da nuna mata dangin miji da iyayensa ba abin riƙewa bane, shi kansa mijin idan ta fiye sake masa sai ya rainata. Daga baya suka koya mata ko inda take ya zo, sai ya biyata kuɗi kan ta amince da shi, iskanci kala kala. Tun yana haƙuri har ya fara gayawa Hajiya Halima, saboda yafi ɗasawa da ita fiye da Gwaggo. Tayi wa Gwaggo maganar, amma ta ce yayi haƙuri, marainiya ce. Ya zamana ta watsar da su Gwaggon ma, ta daina bi ta kansu, idan 'yan uwan Ahmad suka zo, ta dinga haɗe rai kenan tana yi musu wulaƙanci, tare da kora hali. Su Hajiya Turai suka koya mata bin malamai, duk yadda Ahmad yake da biyayya da son iyayensa, amma sai ya shafe lokaci bai je ba. Hajiya Sadiya ta fara magantuwa, saboda shaƙuwarta da Ahmad, tayi ta mita Gwaggo tayi ta bata haƙuri. A haka Gwaggo ma tayi ciwo na sati biyu Allah ya karɓi abarsa. Ahmad yayi kuka kamar babu gobe, a haka aka share zaman makoki. Nan rashin mutuncin Zainab ya ƙaru, dama Saboda Gwaggon ne ya sanya take ɗaga ƙafa a wasu abubuwan. Bayan rasuwar Gwaggo, Ahmad sai ya shafe wata biyar bai je Jigawa ba, dan tun bayan da ya kammala karatu, yaji daɗin Kano yayi zamansa, shima Hajiya Zainab ce ta takura masa ita ba zata koma Jigawa ba ya barta a Kano. Haka shima ya zauna a Kano. Ana haka abokin mahaifin Ahmad, ya sa aka yiwa Ahmad ɗin Minister, da ƙananun shekaru, zo kaga bakin Zainab mijinta ya zama Minister. Duk ranar da yaje Dutse, abune mawuyaci Hajiya Saidya ba tayi kuka ba, tana son Ahmad kamar yadda take son 'ya'yanta, ba zata manta karamcin mahaifiyarsa a gareta ba, amma ƙiri-ƙiri mace ta raba su, duk da shaƙiwar dake tsakaninsu. Wataran tare suke kukan ya ce "Hajiya ki dinga yi mini Addu'a, ki daina yi mini kuka" Ta kan ce "Addu'a kullum cikinta muke, Allah yayi maka albarka" Ya tattara Zainab suka koma Abuja da zama. Sai dai ya fara damuwa da rashin haihuwa da ba ta sake yi ba, ga Khalil ya girma, saboda Ahmad mutum ne mai matuƙar son yara. Ta kance kar ya dameta Allah ne bai kawo mata ba, nan kuwa planing tayi, sai da Ahmad ya shekara Bakwai sannan ta samu ciki. Bayan ta haihu, ta haifi mace ya ce tunda Gwaggo bata raye, bari ya yiwa Hajiya takwara ya sakamata Sadiya, aikuwa tayi tsalle ta dire ta ce bai isa ba, ba za a sakawa 'yar ta wannan sunan ba Fadila take so a saka mata. Saboda a zauna lafiya, haka ya sakawa yarinyar Fadila, duk so da ƙaunar da familynsu ke da shi, a junansu haka suka zuba masa ido, suka bar shi da iyalinsa, kowa ya daina zuwa in da suke saboda tijarar Zainab. Duk kyautar Alhaji Ahmad, da son 'yan uwansa, daga baya sai wanda ta ga dama yake iya yiwa kyauta, gashi Allah ya ɗaukaka shi a danginsu, babu mai kuɗinsa da shahararsa ga shi suna matuƙar ƙaunarsa, amma mace ta mallake shi. Aka bata shawarar kar ta sake haihuwa, yara biyu sun isheta rayuwa, tun da Allah ya bata kowane jinsi, aikuwa haka ta dinga zabga planing sai da haihuwa ta ɗauke gaba ɗaya. Tun Alhaji Ahmad yana saka ran zata kuma haihuwa, har ya fidda rai. Duk ranar da Allah yasa suka je Jigawa, Hajiya Sadiya kamar ta cinye Fadila, tana ƙaunar 'yar Yarinyar saboda tana kama da Gwaggo, amma Zainab ta dinga nuna kamar ƙyamarsu take ma. Dama tunda mahaifinta ya rasu, ta watsar da 'yan gidansu, ko ta kansu bata bi. A haka har rasuwar Hajiya Sadiya, zuwa wannan lokaci Zainab haka take shimfiɗa mulki son ranta, sai abin da take so za ayi. Wasu lokutan Alhaji Ahmad saboda maganar mahaifiyarsa, yake ɗaga mata ƙafa, da tayi ta ja masa kunne a kan maraicin Zainab, wasu lokutan kuma shi kansa bai san yadda wasu abubuwan suke faruwa ba. Amina sai da ta zubar da hawaye, na tausayin Alhaji Ahmad da iyayensa mata, mussaman da taji Hajiya Sadiya har kuka take yi, saboda rabasu da ɗansu da Hajiya Zainab tayi. Sai la'asar sannan suma mota ta kwashe su zuwa gida. Bayan Amina ta gyara part ɗinta, ta dinga tunani a kan yadda zata ɓullowa al'amuran. "Lokaci yayi, da komai zai zo ƙarshe da yardar Allah!" AYSHERCOOL 08081012143GABA DA. GABANTA               NA AISHA ADAM AYSHERCOOL 65 Daddy bai dawo ba sai bayan magariba, abin da ya bashi mamaki, bai wuce yadda ya tarar da su Hajiya Turai a gidan ba. Suka bishi da kallon banza. Wanda a baya har rige-rigen gaisheshi suke yi. Bai kulasu ba, ya wuce sashinsa, inda Amina take. Tun daga hanyar sashin, wani irin sassanyan ƙamshi na musamman yake dukan hancinsa, ya shiga falon da sallama, amma bata nan. Ya miƙa ya nufi bedroom ɗin, yana buɗewa kunnuwansa suka jiyo masa sautin muryar Amina tana rera Karatun Alqur'ani mai girma. Zuwa ya yi ya zauna a kusa da ita, ta cigaba da karatunta, a hankali ya kwanta a kan cinyarta, ya lumshe idanunsa yana jin yadda take zuba karatun Alqur'ani da ka. Sai da ta kai aya ta idar, sannan ta kalleshi ta ɗan shafi gemunsa ta ce "Babyna, sannu da zuwa" "Yauwa sayyada, kamar kar ki daina karatun nan Meenal" Murmushi tayi ta shafa kansa ta ce "Meyasa baka dawo gida ba kaci Abinci?" "Bana son na takura miki ne, naga kina da baƙi, naje na saka a gyara in da aka sauki baƙi, na tarar sun gyara komai fes, ya kika ga familyn namu, ina fatan dai ba wata matsala?" "Ba wata matsala, naji daɗin zuwansu sun ɗebe mini kewa sosai, yaushe zaka kaini Dutse?" "Very soon, ina son muje honeymoon ko 2weeks ne, da mun dawo sai na kai ki" Amina ta ce "Mmm, meye Honeymoon?" "Ban sani ba, Baby zamu samo" dariya tayi tana jan hancinsa, sannan ta ce "Amm na manta, ga kayan garata can, ina son a ɗebar musu nasu, a samu ko aika musu ne ayi" Tashi yayi zaune da mamaki ya kalleta ya ce "Gara kuma, wace irin gara?" "Gara mana da ake yiwa mace idan tayi aure" "Haba Amina, wato zuwa kika yi kika saka Baba a gaba yayi miki gara ko, ni nace miki ina son gara ne?" Tsuke fuska tayi ta ce "To ni na san zasu kawo ne, kawai fa gani nayi an kawo" "Na san halinki, ki gaya mini gaskiya" Kwaɓe fuska tayi za ta yi masa kuka, ya ce "Ya isa shikenan, zan saka a kwashe a mayar gaskiya, ai abin kunya ne a gareni ace dan na auri 'ya sai an mata gara" "Yanzu Daddy ko kara ba zaka yi mini ba sai kasa a kwashi kayan a mayar? Wato kafi ƙarfin iyayena su bamu abu ko? Kar ka manta ni kaɗai suka mallaka komai suka samu dole ni zasu yiwa, amma bakomai na gode" Ganin tayi fushi ya sanya ya sassauta murya ya ce "Babyna ba haka nake nufi ba, kiyi haƙuri dan Allah, na fasa a mayar ɗin komai ya wuce please" Sake haɗe rai tayi ta kawar da kai. Ya sake kwantar da murya ya ce "Haba tawan, smile mana, i have some candy for you" "Cin hanci zaka bani" "Eh, mana in dai zai sanya ki huce" "Hmmm to shikenan, na haƙura tashi muje aci Abinci" ya miƙe ta riƙo hannunsa suka fita falo. Bayan ya gama cin abincin ya nutsu ta ce "Daddy lefe na yayi kyau sosai, Allah ya ƙara arziƙi, ina ga da zai yiwu da Khalil ma ya tara nasa a wurin Anty Maryam, ba laifi ta iya zaɓe ta san kan kaya" Daddy ya ce "Haka ne, wannan kuma ke zaki baki shi shawara, ni yanzu damuwata gininsa da ya tsaya yi masa iyayi da ƙaƙale, ya hanzarta yayi abin da zai yi ayi bikin, tun kan uwarsa ta hana" Amina ta ce "Ta hana kuma, Daddy sai ka bari a fasa auren idan ta hana duk da kaje kayi magana ka kai musu kuɗin aure?" "To Meenal ya zan yi? Kina kallon yadda nake ta fama da ita ai, tunda Allah ya sanya ta san aure muka yi, take tayar mini da hankali, ita kanta taƙi bari nata hankalin ya kwanta, na ma rasa yadda zan yi" "To ai koma menene yake faruwa duk laifinka ne" "Laifina kamar yaya?" "Da ita da yaranta duk a ƙarƙashin ka suke, amma ka sakar mata ragamar gidan, sai abin da ta zartar, yakamata ka dinga tauna tsakuwa dannaya taji tsoro, ba a komai ya kamata ka dinga bari ana jayayya da kai ba, ba zigaka nake ba amma when it comes to serious issues, you have to be so serious, ba wai sai abin da suke so ba, batun auren Khalil idan ka bari aka fasa saboda mahaifiyarsa ba ayiwa yarinyar adalci ba" Daddy ya ɗan yi shiru sannan ya ce "Haka ne maganarki, in Allah ya yarda babu wani abi da zai faru, za ayi auren da yardar Allah, ni ban gaya miki wani abu bama, wani abokina ne da matarsa ta rasu, yake neman ya samu mace mai hankali wadda zata iya kula masa da yaran, duk da yaran ba ƙanana bane ba duk sun manyanta, wallahi nayi masa sha'awar auren sirikar Khalil, matar ba wata babba bace tana da ƙuruciya sosai gata jajirtacciya kuma nutsatsiya, bana son yin magana taga kamar na yi mata wulaƙanci ko na rainata, da na haɗa su" Amina ta gyara zama ta ce "Kai amma naji daɗi, nifa tun da ka gaya mini halin da suke ciki, nake jin rausayinsu wallahi. Yanzu abin da za ayi shi ne, ka yiwa abokin naka maganarta, amma sai ka ɗauke shi kuje a matsayin kun je da niyyar batun auren su Khalil, irin ko suna buƙatar wani abu, ko kuma dai makamnacin haka, kaga zai ganta a nan, idan tayi masa daga baya shi sai ya koma, idan ta amince shikenan idan bata amince ba shikenan". Daddy kawai yayi shiru yana kallon Amina. "Ya kuma naga kana kallona?" "Kawai ina jinjinawa basirarki ne, ke har kin lissafa kin samo solution, to shikenan hakan za ayi, Allah ya sa su daidaita". "Amin Daddy, kaima Allah ya baka lada" Da daddaren ya sake komawa wurin Hajiya Zainab, wannan karon ya tarar da ƙofarta a buɗe. "Meyasa kike rufe ƙofar ki ne?" "Saboda bana ƙaunar ganinka" Daddy ya ce "Ai ba sai kin faɗa ba na sani. Na zo ne na sauke nauyi, duk da yakamata na haɗaku nayi muku nasiha, amma na san halinki sai kinyi abin da zaki zubarwa da kanki mutunci a gaban yarinya, dan haka nazo na sameki ni da ke. Ina magana ne a kan batun rabon kwana ke da abokiyar zamanki, tunda babu buƙatar spending seven days ɗin nan, tunda koma dai menene ya riga ya faru". "Dawa kake tunanin zaka raba kwana ni? Ba dai ni ba ka daina wannan tunanin kuma ka tashi ka bar mini ɗakina tun muna sheda juna da kai, kaje na sallama mata bana buƙatar ka" "Idan ke ba kya buƙatata, ni ina buƙatarki, ba zaki saka in zalunceki ki barni da hakkinki ba" Ta kalleshi sheƙeƙe ta ce "Au, wai kai nan har wani hakki ka sani, ka san daida da ba daidai ba? Kai ko kunya ba ka ji ba, dan Allah ɓace mini daga ɗakina, bana buƙatar ko kallon fuskarka" "Shikenan, kiyi abin da kike so, ni zan yanke abin da naga ya dace, sannan ina saka ran next week zamu bar ƙasar nan tare da Amina, amma ba zamu daɗe ba, baifi muyi 2weeks ba mu dawo". "Ku bar duniyar ma idan kaga dama, aikin banza kawai, kuma wallahi ina sake jan kunneka a kan auren da zaka yiwa Khalil, wallahi idan baka janye Maganar nan ba komai ya biyo baya ka kuka da kanka" Daddy ya girgiza kai ya ce "Ɗanki ne dai, idan kika yi masa baki Allah ya jarrabeshi da auren mace irinki, kanki abin zai dawo" A fusace ta miƙe ta ce "Me kake nufi da auren mace irina? Kana nufin ni mutuniyar banza ce?" "Wannan kuma ke zaki wa kanki alƙalanci" ya juya ya fice ya bar mata ɗakin. "Kan uba, lallai ma mutumin nan" Daddy wurin Khalil ya nufa, ya tarar da shi a falonsa, yana ta waya har Daddyn ya shigo bai sani ba. "Kai Magana na zo muyi fa" Khalil yayi firgigit, ya katse wayar ya hau sosa kai ya ce "Yi haƙuri Daddy, ban san kana nan ba. "Dama ina zaka san na zo, kana nan kana soyayya" shafa kai Khalil yayi yana shafa kansa. Daddy ya zauna a kusa da Khalil ya ce "Ya 'yar tawa, ina fatan tana nan lafiya" "Tana lafiya lau, kalau Daddy, tana cewa ma in gaisheka" "Amma ai baka gaya mini" Khalil yayi murmushi yana shafa kai. "To yanzu kai meye shirinka? Kasan ba a saka wani dogon lokaci ba" "To, dama Daddy batun ginina na ajiye cigaba da ginina saboda a baya naga kamar ba zan samu Hafsa ba, amma to yanzu dai zan cigaba da ginin, sai kuma batun kayan lefen". Daddy ya ce "Ai kaine Khalil, wannan gida naka ka janyo ƙaƙale ƙaƙale da yawa, bana tunanin zai kammla kan lokacin, amma lefen Amina ta ce nata da Hajiya Maryam ta haɗa mata sun yi kyau sosai, ko kaima kuɗin zaka bayar idan ya so ta faɗi duk abin da take so a saya mata" "Shikenan Daddy, duk yadda ka ce yayi, idan kuɗin ne sai na tura" "To babu laifi, sai kuma magana ta biyu, duk yadda ake ciki ka tattara kayanka ka bar garin nan gobe in Allah ya kaimu, idan ba haka ba kuwa mahaifiyarka zata iya hana auren nan" Khalil yayi saroro yana kallon Daddy. Daddy ya ce "Ƙwarai kuwa, tun wuri ka koma duk abin da ake ciki ma dinga waya kawai" Khalil yayi ajiyar zuciya, dan har ga Allah yana son cigaba da zuwa wurin Hafsa, dan su cigaba da samun shaƙuwa da fahimtar juna. Jiki a sanyaye ya ce "To shikenan Daddy, zan koma in Allah ya yarda" "Yauwa, Allah ya taimaka ya sanya albarka" "Amin Daddy na gode sosai" Daddy ya yi masa sallama ya koma wurin Amina. Bayan tafiyar Daddy, Khalil ya ƙudurce gobe da Safe zai ɗau mota ya koma Abuja, ba sai ya jira jirgi ba, karma Mummy ta zo da wani batun da zai zama barazana ga aurensa. Idan yana tare da Amina mantawa yake da komai, yaji kamar babu abin da yake damunsa, saboda yadda take tattalinsa take kula da shi, shi kansa har mamakin irin tsananin son da yake mata yake. A duk lokacin da ta ganshi cikin walwala da fara'a ta kan yi amfani da wannan damar, wurin tuntar da shi abubuwa, da ɗora shi a kan hanyar da ta dace, yadda yakamata yayi wa kansa guzurin lahira a dukiyarsa tun yana raye. A 'yan kwanakin da ya kasance tare da Amina, tunda ta tare duk wanda ya zo gidan nan, sai Amina ta bashi kuɗin mota, sai tayi girkin Abinci ta bawa mutum ya ci ya ƙoshi, sannan ya baka kuɗi. Daddy yana ajiye kuɗi a ɗakinta sosai, kuma ya mata izinin yin amfani da su, dan haka ta samu damar yin kyauta sosai. Washegari ta kasance Litinin ce, Khalil ya kintsa kayansa ya tafi wurin Mummy da sassafe zai yi mata sallama ya tafi. Wani irin kallon bamza tayi masa sanan ta ce "Daga zuwanka har ka gama kwanakin zaka tattara kayanka ka koma ko Khalil. To ina sake jadadda maka ina nan daram a kan bakana, muddin kayi wannan auren sai dai ka nemi wata uwar, dan ba zan cigaba da amsa sunan uwarka ba, tunda ka zaɓi ubanka a kaina, shi yake hure maka kunne" A sanyaye ya ce "Mummy ba haka bane ba, wurin aikine ake nemana" "Rufe mini baki ni, koma waye yake nemanka kaje ka ƙarata, amma zaka dawo ka sameni, kuma aurene ba ka isa ka auri 'yar matsiyata ba, zan gani idan ina da muhimmanci a wurinka" Jiki a saɓule Khalil ya tashi, ko wurin Abdul bai je ba, saboda safiya ce, balle Hafsa duk ya bari a ransa yayi musu sallama ta waya, shirye-shirye kuma sa cigaba da yi ta waya, amma jikinsa yayi sanyi da inkarin da Mummy take, na idan yayi auren nan ba shi ba ita. Tayi mamaki ƙwarai, da Khalil bai nuna wata nadama ba, ya sa kai ya fice babu alamar zai janye batun auren nan. Abin ya ƙular da ita sosai da sosai, miƙewa tayi ta nufi sashin Daddy, tana zuwa ta tsaya a ƙofar bedroom ɗin, ta dinga bugawa kamar zata karya ƙofar. Amina ce ta fito da 'yar riga iya cinyarta, kanta ko ɗan kwali babu tana mutsutsuka idonta. "Malama lafiya kike mana wannan bugun da safiyar nan?" "Ke! Ba wurinki na zo ba, wurin mijina na zo yana ina?" Amina ta rufe ƙofar bedroom ɗin sannan ta ce "Mijinmu dai ko? Bacci yake yi bai tashi ba ya aka yi?" "Ba ruwana da bai tashi ba, ki bani hanya na wuce" Amina ta tare ƙofar ta ce "Uban da ya saka kika masa rashin mutunci, ki ka koro mini shi nan, sai ya sa ki haƙura zuwa lokacin da zai dawo wurinki, kya gaya masa koma menene" "Ke ni kike gayawa haka, sa'arki ce ni? Zaki bani hanya ko saina make ki" Cikin rashin kunya Amina ta ce "Ba zan matsa ba, gobe idan ya kuma wurinki ki koreshi, yana zuwa zan caraf da shi ni. Ai ni Allah ne yayi mini gyaɗar dogo ma samu mijin shashasha, wadda bata da ra'ayin kanta sai na ƙawa, idan basu sa kin kashe auren nan ba ba zaki yi hankali ba" "Ni kike gayawa haka? Dan kin auri mijina gani kike ni sa'arki ce, wallahi sai nayi maganinki" "Allah da yayi ni shine maganina, ba ke ba, Allah sarki rayuwa, ba zan taɓa manta ranar da na zauna a kan kujerar falon mijinki ba, kika ƙare mini zagi da cin mutunci, amma da yake Allah ba yadda bai iya ba, sai gashi ƙirjinsa ne matashina, a kan ruwan cikinsa nake kwana, kin gama yi mini komai da kika sallama mini shi, Baby ya iya soyayya" ba tsoro balle kunya, Amina take gasawa Hajiya Zainab maganganu masu zafin gaske. Jikin Hajiya Zainab har rawa yake, saboda azabar ɓacin rai ta ce "Ni kike gayawa wannan maganar?" "Uwata ce ke da ba zan gaya miki ba? Ko kin manta lokacin da kike cin mutuncin ubana a gabana, ai kaɗan kika gani, ba zan fasa yi miki abin da na ga dama ba, har sai na tabattar da zuciyata ta samu nutsuwa daga baƙin cikin da kika dinga tura mini a zuciyata, abu mafi zafi a rai shi ne zagin ubana a gabana da kike yi" "Na zagi uban naki, matsiyata 'yan ƙauye" Amina ta ce "Ai ba zanji haushi ba yanzu, dan kin zagi Babana mussman da na san asalin balbela, kema daɗinta naki uban ba wani bane ba, da miji kike taƙama idan har za a kira maigadi matsiyaci ban san da wani sunan za a kira mai faskare ba, koda yake koba komai ko da goma ta lalace tafi biyar albarka, saboda rayuwata ta ginu nawa uban ya dage yake jure duk wani cin mutunci ake masa a gidan nan" Cikin tsananin fushi, da zafin nama Hajiya Zainab ta fizgo Amina, ta hankaɗata ƙasa. Amina kuwa ta ware baki, ta kurma uban ihu tana kiran "Wayyo Allahna Daddy ka fito kar ta kasheni, Daddy!Daddy matarka zata illatani" Duk da sama sama yake jiyo ihun Amina, a sukwane ya farka daga baccin da yake, ya fito daga bedroom ɗin, aikuwa yaga Amina a ƙasa hawaye ya wanke mata fuska, Hajiya Zainab kuma na tsaye a kanta tana huci. Ita kuwa Fadila, ta gama shirin makarantarta, ta ƙudurce zata je ta yiwa Daddy maganar kuɗin registration ɗin ta na makaranta, dan haka bayan ta kintsa, ta ɗauko jakarta ta nufi sashin Daddy. Daddy kuwa kan Amina yayi da sauri, ya ɗagota yana faɗin Meenalina, menene meyafaru?" Cikin kuka Amina ta ce "Dukana za tayi, hankaɗe ni tayi ni ƙafata da bayana ciwo suke, dan kawai nace mata bacci kake yi ba zan tasheka ba" Aikuwa ran Daddy ya ɓaci, ya kalli Hajiya Zainab ya ce "Wai meyasa baki da girma ne? Kina cewa nayi abin kunya na auri 'yar cikina, ke kuma me ki ka yi? Zaki yi dambe da 'yar cikinki? A irin haka fa kuka je ke da 'yar ki kuka saka tayi ɓari, duk kashedin da nayi miki a kan Yarinyar nan baki ji ba, so kike sai kin illata ta hankalinki zai kwanta?" "Kai baka san meyafaru ba kawai daga fitowarka zaka hauni da masifa, kai wani irin mutum ne, na dake ta ɗin kayi abin da zaka yi" "Zainab na gaji da kawar miki da kai, koma menene ke kika zo in da take ai, ba ita taje in da kike ba, zan aikata abin da baki tsammani ba, muddin kika cigaba da takurawa rayuwarta, ba ita tayi miki laifi ba, nine da na aureta, komai zaki yi mini, zanniya jurewa bai dameni ba, amna ba zan lanunci cin zarafin 'yar mutane ba dan kawai ina aurenki ba, ita ma matata ce dan haka ki kiyayeni" Ai gaba ɗaya sai Hajiya Zainab taji kamar ƙafafunta sun gaza ɗaukarta. Ya kalli Amina cikin kulawa ya ce "Sannu Meenal, tashi muga" "Ni ƙafar ciwo take mini, ka ɗaukeni muje ka ja mini" ya sunkuya ya ɗauketa kamar 'yar baby, ta kalli Hajiya Zainab tayi mata gwalo. Fadila da taji abinda ya faru, kawai ta juya ta fice kan Mummy ta fito tana kuka. Ikon Allah ne kawai ya kai Fadila makaranta, saboda tuƙi take amma sam ba a hayyacinta take ba, kuka kawai take yi. Daddy kuwa a kan gado ya sauke Amina, ya zauna yana matsa mata ƙafar yana cewa "Sannu, ince ko dai bayan ƙafar ba abin da yake miki ciwo?" Amina ta jinjina kai. Ya cigaba da ja mata yatsun ƙafar, yana faɗin "Sannu babyna, kar ki dinga biye mata dan Allah, kar ta illata mini ke, idan tayi miki wani abun ni ki gaya mini na ɗau mataki, amma dan Allah karki dinga biye nata tayi miki illa" Cikin shagwaɓa ta ce "Nifa ba biye mata nayi ba, kawai daga cewa bacci kake ta hankaɗeni" "To kiyi haƙuri cutyna" yayi maganar yana shafar fuskarta zuwa kan hawayenta. Hajiya Zainab kuwa har ta nufi ɗakinta zuciyarta na yi mata zafi, ta juyo ta dawo ta banka ɗakin. Tana bankawa ta tarar da Amina ta ɗage rigar jikinta, ta ɗora santala santalan ƙafafuwanta a kan nasa, tana goge hawaye, shi kuma sai lallaɓata yake yana kwantar mata da hankali. Kamar zata afka kans Hajiya Zainab ta ce "Kai Ahmad na gaji, na gaji wallahi, na gaji da wannan cin kashin da kake mini. Wallahi ko ni ko wannan sheɗaniyar yarinyar, zaka gane baku da wayo daga kai har ita" Saroro suka yi suna kallon Hajiya Zainab, sai masifa take kamar ta haukace, sai da ta yi ta gama ta fice daga ɗakin. Rarrashin Amina ya cigaba da yi, yana kwantar mata da hankali, a kan in dai yana nan babu abin da Hajiya Zainab za tayi mata. A yadda Fadila ta shigo aji, idnuwanta jawur duk sun kumbura, gaban Yazid ya faɗi ya juya yana binta da kallo. Haka aka yi lectures, yana yi yana kallon Fadila, tana ta share hawaye. Haka suka yi lectures wuni guda, hankalin Yazid yana kanta, yana mamakin menene ya sanyata a wannan halin haka. Ko fita cin abinci bai ga tayi ba, kuma tsawon awannin nan, hawaye take zubarwa, kowa sabgar gabansa yake a ajin. Koda aka tashi ma, Yazid yana zaune yana kallon in da take zaune, kowa ya watse amma sai ɗaiɗaikun mutane, ita kuwa tana zaune ta kifa kanta. Miƙewa yayi ya nufi in da take zaune, ya ɗan daddaki kan teburin, amma bata motsa ba. Ya kira sunanta a hankali "Fadila" kamar wadda take bacci haka tayi firgigit ta tashi. "An tashi kowa ya tafi, amma kina zaune, lafiya kuwa?" Ta girgiza masa kai, ta fara duba jakarta. Zama yayi a kusa da ita ya kalleta ya ce "Ukty meke damunki haka?" "Ban sani ba" ta faɗa cikin tsiwa. "Yi haƙuri, amma tun da kika zo fa kike kuka, me yayi zafi ne haka?" "Na ce maka ban sani ba, ina ruwanka dani ne? Ba kace bani ba kai ba ka rabu da ni mana" Yazid yayi murmushi ya ce "Eh na faɗa, amma ke kika fara ai. Zuciyata ta kasa daurewa, bana son ganin mutum cikin damuwa, yanzu haka ji nake kamar na tayaki, meke faruwa can You share it with me?" Kawai ta sake fashewa da kuka, har da sheshsheƙa. "Fadila nima zaki sani kuka, dan Allah ko menene yake damunki, kiyi haƙuri yi ta maimaita innalillahi wa innalillahi raji'un" yayi maganar a raunane. Kallonsa Fadila tayi, da gaske yake zai tayata kukan, saboda yadda idanunsa suka sauya. "Ni gida zan tafi, bani wuri" tayi maganar tana share hawaye. Jakarta ya ɗauka ya ce "Muje na rakaki mota" tashi tayi tai gaba, yabi bayanta. Har suka isa motarta, kuka take bata fasa ba. Yazid ha ce "Bana tunanin zaki iya tuƙin nan, bani mukullin na kai ki gida" Abin mamaki bata yi masa musu ba, ta miƙa masa mukullin, ba tare da tana tabbacin ya iya jan motar ko bai iya ba. Ya karɓa ya buɗe motar ya buɗe mata ta shiga, shima ya shiga ya kunna motar. Ya ɗan kalleta ya ce "Ina ne adress ɗin?" Nan tayi masa kwatance, ya yi addu'a, sannan ya fara jan motar a hankali. Ganin ta ɗanyi Shiru, tana kallon gefen hanya, ya sanya Yazid ya ce "Yanzu gaya mini, meke damunki kike wannan kukan?" "Wai kai ina ruwanka da abin da yake damuna, bayan kace ba kai ba ni, meya dameka da ni?" "Hmm kin ji babu daɗi kenan, ai ke kika ce mini zaren ba kalar yadin bane" Cikin tsiwa ta ce "To da kalarsa ne?" Ya ce "A'a sorry. Tunda kin daina kukan Alhamdilillah, ita rayuwa haƙuri ake yi da ita, kuma komai yayi zafi magainsa Allah" Yana rarrshinta, amma ji take kamar yana fama mata abin da yake mata ciwo. Yazid ya sha uban mamaki, ganin uban danƙareren gidan su Fadila, yayi horn aka buɗe masa gate, ya shiga da motar ciki. Sai dai yana shiga da motar, taji kamar ya dawo da ita cikin baƙin cikin da take ciki tsundum. "A ina zan yi parking ɗin?" "Kayi a ko ina ne ma" Yazid ya yi parking, amma kan ya farga, tuni Fadila ta buɗe motar ta fice. Amina tana falo tana ƙoƙarin fitowa, Fadila ta dawo ta wuceta fuuuuu kamar korarriya. Amina ko a jikinta ta fito, tana fitowa taga Yazid a tsaye da mukullin mota a hannunsa. Yazid ya ce "Sannu dai" Amina ta ce "Yauwa sannu da zuwa, wa kake nema?" "Amm dama Fadila na kawo gida, kuma bata tsaya ta karɓi mukullin motar ba, naga ta fice ta shiga gida" Amina ta ƙare masa kallo sannan ta ce "Ko kai ne Yazid?" Yazid ya ce "Eh ni ne" Amina ta ce "Masha Allah, sannu da ƙoƙari bani mukullin na bata" Yazid ya bawa Amina mukulli, har zai juya ya tafi ta ce "A'a ka tsaya a baka ko ruwa ka sha mana" Yazid ya ce "A'a na gode" Amina ta ce 'A'a ba zanji daɗi ba gaskiya, dan Allah ka jirani ina zuwa" Yazid ya ce to. Amina ta nufi cikin gida, tana wani irin murmushi da ita kaɗai ta san ma'anarsa. AYSHERCOOL 08081012143GABA DA GABANTA NA AISHA ADAM AYSHERCOOL 66 A falo Amina taga Hajara tana aiki, Amina ta ce "Hajara, ɗan biyoni dan Allah zaki tayani wani ɗan aiki" Hajara ta ce "To uwar ɗakina" tabi bayan Amina. Hajara ta tsaya a falo tana jiran Amina. Amina ta shiga bedroom ta buɗe wardrobe ɗin Daddy, ta ɗauko galla gallan shadda guda biyu, da turare ta saka kuɗi a envelope ta fito ta miƙawa Hajara ta ce "Biyoni" suka fito in da ta bar Yazid a tsaye, ta karɓi kayan hannun Hajara ta miƙawa Yazid ta ce "Gashi muna godiya sosai da sosai" Yazid ya ce "A'a gaskiya ba zan karɓa ba, na gode sosai" Amina ta ɗan tsuke fuska ta ce "Meyasa, ka san babu kyau a baka kyauta ka ƙi karɓa faɗar maznon Allah Sallallahu alaihi Wasallam ce" Ba dan Yazid ya so ba ya karɓa ya ce "Na gode sosai" "Bakomai malam Yazid, Allah ya saka da alheri" Yazid ya jinjina kai, yayi gaba ya fita daga gidan. Hajara ta ce "Uwar ɗakina, wannan kuma waye?" Tayi murmushi ta ce "Nima dai ban kai ga sani ba tukuna, amma wani abu ma shirin faruwa, da zai bawa kowa mamaki" Cikin rashin fahimta, Hajara ta ce "Ban gane ba" "Zaki gane ne Hajara" daga haka ba ta kuma cewa komai ba, ta wuce sashinta. Fadila bayan ta gama koke-kokenta, ta shiga tayi wanka, ta sauya kaya ta fito taje taga a wani hali Mummy take ciki. Sai dai tana zuwa ta tarar da Mummy bata nan. Hanyar Kitchen ta nufa tana kwaɗawa Hajara kira. Hajara ta fito ta ce "Gani" "Ki sama mini abin da zan ci" Hajara ta ce to. har ta juya zata tafi. Fadila ta ce "Kin san in da Mummy ta tafi ne?" "A'a ban sani ba" "Shikenan je ki, kiyi sauri ina jiranki" Fadila ta koma kan dining, ta zauna tana kiran layin Mummy. Amina ce ta sake fitowa, da ɗan ƙaramin plate a hannunta, ɗauke da yankakaen lemo. Tv ta kunna, ta harɗe ƙafarta tana ciye-ciyen ta tana kallo. Amina na ɗaga ido, suka yi ido huɗu da Fadila, Fadila tayi mata wani irin mugun kallo. Amina ta ce "Oho, a dake dai ba zan daku ba, sai dai kallon banzan daga nesa" Tsaki Fadila tayi, ta cigaba da danna wayarta, Amina kuma ta cigaba da ciye-ciye. Hajara ta fito ta kawowa Fadila Abinci ta ajiye, Fadila ta fara ƙoƙarin cakalar Abincin ta ci, sai dai sam baya yi mata daɗi. Ga lambar Mummy ta ƙi shiga gaba ɗaya. Daddy ne yayi sallama a falon, Amina ta amsa masa ta ɗaga kai tana kallonsa tana murmushi. "Meenal, sannu da hutawa" "Sannu da zuwa Ranka ya daɗe" tayi maganar tana tashi tsaye. Ta ƙarasa gabansa ta karɓi ledar hannunsa tana binsa da wani irin kallo tana murmushi. Ya riƙe hannunta suka wuce, ba tare da ya ko kalli in da Fadila take ba, kamar yadda ita ma bata ko yi masa sannu da zuwa ba, saboda kwata kwata ba ta shiga sabgar Daddy gaba ɗaya yanzu. Ganin sun wuce ɗaki abin su hankali kwance, ya sanya Fadila ta tashi ta bar Abincin, tana jin wani abu mai ɗaci yana kai komo a maƙogwaronta saboda baƙin ciki. Shi kuwa Daddy, tun da ya shige wurin Amina bai sake fitowa ba, sai da aka kira magariba. Hajiya Zainab kuwa, tana fita gidan Hajiya Salma ta wuce, Hajiya Salma na ganinta ta san ba lafiya lau ba. A ɗan rikice ta ce "Zainab, meyafaru ne na ganki a wannan birkice haka?" "Ba dole ki gannin a birkice ba, na gaji wallahi Salma na gaji, ƙarar Ahmad zan yi ya sake ni, wannan matsiyaciyar Yarinyar da ace ita ta koreni daga gidan, gara ace ni na bar shi, yarinya kamar karuwa ga sharri, nuna mini yake a kanta zai iya sakina fa" "To ke maye ya haɗaki da ita ma?" Nan ta gayawa Hajiya Salma abin da yafaru da safiyar ranar. "Lallai Ahmad ya wuce yadda muke zato, gaskiya mun yi sake da har ya iya ƙara auren nan ma" Hajiya Zainab ta ce "Ai ni na gaji ma, ya sakeni kawai ba zan zauna baƙin ciki ya kasheni ba" Hajiya Salma ta ce "Kut, baki da hankali, ya sake ki kije ina, ai duk wata hayaniya ayi ta da ke, gidan naki a zo a tarar da ke kice ya sake ki, ba zai yiwu ba, Dole mu nausa Nijar a gobe in Allah ya kaimu, a karɓo asirn da sai ta bar gidan nan da ƙafarta, ki cigaba da mulkinki son ranki" "Ke nifa damuwar tawa da yawa, ya zanyi da batun auren Khalil, yaron nan ƙiri-ƙiri goyon bayan ubansa yake, kuma ubansa ya ɗaure masa gindin ya auri wannan Yarinyar" Hajiya Salma ta ce "Kwantar da hankalinki, duk idan muka je Nijar ɗin za a san abin yi, Sannan kamar yadda na gaya miki, a satin nan baban Salim zai dawo, yana dawowa zan saka shi yaje ya sameshi suyi maganar auren su da Fadila. Kuma mu haɗadu ko ta wayane kan Allah ya sanya ya dawo gari" Hajiya Zainab tayi ajiyar zuciya ta ce "Naji, da tunanina idan muka dawo, ko gidansu Yarinyar nan zamu nema, muje na ciwa uwatta mutunci idan suna da zuciya ai sai su ƙyale mini ɗana" "Ke Ina! Yadda yake a kan tsinin nan yake rawar kai, sai ya ɗau matakin da ya ga dama a kanki ai, ki fara bari muje mu karɓo abin da yakamata, idan ya ci sai mu koma kan Khalil, ko kuma idan ma ba hakan ba, idan sai ya auretan, ki hanata sukuni ki hanata sakat sai rabu da ɗanki, kinga ta komawa iyayenta a ƙaranar bazawara idan kwaɗayi abin yi ne sa ƙara". Hajiya Zainab ta ce 'Kai Salma, har na ɗan ji daɗi wallahi, yanzu abin da za ayi shi ne, ba zan koma gidan nan ba, sai mun dawo daga nijar, na koma da ƙwarina, yanzu idan ina gidan nan, zan iya babbake mu gaba ɗaya kowa ya huta" Hajiya Salma ta ce "Kashe wayoyinki kiyi zamanki wallahi, yaje ya ƙarata". Wasa-wasa har ƙarfe tara na dare zuwa goma, wayar Hajiya Zainab bata shiga, kuma bata dawo gida ba, hankalin Fadila ba ƙaramin tashi yayi ba, tun tana daurewa har ta kasa. Har goma da rabi ba Hajiya Zainab babu dalilinta, hankalin Fadila ya tashi ƙwarai, ta tashi ta tafi sashin Alhaji Ahmad. Da sallama ta shiga falon nasa, ya amsa mata shi da Amina da ke kwance a kan cinyarsa suna kallo. Ta tsaya tayi shiru ba tare da ta ce komai ba. Daddy ya ce "Lafiya ki ka zo, kika tsaya mana a ka?" "Dama, tunda na dawo gida ne, na duba banga Mummy ba, ina ta kiran lambarta amma bata shiga, kuma haryanzu bata dawo ba" Ya ce "Hmm Fadila kenan, sai da buƙatarki ta tashi sannan kika san da zamana, kin ɗauki gaba dani ke da mahaifiyarki kamar wanda ya wofantar da ku, ai shikenan ni bata gaya mini in da zata je ba, nima naje sashinta bata nan, na kira wayarta bata shiga" jiki a sanyaye Fadila ta fice daga falon, tare da mamakin yadda Daddyn ya nuna halin ko in kula da rashin sanin in da mahaifiyarta take. Amina ta ce "Yauwa Sweetheart, ni fa nayi maka laifi" "Meenalina, ai ke ba kya laifi a wurina amma me kika yi?" "Ma buɗe wardrobe ɗinka, na yi kyauta da sabbin shaddoji guda biyu, na kuma ɗebar maka kuɗi dubu ashirin na haɗa na bayar" Daddy ya ce "To ya na iya da ke Meenalin, Allah ya haɗamu a ladan, wa kika bawa?" "Baƙi nayi na basu" "To shikenan, babu laifi ai kece" Ta gyara kwanciyarta ta ce "Mhmmmm, Daddy nikam nayi mamakin yadda lokaci ɗaya Fadila ita ma ta sauya maka, duk da irin soyayar dake tsakaninku ban yi zaton za tayi avoiding ɗinka haka ba" Daddy ya ce "To ya zanyi, tunda abin da mahaifiyarta ta ɗorata a kai kenan" "Ni bana son a zargeni da laifin rabuwar kan iyalanka, amma ya batun aurenta ne, naji kace itama zaka zauna da iyayen wansa zata aura ko?" "Ehh, dan sonake kafin muyi tafiya , mu zauna da su mu tsayar da lokaci". "Amma kayi bincike a kan wanda zata aura ɗin?" Daddy ya ce 'Koma waye ba uwatta ce ta kawo shi ba, ita ta zaɓa mata shi ba, na san ba zata zaɓa mata wanda bata so ba ai" Amina ta ce "Haka ne, Allah ya sanya albarka" Ya amsa da "Amin" Har sun fara shirin kwanciya, Amina ta ce "Daddy, yakamata kaje wurin Fadila, ka ɗan kwantar mata da hankali na san tana cikin tashin hankalin rashin sanin in da mahaifiyarta take, ni kaina na fara tsoro ace ba wanda ya san in da ta tafi" Daddy ya ɗan numfasa ya ce "Amma ai tana da hankali, koma ina take zata dawo, tunda bata da in da yafi nan". "Haka ne, amma ka san ɗa da uwa, kaje ka ga halin da take ciki". Amina tayi ta lallaɓa shi, ya je ya samu Fadila. Yana zuwa ɗakinta ya tarar da ita a zaune tana kuka. Ya ƙarasa in da take ya zauna ya ce "Ki daina wannan kukan haka, is ok, mamanki koma a ina take ina da yaƙinin tana cikin ƙoshin lafiya, tunda da kanta ta fita, kuma na san zata dawo, ki daina wannan koke koken haka" Jinjina masa kai kawai tayi, ba wa dan zata iya daina kukan ba, sai dan fatanta ya gama maganar ya bata wuri, ta samu ta cigaba da kukan, dan koma menene shi ne sila. Haka ta nuna wa Daddy kamar ta haƙura, bayan fitarsa kuwa ta cigaba da kukanta, tana yi tana tsinewa Amina saboda ita ta janyo musu wannan lamarin, da suna zaune cikin kwanciyar hankali amma duk tabi ta hargitsa musu gida. Yazid bayan ya koma gida daga gidan su Fadila ya ga kayan da Amina ta bashi yayi ta mamaki, saboda kai da gani ka san shaddojin manya ne, ga naira dubu ashirin a cikin envelope, har da turare mai kyan gaske. Mamaki ya dinga yi wacece Amina, saboda Fadila ta taɓa gaya masa Cewar su biyu ne kawai a gidansu ita da yayanta, kuma babu ta in da Amina ke kama da Fadila, balle ya ce ko ƙanwarta ce, haka dai yayi ta mamaki shikaɗai. Da daddare sai da ya kira Fadila, yaji ya ta wuni, amma wayar ta ƙi shiga sam haka ya haƙura. Washegari da Safe, Daddy ya karya, yana nan a gida, har wurin ƙarfe sha ɗaya na safe, sannan ya fito da niyyar ya fita. Sai dai yana fitowa ya tarar da Fadila na safa da marwa a falon, idnunta duk sun kumbura alamar bata samu isasshen bacci ba. Ya dube cikin nutsuwa ya ce "Fadila, meyasa baki tafi makaranta ba?" Cikin rauni ta ce masa "Mummy bata dawo ba" Alhaji Ahmad ya ce "Nace ki kwantar da hankalinki, duk in da ta tafi zata dawo, nima na kira wayarta bata shiga, amma ki kwantar da hankalinki, ki zo ki shirya ki tafi makaranta". Ta girgiza kai ta ce "Daddy ba zan iya zuwa ba" "Meyasa?" Kawai ta cigaba da share hawaye, ba tare da ta kuma cewa komai ba. "Shikenan, ki samu ki yi breakfast, Meenal tayi girki, ki samu ki ci, zan san abin yi in sha Allah" Meenal ɗin nan da Daddy ya ce, ba ƙaramin ƙular da ita yayi ba. Suna cikin maganar suka jiyo muryar Amina tana faɗin "Daddy kayi mantuwa fa, ka bar wallet ɗin ka" Fadila ta kalli Amina, ita kanta ji take kamar ta shaƙe Amina kowa ma ya huta. Amina ta ce "Muje na raka ka" Amina ta shige gaba ya bita a baya. Sai da suka je motarsa sannan ya tsaya ya kalli Amina ya ce "Meenal, na fara damuwa da lamarin nan fa, ban san ina Zainab ta tafi ba, duk ta saka mini yarinya a cikin damuwa". Amina ta ce "Nima kaina abin ya fara damuna, amma yakamta ace ko fushi take, zuwa yanzu a san in da ta tafi, ko dan saboda Fadilan" Daddy ya ce "Haka ne, amma kin san ita wasu lokutan bata duba abu ta nutsu kan ta yanke hukunci, ita in dai abu yayi mata shikenan, bana jin Yarinyar nan ta rintsa ko ta ci Abinci" Amina ta ɗna yi jimm sannan ta ce "Gaskiya bata kyauta ba, ni kaina Fadilan ta bani tausayi, yakamta kayi wani abu a kai" Daddy ya ce "Kika bibiya tana wurin ƙawayenta, amma dai zan bincika in sha Allah" "Alright, safe journey Sweetheart". "Thank you dear" yayi maganar tare da kissing ɗin goshinta, ya shiga motarsa yayi gaba. Tuni an canza wani maigadin gidan, Zakiru yana nan a direbansa da kula da harabar gidan. Hajara ma tana nan, da fari Hajiya Zainab ta so ta fatattaketa, amma sanin cewar idan ta fatattaketa babu mai kula da sashinsu, ita da Fadila da sauran ayyuka ya sanya ta barta. Amina ta dawo ta tarar da Fadila tana waya da Khalil tana gaya masa abin da ya faru, tana ta kuka. Sosai ta bawa Amina tausayi, amma ta san tana tankata zasu yi ba daɗi. Amina ta je Kitchen, ta sanya Hajara ta haɗowa Fadila Abinci, suka fito falo tare. Fadila kuwa waya take da Khalil tana. Faɗin "Yaya yakamata kayi wani abu a kai, ko ka kira Daddyn da kanka, dan naga kamar bai ɗau abin serious ba" Khalil ya ce "Ki kwantar da hankalinki, za muyi waya da Daddyn in Allah ya yarda ba wani wurin ta tafi ba" "To Allah ya sa, ka kira shi dan Allah" Amina ta kalli Hajara ta ce "Ajiye mata kayan Abincin" Hajara ta ajiye kwanukan. Amina ta kalli Fadila ta ce "Ga Abinci nan, babanki ya ce a baki dan haka na fita" Fadila ta ɗago ido ta ce "Dalla malama kwashe tarkacenki ki bar mini gabana, nace miki ina buƙatar abincinki ne?" "Idan ma ba kya buƙata a yanzu, a baya kin ci, kuma bana baki Abinci ne dan kin isa ba, duk dan na gyara fadata ne a wurin mahaifinki, ina fatan kin gane. Ni ba irinki bace ba zan wulaƙanta mahaifinki ba, ina biyayya ha umarninsa ne a matsayinsa na mijina, idan kin ga dama ki ci, idan kin so kuma ki watsar ke ta shafa" "Zaki ga ni ta shafa, sai kin bar mana gida tunda nan ɗin ba gida ubanki bane, ko yau ya ga dama zai iya korarki" Amina ta ce "Haka ne, Hajiya Zainab ma ba gidan nata tsohon bane, idan aka tashi korar ni da ita za a kora, gashi nan kan a koreta ma ta kori kanta" A zafafe Fadila ta miƙe ta nuna Amina da yatsa ta ce "Wallahi ki shiga hankalinki, ki fita daga sabgata" "Kuskure mafi girma da zaki sake tafkawa, shi ne nuna ni da yatsa, ki kiyayeni kar ki ƙara" Amina tayi maganar cikin kashedi. Hajiya Zainab kuwa, wayewar garin Allah da da sassafe suka shirya suka ɗau hanyar Nijar. Da ita da Hajiya Salma, da kuma Hajiya Turai, suna tafe suna gaya mata yadda aikin malamin yake kamar yankan wuƙa. Gaba ɗaya idon Hajiya Zainab ya rufe, ba abin da ke zuciyarta illa taga bayan Amina da Alhaji Ahmad, ta wulaƙanta Amina tayi yadda take so da Daddy, dan a yadda take ji a ranta bata ƙi a kashe Amina ta huta da baƙin ciki ba. Fadila na nan a ɗakinta zuciyarta a cunkushe, ji take ita ma tamkar ta bar gidan, saboda yadda zuciyarta ke mata babu daɗi, ga raɗaɗin miyagun maganganu da Amina ta gaggaya mata da suka sake haɗuwa suka dagula mata lissafi suka haifar mata da wani irin ciwon kai mai zafi. Tana kwance idanunta a lumshe, saboda zafi suke mata a dalilin kukan da tayi, tana jin yadda wayarta ke vibrating, ta buɗe idonta da ƙyar, ta ɗauko wayar tana zaton ko Mummy ce, amma taga wata lamba daban. Har zata share sai tayi tunanin idan kuma Mummyn ce ta kirata fa?. Da sauri ta ɗaga wayar ta saka a kunnenta. "Assalamu alaikum warahmatullah, Ukty" Jin muryar Yazid bata Mummy ba ya sanyta yin shiru. "Kina jina kuwa?" "Eh" ta faɗa a taƙaice. "Ina fatan kina lafiya?" "Lafiya lau" Ya ce "Ok, amma ya aka yi baki shigo school ba yau?" "Bana jin daɗin jikina ne, shiyasa" "Subhanallah, to Allah ya baki lafiya, kukan da kika yi ma zai iya saka ki rashin lafiya. Ki daina kukan nan haka" "To" Yazid ya ce "Yauwa ukty, sannan kiyi mini godiya Sister ɗinki ta bani kuɗi da kaya, da fari dai nace ba zan karɓa ba, amma ta matsa kiyi mata godiya dan Allah" Fadila cikin rashin fahimta ta ce "Wace sister tawa kuma? Ai ni bani da wata sister" Yazid ya ɗan yi Jimm sannan ya ce "Wata wadda ta fito bayan kin shiga gida, har ta karɓi car keys ɗinki a hannuna fa" Wani malolon takaici ne ya ƙule Fadila, bayan da ta gano Amina ce, yarinyar ta fiye rawar kai, da neman gindin zama. Fadila ta ce "Ok, na sha magani ne, zan ɗan kwanta" Ya ce "Alright, ba damuwa Allah ya baki lafiya" ko amsawa ba ta yi ba ta kashe wayar tana tsaki. Hajiya Zainab tare da su Turai ne a gaban wani mutum, yana zaune a kan wani buzu, yayi rawani sai wani kasko a gabansa da yake ta fidda hayaƙi, gefe kuma ga ƙasa a cikin wani abin katako. Ya dubi Hajiya Zainab bayan sun gama gaya masa abinda ke tafe da su. "Hajiya ai ba a zama haka, kin yi sake da yawa, da fari a tsaye kike amma daga baya kika ga kamar kin gama shanye shi ki ka miƙe ƙafa" Hajiya Zainab ta ce "Haka ne, amma yanzu meye abin yi?" Ya ɗan kalleta sanann ya ce "Babu damuwa kar ki damu, komai zai zo da sauƙi, zan yi miki wani aiki a nan, sannan zan baki wani ki tafi da shi. Ba wani abu ne mai wahala ba, zaki saka laya ne a hanyar da kika san Yarinyar zata taka ta wuce, da kanta zata bar gidan, sai turaren da zan baki, shima ki dinga turarawa zata ji kamar ana hura mata gida sai ta bar gidan ba zata iya zama da shi ba. Shi kuma zan baki maganin da zaki dafa shi da nama ki bashi ya ci komai zai zo ƙarshe. Sannan zan baki wani ruwa, zaki dinga ƙara ruwan rijiya a kai kina sha kina wanka, sai yadda ki ka yi da shi". Hajiya Zainab ta ce "Malam na gode sosai, nawa zan biya kuɗin aikin?" Ya ce "Ai ba damuwa, wanan ne zuwanki na farko ki bayar da duk abin da ya samu" Hajiya Zainab ta ɗauki kuɗi masu yawan gaske, ta ajiye masa, suma suka faɗi nasu buƙatun, ya basu magani suka tashi suka tafi. Sai a dawowa sannan Hajiya Amina taga uban surƙuƙin wurin da suka je, dare yayi musu a hanya, sai Hotel suka kama suka kwana. Khalil ya kira Daddy a waya, yana tambayarsa a kan ɓatan mahaifiyarsu, Daddy ya ce ya kwantar da hankalinsa, saɓani suka samu tayi zuciya ta fita amma ya san zata dawo. Gefw guda kuma Daddy ya cigaba da shirye-shiryen tafiyarsa da shi da Amina. Wasa-wasa tun Daddy yana basarwa, sai da aka kwana uku babu Hajiya Zainab babu dalilinta, gashi saura kwana biyu tafiyarsu, Fadila ko Abinci bata iya ci, balle ta je makaranta. A kwana na huɗu suna zazzaune a falo, Daddy na rarrashin Fadila, duk tayi wani iri saboda damuwa. Amina tayi juguum, dan abin ya dameta sosai saboda ita ce silar fitar Hajiya Zainab. Suna nan zaune, suka ga an buɗe ƙofa, Hajiya Zainab ce ta shigo, hankalinta kwance. Gaba ɗaya suka bita da kallo, Fadila kuwa ta tashi da gudu ta rungumeta tana faɗin "Mummy Ina kika tafi haka?" Alhaji Ahmad ya kalleta ya ce "Zainab daga ina kike tsawon wannan lokaci, ba tare da na san in da kika je ba?" "Au tambayata ma kake, baƙin cikin da na ƙunsa ne, na tafi naje na sha iska" "Kuma shi ne zaki kashe wayoyinki, kalli halin da kika saka Yarinyar nan" "Koma dai menene ai gani na dawo, dama na tafi ne dan na huce, kuma Alhamdilillah" tayi maganar tana danne fushinta, dan so take ta shawo kansa, har ta dafa naman nan ta bashi ya ci. Girgiza kai kawai yayi, baya son ya biye mata, su dinga zubarwa da juna mutunci a gaban 'yar su. Ta janye hannun Fadila zuwa ɗakinta, ta shiga rarrashinta. "Am sorry Baby, baƙin cikin babanki ne ya isheni naje na huta, kiyi haƙuri na tayar miki da hankali" Tayi ta rarrashin Fadilan, duk da Fadilan tayi mata mita saboda tashin hankalin da ta shiga. Sai da taga Fadila ta samu nutsuwa, sannan ta fara tunanin yadda za tayi da Alhaji Ahmad. Da yamma yana sashinsa tare da Meenal, Hajiya Zainab ta kira shi a waya. Yayi mamakin ganin wayarta. Ya ɗaga yana tunanin dalilin da ya sanya ta kirashi. "Hello Dear" Daddy ya ce "Yau kuma?" Ta ce "Eh mana, meye naga kamar kana mamaki?" "Ai abun ne dole ya bani mamaki, ni da aka ce ba a ƙaunar ganina" "Just forget please, kwana biyun nan na huce ai, i want my husband back" "Anya kuwa kece?" "Nice mana, ina son kazo kayi mini kwanaki na" Ya ce "Hmm, to shikenan tunda ke kika buƙata, dama ni ban wulaƙantar da ke ba, i will be with you" Tayi murmushi ta ce "Sai ka zo" Yayi murmushi ya katse wayar yana jinjina kai. Amina na jinsa, amma tayi kamar bata ji ba, ta cigaba da kallonta. Satar kallonta yake yaga wani action zata yi, amma tayi banza da shi. Ya san halin Amina a kan kishi, ya ɗan yi gyaran murya ya ce "Meenal" ta kalleshi ba tare da ta amsa ba. "Yau zan koma wurin yayarki" Ta ce "Wow, hakan yayi kyau shi ne adalci, Allah ya taimaka" ta mayar da hankalinta kan kallo. Tashi yayi daga in da yake a zaune, ya koma kusa da ita ya zauna, ya ce "Meenal" Ta waiwayo ta kalleshi, ƙoƙarin ɓoyewa take, amma tsagwaron kishi yake gani a idonta. "I know is not easy, but" ta ɗora yatsanta ta girgiza masa kai sannan ta ce "Mijinta ne fa na aura, me zai sa naji haushi kuma, ni dama ka je yanzu kwa fi sasantawa sosai, dan bana son yadda al'amuran gidan nan suke tafiya" ta miƙe tsaye ta ce "Zan je na cigaba da shirya kayana na tafiya, idan da wani abu you can let me know" daga haka ta wuce bedroom ta bar shi a wurin. Har ga Allah Daddy baya son zaman doya da manjar da yake da Hajiya Zainab, dan haka yaji daɗin sakkowar da tayi. Gefe guda kuma bai ji daɗin mood ɗin Amina ba, duk da tayi ƙoƙarin dannewa. Kai tsaye sashin Hajiya Zainab ya tashi ya tafi, ya tarar da ita kamar bai taɓa yi mata wani laifi ba, ta sha kwalliya tayi shar da ita, ta karɓse shi hannu bibbiyu tana ta nan nan da shi. Sosai suke hirar yaushe gamo shi da ita, yana yi mata nasiha da rarrashinta a kan abubuwan da suke faruwa. Sai ta nuna masa ita bata buƙatar wannan zancen. Da daddare yaje yiwa Amina sallama, saboda zai kwana a sashin Hajiya Zainab. Yayi knocking ɗin ƙofar bedroom ɗin, saboda ya ji ta a kulle. Amina ta zo ta buɗe masa, kamar kullum ta haɗe cikin sleeping dress ɗinta, tana ta ƙamshi. Sai dai fuskar nan babu walwalar. "Kin sallameni ne da kika rufe ƙofa?" Ta ce "Eh mana, me yayi saura kuma?" Yayi murmushi ya ce "Zuwa nayi na ganki" "Ka ganni ai, kaje ka kwanta kar ka kasa tashi da wuri gobe in Allah ya kaimu" tura ta yayi cikin ɗakin yabi bayanta, ya mayar da ƙofar ya rufe sannan ya rungumeta a jikinsa. A hankali ta bawa hawayen idonta damar zubowa, wanda take dannewa kar su fito. "I know what you feel my dear, but am sorry I know you are too young for this, a shekarunki kamata yayi ace ka kaɗai ce, amma kowane bawa da yadda Allah yake tsara masa rayuwa, kiyi haƙuri Babyna" "Bakomai Daddy, tunda ina sonka, zan so ka da rahamar Allah kayi mana adalci, at least naji sanyi a raina da kayi hugging ɗina, good night kaje kar ta kuma yin fushi" ya sa hannu ya share mata hawayen fuskarta ya ce "I love You sweet" "Love you more baby" tayi maganar tana murmushi. Kamar kar su rabu haka Daddy ya bar ɗakinta. Gaba ɗaya sai taga ɗakin ya mata girma, tayi 'yan koke kokenta, ta haƙura ta cigaba da tasbihi har tayi bacci. Daddy yayi mamakin tarairaya da rarrashi da ya gani a wurin Hajiya Zainab. Bai kawo komai a ransa ba sai ma farinciki na canzawa da tayi. Da gari ya waye da sassafe, Hajara tayi manakin ganin Hajiya Zainab a Kitchen, da duku-duku abin da bata taɓa gani ba kenan. Da kanta tayi girki ranar, taje ta shirya a dining, ta banka wannan turarrn tun daga sashinta har falo sannan ta koma sashinta. Amina kuwa gaba ɗaya kasa baccin safen ma tayi, bayan ta kammala tilawarta da adduointa sai ta fito falo. Wani irin ƙauri ne ya daki hancin Amina, wanda ya sanya mata wani irin sarawar kai, ta hau tari. Da ƙyar tarin ya tsagaita, taje ta bubbuɗe window, da ƙofa saboda ƙaurin ya fita, tana mamakin wane irin ƙauri ne haka. Mamaki ne yakamta da ta ga dining da Abinci, a ƙarfe bakwai. Ƙarasawa dining ɗin tayi, ta na bubbuɗe kwanukan. Wani haɗaɗɗen farfesun nama Amina ta gani, ɗan kaɗan a cikin flask, take taji ranta ya biya, taji idan ba ta ci naman nan ba, zata iya mutuwa ta hau haɗiye yawu. AYSHERCOOL 08081012143LITTAFINA NA KUƊI NE, ₦500 TA WANNAN ACCOUNT ƊIN 0009450228 AISHA ADAM JAIZ BANK KO KU DUBA AREWABOOKS. Har Amina zata rufe flask ɗin ta juya, ta kuma tsayawa tana kallon naman, sam bata kawo Hajiya Zainab ce ta dafa ba, ta zaci Hajara ce ta tashi ta kammala aiki da wuri ko akwai in da take son zuwa. Amina ta ɗauki spoon, ta ɗan ɗiba ta saka a bakinta. Ya ji spices sai ƙamshi yake, duk da akwai wani ɗan ɗaci da tayi zaton kawai bakinta ne. Amina ta sake ɗiba ta ci, taji yayi mata daɗi sosai da sosai. Jan kujera tayi ta zauna, ta dinga tsamar naman nan tana ci, kan kace meye wannan ta ci ya kai rabi. Hajiya Zainab kuwa sai lallaɓa Daddy take yi, tana yi masa kwarkwasar da sai zai bata kuɗi yake ganinta. Ta sha uwar kwalliya, sai ƙamshi take tayi masa jagora zuwa falo, sai hira take yi masa. Turus tayi lokacin da suka ƙaraso dining, taga Amina zaune da spoon a hannunta tana cin naman da ta tanada saboda Alhaji Ahmad. "Ke, wani irin wulaƙanci ne wannan da rainin hankali, na girka wa Mijina abun ki zo ki zauna kina ci?" Ɗan saroro Amina tayi sannan ta ce "Dan Allah kiyi haƙuri, wallahi ban zaci ke kika dafa masa ba, nayi zaton Hajara ce...... "Ko kuma uwar Hajara ba, saboda tsabar rashin mutunci ko Hajarar ce ta dafa ba kya bari a baki iznin ci ba, zaki zauna na yiwa mijina girki ki cinye" Amina ta ce "Ya salam, amma nace kiyi haƙuri ni wallahi ban san ke kika girka ba, saboda ban taɓa ganin kin yi ba, raina ne ya biya amma ba damuwa ai sai na girka masa wani". A cikin tsananin fushi Hajiya Zainab ta kalli Daddy ta ce "Wallahi tun wuri ka taka wa Yarinyar nan burki, wannan wane irin iskanci ne da rashin mutunci,? Yaya za ayi na dafa abu saboda kai ta zauna ta na ci, yanzu nayi magana ace na fiye kishi da neman rigima ita kuma wannan me tayi?" Daddy ya kalli Amina ya ce "Meenal, meyasa ki ka ci bayan kin san ba ke kika ajiye ba, kin san fa bana son neman magana" "Wallahi Daddy ban san naka ne ta ajiye maka ba, ji nayi ina son ci shiyasa" "Eh tunda gaki mayya ba, dangin mayu kinga nama idan baki ci ba mutuwa zaki yi". Amina ta ce "Ni ba mayya bace, danginmu kuma babu mayu, dan hak.... Ba ta ƙarasa ba Daddy ya ce "Ya isa haka, ki bata haƙuri kawai a wuce wurin" "Amma Daddy tunda kuka fito fa nake bata haƙuri, me kuma take so nace mata?" A ɗan hasale ya ce "Ki bata haƙuri nace, bana son gardama" Amina ta sunkuyar da kanta ta ce "Dan Allah kiyi haƙuri, ban san ke kika girka ba" Daɗi ne ya kama Hajiya Zainab, ganin yadda Daddy ya fara acting, ya sanya taji a ranta ai maganinta ya fara ciksa, dan ma bai ci wannan naman ba, in da Allah ya taimaketa akwai sauran maganin. Ta haɗe rai ta ce "Gaskiya dai ka sake ja mata kunne, kar ta sake yi mini irin haka, idan kuma ta kuma komai nayi mata ita ta saya" Daddy ya ce "Kiyi haƙuri, ba zata sake ba in Sha Allah, kuma in dai nine kar ki damu, na karya haka na gode sosai da kulawa" Amina kuwa miƙewa tayi, ranta babu daɗi garin ta bar wurin, ta kifar da sauran naman ya zube a ƙasa. Daddy ya kalleta ya ce "Ina zaki? Ba zaki zauna ki karya ba?" Hajiya Zainab ta ce "No, bana buƙatarta a nan, daga ni sai kai nake son muyi breakfast, ta samo dai abu ta gyara wannan abin da ta zubar" ko sauraransu Amina ba tayi ba, tai musu banza tayi tafiyarta. Ɗaki ta koma ta nemi wuri ta kwanta, taji yadda naman da taci yake taso mata, ga shi taji kamar tana ƙaurin hayaƙin nan da ta fito ta tarar ya turnuƙe falo. Guntun tsaki ta ja ta na juyi a kan gadonta, daga bisani wani irin bacci yayi awon gaba da ita. A cikin baccin nata ne, taji yadda cikinta yake murɗawa, ta farka ta tashi zaune, abu kamar wasa cikinta ya dinga murɗawa, ta dinga juyi a kan gadon nan, daga baya kuma sai amai. Tun tana iya tashi daga kan gadon ta tafi toilet, har ta nemi wuri ta zauna a toilet ɗin, ta dinga kwara aman nan ba ƙaƙƙautawa, duk ta fita hayyacinta kamar wadda tayi cholera. Babban abin da ya bata haushi bai wuce yadda Daddy ko ya leƙo yayi mata sallama kan ya fita ba, alhalin idan yana wurinta, sai ya je yaga Hajiya Zainab koda kuwa zata ci masa mutunci ne. Bayan fitar Daddy, Hajiya Zainab ta ɗau waya take bawa su Turai labarin abin da ya faru a group. Suka tayata murna saboda alamu ya nuna kamar maganin ya fara aiki, amma Hajiya Turai ta ce "A gaskiya naji haushin cin naman nan da wannan shegiyar 'yar tayi, Allah ya sa shi ne ajalinta" Salma ta ce "Amin dai, sai ki sake dafa masa wani, amma ki tabattar daga ke sai shi a ɗaki, ki bashi ya ci". "Haka za ayi, na fara na turaren nan ma, ni na naman na damu ya ci, kuma shi yafi son kifi fa a kan nama, saboda hawan jini" Turai ta ce "Haka nan zaki lallaɓa shi, sai yaci, mu dai fatanmu buƙatar mu ta biya" Ta ce "Haka ne, in Allah ya yarda zan duk mai yiwuwa, naga na bashi ya ci, sonake naga ya kori Yarinyar nan korar wulaƙanci a gidan nan" "Kar ki da mu, ke dai ki civaba6da gwada maganin" suka cigaba da zigata da baga shawarwarin yadda zata ɓullowa al'amuran. Khalil kuwa ya dage sai shiri yake, yana narka kuɗi a gininsa, kamar wanda zai auro 'yar wani gwamna ko sarki, sannan yana turawa Hajiya Maryam kuɗi domin yi masa sayayar kayan lefe. Sunata cigaba da tsara yadda biki zai kasance. Abdul ya ga yakamata ya sanar da Khalil batun soyayyarsa da Yusra, kar ya zo yaji a wani wurin yaji babu daɗi. Dan haka bayan sun gama hirar yadda abubuwa zasu kasance a bikin Khalil, sai Abdul ya fara sako masa nasa zancen ta hanyar cewa "Malam nima fa na kusa kai kuɗin Auren nan". Khalil ya ce "Are You serious?" "Da gaske nake maka" "Amma gayen nan baka da kirki, amma baka taɓa gaya mini ba, ko ka haɗani da ita mu gaisa ba" Abdul ya ce "Ai ba wata bace a nesa, ta gida ce" "Ok, wacece?" Abdul ya ɗan yi shiru sannan ya ce "Yusra ce, ƙawar Fadila". Khalil ya ce "Ohhh Allah, Allah mai yadda ya so, lallai zaka sha iyayi da rawar kai, ka rasa Fadila amma kusan halinsu ɗaya Allah ya baka wuyanka ɗauka" "Amin na gode da fatan alkhairi" "Ahh haba bakomai, amma gaskiya ku bari a fara nawa sai ayi naku" Abdul ya ce "Saboda wayo, to ban yadda ba" Gaba ɗaya Abdul bai yi zaton Khalil zai ɗau abin so simple haka ba, a zatonsa zai nuna bai ji daɗi ba, saboda a baya ƙanwarsa ya nuna yana so. Yazid kuwa ya kuma haɗuwa da Fadila a makaranta, sai dai fuskar nam babu yabo ba fallasa, da fara'arsa ya ƙarasa gareta yana mata murmushi. "Alhamdilillah, naji daɗi da ban ganki kina kuka ba, amma ya aka yi kwana biyu baki shigo school ba?" Yayi maganar yana ƙoƙarin zama, amma ta matsa gefe dan bata son yadda jikinta ke rawa da sun samu kusanci. Fasa zaman yayi ya ce "Ohhhh sorry, ina fatan yanzu kin watstsake?" Ta ɗan gyaɗa kai ta ce "Yes Alhamdilillah" "Tsarki ya tabatta ga Allah, mun gode masa bisa ni'inominsa da jarabbwowinsa. Kin san ita rayuwa sai ana yi ana taɓa ɗan Adam yake sake samun kusanci ga mahaliccinsa, kuka ba mafita bane ba sam, Addu'a da miƙa lamari ga Allah su ne mafita kin ji?" Kallonsa tayi amma bata amsa ba. "Ya kika yi shiru?" "Ina jinka ai" Ya ce "Alright, yauwa dan Allah ina sake godiya da alherin da aka yi minina gidanku" "Kaga bakomai kar ka damu kawai" ta katse shi. Bai sake cewa komai ba ya bar wurin, ita ji tayi ma gaba ɗaya ta tsani zaman ajin, dan haka ta tashi ta ɗau jakarta ta fice. Yusra ta kira a waya, Yusra ta sanar mata tana common room, dan haka ta wuce ta je ta tarar da ita a can. Ta je ta samu Yusra a can, tana zuwa ta zauna ba tare da ta ce mata komai ba. Yusra ta kalleta a nutse ta ce "Beb, meke faruwa ke ba a rasaki da damuwa menene?" Kaar za tayi kuka ta ce "Komai ma Yusra, gaba ɗaya gidanmu babu daɗi, wannan yarinyar ta ɓata mana jin daɗin rayuwa, ko kin san Mummy sai da ta bar gida kwana huɗu ba wanda ya san in da take" "Subhanallah, amma dai an ganta ko, ai ni baki gaya mini ba" "Ta dawo jiya, baƙin ciki da ɓacin ran da Daddy yake sakata ne ya ta tafi, ba wanda ya san ina taje sai jiya ta dawo, Yarinyar nan munafuka ce, last week tunda na zo school ɗin nan nake kuka, baki ji cin kashin da take yiwa Mummy ba, kuma Daddy yana goya mata baya, da aka tashi daga school yazid ya kaini gida, saboda munafurci ta bashi abu ni ban san me ta bashi ba yake ta ayi mata godiya, da ni na bashi ba lallai ya karɓa" Yusra ta ce "Au kun shirya da Yazid ɗin ne?" "Ke oho masa, ni ba shi ya dameni ba, Yaya Khalil fa ko a jikinsa abin da Daddy yayi wa Mummy, yama koma wurin ta ita da Daddy, duk yadda zan gaya miki ba zaki gane yadda gidanmu ya tarwatse ba" "No, ki daina faɗar haka, gidanku ba zai taɓa tarwatsewa ba, kuma komai zaa wuce da yardar Allah" Fadila ta ce "Allah ya sa, ni ji nake dama muna da wasu 'yan uwa da muke zuwa gidansu, da can zan koma ba zan iya jure wannan tashin hankalin ba" "Fadila Addu'a ita ce mafita a kan komai, dan haka ki miƙa lamuranki ga Allah, ki manta da komai" Fadila ta nemi wuri ta kwanta a cinyar Yusra, tana ganin Yusra ba zata gane halin da take ciki ba. Amina ba ƙaramin ƙulewa tayi ba da Daddy bai shigo ba, ta sha wahala sosai da ƙyar aman da take ya tsaya. Wajen azahar taji ana bubbuga ƙofar bedroom ɗinta, da ƙyar ta taso ta buɗe. Sai taga Hajara a tsaye. Hajara ta ce "Naga gaba ɗaya banga kin fito ba, shine nace bari na zo na duba ko lafiya". Amina ta ce "Wallahi Hajara bana jin daɗi ne, dan Allah ida da gasarar kunu, ki damo mini ki kawon in samu na sha" "Subhanallah, Allah ya sauwaƙe kina ɗaki baki fito ba shiyasa ba wanda ya sani, bari na kawo miki" Amina ta ce "Yauwa na gode" ta koma taje ta kwanta. Mintuna talatin da ɗoriya, sai ga Hajara ta dawo, ta kawowa Amina kunu, ta karɓa tayi mata godiya, ta zauna ta sha kunun sosai dan tana ji yunwa, amma bayan ta gama sha, tana tuna naman nam da ta ci, taji cikinta ya kuma hautsinawa taje ta amayar da shi. Amina ta ce "Na shiga uku ni Amina, anya wannan naman da arziƙi ne, naje na ciyo wa kaina masifa da kaina" Haka ta wuni tana malelekuwa, da kyar aman ya tsaya. Duk ta fita hayyacinta. Wajen ƙarfe shida da rabi, tana kwance bacci ya ɗauketa, taji ƙamshin turaren Daddy. Ta buɗe idonta a hankali ta ganshi zaune a kusa da ita yana shafa kanta. Kallo ɗaya tayi masa ta ture hannunsa, ta juya masa baya. "Meenal lafiya kuwa?" Amina ta ce "Ni ka ƙyaleni" Ya kwantar da murya ya ce "Haba 'yar babyna, nine fa Daddy ne" "Ba wata 'yar babynka, da ka mini wulaƙanci a gaban matarka, ka goya mata baya dan an dafa maka abu na ci, har da wani yi mini faɗa naman ma da naci ya kusa kasheni, kuma wai wunin yau ko ka leƙo ka ganni, bayan idan kana wurina ko zata maka wulaƙanci ita kana leƙawa ka ganta wuni nayi ina ciwon ciki amma banga ka zo in da nake ba" Cikin rarrashi ya ce "Haba Meenal, ya zan bata rashin gaskiya bayan kin san kin yi laifi, zata dinga ganin bana yi mata adalci. Wallahi ina ƙoƙari Amina idan na biyewa son zuciyata ba zan muku adalci ba, saboda na san ina miki son da ni kaina yake bani mamaki. Kuma naje mun yi maganar auren Fadila ne da iyayen wannan yaron, ban zaci zan daɗe haka ba, amma dan Allah kiyi haƙuri" banza tayi masa tana cigaba da zumɓura baki. "Babyna, ko in tsuguna ne? In dai hakan zai saki farinciki sai na durƙusa na baki haƙuri, dan Allah ki daina fushin nan wallahi ni kaina wunin yau babu daɗi nayi shi, nayi missing ɗinki abubuwane suka sha kaina dayawa, amma am sorry Dear" Ya ƙarasa maganar yana juyo da ita ta fuskance shi. Saboda tsabar shagwaɓa sai ta hau kuka har da hawaye, tana tura baki, Daddy kuwa ya lalace a wurin rarrashinta, yana share mata hawaye. Sai da ta ɗan samu nutsuwa sannan ya ce "Yauwa Meenalin Daddy, ko ke fa saura kuma ki yi mini murmushi zuciyata ta samu nutsuwa" Ta noƙe masa kafaɗa. "Please Baby" Ta ce "Ina da sharaɗi" "Wane sharaɗin ne?" "Gaskiya kar ka sake ka ci nama a kwanakin nan, ka san dai kana kan dokokin likita ko?" "In dai wannan ne, shikenan ba zan ci ba i promise, yi murmushin na gani" Murmushin tayi tana share sauran hawayen fuskarta. Murmushin shima yayi ya ce "To yanzu me zaki ci?" "Gasashen Kifi nake so, manyan nan mai miya" "To shikenan, amma taso muje ki ɗan tattaka, ko kya ji dadin jikin ki". Ta ce "Ni ba tattakawa zan yi ba, ban yi wanka ba, duk jikina ciwo yake mini saboda ciwon ciki" Daddy ya miƙe, ya cire babbar riga, ya saka Amina gaba zuwa toilet. Har mai shi ya shafa mata, ya taimaka mata ta sanya wasu kayan, ya kalleta ya ce "Ko muje Asibiti dai, naga jikinki yayi weak?" "Ai ya daina yi mini ciwon, ka sayo mini kifin kawai" "To shikenan, kwanta ki huta yanzu zan dawo" Ta ce "To a dawo lafiya" Ya jinjina mata kai ya fice, yan fita falo ya haɗu a Hajiya Zainab, ta kalleshi ta ce "Dama kana gidan nan tun ɗazu? Nifa bana son munafunci, amma dai ka san yau a wurina kake ko?" Alhaji Ahmad ya ce "Haba Zainab, dan ina wurinki shikenan ba zan leƙa in ga ya take ya ta kwana ba? Yarinyar nan tunda na fita ashe bata da lafiya, hakkinta a kaina yake dole naje naga jikinta" Cikin ɓacin rai ta ce "dole ko? Yayi maka kyau" ta wuce fuuuu ta bar shi a wurin. Da fari ji yayi kamar ya bita, da ya tuna Amina ko Abinci bata ci ba wunin yau, kawai sai ya fice ya tafi saya mata kifinta da ta nema. Hajiya Zainab iya ƙuluwa ta ƙulu, amma ta danne saboda ta sake dafa wani namn, so take ya ci. Amina kuma zaman ɗakin ne ya gundureta, ta ɗan ji daɗin jikinta, dan haka ta fito da niyyar zuwa kitchen, ta dafa tea idan Daddy ya kawo mata kifin, ta samu abin haɗawa. Sai dai kamar ɗazu da safe, yanzu ma falon warin wannan hayaƙin yake yi. Da sauri ta ƙarasa kitchen, saboda jin yadda tari ya fara taso mata. A gurguje ta dafa tea ɗin, ta koma ɗakinta tana tsaki, saboda ita bata ga amfanin wannan hayaƙin ba, bata san ta ina yake shigowa falon ba, dan sam bata yi zaton Hajiya Zainab ke kunna shi ba. Da magariba Daddy ya dawo da kifin Amina, ta dinga murna da ganin kifin nan, ya zauna ya sata a gaba ta ci sosai sannan ya ce "Alhamdilillah, tun da kin samu kin ci kifin sosai, Allah ya baki lafiya, gobe in Allah ya kaimu nake son muje mu yiwa 'yan uwa bangajiya, har Shanono nake son muke, jibi in Allah ya kaimu kuma, zamu je Dutse ta can zamu tashi". Murmushin fuskarta ne ya ƙaru cikin murna ta ce "Amma naji daɗi sosai, Allah ya kaimu da rai da lafiya" "Amin ya rabb, bari na tashi naje wurin Yayarki" Ta gyaɗa kai ta ce "Ok, shikenan kace ina gaisheta" "To zata ji" ya tashi ya tafi. Ta ji daɗin jikinta mussaman yanzu da ta samu ta ci wani abin ya zauna a cikinta. Tashi tayi ta duba littafinta da take rubutun Alqur'ani a ciki, ta sanya hijjabinta ta ɗau biro ta zauna, tana karantawa a hankali tana rubutawa. Ba dan Hajiya Zainab ta so ba, ta saki fuskarta, bayan Daddyn ya rarrasheta a kan Amina ce bata jin daɗi. Ta kawo masa abinci tare da wani farfesun naman, ya kalli naman ya ce "Naman nan a bar shi, zuba mini Abincin kawai" Ta kalleshi ta ce "Saboda me?" "Likita ya hanani cin jan nama, saboda shekaru da yanayin jikina" Ta ɗan rausayar da murya ta ce "Amma sai da ka bari na dafa zaka ce ba zaka ci ba, dan Allah ko kaɗan ka ci mana" ganin duk ta damu ta ɓata fuska, ya sanya ya ɗau fork ya ɗebo naman, murmushi yayi kan ya kai bakinsa, ya tuna da tare za su ci Abinci da Amina, zai fara cin Abinci ƙura masa ido za tayi sai taji yayi Bismillah, idan kuwa bai yi ba sa ta riƙe masa hannu tana haɗe rai kamar wani ɗanta. A hankali yayi Bismillah, ya kai yanka ɗaya bakinsa, sai ya tuna alƙawari yayi wa Amina ba zai ci ba, dan haka ya ce ya ishe shi. Kissar duniya da rarrashi ba wanda Hajiya Zainab ba tayi ba, amma ya ce ba zai ƙara ba ya ƙoshi. Ji tayi kamar ta tsinke shi da mari ta huta, amma ta shareshi. Abu ɗaya ne ya ɗan faranta mata rai, shine maganar da yayi mata na cewa iyayen Salim sun zo ya haɗu da su, sun ce zasu kawo kuɗin Aure da zarar ya dawo, shi kuma ya ce ya basu, sannan zai cigaba da saurarensu. Wannan maganar ce ta ɗan faranta mata rai, amma duk da haka ta shareshi, saboda rashin cin naman nan ba ƙaramin ƙuluwa tayi ba. Da daddare har sun kwanta, yake gaya mata cewar gobe in Allah ya kaimu zasu fita shi da Amina, jibi kuma za suje Dutse daga nan zasu bar ƙasar kwanaki goma ma kawa za suyi su dawo. Sai da Daddy ya gwammace bai yi nata zancen ba, saboda azabar bala'in da ta dinga yi masa a ka, tamkar zata dake shi. Ƙarshe sai juya mata baya yayi, tayi mai isarta ƙasan zuciyarta kuma tana Mamakin yadda aka yi maganin bai fara aiki yadda take so ba. Hajiya Zainab tana can tana bacci, Daddy ya lallaɓa ya tafi wurin Amina, dama ranar girkinta ne, yayi wanka ya shirya ko karyawa ba suyi ba, ya ɗauketa suka fice. Ɗaya gidan nasa suka tafi, ta haɗa musu breakfast, bayan sun kammala suka sake shiri a tsanake suka fita. Gidan Ammi suka fara zuwa, Ammi tayi murna da ganin Amina, ta yi ƙiba sosai ta ƙara kyau. Amina ta hau yiwa Ammi mitar, ita bata dawo ba, Azima ma bata je ba. Ammi ta ce "Ai bai kamata mu dinga yi miki zarya a wannan ƙadamin ba, ita ma nan suka shirya da 'yan ajinku da zasu je miki, nace kar suje tukuna kar wannan abokiyar zaman naki ta tsinkaki a gabansu" Amina ta ce "Ni da yake ma bata tata nake yi ba, idan tayi mini ba raga mata zan yi ba, kullum ni ba mai zuwa wurina, ita Azima ai da ko ita sai ta dinga zuwar mini". Azima ta ce "Ni rabani da zuwa gidan matar aure, ta koreni ta ce mini mijinta ya dawo" Bata wani jima ba, Daddy ya kirata ya ce ta zo suna da wurin zuwa sosai, haka tayi sallama da Ammi da Azima suka tafi. Daddy gidajen wasu daga abokansa na Kano, ya kai Amin suka gaggaisa da iyalansu, tare da yi musu bangajiyar zuwa walimar bikinsu. Amina tayi mamakin yadda Daddy yake da jama'a, amma babu mai iya takawa gidansa saboda masifar matarsa. Sai azahar suka ɗauki hanyar Shanono, Amina sai daɗi take ji, kamar yau zata fara zuwa garin. Inno da bata san da zuwansu ba, ta rasa ina zata ajiyesu dan daɗi, nan da nan aka yiwa Baba waya aka ce Amina ta zo, Baba ya rufe shago ya nufo gida cike da ɗokin son ganin tilon 'yar ta shi. Abin kunya sai ga su Baffa Bala, sun biyo sahun masu zuwa su gaida mijin Amina, kamar ba iyaye ba sai gasu suma. Sai a yau Amina taga sabon gidan da aka sayawa su Baba, manyan gidaje biyu ne aka saya aka haɗesu, aka ƙawata su, ga aiken kayan Abinci da Daddyn yake yi musu. Ba ƙaramin kima Daddyn ya daɗa a wurin Amina ba, ita a rayuwarta duk wanda yake son iyayenta to ya samu zuciyarta. Aikuwa duk wanda ya zo akwai alherin da Daddy zai yi masa, Amina ta sake sosai a gida tare da Inno da Baba, suka yi ta hirar yaushe gamo. Bayan sallar la'asar suka nufo cikin garin Kano. Hajiya Zainab kuwa bayan ta farka ta nemi Alhaji Ahmad ta rasa, ta kira wayarsa ya sanar mata yayi sammako sun fita da Amina. Haka ta dinga zage-zage ita kaɗai a gida, ta zari mayafi ta tafi gidan Hajiya Turai, suka sake tattaunawa a kan batun magungunan wurin malamin, aka tambayeshi ko za a iya amfani da maganin a kifi, ya ce musu a'a lallai a Nama ake so. Har ta dawo da yamma su Amina basu dawo ba, ta zauna a falo ta kasa tsare tana jiran taga ta ina zasu shigo. Aikuwa tana nan zaune, sai gashi sun dawo, Daddy na riƙe da jakar Amina, Zakiru kuma ya shigo da kayan tsaraba, da suka zo da su daga ƙauye. Ba kunya ba mutunci haka Hajiya Zainab ta cigaba da tsigale masa a gaban kowa. Amina tafiyarta tayi ta bar su, dan ta lura ita dai Hajiya Zainab idan har za a biye mata kullum sai an yi tashin hankali da ita. Amina bata san yadda suka ƙare ba, dan tana zuwa sashen ta rage kayan jikinta tayi, ta shiga tayi wanka tayi alwala ta zo ta tada salla. Bayan ta idar Daddy ya shigo, sai dai yanayinsa ya nuna mata yana cikin damuwa, kuma ta san Hajiya Zainab ce ta kunno shi. Ya zauna yayi shiru ya rasa abin da yake masa daɗi, Amina ta ninke abin sallar, ta je ta zauna a kusa da shi, ta rungumo kansa jikinta, tana ɗan shafa bayansa cikin sigar rarrashi ta fara magana "Sweetheart, ni da yaranka da duk masoyanka muna buƙatar ranka da lafiyarka, dan Allah kar ka cutar mana da kanka, saboda wata damuwa da zaka iya ajyeta a gefe muyi rayuwarmu. Damuwarka na jefa ni cikin damuwa nima duk sai na rasa meyake mini daɗi, kayi haƙuri ka ji?" Da fari ji yake kamar zuciyarsa zata tsaga ƙirjinsa ta faso, amma kalaman Amina suka dinga kwantar masa da hankali, sai da taga ya ɗan nutsu, sannan ta ƙyaleshi yaje yayi salla, ya nemi wuri ya kwanta. Washegari yayi shahada ya je wurin Hajiya Zainab yi mata sallama saboda doguwar tafiya da za suyi, tana fara zage zagenta, ya fice ya tafi ya barta. Ko da suka Dutse, danginsa tamkar zasu goya Amina, Amina gata da saurin sabo, ga ungo uban kayan zaƙi na gararta da aka kai musu kawai sai santi suke. Wasun su har suna ita wannan da ake gani ga karkara ce har da abin arziƙi na gara, uwar mulki kuwa ko barbaɗen gishiri ba ai kai mata ba. Amina ta yadda Alhaji Ahmad ɗan gata ne, kuma ɗan dangi gaba da baya, amma saboda tsabar son zuciya na Hajiya Zainab ta sa ya watsar da kowa sai ita. A family house ɗin su Daddy suka kwana, ya ɗauko mata hotuna yana nuna mata hotunan iyayensaa da 'yan uwansa da ya rasa, sai da ya zub da hawaye, saboda iyaye wasu duraku ne masu girman gaske a rayuwar kowane ɗan Adam. Washegari da Azahar, aka kai su Alhaji Ahmad airport, inda jirginsu ya ɗaga zuwa Dubai. Alhaji Ahmad ya samu isashshen lokacin hutawa, da nuna wa 'yar babyn amaryarsa kulawa da soyayya sosai da sosai, ya ɗan samu releif daga yawan hayaniya da tashin hankali da yake fuskanta na Hajiya Zainab. Amina lallaɓa abinta take, ta mayar da shi kamar yaro dai-dai da shekarunta. Ya dinga yawo da ita wuraren shaƙatawa daban daban yana kashe mata kuɗi. Hajiya Zainab saboda azabar baƙin ciki da kishi, gaba ɗaya ta manta bata gayawa Fadila batun maganar aurenta ba, sai ma shirin sake komawa nijar da suke yi a karo na biyu, dan yin wani asirin tunda wannan bai yiwu ba. Sai da taje tana yiwa Fadila sallama, tana sanar mata in da zata tafi ne, Fadila ta ce "Mummy, me kuma zaki je yi a nijar? Muda bamu da kowa a can?" Mummy ta ce "Sirikarki zamu raka, zamu je harkar wani business ne" Cikin mamaki Fadila ta ce "Sirikata kuma? Wacece sirikata?" Mummy tayi murmushi ta ce "Hajiya Salma mana, ni mana manta ban gaya miki ba fa, iyayen Salim sun zo sun yi magana da babanki, ya ce ya basu kuɗi kawai zasu kawo a saka rana". Saroro Fadila tayi tana kallon Hajiya Zainab, ta ce "Mummy yaya za a ba dani ga mutumin da duk abin nan da ake yi ko ganinsa ban taɓa yi ba" Mummy ta dafa kafaɗar Amina ta ce "kar ki damu, an tura masa lambarki, za kuyi magana, ai na san ba zaki bani kunya ba, shi ya ce kin masa ai, bari in tafi kar suyi ta jirana, idan na samu dawowa a yau shikenan, idan ban samu ba, sai dai mun yi waya" ta ɗau jakarta ta nufi hanyar fita, ta bar Fadla da wani yanayi da ta kasa gane kanta, takaici ne ko mamaki. Amina tana cikin bacci, tayi mafarkin wata baƙar mage, ta biyota, tana ta gudu tana kiran sunan Allah, amma duk da haka magen tayi tsalle ta kafa haƙoranta a cikin Amina. "Innalillahi wa innalillahi raji'un, Daddy ka taimakeni" Daddy da yake banɗaki yana wanka, kansa yayi wata irin sarawa, sai da ya dafa bango, da ƙyar ya iya lalubar towel ya ɗaura ya fito. A gigice ya ƙarasa gadon da Amina take, wanda gaba ɗaya ya wanke da jini, ga jikinta sai rawa yake, kan ya ƙarasa in da take yaji jiri yana neman kayar da shi. WANDA KUKE FITAR MINI DA BOOK, NA GODE SOSAI 🙏 ALLAH YA NA KALLONMU DUKA, DAN BA MUYI HAKA DA KU BA. AYSHERCOOL 08081012143NA KUƊI NE ₦500 VIA 0009450228 AISHA ADAM JAIZ BANK SAI EVIDENCE OF PAYMENT TA 08081012143 68 Dafe kai Daddy yayi, ya ɗan jingina da bango, yana kallon Amina, yana kallon yadda jikinta ke ta karkarwa, 'yar rigar baccin jikinta, duk ta ɓaci da jini, farin bedsheet ɗin da ke kan gadon shima yayi kaca kaca da jinin. Da ƙyar Daddy ya ja jikinsa, kansa na cigaba da sarawa. A hankali ya furta "Meenal" Yayi maganar yana ƙarasawa in da take kwance. Ƙanƙame shi tayi tana kuna, jikinta na cigaba da rawa. "Meenal meyasameki haka?" "Daddy tsoro nake ji" "Tsoron me?" Muryarta na rawa ta ce "Wata mage ce take cizona" Bai damu da yadda ta ɓata shi da jini ba, ya sake ƙanƙameta ya ce "Meenal ba wata mage a wurin nan" "Kayi mini Addu'a, zafi nake ji sosai" Ya jinajina mata kai, amma ya kasa furta komai da sunan Addu'a, sai kansa da yake ta juayawa, yaga komai na juya masa, suka sake ƙanƙame juna, ji take kamar numfashin ta zai ɗauke, mararta kamr zata haifi dutse haka take jinta. Amina ce tayi ƙarfin halin fara karanta Adduoi a zuciyarta, a hankali kuma ta fara furtawa a kan harshenta. Sun daɗe a haka, kan daga bisani su ji su tamkar wanda suka farka daga barci. Jin kan ya ɗan lafa masa ya sanya ya ɗan ɗaga Amina daga jikinsa, idanunta duk sun yi wani iri saboda kukan da tayi. "Ya jikin naki?" Tayi ajiyar zuciya ta ce "Da sauƙi" "Bari in taimaka miki ki gyara, sai mu tafi Asibiti" Daddy har tausayi ya bata, saboda yadda shi ma yake fama da kansa, amma sai kaiwa yake yana komowa, da kansa ya wanketa tsaf, ya gyara bedroom ɗin. Duk da jikinsa babu daɗi, haka ya saka Amina a gaba suka tafi Asibiti, Daddy yayi mamaki da aka gwada sigansa da jininsa duk lafiya lau, duk sauran teses ma da aka yi masa komai ya nuna lafiya lau. Sai dai babban abin da ya tayar masa da hankali, bai wuce yadda aka sake tabattar masa da cewar Amina ta sake samun ɓarin juna biyu ba. Shi baya sanin da cikin sai dai yaji ɓari, ji yayi kamar yayi kuka, saboda yana daga abin da yake buri shi ne samun yara. Ɗakin da take kwance ya shiga, ya tarar da ita da drip a hannunta, ta ƙurawa wuri ɗaya ido. Sallamarsa ce ta dawo da ita daga tunanin da take yi. Ya ƙarasa ya zauna a kusa da ita, ya riƙo hannunta a cikin nasa ya ce "Sannu Meenal" "Yauwa Daddy, ya jikin naka? Ina fatan ba wata matsala?" Ya jinjina mata kai ya ce "Eh, sun duba komai normal, amma sun gaya miki meyafaru da ke?" "Eh sun gaya mini, wai na kuma samun abortion ko?" Cikin tausayawa ya ce "Eh haka ne, amma kiyi haƙuri ki kwantar da hankalinki" Ta yi murmushin ƙarfin hali ta ce "Daddy, ai bakomai Allahn da ya bani shi ya karɓa, duk na san ina son na haifi abin da ke cikin, amma Allah ya san dalilin da ya sa suke zubewa" "Haka ne Meenal, amma Meyasa baki gaya mini kina da juna biyu ba?" Ta ɗan gyara kwanciyarta ta ce "Nima ban san akwai ba, tunda nayi wancan ɓarin, ban sake period ba, ban san ina da wani cikin ba" Ya shafa kanta ya ce "Shikenan, Allah ya bamu mai amfani, ina ga zamu ɗan ƙara kwanaki kan mu koma Nigeria, sannan ina son idan mun koma muje kiga ƙwararen likitan mata" "Amma meyasa zamu ƙara zama a nan, kaga a gida baka gaya mata ba" "Amina, bana son damuwa ne, na shafe shekaru ina karatu, neman kuɗi, kula da iyali da suaran hidindumu ina buƙatar hutu ƙwarai da gaske, yanzu muna komawa gidan, ba zata sauya zani ba, zata cigaba da tayar mini da hankali ne kawa, dan haka ki barmu mu huta sosai ma koma, kinga kya ga likitan matan ma a nan kawai" Haka Amina ta haƙura ta ƙyaleshi. Duk gwaje-gwaje da yakamata an yiwa Amina, babu wata matsala da ta nuna cewar ita ke haddasa mata ɓari, a ka sallameta aka bata magunguna suka koma gida. Ita kanta Amina tayi mamakin yadda aka yi hakantake faruwa, cikin farko dai ta san faɗuwar da tayi ne, na biyun nan kuma daga wannan mafarki ta tashi ta ganta cikin jini. 'ko dai aljanu ne zasu shafeni, dan amce suna saka mutum ɓari?' tayi wa kanta tambayar a zuciyarta. Da sauri ta kawar da tunanin ta bawa kanta amsa da ai tana azkar, dan haka babu abin da zai sameta sai abin da Allah ya ƙaddara mata. Kwanaki biyu a tsakani suka ware, suka cigaba da shan soyayya ita da Daddy, ta mayar da shi tamkar ƙaramin yaro daidai ita, yayi ta biyewa shirirtarta, yawo kuwa wuri wuri hake suk tafiya, wataran suyi tseren keke, da makamantansu wanda hakan ya ke ƙara musu kusanci da kuma ƙaunar junansu. A gida kuwa Hajiya Zainab taje ta kuma karɓo wasu asirin, gaba ɗaya hankalinta baya kan Khalil yanzu burinta shine ta wargaza auren Daddy. Sai dai ta jefa Fadila ma a cikin cakwakiya, dan tunda tayi mata zancen za a kawo kuɗin aurenta da mutumin da bata sani ba, ga shiga tashin hankali, dan sam bata jin ƙaunar abin a ranta. Kamar yadda Mummy ta gaya mata, sun bawa Salim lambar wayarta, dan har ma yayi mata magana ta what's app, amma yaƙi tura mata hotonsa, gaba ɗaya sam a tsarin yanayin kalamansa ma bata ji yayi mata ba, hakan ba ƙaramin jefata yayi a damuwa ba. Mummy ta sakata a gaba, tana ta tsara mata yadda zata shiryawa bikinta, domin daga shi ta san ba zata kuma aurar da ɗa ba, amma taga gaba ɗaya Fadilan ta ɓata rai. "Fadila, wai meyake damunki ne?" Kamar ta taɓo wa Fadila in da yake mata ƙaiƙayi ta ce "Ni wallahi Mummy bana son auren nan, dan Allah ki barni in cigaba da karatuna kawai" Mummy ta ce "Haba Fadila, so kike na mutu banga jikokina ba, meye aibun kiyi auren yanzu ki cigaba da karatun naki a gidansa?" "Ni Mummy auren ne bana so, dan Allah kawai a bar maganar nan" "To yanzu Fadila so kike naje na samu Hajiya Salma nace mata ba kya son auren, bayan an riga anyi magana? Ki duba kiga abin da babanki da yayanki suka yi mini, kema watsa mini ƙasa a ido zaki yi kenan? Duk cikinku babu wanda zan raɓa naji daɗi, hankalina ya kwanata kenan?" Ganin yadda gaba ɗaya mood ɗin Mummy ya sauya ne, ya sanya Fadila a sanyaye ta ce 'Mumny kiyi haƙuri dan Allah, ba haka bane ba, shikenan naji na haƙura zan aure shi in dai zaki ji daɗi". "Yauwa 'yar autata, ai na san ke ba zaki bani kunya ba, ba zaki zuba mini ƙasa a ido ba, Allah yayi miki albarka, shi kuma ɗan uwanki shi ma ina nan ina faɗi tashi, dan ba za ayi auren nan ba" Fadila dai bata sake iya cewa komai ba, ta tashi ta koma ɗakinta, ji tayi kamar ta saka hannu a ka ta kurma ihu, saboda amsawa Mummyn da tayi zata auri Salim, alhalin har ga Allah ita bai yi mata ba sam. Gaba ɗaya yanayin da take ciki ya nemi ya shafi karatunta, sam bata mayar da hankali, ɗan karatun da take ƙoƙarin yi ma ta kasa, da ta fara sai tunani, Yazid yana ankare da ita, sai dai baya son yawan shiga sabgarta tana yarfa shi, amma kowa ya kallta ya san akwai damuwa a tare da ita. Ɓangaren Maman Hafsa kuwa, tana ɗan shirninta, da ba a rasa ba, duk da an ɗauke musu kayan ɗaki, amma hankalinta ya kasa kwanciya, saboda bata ajiye ba, ba kuma ta bawa wani ajiya ba. Dama ta san dangin mahaifin Hafsa babu uwar da zasu tsinana musu, mutanen da suka ƙi karɓar kuɗin aurenta, suka dinga ɓata ta a wurin sirikinta, yaushe za a sanya ran zasu yi musu wani abu. Ga unguwa ta ɗauka, wai Liman ne ya karɓi kuɗin auren Hafsa, sa ƙanan maganganu suke yi, wai anya ma kuwa tana da uba, 'yar halak ce, dan idan da dagaske mahaifinta rasuwa yayi, ba za a rasa danginsa da zasu karɓi kuɗin Aurenta ba. Wasu abubuwan ma dai, Hafsan ce take kwantarwa da Maman hankali a kan wasu abubuwan. Khalil kuwa ya zage sai faman ƙoƙarin hattama gininsa yake da kayan lefe, dama gini ne ya ɗauko shi na manya, dan haka sai fama yake yi, 'yan uwan Daddy da abokanansa sai bashi gudunmuwa suke yi. Shi da Abdul suke tsara komai, kayan lefe dama Hajiya Maryam yake turawa kuɗin tana saya wa Hafsa, idan ya tambayeta me take so ayi mata a gidanta, ko na lefe sai ta ce masa ita komai ya sakamata ta gode, juyin duniya Hafsa ba zata taɓa ce masa ga abin da take so ba. Akwai abubuwa da yake buƙatar shawarar Hajiya Zainab, amma ba halin ya tuntuɓeta, ko kiranta a waya baya iya yi, saboda yana tsoron abin da ka iya haifarwa. Aikuwa hakan ba ƙaramin ƙona mata rai yayi ba, ga Daddy da ya ce zai yi kwana goma ya shuɗa, ko nemanta a waya baya yi, shima Khalil ɗin haka. Da kanta ta kira Khalil a waya, yana ganin wayarta ya shiga cikin tashin hankali, dan bai san dalilin kiran ba. Aikuwa kamar ya sani, dan yana ɗagawa ta dira masa bala'i. "Khalil ka zama ɗan kanka ko? Gaba ɗaya ka mayar da ni a bar banza, bani da wata kima a idonka, bani da mutunci saboda ubanka ya goya maka baya ka auri 'yar matsiyata, to duk abin da kake ka ajiye ka dawo gida ina son ganin ka" A ɗan rikice  Khalil ya ce "Mummy, aiki yayi yawa a nan, sai na nemi excuse tukuna" "Ba ruwana da wani excuse, kai ta shafa, ka dawo mini gida, ina son ganinka" Jiki a sanyaye ya ce "To shikenan, zan dawo in sha Allah" Tayi tsaki ta kashe wayarta. Alhaji Ahmad dai sai da ya shafe sati uku shi da Amina, daga kwana goma, sannan suka yi shirin dawowa Nigeria, tunda suka fara shirin tahowa Nigeria, Daddy ya shiga cikin damuwa, saboda ya san da sun dawo zai cigaba da fuskantar tashin hankali daga Hajiya Zainab. Amina ta lura da yanayin da Alhaji Ahmad yake ciki, kuma ta san bai wuce a kan Hajiya Zainab bane ba, ba ta fiye son yi masa shishshigi a kan abinda ya shafe shi da Hajiya Zainab ba. Haka suka gama shirinsu, suka koma Nigeria. Ko da suka sauka, gidan babu kowa, Fadila tana makaranta, Hajiya Zainab ta tafi nata gantali. Hajara ce ta tari su Amina, cikin murna da sakin fuska, nan da nan ta shiga Kitchen, ta fara ƙoƙarin dafa musu Abinci. Amina ta fito falo, ba laifi ko ina a gyare, Hajara tana ƙoƙarin kulawa da komai. Daddy kwanciya yayi a sashin Amina yana bacci, dan ya samu ya ɗan huta. Tun wajen sha biyu na rana suka dawo, Zakiru ya ɗauko su a airport, amma har biyar Hajiya Zainab bata dawo ba. Daddy ya shirya zai ɗan fita, Amina na falo, tana ɗan cin abinci, hakan yayi daidai da shigowar Fadila falon daga makaranta. Tana ganin Amina a zaune a falo, ta kalli Amina, ta ja wani uban tsaki, da ba tayi ma tsammanin ganin Aminan ba, dan basu san da daowarsu yau ba. "Ke Fadila" taji Muryar Daddy ya kira sunanta. Tsayawa tayi cak ta waiwayo, Daddy ya kalleta ya ce "Wa kike yiwa tsaki?" Fadila tayi shiru ba tace komai ba. "Da ke nake wa kike yiwa tsaki?" Yayi maganar a kausashe. Ta ɗan razana ta ce "Daddy ba kowa" "Ai naga abin da kika yi, me tayi miki? Kawai kin shigo kin tarar da ita a zaune, ke baki mata sannu da zuwa ba kawai kin yi mata tsaki. Fadila ki kiyayeni fa, idan kika wulaƙanta Amina tamkar ni kika wulaƙanta, tunda ni na aureta na ajiyeta, ba ita ta ajiye kanta ba, dan haka ki kiyayeni, bata haƙuri" wani abu ne ya soki ƙirjin Fadila, wannan 'yar yarinyar ƙanwar ƙanwar bayanta za a kalla ace ta bata haƙuri?. "Ba magana nake miki ba?" "Kiyi haƙuri" Fadila ta faɗa a taƙaice. "Allah ya ƙara nuna mini kin mata tsaki ko makamancin haka, idan ba zaki mutunta ba to ban lamunci ki shiga sabgarta ba, balle ki ci mata mutunci, na sani mahaifiyarki ke zigaki, amma idan na tattara na aurar da ke, na yiwa tufkar hanci, da sun kawo kuɗin Aure ni ba zan saka lokaci mai tsawo ba, na gaji da halinku" Kasa ɗaga ƙafafuwanta Fadila tayi, jin yayi batun aurar da ita, ga kuma furucinsa na ƙarshe, wai ya gaji da halinsu, duk tarin soyayya da tattali na Daddy a garesu, yau a saboda yayi aure yake musu wannan cin kashin. Da ƙyar ta ja ƙafarta, ta nufi sashinta tuni hawaye ya wanke mata fuska. Amina kuwa cewa tayi, Baby a dawo lafiya. "Yauwa Meenal, Allah ya sa" Bayan fitar Daddy, ita ma sallar tayi, ta dawo ta ɗan kunna turaren wuta a falon. Kamar daga sama sai ga Hajiya Zainab, kamar an korota, Amina ta ɗago kai ta kalli Hajiya Zainab, ta ɗauke kanta ta cigaba da ƙoƙarin kunna Tv. "Baƙar munafuka, na kusa kawo ƙarshenki" Mamaki ne ya kama Amin, ba ko sallama kawai ta fara maganar zata kawo ƙarshenta" "Ni bani da lokacinki, an barwa karnuka faɗa" Amina tayi maganar a hankali, tana cigaba da aikinta. "Ni kike cewa karya?" Ta miƙa hannu zata janyo Amina, Amina tayi maza ta kauce ta ce "Karki kuskura ki kai hannunki jikina, ba ruwanki da ni, ba fa tsoronki nake ji ba da nake yi miki shiru, wallahi kika dakeni sai na rama" "Bari na dakekin, naga uban abin da zaki iya, 'yar matsiyata wadda basu gaji arziƙi ba" Amina ta ce "Daɗinta dai mai faskare bai isa ya nunawa maigadi arziƙi ba, idan har maigadi matsiyaci ne ban san me za a kira mai faskare ba" Kan Amina ta kuma yi a fusace, zata daketa Amina ta kuma sake ja da baya, sai surfa uwar ashariya take kamar bamagujiya. Fadila ce ta fito, bata san Mummy ta dawo ba, sai ganinta tayi a falo tana zage zage tayi kan Amina. Da sauri ta ƙarasa in da Mummy take ta riƙeta, tana faɗin "Mummy dan Allah ki bari" "Ƙyaleni, ki rabu da ni in ci ubanta, ni zata kalla ta zagi ubana?" "A'a fa, ni ban zageki ba, ba faskaren ne sana'ar babanki ba?" Cikin tsawa Fadila ta ce "Ke Amina, karki kuskura ki zagar mini uwa, ki shiga hankalinki" Amina ta ce "Babarki zaki gayawa ta iya kanta, kar ta kuma zagina, sannan ke kuma karki sake ɗaga mini murya" Hajiya Zainab ta sake ƙuluwa, tana miƙa hannu zata daki Amina. "Kai! Meye haka Zainab a gidana? Me kike yi haka?" Waiwayowa tayi ta kalli in da Daddy ya ke ta ce "Sannu shugaban munafukai, dole kace haka mana, ka ɗauki yarinya kaje ka shafe kusan wata guda, ko ta kanmu baka bi, wallahi idan baka ji tsoron Allah ba sai ka wulaƙanta". "A gaban 'yata kike ce mini munafuki ko? Yanzu abin da kike koya mata ita ma taje tayi nata gidan mijin kenan? Ke idan bance kiji tsoron Allah ni kya gaya mini haka? Kin haɗu ke da 'yarki zaku daki 'yar mutane saboda kawai ina aurenta, shikenan na san matakin da zan ɗauka" Ya ture Hajiya Zainab ya janyo Amina, ya ce "Ina fatan ba abin da suka yi miki?" Amina ta ɗaga masa kai alamar eh, ya janyeta suka bar falon. Hajiya Zainab ta nemi wuri ta zauna, ta dafe kanta, gaba ɗaya tayi mamakin yadda gaba daya Asirin da take bai yi aiki ba. A ɗaki kuwa Daddy, rarrashin Amina yake yi "Meenal kinga dalilin da ya sanya nace miki na raba muku gida kenan, ban san me Yasa Zainab ta kasa haƙuri ta karɓi ƙaddara ba" "Daddy, bana son ka ware mini gida, ka gaza yi mini adalci, yanzu na san da anyi wa Fadila aure maybe a samu sassauci a wasu abubuwan" Ya ce "Haka ne, zan san abin yi. Gobe in Allah ya kaimu kuma zan je gidan sirikan Khalil ni da Alhaji Iliyas, mubi shawararki ya ganta idan tayi masa" Amina ta ce "Allah ya daidaita su" Ya amsa da Amin. Daddare duk da yana cikin zullumin tunani, a kan karɓar da Hajiya Zainab zata yi masa, haka ya tunkari sashenta. Sai dai sam bata kula shi ba, balle ta saurareshi, yana zaune a falonta yana duba wayarsa, ta shige bedroom ɗinta, ta saka key ta bar shi ya kwana a falo. Tun da suka dawo Hajiya Zainab ta saka su a gaba, da tashin hankali da rashin mutunci. Da Sassafe ko Amina bai yiwa sallama ba, ya shirya ya bar gidan. Ɗaya gidan nasa yaje ya samu ya ɗan huta. Shi da Alhaji Ilyasu suka je gidan su Hafsa, domin magana a kan shirin bikin su Khalil, suka je a kan su faɗi zaɓin da suke na furnitures, Maman Hafsa ta ce ba su da wani zaɓi, komai aka yi musu sun gode. Kasancewar da biyu suka je, Alhaji Ilyasu yaga maman Hafsa tayi masa, gata nutsatsiya ba zaka ce ma ta haifi Hafsa ba. Alhaji Ahmad ya ce wa Maman Hafsa karta damu kanta a kan shirin bikin nan, zasu ɗauke komai za ayi, karta damu. Mama tayi ta musu godiya, tare da yi musu Adduoi su da magabatansu. A hanya Alhaji Ilyas, ya dinga yaba Maman Hafsa, yana cewa Daddy shi dai tayi masa yana sonta. Daddy ya ce masa "To ni dai tunda na kaika ka ganta, sai ka yiwa kanka sauran aikin" Alhaji Ilyas yayi masa godiya, sannan Daddy ya tafi gida. Dama Daddy ko karyawa bai yi ba, ko zuwa gidan baya son yi, dan ya fara deciding ya koma Lagos, ya huta da tijarar Zainab. Kasancewar a wurinta yake, ba shi da wani zaɓi da ya wuce ya fara zuwa wurin nata, idan ta ga dama ta bashi abinci, idan kuma ta hana shi, ya je ya ci a wurin Amina. A falonta ya tarar da Khalil a zaune a gaban Hajiya Zainab, tana ta zuba masa faɗa ko haɗiyar yawu bata yi. Alhaji Ahmad ya kalli Khalil ya ce "Kai meya dawo da kai?" Khalil da idanunsa suka yi ja, ya ɗaga kai ya kalli Daddy ya ce "Mummy ce ta ce tana son ganina". "Tashi ka je" ya kalli Hajiya Zainab da ta tsare shi da ido. Daddy ya ce "Ka tashi ina yi maka magana" Khalil ya tashi, yana yi yana kallon Hajiya Zainab ya fice daga falon. Hajiya Zainab ta ce "Wallahi duk masifarka, ɗa dai nawa ne, kuma baka isa ka aura masa yarinyar matsiyata ba wadda bana so ba" Alhaji Ahmad ya gazgata maganar Amina, na ya yiwa iyalinsa illa da ya bar ragamar gidansa a hajiya Zainab, bai taɓa tunanin fuskantar irin wannan zazzafar ƙiyayya daga gareta ba. A haka ya lallaɓa yai kwanakinsa biyu a ɗakinta, sai dai a falo yake kwana, dan kulle bedroom ɗin ta take ta bar shi a falo. Komawarsa wurin Amina ne, ya samu sauƙi dan tana ɗaukar lokaci da shi, tana rarrashinsa tana tattalinsa da kwantar masa da hankali. Dama can Hajiya Zainab ba tambayarsa take ba, idan zata fita amma yanzu abin nata ya ƙazanta sai ta wuni bata gida, ba tare da ya san inda ta tafi ba. Ta gama wuninta bata gida, ta dawo suna falon sashinta ita da Fadila suna tattaunawa. Daddy ya shiga da sallama, hannunsa riƙe da leda, Fadila ce kawai ta amsa sallamar a ciki. Ya ƙarasa gaban Hajiya Zainab, ya ajiye mata ya saka hannu a aljihunsa, ya ɗauko kuɗi bandir ɗaya ya ce "Na rage lokacin bikin Khalil, ga invitation ne mun gama komai, nan da sati biyu ne bikin, idan da wani shirye shirye da zakiyi ne shikenan kya sanar da ni. Nayi magana da iyayen wancan yaron, sun zo ɗazu ga kuɗin auren 'yarki nan, dubu ɗari na tsayar da Magana wata biyu kawai na saka!!! AYSHERCOOL 08081012143LITTAFIN NAN NA KUƊI NE, KU TUNTUƁENI TA LAMBAR WAYATA KUYI PAYMENT. 69 Gaban Fadila ne yayi wata irin mummunar faɗuwa jin ance wai an karɓi kuɗin aurenta, ita fa gaba ɗaya wannan Salim ɗin bai yi mata ba, bata son shi, kuma dan cin mutunci da ƙasƙanci, wai dubu ɗari aka kawo kuɗin aurenta. Wani irin gumi ne ya shigo tsatstsafo mata, ji take ina ma mafarki take yi, wannan wane irin abu ne haka, dama da gaske Daddy yake yi, da ya ce zai aurar da ita ya huta, wato ya gaji da ganinta kenan ya daina sonta, saboda yayi aure?. Hajiya Zainab ta miƙe tsaye, ta watsawa Alhaji Ahmad invitations ɗin a jikinsa "Ka kwashi tsiyarka Ahmad, kaje can dama kai ka nema masa auren, kaje ku ƙarata, ba da yawuna ba wallahi" A sanyaye Fadila ta ce "Mummy dan Allah ki bari, Daddy ne fa" "Dalla can rabu da ni, idan ke ubanki ne ni ubana ne? Da ni kake zancen mu zuba mu gani, shege ka fasa tsakanin ni da kai" Girgiza kai kawai yayi, ya fito daga sashinta, ta biyo shi tana cigaba da surfa masa bala'i, Amina kuwa kulolin Abinci ne a hannunta da zata kai dining. Kawai taga Daddy ya fito, Hajiya Zainab ta biyo shi tana watsa masa sauran invitations ɗin. Idanunsa sun yi jawur, tamkar ya zubda hawaye saboda baƙinciki, a gaban 'yarsa take masa wannan tijarar. Da taga watsa masa invitations ɗin bai isheta ba, ta shiga jan rigarsa tana cigaba da gaya masa duk maganar da ta ga dama. Zare babbar rigar yayi, ya bar mata a hannunta yayi gaba, aikuwa ta kuma cukuikuye rigar ta jefe shi da ita, dafe kansa yayi da yaji yayi masa nauyi yayi waje. Ajiye kulolin hannunta Amina tayi, tabi bayansa tana kuka. Tabbas kowane rai akwai irin jarrabwarsa, amma yana daga cikin babbar jarabtar da Allah zai maka, ya haɗaka da abokin zama wanda bana gari ba. "Daddy, Daddy" Amina ta bishi tana kiran sunansa, ta ƙarasa da sauri in da yake, tana zubar da hawaye ta ce "Daddy dan Allah kayi haƙuri" Murmushin ƙarfin hali yayi ya ce "Me kika yi mini kike bani haƙuri" "Daddy abubuwan da suke faruwa a gidan nan basa yi mini daɗi, zuciyata bata jin daɗin abin da ake maka, Daddy ko ka haƙura da ni, idan har hakan zai dawo muku da farinciki a cikin gidan nan" Ajiyar zuciya yayi ya ce "A da ɗin ma ba a cikin farin ciki nake ba, zuwanki ne ya samar mini da shi, ina ga Albarkacin biyayyar da na yiwa mahaifiyata na aureta ne ya sanya, ya kawo mini ke cikin rayuwata, komai zai faru ba zan rabu da ke ba, sai dai mutuwa ta rabamu, ina sonki sosai kuma ni ba abin da kika yi mini, muna tare in sha Allah" "To kazo mu koma cikin gidan, kar ka fita a haka dan Allah" "Bakomai ki bari, zanje na huta ne" Amina ta ce "Ni dai ban yadda ba, kazo mu koma" tayi maganar cikin marairaicewa. Amina ta ja hannunsa suka koma, sashinta tayi masa wurin zama a kan kujerun falonta, ta ɗebo ruwa ta miƙa masa, ya karɓa ya sha ya ɗan lumshe idanunsa zuciyarsa na cigaba da jin zafin abin da matarsa ke masa. Cikin sanyin murya ta ce "Babyna, akwai mutane da yawa da suke amfana da kai, mussman ma'aikatanka, gani ga 'ya'yanka da 'yan uwanka, duk muna sonka muna son lafiyarka, ba zan hanaka son matarka ta fari ba, amma dan Allah kar ka saka damuwarta a ranka ka cutar mana da kanka, muna sonka dan Allah ka mayar da komai ba komai ba, ka ga da taimakon Allah na samu jininka ya daina hawa, amma yanzu idan a'kasa damuwa a ranka aiki zai koma mana baya, mu mayar da hankali a kan shirin bikin da ke gabanmu, da sauran al'amuran rayuwarmu, please ka daina damuwa" Daddy ji yake kamar ya zubar da hawaye, ya kalli Amina da tuni ita tata fuskar ta jiƙe da hawaye, ya janyota jikinsa, ya kwantar da ita, ya lumshe idonsa, hawaye suka zubo daga idonsa, kusan shekaru talatin ba ɗaya yana dakon baƙin cikin da Zainab ke ƙunsa masa, wani an sani wani ba a sani ba, daga shi sai ita da Allan da yayi su, ko tayi masa laifi ya tuna wasiyyar mahaifiyarsa sai ya ƙyaleta kawai, hakan ha sa ta cigaba da cin karenta babu babbaka. Babban abin da yake ci masa tuwo a ƙwarya yadda take nuna masa shi ba komai bane ba a gaban 'ya'yansa. Cikin hikima ya goge hawayen ba tare da Amina ta sani ba, yayi ƙasa da murya ya ce "Amryata" "Na'am Daddy" "Ahmad yana sonki sosai, Allah ya sa mu kasance tare har Aljanna" Ta shafa kansa ta ce "Amin masoyi, ka dinga saka uwargidan ka a addu'a Allah ya shiryeta, ka cigaba da haƙuri" "Shikenan Meenalina, Allah ya ƙara mini haƙuri" Ta ɗago daga jikinsa ta ce "Amin, ko a haka Alhamdilillah mutum ne kai mai haƙurin gaske" Yayi murmushi ya ce "Nayi magana da Hajiya Maryam, na cika mata kuɗin abin da Khalil bai saya ba, za a turo da kayan lefen sai a kai musu" Amina tayi murmushi ta ce "Alhamdilillah, sai a yiwa 'yan Dutse waya, su zo su gani sai a kai" Ya ce "Ok shikenan, sai ayi hakan, kin san Alhaji Ilyas ya koma wurin maman Yarinyar nan fa" Waro ido Amina tayi ta ce "Haba dai, ya aka yi?" Daddy ya ce "Haka ya ce mini, kuma har sun daidaita ma, ina ga rana ɗaya za a ɗaura shi da na su Khalil" Murna Amina ta dinga yi, tana tsalle tana faɗin Alhamdilillah. Murmushi Daddy yayi ganin yadda, Aminan ke ta tsalle tana murna. Da haka da haka, Daddy ya manta da batun Hajiya Zainab. 'yan uwan Daddy sun yi murna sosai da sosai, da jin batun Khalil zai yi Aure, har an nemi suje suga lefe, kuma sune zasu kai ma lefen. Fadila fa abin duniya ya isheta, ta rasa in da zata sanya ranta, saboda yadda ta tsani Salim ɗin nan, wulaƙanci kala kala ba irin wanda ba ta yiwa Salim. Tana kwance a ɗakinta, taga Salim yayi wani status, ta duba taga hotunansa ne ya ɗora, gaba ɗaya bai yi mata ba, bata taɓa saurayi mai muninsa ba, sai iyayin banza da ƙaryar turanci, gashi sam baaya jin haushin wulaƙancin da take yi masa. Ita kanta Mummy taji haushin kuɗin da aka kawowa Fadila, amma saboda ƙawancen da ke tsakaninta da Hajiya Salma ya sanya bata nuna mata ba, suka cigaba shirye shiryen yadda bikin Fadila zai kasance. Fadila ta kasa gayawa kowa damuwarta, dan ko Yusra bata gayaaa an kawo mata kuɗin aure ba, saboda yadda ta tsani Salim. Khalil kuwa ba zama, sai shiga da fita da yake, yana shirin aurensa, amma ƙasan zuciyarsa babu daɗi, saboda yadda duk abin da yake yi babu hannun mahaifiyarsa a ciki, abin yana damunsa sosai da sosai. Gidansu Hafsa ma ba laifi, Mama nata ɗan nata shirin, sai dai batun nata auren, ta so a bari sai an yi na Hafsa tukuna, amma Alhaji Ilyas ya ce ai ba haramun bane ba. Can wurin wani ƙanin kakanta a ƙauye aka je neman auren Maman, saboda danginta duk sun ƙare sun rasu. Ita da fari ma bata Amince da batun auren ba, Hafsa ce ta dinga lallaɓata tana cewa "Mama, ni idan nayi aure zamanki ke kaɗai ba zai yiwu ba, wa zai dinga kula mini da  ke, a muna tare ma kalli sharrin da ake mana, dan Allah Mama ki daure ki amince" Da ƙyar dai ta samu Maman ta amince ita ma. Sai dai lokacin da Daddy yaje musu da batun sauko da bikin, Mama taga abin yayi gaggawa da yawa, amma dai tayi shiru bata son yawan yin jayayya. Hajiya Maryam da kanta ta kawo lefen Khalil gidan Alhaji Ahmad, kuma ba a kai su ko ina ba sai sashen Amina. Ba ƙarya Hajiya Maryam ƙwararriya ce wurin iya zaɓen abin da ya dace. Akwatuna shida ne, babban set, ba ta cika su da tarkace ba, sai kaya masu kyau da tsada, dan babu atamfar ƙasa da naira dubu goma a kayan nan, abin dai sai wanda ya gani. Shi kansa Khalil da ya ga kayan yayi murna sosai, saboda yadda suka haɗu, ji yake kamar ya kwasa yaje ya kaiwa Hafsa da kansa. Kasancewar Mummy bata gidan lokacin da Hajiya Maryam ta zo, ya sanya bayan ta dawo, Khalil yaje ya sameta ya sanar da ita. "Mummy ga kayan lefe can a kawo, na kawo miki nan ki gani ne?" "Kar ka soma kawo mini kayan tsiyarka gabana, bana gaya naka ka nemi wata uwar ba? Kaje can waccan abar da ubanka ya aura ta zame maka uwa, ai ni na yafe ka a matsayin ɗa, 'ya ta ɗaya ni a duniya ka tashi ka bani wuri kan nayi maka mugun baki ka ƙarasa lalacewa, dan tuni ka riga ka gama lalacewa, sai abin da yayi saura" Ire-iren abubuwan da Mummy take yiwa Khalil ne, yake sake karyawa Fadila zuciya, ba dan haka ba da ita ma bore za tayi ta ce bata son wannan mutumin da ake ƙoƙarin haɗata da shi. Sai cigaba da damunta da lamarin yake yi, ya zamana ko Abincin kirki ba ta iya ci, sai dai ta ɓuya tayi kuka. Hankali kwance Amina take shirin auren Khalil, dan mussaman ta buga nata invitation ɗin. Tana yada habaici a falo, tana faɗin "Abu namu na yaran talakawa sai in da ƙarfinmu ya ƙare, dole muyi shiri tunda mun samu duniya abinka da ba a saba ba" Duk wata barazana da tashin hankali da Hajiya Zainab take yi a gidan nan, ba wanda yake saurarta, ga su Turai sun kai ta wurin malamai daban daban amma abu ya gagara yiwuwa, daga Auren Khalil har batun Amina babu wanda tayi galaba a kai. 'yan uwan Daddy kuwa ranar da za a kai lefe, har da wasu daga 'yan uwan Amina suka zo suka cika gidan, sai guɗa suke da sanya albarka suna yiwa Khalil fatan alkhairi. Har maƙwabta suka dinga shigowa suna ganin kayan kan a tafi kaiwa, wanda da waya basu damar shiga gidan ma, balle a gayyacesu wani sha'ani, wannan karon kuwa duk tsukin babu wanda Amina bata aikawa da katin gayyata ba. Ƙarfe huɗu na yamma, aka kai kayan lefen nan na Hafsa, ita ma maƙotansu da wanda ba a rasa ba, sune suka haɗu suka kai lefen. Khalil ya sai kaji da kuɗin da zasu bayar na tukuici ya bawa Hafsa, dan su fita kunya. Aikuwa surutu ya karaɗe unguwar su Hafsa, wai lefenta har da gwal, mai awara tayi goshi zata auri mai kuɗi. Khalil yayi ƙoƙari, duk da gidansa bai kammala ba, Daddy ya ce zai bawa Khalil gida ya zauna a Kano, kan ya kammala gininsa, amma sai dai shi Khalil ɗin ya sai musu furnitures ya saka, idan ya kammala gidansa na can Abuja, zai sai wa Hafsa kayan ɗakinta, idan ya so duk lokacin da suka zo Kano, sai su dinga sauka a can. Abdul ya taimakawa Khalil sosai, dan gidan da Daddy ya basu ba laifi mai kyau ne sosai da sosai. Khalil ya sai komai, da aka zuba a gidan, duk da Khalil ba da kuɗin Daddy ya dogara ba, yana da abin yi, kuma Daddy da 'yan uwa da abokai, sun taimaka masa amma yaji jiki, dan biki ya ɗauko gagarumi wanda ba harkar ƙari a cikinta. Ya zama very busy shi da Abdul, kusan kodayaushe suna tsakanin Kano da Abuja saboda shirin biki. Har gida Yusra ta zo ta samu Fadila tana yi mata mita "Yanzu ke Fadila shirin bikin Yaya Khalil ɗin, amma ki kasa gaya mini, ko mu shirya wani abu, sai a bakin Yaya Abdul naji" Fadila ta yamutsa fuska ta ce "Ke, ni rabani da wannan sabgar bikin, ba ita ce a gabana ba" "Ban gane ba, ba zamu yi ko wani anko ni da ke ba, mu gayyaci mutane ba?" "Girl, Mummy fa ba son auren nan take yi ba, bana tunanin ma zamuje" Cikin mamaki Yusra ta ce "Ban gane ba zaku je ba, bikin Khalil ɗin, ɗan uwanki tilo a duniya kice ba zaki ba, to saboda me? Wai ma meyasa Mummy bata son auren nan ne?" "Yusra, yarinyar fa awara take sayarwa a titi, Mummy akwai wadda ta zaɓa masa amma ya zage wurin Daddy suka haɗa kai da munafukar Yarinyar can zai auri wannan" Yusra ta ce "Haba Fadila, wannan ra'ayin Mummy ne fa, ke meye naki a ciki, ko Mummy bata so amma ace ran aurensa babu ke babu Mummy a wurin bikin tsakani da Allah haka ya dace? Gaskiya ba zai yiwu ba, zan bugo mana kati mu raba, aure ko na dole ne ai abin farinciki ne" "Yusra, ina cikin damuwa ba zan iya zuwa wurin nan ba, ni komai ya daina yi mini daɗi" "Subhanallah, meyafaru kuma?" "Yusra an kawo kuɗin aurena, Daddy ya saka watanni uku kacal, kuma bana son wanda za a aura mini, zaɓin Mummy ne ba nawa ba, bana son nima na watsa mata ƙasa a ido, kamar yadda Daddy da Khalil suka yi, amma wallahi bana son sa zuciyata kamar zata fashe, ina ga bayan bikin nan wai zai zo Nigeria mu gaisa, wallahi bana son shi" Fadila tayi maganar tana hawaye. "Innalillahi wa innalillahi raji'un, kai wannan al'amri da ban mamaki, ki kwantar da hankalinki Fadila, sai kiga albarkacin biyayyar da zakiyi mata kiga kin dace da auren" "Yusra in auri wanda bana so? Taya ya zaman auren zai mini daɗi, bayan babu ɗingon son wanda zan aura ɗin a zuciyata, ina ta dannewa in yiwa Mummy biyayya, ko dan tayi farinciki, amma kamar zan cuci kaina wallahi bana son sa" Rungume Fadila Yusra tayi tana rarrashinta ta ce "Haka ne, jigon kowane Aure soyayya ce, idan babu ita aure baya armashi, amma mu cigaba da Addu'a mu jira hukuncin Allah, amma gaskiya batun kice wai ba zaki wurin bikin Yaya Khalil ba, bai taso ba, ita kan ta Mummy bai kamata tayi haka ba, ɗanta ne fa na fari" "To ni me zance, gaba ɗaya kaina ya kulla matsalolin gidan nan sun yi yawa, duk a dalilin waccan azzalumar Yarinyar". Yusra ta ce "A'a kar ki ce haka, komai kika ga ya faru, tsari ne da iko na ubangiji babu wanda ya isa ya yiwa wani bawa abu, face abin da Allah ya ƙaddara masa" Ta dinga rarrashin Fadilan, har ta samu nasarar ɗaukarta suka ɗan fita, dan Fadilan ta ɗan saki ranta. Da aka tashi kai katin biki Dutse, Amina har dangin Hajiya Zainab da ta watsar, ta aika aka kai musu cewar suna gayyatar su bikin ɗa. Ganin rawar kan da Amina ke tayi a kan bikin ne ya sanya Hajiya Salma ta ce wa Hajiya Zainab "Zainab, kinga idan kika ƙi zuwa bikin nan, za ayi abin kunya, ace ke uwar ɗan nan baki je ba, zamu ji kunya, dan tsaf za a zageki ace kishi ne, dan haka gara kiyi haƙuri ki lallaɓa kije, ki gayyaci manyan mata koba komai a ganki a wurin" Hajiya Zainab ta ce "Ni ba auren nan ne ya dameni ba, ni burina in ga asiran da nayi, sun yi tasiri sun yi aiki, amma shiru har yanzu ba wani labari" Hajiya Salma ta ce "Ki kwantar da hankalinki, zamu cigaba da yi ba fasawa za mu yi ba ai, yanzu dai kawai ki fara shiri wallahi, kin san mijinki babban mutum ne kuma kin san za a haska bikin nan sosai, ace ba a ganki ba abin da mamaki za a bi diddigin jin abin da ya faru". Haka tayi ta lallaɓa Hajiya Zainab, a kan zuwa wurin bikin Khalil. Hafsa jinta take kamar ba ita ba, wai ita ce zata yi aure, zata auri Khalil mutumin da take matuƙar so a rayuwarta. Yusra ta ja Fadila suka sayo kayan fitar biki, ta kai musu wurin tela, aka yi musu ɗinki, da sauran shirye-shirye. Ɓangaren Amina ma, kaya masu tsadar gaske Daddy ya sai mata na fitar biki. Shi kansa Daddy yana ta gayyatar Manyan mutane, ga sanarwa da ake tayi a gidajen watsa labarai. Khalil ya je kaiwa Hafsa kuɗin lalle da kitso, tayi sharr tayi kyau sai sheƙi take yi. Khalil yayi murmushi ya ce "Amarya ba kya laifi, inyee baki yaƙi rufuwa zata auri ɗan beautiful inyeee" Kunya Khalil ya bata, amma ta ce "Kai ne bakinka yaƙi rufuwa, zaka auri 'yar beauty" Ya ce 'Haka ne kam, zan auri 'yar beautyna, ubangiji Allah ya sanya mana albarka a aurenmu My wife" Ta amsa da Amin cikin jin kunya. Sun yi hira sosai sun daɗe tare, sannan ya bata kuɗin yayi mata sallama, sannan ya tafi gida. A ka fara hidmar bikin Khalil, amma duk batun wani abu na ci da sha a wurin biki, Amina Daddy ya bawa ragamar, ita kuma ta haɗa kai da Ammi, dan danƙa amanar samar da Abinda za a ci a wurin taron bikin. Aka fara hada-hadar bikin Khalil, gida ya cika da jama'a, Amina sai shiga take tana fita, wurin samarwa duk wanda ya zo abinci da wurin kwana. Gida ya kaure da hayaniya, sai hada hada ake. Tubarkallah, Hafsa ta sha kyau ranar da aka fara bikin nan, kowace rana akwai shigar da take yi, Ranar dinner ne Hajiya Zainab ta ƙuduri aniyar zata je ita da ƙawayenta, ko dan ta ci mutuncin amarya a wurin. Amina tana can wurin kwalliya, ita da Azima, wurin Dinner tuni ya cika da jama'a. Amarya da Ango na kan high table, Amarya ta sha kyau daga ita har angon, sai dai wasu daga cikin mutanen haryanzu basu iso ba. Ana tsaka da gudanar da taro Sai ga Hajiya Zainab da jama'arta, Khalil bai taɓa tsammanin Mummy zata zo ba, duk da gabansa ya faɗi da aka ce ga babar ango nan, amma yaji daɗin zuwan Mummy wurin. Hajiya Turai ce taje ta karɓe mic daga hannun Mc, ta ce ita zata yi Mc. Ta dinga zubawa Hajiya Zainab kirari, Hajiya Zainab tana hura hanci. "To Alhamdilillah, Allah ya kawo mu biki na ɗan gata, ɗan masu da shi, duk da dai kyan ƙwarya ta bi ƙwarya, amma an samu wata ƙwaryar da tayi gangancin bin akushi, to muna son wannan ƙwaryar ta san da cewa ajalinta ya zo, domin ruwa ba sa'an kwando bane, lokacin fashewarta yayi" Ɗan jimmm Hafsa tayi, tana juya maganar Hajiya Turai. "Jama'a a tafawa angon nan namu dan Allah, kai da ganin angon nan kaga ɗan gata, zaren ba kalar yadin bane, sai dai abu ne na ɗan yau idan Allah haɗa ba yadda ka iya, amma ramin kura ai sai 'ya'yanta. Allah ya kaimu wata uku i yanzu mu dawo bikin ango da galleliyar amarya 'yar dangi" Ran Khalil ba ƙaramin ɓaci yayi ba, Hafsa kuwa tuni jikinta yayi sanyi, idonta ya fara cika da hawaye. Hajiya Turai ta cigaba da cewa "Uwar ango na buƙatar ganin ɗanta a tsakiyar fili, zata yi masa liƙi dj a bamu sauti mai daɗi. Duk da ran Khalil babu daɗi, amma ya miƙe tsaye, ya riƙo hannun Hafsa, jiki a sanyaye ta miƙe. Amma Hajiya Turai ta ce "A'a ango kawai muke buƙata ban da ke" Mc ya ce "Haba Hajiya, ai bikin na ango da amarya ne, ba ango kawai ba". Khalil bai saurari kowa ba, ya janyo hannun Hafsa zuwa ƙasan stage. A hankali ya yiwa Hafsa raɗa "Dan Allah kiyi haƙuri, ki kwantar da hankalinki kar kiyi kuka please" Jinkina masa kai tayi, tana sake jan mayafinta na net, tana rufe fuskarta. Hajiya Zainab ta ƙaraso tsakiyar filin, Hajiya Turai tana ta sake wasa Hajiya Zainab. Liƙi take yiwa Khalil, yana murmushi,  sai dai suna haɗa ido da Hafsa, ta yiwa Hafsan wani irin mugun kallo, sai da Hafsan ta sunkuyar da kanta ƙasa. Hafsa ta ɗarare jikinta, saboda yadda ƙarara suke nuna mata wariya a gaban mutane. Mai hoto yazo zai ɗauki hotuna, Khalil ya matsa jikin Hafsa, amma Hajiya Salma ta janye Hafsa ta ce "Ke matsa, shi da uwarsa za a musu hoto" Kasancewar Umman Hafsa na wurin, ita ma tuni nata jikin yayi sanyi, ganin cin mutuncin da ake yiwa Hafsa a gaban mutane. Tashi tayi ita ma taje wurin, ta tsaya ta gefen Hafsa tana yi mata nasiha a kunnenta. Mai hoto ya ce "Hajiya Yayar amarya ce ke? Naga kuna kama" Umma ta ce "A'a 'ya ta ce" Ya ce "Ya aka yi bamu san kin zo ba, ku haɗu da babar ango ayi muku hoto". Hajiya Salma ta ce "Mun maka kama da wanda zasu jera da matalauta ayi hoto?" Khalil ji yayi kamar ya tsaga ƙasa ya shige, kunyar Mama da Hafsa suka kama shi, ya rasa in da zai saka ransa. Tuni mutane suka fara ƙananan maganganu, wasu suna Allah ya ƙara, kwaɗayi ya kai Hafsa in da za a wulaƙanta ta. Kusan a tare Amina ta iso wurin, ita da wasu daga cikin familyn Daddy da suka je wurin kwalliya. Anty Fiddausi aka fara labartawa rashin mutunci Hajiya Zainab da ƙwayenta ke ta yiwa amarya, alhalin ita uwarta tana wurin tana gani. Ran Anty Fiddausi ya ɓaci matuƙa, ita da ƙannen Daddy da aka gaya musu zancen tare. Anty Fiddausi ta ce "Dole mu nunawa matar nan iyakarta a wurin nan" Ta kira Amina a waya ta ce "Ɗan jira kar ki shigo tukuna, zan saka a sanar da shigowar ki, ina fatan akwai isassun kuɗi a jakarki" Amina ta ce "Eh, amma Anty lafiya kuwa?" "Matar mijinki ce da ƙwayenta ke ta yiwa amarya da danginta wulaƙanci, zata ga tsiya ina zuwa" Anty Fiddausi ta je ta samu Dj, ta ce masa "Kai, ka karɓi mic ka sanar da zuwan Amrayar Alhaji Ahmad Musa Dutse wurin nan, sunanta Hajiya Amina Hassan, ka wasa mini ita, ka koɗata a matsayin 'yar gaban goshin Alhaji Ahmad, kuma uwa a wurin ango, ka san dai irin yadda kuke yi idan kuna son ku samu kuɗi, idan har kayi hakan, zaka samu kuɗi" Aikuwa jiki na tsuma, yaje ya karɓo mic a wurin Hajiya Turai, ya koma kan stage. Ya dinga wasa Amina, ya dinga koɗata a matsayin amarya 'yar gaban goshi, shalele ta gaban motar Alhaji Ahmad Dutse, amarya ba ta laifi ko ta kashe ɗan masu gida, amarya a gidan Engineer kuma uwa a wurin amarya da ango baki ɗaya, ina amfani da wannan dama wurin gabatar muku da Hajiya Amina Hassan, duk mai sonki shi Engeener yake so, mai so ya samu a wurin Engineer yayi tsani da Hajiya Amina. Baya ganin kowa idan ba ke ba, duk sauran mata bururruka yake ganinsu ke kaɗai ce macen da yake gani, ba wata mata a gidansa in bake ba, idan ma akwai to Yasin buranya yake ganinta". Wata uwar ashar Hajiya Turai ta lailayo, yayin da wurin biki aka ɗau shewa, Amina kuwa shigowa tayi cikin ƙasaita, tayi kyau matuƙa ga ƙiba da tayi, hakan ya sanya kayan suka karɓe ta sosai da sosai. Ta shigo tare da jama'arta, duk da kasancewar Amina yarinya ce, amma manyan mata ne suka shigo tare da ita, abinka da mutum mai fara'a da kuma ungo ya sanya take da mutane sosai da sosai. Amina na ƙarasawa in da suke, ta rungume Hafsa tana faɗin "Ubangiji Allah ya sanya alkhairi, ya baku zaman lafiya, ina miki murna 'yar uwata" ta sake rungume Hafsa. Ta buɗe bakin jaka, ta fara liƙa wa Khalil kuɗi shi da Amarya Hafsa. Jama'ar Amina ma da dangin Alhaji Ahmad, suka dinga yi musu liƙi. Aikuwa Dj ya kuma ware maƙogwaro yana wasa Hajiya Amina. "Godiya nake Hajiya Amina da jama'arta, ba Allah ya ƙara danƙon soyayya, duk mai ƙoƙarin kawo tangarɗa tsakaninku Allah ya mayar da shi takalmin sanyawar ki, ki taka shi yadda kike so. Turai ta miƙe ta daki tebur ta ce "Dole mu san abin yi, sai mun watsa taron nan" (KAI MASIFAR HAJIYA ZAINAB NA BANI TSORO 🙄) AYSHERCOOL 08081012143LITTAFIN KUƊI NE, KU TUNTUƁENI A KAN LAMBAR WAYATA DOMIN SAYA 08081012143 70 Hajiya Turai ce ta fara zage zage, Anty Fiddausi tayi hanzari ta fita waje, bodyguards ɗin da ke waje suke tsaron wurin, taje ta sanar da su su zo su fitar musu da Hajiya Turai da Hajiya Zainab. Aikuwa ƙartin nan suka zo suka tasa su a gaba suka yi waje da su, Mummy ta bisu tana bala'i ta ce "Akan me za a korar mata mutaneta". Su Khalil kuwa suna can basu san me ake yi ba, ana can an hargitse da hayaniya da liƙi da raye-raye babu wanda ya san abin da ke faruwa. Hajiya Zainab bin su tayi ta bar wurin, suka bar wurin bikin baki ɗaya suna masifa. Hajiya Zainab suna tafe sai basu haƙuri a hanya, suka rakata har gida, sannan suka tafi. Gidan babu Mutane sai ɗaiɗaiku, Hajiya Zainab ta nufi sashin Amina, tana zuwa kuwa ta tarar da Daddy yana nan. Babu tsammanni ya ga Hajiya Zainab a kansa, yanayin yadda take huci ne, ya sanya ya gane tashin hankali ne ha kawota ba abin arziƙi ba. "Kai ka saka matarka ta ci mini mutunci a wurin bikin ɗana?" Daddy ya kalleta ya ce "Ban gane ba, ni na je wurin ne balle na san me aka yi?" "Ai dole ka faɗi haka mana, taje ta haɗa kai da 'yan uwanka sun ci mini mutunci ni da mutane na, a gaban mutane, wallahi ka tsawatarwa danginka da matarka su fita daga sabgata, aka dinga ci mini mutunci har da kirana buranya a bikin ɗana amma aka kori jama'a ta, wace irin rayuwa ce haka?" Daddy ya ce "Shikenan na ji, zan yi musu magana Allah ya baki haƙuri, hakan bai isheta ba, sai da ta yi ta gama sannan ta fice, ya girgiza kai kawai yana mata fatan shiriya. Yusra da Fadila basu je wurin ba, sai bayan da Mummy ta bar wurin da jama'arta, dan haka basu san meyafaru ba. Sai bayan sha ɗaya sannan aka watse daga wurin. Abdul ne ya ɗauki Khalil da Hafsa a motarsa, zasu kai Hafsa gida. Suna tafe a hanya, Khalil ya lura da jikin Hafsa a sanyaye yake, tayi shiru tana kallon gefe guda. A hankali Khalil ya ce "Hafsat" ta ɗago ta kalleshi. "Ya aka yi ne?" Kasa magana tayi, sai girgiza masa kai kawai da tayi. Jiki a sanyaye ya ce "Hafsa, na san abin da ya faru a wurin biki ne bai miki daɗi ba, amma dan Allah ina roƙonki kiyi haƙuri, komai zai wuce" still ba tace masa komai ba, jin tayi shiru ne ya sanya ya haskata da fitila, yaga tana share hawaye. Take jikinsa ya sake yin sanyi, ya kai hannu yana share mata, duk ta ɓata kwalliyar. "Dan Allah, ba dan ni ba kar ki saka abin nan a ranki, zai wuce in sha Allah" Cikin kuka ta ce "Dama haryanzu Mummy bata sona amma ka ɓoye mini?" "Hafsa meye amfanin na gaya mikin ne? Kuma ba yadda kike tunani ba dan Allah kiyi haƙuri, na sani babu daɗi amma kiyi haƙuri" Mamaki take, ce mata yake zai wuce kamar bai ga yadda aka ci mata mutunci a gaban mutane ba. Ƙoƙarin cigaba da share mata hawayen yake yi, amma ta janye jikinta, ta koma gefe ta mayar da hankalinta kan titi. A haka suka ƙarasa gidansu, ta buɗe motar ta fice ta shiga cikin gida. Khalil yayi ajiyar zuciya ya ce "Kai Allah ka kawo mini ɗauki" Abdul ya ce "Kayi haƙuri Khalil, komai zai wuce a cigaba da Addu'a, Allah zai kawo mafita" "Abdul dole yarinyar nan ta ji babu daɗi, dan Allah kalli cin mutuncin da ƙawayen Mummy suke yi mata a gaban mahaifiyarta, yadda ka san na zabgawa Turan nan mari" "Easy man, kayi haƙuri, ai ga matar Daddy nan tayi maka kara" Khalil ya ce "Ai ni Yarinyar nan tayi mini komai, ba ƙaramin mutuncinta nake gani ba, ka san ina ta saka Daddy a gaba ya shiga Maganar auren, ina ga bayan bikin har garinsu zan je gaida Babanta, dama can mutumina ne muna mutunci da shi" Abdul ya ce "Ka ga ikon Allah ko, shiysa waulaƙanci ba shi da daɗi, ga yadda ka dinga hantararta lokacin da zamu kaita makaranta, gashi yanzu tayi maka rana ai" "Aikuwa dai gashi na gani". Sha ɗaya da rabi baƙi suka yi ta dawowa gida, ana ta hira ana shewa. Yadda Amina ta shiga sashinta, Alhaji Ahmad sai kallonta yake yi, tayi masa kyau sosai da sosai, kamar ya tsokaneta yadda ya saba amma ya maze ya haɗe rai. Amina ta fara cire abun hannunta tana faɗin "Yallaɓai lafiya kuwa? Ya na ganka haka, kuma ko ka ɗan leƙo mana wurin Dinner". Rai a ɗan ɓace ya ce "Wato shi ne kika je kuka raba abin faɗa a wurin biki ke da Zainab, ki ka je a gaban mutane kuka yi hayaniya har kuka saka security suka koreta ita da ƙawayenta meyasa kike biye mata ne? Ko kunyar idon mutane ba kuji ba?" A ɗan dirirce Amina ta ce "Ni ban yi rigima da ita ba ai lokac........ "Ya isa, ba yadda aka yi nake son ji ba, ni fitina ce ba na so, dan Allah kuyi haƙur a gama bikin nan lafiya, kowa ya watse sai ku cigaba da duk abin da kuka ga dama, amma dan Allah kar ku zubar mini da mutunci a idon mutane. Idan kin sauya kayan ɗan samon abin da zan ci, zan tafi in nemi wurin kwana" ko kula shi Amina ba tayi ba, ta wuce ta cire kayanta ta shiga toilet tayi wanka. Ta sauya kaya ta fita ta shiga Kitchen ɗin sashinta, ta fara ƙoƙarin ɗora girki. 'yar autar su Alhaji Ahmad, mai suna Hajiya Bilki, wani ambassador take aure bata ƙasar gaba ɗaya, ko bikin Amina ba ta zo ba, sai bikin Khalil da ta zo suka haɗu da Amina. Familyn suna jin tsornta, har yayyaenta suna shakkarta saboda faɗanta, duk 'ya'yan gidansu suna da haƙuri amma banda Anty Bilki. Suna shigowa daga wurin dinner nan, tun a falo ta fara faɗin ina "Zainab ɗin take? Ita har tana da bakin yiwa wani gorin talauci? Da zata kwaso wasu 'yan tasha su ciwa yarinya mutunci a gaban iyayeta, ko ta manta mun san asalin balbela ne?" Ana ta bawa Anty Bilki haƙuri, a kan a bar zancen, amma ta ce ba za tayi shiru ba, Anty Fauziyya kuwa ta cigaba da zigata tana faɗin "Gaya mata dai, munafuka Ai mu Allah ne ya kawo mana maganinta, baƙar mara mutunci kawai" Har part ɗin Hajiya Zainab Anty Bilki ta je, ta dinga zazzagata masifa. Sanin cewa Hajiya Bilki ta damata ta shanye a rashin mutunci ya sanya tayi shiru da bakinta, suka ƙare mata tas. "Tsawon shekarun nan ke baki san a ƙule muke da ke ba, kin rabamu da ɗan uwanmu kin kankane komai, to su ƙawayen naki baki gaya musu asalinki ba? Kina yawo da yunwa ba suturar kirki takalmi ya siɗe, Allah ya jiƙan Gwaggon mu ta janyo ki inuwa, amma saboda butulu ce ke bayan mutuwarta kalli yadda kika mayar da ɗanta, Hajiya har ta bar duniya tana kukan rabata da ɗanta da kika yi, ba kunya kin hau kan stage kina cin mutuncin sirikar ki, tir da halinki wallahi". Tsit hajiya Zainab tayi, Hajiya Bilki tayi mata wankin babban bargo, sam bata san ta zo garin ba, dan rabonta da ita sun fi shekara Goma. Hajiya Bilki na fita, Hajiya Zainab ta tafi wurin Daddy tana kuka. Ta tarar da shi Amina na haɗa masa tea, Aminan fuskarta babu walwala. "Gaskiya Ahmad ni na gaji da wannan wulaƙanci, me nayi wa 'yan uwanka ne haka? Bayan wulaƙanci da aka yi mini a wurn dinner, bai ishesu ba Bilki ta sani a gaba tana ci mini mutunci a daren nan" Amina ta kalleta ta ce "Alhakina ne, haka kawai ki ka zo kika mini sharri, wai na sa anci mutuncinki, alhalin ni ko ta kanki ban bi ba da naje wurin" "Amina rufe mini baki, kiyi abin da na saki ki tashi" Amina kamar ta fashe saboda ɓacin rai, ta cigaba da haɗa masa tea. Ya kalli Hajiya Zainab ya ce "Ke me kika yi musu suke zagin naki?" "Sai nayi musu wani abu? Ai kafi kowa sanin ba ƙaunata suke yi ba" "Shikenan, ya isa zan yi musu magana" Amina kuwa na gama haɗa masa ta tashi zata bar falon. Ya ce "Ya zaki tafi, baki bani wani cup ɗin ba" "Matarka ta ɗauko maka" ta bashi amsa ta wuce abin ta. Ɗan shiru Hajiya Zainab tayi, a ranta ta ce 'Cikin sauƙi na samu maganinki, idan asiri yaƙi cinki, na ɓullo ta hanyar makirci' Daddy ya ce wa Hajiya Zainab "Ki tashi kije, zan yi magana da su" Girgiza masa kai tayi ta ce "A'a ni dai mu kwana a nan tare, ba zanje su yi mini wani abin ina can kana nan ba" "Kamar yaya, ba abin da za suyi miki ai" "A'a ni dai mu kwana a nan kawai, zan kwanta a kan Carfet, ba sai na koma can ba, da Asuba na koma" Saboda baya son rigima kawai ya ƙyaleta. Amina ko ta kan baƙi bata kuma komawa ba, dan ta san kowa a ƙosje yake, an ci Abinci sosai a wurin dinner, tayi kwanciyarta dama ga ɓacin rai Jin shiru yayi yawa, Amina har tayi bacci ta farka Daddy bai shigo ba, ya sanya ta sauko daga kan gadon, ta duba falo ko ya tafi ne bai ko yi mata sallama ba. Tana buɗe ƙofar bedroom ɗin, ta hango shi tare da Hajiya Zainab, kamar hira ma suke yana ta murmushi. Jinjina kai tayi a ranta ta ce "Lallai ma mutumin nan, kamar ba shi ne kamar yayi kuka ba saboda cin mutuncin da matar nan take masa ba, aikuwa da ni kuke zancen, in dai makirci ne da ni kike zancen gidan kika tarar. Ta koma tayi kwanciyarta, tana jin yadda zuciyarta ke yi mata zafi. Washegari da safe, tun bayan sallar asuba, Amina ta fito falonta, da kalar shigar da ta ga dama. Kitchen ɗin sashinta ta wuce ba tare da ta kula su ba, Daddy binta yayi da kallo, dan ya san a ƙule take, shi kansa ba yadda ya iya ne, gidansa akwai baƙi ita Zainab ba ta ƙi a zubar da mutunci ba, ko a gaban uban waye. Amina ta zo zata kuma wucewa, sai cewa tayi "Amina ba gaisuwa ne?" Amina ta kalleta ta ce "Da can muna gaisawa ne? Mu cigaba a yadda muke a da, bana son takura da kinibibi" Daddy dai yayi shiru bai tofa musu ba. Amina ta gama kintsawa, ta fito ta kalli Daddy ta ce "Baby, kayanka na ɗaurin aure na kan gado, zanje in kula da baƙina" da haka ta fice ta bawa iska ajiyarsu. Gida ya cika da mutane, aka gama haɗuwa aka tafi wurin ɗaurin aure. Duk zafin Hajiya Bilki da ake faɗa, amma Amina bata gani ba, sai ma tasu da ta zo ɗaya. Wuni aka yi ana hada hada, Amina tama manta da batun wata Hajiya Zainab, saboda yadda jama'a suka cika gidan, ga 'yannuwa ta ko ina, Baba da su Inna har da s Baffa Bala duk sun zo, Amina taga 'yan uwan Hajiya Zainab wanda gara ma nata 'yan uwan sun fisu kyan gani, gaba ɗayansu ba wani na kirki duk kamar wasu gajiyayyu haka suke. A ranar ma su Turai ma sun zo da Hajiya Salma, sai dai ba wanda ya shiga sabgarsu. A ranar Hajiya Salma ke gaya wa Fadila, ai jibi Salim zai zo dan yanzu haka yana ƙasar ma Washegari zai iso Kano. Fadila ji tayi kamar ta ce mata yayi zamansa bata san zuwan, amma ba yadda ta iya haka ta haƙura ta yi shiru tana yaƙe. Bayan an yi ɗaurin aure aka yi wunin biki, tun ƙarfe shida su Anty Bilki suka tafi ɗauko amarya. Mama ta yiwa Hafsa nasiha sosai da sosai, duk da ita Maman ba a ranar zata tare ba, sai bayan sati da tariyar Hafsa, gashi in da Maman zata zauna da in da Hafsa zata zauna, akawai nisa sosai da sosai. Hafsa ta sha kuka kamar ba gobe, Mama tayi mata addu'a sosai, sannan aka ɗauketa zuwa gidan Alhaji Khalil. Tun a ranar wasu daga cikin baƙin duk suka riga suka tafi, sai waɗanda ba a rasa ba. Su Inno ma duk suka kama hanya suka tafi Shanono a ranar, su kansu 'yan Dutsen da suka je suka ga gidan Khalil, duk daga can suka dinga tafiya, suka yi ta yaba kirki da karamcin Amina. Khalil kuwa abokai sun rakashi gidansa, wanda suka kai Hafsa suna  ta yaba kyau da tsaruwar gidan. Abdul ya tsaya yayi musu nasiha tare da yi musu fatan alkhairi, yayi musu sallama ya tafi. Bayan Khalil ya dawo daga rakiyar Abdul, ya dawo bedroom ya tarar da Hafsa a in da ya barta cikin mayafinta tana ta goge hawaye. Ya cire babbar rigarsa, ya dawo kusa da ita ya zauna, ya sauke mayafin da ke kanta, ya saka hannu ya ɗago fuskarta da ta jiƙe sharkaf da hawayen, ya girgiza kai ya ce "Madam, haryanzu kukan bai ƙare ba? Ko dai na murna ne?" Duk da kuka take yi, sai da ɗan tura baki jin abin da ya ce. Rungumeta yayi ta gefe, yana lumshe ido, tare da furta "Alhamdilillah, Allah ya cika mini burina, bayan shan gwagwarmaya har na riga na fidda rai da samunki, amma da yake Allah yayi Rabona ce ke, sai gashi Allah ya bani ke" Ita ji tayi duk ya takurata, yadda ya rungumeta ta dai yi shiru, ba ta ce komai ba. "Zo muje muyi alwala muyi salla" Ta miƙe tsaye tana ƙoƙarin ɗaukar mayafinta, ya ƙwace mayafin ya ajiye ya ce "Hijabi Queen, ai an ɗaura" yayi maganar cikin murmushi, suka yi alwala suka dawo suka gabatar da salla. Yayi musu Adduoi sosai da sosai. Sai dai Hafsa ta ci kazar da ya kawo, ta kafe ta ce ita ba ta jin yunwa. Ya ce "Shikenan, kya ci lokacin da kike so, ki sha madarar to" Ta ce "To" ita ma yana kallonta ta sha kaɗan ta ajiye masa. Shi kuwa Khalil dama yunwa yake ji, dan haka ya zauna ya ci ya ƙoshi abin sa. Ya yi ta lallaɓata tamkar ba abin da zai yi mata, ta saki jikinta ta kwanta har bacci ya fara ɗaukarta, yana kallon yadda ta kwanta da kayan jikinta bata sauya ba. Rigimar Khalil ɗin ce ta farkar da ita daga baccin da take yi, haka tayi 'yan koke-kokenta ta ƙyaleshi yayi bajakolin soyyyarsa. Washegari a gidan Daddy kuwa, Amina da wuri ta tashi tayi girki, ta ɗauko fulasanta masu kyan gaske, ta zuba Abinci, ta bawa Zakiru ta ce ya kai gidan Khalil. Zakiru ya ce"Allah sarki, Allah mai yadda ya so, Allah ya ja zamaninki a gidan nan uwar ɗakinmu, mu aurarki da aka yi mu aka yiwa wallahi, kowa ma kyautata masa kike, yanzu duk wulaƙancin matar nan, amma kika yi girki a kaiwa Sirikata?" Amina ta ce "Zakiru kenan, baka rabo da zolaya ka kai musu dan Allah kar rana tayi". Zakiru ya karɓi kwanuka, ya tafi ya kai gidan Khalil. Shi kansa Khalil yayi mamaki, da Zakiru ya ce masa ai Amina ce ta saka a kawo musu Abinci. Bedroom ya nufa, in da Hafsa ke bacci, yana shiga ya tarar da ita ta tashi. Yayi murmushi ya ce "Ashe kin tashi, dama tashi ki zan yi, Amina ta aiko mana da Abinci" "Wace Amina?" Khalil ya ce "Amaryar Daddy" Hafsa ta ce "Wai meyasa baka ce mata Anty ne? Tana da kirki sosai" "What? Anty kuma to ai ko ke kin girmeta" Tayi murmushi ta ce "Ko ma yaya ne, ai Daddy ne yake aurenta, ta cancanci a girmamata ko dan albarkacin Daddy" Ya ce "To naji, sauko muje muyi breakfast" yayi maganar yana miƙa mata hannu ta taso, suka nufi falo. Hafsa sai kallon Khalil take yi, ko zai sauya mata, amma taga babu abin da ya canza mata, sai ma lallaɓata da yake yi cikin tattali da kulawa. Ganin tana ta kallonsa ne ya sanya ya ce "Ya dai, ko na ƙara kyau ne?". Girgiza masa kai tayi, a dai-dai lokacin da hawaye ke zubowa a idonta. A rikice ya ce "Hafsat menene? Me nayi miki kuma?" "Am very sorry Khalil, kowace mace da ta san kanta, babban burinta shi ne ta kai mutuncinta gidan aure, amma ni Najib ya cuceni tayi maganar tana rushewa da wani irin muka, mai ban tausayi. "Dan Allah Hafsa bana son iri wannan maganar, ni kin ji nace miki wani abu? Impact waye ya ce miki baki zo da mutuncinki ba?" Ya rungumeta sosai a jikinsa ya ce "Dan Allah ki cire wannan tunanin daga zuciyarki, Khalil ke yake so ba wani abu daban ba, kuma ni komai normal just forget dear, ba abin da zan ce miki sai ubangiji Allah ya saka miki da alkhairi yayi miki albarka, ina sonki sosai da sosai kuma saboda Allah, Allah ya bar mini ke har ƙarshen rayuwata, ke duk balahirar da ta faru jiya, still kina tunanin baki da daraja a idon mijinki, ki Kwantar da hankalinki kin wuce duk yadda kike tunani a zuciyata, bari na baki abincin da kaina a baki". Khalil yayi ta ƙoƙarin kawar mata da duk wani tunani daga zuciyarta. Wajen sha ɗaya na safe, su Anty Bilki suka yi wa Amina sallama, kamar kar su tafi, tayi ta nanata wa Alhaji Ahmad "Wallahi Engineer a riƙe mana amarya da mutunci da amana, dan ba zamu lamunci duk wani cin kashi da za a mata ba, yanzu muka san kayi aure" Daddy ya ce "Naji, A sauka lafiya masifaffiya" shi kansa Daddy yaji daɗin yadda yaga 'yan uwansa sun taru sun cika gidan, rabom da ya hakan har ya manta. Anty sai da suka je gidan Khalil, suka kuma ganin amarya sannan suka tafi gida. Amina sai da ta tabbatar komai yayi normal, an gyara ko ina a gidan, sannan ta samu nutsuwa. Daddy ne ya shiga sashinta ya tarar tana cin abinci. Tayi kyau sosai a cikin atamfarta da aka yi mata ɗinkin riga da skirt. "Shi ne kike cin abinci bani ko, ba ƙoshi zaki ba ai" Ya zauna kusa da ita, amma Amina ta miƙe ta nufi bedroom. Yayi murmushi ya ce "Na san a rina ai" Ya tashi yabi bayan ta, yana shiga ya tarar da ita tana cin Abincin tana kuka. Ya karɓe plate ɗin ya ajiye a gefe guda, ya tsura wa kyakkyawar fuskarta ido, da hawaye ya samu muhalli a kumatunta. Gyara zamansa yayi yana share mata hawayen fuskarta. "Am sorry dear, ba nayi abin da nayi ne, dan na ɓata miki rai ba, duk nayi ne saboda na tsare mutuncinki, kar in bada wata ƙofa da zata tada jijiyoyin wuyanta, ta zubar mana da mutunci ba ki ɗaya. Baki ga yadda familynmu ke yabonki, ba nayi ne dan na baƙanta miki ba, sai dan kar ki biye mata". Cikin kuka ta ture hannunsa daga fuskarta ta ce "Amma shi ne kuka kwanar mini a falo, saboda tsabar cin fuska" Danne dariyarsa yayi ya ce "To ai ba abin da yafaru, na san ranar a wurinki nake, duk dan a zauna lafiya ne, idan ma abin da kike tunani kenan to bai faru ba" Ta tura baki ta ce "Idan ma ya farun ina ruwana?" "Bai ma farun ba, idan ma ya farun sai in biyaki abin ki yanzu" ya ƙarasa maganar yana murmushi tare da kissing ɗinta. Ta tura baki ta ce "Ni ka bari" "A'a ba zam bari ba sai kin huce" ya lallɓata daga fushin da take yi. Ya ɗauko Abincin ya cigaba da bata tana ci. Saboda tsabar masifa, a washegarin biki, su Turai duka dawo gidan, suna sake ziga Hajiya Zainab a kan yadda zata yi da Khalil da matarsa, da yadda za ta cizguna musu, har Hafsa ta haƙura ta rabu da Khalil ɗin, babu tunanin komai ta dinga ɗaukar shawarar ta su. Fadila tana zaune a ɗakinta, tana duba litattafanta, saboda suna da teses a satin nan, amma ba abin da take ganewa, karatun kawai yi take yi, ga shi tun a daren jiya Mummy ta sanar mata da cewa wai Salim zai zo. Ƙarfe huɗu na yamma, Mummy ta zo ta sameta a ɗakinta, wai ta shirya ga Salim can ya zo. Turus Fadila tayi, kamar ta ɗaura hannu a ka tayi ihu, duk ta ɓata fuska kamar tayi kuka. Mummy ta zauna a kusa da ita ta ce "Haba Autata, ai na san ba zaki bani kunya ba, shiyasa nake alfahari da ke yarinyar kirki" Tausayin Mummy ne ya kamata, dan haka ta sanya a ranta ko dan farincikin Mummy za tayi haƙuri ta auri Salim. Ta ce "To shikenan Mummy, zan yi yadda kike so in sha Allah" "Yauwa yarinyar kirki" jiki ba ƙwari Fadila ta tashi ta shirya, tana ta fargabar yadda zata ga Salim. Jiki a sanyaye Fadila ta nufi harabar gidan, in da Mummy ta gaya mata Salim yana harabar gidan a kan fararen kujeru. A hankali ta ƙarasa ta zauna a ɗaya daga cikin kujerun. Kallo ɗaya tayi masa, wani takaici ya ƙuleta, ita sirirya shi siriri kamar ba namiji ba, ba wani kumari a tare da shi, ga wani sheɗanin kallo da yake yi mata, tamkar ɗan iska yana ɗan taune lips ɗinsa na ƙasa. "Barka da wannan lokaci amaryata" Fadila ta ɗan yamutsa fuska, ta amsa masa. Haka ya dinga zuba mata surutu, ba tare da tana tanka masa ba. Ya ƙaraci surutansa da iyayinsa tare da tsare-tsaren sa, yayi mata sallama ta tashi ta koma cikin gida. A ɗakinta ta zauna kamar tayi kuka, gaba ɗaya Salim haushi ya bata sam bai yi mata ba. Mummy kuwa ta koma wurin Fadila dan jin yadda suka yi da Salim. Fadila bata nuna mata komai ba, ta nuna mata ta amince da batun Salim, amma ƙasan zuciyarta a cunkushe yake da haushin Salim. Kwanan Hafsat biyar a gidan Khalil, kwanaki biyar ɗin nan a jere Amina ta cigaba da aika musu abinci, Khalil ya ɗauketa ya ce bari suje su gaida su Mummy. Tun da Khalil ya ce zasu je gaida Mummy, Hafsa take faɗuwar gaba. Amma haka ta dake, ta tashi tun wuri ta hau girki, ta zuzzuba a manyan flask. Ya ɗauketa a mota suka tafi gidan su Khalil!!! AYSHERCOOL 08081012143LITTAFIN KUƊI NE, KU TUNTUƁENI A KAN LAMBAR WAYATA DOMIN KU SAI NAKU. 08081012143 71 Ba Hafsa ba, hatta shi kansa Khalil ɗin a tsorace yake, dan bai san me zasu je ya tarar ba ko irin karɓar da Mummy zata yi musu ba. Haka nan ya dake, suka cigaba da tafiya. Zakiru yana ganinsu yayi ta koɗa Khalil yana masa kirari da ango ango. Cikin fargaba da ɗar-ɗar ya yi wa Hafsa jagora zuwa cikin gidan. Hajara ya tarar a falo tana ta aiki, tana ganinsu cikin fara'a ta tsaya suka gaisa da Khalil, ya tambayeta Mummy na nan? Ta ce masa eh tana sashinta. Da sallama suka shiga falon Mummy, suka tarar da ita tana zaune a gaban system tana aiki, ɗaga kai tayi ta amsa musu a ciki. Har ƙasa Hafsa ta durƙusa tana gaida Mummy, amma Mummyn ta bita da wani irin mugun kallo ta ɗauke kanta, jikin Hafsa yayi sanyi sosai, kuma ta kasa tashi daga durƙuson da tayi. Khalil cikin ƙarfin hali ya ce "Mummy ina kwana" Ta mayar da dubanta kan Khalil ta ce "Me ka zo yi mini?" Ya ce "Amm, dama zuwa nayi na kawo miki ita mu gaishe ki" "Me na gaya maka lokacin da zaka yi auren nan?" Tayi maganar tana tsareshi da ido, Khalil Yayi shiru ya sunkuyar da kai. "Tambayarka nake me na gaya maka?" Still bai iya cewa komai ba. Ta ɗan ƙura masa ido sannam ta ce "Tun da ba zaka faɗa ba ni bari na tuna maka, ai na gaya maka muddin kayi auren nan, sai dai ka nemi wata uwar, dan haka ka tashi ka bani wuri, ni ba sirikata bace ba, kaje can ka ƙarata ba dai ka bi son zuciyarka ka auri wadda kake so ba, 'yar gajiyayyun mutane, to kuje can ku ƙarata kar ka sake kawo mini ita gidan nan wai da sunan gaisheni, ga 'yar uwarka nan zata share mini hawaye ta auri wanda nake so, na zaɓa mata kai kuma na sallamawa mai awara kai, bani ba kai na bar mata kai. Kuma ba bar mata kai nayi ba ina nan zan waiwayoka ba zan zura ido ka zauna da jinin tsiya ba ba zai yiwu ba, tashi ki kwashi kayanki ku bar mini gabana" Hafsa ta daskare a wurin, ta kasa magana, Khalil ya buɗe baki zai yi magana amma cikin tsawa ta ce "Ka bar mini falo nace, tattarata ku bar gabana, kar ki ma sake ɗaukar kanki a matsayin sirikata" Hafsa ta miƙe ƙafa na rawa, ido ya ciko da hawaye, tayi gaba Khalil ya durƙusa ya ɗauki kwandon kayan Abincin ya biyo bayan Hafsa. Hajara kuwa tana ganin zuwan su Khalil taje ta gaya wa Amina, Amina ta san za a rina dan matar nan bata da mutunci wulaƙanta 'yar mutane za ta yi, tunda ba sonta take yi ba. Amina na ganin sun fito, fuskokinsu babu walwala amma Amina ta washe baki ta nufi Hafsa tana faɗin "Oyoyo amaryarmu, sannunku da zuwa ba dai har kun fito ba?" Khalil ya ce "Eh tafiya za muyi". Amina ta ce "Au da bamu haɗu ba kawai sai kuyi tafiyarku?" Ya ce "No, zamu shigo ku gaisa ai" Amina ta ce "Ba wani mu gaisa, a nan zamu wuni, sannunku da zuwa" ta janyo hannun Hafsa zuwa sashinta, yadda Amina taga idon Hafsa cike da hawaye, ya ƙara tabatta mata da wulaƙanta ta Hajiya Zainab tayi kamar yadda ta saba. A falo suka zauna, Amina ta ce "Khalil jiya Daddy ya gama mita, wai tun da ka tafi ko a waya baka kirashi ba" Khalil ya ce "Wayar ce ta faɗi, screen ɗinta ya fashe" "Aikuwa da tuni ka ganshi a gidanku, na ce ya ɗan bari tukuna. Sister Hafsa ya gida ya baƙunta?" Hafsa ta ƙaƙalo murmushi cikin sanyin muryarta ta ce "Lafiya lau Alhamdilillah" "Masha Allah, ya gajiyar biki? An sha hidima" "Alhamdilillah" Amina ta miƙe ta ce "To mai zan kawo muku ne? Ina da tea idan kuma girki zan yi muku shikenan" Khalil ya ce 'No, mun karya ga ma abinci mun zo da shi, tafiya za muyi" Amina ta ɓata rai ta ce "Saboda me? Bafa nisa Daddy yayi ba, zai dawo ɗaurin Aure ya je, kuma wani irin zuwane wannan? Ai gara ka barta mu wuni a nan zaman kaɗaicin nan babu daɗi" Khalil ya sunkoyo daidai kunnen Hafsa ya ce 'Habibty, na barki tare da ita ba zaki takura ba?" A son Hafsa gara su koma gida, amma ganin yadda Amina ta karɓeta ya sanya ta ce "Eh ka barni" Duk miskilancin Hafsa, haka Amina ta dinga janta da hira, tun tana ɗan ɗari-ɗari, har ta samu ta ɗan sake suka yi ta hira da Amina, ganin ta sake ne ya sanya Khalil ya ce bari ya barta yaje ya dawo, kan nan ma Daddy ya dawo. Amina ta saki jiki da Hafsa, har ta dinga bata labarin ƙauyensu da yadda ta gudo wurin Babanta a birni. A hakan Hafsa ita ma ta ɗan ɓincina mata wani sashi na rayuwarta, Amina taji tausayinta ƙwarai da gaske, gashi Allah ya bata miji mai sonta in da zata huta, amma uwar miji ta sako ta a gaba. Amina ta ce "Kiyi haƙuri, kin san ita rayuwa ba a taɓa barin ɗan Adam haka, sai da jarrabawa". Hafsa ta ce "Amma Anty Amina gani nake rayuwar aurena tana cikin barazana, idan Mummy ta yiwa Khalil aure, kamar zata ƙara tsanata" Daɗi Amina taji, an kirata da Anty, har ana tambayarta abu. A ranta ta ce 'In dai wannan matar ce, zuciyarta kamar ta sheɗan ba Allah a cikinta, ba tare da saninta ba na auri mijinta, yanzu Allah ya ƙaddar auren ɗanta da na talaka, amma ba tayi hankali ba' a zahiri kuma ta ce "Karki damu, ba wanda zai yiwa wani abu sai abin da Allah ya hukunta zai same shi, se me? ta aura masa mata dubu ma idan ta na so, ke ai kanki kawai kika sani, tunda dai yana sonki, ko mata nawa ya aura kiyi ƙoƙarin kiga kin yi maintaning matsayinki a wurinsa, idan ma ta aura masa in ma bata aura masa ba, idan mai hange hange ne zai auro wata, kawai kiyi fatan idan ma auren zata yi masa ta aura masa shashasha, nifa kin ganni idan na shige sashina sai na manta ina da abokiyar zama, ayyukan gabana sun ishe ni, na kula da mijina da sabgogina, yanzu admission nake jira, kema kar ki zauna da kin samu dama ki cigaba da karatunki kawai in dai zai yarda". Hafsa ta ce "Eh zai yarda, yana ma yi mini zancen, amma ya ce na bari ya nutsu daga hidimar bikin nan da yayi" Amina ta ce "Haka ne biki akwai hidima kam, Allah ya baku zaman lafiya" Har bayan la'asar ita Mummy ma sam bata san Hafsa na gidan ba, baga tafi ba, Bayan la'asar Khalil ya dawo, a lokacin ma Daddy ya dawo. Daddy yayi murna sosai da ganinsu, mussaman Hafsa yayi ta yi musu Addu'a da saka albarka, tare da yi musu nasiha a kan haƙuri da juna. Sai da aka yi sallar isha'i sannan suka rako su Khalil, har mota. Fadila da taga wucewarsu abin ya bata mamaki, dan bata ma san sun zo ba. Sashin Mummy ta tafi, tana mamakin yadda suka zo, amma basu zo wurin Mummy ba. "Mummy" "Na'am ya aka yi?" "Mummy Yaya Khalil na gani da matarsa, zasu tafi yanzu kuma banga sun zo wurinki ba" Cikin mamaki ta ce 'Ban gane sun zo zasu tafi ba dama basu tafi ba?" Fadila ta ce "Dama kin san sun zo ne?" "Eh na sani, amma ni korarsa nayi" "Taɓ, aikuwa suna wurin waccan Yarinyar, gasu can Daddy da ita sun yi musu rakiya" A fusace ta ce "What! Yaron nan kuwa yana da tunani? Au wurinta ma ya koma?. Gaba ɗaya Khalil bashi da tunani ba shi kuma da hankali, amma na san abin da zan yi, zan yi maganinsa kuma ita kanta sai na ja mata kunne a kan Khalil, munafuncin Yarinyar nan ya isheni" Fadila ta jinjina kai ta bar ɗakin Mummy. Bayan su Hafsa sun je gida ma, rarrashi da nasiha Khalil ya cigaba da yi mata, dan babu wanda za a yiwa abin da Mummy ta yi wa Hafsa ya ce zai ji daɗi. Cikin sanyin jiki ta ce "Amma auren nan zai yi mana albarka kuwa, tun da har Mummy bata so" Khalil ya ce "In sha Allah, zai yi mana kuma ita ma zata sauko" Hafsa dai kawai jinsa tayi, amma ba dan ta yarda da abin da yace ɗin ba. Ko da Hafsa suka yi waya da Mama, ta gaya mata sunje gidansu Khalil, amma am bata gaya mata yadda suka yi da Mummy ba, dan bata son ɗagawa Maman hankali. Sati guda da Bikin Hafsa, Mama ma ta tare a gidan Alhaji Ilyas, cikin ikon Allah dama yaran nasa ba ƙanana bane ba, duk da girmansu, dan haka suka yi ta murna da auren da mahaifinsu yayi. Haka rayuwa ta cigaba da juyawa, cikin jujjuyar lokaci sakannin zuwa mintun, awanni zuwa sa'oi kwanaki da kuma satuttuka suka dinga shuɗewa. Hafsa ta yi wata guda a gidan Khalil, cikin tsananin so da ƙaunar junansu, sai tattalata yake yi yana nuna mata ƙauna, gefe guda kuma a tsorace take, saboda iƙrarin Mother a kan za ta yiwa Khalil aure, shikenan idan ta yi wa Khalil aure ta kaɗe, dan ta san budurwa zata aura masa, kuma 'yar masu kuɗi, shikenan ita ma ta san wannan rawar kan da yake a kanta, dan yanzu ya aureta ne, amma da ya samu wata zai daina tattalinta. Ranar da ta cika wata biyu, ya ɗauketa ya kaita har gida wurin Mama, Mama tayi murna sosai da ganin Hafsa, tayi sharrr da ita ta sha kwalliya, ita kanta Hafsa tayi murnar ganin Mama, alamu suka nuna tana cikin kwanciyar hankali tare da mijinta da 'ya'yansa. Da suka tashi dawowa gida, sai da ya kai Hafsa gidansu Abdul suka gaida mahaifiyarsa. Washegari kuma, Khalil ya saka Hafsa ta kira Amina, dan ta basu kwatancen gidansu a Shanono zasu je gaida Baba. Amina kamar ta zuba ruwa a ƙasa ta sha, sai murna take bakinta yaƙi rufuwa. Tayi musu kwatance sannan ta ce "Khalil, Dutse fa yaushe zaku je?" Ya ce "A satin nan in Sha Allah" "To yayi kyau, na gode sosai da sosai, dan Allah idan kunje Dutse har gidan 'yan uwan mamanku kuje, kai kayi zumunci da su". Khalil ya ce "In sha Allah, ko kina da saƙon da za a kai Shanono" Ta ce "A'a, ai baifi sati biyu naje, na gode sosai" Ya ce "Babu komai, kar ki damu" Ta kaste wayar, Daddy na fitowa daga wanka, tayi tsalle ta rungume shi. Ya ce 'Tooo, ya aka yi ne?" "Su Khalil ne zasu garinmu, wai zasu je gaida Babana" Yayi murmushi ya ce "Ai yayi kyau, yakamata su faranta miki, kamar yadda kika yi tsayin daka a kan kiga bikinsu ya yiwu" "Kai Alhamdilillah, ji nake kamar nayi rawa wallahi" Yayi murmushi ya ce "ai kin saba dama" Su Khalil sun samu karɓuwa sosai a garinsu Amina, Inno ta karrama su sosai da sosai ita da Baba, Khalil yayi musu alheri da yamma suka juyo Kano, Inno kuwa ta haɗa musu kayan tsaraba sosai tana musu Addu'a. Amina suka yi waya da Baba, ya sanar mata ai su Khalil sun zo, ta dinga murna tana jin daɗi. Shi kam Khalil ba zai taɓa mantawa da abin da Amina tayi masa ba, ko iya ƙoƙarin ta na samun Hafsa da yayi, ya isa ya dinga ganin kimarta. Bayan sun huta kwana biyu, Khalil ya kuma ɗaukar Hafsa zuwa Dutse su gaishe su, kuma suyi musu bangajiya, nan ma sun ga kara da karamci, suka dinga murna dan haka nan gari banza Khalil baya zuwa Dutse. Salim kuwa biki ya nata ƙaratowa yana shiri, sai dai ya fara ƙuluwa da abubuwan da Fadila take yi masa, na wulaƙanci da cin mutunci, dan haka ya fara gaya wa Babarsa abubuwan da Fadilan take yi masa. Hajiya Salma taji haushin hakan matuƙa, dan haka ta kira Hajiya Zainab a waya. Hajiya Zainab bata kawo komai ba a ranta ta ɗaga wayar tana faɗin Hajjaju. "Kin ga Zainab, abin nan idan mai yiwuwa ne ayi, idan ba mai yiwuwa bane ba a bar shi kawai, kince a haɗa auren ɗanki da 'yar 'yar uwata abu bai yiwu ba, zamu haɗa auren yaranmu amma Fadila sai wulaƙanci take yiwa yaron nan, idan fa bata so kawai a bar sabgar nan". Hajiya Zainab ta ce "Me yayi zafi haka ke kuwa? Mu bi komai a sannu dan Allah, zan yi mata magana" Mummy tayi ta bata haƙuri, ta katse wayar ta tafi ɗakin Fadila. Da mamaki Fadila ta kalleta ta ce "Mummy, ya na ganki a ɗakina yanzu?" "Ban sani ba, wato dama munafuntata kika yi, kika ce mini zaki auri yaron nan, amma kike wulaƙanta shi ko? Hajiya Salma ta kirani rai a ɓace ta ce kina wulaƙanta mata ɗa. To kin kyauta kema kije kiyi duk abin da kika ga dama, kuyi ta cusa mini baƙin ciki ke da ubanki da ɗan uwanki tun da haka kuka zaɓa. Ba kwa ƙaunata ba kwa kishina, wai Khalil ya wanke ƙafa ya tafi garinsu yarinyar can, ya kuma je Dutse duk ba tare da sanin na ba, ga baƙincikin babanki kema kuma gashi kin tsiro da naki, na gode" ta juya fuuuuu ta fice ta barwa Fadila ɗakin. Dafe kai Fadila tayi, kawai ta fashe da kuka, tama rasa me za tayi, 'yan kwanakin nan ni ko bacci bata iya yi, saboda tunanin auren nan, ga Mummy sai shirin biki take, ga shi shi kuma munafuki ya na kai ƙararta. Take taji wani irin mugun takaici ya tokare ƙirjinta, tayi jifa da littafin hannunta ta cigaba da kuka. Alhaji Ahmad yana ta shirin komawa Lagos, amma yana tunanin yadda zai bar Amina da Hajiya Zainab a gida, dama a yanzunma yana nan ɗin ba shiri suke ba. Kwanciyar hankalinsa shine yana wurin Amina, amma duk lokacin da yake a wurin Hajiya Zainab, kwanan tashin hankali suke yi. Hafsa na kwamce a kan doguwar kujera, Khalil ya ce ta zauna ta huta, yana ta ɗan yin aikace-aikacen da zai iya yi, Hafsa sai dariya take yi masa, yana mopping tana cewa 'gaskiya wannan mopping ɗin, to kar dai in ce a bar mini abina nayi aji haushi, amma gaskiya ba haka ake yi ba" Yayi dariya ya ce "Aikuwa sai nayi, kuma idan na gama sai kin mini godiya, in gama in je in ɗora girki" Hafsa ta ce "Kaiii, ashe yau ciki zai ɓaci, za ayi ta gudawa" "Aikuwa sai na dafa, kuma sai kin ci" Kamar an wurgota sai ganin Hajiya Zainab suka yi a tsakiyar falon. Miƙewa Hafsa tayi, gaba ɗaya jikinta ya ɗau rawa, ga 'yar rigar jikinta ba in da ta kai. "Mu..mu... Mummy sannu da zuwa" Hafsa tayi maganar cikin rawar murya. Wani kallon banza tayi mata ta ce "Ba shakka, kin zo kin samu wuri kin miƙe ƙafa, kai kuma har ka zama bawa ko? Wato Khalil saboda baka neman albarka saboda ka nuna mini ban isa ba, ka wanke ƙafa ka tafi har Shanono wurin wancan matsiyatan ni kake wulaƙantawa ko Khalil". Jiki ba ƙwari Khalil ya ce "Mummy ba haka bane... "Rufe mini baki, munafuki" ya sunkuyar da kansa ƙasa, yana sake mamkin hali irin na mahaifiyarsa. "To bari kaji in gaya maka, wallahi ba za a taru a mallake mini kai ba, ban haifawa kowace mace bawa ba, ka tattara kayanka ka koma wurin aikinka, wallahi na bincika baka koma ba, hukuncin da zan maka sai ya baka mamaki, kuma ban yarda ka bar garin nan da ita ba, ke kuma ki fara lissafa kwanakin da suka rage miki a gidan nan, dan yadda yake wannan rawar kan a kanki, nan gaba sai abin da Allah yayi, ina ga zai iya dukana ma saboda ke". Khalil ya haɗa hannayensa biyu ya ce "Mummy dan Allah kiyi haƙuri, kinga bama ta jin daɗi, na miki alƙawarin da ta ji sauƙi zan koma" "Au har ya kaimu ga fara jayayya ko Khalil? Da kan ka aureta sai ka tafi ka shafe kwanaki ban saka a idona ba, amma saboda ita ka fara yi mini musu ko? Khalil kar ka ƙure ni nayi maka baki fa" A gigice ya ce "Shikenan, Kiyi haƙuri zan koma in Allah ya yarda". "Kar ma ka koma kaga yadda zan yi da kai, sakarai" yadda ta shigo ta zazzage musu masifa, ko zama ba tayi ba ta juya ta fice. Dama tsarin da tayi, idan ya bar garin zata san yadda zata yi ta kori Hafsa, dan bata ƙaunarta ko kaɗan. Mummy fa ta tatara Fadila ta fita a sabgarta, hakan ya sake jefa Fadila cikin tsananin damuwa, ko Abinci bata iya ci, karatunma ta ajiye bata iyawa gashi test suke yi a makarantar. Da ƙyar a daddafe ta iya yin test ɗin yau, saboda azabar ciwo da kanta yake yi. Bayan sun gama test suna da sauran lectures, sai dai ba zata iya jira ba, kuma gaba ɗaya ko son zuwa gida ba tayi, saboda ta san damuwa zata je ta kuma tarar wa. A hankali ta tashi ta bar ajin, saboda yadda hayaniya tayi yawa a ajin. Wani ajin da babu kowa taje ta samu ta zauna, sai da kanta ha cigaba da yi mata wani irin matsanancin ciwo, ga ƙirjinta yayi nauyi, da ƙyar take numfashi. Har Yazid ya shiga aji, suna jiran malamin da zai shigo musu, yaga kiran Fadila. Ɗaga wayar yayi yana mamakin dalilin kiran nata, dan harara ce take haɗa shi da ita a kwanakin nan. Yana ɗagawa yaji muryarta sama-sama ta ce "Dan Allah ka zo level 4, bani da lafiya ka zo ka kaini gida" Cikin hanzari Yazid ya tashi, ya bar ajin ya nufi level 4, a can ƙarshen ajin ya hangota ta kifa kanta. Ya ƙarasa in da take da sauri yana kiran sunanta. Ɗago idonta tayi sun yi jawur, hawaye ne kawai ke fita daga idonta. "Subhanallah, Fadila meyafaru ne?". "Bani da lafiya, na kira Yusra bata ɗauka ba ina ga suna lectures ne, dan Allah ka kaini gida kaina zai fashe, dishi-dishi nake gani" Yazid ya ce "A'a mu dai je Asibiti, in da kika taɓa kaini ɗin nan, ta so muje" jiki na rawa ta tashi tsaye, ya sa hannu ya karɓi jakarta, sai dai jiri ya kwashe ta, Yazid ya riƙeta. Aikuwa ta fashe da kuka ta ce "Bana gani sosai fa" Yazid cikin damuwa ya ce "Sannu, tashi mu tafi daure". Da ƙyar ta iya tsauwa, ta riƙe gefen rigarsa suka fito a hankali. Suka ƙarasa wurin motarta, ya duba jakarta ya ɗau mukulli ya buɗe motar, ta shiga shi kuma ya zagaya mazaunin direba ya kunna suka bar makarantar. Kan su kai Asibitin duk Fadila ta firgice, sai koke-koke take yi, tana riƙe kanta. Yazid ji yake kamar ya cire mata ciwon, ya dawo da shi jikinta, yadda take yi ɗin nan zaka tabattar tana jin jiki sosai. Suna zuwa asibitin aka karɓesu da gaggawa, kasancewar sun san Fadila nan da nan suka karɓeta, aka kwantar da ita. Doctor Aliyu na ganin Yazid ya ce "A'a mutumin, yau kuma kai kawota?" Yazid ya ɗan yi murmushi. Sosai take kuka tana kiran sunan Mummy. Doctor Aliyu ya ce "Fadila ya isa haka, meyake damunki?" Cikin kuka ta ce "Ni ka ƙyaleni, ina Yazid?" Aliyu ya ce "To Yazid ɗin ne zai baki magani ko ni?" "To ba kana kallona ba, ka ƙi yi mini komai, Zid ka mayar da ni gida in mutu a can" Yazid yayi ƙasa da murya ya ce "Zan maida ke, Addu'a nake yi miki, amma kiyi shiru kin ji" ta fashe da kuka ta ce "Bana gani sosai" "Zai daina in sha Allah, kiyi addu'a" Ta ce "To, amma kaje gidanmu ka kira mini Mummy" Ya ce "To shikenan, zan je in sha Allah" tana ta wannan surutan, gaba ɗaya Yazid ya shiga damuwa, ya zuba mata ido sai rawar sanyi take saboda zafin zazzaɓi" Doctor Aliyu ya ce "Ka kwantar da hankalinka, zafin ciwo ne amma nayi mata allurar bacci, za tayi bacci zazzaɓin ma zai sauka" Yazid ya ce "Allah ya sa" Doctor Aliyu ya auna Bp ɗin Fadila, amma ya ganshi ya hau sosai. Doctor Aliyu ya ce "Ya aka yi jinin Yarinyar nan ya hau haka?" Yazid ya ce "Ban sani ba, nawa ya nuna?" Aliyu ya ce "160/90mmgh, ya hau sosai, bari in je in Kira babanta yakamata su sani, ina ga a nan zamu riƙeta" Jiki a sanyaye Yazid ya ce "To shikenan" Bayan fitar Doctor Aliyu, Yazid ya matsa gaban gadon ya zuba mata ido. Sai yanzu ya lura da yadda ta ƙara ramewa. Kamar mai raɗa yaji tana kiran sunansa. A hankali ya matsar da kunnensa bakinta dan jin me take cewa. "Yazid! Bana son sa ka gaya wa Mummy!!" Ras gaban Yazid ya faɗi, ya kira sunanta amma yaga bacci take she's unconscious, amma tana ta nanata "Bana son shi!!" Tofa! AYSHERCOOL 08081012143LITTAFIN KUƊI NE, MAI BUƘATA YANA IYA TUNTUƁATA A KAN LAMBAR WAYATA. 08081012143 72 Jiki a sanyaye Yazid ya ce "Fadila, me kike cewa ne?" Kasancewar bata hayyacinta bata san meya ke faɗa ba, a cikin baccin ta cigaba da kuka tana cewa bata son shi. Tunani ya shiga yi, waye bata so ɗin ko Kankiya ne? Amma ai Kankiya ya bar makarantar ma tun bayan da abin nan ya faru babu daɗewa. Ya bawa kansa amsa. Doctor Aliyu ne ya shigo ya miƙa wa Yazid takarda, ya ce yaje Pharmacy ya karɓo maganin. Yazid ya karɓa je Pharmacy aka bashi maganin, ya tambayi kuɗinsa aka ce masa ai akwai kuɗi a family file ɗin ba sai ya biya ba. Ya koma ya kai maganin ya tambayi, doctor Aliyu ya kira gidansu Fadila. Doctor Aliyu ya ce "Na kira su, lambar mamanta a kashe babanta kuma bai ɗaga ba". Yazid ya koma wurin Fadila ya zauna, yana ta saƙa da warwara, ya ɗan zuba wa Fadila ido, tayi rama sosai da sosai. 'kenan dalilin damuwarta kenan, kusan kullum cikin kuka?'. Haka yayi ta wasi-wasi har la'asar Fadila bacci take, bata farka ba, Yazid ya tashi yaje yayi salla ya biya ya sayo wa Fadila fruit da kwalin exotic, in da Allah ya taimake shi da 'yan kuɗi a jikinsa. Cikin ikon Allah ya koma babu daɗewa, ta fara motsi zata tashi. Yayi saurin ƙarasawa gaban gadon nata, yana kiran sunanta. Miƙa tayi, Yazid ya kawar da kansa ƙasa, ta kalli Yazid ta ce "Baka tafi ba?" Ya ce "Eh, sannu ya jikin?" "Da sauƙi ina, Doctor Aliyu?" Ya miƙe ya ce "Bari naje nayi masa magana, ko zaki ci wani abun kan yazo?" Ta ɓata rai ta ce "Ni bana ci, ka kira mini shi". Yazid ya tashi, ya kirawo mata Doctor Aliyu. A tare suka shigo ɗakin da take, Aliyu ya kalleta ya ce "Sannu ya jikin?" "Da sauƙi, ka kira mini Mummyn?" Aliyu ya ce "Wayarsu bata shiga, amma zan sake kira meya yake yi miki ciwo yanzu?" "Kaina ne yake ciwo haryanzu wallahi, ga ƙirjina yayi nauyi" Doctor Aliyu ya zauna ya ce "Yauwa yanzu gaya mini, yi min bayani, meke damunki jininki ya hau?" Ta waro ido ta ce "Hawan jini kuma?" "Eh, jininki ya hau, gaya mini meke damunki?" Jikinta ya ɗanyi sanyi, amma ta kasa magana. Aliyu ya ce "Talk mana" Ta ɓata rai ta ce 'Bakomai, ni ka sallameni kawai in tafi gida" Yazid ya ce "Jikin naki a haka zaki tafi?" "Eh ni gida zan tafi" Yazid ya ce "Dan Allah kiyi haƙuri ki zauna" Ta galla masa harara ta ce "Ba zan zauna ɗin ba" Aliyu ya ce "Ke masifaffiya, yana ta ɗawainiya da ke tun da ya kawo ki yake zaune yana kula da ke, amma kina masa masifa ba za a sallame ki ɗin ba" "Kar ka sallame nin, tafiya zan yi da kaina" Aliyu ya ce "Sannu Yazid, kana haƙuri da wannan fitsararriyar, ka fasa da ita zan baka ƙanwata" Duk da yadda take fama da kanta, wata uwar harara ta gallawa Aliyu ta ce "Koma wace kai ka sani, na gaya maka ni ba saurayina bane ɗan ajinmu ne" "To, Allah ya baki haƙuri, bari na sake trying lambar gidanku, ki samu ki ci wani abu, kan a baki magani" Ba tace masa komai ba, Doctor Aliyu ya fice daga ɗakin. Ta kalli Yazid ta ce "Ka daɗe sosai a asibitin nan, ka tashi ka tafi na gode" Yazid ya girgiza kai ya ce "Kar ki damu, kinga ga Fruit na sayo miki ko zaki iya sha" Haka nan taji ya bata tausayi, ta ce "Bani ayaba in ci" Ya ɗauka ya miƙa mata, sai ɗan yamutsa fuska take yi. Ya kalleta cikin kulawa ya ce "Ya aka yi, ya naga kina yamutsa fuska?" Kamar za tayi kuka ta ce "Zazzaɓin ya sauka, amma kaina ciwo yake yi, kuma wai jinina ya hau ni abin ya bani mamaki" Ya kwantar da murya ya ce "Meke damunki har haka da jininki zai hau? Meyafaru ne?" Kawai sai hawaye ya fara bin fuskarta, har da sheshsheƙa. Yazid ya ce "Yi haƙuri, dan Allah ki daina wannan kukan ya isa haka, kinga baki da lafiya". "Ni ka ƙyaleni nayi" Ya ce "No, ba zan iya ba, bana son ganin kukanki, ci ayabar su zo su baki maganin" Ya dinga lallaɓata sai dai tana ci tana kuka, yana cigaba da rarrashinta. Sai bayan la'asar daf da magariba sannan Aliyu ya samu Mummy a waya, ya sanar mata da Fadila fa tana Asibiti tun wurin sha biyu. A rikice ta ɗau mota ta bazamo Asibiti wurin Fadila. Tana zuwa ta nufi Vip rooms tana dubawa, dan ko Doctor Aliyun bata nema ba, cikin sa'a a ɗaki na uku taga Fadila a ciki, gefenta kuma ga Yazid a zaune. Da sauri ta ƙarasa gaban gadon da Fadila take kwance tana faɗin "Fadla, lafiya kuwa? Meyasameki garin yaya aka kawo ki asibiti?" Kasa Magana Fadila tayi, sai kallon Mummy da take yi, hawaye fal idonta. Yazid ya risuna yana gayar da Mummy. Ƙarewa Yazid kallo tayi, daga sama zuwa ƙasa ta ce "Waye wannan?" Ta tambayi Fadila maimakon ta amsa gaisuwar Yazid. "Ɗan ajinmu ne" Fadla ta bata amsa. Still bata amsa masa ba ta ce "Fadila maimakon ki kira gida, sai a kawoki Asibiti ba wanda ya sani?" "To Mummy ba duk an kira lambarku bata shiga ba, ke taki bata shiga ba, ta Daddy kuma baya ɗagawa" Mummy ta ce "Dama ya za ayi ya ɗaga, yana ta waccan banzar yarinyar" ta kalli kayan Fruit ɗin dake kan drower a gefen Fadila ta ce "Wannan kayan fa, waye ya kawo su?" "Yazid ne ya saya mini" ta bata amsa. Hajiya Zainab ta kwaɓe baki ta ce "Waye kuma hakan?" Fadila ta ce "Gashi nan, a kusa da ke" Ɗan guntun tsaki tayi ta ce "Wai meyasameki ne ma?" Fadila ta ɓata fuska ta ce "Kaina ne yake ciwo, da ƙirjina". Yazid ya miƙe ya ɗan risuna ya ce "Mummy ni zan tafi, Ukty as'alullahil azim, rabbil arshil azim an yashfiyaki". Fadila ta ɗan yi murmushi ta ce "Na gode sosai, na zaunar da kai ka gaida gida". Yazid ya yi murmushi ya ce "Bakomai, Allah ya ƙara sauƙi" Har zai fita Mummy ta ce "Kaga, zo ka kwashe wannan kayan ka tafi da su, ka ƙarasa su ka cinye" Fadila ta ce "A'a bar mini ina so, zan ci" Mummy ta ce "Ke ba sai a sai miki wani ba, ai naga shi mabuƙaci ne" Yazid a ƙasan ransa bai ji daɗin abin da Mummyn tayi masa ba, amma ya maze ya ce Bakomai Mummy, Allah ya bata lafiya. "A'a ba Mummy ba, Hajiya Zainab" Yazid ya jinjina kai ya fice. Mummy ta mayar da kallonta ga Fadila ta ce "Ke wai waye wannan?". "Mummy na gaya miki ɗan ajinmu ne, wannan Yazid ɗin ne da nake baki labari kwanaki" Hajiya Zainab ta tsuke fuska ta ce "Meye alaƙarki da shi?" Fadila ta ɗan numfasa ta ce "Kamar dai yadda na gaya miki a baya Mummy, bakomai, Yazid yana taimaka mini sosai a harkar karatu, iyakacinta kenan. Amma ba abin da nake tunani bane ba. "Au ai kema na ɗauka gajiyayyen zaki ɗauko mini, bayan da sa ranarki a ka, kalli wani matsiyacin takalmi a ƙafarsa, yadda idaunsa suka yi fici-ficin Nan da gani yunwa yake ji" Yazida data fara ƙosawa da mitar Mummy ta ce "Ki kwantar da hankalinki, ni ba son Yazid nake ba, ba tsarar aurena bane ba, kawai dai yana da kirki ne" Doctor Aliyu ne ya shigo shi da wasu Nurses guda biyu, yana ganin Mummy yayi murmushi ya ce "Hajiya, ashe kin ƙaraso" Mummy ta ce "Eh, na zo tun ɗazu, ya aiki?" "Alhamdilillah, Hajiya ki ritsa ta tayi miki bayanin meke damunta, jininta ya hau sosai" Hajiya Zainab ta ce "Innalillahi wa innalillahi raji'un, kamar ya hawan jini?" "To gata nan dai ki tambayeta" Hajiya Zainab ta kalli Fadila ta ce "Fadila garin yaya jininki ya hau, a wannan shekarun naki haka?" Shiru Fadila tayi a ranta ta na jin dama zata iya gaya wa Mummy abin da yake damun zuciyarta. Amma tayi shiru ta ce ita ma bata san dalilin hawan jinin ba. Bayan sallar isha'i Daddy yana zaune yana cin Abinci, suna hira da shi da Amina, ta ce "Baby, ɗazu da ka bar samsung ɗinka a gida an kiraka, amma dai ban ɗaga ba. Yayi murmushi ya ce "Meyasa baki ɗaga ba?" "To na sani ko wayar ta sirri ce?" Ya kalleta ya ce "Kina tsoron ko wata ce ta kirani a wayar?" Amina tayi murmushi ta ce "Idan ma watan ce ta kiraka ina ruwana, normal ne ai" Ya ce "Ba wani normal, kizo ki isheni da mita da kumbura baki saboda kishi ba" "Ba wani kishi da zan yi, kowa iya allonsa ya wanke kawai, ni dai na san na riga na sha kwana a nan" tayi maganar tana ɗora hannunta a ƙirjinsa. Ya saka nasa hannun a kan nata hannun yana kallonta ya ce "Tabbas hakane, kin riga kin sha kwana a zuciyar mijinki Amina, Ahmad na matuƙar ƙaunar ki sosai Meenal, kin kawo haske na musamman a rayuwata, kin fitar da ni daga cikin wani duhu da ya dabibaye rayuwata a kan Zumunci da kuma ciyar da dukiyata. Ina alfahari da ke Allah ya yi miki albarka" Tayi murmushi ta kalleshi ta ce "Ni yakamata nayi maka godiya, da ka bani fitilar haska rayuwata ta ilimi, ka dinga kula dani, ka nuna mini nima 'ya ce, duk da yadda iyalanka ke ƙyamata, amma baka ƙyamace ni ba, ka aureni, kake ta nuna mini kulawa ni da iyayena. Ni yakamta nayi maka godiya" Ture kwanukan Abincin yayi, ya ɗorata a kan cinyarsa, ya rungumeta sosai a jikinsa, yana cigaba da gaya mata yadda yake sonta. Kamar ba babban mutum ba, ya ce "Sweetyna". "Na'am Daddy" ta amsa tan jan gemunsa a hankali. "Zan biya mana umara, mu da mutum biyar, kiyi selection wanda kike ganin ya dace mu tafi tare da su". "Wayyo Allahna daɗi, Allah ya ƙara maka arziƙi Daddy, abin da nake ta buri a rayuwata, ina burin zuwa makka". "Da Hajji na so biya mana, amma na san maybe lokacin Babyna yana cikin ki, tafiya ba zata yiwu ba" yayi maganar yana shafa cikinta Tura baki tayi tana murmushi, ya ce au dariya ma na baki, wataƙila yanzu haka ma akwai" Ta kalli hannunsa ta ce "Bakomai a ciki, sai abincin da naci na ƙoshi, ai yakamata na huta ai". "A'a gara dai ki haihu, sai ki huta gaba ɗaya, kiyi selecting mutanen, sai ki gaya mini, yanzu fara ɗauko mini wayar tukuna" Amina ta tashi cikin jin daɗi, taje ta ɗauko masa wayar ta kawo masa. Dubawa yayi, yaga kiran doctor Aliyu ne. Cikin hanzari ya kira wayar doctor Aliyun, aikuwa yai sa'a ta shiga. Bayan sun gaisa doctor Aliyu ya ce "Yallaɓai dama na kiraka ne, saboda Fadila da aka kawo Asibiti, ba lafiya daga makaranta, baka ɗaga ba kuma cikin ikon Allah ma dai daga baya wayar Hajiya ta shiga, gashi ma har ta zo" Daddy ya ce "Subhanallah, meya sameta ne?" Doctor Aliyu ya ce "Eh, ta zo da zazzaɓi mai zafi ne da ciwon kai, sai kuma muka duba jininta ya hau sosai" Gaba ɗaya Daddy ya rikice ya ce "Yanzu a wani hali take ciki?" "Eh, yanzu jikin da sauƙi tama farfaɗo daga allurar baccin da muka yi mata". Daddy ya ce "Shikenan, gani nan, yanzu zan zo in Allah ya yarda" Amina ta ce "Daddy meyafaru ne?" Ya miƙe tsaye yana faɗin "Fadila ce babu lafiya, tana asibiti wai jininta ne ya hau" Amina ta ce "Subhanallah, me zai sakawa Fadla hawan jini a wannan shekarun? Bari na ɗauko mayafina mu tafi tare" Daddy ya ce "A'a, na san Zainab tana can, kar muje ta ɗaga mana hankali a Asibiti, na kiraki a waya" Cikin damuwa Amina ta ce "Shikenan, Allah ya bata lafiya" Daddy ya amsa da Amin ya fice. Tuni Hajiya Zainab ta gayawa su Turai Fadila babu lafiya, dan duk sun zo dubata ma, Hajiya Salma ta ce da safe Salim ma zai zo dubata. Duk yadda Mummy tayi da Fadla a kan ta gaya mata meke damunta, amma taƙi faɗa. Tara saura na dare, sannan Daddy ya isa Asibitin, sai da ya fara tsayawa a ofishin doctor Aliyu, ya kuma yi masa bayanin abin da yake damun Fadila, sai dai Daddy ya bar batun hawan jinin nata a matsayin ko gado ne tunda yana da shi, Amma Aliyu ya tabattar masa da tana da damuwa ne. Bayan sun gama magana da doctor Aliyu, ya tafi ɗakin da Fadila take. Da sallama ya shiga ɗakin, ya hangi Fadilan a zaune a kan gadon, tana shan abu a kofi, wanda su Hajiya Salma ne suka kawo mata. Ya ƙarasa gaban gadon Fadilan cikin kulawa yake faɗin "Sannu Fadila, ya jikin naki?" Fadila ta ce "Da sauƙi" "Allah ya ƙara afuwa, amma meke damunki haka har kika sa shi a ranki, jininki yake hawa?" "Ya wuce baƙin cikinka, yadda ka watsr da mu ka kama matarka, saboda tsabar rashin mutunci tun rana tana Asibitin nan, amma aka kirka kaƙi ɗaga waya, sai yanzu da waccan shashashar ta baka dama sannan ka zo Asibitin, saboda tsabar wulaƙanci ba dole jininta ya hau ba" Hajiya Zainab tayi maganar lokacin da take fitowa daga banɗakin cikin ɗakin. Alhaji Ahmad bai tanka mata ba, ya sake kallon Fadila ya ce "Yanze meye yake miki ciwo?". Ta ce "Kaina ne, kuma da sauƙi sosai" Hajiya Zainab ta cigaba da yi masa tijara. "Ai wallahi kaji kunya, baka da wani basaja da zaka yi mana, dan abin kunya 'yarka na Asibiti baka damu ba, balle ka zo ka ganta saboda kana naniƙe da mace" Daddy ya miƙe ya ce "Fadila Allah ya ƙara Afuwa, zan dawo da safe kin ji ko?" Ta ɗaga masa kai alamar to, ya fice ya bar ɗakin da Fadilan take. Duk da Daddy ya tafi, amma Hajiya Zainab ta zauna ta cigaba da mita. Yana komawa gida, Amina ta dinga yambayarsa ya me jiki, Ya tabattar mata jikinta da sauƙi, ƙila ma a sallameta gobe in Allah ya kaimu. Washegari da safe Fadila tana ta mitar ita a sallameta, amma Doctor Aliyu ya ce sai yamma zai sallameta. Wajen ƙarfe tara na safe, ciwon kai ya fara tasowa Fadila, ta fara koke-koke. Sai da aka yi mata wata allura sannan ta ɗan samu releif. Amina kuwa da wuri ta tashi, tayi girki ta tashi Daddy ta ce ya tashi suje su duba Fadila, amma Daddy ya ce ba zai je da ita ba, sai dai tayi haƙuri idan sun dawo sai ta dubata. Yauma dai da Daddyn yaje Asibitin, sai dai bai samu tarbar arziƙi a wurin Hajiya Zainab ba, haka ya gama zamansa ya tashi ya tafi. Yazid kuwa bayan yaje makaranta, lectures ɗaya aka yi, ya tafi domin ya sake duba Fadila a Asibiti. Sai dai ko da yaje Asibitin, still kallon banza ya samu daga mahaifiyarta, ita kuwa Fadila murmushi ta yi masa ta ce "Ya na ganka makarantar fa?" "Zuwa nayi na ganki sai in tafi, na kira wayarki bata shiga" Ta ce "Ai wayar tana mota, jiki yayi sauƙi sosai, za a sallameni ma in sha Allah" Hajiya Zainab ji take kamar ta ce Yazid ya tashi ya tafi, sai wani iyayi yake yana larabci, yana fama da wasu tsumman kayansa. Salim ne yayi sallama shi ma yazo duba Fadila, tana ganinsa taji kan ta ya kuma sarawa, wani baƙin ciki da takaici suka tokare mata a ƙirjinta, ko sunansa bata ƙaunar ji, balle tayi arba da shi. A tsaye ya gaida Hajiya Zainab, ya ja kujera ya zauna. Wani irin banzan kallo yake yiwa Yazid, wani abu Fadila take gani a idon Yazid, da ta kasa fassara ko menene. Yazid ya tashi yayi musu sallama ya fice. Hajiya Zainab ma ta fita ta basu guri. Salim ya kalli Fadila ya ce "Baby ashe baki da lafiya?" A fusace Fadila ta ce "Ban sani ba, mara mutunci kawai, ka saka mahaifiyata ta dinga fushi da ni, wai ina wulaƙantaka, idan ina wulaƙantaka idan ba zaka iya ba, ai sai ka rabu da ni, na meye zaka kaini ƙara?" Kwantar da murya yayi ya ce "Haba amaryata, yanzu dai kiyi haƙuri kwantar da hankalinki, ni gani nayi ma kin wani rame" yayi maganar yana ƙoƙarin zama a gefen gadon da take. A fusace ta ce "Meye haka ne?" Ya ce "Kamar yaya? Naga kina wani matsawa, ba dai ke zan aura ba? Meye dan na taɓa ki, ai ni zan aureki, ke ki gode Allah ma aurenki zan yi, sauran matan da nake kulawa holewa kawai muke, kin san rayuwar turai, irin wannan abun duk cikin soyayya ne kawai" Yayi maganar yana ƙoƙarin rungumeta, hannunsa ɗaya kuma yana ƙoƙarin ɗaga doguwar rigar jikinta. "Wayyo Allahna Mummy" tayi maganar cikin ihu, hakan yasa taji tamkar ana buga mata guduma a kanta. Ba kunya ba tsoron Allah yake ƙoƙarin haike mata, gashi ta kasa ihun saboda azabar ciwon kai, sai kokowa suke. Jin alamun za a buɗe ƙofar ya sanya ya ƙyaleta, Ba tsammani Mummy ta buɗe ɗakin ta shigo, turus tayi tana kallon Salim, ga Fadila da take ta hawaye shi kuma yana tsaye a gefen gadon. Da sauri ya sha jinin jikinsa, ya fara kame kame "Dama gani nayi kamar ruwan baya tafiya, shi ne na gyara mata, bari naje Mummy" Bata kai ga gano meke faruwa ba ta ce masa "Shikenan, ka gaida Salman" Ta mayar da dubanta ga Fadila ta ce "Ke dai kin fiye rakin tsiya, da kin ji ciwo sai kuka?". Fadila bata amsa mata ba, ta goge hawayen fuskarta, ta ɗauko wayarta dake ringing ta saka a kunnenta. Muryar Yazid taji a sanyaye ya ce "Kina lafiya kuwa?" Ta ce 'Eh meye?" "Gabana ne yake faɗuwa, kamar wani abu ya faru da ke, ko yana shirin faruwa da ke" Mamaki ne ya kama Fadila ta ce "Ba abin da ya sameni, kuka nayi kaina yana ciwo" Yayi ajiyar zuciya ya ce "Ina miki sannu, Allah ya sauwaƙe". Ta ce "Amin na gode" Mummy ɗorawa tayi da yi mata mita, a kan ta gaji da wannan kiran wayar da kuma zuwan da Yazid yake yi. Tana cikin maganar doctor Aliyu ya shigo, hannunsa riƙe da bp machine, yana yiwa Fadila sannu. Ya ƙarasa ya duba jikin Fadila, ya tarar jininta ya kuma hawa. Ya kalli Fadila ya ce "Fadila, Ya haka ne? Jininki ya kuma hawa, gaya mini meke faruwa?" Kawai ta fashe da kuka. Doctor Aliyu ya ce "Gama kukan ki gaya mini" Ya dinga lallaɓata yana rarrshinta, a hankali ta kalli Doctor Aliyu ta ce "Mummy ce". Mummy ta ce "Ni kuma?" Aliyu ya ce "Shhh, Mummy ba ruwanki, magana muke yi" "Gaya mini, me Mummyn tayi?" "Zata haɗani aure da wanda bana so, ina ta ƙoƙarin ɓoyewa na danne dan na aure shi hankalinta ya kwanta, amma ya dinga kai ƙarata yana cewa ina masa wulaƙanci, bata bibiyi meyasa bana son shi ba ta daina kulani, ta daina shiga harkata sai yanzu da bani da lafiya sannan ta cigaba da kulani. Bana iya bacci da cin abinci yanzu kuma da yazo dubani" ta nuna musu yadda ya karceta da farcensa a gefen wuyanta a ƙoƙarin sa na saka hannunsa a rigarta. Cikin kuka ta cigaba da magana "Wallahi ni bana son sa, Mummy bana ƙaunrsa wallahi, tuntuni ma bana son sa, har hoton jikinsa yake turo muni, duk baki bincika ba kike ta fushi da ni" tayi maganar cikin kuka. Mummy ta ce "Subhanallah, ai ni baki mini wannan bayanin ba" Doctor Aliyu ya ce "Gaskiya Mummy baki kyauta ba" Numfashin Fadila ne ya fara yin sama, ta ce "Aliyu kaina ciwo yake" Aliyu ya ce "Bari nayi miki allura" Mummy ta zauna kusa da ita tana ta rarrashinta. Ya sake yi mata allurai tayi bacci. Ƙarshe dai ba a sallami Fadila ba sai washegari, da yamma. Ana sallamarsu gida suka wuce, Mummy tana ta tunanin yadda zata ɓullowa lamarin Fadila, saboda har ga Allah tana son rayuwar Fadila, ƙarshe ta yanke shawarar saka Daddy ya mayar musu da kuɗin auren a mazaunin shi ne baya son auren. Bayan komawarsu gida kuwa, 'yan dubiya suka dinga zuwa duba Fadila, ciki har da Yazid, Yusra da Abdul. Amina ta takura Daddy cewar ya tashi ya rakata sashin Fadila ta dubata, dan bata son fitina, kar taje ita kaɗai suyi faɗa da Mummy. A falo suka tarar da Hajiya Zainab tare da Yazid tana ce masa "Mun gode, zaryar haka ta isa dan Allah, mungode Allah ya saka da alheri, idan kuma abin da kayi mata ne kake son a biyaka ka faɗa, wannan sintirin ya ishe ni idan ba wani abun kake nema ba". Jikin Yazid yayi sanyi, har ya kai ƙofa Amina ta kira sunansa. Tsayawa yayi ya waiwayo, yana ganin Amina yayi murmushi, ya gaisheta ita da Daddy. Daddy ya ce "Waye wannan ɗin?" Amina ta ce "Ɗan makarantar su Fadila ne, kwanaki shi ya kawo ga gida ma" Daddy ya ce "Allah sarki, mun gode sosai kaji Allah yayi albarka" Yazid ya amsa da Amin, ya fita. Daddy ya kalli Amina ya ce "Jeki ki dubata" ya mayar da idonsa kan Hajiya Zainab bayan ya sallami Amina, ya fara ja mata kunne a kan wulaƙanta mutanen da ke zuwa gidan. Sallama Amina tayi ta shiga ɗakin Fadila, Fadila taƙi amsawa ta shiga bin Amina da kallo. "Fadila ya ƙarfin jiki kuma?". "Ban sani ba, algunguma ƙila ma so kika yi ace na mutu, to da raina, abin da kike fatan bai faru ba. Kar kuma ki sake zuwar mini ɗaki bana son munafunci bana ƙaunar ki, bana ƙaunar ganinki". "Fadila ba zuwa nayi muyi musayar yawu ba, dubaki na zo yi, kuma harshenki ya kiyayi furta miyagun kalamai a kaina, ni ɗin nan da kike gani sa'a ce da ni, ina zaune Allah zai kawo abin da zan fanshe wannan wulaƙancin da kike yi mini, ni da gyatumarki muke gwarawa dan haka ki bar shiga hurumina, tun ban saki a aji na koya miki darasin da na koya wa babarki". "Dalla fita ki bani wuri, ke kin isa kiyi mini wani abu, banza 'yar ƙauye duk wata larura da ta sameni da koma menene, duk ba silarki bane, daga zuwa cin arziƙi kin aure mana uba, kuma in sha Allah sai kin koma gidan matsiyatan da kika fito". Har Amina ta yunƙura za tayi magana, taji muryar Alhaji Ahmad a bayanta tana faɗin "Na gode Fadila, ba ita kike yiwa ba ni kika yiwa, kuma ki sani taki uwar ma da take ɗoraki a kan wannan aƙidar daga gidan matalautan ta fito, na gode sosai" Ya ja hannun Amina, suka bar ɗakin. A falo ma Hajiya Zainab ce take tata tijarar, duk da Amina bata san yadda suka yi da Daddy ba. A falo suka zauna yana bawa Amina haƙuri, a kan abin da Fadila tayi mata, amma tayi murmushi ta ce kar ya damu ba komai. Daddare Fadila ta saka Mummy a gaba tana tambayarta "Mummy, to yanzu wani hukunci kika yanke a kan maganata da wannan Salim ɗin?" Mummy ta ce "Ai ban san mutumin banza bane, kuma tun da ba kya son sa dole a bar maganar, babanki zan bawa kuɗin ya mayar musu, bari ya shigo". Kasancewar yau Alhaji Ahmad yana wurin Hajiya Zainab, tun da magariba suka yi sallama da Amina. Washegari da safe, Alhaji Ahmad ya shiga wurin Amina, sai dai taga fuskarsa babu walwala sam. Cikin damuwa Amina ta ce "Yallaɓai lafiya kuwa?" Cikin matuƙar ɓacin rai ya ce "Yanzu abin da Zainab tayi ta mini adalci kenan? Ta san Fadila bata san yaron nan, amma ta kawo shi ta ce shi take so ta aura. Na karɓi kuɗinsu an tsayar da Magana, amma tana gaya mini wai Fadila ba ta so shiyasa take rashin lafiya, ta san da haka amma ta sa na karɓi kuɗinsu aure bai fi wata ya rage ba, kalen ta zubar mini da mutunci a idon mutane". Amina tayi murmushi, tare da ƙulla wani abu a ranta, a fili ta ce "Zauna yallaɓai" Alhaji Ahmad ya zauna yana huci. "Gaskiya idan har ka mayar da kuɗin nan, mutncinka zai zube, sannan kuma bai kamata a yi mata auren dole ba, aure ba zai yiwu da ƙiyayya ba, amma a wannan karon ya zama dole kayi playing role ɗinka na uba, ka nunawa Hajiya Zainab da Fadila kaine a saman su, bai kamata koda yaushe sai abin da suke so ba,. Yakamata a hukunta su saboda gaba". Cikin damuwa ya ce "Meye abin yi? Ni yadda zan tunkari mutanen nan ne ya dameni, tun da ba zan mata auren dle ba," Amina tayi murmushi ta ce ga wata shawara........ (WACE SHAWARA KUKE TUNANIN AMINA ZATA BAYAR MUJE ZUWA) AYSHERCOOL 08081012143LITTAFIN KUƊI NE, MAI BUƘATA NA IYA TUNTUƁATA A KAN LAMBAR WAYATA 08081012143 73 Daddy ya yarda da shawarar da Amina ta bashi, saboda tsabar takaici ko Abinci bai ci ba, dama Hajiya Zainab ko ya kwana a wurinta ko bai kwana ba, a wurin Amina yake cin abinci. Sai da ta bashi ya ci ya ƙoshi sannan ta bari ya fita. Khalil kuwa bai ma san Fadila tayi rashin lafiya ba. Yana nan yana ta ƙoƙarin ganin yadda zai kwantarwa da Hafsa hankali a kan tafiyar nan da Mummy ta sanya yayi ya bar Hafsa. Shi kansa ba a san ransa ba. Ya dinga rarrashin Hafsa yana kwantar mata da hankali, a zahiri ta nuna masa bakomai amma ƙasan zuciyarta babu daɗi, tana son kasancewa da mijinta, su samu shaƙuwa da fahimtar juna, amma Hajiya Zainab ta zo ta gindaya masa wannan sharaɗi, tana ji tana gani, haka Khalil ya tsallake ya koma aiki ya barta, aikuwa yana tafiya ta dinga kuka, saboda zaman da suka yi yana bata kulawa sosai da sosai. Alhamdilillah, Fadila ta ɗan warware daga rashin lafiyar da take yi, taji daɗin jikinta saboda magungunan da take sha, tana ganin yadda Salim ke kiranta a waya, amma taƙi ɗagawa ta share shi, ganin taƙi ɗaga wayar ya sanya ya koma tura mata saƙonnin amma shima Fadila taƙi amsawa. Gaba ɗaya Fadila jira take taji Mummy tace mata an mayar da kuɗin Aurenta da Salim, amma taji shiru. Gaza jurewa tayi, taje ta samu Mummy a sashinsa, Mummy na ganinta cikin kulawa ta ce "Fadila ya jikin naki ne?" A hankali ta ce "Mummy da sauƙi" tayi maganar tana zama a kusa da Mummy. Ta kalli Mummy ta ce "Mummy, haryanzu fa Daddy bai ce komai ba, ga lokaci na cigaba da ja, kuma sai faman damuna yake a waya, dan Allah Mummy kiyi wani abu a kai mana" Mummy ta ce "Kiyi haƙuri Fadila, bana son nayi wani abu da zai sanya Hajiya Salma ta ji haushi a ne, nafi son na nuna mata cewa mahaifinki ne ya nuna baya so. To kuma kinga dai yadda nake fama da shi a kan abubuwa a cikin gidan nan, a duniya abu idan ba wanda ya shafi waccan banzar Yarinyar bace ba, baya ba shi muhimmanci ko kaɗan, amma kiyi haƙuri zan cigaba da yi masa magana, ki yi blocking ɗin lambarsa, zan hura masa wuta dole ya san abin yi, amma daga yau idan abu yana dmaunki kamata yayi ki mini magana mu tattauna". Fadila ta langaɓe kai ta ce "Mumm, ba ƙin saurarata kika yi ba, kawai ki ka fara fushi da ni ba" Mummy ta ce "Shikenan, koma dai menene yakamata ki dinga sanar da ni, kuma fa kawai ɓoye miki nayi ban gaya miki ba, nifa na raina kuɗin nan da suka kawo miki na aure, dan dai kawai kar nayi magana ne, abu yazo ya zama jangwam, amma ai kin fi ƙarfin dubu ɗari, ni Hajiya Salma ta bani mamaki, da ta iya bari aka kawo wannan ɗan kuɗin, nayi shiru ne dai kawai ban yi magana ba" Fadila ta ce "Mhmm, ai shiru dai kawai nayi dan kar na ɓata miki rai, amma ko ba komai a tsiyace ma na zaci ko 200k za a kawo, amma duk matsayin Ubana wai aka kawo mini 100k saboda wulaƙanci sai kace 'yar talakawa". "Koma dai menene idan aka mayar musu da tsiyarsu saje can su ƙarata" Suka cigaba da hira suna tattaunawa. Tun da Khalil ya koma wurin aiki kuwa, Hafsa take rashin lafiya, amma tunda suke waya bata taɓa gaya masa ba, a ƙalla a rana sai suyi waya sama da sau huɗu, sai dai bata yadda suyi Video call sai da daddare, saboda kar ta ɗaga masa hankali da rashin lafiyar da take yi. Ko waya tayi da Mama, ita ma baya gaya mata ga halin da take ciki, ko gaya mata batun komawar Khalil da Mummy ta sa shi a gaba ya koma bata gaya mata ba, saboda bata son ta dinga tayarwa da Maman Hankali, tana murna tayi aure, ta fara kai mata ƙorafi. Ko tambayarta da mama tayi, lokacin da tazo gidanta, ya zamanta da uwar mijinta, sai tace mata lafiya lau babu wata matsala. Ga rashin lafiya, ga tsananin kewar mijinta da take damunta, bata taɓa tunanin haka take matuƙar ƙaunar Khalil ba sai da ya tafi ya barta ɗin nan. Shi ma a nasa ɓangaren, haka yake fama da kewarta, yana son ta kasance a tare da shi, yadda zasu sake sosai ya mantar da ita irin wahalar da ta sha a rayuwa a baya, amma Mummy ta hana. Babban abin da yake tsoro, bai hana idan ya gama gininsa ya nemi ta koma can Mummy ta hana ba. Duk da hakan, Hafsan ita ce take kwantar masa da hankali tare da yi masa nasiha a kan su yi wa Mummyn biyayya hakan ne kawai zai sanya su ji daɗin rayuwar aurensu. Kusan kwanaki biyar kenan, Alhaji Ahmad bai yi magana a kan mayar da kuɗin auren Fadila ba, gashi har tana shirin komawa makaranta, kuma Hajiya Salma nata mitar yadda abubuwa suke gudana game da auren nan da ake shirin yi. Har Falon Amina Hajiya Zainab taje ta iske Daddy, yana zaune yana kallon labarai, Amina kuma na kusa da shi tana tsifar kai. Babu ko sallama taje ta tsaya musu a ka, Amina dai bata ko ɗaga kai ta kalleta ba, Alhaji Ahmad ne ma ya dubeta ya ce "Lafiya?" "Lafiyar kenan, wai kuwa Ahmad kana tsoron Allah kuwa kana tsoron Azabarsa? Kai yanzu gaba ɗaya wannan Yarinyar ita ce a gabanka, abin da take so shi ne a gabanka ka tattarani ka watsar da ni da 'ya'yana?" Daddy ya ce "Ita ce a gabana, tun da nima ba tayi watsi da lamarina kamar yadda kika yi ba, sannan ban gane in da maganarki ta dosa ba". "Ai dama ba zaka gane ba, magana nake a kan kuɗin auren nan, nace maka ka mayar musu da kuɗinsu Fadila bata son yaron nan, amma kayi burus su kuma suna can suna shiri" Daddy ya kauda kansa ya ce "Lokacin da kuka yanke zaku haɗasu ai baku yi shawara da ni ba, baki bari nayi playing role ɗina na uba ba, da nace zan yi wani abu a lokacin, cewa zaki bani da mutunci ban kyauta miki ba, dan haka yadda kuka haɗa abinku suka kawo kuɗi, sai ki koma ku warware su zo su karɓi abin su". A fusace ta ce "Wallahi yanzu na sake tabattar da 'ya'yan naka ma baka ƙaunarsu, tayi maka asiri ta rabaka da su" Amina kuwa haushi ya kamata ta ce "Ai asirin ma iyawa ne, kema ki yi yayi mana". Daddy ya ce "Meenal, kar in kuma jin bakinki" Amina ta kashingiɗa da kujera ta cigaba da tsifarta hankalinta a kan Tv. Hajiya Zainab ta ce "Yanzu ka gwammace jinin Fadila ya cigaba da hawa, ta rasa ranta kayi mata auren dole saboda son zuciyarka?" Daddy ya ce "A'a, saboda son zuciyarki dai" "Kaga, zaka mayar da kuɗin nan ne ko kuma a'a" "Ba zan mayar ba, tun da ku kuka kawo shi a matsayin wanda zata aura, ni ba zan zubar da mutuncina a idon duniya ba". "Kai har wani mutunci ne yayi maka saura a idon duniya, ai tun daga lokacin da ka auri wannan 'yar tsatsitsiyar a bar, ba kunya babu tsorn Allah ka dinga yawo da ita a gari, kuka gama watsewa a titi, ai tun daga nan kayi asarar wani abu wai shi mutunci. Ka fifita son ranka a kan yaranka, zakaga abin da zai faru ka cigaba kar ka fasa, ka cigaba da ƙona muni rai" Bai sake tanka mata har ta fice, a hankali ya ce "Kinga halin matar nan ko Meenali, ba zata canza hali ba" Amina ta ce "Rabu da ita, kayi abin da nace maka kawai, a nan zaka tabattar mata da kaine gaba da ita. Kuma hakan ne zai sanya yaranka su san menene rayuwa. Amma idan aka cigaba a haka, ko wanda take so ɗin ta kawo daga baya, idan ya aureta yadda mahaifiyar ta ke yi maka ita ma haka zata yi a nata gidan, kuma ka san dai mazan nan na ƙarshen zamani, ba kowa ne zai ɗau hakan ba" Ya jinjina kai ya ce "Haka ne, hakan za ayi da ni suke zancen" Fadila kuwa na ɗakin Mummy, tana jiranta ta zo ta bata feedback na yadda suka yi da Daddy. Sai dai Mummyn na shigowa ta kalli fuskarta ta san babu nasara, cikin karaya ta ce "Mummy ya kuka yi?" Ta girgiza kai ta ce "Ke lamarin ubanki yafi ƙarfin tunanina yanzu, mirsisi yaƙi amincewar" Ɗora hannu Fadila tayi a ka ta fashe da kuka, hakan ya saka kanta sarawa ta durƙusa a wurin tana kuka ta ce "Ni wallahi Mummy bana son shi, zuciyata zata iya bugawa, dan Allah Mummy kiyi wani abu a kai, kin san bana son shi, Wallahi na aureshi mutuwa zan yi, zuciyata zata fashe" Mummy ta ce "Ke Fadla nutsu mana, kinga an yi auren ne, kin manta baki da lafiya sai kin kuma kwanciya tukuna". Ai kan ta rufe baki, Fadila ta riƙe ƙirji tana kuka, ta fara numfarfashi sama sama. A gigice Mummy ta riƙeta tana faɗin "Ke Fadila meye haka?" Bata amsa mata ba ta cigaba da kuka tana dafe ƙirji. A gigice Mummy ta ɗai wayarta ta kira Daddy, kamar na zai ɗauka ba sai kuma ya ɗaga. A ruɗe ta ce "Kayi sauri ka zo, jikin Fadila ya tashi" Da sauri ya ajiye wayar, ya fito ya nufi sashin Hajiya Zainab, yana zuwa ya tarar da Fadilan a kwance, tana kuka ga hannunta ta riƙe ƙirjinta. Hajiya Zainab ta kalleshi kamar zata fashe da kuka ta ce "Ka gani ko? Kaga abin da ka ja ina neman na rasa 'ya ta, wallahi duk abin da ya sameta kaine kuma na zan yarda ba" Ya kalli Fadila da ke numfarfashi ya ce "Duk dan saboda ba kya san auren ne kike nema ki halaka kanki?" Tayi shiru tana kuka ba tare da ta furta komai ba. Ya dubeta ya ce 'Ba kya son auren ko?" Ta ɗaga masa kai alamar eh. "Shikenan naji, dama ku kuka kawo shi, aka ce na aura miki, zan mayar musu da kuɗin aurensu, amma bisa sharaɗi, yau muna Alhamis, na baki nan da zuwa ranar Alhamis ki kawo mini mijin da zaki aura, idan ba haka ba zan ɗau matakin da ya dace". Cikin rashin Fahimta Hajiya Zainab ta ce "Ban gane me kake nufi ba". "Ai da hausa nayi maganar, ba da wani yaren ba, dan haka kin ji, idan kun ƙi na zaku ƙi ganin hukuncin da zan yi ba" yana gama maganar ya bar ɗakin. Hajiya Zainab ta ce "Ƙaryar banza, ba wani abu da zai iya yi, sannu ya kike jin jikin naki, ko mu tafi Asibiti?" Fadila ta girgiza kai tana lumshe ido, saboda a hankali ta ji ƙirjin nata yana saki. Sai dai Maganar Daddy ta shiga kai komo a kanta, ita ina taga wani saurayi yanzu da zata ce zata aura, dan farin jinin samari kam akwai su Allah yayi mata su, amma duk wulaƙanci take yi musu ba ta saurarensu, babbar damuwar ta da bata san wane irin mataki Daddyn zai ɗauka ba kamar yadda ya ambata. Har zuwa dare gaba ɗaya ta kasa sukuni, dan sai da Mummy ta kira Doctor Aliyu ya zo gida, ya kuma dubata, ya yi mata allurai tukuna. Yau Daddy yana wurin Hajiya Zainab, sai dai tun da ya shiga wurin nata take dakon, taji ya ce mata wani abu a kan batun kuɗin auren Fadilan, amma ta ji yayi shiru bai ce mata komai ba, yau har ƙofar bedroom ɗinta ta bari a buɗe, amma ya ƙi shiga yayi zamansa a falo Kamar yadda ya ta saba yi masa, ta rufe ƙofarta a Duk lokacin da yake wurinta sai dai ya kwana a falo. Tana cikin bedroom ɗin tana shirin kwanciya, sai ga kiran Hajiya Salma, sai da gabanta ya faɗi, amma ta dake ta ɗaga. "Zainab yanzu ni zaki wulaƙanta a duniya, duk alkhairi da nake miki a rayuwa, ni zaki ciwa mutunci" Cikin pretending Hajiya Zainab ta ce "Innalillahi wa innalillahi raji'un, Salma meyafaru ne?" "Dole kice mini maiyafaru mana, ɗazu mijinki saboda tsabar wulaƙanci da tozarci, ya zo har gida ya samu baban Salim, wai maganar auren nan ayi haƙuri, wai Fadilan bata so" Hajiya Zainab ta ce "To Salma ni ya zan yi, kwanciyar Asibitin nan da tayi ne, da aka ce jininta ya hau likita ya cewa babanta wai wani abu ne yake damunta, da aka matsa sai cewa tayi auren nan ne bata so, ba yadda ban yi da ita ba, amma ta tubure shi kuma kin san halinsa a kan 'ya'ya ya ce dai a haƙura da auren nan, in an kwana biyu ta warware idan tana so sai ayi, na kaɗa na raya amma kasancewar yana ji da shegen taurin kai sai yayi mini banza, ashe mayarwa yayi, aikuwa dole na san abin yi dan ba zan bari zumuncinmu ya ɓaci ba" Hajiya Salma ta ce "A'a, ai aikin gama ya riga ya gama, shi ma Salim ai ɗan gata ne, babansa ba zai bari a wulaƙanta shi ba, Allah ya haɗa kowa da rabonsa". Hajiya Zainab ta ce "Aikuwa ba za ayi haka ba, daga Fadilan har baban nata basu isa ba, ina yabonta salla zata kasa alwala zata watsa mini ƙasa a ido?" Hajiya Salma ta ce "Ai fa sai dai muyi haƙuri Zainab, a tara a gaba, mu dai tun da mun riga mun shirya, zamu saka ya nemo wata ya aura*. "Dan Allah kuyi haƙuri Salma, ba yadda na iya ne" "Bakomai kar ki damu sai da safe" Bayan katse wayar, Hajiha Zainab tayi ajiyar zuciya ta ce "Alhamdilillah, na kashe wannan wutar!". Washegari bayan sallar asuba Hajiya Zainab ta tafi ɗakin Fadila ta tashe ta. Fadila ta tashi tana kallon Mummy tana mamakin dalilin zuwanta a yanzu. "Fadila, ya mayar musu da kuɗinsu, na nuna mata cewar kawai ke kika nuna ba kya so, shi ya sanya ya mayar  musu da kuɗin". Cikin sanyin jiki Fadila ta ce "Amma Mummy, nifa hankalina a tashe yake". "Tashin hankalin me? Ba kin ce ba kya so ba kuma an mayar musu da kuɗin, menene kuma?" Fadila ta ce "Mummy baki je me Daddy ya ce ba? Wai nan da Alhamis na kawo mijin aure ko kuma ya ɗau matakin da ya ga dama ba, Mummy ban San me zai iya yi ba, kuna kinga ni bani da wani wanda zance shi ne tsayayye" Tsaki Mummy ta yi ta ce "Ke dalla can, idan har ina nan ba abin da zai iya yi miki, ki kwantar da hankalinki, ki cigaba da walwala, kinga exams zaki fara ki manta kawai barazana ce yake yi". Fadila tayi ajiyar zuciya ta ce "Shikenan Mummy, na Gode sosai da goyon bayana da kika yi". "Bakomai, Allah ya ƙara miki lafiya". Fadila tayi murmushi ta ce "Amin Mummyna" Alhaji Ahmad kuwa da hanzari yaje sashin Amina, ko tashi ba ta yi ba, ya tasheta. Amina ta tashi tana tura baki ta ce "Meyasa ka tasheni?" "Breakfast zaki haɗa mini" Cikin shagwaɓa ta fara tuttura ƙafa, tana tura baki ta ce 'Amma ba a wurina kake ba fa, baccin nan yayi mini daɗi sosai" Hannu biyu ya saka sauketa daga kan gadon, ya janyo hannunta zuwa kitchen yana faɗin "Oya a dafa mini koma menene". Amina ta ce "Tom na ji, amma sai ka tayani aikin, wallahi kwanan nan bana son yin aiki" Murmushi yayi ya ce "Faɗa mini da mai zan tayaki? In mun gama kayana nake son ki shirya muni, ƙarfe sha biyu fa zan tafi Lagos" da sauri ta kalleshi ta ce "What?! Meyasa?" "Baƙi zan yi da gaggawa, akwai buƙatar in halarta shiyasa" "Yanzu tafiya zaka yi ka barni?" Ya ce "A'a, ba daɗewa zan yi ba, da na gama abin da nake, zan dawo ki gaya mini suwa kika yanke a biyawa umara zamu tafi" "Mhmmm zan yi missing ɗinka, ni bana son ka tafi" Yayi wannan ya ce "I will miss you too" tare suka yi girkin, Suka gama ya karya ta shirya masa kayansa suka fito falo, har sashin Hajiya Zainab ya je, ya kuma yi mata kashedi a kan abin da ya faɗa na Fadla ta fito da miji, sannan yayi mata sallama a kan cewar zai je Lagos, ko ƙurar da ya biyo ya shigo sashen nata bata kalla ba, balle ya sanya ran zata kula shi. Bayan fitarsa ita ma ta shirya ta fice zuwa gidan Hajiya Salma, da sake lallaɓata a kan fasa auren da aka yi. Ko da Fadila taje makaranta, 'yan ajinsu suka yi ta mata sannu, ciki har da Yazid da yafi kowa murnar ganinta cikin ƙoshin lafiya. Bayan ta koma gida da Yamma, Hajiya Zainab ta ɗauki Fadila suka je gidan Khalil. Duk da halin rashin lafiya da Hafsa ke ciki tayi ƙoƙarin sakin fuska ta karɓe su, amma Hajiya Zainab tayi burus, ta dira wa Hafsa wulaƙanci da cin mutumci, tare da zageta wai 'yar matsiyata. Abin ya yiwa Hafsa ciwo, amma ba yadda ta iya haka tayi shiru, dan ta fara tunanin anya ba zata rabu da Khalil ba, ko dan ta huta da wannan wulaƙanci, amma tayi tunani idan ta rabu da shi ta koma ina? Kuma kwata-kwata yaushe tayi auren ma. Fadila har da cewa idan tayi zuciya, ta koma gidan matsiyatan iyayenta, ta rabu da Khalil. Suka gama cin mutuncinsu suka tafi, bayan tafiyarsu ta sha kuka sosai da sosai, ga rashin lafiya ga kaɗaici da damuwa, dan bata shige-shigen gidan kowa, kullum tana gida. Da daddare Khalil ya kirata, suka yi waya suka gama, amma ba ta gaya masa rashin lafiyarta ba balle zuwan su Hajiya Zainab. Kwanaki huɗu da tafiyar Daddy, Amina bata jin daɗin komai, taje ta saka Hajara ta soya mata dankalin hausa, ta ɗauki wani ta feraye ta dawo falo ta zauna tana cin ɗanye. Hajara ta soya dankali ta kawo mata, ta dinga yi masa cin yunwa, ta wuni tana ci tana shan ruwa. Washegari Amina ta tashi da ciwon ciki da amai, saboda dankalin da ta yiwa cin yinwa jiya. Daddy ta kira a waya, ta sanar masa zata je Asibiti ulcer na damunta, ya bata izini. Ta shirya ta saka Zakiru ya ɗauketa domin kaita Asibiti, sai da suka zo wurin unguwar gidan su Khalil, ta tuna sun kwan biyu ba suyi waya da Hafsa ba, dan haka ta ce "Zakiru, dan Allah muje gidan Khalil ko a gurguje mu gaisa". Ba musu Zakiru ya wuce da ita gidan Khalil. Ta ɗan jima tana knocking har ta fidda ran za a buɗe, dan ta kira lambar Hafsa amma bata ɗaga ba, har ta juya kuma sai Hafsa ta buɗe gate ɗin. Murmushi tayi da taga Amina tayi mata sannu da zuwa. Amina ta kalleta da mamaki ta ce "Hafsa lafiyarki ƙalau kuwa?". Hafsa ta ce "Me kika gani? Mu shiga daga ciki dai". Suka shiga falon, Amina na cigaba da kallon Hafsa. "Ya gida ya Daddy?" "Daddy baya nan, Hafsa kalli yadda kika yi wani iri, duk kin rame ko wani abun ne ya haɗaki da Khalil ɗin?" Hafsa na shirin yin magana, amai ya taso mata, ta tashi da sauri ta bar falon, Amina ta tashi ta bita, ta taimaka mata ta gyara jikinta. "Hafsa menene?" Hafsa ta fashe da kuka, Amina ta ce "Hafsa, kar dai auren naki ne ya samu matsala daga yi?" Hafsa ta girgiza kai ta zauna, Amina ta zauna, Hafsa ta ce "Ban gayawa kowa ba sai ke, Khalil ya koma aiki, tun da ya tafi bani da lafiya, bai ma san bani da lafiya ba, amma Mummy ta zo Ita da Fadila suna ta ci mini mutunci, zuciyata tana raya mini na haƙura da auren nan" Ran Amina yayi mummunan ɓaci, tana tunanin Hajiya Zainab wace irin macece. Cikin tausayawa Amina ta ce "To kin ci Abinci ne?". "A'a bana iya cin komai, komai naci amai nake yi, a kwance nake wuni wataran saboda jiri a kwance nake salla". Amina ta jinjina kai ta ce "Amma kike zaune a gida? To kin ganni dama asibiti zani nima, bari na dafa wani abun ki ci, mu tafi Asibitin tare. Hafsa bata musa ta ba, Amina ta shiga Kitchen da kanta, ta dafa musu indomie mai yajin tsiya da dankalin turawa, da kifi. Suka zauna suka ci tare, suna ci suna zare ido ita da Amina, saboda azabar yaji, amma daɗinta suke ji a haka. Hafsa taji daɗin zuwan Amina sosai, dan ji tayi ciwon nata ya ragu. Hafsa ta shirya suka tafi Asibiti tare, sai da a motar ma, amai ta cigaba da yi saboda warin fetur. Can Asibitin da Daddy yake ganin likita suka tafi.  Yadda likita ya yiwa Hafsa tambayoyi, ya tabattar ta galabaita ta daɗe tana ciwo, aka yi mata gwaje gwaje, ga ciki ga jininta yayi ƙasa ga malaria da tayi mata mummunan kamu. Likita yayi faɗa sosai da sosai, a kan yadda Hafsa tayi zamanta a gida tana fama da ciwo. Ita kanta Amina ranta ya ɓaci, aka kwantar da Hafsa, aka dinga saka mata ruwa da allurai. Yadda likita ya zazzage musu haka Amina ta kira Daddy a fusace tana faɗa, ta zayyane masa duk abin da Hajiya Zainab tayi, da yadda ta tarar da Hafsa, dan ita ta manta da tata larurar ma gaba ɗaya. Daddy kansa bai ji daɗin abin da ya faru ba, ya ce "Ban da abin ki Meenali, ai bani na kar zomon ba, amma zan ɗau matakin da ya dace, Allah ya baki haƙuri". "Eh amma ai matarka da ɗanka ne suka yi, kuma yakamta ayi gaggawar takawa Fadila burki a kan abin da take yi" "Na ji, ina nan zuwa garin gobe in Allah ya kaimu zan dawo gida, na gama abin da nake a nan ɗin. zan yi hukuncin da ya dace". Ruwa aka dinga ƙarawa Hafsa ba ƙaƙƙautwa, saboda ko Abinci bata iya yi, ko ruwa ta sha sai tayi amansa. Daddy ya kira Khalil ya dinga yi masa faɗa a kan tafiyar da yayi, ya bar Hafsa a wannan halin. Khalil ya tabattar masa da cewa Mummy ce ta saka shi. Daddy ya ce Lallai lallai, ya dawo gida yazo ya kula da matarsa. Sai Yamma sannan Amina ta koma gida, bayan Mahaifiyar Hafsa ta iso Asibitin. Kamar yadda Daddy ya faɗa, washegari ya dawo gida, ya dawo ya tarar Hajiya Zainab na can nata yawon, Fadilan kuma bata dawo daga makaranta ba. Khalil kuwa a gigice shi ma ya dawo gida, jin batun Hafsa bata da lafiya tana asibiti. Sai dai babban abin da ya faranta masa, jin batun cikin Hafsa. Amina  ta zaunar da Daddy, ta sake gaya masa abin da Hajiya Zainab ta dinga zuwa tana yiwa sirikar ta, kuma ta dinga ziga shi a kan lallai ya aiwatar da shawarar da ta bashi. Sai dare sannan Hajiya Zainab ta dawo, ba ta san ma Daddy ya dawo gidan ba. Suna zaune ita da Fadila, suna shan tea a falonta, sai ganin Alhaji Ahmad tayi. Kallo ɗaya tayi masa, ta kawar da kanta ta cigaba da abin da take yi. Fadila ce ta ce "Daddy sannu da zuwa" Bai amsa ba, ya nemi wuri ya zauna. Ya kalli Hajiya Zainab ya ce "Labari ya iskeni, a kan duk abin da kika aikata, ban san wace irin zuciya ce ba a ƙirjinki Zainab, Allah ya shiryeki. Bari in gaya miki, wallahi muddin kika sake shiga sabgar gidan Khalil, ko ki kayi dalilin rabuwar auren nan, wallahi ki tabbatar kin salwantar da naki auren ne" Da mamaki ta kalleshi ta ce "Ni kake gayawa aurena zai salwanta? To idan ya salwanta sai me, kuma Khalil ɗana ne, dan haka ina da ikon yanke duk wani hukunci a kansa, dan haka shiga sabgar aurensa yanzu na fara, idan ka ga dama ma, a yanzu ma ka sakeni sai menene? Uwar me ka tsinana mini a zamana da kaia banda zunzurutun baƙin ciki da nadama, babu abin da nake yi, aikin banza da na wofi kawai" "Ni kike gayawa aikin banza da na wofi?". "Na faɗa, ka sakeni a yanzu idan ka ga dama, 'ya'yana ne ba zasu rayu da matsiyata ba, kuma sai na yiwa Khalil aure da wadda nake so" tana gama maganar ta miƙe ta shiga bedroom. Cikin jin zafin abin da Hajiya Zainab tayi masa, ya kalli Fadila ya ce "Ina maganarmu, na ki kawo mini mijin da zaki aura?" Fadila tayi shiru tana sunkuyar da kai. Ya jinjina kai ya ce "Da kyau". Washegari Juma'a, bayan Daddy ya dawo daga sallar juma'a, Fadila ma dawowart kenan daga school, tayi wanka ta sauya kaya, sai ga Daddy tare da Amina a ɗakinta. Daddy ya kalli Fadila cikin hanzari ya ce "Tashi maza ki haɗa kayanki, ki haɗa duk abin da zaki iya buƙata" Cikin rashin Fahimta ta ce "Daddy ban gane ba, ina zamu?" "Ki tashi kiyi abin da nace, kin tsaya kina tambayata". Dariyar mugunta Amina take yi mata, a bayan Daddy. Miƙewa Fadila tayi tana bin Daddy da kallo. Cikin tsawa da bin umarni ya kuma maimaita mata abin da ya ce. Nan ta sauke akwati, tana zuba kayanta cikin damuwa, tana son tambayar Daddy, amma a rikice take saboda yadda ya haɗe rai. Akwati ɗaya ta zuba ɗan abin da zata buƙata, ya kalleta ya ce "Ki zuba kayan da zasu wadaceki malama" nan da nan jikinta yayi sanyi ta cigaba da ɗibar kaya hawaye na gangarowa daga idonta, ga Mummy bata nan balle taji ba'asin hakan. Ta zubo kayanta a akwatuna biyu, babba da ƙarama. Daddy ya miƙa mata hannu ya ce "Bani wayoyinki" Cikin rawar murya Fadila ta ce "Dan Allah Daddy ina zamu?" Tayi maganar tana bashi wayoyin. "Biyoni a baya, idan mun je kya gani" Daddy yayi gaba cikin sauri. Amina ta kalleta tayi murmushi ta ce "Ina fatan zaki ɗau darasi a sabuwar makarantar da zaki shiga nan gaba kaɗan, kuma ina miki fatan ya zame miki izina game da cin mutuncin mutane saboda suna talakawa. Idan ke a rashin mutunci kika ƙware to Yau zan tabattar miki da GABA AKWAI GABANTA!!! Ayshercool 08081012143LITTAFIN NAN NA KUƊI NE, MAI BUƘATA YA TUNTUƁENI A KAN LAMBAR WAYATA. 08081012143 74 Muryar Daddy suka jiyo yana cewa "Ki ɗago ƙafa ke nake jira" duk da yadda hawaye ke bin fuskarta, hakan bai hana Fadila watsawa Amina harara ba, Amina bata nuna ta damu ba, tayi mata dariya, Fadila kuma tayi gaba tana jan akwatuna. Ko da suka fito falo, kallon sashin Mummy take kallo, tana ganin ko Mummy zata fito, amma ina Mummy bata nan tana can nata gantalin. Motar Daddy ta shiga, ta saka akwatunanta a cikin motar ya fara driving yana yi yana duba wayarsa. Cike da karaya ta kuma marairaicewa ta ce "Dan Allah Daddy ina zamu?" Shiru Daddy yayi mata, ya cigaba da tuƙi, haka ta ka bakinta tayi shiru, don ganin Daddy ba shi da niyyar ya bata amsa. Ɗaya gidan nasa suka nufa, yana zuwa aka buɗe masa gate ya shiga, yayi parking ya fita daga motar. Ya dubeta ya ce "Fito" Fadila ta fito tana rarraba ido, kamar bata san gidan ba. Ya dubeta ya ce "Wuce ki shiga ki jirani zan dawo". Salo-salo Fadila ta nufi cikin gidan, kamar wadda aka yiwa mummunan baki. Daddy kuma ya ɗaukar wata motar ya sake fita. Zaman dirshen Fadila tayi a falon, tana ta tunanin meke shirin faruwa ne, me Daddy ke shirin aikatawa haka? Gashi ya karɓe mata wayoyinta balle ta kira Mummy. Haɗe kai tayi da gwiwa tayi shiru tana nazari. Fadila na nan zaune a cikin falon, aka yi sallar la'asar, ta tashi ta lalubi banɗaki, ta shiga tayi alwala tayi sallar la'asar, wata irin yunwa ce ke sakatar cikin Fadila, ta dudduba ta samu Fruit a fridge ta ɗan ci. Wasa-wasa har magariba Daddyn bai shigo ba. Tun tana saka ran Daddy zai dawo, har ta fidda rai ta cigaba da zama, ta fara saka ran ko dai Daddy ke niyyar hukuntata, shine ya kawota nan dan ya hukunta ta. Bayan sallar isha'i, sai ga Daddy ya shigo. Zumbur ta miƙe tsaye tana jin sanyi a zuciyarta, ganin Daddy ya shigo. Ya kalleta ya ce "Oya taho mu tafi" a ranta Fadila taji cewar ko gida zasu koma? Amma da tuna uban akwatunan da Daddy ya sanya ta haɗo sai kuma jikinta yayi sanyi. Amma ga mamakinta, sai taga bai nufi hanyar unguwarsu ba, ya ɗau wata uwar doguwar tafiya a titi. Kallon Daddy tayi, tana son tayi magana, amma taga ya haɗe rai babu annuri a kan fuskarsa. Haka ta cigaba da saƙe-saƙe a cikin zuciyarta. Tun Fadila tana jiran taga Daddy yayi burki, har ta zubawa sarautar Allah ido. Wata irin unguwa suka shiga, wadda tudu da kwarinta kawai sai da ya sanya Fadila jiri. A ƙofar wani ɗan ƙaramin gida Daddy yayi parking. Ya buɗe motar ya ce "Ta fito". Fadila ta fito tana ƙarewa unguwar kallo, ko ina duhu. Daddy ya kalleta ya ce "Kwaso akwatunan naki". Cikin mamaki take bin Daddy da kallo, tare da fatan ba a nan zai barta ba. Ta kwaso akwatin tana rarraba ido, da jiran ganin me Daddy zai yi. Kai tsaye Daddy ya nufi ƙofar gidan, Gidan sai ƙamshin sabon fenti yake. Wayarsa ya ɗauko, ya ɗan danna ya kara a kunnensa, ya ce "Gamu mun zo". Mintuna kaɗan sai ga wani ya fito,tana jiyowa wa zata gani? Yazid ne ya fito daga cikin gidan, cikin shadda ash riga da wando yayi kyau sosai. Mamakine ya hana Fadila magana sai kallon Yazid da take yi. Yazid ya durƙusa har ƙasa, ya gaida Daddy. Daddy ya amsa sannan ya ce "gamu mun zo". Yazid ya ce "Bismillah ku shigo" wani irin ƙuntataccen tsakar gida ne, bai wuce kayi taku biyar ba, zaka ƙure shi. Yazid yayi musu jagora wani ɗan mitsitsin falo. Daddy ya kalli Yazid ya ce "To Alhamdilillah, Malam Yazid ga matarka nan na kawo maka" saroro Fadila tayi ta kasa gane kan maganar da Daddy yake yi. Daddy ya kalleta ya ce "Ke kuma ga mijinki nan, na ɗaura miki aure da Yazid, bisa gaza cika sharaɗinmu da kika yi, kuma sai da na bincika na ga ya dace da rayuwarki. Idan kin ga dama ki zauna kiyi masa biyayya idan kin ga dama kuma ki bijire masa. Idan kika sake kika taka mini gida ba tare da na neme ki ba, ban yafe miki, idan kika bari Yazid ya kawo mini ƙararki da kina saɓa masa sai na baki mamaki, kiyi masa biyayya kamar yadda kike mini. Yazid ban yadda ka bata waya ba, kar ta kira kowa sai idan ni na neme ta. Idan kin ga dama ki zauna ki riƙe aurenki, in kin ga dama kuma kiyi masa irin halin da ki ka tashi ki ka ga ana yi a gidanku". A ruɗe ta tashi tana kallon Daddy cikin kuka ta ce 'Daddy, meysa zaka mini auren dole ka kawoni nan, wallahi ba zan iya rayuwa a nan ba, bana son shi wallahi, dan Allah Daddy ka rufa mini asiri". Daddy ya ce "Fadila kema 'ya ce kamar kowa, dole ki cirewa kanki cewar ke kinfi ƙarfin wani, kuma ki sani ba zan miki zaɓin tunmun dare ba, kamar yadda kuka yi ke da mahaifiyarki da farko ba, ga sadakin nan naira dubu talatin" ya ajiye mata a kan ledar ɗakin da ke falon, da ko kukeru babu sai guda ɗaya. Fadila ta sake fashewa da kuka, ta yinƙura zata bi Daddy, amma Daddy ya daka mata tsawa, wanda sai da ta razana. A rayuwarta bata tunanin Daddy ya taɓa yi mata irinta. Daddy ya kalli Yazid ya ce "Allah ya sanya muku albarka" Daddy yayi gaba ya fice, Fadila ta zauna a ƙasa ta dinga wani irin kuka kamar zata shiɗe. Yazid kallonta yake yi, shi kansa ya san wannan al_amari za a sha gwagwarmaya, sai dai ya san duk abin da ya faru, wani iko ne da tsari na Ubangiji, dan yadda abubuwan suka wakana har ya mallaki Fadila, akwai mamaki. Cikin tausayawa ya nufi in da Fadila take, ya kwantar da muryarsa ya ce "Dan Allah Fadila kiyi haƙuri, ki Kwantar da hankalinki" "Dalla rufe mini baki, banza kawai mara imani, wallahi bana ƙaunarka Yazid kuma ba zan zauna a wannan matsiyacin gidan ba, sai na koma gidanmu ba zan zauna a wannan ƙuntatattacen gidan ba" Yayi ajiyar zuciya ya ce "Shikenan, naji na kuma yadda, amma dan Allah kiyi haƙuri, kinga dare ne yanzu, ga abinci in zubo miki ki ci?" "Ba zan ci ba, kana tunanin nayi maka kala da wadda zata karɓi wani abu daga hannunka?". Miƙewa tayi ta nufi hanyar fita tana kuka, amma Yazid ya miƙe cikin zafin nama, ya sha gabanta ya ce "Dan Allah kiyi haƙuri ki zauna, da safe in Allah ya kaimu sai mu san abin yi, kinga baki san kan unguwar nan ba, zaki iya ɓata" Zubewa Fadila tayi a ƙasa ta cigaba da gunjin kuka, Yazid yaje ya kulle ƙofar gidan, ya dawo ya kalleta ya ce "Fadila kin yi salla ko zaki yi? Ki zo na nuna miki in da zaki kwanta" "Dalla kaga malam ka rabu da ni, ka fita sabgata kan na yi maka rashin mutunci" haka Yazid ya ƙyaleta, ta dinga kuka haka ya zuba mata ido. Ƙarshe yaje yayi alwala, ya zo ya tada salla, yana kallonta, ta gaji da kukan,  ta jingina da akwatunanta, ta yi bacci. A hankali Yazid ya tashi, ya shiga ɗan ƙaramin bedroom ɗin da ke ɗauke da makekiyar katifa, sak madubi da sip mai biyu, ya ɗauko wani ƙaton bargo, sabo fil ya zo ya lulluɓeta da shi, ya kunna maganin sauro ya koma gefe ya kwanta yana kallon in da take kwance tana bacci tausayinta ya mamaye zuciyarsa tare da tunanin yadda aka yi ya auri Fadila. Hajiya Zainab kuwa tun da ta dawo, bata bi ta kan komai ba, ta shiga sashinta, tana zuwa ta rage kayan jikinta, ta shiga tayi wanka. Ta dawo falo cikin bada umarni, ta kira Hajara ta sanya ta kawo mata abinci. Amina kallon Hajiya Zainab kawai take yi, da bata san meke faruwa ba sai auna Abinci take yi a cikinta, tsarguwa tayi da kallon da Amina ke yi mata tayi. "To mayya, kurwata tafi ƙarfin ki munafuka" Amina tayi wani irin murmushi ta ce "Ko mayyace ni, bana ci irin kurwarki ba, in ci masifa da jaraba". "Ai shiyasa nake sake nanata miki, banza 'yar ƙauye". "Eh na ji na gode sosai, 'yar birni". Ta ƙarasa maganar tana cigaba da yiwa Hajiya Zainab dariya. Hajiya Zainab bata tashi farga da cewar Fadila bata dawo gida ba, sai magariba. Sashin Fadilan ta nufa, ta duba amma bata ga Fadila ba. Ta dawo falo ta ɗau wayarta, ta kira Fadila amma wayarta ta shiga ba a ɗagawa. Tun tana kiran wayar tana jiran Fadila ta amsa, har ta fara ƙosawa tare da mitar ina Fadila ta ajiye waya bata ɗagawa kuma babu wanda ya san in da ta tafi. Wasa² har isha'i babu Fadila babu dalilinta, nan hankalinta ya sake tashi, ta kira wayar Yusra ko Yusran ta san in da Fadila take, amma ta ce rabonta da Fadila tun shekaranjiya a online. Hajiya Zainab fa ta diririce, ta shiga kiran Alhaji Ahmad, amma shima baya ɗaga wayar. Wajen ƙarfe tara na dare da rabi na dare, sai ga Daddy ya dawo. Sai dai Hajiya Zainab bata san ya dawo ɗin ba. Amina na ganin Daddy tayi murmushi sannan ta ce "Yallaɓai, ya aka yi ne? Sannu da zuwa". Daddy ya ce "Alhamdilillah, na kaita sai dai tana ta  bori". Amina ta ce "Bakomai, zata saba ne, ni nayi imani da Allah tana son sa, komai zai zama tarihi in sha Allah, ka kwantar da hankalinka" Daddy yayi murmushi ya ce "Dama ban ɗaga hankalina ba, na yarda da nagartar yaron". Hajiya Zainab ce ta banko musu cikin bedroom tana zare ido. Ya kalleta ya ce "Lafiya?" "Ai dole ka tambayeni lafiya mana? Tun da baka damu da idan ka dawo ka neme ni ko 'yar ka ba?" "Meyafaru?" "Fadila. Bata dawo ba na kira wayarta tana ringing bata ɗagawa, na kiraka a waya amma ka share baka ɗaga ba". Daddy ya ce "Wayarce a cikin mota, batun Fadila kuma kar ki damu, ki kwantar da hankalinki". Cikin rashin Fahimta ta ce 'Kamar yaya in kwantar da hankalina ban san in da 'ya ta take ba?" "Ai na ce ki kwantar da hankalinki, ni na san in da take kar ki damu" "To ka gaya mini tana ina?" "Tana nan lafiya" yayi maganar yana cire babbar rigarsa. "Wai ban gane tana lafiya ba, ina ka kai mini 'ya ta?" "In da ya dace, kuma bani wuri ina son na huta" ya bata amsa. "Wallahi ba in da zani, sai ka gaya mini in da ka kaita". Ya ce "Aikuwa sai ki ta tsayuwa" Ya rage kayan jikinsa ya shige banɗaki ya barta. Amina ta kalleta ta ce 'Dan Allah ki ɗan bani wuri, zan cire kaya ina son na kwanta". A fusace ta ce 'Idan a kan ki nake sai ki sauke ni, tun da wurinki na zo" Amina tayi mata shiru, ta wuce ta ɗaura towel ta cire kayan jikinta, daga ita sai towel tabi bayan Daddy zuwa toilet. Buɗe baki Hajiya Zainab tayi, tana ganin salon barikanci da iskanci a wurin Amina, sun ma mayar da ita wata mara amfani a wurin. Zuciya ce ta kwasheta ta je ƙofar banɗakin tana duka kamar zata ɓalla ƙofar. "Ka fito ka gaya mini in da 'ya ta take, macuci wanda bai san darajar kansa ba" ta dinga dukan ƙofar iya ƙarfinta. Banza suka yi mata, har ta gaji da bugun, ta koma gefe ta tsaya tana huci. Sun ɗauka ta fita suka fito tare shi da Amina, suka tarar da ita a tsaya tana ta kumbura wuya. Tana ganin sun fito, ta kuma kallon Alhaji Ahmad ta ce "Nace ka gaya mini in da ka kai mini 'ya ta" Daddy ya ce "Zainab, nace kiyi haƙuri ki Kwantar da hankalinki, amma ki sani Fadla tana cikin kwanciyar hankali, da sannu zaki san in da take" Amina kuwa wucewa tayi gaban mudubi tayi zamanta, ta fara shafa manta. Tana jin yadda suka cigaba da fafatawa, tayi kamar ba ta san suna wurin ba, suka gama tashin hankalin su, Hajiya Zainab ta fice daga ɗakin. Daddy ya tako ya dawo kan gadon da Amina ke kwance, shi ma ya hau ya ce "Am sorry Meenalina, duk an ɓata miki rai ko?" Ta ce "A'a" Ya ce "Yauwa, ya maganarmu?" Amina ta ce "Wace maganar?". "Maganar zuwa umara, ina son mu kuma komawa duba matar Khalil, ina son mu koma Lagos a gobe in Allah ya kaimu, idan ba haka ba zata sakani a gaba a kan lallai sai ta san in da Fadila take, idan kuwa ta sani ba zata bari ta zauna ba, sai ta san yadda zata kashe mata auren". Amina ta ce "Amma akwai buƙatar ta san inda take, ka san uwa ce hankalinta ba zai taɓa kwanciya ba". Daddy ya ce "A'a, nima na san zata shiga damuwa, amma ba zan bari ta sani yanzu ba, tayar mana da hankali zata cigaba da yi, ki ƙyaleta kawai". Amina ta ce "Shikenan" "Yanzu dai gaya mini, suwa kika yanke a biyawa" Amina tayi murmushi sannan ta ce "Da farko ina son a biyawa Babana, sai Zakiru sai kuma ƙanin mahaifin Hajiya Zainab sai kuma mai gadin Family house ɗin ku, sai kuma ina neman alfarmar ka biyawa mutum uku da suke da buƙata a family ɗinku, ko da maƙotanku ne, tun da na san a familynku babu wani mai ƙaramin ƙarfi da za a biyawa". Murmushi Daddy yayi, ya ce "Allahu Akbar, abin da yake ƙara mini ƙaunarki rashin son zuciyarki, yanzu har da ƙanin mahaifin Hajiya Zainab a wanda kike so a biyawa, ita da ko da wasa bata taɓa sawa ko biyar na bawa wani nata ba sai dai ƙawaye" Amina ta ce "To Daddy meye a ciki? Allah dai ya ƙara maka arziƙi da kwanciyar hankali mu ci mu bayar" "Amin Babyna, ina alfahari da ke masoyiyata ina ƙaunarki sosai da sosai" yayi maganar yana janyota jikinsa. Ita ma murmushi tayi, ta ce "Nima ina sonka sosai Sweetheart". Washegari da safe, Amina tare da Hajara, suka shiga Kitchen yin girki, sam Amina bata nunawa Hajara ƙyama saboda tana matar gidan, sai ma kyautatawa da take nuna musu, domin bayan aurenta da Daddy yayi, har ƙarin albashi ta sanya yayi musu. Ta dafa abin da zasu karya, da kuma abin da zasu kai wa su Hafsa Asibiti. A dining Amina taje ta shirya abinci, ta koma sashinta da nufin tayi wanka ta tashi Daddy, su karya su tafi dubiyar, saboda da Yamma zasu bar gari. Sai dai me tana zuwa bedroom ɗin nata ta tarar da Hajiya Zainab tana ta zazzagawa Daddy masifa. A fusace Amina ta ce "Nifa gaskiya na gaji da shigo mini ɗaki da kike yi kai tsaye, ki tafi can ki dinga jiransa idan ya zo wurinki kuyi wadda zaku yi, ni ba zan iya jure in kallonki kina cin mutuncin mijina a gabana ba" Hajiya Zainab ta kalleta ta ce 'Ki ka ce mijinki?". Amina ta murguɗa baki ta ce "Eh mana, ko baki ji bane ba, mijinmu ko ma in ce mijina, tun da dai ke kin sallama mini shi". Kallon banza Hajiya Zainab tayi mata ta ce 'Eh kece mayyar namiji, in dai shi ne kije kiyi tayi, a fito mini da 'ya ta kawai, yauwa". Daddy ya ce "Zainab na gaji da wannan rashin mutuncin naki da wulaƙanci". Mummy ta ce "Ai rashin mutunci da wulaƙanci, da kanka kayi cinikinsa ka saya, dan haka dole ka jure shi, ka gaya mini in da 'ya ta take". Daddy ya ce "Ki je, zan yi wanka na karya, Dutse na kaita zanje na ɗaukota idan na gama shirina" Wata masifar ta dira da bala'i, a kan me za a kai mata 'ya Dutse. Saboda ta ƙyaleshi, ya lallaɓata ya ce yanzu zaije ya taho da ita. Amina ta daɗe ba taga azababbiyar mata kamar Hajiya Zainab ba. Bayan yayi wanka ya karya, ya shirya shi da Amina, suka fice. Asibiti suka fara zuwa wurin Hafsa, Khalil ne ya kwana tare da ita, yana jiran Maman Hafsa ta zo, shi kuma ya koma gida. Yana ta kula da ita kamar ya mayar da ita ciki. Yanzun ma yana zaune a gefen gadonta, yana rungume da ita, yana shafa gashin kanta yana mata hira, hannunta kuma ɗauke da drip. Su Daddy na shigowa Hafsa tayi sauri ta rabu da jikin Khalil. Murmushi Daddy yayi ya zauna, suka gaisa yana mata sannu. Amina ma sannun ta shiga yi mata tana yi mata ya jiki. Hafsa ta amsa mata da sauƙi, so take ma a sallame su. Khalil ya ce 'Babu mai sallamarki, sai kin warke". Amina ta miƙo musu fulas, ta ce xGa abinci nan na kawo muku". Khalil yayi murmushi ya ce "Mun gode sosai Anty Amina". A nan Daddy yake gaya masa batun tafiya umara, da kuma waɗanda ya biyawa. Khalil ya ce "Gaskiya Daddy kayi dabara, mussaman biyawa ƙanin babnsu Mummy shi ma, zai ji daɗi wallahi". Daddy ya ce "Ai Antynku ce tayi wannan tunanin, har da Zakiru duk zamu tafi, albarkacin haka har ita Hajara zamu tafi, sun daɗe suna maana aiki a gidan nan, yakamata a mutuntadu, kai kuma idan kuka gama jinyar ka nutsu ka biya muku kai da matarka. sai dai Lagos zamu tafi mu anjima, kai zan bawa gabarar sanar da wanda za a biyawa, da kuma biya musu saboda wani dalili nawa". Amina ta ce "To waye ya ce kace nina ce a biya musu" Daddy ya ce 'Ai yabon gwani ya zama dole Aminatu'. Khalil ya ce "Daddy godiya suke, Anty Amina Allah ya ƙara lafiya da nisan kwana" Amina tayi murmushi ta ce "Amin" Daddy ya ja Khalil suka fice daga ɗakin, Amina kuma ta zauna suka cigaba da hira da Hafsa. A nan Amina ta bata labarin abin da yafaru na aurar da Fadila da Daddy yayi ba wanda ya sani, sannan ta ce wa Hafsa ko Khalil karta gayawa. Daddy kuwa a waje ya sanar da Khalil cewa da zarar Hafsa ta warke, sannan ya gama abin da ya sa shi ɗauki Hafsa su koma Abuja tare, kar ya kuma barinta ita kaɗai, idan ya so su zane a gidansa na Abuja zuwa ya kammala nasa. Khalil ya amince, suna nan Maman Hafsa ta zo, suka gaisa tayi musu godiya sannan suka yi musu sallama suka tafi. Yazid kuwa tun Asuba ya tashi Fadila, amma tayi mursisi taƙi tashi, ba ita ta tashi ba sai shida saura, lokacin ma Yazid bai dawo daga masallaci ba, ga wata irin yunwa da take tatalar cikinta, dan rabonta da Abinci, tun Fruit ɗin da ta ci jiya. Tashi tayi a hankali, ta nufi hanyar fita daga gidan, sai dai ta tarar da ƙofar a rufe. Ta koma falon ta zauna ta takure jikinta, cikinta na cigaba da ƙugi. Bakwai saura Yazid ya shigo gidan da sallama. Banza tayi masa bata amsa ba, ya shigo falon ya zauna a kusa da ita ya kalleta ya ce "Ina kwana?" Tsaki tayi ta kawar da kanta gefe. "Hmm, me kike so ki ci?" A fusace ta ce "Ban sani ba, kaga malam ka tashi ka mayar da ni gidanmu" Yazid ya ce "Meyasa?" "Ban gane meyasa ba? Saboda ba zan zauna da kai ba, nafi ƙarfinka nafi ƙarfin na zauna da kai, ni ba matarka bace, ka tashi ka mayar da ni gidamu, ko ni na tafi". Yazid ya kwantar da muryarsa ya ce "Kiyi haƙuri Fadila, yanzu idan kika fita zaki iya ɓata a unguwar nan, kuma ga furucin da mahaifinki yayi a kan barinki gidan nan ki koma gidanku, kiyi haƙuri ki zauna in cigaba da bashi haƙuri idan ya huce sai muje gidan naku" Cikin kuka Fadila ta ce "Ni ba zan zauna da kai ba, ba ruwanka da furicin da yayi, kasai ka sakeni, ba zan zauna ba". Ya ce "To shikenan, ki bari ki karya tukuna, sai muyi magana" "Babu wata magana da zan yi da kai, kawai k mayar da ni gidanmu, wallahi baka yi mini adalci ba, dan meyasa zaka aureni, ni bana ƙaunarka ban taɓa sonka ba, kuma ban yake maka ba" Shiru Yazid yayi ya dafe kansa, dan ya san an rina an saci zanin mahaukaciya. Suna cikin wannan mujadalar ne, aka yi sallama da ji ka san muryar babbar mace ce. Yazid ya miƙe yana faɗin Hajiya sannu da zuwa shigo. Matar ta sake yin sallama sannan ta shigo falon, da fulas ɗin shayi a hannunta da wani ƙaramin foodflask, ta ajiye tana cewa "Amarya sannu ko, ga kayan kari na kawo muku". Yazid ya ce "Fadila ga Hajiyata, ita ce mariƙiyata uwa ce a wurina" ko kallon in da matar take ba tayi ba, balle ta gaisheta ta kawar da kanta gefe. Yazid bai ji daɗin abin da Fadilan tayi ba, Hajiya ta tashi ta ce 'In dai kuwa wannan ce matar, to Allah ya sauwaƙe ya tayaka riƙo, shiyasa ni sam ban murna da wannan auren ba, yaran masu kuɗi zama da su sai dole". Miƙewa Yazid yayi yana lallaɓa Hajiya dan tayi shiru amma ta ƙi. Fadila kuwa bayan matar ta bi da harara. Haka dai Yazid yayi ta bawa Hajiya haƙuri, ta gama mitarta ta tafi. Ya koma ya cigaba da rarrashin Fadila ta ci Abinci. Hajiya Zainab gajiya tayi da zaman jiran Alhaji Ahmad ya dawo mata da Fadila, ta kira wayar Fadila tun tana shiga har ta daina. Gajiya tayi ta kira Alhaji Ahmad, yana ɗagawa cikin fushi ta fara tambayarsa ya taji haryanzu shiru. Daddy ya ce "Ai nace ki kwantar da hankalinki, tana hannu na gari, Fadila bata Dutse, babu wani abin ƙi da zai sameta kiyi haƙuri ni Yanzu haka ina Lagos ma!!! Ayshercool 08081012143LITTAFIN KUƊI NE, MAI BUƘATA YA TUNTUƁENI A KAN LAMBAR WAYATA. 75 Wani uban zagi Hajiya Zainab ta maka, amma Daddy ya katse kiran ya ƙyaleta. "Ni zaka ciwa mutunci, wallahi baka isa ba, wato ka ajiyeni ka mayar da ni hoto banza, ina jiran ka kawo mini 'ya ta, amma ka zaunar da ni ka ɗau wannan yarinyar mai kama da karuwai ka tafi da ita, to wallahi baka isa ba". Haka ta cigaba da masifa ita kaɗai tana bambami. Yazid kuwa da ƙyar ya lallaɓa Fadila ta ci abinci. Yazid ya kalleta cikin kulawa ya ce "Fadila yakamata na dafa miki ruwa kiyi wanka, mu kuma zaga ki ga gidan naki". Fadila ta yamutsa fuska ta ce "Ina ne gidan, wannan ne gidan? Wannan ai bai yi kama da gida ba". Yazid ya ce "Na ji, amma ki daure ki shiga kiyi wanka ki sauya kayan jikinki" sake takurewa tayi a wuri ɗaya taƙi kallon Yazid. Tana kallonsa ya kwashi akwatunanta, ya kai cikin bedroom ɗin, ya shirya mata kayanta a sip guda ɗaya, ɗaya kuma nasa ne. Ya dawo falon ya wuceta, ya shiga ɗan ƙaramin Kitchen da yake tsakar gidan, ya kunna risho ya ɗora ruwan zafi. Mintuna kaɗan, ruwan yayi zafi, ya juye a bokiti ya sirka, ya dawo ya ce "Dan Allah ki zo ki watsa ruwan kya ji daɗin jikinki" gaskiyar Yazid, tana buƙatar ta watsa ruwa dan gaba ɗaya bata jin daɗin jikinta, dan ko a gida Fadila gwanar wanka ce. Banɗakin da ke tsakar gidan ya kai mata ruwan, ta tarar da banɗakin wani ɗan tsukakke da shi, a ƙuntace ga kan fanfo sai masai pit latrine. Wasu hawayen takaici ne suka zubowa Fadila, ta kalli in da sabon kwandon wanka yake, da soso da kuma sabulu. Haka ta durƙusa tayi wanka, ta zuro kayanta ta fito. Ko da ta fito, Yazid baya nan ya fita, ta shiga bedroom ɗin, ta ƙarewa ɗakin kallo, ƙatuwar katifa ce a ɗakin, sai sip da mudubi, sai wata cupboard ɗauke da uban litattafai na addini da na zamani kamar Library a ɗakin. Taɓe baki tayi, ta buɗe akwatinta, bata ɗauko mayukanta na shafawa ba a ciki. Tsaki tayi, ta tashi ta duba kan madubin ta ga Vaseline, gaba ɗaya warin vaseline ɗin bai yi mata ba, haka ta daure ta shafa. Ta duba ta ɗauki wata 'yar riga me sauƙin nauyi, ta saka ta koma ta nemi wuri ta yi shiru tana tunanin yadda aka yi Yazid ya aureta, da yadda Daddy yayi mata wannan irin maƙasƙancin auren haka. Ta saka hijjabi, tayi sallar azahar, ta idar ta cire hijjabin ta zauna, ta tsunduma duniyar tunani. Sallamar da Yazid yake yi ne ta dawo da ita hayyacinta, ya shigo falon riƙe da ledoji a hannunsa. Kallo ɗaya tayi masa, ta ɗauke kanta zuwa wani wurin daban. Ya shiga Kitchen ya ɗauko plate, ya zazzage mata wata lafiyayyiyar shinkafa da naman kaza. Ya saka mata cokali ya ce "Ga Abinci" "Ni fa ba abincinka nake buƙata ba, ka mayar da ni gidanmu na gaya maka". "Fadila, furucin mahaifinki abu ne mai girma, wanda zai iya yin tasiri a rayuwarki, kiyi haƙuri idan komai ya lafa zan mayar da ke gida da kaina kin ji ki ci Abincinki" "To yaushe zaka mayar da ni?" Yazid ya ce "Da zarar komai ya lafa zan mayar da ke in Sha Allah, amma ranar Monday zamu koma school ko?" Ta kalleshi ta ce "Ni da makarantar nan har abada" "Saboda me?" "Ba zan sake zuwa ba, na gama makaranta" Ya kuma kwantar da murya ya ce "Haba Fadila kin zaɓi kiyi asarar shekarunki da kika fara na karatu?" "To ina ruwanka? Kai kayi asarar su ko ni?" Yayi murmushi ya ce "A'a, ga Abincin". Ba kunya ta karɓe masa Abinci ta fara ci, gefe ya koma shi ma ya fito da ɗan ƙaramin fulask, ya zuba kunu a kofi yayi Bismillah ya fara sha. Bata ci da yawa ba ta ajiye, ta ɗan tsurawa Yazid ido sannan ta ce "Dan Allah meyasa ka aureni, bayan ka son bana sonka?" Murmushi yayi ya ce "Ikon Allah mana, kina mamaki ko? Nima haka nayi mamakin yadda abin ya kasance, amma ki Kwantar da hankalinki dan Allah". "Ba zan kwantar ba" tayi maganar tana hararsa. Haka suka wuni kamar kurame, Babban abin da ya bashi mamaki yadda bata cigaba da yi masa tijara ba, sai tsiwa da hararsa da take ta yi, haka kurum yake yi mata kwarjini, ta kasa cigaba da yi masa rashin mutuncikHausawa suka ce, ba faɗa da malam ba daren) ko da yake ba abin mamaki bane ba, dan Yazid sosai ya duƙufa yake addu'a a kan zaman nasu tare da fatan Allah ya sa ta dangana ta zauna dashi. idan ta ɓangare guda Fadila ta tuna maganar Daddy sai gabanta ya faɗi. Tunani ta shiga yi ko a wane hali Mummy ke ciki yanzu oho. Jikinta yayi sanyi, hawaye ya shiga zubo mata. Cikin kulawa Yazid ya ce "Dan Allah ki daina wannan kukan zuciyata bata so?" Da ɗan ƙarfi ta ce "Kar ta so ɗin, da baka son kukana ai da baka aureni ba". Bai kuma tanka mata ba har zuwa dare, ya kawo mata abinci daga gidan Hajiyarsa. Nan ma ta ci abin ta, tayi sallar isha'i ta nemi wuri a falo ta kwanta. Yazid ya shigo ya kalleta ya ce "Ki shiga ki kwanta, nan akwai sauro sosai" bata ce masa uffan ba, ta tashi ta shiga bedroom ɗin. Kasancewar tana jin bacci sosai, ta kwanta a kan katifar. Can cikin bacci ta waiwaya, taga Yazid yana rage kayan jikinsa, rintse idanunta tayi tana tunanin ko mafarki take yi. Amma ta sake buɗe idonta, taga ya hau kan katifar. Zumbur ta tashi zaune ta ce 'Meye haka?" Yazid ya kalleta ya ce "A ina?". "A ina zaka kwanta?" Yazid ya ce "A kan katifa mana" "Gaskiya ba zan kwana wuri ɗaya da kai ba, ni ban taɓa kwana da wani ƙato a kan shimfiɗa ɗaya ba, kawai ka tashi" Yayi murmushi ya ce "To a ina zan kwanta?". "Ka koma ƙasa ka kwanta" Ba musu ya tashi ya ɗau pillow ya kwanta a ƙasa. Hakan ya sa ta ɗan sake, ta kwanta bacci mai nauyi ya ɗauketa. Idon Yazid biyu, yaji saukar numfashin Fadila alamun tayi bacci, ya tashi tsam ya koma kan katifar ya kwanta a bayanta, ya janyota jikinsa yana sauke ajiyar zuciya, ya saka hanunsa a saitin zuciyarta, ya dinga karanto Alqur'ani yana addu'ar ubangiji Allah ya bata juriya da dangana, dan shi kansa ya san wannan auren na su jarabta ce a gareta, dan bashi da ƙarfin iya aurenta. Ita kuwa jinta a jikin mutum ta zata mafarki take, ta ƙara sakankancewa. Khalil ya shirya, ya zo gida domin gaida Mummy, dan ko ba komai mahaifiyarsa ce. Sai dai ko da yaje, ya tarar da ita bata duk tayi wani iri. Bai samu wata kyakkyawar tarba ba, amma duk da haka bai hana shi cewa "Mummy lafiya kuwa? Meke damunki ne na ganki wani iri?" Mummy duk da a ƙule take da shi, amma ta ce "Ba dole ka ganni a haka ba, kai da ubanka kun haɗa kai kuna yinƙurin ku kasheni, ya ɗauke Fadila ya kaita wani wurin daban sani ba, ya gaya mini Dutse ya kai ta zai ɗaukota, amma tsabar wulaƙanci wai na kira shi a waya, yace mini wai yana Lagos" ta ƙarasa maganar tana fashewa da kuka. Cikin damuwa Khalil ya ce "Mummy dan Allah kiyi haƙuri ki kwantar da hankalinki, ki bi komai a sannu ki daina ɗaga hankalinki, Fadila Daddy ne ya haifeta ba zai cutar da ita ba". Cikin fushi ta dakatar da shi ta hanyar cewa "Kai dalla can rufe mini baki, dama ai kai goyon bayansa dama kake yi, domin kai ma ya tsaya maka ka auri 'yar matsiyata, dole ka goyi bayansa a kan dukkan abin da yake aikatawa, ka kyauta tashi ka bani wuri" Haka Khalil ya tashi ya fita. Zakiru da Hajara kuwa, jin ance za a biya musu umara da Khalil ya sanar musu a zuwansa gidan, suka dinga murna suna jin daɗi, Khalil ya gaya musu Amina ce ta saka a biya musu. Suka dinga murna suna saka wa Amina da iyayenta albarka. Khalil tare da Hafsa suka je Jigawa, suma suka je suka sanar musu yadda aka biya wa wasu umara, har da ƙanin mahaifin Hajiya Zainab. Nan da nan labari ya karaɗe dangi, dan Alhaji Ahmad bai taɓa yi musu alkhairi makamancin haka a rayuwarsu ba. Yazid dai kusan kwanaki biyu suna fafatawa da Fadila, kan ya samu ta ɗan kwantar da hankalinta, dan har hirar arziƙi ta kan shiga tsakanin su, ko da kuwa ba zata amsa masa ba. Yau da safe ya dafa musu tea, ya zo da kayan tea, har da ƙwai. Ya zuzzuba musu ya miƙa mata nata, ta saka hannu ta ɗauka ta karya. Fadila bata aikin komai a gidan nan, Yazid ne yake zagewa yayi komai, daga shara wanke wanke gyaran toilet duk shi ne yake yi, hatta kayan jikinta idan ta cire shi ne yake haɗawa ya wanke, ba abinda ta sani sai dai ta ci ta ƙoshi ta saka shi a gaba tana koke-koke. Ga Yazid yana ta ƙoƙarin sayen duk abincin da ya san zata iya ci. Yanzu ma kukan take yi, tana zaune a kan kujera sai aikin kuka take yi. Yazid ya ƙarasa kan kujerar da take zaue ya zauna a kusa da ita. Tun da Daddy ya kawota gidan nan, wannan ne karon farko da Yazid ya zauna a kusa da ita a ido biyu. Jikinta ne ya ɗau rawa, kamar yadda take yi a baya, idan ya zauna a kusa da ita a school. Haɗe rai tayi ta ce "Dan Allah ka tashi daga kusa da ni" Yazid ya ce "Meyasa? Ya naga jikinki yana rawa?" A fusace ta ce "Idan ba zaka tashi ba, matsa ni na tashi". Yazid ya sake matsawa kusa da ita ya ce "Jikinki da nawa ne, tamkar ƙarfe ne da kuma mayen ƙarfe, jikinki tamkar mayen ƙarfe yake, a duk lokacin da na kasance a kusa da ke, sai jikinki ya fara rawa, kina buƙatar nawa jikin a matsayin ƙarfe, kamar dai haka" ya janyota jikinsa. Aikuwa take jikinta ya daina rawar, sai dai kuma bugun zuciyarta da ya ƙaru, har numfashinta ya fara yin sama. Kasa motsawa tayi, sai shiru da tayi tana kokawa da numfashi. A hankali ya kama gashin kanta da tayi parking ɗin sa. Jin Yazid na neman wuce makaɗi da rawa, kuma gashi ta kasa hana shi, kamar yadda ta taɓa gani a mafarki yau a zahiri hake faruwa, bakin Yazid ne a cikin nata. lokaci ɗaya tayi wata irin zabura ta rabu da jikinsa, ta haɗe rai ta fice tsakar gida ta tafi bakin rariya, tana zubar da miyan bakinta tana tsaki. Ɗan kashingiɗa yayi yana murmushi. Yayi shiru yana tuna farkon ganinsa da ita, zuwa yau da Allah ya sanya cikin ikonsa ta zama matarsa. Ranar da ya fara shiga ajinsu a jami'a, kansa a ƙasa, ya shawo uwar tafiya mai nisa da ƙafarsa, saboda rashin wadataccen kuɗin mota a hannunsa. Yana shiga aji mutum na farko da ya fara sanya idonsa a cikin nasa ita ce Fadila. Ras! Gabansa ya faɗi, ta ƙare masa kallo ta fashe da dariya, amma hakan bai hana shi ganinta ɗauke da wani kyawu na musamman ba, da tun da yake bai taɓa kallon wata mace har ta burgsehi ba, sabgogin gabansa ne suka dame shi. A haka yayi ta'awizzi ya nemi tsari daga sheɗan, amma kamar wasa ƙaramar magana ta nemi komawa Babba, har Alla-Alla yake garin Allah ya waye ya je makaranta dan ya ga Fadila. Komai nata burgsehi yake yi, duk da kasancewarta 'yar wulaƙanci ga izza da girman kai, amma zuciyarsa bata fasa begen Fadila ba. A haka har yayi ta maza ya fara kulata. Duk da da fari bata saurarsa sai wulaƙanci, amma bai gaza ba har zuwa ranar da rashin lafiya ta same shi ta kai shi Asibiti, ji yayi tamkar ya zuba ruwa a ƙasa ya sha dan farinciki. Daga lokacin da suka samu saɓani kuwa, ta ce ita ba kalarsa bace, a 'yan kwanakin nan ko Abinci baya iya ci, har Hajiya sai da ta gane, ta saka shi a gaba da tambaya amma ya ce mata bakomai. Haka rayuwa ta cigaba da tafiya, tare da ƙalubale kala-kala, amma kullum sake jinta yake yi a ransa. Hakan ya sa ya duƙufa da Addu'a, ya san shi ba ɗan kowa bane ba, kuma ba shi da shi. Sai dai yana Addu'a Allah ya cire masa son Fadila a ransa, amma kullum ƙara sonta yake yi. Ranar da Yazid ya kai Fadila gida, Amina ta ganshi sai ta ga yayi mata kama da mutane nagari, duk da kayan jikinsa sun nuna waye shi, amma a nutse yake sosai. Kasancewar Amina ta kan ji Fadila na bawa Mummy labarinsa, kuma ba zata manta ranar da taje ɗakin Fadila ta tarar da ita tana surutan bacci tana kiran sunan Yazid ba, da yadda Fadila ta tayar da jijiyoyin wuyanta a kan Yazid lokacin da ya samu matsala a makaranta. Amina ta gane Yazid yana son Fadila ne, amma Fadilan tana ganin ita ba ajinsa ba ce, amma ko a zahiri sai Amina taga sun dace da aure, duk da Yazid yayi kalar haƙuri, amma Fadila na buƙatar jajirtaccen miji mai ilimin addini, idan ba haka ba duk wanda ta aura zai sha wahala ne kawai, saboda gaba ɗaya bata samu kyakkyawar tarbiyya ba, sai dai duk wannan tunanin na Amina ta san ba mai yiwuwa bane ba, kasancewar an riga an kawo wa Fadilan kuɗi. Amma zuciyarta ta cigaba da raya mata Yazid ya dace da auren Fadila, haka na sai ta tsinci kanta da yi musu Addu'a. Bayan Daddy ya dawo ne, ya ci Abinci ya nutsu, Amina ta sako masa maganar Yazid ta kalli Daddy ta ce "Baby na yi maka laifi fa". Yayi murmushi ya ce "Ai ba kya laifi beutyna, meyafaru?" "Na buɗe ma'ajiyarka na ɗauki shaddoji masu kyau biyu, da kuɗi dubu ashirin nayi kyautarsu wa sirikinka" Ya ce "Duk yadda kika yi daidai ne, ai kayana naki ne, amma wane sirikin nawa kenan?" Amina tayi murmushi tare da gyara zama ta ce "Ina wanda Fadila ta kiraka a waya muna Abuja a kansa, ana shirin ɓata masa jarrabawa wani Yazid?" Ya ce "Ok na tuna" "To ai shine ya kawota" Dasu ya ce "Allah sarki, to babu laifi". "Hmmm ka san wani abu kuwa?" Daddy ya kalleta ya ce "Sai kin faɗa". "Shifa son Fadila yake yi, wasu lokutan na kan ji tana bawa mamanta labarinsa, yana da ilimin addini sosai da sosai, kuma kasan Annabi Sallallahu alaihi Wasallam ya ce idan ɗayanku ya zo neman auren 'ya'yanku, idan har kun yarda da addininsa ku aura masa" "Haka ne malamata, amma ita Fadila ai sun kawo wanda suke so ta aura" Amina ta ce 'Mmm haka ne, amma ka san wanda suke so ta aura ɗin basu taɓa ganinsa ba fa, ina mata sha'awar nagartaccen mutum wanda yake sonta sosai, ba kowa zai iya jure halinta ba, am sorry to say ba ina son muzanta maka 'ya bane ba, amma gaskiya Fadila tana buƙatar auren miji mai sonta sosai mai ilimi da zai iya haƙuri da ita". Daddy ya ce "Maganarki na kam hanya Meenal, amma yanzu muddin na tsiro wannan zancen ba zamu wanyeta ƙalau da mahaifiyarta ba, tunda sun kawo wanda suke so shikenan, duk abin da ya biyo baya ba ruwana" "A'a Daddy, ita matsala kan ta faru ake maganinta, komai ya biyo baya da ruwanka, ai alhakin sama mata miji nagari a wuyanka yake, ba wuyan babarta ba, yakamata a duba sama mata miji nagari, ba kuma lallai ne dan kana mai kuɗi, sai ita ma ta samu mai kuɗi ba, ita rayuwa babu yadda bata juyawa" Daddy ya jinjina kai alamaraa gamsuwa, suka shiga wata hirar. Tun daga ranar Amina ke cigaba da kwaɗaitawa Daddy aurar da Fadila ga mutumin ƙwarai, saboda tana taisayin irin rayuwar da mahaifiyarsu ta ɗora su a kai, muddin ta je gidan wani musamman mutum mara cikakken ilimk da nutsuwa da Wannan halin, to za tayi ta aure ana sakinta ne. Shi kansa Khalil albarkacin auren Hafsa, ya sanya ya fara sauyawa sosai da sosai, duk da ita kanta ba mai son mutane bace ba, amma tana ta nuna masa muhimmancin girmama mutane. Daddy ya fara yadda da maganar Amina, tun bayan yadda Hajiya Zainab ke wulaƙanta shi da cin zarafinsa ko a gaban uban waye. Amina ta kan ce masa "Kaga yadda Hajiya Zainab ke yi maka, Fadla ma haka zata je tana yi a gidan miji, tunda haka ta tashi ta ga ana yi a gidansu, kuma ka san ba kowane namiji ne zai ɗauka ba" Amina bata gaza ba tana roƙawa Fadila, ya bata miji wanda yafi alkhairi da zai zauna da ita saboda Allah yayi haƙuri da hakayenta na banza, amma ita tana fatan ta auri Yazid. Ana haka har kawo rashin lafiya da Fadila tayi, Yazid yake ta zarya a kanta. Zuwa ranar da Daddy ya haɗu da Yazid, Hajiya Zainab tana korarsa, sunansa da Amina ta kira ya sanya Daddy gane shi ne. Dan haka ya sa Amina ta wuce ta duba Fadila, shi kuma yabi Yazid waje. Yazid yayi mamaki da ya tsayar da shi, Daddy ya dube shi ya ce "Yazid mun gode sosai da kulawarka a kan 'ya ta, kayi haƙuri da abin da mahaifiyarta tayi maka" Yazid yayi murmushi ya ce "Bakomai Daddy, ni nayi laifi ma, na shiga matsala a makaranta, Fadila ta kiraka ka warware mini, na so na zo har gida nayi maka godiya amma Fadila ta ce mini ba ka gari" Daddy ya ce 'Wannan ai ba wani abu bane ba, kai ma ɗana ne, bari na baka kuɗin mota" Yazid ya girgiza kai ya ce "A'a ai ina da kuɗin mota Daddy" Daddy ya matsa kusa da shi, ya dafa kafaɗarsa ya zura masa kuɗi a aljihunsa ya ce "Ba a mayar mini da kyauta, na ji irin ɗawainiyar da kake da Fadila na gode sosai ka gaida gida" Bayan Daddy ya koma, a sashin Fadila, yaji yadda take zagin Amina, bayan sun koma sashin Amina ya gama bata haƙuri yake ce mata "Meenal, na daɗe banga nutsatsen yaro da ya burgeni ba kamar yaron nan, yana da dattaku" Amina tayi farat ta ce "Kaga abin da nake gaya maka ko?" Ya ce "Tabbas na gani kam" a ranar ne kuma Hajiya Zainab ta saka Daddy a gaba da zancen sai an mayar da kuɗin Auren Fadila. Amina ta samu wannan damar ta cewa Daddy idan har ya mayar da kuɗin nan ba tare da ya hukunta Fadila ba, haka zasu cigaba da zubar masa da mutunci. Ta bashi shawarar ya sanya Fadila ta fito da wani mijin idan ya mayar da wannan kuɗin, ya karɓi shawararta ya bi, amma Fadila ba ta kawo miji ba, dan haka Amina ta ce yayi bincike a kan Yazid idan har ya yarda da nagartar sa ya aura mata shi. Daddy ya ce "Amma yin hakan kamar nayi mata auren dole ne, tun da ba ita ta kawo shi ta ce ta na so ba" "Ba auren dole bane ba, da bata son shi ba zata saka ka taimake shi ba, yakamata ka hukunta su a kan abin da suke aikatawa". Aikuwa Daddy ya sanya aka yi masa bincike, Yazid ba shi da wata matsala kowa sai alkhairinsa yake faɗa. Sai dai Daddy ya shiga damuwa yana ganin Fadila zata sha wahala, saboda Yazid ba shi da shi, idan har zai aurawa Fadila Yazid sai ya bashi aikin yi. Nan ma Amina cikin kissa ta nuna masa ai hakan ne zai sa tayi hankali, ta gane Cewar a kowane lokaci Allah zai iya karɓe dukiyar kuma shikenan ba zata rayu ba. Daddy yana ta jujjuya maganar, Hajiya Zainab ya shuka masa rashin mutunci, baban abin da ya ƙara ƙular da shi, yadda Hajiya Zainab da Fadila suka je gidan Yazid suka ci wa matarsa mutunci, saboda kawai 'yar talakawa ce, hakan ya sanya ji shawarar Amina ita ce hanyar da zai bi ya hora Fadila. Daddy da kansa ya tafi unguwar su Yazid, kamar yadda ya sa aka yi masa bincike a kan Yazid, ba tare da shi Yazid ɗin ma ya sani ba. Ya saka direbansa yayi masa sallama da Yazid, ko da Yazid yaga Daddy, ruɗewa yayi yana fargabar ko laifi ya yi. Sai dai ganin fuskar Daddyn ɗauke da fara'a, ya sanya ya saki ransa. Daddy yayi masa iso zuwa cikin motarsa, Yazid ya risuna yana haida Daddy. Daddy ya amsa masa sannan ya ɗora da cewa "Yazid na san zaka yi mamakin ganina a gidanku, ba tare da ka san dalili ba, sai dai ba abin mamaki bane ba, kamar yadda na saka aka yi mini bincike a kanka, da irin rayuwar da kake gudanar wa a makaranta, har alaƙarka da 'ya ta na sani, tambaya zan yi maka guda ɗaya, kuma nake son ka bani amsarta tsakani da Allah, kana son Fadila?" Ɗan Jimmm Yazid yayi cikin jin nauyi ya jinjinawa Daddy kai. Daddy ya ce "Yanzu idan na aura maka ita kana da wurin ajiyeta?" A dirirce cikin rashin fahimta Yazid ya ce "Daddy bani da kuɗin aure a yanzu, karatu nake yi bani da tsayayyiar sana'a sai buge-buge kuma Fadila ba ta sona" Daddy ya ce "Amsa kawai nake so ka bani" Yazid ya ce "A'a bani da wurin ajiyeta a yanzu, sai dai a garin su babanmu ina da gona". Daddy ya ce "Kar ka damu, ranar juma'a idan Allah ya kaimu, kaje da magabatanka, babban masallacin juma'a na Dutse zan aura maka ita, sadaki kawai zaka kawo duk abin da kake da shi idan ta tare daga baya ka yi mata, ga dubu ɗari biyar ka rage kayi wani abun, amma daga yau har zuwa ranar ɗaurin aure, kar ka kuskura ta san da wannan maganar" Yazid zai yi Magana, Daddy ya girgiza masa kai, ya ajiye masa kuɗin ya ce yaje ya sallameshi. Tamkar shashasha haka Yazid ya koma gida, yan ganin abin wani irin banbarakwai, yarinya 'yar gata kamar Fadila za a yiwa irin wannan auren?. Ko da Yazid ya sanarwa da Hajiyarsa abin da ke faruwa, Hajiya ta ce bata yarda ba, wataƙila ma Yarinyar wani abun aka ƙunso za a jona masa. Amma ya dinga yiwa Hajiya nasiha tare da nuna a baya ita ta damu da sai yayi aure, ƙila Allah ne ya karɓi addu'ar ta. Ya samu ta haƙura a ranar tayi waya garinsu ta ce a sayar da gonar da Yazid ya gada, a kawo kuɗin zai yi aure. Aikuwa suka haɗo masa da ɗan abin gudunmawa, kowa Yazid ya gayawa zai yi aure sai yayi ta mamaki, me yake da shi da zai yi auren? Da haka aka sai wannan gidan, ya sai wannan kayan ɗakin na hannu a ka gyara su aka zuba. Ranar da za a ɗaura aure ma ya haɗu da ita a makaranta, har hira suka yi, tana bashi labarin yadda ta ji lokacin da bata da lafiya. Yazid yana ta mamakin dalilin babanta na yanke wannan hukuncin haka a kanta. Alhaji Ahmad bai tashi zuwa Dutse ba, sai daf da lokacin sallar juma'a, kuma banda yayyensa sai ƙannen mahaifiinsa su ne kawai suka sani, aka ɗaura aure ya dawo gida. Bayan ya dawo saboda kar Hajiya Zainab ta kawo masa cikas, ya sanya ya ɗau Fadila ya kaita gidan Yazid da kansa.LITTAFIN NAN NA KUƊI NE, MAI BUƘATA YANA IYA TUNTUƁATA A KAN LAMBAR WAYATA 08081012143 76 Cikin ƙosawa ta sake cewa "Ka yi magana mana, ka yi shiru kana kallona" Ya saka hannu ya karɓi hoton daga hannunta, yana ɗan jujjuya shi sanyaye ya lumshe idanunsa sannan ya buɗe su ya ce "Wato Fadila, duk wanda ya rasa uwa yayi kuka. Shiyasa duk da ina murna na aureki, amma bana jin daɗin nesanta ki da Mummy da Daddy yayi ba. Ita uwa wata kyauta ce daga Ubangiji da bata da madadi. Inna wuro kenan, ni kuma ina kiranta Innata. Kamar yadda na samu labari Bafulatana ce ta riga a can wani ƙauye a Jalingon jihar Taraba. Galibinsu fulani ne, sai dai galibinsu ba musulmi bane ba, rigar su Innarmu musulmi ne sai dai basu damu da ilimin addini ba, ba abin da suka sani sai kiwo da kuma tallan Nono. Inna tana da yayye mata biyu sai kuma ita ta uku, suke nan a wurin mahaifinsu. A wurin tallan Nono ne da suke shiga garin Jalingo yi Inna ta ci  karo da ilimin addini ta gane Cewar a duhu suke zaune na jahilci, addinin ma basa gudanar da shi yadda ya dace a rigarsu dan haka ta ɗau ragamar neman ilimi. Idan taje tallan Nono, sai ta zauna cikin makarantu ta ɗau karatu. A lokacin babu wanda ya damu da sai an saka a makaranta kan kaje, ta samu wata makarantar islamiyya tana zuwa. Ta ƙuduri aniyar yin karatun addini mai zurfi. Domin ya zama babbar malamar ita ma ko dan ta dinga wayar da kan 'yan ƙauyen su. Sai dai wannan buri nata bai cika ba, mahaifina ya haɗu da ita, lokacin da suka je rigarsu shi da wani abokinsa sayen shanu. Kasancewar dama ba karatu suke yi ba, kuma 'yan uwanta duk da wuri ake yi musu aure, ya sanya ita ma mahaifinsu ya amince da mahaifina a kan ya kawo kuɗin aure a sanya ƙanƙanin lokaci. Mahaifina yana da mata biyu, mahaifiyata ce ta uku, uwar gidansa Baba Uwani, sai kuma ta biyun Baba Hanne. Babban abin da ya damu mahaifiyata shi ne burinta na karatun addini babu lallai ya cika. Bayan ta auri Mahaifina, ya tafi da ita garinsu da yake cikin Ranon jihar Kano ta tare a gidansa da ke ɗauke da matansa da kuma yaransa biyar da suka kasance duk mata. Kalata ta wurin uba tana nan a raye, amma a lokacin bata garin Rano, tana wani wurin tana aure bayan rasuwar kakana, dan haka babana yana da yayye biyu maza, sai ƙanwarsa mace. Mahaifiyata na da matuƙar haƙuri da kawaici, mabaifina yana sonta sosai da sosai, hakan ya sa ta bijiro masa da son ta koma makaranta, amma ya ce bai yadda ba abin zai zama surutu a gari. Tun da mahaifina ya auro mahaifiyata matansa suka sakota gaba, suke nuna mata ƙiyayya a fili. Idan baya nan suyi ta sakata aiki mai wahala. Mahaifina tsayayyen mutum ne a kan gidansa, yana da rufin Asiri sosai a garinmu an san shi sosai yana da kuɗi, yana dillancin dabbobi har zuwa kudu da maƙotan Nigeria, gidanmu ba a yunwa ko rashin sutura, sai dai ba a damu da ilimi ba sam. A na haka mahaifiyata ta samu juna biyu, sai dai ba wanda ya sani, saboda ba ta laulayi daga ita sai mahaifina suka sani. Babu wanda ya farga mahaifiyata na da juna biyu, sai ganinta kawai suka yi tana naƙuda. Ta yi doguwar naƙuda bata haihu ba, Babana ya ɗauke ta zuwa Asibitin cikin gari, dan duk da rufin Asiri na mahaifina yana cikin karkara da iyalansa. Mahaifiyata ta haifi ɗa namiji, Mahaifina yayi murna sosai da sosai, zai samu magaji, mahaifiyata kuma murnar da take yi, shi ne Allah ya cika mata burinta a kan yaron nan, ya zama masanin addinin Muslunci sosai. Tun da suka koma gida sai ƙananan maganganu, mussaman da suka ga yadda mahaifina ke ta rawar kai a kan haihuwar. Ranar suna mahaifiyata ta roƙi mahaifina ya saka mini suna Yazid. Mahaifina bai sani ba, sunan wani babban malami ne a cikin garin Jalingo da Innata ke zuwa masallacin sa jim wa'azi. Son da yake yiwa mahaifiyata ya sanya shi ya amince, ya sanya mini suna Yazid. 'yan garinsu mahaifiyata sun zo, duk da fulani ne amma wasunsu ba musulmai bane ba suka zo taron suna, mahaifina sai da ya yanka manyan raguna da saniya, aka dinga ci ana rabar da naman a garin, ko baka je suna ba, abu ne mawuyaci ka kasa cin naman da aka yanka da kuma abincin suna. Matan Babana suka kuma mahaifiyata a gaba, abin mamaki a wannan karon har da facaloli, suna mata gorin wai 'yan uwanta maguzawa ne. Mutanen gari suka dinga yi wa matan mahaifina Allah sarki, duk wannan wahalar yaransu mata ne, lokaci ɗaya daga zuwan mahaifiyata ta fara haihuwar namiji, idan babana ya mutu ba zasu samu komai ba. Kasancewar mahaifiyata ba sawa ba fitarwa, ya sanya bata damu da abin da suke yi ba, sannan bata nuna kara a kaina kasancewata ɗan fari. Ba abokan zaman mahaifiyata ba, hatta 'yan uwana yayyena, suke kishi da ni, basa son na raɓesu. Tun ina ƙarami mahaifiyata ke mini kirana da Gwani Yazidu magajin malam. Bayan na fara tasawa, ɗan abin da mahaifiyata ta sani na ilimin addini ta fara koya mini, hatta magana tayi iyaka ƙoƙarin ta bakina ya buɗe da la'ilahailallah. Irin koyon maganar nan na yara, da bisimilla istigfari ta dinga koya mini bakina ya buɗe da su, bana zuwa ko ina ba wanda yake ɗaukata kullum ina tare da mahaifiyata hakan ya sanya nayi saurin iyawa. Shekaruna uku a duniya, Innata ta matsa a kan lallai mahaifina ya kaini makaranta, ya nuna mata nayi ƙanƙanta da yawa amma ta dage, da ƙyar ta bari na shekara huɗu. Ya sakani a wata makarantar addini da take ƙauyenmu, sai dai akwai nisa sosai daga gidamu zuwa makarantar dan haka mussaman yake biya malamin makarantar kuɗi, ya dinga sawa ana zuwa a ɗaukeni ko a dawo dani. Cikin ikon Allah nan da nan, kasancewar ƙwaƙwalwar yarinta, na dinga ɗaukar karatun Alkur'ani da malamin ke tsaye a kaina yana koya mini. Tamkar ɗan ƙaramin ɗansa haka ya mayar da ni, ya kan ɗorani har a kan cinyarsa yana koya mini karatun Alkur'ani. Sai dai ƙiyayyar da ake nuna mini a gidanmu  ta sanya bana sakewa ko a cikin yara, dan ko tsakar gida na fito wasa, sai yayyena su ci zalina. Kullum ina naniƙe da Innata ko ina makaranta. Batun gata a wurin mahaifina ba a magana, duk abin da ya ɗinka sai ya ɗinka mini, ga mahafiyata ma bata wasa da Abincin da zan ci, bata bani cimar banza, gashi da ƙananan shekaruna amma girmamani take saboda sunan da aka saka mini. Daga cikin abin da yake ƙonawa mahaifiyata rai, shi ne yadda abokan zamanta kan kirani da jikan maguzawa saboda a danginta akwai wanda ba Musulmi ba, cikin izgilanci idan ta kirani magajin Malam, sai suce ko kuma jilan maguzawa ba. Sai da na shekara bakwai a duniya, sannan mahaifiyata ta kuma haihuwa, ta sake haihuwar ɗa namiji, aikuwa matan gidan nan tamkar su kasheta, saboda 'ya'ya maza take haifa. aka saka wa jaririn sunan Huzaifa. Duk da Inna ta kuma haihuwa, hakan bai hana ta daina sona ba, tare da cigaba da kula da mu. Ban fi shekaru goma ba, Mahaifina ya fara tafiya da ni wuraren kasuwancin sa, idan yana gari wasu lokutan haka yake zamansa yayi ta hira da ni, yana mini hirar kasiwancinsa duk da ba ganewa na ke yi ba. Ya biya aikin umara ni da shi ya tafi da ni. Hakan ya ƙara rura wutar ƙiyayyata a zukatan matan gidan, kamar su cinye ni su huta. Inna tana yawan gaya masa ya dinga ƙoƙarin yin adalci a tsakanin yaransa bai kamata ya tafi da ni umara ba. Amma buɗar bakinsa ya ce mata "Su 'ya'yan su da nake aurarwa na ke kashe musu kuɗi nawa na taɓa bawa Yazid, ina adalci a tsakanin su" Ƙanina Huzaifa shima ya fara tasawa, sai dai halina da na Huzaifa ba iri ɗaya bane ba. Huzaifa yaro ne mai ƙiriniyar gaske, ga ta'adin tsiya, Inna tana can tana aiki Huzaifa zai fita tsakar gida ya shiga neman magana a tsakar gida. Su kama mutan gidan su kama Huzaifa su yi ta duka suna zagi, abin da yake matuƙar ƙona mini rai, in ga an daki ɗan uwana. Duk rashin maganata ina jin haushin in ga an taɓa gudan jinina. A lokacin na kai shekaru goma sha uku, ina haddar Alqur'ani sosai da sosai, tun Huzaifa na shekara uku nake tafiya da shi makarantar mu. Idan muna gida kuma ina koya masa karatun. Ba zan manta watarana ba, babbar yayarmu da aka yi mata aure tuni, mai suna Yaya Gaji ta zo ita da yaranta. Suna cikin wasa tare da Huzaifa da yaranta, faɗa ya kaure a tsakanin sa da ɗanta Sani, yayyensa suka haɗu suka dinga dukan Huzaifa, da ƙyar na ƙwace shi, na kalli ɗaya daga cikin yayyena da har da su a dukan Huzaifa, abin da ban taɓa ba nace "Allah ya saka maka" ba tsammani na ji saukar mari yayata mariya ta mareni tare da ɗorawa da zagina. Duk ƙanƙantar Huzaifa da yaga an mari yayansa, haka ya fara kaiwa Mariya duka, haka na janye Huzaifa muka bar tsakar gidan. Sai dai ko mintuna goma ba ayi da dukana da Mariya tayi ba, ta ƙone a hannu da ruɗen tuwo, a take ta kurma ihu, ba a ɗau tsawon lokaci ba hannun ya saɓule a take. Mariya ta sha jinya dan kamar hannun ba zai warke ba, shi kuwa Huzaifa kamar an sake tunzura shi kullum rashin jinsa gaba yake yi. Hatta Innarmu suna yawan yin faɗa da Huzaifa, ni kuwa ko Inna bana son na ga tana taɓa mini Huzaifa. Gaba ɗaya hankalina baya kan kasuwancin da mahaifina ke ta janyo ni kan harkar. Ina nan na mayar da hankali a kan karatu na, tare da kula da ƙanina abin ƙaunata. Kwatsam! Matan mahaifina suka tsiro da wani camfi, wai in dai aka taɓawa Inna 'ya'ya sai wata masifa ta afkawa mutum, bayan jikan maguzawa da suke kirana da shi, suka fara ƙoƙarin laƙaba mini maita ni da mahaifiyata. Ina da shekaru goma sha huɗu, na sauke Alƙur'ani hadda, malaminmu ya fara batun a turani makaranta cikin gari, domin samun cigaba da karatuna na addini. Mahaifina ya fara iƙirarin karatun ya isa haka, yana son ya sakani a kan kasuwancin sa sosai, amma mahaifiyata ta cigaba da lallaɓa mahaifina, a kan ya bar ni na cigaba da karatun. Son da yake yi mata ya sanya wasu lokutan, baya son yin abin da zai sanya ta cikin damuwa. Makarantar da zan tafi ta kwana ce, amma zallar ilimin addini ne ake koyarwa a ciki. Inna tana ta yi mini shirye shiryen tafiya, ni kuma kewarta da ta ƙanina ta fara damuna, ina son karatuna amma kuma ina ƙaunar iyayena da ƙanina. A nata shirin tafiyata ne, a lokacin  kuma Innarmu ta fara wata irin rashin lafiya, ga kuma tsohon ciki, ga wasu irin ƙuraje da suka fara fito mata a jikinta. Nan na ji ba zan iya tafiya na bar sanyin idaniyata a wannan hali na rashin lafiya ba. Inna ta dafa kafaɗata ta ce "Haba Gwani ɗan Inna magajin malam, ba ka son Inna ta yi alfahari da kai, ka zama babban malami?" "Inna ina so, amma baki da lafiya fa" "Bakomai, kar ka damu zan ji sauƙi in sha Allah" Huzaifa ya kalli Inna ya ce "Inna, wai almajiranci za a kai yayana, ni gaskiya zan bi shi in da za shi" Inna ta ce "A'a ba almajiranci bane ba, karatu zai je yi" Huzaifa ya fara kuka ya riƙe ƙafar Yazid ya ce "Gwani Dan Allah kar ka tafi ka barni, dukana su Mariya zasu cigaba da yi, kuma wa zai kaini makaranta? Da wa zan dinga cin abinci?". Na durƙusa na rungume ɗan uwana, ina rarrashinsa. Inna ta matsa na tafi makaranta. Ta riƙe hannuna ta ce "Allah ya yi riƙo da hannunka, Allah ya shiga lamarinka ka mayar da hankali sosai Yazid, Allah ya baka ilimi mai amfani" Baba da kansa ya kai ni makaranta, tare da Malamina na garinmu Malam Kabir, makarantar babbace, kuma boko ce da islamiyya a haɗe. Dama idan ɗaliban Malam Kabir sun yi sauka, wanda suke buƙatar ɗora karatunsu, wannan makarantar Malam Kabir ke tura ɗaliban sa, saboda yana da connection da su. A nan shugaban makarantar ya yiwa babana bayanin makarantar an buɗe ɓangaren boko ma, idan yana buƙata in haɗa duka. Baba ya ce a bani zaɓi idan ina so, nan na ce masa ina so, babana ya biya komai, kuɗin makaranta ta sai da Baba ya tafe na shekara uku, saboda Babana yana da arziƙi dai-dai gwargwado. Iya kayan Abinci da na tafi da su kuwa, ba a magana ya bani kuɗi masu yawa, ya rungumeni yana cewa Gwani Yazid zan yi kewarka sosai zan dinga zuwa ina dubaka. Ni kaina na ji babu daɗi tafiyar Babana, ga kuma kewar Innata da ƙanina Huzaifa. Na mayar da hankali sosai a kan karatuna, sai dai ni bokon nan tana mini wahala, dan makarantar kanta sun fi ƙarfi a kan ilimin addini, amma duk da haka ban sare ba, na ɗorawa raina ina son yin karatun. A lokacin babu waya, dan haka ban san halin da Inna da Huzaifa suke ciki ba, duk da abin yana damuna, Baba yana zuwa kawo mini ziyara sai ya ce mini kowa yana nan lafiya ba sai na zo ba gida ba, in zauna in yi karatuna dan cika burin mahaifiyata. Kusan watanni huɗu ina makaranta ban je gida ba, Baba ya hanani, gashi an shigar wata na biyar, Baba kuma ya shafe lokaci bai zo ba, na tayar da hankalina na ce zani gida. A ka bani kwana uku a makaranta. Sai kuma Yazid yayi shiru ya sunkuyar da kansa. Cikin ƙosawa Fadila ta gyara zama ta ta ce "Cigaba mana" Yayi ajiyar zuciya ya ce "Da na koma gida, Allah ya yiwa Babar Gwani rasuwa, wato Innarmu. Naƙuda ta kamata Baba baya gari, matan gidan nan aka rasa mai kaita Asibiti. Tun lokacin da take da cikin kasancewar mahaifinmu ya ɗan fara wayewa da wasu al'amura na zamani, ya bar Inna ta je awo, kuma a wurin awon an sanar mata da ta fara naƙuda ta je Asibiti kar ta haihu a gida, ni da ita take gaya mini haka, amma ba su taimaka mata ba, dama tana halin rashin lafiya naƙuda ta risketa, tayi jijjiga ta rasu, ta bar ɗan jaririn, kamar yadda na samu labari har ta mutu tana tsaka da naƙuda addu'a take yi mini, Allah ka cika mini burina a kan Gwani, Allah ka shirya mini 'ya'yana ka duba mini ka tsare mini shi, da shi da ɗan uwansa Allah ka zama gatansa. Da ire-iren wannan addu'a ta cika. Baki ba zai iya bayyana halin da na shiga ba, na tarar da Huzaifa ya yi baƙi, ya rame na nemi a nuna mini mai ta haifa amma aka ce washegari shi ma ya koma. Duk yadda na so na yi tawakalli na kasa, na shiga ɗakinta na tatarao kayanta na saka a gaba na dinga kuka. Bayan an share zaman makoki, dangin mahaifiyata suka ce zasu tafi da Huzaifa, tun da yarone a ƙarami, bai fi shekara takwas zuwa tara ba, amma matan mahaifina suka ce, kar ya yarda a kai masa ɗansa cikin maguzawa. Aikuwa mahaifina ya hana su, mahaifiyarsa ta so saka baki, amma ta yi shiru saboda duk 'yan'yanta shi ne mai kuɗi ba ta son ɓacin ransa. Sai dai tun a wurin zaman makokin Inna, na fuskanci sauyi daga wurin Baba, kamar ba ya son ganina, da ya ganni sai ya kawar da kansa, idan na zauna a wuri sai ya tashi, ya yi ta hantarata na rasa dalilin haka, amma na bar shi da kawai alhinin mutuwar Inna ne. Duk da ƙarancin shekaru na Huzaifa, ya dinga ce mini "Gwani, Inna ta ce kayi karatu, ka cika mata burinta" Na rungume Huzaifa ina kuka, ina tunanin yadda zan bar shi a gidan shikaɗai. Mahifina ya koma kan kasuwancin sa, ba tare da ya mini ko sallama ba. Ga wasiyyar Inna a raina ga tausayin Huzaifa, tabbas da ya dauke Alqur'ani da da shi zan tafi makarantar mu. Tun ina gidan ban koma ba, abinci sai an ga dama ake bamu, a daddafe na kwan goma, Huzaifa yana nanata mini in koma makaranta. Dauriya da juriya ce kawai ta sanya ni na koma makaranta, na ji duniyar ta isheni, ta daina mini daɗi, bana gane komai, karatunma da ƙyar nake yi, Allah ya jiƙan shugaban makarantarmu Malam Umaru mai allo, ya dinga rarrashina yana bani haƙuri. A haka na cigaba da karatu, ina tunanin halin da ƙanina yake ciki, da ƙyar na yi watanni biyu, kayan Abinci na suka ƙare kaf, ga Baba ya daina zuwa makarantar gaba ɗaya ganina. Wani ɗan makarantarmu da muka yi makaranta tare a garinmu da yaje gida ya dawo, yake sanar mini wai akwai matsala a gidanmu ƙanina babu lafiya. Ranar ko baccin awa guda ban ba, gari na wayewa na nemi izini na tafi garinmu. Da na je gidan mu ba wanda ya saurareni, balle ya iya gaya mini abin da ya faru, sai a waje ake gaya mini, wai Huzaifa na babban Asibitin cikin gari. Kuɗin hannuna ba su taka kara sun karya ba, na tafi Asibitin da aka gaya mini, sai da ƙyar na gano a in da aka kwantar da Huzaifa. Na tarar da shi Kansa da hannunsa duk bandeji, ga ƙafarsa ma haka. Cikin tashin hankali na ƙarasa wurinsa, na riƙe shi cikin kuka na ce "Gwani Huzaifa, meyafaru da kai haka?" Leɓensa a bushe ya kalleni, ya riƙo hannuna da hannunsa mai lafiya ya riƙe, amma bai ce komai ba sai hawaye da ke bin gefen idonsa. Na kuma matsawa na ce "Waye yake zaune a wurinka" Ya girgiza kai ya ce "Ba kowa, Baba uwani ce ta zo ta tafi, amma ba ta kula da ni ba ta bani ruwa" Cikin kuka na ce "gayamini, meya sameka ƙanina". Huzaifa ya ce "Zan gaya maka, amma kar ka gayawa kowa" "Ba wanda zan gayawa" Huzaifa ya yi ƙasa da muryarsa ya ce "Sani ɗan gidan Yaya Gaji ne, da muka je ɗiban ruwa bayan gari, ya hankaɗani a rijiya, ya gudu ya barni, ban san yadda aka yi na fito ba, na ganni a nan, wannan masu saka farar rigar sun ce na karye a hannu na da ƙafata, a biya kuɗi a gyara mini." Na sake matsawa na rungumeshi ina kuka, shi ma cikin kukan ya ce "Baba bai zo ya ganni ba, kuma Inna Gaji ta ce ta gaji da zuwa wurina, dan Allah Yaya kar ka tafi ka bar ni a nan" "Babu in da zanje Huzaifa, ina nan a wurinka". Muna cikin wannan halin wani likita ya shigo, ya kalleni ya kalli Huzaifa ya ce "Ɗan uwanka ne?" Na jinjina masa kai alamar eh. Cikin faɗa ya ce 'Amma 'yan gidanku ba su da mutunci, mun gaya musu a zo a biya kuɗi mu ɗora yaron nan, ayi masa hoton kai da na ƙirji da sauran tasa tasai, ya zubar da jini sosai kalli yadda fatarsa tayi haske saboda rashin jini, kuma idan yayi tari gudan jini ne yake fita, amma sun yi buris kamar an kawao dabba an ajiye,mai jinya ma babu, Mutanen karkara sai dai su haifi 'ya'ya amma ba a iya kula da su ba". Na kwantar da murya na ce "Dan Allah likita ka yi haƙuri, ina ga babanmu bai sani ba, amma zai iya biyan ko nawa ne, bari zan je gida na gaya masa". Likita ya ce "Ka hanzarta, dan muna buƙatar ganin baban naku, ance babar yaron ta rasu, amma ai yakamata ya sanya ido a kan yaransa, ya za ayi a tura wannan ɗan mistitsin yaron ɗiban ruwa a rijiyar ƙauye da bata da ɗauri balle murfi ba dole ya faɗa ba?" Likitan nan ya yi ta sababi ina ba shi haƙuri. Da ƙyar na lallaɓa Huzaifa, ya haƙura na ninka na koma gida a ƙafa, saboda bani da kuɗin mota, na yi sa'a na tarar da Baba a gida. Na gaishe shi amma ya ƙi amsawa sai tsawa da yayi mini, yana tambayata ko lafiya?. Nan na sanar masa da abin da likita ya ce, abin mamaki duk soyayya tarairya da kulawar Baba ga 'ya'ya musamman idan mutum ba shi da lafiya ba ga matan ba ba ga mazan ba, muddin ɗansa ba shi da lafiya sai ya shiga damuwa, amma a wannan karon sai ya hauni da faɗa, wai na tashi na ba shi wuri. Na shiga tunanin laifin da na yiwa Baba har na fusanci wannan wulaƙanci amma na kasa ganowa, na sake marairaicewa ina masa kuka da magiya, amma ƙarshe ya hau neman madoki. Matan Babana da ke tsakar gida kuma suka saka shewa suna dariya. Wata uwar yunwa na sakata ta, amma ba ta abincin nake ba, na shiga ɗakin Inna na tattara samirunta, da kwallaye, na fita da su, na je na sayar na sai Abinci na yi kuɗin mota zuwa Asibiti, da niyyar na kai kuɗin idan ya so ko wani abun a fara yiwa Hauzaifa. Amma ina zuwa na tarar da ma'aikata a kansa yana ta aman jini, da wani irin numfashi, wata Nurse tana faɗin wannan yaron da wuya ya tashi, da alama da ka ya dira a rijiyar ko ya samu internal injury a cikin kansa ko kuma dai a ƙirjinsa!!!YAU TAKE JAJIBERIN ZAƁE A NIGERIA, MASU ƘURI'A A HANNU KU TAIMAKA KU ZAƁA MANA SHUGABANNI NA GARI MASU TSORON ALLAH, KUN GA DAI IRIN HALIN HA'ULA'I DA MUKA TSINCI KANMU A WANNAN RINTSIN, TSADAR KAYAN MASARUFI, RASHIN TSARO, YAJIN AIKI DA SAURANSU. DUK DA BA WANI MUKE ZARGI DA SAMU A HALIN DA MUKE CIKI BA, JARABTA CE DAGA ALLAH. MUNA FATAN UBANGIJI ALLAH YA ZAƁA MANA SHUGABANNI NA GARI AMIN. 77 Dariya ce ta kusa ƙwacewa Yazid ya ce "Banda ragon azanci, ya zaki saki kayan kuma ki hau rufe jiki? Me ma zan kalla? Ki shirya a nutse" bin sa tayi da kallo, ta kasa motsawa balle ta ɗau kayan sai ɓoye jiki da take yi. Ya ƙarasa ya ɗau kayan ya ɗora mata a kafaɗarta. Cikin tsiwa ta ce "Ni ka fita na saka kaya" Shiru ya yi mata, ya wuceta ya buɗe sip, ya ɗauko kayansa yana ƙoƙarin sauyawa, alhalin da ba haka yake yi ba, sai ya ɗebi kayansa ya tafi banɗakin tsakar gida. "Wai me zaka yi haka?" "Me kika gani a hannuna? Kaya zan saka" "Kuma a cikin ɗakin nan a gabana?" Yazid ya ce "Yau naga ikon Allah, kiyi harkarki nayi tawa mana, ina ruwanki da ni ne?" Ya ƙarasa maganar yana zare singlet ɗin jikinsa. Juya masa baya tayi, dama kaya ne suke rage masa girma kokuwa dai tsananin kwarjinin da yayi mata ne?. Kwasar kayanta tayi, ta nufi ɗan mitsitsin banɗakin da ke cikin ɗakin, wanda da ƙyar take iya juyin kirki a cikin sa. Tana daf da shiga taji ya ce "Masha Allah, ƙafafuwanki gwanin ban sha'awa" Ƙirjinta ne yake dukan uku uku, tana mamakin fitsarar da Yazid ya ke gwada mata, a haka kamar na ruwansa, abin da yayi mata jiya ta tuna a ranta ta ce 'Lallai ma mutumin nan'. 'wai kayan sun gagara ki saka ne, ko sai na shigo na taya ki sawa?" Shiru tayi masa, ta gama sanya kayan sannan ta fito, ta wani haɗe rai karma ya kawo mata wargi. Shima basarwa yayi, ya ɗauki mukulli suka fita. Mamakin irin unguwarsu Yazid take, kasancewar yamma ce, galibin yaran unguwar suna gindin kwata suna suyar awara, wasu na sayar da dankali, wasu wainar fulawa. Ga azabar lunguna da kwatoci ko ina, ga uban tumaki da awaki, kana tafe kana basu hanyar wucewa, banda kajin hausa da suke nasu shagalin tsakanin layukan. Sai a lokacin yake tabattar da da tayi yinƙurin guduwa, sai ta sha wahala, wannan unguwar ai tsaf za a yi garkuwa da mutum. Ganin yadda take ta ƙarewa unguwar kallo ne ya sanya Yazid ya ce "Ki tayani addu'a, ubangiji Allah ya yassare muni na saya mana gida a duk unguwar da kike so, mu koma Allah ya kawo mini buɗi" "Ku koma kai da wa?" "Ni da matata mana" ya bata amsa Taɓe baki tayi ta ce "Ka sa a ranka kawai ajiyata aka kawo maka, daga yanzu zuwa Kowane lokaci zamu iya rabuwa" "Ba kya so na saboda ni talaka ne ko Fadila?" Ba kara ta ce "Eh, ai kaima ka san ni ba tsarar aurenka bace, na yi wani ƙaramin laifi ne Daddy ya hukuntani ta wannan hanyar, kuma na san ba zai wuce wannan banzar yarinyar ce ta saka shi yayi mini haka ba, dan haka kurum Daddy ba zai mini irin wannan auren ba kamar mara galihu". Jiki a sanyaye ya ce "Haka ne, amma Allah ya sani, ni dai ina sonki, Allah ya tabbatar mana da alkhairi" daga haka bai kuma cewa komai ba har suka isa gidan Hajiya. Ko da suka yi sallama, tana tsakar gida ta gama girki, fuskarta babu yabo ba fallasa, ta karɓesu, ta je ta ɗauko tabarma ta shimfiɗa musu. Yazid ne ya fara gaisheta, sannan Fadila ta gaisheta, gaba ɗaya matar ba tayi mata ba, mussaman yanzu da take ƙure Fadilan da ido. Hira ta shiga yi da ɗanta, amma Fadila ta lura tunda suka yi maganar nan a hanya, duk jikinsa yake a sanyaye. Fadila ta yi shiru kamar bata wurin, amma a hirar ta su, ta fuskanci akwai matuƙar shaƙuwa da soyayya tsakaninsa da Hajiyar tasa. Hajiyar ce ta tashi ta ce "Yazid tunda kuna nan, bari na shiga gidan can nayi musu jaje, an haura musu an yashe su" Yazid ya ce "Subhanallah, Allah ya tsare ya mayar da alkhairi" Ta amsa da Amin ta ɗau hijjabinta ta saka ta fita. Tana fita Fadila ta kalleshi ta ce "Ka tashi mu tafi ni na gaji" Yazid ya ce "Kiyi haƙuri ta dawo dan Allah" tayi shiru bata sake cewa komai ba. Sai da aka yi sallar magariba, sannan suka yi wa Hajiya sallama suka tafi. Amma har suka je gida Yazid bai kuma cewa Fadila komai ba. Shi ya ja su suka yi sallar isha'i tare, daga haka suka zauna kowa yayi shiru. Yazid ya ce "Zaki ci Abinci yanzu ne?" Ta ce "Eh bari in zuba" ta tashi ta tafi Kitchen da kanta, ta zubo Shinkafa da wake ce da mai da salak, cikin ikon Allah duk abin da Yazid ya dafa ya bata ba musu take karɓa ta ci. Ta dawo falon ta ajiye Abincin a gabansa, da cokula biyu ta ce "Bismillah mu ci" kallonta ya yi ya ce "Ba zan iya cin Abincin ba, kawai ki ci" "To ai naga ba abin da ka ci" "Eh zan ci ne, ki ci kawai bari in ɗan fita zan dawo" Haɗe rai ta yi ta ce "Wallahi kana fita nima fita zan yi, ni fa tsoron gidan nan nake ji, kawai kayi haƙuri da fitar mu ci abinci" Ɗan dafe kansa yayi ya ce "Da gaske na ƙoshi fa, ki ci kawai Fadila" zama tashi ta yi ta bar masa falon, dan gaba ɗaya shirun da yayi bai mata daɗi ba. Bai gaji ba ya bita ɗakin, ya tarar tayi kwanciyarta, ya ƙarasa kan katifar ya riƙo hannunta ya ce "Haba matar, fushi ki ka yi? Ki zo ki ci abinci kar ki kwana da yunwa" "Ba zan ci ba" "Tuba nake, Allah ya baki haƙuri zo muje mu ci tare, a baki ma zan baki yauwa Sweetheart" tana tura baki ya lallaɓota ta dawo suka ci Abincin tare. Sai dai ƙasan zuciyar Yazid babu daɗi, idan ya tuna Fadila tana gaya masa bata son sa kuma ba zata zauna da shi ba. Bayan sun gama ne, Fadila ta hau yi masa surutu. "Wai yau ba zaka islamiyyar ba?" "Yau Alhamis ai ba islamiyya, kuma na so naje na ɗau nawa karatun, amma kin ce idan na fita zaki fita ni kuma bana son ki tafi ki barni" dariya tayi ta ce "Ai dan kar ka tafi ka barni ne, tsoro nake ji amma ba in da zan iya zuwa, na san ma idan na fita ɓata zan yi". "Unguwar talakawa dama, idan ba wanda ya saba zama a ciki ba, na za gane kanta ba". Ta basar da zancen ta ce 'Wai duk wannan karatun naka, kai ma zuwa kake yi ana kuma koya maka?" Yayi murmushi ya ce "Eh mana, ai shi ilimi kogi ne ba a ƙure masa". Ta ce "Haka ne, to duk wannan litattafan na uwar ɗaki ka iya su?" Ya ce 'Alhamdilillah, duk na iya wasu kuma ina bincike a kansu ne". Ta ce "Lallai ka na da ilimin addini sosai" "Idan na dawo da daddare kema sai na dinga koya miki" "To, zaka koya mini larabci ma?" Ya ce "to zan saka miki kuɗin laraba, ki dinga biyana, sannan na koya miki" Dariya take, shi kuma ya zuba mata ido, yana jin daɗin yadda yau ta saki jiki da shi sosai. Ɗan shiru tayi sannan ta ce "Wai ina familynka, ko kaima auren dolen aka yi maka kamar yadda Daddy yayi mini, ko Mummy bata san ya aurar da ni ba?" Jikinsa ne yayi sanyi, Ya ɗan kalleta ya ce "Auren dole aka yi miki fa ko? Ni ba na dole aka yi mini ba, tun da ni ina son ki sosai. Familyna suna wani wuri mai nisa sosai" "To amma naga basu zo ba?" "Eh za su zo wataran" Ta ɗan yi hamma tare da miƙa, ta tashi tsaye ta ce "Bacci ya zo, sai da safe" "In zo mu kwanta tare" "A'a ba kyau" tayi maganar tana shigewa bedroom ɗin. Murmushi yayi a hankali ya ce "Ya ubangiji Allah ka ƙara sanya salama a zuciyar matata ta zauna da ni, ni kuma ka bani ikon kyautata mata". Al'amura sun yi nisa, tsakanin Abdul da kuma Yusra, dan sun samu fahimtar juna, dubu ɗari takwas ya bayar na komai da komai banda sadaki. Aikuwa Abdul ya ga kara, dan iyayenta sun nuna farincikinsu sosai da sosai, dan a yadda suke nunawa su farincikin 'yar su ya fiye musu komai. Suka nuna masa kar ya takura kansa duk abin da Allah ya bashi ya kawo musu. Sun sami fahimtar juna sosai da soyaya a tsakaninsu. Yusra kullum cikin yi masa zancen Fadila take, na haryanzu ba a san in da take ba. Yayi ta rarrashinta yana kwantar mata da hankali, yana nuna mata ai Fadila ba wani abu ne ya sameta ba, tun da dai Daddy ne ya ɗauketa. Khalil yana ta shirin komawa Abuja, amma yanayin jikin Hafsa ne ya hana su tafi, dan wataran sai Mama ta zo ta wuni tare da ita, tana shan wahala sosai da sosai akan laulayin nan. Gefe guda kuma zuciyarsa na matuƙar tausayin Mummy, duk ta firgice kamar wadda aka ce an sace Fadilan. Da kansa ya kira Daddy a waya, yana masa magiyar yayi haƙuri ya taimaka ya gayawa mahaifiyarsu in da Fadila take. Alhaji Ahmad ya ce "Kana ji na Khalil?" "Eh Daddy" "Tun tasowarku, na kasance ina biyewa abin da kuke so da wanda mahaifiyarku take so, na yi haƙuri na ɗau hakan bakomai ba, dai daga baya na gano illar da hakan da yake da shi a rayuwarku, mussaman Fadila da take mace, Fadila 'ya ta ce, ba zan yi abin da zan cutar da ita ba, dan haka ka ƙyaleni ina sane da abin da nake yi, hakan tamkar hukunci ne ga mahaifiyarku da ita kanta Fadila, kana sane da yadda suka saka na karɓi kuɗin auren mutane, suka dawo daga baya wai ba sa so, an san bata so aka kawo mini shi?, Kar ka ga laifina Khalil, da ku da mahaifiyarku duk ina ƙaunarku, duk abin da nake yi zuciyata bata mini daɗi da alaƙar da ke tsakanina da matata ta fari, amma ba yadda na iya da halinta, kayi haƙuri lokaci na nan zuwa da zan faɗi in da take" Khalil ya ce 'Shikenan Daddy. Na kammala aikin da ka sakani, kuma nima a satin nan zamu koma Abuja in sha Allah" Daddy ya ce "Masha Allah, Allah ya dafa a gaishe mini da ɗiyata". "Za taji in sha Allah, a gaida Antyn" "Zata ji in sha Allah" Baba Hassan tamkar ya zuba ruwa a ƙasa ya sha, saboda murnar ya ji zai je Saudiyya, masu taya shi murna nayi, masu yaƙe na yi, dan zukatan su Baffa babu daɗi zinƙire yake da hassada a kan yadda Allah ya ɗaga 'yarsa duk da suna cin arzikinta, dan kusan duk wata kayan Abinci da kuɗi na tafe, kuma tare da su ake ci amma basa gani. Yazid ya kammala sallolin darensa kenan, da addu'oi, Kamar yadda ya saba ya ɗora hannunsa a kan Fadila, yayi ta mata addu'a sannan ya kwanta. Ya kwanta babu da daɗewa, yaga Fadila ta tashi, fitsari ya tasheta, har ta nufi banɗakin cikin ɗaki, amma ta fasa saboda tsoro take ji, saboda ba wuta gashi bata san in da fitilarsu take ba, dan haka ta tafi banɗakin tsakar gida. Shi ma kasa shiga banɗakin tayi, ta tsuguna a tsakar tayi fitsarinta, ta tashi tana wanke ƙafarta, tayi arba da wata mage ɗirkekiya. A guja ta ƙwala ihu ta shiga ɗaki da gudu, ta faɗa kan Yazid tana rirriƙe shi. A rikice ya ce "Lafiya menene?" "Mage ce" ta bashi amsa. "Kuma sai ki dinga gudu haka? Maimakon kiyi addu'a" Cikin shagwaɓa ta ce "Mhmmm ni tsoronta nake ji, dan Allah ka tashi ka koreta, ka rufe mana ƙofa karta shigo". Ya ce "A'a nima gaskiya tsoronta nake ji" "Dan Allah ka tashi" Shima ya shagwaɓe murya ya ce "Ni gaskiya tsoronta nake ji, kuma naga kamar ta shigo ma" Sake ƙanƙame shi tayi ta na jin tsigar jikinta na tashi, saboda bata son mage. Hakan ya bawa Yazid damar nufin cikar kuɗirinsa a matsayinsa na mijinta. Yadda hannunsa ke yawo a jikinta, ya sanya ta sake shiga tsoro da firgicin gaske. Kamar wadda aka cirewa kuzari, ta kasa kayaɓus balle tayi yinƙurin hana shi, sai da taji abin nasa ya wuce tunaninta. Lokaci guda burkin sarrafa kansa ya ƙwace masa, sai da ya kai ga samun abin da zuciyarsa ta makance a kan samu. Fadila ba ta jin haushin Yazid kamar yadda ta ji haushin kanta ba, tana jinjina sokonci da wautar da tayi, na barin Yazid yayi awon gaba da abu mafi daraja a tare da ita, yanzu sai ya ce dama abin da take so kenan. Haka ya taimaka mata ta kintsa, yana jiran kwandon bala'in da zata sauke masa, amma tayi masa shiru ba ta ce komai ba. Washegari da safe ko abin karin da ya bata bata karɓa ta ci ba, ya gama surutansa da rarrashinsa amma ko kallonsa ba tayi ba. Gashi yana da jarrabawa ƙarfe sha ɗaya na safe. Ba yadda ya iya haka ya fita ya barta. Yauma yarinyar nan Maryam ita ta shigowa Fadila, Fadila ta ji daɗin zuwanta, tayi mata shara da wanke wanke. Yau Yazid saboda sauri, ko gyaran gidan bai yi ba, ya ƙare a zaman rarrashinta. Da kanta ta shiga bedroom ta tattare kayansa da ya cire ya ajiye, ta kwashe nata ma, ta gyara ko ina, tunawa tayi a gida wataran a falo ma take yada komai, sai dai a kwaso a biyota da shi, bata son ƙazanta amma bata iya gyara sai da ayi mata. Haka nan duk da jikinta babu daɗi ta gyara ɗakin. Ta dawo ta ɗauko musu abincin safen da ya dafa, suka ci ita da Maryam. Suna ta hira har sha ɗaya, ta lura yarinyar a nutse take, a hirar tasu ne ma, yarinyar take gaya mata Yazid malaminsu ne a makarantar dare, har take bata labarin 'yan ajinsa ajin sauka sunce zasu gidansa, da irin kirkin Yazid, ko a makaranta. Fadla ta ce "Suwaye 'yan ajin saukar?" Maryam ta ce "waɗan suka yi sauka, suka kuma dawowa?" "To ya za ayi maza su zo gidana?" Maryam ta ce "Ai ba maza bane, 'yan mata ne fa manya, suma suna koyarwa, ai zasu zo ki gansu". Haka nan Sai Fadila ta ji babu daɗi, har da ɗan ɓata rai. Can Maryam ta ce 'Anty, ba zaki ɗora girki ba?" Fadila ta ce "Kin iya girkin ne?" Maryam ta ce "Eh ina yiwa Antyna" Fadila ta ce "Ina mamanki?" "Ta mutu, shi ne yayata ta ɗaukeni" Tausayinta ya kama Fadila ta ce "Allah sarki, Allah ya jiƙanta to me kika iya dafawa?" "Duk abin da kike so na iya" "To tashi mu je Kitchen ɗin" Fadila saboda zama da Yusra, ta iya wasu abubuwan a girki, dan haka ta wayance, tana ganin yadda Maryam ke girkin, saboda ko bakomai yakamata Yazid ya dinga hutawa, ta dinga rage masa ayyuka. Taliya suka dafa da miya, sai azahar lokacin islamiyya sannan Maryam ta tafi, Fadila ta rasa me zata bata, dan yarinyar tana taimaka mata, alhalin ba wanda ta shiga a layin ta yiwa sallama ta ce gata ta tare, ba Yadda Yazid bai yi da ita ba, amma taƙi zuwan. Yazid ya sha mamaki da ya dawo, ya shiga Kitchen amma ya tarar da abinci. Ya dawo don ya tambayeta, duk da tunda ya dawo harara ce kawai take shiga tsakaninsu. "Sweetheart, a ina muka samu abinci". "Kaje can ka nemi Sweetheart ɗin ka" "To Allah ya baki haƙuri, waye ya kawo mana abinci?" "Dafawa nayi" ta bashi amsa. "Wow, inyee ashe ta iya girki babyn" Zumɓura baki tayi ya shareshi. Duk yadda ta so ta basar da Yazid, amma ya zuba abincin, ya dinga zuba mata santi, ta ji daɗin yabawar da yayi, amma ta shareshi dan haushinsa take ji. Tashi tayi ta koma bedroom ta kwanta abinta. Yau da daddare ta tubure ba zai hau mta katifa ba saboda ƙarfin hali, falo ya koma ya ƙyale mata ɗakin ma gaba ɗaya. Tayi juyi ya kai sau biyu, amma Yazid na kan sallaya yana ibada. Ita yawan ibadar Yazid har mamaki yake bata. Ji tayi yayi shiru da karatun da yake yi, ya tattara hankalinsa a kan wani abu, da bata san ko menene ba. Ƙasa ƙasa taji Kamar Yazid kuka yake yi. Kasa kwanciyar tayi, har ta fito ta je daf da shi, bai sani ba. Hannu ta saka ta zare hoton da yake hannunsa. Wata kyakkyawar Bafulatana ce a jiki,  mai matuƙar kyau na ɗaukar hankali. "Wacece wannan?" Ta jefo masa tambayar. Shiru yayi ya zuba mata ido, ya kasa furta komai. Littafin kuɗi ne, ku tuntuɓeni domin saya. Ayshercool 08081012143LITTAFIN NAN NA KUƊI NE, MAI BUƘATA YANA IYA TUNTUƁATA A KAN LAMBAR WAYATA 08081012143 76 Cikin ƙosawa ta sake cewa "Ka yi magana mana, ka yi shiru kana kallona" Ya saka hannu ya karɓi hoton daga hannunta, yana ɗan jujjuya shi sanyaye ya lumshe idanunsa sannan ya buɗe su ya ce "Wato Fadila, duk wanda ya rasa uwa yayi kuka. Shiyasa duk da ina murna na aureki, amma bana jin daɗin nesanta ki da Mummy da Daddy yayi ba. Ita uwa wata kyauta ce daga Ubangiji da bata da madadi. Inna wuro kenan, ni kuma ina kiranta Innata. Kamar yadda na samu labari Bafulatana ce ta riga a can wani ƙauye a Jalingon jihar Taraba. Galibinsu fulani ne, sai dai galibinsu ba musulmi bane ba, rigar su Innarmu musulmi ne sai dai basu damu da ilimin addini ba, ba abin da suka sani sai kiwo da kuma tallan Nono. Inna tana da yayye mata biyu sai kuma ita ta uku, suke nan a wurin mahaifinsu. A wurin tallan Nono ne da suke shiga garin Jalingo yi Inna ta ci  karo da ilimin addini ta gane Cewar a duhu suke zaune na jahilci, addinin ma basa gudanar da shi yadda ya dace a rigarsu dan haka ta ɗau ragamar neman ilimi. Idan taje tallan Nono, sai ta zauna cikin makarantu ta ɗau karatu. A lokacin babu wanda ya damu da sai an saka a makaranta kan kaje, ta samu wata makarantar islamiyya tana zuwa. Ta ƙuduri aniyar yin karatun addini mai zurfi. Domin ya zama babbar malamar ita ma ko dan ta dinga wayar da kan 'yan ƙauyen su. Sai dai wannan buri nata bai cika ba, mahaifina ya haɗu da ita, lokacin da suka je rigarsu shi da wani abokinsa sayen shanu. Kasancewar dama ba karatu suke yi ba, kuma 'yan uwanta duk da wuri ake yi musu aure, ya sanya ita ma mahaifinsu ya amince da mahaifina a kan ya kawo kuɗin aure a sanya ƙanƙanin lokaci. Mahaifina yana da mata biyu, mahaifiyata ce ta uku, uwar gidansa Baba Uwani, sai kuma ta biyun Baba Hanne. Babban abin da ya damu mahaifiyata shi ne burinta na karatun addini babu lallai ya cika. Bayan ta auri Mahaifina, ya tafi da ita garinsu da yake cikin Ranon jihar Kano ta tare a gidansa da ke ɗauke da matansa da kuma yaransa biyar da suka kasance duk mata. Kalata ta wurin uba tana nan a raye, amma a lokacin bata garin Rano, tana wani wurin tana aure bayan rasuwar kakana, dan haka babana yana da yayye biyu maza, sai ƙanwarsa mace. Mahaifiyata na da matuƙar haƙuri da kawaici, mabaifina yana sonta sosai da sosai, hakan ya sa ta bijiro masa da son ta koma makaranta, amma ya ce bai yadda ba abin zai zama surutu a gari. Tun da mahaifina ya auro mahaifiyata matansa suka sakota gaba, suke nuna mata ƙiyayya a fili. Idan baya nan suyi ta sakata aiki mai wahala. Mahaifina tsayayyen mutum ne a kan gidansa, yana da rufin Asiri sosai a garinmu an san shi sosai yana da kuɗi, yana dillancin dabbobi har zuwa kudu da maƙotan Nigeria, gidanmu ba a yunwa ko rashin sutura, sai dai ba a damu da ilimi ba sam. A na haka mahaifiyata ta samu juna biyu, sai dai ba wanda ya sani, saboda ba ta laulayi daga ita sai mahaifina suka sani. Babu wanda ya farga mahaifiyata na da juna biyu, sai ganinta kawai suka yi tana naƙuda. Ta yi doguwar naƙuda bata haihu ba, Babana ya ɗauke ta zuwa Asibitin cikin gari, dan duk da rufin Asiri na mahaifina yana cikin karkara da iyalansa. Mahaifiyata ta haifi ɗa namiji, Mahaifina yayi murna sosai da sosai, zai samu magaji, mahaifiyata kuma murnar da take yi, shi ne Allah ya cika mata burinta a kan yaron nan, ya zama masanin addinin Muslunci sosai. Tun da suka koma gida sai ƙananan maganganu, mussaman da suka ga yadda mahaifina ke ta rawar kai a kan haihuwar. Ranar suna mahaifiyata ta roƙi mahaifina ya saka mini suna Yazid. Mahaifina bai sani ba, sunan wani babban malami ne a cikin garin Jalingo da Innata ke zuwa masallacin sa jim wa'azi. Son da yake yiwa mahaifiyata ya sanya shi ya amince, ya sanya mini suna Yazid. 'yan garinsu mahaifiyata sun zo, duk da fulani ne amma wasunsu ba musulmai bane ba suka zo taron suna, mahaifina sai da ya yanka manyan raguna da saniya, aka dinga ci ana rabar da naman a garin, ko baka je suna ba, abu ne mawuyaci ka kasa cin naman da aka yanka da kuma abincin suna. Matan Babana suka kuma mahaifiyata a gaba, abin mamaki a wannan karon har da facaloli, suna mata gorin wai 'yan uwanta maguzawa ne. Mutanen gari suka dinga yi wa matan mahaifina Allah sarki, duk wannan wahalar yaransu mata ne, lokaci ɗaya daga zuwan mahaifiyata ta fara haihuwar namiji, idan babana ya mutu ba zasu samu komai ba. Kasancewar mahaifiyata ba sawa ba fitarwa, ya sanya bata damu da abin da suke yi ba, sannan bata nuna kara a kaina kasancewata ɗan fari. Ba abokan zaman mahaifiyata ba, hatta 'yan uwana yayyena, suke kishi da ni, basa son na raɓesu. Tun ina ƙarami mahaifiyata ke mini kirana da Gwani Yazidu magajin malam. Bayan na fara tasawa, ɗan abin da mahaifiyata ta sani na ilimin addini ta fara koya mini, hatta magana tayi iyaka ƙoƙarin ta bakina ya buɗe da la'ilahailallah. Irin koyon maganar nan na yara, da bisimilla istigfari ta dinga koya mini bakina ya buɗe da su, bana zuwa ko ina ba wanda yake ɗaukata kullum ina tare da mahaifiyata hakan ya sanya nayi saurin iyawa. Shekaruna uku a duniya, Innata ta matsa a kan lallai mahaifina ya kaini makaranta, ya nuna mata nayi ƙanƙanta da yawa amma ta dage, da ƙyar ta bari na shekara huɗu. Ya sakani a wata makarantar addini da take ƙauyenmu, sai dai akwai nisa sosai daga gidamu zuwa makarantar dan haka mussaman yake biya malamin makarantar kuɗi, ya dinga sawa ana zuwa a ɗaukeni ko a dawo dani. Cikin ikon Allah nan da nan, kasancewar ƙwaƙwalwar yarinta, na dinga ɗaukar karatun Alkur'ani da malamin ke tsaye a kaina yana koya mini. Tamkar ɗan ƙaramin ɗansa haka ya mayar da ni, ya kan ɗorani har a kan cinyarsa yana koya mini karatun Alkur'ani. Sai dai ƙiyayyar da ake nuna mini a gidanmu  ta sanya bana sakewa ko a cikin yara, dan ko tsakar gida na fito wasa, sai yayyena su ci zalina. Kullum ina naniƙe da Innata ko ina makaranta. Batun gata a wurin mahaifina ba a magana, duk abin da ya ɗinka sai ya ɗinka mini, ga mahafiyata ma bata wasa da Abincin da zan ci, bata bani cimar banza, gashi da ƙananan shekaruna amma girmamani take saboda sunan da aka saka mini. Daga cikin abin da yake ƙonawa mahaifiyata rai, shi ne yadda abokan zamanta kan kirani da jikan maguzawa saboda a danginta akwai wanda ba Musulmi ba, cikin izgilanci idan ta kirani magajin Malam, sai suce ko kuma jilan maguzawa ba. Sai da na shekara bakwai a duniya, sannan mahaifiyata ta kuma haihuwa, ta sake haihuwar ɗa namiji, aikuwa matan gidan nan tamkar su kasheta, saboda 'ya'ya maza take haifa. aka saka wa jaririn sunan Huzaifa. Duk da Inna ta kuma haihuwa, hakan bai hana ta daina sona ba, tare da cigaba da kula da mu. Ban fi shekaru goma ba, Mahaifina ya fara tafiya da ni wuraren kasuwancin sa, idan yana gari wasu lokutan haka yake zamansa yayi ta hira da ni, yana mini hirar kasiwancinsa duk da ba ganewa na ke yi ba. Ya biya aikin umara ni da shi ya tafi da ni. Hakan ya ƙara rura wutar ƙiyayyata a zukatan matan gidan, kamar su cinye ni su huta. Inna tana yawan gaya masa ya dinga ƙoƙarin yin adalci a tsakanin yaransa bai kamata ya tafi da ni umara ba. Amma buɗar bakinsa ya ce mata "Su 'ya'yan su da nake aurarwa na ke kashe musu kuɗi nawa na taɓa bawa Yazid, ina adalci a tsakanin su" Ƙanina Huzaifa shima ya fara tasawa, sai dai halina da na Huzaifa ba iri ɗaya bane ba. Huzaifa yaro ne mai ƙiriniyar gaske, ga ta'adin tsiya, Inna tana can tana aiki Huzaifa zai fita tsakar gida ya shiga neman magana a tsakar gida. Su kama mutan gidan su kama Huzaifa su yi ta duka suna zagi, abin da yake matuƙar ƙona mini rai, in ga an daki ɗan uwana. Duk rashin maganata ina jin haushin in ga an taɓa gudan jinina. A lokacin na kai shekaru goma sha uku, ina haddar Alqur'ani sosai da sosai, tun Huzaifa na shekara uku nake tafiya da shi makarantar mu. Idan muna gida kuma ina koya masa karatun. Ba zan manta watarana ba, babbar yayarmu da aka yi mata aure tuni, mai suna Yaya Gaji ta zo ita da yaranta. Suna cikin wasa tare da Huzaifa da yaranta, faɗa ya kaure a tsakanin sa da ɗanta Sani, yayyensa suka haɗu suka dinga dukan Huzaifa, da ƙyar na ƙwace shi, na kalli ɗaya daga cikin yayyena da har da su a dukan Huzaifa, abin da ban taɓa ba nace "Allah ya saka maka" ba tsammani na ji saukar mari yayata mariya ta mareni tare da ɗorawa da zagina. Duk ƙanƙantar Huzaifa da yaga an mari yayansa, haka ya fara kaiwa Mariya duka, haka na janye Huzaifa muka bar tsakar gidan. Sai dai ko mintuna goma ba ayi da dukana da Mariya tayi ba, ta ƙone a hannu da ruɗen tuwo, a take ta kurma ihu, ba a ɗau tsawon lokaci ba hannun ya saɓule a take. Mariya ta sha jinya dan kamar hannun ba zai warke ba, shi kuwa Huzaifa kamar an sake tunzura shi kullum rashin jinsa gaba yake yi. Hatta Innarmu suna yawan yin faɗa da Huzaifa, ni kuwa ko Inna bana son na ga tana taɓa mini Huzaifa. Gaba ɗaya hankalina baya kan kasuwancin da mahaifina ke ta janyo ni kan harkar. Ina nan na mayar da hankali a kan karatu na, tare da kula da ƙanina abin ƙaunata. Kwatsam! Matan mahaifina suka tsiro da wani camfi, wai in dai aka taɓawa Inna 'ya'ya sai wata masifa ta afkawa mutum, bayan jikan maguzawa da suke kirana da shi, suka fara ƙoƙarin laƙaba mini maita ni da mahaifiyata. Ina da shekaru goma sha huɗu, na sauke Alƙur'ani hadda, malaminmu ya fara batun a turani makaranta cikin gari, domin samun cigaba da karatuna na addini. Mahaifina ya fara iƙirarin karatun ya isa haka, yana son ya sakani a kan kasuwancin sa sosai, amma mahaifiyata ta cigaba da lallaɓa mahaifina, a kan ya bar ni na cigaba da karatun. Son da yake yi mata ya sanya wasu lokutan, baya son yin abin da zai sanya ta cikin damuwa. Makarantar da zan tafi ta kwana ce, amma zallar ilimin addini ne ake koyarwa a ciki. Inna tana ta yi mini shirye shiryen tafiya, ni kuma kewarta da ta ƙanina ta fara damuna, ina son karatuna amma kuma ina ƙaunar iyayena da ƙanina. A nata shirin tafiyata ne, a lokacin  kuma Innarmu ta fara wata irin rashin lafiya, ga kuma tsohon ciki, ga wasu irin ƙuraje da suka fara fito mata a jikinta. Nan na ji ba zan iya tafiya na bar sanyin idaniyata a wannan hali na rashin lafiya ba. Inna ta dafa kafaɗata ta ce "Haba Gwani ɗan Inna magajin malam, ba ka son Inna ta yi alfahari da kai, ka zama babban malami?" "Inna ina so, amma baki da lafiya fa" "Bakomai, kar ka damu zan ji sauƙi in sha Allah" Huzaifa ya kalli Inna ya ce "Inna, wai almajiranci za a kai yayana, ni gaskiya zan bi shi in da za shi" Inna ta ce "A'a ba almajiranci bane ba, karatu zai je yi" Huzaifa ya fara kuka ya riƙe ƙafar Yazid ya ce "Gwani Dan Allah kar ka tafi ka barni, dukana su Mariya zasu cigaba da yi, kuma wa zai kaini makaranta? Da wa zan dinga cin abinci?". Na durƙusa na rungume ɗan uwana, ina rarrashinsa. Inna ta matsa na tafi makaranta. Ta riƙe hannuna ta ce "Allah ya yi riƙo da hannunka, Allah ya shiga lamarinka ka mayar da hankali sosai Yazid, Allah ya baka ilimi mai amfani" Baba da kansa ya kai ni makaranta, tare da Malamina na garinmu Malam Kabir, makarantar babbace, kuma boko ce da islamiyya a haɗe. Dama idan ɗaliban Malam Kabir sun yi sauka, wanda suke buƙatar ɗora karatunsu, wannan makarantar Malam Kabir ke tura ɗaliban sa, saboda yana da connection da su. A nan shugaban makarantar ya yiwa babana bayanin makarantar an buɗe ɓangaren boko ma, idan yana buƙata in haɗa duka. Baba ya ce a bani zaɓi idan ina so, nan na ce masa ina so, babana ya biya komai, kuɗin makaranta ta sai da Baba ya tafe na shekara uku, saboda Babana yana da arziƙi dai-dai gwargwado. Iya kayan Abinci da na tafi da su kuwa, ba a magana ya bani kuɗi masu yawa, ya rungumeni yana cewa Gwani Yazid zan yi kewarka sosai zan dinga zuwa ina dubaka. Ni kaina na ji babu daɗi tafiyar Babana, ga kuma kewar Innata da ƙanina Huzaifa. Na mayar da hankali sosai a kan karatuna, sai dai ni bokon nan tana mini wahala, dan makarantar kanta sun fi ƙarfi a kan ilimin addini, amma duk da haka ban sare ba, na ɗorawa raina ina son yin karatun. A lokacin babu waya, dan haka ban san halin da Inna da Huzaifa suke ciki ba, duk da abin yana damuna, Baba yana zuwa kawo mini ziyara sai ya ce mini kowa yana nan lafiya ba sai na zo ba gida ba, in zauna in yi karatuna dan cika burin mahaifiyata. Kusan watanni huɗu ina makaranta ban je gida ba, Baba ya hanani, gashi an shigar wata na biyar, Baba kuma ya shafe lokaci bai zo ba, na tayar da hankalina na ce zani gida. A ka bani kwana uku a makaranta. Sai kuma Yazid yayi shiru ya sunkuyar da kansa. Cikin ƙosawa Fadila ta gyara zama ta ta ce "Cigaba mana" Yayi ajiyar zuciya ya ce "Da na koma gida, Allah ya yiwa Babar Gwani rasuwa, wato Innarmu. Naƙuda ta kamata Baba baya gari, matan gidan nan aka rasa mai kaita Asibiti. Tun lokacin da take da cikin kasancewar mahaifinmu ya ɗan fara wayewa da wasu al'amura na zamani, ya bar Inna ta je awo, kuma a wurin awon an sanar mata da ta fara naƙuda ta je Asibiti kar ta haihu a gida, ni da ita take gaya mini haka, amma ba su taimaka mata ba, dama tana halin rashin lafiya naƙuda ta risketa, tayi jijjiga ta rasu, ta bar ɗan jaririn, kamar yadda na samu labari har ta mutu tana tsaka da naƙuda addu'a take yi mini, Allah ka cika mini burina a kan Gwani, Allah ka shirya mini 'ya'yana ka duba mini ka tsare mini shi, da shi da ɗan uwansa Allah ka zama gatansa. Da ire-iren wannan addu'a ta cika. Baki ba zai iya bayyana halin da na shiga ba, na tarar da Huzaifa ya yi baƙi, ya rame na nemi a nuna mini mai ta haifa amma aka ce washegari shi ma ya koma. Duk yadda na so na yi tawakalli na kasa, na shiga ɗakinta na tatarao kayanta na saka a gaba na dinga kuka. Bayan an share zaman makoki, dangin mahaifiyata suka ce zasu tafi da Huzaifa, tun da yarone a ƙarami, bai fi shekara takwas zuwa tara ba, amma matan mahaifina suka ce, kar ya yarda a kai masa ɗansa cikin maguzawa. Aikuwa mahaifina ya hana su, mahaifiyarsa ta so saka baki, amma ta yi shiru saboda duk 'yan'yanta shi ne mai kuɗi ba ta son ɓacin ransa. Sai dai tun a wurin zaman makokin Inna, na fuskanci sauyi daga wurin Baba, kamar ba ya son ganina, da ya ganni sai ya kawar da kansa, idan na zauna a wuri sai ya tashi, ya yi ta hantarata na rasa dalilin haka, amma na bar shi da kawai alhinin mutuwar Inna ne. Duk da ƙarancin shekaru na Huzaifa, ya dinga ce mini "Gwani, Inna ta ce kayi karatu, ka cika mata burinta" Na rungume Huzaifa ina kuka, ina tunanin yadda zan bar shi a gidan shikaɗai. Mahifina ya koma kan kasuwancin sa, ba tare da ya mini ko sallama ba. Ga wasiyyar Inna a raina ga tausayin Huzaifa, tabbas da ya dauke Alqur'ani da da shi zan tafi makarantar mu. Tun ina gidan ban koma ba, abinci sai an ga dama ake bamu, a daddafe na kwan goma, Huzaifa yana nanata mini in koma makaranta. Dauriya da juriya ce kawai ta sanya ni na koma makaranta, na ji duniyar ta isheni, ta daina mini daɗi, bana gane komai, karatunma da ƙyar nake yi, Allah ya jiƙan shugaban makarantarmu Malam Umaru mai allo, ya dinga rarrashina yana bani haƙuri. A haka na cigaba da karatu, ina tunanin halin da ƙanina yake ciki, da ƙyar na yi watanni biyu, kayan Abinci na suka ƙare kaf, ga Baba ya daina zuwa makarantar gaba ɗaya ganina. Wani ɗan makarantarmu da muka yi makaranta tare a garinmu da yaje gida ya dawo, yake sanar mini wai akwai matsala a gidanmu ƙanina babu lafiya. Ranar ko baccin awa guda ban ba, gari na wayewa na nemi izini na tafi garinmu. Da na je gidan mu ba wanda ya saurareni, balle ya iya gaya mini abin da ya faru, sai a waje ake gaya mini, wai Huzaifa na babban Asibitin cikin gari. Kuɗin hannuna ba su taka kara sun karya ba, na tafi Asibitin da aka gaya mini, sai da ƙyar na gano a in da aka kwantar da Huzaifa. Na tarar da shi Kansa da hannunsa duk bandeji, ga ƙafarsa ma haka. Cikin tashin hankali na ƙarasa wurinsa, na riƙe shi cikin kuka na ce "Gwani Huzaifa, meyafaru da kai haka?" Leɓensa a bushe ya kalleni, ya riƙo hannuna da hannunsa mai lafiya ya riƙe, amma bai ce komai ba sai hawaye da ke bin gefen idonsa. Na kuma matsawa na ce "Waye yake zaune a wurinka" Ya girgiza kai ya ce "Ba kowa, Baba uwani ce ta zo ta tafi, amma ba ta kula da ni ba ta bani ruwa" Cikin kuka na ce "gayamini, meya sameka ƙanina". Huzaifa ya ce "Zan gaya maka, amma kar ka gayawa kowa" "Ba wanda zan gayawa" Huzaifa ya yi ƙasa da muryarsa ya ce "Sani ɗan gidan Yaya Gaji ne, da muka je ɗiban ruwa bayan gari, ya hankaɗani a rijiya, ya gudu ya barni, ban san yadda aka yi na fito ba, na ganni a nan, wannan masu saka farar rigar sun ce na karye a hannu na da ƙafata, a biya kuɗi a gyara mini." Na sake matsawa na rungumeshi ina kuka, shi ma cikin kukan ya ce "Baba bai zo ya ganni ba, kuma Inna Gaji ta ce ta gaji da zuwa wurina, dan Allah Yaya kar ka tafi ka bar ni a nan" "Babu in da zanje Huzaifa, ina nan a wurinka". Muna cikin wannan halin wani likita ya shigo, ya kalleni ya kalli Huzaifa ya ce "Ɗan uwanka ne?" Na jinjina masa kai alamar eh. Cikin faɗa ya ce 'Amma 'yan gidanku ba su da mutunci, mun gaya musu a zo a biya kuɗi mu ɗora yaron nan, ayi masa hoton kai da na ƙirji da sauran tasa tasai, ya zubar da jini sosai kalli yadda fatarsa tayi haske saboda rashin jini, kuma idan yayi tari gudan jini ne yake fita, amma sun yi buris kamar an kawao dabba an ajiye,mai jinya ma babu, Mutanen karkara sai dai su haifi 'ya'ya amma ba a iya kula da su ba". Na kwantar da murya na ce "Dan Allah likita ka yi haƙuri, ina ga babanmu bai sani ba, amma zai iya biyan ko nawa ne, bari zan je gida na gaya masa". Likita ya ce "Ka hanzarta, dan muna buƙatar ganin baban naku, ance babar yaron ta rasu, amma ai yakamata ya sanya ido a kan yaransa, ya za ayi a tura wannan ɗan mistitsin yaron ɗiban ruwa a rijiyar ƙauye da bata da ɗauri balle murfi ba dole ya faɗa ba?" Likitan nan ya yi ta sababi ina ba shi haƙuri. Da ƙyar na lallaɓa Huzaifa, ya haƙura na ninka na koma gida a ƙafa, saboda bani da kuɗin mota, na yi sa'a na tarar da Baba a gida. Na gaishe shi amma ya ƙi amsawa sai tsawa da yayi mini, yana tambayata ko lafiya?. Nan na sanar masa da abin da likita ya ce, abin mamaki duk soyayya tarairya da kulawar Baba ga 'ya'ya musamman idan mutum ba shi da lafiya ba ga matan ba ba ga mazan ba, muddin ɗansa ba shi da lafiya sai ya shiga damuwa, amma a wannan karon sai ya hauni da faɗa, wai na tashi na ba shi wuri. Na shiga tunanin laifin da na yiwa Baba har na fusanci wannan wulaƙanci amma na kasa ganowa, na sake marairaicewa ina masa kuka da magiya, amma ƙarshe ya hau neman madoki. Matan Babana da ke tsakar gida kuma suka saka shewa suna dariya. Wata uwar yunwa na sakata ta, amma ba ta abincin nake ba, na shiga ɗakin Inna na tattara samirunta, da kwallaye, na fita da su, na je na sayar na sai Abinci na yi kuɗin mota zuwa Asibiti, da niyyar na kai kuɗin idan ya so ko wani abun a fara yiwa Hauzaifa. Amma ina zuwa na tarar da ma'aikata a kansa yana ta aman jini, da wani irin numfashi, wata Nurse tana faɗin wannan yaron da wuya ya tashi, da alama da ka ya dira a rijiyar ko ya samu internal injury a cikin kansa ko kuma dai a ƙirjinsa!!!YAU TAKE JAJIBERIN ZAƁE A NIGERIA, MASU ƘURI'A A HANNU KU TAIMAKA KU ZAƁA MANA SHUGABANNI NA GARI MASU TSORON ALLAH, KUN GA DAI IRIN HALIN HA'ULA'I DA MUKA TSINCI KANMU A WANNAN RINTSIN, TSADAR KAYAN MASARUFI, RASHIN TSARO, YAJIN AIKI DA SAURANSU. DUK DA BA WANI MUKE ZARGI DA SAMU A HALIN DA MUKE CIKI BA, JARABTA CE DAGA ALLAH. MUNA FATAN UBANGIJI ALLAH YA ZAƁA MANA SHUGABANNI NA GARI AMIN. 77 Dariya ce ta kusa ƙwacewa Yazid ya ce "Banda ragon azanci, ya zaki saki kayan kuma ki hau rufe jiki? Me ma zan kalla? Ki shirya a nutse" bin sa tayi da kallo, ta kasa motsawa balle ta ɗau kayan sai ɓoye jiki da take yi. Ya ƙarasa ya ɗau kayan ya ɗora mata a kafaɗarta. Cikin tsiwa ta ce "Ni ka fita na saka kaya" Shiru ya yi mata, ya wuceta ya buɗe sip, ya ɗauko kayansa yana ƙoƙarin sauyawa, alhalin da ba haka yake yi ba, sai ya ɗebi kayansa ya tafi banɗakin tsakar gida. "Wai me zaka yi haka?" "Me kika gani a hannuna? Kaya zan saka" "Kuma a cikin ɗakin nan a gabana?" Yazid ya ce "Yau naga ikon Allah, kiyi harkarki nayi tawa mana, ina ruwanki da ni ne?" Ya ƙarasa maganar yana zare singlet ɗin jikinsa. Juya masa baya tayi, dama kaya ne suke rage masa girma kokuwa dai tsananin kwarjinin da yayi mata ne?. Kwasar kayanta tayi, ta nufi ɗan mitsitsin banɗakin da ke cikin ɗakin, wanda da ƙyar take iya juyin kirki a cikin sa. Tana daf da shiga taji ya ce "Masha Allah, ƙafafuwanki gwanin ban sha'awa" Ƙirjinta ne yake dukan uku uku, tana mamakin fitsarar da Yazid ya ke gwada mata, a haka kamar na ruwansa, abin da yayi mata jiya ta tuna a ranta ta ce 'Lallai ma mutumin nan'. 'wai kayan sun gagara ki saka ne, ko sai na shigo na taya ki sawa?" Shiru tayi masa, ta gama sanya kayan sannan ta fito, ta wani haɗe rai karma ya kawo mata wargi. Shima basarwa yayi, ya ɗauki mukulli suka fita. Mamakin irin unguwarsu Yazid take, kasancewar yamma ce, galibin yaran unguwar suna gindin kwata suna suyar awara, wasu na sayar da dankali, wasu wainar fulawa. Ga azabar lunguna da kwatoci ko ina, ga uban tumaki da awaki, kana tafe kana basu hanyar wucewa, banda kajin hausa da suke nasu shagalin tsakanin layukan. Sai a lokacin yake tabattar da da tayi yinƙurin guduwa, sai ta sha wahala, wannan unguwar ai tsaf za a yi garkuwa da mutum. Ganin yadda take ta ƙarewa unguwar kallo ne ya sanya Yazid ya ce "Ki tayani addu'a, ubangiji Allah ya yassare muni na saya mana gida a duk unguwar da kike so, mu koma Allah ya kawo mini buɗi" "Ku koma kai da wa?" "Ni da matata mana" ya bata amsa Taɓe baki tayi ta ce "Ka sa a ranka kawai ajiyata aka kawo maka, daga yanzu zuwa Kowane lokaci zamu iya rabuwa" "Ba kya so na saboda ni talaka ne ko Fadila?" Ba kara ta ce "Eh, ai kaima ka san ni ba tsarar aurenka bace, na yi wani ƙaramin laifi ne Daddy ya hukuntani ta wannan hanyar, kuma na san ba zai wuce wannan banzar yarinyar ce ta saka shi yayi mini haka ba, dan haka kurum Daddy ba zai mini irin wannan auren ba kamar mara galihu". Jiki a sanyaye ya ce "Haka ne, amma Allah ya sani, ni dai ina sonki, Allah ya tabbatar mana da alkhairi" daga haka bai kuma cewa komai ba har suka isa gidan Hajiya. Ko da suka yi sallama, tana tsakar gida ta gama girki, fuskarta babu yabo ba fallasa, ta karɓesu, ta je ta ɗauko tabarma ta shimfiɗa musu. Yazid ne ya fara gaisheta, sannan Fadila ta gaisheta, gaba ɗaya matar ba tayi mata ba, mussaman yanzu da take ƙure Fadilan da ido. Hira ta shiga yi da ɗanta, amma Fadila ta lura tunda suka yi maganar nan a hanya, duk jikinsa yake a sanyaye. Fadila ta yi shiru kamar bata wurin, amma a hirar ta su, ta fuskanci akwai matuƙar shaƙuwa da soyayya tsakaninsa da Hajiyar tasa. Hajiyar ce ta tashi ta ce "Yazid tunda kuna nan, bari na shiga gidan can nayi musu jaje, an haura musu an yashe su" Yazid ya ce "Subhanallah, Allah ya tsare ya mayar da alkhairi" Ta amsa da Amin ta ɗau hijjabinta ta saka ta fita. Tana fita Fadila ta kalleshi ta ce "Ka tashi mu tafi ni na gaji" Yazid ya ce "Kiyi haƙuri ta dawo dan Allah" tayi shiru bata sake cewa komai ba. Sai da aka yi sallar magariba, sannan suka yi wa Hajiya sallama suka tafi. Amma har suka je gida Yazid bai kuma cewa Fadila komai ba. Shi ya ja su suka yi sallar isha'i tare, daga haka suka zauna kowa yayi shiru. Yazid ya ce "Zaki ci Abinci yanzu ne?" Ta ce "Eh bari in zuba" ta tashi ta tafi Kitchen da kanta, ta zubo Shinkafa da wake ce da mai da salak, cikin ikon Allah duk abin da Yazid ya dafa ya bata ba musu take karɓa ta ci. Ta dawo falon ta ajiye Abincin a gabansa, da cokula biyu ta ce "Bismillah mu ci" kallonta ya yi ya ce "Ba zan iya cin Abincin ba, kawai ki ci" "To ai naga ba abin da ka ci" "Eh zan ci ne, ki ci kawai bari in ɗan fita zan dawo" Haɗe rai ta yi ta ce "Wallahi kana fita nima fita zan yi, ni fa tsoron gidan nan nake ji, kawai kayi haƙuri da fitar mu ci abinci" Ɗan dafe kansa yayi ya ce "Da gaske na ƙoshi fa, ki ci kawai Fadila" zama tashi ta yi ta bar masa falon, dan gaba ɗaya shirun da yayi bai mata daɗi ba. Bai gaji ba ya bita ɗakin, ya tarar tayi kwanciyarta, ya ƙarasa kan katifar ya riƙo hannunta ya ce "Haba matar, fushi ki ka yi? Ki zo ki ci abinci kar ki kwana da yunwa" "Ba zan ci ba" "Tuba nake, Allah ya baki haƙuri zo muje mu ci tare, a baki ma zan baki yauwa Sweetheart" tana tura baki ya lallaɓota ta dawo suka ci Abincin tare. Sai dai ƙasan zuciyar Yazid babu daɗi, idan ya tuna Fadila tana gaya masa bata son sa kuma ba zata zauna da shi ba. Bayan sun gama ne, Fadila ta hau yi masa surutu. "Wai yau ba zaka islamiyyar ba?" "Yau Alhamis ai ba islamiyya, kuma na so naje na ɗau nawa karatun, amma kin ce idan na fita zaki fita ni kuma bana son ki tafi ki barni" dariya tayi ta ce "Ai dan kar ka tafi ka barni ne, tsoro nake ji amma ba in da zan iya zuwa, na san ma idan na fita ɓata zan yi". "Unguwar talakawa dama, idan ba wanda ya saba zama a ciki ba, na za gane kanta ba". Ta basar da zancen ta ce 'Wai duk wannan karatun naka, kai ma zuwa kake yi ana kuma koya maka?" Yayi murmushi ya ce "Eh mana, ai shi ilimi kogi ne ba a ƙure masa". Ta ce "Haka ne, to duk wannan litattafan na uwar ɗaki ka iya su?" Ya ce 'Alhamdilillah, duk na iya wasu kuma ina bincike a kansu ne". Ta ce "Lallai ka na da ilimin addini sosai" "Idan na dawo da daddare kema sai na dinga koya miki" "To, zaka koya mini larabci ma?" Ya ce "to zan saka miki kuɗin laraba, ki dinga biyana, sannan na koya miki" Dariya take, shi kuma ya zuba mata ido, yana jin daɗin yadda yau ta saki jiki da shi sosai. Ɗan shiru tayi sannan ta ce "Wai ina familynka, ko kaima auren dolen aka yi maka kamar yadda Daddy yayi mini, ko Mummy bata san ya aurar da ni ba?" Jikinsa ne yayi sanyi, Ya ɗan kalleta ya ce "Auren dole aka yi miki fa ko? Ni ba na dole aka yi mini ba, tun da ni ina son ki sosai. Familyna suna wani wuri mai nisa sosai" "To amma naga basu zo ba?" "Eh za su zo wataran" Ta ɗan yi hamma tare da miƙa, ta tashi tsaye ta ce "Bacci ya zo, sai da safe" "In zo mu kwanta tare" "A'a ba kyau" tayi maganar tana shigewa bedroom ɗin. Murmushi yayi a hankali ya ce "Ya ubangiji Allah ka ƙara sanya salama a zuciyar matata ta zauna da ni, ni kuma ka bani ikon kyautata mata". Al'amura sun yi nisa, tsakanin Abdul da kuma Yusra, dan sun samu fahimtar juna, dubu ɗari takwas ya bayar na komai da komai banda sadaki. Aikuwa Abdul ya ga kara, dan iyayenta sun nuna farincikinsu sosai da sosai, dan a yadda suke nunawa su farincikin 'yar su ya fiye musu komai. Suka nuna masa kar ya takura kansa duk abin da Allah ya bashi ya kawo musu. Sun sami fahimtar juna sosai da soyaya a tsakaninsu. Yusra kullum cikin yi masa zancen Fadila take, na haryanzu ba a san in da take ba. Yayi ta rarrashinta yana kwantar mata da hankali, yana nuna mata ai Fadila ba wani abu ne ya sameta ba, tun da dai Daddy ne ya ɗauketa. Khalil yana ta shirin komawa Abuja, amma yanayin jikin Hafsa ne ya hana su tafi, dan wataran sai Mama ta zo ta wuni tare da ita, tana shan wahala sosai da sosai akan laulayin nan. Gefe guda kuma zuciyarsa na matuƙar tausayin Mummy, duk ta firgice kamar wadda aka ce an sace Fadilan. Da kansa ya kira Daddy a waya, yana masa magiyar yayi haƙuri ya taimaka ya gayawa mahaifiyarsu in da Fadila take. Alhaji Ahmad ya ce "Kana ji na Khalil?" "Eh Daddy" "Tun tasowarku, na kasance ina biyewa abin da kuke so da wanda mahaifiyarku take so, na yi haƙuri na ɗau hakan bakomai ba, dai daga baya na gano illar da hakan da yake da shi a rayuwarku, mussaman Fadila da take mace, Fadila 'ya ta ce, ba zan yi abin da zan cutar da ita ba, dan haka ka ƙyaleni ina sane da abin da nake yi, hakan tamkar hukunci ne ga mahaifiyarku da ita kanta Fadila, kana sane da yadda suka saka na karɓi kuɗin auren mutane, suka dawo daga baya wai ba sa so, an san bata so aka kawo mini shi?, Kar ka ga laifina Khalil, da ku da mahaifiyarku duk ina ƙaunarku, duk abin da nake yi zuciyata bata mini daɗi da alaƙar da ke tsakanina da matata ta fari, amma ba yadda na iya da halinta, kayi haƙuri lokaci na nan zuwa da zan faɗi in da take" Khalil ya ce 'Shikenan Daddy. Na kammala aikin da ka sakani, kuma nima a satin nan zamu koma Abuja in sha Allah" Daddy ya ce "Masha Allah, Allah ya dafa a gaishe mini da ɗiyata". "Za taji in sha Allah, a gaida Antyn" "Zata ji in sha Allah" Baba Hassan tamkar ya zuba ruwa a ƙasa ya sha, saboda murnar ya ji zai je Saudiyya, masu taya shi murna nayi, masu yaƙe na yi, dan zukatan su Baffa babu daɗi zinƙire yake da hassada a kan yadda Allah ya ɗaga 'yarsa duk da suna cin arzikinta, dan kusan duk wata kayan Abinci da kuɗi na tafe, kuma tare da su ake ci amma basa gani. Yazid ya kammala sallolin darensa kenan, da addu'oi, Kamar yadda ya saba ya ɗora hannunsa a kan Fadila, yayi ta mata addu'a sannan ya kwanta. Ya kwanta babu da daɗewa, yaga Fadila ta tashi, fitsari ya tasheta, har ta nufi banɗakin cikin ɗaki, amma ta fasa saboda tsoro take ji, saboda ba wuta gashi bata san in da fitilarsu take ba, dan haka ta tafi banɗakin tsakar gida. Shi ma kasa shiga banɗakin tayi, ta tsuguna a tsakar tayi fitsarinta, ta tashi tana wanke ƙafarta, tayi arba da wata mage ɗirkekiya. A guja ta ƙwala ihu ta shiga ɗaki da gudu, ta faɗa kan Yazid tana rirriƙe shi. A rikice ya ce "Lafiya menene?" "Mage ce" ta bashi amsa. "Kuma sai ki dinga gudu haka? Maimakon kiyi addu'a" Cikin shagwaɓa ta ce "Mhmmm ni tsoronta nake ji, dan Allah ka tashi ka koreta, ka rufe mana ƙofa karta shigo". Ya ce "A'a nima gaskiya tsoronta nake ji" "Dan Allah ka tashi" Shima ya shagwaɓe murya ya ce "Ni gaskiya tsoronta nake ji, kuma naga kamar ta shigo ma" Sake ƙanƙame shi tayi ta na jin tsigar jikinta na tashi, saboda bata son mage. Hakan ya bawa Yazid damar nufin cikar kuɗirinsa a matsayinsa na mijinta. Yadda hannunsa ke yawo a jikinta, ya sanya ta sake shiga tsoro da firgicin gaske. Kamar wadda aka cirewa kuzari, ta kasa kayaɓus balle tayi yinƙurin hana shi, sai da taji abin nasa ya wuce tunaninta. Lokaci guda burkin sarrafa kansa ya ƙwace masa, sai da ya kai ga samun abin da zuciyarsa ta makance a kan samu. Fadila ba ta jin haushin Yazid kamar yadda ta ji haushin kanta ba, tana jinjina sokonci da wautar da tayi, na barin Yazid yayi awon gaba da abu mafi daraja a tare da ita, yanzu sai ya ce dama abin da take so kenan. Haka ya taimaka mata ta kintsa, yana jiran kwandon bala'in da zata sauke masa, amma tayi masa shiru ba ta ce komai ba. Washegari da safe ko abin karin da ya bata bata karɓa ta ci ba, ya gama surutansa da rarrashinsa amma ko kallonsa ba tayi ba. Gashi yana da jarrabawa ƙarfe sha ɗaya na safe. Ba yadda ya iya haka ya fita ya barta. Yauma yarinyar nan Maryam ita ta shigowa Fadila, Fadila ta ji daɗin zuwanta, tayi mata shara da wanke wanke. Yau Yazid saboda sauri, ko gyaran gidan bai yi ba, ya ƙare a zaman rarrashinta. Da kanta ta shiga bedroom ta tattare kayansa da ya cire ya ajiye, ta kwashe nata ma, ta gyara ko ina, tunawa tayi a gida wataran a falo ma take yada komai, sai dai a kwaso a biyota da shi, bata son ƙazanta amma bata iya gyara sai da ayi mata. Haka nan duk da jikinta babu daɗi ta gyara ɗakin. Ta dawo ta ɗauko musu abincin safen da ya dafa, suka ci ita da Maryam. Suna ta hira har sha ɗaya, ta lura yarinyar a nutse take, a hirar tasu ne ma, yarinyar take gaya mata Yazid malaminsu ne a makarantar dare, har take bata labarin 'yan ajinsa ajin sauka sunce zasu gidansa, da irin kirkin Yazid, ko a makaranta. Fadla ta ce "Suwaye 'yan ajin saukar?" Maryam ta ce "waɗan suka yi sauka, suka kuma dawowa?" "To ya za ayi maza su zo gidana?" Maryam ta ce "Ai ba maza bane, 'yan mata ne fa manya, suma suna koyarwa, ai zasu zo ki gansu". Haka nan Sai Fadila ta ji babu daɗi, har da ɗan ɓata rai. Can Maryam ta ce 'Anty, ba zaki ɗora girki ba?" Fadila ta ce "Kin iya girkin ne?" Maryam ta ce "Eh ina yiwa Antyna" Fadila ta ce "Ina mamanki?" "Ta mutu, shi ne yayata ta ɗaukeni" Tausayinta ya kama Fadila ta ce "Allah sarki, Allah ya jiƙanta to me kika iya dafawa?" "Duk abin da kike so na iya" "To tashi mu je Kitchen ɗin" Fadila saboda zama da Yusra, ta iya wasu abubuwan a girki, dan haka ta wayance, tana ganin yadda Maryam ke girkin, saboda ko bakomai yakamata Yazid ya dinga hutawa, ta dinga rage masa ayyuka. Taliya suka dafa da miya, sai azahar lokacin islamiyya sannan Maryam ta tafi, Fadila ta rasa me zata bata, dan yarinyar tana taimaka mata, alhalin ba wanda ta shiga a layin ta yiwa sallama ta ce gata ta tare, ba Yadda Yazid bai yi da ita ba, amma taƙi zuwan. Yazid ya sha mamaki da ya dawo, ya shiga Kitchen amma ya tarar da abinci. Ya dawo don ya tambayeta, duk da tunda ya dawo harara ce kawai take shiga tsakaninsu. "Sweetheart, a ina muka samu abinci". "Kaje can ka nemi Sweetheart ɗin ka" "To Allah ya baki haƙuri, waye ya kawo mana abinci?" "Dafawa nayi" ta bashi amsa. "Wow, inyee ashe ta iya girki babyn" Zumɓura baki tayi ya shareshi. Duk yadda ta so ta basar da Yazid, amma ya zuba abincin, ya dinga zuba mata santi, ta ji daɗin yabawar da yayi, amma ta shareshi dan haushinsa take ji. Tashi tayi ta koma bedroom ta kwanta abinta. Yau da daddare ta tubure ba zai hau mta katifa ba saboda ƙarfin hali, falo ya koma ya ƙyale mata ɗakin ma gaba ɗaya. Tayi juyi ya kai sau biyu, amma Yazid na kan sallaya yana ibada. Ita yawan ibadar Yazid har mamaki yake bata. Ji tayi yayi shiru da karatun da yake yi, ya tattara hankalinsa a kan wani abu, da bata san ko menene ba. Ƙasa ƙasa taji Kamar Yazid kuka yake yi. Kasa kwanciyar tayi, har ta fito ta je daf da shi, bai sani ba. Hannu ta saka ta zare hoton da yake hannunsa. Wata kyakkyawar Bafulatana ce a jiki,  mai matuƙar kyau na ɗaukar hankali. "Wacece wannan?" Ta jefo masa tambayar. Shiru yayi ya zuba mata ido, ya kasa furta komai. Littafin kuɗi ne, ku tuntuɓeni domin saya. Ayshercool 08081012143LITTAFIN KUƊI NE, MAI BUƘATA YA TUNTUƁENI A KAN LAMBAR WAYATA. 08081012143 79 Yazid ya sake numfasawa sannan ya ɗora da cewa "Na ƙarasa gaban gadon da Huzaifa yake da sauri, ina kiran sunasa cikin tashin hankali, na ga jikinsana wata irin karkarwa, idanunsa na ƙaƙƙafewa, na tafi ina ture likitocin ina riƙe Huzaifa, sai dai jikinsa ya yi sanyi ƙalau. A fusace ɗaya daga likitocin ya kalleni ya ce "Ina baban naku da ka ce zaku taho tare, kun tafi kun bar yaro babu kowa a kansa ga jikinsa ya rikice" Cikin rashin sanin abin yi na ce masa "Ba ya gari baban namu" Ya dubeni ya ce "Allah wadaram halin mutumin ƙauye da bai san komai ba sai dai yayi jima'i ya haifi yara ya sake su kamar kaji" Ba zan iya misalta baƙin ciki da ɓacin ran maganar da likitan nan ya faɗa ba, sai dai me banga laifinsa ba tun da an rasa mai zuwa ya nuna kulawa ga ɗan uwan nawa. Amma lamarin yadda lokaci ɗaya mahaifinmu ya watsar da mu na cigaba da ɗaure mini kai, na kasa manta yadda ya ke shiga damuwa idan waninmu ba shi da lafiya, akwai lokacin da kunama ta taɓa cizon Huzaifa, salla ce kawai take fitar da Baba, amma yana gida yana taya Inna jinya, amma yau Huzaifa a halin ya rayu ko ya mutu, Baba ya gaza zuwa ya ganshi. Likitocin suka cigaba da masifa, suka ɗan yi masa abin da zasu iya, suka bar ɗakin suka barni da ga ni sai Huzaifa. Na yi kuka kamar ba gobe, saboda halin da yake ciki, bani da halin taimaka masa, a halin yanzu ko motsi baya iya yi, kawai dai gashi nan a kwance. Na gama kukana na tashi na yi alwala, na samu wuri na dinga salla ina yiwa Huzaifa Addu'a samun lafiya. Sai dai cikin dare Allah ya yiwa Huzaifa cikawa. Yazid ya ɗan yi shiru ya bawa hawayen da yake idonsa damar zubowa, ya sanya hannunsa ya share, ya cigaba da cewa "Mahaifinmu ya kasa zuwa ayi yadda za ayi a ɗauko gawar Huzaifa, sai yayansa na roƙa, shi ne ya zo Asibitin da kyar aka ɗauko Huzaifa aka kawo shi gida aka yi masa sutura aka binme shi. A baya na kan yi mamakin yadda mahaifina baya jituwa sosai da 'yan uwansa, daga baya kuma na fuskanci kamar suna ɗan jin haushin mahaifina saboda dukiyar da Allah ya bashi. Aka share makokin Huzaifa, zuciyata a cunkushe da damuwa, tsakaninsa da Innarmu wata biyu ne kawai, zaman gidan mu babu daɗi, saboda takura da hantara da nake fuskanta ga ƙiyayyar da mahaifina yake nuna mini a zahiri kamar ɗan gaba da fatiha ba ɗansa ba. Gaba ɗaya na ji zaman gidan ya isheni, na ɗaura aniyar komawa makarantarmu, sai dai tuna bani da abincin da zan ci a makarantar ya sanya jikina yin sanyi, ga shi a tsukin lokacin ciwona na asma na yawan tashi, ko magani bani da shi. Mahaifina kuwa babu fuskar da zan tambayeshi, ɗakin Innarmu na sake duddubawa na samu abin da yayi saura na tattara, na je na sayar da sauran kuɗin hannuna na koma makaranta. Sai dai kuɗin hannuna na san ba in da zasu kaini, na dinga tattala su, lokaci lokaci mussaman ranar juma'a na kan shiga cikin gari, don duba sana'ar da zan yi na samu kuɗin riƙewa, sai dai da na yi aikin wahala sosai sai na kwanta ciwo. Haka na cigaba da karatu cikin tsananin wahala, ga ni ni bana aboki, saboda kar aboki ya bani abin da zai mini gori a gaba. Sai gashi wanda suke zuwa da wurin su ci a baya duk sun watse saboda a lokacin bani da shi. Idan abin ya tsananta gareni na kan tafi kibiya in da Kakata ta wurin uba take aure, idan na je ne sai ta ɗan harhaɗa mini abin da take da shi ta bani. Watarana kakata ta gama haɗa mini ɗan kayan Abincin da take da shi, ta ga ina ta shiri zan tafi ta kalleni ta ce "Ba zaka bari sai rana tayi sanyi ka tafi ba?". Na ce mata "Rano nake son na ƙarasa, idan Baba yana nan na ganshi na gaishe shi" Cikin tausayawa ta ce 'Yazid ka yi haƙuri, ka koma makarantar ka kawai ita ce rufin asirinka" Cikin damuwa na kalleta na ce "Amma saboda me?" "An riga an shiga tsakaninka da mahaifinka, dan haka kayi haƙuri ka cigaba da addu'a kawai nima ita nake yi". Cikin rashin Fahimta na ce mata 'Kenan Baba ya gaya miki laifin da na yi masa ya sanya ya dai na kulani, ni yaƙi gaya mini me na yi masa". Ta ce "Bayan abin da ya faru na rasuwar Huzaifa, na kirashi na yi masa faɗa tare da tambayar daliin da ya sanya ya bari har Huzaifa ya mutu bai je kansa ya biya kuɗin aikin ba, amma ya ce dani shi ma bai san dalili ba, kawai dai ba ya ƙaunar ganinku ne gaba ɗaya". Jikina a sanyaye na tambayeta ko wani abun muka yi masa, amma ta ce "Ba wani abu da kuka yi masa, ka cigaba da addu'a. Dan an shiga tsakaninku da shi ne" Ni dai a lokacin ban gane ne take nufi da hakan ba, na dage ni tafiya zan yi yanzu. Bayan mun yi sallama cike da son ganin mahaifina na tafi Rano, sai dai ba zan manta da wanan ranar ba, a gabana babana ya ce kar na ƙara zuwar masa gida, baya ko ƙaunar ganina. A tsakar gida a gaban 'yan uwana, suka dinga mini dariya, suna cewa Allah ya ƙara baƙin jinin uwata da baƙin halinta ne yake bibiyata da ƙanina. Kuma a haka zan ƙare cikin wahala Na riƙe ƙafar Baba ina kuka na ce "Dan Allah Baba idan laifi na yi maka ka yi haƙuri dan Allah, dan girman Allah ba za sake ba kar ka rabani da kai kai ne kawai ka rage mini ba Inna ba Huzaifa" Tsananin tausayina da soyayyata na gani a cikin idonsa, amma a zahiri a kan fuskarsa ya dinga yi mini masifa, ya ce na tashi na bar masa gida baya son ya sake ganina. Na tashi na nufi ɗakin Inna, na zauna na yi kuka na kwashi sauran kayana, na tattare kayan Inna na litattafanta, da hotunanmu na fito na bar gidan har na yi nisa sosai, ina tafe ina kuka na ji ana kirana, na tsaya na waiwaya na hangi 'yar autar su Baba Anty Sa'a. Ta ƙaraso in da nake idonta cike da ƙwalla, duk da tana cikin wanda suka nunawa Inna ƙiyayya, amma ta dafa kafaɗata ta ce "Yazid na ji abin da yaya yayi maka, dan Allah kayi haƙuri kayi ta addu'a a duk in da kake, Allah ya sa ya dawo hankalinsa, ga wannan ka riƙe ka tafi da shi makarantar idan ba dole ba, ka daina zuwa gidan nan gaba ɗaya, kar kai ma su yi maka abin da suka yiwa Huzaifa". Yazid ya ce "Me suka yiwa Huzaifa?" "Bakomai, ba sai ka bincika ba, ka tafi kawai Allah ya tsare" ta danƙa mini kuɗi a hannuna ta juya ta tafi. Na riƙe kuɗin na tafi tasha na hau mota na koma makaranta. Haka rayuwa ta cigaba, ina ji ina gani na rabu da mahaifina, ina aji biyar Sakandire Kakata da take ɗan tallafa mini ita ma ta rasu, nake ta wahala. 'yan uwan mahaifiyata su na zuwa gidanmu wurina, amma sai matan mahaifina suka ce musu wai na gudu na bar gida, ba wanda ya san in da nake na shiga duniya. Tun suna zuwa har suka daina, dan ko mutuwar Huzaifa ba wanda ya gaya musu, sai da ga baya sannan suka sani. Al'amura suka cushe mini, wataran sai na wuni na kwan ban ci abinci ba, har shugaban makarantarmu ya kan tambayeni, wai ina Babana kwana biyu ya daina zuwa in da nake saɓanin da baya rufa wata bai zo ba, na ce masa ayyuka ne suka yi masa yawa shi ya sa. A aji na uku lokacin da zamu yi Waec, abubuwa suka cakuɗe mini, in da Allah ya taimakeni na ci qualifying saura Neco. Aka canza mana wani shugaban makarantar, wanda aka kawo ya ga yadda nake da ƙoƙari, sai ya dinga amfani da ni yana neman scholarship a wurin Manyan mutane, wai a taimakawa rayuwata ina da ƙwazo kar ƙwazona ya tafi a banza, idan aka ce a kawo takarduna sai yayi ciwa-ciwa ya bada sunan wani da sunana ya karɓi kuɗi, ni da ban san me ake yi ba, sai daga baya a bakin ɗalibai na ji. Idan aka je musabaƙa, duk abin da aka samu ba ya bani wani abin kiri, naga kamar yana nema ya koma business da Alqur'ani, dan haka na daina zuwa musabaƙar, na ce ba zan sake zuwa ba, aikuwa ashe ya ƙulu, bayan qualifying ta fito na ci, amma daga baya sai ya ce ai ba duka aka biya mana kuɗin jarrabwar ba, dan haka mu nemo kuɗi. Ban yi gangancin zuwa gidanmu ba, na je wurin wani abokin mahaifina, ba dan raina yana so ba, amma ganin a kan harkar karatu ne, ya sanya na je ya taimaka mini. Amma ya ce ubana ma ya gaza ɗaukar ɗawainiyata balle shi? In yi haƙuri ba shi da shi. Rabona da garin su Inna tun tana raye, da kyar na samu rancen kudi na tafi garin nasu, sai dai na sha wahala kan na samo su dan sun koma Maraya sun bar riga. Da suka ganni tamkar su goyani dan murna, sai koke-koke suna tuna 'yar uwarsu. Yayar Inna da take bi Hajiya tana nan lokacin ta je ganin gida ta ce mini "Ina ka tafi, muka dinga zuwa garinku aka ce wai ba a san in da kake ba?" Da na so yin ƙwauron baki, amma naga bani da wata mafita, mussaman da idan na gama makaranta bani da wurin zuwa. Nan na gaya musu duk yadda ake ciki, a lokacin kakata ta tsufa, kakana kuma dama tun kan a haifeni ya rasu. Hajiya sai da ta yi kuka da ta ji irin wahalar da nake sha, suna nan basu sani ba, a ranar aka saka aka sayar da saniya guda, wai dama tawa ce ta wurin Innarmu tana da dabbobi a ƙauyen. Aka sayar da ita kusan dubu casa'in da ɗoriya, sannan ta ce da ni zata tafi cikin garin Kano in da take aure a Kano. Tare da alwashin muddin tana raye ba zan wulaƙanta ba, dan tamkar ta wulaƙanta Inna wuro ne idan na wulaƙanta. Ta tafi da ni Kano, gidanta inda take aure, sai dai bata taɓa haihuwa ba ita. Kwanana biyu a gidanta, tana ta bani kulawa nace mata zan koma makaranta, tare muka je makarantar dan taga a in da nake, tare da sayayyata ta kayan Abinci fal. Na koma makaranta ina ɗan jin daɗin na samu wurin zama idan na gama makarantata. Alhamdilillah kwanci tashi asarar mai rai, na kammala makaranta, na koma Kano wurin Hajiya, sai dai zuciyata na gida wurin mahaifina. Na sanarwa da Hajiya dan Allah ta rakani muje Rano, in ga Baba da sauran 'yan uwana, kuma idan laifi na yi masa ta tayani bashi haƙuri. Yadda Hajiya ke nuna mini ƙauna abin ba a magana, dan haka ta shirya muka je Rano tare, kusan shekaru biyu rabona da garin, sai dai bata sauya zani ba, mahaifina a gaban Hajiya ya kuma maimaita baya ƙaunata. Matan gidan nan ma da yara suka dinga zage-zage da habaici wai kamar maye tun da ya ce baya son ganina kar na sake zuwar musu gida. Ran Hajiya ya ɓaci sosai, dan sai da suka yi sa'insa da mahaifina, ba ta taɓa zaton abin ya kai haka ba, ta ce in sha Allah ba zan sake zuwar musu gida ba. Baba uwani ta ce in dai nine ita ma sai ta koreni, dan duk inda muka raɓa da uwata masifa ke bibiyar wurin. Ba ta kula su ba, muka baro Rano zuwa Kano. Mijin Hajiya ma mutumin kirki ne, ba zaka taɓa cewa basu suka haifeni ba, result ɗinmu ya fito Neco da Waec duk na yi nasara. Mijin Hajiya ya shiga ya fita na samu admission a Jami'a na ɗora karatuna na Islamic studies, amma a hakan ina cigaba da zuwa Islamiyya ƙarin karatu. Duk da yadda na samu kwanciyar hankali kullum tunanina yana gida, da son ganin mahaifina ga kewar Innata da ƙanina da suka kasa barina. Abinda na fuskanta a zamana da Hajiya shi ne ita kuma dangin miji ne basa ƙaunarta sam, tsanar da suke mata har ta shafeni nima. Ina level 2 Allah ya karɓi mijin Hajiya, sakamakon hatsrin mota da suka yi. Bayan zaman makoki, Hajiya ta ce ba zata koma Jalingo ba saboda karatuna, kuma ba zan iya rayuwar can ba. Dangin mijinta suka takura a raba gado, aka raba ta samu gidan da take ciki a yanzu. Sai da na ji tamkar in haƙura da zuwa makaranta, saboda tsananin rayuwa, abubuwa suka ƙara tsanani. Hajiya ba ta da wata babbar sana'a, nima sai faɗi tashi, sai da Hajiya ta dangana da zuwa naiman a taimako gidajen masu kuɗin unguwarmu a kan karatuna, amma abu ya ci tura, ta koma Jalingo aka kuma sayar da shanun Innata, da haka na kammala makarantar, har na je na yi service a Maiduguri. Bayan na gama na dawo na yi remidial, na koma science, a haka na lallaɓa na yi computer science diploma bayan wancan degree. Duk wannan abun ba wanda ya taɓa nema na a danginmu. Na samu Islamiyya na fara koyarwa, ɗan abin da na samo muna ci da Hajiya, tana ta mini fatan Allah ya sanya na samu aikin yi. Wani mutum a unguwarmu ya zo ya samu Hajiya ya ce ya yaba da hankalina dan Allah yana son ya buɗe Cafe in dinga riƙe masa yana biyana. Hajiya tayi ta murna, da fari da ta zo mini da maganar ban amince ba, amma ganin ita ta yarda da lamarin, ya sanya nima na anince kawai dan ba wani abin dama nake yi ba a wannan lokacin. Abu kamar wasa ya buɗe mini Cafe, kusan a cikin unguwa dai, ni wurin ne kawai Cafe. Nan da nan aka fara samun alheri, sai dai saɓanin yadda yayi alƙawari baya iya cikawa ta hanyar biyana hakkina yadda Yakamata. Bance masa komai ba kuma kuɗinsa bai taɓa ciwon kai ba, sai dai hakan ina zuwa koyon gyaran mota a wani gareji, na samu ubangida mai ƙaunata, da safe na je gareji, da yamma na je Cafe da daddare na je koyarwa aikina kenan kawai. A gareji nake samun 'yan kuɗaɗen kashewata, amma aka samu ɗan mutumin da ya buɗe mini Cafe Alhaji Hashimu ya je ya sameshi ya ce masa ina wadaƙa da kuɗin shagonsa. Mutumin nan ya zo ya dinga ci mini mutunci a kan haka, na shawarci Hajiya ta ce in haƙura in ƙyale masa wurinsa ita ma ta amince. Na je na sameshi na ce masa yayi haƙuri, ya nemi wani ya cigaba da kula masa da wurin Cafe ɗin, ni na daina. Na bar wurinsa da kwana biyu, 'yan sanda suka je har garejin da nake koyon aikin gyaran mota, ban san me na yi ba sai da muka je na tarar da Alhaji Hashimu da nake kulawa da Cafe, wai ya shigar da ƙarata na kwashe masa computers kusan goma sha biyar bayan computer biyar ce a wurin, da injin photocopy da kuma almundahanar kuɗi na POs tsananin mamaki ya sanya na kasa kare kaina, saboda mamakin abinda mutumin nan yayi mini. Aka yi ƙiyasin abin da na yi masa asara wai har naira miliyan da dubu ɗari da hamsin. Hankalin Hajiya ya tashi fiye da tunaninki, tayi kuka ta ce ba yadda za ayi na yi sata ba halina bane ba, amma mutumin nan yayi mirsisi ya ce a biya shi kuɗinsa ko ya kai ni kurkuku. Hajiya ta shirya ta tafi ƙauyenmu wurin Baba, ta sanar masa tana kuka ya taimaka kar a kaini kurkuku, amma Baba ya ce babu ruwansa, dan bai ma san haryanzu ina wurinta ba. Ta koma Jalingo ta je ta sayar da duk ragowar shanuna har da nata, ta dawo a kwana uku, lokacin ana ta shirin kai ni kotu. Mutanen unguwa suka ce ba yadda za ayi na aikata abin da ake zargina da shi, dan haka mai ɗari mai goma suna ta karo karo a biya Alhaji Hashimu kuɗinsa, amma da yake ya so tozartani ya ce ba zai karɓi kuɗi a tsinke ba. Cikin ikon Allah sai gani na yi Hajiya ta kawo kuɗin nan cif, ta ce idan sharri yayi mini, mun barwa Allah. Muka koma gida, fita ma gagarata take saboda kunya, amma mutane suka dinga mini jaje suna fatan Allah ya saka mini abin da yayi mini. Bayan faruwar lamarin ne, muka dinga jin mutane na faɗar halin Alhaji Hashimu marasa kyau. Na mayar da hankali a kan rayuwata da zuwa garejina, sai dai tun da a ƙarƙashin wani nake, ba wani abu nake samu ba. Ana haka na kuma cewa Hajiya da zan samu dama da na kuma komawa makaranta, Hajiya ta ce "Abu ne mai kyau ai, Allah ya kawo damar" Kasancewar na san kan Computer na shiga na dinga neman tallafin karatun addinin musulunci a ƙasashen waje. Sannan na nemi wani a Nigeria. Tun ina saka ran zan samu har na cire rai. Lokaci ɗaya na ji hankalina yayi gida, ina son zuwa naga babana, amma na san da zarar na gaya wa Hajiya, ba zata amince ba, dan haka na shirya bata sani ba, na tafi Rano ko da zan je Baba ya koroni na samu na ganshi na ji daɗi. Sai dai da na je Rano na tarar da Baba cikin hali na rashin lafiya, ga rashin kulawa, Mutanen gidan sabgar gabansu kawai suke yi, suna wadaƙa da kuɗinsa. Cikin damuwa na samu uwargidan Baba, nace mata "Baba Uwani meyasa ba a kai Baba Asibiti ba? Meya same shi haka?" Cikin masifa ta ce "Ban sani ba, kai da kazo ai sai ka kai shi, jarababbe ya koreka ya koreka amma ka nace sai ka ce ɗan jaraba, ko da yake ai jinin maita da ka tsotsa a jikin uwarka da rashin zuciya" ban ji haushi ba na tafi wurin ƙannensa, sai dai da ƙyar suka amince aka kai Baba Asibiti. Kan a kai shi Asibiti, na gyara masa Jikinsa, dan a cikin ƙazanta same shi. Jininsa ne ya hau sosai, baya iya komai da kansa. Aka karɓe shi aka kwantar da shi a Asibiti. Sai daga baya na kira Hajiya, na sanar da ita abin da ake ci. Aikuwa ta yi faɗa sosai da sosai a kan dan meyasa na tafi ban gaya mata ba. washegari ta biyoni, dan da nufinta ma ta taho da ni, amma halin da ta tarar da Baba a ciki ya sanya tayi sanyi. Duk wahala da ɗawainiya da Baba ya dinga yi da iyalansa da 'yan uwansa lokacin yana da lafiya, yanzu ba shi da lafiya sun gaza kulawa da shi. Kuma suka hana a firfito da kayansa da kuɗaɗensa ayi masa magani. Haka na dinga fama dan ganin Baba ya samu lafiya. Ko magana baya iya yi, sai dai idan ya buɗe ido ya kalleni yayi ta kuka, har a wannan lokacin ina jin soyayarsa a raina, gaba ɗaya na manta abin da yayi mini, burina kawai na ga Allah ya bashi lafiya. Jikinsa ya fara kyau yana sauƙi, duk da bakinsa yayi wani iri, amma a haka ya lallaɓa ya fara yi mini magana. "Gwani, dan Allah ka yafe mini abubuwan da suka faru, ni kaina ban san yadda aka yi hakan ta dinga faruwa ba, a cikin zuciyata ina so da tausayinku amma a zahiri bana iya komai. Dan Allah ka yafe mini Yazid wallahi ina ƙaunarka" Na rungumeshi a jikina na ce "Baba ka daina wannan maganar, ina ƙaunarka sosai Allah ya baka lafiya". Ya kuma numfasawa ya ce "Allah ya jiƙan mahaifiyarka da ɗan uwanka. Yazid ba zan yafewa matana ba, ban taɓa tunanin zasu mini abin da suka yi mini ba, sun haɗa kai da 'yan uwana sun cutar da ni duk saboda wannan rufin Asiri da Allah ya yi mini" ya ƙarasa maganar hawaye. Na rungumeshi ina share masa hawayen, ina jin soyayarsa na sake ratsani da farincikin ganina a tare da shi. Sai dai ashe sauƙin tafiya ne, da har na samu yayi mini magana, kamar yadda Huzaifa ya cika a kan idona, haka Baba ma ya koma ga Allah a rungume a jikina. A wannan lokacin zuciyata bushewa ta yi, na kasa kukan ma sai na zuci. Ina ji ina gani gidanmu yanzu bani da kowa, 'yan uwana kuma ganina suke kamar bare a cikinsu. Sai da aka yi sadakar bakwai, sannan na dawo gida wurin Hajiya. A daidai wannan lokacin ne kuma, na samu scholarship da na nema na Nigeria, na shiga makaranta da muka haɗu da ke. Kuma mace ta farko da na ji na yarda ki shigo cikin rayuwata, duk da ina jin tsoron sharrin mutane. A Wannan lokacin, idan bani da kuɗin motar zuwa makaranta, da an idar da sallar asuba, nake fara tafiyar ƙasa in ci ƙarfin tafiya sosai kan na hau mota na ƙarasa. Wataran na tafi cikina babu abinci, ga ciwon so na damuna, ga budurwar tawa da tsiyar tsiwa, kuma malaminmu ya sako ni a gaba. Ya ƙarasa yana murmushi duk da hawaye a fuskarsa. Ya ɗora da cewar "Ganin tsananin da wahalar ta yi mini yawa, ya sanya Hajiya ta ce lallai na je garinmu ayi batun rabon gado, a raba a bani dan da alama 'yan uwan mahaifina kansu suna zalamar dukiyar kar su cinye su bani abin da suka ga dama. Ni dai nace ta ƙyaleni kawai, na rasa iyayena balle wata dukiya. Ganin bani da niyyar zuwa ya sanya ita ta je da kanta, suka din ga yi mata gori wai ita a wa? Aikuwa ta ce tunda ba zasu raba su bani nawa ba, Next da jami'an tsaro zata zo. An kai ruwa rana kan su yarda a raba gadon nan, dan duk sun cinye abubuwa da dama, ciki har da filina da na Huzaifa da ya saya mana, bayan suna Baba ya gina wa matan ƙaton gidan gona ya ce nasu ne. Sai a shekarar nan aka raba aka bani abin da ya sauwwaƙa, dan ni ban san yadda aka yi rabon ba. Dan Hajiya ta so ta ɗaga maganar filin Huzaifa na ce ta yi haƙuri ta ƙyalesu. Bai fi watanni da rabon ba, sai gashi Allah ya kawo aurena da ke, Hajiya ba ta so, saboda abin da ya faru tsakanina da Alhaji Hashimu gani take masu kuɗi duk basu da kirki duba da wahalar da muka sha a baya da gaza samun taimako, amma na ce tayi mini Addu'a ni ina so. Aka je aka sayar da abin da na samu na gado, aka sai wannan gidan da duk kayan da ki ka gani a ciki. Fadila ba ta san iya adadin hawayen da ta zubar ba kan Yazid ya gama bata labarin ba, bata tunanin ta taɓa jin abin ban tausayi kamar wannan, ko lokacin da gari ya cika da labarin Widad 'yar gidan Alhaji Nasir Daula irin wahalar da mijinta Yusuf ya sha a rayuwa bata tunanin ta kai wadda Yazid ya sha. (Mai son ya ji waccece ƙaddarar Widad da Yusuf ya nemi book ɗin Aƙidata) Sosai Yazid yake kuka, har ya fara tari, Fadila ta saka hannayeta biyu ta tallafo fuskar Yazid ta na goge masa hawaye. A sanyaye ta ce "Allah ya jiƙan Inna da Huzaifa da kuma Baba" Jinjina mata kai yayi ya kasa Magana. "Bari na shimfiɗa mana bargo a falo, saboda na ji kana tari akwai zafi a nan sosai" ya ɗaga mata kai. Ta ɗau bargo, ta je falo ta shimfiɗa musu, ta kai musu pillow. Ta dawo cikin kulawa kamar ta goya Yazid, ta kamo hannun Yazid zuwa falo, ya nemi wuri ya kwanta yayi shiru yana jin yadda komai ke dawowa kwanyarsa kamar yanzu ake yi. "Dan Allah ka daina kuka ka ji" ya share hawayen fuskarsa ya ce "To" Ta cigaba da goge masa hawayen, wani irin tausayinsa na ratsa lungu da saƙo ma zuciyarta. Taɓa shi ta kuma yi, ta ji yayi bacci ma a haka. Ta tashi zaune tana kallon in da yake kwance. Ta saka hannu ta toshe bakinta, ta koma gefe ta fashe da kuka. A hankali ta ce "I don't know what you are going through, na sake jefa ka a damuwa, na dinga yi maka wulaƙanci. Allah sarki kullum fuskarka cikin murmushi ba mai cewa you are going through all this hardship. Na dinga yi wa yanayinka dariya, kana taimakona, kana kulawa da ni, amma nake ta maka wulaƙanci, ƙila da a lokacin na san halin da kake ciki da na taimaka maka. Mutane da yawa muna ganin murmushinsu, ba tare da mun san meye a ƙasan zukatansu ba, wani kyautatawarmu ita kaɗai ce silar farincikinsu. Why would I do all this to him, bai kamata ba abin da na yi, bayan wahalar da yake ciki". Sai da ta yi mai isarta, sannan ta tashi ta koma kan shimfiɗar su, shi tuni yayi baccinsa ma. Kwanciya ta yi a jikinsa, ta rungumeshi sosai tana kuka. Allah sarki wataƙila akwai ire-iren wanda suke a irin halin da Yazid ya ke ciki, suka je neman taimako gidansu amma Mummy ta hana. Lokacin ji take da zata haɗu da waɗanda suka zalinci Yazid a rayuwarsa sai ta rama masa. "Am sorry Yazid, in sha Allah ba zan rabu da kai ba, ina son ka yi farinciki ba zan sake barin na kuma kuskuren saka ka a dmauwa ba, wadda ka shiga a baya ma ta isa" haka tayi ta surutai tana kuka!. Ayshercool 08081012143LITTAFIN KUƊI NE, MAI BUƘATA YANA IYA TUNTUƁATA A KAN LAMBAR WAYATA 08081012143 80 Gaba ɗaya idon Fadila ya bushe, bacci ya ƙaurecwa idonta sai tunani da koke-koke, Yazid kuwa baccinsa yake dan yau ko damar tashi sallar dare bai yi ba. Sai gefin Asuba sannan ta samu bacci ya ɗauketa. Kan Yazid ya fita sallar Asuba ya tashe ta, amma har ya je ya dawo ba ta tashi ba. "Habibty, ki tashi gari ya yi haske amma baki yi salla ba". Da ƙyar Fadila ta iya tashi, saboda yadda jikinta duk ya mutu, ga kuma rashin bacci da ba ta samu ba jiyan. Da ƙyar ta iya tashi tayi alwala ta zo ta yi salla, tana idarwa ta kuma kwanciya a kan bargon ta takure jikinta ta cigaba da bacci. Yazid ya 6 "Fadila ko azkar fa baki yi ba, kika kuma kwanciya" yayi maganar yana ɗagota. 'Ni dan Allah ka ƙyaleni bacci nake ji" tayi maganar a shagwaɓe tana sake lumshe ido. Cikin rarrashi ya ce "Dan Allah a tashi ayi azkar, sai ki cigaba da baccin". Zamewa tayi daga jikinsa, ta kuma kwanciya tana lumshe ido, kallonta yayi yana murmushi, yana sake jin sonta da ƙaunarta a cikin zuciyarsa. Amina kuwa kwanakinsu huɗu a Saudiyya, Amina jinta take kamar ba ita ba, wai ita ce yau a ƙasa mai tsarki Allah sarki rayuwa. Babban abin da ya ƙara farantawa Amina rai, shi ne yadda Alhaji Ahmad ya biya kuɗin umara har Inno, ga Hajara da su Zakiru. Amina ta rasa in da zata saka kanta dan daɗi, sai dai tun a Nigeria Amina ta fuskanci tana da ciki, sai rashin lafiya ta ke yi a tsaitsaye, amma tayi shiru da bakinta ba wanda ta bari ya gane, ga zazzaɓin dare da yake damunta, amma ta mayar da hankali a kan ibadarta sosai da sosai, tana gaya wa Allah buƙatunta. Khalil ma ya bar Kano, suna can Abuja da shi da Hafsa, yana tattalinta da kuma cikin da yak jikinta, gefe guda kuma ga shirin bikin Abdul da suke ta yi. A hankali tayi juyi, ta jiyo Yazid yana ta aiki a tsakar gida, ya gama komai na aikace-aikace, ta tashi jikinta duk a mace, ta naɗe bargon ta kai ɗaki, ta shiga toilet ɗin bedroom ta hi brush ta dawo tsakar gida ta kalleshi ta ce "Sannu da aiki" Ya ɗago ya kalleta ya ce "Yauwa Madam, baccin ya isheki?" 'Alhamdilillah, ya isheni yunwa nake ji dai" Yazid ya ce "Ga kunu na dama, na sayo mana dankali naga kamar kin gaji da ƙosan" Fadila ta ƙarasa tana leƙa Kitchen ɗin ta ce "Nuna mini yakake dama kunun?" Yazid ya ce "Ai na gama, da kin ta so tun ɗazu da kin gani" kuma leƙawa ta yi, ta hango ɗan ƙaramin buhun shinkafa, da galan ɗin mai ga kuma kayan miya, duk a Kitchen ɗin. Zama tayi a kusa da shi ta ce "A ina ka samu kuɗi?" "Allah ne ya bani" ya bata amsa. "A ina?" "Ai tunda Allah ya sa na aureki, Allah yake buɗe mini ƙofofin arziƙi ya ko ina, kina bacci na je gidan Hajiya, abokin baba ne yayi mana biyan bashi da kuma sauran dukiyar Baba da take hannunsa, aka raba mana aka sako mini nawa ta account, shi ne na sai mana kayan Abinci mu da Hajiya. Da daddare in Sha Allah zamu je ki sai kayan sawa da na kwalliya wanda zan iya saya. Dan Allah ki ƙara haƙuri kin ji Fadila, komai lokaci ne zai wuce in Sha Allah zan cigaba da ƙoƙarin ganin komai ya tafi dai-dai". Ɗan shiru ta yi sannan ta ce "Amma tunda kana da takardun karatunka a ƙasa, ka je wurin Daddy ya samo maka aiki mana" Yazid ya girgiza kai ya ce "Da akwai buƙatar hakan da yayi tun kan ya bani ke, ni dai dan Allah kiyi haƙuri ba sai na je ba komai zai wuce kin ji?" Tayi ajiyar zuciya ta ce "Zubo mana abincin mu ci" Yazid ya zuzzuba musu, shi yana daga Kitchen, ita kuma tana daga waje suka karya, sai dai tana ankare da yanayin Yazid yau ba ya cikin walwala. Bayan sun gama, ta tattare kwanukan ta wanke, suka koma falo, kallonsa kawai take yi, tana tunanin wane abu za ta yiwa Yazid wanda zai sa ya ji daɗi, ya rage raɗaɗin abin da yake damunsa a zuciyarsa a tsawon lokaci. Yana ɗago ido suka yi ido huɗu, murmushi yayi mata ya ce "Meye kika kallona?" "Me nake kallo?" Ta ɗan yi maganar cikin tsiwa. "To ni ina na sani, ai ke zan tambaya". Ta ce "Hmm, ni yaushe zamu je Taraba wurin kakarka?" Ya ɗan yi murmushi ya ce "Ai bata wani gane mutane sosai, ta tsufa sosai da sosai, zasu zo ne Rano nake son zuwa" "Ka je kayi me a can?" "In ga 'yan uwana mana" ya bata amsa. Haushi ne ya kama Fadila ta ce "Me zaka je ka yi musu kuma? Wai kai baka zuciya ne? Kodayake ni ka raina a makaranta da kace bani ba kai kayi fushi" tayi maganar tana tura baki. Tashi yayi ya matsa kusa da ita, ya rungumeta yana mata magana a kunne "Wancan lokacin ma ina cikin damuwa ne, kuma ina fargabar Kankiya ya rabani da karatuna. Amma na azabtu a wannan lokacin mussaman da nake zuwa ina ganinki kina ganina amma ba zan iya yi miki magana ba. Na kuma zo ina kallonki cikin damuwa na zo ko Abincin kirki bana iya ci, saboda yanayin da nake ganinki. Mace ta farko da ta shiga zuciyar Yazid, da nake jin idan ba ke ba Yazid, Allah ne ya dubeni ba da dabarata ba, ba da komai ba na sameki ni na san bani da abin da zan iya aurenki da shi Fadila, amma believe me ina sonki sosai da sosai, dan Allah kiyi haƙuri da yanayin da nake ciki na babu amma na san komai lokaci ne" ya ƙarasa maganar yana lumshe idanunsa da suka yi ja, ya ɗora hancinsa a kan nata suna jin numfashin juna. Gaba ɗaya jikinta ya saki, ta yi shiru tana sauraren Yazid tare da jinta a gajimare. "Talk please" yayi maganar ba tare da ya buɗe idonsa ba. Ita dai tayi masa shiru dan bata san me zata ce masa ba. A hankali ya haɗe bakinsu, yana kissing ɗin ta, ya buɗe idonsa ya kalleta ya ce "yau ba za a wanke bakin ba?" Dariya tayi ta tashi zaune ta ce "Ba zaka fita bane yau?". Ya ce "Korata ma kike kenan, to ba in da zani, muna gidan nan tare sai Allah ya kaimu yamma zan fita, idan na dawo daga makaranta kuma sai mu fita" Tare suka wuni a gidan, suka yi girki tare, sai yamma ya shirya zai fita, ita kuma ta tsiri shagwaɓa wai ba zai fita ba. Yazid ji yake kamar ya koma yayi zamansa, gani yake kamar a mafarki, Fadila na ta lallaɓa shi tana bashi kulawa. Bayan fitar Yazid, Fadila ta ƙara gyara gida, ta ji sallama. Leƙowa tayi daga falo, ta ga Maryam. Fadila ta ce "Maryam, ina kika shiga kwana biyu?" Maryam ta ce "Ina nan Anty, ni da 'yan makarantarmu ne na yo gaba na bar su, wai zasu zo su gaisheki" Fadila ta ce "To Allah ya kawo su" suna cikin maganar kuwa suka ji sallama. Fadila ta amsa musu ta ce su shigo, zaratan 'yan mata ne su kusan takwas suka shigo, haka nan gaban Fadila ya faɗi da ta gansu. Ta daka ta basu wurin zama, suka shiga gaisheta, kamar karta amsa amma sai ta tuna alƙawarin da tayi wa kanta na ta daina wulaƙanta ɗan Adam. Dan haka ta sake ta amsa musu. Ta je Kitchen ta ɗauko musu pure water a plate, ta kawo musu. Ta ɗora da cewa "Gashi ban san da zuwanku ba, da na yi girki da ku" "Wallahi bakomai kar ki damu, mun gode sosai hakan ma, a gaida malam" Suka ajiye mata wata leda suka tashi suka tafi. Fadila ba ta kula da kayan da suka kawo mata ba, Maryam ta shiga bata labarin ɗaliban da sunansu, har da wadda ta ce tana son Yazid amma shi bai ma sani ba. Fadila ta kawar da hirar, Maryam ta fara tayata aikin Abincin dare. Yayar Maryam ce ta zo dan kiran Maryam ɗin ta aiketa, sai a nan nema suka gaisa da Fadila, amma ba dan haka ba ko kalar Fadila Maryam ba ta sani ba, saboda babu wanda ta shiga ta yiwa sallama. Bayan la'asar sosai sannan Yazid ya dawo, ta kawo masa abinci yana ta mata hira, amma ya ga tana basarwa ta ƙi kulashi, sai yayi shiru ya fara cin abincin, ya kammala ya fita da kwanon da kansa ya dawo ya zauna yana satar kallonta. "Wai suwa kake koyarwa a makarantar da kake zuwa ne?" Ta jefo masa tambayar unexpected. Yazid ya kalleta ya ce "Ɗalibai mana" "Maza ko mata?" Ta tambayeshi tana tsareshi da ido. "Duk wanda ta kama ina koyarwa amma menene?" "Ba wani duk wanda ta kama kana koyarwa, 'yan mata kake koyarwa". Ta ƙarasa maganar tana harararsa. "To Fadila laifi ne dan na koyar da su ɗalibaina ne" Ta ce "Au sunana ma haka kake faɗa kai tsaye Fadila ko, to ɗaliban naka sun zo har da budurwar ka" Ya waro ido ya ce 'Ni ɗin, ni ina naga wata budurwa? Wallahi Fadila ɗalibaina ne" Kicin-kicin tayi da fuska ta ce "Oho maka dai, ga abin da suka kawo can a ajiye maka" Gaba ɗaya Yazid ya shiga damuwa, ya zauna a gabanta ya riƙe hannunta ya ce "Wallahi Fadila ni bani da wata budurwa, ɗalibai na ne kawai ni bakomai a tsakanin mu" murmushi ta yi ta ce "To shikenan na yarda". Murmushi yayi ya ce "Meyasa ba kya son nayi budurwa?" "Au budurwar zaka yi? Wallahi duk ranar da na tabattar da kayi wata budurwa sai dai ka dawo ka tarar bana nan" Murmushin sa da ya saba yayi ya ce "Babu ma abin da zai kaini, dan Allah Fadila kina sona?" Yayi maganar cikin marairaicewa. Kallonsa ta yi ta kwashe da dariya, har hularta na cirewa daga kanta. "Fadila meye ya baki dariya kuma?" "Bakomai, miƙo ledar nan na ga me 'yan matan naka suka kawo mana" "Ba zaki daina wannan zancen 'yan matan ba ko?" Rungumeshi ta yi ta ce "Gwani ɗan Inna" Lumshe idonsa yayi yana jin daɗin yanayin. "Dan Allah ko sau ɗaya Fadila, bana son na cigaba da zama da ke ina takura miki ba kya sona" Miƙa masa hannunta ta yi ta ce "Biyani sai in gaya maka ina sonka ko bana sonka" Gani ta yi jikinsa yayi sanyi, yana cigaba da kallonta. Ta kai hannunta fuskarsa tana cigaba da murmushi. "Fadila da kin san matsayin da kike da shi a wurina kuwa, da kin san matsayin da kike da shi a nan da baki ɗau maganata wasa kina dariya ba" yayi maganar yana nuna saitin zuciyarsa. "Meye a nan ɗin da ka nuna" tayi maganar tana dariya. Yazid ya ce "Irin abin da yake cikin ƙirjinki" "A'a gaskiya da banbanci ƙirjina da naka ba ɗaya bane, kenan bani da maraba da maza" a tare suka yi dariya yana cewa Allah ya shiryeki. Yau ko makaranta bai je ba, Ya sa Fadila ta shirya suka fara zuwa gidan Hajiya, sannan suka wuce titi ya samar musu napep, wani store suka shiga, Fadila ta ɗan sai abin da take buƙata, suka wuce ya sai musu Abinci sannan suka dawo gida. Fadila ta ji daɗin fitar da suka yi,haka kurum ta tsinci kanta cikin nishaɗi. Sai da suka dawo suka ci Abincin dare sannan ta bi ta kan kayan da ɗaliban Yazid suka kawo mat, turaren wuta ne suka kawo mata, fal da humra. Ta turawa Yazid gabansa ta ce "Ga abin da 'yan matanka suka kawo wa matarka" "Ai ke suka kawowa bani ba" "Ai sai ka yi musu godiya, idan ma dai 'yan matanka ne ba damuwa fa, da na ƙara gaba sai ka yi aurenka". Shiru yayi mata, duk sai da ta ɗan gane bai ji daɗin abin da ta ce ba. Ya ƙi kulata, ta shirya kwanciya ta kwanta, shi kuma yayi zamansa ya buɗe Alqur'ani ya fara tilawa. Kusan awa biyu, amma ba shi da niyyar tashi. Dan haka ta fito daga net ɗin ta dawo kusa da shi ta zauna. Miƙa hannu ta yi ta rufe Alqur'anin, amma ya shareta ya cigaba da yi da ka. "Ka shiga time ɗina fa sir" ta faɗa tana riƙe masa hanci. Yazid ya ce "Ke, sai kin ƙarasani tukuna? Ke da ba kya so na wane time ɗin naki na shiga?" "Ni zaka yiwa wayo, fushi kake da ni ko?" Ya ce "Ni na isa na yi fushi da ke?" Ta ɗan sauke numfashi ta ce "Zid ina gane wa idan abu bai maka daɗi ba, amma sai ka danne fushi da murmushi, shikenan dai mu je ka kwanta" Kamar ƙaramin yaro ya noƙe mata kafaɗa. "To ƙaddara ina sonka, shikenan" "Ba shikenan ba, anjima kuma sai ki ce ba kya so na" Murmushi Fadila ta yi ta ce "Bayan ka gama tofeni da Addu'a cikin dare, kana sa mini hannu a riga ai ina jinka wataran". "Sharri zaki mini" "To ka ce ba ayi ba mana, kana ta tofeni da Addu'a, ka mallekeni" Yace "Ni addu'a kawai nake miki ta kariya, ni ban san zancen da kika gama ba" haka suka kwanta Yazid yana jin farincikin ganin Fadila na nuna masa kulawa da soyayya. Sannu a hankali ta gama sakin jiki da shi, ta rungumi rayuwa a yadda ta zo mata, ta rungumi Yazid da sai a yanzu ta gano yadda take mutuwar son sa. Sai da Amina suka yi wata da sati uku, da tafiyarsu Lagos zuwa umara, sannan suka dawo Kano. Tun da suka dawo Daddy yake fargaba, dan ya san halin Zainab sarai. Jin labarin su Amina sun dawo, ya sanya maƙwabta suka dinga shigowa sannu da zuwa suna yi wa Amina sannu da zuwa. Zakiru da Hajara kuwa duk garuruwansu suka wuce, domin suma su samu su ɗan huta sannan su dawo bakin aiki. Kamar yadda Daddy ya tsammata, haka Hajiya Zainab taje ta titsiye shi, cikin faɗa da tashin hankali, a kan lallai ya gaya mata in da Fadila take, amma still ba ta samu wata gamshashiyar amsa daga gareshi ba, hakan ya ƙara tunzarata, tayi masa cin mutunci san ranta ta koma sashinta ta zauna ta dinga kuka kamar ƙaramar yarinya. Washegari da sassafe Hajiya Zainab ta shirya ta nufi Dutse,bata tsaya ko ina ba, sai gidan kawun Alhaji Ahmad, gaba ɗaya mutan gidan bin ta ska dinga yi da kallo, dan rabon da ta tako taje Dutse har sun manta, balle ta je gidansu, amma yau suka ganta a gidan. Ta sanar musu da wurin Kawu ta zo, suka je suka yi mata iso a wurnsa. Shi kansa mamakine ya kama shi, tare da tambayarta ko lafiya? Fashewa da kuka Mummy ta yi ta ce 'ƙarar Ahmad na kawo maka, yau an kusa shiga wata na uku, ya ɗauke mini Fadla ya kaita in da ban sani ba, nayi-nayi ya ƙi gaya mini in da take" Kawu ya ce "Ke Zainab ban da abinki wannan ai abin da zaku iya sasanta kanku nex. "Nifa na yi iya yina, amma yaƙi saurarata ni dai ku saka baki ya gaya mini in da 'ya ta take". Kawu ya ce "Shikenan, zamu zo gidan naki in sha Allah, ki koma gida" jin ya bata tabbacin zai zo ya saka Alhaji Ahmad a gaba ya gayamata in da Fadila take, hankalinta ya ɗan kwanta, ta fito ta fice. Tana ƙofar gida tana shirin kunna mota, sai ga wata ƙanwarta, tana ganinta ta ce "Laa Anty Zainab, dama kin shigo Dutse Baba Auwalu ya dawo daga umara mun ji abin arziƙi Allah ya saka" Ko saurarata ba tayi ba, ta ja motarta ta bar wurin, dan ga san ta tsaya ne ta gaya mata Baba Auwalu ya dawo dan gulma, tunda sun san kishiya ce ta saka aka biya masa. Fadila kuwa ta kwantar da hankalinta, tana rayuwarta sannu a hankali da Yazid, wata irin soyayya suke yi kamar su cinye juna take, ji take yi Allahn da ya haɗata da Yazid ne kawai zai iya rabata da shi, saboda yadda yake kulawa da ita ne da yake da biye mata da yake yi, ya sanya take taɓararta son ranta. Tana matuƙar tausaya masa saboda labarin rayuwarsa da ta ji, yayin da shi ma yake tausaya mata na wannan sauyin da ta samu lokaci guda. Yau ma suna kwance ya gama yi mata ƙarin Alqur'ani, da litattafan Addini. Fadila ta fuskanci cewar ƙarancin ilimin addini ya taka muhimmiyar rawa a rayuwarsu, da ya sanya suke aikata wasu abubuwan. Suna kwance Fadila ta ɗora masa ƙafafuwanta a jikinsa. Yana jinta tana neman magana amma yayi mata shiru. Can ya kira sunanta "Matar" "Mmmm" "So nake muje Rano" Yazid yayi maganar yana murginawa kusa da ita. Fadila ta ce "Mu je mu yi me?" Yazid ya ce "Muje kiga 'yan uwana da dangina mana, idan Allah ya bamu haihuwa ma kinga kin san in da dangina suke" Fadila ta ɗan yamutsa fuska ta ce "Waye zai haihun?" "Ke mana Habibty" Fadila ta ce "Taɓ, gaskiya na yi ƙanƙanta da wata haihuwa" Yazid ya ce "Au Ba zaki haihu ba amma kin iya zuwa ki sakani gaba kina a baki time ɗinki ko kina lallaɓani?" Yayi maganar cikin zolaya. Dariya Fadila ta yi ta ce "Nake lallaɓaka ayi me? Ka jika har da sharri abin naka, to amma dai ka san ba a haka aka kawo maka amanata ba ko? Saliha ce ni ba abin da na sani" "Mhmm shiyasa idan na zauna kusa da mutum a makaranta yake rawar jiki ko?" Buɗe baki tayi ta ce "Laaa wai haka ka iya sharri Zid?". "Kice ba ayi haka ba? Kullum kina liƙe da ni, ni matsa ki bani wuri na yi bacci" rasa me zata yiwa Yazid ta huce tayi ta ɗau pillonta tana kwaɗa masa. Dariya yake yi, ya ja hancinta ya ce "Ki kwanta kar mu kasa tashi gobe in Allah ya kaimu". Fadila ta tura baki ta ce "Wallahi zan rama, dani kake zancen" ya rungumeta yana murmushi. Wuta aka kawo, haske ya gauraye ɗakin Fadila ta ɗan rintse idanunta ta ce "Dama baka kashe fitila ba" "Eh, tashi ki kashe mana" "Naƙi ɗin" ta faɗa tana lumshe idanunsa. Gani yayi ta zabura ta tashi da sauri, shima ya tashi zaune ya ce "Wifey menene?". "Zid kaina ne ya fara yi mini irin wannan ciwon da na kwanta a asibiti" A gigice ya ce "Subhanallah ko jinin naki ne ya hau?" Ta girgiza masa kai ta ce "Zid kaina zai fashe, duhu fa nake gani". Take ya gigice "Fadila menene?" Yayi maganar yana riƙeta. Fizge-fizge ta dinga yi tana neman ta fita hayyacinta. Yazid ne ya fara yi mata addu'a yana tofa mata, amma sai mimmiƙewa take tana wani irin numfashi. "Bana ganinka fa Zid, duhu nake gani kaina zai rabe biyu, bana gani fa" Sosai ya rungumeta a jikinsa, ya ɗora hannunsa a kanta yana karanto mata addu'a. Su Kawu ne zaune a falon gidan Alhaji Ahmad, ga Hajiya Zainab duk suna zaune a falo. Kawu Hamza ne da Kawu Ali ƙannen mahaifin Alhaji Ahmad, da suka yi wancan zaman tare da su lokacin da za a gaya mata auren Alhaji Ahmad. Kawu Hamza ya ce "Ahmad, kar kace mini ba tare da saninta ka yanke hukunci da ka yanke ba, ace tsawon wannan lokaci ba ta san in da ka kai mata 'ya ba?" Daddy ya ce "Kawu ban yi mata haka ba dan na wulaƙanta ta, sai dan sanin cewa idan na gaya mata zata iya ɓata komai" A fusace fuska duk hawaye ta ce "Ni bana son wani dogon jawabi, ka gaya mini in da 'ya ta take, saboda rashin tausayi da imani ka ɗauke mini 'ya ka kaita wani wurin, kuma ka ɗau matarka kayi tafiyarka ka barni ko na mutu ko na rayu ba ka damu ba, ina ka kai mini 'ya ta?" Daddy ya ce "Na aurar da Fadila ne ha mutumin da ya dace da rayuwarta" Cikin rashin fahimta ta ce "Kamar yaya?" "Kamar yadda nake gaya miki, Fadila na ɗakin mijinta yanzu haka" Kawu Hamza ya ce "Haka ne, a Dutse aka ɗaurawa Fadila aure, sai dai mu bamu san ne gaya miki ba!!! Ayshercool 08081012143LITTAFIN KUƊI NE, MAI BUƘATA YA TUNTUƁENI A KAN LAMBAR WAYATA. 81 "Ahmad kana cikin hayyacinka kuwa? Ko dai ka sha wani abun ne?" Daddy ya ce "Tun da nake da ke na taɓa shaye shaye ne?" Cikin ƙunar rai ta ce "Zata iya yiwuwa ka fara a 'yan tsukin kwanakin nan, wace irin maganar banza ce haka kake yin ta? ta yaya zaka yiwa Fadila aure babu sani na, aure ba shiri bakomai kamar auren dabbobi" Daddy ya ce 'Ai dama nine nake da alhakin aurar da ita ga mutumin da ya dace ba ke ba. Da fari kin kawo naki zaɓin kun dawo kun janye, kun zubar mini da mutuncina a idon a duniya, dan haka na aurata ga wanda na ga ya dace" Ta kalli Daddy ta ce 'Ahmad so kake ka ga na haukace ina bin bola saboda baƙin cikinka ko? To da ikon Allah, sai dai kaga haka a kanka, kuma na baka nan da awa ashirin da huɗu duk in da 'ya ta take ka fito mini da ita, idan ba haka ba wallahi kotu zan kai ka azzalumi mara imani Ahmad ka kasheni ka huta kawai mana" Kawu Ali ya ce "A'a Zainab ba a haka, bai kamata kiyi haka ba uban 'ya'yanki ne fa, dan Allah ku zauna kuyi sulhu a tsakanin ku" A fusace ta ce "Babu sulhu a tsakanina da wannan mutumin, dama ai kune kuke shirya kowane munafunci, kuma kuke ƙara goya masa baya, komai yayi ai daidai ne a wurinku, tunda ni ba 'yar ku bace ba dole ku dinga goya masa baya, to wallahi na gaji da baƙin cikin da mutumin nan yake ƙunsa mini a cikin gidan nan, wallahi ƙararsa zan kai muddin bai dawo mini da 'ya ta ba, ai ba shikaɗai ya haifeta ba" ta tashi fuuuu ta bar falon. Su Kawu sun yiwa Daddy faɗa sos6, tare da nuna masa rashin kyautawar abinda ya aikata na aurar da Fadila ba tare da ta sani ba, ko a lokacin su kansu sun yi masa magana a kan wannan wane iri aure ne bagatatan kamar yaƙi, amma ya ce musu yana da dalili, ya yi ta basu haƙuri dai suka tafi. Ba ƙaramin tausayin Hajiya Zainab ya ji ba, shi kansa ya ga uwar ramar da tayi bayan dawowarsu, ya san tana cikin damuwa, amma yanzu da zarar yayi wani yunƙuri ci masa mutunci za ta yi, amma bai haƙura ba, ya nufi sashinta, duk dan ya samu a zauna lafiya, amma yana shiga ta dinga zazzaga masa masifa da tashin hankali, sai da ya gwammace bai je in da take ba. Yana bata haƙuri da lallaɓata tana buntsirewa tana cin mutuncin sa dana kwaunnan sa. Take ya ji zuciyarsa ta kuma bushewa, bama ya dana sanin auren da ya yiwa Fadilan, a ransa ya sake ganin hakan shi ne daidai. Da ya aurar da ita ta je tana irin halin mahaifiyarta, gara da Amina ta bashi Shawarar yin haka. Yana zuwa sashin Amina kuma, ya tarar da ita a toilet, tana ta sheƙa uban amai, kamar zata amayo kayan cikinta. Take ya manta da zafin da Hajiya Zainab ta haɗa masa, ya tattara hankalinsa a kan Amina, ya shiga toilet ɗin ya taimaka mata ta gyara jikinta suka fito yana mata sannu. Ta kalleshi ta ce "Dear ina su Kawun ko har sun tafi?" Daddy ya ce 'Eh sun tafi" Ta ce "Subhanallah, yanzu ya kuka yi ni da muka dawo gani nayi ta rame sosai, yakamata kawai a gayamata gaskiya in da Fadila take" "Meenal, kin san halinta lokacin da ake lallaɓata a lokacin take wulaƙanci, dan haka ki nar wannan zancen tukuna tun yaushe ne ba ki da lafiya?" Tunani tayi idan ta ce masa ta kwana biyu zai ji babu daɗi, dan haka ta ce masa "Yaune kawai na tashi cikina babu daɗi, nake ta amai" Ya ce "Shirya muje Asibiti a duba mini ke, na tsorata da wannan aman". Babu musu ta shirya, suka fita domin zuwa Asibiti, a hanya ne Amina take bashi shawara yakamata ya kira Yazid ya ji suke, idan da dama ma ya je da kansa ya duba su" Daddy ya ce "Ai da muna Lagosa na kirashi, ya ce mini babu matsala, ba zan je ba yanzu zan kuma kiransa dai a waya, ko na gayyace shi gida na ji abin da yake wakana, amma ba zan je ta ganni ba zan iya mayar da aikin baya" Amina ta ce 'Kuma haka ne, to Allah ya jishe mu alkhairi" Ya amsa mata da Amin. Bayan gwaje-gwaje da yakamata ayi mata, likita ya tabattar da tana da ciki. Dama ita ta sani, Daddy sai murna yake yi, sai dai ta wani fannin Amina bata wani murna, saboda zata fara zuwa makaranta, gashi da alama cikin mata ya zo da laulayi, sai dai ba ta son ta ɓatawa Daddy rai, dan haka ta biye masa yana ta murna yana Addu'a Allah ya bar masa. Wata irin miƙa Fadila take tana nishi, sai jujjuya kai take yi, Yazid ya dinga karanta mata Alqur'ani ta dinga mimmiƙewa tana wani irin gunjin kuka, ya daɗe a rungume da ita yana yi mata Addu'a, kan Allah ya taimake shi jikinta ya saki ya yi sanyi ta hau bacci. Mamaki ya shiga yi, dama Fadila na da iska ne? Amma shi bai taɓa ganin alamar hakan a tare da ita ba to yaya aka yi haka ta faru? Hajiya Zainab kuwa ji tayi kamar ta sha guba ta mutu dan baƙin ciki, ta rasa in da zata saka kanta bata san da me zata kwatanta irin abin da Alhaji Ahmad yayi mata ba. Kamar yadda ya zame mata kamar wahayi duk abin da ha sameta sai ta sanar da su Hajiya Salma, haka ta ɗau mota ta tafi shagon Hajiya Salman, aikuwa ta tarar da ita da Hajiya Turai duk suna tare. Suna ganin a yadda ta zo suka san akwai damuwa. Aikuwa ta zazzage musu duk abin da yake faruwa. Hajiya Salma ce ta kwarara ashar ta ce "Ban taɓa ganin azzalumin mutum da baya tsoron Allah ba, yanzu ƙiyayyar har ta kai ga haka? 'yar da ya haifa, wallahi mutumin nan baya tsoron Allah, kuma ko ki yarda ko karki yarda wannan sheɗaniyar Yarinyar da yake tare da ita, ita ce take yi masa asiri, gara tun wuri ki bazama ki nemi abin yi, idan ke ba zaki iya ba mu sai muje mu nemo miki taimako. Kina kallo yanzu ko kuɗaɗen da kike samu a wurinsa yaushe rabon da ki samu? Duk ta toshe komai ita kaɗai take samun komai ta nayar da ke hoto, wai ma wa ya aurawa Fadilan?" Jiki a sanyaye Mummy ta girgiza kai ta ce "Nima ban sani ba" Hajiya Turai ta ce "Ni na ma rasa bakin magana, ƙarshen raini da wulaƙanci dai yayi miki shi, dole ki san duk yadda zaki yi ki nemo 'yarki" Yadda suka dinga zigata suna nuna mata Daddy ya gama wulaƙantata ne ya sanya ya kuma hawa, har take jin a duniya ta ƙara tsanar uban 'ya'yan nata. Yazid kuwa kusan raba dare yayi yana yiwa Fadila Addu'oi. Da Asuba ko sallar asuba bai fita ba a gida yayi salla, ya tasheta tayi salla, da yayi mata batun ya jikinta? Sai ta ce masa ai ita lafiyarta ƙalau babu abin da ya sameta gaba ɗaya. Yazid ya bar maganar a ransa, sai da ya saka mata ido sosai, wurin kula da ibada da Addu'oi, duk da wasu lokutan sai sun yi faɗa dan tana cewa ya takura mata. Kwana kusan biyar, ta ware sosai ya kuma taso mata da maganar za suje Rano. Ita kwata kwata bata son zuwa Ranon nan, dan ba ta ga abin da Yazid zai koma yayi a garin da suka nuna basa buƙatar sa ba. Ita kanta Hajiya mita ta dinga yi, a kan Yazid ya haƙura da Ranon nan, amma yayi ta lallaɓata yana bata haƙuri. "Dan Allah Hajiya kiyi haƙuri ki bari na je, na kai musu Fadila ma su gaisa, tun da 'yan uwana ne babu yadda na iya, yakamata ta san suwaye dangina, idan aka kwana biyu kuma sai mu je Jalingo" Hajiya ta ce "Dan dai ka matsa ne Yazid, amma ni banga amfanin mutanen nan a tare da kai ba, bayan ƙiri-ƙiri sun nuna ba ƙaunarka suke yi ba" Yazid ya ce "Duk da haka Hajiya, ko ina so ko bana so ai 'yan uwana ne" "Eh na san 'yan uwanka ne, amma matarka da zaka ɗauka ka kai musu fa, dama ita ma gata ga yadda take, kuma kaje su kunyata ka a gabanta kai baka tunanin haka kwata kwata?". Yazid ya ce "Hajiya ai ya san komai na gaya mata" "Ka gaya mata kuma, shikenan Allah ya tsare, amma ban yadda ka kaita ku je ka kwanar musu da 'ya a wannan garin ba, kar su yi mata wani abun" Yazid ya ce "In sha Allah ba kwana za mu yi ba, a ranar zamu dawo". Washegari da sassafe Yazid suka shirya, suka nufi tasha. Tun da Fadila take bata taɓa zuwa tasha ba, galibi a jirgi suke zirga-zirga, sai kuma Dutse da sukan je a mota. Fadila tana cikin dogon hijjabi, har da face mask a fuskarta, ba a ganin fuskarta. Warin da wasu da ga cikin matafiyan suke yi ne da warin fetur, ya sanya zuciyar Fadila tashi, ta riƙo hannun Yazid ta ce "Zid" "Na'am Baby, menene?" "Zuciyata tashi take, wannan warin fetur ɗin ya dameni, ga wani wari da na kasa gane kona menene" Cikin kulawa ya ce "Ko wani abun zan sai miki ki saka a bakinki?" Ta ce "Eh sai mini" Kafin su fara tafiya, Yazid ya sauka, ya sayo mata kwakwa da dabino, da aya fal, ya kawo mata. Cikin hijjabinta ta shiga ta jingina da jikin Yazid, tayi ta ciye-ciyen ta, har aka fara tafiya. Ƙarfe sha ɗaya na safe suka isa garin Rano, suka samu wata motar suka ƙarasa. Garin gwanin ban sha'awa sun yi noman rani, ko ina koren ganye, ga su da hanyoyi masu kyau, ko ina titi ha fitlinsi na solar duk a kan titunan. Duk da gidan su Yazid ginin ƙasa ne, amma tun daga ƙofar gidan zaka san me gidan yana da rufin asiri,ginin ya ginu doguwar katanga ce sosai. Ga soraye sun kai takwas kan ka dangana da cikin gidan. Gidan yana ɗauke da ƙaton tsakar gida iya ganinka, da ɗakuna kashi-kashi a ciki. Ko da yake ginin na da ne, amma ka san talaka ba zai iya irin wannan ginin ba. Suna wuce sorayen Yazid yana mata bayanin wasu daga abubuwan da suka faur a baya. Da sallama suka shiga gidan, suka tarar da yaran gidan suna ta kaiwa da komowa a tsakar gidan. Wata budurwa ce ta amsa sallamar, tana ƙarewa su Yazid kallo. Yazid ya ce "Haulat ina mutan gidan ne?" Wadda aka kira Haulat ta ce "Ba sa nan an kai Baba Uwani gidan mai magani, amma yanzu zasu dawo" Ya ce "To bamu abin zama kan su dawo" Ba musu ta shiga ta ɗauko musu tabarma, ta dawo ta shimfiɗa musu. Suka nemi wuri suka zauna. Fadila na cigaba da ƙarewa gidan kallo. "Zid ina ne ɗakin Inna?" Yazid ya nuna mata da hannunsa ya ce "Gashi can, naga ma yanzu shirgi suke tarawa a ɗakin" Ta ce "Allah sarki, Allah yayi musu rahama baki ɗaya" "Amin my wife, na gode sosai" Suka cigaba da hira, yana bata labari, kasancewar ya san yanayin gidan nasu sai a hankali, hatta ruwan da zata sha sai da ya saya mata. Suna nan zaune suna hira, 'yan ƙanan jikokin gidan da yaran maƙota suna ta kaiwa suna komowa a gidan. Hayaniya suka fara ji, ana ƙoƙarin shigowa da wani abu, gaba ɗaya hankalin Yazid da na Fadila ya koma kan hanyar shigowa. Wasu samari ne suka shigo da abu a cikin tabarma, sai daga baya Yazid ya lura da yayyensa mata da suka shigo daga baya. Abin da aka ajiye a cikin tabarmar ne ya ɗan tsorata Fadila, mace ce ƙafarta ta kumbuta himmm, da cikinta fuskarta duk wasu irin ƙuraje, gashi tayi baƙi sosai. A gigice Yazid ya tashi ya nufi in da matar take yana faɗin "Baba Uwani, meya sameki haka?" Da ƙyar matar ta iya ɗaga kanta ta kalli Yazid ta ce "Gwani kai ne yaushe ka zo?" "Tun ɗazu muka zo matar da na aura na kawo muku ku gaisa, amma meya sameki haka?" Ta fashe da kuka, yayin da yayyen nasa kuma suke bin Fadila da ke zaune a gefe da kallo, fara tas da ita me kyau wai yake faɗin matarsa ce. Ita kuwa Fadila ta haɗe rai, ta ja face mask ta rufe fuskarta, dan duk sai ta ji haushin su ya kamata, dan da alama yanayin tsayinsu da idanuwansu ya tabattar mata da yayyensa ne. Matar ta riƙe hannun Yazid tana kuka ta ce "Yazid ka ga yadda Allah ya mayar da ni, hakkinka sai bibiyarmu yake yi ni da Hanne, yanzu ita tana can tana fama da ciwon miyagun baƙaƙen aljanu, jikana Sani ma an shanye masa hannu da ƙafa, nima ka kalli yadda Allah ya mayar da ni, kuma mai magani ya ce dole na nemi afuwar wanda muka yiwa asiri9" Yaya Gaji da ke kusa da Baba Uwani ta ce "Baba dan Allah kiyi shiru, wannan ba abin da zaki tsaya kina faɗa bane ba dan Allah". Baba Uwana ta girgiza kai ta ce "Bar ni Gaji, nikaɗai na san me nake ji ban sani ba ko gaya masan ya sanya na samu sauƙi" ta kuma mayar da idonta kan Yazid da fuskarsa ta bayyanar da damuwa ta riƙo hannunsa ta ce "Yazid dan Allah ka yafe mana, bayan auren mahaifiyarka muka ɗora mata tsana, ta fara haifar ka facaloli suka ziga mu wai idan ba muyi a hankali ba sai ta haifi maza duk ta kwashe dukiyar mahaifinku, muka fara bin malamai, a kan a kashe ka amma abu ya gagara, mahaifinku ya ɗora ransa a kanka, Babarka ta zo ta sake haihuwar Huzaifa, hankalinmu ya sake tashi. Muka cigaba da bibiyar malamai aka yiwa Babarka sihiri aljani ya dinga bibiyarta yana feso mata da wasu ƙuraje a haka har ta rasu. Bayan tafiyarka makaranta, muka cigaba da bin malamai a kanka ka lalace, amma abu ya gagara sai muka koma yiwa babanka asiri a kan ya tsaneka, abun ya fara kamashi, aljanin da yake aikin ya ce sai an bashi jini shi ne zai yi aikin har ƙarshen rayuwarsa ba zai sake ƙaunarku ba, hankalinmu ya tashi muna tunanin yadda za ayi, saboda idonmu ya rufe buƙatarmu muke son ta biya kawai. Muka sadaukarwa da aljanin Jinin shanun mahaifinka goma yayi asararsu suka mutu, bayan mutuwar babarka muka dinga gallazawa Huzaifa a gidan nan, ƙarshe muka saka Sani ɗan wurin Gaji ya ja Huzaifa bayan gari, ya hankaɗashi rijiya ya tafi ya bar shi. Mu muka yi Asiri mahaifinku ya tsaneka ya koreka, muka dinga asirin sai ka lalace ko kai ma ka mutu, amma abin bai yiwu ba aka zo babanku ya rasu, muka dinga tattara kayansa muna sayarwa muna rabawa dan kar a raba gado ka samu dukiyarsa da yawa, babanka kan ya mutu asirin ya bar jikinsa ya ce ba zai yafe mana ba, amma dan Allah kai tun da kai kana raye ka yafe mana ko ma samu sassauci" Sunkuyar da kai Yazid yayi, hawaye na zuba daga idonsa ya sunkuyar da kansa ƙasa. Baba Uwani ta rirriƙe hannunsa tana kuka. Yazid ya ce "Baba kar ki sake cewa wai kune kuka yi mana wani abu, babu wani bawa da ya isa ya yiwa wani kowane irin abu sai abin da Allah ya ƙaddara zai samu bawa, ubangiji Allah ya yafe mana baki ɗaya. Miƙewa Fadila ta yi, ta saka takalmanta, ta je in da Yazid yake ta fizge hannunsa daga na Baba Uwani ta ce "Be yafe ba, Allah ya saka musu, in sha Allah sai kin fi haka wulaƙanta kan ki mutu, da ke da Wanda duk suka cutar da baiwar Allah da ba ta ji ba bata gani ba, ka tashi mu tafi" Yazid ya ce "Fadila me kike yi haka ne? Allah yana son bayinsa masu yafiya, ina son na dinga zumunci da 'yan uwana". "Ni na isheka zumuncin, wallahi ko ka yafe mata Allah ba zai yafe musu ba, shirka suka yi ai wallahi ko ka yafe ni ban yafe musu ba, ka tashi mu tafi" Fadila ta yi maganar tana kuka, saboda yadda abin da Baba Uwani ta faɗa ya girgizata, rashin imanin ya wuce tunaninta. Gaba ɗaya bin Fadila suka yi da kallo, Yazid ya miƙe tsaye ya ce "Fadil... "Ni karka kira sunana kawai ka taho mu tafi kawai" Jikin Fadila har rawa yake yi, saboda bata taɓa jin zunzurutun rashin imani irin wannan ba. Ganin da yayi tana neman ta fice daga gidan, ya sanya ya bi bayanta, sai da suka je waje sannan ya cimmata. Yana ƙoƙarin yi mata magana, amma ta fashe masa da kuka ta ce ita ya zo su tafi. Ganin yadda ta burkice gaba ɗaya ne ya sanya Yazid rarrashinta ya ce tafiya za su yi. Cikin gida kuwa Baba Uwani fashewa ta kuna yi da kuka tana miƙa hannu tana cewa su kira mata Yazid, ya zo ya yafe mata ko zata daina jin zafin da jikinta yake yi mata. Yaya Uwani ta ce "Kinga ni ko Baba, yanzu meye amfanin gaya masan kawai kin tonawa kanki asiri". Cikin tsananin zafin ciwo Baba Uwani ta ce "Gaji baki san me nake ji ba a ciwon nan, kamar ƙonani ake a cikin naman jikina, ku cire mini ciwon nan ko na tsine muku" haka ta dinga kururuwa tana ihu. Fadila kuwa har suka je gida kuka kawai take yi, dan gaba ɗaya sai da hankalin mutanen motar ya dawo kansu. Har suka je gida bata iya cewa uffan, saboda tsananin tsoro da tashin hankali. Har suka isa gida gefin la'asar, Fadila ko magana bata iya yi. Bayan sun yi sallar la'asar, ya tashi ya fara ƙoƙarin ɗora girki, dan ya san tana jin yunwa. Sai dai tun da suka dawo ɗin, Fadila ta kwanta tayi shiru a falo, tana jinjina tsananin rashin tsoron Allah na wasu mutanen. Tunani take ta yi, ta gano laifin da mahaifiyar Yazid ta yi wa mutan gidan, da har ta cancanci wannan zalunci daga garesu, sai dai ta kasa ganowa. Kamar dai Daddy daya auri mai aikin Mummy. Zuciyarta ta tuna mata. 'kai ai ko Mummy da aka auri 'yar aikinta, bana tunanin zata yi abin da wannan mutanen suka yi'. Yazid ya dawo falon, ya ɗago Fadila da ke kwance, ya rungumeta a jikinsa ya fara yi mata magana cikin taushin murya "Fadila, dan Allah ki Kwantar da hankalinki, ni kaina ban san zamu tarar da wannan tashin hankalin ba, amma ko na yafe musu ko ban yafe ba, Allah ya hukunta su, ba kiga halin da take ciki ba" Bakinta na rawa ta ce "Zid na tsorata, wallahi tun da nake a rayuwata ban zata ana yiwa mutum asiri da gaske ba, dan Allah kar ka yafe musu" Ƙwalla ce ta taru a idon Yazid, yayi murmushi ya ce "Shikenan, amma Fadila shi Asiri gaskiya ne, an yiwa annabin rahama ma, shiyasa nake son ki dinga kula da ibada a kan lokaci da kuma azkar" "Zid sun cutar min da kai, ni ba zan yafe ba" ta ƙarasa maganar hawaye na kuma bin gefen idonta, ga wani tsoro da yake kuma shigarta. "To kiyi haƙuri, shima Yazid ɗin na ki Allah ya miƙawa lamuransa shi ya sanya ya kare shi, amma a cikin 'yan uwana akwai wanda basu da laifi, kuma ko bana so 'yan uwana ne". "Ni na isheka, ni da Hajiya, kuma sai na gaya mata kar ta kuma barinka ka je, kar su kuma yi maka wani abun, idan ba sa sonka ni ina sonka" Murmushi ya yi ya ce "Kukan ya isa haka" Ko Abinci da ƙyar ya tursasata ta ci, gaba ɗaya bata walwala, da magariba sai ga Hajiya ta zo gidan, dan ta kira Yazid wayar ba ta shiga. Sai dai yadda ta ga Fadila kamar ta daɗe tana ciwo ne abin ya bata mamaki. Ta kalli fuskokin duk babu walwala ta kalli Yazid ta ce "Yazid, me aka yi mata ne?" Yazid ya ce "Bakomai Hajiya, kawai gajiyar tafiya ce" Hajiya ta kalli Fadila ta ce "Gaya mini me suka yi miki, ko wani abun ya faru da kuka je?" Fadila ta girgiza mata kai alamar a'a. Ganin sun ƙi gaya mata komai, ya sanya tayi musu sannu da zuwa ta tashi ta tafi. Wasa wasa ƙaramar magana ta nemi zama babba, dan kusan kwanaki uku Fadila a tsorace take, ta kasa sakin jikinta, ko fita ya ce zai yi sa taga kamar wani abu zai same shi, gaba ɗaya ya kasa gane kanta, sai koke-koke da take yi. Gashi yanzu duk dare sai wannan ciwon kan ya tayar mata, sai ya kusa raba dare a kanta yana mata addu'a sannan take iya bacci. Yau ma har ya fara bacci, ta fara mimmiƙewa tana kuka. Yazid ya zaune ya riƙe kanta da hannunsa ya dinga karanto mata Alqur'ani. Can tayi miƙa cikin wata irin murya ta ce "Dalla malam sakar mini kaina" Yazid ya ce "Meye haɗinku da matata?" Cikin wata irin murya ta ce "Kaga ba ruwanka da mu, aiki aka saka mu, kuma muke aiwatarwa dan haka kayi rayuwarka mu yi ta mu, ka barmu mu yi aikinmu" "Waye ya saku aikin?" "Babu ruwanka ka ƙyalemu" Yazid ya ce "Ƙona ku zan yi, na daɗe ina zargin ko ku kuke shafarta, amma ban tabattar ba, yanzu tun da kun magantu zan ƙonaku ƙonawa ta har abada" Girgiza kai ta hau yi, ta ce "A'a kar ka ƙona mu, dole mu cika aikin nan an riga an biyamu" Yazid ya ce "Waye ya saka ku?" "Amina ce ta je wurin uban gidanmu, shi kuma ya kiramu ya bamu aikin" "Wacece Amina?" Yayi maganar yana sake riƙe kan Fadila. "Wayyo Allahna, matar babanta wadda ta saka aka aura maka ita" Cigaba da karatun Alqur'ani Yazid yayi babu ƙaƙƙautawa, wani irin kuka Fadila take yi tana gurnani kamar ba mutum ba. "Wayyo Allah, kayi haƙuri ba Amina bace ba, ba ita bace ba" Bai saurara da karatun ba, sai da jikinta yayi sanyi sosai, bacci ya kwasheta. Ya zuba mata ido tausayin ta na ratsa shi, abin da Fadila take ta tsoro ya sameta. Haka rayuwa ta cigaba da tafiya, kusan duk dare sai ta hana Yazid bacci, da safe kuma kusan wuni take da ciwon kai, ga yawan firgita da take yi, gaba ɗaya duk ta rame, gashi bata yarda ya yi nisa ya barta, in da Allah ya taimake shi an yi hutun makaranta lokacin. Ba wanda ya san halin da ake ciki, kusan kullum cikin yi mata saukar Alqur'ani yake, da magungunan addinin musulunci. Har ya ɗan samu ta fara warewa, ta rage yawan firgita da take yi. Hajiya Zainab ta saka Daddy a gaba da tashin hankali da tijara, amma ya shareta ko a jikinsa, har Allah ya isa tayi masa amma yaƙi gaya mata in da Fadila take. Amina kuwa yanzu Hajiya Zainab tausayi take bata, tayi-tayi Daddy ya sanar da ita in da Fadila take amma ya ce ba yanzu ba tukuna. Yau Yazid bayan ya dawo daga makaranta, yana ta sauri kasamcewar tunda Fadila ta fara rashin lafiya baya fita ya daɗe, sai dai da ya je gidan ya tarar da shi a rufe, ya buɗe ƙofar ya shiga gidan da sallama amma shiru ba a amsa ba. Ya yada ledar hannunsa ya shiga ɗaki da saur yana kiran sunan Fadila amma ba ita ba dalilinta! (Tofa jam'a wa kuke tunanin ya yiwa Fadila turen aljanu! Kuma wane aiki aka saka su a kanta???) Littafin kuɗi ne, a biyani hakkina kan a karanta. 08081012143LITTAFIN KUƊI NE, MAI BUƘATA YANA IYA TUNTUƁATA A KAN LAMBAR WAYATA 08081012143 82 A gigice Yazid ya cigaba da duddubawa yana kiran sunan Fadila, gaba ɗaya ya rikice sanin Cewar bata da lafiya, a gigice ya rufe gidan, ya nufi gidan Hajiya dan ya sanar da ita halin da ake ciki. A tsakar gida ya tarar da Hajiya tana aiki, ɗagowa tayi ta kalli Yazid, ganin tamkar an wurgo shi babu ko sallama. "Yazid Lafiya kuwa?" Kamar zai fashe da kuka ya ce "Hajiya, Fadila ban ganta ba na je gida bata nan" "To kuma shi ne zaka ɗaga hankali haka?" Cikin damuwa ya ce "Hajiya ba ta da lafiya fa, Hajiya, Fadila Amana ce a wurina na je gida bata nan" Ganin yadda idanunsa suka yi ja kamar zai fashe da kuka, ya sanya ta ce "Ikon Allah, lallai soyayya ruwan zuma kai da ita ban san wanda ya fi wani son wani ba, nan ta saka wata yarinya ta rakota, ba ta da lafiya babu kunya tun ɗazu take cewa wai haryanzu baka zo ba na kira mata kai?" Ajiyar zuciya ya sauke ya ce "Tana ina?" Hajiya ta ɗan yi murmushi ta ce "Tana ɗaki" Da sauri ya shiga ɗakin, ya tarar da katifar Hajiya a falo, Fadila tana kai tana bacci gefe ga ledar magunguna. Yazid ya durƙusa ya kai hannunsa jikinta, wani irin hucin zafi yaji yan fita daga jikinta. Ya kai hannunsa wuyanta, ya ji tamkar an kunna oven saboda zafi. Cikin magagin ciwo Fadila ta ce "Hajiya, Zid ɗin bai dawo ba?" Yazid ya ce "Fadila, kin ganni nan sannu" "Yauwa, Zid jikina zafi" Cikin kulawa ya ce "Sannu, na je gida ba kya nan" miƙa hannu tayi, ta janyo nasa ta saka a wuyanta, tana lumshe ido. Hajiya ce ta yi sallama ta shigo falon, ta dubi Yazid ta ce "Yazid ina ganin mu kaita Asibiti, nan suka zo ita da wata yarinya, wai ta je ta tarar da ita tana amai, wai tsoro take ji ta cewa Yarinyar ta rakota gidan nan" Idanun Fadila a rufe ta ce "Maryam ce, ita na ce ta rakoni" Yazid ya ce "To sannu" Ta ce "Yauwa" Hajiya ta ce "Kuɗin hannuna ba su da yawa, shine nace bari kafin ka dawo a san abin yi, na kira Nurse Sadiya, ta yi mata allurar zazzaɓi, ɗazu har ya ɗan sauka, amma yanzu ya kuma dawowa, sai kuma amai da take ta yi". Yazid ya ce "Bari muje Asibitin akwai dubu huɗu a jikina" Hajiya ta ce "Ni ma akwai dubu biyu a hannuna, amma ka je gida ka ɗauko mata wasu kayan, nayi-nayi ta cire rigar na bata zani taƙi, duk ta kuma ɓata rigar da amai, ka je ka kawo rigar ka taho da kayan shayi ta ɗan ci wani abu sai mu tafi" Yazid ya amsa da to, ya koma gida ya ɗaukowa Fadila kaya, ya sayo kayan tea ya dawo. Da ƙyar Fadila ta iya tashi zaune, tana jin yunwa sosai ga ƙishirwa saboda zazzaɓi, dan haka shayin nan da zafinsa da komai, ta kafa kai ta finga zuƙa ko sauke kofi ba ta yi, tana gamawa ta dawo da shi, tayi ta amai ba ƙaƙƙautawa. Sosai Yazid yake jin tausayinta, ya gyara mata jikinta ya sauya mata riga, ya fita ya samo abin hawa, suka tafi Asibiti. Wani ƙaramin Asibiti suka fara zuwa, nan da nan aka ce a kwantar da ita a saka mata ruwa, sannan a ka rubuta mata teses. Fadila sai surutai take saboda zafin zazzaɓi, ta kira sunan Hajiya, ta kira Yazid, in anjima ta kira Daddy. Hajiya ce ta cire hular kan Fadila ta dinga jiƙata da ruwa tana shafa mata. Likitan ne ya shigo da sakamakon gwaje-gwajen a hannunsa, ya kalli Yazid ya ce "Kai ne mijinta?" Yazid ya ce "Eh ni ne" "To tana da ciki ne, yaushe ne period ɗinta na ƙarshe?" Yazid ya ɗan yi shiru ya ce "Ai ina ga tun da muka yi aure ba tayi ba". "Ok, wata nawa kenan?" Yazid ya ce "Wata uku" Likitan ya ce "Wow, so congratulations, but gaskiya akwai typhoid ga malaria duk a jininta, yakamata ku kula sosai, saboda wannan zazzaɓin illa ne a gareta da kuma ɗan cikinta" Yazid ya jinjina kai cike da jin nauyin Hajiya da ke zaune a wurin. Daga ƙarshe likitan ya ce "Zasu zauna har zuwa dare, ayi ta saka mata drip har jikinta ya ɗan yi ƙwari" Yazid ya yiwa likitan godiya. Hajiya ta kalli Yazid ta ɗan girgiza kai ta ce "Allah ya inganta, sai ayi ta kula da ita, naga cikin nata da laulayi ya zo" Yazid ya sunkuyar da kai yayi shiru kamar mara gaskiya. Fadila ta yi juyi ta ce "Zid" Ya amsa da "Na'am, sannu" "Yauwa, wai ciki ne da ni ko?" "Mm haka suka ce" "To dama ana yin haka ne? Watanmu uku da aure kuma cikina wata uku,ba sai an daɗe ake samun ciki ba?" Yazid ya rasa amsa da zai bata, Hajiya ta riƙe hannun Fadila ta ce "Kiyi shiri da bakinki kin ji, sannu Allah ya inganta ya raba lafiya" Fadila ta ce "Amin, Allah ya sa kaina ya daina ciwo" Hajiya ta ce "Amin ya Allah, ko zaki ci wani abun ne?" Fadila ta girgiza kai ta ce "Ina jin yunwa, amma idan na ci amai zan yi" Haka suka cigaba da kula da Fadila, sai bayan magariba aka sallamesu, ga ɗan samu ƙwarin jikinta, suka tafi gida. Yazid murna kamar ya zuba ruwa a ƙasa ya sha, saboda farinciki da samun cikin Fadila, sai lallaɓata yake yi. Sai dai abin tausayi duk da wannan wahalar da ta wuni tana fama cikin dare kuma aljanu suka hanata bacci. Yazid ya fara wani tunani a kan lamarin nan na Fadila, dan yana ruƙiya yana cire wasu wasu kuma suna zuwa. Washegari kuma cikin ikon Allah ta tashi jikinta da sauƙi sosai, da wuri Hajiya ta zo dubata, ta damo mata kunun gyaɗa ya sha madara ta kawo mata. Fadila ta dinga kallon Hajiya tana jin ƙaunar matar a ranta, mussaman yadda tayi ɗawainiya da ita. Tunani tayi a ranta, ta san da Mummy ce babu lallai ta yiwa ɗan wani haka, tana kewar mahaifiyarta tana son ta ganta, ko ba komai tayi mata nasiha a kan wasu abubuwan. Hajiya ta daɗe a gidan, har Maryam ta shigo duba Fadila ita da Antynta. Makarantar su Fadila kuwa sun yi cigiyarta har sun gaji, an kira lambarta bata shiga, gashi ita ba ƙawaye ba balle ace ga wadda ta san gidansu. Yazid yana jin ana ta cigiyarta amma bai ce komai ba yayi shiru da bakinsa. Kwanaki biyu Fadila laulayi yayi sauƙi, sai rigima da kwaɗayi ba ta cin Abinci sam, ga Yazid abubuwa sai a hankali amma haka duk abin da tak so shi yake yi mata. Yau ta tashi da cewa ita Cake ɗin Yusra zata ci, dan haka idan ya je makaranta ya je ya samu Yusra da nufin shi ne zai sayi cake ɗin Duk abin da Fadila take so shi yake mata, sai dai idan ya aka zo wurin yin Adduoi ne idan ta yi masa taurin kai a nan ne suke yin faɗa. Bayan ya je makaranta, suka samu free period, ya tafi department ɗin su Yusra, cikin sa'a ya ganta a kan barandar ajinsu a tsaye. Tana ganinsa ta yi murmushi tana faɗin "Wata sabon gani Yazid, ka ɓuya yadda Fadila ta ɓace kaima bana ganinka" Yazid ya ɗan yi murmushi yana tanbayarta ya karatu. Ta ce "Alhamdilillah, ka ga sai neman Fadila ka yi ka rasa ko?, almost 3months kenan, ni kaina ban san in da take ba, wai laifi ta yiwa Daddynta, ka san da har an kawo kuɗinta, ta tubure ta ce bata son mijin, shi ne Daddy ya ɗauketa, ni daga bayan nan kamar ji na yi amce wai ya yi mata aure, amma na san hakan ba mai yiwuwa bane ba, dan Allah ka tayamu da Addu'a Allah ya sa ya haƙora ya dawo mana da ita, baka ga yadda Mummy ke cikin damuwa ba". Yazid cikin sanyin jiki ya ce "Allah sarki, in sha Allah tana in da ake kula da ita, Allah ya daidaita" Yusra ta amsa da "Amin, kaga ga bikina ya ƙarato amma bata nan, tare muke shirya kowane tsare-tsare da zamu yi da bukukuwanmu, she's my best friend amma yanzu bata nan ina cikin damuwa" tayi maganar a sanyaye. "Eyya kar ki damu, ki kwantar da hankalinki zata dawo Very soon in sha Allah, yaushe ne bikin?" "Saura four months, zan auri abokin Yayanta, amma har yayan nata shi ma bai san inda take ba" Allah sarki abota ba ƙarya ba, sosai fuskar Yusra ke nuna tana cikin matsananciyar damuwa. Ina ga mahaifiyar ta kuma da ta kawota duniya, akwai yiwuwar ya je ya samu Daddyn Fadila ya bashi haƙuri ya sassauta mata hukuncin da yayi mata ko dan albarkacin masoyanta. Yazid ya ce "Dama na taɓa cin irin vanilla cake ɗinki a wurin Fadila, shine nake so amma ban sani ba ko kina bada na dubu ɗaya" Murmushi ta yi ta ce "Ko kyauta ka ce na baka ai zan baka Bestyn besty, kar ka damu gobe in Allah ya kaimu ba zan shigo school ba, amma zan bayar a kawo maka in sha Allah" Ya ce "Madalla na gode sosai da sosai, ga dubun" ta girgiza masa kai ta ce "Ka bar shi kawai za a kawo maka in sha Allah". Yazid ya ce "A'a dan Allah ki karɓa, abinki na sana'a" Yusra ta ce "Fadila ma idan ta ci bata biya, kar ka damu" tayi maganar tana murmushi. Ta wani fannin halinsu ya sha banban ita da Fadila, amma wasu lokutan Yusra ta fi sauƙin kai. Yazid tayi ta mata godiya, sannan ya koma aji, yana ajin ne Daddy ya kira shi a waya, ya ce masa idan babu abin da yake yi yana son ganinsa. Hakanan Yazid ya ji gabansa ya faɗi, ya shiga fatan Allah ya sa lafiya. Bayan sun kammala lectures sun tashi, ya tari abin hawa ya tafi gidansu Fadila, suka gaisa da Zakiru, ya sanarwa da Zakiru cewar wurin Daddy ya zo. Zakiru ya kira Daddy a waya ya sanar masa yayi baƙo, ya cewa Zakiru ace masa ya shiga. Zakiru ya sanar da Yazid saƙon Daddy, Yazid ya doshi cikin gidan. A falo ya tsaya yana duru-duru da tunanin ina shiga, Mummy ce ta fito daga sashinta, hannunta riƙe da jug, kallo yayi mata ya ga ta yi wata irin rama sosai da sosai, duk da ba wani sosai ya ganta a baya ba amma ta rame. Durƙusawa yayi yana gaisheta, ta kalleshi a wulaƙance ta ce "Kai kuma daga ina zaka shigowa mutane gida haka har cikin falo?" "A'a Mummy, dama Daddy ne ya ce yana son ganina" Cikin mamaki ta ce "Ya ke son ganinka kai a wa? Me kayi masa yake nemanka". Amina ce ta fito, dan jikinta ya bata wataƙila Hajiya Zainab ta hana shi shiga. "Yazid sannu da zuwa, ƙaraso shigo yana ciki Daddyn" Yazid ya ɗan risuna ya ce "Mummy bari in je" Tsaki Mummy ba tare da ta kuma cewa komai ba. Yazid kuwa ya bi bayan Amina zuwa katafaren falonta. Ta nuna masa kujera ta ce "Bismillah zauna, bari na kira shi" Ta juya ta nufi bedroom, Yazid ya ɗan ɗaga kai yana kallon falon, ya jinjina kai ya ce dole Fadila ta ce wannan gidan nasa ba gida bane ba, amma cikin ikon Allah ta haƙura ta zauna. Daddy ne ya fito fuskarsa ɗauke da fara'a, ya ƙaraso cikin falon. Yazid ya zube gwiwowinsa a ƙasa yana gaida Daddy. Daddy ya amsa masa tare da saka hannunsa a nasa suka yi musabaha. Daddy ya zauna cikin murmushi da kulawa ya ce "Yaron kirki na takuraka na maka kiran gaggawa ko?" Yazid cikin murmushinsa ya ce "A'a bakomai Daddy, ai ban san kun dawo ba, da na zo sannu da zuwa" "Kar ka damu bakomai, ya karatun ya matar taka?". "Tana nan lafiya Daddy". Amina ce ta zo ta jerewa Yazid Abinci, suka kuma gaisawa ta zauna a kusa da Daddy. Daddy ya ɗan dubi Yazid ya ce "To Yazid ya ake ciki? Ta haƙura ta zauna ko akwai wata matsala idan da matsala ka gaya mini, a san abin yi dan na san idan akwai ɗin ma kai ba faɗa za ka yi ba" Yazid ya ce "A'a Daddy, babu wata Matsala" "A'a Yazid, kar ka yi mini hakinku na Fulani, kar ka yi kara ko ka ɓoye mini wani abu, ka gaya mini bakomai. Ni na san halin Fadila kamar yunwar cikina, na san kana nan kana fama da ita. Na yi mamaki ma da ta zauna tsawon wannan lokacin ba ta dawo ba" Yazid yana shirin yin Magana wayarsa ta fara ringing. Ya ciro wayar ya ga Hajiya ce, ya kalli Daddy ya ce bari ya amsa waya. Daddy ya jinjina masa kai. Ya ɗaga wayar ya saka a kunnensa, kasancewar ba ya ji sosai ƙasa-ƙasa yake jin muryar Hajiya, ya sanya ya saka wayar a hansfree. "Hello Hajiya, ina jinki" Hajiya ta ce "Yauwa, dama matarka ce ta zo ta sani a gaba, wai na bata waya zata maka magana" Yazid ya ce "Ok to" A shagwaɓe muryarta ta daki dodon kunnensa "Hello Zid" "Mmm" "Ka karɓo mini cake ɗin?" "A'a ai kinga yau na gaya mata, sai gobe in Allah ya kaimu zata kawo" "Mhmmm to ni fa yunwa na ke ji, Hajiya ta dafa doya ta bani, amma na kasa ci" Ga Daddy a zaune a wurin, gaba daya kunya ta kama Yazid a hankali ya ce "To me zaki ci?" "Idan kana da kuɗi, ka sayo mini mangwaro, sai abarba ta kan masu talla amma rabi nake so" A taƙaice Yazid ya ce "To" "Wai ya na ji kana amsa mini wayar da ƙyar ne kamar wanda ya je gidan sirkai, Zid ko wurin budurwa ka je?" "A'a" "To kayi magana mana" "Gashi ina yi" Fadila ta ce "Wallahi idan wurin budurwa ka je ka dawo zan gane" Yayi murmushi ya ce "Ni ban je wurin kowa ba" Fadila ta ce "Zid" "Na'am" "Ka ce kana sona idan ba wurin budurwa ka je ba" Tayi maganar cikin shagwaɓa. Cikin harshen larabci ya ce "Zan faɗa idan na dawo gidan" Da hausa ta ce "Ni ban yadda ba, kuma ka taho mini da rake, idan ka dawo zan gane in da ka tafi ai" Sauke wayar yayi a ƙasa kamar ya nutse da kunya. Amina a ranta ta ce "Su o'o an gamu' Daddy kuwa murmushi ya kasa barin fuskar sa ya ce "Lallai na yarda babu wata matsala, sai haƙuri ka san su rigimarsu ba ta ƙarewa" Amina ta ce "Ai ku ɗin ne sai ana haɗa muku da rigima" Daddy ya ce "Ai shikenan, Allah ya ƙara mana haƙuri" Amina ta ce "Yazid, sai dai ban sani ba ko kana cin tuwo, tuwon Shinkafa muka yi da miyar gyaɗa, sai lemon kwakwa" Yazid ya ce "Alhamdilillah, ai a ƙoshe nake" Daddy ya ce "A'a sai ka ci Abinci zaka tafi". Yazid ya ce "Daddy a ƙoshe nake, zan ne na kai mata saƙonta tana jirana" Amina ta ce "Kar ka damu, in dai furits ne, sai a haɗa maka ka tafi mata da su" Ganin Yazid ya dage ba zai ci abinci ba, ya sanya Amina ta je Kitchen ta samo kwanuka ta juye masa abincin,ta haɗo masa Fruit da kayan tsarabarsu ta bashi, Daddy ya ɗora masa da kuɗi, sai dai dan yana jun kunyar Daddy ne, amma da ba zai karɓi kuɗin ba. Daddy ya ce bari ya ragewa Yazid ɗin hanya, suna tafe ne Yazid ya ke cewa "Daddy, dan Allah ka janye Maganar ka a kan Fadila, ka bari na kawo ta gida ta ganku, tana cikin damuwa" Daddy ya numfasa ya ce "Yazid, ni kaina ina kewar 'ya ta, amma da zarar na ce ta zo gidan nan,za a iya samun matsala zata iya cewa ba zata koma ba, ko kuma mahaifiyarta ta ce ba zata koma ba". "Daddy Fadila ba zata yi haka ba, dan Allah ina nema mata afuwa laifin da tayi, dan Allah a sassauta mata" Daddy yayi murmushi ya ce "Za'a duba in sha Allah" "To Daddy godiya muke, Allah ya ƙara girma" "Amin Yazid, ni ma ina yi maka godiya" Yazid ji yayi kamar ya sanarwa da Daddy larurar da Fadila take fama, amma yayi shiru saboda kar ya ɗaga masa hankali. A gida ya tarar da Fadila, ta yi masa sannu da zuwa, tana Alla Alla ya zo ya buɗe ledar da ya zo da ita ta samu abin da zata ci. Ganinsa da abinci bai sanya ta tambayi ina ya samo ba, yana can yana wanka ta zuba abunta ta fara ci, sai fitowa yayi ya ganta ta na ta zuba loma. "Ke baki san a ina na samo Abinci ba kin zauna kina ci?" "Koma dai a ina ka samo shikenan, rabon da na ci Abinci har na manta, ni kamar ma na san irin wannan girkin" Yayi murmushi ya ce "Gama ci tukuna" Sai da ta gama cin abincin sannan ta kalleshi ta ce "Yauwa wai ina kaje ne, kuma a ina ka samo Abinci?". Yazid bai ɓoye mata ba ya gaya mata. Tsuke fuska Fadila ta yi ta ce "Da na san ita ta bada wannan abincin, da ba zan ci ba" Ya zuba mata ido ya ce "Saboda me?" "Na tsani yarinyar nan, bana ƙaunarta ita ce silar rusa dukkanin farincikin gidanmu, kalli halin da jefamu a gidan nan" tayi maganar iya gaskiyarta. Yazid ya numfasa sannan ya ce "Kina dana sanin aurena ne?" Ta girgiza kai ta ce "A'a amma meyasa kake tunanin haka?" "Na ga da saka hannun ta a cikin aurena da ke, duk da ban san zaman da kuka yi a gidan ba, amma banga dalilin da zai saka ki tsaneta ba". Fadila ta bashi labarin yadda Amina ta auri Mahaifinta. Ya dubi Fadila a tsanake ya ce "To meye laifinta dan ta auri mahaifinki, na san zaki ga kamar na yi miki ba dai-dai ba, amma Fadila da ni na samu matan uba kamar irin taki, wataƙila da ban tagayyara haka ba, rashin tawakalli ke sanya mu ɓata wasu lokutan. Kusan matsayi guda ne na Amina da Innata, matan babana suka kasa jurewa suka fara cutar da mahaifiyata, meye laifin Innata a kan su take?" Fadila ta girgiza kai alamar a'a. "To kusan haka ne, na san wataƙila kin taya Mummy kishi a kan aurenta da Daddy yayi, amma kema a kanki take? Ya aka yi kika san ta tarwatsa muku farinciki? Laifi kika yiwa Daddy ya ɗau matakin aura mini ke, amma ki sawa ranki cewa dama Allah ya ƙaddara zan aureki ko da ita ko babu. Kin san babbar musiba a rayuwa? Ace mahaifinka yana biye biyen mata shi ne babbaan bala'i da tashin hankali, amma dan dai ya yi aure da sauƙi, tunda ya kare mutuncinku da nasa a idon duniya, idan kika ce kin tsaneta mahaifinki ne ya ajiyeta. Kuma Fadila baiwar Allah nan tana da kirki sosai, ki kamanta ta da nawa matan uban ya isheki misali Fadila" Ɗan yamutsa fuska tayi ta ce "Na ji, dan Allah mu bar wannan zancen bana so" Ya ce "Shikenan, an bar shi" Daga nan suka shiga wata hirar, yake gaya mata ai Yusra ta ce masa aure zata yi, zata auri abokin Khalil. Fadila ta yi murmushi ta ce "Allah sarki, he's my ex Allah ya sanya alkhairi, gayen nan ya soni sosai" "Amma ai zaki bikin idan lokacin bikin ya yi ko?" "To gani nan dai" ta faɗa jikinta a sanyaye. Alhamdilillah, jikin Fadila ya ɗan yi sauƙi da yawan iskar da take yi, saboda yawan Addu'oi da Yazid yake yi mata kuma yake koya mata. Hajiya Turai ce da Hajiya Salma zaune a falon Hajiya Zainab, Hajiya Turai ta na yi mata baynin wasu garin magunguna. "Zainab, tun da dai shi mijin nan naki haka Allah ya yi shi , ki bishi ta yadda yake so, wannan wasu zafafan kayan nata ne da ga Chadi, kiyi amfani da su ki lallaɓa shi ko Allah ya sa ya faɗi in da Fadilan take, tun da dai kin masa tashin hankali amma yaƙi yarda" Hajiya Zainab ta ce "Hmmm ai ni lamarin sa yanzu tsoro yake bani, ban taɓa tunanin haka yake da masifar taurin kai ba sai yanzu a wannan karon". Hajiya Salma ta ce "Rabu da shi, ai ta ko ina ɓullo masa za muyi, ga wannan kayan hayaƙin suma ki dinga yi, ita ma Fadila ta bani mamaki da tsawon wannan lokacin ta kasa waiwayar gida, ta je ta zauna, ko wa ya aurawa ita oho?" "Koma wa ya aurawa, zan bishi a sannu na gano in da 'ya ta take. Ayshercool 08081012143LITTAFIN KUƊI NE, MAI BUƘATA YANA IYA TUNTUƁATA A KAN LAMBAR WAYATA DOMIN SAYEN NASA. 08081012143 83 Washegari Yusra ta aikowa da Yazid kayan cake fal, har da Abinci, babban dalilin da ya sanya Yusra ta bawa Yazid kayan nan haka shi ne saboda Fadila ta ce mata tana son ta dinga taimakawa Yazid amma babu lallai ya amince. Shi kansa yayi mamakin uban abin da ta haɗo ta aiko masan, Fadila kuwa da ya je da kayan tamkar ta yi rawa dan murna, wuni ta yi tana aikin ciye ciye, saboda dama ba abinci take ci ba, sai dai tana ci tana amai amma ta ƙi haƙura ta dinga tura cake ɗin. Ba ƙaramin tausayi take bawa Yazid ba, duk da fatarta ta sake murjewa amma tayi rama saboda laulayi. Daddy kuwa bayan ya koma gida, Amina ta ke yi masa Congratulations, cikin rashin fahimta yake tambayarta meyafaru? Amina ta ce "Mutuniyarka fa ina kyautata zaton an gamu ne". Cikin rashin Fahimta ya ce "Ban fahimta ba" "Ina ga cikine da ita fa" Da sauri Daddy ya ce "Haba dai?" "Baka ji yana cewa ba ta da lafiya ba, tana masa lissafin abin da zai sai mata ba" Daddy ya ce "Alhamdilillah, Allah ya tabattar ya amince, ikon Allah zan ɗau ɗa na ɗau jikoki dan ina kyautata zaton Hafsa zata riga haihuwa" Amina ta ce "Hmmmm ko kunya baya ji, ana haifa masa jikoki kuma za a haifa masa 'ya'ya gaskiya daga wannan a barwa yara su yi" Daddy ya ce "Ke kin isa ma? Ko goma zaki haifa mini ina so Meenal, ke ta mussaman ce sosai a wurina, kin zo mini da alkhairi da dama a cikin rayuwata" Ta shafi dogon gemun Daddy tana murmushi ta ce "Ina sonka Yallaɓai" "Ina sonki sosai Meenalina, next week za a kawo motarki in sha Allah, and ina son jin idan kina da intrest a kan wani business, sai in san abin yi" Ta yi murmushi ta ce "Ban rasa komai ba daga gareka, ga gidan gonata can a garinmu, ka sa ana kula mini da shi, a yanzu dai bana buƙatar komai, karatuna zan mayar da hankali a kai sosai for now". "To Allah ya dafa yayi miki jagora 'yar Babyn Ahmad" Murmushi tayi tare da jinjina masa ta ce "Godiya nake ranka ya daɗe" Yazid ya na zaune ya kammala karatun sa, ya dubi in da Fadila ke zaune tana kallonsa, "Fadila" ya kira sunanta. Ta kalleshi ta tsuke fuska ta ce "Meye kuma na kiran sunana haka kai tsaye?" Yazid ya ce "Magana ce mai muhimmanci, ina son zamu je Dutse ne mu je mu gaishe su" Fadila ta tsuke fuska ta ce " Ni ba zani ba" "Amma saboda me?" "Kaga nifa ba wani sabawa na yi da su ba, me zan je na yi musu?" Yazid cikin mamaki ya dubi Fadila ya ce "Ba family ɗinku ne duka a can ba, both na Daddy da na Mummy?" "Eh amma ba wani zuwa nake yi ba, ni ba wani sabawa na yi da su ba". Yazid ya ce "Haba gaskiya baki kyauta ba, zamu je mu gaishe su daga nan sai mu tafi Jalingo" Jiki a sanyaye Fadila ta ce "Idan muka je Dutse, Mummy zata san mun je, kuma idan ta san mun je sai ta nemi in da nake, kuma idan ta gano in da nake, zata iya samun saɓani da Daddy. Ina kewar Mummy, amma idan ta san in da nake za a iya samun matsala". Yazid ya tashi ya koma kusa da ita, ya rungumeta a jikinsa ya ce "Dan Allah kiyi haƙuri kin ji Babyna, komai zai wuce ko da Albarkacin biyayyar da kika yiwa Daddy da kuma biyayyar aure da kike yi mini, ba zaki wulaƙanta ba, komai zai wuce" Fadila ta kalleshi ta ce "Da gaske ina yi maka Biyayya Zid?" "Alhamdilillah, kina yi mini daidai gwargwado, ban taɓa zaton zaki yi mini biyayya ba, duba da yanayin ki muna school, ga tsiwa ga rashin ta ido, ban zaci zaki zauna da ni ba ba tare da kin bujure kin bar gidana ba. Mussaman duba da yadda kika ce ba kya sona na shiga damuwa sosai, sai gashi cikin iko na Ubangiji Allah ya mallaka mini ke". Fadila ta yi murmushi ta ce "Hmmm, Duk da tarin samarina ciki har da wanda Yusra zata aura yanzu, babu wanda ya taɓa burgeni, kowa sai in ga yana da irin tasa matsalar da ba zan iya son shi ba, ko bai kai matsayin da zai iya aurena ba. Ka san bayan dariyar da nake yi maka na rashin iya turanci, lokaci guda ka kwance mini lissafi lokacin da na je masallacin juma'a, na ji kana huɗuba da larabci, yadda ka ke yi mini larabci, da yadda kake iya kwafar handwriting ɗina ya sanya ka fara burgeni. Lokaci guda sai na dinga mafarkinka, har da rana fa, ga abubuwan ban mamaki da kake yi ciki har da signing ɗina, da kuma yadda jikina yake yin rawa idan ka zauna a kusa da ni, ni fa har na fara tunanin ko ba mutum bane ba kai, ni dan Allah me kayi mini ne?" Yazid ya yi murmushi ya ce "Ni ba abin da na yi miki, kwarjini kawai nake yi miki. Tun a lokacin nan da na kamu da sonki, na kasa jurewa na gaya miki, amma ki ka ce ba kya so na, sai da na yi kuka. Ni a rayuwata harkar karatuna na sanya a gaba, lokaci guda ina ganinki na ji wata irin soyayyarki mai ƙarfi ta kamani, amma kika ce ba kya sona, ranar da na dawo gida a ɗaki na wuni, kamar ƙaramin yaro haka na kasa cin Abinci, sai da na zubar da hawaye sosai". Tashi zaune Fadila ta yi, ta tallafo fuskar sa tana kallonsa ta ce "Allah sarki My Zid, am very sorry sweetheart, tun muna school na fara sonka, sai dai a lokacin ni ɗin sai a hankali, na fara tunanin yadda zan shiga rayuwarka na taimaka maka, ba yadda na iya Mummy ta kawo wani wanda take son na aura. Komai dai ya riga ya wuce tun da gashi Allah ya ƙaddara aurena da kai" Shima ya shafi gefen fuskarta ya ce "Haka ne, Allah mai kyauta da ƙari, ya bani ke a lokacin da ban zata ba, kuma ga Baby zai bani, fatana Allah ya sauke ki lafiya" Fadila ta kalli cikin nata sannan ta kalli Yazid ta ce "Zid wai ya sunan Inna na gaskiya?" Yazid ya ce "Sunanta Khadija". "Allah ya bani 'ya mace na saka mata sunan Inna" "Da gaske idan Allah ya sa kika haifi mace, sunan Innata zaki saka mata?" Fadila ta ce "In sha Allah, idan har macece sunan Inna zata ci, ban taɓa ganinta ba amma na ji a raina ina ƙaunarta" "Allah sarki my wife, ina godiya da wannan karamci na ki" Ta yi murmushi ta ce "A wurinka na koya ai in dai karamci ne" Suka cigaba da hira suna tsara yadda tafiyarsu za ta kasance. Kasancewar yau Daddy yana ɓangaren Hajiya Zainab, ya sha mamakin yadda ya ga tana ta wani nan nan da shi, dai lallaɓa shi take yi, ƙarewa yau da kanta ta kai masa kanta. Abin ya bashi mamakin yadda ya ga tayi ladab, sai dai ya san banza ba ta kai zomo kasuwa, ba a banza take ta masa wannan ladabin ba dan ya san halinta sarai. Ya dubeta ya ce "Mhmmm wannan ladabin fa? Na san da wata a ƙasa". Ta dube shi ita ma ta ce "Haka ma zaka ce, shikenan na ji na kuma yarda, dan Allah Ahmad ba dan ni ba ba kuma dan halina ba, ka dawo mini da 'ya ta dan girman Allah, ko tausayina ba ka ji ne?" Yayi murmushi ya ce "Kin fasa kaini ƙarar kenan?" "Dan Allah ka bar wannan maganar, na yi ta ne cikin fushi, kuma ko ƙarar taka na kai na san ni ce a ƙasa, dan girman Allah ka dawo mini da 'ya ta" Daddy ya ɗan gyara kwanciyarsa sannan ya ce "Ki daina zancen fa na dawo miki da 'yar ki, na gaya miki aurar da ita na yi ai, sai dai ta zo ta koma, shima sai da izinin mijinta dan ba zan goyi bayan ta dinga aikata abin da kike yi ba" "Wai da Allah da gaske aurar da Fadila ka yi? Ahmad yanzu ƙiyayyar da kake yi mana har ta kai ga haka, wane irin aure ne haka kamar auren tsuntsuwa? Shikenan tunda ka auri yarinyar nan ka mayar da ni wata mara amfani ni da yarana? Wannan ai kamar ka wulaƙanta 'yar ka ne da nuna cewa bata da kima da daraja ga wanda ka bawa airen nata". Daddy ya ce "Ban bayar da aurenta ga mutumin banza ba, kuma 'yar da ta fi kowace 'ya gata ma, 'yar Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam, ba ayi mata abin da kike burin sai kin yi a auren taki 'yar ba". A hasale ta ce "Amma ai ka kashe kuɗi ka yiwa Yarinyar da ka aura, saboda ita ce 'ya Fadila kuma ba 'ya bace ba ko?Tun da ta zo gaba ɗaya ta tarwatsa mini gida" "Amina walimar kammala karatunta kawai na yi mata, kuma ita ma Fadilan da tabi umarnina, ta fito da miji a lokacin da na bata da haka ba ta faru ba" Fashewa ta yi da kuka cikin sheshsheƙa ta ce "Ahmad ba ka san me nake ji a zuciyata ba ko? Wallahi muddin wani ciwon ya kamani ko na mutu kaine sila, ko baccin kirki bana iya yi, ban san a in da 'ya ta take kwana take tashi ba, ba ka tausayin halin da nake ciki, mun doshi wata na huɗu ban san in da 'ya ta take ba, ba ka yi mini adalci ba" Tausayinta ne ya kama shi, sai dai wasu lokutan ita ɗin ba abin tausayi ba ce ba sam, saboda halinta. Daddy ya ce "Shikenan, zan kawo miki Fadila ki ganta, amma ba zan gaya miki takamaiman lokaci ba, idan har na kawota ba kya nan kin tafi yawonki, shikenan kin yiwa kanki zata koma gidanta ne" Jinjina kai ta yi cikin amincewa, tana goge hawaye. **** Yazid kuwa sun gama shirinsu tsaf, shi da Fadila suka tafi gidan Hajiya, domin tare da ita za su tafi Jalingo. Suna zuwa suka tarar da ita ta gama girki tana kwashe abinci. Yazid ya ce "Hajiya girki kuma kike yi?" Hajiya ta ce "Eh na yi mana girki ne, saboda kar mu rasa abin da zamu ci a hanya, kuma ga mai juna biyu". Yazid ya jinjina kai ba tare da ya ce komai ba. Hajiya ta fito da tukunyar Abincin a hannunta zata kankare ta wanke tukunyar, dan bata son ta tafi ta bar datti a gidan. Hajiya na shirin zuba ruwa a kan ƙanzon, Fadila ta yi sauri ta ce "Hajiya dan Allah kar ki zuba ruwa a ƙanzon ina so" Hajiya ta ce "Me zaki da shi?" "Hajiya so nake, sha'awa ya bani zan ci" Yazid ya kalleta ya ce "Ci kuma, ƙanzon?" Ta ce "Eh ɗin ina ruwanka" Yazid ya ce "Wai ban gane ƙanzo ba, idan yunwa kike ji, a zubo miki Abinci mana" Fadila ta tura baki ta ce "Ni ba abinci zan ci ba, ƙanzon nake so" Hajiya ta yi murmushi ta ce "Ai ciki ba abin da ba ya sawa, a me zan zuba miki ƙanzon" Fadila ta yi murmushi ta ce "A zuba mini a leda, sai a zuba mini yaji a kai, mu tafi da shi" Yazid ya buɗe baki ya ce "Wai hanya zamu tafi kina cin ƙanzo Fadila?" Fadila ta ce "Ba fa a hanya zan ci ba, sai mun hau mota". Hajiya kuwa ta biyewa Fadila, ta kankarewa Fadila ƙanzon nan tas, ta zuba mata a wani ɗan fulas mai murfi, ta zuba mata mai da yaji, Fadila sai haɗiye yawu take tana murna wai ƙanzo da mai da yaji. Yazid kuwa sai bin ta yake da kallo, tausayi ma gaba ɗaya take ba shi, lallai mata na shan wahala, amma banda lamarin ciki, me mutum zai yi da ƙanzo?. Ƙarfe goma na safe suka ɗau hanyar Jalingo, suna tafe a hanya Fadila rungume da fulas ɗin ta na ƙanzo a hijjabi, suna tafe sai ta shige hijjabi ta ci ƙanzonta ta fito. Tun ana tafiyar nan ta marmari,har Fadila ta gaji, gaba ɗaya jikinta ko ina ya yi mata tsami, tun tana ɓata rai har ta fara share hawaye a wayance. Ganin Hajiya ta yi bacci ne ya sanya Yazid ya riƙe hannun Fadila, murya ƙasa-ƙasa ya ce mata "Kiyi haƙuri kin ji, mun kusa ƙarasawa in sha Allah, da ina da kuɗin jirgi da shi zan biya mana, kiyi haƙuri na yi alƙawarin yi miki tausa idan muka isa" Jinjina masa kai ta yi, tun kan su bar Kano ta cinye ƙanzonta, da aka tsaya salla kuma, Hajiya da Yazid ne suka ci Abincin, wai ita ba ta ci tuwo take so, ƙarshe ta ɓuge da shan sprite da yalo. Yazid duk da a takure ya ke shi ma a motar, amma ya gyara zamansa ya ce "Kwanta a kafaɗata sai ki yi bacci, naga idonki ya yi ja sosai". Dan Hankalin Yazid ya kwanta, ta ɗan zame ta kwanta a jikinsa, amma gaba ɗaya zaman motar nan babu daɗi, ga matsi ga zafi. Aikuwa wani wahalallen bacci ya ɗauke ta, Yazid kusa ko motsin kirki baya yi dan kar ta tashi. Ba su suka isa garin nan ba, sai wajen goma saura na dare, Fadila ta riga ta gama gajiya tilis. Ba laifi gidan kakannin Yazid yana da kyau, duk da ginin ƙasa ne amma tsaf da shi. Suna zuwa gidan Fadila kamar ta faɗi, saboda wani irin jiri da take fama da shi. Nan da nan suka hau yarensu na fulatanci, da ba abin da Fadila take ganewa. Ba ta san mai suke faɗa da yaren ba, ta ga wata mata ta ƙaraso ta rungumeta, cikin gurɓatacciyar hausarta tana musu sannu da zuwa. Cikin wani ɗaki suka shiga, in da suka tarar da wata dattijuwa, ita ma sai fulatanci take yi, kai da gani ka san suna cikin farinciki. Kasancewar da wuta, ya sanya Fadila ƙarewa ɗakin kallo, tsaf da shi sai ƙamshin turaren wuta da ya haɗe ƙarnin man shanu. Da hausa Dattijuwar take faɗin wannan ce sirikar tawa? Sannu da zuwa, ke kika auri jikana matso kusa da ni" Yazid dai tuni ya nufi wurin yin salla, Fadila kuwa bayan an gama wannan gaishe gaishen, da yaren da ba ji take yi ba, da ƙyar ta yi alwala sallar ma a zaune ta yi, saboda ta wahala. Ta nemi wuri ta kwanta, wata mata mai kama da Hajiya wadda tun shigowarsu Fadila ta ji ana cewa Dada ce ta shiga da abinci, tuwon Alkama ne da miyar kuɓewa ta sha kifi. Duk san tuwon da Fadila ta gama kwarmato a mota, amma ta ce ita ba ta ci bacci take ji. Cikin harshen fulatanci, Kakar Yazid take cewa ba ta ji daɗi ba matar Yazid ta ƙi cin abinci. Hajiya ta ce "Kiyi haƙuri, tana da juna biyu ne, bakomai take iya ci ba" ai nan ta ƙara murna, can kuma sai hawaye saboda tuna Inna wuro mahaifiyar Yazid. Yazid sun daɗe suna hira, sannan mijin Dada ya zo suka tafi in da za a sauki Yazid. Yazid sai Addu'a yake yi, Allah ya sa kar ciwon Fadila ya tashi a garin nan cikin wannan dare. Lafiya lau har Asuba, Hajiya ta tashi Fadila ta haɗa mata ruwa mai zafi ta yi wanka tayi alwala ta yi sallar asuba ta koma bacci. Surutunsu ne ya tasheta, Yazid ya zo tuni, suna ɗakin yana kallonta a kan gado tana ta bacci. Ga gadon na da katifa mak spring, ba abin da yake mata daɗi irin yadda idan tayi juyi, spring ɗin yake sama yana ƙasa da ita. Bayan ta tashi suka gaisa da Mutanen gidan, Sannan ta fita tsakar gida wanke baki. Tsayawa ta yi tana kallon 'yar guntuwar katangar gidan, kasancewar Fadila doguwa ce, tana ganin gidajen waje, sai da ko ina shanu ne a garin. Ta gama brush ɗin ta miƙe, taga Yazid a bayanta. Ya ƙarasa in da take yana faɗin "Ina kwana dear?" "Lafiya lau" ta bashi amsa. "To yaya, ya gajiya jiya kin yi bacci fa wuri" Ta ce "Ba dole ba, na gaji ne sosai, a ina ka kwana?" Yazid ya ce "Gidan Dada, ita ma yayar Inna ce, amma ƙanwar Hajiya ce" Fadila ta ce "Kamarsu ɗaya, har wannan kakar taku" Yayi murmushi ya ce bari na yi gaba, kar a fito a ce na yi rashin kunya" Dariya ta yi ta koma ɗakin, sai sannu suke yi mata, kamar mai ciwo tana amsawa. Dada ta fita ta shigo da kwanuka, ta ajiye a gaban Fadila, ta ce "Amarya ga abinci nan" Fadila dama yunwa take ji, dan haka babu baƙunta ta fara buɗewa, madara ta gani a cikin wani kwano, kamar madarar ruwa ta kalli Hajiya ta ce 'Hajiya meye wannan?" Hajiya ta ce "Nono ne yanzu aka tatso shi, aka saka masa zuma, shi zaki fara sha, nan garin da haka ake rainon ciki, ba irin cimarku ta birni ba" Fadila ta kai kwanon bakinta, ta fara sha, madarar ga garɗi, sai dai da ɗumi sosai, da farko ƙyama ya bata a hankali kuma ta ji ya mata daɗi. Suna can suna hira ta kuma buɗe kwano ɗaya, naman zabo ne a soye fal a cikin tasa. Duk da yadda Yazid yake ƙoƙarin sayen nama a gida, amma kamar ba ta taɓa cin nama ba, haka ta zage ta na ci. Garin ba su da wani cigaba, dai dai kyautatawa da karamci, dan daga jin ance ga matar Yazid, ɗan wajen Kubra, maƙota da 'yan uwa suka dinga shigowa ana gaisawa, kowa da abin alkhairin da zai kawo mata ya bata. Dada da Gwaggo kamar su goya Fadila, duk tsufan Gwaggo da rashin gane mutanenta, amma tana gane Fadila sosai. Gashi ba Mutane ne masu wata wadata ba, amma irin Abincin da Fadila ke ci a garin, har ƙiba ta fara, naman safe daban na dare daban, madarar nan ta sassafe mai ɗumi kullum sai ta sha ta da zuma, gashi tunda Dada ta bata wani magani, ba ta sake yin amai ba. Yazid yana son su koma gida, dan tun washegarin zuwansu Daddy ya kirashi, a kan yana son ya zo gidansu, amma Yazid ya gaya masa basa gari, yana son Fadila ta fara zuwa awo, amma ta ita bama ta son tafiya, dan da fari ya zata ma ba zata iya zaman garin ba. A sati guda har gaisuwa da fulatanci da abin da ba a rasa ba ta iya. Ga ƙibar ciki da kyau, ga na kyakkyawan abinci da iska mai kyau na karkara, dan sosai ta sake da su suka saba. Wasa² sai da suka yi sati biyu cirr, shi Yazid ji yake kamar a kan ƙaya yake, duk a takure yake, amma ita yadda suke nuna mata soyayya da karamci ya sanya ta ji bata son rabuwa da su. Da suka tashi tafiya kuwa, Fadila ta samu alkairi sosai da sosai, kakar Yazid har da kukanta wai yaushe za a dawo mata da Fadila, ita dai tana son Fadila. Yazid ya ce mata zasu sake dawowa in sha Allah. Ita kanta Hajiya, ta ji daɗin Yadda Fadilan ta dinga nuna wa mahaifiyarsu kulawa, dan duk wanda ka nuna kana son mahaifinsa ka gama masa komai. Suka shiryo suka nufo Kano. A sati biyun nan kuwa, Mummy ba ta fita ko ina, tana zuba idon ta ina za a kawo mata Fadila, amma ta ji shiru, haka ta cigaba da mita tana matsawa Daddy a kan ya cika alƙawari. Su Fadila suka dawo gida lafiya, tana ta jin daɗin karamcin da dangin Yazid suka nuna mata. Sai dai gidan su duk yayi ƙura, Yazid ya zage ya gyara gidan, dan Fadila kwanciya tayi ta ce ita a gajiye ta ke. Ta huta ta dinga firfito da kayan tsarabar da aka bata, tana ta murna amma taga Yazid yana hararata. Ɗan tsuke fuska ta yi ta ce "Me na yi maka?" Ya ce "Ban sani ba, ƙememe ki ka yi zamanki wai ke ba zamu dawo gida ba a kan lokaci, ki ka sa sai da muka yi sati biyu, ke ko tunanin kina da miji ba kya yi ko?" Tura baki ta yi ta ce "To me zan maka?" "Au haka ma zaki ce ko?" Ɗaga masa gira ta yi, tana saka mazarƙwaila a bakinta. Yazid ya ce "Allah ya shiryeki, kuma gobe in Allah ya kaimu da safe zamu je Asibiti ki fara antenatal" Ta ce "To ɗan ustazuna, na ga dai haushina ka ke ji, kayi haƙuri ka ji masoyin" "Ba wani masoyi, kawai daga zuwa ziyara kika shantake" "To idan muka dawo kai zaka dinga samo mini madara da zuma ne? Ko zaka dinga ba ni naman nan me daɗi" "Kwaɗayayyiya dama kwaɗayi ne ya zaunar da ke, salon ace bana ba ki Abinci, a nan komai na sayo miki ko na dafa miki, sai ki ce ke ba kya so". "Eh naji kwaɗayayyiyar, ni dama ka mayar da ni" Yazid ya ce "Tashi ki koma sai kin dawo". Washegari Monday, Yazid yana ta so Fadila tayi ta shirya su tafi, amma ta tsaya a gaban mudubi, tana ƙarewa kanta kallo. "Zid da na yi ƙiba nafi kyau ko?" Yazid ya ce "Eh, ta yi miki kyau sosai" "Kenan dama baka san siriryar mace?" Tasowa Yazid yayi, ya karɓi kayan ya fara saka mata, dan idan ya biye mata yau ma ba za a fara zuwa awon ba. Amma a hakan mita ta cigaba da yi, ashe dama kallonta kawai yake baya sonta saboda ba ta da ƙiba. Ya rakata Asibiti, aka yi mata duk abinda yakamata, sannan suka taho gida, sai dai duk ta ga jikinsa a sanyaye. "Ɗan ustazuna, meke damunka, na ga kayi wani iri, ko ni ce na ɓata maka rai?" Ya ce "A'a, baki yi mini Komai ba, Daddy ya ce zai turo a ɗauke ki" "A ɗaukeni a kaini ina?" Ta yi maganar tana kallonsa. "Gida za a kai ki, fatana Allah ya sa ki dawo" Haka nan ita ma sai ta ji tana fargaba. Rungumo shi ta yi a jikinta ta ce "Babu abin da zai faru in sha Allah, ina sonka Zid sosai babu abin da zai rabani da kai da yardar Allah, muje ka rakani ma sai mu dawo tare". Yazid ya ce "A'a, Daddy ya ce ba tare zamu je ba, yanzu idan mun ƙarasa masu ɗaukarki suna titi suna jiranmu" Shafa kansa ta dinga yi a hankali ta ce "Ka kwantar da hankalinka, ba wata damuwa in Allah yarda" Haka suka ƙarasa titin unguwar su, unguwar da har yau Fadila ko sunanta ba ta sani ba, suka tarar da zuƙeƙiyar mota mai tint. 'yan sanda ne guda biyu a motar, suka ƙarasa gaban motar, suka gaisa da Yazid, ta buɗe motar ta shiga, gaba ɗaya sai tausayin Yazid ya kamata, ta dinga ɗaga masa hannu, shima jiki a sanyayen yake ɗaga mata hannu". Bai san dalilin ɗaukar Fadilan da Daddy ya turo ayi ba, dan bai yi masa cikakken bayani ba. "Allah ka sa su dawo mini da matata". Ya tafi gida yana ta Addu'a cike da fargaba! Ayshercool 08081012143LITTAFIN KUƊI NE, MAI BUƘATA YANA IYA TUNTUƁATA A KAN LAMBAR WAYATA DOMIN YA SAYA. 08081012143 84 Gaba ɗaya jikin Yazid yayi sanyi sosai da sosai, ya kasa sakewa yayi ta tunani daban daban a ransa, ya fara addu'a Allah ya taimake shi ya sanya Fadila ta dawo gareshi. Sun ɗan yi tafiya mai nisa, sam Fadila bata gane kan hanyar da ake bi, sai dai ganinsu ta yi a gidan Daddy. A ƙofar gidan suka tarar da Daddy, zaune a cikin mota shi da Amina, ɗan sandan ya kalli Fadila ya ce "Ranki ya daɗe ga Alhajin can" Fadila ta buɗe motar ta fita, ta nufi wadda su Daddy ke ciki, Amina ta ɗan ƙura mata ido, Fadila sai cukuikuye hannu take a cikin hijjabinta tana ɓoye cikin. Duk da ta yi farinciki da ganin Daddy, amma tana ganin sa tare da Amina, ranta ya ɓaci, ta tuna irin auren wulaƙancin da aka yi mata. A hankali ta ƙarasa ta buɗe motar ta shiga ta zauna, sannan ta ce "Daddy ina wuni?" "Lafiya ƙalau, ya mai gidan na ki?" Fadila ta ce "Yana nan lafiya" Shi kansa Daddy yayi mamakin yadda Fadila tayi ƙiba, dan a yadda take ba zaka taɓa cewa zata yi ƙiba ba. Ba wanda ya kuma kulata a tsakanin shi da Amina, dama Fadilan ma ba ta kulata ba. Daddy cikin tsuke fuska ya ce "Zan kai ki gida kiga mahaifiyarki, amma muddin kika kuskura ki ka yi wani misbehaving, matakin da zan ɗauka ba zai miki daɗi ba, kuma ban yarda ki gaya mata waye mijin da na aura miki ba" bai jira mai Fadila za ga ce ba ya ba motar suka bar wurin. Suna tafe suna hirarsu shi da Amina, Amina na ta cin dubulan, duk da yadda Fadila ke jin kamar ta jefa Amina waje dan haushinta take ji, amma zuciyarta ta dinga raya mata ta roƙi Amina ta sanmata dubulan ɗin nan saboda ranta ya biya. Amma ta dake ta daure ta kawar da kanta gefe. Daddy ya na son yayi wa Fadila hira, ya yi mata tambayoyi saboda ba ƙaramin kewarta ya yi ba, amma yana gudun aikata hakan, azo a samu matsala daga baya. Ko da suka shigo layinsu, gani take tamkar ta yi shekaru masu yawa rabonta da layin, hatta gidan ma duk yayi mata wani iri. Daddy na yin parking ta a fito jiki na rawa, ta nufi cikin gidan da sauri, har da tuntuɓe, tausayinta ya kama Amina. Ta kalli Daddy ta ce "Allah sarki, Allah ne kaɗai ya san yadda ta rayu tsawon wannan lokacin ba tare da gani ko kiran mahaifiyarta ba, gaskiya ta cancanci yabo, ta yi haƙuri kuma ta yi biyayya" Daddy ya yi murmushi ya ce "To lawyer, amma koma dai meye ai ba a wahala take ba, kalli yadda ta koma fa" Amina ta ce "Haka ne, amma duk da haka gurbin uwa daban yake". Ita kuwa Fadila da gudu ta ƙarasa sashin Mummy, ko nauyin cikin bata ji, a falon Mummy suka haɗu, Fadila ta faɗa jikinta tana kuka. Rungumeta sosai Hajiya Zainab ta yi, ita ma ta fashe da kukan. "Fadila, ina ya kai mini ke tsawon wannan lokacin, da kika kasa ɓallowa ki dawo gida, hankalina duk a tashe ban san in da kike ba, na shiga damuwa sosai" Fadila ta ɗago tana faɗin "Mummy, babu yadda za ayi na iya zuwa, ya ce idan na zo bai nemeni ba bai yafe ba, ni kaina na yi kewarki Mummy". Gani ta yi Mummy tana ƙare mata kallo, daga sama har ƙasa, ta miƙa hannu ta janye hijjabin Fadila, sai ga ciki ya fara tasawa" Waro ido Hajiya Zainab ta yi ta ce "Fadila da gaske aure yayi miki? Shi ne har kika yadda ki ka yi ciki, a garin yaya ki ka samu Ciki Fadila?" Fadila ta yi shiru tare da sunkuyar da kai ƙasa. "Sannin yadda aka yi ta samu ciki ba huruminki bane ba, tun da dai aurar da ita na yi, ba wai sakinta na yi a duniya haka ba" suka jiyo muryar Daddy, Hajiya Zainab ta kalli in da Daddy ke tsaye, Fadila kuma ta sunkuyar da kai kamar mara gaskiya. Cikin takaici Hajiya Zainab ta ce "Amma ta yaya mutane zasu yadda aure ta yi, bayan babu wanda ya san da hakan?" Daddy ya ce "Ai ba dole ne sai kowa da kowa ya sani ba, tun da mun cika sharaɗin abin da Addini ya tanada, gata nan zuwa yamma zan mayar da ita" Jin Daddy kawai Hajiya Zainab ta yi, dan ba ta ga abin da zai sa ta bari ya sake ɗauke Fadila daga gabanta ba. Ya juya ya fita ya bar ɗakin, jan Fadila ta yi zuwa ɗakinta, ta rufe bedroom sannan ta kalli Fadila ta ce "Fadila, wai ɗan gidan wa ma ya aura miki ne?" Jiki a sanyaye Fadila ta girgiza kai ta ce "Mummy ba ɗan kowa bane ba, ba shi da komai sai Allah, amma ban rasa ci ba ban rasa sha ba da abin da zan saka jikina" Mummy ta ce "Ke! Wai yana ga kina acting kamar kina son auren, bayan auren dole yayi miki, a ina mijin yake kuma waye shi?" Fadila ta ce "Mummy ko na gaya miki ba zaki gane shi ba". A hasale ta ce 'Ke dalla ki mini bayani a ina yake, mara tunani da ga zuwa kin ƙunso ciki kamar abin da kike jira kenan, ke ko kishin kanki ba kya ji kuma ba kya tausayina, maimakon ki ɓallo ki gudo amma kika miƙe ƙafa, har da ɗaukar ciki, to bari ki ji na gaya miki, ba in da zaki koma daga nan, kuma wannan banzan cikin sai an zubar da shi. Wato saboda dai ya nuna mini ban isa ba, shi ne ya aurawa Khalil 'yar talakawa ya rabani da shi, kema ya samo wani wahalallen ya aura miki, dan cin zarafi, to bai isa ba yayi kaɗan ba in da zaki koma". Fadila ji ta yi tamkar ta cewa Mummy, dan Allah ta ƙyaleta tana son aurenta, amma ta yi shiru, dan kar su ɓata. Hira suka dinga yi, Mummy na cigaba da alwashin sai ta wulaƙanta Amina kamar yadda ta kassara mata iyali, kuma ko ta tsiya sai ta kashe auren da aka yiwa Fadila. Ita Fadila hankalinta yana can kan Yazid, ba ta san a wani hali yake ba, ta san shi da saurin rikicewa, ta kasa manta yadda ta ga fuskarsa ta sauya da zata tafi. Ta tafi ɗakinta, ta je ta yi wanka, ta saka wasu kayan, ta tsaya a gaban mudubi tana kallon kanta, ita kanta ta san ta yi ƙiba sosai ta yi murmushi ta ce 'Su ɗan ustazuna an iya raino, duk na yi ƙiba" sai kuma ta shafi cikin jikinta ta ce "Allah ya kawo mini abin da ke cikin nawa lafiya, ina son na ganka amma Mummy ta fara iƙrarin rabani da kai" Duk da yadda ta so ta zauna su yi hira sosai da Mummy, amma ta kasa saboda baccin da take ji, ga sauran gajiyar hanya na tafiya Jalingo da suka yi. Hajiya Zainab kuwa ta kasa ta tsare, tana tunanin yadda za ta yi da cikin Fadila, da kuma shirin ko ta kwana a kan sai dai su yi wadda za su yi ita da Alhaji Ahmad, amma ba zata taɓa bari ya kuma ɗauke mata Fadila ba. Sai la'asar Fadila ta tashi, Hajiya Zainab ta shirya mata Abinci, Fadila ta kalli Mummy ta ce "Mummy ni bana son wannan Abincin, idan na koma gida na san Hajiyarsa ta aiko mini da tuwo, ni yanzu da zan samu ƙosai ne ma dai da sauƙi" "Ke dalla can rufe mini baki, sai ka ce wani cikin arziƙi to bari ki ji na gaya miki, sai kin rabu da cikin nan, maza ɗau Abinci ki ci". Fadila ta ce "To bari na yi salla" Bayan ta yi salla kuwa, ficewa ta yi ta tafi Kitchen, ta tarar Hajara na ta aiki, Hajara ta gaisheta cikin girmamawa, ta amsa mata ba yabo ba fallasa, ta nufi Fridge. Hamdala ta yi da taga manyan mangwaro a ciki, ta zauna ta dinga sha kamar mayuwanciya, sannan ta baro Kitchen ɗin. Sashinta ta koma, ta sake tattaro abin za take buƙata na kayan ta, ta haɗe wuri guda ta kai su falo ta ajiye. Sannan ta koma wurin Mummy, ɗan kaɗan ta ci Abincin, Fadila na son yin hira da Mummy, amma Mummy ban da zancen kashe mata aure da zubar da ciki babu abin da take yi, gaba ɗaya jikinta ya yi sanyi. Wani hali Yazid zai shiga idan aka kashe auren nan, aka kuma zubar masa da ciki, za a sake jefa shi cikin damuwa. Fadila ta ce "Mummy, mijina maraya ne rayuwarsa akwai abin ban tausayi.... Kan ta ƙarasa Hajiya Zainab ta ce "Eh, kema na ki uban na ƙoƙarin mayar da ke marainiya ba, kuma mara amfani da ba ta san ciwon kanta ba, ni gani nake ke murna ma kike yi da auren da aka yi miki ko?" Fadila ta yi shiru ta sunkuyar da kai. Biyar da rabi, sai ga Daddy a sashin Mummy, yana kiran Fadila, Fadila ta amsa ya ce "Maza ta so muje na mayar da ke" Miƙewa Hajiya Zainab tayi ta ce "Babu wannan maganar, ai kuma ta zo kenan, ba ka isa ba fa" Daddy ya kalleta ya ce 'Haka muka yi da ke?" "Da ka tashi aurar da ita, ni wace yarjejeniyar muka yi? Babu in da zata, ta zo kenan ba zan yadda ka sake rabani da ita ba, ban san in da zaka kai ta ba" Daddy ya ce "Babu in zan kai ta sai ɗakin mijinta, kuma da gani kema kin san ba a wahala take ba, dan haka kar mu zo muna jayayya da ke, har ta kaimu ga ɓacin rai". Cikin rashin girmamwa ta ce "Ta daɗe ba ta kaimu ga ɓacin ran ba, wallahi babu in da zata je". Daddy ya kalli Fadila ya ce "Ke kin san yadda muka yi, dan haka ta so mu tafi" Aikuwa Fadila ta miƙe, ta yafa mayafin jallabiyarta ta nufi in da Daddy yake, dan yanzu haka tana son sanin halin da Yazid yake ciki. Cikin mamaki ta ce "Fadila, au watsa mini ƙasa zaki yi a ido? Kin zaɓi ki koma cikin tsiya da wahalar da ya zaɓa miki?" Fadila ta girgiza kai ta ce "A'a Mummy, amma na riga na yiwa Daddy alƙawarin ba zan yi gardama ba, ina son gobe ma ya sake bani dama na zo na ganku, bana son irin abubuwan da suke faruwa a tsakanin ku, kuma in da nice ki kwantar da hankalinki, mijina talaka ne amma yana kula dani, babu abin da zai sameni akasin alkhairi, adduraki nake buƙata a duk in da nake Mummy, kiyi haƙuri ki Kwantar da hankalinki" Daddy ya ce "Alhamdilillah, 'yar ta ki ma har ta fiki tunani da hankali, wuce muje kar muyi yamma". Fadila ta yi gaba tana goge hawaye, tana yi tana waiwayen Mummy, yayin da Mummy ta yi turus tana bin Fadila da kallo, Fadila ta ɗau sauran kayanta da ta tattara tai waje. Abin ba ƙaramin ɗaure wa Mummy kai ya yi ba, anya ba asiri ya yi wa Fadila ba? Gaba ɗaya kamar an canza mata Fadilan baki ɗaya. Babban abin da ya ƙular da Fadila bai wuce yadda yanzu ma tare da Amina za aje mayar da ita ba, ko meye dalilin hakan oho. Ta buɗe mota ta shiga tana kuka, Daddy ya ƙaraso ya buɗe motar shi ma ya shiga, shi kansa Fadila ta bashi makaki ba kaɗan ba. Sannu a hankali ya fara jan motar, Fadila sai waiwaya wa take ko Mummy za ta fito, sai ta ji duk babu daɗi na watsa wa Mummy ƙasa a ido da tayi. Daddy ya numfasa ya ce "Fadila" "Na'am ta amsa idonta fal hawaye". "Kiyi haƙuri, mahaifiyarki za ta sakko ita ma, kamar yadda na fuskanci sauyi a tare da halayenki, ita ma ki dinga yi mata addu'a, daga cikin dalilan da ya sanya na aurar da ke ga mutum mai ilimin addini shi ne fatan samun sauya halayen da kika ta so a kai. Alhamdilillah an samu sauyi, kuma kin yi dauriya da biyayya ƙara haƙuri Allah ya yi miki albarka. Fadila babu lallai ki samu mijin da zai so ki ya tattalaki kamar yadda mijinki yake miki, na ce a sama masa aiki ya ke ta bani haƙuri a kan kar in damu yana kula da ke. Har CID ne da ni a nan unguwar ta ku da suke kula da motsinku, kuma yaba da jajircewar mijinki bashi da shi amma yana ƙoƙari. Idan kika yadda mahaifiyarki ta kashe miki aure, na farko dai ba zata iya samo miki miji mai nagartar naki ba, dan kuɗi ba sune kwanciyar hankali ba. Sannan hakkinsa sai ya kamaku, ga kuma rabo ana sa ran samu a tsakaninku, dan haka ki ƙara haƙuri kin ji autana" Cikin kuka ta ce "To Daddy" Amina ta yi shiru, amma duk jikinta yayi sanyi Fadila ta bata tausayi sosai da sosai, ba kowane ɗa ne zai iya jure irin wannan punishment ɗin ba. Shi kansa Daddyn dauriya kawai yake yi, ya ce "Ai dai kina son sa ko? Zid ake ce masa ko menene?" Yayi Maganar cikin sigar wasa. Murmushi ta yi duk da hawayen da ke fuskarta. Ya ce "Ai yana gabana lokacin da ake yi masa kashedin idan wurin budurwa ya je za a gane. Dan Allah Fadila kar ki yi kishi irin na mahaifiyarki, kishi halak ne amma kiyi mai tsafta, mu maza sai haƙuri zaki tara da yawa da ƙyar ki samu wanda baya son samun ƙari, komai kyautatawa da halaccin matarsa, sai dai masu hankalin cikinmu ko mata nawa zasu aura, ba sa manta halarcin matar fari, kuma ba sa wulaƙanta ta, sai dai ya danganta da halin matar. Nan gaba ko Allah ya hore masa ya ce zai ƙara aure, kalleshi kawai kiyi kamar baki damu ba, wannan abu ya fi komai ɓata mana rai, gashi nan ina ta baki satar amsa, kuma banda tarkacen ƙawaye mu mun fi so muga a kodayaushe mune abu na farko a gareku, ku fifita mu fiye da kowa, ku bamu muhimmanci kar ku saka wani abu a gabanmu sai a zauna lafiya, banda kishi na rashin ji Fadila" Fadila ta ce "Ai ni ya ce ba zai yi mini kishiya ba" Murmushi Daddy ya yi ya ce "Eh lallai soyayya ta yi daɗi, to Allah ya sa". Duk da duhun magariba ya rufa, dan sai da suka tsaya Daddy yayi salla, sannan suka ƙarasa unguwar su Yazid, a titi Fadila ta sauke glass tana faɗin "Daddy gashi can" ta ƙarasa maganar tana ɗagawa Yazid hannu. Slow Daddy ya yi da motar ya tsaya, Yazid ya ta so da sauri, hannunsa riƙe da leda, a kan dakalin wani masallaci yana ta rarraba ido a titi. Cikin fara'a ya ƙaraso, ya risuna yana gaida Daddy. Daddy ya ce "Afuwan, na ɗauke maka mata wuni guda ko? Tuba nake" Yazid ya yi murmushi yana sunkuyar da kai. Fadila ta buɗe motar zata sauka, Daddy ya ce "To Hajiya, ai kya bari na ƙarasa da ku ko?" Sai kuma kunya ta kamata. Daddy ya ce Yazid ya shiga ya ƙarasa da su gidan, aikuwa ya shiga, nan suka gaisa da Amina ma. Fadila ta yi ƙasa da murya tana taɓa ledar hannunsa ta ce "Me ka sayo mana?" "Kununki ne da nake sayo miki da kuma kifi" A hankali take faɗin zan ci daɗi. Sai kuma ta matsa jikinsa take raɗa masa "Kayi missing ɗi na ko?" Yazid ya yi murmushi ya girgiza mata kai. "To me ka zauna yi a titi kana jira?" A hankali ya ce "hutawa kawai nake yi" Hannu ta kai ta matse masa hanci a hankali ta ce "Ba wani nan" Daddy yana kallonsu ta mudubi, kawai ya ɗan yi murmushi, kamar ba yanzu ta gama koke-koke a mota ba. Har ƙofar gidansu Yazid suka isa, Amina ta jinjina wa Fadila haƙurin da ta yi na zama a gidan nan, saboda yadda take ji da kanta a baya. Yazid ya ce "Amma dai Daddy ai zaku shigo ko?" Daddy ya kalli Amina ya ce "Mu shiga?" Amina ta ce 'Ai ko ba zaka shiga ba, ni zan shiga na yi salla". Yazid ya ƙarasa yana buɗe gidan, Daddy ya buɗe boot ɗin mota, ya kalli Fadila ya ce "Zo ki taya antynki ɗaukar kayan nan" Ba ƙaramin ƙulewa Fadila ta yi ba, amma ba yadda ta iya, ta zo ta taya Amina ɗaukar fulasan abinci. Ganin bayan motar ta yi shaƙe da kayan Abinci ɗanye, Daddy ya yiwa Yazid alama da ya zo. Yazid ya ƙaraso yana risunawa, Daddy ya ce "Yazid ka samo yara su shigar muku da kayan nan, sai a biya su". Yazid ya ɗan yi turus yana kallon kayan, Daddy  ya ce "ya na ga kayi shiru?" Yazid cikin sanyin jiki ya ce "Daddy muna da abinci, ina ƙoƙarin ajiyewa idan mun shiga ma zaka ganix Daddy ya dafa kafaɗar Yazid ya ce "Yazid ba gazawarka na gani ba, kawai na baku ne dan na tallafa maka". Yazid ya ce "Daddy kar zuciyata ta mutu ne" Daddy ya yi murmushi ya ce "Ai kai jarumi ne, kuma na yaba da ƙoƙarinka kar ka damu" Ba dan Yazid ya so ba, haka ya yarda ya karɓi kayan nan aka shiga da su cikin gidan. Amina ta yi alwala, Fadila ba tare da ta kulata ba ta bata darduma domin ta yi salla. Sai dai Fadila sai kallon cikin Amina take yi, ya yi girma sosai kamar ta kusa haihuwa, da ƙyar take sallar ma. Daddy har cikin gidan ya shiga, shi kansa Daddy ya ga gidan yayi ƙanƙanta, amma farincikin da ke kan fuskar Fadila ya tabbatar masa da tana cikin farinciki. Daddy ya shiga falon ya zauna, aka yi sa'a aka kawo wuta. Yazid ya ce yana zuwa, ya fita Fadila suka yi ta hira da Daddy. Ba a jima ba sai ga Yazid ya dawo hannunsa da leda ya sayo manyan lemuka, ya shiga Kitchen ya haɗo kwanukan Abinci, da flask na girkin da yayi da rana ya zo ya jera. Daddy ya ce "Ohh, Yazid sannu da aiki, ke Madam meye aikin ki ne na ga shi yake yin komai". Fadila ta ce "Daddy bani da lafiya fa" Daddy kawai ya girgiza kai, shinkafa da miya ga kayan ganye da kifi, Yazid ya ajiye musu. Amina ta sake ta ci Abincin, dan ba ta iya cin Abincin da ta girka. Har ku san tara na dare, Daddy ya ce Yakamata su je su gaisa da Hajiya. Amina ta ce "Yakamata a ɗebarwa Hajiyan Abincin nan a kai mata ita ma". Daddy ya ce "Haka ne, Fadila ɗauko kwano ki zuba mata". Sai a yanzu Fadila ta san meye a cikin fulasan, wainar masa cikin fulas, ga uwar miya mai rai da lafiya ta sha nama, gefe kuma ga fulas ɗin dubulan. Fadila ta ɗaga kai ta kalli Amina, a rant ta ce "Wai ita a dole ga me kirki, to in dai ni ce kin yi a banza" Hajiya kuwa ta yi murnar ganin Alhaji Ahmad, suma ta karrama su, sai wajen goma na dare su Daddy suka tafi. Mummy kuwa ta sha mamakin abin da Fadila ta yi, gaba ɗaya jikinta ya yi sanyi sai dai ta fara tunanin ko Asiri aka yi mata idan ba haka ba yadda za ayi Fadila ta yi haka. Hajiya Turai ta kira a waya, gaba ɗaya jikin Mummy a sanyaye yake. Hajiya Turai ta ɗaga wayar tare da yin sallama. Mummy ta amsa jiki a sanyaye. Hajiya Turai ta ce "Yaya, ya dawo miki da ita ɗin ne?" Mummy ta ce "Hajiya Turai, akwai lauje cikin naɗi a wannan lamarin, Turai ya dawo mini da Fadila da ciki, kuma ta zaɓi babanta a kaina, dan ta zaɓi komawa in da ya aurar da ita, duk da ƙoƙarin da nayi a kan na riƙeta kar ta koma amma yarinyar nan ta watsa mini ƙasa a ido, kuma wallahi da alama wani talakan ya aura mata". Turai ta ce "Innalillahi wa innalillahi raji'un, wallahi Zainab wannan yarinyar da mijinki ya aura ita ta rusa miki gida" "Turai ni yanzu ba ta wannan nake yi ba, ta yadda 'ya ta zata dawo gareni nake, idan Fadila ta haife cikin nan shikenan" Turai ta ce "Yanzu kin gano in da take ne? Kuma waye mijin?" "Wallahi ban sani ba, tun da ta zo fa bacci take yi, ni gaba ɗaya kamar an canza mini Yarinyar nan, ban gane kanta ba kamar ba Fadila ba, shikenan ba Khalil ba Fadila?" Tayi maganar cikin ƙunci da ɓacin rai. "Kiyi haƙuri, yanzu dai ki fara mayar da kai mu gano a in da take, amma tukuna ma ko sunan unguwar da take baki sani ba, ko lambar wayarta". Cikin karaya Mummy ta ce "Na gaya miki kamar wadda ake hurawa wuta, ko hirar kirki ba muyi da ita ba, gaba ɗaya ma ƙin sakin jiki tayi da ni" Hajiya Turai ta ce "Ke bana raba ɗaya biyu, an asirce miki 'ya wannan maganar ba ta waya bace ba, bari sai mun zauna tukuna". Ta ce "Shikenan sai anjima". Fadila kuwa Yazid ya dinga yi mata mita, yana mata faɗa, ganin ta zage tana rawar jiki tana cin abin da Amina ta dafo ta kawo mata, amma sai wulaƙanci take yi mata, yayi ta mata nasiha da nuna mata abin da take yi ba daidai bane ba. Bayan ya sakko daga fushin wucin gadin da yayi da ita ne, yake tambayarta ya gidan ya kuma Mummy. Shareshi ta yi bata kula shi ba, Ya ce "Magana fa nake miki". "Ina ruwanka da ni, ba faɗa ka ke yi mini ba" "Na yi miki faɗan, ke gaskiya ce ba kya so ko?" Tayi shiru tana cuna baki, Nasiha Yazid ya shiga yi mata, a kan abubuwan da take yiwa Amina. Khalil kuwa hankalinsa a kwance yake, ya samu nutsuwa sosai da sosai, ya samawa Hafsa makaranta, yake ta ƙoƙarin biya mata kuɗin makaranta a Kaduna, duk sati biyu take zuwa Abuja in da yake ta yi weekends, ga ɗawainiyar ciki, amma kasancewar ta saka kanta ya sanya ba ta jin wahalar hakan. Su kan zo Kano idan aka yi hutu, sai dai bai fiye kaita gidan Mummy ba, sai dai shi ya je shi kaɗai. Daddy ya gaya wa Khalil batun auren da ya yiwa Fadila, Khalil ya tausayawa Mummy, dan abin da take gudu ne duk ya baibaiyeta. Daddy ya ce masa kan su bar Kano, ya je gidan Fadila su gaisa. Yazid ya ji daɗin zuwan su Khalil, kamar ɗan uwansa ne ya zo, sai murna yake yi. Zama da Yazid da yawan nasiharsa a greta ya sanya ta sakarwa Hafsa fuska, har suka ɗan taɓa hira, Fadila har da tambayar me za ta dafa musu? Khalil ya ce "Allahu Akbar, Daddy ya iya punishment, su Fadila an nutsu" Hararar Khalil tayi ta ce "Ka ga ka kiyayeni, na gaya maka". Hafsa ta ce "Ba sai kin dafa mana komai ba, kar mu saki wahala". Yazid ya ce "Ba wata wahala, ai baƙinmu ne ku" Fadila ta ce "Ina da komai na Abinci, ku faɗi abin da kuke so". Hafsa ta ce "Duk abin da kika dafa zamu ci" Fadila ta ce "To shikenan" ta tashi ta fita tsakar gida aikin girki, Hafsa ta biyota tana tayata. Ranar wuni suka yi tare, Fadila ta ji daɗin zuwansu, dan rabonta da Khalil har ta manta. Duk da Hafsa miskila ce, amma ta ji daɗin sakin fuskar da Fadila ta yi mata, dan tsakar gida suka dawo tare suka ci Abinci, suka bar su Yazid a ɗaki. "Fadila mijinki yana da kirki, Allah ya sanya yayi miki halacci kamar yadda kika yi haƙurin zama dashi gashi da karamci" Fadila ta ce "Ai a raina bana tunanin zai mini wani abu makamancin butulci, ya daɗe yana sona fa, Ashe Allah ya ƙaddara sai ya aureni" Fadila ta yi ta bata labarin abubuwan da suka dinga faruwa a makaranta tsakaninta da Yazid. Hafsa ma sai ta fara bata labarin yadda suka haɗu da Khalil, har kamata da 'yan sanda suka yi ya karɓota, a haka har labari ya gangaro har wani daga cikin halin da suka shiga na matsin rayuwa. Zuru Fadila ta yi da ido, tana jin Hafsa, da irin ƙalubalen rayuwar da ta fuskanta ita ma bayan rashin mahaifinta. Wata irin kunya da nadamar abin da suka dinga aikatawa ita da mahaifiyar ta ne ya kamata, gaskiya sun yi kuskure sosai da sosai, wasu mutanen na fama da rayuwa da tsananin buƙata, amma ba su taimake su ba, sai ma sake jefa su cikin wata damuwar ta hanyar muzgunawa. A zahiri Fadila ta wayance, tana ɗan rarrashin Hafsa. Gaba ɗaya tausayin Hafsa ya kamata, tare da dana sanin abubuwan da suka aikata a baya. Bayan la'asar suka shirya zasu tafi, idon Fadila ya cika da hawaye, Khalil ya ce "Ke kuma menene?" Ta girgiza masa kai alamar bakomai hawayen da take ƙoƙarin riƙewa suka fara zubo mata. Jan hannunta yayi zuwa soro, ya kalleta ya ce "Fadila menene? Auren ne ba kya so ko?" Ta ce "A'a Yaya Khalil, ina son aurena, kuma ina son mijina, yana kula da ni fiye da tunaninka, kawai dai ina missing ɗinku ne, kuma wallahi nadama nake yi Yaya Khalil abubuwan da muka yi a baya, yanzu matarka take bani labarin rayuwarta, idan ka ji labarin Yazid ma abin tausayi, gashi dukkanin su babu wanda ban taɓa cizgunawa ba, dan Allah Yaya Khalil ka ɗan nema mana yafiyarta dan Allah" Khalil ya rungumeta a jikinsa yana share mata hawaye ya ce "Hafsa ba ta da matsala, kar ki damu kin ji". "Wallahi na yi nadama sosai da sosai, sannan dan Allah Khalil ka ɗan taushi Mummy ta yi haƙuri, ta fara iƙrarin zata kashe mini aure ranar da muka je, dan Allah Yaya Khalil ka ɗan tayani tausarta, bana son watsa mata ƙasa a ido, amma wallahi ina son aurena da mijina, Yazid tun muna makaranta yake sona, dan Allah ka bata haƙuri, wallahi ina sonta sosai ita ma, amma dan Allah ta barni na zauna da mijina ni duk talaucinsa ina son sa" Murmushi Khalil ya yi, ya goge mata hawaye ya ce "Shikenan, kar ki damu komai zai wuce in Allah ya yarda" "To yaushe zaku dawo?" Khalil ya ce "Sai dai kuma ku zo mana kan mu koma" "To shikenan, zan tambayi Zid zamu zo in sha Allah, amma kar ka gaya wa Mummy in da nake, idan ba haka ba zata zo ta ce sai na koma gida" "Kar ka damu, sai da muka yi wannan yarjejeniyar da Daddy, sannan ya yadda muka zo" Yazid kuwa duk a tsorace ya ke, kar ya je wani abun yayi wa Fadila bai sani ba take kai ƙararsa. Khalil ya ce "Baby Hafsat, taho mu tafi yamma ta yi fa". Fadila ta ce "Sai su Baby, to Baby Hafsat yaushe zaku dawo dan Allah?" Hafsa ta ce "Ai ni ko cewa kika yi na kwana a nan zan kwana" Murmushi Fadila ta yi, suka fito suka raka su Hafsa har bakin mota suna ɗaga musu hannu. Ayshercool 0808101214385 Bayan sun raka su Hafsa sun tafi, suka dawo gida Fadila ta gyara gidan, ta dawo falo ta tarar da Yazid ya zauna yayi shiru yana tunani. "Zid menene kuma?" A hankali ya waiwayo ya kalleta ya ce "Fadila bana jin daɗin a duk lokacin da wani daga gidanku ya zo na ga kina kuka, duk sai na shiga damuwa dan Allah idan wani abun nake yi miki da ba kya so, ni ki dinga gaya mini, kar su zata ko ina muzguna miki ne" Murmushi ta yi, ta zauna a kan cinyarsa ta kalleshi, ta kai hannu ta tallafi fuskarsa ta ce "Allah ne kaɗai ya san irin son da nake yi maka ɗan ustazuna, wani abu ya daina baka tsoro, sai dai ni a halitta ta ne yawan kuka, kuma kaga duk na yi nesa da 'yan uwana da iyayena idan za a zo wurina sai dai a ɓoye, saboda kar Mummy ta sani, shi ne yake sani damuwa, amma ni ba abin da kake mini da zan iya kai ƙararka sai fatan Allah ya biya ka". Ta ƙarasa maganar tana shafa sajensa, ga wata irin ƙaunarsa da take ji a zuciyarta. Yayi ajiyar zuciya ya ce "Shikenan,amma dai ina sake baki haƙuri komai zai wuce in Allah ya yarda" "Haka ne, hira muke yi da matar Yaya Khalil, take ɗan bani labarin rayuwarta, wallahi Zid na ji kunyar ta fiye ds da yadda na ji kunyarka a kan abubuwan da na dinga yi maka. 'yar uwata mace muka sakota a gaba da wulaƙanci saboda talaka ce, har wurin da take sayar da awara fa Mummy ta je ta yi mata wulaƙanci, wallahi zuciyata babu daɗi, kuma sai na ji nauyinta na kasa cewa ta yafe mana wallahi ban kyauta ba abubuwan da na dinga yi" Ya kwantar da kanta a ƙijinsa, yana wasa d gashin kanta sannan ya ce "Alhamdilillah, tun da har Allah ya sanya kin fuskanci kuskurenki, sai ki yi ta istigfari, sannan ki cigaba da yiwa Mummy ma Addu'a" ta jinjina masa kai alamar to. "Yarinya ta nutsu, ta auri ɗan shawalwalin ustaz" yayi maganar yana tsokanarta. Hannu ta saka tana matsa masa Adams apple da yake maƙogwaronsa. Buge hannunta yayi ya ce "Ba na hana ba" Ta ƙara kai hannu ta matsa tana dariya. Hajiya Zainab kuwa dama ladabin da ta yi wa Daddy, dan ya dawo mata da Fadila ne, yanzu kuma ta sako shi gaba, a kan lallai sai ya gaya mata waye mijin da ya aurawa Fadila, kuma a ina yake? Daddy yayi mursisi ya ce ba zai gaya mata ba, tun da dai ba zata canza hali ba, ya san idan har ya kuskura ya gaya mata sai ta kaso auren nan. Fadila kuwa ta yi lafiya, ta mayar da hankali sosai a kan karatun da Yazid yake koya mata a gida, ayyukan gida kuwa cikin ikon Allah da taimakon Maryam duk ta iya ayyukan gida ita take kayanta. Wanki ne dai ba ta yi, iyaka ta wanke undewars ɗinta, sai Yazid ya dawo zai bi dare ya yi musu wanki. Ba laifi Yazid yana samu a kan harkar kanikancin da yake yi, ɓangaren fentin mota ne, duk da gyaran ma ya iya, ga uban gidansa baya yi masa mugunta saboda jajircewasa da gaskiya a kan sana'ar, ga makarantar da yake zuwa koyarwa, suma suna biyansa sun ƙara masa ma albashi, Yazid shi ne har gidan buredi duk in da ya san zai buga ya tashi ya samu halal yana yi, sam ba ya samun isasshen hutu, gashi dare kuma maimakon ya huta, yana tsananta ibada da daddare sosai. Yana yawan gaya wa Fadila cewar tun da Allah ya sa ya aureta, ƙofofin samu suke ta buɗe masa da kuma alkhairai ta kowace fuska. Yayin da ita ma take alfahari da samunsa a matsayin mijinta, saboda Yazid mutum ne na gari. *** Hajiya Zainab duk iya tijararta da bala'inta, Alhaji Ahmad bai yadda ya gaya mata in da Fadila take aure ba, balle ya gaya mata wa ya aura mata, Hajiya Zainab ba ta taɓa sanin yana da wannan uban taurin kan ba sai a yanzu, ashe a baya ƙyaleta kawai ya ke yi take abin da ta ga dama, gashi ba ta san Amina na da ciki ba, sai daga baya ta lura da tsohon cikin da yake jikin Amina, ga takaicin cikin jikin Fadila da ta gani, gaba ɗaya ta rasa in da zata saka kanta. Su Hajiya Salma na ta banka mata magunguna, wai suna karɓo mata a wurin malamai, wanda zata sake mallake Alhaji Ahmad, ta sha wannan ta jiƙa wancan ta turara wannan amma bata sauya zani ba. Gaba ɗaya kana ganinta ka san a firgice take, Amina kuwa hankalinta a kwance yake, 'yan ƙauyansu na ta amfana da dukiyar Alhaji Ahmad, ba su ba har danginsa da maƙwabtansu suna morar dukiyar nan. Sai sunan Hajiya Zainab ya fara ɓata sai na Amina, a matsayin matarsa, haka zalika Amina ba ta manta uwar ɗakinta ba Hajiya Maryam, ga kuma Ammi. Azima ma an yi bikinta, ta auri abokin ƙanin Ammi an sha biki sosai, Amina ga ciki ga shagalin biki. Maman Hafsa ita ma Alhamdilillah, ta samu kwanciyar hankali da sauƙin rayuwa, duk da da girmanta ta auri Alhaji Ilyas, amma yana matuƙar ji da ita, mussaman yadda ta rungumi 'ya'yansa ta riƙe kamar nata, ta samu damarmaki a wurinsa, dan har yaran maƙotansu, ta sanya ya dinga samarwa aiki, a tarayya. Watarana da weekends, Mama tana tare da ƙaramin ɗan Alhaji Ilyas, mai shekaru goma sha biyu tana koya masa karatu, Hafsa ta zo gidan ita da Khalil duk suna tare suka yi baƙi. Sai da ba ƙaramin mamaki suka yi ba, da ganin suwaye baƙin. Mahaifiyar Najib ce, da ƙanwarta suka zo, sai ƙarewa gidan kallo suke yi, gida kamar na wani sanata saboda kyau tsaruwa. Mama ce ta iya ƙarfin halin yi musu sannu da zuwa, suka zauna suna kallon Hafsa da ta haɗe rai. Kasancewar Khalil bai san su ba ya sanya ya gaishe su, yana ƙoƙarin tashi ya bar falon, amma Mama ta ce yayi zamansa. Babar Najib ta kalli Hafsa ta ce "Ohh Hafsa aka yi aure amma babu gayyata, to Allah ya sanya alkhairi". Haushi ne ya kama Hafsa, Mutanen da suka ƙi karɓar mata kuɗin aure ne ke wannan maganar banzan. Mama ta saka aka kawo musu ruwa da lemuka, suka dirarwa ruwan robar nan kamar ba su ta ɓa sha ba da lemo, suka duma jarka a baki suna kwankwaɗa. Shi dai Khalil sai mamakin Suwaye wannan yake. Sai da suka sake nutsuwa, Sannan babar Najib ta ce "Dama alfarma na zo nema wurinki, daga irin arziƙin da Allah ya yi muku ke da 'yar ki". Mama ta ce "Ina jinki" Ta gyara zamanta tana matso hawaye ta ce "Wallahi kinga baban su Hafsan aka kama, bashi ya yi masa yawa, an kai shi kurkuku, hatta gidan da muke ciki, kotu na ƙoƙarin waƙafce shi, ga Najib sai a hankali ba sana'a ba aikin yi, yanzu haka shaye shaye yake yi, Abin da zamu ci ma gararmu yake yi, ki taimaka dan Allah" Sai yanzu Khalil ya gane in da zancen ya dosa, sannan ya gane ma suwaye. Aikuwa nan da nan ransa ya ɓaci, dan ba ya ƙaunar ko sunan yaron nan Najib, balle wata alaƙa ta sake haɗasu da su Hafsa, cikin fusata ya ce "Hajiya, nan ba wurin neman taimako bane ba, ko kin manta lokacin da su kuka watsar da su, ko ba dai mijin naki ne wanda aka kawo kuɗin aurenta ya ƙi karɓa ba, yai ta kusheta ba, ba za a taimaka ba ɗin, kuma daga rana mai kamar irin ta yau, kar ku sake zuwa gidan nan". Babar Najib ta ce "Yaro me yayi zafi haka? Dan Allah ai bai kamata a dinga tuna baya ba, dan Allah ki saka baki komai ya wuce dan Allah" Mama ba ta taɓa wulaƙanta ɗan Adam ba, amma a wannan karon ji take tamkar ta rufe matar nan da duka, dan ba zata taɓa manta baƙar wahalar da matar nan ta gana mata ba ita da mijinta lokacin tana kishiyarta. Mama ta duba bayan kujera, ta ɗauko kuɗi dubu biyar, ta ajiye mata ta ce "Suwaiba, dan Allah ga wannan kya hau mota, amma dan Allah dan annabi kar ki sake zuwar mini gida, bana son ɗan abin da yayi saura na mutunci ya ƙarasa zubewa, muddin mijina ya san haryanzu akwai wata alaƙa a tsakaninmu akwai matsala, dan haka dan Allah ki yi haƙuri da wannan dan Allah kar ki sake zuwa". Ta kalli Mama ta ce "Yanzu wulaƙanta ni zaki yi, dan Allah ya rufa miki Asiri?" "Lokacin da Allah ya rufa mukun ni ba tone nawa asirin ku ka yi ba?" Khalil rai a ɓace ya yi mata fata-fata ya koreta, saboda ya tsani matar da duk abin da ya shafi Najib. Fadila cikinta ya shiga wata na bakwai, amma bata son wanka, wai saboda warin sabulun damunta yake yi, sai Yazid yayi ta lallaɓata tukuna, kan ya tafi makaranta sai ya yi mata wanka, da daddare ma haka, aikin gida ba komai take iya yi ba. Kwatsam ciwon aljanu ya kuma dawo mata, babu ciwon kai babu komai sai ta yanke jiki ta faɗi, ga ciki, haka kurum kuma sai ta fara zubar da jini, jini sosai, amma da ya kaita Asibiti idan aka yi gwaje gwaje sai ace cikin lafiya ƙalau. In da Allah ya taimaki Yazid, Daddy ya basu kayan Abinci amma duk kuɗin da ya samu kusan a kan larurar Fadila yake tafiya. Gashi yayi shiru ba wanda ya gayawa, basa baccin kirki sam, saboda yanayin jikin Fadila. Idan tana hayyacinta tai ta kuka ta ce "Wallahi Zid ni tunda nake a gidan mu, ban taɓa yin wani aljanu ba, amma ana tsorata ni sosai, kuma ina addu'a" Yazid ya ce "Dan Allah ki daina kukan nan, ni babban fatana Allah ya rabaki da cikin nan lafiya, ya kuma baki lafiya sai dai ina nan ina Addu'a duk wanda ya yi miki Allah ya mayar masa, tun da ba zai daina ba, dan Allah ki cigaba da Adduoin da na ke baki". Ya ƙarasa maganar yana share mata hawayen da ya wanke mata fuska. "Na gode sosai Zid, na san ba kowane miji ne zai iya haƙuri ya zauna da ni, da wannan ciwon ba, kayi haƙuri" "Haba Fadila, a hannuna fa larurar ta sameki dan me zan guje ki? Allah ya bamu lafiya a daina kuka dan Allah" Haka yayi ta rarrashinta yana kwantar mata da hankali, lokaci lokaci, Yana kissing ɗin goshinta yana kwantar mata da hankali, dan ita kanta tana cikin damuwa a kan wannan larura da take fama, wasu lokutan ko bata da lafiya sai ta daure ta yi shiru, saboda tausayinsa da take ji sosai. Su Khalil kuwa kwanci tashi asarar rai, suka shiga watan haihuwa, ta karɓu maternity leave ta dawo Kano Khalil duk sati biyu sai ya zo gida, wasu lokutan kuma a 'ya'yan Mama ake samun mai zuwa ta zauna da ita. Amina kuwa na ta yafi na kowa, dan wasu lokutan idan ta zauna sai Daddy ya taimaka mata ta tashi, ƙarshe sai ƙauye Daddy ya je ya ɗauko wa Amina wata tsohuwa 'yar uwar Inno aka kawo mata, take taimaka mata. Daddy kansa gaba ɗaya Kano ya dawo sa zama, saboda yanayin jikin Amina. Hafsa ta tashi da matsanancin ciwon mara, sai dai Khalil shi ya fuskanci bta da lafiya, dan miskilancin nan nata yana nan. Kwana tayi tana fama, da Asuba Khalil ya fuskanta, ya ɗauketa suka tafi Asibiti, suna zuwa Asibiti aka ce haihuwa ce. Gida Khalil ya koma ya ɗebo kayan Hafsa na haihuwa, ya kira Mama a waya ya sanar mata, ya kira Daddy ma ya ce masa gasu suna Asibiti. Ya kira Mummy ya sanar mata, amma Mummy ta ce "To ina ruwana, bance kar ka sake sakani a sabgar harkar aurenka ba? Sai ka kira talakawan iyayenta ka sanar musu". Jiki a sanyaye ya kashe wayar, ya kwashi kayan ya tafi kai wa Asibiti. Khalil ya kasa zama ya kasa tsaye, haka Mama ta zo ta samesu, Amina ma kasa nutsuwa ta yi, tana jin ance Hafsa na Asibiti ta tashi hankalinta, ta ce sai ta bi Daddy Asibiti. Sai wajen ƙarfe huɗu na yamma tun Asuba, sannan Allah ya sauki Hafsa lafiya, ta haifi sankacecen ɗa namiji mai kama da Khalil sak. Ana miƙowa Khalil jaririn cikin murna ya rungume shi, yana faɗin Alhamdilillah. Ya nufi Daddy da jaririn, Daddy ya karɓi Babyn yana faɗin "Alhamdilillah, Congratulations Khalil" Khalil baki ya ƙi rufuwa, Amina tana daga zaune ta ce "Ni ba za a bani na gan shi ba?" Khalil ya ce "Anty Amina waya isa ya hana ki jariri" Khalil ya karɓe jariri a hannun Daddy ya miƙawa Amina. Daddy ya ce "Ikon Allah, shi ne aka ƙwace ɗan daga hannuna". Khalil ya ce "Yi haƙuri Daddy" Amina ta karɓi jaririn tana faɗin "Masha Allah, wayyo Allahna beautiful baby boy Allah ya raya mana da imani, ya raya mana bisa tafarkin Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam" Amina ta dinga yi masa Addu'a. Daddy ya ce "To sai ki kawo a bawa kakarsa ma ta gan shi" Amina ta kalli Mama dake sunkuyar da kai ta ce "Mama zan baki shi, bari na gama ganinsa". Mama ta ce "Ai ba komai, naku ne" Wata Nurse ce ta fito ta ce "Zasu iya shiga su ga Hafsa". Khalil babu ko kunya ya dinga rawar kai, yana lallaɓa Hafsa yana yi mata sannu. Mama tayi waya gida, 'ya'yan mijinta suka zo da manyan kulolin Abinci, nan da nan Asibiti ya fara ɗaukar harami. Daddy ne ya kira Yazid a waya, ya sanar masa da cewa Hafsa ta haihu. Murna Yazid ya dinga yi ya ce gasu nan zuwa. Fadila na banɗaki, ta fito tana tambayarsa murnar me kake ne?". "Matar Khalil ce ta haihu" zabura tayi ta ce"Dan Allah? Kirawo mini su a waya" Yazid ya kunna wayarsa, ya kira wayar Daddy, Yazid ya ce "Daddy ga Fadila" Fadila ta karɓe wayar ta ce "Daddy ka bawa mai jegon" Daddy ya ce "Ikon Allah, ba ma da ni ake son ayi magana ba, to shikenan" Daddy ya miƙawa Hafsa waya. Hafsa ta ce 'Hello Anty Fadila". Fadila ta ce 'Ba wata Anty, shi ne kika rigani haihuwa ko? Ashe ma haihuwar ba wuya, har kin haihu" Hafsa ta yi murmushi ta ce "Hmm zaki yi bayani ne, yaushe zaku zo?". "Ai yanzn nan makuwa, sannu gamu nan zuwa, da wa yake kama jaririn ko jaririyar?" Hafsa ta ce 'Namiji ne da yake kama kuma" Fadila baki har kunne ta ce "Shikenan gamu nan" Shaf-shaf ta shirya, ta saka Yazid a gaba, suka tafi Asibiti. Ai tuni Asibiti ya ɗau harami, ya cika da mutane masu zuwa barka. Rungume Hafsa ta je tayi tana faɗin "Sannu dan Allah" Amina kuwa mamaki ne ma ya kamata, yaushe Fadila har suka daidaita da Hafsa haka, lallai ta yi hankali yanzu. Fadila ta karɓi jaririn nan tana wow Masha Allah, su Yaya Khalil an zama Father, dama nima na haihu kan mu bar Asibitin nan". Sosai ta basu dariya, saboda ba ta san ya abin yake ba, ta tashi ta kaiwa Yazid jaririn tana cewa "Zid Allah ya kawo mana namu muma kamar haka" Daddy ya ce "Wai ke wace irin mara kunya ce haka ne?" Sai kuma da Daddy yayi maganar sannan ta sunkuyar da kai ta ji kunya. Sai da magariba aka sallami Hafsa, suka ɗunguma zuwa gidansu na Kano. Da ƙyar Yazid ya ja Fadila, suka tafi gida saboda da ƙyar take yadda a ɗauki ɗan nan. Ko da Hajiya Zainab ta samu labarin haihuwar matar Khalil ta bakin Daddy, kawai sai ta ji daɗi, ta samu jika sai dai ba ta in da ta so samu ba, saboda abubuwa sun yi mata yawan da ta manta da sabgar Khalil da yi masa aure. Sai dai ba ta iya yanke hukunci ita kaɗai ba, ta kira su Hajiya Turai ta sanar musu, Hajiya Salma ta ce "To ke ina ruwanki? Ki ƙyale su su yi sabgarsu" Hajiya Turai ta ce "A'a ba a haka, jikan fari ai ko da ba kya son ta ɗanki ne fa uban yaron, dan Allah ki shirya ki je ki ga yaron jikan fari fa" Hajiya Salma ta ce "Ke Turai meye haka ne? Tayaya za ta je bayan ba ƙaunar yarinyar ta ke yi ba, ai kuwa da ajinta ya zube". Hajiya Turai ta ce "Albarkacin zuwan da zaki yi ma, wataƙila ki sake ganin Fadila, ko ki ji labarin in da take, kawai ki shirya ki je". Zuciyar Mummy ta fi karkata da ta je ɗin, dan haka ta amince zata je. Tuni Mutanen Dutse ma suka samu labari, suka dinga murna Alhaji Ahmad ya ɗau jika. Kasancewar Yazid ya gaya wa HakiyaWashegari da safe Hajiya ta shirya ta ce su tafi tare ta je ta yi barka, Fadila ta gama duk aikinta da wuri, suka tafi gidan Khalil. Hafsa kuwa da Mama sun mutunta Hajiya sosai, bayan ta yi musu barka ta tashi ta tafi gida. Yazid ma tafiya ya yi, ya bar Fadila, can Amina ma ta zo, duk da haushinta da take ji, amma tausayi take bata, ga cikin yayi ƙasa sosai, gashi har rinjyarta yake yi saboda girma. Fadila dai cikinta baya hanata harkokin ta, amma na Amina ko salla a zaune take yi. Hafsa kamar ya da ƙanwa ita da Fadila, Fadila kamar ita ce uwar ɗan, sai hada-hada ake yi. Da yamma Yazid ya zo zai tafi da Fadila, Khalil ya ce sai Yazid ya shigo ya sake ganin jariri kuma ya ci Abinci. Suka haɗu a falo suna ta surutu, dan Mama bar musu falon ta yi, Amina tana gefe sai ana hira sai su Fadila su sauya yare zuwa larabci. Khalil ya ce 'Nifa bana son haka, wannan wane irin abune ana magana ku wani dinga sauya yare, Anty Amina ce kawai take jin me kuke cewa, madam ko ke kina ji?" Yayi Maganar yana kallon Hafsa. Ta ce "A'a duk kanwar ja ce, ɗan larabcin nawa na ƙawa'idi ne kawai" Dariya suke yi sosai, kawai suka ga Mummy tare da Hajiya Turai a tsakiyar falon. Sai da Hafsa ta zabura da ganin Mummy, haka Fadila ma. Idonta ne ya sauka a kan Fadila dake jingine da jikin Yazid. Ayshercool 08181012143https://youtube.com/@CoolhausaNovels Subscribe my YouTube channel, to get the latest hausa Novels. 86 Sarai ta gane Yazid, amma sai kanta ya kulle ta ce "Fadila, waye wannan?" Cikin girmamawa Yazid ya risuna yana cewa "Mummy ina wuni" Bata amsa masa ba sai cigaba da tambaya da tayi. Khalil ya aro jarumta ya ce "Mummy, dan Allah ki kwantar da hankalinki, bari na yi miki bayani, ba wani abin tayar da hankali bane ba, amma ki fara zama ki ga jikan naki" "Kai dalla rufe mini baki, sai zuba kake kamar jefaffe, tambayarku nake waye shi?" "Mummy mijina ne, Yazid kenan shi Daddy ya aura mini" Fadila ta bata amsa. Hajiya Zainab ta riƙe ƙugu ta ce "Turƙashi, dama a kan wannan ɗin kika watsa mini ƙasa a ido? Wannan abun shi ne mijin naki? Lallai Ahmad ya shirya tozartani" Hajiya Turai ta ce "Taɓ, da wannan ba gara Salim ɗan gidan Hajiya Salma ba, yaro da kuɗinsa da mutuncinsa, dan Allah kalli meye abin son a wannan? Kalli rigar wuyansa ba dan a wanke take ba ai baifi ka yi duster da ita ba, to ban ƙi ba ko wannan hasken da gemun take yiwa amma wannan dai ba sa'an aurenki bane ba Fadila, har da miƙewa ki ƙunshi ciki" Rai a ɓace Fadila ta ce "Ba ruwanki da mijina kar ki sake zagar mini shi, ni ina son sa a haka" tayi maganar cikin tsiwa. Buɗe baki Hajiha Turai ta yi ta ce "Fadila ni kike gayawa haka?" Fadila ta buɗe baki za ta yi magana Hajiya Zainab ta ce "Idan kika kuskura kika kuma faɗar wata Magana ta rashin kumya sai na ɓarar da ke, wawuya mara wayo me wanan ya ci balle ya baki, kalleshi a gajiye" Khalil ya rasa bakin magana, saboda gaba ɗaya sun riga sun gama cin mutuncin Yazid. Amina da ke gefe da uban cikinta ta ce "Wallahi idan ki ka cigaba da biyewa ƙawaye, sai sun saka yaranki sun tsaneki, Mutanen nan hassada kawai suke yi miki. Banda abin kunya sirikinki ne fa ya zaki tsaya kina gaya masa wannan maganganun ba kya tunanin nan gaba a zo aji kunya" "Ke kuma wa ya kasa dake 'yar hau, 'yar bani na iya ai duk wani munafunci ke kike kitsa shi, kin tsallake tsiya da talauci kin zo kin aure mata miji kina zuba mulki kin kassara mata gida". Amina ta ce "Au har da su kaza a cin danƙo, ke kuma a wa kare da gudun layya? Ai mace sai ta kai take iya shimfiɗa mulki a gidan mijinta, faɗi ki ƙara ni na saka aka yi wannan aure, kuma Allahn da ya haɗa shi ka raba shi, idan kuma ba aje makaranta ba sai a cigaba da jayayya da ikon Allah". "Zaki rufe mini baki ko saina ɓarar da ke banza" Hajiya Zainab tayi maganar kamar zata kaiwa Amina duka. "To ɓarar da ni mana, tijarar mai gidan ma ta isheki, kece duk abin da ki ka yi abin kunya ne a gareki, duk sirikanki ne a nan da nake alfahari da su, kuma Alhaji Ahmad yake alfahari da su, amma lokaci yayi da zaki gane cewa wannan ƙawayen naki cutar ki kawai suke yi". Hajiya Turai ta ce"Kinga bar wannan mahaukaciyar, ki kamo wannan mara wayon mu tafi gida" Khalil sai basu haƙuri yake yi, amma Hajiya Turai na ta zigata tana sake zubar da mutuncinta a gaban sirikai. Ta kalli Fadila ta ce "Zaki taso mu bar gidan nan ko kuwa?" Fadila ta riƙe hannun Yazid ta ce "Dan Allah Mummy ki ƙyalemu, ina son sa wallahi" "Ni ki ke gayawa kina sonsa, talakan Fadila? babu shakka ubanki ya jiƙa wata tsiyar ya baki kin sha, zaki taso ko saina zo? Aini gara da Allah ya sa na zo ɗin na bi shawarar ki Turai" Kuka Fadila ta fashe da shi ta ce 'Mummy ba juya miki baya zan yi ba, amma a halin da nake ciki ba zaki iya kulawa da ni ba, dan Allah Mummy ki yi haƙuri maraya ne ina son mijina" Khalil ya ce "Dan Allah Mummy ki yi haƙuri ki ƙylesu, kalli yadda take kuka kuma wallahi Yazid mutumin kirki ne" Mummy ta ce "Ka auri 'yar gidan babu shi ne kake so itama sai ta haɗa zuriya da talaka ko?" Mama da tun ɗazu take jin abin d ake faruwa ba ta ce komai ba, Fadila ta bata tausayi da Yazid, yadda Fadila ke ta kuka tana rirriƙe Yazid, shi kuma yayi shiru ga cin mutuncinsa da aka yi. Mama ta ce "Dan Allah Hajiya kiyi haƙuri, shi ɗan yau ba ayi masa haka, ka samu mai riƙe maka ɗan ma wani ni'imar ne, dan Allah ki daina wannan maganganun a gaban sirikanki". Hajiya Turai ta yi farat ta ce "Ke kuma waya kasa da ke, ita kuma wacece wannan?" Khalil ya nuna Hajiya Turai ya ce "Sirikata ce, kuma ki kiyayi harshenki kar ki sake ki zageta uwace a wurina" "Khalil Turan kake gaya wa haka?" Yazid ne ya ɗago da sauri, yana nanata sunan Turai. Khalil ya ce "Mummy wallahi gaskiya Anty Amina take gaya miki, mutanen nan ba ƙaunarki suke yi ba, hassada suke yi miki" "Ni kake kalli kake gaya wa haka Khalil?". Amina ta gyaɗa kai ta ce "Hmm a dai juri zuwa rafi, wannan yaran da kike taƙama da su, sai wannan matan sun saka sun tsaneki" Yazid ya miƙe tsaye jiki a sanyaye, zai bar falon. Mummy ta ce "Kai tsaya, ka bani takardar sakin 'ya ta, dan ba zata cigaba da rayuwa da kai ba". Khalil ya ce "A'a Mummy, dan Allah kiyi haƙuri kar ki yi haka" Fadila kuwa ta rirriƙe hannun Yazid ta ce "A'a dan Allah Zid kar ka sakeni, ina sonka dan Allah Mummy ni ki ƙyaleni zan iya zama da shi". "Ni kike gayawa haka Fadila? Kin zaɓi wannan matsiyacin a kaina". "Mummy ba haka ne ba, muna son juna tun a makaranta, dan Allah ki ƙyalemu wallahi ina son sa" "Fadila ni zaki watsawa ƙasa a ido ko? To muddin kika zaɓe shi babu ni babu ke". Gwanin ban tausayi Fadila ta ce "Wallahi Mummy ina sonki, amma ina son mijina ma, Zid dan Allah ka gaya mata ina sonka dan Allah kayi haƙuri kar ka sakeni". Turai ta ce "Wallahi sai ya sake ki, shashasha mara tunani, kai da ganin wannan ka ga wahalalle" ta yi maganar tare da fizge hannun Fadila daga na Yazid. Yazid da yake ta sunkuyar da kai, ransa ba daɗi ya ɗago idonsa, ya kalli Hajiya Turai ko ƙiftawa ba ya yi. Take ta ji jikinta ya hau tsuma, kamar zata fita daga hayyacinta ta kasa gane a wane yanayi take. Ya miƙawa Fadila hannu, ta fizge hannunta daga na Turai ta riƙe na Yazid. Yazid ya kalli Hajiya Turai ya ce "Baki da hurumin da zaki cigaba da zagina, idan ita Mummy ta yi ta isa ne, sannan ina son sanar da ke cewa saƙonku ke da Hajiya Salma yana isowa gareni, kuma reshe na daf da juyewa kan mujiya, abin da kike ji ɗin nan a yanzu ka iya kawo ƙarshen abin da kuke aikatawa daga ke har ita, zaɓi ya rage naku ko ku janye ku nemi afuwar wadda kuke cutarwa, ko kuma ƙarshen abun yayi muni. Sannan Ina son Fadila bani na nemi aurenta ba, Daddy ne ya aureta ya kuma bani amanarta. Idan har ya dawo ya ce na bashi amanrsa zan dawo masa da ita, amma for now dan Allah kiyi haƙuri Mummy" Ya juya zai fice, Fadila ta ƙara riƙe hannunsa gam, suka yi waje, har da ɗan gudunta. Amina da ke gefe ta ce "An dai ji kunya wallahi, su Balama an yi asarar kunnuwa, baku da aiki sai sintirin gidan Mutane kuna zigata a kan abin da ku ba haka kuke aikatawa a naku gidajen ba, ta ƙarasa maganar tana tashi tsaye da ƙyar. Hajiya Turai kuwa jikinta sai rawa yake yi, gaba ɗaya ta kasa nutsuwa, ji take yi tamkar zata haukace ko ta bar duniyar. Da ƙyar Amina take takawa ta bar falon, ta fice daga gidan gaba ɗaya, ta je ta samu abin hawa ta hau dan ta koma gida, ba zata iya jiran Daddy ba, saboda abin Kunyar da Hajiya Zainab ta aikata yayi yawa, abin da Kunya. Hajiya Zainab kuwa a saɓule ta bar gidan, ba tare da ta iya cewa komai ba, ko a mafarki ba ta yi zaton Fadila zata aikata abin da ta yi mata ba a yanzu, ta kunyata a gaban Mutane. Daddy cikin mamaki yake tambayar Amina dan me zata hau napep a wannan halin da take ciki, tafiya da ƙyar. A ɗan hasale Amina ta ce "Ba dole na dawo ba, matarka ta je tana abin kunya a gaban sirikai da mutanen gida, wallahi Zainaba ba zata taɓa hankali ba, zuwa ta yi gidan Khalil ta tarar da Fadila da mijinta, ka ga cin mutuncin da suka yiwa Yazid ita da ƙawarta Turai take ko Afrika? Suka ci mutuncin bawan Allah nan suna ce masa matsiyaci, cin mutuncin bai tsaya a kansu ba har da mahaifiyar mai jego, wace irin rayuwa ce haka?" Daddy yana matuƙar jin Yazid a ransa, yana ganinsa tamkar ɗansa, nan da nan ransa ya ɓaci, hankalinsa ya tashi ya fice fuuuuu. Amina ta taka ta bi bayansa tana kiran sunansa. A falo ya tarar da Hajiya Zainab tana zaune rai a ɓace, Hajiya Turai na yi mata magana. "Uban wa kika tambaya kika je gidan Khalil, har kika ciwa mijin 'yar ki mutunci?". Hajiya Zainab ta kalli Amina da ke bayan Alhaji Ahmad a tsaye ta ce "To jikar munafukai, har kin zo kin sanar masa kenan, to na je ɗin kuma na yi ɗin, kuma wallahi Fadila ba zata cigaba da zama da wannan matsiyacin ba". "Kafin ta kaimu ga haka, Zainab na sake ki, saki ɗaya ki bar mini gida, tun da ni nake aureki ba ke kike aurena ba" Ba Hajiya Zainab ba hatta Turai sai da ta yi turus, basu taɓa kawo Alhaji Ahmad zai aikata haka ba. Hajiya Zainab ta ce "Ai na ci dubu sai ceto Ahmad, yau ka tabattar mini da cewa ka riƙa, dan haka na ji na gode amma wallahi ba zan bar gidan nan ba, sai dai kai ka fita". Daddy zai yi Magana Amina ta riƙe hannunsa tana girgiza masa kai ta ce "Dan girman Allah kar ka sake magana, sheɗan ne yake sake zigaka kr ka kuma furta komai, yi haƙuri" Amina tayi gaskiya, dan a yadda ya ke ji zai iya cikasa mata saki biyun. A matuƙar fusace Daddy ya bar falon, Amina ta kalli Hajiya Zainab ta ce "Ai dama ƙarshen alewa ƙasa, dama auren na ki suke yiwa baƙin ciki, kinga biyu babu ba miji ba 'ya'ya duk sun zama nawa, yanzu dai kin ga abin da 'yar ƙauye Jahila 'yar talakawa ka iya yi ai dama ita GABA DA GABNTA, kuma Allah ba yadda bai iya ba, abin da kike gudu gashi nan ya baibaye ki. Yanzu ya rage naki, ko dai ki nutsu ki koma ga Allah ko kuma yanzu ki ka fara gani". Hajiya Turai ta ce "Dalla saurara waye ya saka da ke, kin kashe mata aure kin ji daɗi, ki bi bokaye kin mallake miji kin saka ya saketa" Amina ta yi murmushi ta ce "Ai tun kan na fara bin boka take yi, kin san shi ma asirin iyawa ne, wani ya daɗe yana yi amma bai ci ba" Hajiya Zainab da ta yi shiru, zuciyarta na bugawa cike da fargaba. Yazid kuwa har suka je gida Fadila tana kuka, Yazid kuwa ya kasa magana, saboda zuciyarsa babu daɗi sam. Ko da suka je gidan ma, Yazid bai ce wa Fadila komai ba, hakan ya ƙara jefa Fadila a damuwa, dan sosai ta ga damuwa a fuskar Yazid. Jiki a sanyaye ta dafa shi ta ce "Zid, dan Allah ka yi haƙuri da abin da ya faru, haka Mummy take a baya na biye mata, yanzu kuma na gane kuskurenmu, amma dan Allah ka yi haƙuri ita ma zata gane". Yazid ya ce "Kar ki damu Fadila, ni ba yau na saba gamuwa da irin wannan ƙalubalen ba, duk abin da za ayi mini barin abin da aka yi mini ne a gidanmu, ni wannan Hajiya Turai ɗin ce ta tsaye minin a rai". Fadila ta ce "Yauwa a ina ka san su ne?" Yazid ya numfasa ya ce "Kar ki damu da wannan, amma da gaske sune ƙawayen Mummy?" Fadila ta ce "Eh, ƙawayenta ne, nima tashi na yi na gansu tare" Yayi ajiyar zuciya ya ce "Da ta san illarsu a gareta da cutarwar da suke yi mata, data rabu da su tuntuni amma shi ramin ƙarya ai ƙurarrene, kamar yadda Amina ta faɗa, Hassada suke yi mata". Fadila ta Kwantar da kanta a jikin Yazid ta ce "Nima da ta faɗi hakan na yi wannan tunanin, ita fa Hajiya Salman nan ita ce da aka ce da zan auri ɗanta, aka fasa na ce bana so Daddy ya Aura mini kai, su yi ta saka Mummy tana basu kuɗi, kuma ta na yiwa Daddy rashin kunya". Yazid ya dakatar da Fadila, ya sauya zancen da wani. Ita Hajiya Zainab sai abun ya zame mata goma da ashirin, dan wani irin matsanancin ciwon baya da na ciki take fama da shi, amma ta kasa mayar da hankali a kan ciwonta sai a kan yadda zata fanshe tozarcin da Alhaji Ahmad yayi mata. Ranar suna aka sha shagalin sunan jairiryar su Khalil, aka saka mata sunan mahaifiyar Hafsat. 'yan Dutse suma sun je suna sosai, an ci an sha an yi buduri sosai, kuma Hafsa sun samu abin arziƙi sosai kama daga kuɗi zuwa ga sutura. Hajiya Zainab ta girgiza da abin da Daddy ya aikata mata na sakin nan, ta rasa in da zata saka kanta, Hajiya Salma sai zigata take tan cewa ai ba kanki farau ba, kar ki damu amma zai gane kuskurensa. Amina kuwa bin Daddy take tana roƙonsa a kan ya taimaka ya mayar da Mummy amma yayi burus. Sai da ƙyar dan sai da tayi fushi ta daina kula shi, sannan ya mayar da Hajiya Zainab. Yazid ya dage iya ƙoƙarinsa, ya buɗe inshoran lafiya, saboda haihuwar Fadila, da ya samu 'yan kuɗi, sai ya ɗauketa su je su ɗan sayo kayan jarirai. Fadila kwana Biyar da shigar cikinta watanni tara, ta ji cikinta na ciwo kaɗan kaɗa , ta yi wanka ta shirya ta ce wa Yazid "Zid ina ga fa haihuwa zan yi, ta shi muje Asibiti na haihu" Yazid ya kalleta ya ce "A haka zaki haihun?" "Ni dai ka tashi, kar na haihu a wurin nan, a Asibiti ance da mun ji ciwo muje Asibiti" Yazid ya tashi ya ɗau akwatin da suka haɗa na kayan jarirai, Fadila ta ce suje su kira Hajiya, amma ya ce "A'a su je tukuna su ji me za ace a Asibitin". Haka suka tafi Fadila na ta zuba hira a napep, suka je Asibiti Fadila ta faɗi abin da yake damunta. Nurse ɗin ta kalli Fadila ta ce "Lallai kam" Da za su je A dubata har da kallon Yazid ta ce "Kar fa ka yi nisa, yanzun nan zan haihu na fito" shi dai Yazid duk da bai san yadda ake haihuwa ba, amma ana faɗar da wahala amma Fadila dumur da ita tana cewa haihuwa za ta yi. Aka shiga labor room aka ce ta hau gadon ta kwanta a dubata, ta hau ta kwanta da uban dogon wandonta a jikinta. Nurse ta kalleta ta ce "A haka zaki haihun? Malama sai kin cire wannan wandon" Fadila ta waro ido ta ce "Kai wando kuma? ta ina zan haihun?". "Ta in da cikin ya shiga" ta bata amsa tana haɗe rai. Fadila ta ce "Kinga kar ki raina mini Hankali mana, bance ki zageni ba, nifa sai in fasa haihuwar nan a nan in koma gida". Nurse ta cire safa ta ce "Ba haihuwa zaki yi ba". Nurse ɗin ta je ta samu Yaizd ta ce "Wannan Yarinyar ba haihuwa za ta yi ba, idan ta fara naƙudar ta dawo" Kan yayi magana sai ga Fadila ta fito tana tura baki. Yazid ya ce "Habibty, ya aka yi ne?" Fadila ta kalleshi ta ce "Ni zata gayawa baƙar magana daga tambayarta, ni kuwa na ce na fasa haihuwar a nan, a gida zan haihu" Yazid ya ce "Anya Fadila, ki tsaya su yi miki abin da ya dace". "Ba zan zauna ba gaskiya, mu tafi gida kawai" Yazid ya ƙyaleta suka koma gida, suka koma ta danƙari Abincinta, ta sha tofin da Yazid yake yi mata, ta yi kwanciyarta ta hau bacci. Bayan azahar Fadila ta tashi, ta ji mararta na ciwo har ƙafafuwan ta, ta dake ta yi salla, ta cigaba aiki, abu kamar wasa tana jurewa, abu har ya gagara, Yazid ya dawo daga makarantar dare, ya tarar da ita da ƙyar take iya magana. Shi ya zata ma mutanen ne zasu tayara mata, ya zauna yana yi mata Addu'oi. Cikin numfarfashi ta ce "Zid ka kaini Asibiti, zan mutu" a gigice ya fita neman abin hawa ya rasa, ya tafi gidan Hajiya ya sanar mata. Hajiya ta je ta ƙwanƙwasawa wani maƙocinsu ƙofa, ya ɗauko mota aka saka Fadila da kayanta, zuwa Asibiti. A wannan karon Fadila babu gardama, abin da aka ce ta yi shi take yi, duk da haihuwar da saura, amma suka ce a bata gado Yazid ya riƙeta su yi ta zagayawa. Hajiya ta koma gida, ta dafo ruwan zafi ta dawo Asibiti. Suna zagaye idan ciwo ya lafa tayi ta surutu, idan ciwo ya tashi sai bakinta ya mutu. Wasa-wasa tafiyarma ta gagari Fadila, sai kuka da take yi. Hajiya ta ce "Kiyi haƙuri Fadila addu'a ake yi, ba kuka ba". Fadila ta ce "Hajiya baki san me nake ji ba" Hajiya ta ce "Ki yi haƙuri to, yi ta Addu'a". Tafiya ta gagari Fadila, aka shiga da ita labor room, sai dai laborn nata kamar ana jansa, sauri yake sosai kamar ba haihuwar fari ba. Ta ce a kira mata Yazid, Nurse ɗin ta ce maza ba sa shigowa, aikuwa ta dinga kurma ihu tana ƙwala masa kira. Ba shiri Nurse ɗin ta kirawo shi, kasancewar ita kaɗai ce ke laborn a labor room ɗin. Yazid ya zo kanta ya tallafota yana yi mata sannu, tare da yi mata Addu'oi. Can mai karɓar haihuwar ta cewa Yazid "Kaga rabu da ita, zaka iya zuwa waje ka jiramu, ta kusa haihuwa in sha Allah". Yazid ya ce to,ya tashi zai fita, ta sake fashewa da kuka tana kiransa. Ya tsaya cak ya waiwayo yana kallonta cikin tausayawa. "Dan Allah kar ka tafi, ka dawo ka cigaba da yi mini Addu'a" Nurse ta ce "Dan Allah ki bar shi ya je ya huta, ga dare kiyi haƙuri mana ki daure". "Wai ke ina ruwanki da ni ne? Kina ina lokacin da na samu cikin, was he not behind all this am going through?" Yazid ya buɗe baki, ga kunya ta ishe shi, bakinta ya ƙi mutuwa. Nurse ta yi murmushi ta ce "Haka ne da gaskiyarki, Allah ya taimaka". Yazid ya kuma tallafota yana mata sannu, ta tureshi ta ce ya fita ya bata wuri, ba ta son ganinsa ma. Da taga kuma zai fita sai ta saka kuka "Zid tafiya zaka yi ka barni, baka tausaya mini ko? Dan Allah ka yi haƙuri zo ka tsaya ta nan ka cigaba da yi mini Addu'a" Mirsisi Fadila ta hana Yazid fita, ta na kuka yana kuka saboda tausayi a haka ta haihu. "Alhamdilillah barka da arziƙi, gaskiya laborn nan yayi sauri, haihuwar fari?" Fadila ta ce "Duk uwar wannan wahalar da na sha?" "Eh mana" matar ta faɗa tana dariya. Jaririya ce jawur da ita, 4kg Yazid sai Alhamis yake jerawa yana yiwa Fadila sannu. Aka gyara jaririyar aka bashi, ya ruƙunƙumeta yana yi mata Addu'a, ya fito da ita. Nurse ta kalli Fadila ta ce "Ke na ce mijinki ya fita, amma kika hana shi, baki san wasu idan suka ga wannan ƙazantar haihuwar suna ƙyamar matan su ba?" Fadila ta ce "Mijina ba irin saura bane ba" Hajiya kuwa harda hawayen ta na farinciki ita ma. Kasancewar cikin dare Fadila ta haihu, Yazid ya turawa Daddy message kawai. Daddy ya tashi sallar Asuba, ya ga message ɗin, yana gaya wa Amina ta dinga murna, kamar ita ce ta haihu. Nan da nan Amina ta saka aka ɗora ruwa, tana ta shiri. Daddy ya ce "Madam ba fa in da zaki je, kina tashin nan da ƙyar ki zauna da ƙyar". "Dan Allah Daddy Kar mu yi haka da kai, ka barni na je dan Allah". Yayi murmushi ya ce "Shikenan, shirya mu je uwar iyali" murmushi ta yi ta shiga wanka. Hafsa kuwa suna samun labarin haihuwar ta kira Yazid. "Ɗan ustazunta, dan na rigata haihuwa shi ne ta tsokano haihuwa ita ma, to ai shikenan sai mun zo" Fadila tana gefen Yazid tana karyawa, sai murmushi ta ke, kasancewar tana jin su. Daddy ne suka yi sallama a ɗakin, Amina na janyo ƙafa da ƙyar suka shigo. Kallon Amina ta yi da tausayawa, wannan cikin nata kamar zai rinjayeta ta faɗi. Amina ta zauna da ƙyar, sai sannu ake yi mata. Yazid ya ce "Sannu Antynmu, a haka kika fito?" Daddy ya ƙarasa ya rungume Fadila yana faɗin "Congratulations sweetheart" "Thank you Daddy" "Hajiya miƙo wa Daddy Innata ya ganta" Yazid ya ce "Ke ba kya kara ne?" Murmushi suka yi, aka miƙawa Daddy jaririyar. Daddy ya shafa kan jaririyar, yana yi mata Addu'a, yarinyarsu kyakykyawar gaske. Amina ta ce "Daddy baka bani ita ba" Daddy ya ce "To gata" ya miƙa mata jaririyar. Amina ta ce "Masha Allah, an haifa mana balarabiya" tayi maganar tana juya 'yar jairiryar da ke ta bacci. Suka yi murmushi, Fadila ta yi ƙasa da murya ta ce "Daddy, ka gaya wa Mummy na haihu ne?" Daddy ya ce "Eh na gaya mata kan mu fito". "To za ta zo?" Daddy ya ce "Fadila, ku yiwa mahaifiyarku Addu'a kawai, ta yi nisa ba ta jin kira, ta ce ba zata zo ba, tun da kin zaɓi mijinki, amma dan Allah kar ki ɗaga hankalinki, kiyi haƙuri na san ni kike yiwa biyayya, to ba zaki taɓe ba in sha Allah". Fadila ta Kwantar da kanta a kan kafaɗar Daddy, ta ce "Daddy yanzu za a sallame ni, daga nan zamu tafi gida ku tayani neman afuwar Mummy, haihuwa babu sauƙi Daddy, bai kamata na yiwa Mummy haka ba, amma kai ma dole ne na yi maka biyayya, kuma aurena yana da muhimmanci, mu je ku tayani bata haƙuri, sannan akwai wani abu da nake son ta sani" Daddy ya yi ajiyar zuciya ya ce "Shikenan, amma ki daina kuka" Ta jinjina masa kai alamar to. Likita ya zo ya duba Fadila, ya rubuta mata sallama, da yadda zata kula da ɗinkin da aka yi mata. Gaba ɗaya suka tafi gida, su Khalil ma can gidan suka bisu. Suka tarar da Hajiya Zainab ta kame a falo, tana hura hanci, Fadila ta nufi in da Mummy ta ke zaune. Hajiya Zainab ta tsuke fuska sosai, ta kawar da kanta gefe. Ayshercool 08081012143LITTAFIN KUƊI NE, MAI BUƘATA YANA IYA TUNTUƁATA A KAN LAMBAR WAYATA. 08081012143 https://youtube.com/@CoolhausaNovels 87 "Mummy ina kwana?" Fadila ta faɗa a sanyaye. "Lafiya lau" ta amsa mata a taƙaice, Amina ta ja Hajiyar Yazid zuwa sashinta, gudun kar ayi abin kunya a gabanta, dan babu uwar da zata ji daɗin a wulaƙanta mata ɗa a gabanta. Yazid ma ya ƙarasa gaban Mummy ya durƙusa a gabanta, ya ce "Mummy ina kwana". Kallon Yazid ta yi ta watsar, ta cigaba da kallon Tv. Daddy ne ya shigo rungume da jaririyar su Yazid a hannunsa, ya shigo, ya tarar da su Yazid a gabanta, Fadila tana kuka. Daddy ya ƙarasa ya kamo hannun Fadila, ya miƙar da ita ya kalli Yazid ya ce "Malam Yazid, ta so mana" jiki a sanyaye Yazid ya tashi, Daddy ya janye 'ya'yansa ya wuce da su sashin Amina. Miƙewa Hajiya Zainab tayi ta bi bayansu da kallo, wasu irin hawaye ne suka zubo mata daga idonta, kenan da gaske Amina ta ƙwace mata miji da 'ya'ya. Ɗakinta ta nufa, jikinta a sanyaye, ta dafa kanta ta furta "Na shiga uku, komai sai sake kwaɓe mini yake yi". Tana son ganin abin da Khalil ya haifa, ga na Fadila kuma, babban abin da ya sake jefata a ɓacin rai, butulcin da Fadila ta yi mata, ta zaɓi wannan talakan yaron a kanta. Wai yanzu Fadila ce ta haihu da wannan talakan, Innalillahi wa innalillahi raji'un. Ta dafe kanta da yake mata tsananin ciwo, ta zauna tana ajiyar zuciya. A sashin Amina kuwa, ta saka 'yan aiki sai sauke musu kaɓakin alkhairi ake yi na Abinci, aka yi ta kiran 'yan uwa da dangi ana sanar musu da haihuwa. Fadila dai duk jikinta babu daɗi, saboda rashin samun karɓuwa a wurin mahaifiyarta. Su Khalil ma suka ƙaraso gidan, suka tare a sashen Amina, sai hada-hada ake. Yazid da Hajiya suka yi musu sallama a kan zasu je su dawo. Fadila sai kallon Amina take, sai ƙoƙarin kyautatawa kowa take yi, yanda ta ke karrama Hajiyar Yazid kamar mahaifiyarta. Hajara ma sai ɗorawa take tana saukewa, ana bawa wanda suka zo barka Abinci. Da yawa maƙota sai a yanzu suka san an yiwa Fadila aure, su dai sun daina ganinta kawai. Amina ta yi ta aikawa ana sanar da mutane haihuwar Fadila. Da magariba sai ga Yusra a gidan, da Hajara ta haɗu a hanyar shiga main falon, ta kalli Hajara ta ce "Wai da gaske Fadila ta haihu Hajara?". Hajara ta ce "Eh, tana sashin Amina". Yusra ta ce "Amina kuma?" Da sauri ta shiga cikin gidan. Saboda rabonta da Fadila watanni tara kenan ko a waya. Fadila na ganin Yusra, suka saka ihu suka rungume juna, har da hawayensu na farinciki. Yusra ta ce "Girl, dama da gaske auren aka yi miki? Mummy ta gaya mini amma na yi mamaki". Fadila ta ce "Ke dai bari, nan da mutane sosai, zo mu je ɗakina" Yusra ta ce "Ina abin da kika haifa ɗin?" Fadila ta ce "Zo muje, kya dawo ki ganta daga baya". Suka wuce ɗakin Fadila, suka nemi wuri suka zauna. Yusra ta ce "Girl auren nan ya karɓeki, kinga yadda ki ka yi ƙiba kuwa? Amma ban so aurenki ya zo mana a haka ba, bani labari ya aka yi abubuwa suka zo a haka?" Hawaye ne ya gangaro da ga idon Fadila, ta gyara zamanta da ƙyar, ta bawa Yusra labarin komai har zuwa yanzu. Yusra ta waro ido ta ce "You mean Yazid Daddy ya aura miki? Ya aka yi ya san shi?". "Amina ce ta saka ya aura mini shi, Yusra ina son Yazid sosai, faɗar irin alkhairinsa gareni ba zai faɗu ba, haihuwar nan tawa fa, leshin suna kawai na dubu Ashirin ya saya mini, 'yar nan da na haifa, baki ga kayan da ya saya mata ba, Yazid yana wahalta mini duk da ba shi da shi" Yusra cikin mamaki ta gyara zama ta ce 'You mean Yazid dai shi ne mijinki Fadila?" Fadila ta jinjina mata kai ta ce "Yazid ne mijina". "Amma Fadila mun sha haɗuwa da Yazid, amma bai taɓa gaya mini kuna tare ba". Fadila ta yi murmushi ta ce 'Ni na hana shi ya gaya miki, saboda Daddy ya ce kar mu sake wani ya san shi ne mijina, saboda kar Mummy ta sani, Yusra ina son mijina, amna Mummy ta ƙi karɓata ya juya mini baya". Sosai Fadila ta ke kuka, Yusra tayi ta rarrashinta, Yusra ta dubi Fadila ta ce "Fadila na yi miki murnar auren Yazid, mutum ne nagartacce, mai kirki, Allah dai ya ƙaddara sai kun yi aure". "Haka ne, ina laulayin cikin nan har wurinki na aiko shi, ya sai mini cake kika bamu kyauta" Yusra ta ce "Allah sarki, ya ƙi gaya mini kuna tare, na sha kuka sosai rashinki bestyna". Fadila ta dafata ta ce "Matar Abdul, yaushe ne bikin?" Jiki a ɗan sanyaye Yusra ta ce "Wallahi tun muna tare nake jin nauyin sanar miki Abdul zan aura Fadila, saura sati biyu bikinmu". Fadila ta ce "Kar ki damu Yusra, ai kin san ni ba son Abdul nake ba, amma na tayaki murna, dan halayensu na yanayi da na Yazid, Allah ya kaimu lokacin". "Amin Fadila, wai abin har ya kai sai dai kiyi jegon a sashin Amina?" Fadila ta rausayar da kai ta ce "Gashi kina gani, ko abin da na haifa ba ta gani ba, Yusra na yadda da zancen Amina, wallahi su Hajiya Turai suna ziga Mummy ne kawai suna cutarta" Yusra ta ce "Kin san na daɗe da fuskantar hakan, magana me kawai ban yi ba dan kar ki ji haushi, wallahi Fadila yakamata ki ajiye duk wani kishi da tashin hankali, ki saka a ranki auren Daddy da Amina ta yi, Allah ya riga ya rubuta hakan, amma wallahi mai ƙaunarku ce, kuma abubuwanta ba ganin ido bane ba, kalli halin da take ciki, amma sai ɗawainiya ta ke yi da ke, dan Allah ki daina gaba da ita" Fadila ta ɗan murza zoben hannunta ta ce "Nima na yi wannan tunanin, ba dan su Hajiya Turai ba da wasu abubuwan basu faru ba. Yusra a baya Jahilci ne yayi mini katutu na ƙarancim ilimin addini, zamana da Yazid ya sanya na gano abubuwa da yawa. Yusra baki ji labarin Yazid ba abin tausayi, amma nima na zo na dinga muzguna masa a makaranta, ba tare da tunanin ya zai ji a ransa ba. Matar Yaya Khalil, ita ma baki ji nata labarin ba, amma ita ma muka sakata a gaba da wulaƙanci ina dana sani sosai a kan wasu abubuwan" Yusra ta sharewa Fadila hawaye ta ce "Kiyi haƙuri, ai Allah mai afuwa ne, mu cigaba da yi wa Mummy Addu'a kawai" Haka suka yi ta hira, sannan suka koma sashin Amina, Yusra ta ga jaririyar su Fadila. Sai dai Fadila ta roƙi Yusra a kan kar ta gaya wa kowa a makarantar cewar ta auri Yazid. Sosai mutane suka cika gidan Alhaji Ahmad, mutanen Dutse 'yan garin su Amina, duk suka cika gidan. Sai dai duk wannan budurin, Hajiya Zainab bata ko fitowa, balle ta ga me Fadila ta haifa, hakan ya sake jefa Fadila cikin tsananin damuwa, tana farinciki idan ta ga mutanen da suka taru dominta, amma ta rasa kulawar mahaifiya, a kan abin da bai taka kara ya karya ba. Hajiya Zainab, bayan damuwar da take ciki, ciwo sai gaba yake yi, da ƙyar take iya fitsari, ga ciwon ciki da na baya. Tun da Inno ta zo, ita ke yiwa jaririyar nan wanka, ta haɗa wa Fadila ruwan wankan jego, tamkar jikarta haka take kula da ita, hakan ya sanya jikin Fadila ya yi sanyi, da irin rashin mutuncin da ta ke yiwa Amina, duba da yadda mahaifiyar Amina ke ta mutunta ta da son 'yar ta. Ga shi Hajiyar Yazid kullum idan zata zo, sai ta zo da Abinci fal nama, ta kawo wa Fadila, duk da ta san gidansu akwai. Idan Amina ta yi magana, sai Hajiya ta ce "Ƙyaleta kuɗin mijinta ne". Ranar suna ana ta shiri, Daddy ya kama musu babban hall da za ayi taron suna. Kuma Yazid daidai gwargwado yayi ƙoƙari, iya ƙarfinsa. Amina ce ta ga Fadila ta ɓuya tana kuka, babu komai a ran Amina ta dafa Fadila ta ce "Fadila kukan me kike yi?" Fadila ta girgiza kai ta ce "Ba komai". Amina ta ce "Na san ba zai wuce a kan abin da yake tsakaninki da mahaifiyarki ba, amma kiyi haƙuri mai wucewa ne, duk tsananin fushin da ta yi zata huce. Ki cigaba da yi mata Addu'a" Cikin kuka Fadila ta ce "Cewa fa ta yi babu ni babu ita". "Faɗa kawai take yi, amma zata sakko, ai tsakanin ɗa da uwa sai Allah" Khalil ma yayi yinƙurin zuwa ya samu Mummy, a kan ta yi haƙuri ta sassauta fushin da take yi da su. Amma ta ci mutuncinsa ta koreshi. Ranar suna an ci an sha, aka sakawa yarinyar suna Khadija ana kiranta Hidaya, sai dai zancen duniya ba ya ɓuya, da yawa mutane sun samu labarin rashin saurarar 'ya'yanta da Hajiya Zainab ta yi saboda sun auri talaka, hakan ya sanya fa yawa mutane suka dinga Allah wadai da halinta ciki har da 'yan uwanta da suka zo suna. Bayan suna jama'a suka watse, sai Fadila da Amina, da Dattijuwar da take yi mata wanka. Amina tana daga zaune, har wanka take yiwa Hidaya. Hajiya Zainab na zaune, a babban falo, jikinta babu daɗi su Hajiya Turai sun zo dubata, sai ga Fadila ta fito ita da Yazid, sai Khalil da Hafsa. Fadila na ganin Mummy, jikinta yayi sanyi, ta nufi in da Mummy take hannunta riƙe da jaririyarta. Sai dai tana ƙarasawa ta yi wata uwar ƙara ta saki Yarinyar a ƙasa, ita ma ta faɗi ganin Hajiya Salma ta rikiɗe ta zama wata ƙatuwar mage. Ƙarar da tayi sai da Daddy ya fito shi da Amina, saboda iya ƙarfinta ta yi, jarirriyar ta fashe da kuka. Khalil ne ya ɗauki Hidaya, yana faɗin Innalillahi wa innalillahi raji'un. Hatta su Hajara sai da suka fito a gigice. Yazid ne ya ƙaraso gareta cikin damuwa, ya ɗagota yana kiran sunanta. Ruƙunƙume Yazid ta yi, tana wani irin kuka, sai karta masa farce take a wuyansa ta ce "Zid ka yi mini Addu'a zan mutu, Wata ƙatuwar mage nake gani fa". A gigice Daddy ya yo kan su yana faɗin, Me ya sameta?" Hajiya Zainab kanta saukowa ta yi daga kan kujera ta yo kan Fadila. Yazid ya ɗaga kai ya ƙurawa su Hajiya Turai ido, sai jikin Turai ya fara rawa, ya kalli Hajiya Salma ya ce "Hajiya Salma ko?" Da mamaki ta kalli Yazid ta ce "Lafiya, a ina ka sanni?" Yazid ya ce "Ban sanki ba, amma kamar yadda na bada saƙo a gaya miki, kika yi burus yau Allah ya kawo ƙarshen ku, da abin da kuke yi" Daddy ya ce "Yazid menene? Kayi mana bayani" Fadila dai sai tura kanta take a ƙirjin Yazid, jikinta na rawa. Yazid ya ɗan zame rigarsa, ya nunawa Daddy wuyansa zuwa kafaɗarsa, wurin tamkar an tsatsaga masa da reza. Ya ce "Daddy, tun bayan aurena da Fadila, baifi da watanni uku ba, kusan bama bacci da daddare, kwana nake yi mata Addu'a, wannan raunin na jikina duk ita take yi mini. Duk da zancen aljani mafi yawa ƙarya ne, amma sun tabattar da Hajiya Salma ce ta turo mata su". Salati suka ɗauka, Hajiya Salma ta fara kumfar bakin za ayi mata sharri. Yazid ya kalli Hajiya Turai ya ce "Ƙarya na yi?" Ta sunkuyar da kai ta ce "A'a, tabbas muna yiwa Hajiya Zainab asiri. Tun bayan haɗuwarmu da ita, duk mijinta yafi namu kuɗi, muka fara koya mata bin bokaye, dan ta mallake shi. Sai dai tana da rowar tsiya, dan haka ita ma muka fara kai sunanta wurin malamai, aka bamu wata laya aka jefa a tsohuwar rijiya, ya zamana ba ta jin maganar kowa sai ta mu, kuma duk abin da muke so ta bamu zata nemo ta bamu. Ana haka aurena ya mutu, na yi ta ƙoƙarin na samu na auri mijinta, amma ya ƙi, ba asirin da ban yi masa ba, amma abu bai yiwu ba, na koma zaman Saudiyya. Hajiya Salma ma ba yadda ba tayi ba, a kan ta samu ya auri ƙnawarta ba nan ma ba nasara. Sai daga baya na haƙura mijina ya mayar da ni. Bayan Alhaji Ahmad yayi aure, muka yi amfani da wannan damar, muna kaita karɓo asiri, ana kuma asirce mana ita. Aka karɓo maganin da za a zubar da cikin abokiyar zamanta Amina, amma mu idan cikin ya zube, za a sadaukar wa da wani aljani jinin yayi mana namu aikin. Sau biyu muka yi nasara kawai, bokan ya sanar mana, Amina ba zata taɓu ba sai dai ayi ta amfani da makirci a kanta. Muka ɓullo da batun haɗa Khalil aure da 'yar ƙanwar Hajiya Salma, da nufin idan suka haihu, sai a kashe Khalil, amma Abin bai yiwu ba. Muka bijiro da zancen, auren Fadila da ɗan Hajiya Salma, shima duk dan muyi yadda zamu yi mu tatsi kuɗi sosai a hannunku, muka dinga zuwa muna yin asiri a kan ta so Salim, amma abu ya ƙi ci, ƙarshe muna tsaka da wani aikin a kanta, sai ji muka yi an aurar da ita. Muka dinga yi mata turen aljanu a kan duk in da take ta dawo, ta bijire akan lallai sai ta auri Salim, amma abu ya gagara. Bokaye suka ce babu aure a tsakanin ta da Salim. Kasancewar Hajiya Zainab, bata da abin so kamar Fadila, sai muka zaɓi haukata Fadila, saboda mu ƙuntata mata, dan har ga Allah muna hassada da ni'imar da ta fi mu. Shine muke ta tura mata aljanu, idan aka ce an ƙona wasu sai mu sake biya a tura wasu, kuma galibin kuɗin da muke bayarwar, a hannun Hajiya Zainab muke karɓarsu. Dan Allah ku yafe mana, yanzu haka wani irin zugi nake ji a jikina, kamar zan haukace, ku yafe mana dan Allah". Amina fashewa ta yi da kuka, jikinta ya ɗau wata irin rawa. Fadila cikin kuka ta ce"Mummy, ashe Zaki iya zuwa wurin bokaye a cutar da wani, gashi nan abin ya ƙare a kanmu, har da wanda bai ji ba bai gani ba, Yazid yafi ƙarfin wattanni baya rintsawa, tamkar zan haukace, haka na dinga faɗuwa da tsohon ciki Mummy Why?" Khalil kansa jikinsa rawa yake yi, sosai hawaye ke zuba daga idon Daddy. Ya ce "Ku je dan kanku, Allah ne kawai zai saka mini cutarwar da kuka yi mini, na barku da Allah. Sosai Amina jikinta ya cigaba da rawa, Daddy ya ɗagata ya ce maza Khalil ya je ya fito da mota. Hajiya Zainab kuwa ɗora hannu ta yi a ka, ta fashe da kuka tana nanata "Innalillahi wa innalillahi raji'un, kun cuceni Allah ya isa ban yafe ba". Ganin ba abin da aka yi musu, ya sanya sum-sum, Hajiya Turai da Salma suka fice daga gidan. Hafsa kuwa zuruuu ta yi, abin yana ɗaure mata kai. Kuka Mummy take tana wani irin gunji, ba ta taɓa zaton su Turai za su yi mata haka ba. Fadila da ta ɗan farfaɗo tashi ta yi ta ce wa Yazid ya bar falon da ita. Hafsa ta ɗau jariran, ta bi bayansu. Tare da Hajara aka tafi kai Amina Asibiti, Daddy ba magana sai kuka kawai. Suna zuwa Asibiti, aka ce cs za a shiga da Amina da gaggawa, dan jininta ya hau ba za a bari ta yi naƙuda ba. Nan da nan Khalil ya ɗau Hajara suka dawo gida, ya sanar da su Fadila abin da ake ciki, aka kwashi kayan Amina na haihuwa suka nufi Asibiti. Daddy ya ce ba za a kira su Inno ba, sai an gama aikin. Awa ɗaya da rabi, aka fito da jarirai maza biyu, an yi mata aikin. Daddy sai ya rasa me zai yi, Amina firgici ne ya sanya jininta hawa, ga baƙin ciki ga farinciki. Ba wanda ya kuma bi ta kan Hajiya Zainab, sai magariba, ya zo ya tarar da ita a sume a sashinta. Hankali a tashe ya ɗauketa zuwa Asibitin da Amina take, sai dai babu wanda ya san musababbin suman nata. Hajiya Turai da Salma kuwa, suna tafe a motar Hajiya Salma, suna faɗa, tana yiwa Turai masifar dan me zata tona musu Asiri. Aikuwa Turai ta hauta da bala'i, tana cewa bata san me take ji a jikinta bane, ji ta yi idan ba ta faɗa ba zata mutu. Suna wannan masifar, Tirela ta taho, garin su kauce mata motar ta kifa, Hajiya Turai ko shurawa ba ta yi ba. Ahalin Daddy da basu san wainar da aka toya ba, sai labarin haihuwa da suka ji, suka yi ta murna suna cewa arziƙi ya sauka a gidan Alhaji Ahmad. Khalil ne yake zuwa duba Mummy, Sai Yazid. Yazid ya yi ta yiwa Fadila faɗa a kan lallai kar ta ce zata ƙullaci Mummy, dan ba wanda baya kuskure a rayuwa. Da Hajiya Zainab ta sake farkawa, ta ga Fadila da Yazid, ga Hafsa ga Khalil a tsaye a kanta, sai ta fashe da kuka tana faɗin "Dan girman Allah ku yafe mini, kuma ku rufa mini asiri, ina miji na in nemi yafiyarsa ina Amina, ashe abin da take gaya mini gaskiya ne, Fadila ku yafe mini". Yazid ya ce "Mummy duk sun yafe miki, Daddy ma zai zo wurinki in sha Allah, Amina an mata aiki ta haifi yara maza biyu" Ta kalli Yazid ta ce " Ɗan nan dan Allah ku yafe mini, na san ba zan tsawon rai ba, likita ya tabattar mininda shaye-shayen magungunan hausa barkatai da na dinga yi, wanda ban san da me aka haɗasu ba ya sanya ƙodata ɗaya ta gaza, dan Allah ku yafe mini, kar na mutu da hakkinku". Fadila ta fashe da kuka, ta rungume Mummy, tana Cewa "Mun yafe miki Mummy, ba zaki mutu yanzu ba, dan Allah ki daina faɗar haka". Fadila ta tashi da sauri, ta koma ɗakin da Amina take kwance, Daddy na zaune a gefe, da jarirai a hannunsa. Fadila ta zube a gaban gadon Amina ta riƙe hannun Amina ta ce "Dan Allah Amina ki yafe wa Mummy, kin san wani abun ba laifinta bane ba, Daddy dan Allah ku yafe mata, likitoci sun tabattar da Mummy ta gamu da renal failure". Waro ido suka yi gaba ɗaya, Amina duk da halin da take ciki sai da ta tsure ta ce 'Ciwon ƙoda kuma?" Fadila ta jinjina kai tana kuka. Tashi Daddy ya yi ya fita, dan tun da aka kawo Hajiya Zainab bai leƙa ya ganta ba, saboda ya sha mamakin abin da ya ji ta aikata ba tare da ta musa ba. Yana zuwa ya tarar da ita, ta rirriƙe Khalil tana kuka. Tana ganin Daddy ta saki Khalil, tana miƙawa Daddy hannu tana kuka. Daddy ya ƙarasa kusa da ita ya zauna, ya kalleta ya ce "Wane likitan ne ya ce kina da wannan ciwon?" Cikin kuka ta ce "Likita ba zai yi ƙarya ba, ƙodata ɗaya ta samu matsala, Ahmad na san na cutar da kai, dan Allah kayi haƙuri na san ba zan yi tsawon rai ba, na yi dana sanin abubuwan da na aikata, dan Allah ka yi haƙuri Ahmad ka yafe mini". Daddy ya dubi Khalil ya ce "Ka je ka zo mini da likitan da yake dubata". Jiki a sanyaye Khalil ya fita daga ɗakin, kasancewar Amina ta fara takawa, dan kwanaki uku kenan da yi mata Cs, hankali a tashe ta shigo ɗakin da Mummy ke kwance ta riƙa hannun Daddy tana kuka, amma ya ƙi magana sai Hafsa da Yazid da kuma Fadila. Amina ta ƙarasa gaban gadon tana faɗin "Sannu Hajiya, wai ciwon ƙoda ni ai ban san a nan Asibitin kike ba". Duk da wani irin kishi da yake tasowa Hajiya Zainab, a kan Amina, amma ta ga ƙoƙarin Amina da ta zo dubata. Likita ne ya shigo, suka gaisa da Daddy, Daddy ya tambayeshi meke damun matarsa. Nan likita yayi masa bayanin cewar, magunguna da take sha ba bisa ƙa'ida ba, ya sanya ƙodarta ɗaya ta taɓu. Amma idan aka bi ƙa'idojin da zasu saka, zata iya rayuwa da guda ɗaya. Hajiya Zainab ta riƙo hannun Amina ta ce "Ba wani tsawon rai da zan, ni na san mutuwa zan yi, dan Allah ki yafe mini, na san kema na cutar da ke, ki kuma saka baki ya yafe mini dan Allah". Amina ta kalli Daddy ta ce "Daddy, dan Allah do something, dan Allah ka yafe mata. Fadila ma kuka take yi sosai da sosai. Daddy ya yi ajiyar zuciya ya ce "Shikenan, Allah ya bata lafiya, ni yanzu fatana ta samu lafiya Allah ya yafe mana baki ɗaya". Yazid ne da suka bashi tausayi, ya ce "Allah ya saka da alheri Daddy, Allah ya ƙara girma. Fadila ta rungume Daddy tana yi masa godiya. Ita ma Hajiya Zainab godiyar ta dinga yi, ta ce "A bani jariran na gansu, Hafsa ku yafe mini dan Allah" Hafsa ta ce "Bakomai Mummy" cikin murmushi ta sauko da jaririyar ta miƙawa Mama, Fadila ma ta ce Mummy bari na karɓo miki Hidaya ma. Ta fita da sauri, ta koma ɗakin da aka kwantar da Amina, Inno tana goye da Hidaya, Hajara kuma na bawa jariran madara. Fadila ta ce "Inno, Mummy ce zata ɗau Hidaya" Inno ta yi murmushi ta ce "To muje in sake duba jikin nata". Fadila ta ce "Yauwa Hajara taho da 'yan biyu ma". Haka suka ɗunguma zuwa ɗakin da Mummy take. Duk suka jere mata yaran, tana kuka ta dinga shafa kan yaran tana kuka tana su yafe mata. Amina ta ce "Hajiya dan Allah ki daina kuka, komai ya wuce tun da dai kin fuskanci gaskiya, Allah ya yafe mana baki ɗaya ya baki lafiya". Gaba ɗaya jikin Hajiya Zainab yayi sanyi, duk motsi ta dinga neman afuwa kenan. Mutanen da suka sake dawowa sunan Amina, sun yi mamakin ganin Hajiya Zainab duk ta rame tayi sanyi. Ammi su Hajiya Maryam, da Azima da 'yan makarantar su Amina duk sun zo suna, kuma sun yi wa Amina alkhairi. Hajiya Salma dai, ba ta mutu ba, sai dai lakarta ta taɓu, ba zata iya yiwa kanta komai ba, sai dai a kwantar a tayar. Bayan sunan jariran Amina, Fadila ta ce zata koma gida, dan jikin Mummy ma da sauƙi sosai da sosai. Amina ta cigaba da lallaɓa Daddy, tana nuna masa Cewar Hajiya Zainab ta saduda, dan haka yayi haƙuri komai ya wuce. Allah ya sa Amina ta shawo kan Daddy, ya biya kuɗi aka fita da Hajiya Zainab Indiya, domin cigaba da kula da lafiyar ta. Daddy ya bawa Yazid aiki a kamfaninsa da zai buɗe na kwangila a Kano. Yazid dai ya karɓa ne kawai, amma ya barwa kansa cewa zai cigaba da lalaubawa idan ya samu wani aikin zai tafi, baya son ace Daddy ya dinga yi masa komai, dan yana auren 'yar sa. Still Daddy ya kuma bawa Abdul aiki a kamfanin, dam ba zai manta alkhairin sa ba shima, a lokacin ya auri Yusra ma. Babban muƙami Daddy ya bawa Yazid, ga zuwa makaranta, Yazid ya zama busy sosai, ya nemawa Fadila School of Nursing, cikin ikon Allah kuma ta warke daga ciwon iskokai. Baba Uwani kuwa, matar Baban Yazid ita ma ta rasu tuni, amma Yazid bai yadda ya yanke alaƙa da 'yan uwansa gaba ɗaya ba. Bayan Hajiya Zainab ta dawo daga indiya, jikinta yayi kyau sosai da sosai. Daddy ya sakata a gaba, zuwa Dutse ta dinga bawa mutanen da ta ɓatawa haƙuri ciki har da danginta. Ta yi nadama sosai da sosai, tayi mamakin zaluncin da su Hajiya Turai suka yi mata. Tana ji tana gani dai, Amina ta ƙwace mata gida, sai abin da Amina ta ce shi ake yi, sai dai Aminan na iya ƙoƙarin ta wurin yi mata adalci. Abubuwa suka ƙara yiwa Amina yawa, ga 'yan biyu watanninsu takwas ta kuma samun ciki, an sha daru sosai dan cewa ta yi zubarwa za tayi, ita ga karatu, ga kula da yara ga kuma ciki. Sai da Daddy aya zazzare mata ido sannan ta haƙura, ga laulayi ga makaranta, dan ma Kusan kodayaushe twins suna wurin Hajara ko Hajiya Zainab. Ganin yaran na ɗebe mata kewa, Fadila ma ta zo ta dire mata Hidaya ta tafi makaranta, suka mayar da ita tamkar Nanny. Mijin Hajiya Salma ya tsallake ya je yayi wani auren ya barta, ɗanta Salim ya tattara ɗan abin da take da shi, ya dinga facakarsa, suka barta a wahala ga jinya. Bayan Yazid ya kammala makaranta, ya samu scholarship a Saudiyya, a lokacin Fadila ta gama school of Nursing ita ma, ya tattara ta da 'yarsa suka bar ƙasar. Cikin ikon Allah yana karatu a ƙasar ya samu aiki, ya sake mayar da Fadila makaranta, ya buɗe wa Hajiyarsa wurin sana'a a Nigeria. Sai da suka shekara Bakwai a Saudiyya, sannan suka dawo Nigeria, Fadila ta kuma haihuwar ɗa namiji, Amina kuma ta kuma haifar maza biyu da mace ɗaya. Yazid ya samu alkhairi sosai zamansu a Saudiyya, ya dawo ya samu aikin yi a Nigeria, ga gefe guda Daddy na ta sake janyo shi cikin harkokinsa, dan so yake ya sakar musu shi da Khalil shi kuma ya huta. Kwatsam an gayyaci su Yazid za su yiwa wasu malaman jami'o'i wurin screening, waɗanda za a tura su wani course ƙasar waje. Babu tsammani har da Kankiya a cikin waɗanda Yazid zai tantance, Kankiya ya rikice, ya ƙadarra Yazid ba zai bari yayi nasara ba, amma ya ga Yazid ya girmama shi, yana nuna wa abokan aikinsa ai wannan malaminsa ne. Kankiya duk kunya ta kama shi, ya dinga neman yafiyar Yazid, a nan Yazid ya sanar masa ya auri Fadila har da yara. Kankiya ya taya shi murna sosai, Yazid ya yi masa tantancewar sa cikin mutunci da girmamawa. Haka rayuwa ta cigaba da gudana, dukkanin ahalin suka cigaba da rayuwa cikin farinciki, sai dai Hajiya Zainab ta ƙarasa rayuwarta tamkar mujiya, dan Mutane ba su daina zunɗenta da bada labarin mugun halinta ba. TAMMAT BIHAMDILLAH, ALHAMDILILLAH, ALHAMDILILLAH, ALHAMDILILLAH. A NAN NA KAWO MUKU ƘARSHEN WANNAN LITTAFI, NA GABA DA GABANTA. INA JINJINA TARE DA MIƘA SAƘON GODIYA TA GA MASOYAN ALƘALAMIN AYSHERCOOL BARKA DA JUMURIN BIBIYAR LITTAFINA. JAMA'ATA NA WHAT'S APP, MUTANEN AREWABOOKS, WANDA SUKA BANI KYAUTAR DATA DA SAURANSU DUK INA GODIYA, ALLAH YA BAR ƘAUNA. WANDA SUKA SAI BOOK ƊINA SUKA FITAR MINI BANYA BANYA.....🙄 INA SAI BABBAN BOOK AKE FITARWA, AMMA KUKA SAYA KUKA FITAR MINI KUN KORI GABA, PAID BOOK NA GABA B.S B.S😒😒😒 IN SHA ALLAH LITTAFIN GABA GABANTA ZAI ZO A YOUTUBE CHANNEL ƊINA TA COOL HAUSA NOVELS NA BAYAN SALLA IDAN ALLAH YA KAIMU. GA AZUMI YANA GABATOWA, IDAN ALLAH YA SA MUNA DA RABON GANI, ALLAH YA SANYA MU CIKIN 'YANTATTUN BAYINSA. DAN ALLAH WANDA YA TUNA DA NI A CIKIN WANNAN WATAN MAI ALFARMA YA SANYA NI A CIKIN ADDU'A PLEASE 🙏🙏🙏 DOMIN GYARA, SHARHI KO SHAWARA A KAN DUKKAN BOOKS ƊINA. GA LAMBAR WAYATA ANA IYA TUNTUƁATA KAI TSAYE. 08081012143 AREWABOOKS AYSHERCOOL7724 WATPAD AYSHERCOOL 7724 KAR A MANTA DA SUBSCRIBING YOUTUBE CHANNEL ƊINA. SAI MUN HAƊU A SABON BOOK IDAN ALLAH YA KAIMU BAYAN SALLA. MEENA VIP GROUP HAUSA NOVEL DOCUMENT for more information contact on +234 7014979567 WhatsApp ONLY Downloaded from GNOVELS.COM.NG This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG For feedback and support Facebook : https://facebook.com/gnovels Twitter : https://twitter.com/gnovels Telegram : https://t.me/gnovels