🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAI JIN K'AI. DIKKAN YABO DA GODIYA SUN TABBATA GA ALLAH S.W.T. TSIRA DA AMINCI SU K'ARA TABBATA GA SHUGABAN HALITTU S.A W ,IYALAN SA DA SAHABBAN SA, DA WA'YANDA SUKA BIYO BAYAN SU DA KYAUTATAWA HAR ZUWA RANAR K'ARSHE... *INA ROK'ON ALLAH YADDA NA FARA WANNAN LITTAFI LAFIYA ,SUBHANAHU YA BANI IKON ISAR DA SAK'ON DAKE CIKI AKAN DAIDAI. DA FATAR MASOYA NA ZAKU CI GABA DA NUNA MUN K'AUNAR DA KUKA SABA NUNA MUN?...* *LABARIN GIDAN MISBAHU, LABARI NE MAI D'AUKE DA DARUSSA IRI DABAN-DABAN. LABARI NE WANDA NASAN INSHA ALLAHU ZAI ILIMANTAR ,YA KUMA K'AYATAR DAKU MASU KARATU. INA FATAR ZAKU BIYO NI DAN JIN YADDA LABARIN ZE RIK'A ZUWA MUKU SAND'A-SAND'A!..* *_BABI NA D'AYA..._* *____________________* _Garin sakkwato. Unguwar Sama Road . Unguwa ce ta hamshak'an mutane, Wanda kuwa ke mallakar muhilli a unguwar se Wanda yaji gishiri ma'ana Naira ,ya kuma amsa sunan shi ,shi, shi d'in ne. Unguwa ce ta manyan mutane ,manya-manyan 'yan siyasa ,hamshak'an 'yan kasuwa da kuma masu hannu da shuni, kai duk wani me fad'i aji indai a garin sakkwato ne ,to zaka samu yana da gida a wannan katafaren unguwar, hatta 'yan zaku zamu masu zuwa suyi kud'i a garin ba'a barsu a baya ba..._ _Gidan misbahu na d'aya daga cikin manyan gidaje a layin NAIRA... Babban gida ne ginin zamani da aka kashe ainahin abunda ake kira NAIRAR,,, gida ne Wanda aka qawata shi da duk wani abun more rayuwa. Kai da ka kalla gidan kasan k'erarren gini ne,,, Gate d'in gidan wato babban k'ofar shiga ,shi kad'ai kanshi abun kallo ne ,daga ciki kuwa misalta irin tsaruwa da had'uwar gidan b'ata lokaci ne ,dan kuwa se Wanda ya gani..._ _Apartment wato sashe -sashe a gidan kusan akwai fanni sama da goma,,, fannin wasar yara ,wato playground daga hagu , idan kuma ka mik'e hanya ce daze sadaka da Swimming pool ,Wato wajen wanka. Daga nan kuma zuwa ainahin babban store da ake zuba komai da komai na buk'atun rayuwar gidan na yau da kullum, shima tafiya ce da ak'alla zata kai Nisan kilometres ukku._ _daga bayan gidan kuma Sashen kiwon dabbobi ne daban, wato GIDAN GONA,,,kama daga kajin gida Dana turawa, tsuntsaye ,gidan kifi, raguna ,shanaye dadai sauran su._ _ko wani fanni an keb'ance masa nasa ma'aikatan masu kula da sashen kacokam..._ _KUBRA ce zaune kan kushin ,cikin shiga ta alfarma. A zagaye take da k'awayen ta 'yan duniya ,ko wacce da kalan nata fetsarancin_. _Kwalbar shisha ce a hannun jakadiyar uwar 'YAN BARIKi, tana zuk'a ,tana busar da hayak'in cike da k'ware wa. A cikin k'adangarun barikin kowacce da fannin data fi k'ware wa, wannan ta zuk'i sigari ,waccan k'waya ,wata kuma ainahin syrup na shaye-shaye ,idan aka d'aga sedai a sauke kwalban an shaye_ _Sannu a hankali k'arar sauti ke tashi daga babban parloun. Daga inda suke zaune suke taka rawar su ta 'yan bariki, cike da shauk'i da nanaye._ _Wata dakakkiyar mota k'irar marsandi ce tayi parking ,adaidai inda aka tanada Dan ajiye manyan motocin gidan. Matsakaitan 'yan mata ne su ukku suka fito daga motan. Ko waccen su saye take da purple uniform , hannayen su kuma rik'e da alqur'anai ,da alama daga makarantar islamiyya suka dawo. Kai da kalli yaran base an gaya maka kiwon cornflakes da madara bane ,zallar Hutu ce ta bayyana a fuskokin su ,gasu kyawawa,farin su daidai gwargwado. Har sun kama hanyar da zata sada su da babban sashen gidan ,se kuma babbar cikin su taja ta tsaya tare da dafa kai ,a lokaci d'aya ta fadi "Oh shit!". K'aramar cikin su ce ta dube ta tare da cewa " Yaya suxee lafiya?" Wacce aka kira da Yaya suxee tace "Wallahi waya na ,na manta a wurin sayyadi ,Dan d'azu na bashi ya tura mun wasu wa'azuzzuka ,to kamar ban karb'a ba! " ta dubi ta tsakiyan tare da cewa " Dan Allah Haseena kije ki karb'a makullin mota wajen baba lawan ki duba mun daga daga inda na zauna ,kiga ko tana ciki" Wacce aka kira da Haseena naga ta amsa da "Toh Yaya!". Sannan ta mik'a mata Qur'anan hannun ta ,ta juya zata yi kamar yadda yayar tata ta umurce ta. Har tayi nisa ,Se k'aramar su ta juya ta kalli suxee tare da b'ata fuska. Murmushi suxee ta sakar mata tare da cewa " ya ne Auta kin gaji ne?". Cike da shagwab'a Auta tace "Ni kam na gaji Yaya suxee. Allah ni tafiya ta zanyi". Ta fad'i tare da juyawa ta fara tafiya. " Lalalala! Yanzu Auta bazaki jira muba ,shine zaki tafi?". Suxee tace tare da rik'e hab'a. Ita dai Auta bata ma jiyo ba ,se tafiyar ta take tana wani karya wuya. Har takai daidai volcony d'in daze sada ta da main parloun gidan ,se kuma ta fasa shiga ,juya wa tayi ,Wanda yayi daidai da dawowar Haseena ,tana cewa "Allah Anty na duba ban gani ba. Ki Bari gobe idan munje islamiyya se ki tambayi sayyadi ,inaga dai acan kika bar wayan". Haseena ta fad'a cike da kulawa ga 'yar uwar ta ta. " O-Ow!" Inji suxee sannan tace "Toh bakomai muje". Har sun kusa k'arasa wa inda Auta ke tsaye. Auta ta k'wala mata kira " Yaya suxee! " d'agowar da zata yi ,se Auta ta Ciro wayar da suxeen ke nema tace "Kinga fa wayar ki nan. A jikin ki ya fad'o da zamu shiga mota ,shine ni kuma na d'auke miki ,nace sena baki wahala sannan zan baki" Auta ta fad'a cike da tsokana. Zaro ido Haseena tayi tana cewa "Dan Iskanci Ashe wayar na hannun ki ,shine kika bari na wahala! To kawo ki karb'a chocolate"... Haseena tace cike da wayo ,a cewar ta idan ta kawo seta doddoke ta ,na wahalan data saka ta. Auta yarinya ce me wayon tsira ,gwalo tayi wa Haseena, tare da murd'a handle d'in k'ofar ta shige. K'yacci Haseena tayi tana cewa " zan kama ki ne ai." Duban ta ta maida wajen suxee tace "Yaya suxee kina gani fa kuma kin k'i kice komai?" Dariya yadda Haseena tayi magana yaba suxee ,tace " To in banda abun ki Haseena ,aika-aikatan auta wani iri ne baki gani ba dahar wannan ze dame ki. Kar ki manta itace sanadiyyar lalacewar waccan tsohuwar wayar nawa ,ta tab'a d'aukan wayan ta shige toilet d'in mu tana buga game ,da taji wayar tayi zafi ,sink ta cika da ruwa ta jefa wayan, wai wayar ta huce ,a cewar ta wai Dan kar in gane".. Dariya dikkan su suka saka ,suxee tace " to kinga ni yanzu sha'anin Auta sedai in bi ta a hankali ,da Yaya ma na samu swt daddy canza min wannan? " "ai kau dai Yaya ,b'annar Auta sedai mu had'a ta da addu'a". Haseena ta fad'a tana dariya. A tare suka k'arasa cikin gidan. Se hirar rashin jin Auta suke yi... Tun daga babban parlour ,suka fara jiyo k'arar sauti na tashi daga parloun sama ,ko basu tambaya ba sun San mahaifiyar su ce ,kuma inda sabo yaci ace sun saba ,amma da yake rayuwar su da nata ya banbanta ,har kawo yanzu sun kasa sabawa da bahaguwar rayuwar ta. B'ata fuska suxee tayi ,tana fad'in " mum again?". Gyad'a kai haseena tayi tare da cewa "Ai kema kin San se ita ,madushiyar duk duniya kenan indai wajen jin sauti ne ,ba tada aikin daya wuce wannan." Haseena ta fad'a ,fuskar nan nata ko oho. "Stop Haseenaaaah!" Suxee ta daka mata tsawa ,tace "Bana hana ki fad'in wani kalami Mara dad'i akan mahaifiyar mu ba? Uwa fa uwa ce. Ya kamata ki kula sosai". " I'm so sorry ,Yaya insha Allah bazan sake ba, amma fa da ana sake uwa wllh Dana dad'e da sake mummy ,Dan Sam bata cancanci ta zama uwar mu ba." haseena ta fad'a. Bata jira amsar da suxee zata bata ba, da canza hanya. Cikin tsananin b'acin rai da takaicin hali mahaifiyar tasu suxee ta haura parloun sama ,inda ta tabbatar daga nan sautin ke tashi... MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [7/11, 5:45 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA BIYU_ *____________________* _A fusace suxee ta haura ,tana zuwa bata bi takan kowa ba ta nufi homes theatres d'in dake fitar da wani irin sauti ,Wanda hatta dakin na k'asan gidan amsa wa yake yi. Takai hannu zata kashe hajja Fati da daka mata tsawo (babbar k'awar kubra kenan indai a fannin shan sha'ani ne) ,se akayi sa'a kuma duk aciki Suxee tafi tsanar ta, a cewar ta idan da badan hajja Fati ba ,komai na mahaifiyar su ze zo da sauk'i._ "Ke suxee! Kar ki kuskura ki fara kashe mana sauti, kar ki fara". Hajja Fati ta fad'a cike da gargad'i. D'an d'agowa Suxee tayi tana mata wani irin kallon tsana ,bata bi takan taba kawai takai hannu ta kashe sautin. Takun dabai Gaza biyar zuwa shida ba hajja Fati tayi ,se gata a gaban Suxee ,d'agowar da Suxee zatayi base kawai taji saukar wani gigitaccen mari ba. A razane ta d'ago tana kallon ta tare da dafe kuncin ta. " Akan na kashe sauti shine zaki mare ni? Naga cewar duk abunda kuke yi banga na samu ladan a ciki ba ,se ma tarin sab'o da zunubi da kuke kwasarwa kan Ku"... Kubra dake daga zaune tana kallon duk abunda yake faruwa ,tashi tayi tsaye tana tafi hannu bibbiyu. Har ta k'araso inda suke tsaye sannan ta dena tafin. Wani kallon yaushe kika girma dahar zaki gaya mana Allah kubra ta watsa wa Suxee tare da cewa "Dube ki fa ,dika dika tashin yaushe ce ki? Suxee tun kafin kisan zaki zo duniya nayi islamiyya na kuma San Allah." Kubra maida duban ta tayi kan hajja Fati tayi tace "Hajja Fati wallahi kin mata da sauk'i ma ,a tunani na sekin kusa sumar da ita ,Dan na fuskanci k'wak'walwar ta na buqatar saiti." "Ai ki manta kawai hajia kubra ,dika dika suxee guda nawa ne ,yarinya ce bata San inda duniyar tasa gaba ba. Ina ganin wannan ma yayi mu bata lokaci ,nasan idan ta k'ara girma zata gane abunda muke ba kuskure bane kamar yadda take tunani ,ke wallahi ma se ta nemi ki d'ora ta a hanya ma" ...cewar hajja Fati "Allah ko?" Kubra ta fad'a cike da jin dad'i "Sosai ma kuwa" inji hajja Fati ,tana wani murmushin su na 'yan duniya. Hannu kubra ta bata suka kashe. A lokacin Wasu sababbin hawayen bak'in ciki ya shiga wanke wa Suxee fuska. Cikin muryar kuka ta fara magana "Tir da irin wannan shed'aniyar rayuwar taku ,dahar kuke tunanin zaku wayi gari Ku ganni a tawagar Ku, to idan ma mafarki kuke gara Ku farka ,Ku kuma sake tunani ,ni suxee bazan tab'a kasancewa a cikin Ku ba ,a yayin da bazan tab'a aikata abun da kuke so na aikata ba na sab'on Allah." Lubcy dake daga gefe tana jin ruguntsumin da ake tafkawa. Tasowa tayi cikin tafiyar ta ta k'asaita ta k'araso inda suke ,tafe take tana busar da hayak'in sigarin da take zuk'a. Tafa kafad'ar Suxee tayi a lokaci d'aya kuma tana zagaya ta ,kai kace me shirin lashe mata kurwa. Murya can k'asa kamar me rad'a ,lubcy tace "Cool down mana 'ya ta ! Dube ki fa yadda kike ta asarar hawayen ki ,kan abunda be taka kara ya karya kiyashi ba. Ki kwantar da hankalin ki ,wannan d'in da kike ganin muna yi bakomai bane ,waye ce da zamani. Suxee ki kalle ki ,kina da kyan fuska Dana sura ,zaki yi fitting ko wani namiji ehn. Ki ajiye guntun wa'azin ki a gefe kizo ki mori rayuwar ki ,kai kima gode wa Allah dahar ya baki uwa me tunani da hangen nisa." Kwab'e hannun lubcy suxee tayi dake kafad'an ta ,ta gudu ta fice daga parloun tana k'ara fashewa da wani kuka me ban tausayi. Ta gama sauka stairs kenan taji tayi karo da mutum ,d'agowar da zatayi ta duba ,se taga daddyn ta yana sakar mata murmushi. Fad'awa jikin shi tayi tare da sake wani sabon kukan, lallashin ta ya shiga yi yana bubbuga bayan ta, kamar wata k'aramar yarinya 'yar goye ,ko be tambayi me ya same ta ba ,yasan baze wuce ita da ballagazar mahaifiyar taba. Janta yayi suka k'arasa cikin parloun ,ya zaunar da ita kan kujera ,sannan ya mik'e ya nufi parloun sama a fusace "Kubra!" Ya kira ta cikin kakkausar murya. Wani kallon raini ta d'ago tana bin shi dashi. Be jira ta amsa ba ya fara mata gargad'i "Duk iskanci da shed'anancin da kika San kina ji ko kike yi ,ya tsaya iya kan ki ,kar ki kuskura ki tsoma 'ya'ya na a ciki ,hakan kuwa ba k'aramin sab'ani zamu samu ba, zaki iya mun komai ,ya tsaya iya kaina amma kar ya shafi 'ya'ya na. Na gaya miki". Ya k'arasa naganan tare da nuna ta da d'an yatsa. Kallon lallai kinyi sake d'an zaki ya girma hajja Fati take yi mata ganin bata ce masa komai ba. Ita ma ido tayi mata alamar kar ta damu. Daddy ci gaba yayi " sannan Ku kuma..." Cak ya tsaya kamar Wanda aka zare wa lakka, sakamakon wani kambu da kubra ta murza Wanda ke mak'ale a tsintsiyar hannun ta. "Fita ka bani waje sakarai kawai" shine kawai abunda kubra ta furta ,a mamaki na se naga daddy ya fita da sauri. Dariya dikkan su suka saka ,hajja Fati tace "Haba yanzu dai naji magana ,amma yazo ze wani ishe mu da wak'e-wak'en shi na banza da wofi". " Dama na barshi ne ya sarara kwana biyu ,amma tunda be San azziki ba ,yanzu ze dawo yin rayuwar kambu ,se yadda kambu yayi dashi." Kubra ta fad'a cikin isa da gadara. Wani dariyar shed'anancin suka sake fashewa dashi, a lokaci d'aya suna mata wani irin kirari Wanda su kad'ai suka San me hakan ke nufi... MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [7/12, 3:07 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA UKU_ *_____________________* _Da daddare misalin k'arfe goma sha d'aya na dare ,kubra ce a side d'in ta cikin shigarta na bacci , har ta kwanta ,se kuma ta tuna cewar gobe zata je k'asar NIJAR ita da hajja Fati Dan sako kambun ta, gashi ba wani isash-shen kud'i a hannun ta, wani guntun tsaki taja ,kafin ta sauko daga kan gadon._ _makeken wardrobe d'in ta ta bud'e ,ta d'auki kambun ta ,murza shi tayi sannan ta mak'ala shi a hannun ta. Gaban daddy ne yayi wani mummunan fad'uwa a lokacin da kubra ta murza kambun ta ,duk se yaji ya rasa me ke masa dad'i a wannan lokacin. Kai tsaye sashen shi ta nufa ,a d'aki ta same shi zaune da system a gaban shi ,sedai ga dikkan alama hankalin shi ba a wajen yake ba. Kamar ba kubran daya Sani ba ,k'arasowa tayi har inda yake zaune ,tad'an matsar da system din da ke gaban shi sannan ta samu guri ta zauna. D'an d'agowa yayi da mamaki yana bin ta da ido ,sanin kanshi ne azziki baya kawo kubra sashen shi._ _wani irin shu'umin murmushi ta sakar mishi tare da shafo gefen fuskar shi ,a lokaci d'aya kuma tace_ "Makullin drawer-n kud'in ka zaka bani" ta fad'a kamar me rad'a. Wani irin d'agowa daddy yayi yana mata kallon baki da hankali. Magana ze yi ,kawai se ta murza kambun hannun ta, nan take yaji kanshi yayi wani mumunan sarawa ,murmushin zaka bani ko Yaya ta masa ,sannan ta sake tambayar sa "Ina keys d'in?"... Jiki a sanyaye daddy ya tashi ,ya d'auko mata makullan ya mik'a mata. Karb'a tayi tana bubbuga k'afad'ar shi tare da cewa " wise man!" Sannan ta mik'e ta nufi drawern da kud'in suke. Bud'e wa tayi bata wani sha wahala ba dan tasan pin d'in bud'e akwatin kud'in. Kud'i kubra ta iba bani da kud'i ba ,kud'i bana wasa ba ,ni kaina bazan ce ga adadin kud'in ba. Bayan ta iba ,maida wa tayi ta rufe tare kai masa sambata a goshi ,sannan ta cillamai makullin ta fice abunta. Bayan ta fita ne daddy ya fara tunanin Maya faru dashi cikin 'yan mintunan nan ,yadai ga shigowar kubra har zuwa zaman da tayi ,amma baya nan kuma baze iya tuna komai ba. Kai ya dafe tare da furta "innalillahi wa'inna ilaihi raji'un! Hasbunallahu wani'imal wakil" har so uku ,nan danan yaji komai daya faru kamar a mafarki ne ,tashi yayi ya d'auro alwala ,ya gabatar da sallan nafila ,yana kan dadduma har aka kira sallan asuba ,seda ya shiga d'akin su suxee ya tashe su sannan ya fito da niyyar zuwa masallaci ,fitowar shi keda wuya, yaga wucewar hasken motar kubra ,alamar fita tayi. D'an tsayawa yayi kamar me tunani ,se kuma ya girgiza kai ya wuce abun shi... Misalin k'arfe Tara na safe ,suxee da haseena suka fara shirye-shiryen breakfast kamar yadda suka saba. Ruwan zafin tea suka fara d'orawa ,sannan suka soya Doya da k'wai ,indomie suka dafa wa auta ,Dan bata da abun breakfast daya wuce wannan ,shi kuma daddy suka dama masa kunun gyad'a ,kasancewar yafi qaunar karyawa dashi sama da komai. Goma da rabi daidai suka kammala tare da tsaftace ko ina. parlorn daddy suka kai komai ,akan dining suka jera. Suxee tace "Yauwa haseena tunda mun gama komai inaga ,kije ki ta do Auta ,ni kuma in taso daddy! Kuma Dan Allah kiyi mata a hankali nasan halin ki" Kwashewa da dariya haseena tayi tana cewa "Kai Yaya suxee, ai Autar ce wata sa'in da k'ule me rai wallahi " Suxee tace "nidai na gaya miki... Bayan sun kammala karyawa ,daddy Yace " inaga tunda kun samu Hutu ,kamata yayi mu shirya muje mu gaida Hajiya ta(mahaifiyar shi kenan). Tsalle auta ta daka tana cewa "Daddy yaushe zamu je?" Murmushi daddy yayi irin nasu na manya ,kafin yace "A yau ma idan kuna so ai se muje Auta, kano aina maida ta kamar gida ,inaga se mubi jirgi kawai ma" Nan danan suka cika parloun da ihu ,murna sosai suke yi zasu je ganin Hajiya. Cikin tsantsar so da qauna daddy ke bin su da kallo daya bayan daya ,idan akwai abunda daddy yafi so a duniya be fi sama da farin cikin 'ya'yan shiba. cikin k'ank'anin lokaci suka shirya komai nasu ,a akwati daya suka shirya komai, misalin k'arfe biyu suka fita ,koda ukku tayi suna garin kano... _Nijar..._ kubra ce zaune ita da hajja Fati a gaban boka RUBATSI... Wani arnen dariya RUBATSI ya fashe dashi irin nasu na abokan Iblis ,a lokaci d'aya kuma yana duba tsatsubar tsafin sa. Ihu ya saki Wanda ya k'are d'e gaba d'aya dajin tarnak'aki , nan take tsuntsaye suka fara tashi ,wasu kuma sedai suka fad'o k'asa a mace ,saboda tsananin girman tsafin RUBATSI... Wani bak'in madubi ya daka ,cikin k'ank'anin lokaci se ga daddy ya fito a ciki. Dariyar shi me tsinka hanjin me saurare ya sake fashewa dashi ,kafin ya gimtse fuska a take kamar be tab'a dariya a duniya ba. "A yanzu haka mijin ki yana kano tare da 'ya'yan ki ,sannan wannan zuwan nashi ba alkhairi bane Dan kuwa ,a wannan zuwan mahaifiyar shi ta gama shirya komai Dan tabbatar da ya sake k'ara aure"... Wani zaro ido kubra da hajja Fati suka shiga yi ,a lokaci d'aya hanjin kubra ya shiga k'ugi... MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [7/13, 1:13 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA HUD'U_ *_____________________* _Tsabar kad'uwa da mamaki ne ya cika kubra ,Wanda ya assassa mata tunani iri daban daban._ _A tunanin ta tunda take da Misbahu bai tab'a tunanin k'arin aure ba sama da shekara goma sha takwas makamancin wannan be tab'a tasowa ba se ayau kuma ayanzu kamar yadda boka RUBATSI ya sheda mata._ _Hajja Fati ce tayi k'arfin halin cewa_ "Tsafi ya da fa! Yanzu menene abun yi kenan?" Se a lokacin kubra ta dawo daga garin tunanin data je. Wata fajirarriyar dariya Boka RUBATSI ya fashe dashi tare da cewa "Menene kuwa bazamu iya ba, wani aiki ne a doron duniya ze buwayi RUBATSI? Nine fa na gagari na gagari kowa,,, gagararren ma ni RUBATSI gagarar shi nake yi! A kashe,,,,a b'adda ,,,, a raba,,,,a yanka ashanye jini,,, gigitarwa ko hauka,,, wannan sune aiki mafi sauqi a wajen RUBATSI... Duk abunda kuke so Ku k'addara anyi an gama kawai"... Cikin jin dad'i hajja Fati tace" ni fa aganina kawai boka a b'adda ta, ta yadda hatta mahaifiyar ta data haife ta bazata k'ara tunanin ta haifi me sunan taba. Kawai a jefa ta wata uwa duniya." Kundin tsafi boka RUBATSI ya buga ,kafin Yace "Wannan Abu ai me sauk'i ne da k'arfin tsafi." Hannu ya maida cikin kundin tsafin dake gaban shi ,tare da rufe ido ,se wasu sambatu yake yi irin nasu na guma-guman arna. Cikin mintin dabe Gaza sha biyar ba ,se ga aljani ya bayyana. A firgice kubra ta k'ank'ame hajja Fati, Dan kubra badai tsoro ba. Ita kanta hajja Fati dukda taurin rai irin nata ,ba k'aramin girgiza tayi ba. Cikin wani harshe wanda ba wanda yake gane me suke cewa ,irin nasu na tsakanin Aljani da wakilin aljanin RUBATSI ke magana da wannan aljanin. Suna gama wa kuma b'at aka neme aljanin aka rasa, a wannan karon fitsari ne ya kusa tsiyayowa daga marar Kubra... Boka RUBATSI Yace "Wannan da kuka gani aljani SUFURSUNARI kenan. Cika aiki nake kiran shi. Kada Ku damu shine ya karb'i aikin Ku. Sedai ya buk'aci da akawo gashin kan wannan matar da aka d'aura auren ta da mijin ki ,da kuma d'ankwalin dake d'aure akan ta lokacin dazata shiga gidan. Ga wannan " ya mik'a musu wasu k'ullin magani da SUFURSUNARI yazo dashi. Yace "wannan Jan maganin ki tabbata Mijin ki yaci a abinci ko abun sha, sannan wannan bak'in kuma inaso kiyi girki ki had'a shi a ciki ,ki aikawa Amaryar. Wannan kenan ,na sallame Ku..." Mak'udan kud'i Kubra ta Ciro ta zube su a gaban boka RUBATSI, sannan suka kama hanyar komawa gida. B'angaren hajiyar Daddy kuma. Bayan sun kammala cin abinci da daddare ,tace "idan ka gama kazo d'aki inason ganin ka" ta fad'a tare da mik'ewa ta wuce gaba ,shi kuma daddy yana bin ta a baya, har suka shiga d'akin ta. Gefen gado ta zauna ,shi kuma ya samu guri a k'asa ya zauna. Hajiya ta kira sunan shi "Daddy!" Dan haka kowa ke kiran shi saboda sunan kakan shine yaci. D'agowa yayi cikin ladaba Ya amsa da "na'am Hajiya!" Ajiyan zuciya Hajiya ta sauke kafin ta soma masa magana cikin sigar lallashi "Daddy sanin kan ka ne ,duk uwa baza yi abunda ze cutar da 'ya'yan ta ba koda kuwa 'ya'yan shegu ne balle na sunnah. Hak'ik'a rayuwar gidan ka kullum dashi nake kwana arai ,kwatakwata Allah be baka matar azziki ba, kubra mata ce da sedai ace Allah ya kyauta kawai, to na gaji da d'abi'un ta ,Sam baza'a ci gaba da tafiya haka ba. Saboda haka na binciko maka wata 'yar azzikin daga 'ya'yan qawaye na. Na shirya komai ,har ma an d'aura auren Ku d'azu da ranannan. Fatar zaka karb'a wannan auren hannu bibbiyu?"... Darammm!!!Dasss!!! Gaban daddy yayi wani mummunan fad'uwa kamar an buga durom. Kasa cewa komai yayi se ma k'asa da yayi dakai. Lura da yana yin daya shiga Hajiya tayi. Tace "Daddy ko hakan me yi maka bane? Idan baka so base anje ko inaba se a warware auren ,tunda burin ka ka watsa min k'asa a ido, ka kuma nunawa duniya ban isa ba ,to ai shi kenan". Hajiya ta fad'a a fusace. Cikin nuna damuwa daddy yace " Hajia kiyi hak'uri ,dama kubra nake tunani ,kar taga kamar ba'ayi mata adalci ba, sannan kinsan yadda zaman namu yake" Jinjina kai Hajiya tayi kafin tace "Naji kuma nasan komai ,sannan ka kwantar da hankalin ka ,wannan auren na maka shine dan ka samu kwanciyar hankali da nutsuwa a gidan ka. Kubra kuma bata isa tayi maka abunda Allah be nufa akan ka ba ,saboda haka ,muna nan mun sa rok'on Allah, komai kuma ze zo da sauk'i ,albarka ta na tare dakai. Allah yasan ya wa abun albarka" "Ameen" daddy ya amsa. Kafin suka fara tsare-tsaren yadda komai ze kasance. A washe gari ,a ranar ne daddy ze koma ,kuma lallai lallai Hajiya tace sedai ya wuce da Amaryar shi, ba yadda ya iya haka ya amince Amarya kaltum ce a zaune taci ado ,ba lefi kuma tana da kyawun ta daidai misali daka ganta base an gaya maka kasan shuwa ce. Hajiya khairi itace mahaifiyar kaltum. Zaune suke tana gayawa kaltum yadda shirin su ze kasance "Kaltum kin dai ga yadda nasha bak'ar wahala na kuma b'ata naira kafin na samu auren nan naki ya tabbata ko? To ba bacci zaki je yi ba ,tun wuri ya kamata ki San me kike yi ki kuma San gidan da zaki shiga. Kin dai ji abunda malam ya gaya mana ,matar shi kanta hatsabibiyar mata ce ,idan ba munyi da gaske ba zata ma iya kad'o ki... Ungo wannan" ta mik'a mata wasu qullolin magani tare da wata laya. Tace "Wannan maganin ki tabbata dashi zaki rik'a masa girki ,wannan layar kuma a cikin filon da yake kwana akai anan zaki tsaga ki sake se ki d'inke da farin zare, daga nan magana ta k'are ,se na ji labari daga wajen ki." "Karki damu hajiyar kaltum ,kisa aranki anyi an gama komai ,be matar shi kad'ai ba hatta hajiyar shi se ta dawo k'ark'ashin iko na"...cewar kaltum da kwatakwata ma idan ka ganta bazaka ce tana magana ba ,zubin ta irin zubin salihan matan nan ne ,sedai masifar dake cikin kaltum ya fita girma ,ita da kanta tsoron shu'umancin ta take yi... Dariya suka fashe dashi tare da kashe hannu... Hajiyar kaltum ta dafa kaltum tare da cewa " nasan ki sarai kaltum. Barewa bazayi gudu d'an ta yayi rarrafe ba. Fatar Nasara 'ya ta"... Wani irin shu'umin murmushi kaltum tayi me k'ara wa fuskar ta kwarjini da haiba tare da lumshe manyan idanuwan ta ,tace "Nagode Hajiya ta"... MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [7/14, 6:32 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA BIYAR_ *_____________________* _GARIN SAKWKWATO_ _Tun kafin su k'araso, daddy yasa aka gyara d'aya daga cikin sassan dake gidan shi ,sashen dake tsakanin na kubra Dana shi ,nan yasa aka gyara wa Khaltum._ _Duk wani abunda ake buk'ata kama daga ,kayan d'aki Dana kitchen da duk wani abunda yasan ana zuba wa a d'akin amarya seda yasa aka zuba wa khaltum su, kaya masu kyau da tsada na zamani ,duk daddy yasa an zuba su a sashen Khaltum._ _Tun da aka wangale musu gate suka shigo ,khaltum ke santin gidan ,komai na gidan me tsari ne ,bata gasgata maganar hajiyar taba ,seda suka shiga harabar gidan anan ta gane wa idanuwan ta aljannar duniya._ _shiru ita dai ta kasa cewa komai. Bayan driver yayi parking ne ,daddy yace wa suxee_ "Yauwa Hajiya k'arama (sunan dayake kiran ta dashi kenan ,kasancewar sunan hajiyar shi ya saka mata). Kije ki nuna wa Antyn Ku sashen ta ,na gaya miki ai shine na tsakayi ko?" Suxee k'ara fad'ad'a murmushin dake fuskar ta tayi ,Dan ita tun lokacin da daddy ya sanar musu auren ,dad'i taji mishi sosai ta kuma taya shi murna ,Haseena ce dai ke aikin kumbure-kumburen ta ,da k'ananan maganganun ta ,a cewar ta ,suna fama da kubra ,shine za'a tashi a k'ara musu wani jangwam d'in. Seda suxee tayi da gaske ,sannan haseena ta sassauto. Amsa masa tayi da "To daddy"! Sannan ta kalli haseena tace " Haseena ke kuma kid'an taya mu d'aukan kayan zuwa ciki" Yatsine fuska haseena tayi ,kafin tace "Nifa Yaya suxee gaba d'aya na gama gajiya ne ,ga baba lawali nan kisa ya shiga muku dasu" tana gama fad'in haka ,anan tabar su ,tayi wuce war ta. Murmushi daddy yayi ,shida kanshi shakkar haseena yake yi ,Dan haseena badai masifa ba kam ,ita bata iya Abu da zuciya biyu ba ,ko ya maka dad'i ko karya maka ,idan gaskiya yazo zata fad'eta. Magana yawa baba lawali akan ya taya su suxee shiga da kayan ciki. Suxee ce ta fara yin gaba d'auke da jakar kayan Khaltum ,ita kuma tana biye da ita a baya sad'af sad'af kamar wacce tayi k'arya. Da talatu suka fara cin karo a sashen khaltum, gaishe su tayi sannan tace wa suxee "Hajiya k'arama Dama Alh ne yayi waya akan mu gyara wannan sashen za'ayi bak'i ,sannan yace daga yanzu ni zan ci gaba da kula da sashen". " good" suxee ta fad'a, kafin taci gaba da cewa "to bak'i dai gasu sun zo ,kuma ba masu tafiya bane ,masu zama ne insha Allah" a zuciyar khaltum kuwa cewa tayi zama daram-dam ma kuwa. Suxee nuna khaltum tayi tare da cewa "Talatu wannan da kike gani ba bak'uwa bace ,Amaryar daddy ce ,da fatar zaki yi mata biyayya kamar yadda kike wa sauran manyan gidan?"... Washe baki talatu tayi tana fad'in " Ah Ah! Kice Alh aure ya k'ara? To ubangiji Allah ya basu zaman lafiya." "Ameen " suxee da khaltum suka amsa dashi ,kafin ta mik'a wa talatu jakar kayan khaltum, tare da cewa "Anty Amarya muje ciki in nunna miki yadda gurin yake kafin in k'arasa cikin gida ko?" Ba musu khaltum tabi bayan ta ,talatu kuma na biye dasu a baya. Wani had'iyar yawu khaltum tayi lokacin da taga irin dukiyar da aka narka a sashen ta. Komai na garin me tsari ne. Babban parlour ne a k'asa Wanda ke zagaye da d'akuna uku kowanne da toilet d'in shi a ciki. kitchen had'e da store a ciki ,se dining area daga cikin parloun. Yadda k'asan yake haka saman yake sedai shi d'aki biyu ne ,da babban parlour. Komai a tsare yake gwanin ban sha'awa. Da murmushi shimfid'e akan fuskar suxee tace "To Anty Amaryar ,wannan shine b'angaren ki ,da fatar komai ya miki? Idan da akwai abunda kike buqata zaki iya sanar da talatu se ta fad'a mun " Wani guntun numfashi khaltum ta sauke ,kafin tace "Kar ki damu kanki suxee komai yayi ,nagode sosai da kulawar ki. " "Bakomai Anty Amarya kema ai yanzu kin shigo cikin mu. Ni zan wuce sashen mu" suxee ta fad'a tare da mik'ewa. "A huta gajiya. ki gaida mumyn taku Dan Allah kafin in shigo" khaltum ta fad'a kamar mutuniyar kirki "Zata ji insha Allah" suxee ta bata amsa sannan tayi ficewar ta... Sashen su ta nufa. Seda ta fara laqewa d'akin kubra taga bata nan ,sannan ta sauko k'asa zuwa d'akin su. Wanka haseena tayi sannan tawa Auta. Suxee ce ta shigo d'auke da sallama ,kan gado ta fad'a tare da fad'in "Wash Allah! Na gaji sosai. Haseena akwai ruwan zafi a hitan toilet kuwa naga kamar kunyi wanka?" "Eh akwai" haseena ta bata amsa a tak'aice ,Dan gaba d'aya haushin suxee take ji ,musamman data ga ta fiye zak'ewa akan auren da daddy ya k'ara. Kaya suxee ta cire ,ta fad'a wanka. Bayan ta fito ne ,tana cikin shirya take cewa haseena "kin shiga d'akin mummy kuwa?" D'an d'agowa haseena tayi tana duban ta lokacin tana had'awa Auta cornflakes ,maida duban ta tayi kan abunda take kafin tace "Banje ba! Da alama ma bata gidan nan." "Taya akayi kika gane, keda baki duba ba?" "Ji fa Yaya suxee, to ni a abubuwan mummy wanne ne ban Riga na gama karanta ba? Muddin kika shigo baki ji tashin sauti ba ,to karki ma wahalar da kanki da zuwa duba ta ,bata nan ne kawai. Mummy na nanne zata bari kunnuwan jama'a ya sarara?" Murmushi suxee tayi ,ko ba'a fad'a ba tasan gaskiya Haseena ta fad'i. Tace " Hakane kam. Bata ma nan Dan na duba". "Uhm" inji haseena alamar kan ki ake ji. Waya Haseena ta janyo tare da dialing wata number Dana ga ta saka 'MY HEADACHE'. Seda ya kusa tsinkewa sannan aka d'auka... "Kina ina?" Haseena ta tambaya. A mamaki ne muryan kubra naji ya daki speakern wayan. Kubra dake hotel tare da wani hamshak'in d'an siyasa suna aikata masha'an su ta amsa da "Ina gidan hajja Fati. Ya akayi kun dawo ne?" "Eh mun dawo ,Dan Allah ki dawo gida haka ,nace dai hajja Fatin nan koda yaushe kuna tare kamar cingom? To idan baki dawo Dan mu ba ,se ki dawo Dan kishiyar ki"!! A zaton Haseena ko fad'in hakan ze tashi hankalin kubra ne ,amma amamakin ta ,dariya taji kubran nayi tare da cewa "Cool down baby! Wacece kuma kishiya ,ban dawo Dan 'ya'ya naba, shine zan wani dawo Dan wata Abu wai kishiya? To ban gama abunda nake yi ba ,idan na gama ai zan dawo ko? Haseena tantama take anya ma kubra taji abunda ta fad'a kuwa? Sake maimaita mata tayi " mummy aure fa nace miki daddy ya k'ara shine kuma kike dariya?" "Nasani ai Haseena, ba abunda bansani ba akan auren shi ,da naso in hana bama za'a kai yanzu ba ,banda lokacin su ne kawai." Cewar kubra Haseena harta bud'e baki zata yi magana "Mummy! " kubra ta katse ta "Ke ni karki dame ni ,kisha fa mun kan Auta. Take care"... Bata jira jin me Haseenan zata k'ara ce mata ba ,ta yanke kiran. Misalin k'arfe takwas na dare ,kubra tabar hotel d'in cikin shirin ta na zuwa club ,a cewar ta akwai babban casu da za'ayi a _shisha palace_ ,Wanda bata ka wani dalili daze sa tayi missing ba... A b'angaren kubra kuwa ,abinci ta girka mai rai da lafiya iya k'warewar ta. Ta shirya komai akan dining sannan tayi dialing numbern daddy data rubuta wa _Alhaji na_, bugu d'aya biyu daddy ya d'auka. Cike da kissa kubra ke magana " Dadddy na gama girki ,ka gaya wa su Hajiya k'arama ko" Cike dajin dad'in yadda ta nuna damuwa da 'ya'yan shi yace "To zan fad'a musu ,zaki gan su" A shagwab'e tace "daddy to kai fa?" Yace "karki damu ,ni bana jin yunwa ,idan ma ina da buk'ata Hajiya k'arama ce me girki na ,da abincin ta k'adai na saba. " K'ara kashe murya tayi zatayi magana ,amma se jin tayi ya kashe wayan. Tsaki taja ,tare da fad'in "Can da yawar ka. Tukunna ma ,ba'a fara wasar ba ai". Daddy dase a lokacin yayi saving numbern khaltum, yana yanke kiran ya kira suxee dake kitchen ita da haseena suna shirya masa abinci, sheda mata yayi yadda yayi da khaltum ,tace " to daddy zamu je insha Allah " shine amsar data bashi sannan ta yanke kiran. Haseena ce ta dube ta ,tare da cewa "Keda waye kuma ?" Suxee tace "Daddy ne ,wai muje inji Anty Amarya ta gama mana abinci" Baki haseena ta tab'e tana fad'in "Ikon Allah. Wani iyayi ne wannan kuma? Da can kafin tazo wake dafa mana? Inace muke dafa wa kan mu?" Suxee da dama tasan za'ayi haka tace "Haba haseena daga abun azziki? Ina lefin ta?" Haseena tace "kinga ni ban hanaki zuwa ba ,nidai bazani ba ,se kije keda Auta. Auta dake tsakar kitchen d'in tana wasan ta ta karb'e da " nima baza niba Yaya suxee "... Suxee kad'ai taje taci abincin ta ta dawo. Satin kubra d'aya a gidan ,hankalin ta a kwance ,tana cin gashin kanta ,babban abunda ke damun ta shine ,daddy ko so d'aya be tab'a neman ta da mu'amalar aure ba. A Daren ranar ta shirya tsaf Dan tunkarar shi , A wannen Daren ne kuma kubra ta dawo, wacce kusan tun tafiyar su daddy ,bata gidan se yau Allah yayi dawowar ta... MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [7/14, 9:39 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA SHIDA_ *_____________________* _Kubra Kai tsaye sashen ta ta nufa. Da shigar sauti ta kunna sannan ,sannan ta shiga wanka. Kwalliya ta zauna ta tsantsara Wanda ya amshi kyaky-kyawar fuskar ta, doguwar Riga ta zuba ,Wanda ya amsa sunan shi ,gashi daka gani kai kace Dan ita akayi rigar... Wani abun se mata masu diri_ _Haseena najin kid'an na tashi ,dariyar takaici tayi ,Auta ce ta tambaye ta_ "Yaya haseena waye ya kun nawa mummy hoppers d'in ta?" Cike da takaici haseena tace "Waye kuwa ze kunna mata? Kakar d'an k'wairo ce ta dawo da kanta ,kyaji ma fiye da haka" Suxee dake fito wa daga toilet ,dariya maganar haseenan ya bata ,tace "Wllh ba kida kirki haseena! Mummyn ce ma kakar d'an k'wairo? A'ah kakar Baban gida kaka dawo ne ,shine ke tashe" "Ai tama wuce nan alqur'qn". Haseena ta bata amsa ita fuskar ta d'auke da dariya. A tare suke je duba ta ,Kafin sukai har auta ta riga su kaiwa. Cab'e ta kubra tayi fad'in " Auta ta takaina! Nayi kewar ki sosai." Tsuke baki auta tayi tare da cewa "Ni bakiyi kewa na ba ,inda haka ne shine zaki yi tafiya baki je dani ba? Ni sauke nima ,mun b'ata" ...Auta ta fad'a ciki da yarinta Murmushi kubra tayi tare da shafo gefen fuskar ta ,tace cikin sigar lallashi "Haba Auta ,yau kuma da mummy ake fad'a? To kiyi hak'uri ,ba gashi yanzu na dawo ba? " Sallamar su suxee ne ya katse ta. Gaishe ta sukayi a ladabce ,kafin suka samu guri suka zaune kan lallausan kushin d'in da yayi daidai da tsarin parloun. Suxee tace "mummy da kin gaya mana zaki dawo ai da se mu gyara miki waje ,ko musa a gyara" Wani uwar harara haseena ta banka mata tare da cewa "Meyasa kike bin son ran mummy ne Yaya suxee? Kafin kice haka me yasa bazaki fara tambayar ta inda taje ba harna tsawon sati d'aya. Kuma da izinin wa taje , nasan tabbas daddy be Sani ba." Alama suxee tayiwa haseena alamar ta rufe mata baki ,amma Haseena bata ji waji ba ,ta d'ora da "Ya ga gaskiya ga rantsuwa! Idan ma bazata dawo Dan kowa ba aise ta dawo Dan mu. Tsakanin mu da mahaifiyar mu ba wani shak'uwa ko jin k'ai ,se anyi magana tace tana son mu. Yanzu ki duba fa irin abunda sakacin ta ya janyo mata ,gashi nan daddy yaje ya k'aro aure ,kuma duk akan halayen ta ne. Sati d'aya da zuwan Anty khaltum kenan. Amma bata San mummy ba mummy bata San taba ,idan ta gane irin halin da muke ciki dake wallahi ba abunda zaki siya mana se wulaqanci, Wanda b zamu lamunce ba." Wata uwar tsawa suxee ta daka wa haseena "Enough haseena!!!" "Ank'i ayi enough d'in." Haseena ta maida mata a hasale ,sannan ta maida duban ta ga kubra tace "Idan baki gyara ma inaga an kawo wacce zata gyara ki ,idan kuma ita ma d'in ba'ayi dace ba ,ina add'uan allah ya kawo me canza ki da gaggawa. Ya kamata ki iya takun ki Dan girman Allah karki ja mana gori da gore-gore. Yanzu bamu kad'ai bane a gidan, na rok'e ki"... Haseena ta k'arasa maganan tare had'a hannayen ta biyu alamar rok'o. Tana kaiwa nan tayi ficewar ta. Suxee da kamar taci kanta ,kallon mummy take idon ta cike da hawaye tace " mummy kindai gani ko? Kin ga abunda son zuciyar ki yake nema yaja miki ko? Duba fa ,haseena 'yar cikin ki take tsaya wa a gaban ki ta gaggaya miki maganganu marasa dad'i, duk da akan gaskiyar ta take kuma duk abunda take fad'a nasani kum kema kinsan gaskiya ne. Dan Allah mummy... "Ke!ke!!! Malama dakata mun Dan Allah. " kubra ta katse suxee ,sannan taci gaba da cewa... "Naku a mene ku kuma? Rayuwa ta ko rayuwar Ku? Na hanaku kuma kuyi yadda kuke so ne? Se kune 'ya'yan ciki na zaku hanani sakata in wala? To baki isa ba, Wanda ya ajiye Ku ma yayi kad'an. Dan Allah matsa mun in wuce ,inje inyi abunda ze fish-she ni." Kubra ta fad'a kamar zata bangaje suxee. Anan tabar auta ta nufi sashen Daddy. Mamakin wani irin hali kubra keda shi ,ya hana suxee koda taku d'aya. A ranta take cewa "wato duk cin kashin mummy akaina ya k'are ,amma Haseena idan tana yi mata fad'a ko tari. To indai hakan ze sa ta gyara zan bar ta da Haseenan taji idan da dad'i. " Allah ya kyauta" shine abunda suxee ta furta a fili ,sannan ta kama hannun Auta suka sauko k'asa zuwa d'akin su. Kubra tafe take Cikin takun ta na k'asaita kamar wacce bata son taka k'asa a haka ta nufi sashen daddy... Khaltum ce zaune kan kushin d'in da ke cikin uwar d'akan daddy. Taci ado se zuba wani fitinannen k'amshi take, kai kace baza'a mutu ba. Tana jin an shigo parloun a cewar ta ko su suxee ne ,se kawai tayi maza maza ta haye kan gado ta kwanta ,a cewar ta ko da su Suxee idan daddy ya fito ya ganta akan gado ze hak'ura ya bata lokacin ta. Bata San daddy ya wuce nan ba indai akan 'ya'yan shine. Ganin ba kowa a parlour yasa kubra ta nufi bedroom d'in shi. Knocking ta fara yi Dan ta tabbatar ko yana ciki, shiru bata ji alamar akwai mutum ba ,sake knocking tayi ,cikin tsawa khaltum tace "Dallah wai waye ke damun mutane ne haka?" Duk da kubra bata San muryar wacece ba ,amma tasan baze wuce gurguntaccen auren da akace mata yayi ba. Bata yi magana ba ,se sake knocking d'in d'akin data yi. A fusace khaltum ta taso tana fad'in "Uban waye?" Tana bud'e k'ofar se jin k'arin mari kake yi "Tassss!!! TO MASU KARATU, DAN JIN WAYA MARI WANI A CIKIN SU ,SE KU BIYO NI A SHAFI NA GABA IDAN ALLAH YA KAIMU... MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [7/15, 2:49 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA BAKWAI_ *_____________________* _A take khaltum ta fara ganin wasu taurari na mata yawo tsabar gigitar data yi. Seda ta natsu hankalin ta ya dawo jikin ta ,sannan ta k'ara ware idanuwan ta Dan ganin me ya faru a yanzu_ _Das... Ta sauke idanuwan ta akan kubra ,dake sakar mata wani uban murmushi ,kamar ba itace ta wanke ta mari yanzu ba_ _"wow masha Allah "_ khaltum ta furta a ranta lokacin data yi tozali da kyawun kubra. " tabbas ke me kyau ce ,kin cika duk wasu qualities na mace daga waje bansani ba ko a cikin ba kamar wajen ne. Ko mak'iyan Allah yasan ke kyaky-kyawar gaske ce"... Khaltum ta saki fad'a cikin ranta. "Bani wuri in wuce 'yan mata". Kubra ta fad'a tare da kutsa kai cikin bedroom d'in. Da ido khaltum ke binta har ta samu wuri ta zauna akan d'aya daga cikin lallausun kushin d'in da ke d'akin. Tace " ya kika tsaya a tsaye khaltum keda d'akin mijin ki ? Kizo ki zauna mana" ,kubra tace wa khaltum tana me nuna mata wurin zama. Gaban khaltum ne ya shiga dukan uku-uku, lokacin da taji kubra ta kira sunan ta. Bata yi mamakin hakan ba ,dan tasan zata iya sanin sunan ta daga bakin mijin ta ko 'ya'yan ta. Jiki ba k'wari haka ta dinga taku kamar hawainiya, har ta k'araso ta zauna. Kubra zare gilashin dake idon ta tayi ,tare da ajiye shi a gefe. Sannan tace "Sannu da zuwa Amarya khaltum. Nasan baki sanni ba ,baki kuma tab'a gani na ba ko? Amma ai nasan dai idon ki yasan k'ima? Sunana kubra , Mata kuma uwar gidan MISBAHU." Wani irin shu'umin murmushi kubra tayi kafin taci gaba da cewa. "Inaso ki iya ,takun ki ,kar kiyi tunanin kinzo Dan ki mallaki gida na ne. Bari kiji ,auren ki ma da banso ba da kawo yanzu ya zama tarihi. Nasan duk wani shiri da kuke yi keda mahaifiyar ki ,zuwan Ku gurin malamin Jibiya ,irin kashe kud'in da kuka yi kafin kuka dace a naku, da irin abubuwan daya Baku na ganin kinzo kin juya mun gida, ke hatta yawon malamai da kuka yi kafin Ku dace duk a tafin hannu na yake." Dariyar gefen baki kubra tayi taci gaba da cewa "Wai ke Amarya ko? Sati d'aya kenan baki San miji ba be sanki ba. Wannan auren soyayya ne ko auren had'i ? To wannan duk yana cikin tsarin kubra. Bayan ke ma akwai wacce ko ince masu zuwa, ina nufin aure ze k'ara. Saboda haka ki iya takun ki ,ni bakya gaba na ,idan kuwa kika ce zaki shigo gona ta ,shakka babu zaki zama tarihi a doron k'asa. Nice kubra, _gidan Misbahu_ gida na ne, wannan kuma yanki na ne, inaso ki rik'e wannan." Har ta mik'e ,se kuma ta koma ta zauna tare da cewa "Am! Nace marin Dana miki ,karki d'auka ko Neman magana nazo yi, ke bakiyi matsayin da zan yi dake ba,hasalima kamar yadda na gaya miki bakya gaba na ,kuma karkiyi k'ok'arin shiga gona ta, ki tsaya a matsayin ki ,azziki dai kika zo dangwala ko? To u're highly wlcm. Na miki ne saboda gobe kisan yadda zakiyi magana da manya. Bana tunanin ni da yanki ne sena nemi izinin shiga. Me Abu ne da abun shi maganin akwab'e shi. Sannan maganan Amarci,,, Nina hana komai ya wakana a tsakanin ki ,saboda inaso ki d'an San koni wacece da kuma abunda zan iya aikatawa,,, amma yanzu Dana shigo na ganki se kuma kika bani tausayi ,saboda haka zan baki dama ,amma fa yau inason kisani duk wani shirin ki baze yi tasiri ba ,sedai ko zuwa gobe zan duba ingani ,idan kuma kina ganin kamar ba haka ba ,zaki iya jarabawa kika idan hak'arki zata cimma ruwa..." Fitowar daddy daga toilet ne yasa kubra tsagaitawa ,nufo shi tayi tare da rumgume shi tana fad'in "Nayi kewar ka sosai daddy" Shima daddy rumgume ta yayi cikin murnar ganin ta ,tare da cewa "Nima haka my wife" Janye ta daddy yayi daga jikin shi tare da cewa "My wife kiyi hak'uri ,nayi miki wani lefi ,nima badan inaso ba" Murmushin jin dad'i kubra tayi tare da nuna khaltum alamar akan wannan kake magana? Gyad'a mata kai yayi alamar eh. Bud'e baki daddy yayi zeyi magana kubra ta had'e bakin su waje d'aya, cikin k'warewa da salo take tsotsar bakin shi, a hankali ta zare bakin ta daga nashi tare da masa magana k'asa-k'asa kamar me rad'a "Daddy indai wannan ne karka damu, na Riga nasan komai akai" maida duban ta tayi inda khaltum ke daskare a zaune, kai kace an dasa karas ,,ko motsin kirki bata yi ,murmushin mugunta tayi mata ,sannan ta maida duban ta ga daddy tace "Inaga ka fara kimanta mata daga gobe ,bance kuma ya wuce iyaka ba". Godia daddy ya mata ,sannan ta nufi inda khaltum ke zaune, hugging d'in ta tayi ,tare da bubbuga bayan ta ,tana cewa " Asha amarci lafiya! Ina fatar zuwa yanzu kin gane kuyanga ko da an 'yanta ta bata isa ta kamo matsayin takalmin ban d'akin uwar gijiyar taba? Saboda haka ki kula"... Seda safe tayi musu sannan ta wuce abunta tana kwasar dariyar da ita kad'ai tasan ma'anar sa... Kusan ranar khaltum baccin bak'in ciki tayi ,Dan a iya gajeren tunanin ba kubra bata kai haka ba ,se yanzu take gasgata lallai ita d'in hatsabibiyar gaske ce. Tayi iya bakin k'ok'arin ta na ganin daddy ya kusance ta a wannan Daren sakamakon wani maganin mallaka data matsa, amma ina abun ya faskara ,a Dole ta hak'ura ta k'yale shi badan taso ba. Allah Allah take kawai gari ya waye ta kira mahaifiyar ta Hajiya khairi ,ta sanar mata komai... Dan iya tsorata khaltum ta tsorata da kubra, maganganun data gaya mata su kad'ai ke mata reto a dodon kunne... _Washe gari_... MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [7/16, 4:56 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA TAKWAS_ *_____________________* _Washe gari tunda sassafe Khaltum tabar sashen Daddy. Kai tsaye sashen ta ta nufa, wayar ta ta shiga daddubawa ,tunowa data yi ta kashe wayar tun jiya da daddare ta jefa ta a drawern gado yasa ta janyo drawern tare da d'auko wayan._ _Numbern mahaifiyar ta(Hajiya khairi) tayi dialing, har ta gama ringing ba'a d'aga, sake kira tayi a karo na biyu har ta kusa tsinkewa sannan Hajiya khairi ta d'aga ,da alama bacci ma take yi. Ko gaishe ta bata tsaya yi ba ,tsabar tarbiyya irin na khaltum base ta hau fad'a ba_ "Haba Hajiya, ke yanzu har kinga ta bacci ni ina nan cikin masifa? To bacci be ganshi ,matar daddy kwatakwata baza ta barni inji dad'in rayuwar aure na ba, sannan wallahi duk yadda kike tunanin hatsabibancin ta to ta wuce nan"... Nan khaltum ta sheda wa Hajiya khairi duk yadda suka da kubra a Daren jiya, hatta rashin kusantar ta da Daddy beyi ba seda ta rattafa mata. Hak'uri Hajiya khairi ta bata ,tare da kwantar mata da hankali, sannan ta tabbatar mata ,zata kira malam Jibiya ta sanar dashi halin da ake ciki, Wanda se a lokacin khaltum taji ta fara samun natsuwa, da haka sukayi sallama akan zata kira ta da yamma taji yadda sukayi... A b'angaren kubra kuwa, misalin k'arfe Tara ta tashi ,wanka tayi ta shirya sannan ta fito ,lokacin su suxee na kitchen suna shirya breakfast, kota kan su bata bi ba kawai ta fice abunta ... Sashen Daddy ta nufa ,a lokacin yana cikin shirin tafiya kano ,sakamakon kiran gaggawan da Hajiya Gwaggo(mahaifiyar Baban shi. Kakar shi kenan) tayi masa. Kyau iya kyau daddy kyaky-kyawan gaske ne ,duk macen data kalle shi babu kissa tasan ya had'u ,ya kuma cika duk wani sharud'd'a da tsari na jarumin namiji tsaye dakyau zaune dakyau. Wata bugaggiyar gizna Shadda ce sanye a jikin shi kalar ruwan ganye ,Wanda taji aikin wuta daga tsakiya ,d'inkin two buttons ne tazarce ,hular kanshi kalar shaddar dake jikin shice ,me ratsen brown daga tsakiya ,ba kad'an ba shigar ta amshi jikin shi. Agogon hannu ya d'aura bak'i a tsintsiyar hannun shi na hagu ,sannan ta taje sajen da ke zagaye da fuskar shi Wanda ya had'e da d'an madaidaicin gemun shi bak'i sid'if. Gilashin idon shi se yayi kala da hadarin damuna, takalmin k'afar shi black cover ne Wanda yaji Polish me walk'iya, a tak'aice dai Wanka yabi jiki musamman gashi fari , faffad'a ga tsawo ga zati... Gaban madubin bedroom d'in shi ya tsaye ,yana feshe jikin shi da turaruka masu matuqar k'amshi da tsada. Wallet d'in shi da wayoyin shi ya kwasa tare da saka wa a aljihu. Murd'o k'ofar d'akin da akayi yasa ya maida duban shi gun k'ofar Dan ganin waye me shigo wa... Kubra ya gani ,tun daga nisa ya fara sakar mata murmushi, itama maida mishi tayi ,Dan ba kad'an ba taji yayi masifar burge ta... Gaishe shi tayi kamar da gaske ,ya amsa mata fuskar shi a sake ,tare da tambayar yadda ta kwana. "Daddy wannan kyalliyar haka se ina kuma?" Kubra ta tambaye shi kamar bata masa bin k'wak'waf. Murmushi Daddy yayi tare da cewa "Kaji ki wai kwalliya, ina wani kwalliya anan? Tafiya fama zanyi zuwa kano, Hajiya Gwaggo ce ke nema na, so I think ma k'ila inyi kwana d'aya ko biyu"... " Dama ka dena wahalar da kan ka da yimun bayani ,babu wani Abu da zakayi Wanda bansani ba dahar nake Neman k'arin bayani" kubra ta furta aranta ,a fili kuma tace "Ohkkk! Anyway! Ni daman kud'in hannuna ne ya k'are shiyasa nace bari inji ko zan samu chicken change a wajen ka" ,ta fad'a cike da gadara ,kamar irin ta bashi ajiyar nan. Ajiyar zuciya daddy ya sauke ,sannan yace "Ba damuwa zan miki transfer". " OK to" shine amsar da kubra ta bashi sannan tayi ficewar ta. Shima daddy be wani b'ata lokaci ba sanin da yayi su suxee nacan na jiran shi suyi breakfast, gashi flight d'in k'arfe sha d'aya na safe ze bi. Sashen kubra ya nufa , ta parloun k'asa yabi ,koda ya shiga a zazzaune ya same su , alamar shi suke jira. Tun kafin ya k'araso yake annashuwan ganin su ,suma cikin tsananin k'auna suka gaishe shi ,fuska a sake ya amsa ,sannan ya samu guri ya zauna , cikin farin ciki suka cin abincin su ,bayan sun gama yake sanar dasu tafiyar daze yi ,Addu'a sosai yaran suka mishi ,yaji dad'i har cikin ranshi. A tare suka nufi sashen shi ya d'auko jakar shi ,sannan suka fito zuwa parking space ,rakiya suka masa har airport ,seda jirgin shi ya tashi sannan driver ya dawo dasu gida. A garden suka yada zango har Auta se hira sauke abun su gwanin sha'awa ,suna nan suka hango wuce war motan kubra. Tab'e baki Haseena tayi ,a ranta tace "kifi jirgi gudu ,ruwa izo hadda matuk'a jirgi" a fili kuma tace "Duba kiga mummy Yaya suxee daddy na fita itama ta fice" Murmushin takaici suxee tayi tare da cewa "Hmm Haseena kenan! To Allah na tuba mummy ko daddy na nan tana fasa fita ne? Ai sema abunda yayi gaba. Ki duba lokacin dayayi rashin lafiyan hawan jini ,kamar daddy baze yi rai ba ,amma a ranar me kika ga tayi ,Dubai fa ta wuce wajen birthday d'in k'awarta, kuma ita ta shirya komai. Tunda mummy bata zauna a wancan lokacin da daddy yafi buqatar taba ,to banga dalilin daze sata ta zauna ba"... " hakane kuma fa! Allah dai ya kyauta " haseena ta fad'a cike da takaici... Suna nan suna hira, khaltum ta fito kamar wata gigitacciya ,se waige waige take kamar me Neman wani Abu... Kamar ance ta duba ta garden ta hango su suxee zaune kan lilo ,da gudu ta k'araso wajen tana tambayar daddy fa? A lokacin suxee waya take yi dan haka bata lura da ita ba, Haseena kuma yi tayi kamar bata ma San da ita ba "Ba tambayar Ku nake ba? Ina ubqn Ku? " cike da mamaki suxee tace "Haba Anty Amarya, ina uban mu kuma? Ina lefin kice mana ina daddy? To bayanan yayi tafiya" Wani gigitaccen mari suxee taji khaltum ta d'auke ta dashi. Aiko kamar daga sama ,itama khaltum d'in taji an wanke ta da mari...A hasale haseena ta furta "Ke har kin isa?"... Tofa! Jama'a Dan jin meke shirin kunno kai ,se kuci gaba da bibiyar wannan k'ayataccen labarin... MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [7/17, 7:33 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA TARA_ *_____________________* Tsabar a rud'e khaltum take bata ko bi takan Marin da haseena ta sharara mata ba. Had'a hannaye biyu tayi alamar pleading tana cewa "Dan Allah Ku gayamun ina daddyn Ku yake?" Da mamaki suke binta da ido "na rok'e Ku Ku gayamun" khaltum ta sake maimaitawa. "K'arya kike nufin zamu miki? To bayanan ,yanzu haka yana cikin kano" haseena ta bata amsa a d'an tsawace... Ihu khaltum ta fasa ,da gudu ta koma cikin gida. Tana shiga d'akin ta ta fara Neman waya ,Hajiya khairi ta danna wa Kira ,daga b'angaren Hajiya khairi kuwa tana d'aga wa tambayar ta tayi "khaltum Yaya?" "Wallahi Hajiya ban same shi ba ,na tambayi yaran shi ,sunce wai ya tafi kano ,gashi a jirgi ya tafi ,zancen Dana ke miki ma yanzu haka yana kano"... Khaltum ta fad'a cike da tashin hankali. " Aiko an yanka ta tashi ,Dan malam ya tabbatar mun lallai duk yadda za'ayi a hana shi tafiyan nan ,idan kuwa ya tafi to labari ze sauya" cewar Hajiya khairi ,ta fad'a cike da takaici Cikin tsananin tashin hankali khaltum tace "to yanzu Hajiya ya za'ayi kenan? Sannan me malam ya fad'a miki ze faru idan daddy yakai kano" khaltum ta tambaya Hajiya khairi tace" gaskiya be sanar dani ba ,a iya dube duben shi kuma ,k'asa bata bashi izinin sanin meze faru ba ,amma lallai ya tabbatar mun da akwai matsala, Wanda har idan bamu yi da gaske ba ,matsalar ze iya zama sanadiyyar auren ki" Hannu khaltum ta d'ora akai tana fad'in "na shiga uku Hajiya ,meke shirin faruwa dani?" Cikin lallashi Hajiya khairi tace "ki kwantar da hankalin ki ,yanzu abunda nake buqata dake shine ,duk yadda za'ayi ki samo kud'i yau d'in nan ba se gobe ba ki turomin, ni kuma zan wuce Jibiya ,insakar wa malam kud'i Dan yaji dad'in baza mana aiki"... Cikin sassark'ewar murya khaltum tace " To...to.. Shi kenan yanzu base anjima ba ,zan turo da kud'in ,Dan Allah Hajiya ayi duk wani abunda ya kamata!" "Karki damu gudan jini ta, sena jiki". Khaltum na ajiye wayar ,sashen Daddy ta nufa ,dube dube ta farayi ta inda zata ga kud'i, aikuwa kamar ance ta bud'e drawer ,se ga kud'i ta gani ,ta kuma yi sa'a be saka key ba ,bata wani b'ata lokaci ba ,ta fara jidan kud'in, kud'i khaltum ta iba ,ba nida kud'i ba ,Dan ko ita kanta bazata ce ga adadin abunda ta d'auka ba. Sashen ta ta koma, ta shirya kud'in a wata madaidaiciyar jaka, sannan ta yafa mayafi ,tare da d'aukan makullin motan da daddy ya bata shekaran jiya ,A gigice taja motan ,tabar haraban gidan... Su dai su suxee ikon Allah ne ya hana su magana ,dak'yar suxee ta bud'e baki ta iya cewa " ita kuwa Anty Amarya meke damun ta ne yau?" "Me kuwa yake damun ta? In banda shashanci ,keda kin gani kinsan ai wata katamarmarar take k'ullawa, kuma da ikon Allah kan ta ze k'are".. Haseena ta fad'a tana wani yatsina fuska " To Allah ya sawwaqe!" Inji suxee. Sun d'an jima suna tattauna lamarin kafin daga baya ,suka koma cikin gida. Wuraren bayan magrib ,kubra ta dawo ,a daidai lokacin da khaltum ke shigowa itama. A tare sukayi parking ,kubra ta ce ta fara fitowa ,kafin khaltum ta bud'e marfin motar ta ,sedai bata kai ga fitowa ba. Tsaya wa kubra tayi ta k'are wa khaltum kallo ,sannan ta wani irin fashewa da dariya ,k'arasowa kubran tayi har inda khaltum tayi parking d'in motar ta. "Khaltum kenan" kubra ta kira sunan ta ,wanda yasa khaltum d'agowa a d'an tsorace. Kubra tace "da zaki dena wahalar da kanki da kin sauqaqa wa rayuwar ki ki kuma hutar da zuciyar ki, ni banga abun d'aga hankali ba. Nasan duk iya k'warewar malamin ki da iya binciken shi baze tab'a gano miki meke shirin faruwa ba ,to base kin bama kanki wahala ba wajen tunanin meze faru, ni da kinyi shawara dani ma base kin yi wahalar turawa da kud'in kiba. Daddy dai kamar yadda na tab'a gaya miki ze k'ara aure kul bad'ad'e kul bajima ,to lokacin ne yazo ,aure ba fashi , ke baki isa ki hana wannan auren ba, idan kuma kinji zaki iya to ga hanya nan. Ke duk ni fa da hatsabibanci na to wacce za'a kawo ta yaga wa tunani na. Kuma kamar yadda aka gaya miki muddin bakiyi da gaske ba ,auren ta kamar k'arewar auren kine a gidan nan. Cikin tsananin tashin hankali khaltum ta fito a mota ,rirrik'e kubra tayi tare da fad'in "Dan Allah kubra ki gaya mun to yanzu menene mafita? Wallahi na sadu da ,nabi Allah na biki" Sake fashewa da wani dariyan kubra tayi tare da cewa "Haba da wuri haka? Aina d'auka bazaki iya zubarda makaman yak'in ki cikin sauqi haka ba? Ke Nifa da nice ke ,tun farko bazan tsaya b'ata wa kaina lokaci ba ,mantawa zanyi da komai da kowa , Neman gindin zama kawai zan yi, amma da kika shigo ,se kike k'ok'arin shiga gonar daba naki ba" Wani irin marayan kuka khaltum ta saki ,tana fad'in "Dan Allah kiyi hak'uri, wallahi bansan abun haka yake ba ,amma da zaki bani dama se mu had'a kai". " kar ki damu " inji kubra "kije ki saurare ni zuwa anjima ,na dad'e da gane ke 'yar hannu ce ,na barki ne ki gama guje-gujen ki dawo hannuna." Kubra ta fad'a cike da salo tana wani kashewa khaltum ido d'aya. Wani irin dad'i ne ya mamaye khaltum ,godiya tayi wa kubra kafin sukayi sallama akan cewar kubran zata kawo mata ziyara anjima. Misalin Tara na dare ,kubra ta gama shirin ta tsaf na zuwa sashen khaltum. Cikin wasu mayatattun kayan bacci ta shirya ,se baza k'amshi take yi ,kai tsaye ta nufi sashen khaltum d'in. Knocking tayi mata ,tazo ta bud'e, sedai ita sab'anin kubra ,Dan kuwa hijabi ne a jikin ta tun daga sama har k'asa. Kallo kubra ta bita dashi tare da cewa "Menene wannan?" Tana wani nuna hijabin jikin khaltum d'in. Wani shu'umin murmushi khaltum d'in tayi irin nasu na k'wararrun 'yan bariki, sannan ta mata alama da ido ,akan ta k'araso ciki mana... Kubra na shiga khaltum ta maida k'ofar ta datse tare da saka ki ,kallon juna suka shiga yi ido cikin ido, sun d'au kamar mintuna 5- 10 ,kafin daga bisani khaltum ta zare hijabin jikin ta. "Wowww!" Kubra ta furta lokacin da tayi tozali da kyaky-kyawar surar khaltum, musamman boobs d'in ta da suka a tsaye k'am kamar zasu tsole mata ita. Cike da k'warewa kubra ta taso ta nufo khaltum, taku take d'aid'ai har ta k'araso gaban ta ,nan fa ta fara gogan ta ,tana shinshinar ta ,kan kace me sun fara fita a hayyacin su ,dak'yar suka kai Kansu d'aki ,anan fa suka baje haja, harka in ba kayi bani wuri... MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [7/18, 1:45 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA GOMA_ *_____________________* _Tun daga wannan rana kubra da khaltum suke jone ,komai tare suke yi ,duk kuma wasu wa'ani na shashanci da kubra ke zuwa yanzu su biyo suke zuwa ,idan ka gan su a zaune suna hira suna kashe hannu kai kace Yaya da qanwa ne ,ko wasu aminan juna. Sosai kubra ta take wa khaltum kan maciji ,ita kuma se wasa da wutsiyar take yi, a cewar khaltum bata tab'a sanin haka jin dad'in duniya yake ba se da ta had'u da kubra ,da can haukan banza take yi tana nema tayiwa kanta tsiya._ _Y'ar kulawar da daddy ke samu a wajen khaltum gaba d'aya yanzu ta tattara ta dena ,ita dama uwar gayya ba'a maganar ta ,Dan ita igiyoyin auren ne kawai a kanta ba wai auren ba. Wata k'urar ce ta taso Dan kuwa gaba d'aya suka had'ewa daddy da yaran shi kai, lamarin ba k'aramin d'aure daddy da 'ya'yan shi kai yayi ba. Ga uban asiri da suke banka mishi k'wak'walwan shi kamar ze buga wasu lokuttan ,Dan akwai lokacin da idan yana zaune ,matuqar kubra zata murd'a wannan kambun ,to fa beda sukuni ,yadda kasan ana yak'i akan sa haka yake ji ,gefe d'aya kuma ga k'unar zuci..._ _Sha'anin kubra baya wani damun shi akan na khaltum Dan ita inda sabo ya saba. Amma khaltum dika-dika yaushe tazo gidan ,a yadda tazo kuma da yanayin ta ko ance masa zata rikid'e ta canza kala baze tab'a yadda ba. Ba abunda yafi tunawa irin idan yace baya da ra'ayin kwanciya da ita a wasu lokuttan ,se ta mayance ,ta nace ,ta kuma dage ,wata sa'in Dan dole badan yaso ba haka yake biye mata har seta gamsu ,bama wannan ba ,idan ya fita kafin ya dawo ta gyara masa bedroom, an girka masa abinci ,ana jiran dawowar shi,,,Sam daddy ya kasa yadda dawai khaltum ce ta koma haka..._ _Gaba d'aya ya rasa yadda zeyi da ruwar shi ,abubuwa sun taru sun tsaya mishi akai ,ganin suna nema su kassara shi yasa ya yanke shawaran kwashe yaran shi ya tafi kano nad'an wani lokaci ko ze samu kwanciyar hankali, a wannan karan kuma yaci alwashin karb'an auren da Hajiya Gwaggo ta nema masa hannu bibbiyu. Wannan duk fa a ranshi yake sak'awa._ _A ranar da yake ta shirye-shiryen tafiya. Sashen kubra ya shigo ,ganin be ga su suxee ba yasa ya haura sama ,ba abunda ke tashi se k'arar sauti ,kamar parloun ze tsage. Tambayar su yake yi ina su suxee? Amma ba wacce ta tanka shi, daga k'arshe ma khaltum tsaki taja ,sannan taci Gaba da cashewar ta. Suxee kamar tasan dama ze zo Neman ta ,sashen ta nufo shi kuma lokacin daddy na saukowa ,Duk lokacin da suxee zata ci karo da Daddy se kariyar zuciya tazo mata ,gaba d'aya ya lalace ya rame ,yadda kasan wani mahaukaci ,har takai ta kawo yana tafe yana 'yan sambatu shi kad'ai._ Murmushi ta sakar masa a lokaci d'aya hawaye ya taru mata a ido. "U-um! Wannan hawayen fa Hajiya k'arama?" Daddy ta tambaye ta tare da maida kanshi gefe yana goge hawayen tausayin 'yar sa. Hannun ta ya janyo ta matso daf dashi ,kan ta ya d'aga sama tare da kiran sunan ta "Hajiya k'arama!" A maimakon yaga ta amsa se kawai ta fashe da wani irin kuka me tsuma zuciyar me sauraro. Haseena dake gefe Wanda fitowar ta kenan tagan su a tsaye ,itama kukan take yi. Hango ta da daddy yayi yasa ,ya goge hawayen shi ,itama suxee ya share mata nata ,sannan yace "Duba ki gani amma dai munyi girman kawai! Ji fa itama ga haseena can kukan take saboda ta gan mu muna kuka. To ya isa haka ,muje Ku gama shirya kayan Ku ,Dan gobe ne tafiyar mu insha Allahu." Murmushin k'arfin hali ya mata ,ita ma ta k'ak'aro ta maida masa ,a haka suka k'arasa sashen shi, yana k'arasowa inda haseena take tsaye ,hannu yasa ita ma ya mak'alo kafad'an ta ,a haka suka k'arasa ciki... Wunin ranar Daddy da yaran shi a sashen shi suka wuni ,da daddare misalin k'arfe 10 suka ji k'arar sauti na tashi ,wannan karon ba'a sashen kubra kawai bane ,a gidan ne duka. K'arar sautin yayi yawa Wanda har ze iya hana mutum bacci, wannan ne yasa suxee da haseena fitowa Dan ganin meke faruwa. Gidan cike yake cindim da mutane maza da mata ,ga motoci nan na gayu an pappaka yadda kasan club. A haka har suka k'araso inda Mutanen suke. Haseena ce tayi k'arfin halin tambayar wasu data gani d'an nisa dasu. "Dan Allah taron me ake yi ne haka?" ...shiru ba Wanda ya amsa ta ,maimaita tambayar ta sake yi nan ma ba Wanda ya amsa ta ,d'aga idon da zata yi base ganin kubra da khaltum tayi ba akan stage ,sun sha mayen kyau ,suna kissing d'in juna ,ga kayan shaye-shaye nan a gaban su an jera kamar baza'a mutu ba. Cikin tsananin tashin hankali ta waigo ,se jin tayi taci karo da mutum ,wani razana ta k'ara yi ,koda ta juya ba se ganin tayi wasu gayu a tsaitsaye akan ta ba ,mammatso ta suke yi tana matsawa baya a haka har taji ta matse ta wata mota dake bayan ta. Kuka take yi ,tana fadin "Me nayi muku? Let me go please!" Suxee na hango haka ta nufo su da sauri ,dukan su tashi ga ta baya iya k'arfin ta tana fad'in "let mah sister go please, please ah beg of u!" Amma a mamakin ta ko gezau. D'ayan ne yakai hannu yana Shafa gefen fuskar Haseena ,tare da cewa "So cute and sexy" Wani uban ihu haseena tayi ,Wanda yayi daidai da fitowar daddy ,Dan shi ko kad'an be San sun fito ba ,da baze barsu ba ,a guje yake yafe ,musamman da yake cin karo da wasu gurb'atattun mutane a gidan ,kai ko ba'a fad'a maka ba kasan wa'yan nan Mutanen bana gari bane. Ihu haseena keyi ba k'ak'k'autawa ,a lokaci d'aya suxee na ihun kiran sunan shi "Daddy!!!Daddy!!!" Cikin tsananin tashin hankali da kid'ime wa daddy yake tafe yana waige waige ,ko ze gane ta inda ihun ke fitowa... Abunda ya gane wa idon shi yasa yayi mutuwar tsaye ,a lokaci d'aya numfashin shi da bugun Zuciyar shi suka tsaya cak... MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [7/18, 10:21 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA GOMA SHA D'AYA_ *_______________________* _Wani irin mututwar zuciya ce ce tazo wa daddy lokacin daya ga wani gaye na k'ok'arin yiwa haseena fyad'e ,a gefe d'aya kuma ga suxee a hannu wani ya damk'e ta. Wani irin kuzari da jarumta daddy ya tattaro had'id'a duk wani k'arfi daya San Allah ya bashi ,Wanda shi kanshi be San dashi ba ,wani tuma yayi ya daka tsalle se akan gayen nan dake k'ok'arin ciwa haseena zarafi ,fyad'a guda daddy ya masa seda ya sumar dashi ,d'ayan gayen dake rik'e da suxee na ganin haka ,ba shiri ya sake ta ,ya ari na kare ,da gudu daddy ya tattaro 'ya'yan shi dake ta faman kukan wahala ,duk jikin su Yaya jawur abun ka da farar fata._ _Ciki ya shige dasu ,se faman lallashin su yake yi. Daddy kasa barin garin Allah ya waye yayi ,cikin Daren ya tattara 'ya'yan shi da kayan su sukar bar gidan, suxee ce ta shiga gidan baya tare da Auta dake ta faman sharar bacci hankalin ta kwance, haseena kuma ta shiga gidan gaba. Daddy tunani ya farayi ,ina ze nufa? Har yayi tunanin ko su wuce hotel ,se kuma ya tuna da gidan Aminin shi haji jamil, har ya d'au hanyar KARAMCI HOTEL ,se kuma ya karya kwana zuwa GUIWA LOWCOST, Wanda acan Haji jamil ke zaune._ _Yana isa k'ofar gate d'in gidan ,ya kira shi a waya ,tare da sheda masa zuwan sa. Hankalin Hajj Jamil idan yayi dubu ya tashi ,musamman daya duba ogogon bango ,yaga kusan sha biyu saura na dare ,shi kanshi har ya rufe gida ,wani d'an aiki ne ya hana shi bacci ,shi kanshi da tuni ya dad'e dakai Lagos. Yanayin muryan Daddy ya k'ara tabbatar masa da akwai matsala ,Dan haka be wani b'ata lokaci ba ,jallabiya kawai ya zura wa jikin shi tare da d'aukan makullan gida ,ya fito._ _Seda yad'anyi tafiya kamar na rabin kilo meter kafin ya kawo bakin gate d'in. Addu'a yayi tare da bud'e K'aramar k'ofa . Fitillun mota daddy ya hasko masa ,alamar ya bud'e masa gate ,maida k'ofar yayi ya rufe sannan ya saka makullin babban kwad'on gate d'in. Yana aniyar bud'e wa ne ,me gadin shi yayi firgigit ya fito hannun shi d'auke da gora da adda, hasken toci ya dannawa hajj Jamil a ido ,kan kace me har ya mamaye shi yana aniyar rafka masa gora a tsakaiyar baya. Seda Hajj Jamil ya daka masa wata uwar tsawa ,sannan ya shiga taitayin shi._ "Dan Allah kayi hak'uri Alhaji ,wallahi ban gane kai bane ,saboda nasan abune me wuya ka fito tsakar dare haka ,muddin ba tafiya kayi ba". Cewar Tukur me gadi. Wani siririn ajiyar zuciya Hajj Jamil ya sauke kafin yace " Ba komai ,nasan ai baka gane waye ba, nima dole ce ta fito dani"... Cike da nuna damuwa Tukur me gadi yace "to amma Alhaji lafiya kuwa ka fito cikin Daren nan ,kuma baka tashe ni ba?" "Kar ka damu lafiya qlau Tukur ,Bak'i nayi ne ,kuma tafiyar dare sukayi shine suka mun waya sun iso" Hajj Jamil ya bashi amsa. Daga nan ya maida hankalin shi wajen bud'e gate d'in. Shidai Tukur hankalin shi be kyauta ba seda yaga shigowar su daddy ,Hajj Jamil ya maida gate d'in ya rufe tare da yin Addu'a sannan ya koma d'aki. Fuska a sake Hajj Jamil ya tari Daddy ,se anan take gaya masa tare dasu Haseena yake. Marfin motan gaba Hajj Jamil ya bud'e ,a lokaci d'aya kuma suxee ta bud'e marfin baya ta fito. Nan take Hajj Jamil ya d'aga waya ya kira Hajar ,Dan yasan ita kad'ai ce bata isa bacci ba a wannan lokacin kasancewar ta ma'abociya karatun alqur'ani da sallar dare ,bata runtsawa se ta tabbatar tayi raka'atanul fajr ,ta kuma jira an tada sallan asuba tayi ,sannan bata tashi a inda take har se ta tabbatar rana ta hudo sannan take samun yin bacci ,shima ba wani isash-she ba ,saboda aikace-aikacen gida... Bugu d'aya biyu ,ta d'auki wayan tare da yin sallama ,cikin siririyar muryatta be matuqar dad'in sauraro. Amsa sallamar yayi tare da cewa "Haajar ki zo ki shiga da bak'i a haraba!" "Tohm gani nan zuwa insha Allah!" Ta fad'a tare da mik'e wa ,dama akwai Baban hijabi a jikin ta har k'asa. Tafe take tana d'an rare karatun alqur'qni k'asa-k'asa ,a haka har ta k'araso inda suke a tsaye. D'an gurfa nawa tayi ta gaida Daddy a nitse ,kafin ta mik'a wa suxee hannu tare da yi mata sallama suka gaisa ,haka da haseena ma. Duk da irin tashin hankalin da daddy ke ciki ,be hana yaji Haajar ta burge shi ba. "Ki shiga dasu ciki!" Cewar Hajj Jamil. Daddy ne ya bud'e mota ,ya d'auko Auta ,da sauri hajar ta k'araso ta karb'e ta a hannun shi. Sannan ta maida duban ta gun su suxee tace "Sisters muje ko?" Jiki a sab'ule suka rufa mata baya ,har suka k'arasa ciki. Seda suka tafi sannan hajj Jamil ya maida duban shi wajen Daddy tare da cewa "Daddy mu k'arasa ciki muma ko?" A tare suka shiga sashen Hajj Jamil ,kasancewar me d'akin shi Hajiya zaliha tayi tafiya. Hajj Jamil beyi k'ok'arin tambayar Daddy meke faruwa ba ,seda ya kawo masa lemu me sanyi yasha ya sarara ,sannan yake tambayar sa "Daddy wai meya ke faruwa ne haka ,ka kwaso 'ya'ya cikin Daren nan ,kuma daga gani ma yaran suma ba'a hayyacin su suke ba?" Wani guntun ajiyan zuciya daddy ya sauke sannan ya fara zayyanawa Hajj Jamil duk abunda yake faruwa ,daga auren khaltum ,zuwa had'e masa kai da suka yi ,har kawo abunda ya faru a Daren yau d'in... Cikin tsananin tashin hankali ,da rud'ani hajj Jamil ya dafe kai tare da furta "Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un. Hasbunallahu wani'imal wakil"... A Daren ranar kusan daga Daddy har Hajj Jamil basu iya runtsawa ba ,jamamin lamarin suka kwana suna yi... MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [7/19, 3:43 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA GOMA SHA BIYU_ *_________________________* _Sai wuraren asuba su daddy suka samu damar runtsawa ,ko kiran sallan da akayi daga shi har Hajj Jamil ba Wanda yaji. A b'angaren Haajar kuwa ,har ta tashi su suxee ,ganin ana k'ok'arin tada sallah su Daddy basu fito ba yasa ta kira Hajj Jamil a waya. Har wayan ya gama ringin be d'aga ba, mamaki ne ya kamata ,cikin ranta take cewa "yau kuma wani irin nauyin bacci Abbu samir yayi" (haka take kiran shi ,Wanda suna ne na alkunyar d'an shi na farko). Sake kiran wayar tayi a karo na biyu ,nan ma ba'a d'aga ba, ganin lokaci na k'urewa yasa ta fito zuwa sashen shi. Batayi tunanin ganin kowa a parloun ba ,Dan haka kawai ta murd'a handle d'in ta shiga bakin ta d'auke da sallama, se ta kunne bulb d'in parlourn (wato haske), A mamakin ta se ganin su tayi kwakw-kwance akan kushin da alama hira suke bacci ya kwashe su ,kuma daka ga yanayin baccin kai kasan basu San suna yi ba, baran ma daddy da k'afar shi d'aya ke kan kushin d'in, d'aya kuma a k'asa, shi kuwa Hajj Jamil ga system nan a gaban shi se aiki take ita kad'ai ,kan shi jingine da kujera._ _Tunanin yadda zata fara tashin su tayi ,Dan haka kawai se ta yanke shawaran bubbuga k'ofa, shiru ba Wanda ya motsa. Jin kamar za'a tada sallah ,gashi bata so suyi asarar jam'i yasa ta k'araso da sauri ta shiga tashin su. Hajj Jamil ta fara tadawa ,sannan ta bubbugi k'afar Daddy "Abbu samir Ku tashi lokacin sallah ya fara k'urewa" ta fad'a cikin siririyar muryar ta. Ba shiri daddy ya mik'e ,kafin Hajj Jamil shima ya wats-tsake ,wani dogon mik'a yayi tare da salati ,ganin sun tashi yasa tabar sashen zuwa nasu sashen. A gaggauce su Daddy sukayi alwalla ,suka fita zuwa masallaci, koda suka fita tukur na jiran fitowar su , a tare suka k'arasa masallacin. _Haajar koda ta koma taradda su suxee tayi har sun fara sallah, ita ma gabatar da nata sallan tayi ,seda ta kammala ta Shafa Addu'a, sannan ta dubi suxee data lura kamar itace babban, murmushi ta sakar mata tare da cewa "Kun tashi lafiya sisters?" Suxee Murmushin itama ta maida mata ,tare da amsa gaisuwar "Lafiya qlau sister. Ya gajiya?" "Gajiya ai se Ku masu tafiya" Haajar ta fad'a fuska a sake. Haseena ma gaishe su tayi kafin ta koma ta kwanta. Haajar maida duban ta tayi gun suxee tace "Sedai sister bansan sunayen Ku ba?" Murmushi suxee tayi tare da cewa "Sunana Suwaiba ,amma ana kira na da suxee ,Baba na kuma na kira na Hajiya k'arama ,saboda sunan mahaifiyar shi ce". Nuna Haseena tayi data yi d'aid'ai tana kwasan baccin ta tace " wannan kuma Haseena ita take bi mun, se Auta Shukra" Jin jina kai Haajar tayi tare da cewa "Sunaye masu dad'i da ma'ana. Naji dad'in had'uwa daku" "Muma haka!" Suxee ta fad'a cike dajin dad'in kasantuwa da Haajar. Misalin k'arfe takwas ,Haajar ta fito ta nufi kitchen, koda ta fito babah ta-tata me aiki har ta gyara ko ina, amma bata taradda ita a kitchen d'in ba. Tunani ta fara akan me zata dafa ,Wanda tasan bak'in su zasu so shi. Tuno wa data yi Hajj Jamil yafi son yin breakfast da kunun gyad'a me madara yasa tayi tunanin ma Daddy ze so shi, nan ta shiga shirya musu kunun gyad'a me d'an karan daddy da d'aukan ido, a lokaci d'aya kuma ta soya Arish tare da yi masa mahad'i na sauce din k'wai da soyayyen anta. Seda ta kammala ta zuzzuba a mazubi me kyau, tana k'ok'arin fitowa se ga suxee ta fito ,k'amshi tabi har ya kawo ta kitchen d'in. Haajar na ganin ta suka sakarwa juna murmushi. Ciki suxee ta k'araso tana fad'in " kai Sister Haajar ,shine baki tashe ni munyi tare ba?" Haajar dake ta kai kawo tana k'ok'arin tsaftace wajen tace "Haba dai Hajiya k'arama! Idan nayi haka ,ai da ban kyauta ba. Kufa bak'i na ne ,ko kin manta hadisi na manzo s.a.w dayace , " Imanin d'ayan mu baya cika ,har se ya kyautatawa bak'on sa?" To kinga kar nayi missing wannan aikin ladan. Kuma ma kuda kuka zo jiya-jiya ,ina wani kika isa fara tayani aiki? Aikya bari ki huta tukunna" Dariya kawai suxee tayi, a ranta take jinjina karamci irin na Haajar. A tare suka kwashe komai ,suka kai babban parloun gidan inda aka saba karyawa, sannan suka dawo suka k'arasa gyara kitchen. Haajar ce ta dubi suxee tare da cewa "Sannu da k'ok'ari" "Kaji sister Haajar, wai sannu ,se kace wani aikin kirki kika bari nayi ,aike za'ayi wa sannu." Murmushi Haajar tayi sannan tace " Yanzu dai muje muyi wanka kafin su Abbu Sameer su fito. A tare suka Jere ,kai idan ka gansu zaka d'auka sun jima tare ne. Seda suka gama shiri tsaf suka jero zasu fito ,Suxee ta ke k'are wa Haajar kallo, badai wani kwalliya tayi ba ,Dan tana gani ma ko powder bata Shafa ba, iya mai kawai ta Shafa se man baki. Doguwar Riga ne yellow a jikin ,Wanda ya tafi da shape d'in ta. Fuskar ta dauke d'auke take da manyan idanuwa zagaye da zara-zaran gashin ido ,tana da karan hanci ,ga bakin ta daidai ita. Tana da hasken fata daidai misali, Wanda daka kalle ta kai kasan ba hasken fatar bane kad'ai hadda tsabar Hutu da kwanciyar hankali. Abunda yafi d'aukar hankali a jikin ta be wuce surar taba. Wato idan boobs na wa mace yawa to zamu iya cewa har yawa Haajar yawa ,daga daidai hak'ark'arin ta kuma zuwa cikin ta ,a lafe yake abunda abunda ke kira (flat tummy), daga k'ugunta kuma ya baje. A tak'aice dai Haajar na d'aya daga cikin matan da ake kira a hausance masu siffar koka-kola, a turance kuma tana cikin mata da bature ke kira (MODERATE),,,,,komai nata me kyau ne, ba namiji ba ko mace ta kalli Haajar zata so ta k'ara kallon ta, komai nata me kyau ne da tsari ,se a yanzu suxee ta gane dalilin daya sa Haajar ta lizimci saka hijabi, Dan daga jiya zuwa yau ,so d'aya ta lura haajar ta cire hijabi ,shine da zata shiga wanka, kuma tana gama shirin ta ,wani hijabin ta d'auko ta saka me hannu. Hijabin data saka wa kuma be hana ka gane ita d'in me shape ce ,sedai yana taimakawa wajen rage ido akan ta ,ba kamar idan babu hijabin a jikin taba... A hankali Suxee ta furta "fataba rakallahu ahsanul khaliqin"... MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [7/19, 9:27 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA GOMA SHA UKU_ *________________________* _Koda suka fito a parlour suka taradda su daddy. Cike da k'warewar zamantakewar rayuwa na yau da kullum Haajar ta k'arasa tana fad'in_ _"Allah sarki Dan Allah kuyi hak'uri nasan kuna ta jira ,ni ban ma zata kun tashi bane"_ "Au to bari kar mu tashi ,tunda ana cin bacci a k'washi ne" inji Hajj Jamil kenan. Shidai Daddy se dariya yake musu. D'an gurfa nawa Haajar tayi ta gaishe da Daddy ,fuska a sake ya amsata ,sannan ta gaishe da Hajj Jamil cike da girmama wa. Su suxee ma k'arasowa suka yi ,suka gaishe su a ladabce. Hajj Jamil janyo Auta yayi yana fad'in "Autar daddy yaya? Kinsha bacci ko?" Itadai auta se gyad'a masa kai take yi ,Dan tana da wani Abu d'aya ba ,matuqar tazo bak'on wuri koma wa take yadda kasan ruwa ya tafi da ita ,wannan kuma ba tarbiyyan kowa bane face Haseena, ba kuma wai Dan basu saba da Hajj Jamil bane ,har gidan shi suna zuwa lokaci bayan lokaci ,se dai basu tab'a zuwa sun kwana bane ,shiyasa suka kasa sabawa da gidan ,sannan da ace akwai qawance me k'arfi ne tsakanin kubra da Hajiya zaliha matar Hajj Jamil to da shak'uwar tafi yawa ,to kubra bata qawance se daidai da ita ,Hajiya zaliha bata cikin tsarin irin matan da ajin su yakai a wajen kubra, Hajj Jamil dai da daddy su suke Abokan tan su cike da nuna wa juna qauna, Dan da sun biye matan su ma baza su yi ba ,to se Allah yasa Abokan takan su bana yanzu bane ,Abotar su ta samu asali ne tun suna yara ,komai nasu tare suke yi ,har suka zama kamar 'yan uwan juna ,duk abunda ya shafi d'aya kamar ya shafi d'aya ne... Su suxee kujera suka ja suka zauna ,inda Haajar ke serving d'in su ,su daddy ta fara zuba wa ,sannan ta zuba wasu haseena ,kowa yaci abincin se santi suke yi ,banda Auta da se wani cakalan abincin take yi, Haajar na lura da ita tace "Auta ya ke bakya cin abincin?" Cike da shagwab'a Auta tace "Ni na k'oshi" Karaf Haseena ta k'wace zancen "A-hap! Auta ce fa, ai wallahi baki ga komai ba indai wajen cin abinci ne ,haka take" "A'a ba wani ,Ku dai bakwa mata yadda zata ci d'in ne." Cewar Haajar ,sannan taci gaba da cewa "Auta zaki sha chocolate? " da sauri Auta ta kad'a kai ,Dan an ambato mata favourite d'in ta. Haajar taci gaba da cewa "yauwa to taso abinki kinji ,indai kika ci abinci sosai naga kinci ,to zan baki chocolate kisha kin ji". Mak'e ka fad'a Auta tayi alamar rashin yadda. Wanda seda abun ya bama kusan kowa dake wurin dariya , itama Haajar d'in dariya take ,tashi tayi taje d'aki ,ta d'auko mata chocolate d'in tare da cewa " kin gani ko ,to zaki ci se in baki" Ba musu Auta ta sauka kan carpet inda Haajar d'in ke zaune da plate d'in abinci. A baki tashiga bata ,har seda taci sosai ,sannan ta mik'a mata chocolate d'in. Kowa se jinjina lamarin yake ,yau Auta ce taci abinci sosai haka, Daddy kam abun ba k'aramin burge shi yayi ba ,dan yana matuqar son a nuna wa yaran shi kulawa... Bayan sun kammala, Haajar da Suxee suka kwashe komai suka kai kitchen, haseena kuma ta tsaftace dinning area d'in. Daga nan daddy da Hajj Jamil suka koma parlour suna ta tattauna matsalolin yau da kullum, a inda su Haajar suka fara shirye-shiryen d'ora abincin rana. A tattaunawan da Daddy keyi da Hajj Jamil ne yake sheda masa tafiyar zuwa kano. "To amma tafiyan Nada muhimmanci ne?" Hajj Jamil ya tambaye shi Daddy yace "eh to Hajiya Gwaggo ce ke kirana ,kasan wancan zuwan Dana yi bata da lafiya an tafi da ita Sudan, to nasan baze wuce labarin auren khaltum da akayi bata nan ba" Ajiyan zuciya Hajj Jamil ya sauke ,kafin yace "To ina ganin kaje kai kad'ai kabar su Hajiya k'arama anan ,Dan kar kaje dasu kuma Abu na babban gida ,se ya zama gutsiri tsoma, in yaso duk yadda kuka yi Seka sanar mun" Cike dajin dad'i ,daddy yace "To shikenan. " kwana nawa zaka yi? Hajj Jamil ya tambaye shi Daddy yace "Har wani kwana ki zan ke inyi ,inaga cikin ma nayi in kwana d'aya ko biyu". " to ba damuwa ,Allah ya kaika lafiya ,ya kuma dawo dakai lafiya" Daddy ya amsa da "Ameen" Seda suka ci abincin rana ,Daddy ke sheda wa suxee tafiyan shi ,sosai taji dad'in daya ce ze bar su a gidan Hajj Jamil ,Dan dama abun da ke ranta kenan ,badan komai ba sedan Haajar ,lura akwai abubuwan k'aruwa sosai da baiwa a tattare da Haajar. Addu'a ta masa na Allah ya tsare. Misalin k'arfe uku na rana Hajj Jamil yakai daddy Airport, tare da masa addu'an Allah yasa suji alkhairi, duk da a k'asan zuciyar Hajj Jamil yasan Abu ne me wuyan gaske ace Hajiya Gwaggo tayi wa mutum kiran azziki, amma ba yadda ya iya ,sedai yabi lamarin da Addu'a... _GARIN KANO, HAD'EJA ROAD..._ MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [7/20, 2:45 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA SHA HUD'U_ *__________________________* _Daddy na isa kai tsaye sashen Hajiya Gwaggo ya nufa ,be ko yi tunanin fara ganin hajiyar shi ba ,Dan kuwa matuqar Hajiya Gwaggo ta samu labarin seda ya biya can kafin ya shigo wurin ta ,to fa jarabar duniya se Wanda ta manta ,kai bashi kad'ai ba hatta hajiyar tashi ya ja mata jangum. Gashi dai asalin mijin Hajiya Gwaggon ya rasu ,wato kakan daddy namiji ,amma bashi yasa Hajiya Gwaggo ta canza wasu halayen nata ba ,ita ke mulkin komai tun kakan daddy Nada rai ,ba Wanda ya isa ya d'aga d'an tsaya matuqar tana wuri ,da tace 'Eh' kuma ba a haifi Wanda ze ce a'ah ba, kishiyar ta Hajiya sakina ba k'aramin wahala tasha ba a hannun Hajiya Gwaggo ,musamman ita da yaran ta mata ne gaba d'aya ,bata tab'a haihuwan namiji ba ,ita ko Hajiya Gwaggo yaranta biyar maza ,kakan daddy shine Auta ,to fa se abunda ta b'ata, wannan yasa lokacin da me gidan ya rasu ,ta kame komai tayi kane -Kane ,rabon gado ma da akace za'ayi hana wa tayi ,daga k'arshe ma kawai se ta kuka ,wai dama so ake ya mutu aci gado ,to ba abunda ya isa matuqar tana da rai , ba yadda za'ayi da ita ,haka aka hak'ura aka k'yale ta ,haka dai kishiryar tata ke zaman hak'uri a gidan ,da Allah ya tashi nuna ikon shi ma ,gaba d'aya yaran Hajiya sakina biyar mata ,manya-manyan attajirai suka aura ,daga wacce ta aura mijin ta bako sisi ,suka kud'ance tare ,se wacce taje ta taradda azzikin, ba yadda basu yi ba akan ta koma d'aya daga cikin gidajen da aka Gina mata amma ina k'yameme Hajiya sakina tak'i ,saboda ta saba da zaman wannan family house d'in. Duk kuma lokacin da zasu zo da abun azziki ,ko da basu yi niyyar bawa Hajiya Gwaggo ba ,tilas Hajiya sakina ke matsa musu se sun je sun bata, saboda a zauna lafiya ,sannan rayuwar mu ba d'aya ba ,Hajiya sakina mace ce me sauqin hali da faranfaran da mutane ,ita ko Hajiya Gwaggo tak'adarin budurci ne ke yawo akanta sama da shekaru aru aru Ana Abu d'aya, da Allah ma yaso nuna mata ishara ,kaf a 'ya'yan ta mazan nan data ke tak'amar ta Haifa gwal ,Alhaji k'arami Baban Daddy shine kad'ai Wanda Allah ya d'aga a cikin su ,shiyasa komai nashi take ham-ham. Sannan kaf a sauran 'ya'yan daga Wanda yabar 'kasa zuwa Neman nakan shi ,se Wanda yana wani gari da iyalan sa ,Baban daddy ne kawai tayi wa kafi a kusa da ita. To sauqin suma tsufa daya kamata gadan-gadan ,ciwon yau daban na gobe daban. Wannan kenan..._ _Sallama yayi ,ba kowa a sashen duk mutanen gidan suna sashen Hajiya sakina ,Dan kusan kullum acan ake wuni. K'arasa wa yayi suka gaggaisa ,Hajiya sakina na tambayar shi iyalan sa ,yace duk suna lafiya. Ba wani jimawa yayi ba ,Dan yasan masifar kakar tashi ,yace wa Hajiya sakina_ "Bari inje mu gaisa da Hajiya Gwaggo" Tace "To shikenan. Ga wannan hurar me sanyi kaje da ita kasha ,yanzu na gama damun ta kaga ludayi nan gashi, nasan an kwaso hanya" ta mik'awa daddy k'waryan furan ,daya ji kidirmo ,ga k'ank'ara an farfasa a ciki. Kai daga ganin furar nan zata yi dad'i musamman irin lokacin zafin nan...lolz😛 Godia Daddy ya mata sosai, sannan ya d'auka ya nufi sashen Hajiya Gwaggo, a lokacin ta fito daga ban d'aki. Har k'asa ya zube ya gaishe ta a ladabce kamar yadda ya saba. A yatsine ta amsa shi. Kafin ta soma halin nata "Se yau kaga damar zuwa ,ko da yake inaga se yau uwar taka suwaiba ta baka izinin zuwa inajin ,wato ni ban isa ba ,ban kuma da muhimmanci a wajen Ku dahar zaku yi Abu ba tare da kun sanar dani ba ,tun ba yau ba ,na riga na gane dakai da uwar ka suwaiba so kuke in mutu, to wallahi ahir d'in Ku ,k'walelen kare da antar kura ,ni d'in nan da bakwasan gani wallahi se kun ganni. To kunyi yadda kuke so ,yanzu nima zakaji nawa hukuncin ,saboda haka ka bud'e kunnuwan ka dakyau kaji ni. Kai bama zan fad'a a gaban ka kai kad'ai ba tashi muje ayi a gaban suwaibar". Tana gama fad'in haka tayi gaba. Shidai daddy be ce mata ci kanki ba ,Dan Allah yayi mai sanyin hali ,girgiza kai kurum yayi sannan ya tashi yabi bayan ta. A b'angaren hajiyar daddy ,tun da taji sallamar Hajiya Gwaggo gaban ta ya shiga dukan tara-tara ,Dan tasan azziki baya kawo ta se dai akasin shi. Tsaye ta tashi tana mata sannu da zuwa ,sallamar Daddy yasa ta maida duban ta gun k'ofar shigo wa ,a mamakin shine yaushe Daddy yazo? Kuma meya kawo shi a wannan lokacin? Gashi ta ganshi da Hajiya Gwaggo, tasan ko ba'a fad'a mata ba ita ta kira shi. Nan fa hankalin ta ya k'ara tashi ,Dan tasan wani matsalar ce zata kunno kai. Daddy gaida Hajia yayi ,ta amsa fuska a sake. Bata ko zauna ba ,ta mike ta d'auko wa Hajiya Gwaggo ruwa ,taje a gaban ta "Ba ruwan ki ya kawo ni ba ,ni za'a gaya wa ruwa ,nida keda ruwan tukunyar k'asa ta dauri ,masu k'ara lafiya. To ki saurare ni dakyau. Kunyi San ranku ,azzikin Ku d'aya da bana nan. Kinje kin nemo masa mata kin aura mata ,kuma 'yar wannan battalalliyar qawar taki, saboda kun ga jini na me kyau ne ,anga azziki ,shine Dan mugunta Dan kika nema masa aure, to bazan ce ya sake ta ba ,tunda an riga anyi ,amma ina me tabbatar miki ,Wani auren ze sake ,kuma nice nan zan sama masa mata 'yar azziki..." Daddy ji yayi kamar an buga masa guduma... Hajiya ma haka taji abun kamar saukar aradu, wai Aure... "Aure kuma???" Daddy ya furta ba tare dama yasan maganar ta fito fili ba "Eh aure. Wannan umurni na ne ba shawara ba". Hajiya Gwaggo ta fad'a tana wani irin gimtse fuska ... MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [7/21, 3:08 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA GOMA SHA BIYAR_ *________________________* _Magana daddy yaso yi amma Hajiyar shi ta katse shi. K'ak'aro murmushin dole tayi ,kafin tace "Hajiya Gwaggo insha Allahu zaki same mu masu yi miki biyayya, kada Allah ya kawo randa zaki yi magana ni suwaiba ince ba haka ba ,ki qaddara bani bace insha Allahu Rabbi. Aure kuma ba wai nayi wa Daddy shi akan wata manufa bane, nayi mishi ne ko Dan in Samar musu nutsuwa shi da iyalan shi. Amma Dan Allah kiyi hak'uri idan kina ganin an miki ba daidai ba"_ _tsabar jaraba irin na Hajiya Gwaggo duk lallamin nan da Hajiya tayi mata be yi nata ba ,a'a wai Dan me za'a ce mata idan tana ganin an mata lefi tayi hak'uri, nan fa ta fara zazzaga musu ,se abunda ta manta. " Nace dai ba ke kad'ai kike da iko dashi ba ,har wani wai idan an mun lefi in yi hak'uri, to bazan yi hak'urin ba da guntun tsugudidin ki, ba abunda ya kawo ni ba kenan. Kai kuma..."_ _ta fad'a tana nuna Daddy dake zaune ya sunkuyar dakai ,shi kad'ai yasan me yake ji a k'asan ran shi. D'an d'agowa yayi yana duban ta ,ai fa wannan be yi mata ba "Au bazaka iya amsawa ba ,kai kurma ne? To ka amsa ko kar ka amsa wannan matsalar ka ce"_ _Taci gaba da cewa " Yarinya dai ba wata bace in la wacce nasani kuka Sani ,yarinya 'yar gidan mutunci ,ga kamala da tsari. Sama da shekaru aru-aru da muke zaune a layin nan ban tab'a jin ance sunyi rigima da wuni ba, ba kowa bace illa LUBABATU... Kai idan baka sheda ta ba , ita suwaibar uwar ka ai ta Santa farin Sani ,balle ma baka isa kace baka gane wacce Lubabatun ba, saboda duk zuwan da kayi tana zuwa yi maka sannu da zuwa ,har ma tayo maka girki. Saboda haka na gama magana da iyayen ta ,se da nayi da gaske ma kafin suka amince ,mun kuma tsaida ranar biki ,nan da wata biyu me kamawa, se ka fara shirye-shirye ,ka kuma turo mana da isassun kud'i ,kar muji kunya ,kaji na gaya maka, kafin ka tafi se ka leqa Ku gaisa"_ _Hajiya Gwaggo ta k'arasa fad'a yayin da take barin d'akin..._ _Wani takaici ne ya tokare wa Daddy mak'oshi ,babu ma abunda yafi bak'an ta mishi rai ,irin da Hajiya Gwaggo ke cewa ,seda tayi da gaske sannan aka bata wannan auren ,kai kace saka ta yayi. Wani abun takaicin ma wai ya leqa ,kamar shi ,maimakon ma tace zan tura a kira maka ita ,shine zata ce ya leqa da girman shi"... Daddy ke ta zancen zucin shi shi kad'ai. Ita dai Hajiyar Daddy kusan bugun zuciyar ta ne ya kusa tsayawa cak ,,,, Dan wannan ba k'aramin al-amari bane. Ta gane Lubabatun da ake magana ,se dai tana jin wasu rad'e-rad'in maganganu marasa dad'i akan gidan su ,ta kuma ji ance ta tab'a aure ,amma fa badan ta tabbatar ba. Wani gajeren ajiyan zuciya ta sauke ,tare da zuba wa Daddy ido, ita gaba d'aya ma wallahi tausayin shi take ji ,shi ba wani babba ba can amma duk an taru an kashe masa rayuwa da gurb'atattun mata marasa tsoron Allah. Gashi bata da wani abun yi daya wuce ta dage wajen gayawa Allah... Hajiya keta sak'e-sak'e a ranta. Kafin ta kira sunan daddy cikin Muryar lallashi. "MISBAHU!!!" Da sauri Daddy ya d'ago ,Dan idan baze manta ba wannan shine karo na biyu da Hajiya ta kira sunan shi ,tun da kuwa yake da ita. A sanyaye ta fara basa baki "Kayi hak'uri kuma ka d'auki abunda abunda yake faruwa dakai a matsayin qaddarar rayuwar ka. Allah na sane dakai ,be manta dakai ba. Cewar kawai kayi imani bashi ze sa Allah ya kasa jarabtar kaba, dole ne ayi maka gwaji ,musamman ma kai da Allah yayi wa bud'i. Menene Allah be baka ba na duniya? To se kuma kace a had'a maka dad'in duniya gaba d'aya? Baze yu ba ,Shiyasa Allah ya maka jarabawa da mafi girman jarabta, Dan mace qalubale ce ,kuma babbar jarabawa ce a rayuwa. Dan haka kayi k'ok'arin danne zuciyar ka wajen ganin ka ci wannan jarabawar. Sannan kar ka damu zanyi iya bakin k'ok'ari na wajen yin bincike akan ita wannan yarinya ,Addu'a kuma ba fasawa nayi ba koda yaushe albarka ta na tare dakai. Kar ka kuma yi mamakin wannan itace jarabawar ka ta k'arshe ,ta iya yuwa kuma a wannan karon kaji dad'in aure ina fatar hakan..." Shiru ne ya biyo baya nad'an wani lokaci kafin Hajiya ta tambaye shi "to yanzu ya zaman iyalan naka yake a can?" A tunani na ko Daddy ze gayawa Hajiya duk abunda yake faruwa ,sedai Banyi mamakin jin be wani tsawaita zancen ba ,Dan Allah yayi Daddy wani mutum me matuqar zurfin ciki. A sanyaye yace "Suna can lafiya qlau ,sedai zaman ba dad'i gaba d'ayan su ,Dan kusan duk wani Abu da kubra keyi shi khaltum ta koma yi ita ma ,duk dai abun se hamdala". " Oh Allah! Ka kawo mana d'auki da sassauci acikin wannan al'amarin" cewar hajiyar Daddy. Daddy yace "shiyasa naso ace da Hajiya Gwaggo zata bar maganan auren nan ,jna ga zefi sauqi ,wancan wutar ma dake gaba na se dad'a huruwa take ,balle kuma ace na kai wata ,Hajiya kar fa su kashe ni" Murmushi irin nasu na manya Hajiya tayi tare da cewa "bame kashe wani se kwanan shi ya k'are ,rayuwar ka ba'a hannun su take ba ,a hannun Allah take, idan ma wannan bashi bane k'arshen ijabar ,to ina ji a jiki bada jimawa ba ,Allah ze musanya maka da mafi alkhairi insha Allahu.""" A ranar dai daddy da Hajiya kwana suka yi suna tattauna matsalolin gidan shi, da daddare yaso ya tafi sashen bak'i ya kwana ,ko ya samu yaji rad'ad'in da zuciyar sa ke masa ya ragu ,amma tsakanin d'a da mahaifi se Allah ,tunda Hajiya ta karanto akwai damuwa a tattare dashi ,hana shi fita tayi ,se dai suka kwana a sashen ta. Ko parlour bata bari ya tako ba ,gadon ta ta sauka ta bashi ,ita kuma tayi shimfid'a a k'asa, ranar kwana yi masa nasihohi tayi ,tare da lallashin zuciyar shi ,a haka Daddy be ma San bacci yayi awon gaba dashi ba... _washe gari tunda sassafe Hajiya sakina (kishiyar Hajiya Gwaggo), ta auko wa daddy da abun karin kumallo..._ MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [7/23, 2:19 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA SHA SHIDA_ *_________________________* _Tun bayan tafiyan Daddy kano ,su suxee ke cikin walwala da kwanciyar hankali. Sosai Haajar ke saka su nishad'i ,musamman data gane kamar akwai damuwa a tattare dasu, ba kuma wai sun gaya mata bane , a'a hasalima wani magana ta b'angaren rayuwar junan su be shiga tsakanin su ba ,saboda Haajar ba mace bace me yawan magana musamman akan abunda be shafe ta ba ko ba'a saka ta a ciki ba ,amma tana da Abu d'aya Wanda zamu iya cewa yana daga cikin baiwar da Allah ya mata ,duk yadda mutum yake cikin damuwa kuma yake k'ok'arin b'oye ta ,to hakan a wurin Haajar kamar ma k'ok'arin bayyana mata kake yi ,ba dai zata ga abun bane saboda batasan gaibu ba ,amma tana da hasashe nad'an Adam, da ace zata nazarci matsalar ka sosai ,to idan da zata furta cewa ga abunda ke damun ka ,kuma seka ga insha Allahu kamar ta sara akan gab'a ,ko kuma k'anin hakan. Sosai take kutse cikin rawar su haseena Dan ganin ta kwatanta wargatsa abunda zata iya na damuwar su ,seda tayi duk yadda tayi suka sake da ita ,Auta kam ta samu sabuwar Anty Dan ko abinci idan dai ba Haajar ce zata bata ba ,to bafa zata ci bane ,idan ma aka matsa mata se ta tsiri k'ananan kukan ta ,haka dai Haajar ke biye ta ,Ashe dama Auta fili take nema ta b'arje gumin ta ,samun wuri yasa har ta fara wani shagwab'an iyayi da bata yi da a gidan su. Sautari idan Suxee tana ganin yadda Auta ta samu kyaky-kyawar kulawa a wurin Haajar, har k'wallan tausayin kan su take yi, saboda a rayuwa su basu tab'a sanin menene soyayyar uwa ba, se dai ta uba ,shima ba wani kyaky-kyawar kulawa ba saboda d'an kasuwa ne ,ba zama yake yi ba. Ba Auta kad'ai ba ,hatta su d'in da suke manya Haajar bata saka musu ido ba. Bata tab'a barin su cikin kad'ai ci ,ko wani lokaci takan nemi abunda zasu yi me amfani Dan karta barsu zaman tunani._ _Hajj Jamil ma ba'a barshi a baya ba wajen basu kulawar data dace ,haka yake jan su a jiki tamkar 'ya'yan daya Haifa na cikin su ,Dan tsakanin shi da Daddy fad'in alaqar b'ata lokaci ne , 'yan uwa ma na jini sunyi kad'an su nuna musu so da qaunar junan su. Shi gaba d'aya ma yaran tausayi suke bashi ,kusan da abun yake kwana arai dashi kuma yake tashi ,koda yaushe tunanin shi shine ina mafita ,haka dai ya fawwala allah al-amarin ,be kuma yi k'asa a guiwa ba wajen ci gaba da gayawa ubangiji matsalar da suke ciki. Wannan yasa idan ya dawo da daddare se ya tafi can sashen nasu ,yayi ta Jan su da hiran ban dariya ,a haka se sukai k'arfe goma na dare, kawo lokacin wani shak'uwa me k'arfi ne ya sake shiga tsakanin shi dasu suxee Wanda ada babu._ _Kwanan su suxee uku ne kawai a gidan Hajj Jamil ,Amma idan ka gansu kai kace sun shekara ne. Sosai suka sake suka gudanar da al-amarin su ,tamkar suna gidan Daddy, kai wani abun ma da suke anan basa yin shi acan ,saboda sun San a gida ko sunyi ba duba musu za'ayi ba. Rayuwar se ta koma musu sabuwa fil ,se dai idan suxee ta tuna cewa ,idan fa Daddy ya dawo zasu koma gida ,duk se wani bargon tsoro ya lullub'e ta ,Dan ta riga ta gama tsorata da gidan zuwa yanzu._ _Se da daddy ya kwana uku ,yana shan nono wajen Hajiya ,Dan gaba d'aya kulawar da Hajiya ke bashi a kwana ukun nan yasa ya fara mantawa da wasu matsalolin. Zallar soyayya da qauna ,so irin na d'a da mahaifi ,shi Hajiya ke nuna wa daddy ,ji take kamar ta hana shi komawa ,amma hakan baze samu ba. Daze tafi Hajiya harda 'yar k'wallan ta ,ba tada dai matsalar komai na buqatun rayuwa Dan gaskiya Daddy na k'ok'ari ta wannan fannin ,ba ma ita ba ,na tare da ita ma na cin albarkacin ta. Be yiwa Hajiya Gwaggo sallama ba ,Dan ita a tunanin ta tun ranar ya koma, sashen Hajiya sakina kawai ya shiga ,Fura ta bashi manya-manya da aka saka a cikin bakko guda uku tace "ga wannan akaiwa iyalin ,nasan Hajiya k'arama dason fura". Godia sosai Daddy ya mata ,kafin ya kama hanya ,a ransa yake raya cewa ina ma Hajiya sakina ce kakar shi ba Hajiya Gwaggo ba ,Dan kwatakwata rayuwar su ta banbanta._ _tun bayan fitowar daddy gaban shi ke fad'i ,har zuwa lokacin daya kira Hajj Jamil ya sheda masa yau ze dawo ,gaban sa be dena fad'uwa ba. Be kawo komai a ranshi ba ,Se da ya shigo garin sakkwato ,nan fa zuciyar shi ta fara wani irin tsalle kamar zata fad'o k'asa. Yanayin yadda yake ji kamar wani al-amari ne ke shirin faruwa dashi, se kuma tunanin shi ya rabu gida uku ,Hajiyar shi ya fara tunowa ,musamman daya San yadda suka rabu bata so ba ,wata zuciyar tace masa kai ba ita ba ,se kuma ya fara tunanin su suxee ,nan ma dai zuciyar shi ta k'aryata shi ,Gidan shi ya tuno ,Sam zuciyar shi ma ta kasa bari ya tuno su ,A haka dai ya kama hangar gidan Hajj Jamil, sosai bugun zuciyar shi ya tsananta ,hankalin shi se ya k'ara tashi ,Allah Allah yake yaje yaga 'ya'yan shi, Dan gaba d'aya ya kasa samun natsuwa..._ _A bakin gate yaci karo da Hajj Jamil ,da alama shima dawowar shi kenan. Da fara'a sosai a fuskokin su ,suka yi musaba. Se a lokacin Daddy ya fara jin sauqin abunda yake ji ,Dan ganin Hajj Jamil da yayi cikin walwala da annashuwa a yanzu ya tabbatar masa daba wata matsala. A tare suka k'arasa cikin gida. Se hiran yaushe rabo suke yi ,se kace wa'yanda suka dad'e basu ga juna ba. A haraban gidan suka ci karo da Auta ta rugo da gudu ,Nan fa hankalin Daddy ya tashi ,a tunanin shi ko wata matsalar ce. Haseena ce ta fito itama a guje da alama ita auta ke wa guje-guje ,kamo ta tayi ,tana wani tsalle-tsalle tare da fad'in "Ni bana so, ni bakya zaki mun ba Anty Haajar ce",,,, wannan yayi daidai da fitowar Haajar ,aiko Auta na ganin ta ,k'wace hannun ta tayi daga na haseena ,ta ruga a guje tare da fad'a wa jikin Haajar. Da gudu Haajar d'in ta d'auke ta cas, suka shige ciki. Gwalo Auta ta dinga yiwa haseena. K'wacci haseena tayi tana fad'in " Zan kama ki ne yarinya ,se kinyi bayani"... Wani irin sanyin Dad'i ne ya mamaye zuciyar Daddy Wanda ya assasa k'wacewar wani siririn dariya a bakin shi... MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [7/23, 10:25 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA SHA BAKWAI_ *__________________________* _Sashen Hajj Jamil suka nufa ,dama Hajj Jamil ya sanar da Haajar dawowan daddy ,Dan haka ta shirya masa abinci da abun sha gwargwadon k'warewar ta. Bayan yaci abinci ya huta ,gaba d'aya suka je masa sannu da zuwa ,sosai yaji dad'in yadda yaga yaran shi cikin walwala, godia yawa Haajar sosai akan k'ok'arin da take yi wajen kula da yaran. Auta na wajen shi yana mata wasa ,tana ganin su Haajar zasu fita da gudu ta biyo musu ,tare da rik'e hannun Haajar_ _Bayan sun fice ne ,daddy ya maida duban shi ga Hajj Jamil. Yake cewa "Gaskiya yarinyar nada natsuwa ,A yadda na fahimce ta kuma tana da ilimin addini dan naga komai nata kamar a k'a'idan ce take yin sa, gata dai daga gani bata wasu shekaru sosai ,amma tasan komai na zamantakewa. Murmushi Hajj jamil yayi tare da cewa " Ai indai haajar ce haka take Abokina ,bata da matsalar rayuwa". "Ta huta" shine abunda daddy ya fad'a a tak'aice kafin ya soma Gaya wa Hajj Jamil duk yadda yayi da Hajiya Gwaggo ,be rage masa komai ba. Sosai Hajj Jamil ya jinjina lamarin. Shiru ne ya biyo baya nad'an wani lokaci kafin Hajj Jamil ya sauke wani gajeren numfashi tare da cewa_ "Yanzu zuwa yaushe tace maka za'ayi bikin?" "Kamar yadda tace dai ,ta Riga ta gama magana da iyayen yarinyar nan da wata biyu masu zuwa, amma kuma ai kasan lokaci na hannun Allah ne!" Daddy yaba Hajj Jamil amsa ,fuskar nan tashi d'auke da damuwa, yaci gaba da cewa "Yanzu menene abun yi kenan?" Hannu biyu Hajj Jamil yasa rik'e da hab'a, alamar yana wani tunani daban. D'agowa yayi yana duban daddy na wasu 'yan mintuna ,kafin yace "Ni ina ganin a yadda nasan Hajiya Gwaggo ,ba wani hanya da zamu b'ullo mata Dan tsaida wannan auren ,kamar dai yadda ta gaya maka inda tana da rai ba fa shi ,to fa haka zancen yake. Abu d'aya nake tunanin shine mafita ,Wanda kuma idan akayi dace shine jigon rayuwar ka dama na gidan ka gaba d'aya..." Cike da mamaki daddy yace "menene wannan kuwa Hajj Jamil" Dan shi fa Daddy a nashi bahagon tunanin ,rayuwar shi kamar ta gama nakasa ne ,gani yake ba yada wata mafita daya wuce yaci gaba da hak'uri har Allah yayi ikon shi akan shi. Cike da kulawa Hajj Jamil ya maida hankalin shi gaba d'aya wajen Daddy. Shiru ne ya biyo baya nad'an wani lokaci ,kafin Hajj Jamil ya fara magana a nutse "Ni ina ganin lokaci yayi daya kamata muyi wa toka hanci. A gani na MISBAHU rayuwar Gidan ka na buqatar mace me TAUHIDI,,, ita kad'ai ce zata iya zama dakai da zuciya d'aya ,ta kuma yi yak'i wajen ganin ta dawo maka da martabar kujeran ka na cikakken namiji me inci. Ina ganin lokaci yayi da zaka farka daga dogon suman da kayi ,dan wannan ya wuce a kira shi da nannauyan bacci. MISBAHU ,kwatakwata baka San me ake cewa jin dad'in rayuwar aure ba ,kai ba jin dad'in aure kad'ai ba ,baka ma San me ake cewa soyayya ba ,idan ban manta ba ,daga auren ka na farko har zuwa na ukun nan da ake shirin yi ,ba Wanda kayi Dan ra'ayin kan ka, ko wacce had'a ka akayi da ita. Kubra matar ka ta farko Hajiya Gwaggo ce sanadiyyar auren ,wanda 'ya ce ga Abokin mahaifin ka Allah ya jik'an rai ,ga Khaltum ita kuma wacce zab'in Hajiya ce, ga wannan za ake magana ita duk dai zani ce ta tadda muje. To yaushe zakayi incin kanka ,da har zaka fara bawa zuciyar ka daman ta zab'i abunda take so? Ko kuwa kana nufin haka rayuwar ka zata ci gaba da tafiya a gurgunce?" Tunda Hajj Jamil ya fara magana ,daddy ya natsu yana sauraren shi ,tabbas yasan duk abunda yake gaya masa gaskiya ne ,Amma shi ta ina ma ya kamata ya fara ,tunda yake a rayuwa be tab'a furta wa wata 'ya mace Kalmar so ba, shi dama baya shiga sabgar mata ,to ta ina kuma ze fara Neman mace har ma me TAUHIDI... Ajiyan zuciya ya sauke, kafin yace "To yanzu Hajj Jamil ta ina zan fara?" "Bincika wa zaka yi ,ko kuma kasa a duba maka ,sannan se kaci gaba da Addu'a." "Shi kenan Allah yasa a dace d'in, zanyi bakin k'ok'ari na" inji daddy Hajj Jamil yace "gaskiya kam da yafi". A ranar ma Daddy a gidan hajj Jamil ya kwana. Washe gari da ze koma gidan shi, Hajj Jamil ya buqaci akan yabar su suxee sud'an kwana biyu anan d'in, tunda ga Haajar nan tana tare dasu ,har zuwa lokacin da ze k'ara auren sa na uku ,ita kuma aga kamun ludayin ta. Daddy be musa masa ba ,Dan be tab'a jin akwai wata alfarma da Hajj Jamil ze nema a wajen sa ya kasa yi masa ba. Koda su suxee suka samu labarin zasu zauna a gidan Hajj Jamil nad'an wani lokaci ,sosai suka yi murna ,Dan haseena har cewa tayi " Allah yasa ma Daddy yabar mu anan gaba d'aya "... GIDAN DADDY...tun bayan tafiyar daddy da yaran shi ,su kubra suka bar k'asar zuwa GERMANY... MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [7/24, 8:55 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA GOMA SHA TAKWAS_ *_________________________* _Bayan Daddy ya dawo gida ,bedroom d'in shi ,ya wuce Dan ya aje kayan shi ya watsa ruwa ,be ko lura da drawern kud'in shi dake bud'e ba. Se bayan ya fito wanka ne ,ya nufi Wardrobe Dan d'aukan k'ananan kaya ya sanya wa jikin shi ,sakamakon wani zafi da ake a wunin ranar. Guiwar k'afar shine yaci karo da marfin drawern dake bud'e ta k'asa. D'an guntun tsaki yayi ,tare da rusunawa ze rufe marfin ,amma a mamakin shi wayam drawern bako sisi ,zaro ido ya shiga yi ,gaba d'aya gurfanewa yayi akan guiwowin shi guda biyu ya shiga bin cike drowowin d'akin amma taro ba sisi. Nan take wani zufa ya fara tartso masa ,kud'i ne ba k'ananan kud'i ba ya ajiye ,Wanda shi kanshi baze ce ga adadin su ba. Tunani ya fara yi ,waye ze masa wannan mummunan abun ,to ko dai bayan tafiya na b'arayi sun shigo ne? Daddy ya tambayi kan shi. Dak'yar ya iya mik'e wa ,ya saka k'ananan kayan daya daya Ciro ,fito wa yayi ya nufi wajen me gadi ,jikin shi a mace yake tafiyan, har wani dishi-dishi yake gani ,a haka har ya iso wajen me gadi. Babangida me gadi na ganin shi ,da sauri ya k'araso_ "Barka da fitowa Alhaji!" kasa bud'e baki daddy yayi ya amsa ,dak'yar ya iya k'arfin halin cewa "Babangida bayan nayi tafiya dawa dawa yazo gidan nan?" Babangida yace "Eh to gaskiya Alhaji ,kasan yadda gidan namu yake koda yaushe cikin bak'i su Hajiya suke maza da mata. Bayan tafiyar Ku ma dai hakan ne ,sedai awa she gari suma Hajiya uwargida d Hajiya amarya suka yi tafiya ,sun gaya mun cewa ,duk Wanda yazo Neman su ince sun tafi wace k'asa ma??? Am yauwa GERMANY!!!" "Akwai wa'yanda suka shiga sashen na ne?" Daddy ya sake tambayar shi Babangida yace "A'ah to gaskiya Alhaji bazan San wannan ba, sedai ko su Hajiya ,Dan su kad'ai nake ganin suke wurgawa ta wajejen". Wani irin jiri ne ya iba daddy ,saura kad'an yakai k'asa ,badan Babangida yayi saurin taro shi ba. A kid'ime babangida ke fad'in " ba kada lafiya ne Alhaji?? Ko dai akai ka Asibiti ne???" Shidai daddy shi kad'ai yasan me yake ji ,kai ya gyad'a wa babangida alamar a'ah ,sannan ya masa nuni akan ya taimaka masa ya koma ciki. Da taimakon babangida daddy ya k'arasa ciki, suna shiga parlou daddy yace "Banni anan in kwanta ,zaka iya tafiya". Daddy ya fad'a murya can k'asa. Fatar samun sauqi babangida ya yiwa daddy sannan yaja masa k'ofa ya koma bakin aikin shi cike da tausayin me gidan nashi. Bayan fitar babangida ,tashi daddy yayi yana daddafa bango saboda wani irin jiri dake shirin buga shi da k'asa ,wayar shi ya lalubo ya turawa Hajj Jamil text, seda ya tabbatar yaje sannan ya kashe wayar ya ajiye. Kan kace me zazzab'i me zafin gaske ya rufe daddy ,jikin shi har karkarwa yake yi ,idanuwan shi na wani kakkafewa kamar me shirin barin duniya. _Ina gida ba nida lafiya ,I need ur help_ Hajj Jamil ya furta " Subhanallahi ! Bayan ya gama karanta text d'in daddy. Cikin ran shi yake raya, me kuma ya faru bayan ya koma gida, bayan ni nan mun rabu lafiya qlau dashi?" Ganin baze samu amsa a wajen kowa ba ,yasa yayi hanzarin d'aukan mukullan motar shi ,ba tare da ya ga yawa kowa inda zashi ba. Cikin mintunan da basu gaza sha biyar zuwa ashirin ba Hajj Jamil yakai gidan Daddy ,a bakin gate yayi parking motar shi ,Dan ba yada kuzarin dahar ze iya shiga da mota ,da sauri yayi parking motar ya shiga gidan. Masu gadi se gaida shi suke amma ina ,shi ko jin su ma bayayi ,hankalin shi ya wurin yaje yaga halin da aminin shi ya shiga. Sauri yake yi hadda d'an had'a wa da gudu ,a haka har ya k'arasa sashen Daddy Be tsaya wata wata ba kawai ya bud'e k'ofar tare da sa kai cikin parloun ,da sallama d'auke a bakin shi. Waige waige ya shiga yi yana baza ido ,yaga ta inda ze hango mutum amma be hango kowa ba. Sallama ya sake yi ta yadda idan ma akwai mutum yasan ze iya jiyo shi amma shiru. Ganin ba alamar kowa yasa ya nufi bedroom d'in. Se da ya fara knocking tukunna ,Nan ma shiru. Tunani ya fara yi ,to ina Daddy ze shiga ,bayan ya gaya masa yana gida ba yada lafiya ,k'ofar fita ya nufa ,da niyyar yaje ya tambayi koda d'aya daga cikin masu aikin gidan. Har yakai bakin k'ofa ,se kuma wata zuciyar tace masa 'kai koma dai ka duba ciki ,Daddy na nan ba inda ze je' ,fasa fita yayi ,maida k'ofar yayi ya rufe ,sannan ya nufi bedroom d'in, wannan karon yana zuwa bud'e wa yayi tare da shiga ciki. Taku d'aya yayi ,be kai na biyu ba ,ya hango Daddy tsube a tsakar d'aki warwass. Ba shiri ya k'araso da gudu a lokaci d'aya yana furta "innalillahi wa'inna ilaihi raji'un" "MISBAHU!!! MISBAHU!!!" Hajj Jamil ya shiga girgiza shi yana kiran sunan shi ,cike da tashin hankali da fargaba. Juyo shin da zeyi ,se yaga ko numfashi baya yi ,se wasu siririn hawayen dake saukowa daga gefen idon shi na hagu... MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [7/25, 2:43 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA GOMA SHA TARA_ *_________________________* _Gaba d'aya hankalin Hajj Jamil idan yayi dubu ya tashi. Tunanin meze yi meze yi ya fara yi ,tunowa da yayi yana da numbern babangida me gadi ,yasa yayi saurin Ciro wayar shi ,ya kira shi ,bugu d'aya ya d'auka tare da gaishe shi "Ka same ni yanzu a sashen daddy ,kayi sauri ina jiran ka". Shine kawai abunda Hajj Jamil ya iya cewa tare da yanke kiran. Cikin mintuna da basu gaza biyar zuwa goma ba se ga babangida ya shigo ,ganin ba kowa a parloun kuma k'ofar bedroom d'in a bud'e yake yasa ya shiga kai tsaye ,Dan yasan koma menene to ba lafiya ba._ _Ganin daddy da babangida yayi a kwance a k'asa kamar matacce yasa shima hankalin shi ya tashi ,kafin yace komai ,Hajj Jamil yace " yanzu ba lokacin magana bane ,kama shi mu saka shi a mota",,,, da taimakon babangida aka saka Daddy a mota, Ba b'ata lokaci Hajj Jamil yaja motar ,be yi tunanin kai Daddy babban asitin garin sakkwato ba ,Dan yasan daddy sanannen mutum ne, a take abun ze baza duniya ,Dan haka se ya yanke shawaran kiran wani abokin su dake aiki a asibitin UDUTH ,ya sheda masa abunda ke faruwa ,ya kuma fad'a masa dalilin sa na rashin son kai daddy babban asibiti. Kasancewar manyan likitocin nan se ka same su da asibitin kan su a waje ,wato private hospital, nan Dr Zaidu yawa hajj Jamil kwatancen asibitin shi, tun basu gama wayar ba Hajj Jamil ya karyar dakan motar shi zuwa asibitin da Dr Zaidu ya kwatanta masa._ _Dr Zaidu k'wararren likita ne daya samu yabo da k'warewa akan aikin shi. Hajj Jamil na isa ba b'ata lokaci Dr yasa aka shiga dashi ciki._ _Tambayar Hajj Jamil Dr. Zaidu yake yi akan me ya samu daddy? Hajj Jamil yace "wallahi Dr. Bansani ba ,nidai nasan yana fama da zazzab'i, to kuma yau muna tare ,bayan ya koma gida ne na samu labarin ciwon ya masa tsanani ,kafin in kaima shine na taradda shi a haka yadda kagan shi"._ _"OK to ,zanyi iya bakin k'ok'ari na insha Allah!"_ Shine kawai abun da Dr.Zaidu ya samu damar fad'a, kafin ya nufi d'akin da aka kai daddy ,Wanda yake zagaye da kayan aiki. Dr.Zaidu yayi iya bakin k'ok'arin shi ,Dan kusan wuni yayi zungur akan Daddy ,kafin Allah ya bashi damar gano kan matsalar ,bashi ya fito ba se wuraren Bayan magirb. Bayan ya kammala aikin shi ,ya umurci wasu daga cikin nurses din shi dasu kai Daddy d'akin Hutu. Hajj Jamil na zaune a wajen ,ya had'a cikin hannun shi da fuska ,aka fito da daddy ,Wanda har a lokacin akwak oxygen (wato na'urar k'ara numfashi) sanye a hancin shi. Ciwon wuni d'aya duk Daddy yabi ya k'are ,Hajj Jamil ya furta a k'asan ran shi. Da ido yabi gadon har aka wuce daddy ,be San lokacin da wasu hawayen tausayin Daddy ya fara gangaro mishi ba. Ganin Dr Zaidu na zuwa ,yasa yayi saurin goge hawayen shi ,kafin ya k'araso yayi saurin mik'e wa ,tare da bashi hannu ,se a lokacin suka samu damar gaisawa. Dr Zaidu yace "muje office d'ina akwai bayanin Dane ke so in maka". Kai kawai Hajj Jamil ya gyad'a ba tare da ya amsa ba ,sannan yabi bayan Dr. Bayan Dr ya zauna ,ya umurci Hajj Jamil akan shima ya zauna. Shidai gaba d'aya jikin shi a sanyaye yake. Zama yayi tare da zuba wa Dr Zaidu jajayen idanuwan shi. Dr zare gilashin dake manne a idon shi yayi ,sannan ya fara yiwa Hajj Jamil bayanin ciwon Daddy " wato a gaskiya Hajj MISBAHU na cikin wani hali ,badan ma kayi saurin kawo shi asibiti ba ,Allah ya tsare da ba'asan me ze faru ba. A iya gwaje-gwajen Dana masa ,na gane cewa yana d'auke da ciwon kasawar zuciya wato (Heart failure) Wanda idan yayi wa mutum yawa yakan iya leading to Heart attack wato (bugawar zuciya) ,wannan ciwo ba k'aramin ciwo bane da k'alubale ga Wanda yake d'auke dashi ,musamman ga magidanci irin wannan. Ba komai be kawo wannan ciwon ba illa matsanancin damuwa da k'alubalen rayuwa Wanda mutum ya kasa maganin shi ,sannan iya abunda na gano ciwon ya dad'e yana cin shi ,alama ta nuna nuna kuma baya tsare shan magani. Hajj Jamil wannan ciwon ba ciwon da za'ayi wasa dashan magani bane ,wallahi idan aka bari ,kaga yadda aka kawo shi yau ,idan aka Bari ya sake fad'uwa da kanshi har so ukku ,to ina me tabbatar maka idan kowanne yana tashi to ana ukkun sedai wani bashi ba , 'ka'idar wannan ciwon kenan. Kar kuma kayi zaton magani kawai ze iya warkar dashi ,ko alama. Wannan ciwon na buk'atar mataimaka ,musamman ma na MISBAHU daya masa mugun kamu. Dole ne se an kiyaye wasu abubuwan. Duk wani abunda baya so ya zama wajibi a Nisan ta shi da ganin shi ,a kuma yi k'ok'ari wajen faranta masa ta hanyar abunda yake so ko yafi so ,kar a barshi ya kad'aita shi kad'ai a guri ,Dan zaman kad'aici ne ke janyo har mutum ya fara tunanin abunda bashi bane. Sannan stress ya masa yawa ,yana buk'atar ya samu Hutu sosai Dan dawo da kuzarin jikin shi. Kaga wa'yannan abubuwan Dana gaya maka a yanzu ,matuqar aka kuskure ayin Abu d'aya gaskiya labarin ze sha banban ,saboda da wannan kad'ai ne zamu iya shawo kan abun cikin sauqi ,karka manta yana da hawan jini, Wanda shima ya taimaka wajen janyo masa wannan ciwon ,jinin shi yahau kuma fiye da tunanin ka. To me kake tunanin rashin kulawa ga mutum me hawan jini da kasawar zuciya? A gaskiya rayuwar MISBAHU na kokuwa ne tsakanin rayuwa da mutuwa. Zan d'ora shi akan magani na biyu ,Wanda muna fatar Allah yasa a dace. Badan ma yana kokari wajen yak'i da zuciyar shi ba ,da abun yafi haka ,da alama abubuwan sun soma fin k'arfin shine shiyasa har ya ciwon ya damk'e shi sosai. Yanzu an masa duk wani abunda ya kamata ,sannan akwai allurar bacci a cikin drip din da ake saka mishi ,idan ya k'are ze iya farkawa a koda yaushe ,amma yana buqatar isash-shen bacci ,saboda haka idan ma be farka akan lokaci ba kar kayi tunanin ko wata matsala ne ,a bash-shi yayi"... Tunda Dr Zaidu ya fara bayani Hajj Jamil ya shiga cikin matsanancin tashin hankali da rud'ani "hawan jini da kasawar zuciyar? Kuma ze iya rasa ran sa akoda yaushe?" Shine abunda hajj Jamil keta maimaitawa a k'asan ran shi. Godia sosai yawa Dr Zaidu ,sannan ya tashi ya fice jiki ba k'wari. D'akin hutun da aka kai Daddy nan ya nufa kai tsaye. Kujeran dake gefen gadon ya samu ya zauna, tare da tsurawa daddy idanu, baccin da yake yi da yanayin yadda yake fitar da numfashi dak'yar kai da ka gani kasan na wahala ne. Nan danan hawaye suka fara bin kuncin Hajj Jamil, kuka yake sosai ,musamman idan ya tuno da Dalilin shigar aminin shi wannan halin iyalan shine. Kwana yayi zubadda k'walla da Allah wadai matan daddy, gefe d'aya kuma idan ya tuna da sharud'od'in da Dr. Ya gindaye se ya fara tunanin taya za'a fara ,bayan _GIDAN MISBAHU_ gida ne daba d'igon kwanciyar hankali a ciki,,,Gida ne daba abunda ke k'unshe a cikin shi se tarin k'unci da takaici. A iya abubuwan da suke faruwa da Daddy ,ba k'aramin namijin k'ok'ari yaga yayi ba ,sama da shekaru yana fama da Abu d'aya, ba wani ci gaba ,a maimakon ma a samu ci Gaba da daidaiton al-amurra a'ah se ma dad'a rugujewa da komai ke yi. A daren ranar Hajj Jamil kwana yayi kusa da Daddy yana ta tufka da warwaren yadda ze b'ullowa wannan al'amari na _GIDAN MISBAHU_. MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [7/25, 8:19 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA ASHIRIN_ *_____________________* _Har Washe gari Daddy be farfad'o ba. Yadda Hajj Jamil yaga dare haka yaga safiya ,gaba d'aya bacci yayi k'aura daga idanuwan shi, Masallaci ma kasa zuwa yayi ,se dai ya kira Dr.Zaidu ya aiko masa da sallaya. Toilet din cikin d'akin ya shiga yayi alwala , koda ya fito ,wata nurse yaga ni ta ajiye masa sallayar kan kujera ,duba Daddy tayi dahar lokacin yake bacci ,tayi wasu 'yan rubuce-rubuce irin nasu na majinyatar lafiya ,kafin tayi ficewar ta._ _Hajj Jamil har yayi kabbara ze tada sallah ,ya tuno da gaba d'aya jiya ya manta be yi sallar magrib da isha'i ba ,mamaki ne ya kama shi ,a ranshi yake cewa wannan wani irin makuwa ne yayi jiya? Tunda yake be tab'a had'a sallah ba, amma Daya tuno da halin dayaga daddy a Daren jiya duk se jikin shi ya sake yin sanyi._ _Haka dai yayi ta jero salloli ,bayan ya gama ya zauna kan sallaya ,yafi sama da awa biyu yana kai wa Allah k'arar GIDAN MISBAHU. Har rana ta fito sosai ba yada labari ,kasancewar d'akin da suke ko ina a kulle yake ,babu wani kafa dazaka iya hango hasken waje, sedai iya fitullun dake d'akin masu haske ,Ga sanyin A/C daya karad'e d'akin._ _wayar shi ya janyo ,sakamakon hasken daya ga tana fiddawa ,alamar shigowar kira. Sunan Haajar ya gani akan screen d'in. Wani d'an guntun ajiyan Zuciya ya sauke ,shi gaba d'aya ma ya manta dasu ,gashi ya kamata ya sanar dasu ,saboda yasan zasu yi ta jiran shi, amma kuma koda ze kira sedai ko ya sanar da Haajar ita kad'ai, saboda yasan idan su suxee suka Sani dole zasu shiga wani hali ,musamman idan muka duba yadda daddy ya zame musu uwa da uba, a gurin shi kad'ai suke jin sanyi da dad'in rayuwa, inba yanzu da suka koma gidan Hajj Jamil ba ,shine fa abubuwa suka fara daidaituwar musu..._ _Har kiran ya tsinke Hajj Jamil be Sani ba ,saboda d'an gajeren tunanin daya fa d'a. Seda ta sake kiran shi akaro na biyu sannan ya d'auka tare da yin sallama._ _daga b'angaren Haajar ma sallamar tayi ,bayan sun gaisa cike da damuwa take tambayar shi a ina kwana?_ "Abbu sameer Hankalin mu gaba d'aya ya tashi ,musamman ma Hajiya k'arama ,tun jiya ta karb'a numbern ka take ta kira ,ta kira yafi sau a k'irga, amma baka d'auka ba." A nutse Hajj Jamil ya rufe idanuwan shi ,sannan ya sake bud'e su. Gaba d'aya baya so yaji abunda ze dami yaran daddy a rayuwa, wani d'aci yake ji a k'asan zuciyar shi duk lokacin daze ga ko yaji matsala a tattare dasu. "Tana ina yanzu?" Hajj Jamil ya tambaya Haajar tace "ta shiga wanka" "Ke kad'ai ce a wurin da kike?" Hajj Jamil ya sake tambayar ta Tace "Eh! Ni kad'ai ce." Wani siririn ajiyar zuciya ya sake saukewa a karo na biyu ,kafin ya soma bama Haajar labarin dalilin daya hana shi kwana a gida, ya k'arasa zancen da cewa "Amma bana son su Hajiya k'arama su Sani ,hankalin su ze tashi. Ki dafo abinci ki kawo ,nasan idan ya farfad'o ze iya Neman abinci". Nan ya kwanta mata asibitin ,yace tasa drivern gida ya kawo ta. Iya tashin hankali Haajar ta shiga tashin hankali, bata dad'e da sanin Daddy ba ,amma kuma ta rasa me yasa ta damu da komai nashi. A kid'ime ta amsa da " toh" ,suna cikin wayar ne Suxee ta fito wanka ,tana tsane ruwan jikin ta ,ganin Haajar na waya yasa ta k'araso da sauri tana tambayar ta "Abbu sameer ne?" Gyad'a mata kai Haajar tayi alamar Eh. Ai Suxee bata jira Haajar ta bata wayar ba ta fizge tare manna wa a d'an madaidaicin kunnen ta na gefen hagu, a lokaci d'aya tana fad'in "Abbu sameer lafiya kake kuwa ? Meya same ka? Meyasa bakwa kwana a gida ba jiya? Hankalin mu ya tashi sosai ,jiya ban iya yin bacci ba, gashi nata kiran wayar ka baka d'aga ba. Me yake faruwa ne??" Dika a lokaci d'aya ta shiga jero masa tambayoyi ba k'ak'k'autawa. Wani irin lumshe ido Hajj Jamil yayi ,a lokaci d'aya kuma yadda Suxee ke masa magana yaso ya bashi dariya... Jin yayi shiru yasa ta fara hawaye, a tunanin ta ko yana cikin matsala ne ,dama gata gwanar kuka ,Hausa wa suka ce _tusa hali balle anci wake_. Jin da yayi alamar kamar ta fara kuka yasa ,yayi saurin amsa ta da cewa "A'ah Hajiya k'arama lafiya ta qalau ,wata 'yar matsala ce kawai ta hana ni dawo wa jiyan" Har lokacin bata dena ruwan hawayen ba, cikin muryar kuka tace "kace lafiyar ka qalau ,kuma kace wata 'yar matsala ce ta hana ka dawo wa jiya ,alamaun kenan dai kana cikin matsala" ta k'arasa maganan tare da fashewa da wani sabon kuka kamar wacce aka daka Dafe Kai Hajj Jamil yayi tare da cewa "wai ni Allah na ,Hajiya k'arama rigima. To tsaya in miki baya kiji ni dakyau... Wani aboki na ne aka kira ni ba yada lafiya shine dani da Daddy muka zo duba shi ,to ba d'an garin nan bane, ba yada kowa anan ,shiyasa ni nakwana dashi ,daddy kuma an kira shi za'a sauke masa wasu kaya yau a store shiyasa ya tafi aida shi zan bari ya kwana anan ni kuma in dawo wajen Ku." Se a lokacin daya mata wannan bayanin ne tukunna ta samu kwanciyar hankali. Share hawayen ta tayi ,tare da cewa "Allah sarki ,Allah ya bashi lafiya! Muna yi masa ya jiki" Murmushi Hajj Jamil yayi tare da cewa "Ameen Hajiya ta. To kiyi dariya mana, bana son wannan k'ananan kukan". Wani murmushi ne ya k'wace mata ba tare da tayi niyyan yi ba Wanda ke k'ara fito mata da asirin kyawun ta, daga b'angaren shima ,murmushin yayi kamar yana ganin ta tare da cewa " Good gurl. Se anjima idan na kira ko?" Gyad'a masa kai tayi kamar yana ganin ta ,se kuma tace "OK take care". Kafin suka aje wayar. Haajar tuni ta b'ace a wajen ,ta shiga hada-hadar girkin da zata kai. Dan gaba daya hankalin ta baya jikin ta ,burin ta kawai shine taje taga wani hali Daddy ke ciki... Daga b'angaren Hajj Jamil kuwa ,bayan ya kashe wayar ,murmushi ne d'auke a fuskar shi ,cikin zuciyar shi yake raya stubbornness irin na Suxee, yarinyar na burge shi ,musamman yadda bata iya b'oye damuwar ta, kai tsaye ce ita. A fili kuma ya furta " Suxee rigima ". Mamaki ne ya kamashi lokacin daya duba agogo yaga sha biyu saura na rana ,duban shi ya maida inda Daddy ke kwance akan gadon asibiti, se ya fara tunanin meya sa Daddy be farka ba har zuwa wannan lokacin??? Nan kuma hankalin shi ya sake tashi... MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [7/26, 2:26 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA ASHIRIN DA D'AYA_ *____________________________* _Har ya yanke shawaran yaje ya sanar da Dr.Zaidu, se kuma ya tuna maganar da Dr Zaidun ya gaya masa jiya ,akan an masa allurorin bacci masu k'arfi ,amma ze iya farkawa a koda yaushe,,,,, 'to amma me yasa be farka ba har yanzu?' Hajj Jamil ya tambayi kan shi..._ _Sallar azahar ma kasa fita yayi ,anan cikin d'akin ya sake yin sallah ,Dan gaba d'aya jikin shi ya soma yin sanyi. Wuraren k'arfe uku na rana Haajar ta masa waya akan gata tazo asibitin, ya gaya mata suna Amenity room3. Bata wani sha wahala ba ta gane d'akin ,knocking ta masa ya bata izinin ta shigo, tura k'ofar tayi ta shiga bakin ta d'auke da sallama._ _Gaishe da Hajj Jamil tayi cike da girmamawa ,kafin ta ajiye basket d'in data zo dashi na abinci ,taja kujeran dake gefen gadon ta zauna._ _Ido ta zubawa Daddy nad'an wani lokaci, Gaba d'aya se da ta k'are masa kallo ,se taga kamar ba daddyn data Sani bane a kwanaki bakwai dasuka wuce ,ganin duk yabi ya rame yayi bak'i, tausayin shine ya k'ara kamata ,dukda bata San menene ainahin abunda ke damun shi ba,,, duban ta ta maida ga Hajj Jamil Wanda badan Daddy bane a kwance ,zaka d'auka shine Mara lafiyan, duk yabi yayi wani zuru-zuru. Fasa maganan da zata yi tayi._ _tashi tayi ta nufi basket d'in da tazo dashi. Flask ta Ciro ta aje gefe sannan ta d'auko cup da k'aramin spoon na shan tea. Tea ta had'a me kauri sosai Wanda ruwan zafin yaji kayan k'amshi ,sannan ta zuba doya da sauce d'in k'wai a plate ta kai gaban Hajj Jamil inda yake zaune kan sallaya ,ta aje masa, Dan base ta tambaya ba daga ganin shi akwai yunwa a tattare dashi. Ai Hajj Jamil kamar yana jira ,Kofin tean ya d'auka tare dakai wa bakin shi ,duk da irin zafi da tean yake dashi ,kurb'a ukku yayi sedai ya aje kofi, kan kace me zufa ya fara karyo masa ,Dan idan be manta ba rabon shi da abinci ,tun jiya war haka, A hankali ya fara cin doyan ,seda yaci sosai sannan yayi hamdala tareda ajiye cokalin me yatsu. Ruwan roba me sanyi ta sake kai masa ,ya karb'a yasha. Se a lokacin yaji kuzarin shi ya fara dawowa ba._ "Ya kika baro su Auta?" Ya tambaye ta. Tace "Lafiyan su qalau ,dak'yar ma na sab'e mata ai ,seda na had'a ta da chocolate sannan ta banni na fito. Su suxee kuma na gaya musu zanje duba abokin ka da aka kwantar a asibiti, Hajiya k'arama taso ta biyo ni ,Dan ita gaba d'aya jikin ta yak'i ya bata, gani take yi kamar Kaine ba kada lafiya! Se da nayi ta bata baki tare da cewa ta d'ora mana girkin dare kafin in dawo ,shine fa ta hak'ura da zuwan." Murmushi Hajj Jamil yayi Dan yasan Dole za'a zo wajen. Wani murmushin ya sake yi a Karo na biyu ,sedai wannan kaida ka gani kasan na k'unci ne sa takaici. Yace "Ki duba ki gani ,sun damu dani fiye da yadda bakya tunani ,suna mun kallo d'aya da mahaifin su kuma saboda shi. Yanzu ki qaddara sun samu labarin mahaifin nasu ne a kwance , me kike tunanin ze faru?" Jinjina kai Haajar tayi ,tare da cewa "hakane kam! Suna da nuna damuwa da mutum sosai ,kuma kamar yadda la lura akwai shak'uwa me tsanani a tsakanin su"... Kad'a kai kawai Hajj Jamil yayi tare da cewa "Shine farin cikin su ,kuma shima sune kad'ai yake duba yaji sanyi a rayuwar shi. Akwai shak'uwa tsakanin su fiye da yadda tunanin ki ke baki" Gyara zama Haajar tayi kafin tace "To amma meke damun shi ne haka ,wani irin ciwo ne wannan ,kuma menene dalilin ciwon?" Ta jero masa tambayoyin Jere da juna. "Heart failure ,da hawan jini ke damun shi".. Ya bata amsa a tak'aice. Zaro ido Haajar ta shiga yi tare da maimaita maganan " Heart failure da hawan jini??" Idon ta takai inda Daddy ke kwance cike da tausayin shi ta furta _"Inna lillahi wa'inna ilaihi raji'un "_... " Amma taya akayi wannan gagaruman ciwon ya had'u masa waje d'aya kuma a lokaci guda?" "Iyalan shi ne sanadi!" Hajj Jamil ya bata amsa. Da mamaki take bin shi da kallo ,alamar bata gane me yake cewa ba, tare da cewa "Amma taya ya iyalan sa zasu zama sune sanadiyyar nakasa masa rayuwa?" "Eh iyalan sa!" Ya sake maimaita mata. Ya d'ora da cewa "ko kina mamaki ne?" "Abun ne ai akwai mamaki. Iyalan sa fa?" Haajar ta maimaita. Be jira ta sake wurgo masa wani tambayar ba ,ya fara bata labarin Daddy ,tun daga farko har k'arshe ,be rage mata komai ba dan gane da rayuwar Daddy... MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [7/26, 9:36 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA ASHIRIN DA BIYU_ *____________________________* _Gaba d'aya jikin Haajar ne yayi sanyi matuqa, girgiza kai ta shiga yi a lokaci d'aya wasu hawayen tausayin Daddy na sauko wa daga idanuwan ta. Tun da take a rayuwar ta bata tab'a cin karo da wani labari me kama da wanda taji yanzu ba balle makamancin shi, da wani ne yake bata wannan labarin ba qanin mahaifin taba ,shakka babu ba zata gasgata wannan batu ba ,ta kuma San a tsakanin ta da Hajj Jamil akwai wasa amma ba irin wannan ba._ _Haajar mace ce me tausayi da saurin karaya. share hawayen ta tayi a hankali ta furta "Abbu Sameer!" ,,,, d'ago ido Hajj Jamil yayi yana kallon ta. Tashi tayi daga inda take zaune ,ta koma gefen Hajj Jamil daidai inda yake zaune akan sallaya ta samu guri itama ta zauna._ _Magana ta fara yi masa k'asa-k'asa kamar me rad'a, ta yadda ba Wanda ze iya jiyo me suke fad'a, sun d'au sama da awa d'aya suna magana, daga k'arshe Hajj Jamil yace_ "To shikenan ,ni nasan abunda zanyi. Allah ya taimake mu baki d'aya". Haajar ta amsa da " Ameen". Sannan ta d'ora da cewa "to yanzu Abbu Sameer me ake ciki game da rashin lafiyar Daddy? Naga tunda na shigo be farka ba?" Hajj Jamil yace "Yadda kika ganshi haka ,haka yake tun Daren jiya, ni kaina abun ya soma damuna". Shiru ne ya biyo baya nad'an wani lokaci, kafin Haajar ta mik'e tsaye. Basket d'in da tazo dashi ta nufa, ruwan zam-zam ta d'auko had'e da kofi, dawowa tayi ta zauna ,tare da tsiyaya ruwan zam-zam d'in gaba d'aya a kofin kasancewar ruwan Nada yawa kuma kofin ma Nada d'an girma. _SURATUL FATIHA_ ta tofa k'afa bakwai kowacce da bismillan ta, tsiyaye wa tayi cikin gora, ta rage saura a kofin, sannan ta mik'awa Hajj Jamil tare da cewa " Abbu Sameer kayi k'ok'ari ka bashi yasha wannan ,ka rage kad'an ka shafe masa sauran a jiki ,tun daga tsakiyar kanshi har tafin k'afar shi. Gobe da safe ma haka ,se kayi amfani da na cikin goran, idan zan zo gobe zan zo da wani ,a k'alla a samu tsawon kwana uku ana masa haka ,da yaddan Allah koma wani irin ciwo ne ze samu waraka." Cike dajin dad'i Hajj Jamil yasa hannu ya karb'a tare da ajiye wa a gefen sa. Haajar tace "yanzu fa zaka masa base anjima ma" Yace "to ai kinga yanzu be farka ba ,na d'auka ko se idan ya farfad'o ne?" Girgiza kai Haajar tayi tare da cewa "A'ah yanzu za'a yi ,ai ma ze taimaka wasa wajen farfad'owan ,shiyasa nace zamuyi kamar na kwana ukku haka ,kafin muga yadda jikin yayi". Mik'e wa Hajj Jamil yayi ya fara k'ok'arin yin kamar yadda Haajar tace ,sedai ya kasa ma taya ze tsiyaya wa daddy ruwan a baki ,kasancewar bakin nashi a rufe yake. K'arasa wa Haajar tayi wurin gadon tana cewa " Bari kaga in taimaka maka." Ruwan kofin ta karb'a ta rik'e sannan matse hancin Daddy. Mik'e wa Hajj Jamil ruwan tayi ,tace "kayi bismillah ka bashi." Nan ya shiga tsiyaya wa daddy ruwan addu'an yana sha, seda taga yasha sosai ,sannan ta sake masa hanci tare sa cewa "Ya isa haka ,ka shafe masa sauran a jiki." D'an basu waje tayi ,saboda be halatta taga tsaraicin saba. Waje ta fita ,tace "Ina zuwa". Hajj Jamil yasan manufarta nayin haka ,murmushi kawai yayi sannan ya fara k'ok'arin shafe masa jikin sa. Tunda ya fara shafawa daddy ruwan Addu'an nan yake ta sauke ajiyan zuciya, Mamaki ne ya cika Hajj Jamil, Dan daddy yayi ajiyan zuciya kusan har so uku. A hankali Daddy ya fara k'ok'arin bud'e idanuwan shi ,ya sauke su akan Hajj Jamil, shi kuma mamaki ne da tsoron Allah ya kama shi ,da sauri ya k'araso yana wa daddy sannu. Daddy dake kwance ,ji yayi kamar an zare masa lakka ,ga kuma baya jin wani ciwo a tattare dashi ,se dai k'arfin jikin ne da kuzari babu. Farkawar Daddy yayi daidai da shigowar Haajar ,Hajj Jamil yace " kinga zuwan ki ya zame mana alkhairi, gashi wallahi har ya bud'e ido" Murmushi kawai Haajar tayi tare da cewa "Dama ze farka ,wuyar ta ayi ne dai kawai". Duban ta ta maida wurin Daddy tace " Sannu Daddy ya jikin naka?" Murya can k'asa daddy ya amsa mata da "ALHAMDULILLAHI!" Ta sake tambayar sa "kana jin wani Abu yanzu?" Girgiza mata kai yayi alamar A'ah. Kallon Hajj Jamil tayi da ikon Allah ya hana shi magana tace "Abbu Sameer ,inaga ze buqaci zagawa bayan gida ,kad'an kama shi ka kaishi." Kallon mamaki Hajj Jamil yake bin ta dashi ,yace "ta ina kuma ze iya wani zuwa toilet mutumin daya farka yanzu yanzu!" A hankali ta lumshe matsakaitan idanuwan ta, tare da nad'e hannun ta a k'irji ,tace "ka kaishi ka gani". Hajj Jamil be San ma'anar ta na cewa hakan ba ,amma ba yada wani zab'i daya wuce yayi yadda tace ,Dan Haajar d'in ce gaba d'aya ta rikid'e masa ,sanin daya mata Ashe ta wuce nan. A hankali Ya taimakawa Daddy ya tashi, toilet d'in cikin d'akin ya kaishi ,a mamakin shi suna shiga kamar Daddy na jira ,wani irin fitsari jawur kamar jini ,ga yawa ,sun kusa mintuna talatin a band'aki. Ruwa daddy ya shiga antaya wa tun daga saman kanshi ,sakamakon wani zafi daya ji yana taso masa ,had'i da kuskure bakin sa ,kafin nan suka fito. Ko kafin su fito ,Haajar ta had'a wa Daddy tea me kauri ,sedai bata saka Sikari a ciki ba. Koda suka fito ,ba lefi ya samu kuzari ba kamar yadda suka shiga ba ,Dan har tafiya yake da k'afar shi ,iya gefen shi kawai Hajj Jamil ya rik'o. Seda ya zaunar dashi ,sannan Haajar ta mik'a masa kofin tea-n. Hankali a kwance daddy ke kurb'an shayin sa, sedai wani d'an karan zufa daya shiga anbaliya yana wanke masa tun daga fuskar shi har zuwa cikin shi ,kamar an kwara masa ruwa. Duk Sanyin dake tashi ,be hana tsufan ci gaba da tsats-tsago masa ba. Hajj Jamil kallon Haajar yayi ,data ke tsaye ta had'a hannuwa biyu tana ta faman aikin murmushi A sanyaye ta furta "ALHAMDULILLAHI ALA KULLI HALIN! Sauqi ya samu... MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [7/27, 9:15 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA ASHIRIN DA UKU_ *___________________________* _Sosai jikin Daddy ya fara warewa ,har d'an hira suke tab'a wa sama-sama, se wuraren bayan magrib Hajj Jamil ya kira driven shi yazo ya maida Haajar gida. Washe gari tun da wuri ta fara shirin koma wa asibitin dan dubo jikin Daddy, tuwan semo tayi masa da miyar kub'ewa d'anye Wanda yaji bushash-shen kifi ,se Farfesun kayan jiki daya ji kayan k'amshi, har ta kusa kammala wa ta tuno da bata d'ora ruwan zafin tea ba ,da sauri ta kunna d'an k'aramin gas d'in da ba komai akai ta d'ora tare da saka kayan k'amshi,,,, duk d'ora da saukewan nan da Haajar ke yi, ba abunda ta dafa ba tare da ta tsiyaya MA'UL WARDI (ROSE WATER) a ciki ba, musamman a ruwan shayin ,se da ta kusa juye Rabin kwalbar MA'UL WARDIN, seda ta kammala komai sannan ta gasa musu bredi Wanda yaji butter ,k'wai dafaffe da kayan miya, wannan kuma tayi ne Dan Neman sauyi ,amaimakon takai bredin gayan shi ,se tada'an masa mahad'i..._ _Cikin lokaci ta kammala komai da komai ,ta jera a kwando ,fridge d'in kitchen d'in ta bud'e tare da d'auko wani d'an madaidaicin bowl me marfi ,fruit ne a ciki ya kuwa yi sanyi. K'arfe Tara na safe ,drivern Hajj yazo yana jiran ta. Bata yi k'ok'arin tashin su suxee ba ganin suna bacci ,sedai ta ajiye musu nasu breakfast din kan dinning yadda idan suka tashi base sun wahala ba ,ci kawai zasu yi._ _Ruwa ta sake watsawa ,bata wani b'ata lokaci ba ta shirya cikin atamfa d'in kin Riga da sket Wanda yabi jikin ta, mai kawai ta Shafa se madaran turare na jiki me sanyin k'amshi, sanin data yi na Haramun ne mace ta fita tana k'amshi yasa ,bata fesa turare a kayan ta, tana k'amshi amma ba me tashi sosai d'in nan ba ,k'amshi irin se Wanda ke kusa da ita sosai ze iya jiyo shi,,, Abaya ta d'ora akan kayan tare da yin rolling da mayafin. Duk da ba wani kwalliya tayi sosai ba amma kuma tayi matuqar yin kyau. Kwandon kayan abincin ta rik'o da hannu d'aya, d'ayan hannun ta kuma tana rik'e da wayar ta._ _Kamilu na ganin ta fito da sauri ya k'araso Dan ya karb'a kayan hannun ta. Fuskar Haajar d'auke da fara'a tace_ "Lah! A'ah Allah malam kamilu dama ka barshi ,muyi sauri mu tafi dai ,lokaci na k'ure wa." Gidan baya ta bud'e ta aje kwandon ,sannan ta bud'e gidan gaba ta shiga. Cikin mintunan da basu gaza goma zuwa sha biyar ba ,suka isa asibitin. Tura k'ofar d'akin tayi ta shiga tare da sallama. Ba kowa a d'akin ,D'aga idon da zatayi ta hango Daddy a zaune akan sallaya ,da alama ramakon salloli yake yi ,motsin ruwan data jiyo a bayi ya tabbatar Mata da Hajj Jamil ne a ciki. Cike da farin ciki ta samu guri ta zauna ,tana d'an danna wayar ta ,a hankali kuma tana d'agowa tana duba Daddy taga ko ya idar da sallan. Hajj Jamil na fitowa ya ganta ,k'ara fad'ad'a murmushin dake fuskar shi yayi ,yana fad'in "A'ah har kin zo kenan ?" Tace "Allah ya nufa Abbu Sameer. An tashi lafiya?" "Lafiya qlau, Alhamdulillah. Ya su Auta?" Tace "lafiyan su qlau ,ai basu ma San na fito ba ,Dan bacci suke yi koda na fito ,ni kuma bana so in tashe su shiyasa". Hajj Jamil yace " Ah hakan ma yayi kyau" "Abbu Sameer yame jiki?" Haajar ta tambaya cike da kulawa Yace "Alhamdulillahi Haajr ,Jiki da sauqi sosai ,gashi nan ma yana sallah. Ai ke da kin gani kin San jiki yayi kyau". Murmushi sosai Haajar ke yi Wanda yayi sanadiyyar bayyanar fararen hak'oran ta ,tare da cewa " gaskiya kam jiki yayi kyau. Allah yasa kaffara ne" Bayan Daddy ya idar da sallah ,Haajar ta masa ya jiki ,har cikin zuciyar shi yake jin dad'in yadda take nuna damuwa akan shi da 'ya'yan shi. Addu'a tayi masa Wanda Manzon Allah s.a.w ya koyar damu idan ka ziyarci Mara lafiya ,ka karanta: " لاَ بَأْسَ طَهُورٌ إِنْ شَاءَ اللَّهُ Laa ba'sa tahoorun 'inshaa'Allaah. : أَسْأَلُ اللَّهَ الْعَظِيمَ، رَبَّ الْعَرْشِ الْعَظِيمِ أَنْ يَشْفِيَكَ 'As'alullaahal-'Adheema Rabbal-'Arshil-'Adheemi 'an yashfiyaka.( k'afa bakwai)... Daddy jin yayi Haajar ta k'ara kwanta masa arai ,komai nata cikin hankali da nutsuwa take gudanar dashi. Da kanta tayi serving d'in su ,Tas daddy ya cinye har da Neman k'ari ,ga uban santi daya ke ta zuba wa, Hajj Jamil da Haajar se dariya suke masa ,Dan Daddy badai barkwanci ba ,haka yayi ta basu dariya, se dai be jima da gaba cin abincin ba ,Se wani amai ya taso masa ,da sauri ya tashi ya nufi toilet ,har saura kad'an ya fad'i, wani irin amai bak'ik'irin ya shiga kwararawa ba girma ba azziki kamar Wanda yaci guba, ba shiri Hajj Jamil ya aje plate d'in da yake cin abinci ya tashi ze nufi toilet d'in. Haajar tace "Abbu sameer ka bash-shi yayi aman shine samun sauk'in shi ,dama nasan dole zeyi aman saboda da MA'UL WARDI na dafa masa ruwan shayi ,kuma shi dama MA'UL WARDI haka yake ,indai kana tunanin ko an yiwa mutum sihiri ne ,zaka saka a abinci mutum yaci ,ko kuma ma kaba mutum shi zallah yasha ,tare da tofa wasu Addu'o'i karya sihiri na sirri, saboda haka karka wani tashi hankalin ka ,ka duba kaga ni idan ya gama seka taimaka masa ya wanke jikin sa. Gaba d'aya jikin Hajj Jamil duk yayi sanyi ,haka ya nufi toilet d'in, yadda ya ga Daddy na kwarara amai ga aman ba kyan wani ba k'aramin tausaya masa yayi ba. Sun kusa minti talatin a toilet d'in kafin suka fito ,Jikin Daddy har wani karkarwan sanyi yake yi ,gado ya koma ya kwanta ,Hajj Jamil yaja masa abun rufa ,tare da rage k'arfin Sanyin A/C, saboda yadda yaga jikin shi na wani cira. Kusan dai daddy ranar a kwance ya wuni da zazzab'i, Dr.Zaidu kuma na iya bakin k'ok'arin shi ,dukda be San wainar da ake toyawa ba. Ranar Haajar bata wani jima ba sosai a asibitin ta koma gida. Kwana ukku ,duk tayiwa Daddy abinci da MA'UL WARDI se yayi irin wannan aman daya yi kwana biyu da suka wuce ,se dai ba kamar ranar daya fara yi ba. A hankali sauk'i na samuwa. Satin shi d'aya Haajar na iya bakin k'ok'arin ta ,Alhamdulillahi daddy ya samu sauqi tangaram, shi da kanshi ya lura da akwai abunda Haajar ke sako masa a abinci da idan yaci yake saka shi wannan aman ,amma shi kan shi yasan ba aman lafiya bane yake yi ,ga kuma wasu sababbin canji daya ke ji a jikin shi, har wani raman wahala yayi ,yayi bak'i... Bayan sati d'aya Daddy ya samu kanshi ,aka sallame shi daga asibiti, Tare da Haajar gaba d'aya suka wuce gidan Hajj Jamil. Bayan sun zauna Hajj Jamil ke cewa "Nifa inaganin idan zaka koma gida tare dasu Auta zaka tafi saboda suna kewar ka sosai ,se dai wannan karon tare da Haajar zaku tafi ,taje tad'an kwana biyu tunda dama anan d'in ba kowa Zaliha bata dawo ba har yanzu ,daga ita ne se 'yan aiki ,itama idan taje can d'in zata fi sake wa ,kuma kaga zata kula dasu Auta".. Daddy ya dad'e yana jinjina lamarin ,har k'asan zuciyar shi yaji dad'i ,amma be San yadda Haajar zata d'auki lamarin ba. Ganin yayi shiru yasa Hajj Jamil cewa " ko hakan be maka bane?" Ajiyan zuciya Daddy ya sauke ,kafin yace "ba wai be mun bane. Ni inaga ita Haajar d'in zata amince kuwa? Karfa mu cika zak'e mata da yawa ,d'an Abun azzikin ma da take yi mana tazo ta dena". Daddy ya fad'a iya gaskiyar sh. Dariya maganan yaba Hajj Jamil yace " Haajar fa 'ya tace ,kuma kaima 'yar ka ce" Wani kallo daddy ya masa alamar ta ina? Hajj Jamil daya gane cewa yana son k'arin bayani yasa yace "Kaddai kace mun baka San Haajar ba? Ko da yake ba lallai kasanta ba ,Dan ba'anan take zaune ba ,tana can tare da Asadussunnah a Sudan ,da wani aiki yakai shi can shine ya tafi da ita ,acan tayi karatun ta, kwatakwata bata shekara biyu da dawowa Nigeria ba" Zaro ido daddy ya shiga yi tare da cewa "kaddai kace mun 'yar Asadussunnah ce Haajar? Lallai kuma idan hakane nayi b'atan kai, mutum da 'yar shi sukutum" Hajj Jamil yace "Aikuwa dai" Mahaifin Haajar Dr. Imam Ali Asadussunnah ,shahararren malamin addini ne daya shahara ba a iya jahar shi ta jigawa kad'ai ba ,Nigeria da kewaye babu inda sunan shi da alkhairan sa na fad'akarwa be zaga ba, a b'angare d'aya kuma k'wararre ne kuma likita ne wajen had'a magungunan Islamic... Wannan kad'an kenan... *__________________________* Garin kano... Hajiya Gwaggo ta dage se shirye-shiryen bikin suke yi ita da dangin amarya ,Amarya lubabatu kuwa ta gama shirin ta tsab na amarcewa a gidan daddy, koda yaushe tana sashen Hajiya Gwaggo ,daga su kitsa wannan se su kwance wancan. Ko da bansan me suke kitsewa ba ,amma daga gani kai kasan ba alkhairi bane... MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [7/28, 9:41 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA ASHIRIN DA HUD'U_ *___________________________* _A Ranar da suka dawo gidan ,a ranar Suxee da Haseena suka zazzaga da Haajar ko ina na gidan ,tare da nunnuna mata wasu abubuwan ,a sashen kubra sukayi branch har ita ,saboda su suxee ,bata son duk wani Abu daze sa tayi nisa dasu._ _Duk da basu da masaniyar ko tasan komai game da gidan su ,amma shak'uwar su da ita yasa suka kasa b'oye mata komai, duk wani Abu na rayuwar gidan a wuni d'aya ta San shi ,hakan kuma ba k'aramin taimaka mata ze yi ba ta fannin zamantakewar ta a gida. Auta kuma kamar an tsoma ya a aljannah ,Dan kuwa murna take sosai da suka taho tare da Haajar gidan su._ _A ranar base gobe ba ,Haajar tasa aka fitar da duk wani na'urar jin sauti a gidan ba tare da wani shakku ko tsoron me ze je ya dawo ba. Haka ma duk wani hoton bango ,se dai na iya sashen Daddy kawai tasa aka kwashe aka k'ona su. Ita dasu Suxee suka shiga sashen ,suka gyara masa shi ,gyara Wanda tun da yake be tab'a samun irin sa ba ,Dan seda ta sauya wa komai mazauni ,idan ba ka lura dakyau ba ,kana shiga sashen zaka zata ko wasu kayayyakin aka sauya, Hatta kayan daddy na cikin Sip seda ta fito dasu duka ,wani abun mamaki data bi kayan d'aya bayan seta ga akwai killatattun kayan da akawa alama da farin zari ta wuya ,mamakin duniya ne ya hana ta magana ,kwatakwata jikin ta be bata daidai ba ,Dan haka tabi kayan d'aya bayan d'aya, duk Wanda ta gani da wannan alamar seda ta tsame shi, sannan ta maida masa sauran ta Jere su tsaf ,komai ta nema masa mazaunin sa na musamman, hatta filon kwanciya da Khaltum ta kawo guda d'aya na mugun abun ta seda Haajar ta sauya wani,,,, seda ta fara turara 'ya'yan Habbatussauda ,sannan ta bishi da turaren wuta me masifar k'amshi, kan kace me wuri ya zagaye da wani daddad'an k'amshi, Wanda kafin ka iya gano ainahin wani irin turare ne ,sedai idan dama ka sama tu'ammali da kayan k'amshi ne kad'ai. Ko ina k'amshi ke tashi ,tun daga dosowa farkon shiva sashen ,parlou ne ,duka d'akuna ukun dake zagaye da parloun da ban d'akin su ,hatta kayan Daddy idan ka bud'e sip din k'amshin turaren kaga na maza ne zaka ji yana bugar k'ofofin hancin ka. Seda ta tabbata an gyara komai ,sannan ta ciro m-card d'in wayar ta ,tayi placing a manyan na'aurar sautin dake parloun, cikin sakan talatin tayi setting d'in komai ,se ga k'ira'ar AHAMD SULEIMAN na tashi a karo na farko a sashen Daddy._ _Gaba d'aya yaran jin su suke kamar a wata sabuwar duniyar daban sab'anin Wanda suke ciki a yanzu. Da daddare tare suka shiga kitchen ,girke-girke sukayi sosai ,sedai babu na Daddy a ciki ,daban Haajar tayi masa nasa saboda rashin lafiyar hawan jinin shi._ _A karo na farko da masu aikin gidan suka ci abincin gidan ,Dan gaba d'aya Haajar seda ta aika musu da abincin data girka had'i da abun sha me sanyi. Ranar kowa ya tabbatar da Haajar tazo GIDAN MISBAHU, Dan alama na sauyin nayi daya kai wa ahalin gidan ziyara._ _Da daddare bayan daddy ya dawo yaga abubuwan ban mamaki ,gaba d'aya gidan se yake gani kamar ba gidan daya Sani ba ,Dan tun daga gate masu gadi suka fara cewa Daddy sun ga abun alkhairi ,a taya su yiwa Hajiya Godia, duk da be San wata Hajiya suke nufi ba da kuma alkhairin da suke magana tayi musu ,tunani ya fara yi ,ko su kubra sun dawo ne? Wata zuciyar tace masa "Alkhairi daga wajen su kubra anya Abu ne me matuqar wahalar gaske"... Da wannan tunani-tunanin daddy ya k'arasa ciki... Shi dai daddy da ido ya dinga bin su ,be kashe k'wark'watan idon shiba ,se da ya doshi sashen shi ,wani irin masihircin k'amshi me sanya nutsuwa ya daki madaidaitan k'ofar hancin shi ,bin ko ina yake da kallo kamar yau ne rana ta farko daya fara shigowa sashen nashi. Zama yayi kan kujera mazaunin mutum d'aya, tare da jinginar da kanshi had'ida lumshe matsakaitan idanuwan shi ,a lokaci d'aya kuma yana k'ara shak'ar daddad'an k'amshin dake ambiya a parloun, ya jima a haka ,kafin ya shiga d'aki Dan rage kayan jikin shi ,nan ma kusan idanuwan shi zazzago ne basu yi ,Dan ganin abun mamaki. Daya shiga toilet Dan watsa ruwa kusan mintunan shi sama da talatin ya kasa fitowa ,ji yake kamar ya kwana a ciki, Hamdala ya sake yiwa ubangiji daya kawo masa sauyi a rayuwar shi cikin d'an k'ank'anin lokaci, ji yake ina ma ace Haajar matar shice ,gaskiya da se yafi kowa sa'ar mata, amma ta ina ma hakan ze yiwu? Wata zuciyar kuma tace masa ,ka fiye zak'ewa MISBAHU, daga ganin sarkin fawa se miya tayi zak'i?,,,,da sauri ya kauda wannan tunanin ,seda yayi sallah kafin ya fito parlour. A zazzaune ya tarar dasu Haajar kan kujeran dinning da alama shi suke jira suci abinci,,,, dikkan su sannu da zuwa suka masa fuskokin su d'auke da farin ciki ,shima ya amsa fuske a sake ,bayan ya zauna ya ke tuna rabon da yaga yaran shi cikin irin wannan farin cikin har ya manta. Amma se gashi rana d'aya, kusan har k'ok'arin manta wa da duk wani damuwar su suke yi ,ina ma ace farin ciki da walwala ze d'ore mana kamar haka,,, Daddy ya furta cikin ran shi... Dramar da ake yi wajen cin abincin ne ya dawo masa da hankalin sa. Cike da shagwab'a da samun wuri Auta tace "Ni fa Anty Haajar ni zaki fara zuba mawa" Wani siririn tsaki Haseena taja ,tare da cewa "kinga Anty Haajar Dan Allah ni ki fara zuba mun ,wallahi baki ji wani irin azababben yunwa da nake ji ba yau ,wannan irin aikin da muka tik'a da biyana za'ayi ai nasan kud'in da za'a bani yaci ya siya mun gida da mota har da 'yan chicken change"... Gaba d'aya wajen kowa dariya yake yi har Daddy, Haajar tace " Ayyo! To dama an gaya miki komai a banza ake samun shi? Ai komai na rayuwa da kike ganin shi dole seka wahala tukunna kake samun abunda kake so Haseena ,wannan kad'ai ma ya ishe ki darasi" "Aikam dai" Haseena ta fad'a tana jinjina kai. Auta aka fara zuba wa ,tana fad'in "yeeh Yaya haseena ni aka fara zuba mawa" ta k'arasa maganan tana mata gwalo. Kowa se dariya yake mata ,banda Haseena data cika tayi fam Dan kwatakwata ita ba tada hak'uri ne. Seda ta gama serving d'in kowa sannan ,taji da Daddy da ke cewa "Ai na d'auka 'ya'yan ki kad'ai kika sani ,saura kad'an Gidan Abinci yayi bak'o." Dariya dikkan su suka saka, seda daddy ya saki zancen sannan yama fara wai me nace ma? cewa fa nayi 'ya'yan ta ,kar yarinyar nan ta gano wani Abu a tattare dani fa, gaskiya ba k'aramar kwab'a nayi ba. Seda ya kalli kowa yaga hankalin sa baya kan shi ,kamar ma basu ji meya fad'a sosai ba da farko. Wani ajiyan zuciya ya sauke ,tare da furta Alhmdllh' a k'asan zuciyar shi, Dan shi Daddy Gaba d'aya ganin Haajar yake kamar matar shi ,musamman yadda suka zauna haka ,se yake ayyana inama ita kad'ai ce matar shi kuma uwar yaran shi ,lallai da yafi ko wani namiji alfahari da samun nagartacciyar iyali... Murmushi kawai yayi sannan yayi bismillah tare da kai abinci bakin shi. Duk wani motsin da yake be San a idon Haajar yake yin sa ba ,kawai dai ta share ne tayi kamar hankalin ta bata wajen shi. Cikin k'ank'anin lokaci daddy ya kauda abincin dake plate d'in shi ,dama ba wani da yawa ta zuba masa ba, ganin yana k'ok'arin bud'e kula ya k'ara ,Haajar tayi saurin taron hanzarin shi da cewa "Bari in k'ara maka ,murmushin jin dad'i yayi ,tare da cewa " Nagode? " Wani kulan daban Haajar ta bud'e ta zuba masa abincin dake ciki. Nan danan Daddy ya fara auna shi ciki,,,, sedai dak'yar ya k'arasa had'iye abincin bakin shi ,wani irin kallon menene wannan? Yake bin Haajar d'in dashi. Gira ta d'aga mai alamar akwai matsala ne? Daddy yace "Anya wannan abinci na ne kuwa?" "Me ka gani?" Haajar ta tambaya kamar bata San komai ba Yace "Naji abincin ne ba kamar irin Wanda na gama ci ba, kamar ma fa ba'asa gishiri ba ,ko me agwagi ne ake kiran sama na kasa ganewa!" Dariya dikkan su suka fashe dashi, haseena tace "Daddy me zabo ake cewa ,ba me agwagi ba". " komai dai menene Ku kuka San shi ,nida ba shiga kitchen nake ba ,taya zan wani San sunayen maggi?" Haajar ajiye cokalin hannun ta tayi ,tare da nad'e hannaye a k'irji tace "Wannan abincin daga yau irin shi zaka dinga ci ,saboda tsaro" Daddy wani zaro iro ya shiga yi tare da cewa " ni d'in kuma? Wai saboda me?" Haajar tace "ka manta masu rashin lafiyar hawan jini abincin su daban ne? To abincin ka kenan har se an gwada ka an tabbatar mana da baka tare wannan ciwon kuma, idan ka bani had'in kai ,wata d'aya yayi yawa kaga komai ya wuce ,ka fara cin abinci kamar namu?" Shiru Daddy yayi ,har cikin zuciyar shi yayi matuqar jin dad'in yadda Haajar take nuna damuwa da ciwon shi ,Dan shi yanzu har manta wa yake wai yana da hawan jini. Murmushin k'asan zuci yayi , a fili kuma ,had'e girar sama Dana k'asa yayi ,tare da cewa "Ba wani wata d'aya da zanyi ina cin wannan abincin gaskiya ,kuma bari ki gani" Basarwa Haajar tayi tare da cewa "OK fine". Auta ce tace " Anty Haajar nima a k'ara mun, amma ba irin na Daddy ba. "Oh no my baby girl! Ai bama zaki ci irin na Daddy ba , bari in k'ara miki kinji" Dariya sosai Auta ke yi , da gudu ta zagaye ta kujeran da daddy ke zaune ta rad'a masa a kunne "Daddy kaga na sake yiwa Anty Haajar wayo ko? Kamar yadda na mata wayo tazo gidan mu. Kaima ka dinga mata mayo irin nawa" Kusan dariya maganar Autan yaso yaba Daddy, shima rad'a ya mata kamar yadda tayi masa yace "Kice dama wayo kika mata ta biyo ki? To amma me kika ce mata?" With full confidence Auta tace "daddy ce mata nayi fa idan bata zo gidan muba ,kuka zan dinga yi kuma bazan sake zuwa makaranta ba, to shine ita kuma bata so inyi kuka kuma bata so in dena zuwa makaranta ,shine fa ta biyo mu".. Dariyar abun Daddy ya dinga yi ,tare da cewa " give me 5" bashi hannu Auta tayi suka kashe ,yace "Good girl ,u make it,,, maza je kici abincin ki kar Antyn ki ta gano kin gaya mun wayon da kika mata"... Da sauri Auta ta koma kujeran ta ta zauna tana dariya. Haseena tasowa tayi tazo wuce wa tace " Daddy inji abincin ka" wani irin Harara ya watsa mata ,daya sa tayi saurin rufe bakin ta tabar wurin tana dariya. Kallon Haajar yayi data gimtse dariyar ta yace "Kinga abunda kika janyo mun ko?" Tashi tayi itama tabar wurin tana masa dariya ,ba tare da ta amsa shiba. Parlour suka dawo suka zauna suna kallo cike da raha ,har kusan sha biyu na dare kafin suka koma sashen Kubra... *____________________________* Garin kano,,,, a kwana a tashi bikin Daddy da lubabutu ya rage saura sati biyu currrr! Shi Daddy Sam yama manta da zancen wani biki... MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [7/30, 1:42 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA ASHIRIN DA BIYAR_ *___________________________* _Hajiyar Daddy tayi iya bakin k'ok'arin ta wajen ganin ta binciko halayen Lubabatu Dana iyayen ta ,amma duk Wanda tasa binciken amsar guda d'aya ce ,cewar su d'in Mutanen kirki ne ,sedai lubabatun bazawara ce ta tab'a aure ,shekaran su biyu Allah ya yiwa mijin rasuwa. Wannan shine kad'ai abunda ta iya gano wa ,gashi tayi binciken yafi sau a k'irga amma bayan yabon lubabatu da iyayen ta ba abunda ke zuwa kunnen ta. Ita dai Hajiya hankalin ta be kwanta da hakan ba ,amma ba yadda ta iya dole ta koyarwa zuciyar ta natsuwa da kuma son wannan auren ,Dan sau tari ma idan ta zauna se tayi ta tunanin anya badan bata son auren bane yasa take kawo shakku da kokonto, wata zuciyar kuma tace mata ,duk wani abunda ze fito indai ta b'angaren Hajiya Gwaggo ne to babu alkhairi a cikin sa ,daga k'arshe dai wani sashen zuciyar nata yake ayyana mata cewar 'suwaiba ba yadda zaki yi kuma ba kida abun yi ,daya wuce ki mik'awa Allah wannan al-amarin sannan kuma ki dage da Addu'a tare da nema wa MISBAHU zab'in Allah da alkhairi a cikin wannan auren ,ki kuma ci Gaba da saka mishi albarka ,saboda Addu'ar uwa mace tamkar taki ne tsiro take. Wannan shine kad'ai mafita a wajen ki'... Wani ajiyan zuciya Hajiya ta sauke tare da furta "Allah ya maka jagoranchi acikin al-amurran ka MISBAHU... Wani iska ta furzar tare da tashi taci gaba da ayyukan ta nayau da kullum..._ _Hajiya Gwaggo duk yadda taso ayi cakwaikwaiwa a wannan bikin ya faskara ,saboda lubabatu ta hana ,a cewar ta ita batason bidi'a ,bayan walima babu abunda za'ayi shima se idan an d'aure aure ,yinin biki ma bayi zatayi ba ,saboda bata son duk wani abunda ze tab'arb'are albarkar auren ta ,riya da bidi'a kuma na d'aya daga cikin rukuni na farko dake hana albarkan aure. Badan Hajiya Gwaggo taso ba amma haka ta hak'ura Dan Dole ,Dan gaba d'aya se ma fara jin haushin Lubabatun tayi, a haka dai biki keta k'aratowa ,babu wani alama daga b'angarorin guda biyu da zaka gane cewa hidimar aure ake yi ,aure ne dai gashi nan yadda kasan ma auren na dole ne ,Dan komai a kaffa-kaffa da nuk'u-nuk'u ake yin shi ,ba kowa ne yasan da zancen sha'anin ba ,se na jikin su..._ *______________________* Ranar asabar ,ya kamata daddy na gida yinin ranar be lek'a koda k'ofar gida ba ,tun bayan daya dawo sallar asuba ,Dan kusan yanzu jam'i baya wucewa shi ,saboda akwai agogo me tunatar dashi koda ya shafa'a wato Haajar. Bayan ya dawo sallar azahar ,Gaba d'aya dashi dasu Haajar suka d'unguma zuwa gidan gonar shi ,dake ta bayan gidan shi ,Wanda akwai gate da za'a iya shiga kai tsaye ta cikin gidan shi ,tsabar tsafta da kula da wurin ke samu ba dare ba rana yasa idan ba ance maka da akwai gidan gona a wajen ba ,Abu ne me matuqar wuya ga iya ganewa sab'anin sauran gidan gonakin ,sedai d'an abunda ba'a rasa ba na yanayin dabbobi. Tun daga bakin gate Ma'aikatan wurin keta murna da zuwan daddy, duk Wanda ya gansu da sauri yake k'arasowa yana kwasar gaisuwa da mamakin ganin daddy a wannan lokacin ,bayan lokaci me tsawo daya d'auka baya kawowa wurin ziyara ,yau kuma se gashi. Sannu a hankali suka shiga zaga wajen suna d'an tab'a hirar yadda abubuwa suka k'ara bunk'asa a wajen , nau'i-nau'i na dabbobi indai naci ne a gida gasu nan barkatai ,kusan cikin wurin ma gaba d'aya ya yiwa wasu dabbobin kad'an dole seda aka killace wasu daga waje. A cikin hirar da suke yi ne jifa-jifa ,Haajar ke cewa " Ni kuwa Daddy wai kana fitar da zakkah kuwa?" Dariya maganar taba wa daddy, maimaitawa yayi "wai ma ina fitar da zakkah? To amma me kika gani?" Itama dariya taba kanta tace "Ah to eh mana, naga gidan gonar nan cike yake da albarkatun dabbobi ,amma banga alamar ana fitar da d'aya daga ciki ba ,Banga kuma alamar ana saida wa ba. Sannan ni a ganina iya wannan ma zaka iya fitar da zakka dashi ba ,ba Dole saka d'iba wani b'angare daga cikin dukiyar kaba". Daddy rage fara'ar dake fuskar ki yayi ,tare da cewa " A gaskiya Antyn Auta(haka yake kiran ta tun had'uwar su a gidan Hajj Jamil) bazan iya ce miki wani Abu dangane da gidan gonar nan ba, ke ni hasalima bansan komai dake gudana a gidan ba, maganar zakka ko makamancin wannan gaskiya bana yi ,ba kuma bana son yi bane ,duk lokacin dana k'udurci yin wani abun alkhairin wallahil azim se inji na kasa ,ban kuma San dalili ba ,kinga naman miya ma na gida siyan shi nake yi ,ina da me nama dake kawo mun duk wata." Tsabar mamaki ne ya hana Haajar magana ,tace "to idan ba zaka damu ba ,inaso inyi wani Abu akai ,Amma kafin nan muje mu gana da manajan dake kula da komai na wajen". Murmushi daddy yayi ,Dan shi harga Allah yana son Haajar a cikin al-amurran shi ,Dan hakan ba k'aramin ci gaba dake kawo masa ba. Ce mata yayi " Karki damu Antyn Auta ,na riga na miki izini da komai nawa tun ba yau ba" "Nagode sosai" Haajar ta fad'a cike dajin dad'i "Kar ki damu ,cancantar kice tasa hakan ,ai kinfi k'arfin hakan a waje na ,kana da kamar Wanda yaso naka ne?" Murmushi Haajar tayi tare da cewa "Babu" Yace "to kin gani ,Wanda yaso naka ,tamkar kai d'in yaso kacokam ,koba haka bane?" Daddy ya fad'a cike da raha Ita dai Haajar se faman murmushi take yi tace "Hakane kam" A haka dai suka suka k'arasa ciki wajen manager ,suna d'an tab'a hirar su na MAKAHON SO DA LINZAMI... Yayin da su suxee kuma suka tafi nasu yin a cikin gidan gonar... Da fara'a sosai maganer ya tarbe su ,wurin zama ya basu tare da d'auko musu abun sha ,Godia Haajar tayi masa dukda basu sha ba ,kafin ta fara masa tambayoyi akan yadda suke gudanar da aikin gidan gonar. A yadda manager ya sheda mata ,Komai na tafiya yadda ya kamata daga b'angaren su ,ana kuma samun ci gaba sosai ,ribar da ake samu kuma yana tafiya ne kai tsaye ta asusun bankin Kubra uwar gidan daddy. Mamaki ne sosai ya narkar da zuciyar Haajar lokacin da manager ya ambato adadin kimanin kud'ad'en dake shiga asusun bankin kubra a matsayin riba ,Wanda ya tabbatar musu da cewar, ba a cikin wa'yannan kud'in suke biyan ma'aikatan wajen ba ,ba kuma a ciki suke siyan duk wani abun da dabbobin ke buk'ata ba. Shidai Daddy nashi ido ne ,dukda shima ba kad'an ba ya shiga mamaki ,sedai ba yada wani abun da ze iyayi akai, a karo ba farko daya fara jin Kubra ba k'aramin yaudarar shi take ba ,Wanda ya k'ara tabbatar masa da cewar bata qaunar ci gaban shi a rayuwa. Haajar ce ta katse masa tunani data fara cewa "Duk naji bayanan ka manager na kuma fahimta, sedai za'a kawo wasu 'yan sauye-sauye Wanda ina fatar zamu samu had'in kan ka" "Insha Allahu ranki ya dad'e" cewar Manager Murmushi Haajar tayi tare da cewa "ze fi kyau ka kirani da Haajar shine sunana" Shima manager murmushi yayi tare da cewa "Ayi mun afuwa Hajiya Haajar" Ita ma dai murmushin ta sake yi masa ,sedai bata k'ara bi takan wannan jayayyar ba ,ta fara masa bayani kai tsaye akan hasashen zuciyar ta. "Amma kafin kaji sababbin tsare-tsaren da zamu kawo ,zan so sanin nawa ne albashin ma'aikatan gidan gonar nan Gaba d'aya" Haajar ta fad'a tare da maida hankalin ta kacokam wurin manager Dan jin bayanin sa dalla-dalla. A nutse manager ya fara mata bayani "Eh to, ma'aikatan namu dai sun kasu kashi uku ne: akwai k'ananan ma'aikata masu share share ,akwai masu kula da b'angaren abincin dabbobi akwai kuma masu kula da fannen cinikayya nayau da kullum. kamar dai k'ananan ma'aikatan mu nuna biyan su naira dubu ashirin da uku duk wata ,,, kashi na biyu kuma muna biyan su naira dubu talatin ,se mu kuma kamar ni misali ina d'aukar naira dubu Hamsin da biyu a wata... Kinji yadda lissafin yake" Wani siririn ajiyan zuciya Haajar ta sauke tare da cewa "Naji naka, nima kuma ina son ka saurari nawa kaji dakyau ,bana so a samu wani tangard'a. Abu na farko ,inaso a datse ribar da ake samu daga shiga asusun madam ,kai tsaye kud'in su dinga shiga asusun ajiyar Alhaji MISBAHU... Na biyu; zaku samu k'arin albashi bisa ga la'akari Dana yi na cewa aikin Ku yafi kud'in da ake biyan Ku ,wannan Abu ne me kyau kuma,,, daga yau ma'aikatan mu kashi na d'aya ,zan fara taKu kenan, albashin Ku ya tashi daga hamsin da biyu ,ya koma saba'in da biyu,,, kashi na biyu kuma daga naira dubu talatin zasu dawo suna d'aukar naira dubu Arba'in da biyar,,,, se kashi na uku masu d'aukar naira dubu ashirin da ukku zasu dinga d'aukan naira dubu talatin da biyar insha Allahu zamu fara daga watannan me kamawa" Wani irin wage baki manager keyi kamar Wanda akayi wa albishiri da aljannah, zama ya gyara sosai Dan jin sauran bayanan. Haajar ta d'ora da cewa " bayan wannan kuma ,duk watan Allah ,a dinga ibar kaji na gida Dana turawa ,a raba guda biyar tun daga farkon layin nan har k'arshe bance a cire kowa ba daga gida me gate har Mara gate , a kuma tabbatar da angyara kafin a raba musu ,Dan muradin mu shine sanya nishad'i a zukatan bayin Allah ,,,, sannan kuma ban cire kuba ,duk watan Allan nan idan ya kama ,duk ma'aikatan dake gidan gonar nan ,babba da yaro a basa kaji biyar. Abu na kusa dana k'arshe shine a bud'e gate d'in can na baya ,a kuma buga poster na tallata Nau'ikan dabbobin da muke dasu a gidan gonar nan ,ga duk me buk'ata k'ofa a bud'e take ,ze iya zuwa ya siya ,sannan adadin cinikin da mutum ya muku akwai percentage na bonus da zaku bashi ,Wanda idan na gama tsara komai zan aiko muku ,koma inzo da kaina. Se Abu na k'arshe ,duk bayan sati biyu a dinga aikawa da kaji da kuma naman rago cikin gida. Idan ana da buk'atar wani abun bayan wannan zan yi maka magana... Amma Dan Allah manager ayi k'ok'arin wajen kiyaye wannan yanzu ,idan wani abun ya sake tasowa za'a sanar dakai.." Godia sosai manager ya dinga yiwa Haajar kamar ze kama k'afar ta Dan tsabar murna ,sama se kusan tunda aka kafa gidan gonar nan dashi aka fara ,amma wannan shine karo na farko daya tab'a samun promotion. Wasu takaddu yaba daddy yasa hannu ,kafin ya musu rakiya ,har waje... Ranar kusan duk ma'aikatan gidan gonar da farin ciki suka kwana na abun alkhairin da Haajar tayi musu... Manager be kawo komai a ransa ba ganin Haajar ta kawo sauyi a gidan gonar lokaci d'aya, musamman daya ganta tare da mamallakin wurin wato daddy, da farko ya d'auka ko lawyer ce saboda yadda take magana da cikakken yak'ini ba tsoro, amma kuma daga bisani yanayin yadda take bada umurni kai tsaye ga Daddy a zaune be hana ba yasa yayi tunanin ko matar Daddy ce, Dan bayan sun fito yake yiwa daddy Allah ya sanya alkhairi, shidai daddy amsa shi kurum yayi ba Dan yasa me yake nufi ba... Shi karan kanshi Daddy gaba d'aya ya rasa Wani irin farin ciki yake ciki ,Dan babu abunda Haajar tayi guda d'aya Wanda be burge shiba ,kai komai ma tayi burge shi take yi ,musamman yadda cikin d'an k'ank'anin lokaci take ta k'ok'arin kawo wa al-amurran shi canji ,kuma ALHAMDULILLAHI yana ganin nasarori daci gaba... MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [8/1, 2:26 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* *ASSALAMU ALAIKUM. INA TAYA MASOYANA DA D'AUKACIN AL-UMMAR MUSULMAI BAKI D'AYA MURNAR ZAGAYOWAR BABBAR SALLAH, DA FATAR MUN YI SALLAH LAFIYA, ALLAH YA MAIMAITA MANA AMEEN...* _BABI NA ASHIRIN DA SHIDA_ *___________________________* _Babu yadda Hajiya Gwaggo bata yi da daddy ba akan yazo d'aurin aure, amma shi Sam wannan auren baya gaban shi ,hasalima baya wani ji a jikin shi wai shi za'a d'aura wa aure. Ana gobe za'a d'aura auren ,suna zaune a parloun shi ,shida su Haajar ,yake sanar dasu zancen auren. Ba Haajar ba hatta su suxee jin Abu sukayi kamar saukar aradu. Had'a baki sukayi wajen cewa "Aure kuma Daddy?"..._ _Daddy yace " ni kaina ba'a son raina za'a yi wannan auren ba ,sedai muna fatar Allah yasa zuwan ta ya zame mana alkhairi. "_ Tab'e baki Haseena tayi tare da cewa " Wallahi daddy ni na gaji da wannan auren da ke nema maka ,kai me ze hana ka nema da kan ka ,toma da kake maganar Allah yasa zuwan ta ya zame mana alkhairi ,ni fa gani nake duk wacce zata zo koda da alkhairin ne baza ta kai mana kamar Anty Haajar ba ,mu Allah ma da ba'a wani tsira yi maka wannan auren ba ,kawai da ka barmu munyi zaman mu a haka"... Har cikin ran daddy yasan abunda Haseena ta fad'a ba k'arya a ciki ,amma shima ba yadda ya iya ne ,cewa yayi " Banda abun ki haseena ba dole in k'ara aure Ba ,tunda ba nida wacce ke Sona ,kuma da kike wani maganar Anty Haajar, Anty Haajar ai ba matata bace ko?" ,,, da biyu daddy yayi wannan maganan Dan gaba d'aya yi yake yana duban Haajar... Wani irin fad'uwar gaba Haajar taji ,,, kauda maganar tayi da cewa "to in banda abun ki haseena,, kin tab'a ganin ka auri mutum badan kana son shi ba? Kuma ma har ka yadda ka zauna dashi ,kaji zaka iya ne ai. Sannan da kike wani zance na ,ni ai ba matar daddyn Ku bace ,kuma tafiya zanyi"... Aikuwar maganar se a kunnen Auta dake gefe tana wasa ,da sauri ta k'araso inda suke zazzaune ta dafa kafad'ar Haajar tare da cewa " Anty Haajar wai tafiya zakiyi?" Kowa juyowa yayi yana kallon ta. Murmushin dole Haajar ta kakaro tare da Shafa kan Auta tace "Eh mana Shukra " Auta tace "To amma dai tare zamu tafi ko?" Haajar tace "A'ah kina gidan Ku ,nima kinga gidan mu zan tafi!" Nan fa auta ta shiga rero kuka ba girma ba azziki ,kan kace me kukan har ya soma sakar mata zazzab'i. Da sauri Haajar ta janyo ta jikin ta "Na shiga aljannah na kasa fita ,Shukra Dan nace zan tafi shine kike wannan kukan?" Gyad'a kai Auta tayi ido jawur. Haajar tace "to na fasa tafiya saboda ke ,idan ma zan tafi to tare zamu tafi kinji yarinyar kirki". Rumgume Haajar Auta tayi tare da sakin wani ihu " Yeeeeeeeeeh! Anty Haajar tace tare zamu tafi" daga nan bata k'ara bi takan wasan ba ,zuwa tayi ta lafe kan cinyar Haajar ,Haajar d'in na bubbaga bayan ta kan kace me bacci ya kwashe ta ,se wani ajiyan zuciya take sauke wa ,kamar wacce akawa dukan tsiya. Mamaki ne ya kama daddy Dan shi be tab'a tsammanin Shak'uwar dake tsakanin Haajar da Auta yakai haka ba... Tsabar takaici haseena tace "To wai daddy meze hana ka auri Anty Haajar d'in ta zauna damu, kana ganin dai abubuwan da take mana da kulawar da muke samu a wajen ta ,Wanda ko mahaifiyar da ta haife mu bata yi lokacin mu ba balle har mu samu wannan. Shine me kake tunani idan Anty Haajar ta tafi tabar mu? Ya kake tunanin auren da zakayi ze iya maye mana gurbin ta? ,nidai inaga gaskiya daddy ya kamata ka zauna kayi tunani akai. Nifa se nake ganin Anty Haajar d'in ce ma bata dace damu ba"... Haseena ta fad'a cike dajin haushin Daddy, Dan ita akan haajar gaba d'aya yanzu lefin shi take gani. Kallon Suxee daddy yayi ,alamar kina jin abunda haseena ke fad'a? Gyad'a masa kai tayi tare da lumshe fararen idanuwan ta alamar gamsuwa da zantuttukan Haseena. Kafin daddy yace wani Abu Haajar tayi saurin katse zancen da cewa " Dan Allah ka manta da maganganun su ,kasan har yanzu yara ne. Muna tayaka murnar auren da zakayi Daddy, Allah kuma ya tabbatar da alkhairi." Ta k'arashe maganar tare da mik'ewa tsaye ta ciccib'i Auta ta d'ora ta a kafad'ar ta, sannan tace masa "seda safe". Tana kai aya ,tayi ficewar ta. Suxee da haseena ma tashi suka yi tare dayi masa seda safe suka bi bayan Haajar. Kusan daddy sumar zaune yayi ,Dan gaba d'aya ya lura yaran shi sun fi damuwa da Haajar sama dashi ,sannan bawai son Haajar bane baya yi , A'ah kawai yana tunanin yadda ze tunkari Haajar ne da zancen so, zuciyar shi na raya mishi Haajar bazata tab'a son shi. Wani d'an siririn tsuki yayi tare da Furta wa a k'asan zuciyar shi "Suna gani ma har sun fi ni son ta ne ,duk son da suke mata be kai kwantankwacin Wanda nake mata ba ,balle har ya kamo k'afar shi"... Haka dai daddy ya koma kamar wani sabon zararre a wannan Daren ,kasa bacci yayi ,kwana yayi yana sak'e-sak'en yadda ze b'ullowa al-amarin, se wuraren asuba bacci yayi awon gaba dashi... Washe gari da safe, Su Haajar basu zo breakfast a sashen daddy ba kamar yadda suka saba ,a gefen su sukayi ,sedai suxee ta kai masa nasa ,kuma koda taje ta tarar yana bacci ,bata yi k'ok'arin tashin shi ba ,ajiye masa kulolin abincin kawai tayi ta k'ara gaba. Daya fito, dukkan alamu sun nuna masa ba'a nan suka yi breakfast ba ,alama ta d'aya daya gane kuwa shine rashin jin k'amshi na tashi ,Dan 'ka'ida ne kafin su fara cin abinci se an gyara wurin ,k'amshin turaren wuta na tashi kamar baza'a mutu ba. Alama ta biyu kuma ganin kula biyu daya yi akan dinning yasan nashi ne kawai dan ba haka suka saba jera abincin ba... Ya kusa mintuna goma a tsaye yana k'are wa wurin kallo ,kafin daga bisani yaje ya zauna ya fara cin abincin, se dai kwatakwata baya jin gard'in a bakin sa ,haka yake cin abincin kamar yana tauna magani ,tsabar ba haka ta saba zama yaci abincin ba ,har cikin ranshi yake kewar rashin ganin su a yanzu, amma daya yi wani tunani ,se kawai ya dake ,tare da cewa "dani kuke zancen ,bazan tab'a Neman Ku ba ,Dan kanku zaku dawo"... Yana kammala cin abincin shi ,yayi ficewar shi zuwa sabgogin shi... A ranar yasa aka gyara d'aya daga cikin sassan dake gidan ,tare da zuba duk wani abun buk'ata ,Dan ya musu waya akan kar su zo masa da komai, sedai sashen be kai girman nasu Kubra ba ,sannan shi iya na k'asa ne flat babu bene... Da daddare aka kawo Amarya. Tun ranar da aka kawo amarya daddy be sake sa su Haajar a ido ba ,abincin ma da yake tunanin ko zasu aiko masa tun a ranar farko shima shiru babu alama ko samatan hakan. Wani abun takaicin ma, duk hasashen da daddy ke yi shine za'a kawo masa amarya ya amayar da shak'uwar sa ,amma ina sedai hak'ar shi bata cimma ruwa ba... _Ku biyo ni Dan jin dramar da daddy da lubabatu a ranar da aka kawo ta_😂👌🏻 MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [8/2, 2:06 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA ASHIRIN DA BAKWAI_ *____________________________* _A ranar da aka kawo lubabatu ,daddy na zaman jiran ta a sashen shi shiru har kusan biyu na dare bata ba labarin ta,,, daya kira ta a waya akan yana Neman ta ,se ce masa tayi shi me yake da baze zo inda take ba, hala be San gajiyar hidima bane, ai seda tace ya biya musu jirgi amma yak'i yace dole sedai ta mota ,to ita yanzu gaskiya ta gaji ,daga kan gado ma bazata iya sauka ba ,idan Abu me muhimmanci yake d'auke dashi yaje ya same ta...shirun da lubabatu taji daddy yayi yasa taja wani d'an siririn tsaki tana fad'in "naga alama ba abunda ke damun ka, saboda haka se da safe". Ta k'arasa maganan tare da yanke kiran_ _Washe gari da 'yan rakiyar amarya zasu koma ,da kanta taje ta sami daddy kwance akan gado yana bacci. Iskan bakin ta ta shiga hura masa a kunne daddy na k'ara bin gado, a tunanin shi ko iskan panka ne ,dadai yaji abun baze k'are ba ,bud'e lumsassun idanuwan shi yayi tare da zuba su akan lubabatu, murmushi ta sakar mishi cike da k'warewa tana fad'in_ " Ango kasha k'amshi! Wannan irin makara haka. To ka tashi kayi wanka ,muje mu samu bak'in mu ,Dan yau zasu tafi yanzu haka ma shirya-shiryen tafiyar suke yi ,gaka se a samu abunda za'a basu ,ina lefin wa'yanda suka yo tafiya fiye da kilomita 200 Dan su kawo maka amarya ,kai fa suka yiwa wannan k'ok'arin ,saboda haka Dan Allah idan zaka sallame su ai musu sallama me tsuko da za'a tabbatar da lallai cewa na zo _GIDAN MISBAHU_ ta k'arasa maganan tare da yin wani irin k'ara. Shidai daddy da ido ya bita ,a ranshi yake cewa wannan kuwa lafiyar ta? Kamar taji me yace tace "Lafiya dai?" Yak'e daddy ya mata tare da cewa "Bakomai" ,,,,daga haka be k'ara mata ba be rage mata ba ,ya tashi ya fad'a toilet ,wanka yayi tare da d'auro alwala. Towel ya fito dashi iya k'ugun shi... Har lokacin Lubabatu na zaune kan gado. Ko ta kanta be biba ,ya bud'e sif d'in shi tare da d'auko mayukan shafawan shi da turaruka...taso wa lubabatu tayi cike da k'ware wa ta k'araso har inda daddy ke zaune ,karb'an man shafawar tayi daga hannun shi ,ta shig Shafa masa tana wani irin salo me gigita tunanin d'an Adam,,, jin da daddy yayi kamar ze sauka a network yasa yayi saurin dawo wa hayyacin shi tare da mik'e wa zunb'ur ya Fara k'ok'arin saka kayan shi, har lokacin idanuwan lubabatu na kan shi ,se bin shi take da wani mayataccen kallo na k'urulla ,tana had'e yawu... Daddy kauda kanshi yayi gaba d'aya daga gefen ta ya maida hankali gun saka kayan shi ,seda ya gama yazo ya wuce ta gaban ta ze fita, hannu lubabatu tasa tare da janyo shi baya ,tana fad'in "Haba ranka ya dad'e ,kafa San kai na tsaya jira ,daka gama ai se kace mun in taso muje ko?" Shidai daddy be ce mata ci kanki ba. Taso wa tayi ta sagala hannun ta cikin gurwar hannun shi a haka suka fito se surutai take masa ,wani yayi murmushi wani kuma ya share ta... Fitowar su yayi daidai da dawowar su Haajar da alama siyayya suka fita yi ,Dan ko waccen su d'auke take da ladodi a hannuwan ta. Ganin su yasa ya k'ara fad'ad'a murmushin dake shimfid'e a fuskar shi... A zaton shi ko zasu k'araso a gaisa ne ,se dai hasashen shi yasha banban ,Dan kuma gimtsewa suka yi gaba d'ayan su tare da d'auke kai kamar ma basu ganshi ba ,daga k'arshe ma suka canza hanya ,suka bi ta baya... Wani iri daddy yaji a ranshi. Lubabatu dake ganin duk abunda ke faruwa ,cike da isa tace "Alhajin Allah wa'yancan ba 'ya'yanka bane?" Gyad'a mata kai yayi alamar eh. Wani siririn tsaki taja tare da cewa "Dan wulaqanci tsabar sun raina mutane shine baza su iya zuwa su gaishe mu ba? Ko ba komai ai naci albarkacin uban su kai ko? Ga bak'in mu a cikin gidan nan ,yaran nan Dan fitsara basu je sun gaishe suba, me kake tunanin bak'in namu zasu d'auka ,ai gani zasuyi kamar yaran basu da tarbiya ,aje ana cewa 'ya'yan mijina basu da ta ido , aini zasu zubar wada daraja, da a gaban mutane sukayi haka me kake tunani ,lefin mu za'a gani ,gaskiya kayi musu magana Dan wannan raini ne"... Ta k'arasa maganan tana goge hawaye ,kona menene ohon mata. Ai fa nan daddy ya k'ara harzuk'a ,Allah Allah yake yaje gama sallamar bak'in ya koma ta kan su, yaji dalilin su na son zubar masa da mutunci agaban matar data zo jiya-jiya. Sama sama ya gama sallamar bak'in se murna suke yi ,Dan kyauta daddy yayi musu na gasken gaske ba nida kyauta ba, ya kuma basu mota aka maida su har gida cike da abun alkhairi... Daga nan kai tsaye sashen kubra ya nufa ,d'akin su suxee ya wuce kai tsaye ,yana zuwa ya banka d'akin tare da fara sauke musu ruwan jaraba " Yanzu Ku har kunyi girman da zaku nemi Ku zubar mana da k'ima da daraja a idon mutane ,me kukayi kenan, kunzo kun wuce ta gaban mutane Baku san Ku gaishe su ba ,wani irin hali ne wannan? To bari kuji Sam Sam bazan d'auki wannan sabon iskancin Baku ba ,waji bane idan kuka tashi kuje da safe Ku gaida mutane"... Haka dai daddy ke ta zuba ruwan bala'i ba girma ba azziki kamar Wanda aka yiwa abunda yafi haka. Ga baki d'ayan su ba Wanda yace masa uffan har Auta dake zaune kan centre carpet tana shan ice-cream abun ta. Tab'e baki haseena tayi tare da cewa "Cabd'i jamm!!! Ita kuma wannan da haka tazo? To Allah ya kawo sauqi"... Daddy da kamar dama a jiraye yake, tasss!!! Kake ji ya d'auke haseena da wani irin zafaffen mari... Gaba d'ayan su kamar an musu shock ,Suxee har da dafe kuncin ta ,Dan gaba d'aya ji tayi kamar a fuskar ta aka sauke wannan marin... Zaro ido suka shiga yi fuskar kowa d'auke da mamaki... Hatta auta seda ta razana Dan garin firgita har seda ta b'arar da roban ice-cream d'in ta ,kuka ta fara yi Dan ta tsorata ,da gudu tazo ta fad'a kan Haajar ,Haajar d'in ta rumgume ta tana bubbuga bayan ta alamar rarrashi... Hannu ya shiga nuna musu tare da cewa " how dare u! Ina magana kina magana ,wacece ke. U better watch ur actions nonsense"... Yana gama fad'in haka yayi ficewar shi kamar Wanda ze tashi sama... Haseena dafe ta kunci tana k'ara hakaito abunda ya faru kamar a mafarki ,Suxee rik'e da hab'a tana mamakin ikon Allah, Haajar kuwa rumgume da auta dake ta faman sauke ajiyan zuciya... Suxee tace "Allah gamu gare ka ,jiya jiya daga zuwan ta, a kwana daya hakan ya fara faruwa ,me kuke tunani idan wannan takai wata d'aya a gidan nan? Ya kamata musan abun yi fa. Baku ga wani irin kallo data ke bin mu dashi d'azu ba?".. Cewar suxee Wani irin murmushin mugunta haseena tayi kamar ba ita aka sauke wa mari yanzu ba tace " Ku banni da ita ,idan tasan wata ai batasan wata ba. Mummy zan kira duk inda suka je su dawo ,Dan sune kad'ai zasu mana maganin wannan me d'anyen kan, mu da muke da Hajiya kubra har za'a zo a nuna mana bariki?"... Maganar seda taso taba Haajar dariya ,amma ta basar. Tunanin mafita take yi ,kafin daga baya ta sauke ajiyan zuciya alamar ta gano abun yi... _kudan yi hak'uri da wannan. Kunsan hidimar sallah ,har yanzu ban gama samun kaina bane, amma Dana warware zaku jini insha Allahu. One luv💖🥰🥰. MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [8/2, 9:17 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA ASHIRIN DA TAKWAS_ *____________________________* _Satin Lubabatu d'aya gaba d'aya Daddy ya rikirkice ya susu ce ,saboda ya samu kan zaran ,ga daddy mutum ne me tsananin son shan d'umin mace kawai Dan baya samu ne ,kuma gashi shiba ma'aboci Neman mata bane, Allah be tab'a d'ora mishi son bin matan banza ba. Har ya fara manta yadda ake kwanciya da mace tsabar an dad'e ba'a had'u ba ,se ga lubabatu, ita ma se da yayi kamar yanayi tukunna ya samu kanta ,bayan d'an k'aran wahalar data bashi. Dan a ranar farko daze kusance ta ita ta fara tsokano shi ,seda ta bari yawun shi ya tsinke yana gab ,sannan ta fara wani salon iya shege ,wai "Haba Alhajin Allah! Fisabilillahi haka ake wa amarya dama ,ranar da zaka fara kusantar matar ka ce ba wani kyautata wa se kace dai ba auren soyayya ba". Duk yadda daddy yayi k'i lubabatu tayi ,kud'i take so daddy ya bata gashi ranar ba kash a hannun shi ,yace ya mata transfer tace ita bata yadda ba. Sha biyu na dare daddy ya fito zuwa ATM Ciro kud'i ,se bayan ya dawo ya tuna da akwai ma kud'i a motar shi ,kwasa yayi dika ya had'a mata ,kud'i ya bata tsabar su Wanda ko shi be San ko nawa bane... Ai fa Lubabatu wasai, a Daren seda ta kusa mantar da daddy kowa nashi ,Dan seda ta tabbatar masa yayi aure, a wannan Daren daddy seda yayi d'an k'aramin hauka Dan tsabar kad'ewa da zautuwa ,sosai lubabatu ta bashi had'in kai ya murje ta son ranshi... Tun da lubabatu ta gano logon daddy ,shi kenan abun nema ya samu ,ta fara masa yawo da hankali ,idan ya matsa mata se ta nemi wani abun me tsoka Wanda daddy baya iya cewa A'ah._ _Tunda daddy ya gane shima ,se ya sakewa lubabatu bakin aljihun shi ,ya take mata kan maciji tana wasa da wutsiya. Wata sabuwar rayuwa suke bud'e ,aiki in baka yi bani wuri. Koda yaushe lubabatu na mak'ale da daddy tana masa kissa da kisisina ,shagwab'a da karairaya se Wanda ta manta._ Tun su Haajar suna tunanin ko daddy ze neme su ,shiru suke ji babu alamar hakan ,Dan gaba d'aya daddy mantawa yake dasu ,baya ta tasu ,ina ya fito lubabatu ina zashi lubabatu... Wata safiyar asabar su suxee na zaune suna tattauna matsalolin gidan, Haajar ke cewa "Ni fa se nake ganin kamar bamuyi aiki da tunani ba, gaba d'aya mun yi wawanci wallahi ,ko Abbu Sameer daba fad'a masa fad'a yayi ta mun akan bamu kyauta ba ,to taya ma zamu ci ribar abun matuqar ba muna gano meke tafiya a can d'in ba. Ina ganin ya kamata mu sake taku"... Haajar ta fad'a ,amma a cikin zuciyar ta ita kad'ai tasan me take shirya wa... Sauke ajiyan zuciya Suxee tayi kafin tace "nima fa abun ya soma damuna wllh Anty Haajar, idan zan iya tuna wa rabon mu da daddy tun randa ya shigo ya bud'e mana wuta ,washe garin kawo Amaryar sa kenan, yau gashi ana Neman wata kwatakwata daddy baya Neman mu ,kamar ma babu mu a gidan se sha'anin gaban shi kawai yake yi. Kuna gani fa kullum da yamma d'aukar matar nan yake suna fita kuma timing d'in su basa dawowa gidan se dare, ni wallahi ina jiyewa daddy tsoron kar yaje ya sakewa matar nan da yawa tazo ta ruzga dashi. Ga dai shi yanzu komai na tafiya daidai da alama tana kula dashi ,Dan ni nasan da akasin haka ne da tuni daddy ya neme mu, amma shirun yayi yawa ya kamata mu saka ido sosai"... Murmushi Haajar kawai tayi Dan ita tuni tasan duk abunda ke guda na , kawai tana jira lokaci yayi ne. Haseena tace " maganan ki gaskiya ne Yaya suxee, ni kaina abun ya fara d'aure mun kai ,amma ya kamata muyi wa toka hanci... Anan dai suka gama shirin su akan zasu je sashen daddy da daddare suga wainar da ake toya wa ,bayan Haajar ta jawa haseena kunne akan duk abunda zata gani kar ta yadda ta maganta ,Dan tasan halin ta bata gani bata tanka ba ,bata bi takan Suxee ba Dan ita bata fiye magana ba mace ce me zurfin ciki da qawaci ,duk abunda zesa kaga suxee tayi magana to ba kad'an bane... Girki sukayi kamar yadda suka saba ,kowaccen su tasha doguwar Riga har Auta kamar masu shirin fita ,sashen daddy suka nufa kowaccen su da abunda take sak'awa a ranta... Da sallama suka tura k'ofar parlourn suka shiga. Tsakar parloun kan carpet suka hango daddy da lubabatu cikin shigar k'ananan kaya ,daddy na bata abinci a baki ,ita ko lubabatu se zuba masa ruwan shagwab'a take yi ,gaba d'aya daddy yabi ya susuce se biye Mata take ,Dan duk wani abun da lubabatu zata yi burge shi take yi ,baya son jin lefin ta ko abun da ya tab'a ta. Ze kuma iya rufe ido ya ciwa ko waye mutunci akan ta... Kallon kallon su Haajar suka shiga yiwa junan su. Sun kusa mintuna goma a tsaye ,sallama kuwa sun yi tafi a k'irga amma ba alamar an San da zuwan su balle a musu izinin shigo wa... "Tofa! Wani sabon salo wai biredi a lefe. Kuga ikon Allah fa. Dole ya manta damu ai" cewar Haseena. Wani d'an guntun tsaki taja tana k'ok'arin fita Haajar ta dakatar da ita. Kallon tsaf Haajar tayi musu kafin ta k'arasa ciki tare da cewa su suxee "kuzo muje" ba musu suka bi bayan ta... Fuska a sake Haajar ta fara gaida daddy sauran ma suka gaishe shi. Ba tare da ya d'ago ya dubi d'aya daga cikin suba ya amsa musu da "lafiya". Gaida Amaryar sukayi ,sedai ita ba kamar daddy ba ,ta amsa su ba yabo ba fallasa. Sun d'an dad'e a zaune ba Wanda yace musu uffan kafin lubabatu tace " Ku se yau kuka ga damar zuwa gaishe da sabuwar uwar taku?" Suxee da haseena kallon junan su sukayi kafin suka maida duban su gun lubabatu. Haseena har ta bud'e baki zata yi magana Haajar ta kitse mata hanzari da cewa "Ayi hak'uri. Dama mun d'an bar Ku ne Ku samu Hutu shiyasa bamu lek'o kuba ,amma ayi mana afuwa". Tab'e baki lubabatu tayi kafin tace " Ba damuwa mun gode da ziyara. Alhajin Allah tashi mu shiga daga ciki na fara jin bacci" lubabatu ta fad'a cikin kissa tana duban daddy. Ba musu daddy ya tashi ya shige gaba ita kuma tana bite dashi a baya. Kayan kallo ta kashe ,har takai k'ofar shiga bedroom ta jiyo tace "Idan kun fita ,Ku d'an ja mana k'ofar. Seda safen Ku"... Ta k'arasa maganan tare murd'a k'ofa ta shige. Shigar ta ba dad'e wa ka fara jiyo muryoyin su daddy na mata wasa tana fashewa da dariya... Su Suxee jiki ba k'wari suka kwashi jiki da kulolin da suka shigo dashi suka koma sashen Ku. A ranar kwana tattaunawa sukayi yadda zasu b'ullowa wannan rikitaccen al-amarin... MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [8/6, 7:00 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA ASHIRIN DA TARA_ *___________________________* _A Daren ranar Lubabatu tayi wani mugun mafarki akan Haajar. Mafarkin da yayi masifar firgita ta ,lokacin data farko ko ba'a ce maka a tsorace ta farka ba yanayin ta ze tabbatar maka da hakan ,Dan kuwa jik'ewa tayi sharkaf da gumi kamar wacce yaje jihadi da zuciya d'aya. Abun yayi matuqar gigita ta da d'aure mata kai ,Dan wannan kusan shine karo na ukku tana munanan mafarkai akan Haajar, kwatakwata yarinyar bata gaban ta ,amma tun da ta fara mafarkin ta ta tabbatar akwai wani abun a k'asa Wanda bata San dashi ba ,tayi iya dabarar da zatayi wajen tambayar daddy game da Haajar amma ce mata yake 'yar sa ce. A wannan karon data sake tambayar shi game da ita tare da shigar d k'orafin ta akan lallai lallai sedai yasa haajar tabar gidan wanda shine karo na uku... Cike da masifa daddy yace "So nawa zan gaya miki Haajar 'yata ce ,me yasa kika damu akan ta yarinyar da bata damu da sabgogin kiba? 'Yar Aminina ce Hajj Jamil. Daga yau se yau kuma bana so in sake jin kinyi magana akan ta,,,, maganan Haajar tabar gidan nan Dan wata biyan buqatar kanki kuma be ko taso ba ,Dan kuwa kamar yadda ko inada rai ko bana Raye Hajj Jamil nada ikon rik'e 'ya'yana ,to haka nima nake da iko akan nashi 'ya'yan. Idan kuma baka sani ba yau zan gaya miki ,ita d'in wata rashe ce daga cikin rassan gida na ,kuma bango ce daga jikin katangar gida na ,saboda haka ki iya bakin ki akanta ,ki kuma sake takun ki. So nawa kina bijiromun da batu akan ta ina share wa ,har takai ta kawo yau seda kika kaini qul, to kinji Ina fatar kuma zaki kiyaye..." Daddy na gama fad'a mata haka ya tashi ya fice._ _Lubabatu dake nan gumi na tsats-tsafo mata tace "Ni nasani ,nasan za'azo wajen, nasan tunda nake ta yawan mugayen mafarkai akan ta dole d'in ita wata ce amma ba zata zama 'yarka ta cikin kaba. Kuma nayi nayi tabar gidan nan amma kak'i ,k'arshe ma duk lokacin dazan maka magana akan ta se rigima ya had'a mu. To lallai MISBAHU ka d'ebo ruwan dafa kanka ,naso mu zauna lafiya amma tunda kace babban maqiyinka kenan lafiyar yanzu zan fito maka da ainahin wacece ni ,zaka San wacece lubabatu Dan iya dad'i ne kasani baka San d'aci na ba ,gaba na kake gani ba baya na ba, yau zaka tabbatar da sahun giwa ya taka na rak'umi..."_ Tana gama fad'ar hakan ta tashi daga kan gadon ,wayar ta ta nemo tare da Dan nawa D'AN QANI kira... Bugu d'aya biyu ya d'auka " Ka same ni yanzu yanzu a gida " shine kawai abunda naji lubabatu ta fad'a tare da yanke kiran... Safa da marwa ta shiga yi a tsakar parloun, takai ta kawo tare cije hannu biyu shine kad'ai aikin da take yi. Ba ita taji sanyin rai ba har seda D'AN QANI ya kira ta ya sheda mata gashi nan ya iso ,tace ya shigo ya same ta a parlou. Ajiye wayar tayi ta fad'a wanka. Ruwa ta sakar wa kanta daga sama har k'asa. Koda ta fito a bakin gado taga daddy yana duba wasu takaddu. A zato na ko zata firgita na shigo wada daddy wani datayi har cikin gida duk da bansan ko waye ba ,sedai bansan lubabatu ba ,a mamaki na k'arasawa tayi ta zauna tare da kauda kan ta gefe. Daddy ne yace "haba yanzu tsakani da Allah kinsan yaron nan BASHAR yazo shine kika barshi a zaune shi kad'ai ,ai da se ki bari ki bashi ko abun sha ne kafin ki shiga wanka." "Naji"... Shine iya amsar da lubabatu taba daddy tare da zura doguwar rigar ta tabar masa d'akin. Daddy ko a jikin shi Dan inda sabo yaci ace ya saba da halin mata ,be k'ara bi ta kanta ba ,ya d'auki takaddun daze d'auka ya fice abun shi... Maganganu sosai Lubabatu ta tattauna da Wanda daddy kira da BASHAR ,sun kusa awa uku suna magana kafin daga baya ta rako sa suka fito haraba ze tafi... A lokacin da lubabatu suka fito ,su Haajar na garden dama fakon ta suke yi Dan akwai abunda zasu yi... Haseena ce tace " shi kuma wancan waye? Dan ni kwatakwata gayen be mun ba, sannan wannan shine gani na uku Dana masa a gidan nan suna fitowa tare da waccan matar ,ranar ma tare da daddy suka fito su uku har kud'i naga ya bashi"... Suxee tace "gaskiya bansan shiba ,Dan ni yau na fara ganin sa ,dukda nima be kwanta mun ba ,amma yana da kyau mu dinga kyautatawa mutum zato"... "Wannan haka yake" cewar Haajar ,ta fad'a dukda itama wani b'angare na zuciyar ta na sak'a mata ba dad'i game da gayen... "Koma dai menene zan binciki me gadi game dashi idan suka fita. Ku kuje kuyi abunda zaku yi ni zan tsaya anan in kula da komai" inji haseena Dan gaba d'aya ta fisu zafin nama... Ba musu haajar da suxee suka koma ciki da sauri ,Suxee ce ta shiga ta d'auko wani bokiti me marfi ,ta k'araso inda Haajar ke tsaye tana jiran ta. Gaba d'aya daka gan su kai kaga tafiyar marasa gaskiya ,dan kuwa Tafiya suke suna waigen bayan su ,a haka har suka k'arasa ta baya ,mahad'in tankin dake kai ruwa band'akin daddy yake. Da sauri Haajar ta bud'e tankin tare da zura tiyo ta ciki ruwan ya dinga kwaranya cikin fulawowin sashen, manufar su shine su rage ruwan kafin su zuba ruwan maganin dake d'auke a bokiti me marfin da suka zo dashi. Allah Allah suke ruwan ya gama raguwa ,amma ina saboda ruwan Nada d'an yawa ,dukda cewa na band'akin daddy kad'ai ne amma masu aikin kula da ruwan se sun tabbatar dasun cika tankin kafin suke kashe ruwan... Duk dad'ewar da lubabatu tayi a waje tana magana da wannan gayen su Haajar basu samu damar kammala abunda suke ba, Dan iya kwance marfin tankin ma wani aiki ne me zaman kanshi ,dak'yar Haajar tayi nasaran kwanto shi shima da taimakon suxee... Gashi har lubabatu ta shigo cikin gida. Tafiya take zuciyar ta na mata sak'e-sak'e iri daban daban, a haka har takai sashen daddy zata shiga... Marfin tankin dake hannun suxee ne ya fad'o k'asa a bisa kuskure tare da gangaro wa har inda me tahowa ze iya hango shi. Da sauri Suxee taso ta d'auko amma Haajar ta janyo ta tare da rufe mata baki ,sannan ta mata rad'a a kunne cewar tana jin alamar kamar akwai wani a wajen... Mamaki ne ya kama lubabatu ta yadda akayi marfin tanki ya fad'o bayan a datse yake, gashi ta duba ba iska ake yi ba balle ko ace iske ne ya yaddo shi, kai iskan ma se me k'arfi ne kad'ai zeyi nasarar yaddo da wannan marfin ,Dan ba wawan d'auri aka asa ba... "Kai sedai idan wani ne a wurin" Lubabatu ta fad'a ,tare da nufar wurin cikin takun ta na k'asaita. Har ta isa wajen ta zuk'unna zata d'auka... Wanda kuma zata iya nasarar hango su Haajar dake lab'e a bayan tankin ,duk sun sun tsorata ,fatar su shine kada Allah yaba lubabatu damar ganin su ko kuma Allah ya kawo musu wani d'aukin daga gefe ,Dan kuwa idan ta gansu wani sabon shafin dramma za'a bud'e, gashi basu zuba ruwan maganin da suke ta k'ok'arin zuba wa ba.... _Kuyi hak'uri da wannan jikin ne nawa har yanzu be ida warware ba. Nagode sa Addu'o'inku Allah yabar zumunci_ MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [8/6, 7:00 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA TALATIN_ *_____________________* Abunda ke d'auke a bokitin dasu Haajar ke d'auke dashi ruwan magani ne da Haajar ta had'a na K'AIK'AYI KOMA KAN MASHEK'IYA DA FARFATSIN MAK'ARE... Wanda keda matuqar muhimmanci ta tasiri ga duk Wanda ake tunanin akwai sihiri a jikin shi ,hassada ko Abu me kama da wannan. Ga yadda yake; HANYA MAFI SAUKI TA WARWARE SIHIRI KO KARYA SAMMU KO JIFA KO RUGUJE TASIRIN MAHASSADA DA MASHARRANTA DA MAQIYA *_____________________________* A nemi: - Kaikayi Koma kan mashekiya - Farfatsin Mak'era Kaikayi Koma kan mashekiya Ciyawace ana samunta a gun yan ganye ko masu sai da ganyayyaki na magungunan gargajiya . Farfatsin makera Ana samunsa ne shi kuma a makera. In aka ce Farfatsin makera shine lokacin da aka saka karfe a wuta yayi Jah, Yayin da ake dukansa domin mayar dashi wani Abu toh a lokacin da ake dukansa yana fitar da wani B'awo-b'awo fari, toh Wannan sabon b'awon shine Farfatsin makera, shi Farfatsin makera ba baki bane fari ne, kuma Bashi da Karfi Sosai, kuma ba baki bane farine Kamar dalma, amma banda Farfatsin dalmar tukunyar karfe... Farfatsin makera na Asalin bakin karfe. A hada wadannan abubuwa Guda biyu waje daya a dakesu su dawo gari, adadinsu Ya zama daya, sai a zuba a cikin wani bokiti ko roba ko mazubi me kyau, sai a zuba ruwa a ciki, sai a barshi Ya kwana, washe gari sai a tofa suratul tafiha k'afa bakwai a ciki, a dinga sha da tafin hannun dama sau uku, sai kuma a yi wanka, haka za a dinga yi na kwana uku ko kwanaki bakwai a jere ba a tsallakewa. Wallahi duk Sharrin mutum duk hassadarsa in Ya matsa maka in kayi Wannan sha da Wankan wallahi sai Ya Koma kansa da yardar ALLAH kuma duk me son ganin bayanka wallahi saidai kai Kaga bayansa, batun Jifa ko sammu ko hassada ko kiyayya cikin lokaci Guda yake ruguzawa, sannan yana boye kurwa (spirit/Arwah) mayu baza su ga kurwarka ba bare su tab'a ka, kuma in mutum yana Cutar da kai daga ranar da kayi Wannan sha da Wankan wallahi Allah zai gwada maka shi ko ita a cikin barcinka a mafarki, in ka gani Kar kace masa/mata komai, ka godewa Allah ka cigaba da neman kariya Kawai... Wannan kenan a tak'aice ,fatar Allah ya k'ara karemu daga sharrin masu sharri... Domin Neman k'arin bayani zaku iya tuntub'ar Mlm Abdulrashid Adam Ahmad d'an baiwa kan wannan lambar 08060606050. Lubabatu har ta zuqunna zata d'au marfin tankin ,haseena ta k'araso a guje Wanda har seda ta bangaje lubabatu ,idan kaga yadda tayo gadon kai kace biyo ta akayi, Ba shiri lubabatu ta saki marfin ta kama hannun k'ofar parloun daddy ta shige ,dawo wa haseena tayi da gudu tace wa Haajar "Anty Haajar kiyi sauri ki zuba waccan matar ce ,kuma zata iya fitowa, cikin hanzari Haajar ta tattaka matakalan tahau ta juye ruwan maganin sannan haseena suka mik'a mata marfin tankin ta kulle ta sauko. Da sauri suka bar wajen ,se haseena suka bari data zuk'unna wajen famfon dake gefen wajen tayi kamar tana wanke fuska... Lubabatu ce ta fito cike da tsiwa ,tana fad'in " Ke!ke!" Haseena tayi banza da ita. Seda lubabatu ta k'araso har inda haseenan ke wasa da ruwan famfo ta sakar mata duk a gadon baya "ke kurma ce? Baki ji ina miki magana bane?" D'agowa haseena tayi tana mata wani kallon raini tare da cewa "dama magana kike? Ai ban d'auka dani kike ba. To da can baki San sunana bane kike ta famar wahalar da fatar bakin ki?" A hasale lubabatu tace "Bansani ba" Cike da tsiwa Haseena tace "da kince MISBAHU ma ai da base kin k'araso ba zan juyo ,Dan mune kad'ai 'ya'ya a _GIDAN MISBAHU_, kuma duk inda naji wannan sunan dole zan waiga inji ko lafiya saboda muhimmanci me sunan a waje na" haseena ta fad'a ko a jikin ta... Ihu lubabatu ta mata "keeee! Karki kuskura ki kawo mun raini k'aramar Mara kunya"... Hannu ta d'aka zata kaiwa Haseena duka Bata rufe baki ba itama haseena ta daka mata tsawo tare da nuna mata Dan yatsa alamar kashe di " Karki kuskura. Ki tsaya iya matsayin ki amma banda kaiwa kura harawar rago, Dan kuwa ba abincin ta bane. K'ashi se kare shi kuma nama se kura. Is better u mind u own business"... Tana gama fad'ar hakan taja wani siririn tsaki tare da barin waje. Takaici ne ya taru ya tsaya wa lubabatu a wuya ,ta rasa yadda zatayi ,abubuwa sun cakud'e mata ,ga wancan yanzu kuma ga wannan. Cike da b'acin rai tama fasa komawa sashen daddy ,sashen ta ta wuce kai tsaye, Dan tsabar bak'in ciki ma ko ta kan marfin tankin bata k'ara bi ba... Bayan haseena ta koma sashen su, ta taradda su Haajar na jiran ta. Tambayar ta sukayi ya tayi da lubabatu Dan basa so ace ta gano ,muddin ta gane an zuba wani Abu a ruwan nan to zata ma iya hana daddy yayi wanka dashi ,wannan shine fargaban Haajar. Haseena tace Ku manta da wannan na gama da matsalar ta. Haajar tace "A'ah fa" Suxee tace "Anty Haajar I trust haseena ,she can do more than dis" Haseena tace "4get kawai. Akan wannan gayen, na tambayi me gadi yace wai Daddy yace ya dinga barin shi yana shigowa saboda k'anin matar shi ne, amma duk da haka ya kamata mu kula sosai ,zan kuma ci gaba da saka musu ido. Yanzu menene next?""... Da haka dai suka ci gaba da tattaunawa akan yadda tsarin su ze kasance. Wanda a b'angaren Lubabatu ma kusan raba dare tayi tana tufka da warwara..... MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [8/7, 11:58 AM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA TALATIN DA D'AYA_ *____________________________* _Da daddare bayan daddy ya dawo kuwa akayi sa'a yayi wanka ,ruwan maganin ya tab'a jikin shi. Tunda daddy ya shiga ruwan nan ya sauka akan shi gaba d'aya yaji kamar an zare masa lakkar jikin shi ,shi dai yasan lafiya qalau ya dawo ,amma yanzu wasu 'yan sauye sauye yake ji a jikin shi Wanda ya kasa gane ko menene ,ba zazzab'i ba balle yace ko rashin lafiya ne ,balle yunwa Dan daya fita seda ya biya ta gidan Hajj Jamil dam ya ciko masa cikin shi, to amma ya rasa me ke masa dad'i._ _Zama yayi har kusan d'aya na dare ya fara tunanin wasu abubuwan da suka wuce ,daya ga dai wannan baze fish she shiba haka ya tashi ya d'auro alwala ya gabatar da sallan lafila ,yayi addu'o'i sosai akan Allah ya shiga lamarin gidan shi ya kuma kawo masa sauyi na alkhairi cikin gaggawa ,,,,wannan shine addu'an shi na k'arshe kafin ya Shafa yaci gaba da zama akan dadduman. Abun mamaki a karo na farko kenan da daddy ya tab'a tashi yayi sallar dare ya rok'i Allah akan sha'anin gidan shi, ba baya sallan daren ba yana yi idan buqatun shi sun taso na kasuwanci ,amma dai akan gidan shi kam kamar wannan ne na farko, be kuma San dalilin daya sa baya iya kai kukan shi ga Allah game da sha'anin gidan shiba, ya dad'e akan sallaye zaune har bacci ya soma d'aukan shi. A baccin Dave wuce mintuna talatin ba yayi wani rikitaccen mafarki daya kasa gane shi..._ Farkawa yayi Kamar daga sama ya fara jiyo hayaniya, hankalin shi be gama natsuwa ba se jin yayi an sa key ana bud'e k'ofar parloun shi tare da banko k'ofar ,shi dai daddy gaba d'aya ya kasa koda motsi zaune yake darsashan kamar an dasa icen karas ya zuba wa sarautar Allah ido yaga waye me shigowa... Wasu manya manyan gardawa ya gani su uku ko wanne d'auke da bindiga k'irar AK47 fuskokin su rufe da bak'in k'yalle ,ba abunda zaka iya hangowa daga fuskar su se idanuwa. Da ga suka ja daidai inda daddy ke zaune kan sallaya ,be k'arewa idanuwan shi kallo ba seda yaga wani ya shigo yana janye da mutum ,seda suka kawo daidai inda yake sannan suka je fata. Ya duba wa ze gani idan ba Haajar ba ,fuska da idanuwan nan nata sun kad'e sunyi jajir ,gata duk a d'ad'd'aure da igila kamar goro, hatta bakin ta k'yalle suka saka suka k'ulle Dan kar ta musu hayaniya,,,, kaida ka gani base ka tambaya ba kasan 'yan fashi ne kuma guma-guman ,marasa imani... Da sauri daddy ya mik'e yana fad'in "Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un!!!" Wani daga cikin su ne yayi nasarar maida shi zaune ,ta hanyar daka masa kan bindiga a kafad'a. Koma wa zaune Daddy yayi tare da sake maimaita Kalmar "Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un!". Har so uku. K'ofa suka wangale masa ya hango Suxee ,haseena da Auta duk an d'ad'd'aure su a jikin bishiyar dake kallon sashen shi ,ko wacce an rufe mata baki da k'yalle ihun su baza'a ji ba sedai gunguni... Nan fa hankalin Daddy idan yayi dubu ya sake tashi. Lallai wannan musibar babba ce ,ya furta a cikin ran shi ,ya sake furta Allah gamu gare ka k'asa-k'asa da muryar da shi kad'ai ze iya jiyo abunda yace. Dak'yar daddy ya iya tattaro wata nutsuwa data k'wace masa had'id'a wata jarumta Wanda shi kanshi be San yana da ita ba, idanuwan shine suka kad'e suka canza launi zuwa ja jamar Wanda aka watsawa barkono Dan tsabar tafasar da zuciyar shi ke yi. Har wani kokuwa lab'b'ansa na k'asa Dana sama keyi wajen furta " Me kuke so?" Babban cikin su daya wurgo Haajar ciki ,ya k'araso ya zauna kan kushin tare da d'ora k'afar shi kan gadon bayan Haajar dake kwance malala a k'asa tana shashsheka, yace cike da k'warewa kan aikin shi na ta'addanci "Saurin me kake yi? Dama kana tunanin munzo shan shayi ne ko cin gurasa? Sanin kanka ne Azziki baya kawo mu se tsiya. Daka kwantar da hankalin ma ai zamu gaya maka meke tafe damu Wanda zamu tabbatar maka daba shawarar ka muke nema ba umurni muke baka"... Bakin daddy be mutu ba sake cewa " Ku gaya mun me kuke so ,idan kud'i ne zan Baku amma kar Ku kuskura Ku tab'a mun iyalina".. Wani shed'anin dariya wannan d'an ta'addan ya fashe dashi ,seda ya tsagaita sannan yace "kud'i!!! Kud'i kace ko? To daga naira d'aya zuwa naira million hamsin zan iya magance maka idan kana da buqata, kud'in ka chicken change dahar kake mun barazana dasu ,ka adana su dakyau Dan nasan zasu maka amfani wajen cefanan gobe, sakarai kawai"... Ran daddy iya b'aci ya fara kaiwa maqura Dan kuwa jikin shi har cira yake yi ,Dan ya gane wannan b'arayin ba kud'i ne ya kawo suba illa cin mutunci... Ogan tashi yayi daga zaune ya fara zagaye su daddy dake tsakiyar su se kace wani gafiya ,yafe yake yana Jan zungureriyar bindigar shi a k'asa dake k'ara tsabar taji ado da albarusai zagaye da ita... Yace cikin kakkausar murya "Naji ka ambaci iyalin ka ko? Wannan" ya nuna Haajar da bindiga itama iyalinka ce?" Shiru daddy be amsa suba. Wani irin shed'anin dariya ya sake fashewa dashi kafin yace "Zan kuwa so ka tabbatar mun da haka. Ka kawo yarinya me kyau irin wannan ka aje a gidan ka da sunan holewa kana yaudaran mutane. Gata kyaky-kyawar gaske kuwa" ya k'arasa maganan tare da zuk'unna wa daidai setin fuskar Haajar yana kwashe gashin daya rufe mata ido... Wani d'aci da takaici ne ya daki k'irjin daddy ,Wanda ya haifar masa da wani irin kishi dashi kanshi be San yana dashi ba, a hasale ya sake maimaita tambayar shi "Nace Ku gayamun me kuke so in Baku Ku fita Ku bar mun gida na" "Kwantar da hankalin ka ,fita mubar maka gidan ka ai ya zama dole ,kar manta mu bak'i ne amma bana zana ba na tafiya ,ziyara mukan kawo saboda a gana a kuma sada zumunta. Abunda muke so d'aya ne be kai biyu ba. Da kuma zaka bamu had'in kai cikin mintuna da basu Gaza sha biyar ba zamu yi komai mu gama cikin lokaci, kaga ka taimaki kan ka ka kuma yi mana saving time ,Dan lokaci da kake gani Abu ne me matuqar amfani a rayuwar mu." Dake wa tare da sake fuska d'an ta'addan yayi kafin yaci gaba da cewa "kaga wannan kyaky-kyawar budurwan bake so kawai inga ka angon ce da ita nad'an wani lokaci ,idan kayi mun wannan ka gama mun komai ,idan kuma kak'i labari ze sauya"... Wani irin zaro ido Haajar tayi ,tsantsar firgici da tsoro yasa bugun zuciyar ta tsananta kamar ana harba ganga ,daddy ko jin maganar yayi kamar saukar arado. " ina baze yu ba ,idan ma turo Ku akayi to kuje Ku sanar da me shi yayi a banza ,Dan wallahil azim sedai Ku d'auki raina dadai in aikata abunda kuke so in aikata" daddy ya fad'a rai a matuqar b'ace... Ogan 'yan fashin yace "lallai kuwa daka tafka kuskuren dahar kabar duniya ba zaka tab'a manta wa dashi ba. Kaga wa'yancan yaran naka ,ya nuna masa k'ofa ,a gaban ka zan kwanta dasu d'aya bayan d'aya kuma in saka yarana suyi kamar yadda nayi ,bayan mun gama kuma zan kashe su a gaban ba ba'a bayan kaba. Ina tunanin wannan shine Abu mafi d'aci da koda ban kashe kaba ze iya zama sanadiyyar bugawar zuciyar ka cikin sakan talatin. Saboda haka wanne ka zab'a??? Ban kuma cire maka ko wacce a cikin suba hatta 'yar k'aramar cikin su (da cewa auta) Dan k'ananan yaran ma kusan sun fi manya gishiri, kai wannan d'in ma ya nuna Haajar itama bazamu bar maka mutuncin taba warwas zamu maka haihuwar mayya akace ina d'a tace ta cinye".... Shiru daddy yayi Dan gaba ki d'aya yanzu kam ya sare, babu abunda yake ambata a k'asan zuciyar shi se sunan Allah da Neman taimako a wajen shi. Ganin yayi shiru yasa ogan 'yan fashin cewa " karka manta na gaya maka lokaci Abu ne mai tsada a wajen mu, saboda haka kai idan tsabar ya gagare ka ni na tsabar maka.... Ku rufe min su"... Ogan ya k'arasa fad'a tare da nufar hanyar waje alamar wajen su suxee ya nufa... Kuka Haajar take yi tana shurin daddy akan yayi wani Abu ,amma..... MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [8/8, 7:20 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA TALATIN DA BIYU_ *___________________________* _Har ogan 'yan fashin ya kusa fita ,Haajar ta sance d'aurin dake bakin ta tare da dakatar dashi cikin disash-shen muryar ta da baya fita sosai. Dawo wa baya yayi cikin isa da k'asaita tare da d'aga kai alamar ya akayi?_ _Haajar dake shash-shekan kuka tace "Dan Allah kuyi hak'uri Ku k'yale su kar Ku musu komai ,ze yi duk abunda kuke so yayi indai baza Ku tab'a wa'yancan yaran ba"... Da mamaki daddy ya kafe ta da ido tare da cewa " Haajar ba kida hankali ne? Ba kiji abunda yake so na aikata miki bane? Fyad'e fa yace ko bakiji bane?" Wasu hawayen bak'in ciki ne da takaici ya shiga reto a fuskar Haajar wani na bin wani ,k'ok'arin share hawayen ta tayi tace "Daddy naji sosai ,naji abunda suke so ka aikata mun. Amma kai ma baka ji abunda suka fad'a bane akan cewa lallai idan bakayi hakan ba zasu lalata rayuwar su Haseena? Me wa'yannan yaran suka sani? Me suka yi dahar suka cancanci irin wannan d'anyen aika-aikar? Saboda haka bazan iya jure kallon su a irin wani yanayi me kama da wannan ba balle kwatankwacin sa ,na yadda na bada kaina fansa akan su." Wani irin rufe ido Daddy yayi yana jin wani d'aci a ranshi, a lokaci guda kuma son Haajar ya k'ara ratsa kowani sassa da jijiyoyi na jikin shi. Kafin yayi magana yaji ogan 'yan fashin nan na tafi, tare da cewa "Good! Kin kyauta sosai. Saboda haka na Baku minti goma. Idan mintuna goman nan suka cika ba kuyi kamar yadda nace ba ,to lallai Ku shirya haihuwar wasu 'ya'yan amma ba wa'yancan na waje ba..." K'ofa yasa aka bud'e, yace "Ku kalla Ku gani" Waigawar da zasuyi suka ga mutum uku akan su suxee kowanne ya d'ora musu bindiga akai, alamar a shirye yake yayi harbi matuqar an bashi umurni,,,sannan yasa aka rufe masa k'ofar... Hankalin haajar ne ya sake tashi. Ganin da tayi na daddy baze iya tunkaro taba yasa ta kai masa kanta. Tana ji tana gani daddy ya rabata ta da 'yan matancin ta. Duk da irin rad'ad'i da azaba dake k'ok'arin ratsa ta a wannan lokacin bakin ta be kasa furta addu'ar saduwa ba. Shigan da daddy ya mata wani irin shiga ne dashi kanshi be San yayi shi ba ,shiga ne irin Wanda ya saba yi da matan shi ,a tunanin shi duk hakan take. Wani abun da na lura dashi shine kamar duk a cikin matan daddy be tab'a auren ainahin abunda ake cewa cikakkiyar budurwa ba ,Dan yanayin yadda yake shigar Haajar ya tabbatar da hakan... Wani irin k'ara Haajar ta saki lokacin da daddy yayi nasarar yaga mata rigar budurcin ta, saboda wani irin azaba daya ratsa ta Wanda bata tab'a sanin akwai shi a duniya ba. A hankali take sauke numfashin ta Dan gaba ki d'aya iskan duniyar nan ji tayi ya mata kad'an wajen shak'a... Wani irin son ta da tausayin tane ya kama daddy ,be San lokacin da hawaye ya fara zubo masa ba, musamman daya ke ganin wacce tafiye masa komai a rayuwa a cikin wannan halin.... Wani dariyar ta'addanci ogan 'yan fashin nan yayi, had'ida wani irin tafi me k'ara, tare da cewa "Job done! Good of u!" Yana gama fad'ar hakan yayi pito ,gaba d'aya yaran shi suka zagaye shi. Hannu ya Sara wa daddy tare da cewa "Good bye"... Yana gama fad'ar hakan suka bar wajen da alama tafiya suka yi gaba d'aya... Suna fito ba shiri daddy yayo kan Haajar yana jijjiga ta ganin da yayi kamar ko numfashi bata yi ,d'ago ta daze yi se ganin yayi tana zubarda jini. Iya gigicewa daddy ya gigita. Jijjiga ya shiga yi yana kuka kamar wani yaro tare da sako zance iri-iri "Dan Allah ki tashi Haajar. Ki tashi,,,Haajar karki tafi ki barni ,kyace rayuwa ta ,ban tab'a sanin menene dad'in rayuwa ba seda na had'u dake ,kece jin dad'i na dani da yarana,,,,Haajar!!!" Daddy ya dinga maimaitawa kamar wani zazzautacce. A hankali Haajar ta fara bud'e jajayen idanuwan ta. K'ok'arin d'aga hannun ta take yi a haka har ta samu nasarar cin k'arfin hannun ,tana nuna masa k'ofa. Cike da zumud'i daddy yace "me kike so?" Hannun ta ya kalla yaga inda take nuna masa alamar yaje ya dubo su haseena... Yace "Su Auta?". Lumshe ida tayi ,se ga wasu siraran hawaye nabin gefen kuncin ta... Yace " bazan iya nisa dake ba Haajar " Tattaro duk wani kuzarin ta tayi ta bud'e baki a hankali tace cikin muryatta da se kayi da gaske kafin ka iya gano me take cewa tace "Kaje ka dubo su daddy"... Ba shiri daddy ya ajiye ta ,Dan duk dramar nan da ake akan hannun shi take, ya nufi wajen. A d'ad'd'aure yagan su ,da alama tun d'aurin da suka musu na farko ne ,sun galabaita ,gaba d'aya k'arfin su ya k'are. K'ok'arin kwance su ya fara yi. Auta har bacci ya d'auke ta daga nan inda take a d'aure, Suxee kuwa tun tana kukan ,har ya koma sedai hawaye na ke zuba daga idanuwan ta. Tsoro daddy yaji lokacin daya ga ya kwance haseena ta fad'o a jikin shi warwas ,ya d'ago ta ,se jin yayi ya canb'ala hannun shi cikin jini, dubawar daze yi se ganin yayi ta dafe gefen cikin ta ,ga wani jini me guda-guda dake b'ul'bulowa... Murya a rud'e daddy yace " meya same ta? Haseena!!!Haseena!!! " Cikin muryar kuka suxee tace "Harbin ta sukayi da bindiga daddy saboda ta musu taurin kai. Sun zo suci zarafin mune ita kuma ta nuna bata yadda ba ,shine suka harbe ta a ciki...." Wani irin tashin hankali ne ya bayyana k'arara a tattare da Daddy. Kuka yake yana fad'in "me yasa zasu mun haka? Me na musu? Me iyali na suka musu da suka cancanci wannan wulaqancin haka???"... Ganin baze samu amsar tambayoyin shi a wajen kowa ba yasa ya tashi a daburce ya suri Haseena yakai ta mota ,sannan ya dawo ya d'auko Haajar a k'irjin shi kamar wata 'yar tsana yakai ta mota itama ,suxee ta d'auki auta ,suka bar gidan ,basu taka burki ko inaba se asibitin Dr. Zaidu... A can suka kwana gaba d'ayan su... Seda safe ya kira Hajj Jamil yake sheda masa akan ya same sa asibitin Dr. Zaidu ,amma be sanar dashi komai ba. Hankalin Hajj Jamil ya tashi sosai Dan a tunanin shi ko ciwon Daddy ne ya sake tashi. Barin abunda yake yi yayi ya taka mota se asibitin... _Washe gari su Hajiya Kubra suka duro Nigeria_.... MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [8/9, 4:19 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA TALATIN DA UKU_ *___________________________* _Da Suxee Hajj Jamil ya fara cin karo ,tsabar tsoro yasa tana ganin shi da gudu taje ta rumgume shi tare da fashewa da wani marayan kuka me ban tausayi. Wannan Abu ba kad'an ba ya sake d'aga hankalin hajj Jamil har ya rasa da wani Kalma ze yi amfani wajen lallashin suxee Dan duk a tunanin shi ko wani abun ne ya samu Daddy. Lallashin ta ya shiga yi da duk wani kalma me taushi daya zo bakin shi. Seda suka samu wuri suka zauna ,sannan yake tambayar ta ina Daddy???_ _Suxee na kuka nan ta gaya masa duk wani abun da ya faru a Daren jiya har kawo zuwan su asibiti. Wani irin imani ne da tsoron Allah ya cika zuciyar Hajj Jamil ,a lokaci d'aya wani tsoro ya dad'a mamaye masa k'irji_ Be iya cewa komai ba se "Yanzu ina daddy yake?" A tare suka shiga inda wani d'aki na kwanan likitoci da Dr. Zaidu yakai daddy dan ya huta ya kuma samu kwanciyar hankali. Hannu biyu daddy yasa ya rik'e hab'a ,idon shi a lumshe kamar me bacci ,a zahiri kuma kwanto yayi ba bacci ba. Auta ce kan gado daga gefen shi tana rankon baccin wahala. Wani irin tausayin daddy ne ya k'ara kama Haj Jamil. K'araso yayi har inda daddy ke zaune ya dafa kafad'ar shi ,tare da kiran sunan shi a sanyaye D'agowa daddy yayi yana duban shi ,ba tare da ya sani ba wasu siraren hawayen suka fara gangaro masa. Zuciyar hajj Jamil ce ta sake karaya. Girgiza masa kai yayi alamar hakan be kamata ba, tare da nuna masa Suxee dake gefe itama tana aikin zubarda k'walla tun Daren jiya Hannun daddy ya rik'o suka fito waje. Ya dubi suxee yace ki zauna muna zuwa ,kuma ki dena wannan kukan bana so. Kai kawai ta iya gyad'a masa ba tare da ta iya tare hawayen dake ambaliya a fuskar taba. Mota suka shiga ,Haj Jamil ya data motar. Gidan shi suka nufa. Seda ya tabbata daddy yayi wanka ya kawo masa Abu me sanyi ,dan yasan shine kad'ai abunda daddy ze iya sha a wannan lokacin... Bayan ya huta sannan Haj Jamil ya fara tausasan daddy da duk wani Kalma na lallashi daya sani a duniya ,tare da k'ara ankarar dashi game da 'yar taqaitaccen nasiha akan qaddara ta alkhairi data sharri. Ya k'arasa maganan tare da cewa "MISBAHU bawai dan kace kayi imani bane kawai yasa Allah ze barka baze jarrabe ka ba. Cewa kayi imani bashi ya nuna Allah baze yi maka gwaji yaga shin lallai imanin nan da kace kayi da gaske ne ko be kai zuciya ba. Saboda haka duk ka d'auki wannan a matsayin jarabawa daga Allah, kowa da tasa kalan qaddarar wani idan kaji nashi zaka ce naka ba komai bane ,saboda duk yadda kam cikin masifa wallahi wani ya fika ,haka duk yadda kake cikin jin dad'i wani ya fika. To Dan haka ka d'auka wannan shine kalar taka qaddarar kuma ka gode wa Allah da abun ya tsaya iya nan"... Har cikin ran dad'i yaji dad'in maganganun Haj Jamil ya kuma San gaskiya yake gaya masa amma wani b'angare na zuciyar tashi na k'aryata hakan. A hankali ya sauke ajiyan zuciya tare da cewa " Haj Jamil yanzu har kana ganin akwai Wanda ya kaini shiga masifa balle har ya fini??" Murmushi Haj Jamil yayi tare da cewa "wani tunda aka haife shi a masifa ya fad'a a haka kuma yake ci gaba da rayuwar shi, kai kuwa se da kayi auren farko tukunna kasan menene matsalar rayuwa ,Ashe ma ubangiji nason ka...yanzu kai idan baka Bawa zuciyar ka hak'uri ba ,taya zaka iya rarrashin yaran nan?" Sauke numfashi daddy yayi kafin yace "Hakane! Amma Haa.." Be k'arasa kiran sunan Haajar ba Hajj Jamil yace "mu bar wannan maganar yanzu ,zamu tattauna akai wani lokacin"... Da haka dai Hajj Jamil yaci gaba daba daddy baki har ya samu kanshi. Seda ya tabbatar ya samu nutsuwa sannan suka koma asibitin. A hanyar su ta koma wa asibitin suka tsaya suka siyawa suxee da auta abinci, duk da daddy yasan halin suxee sarai da qawa zuci ba lallai ta iya sawa bakin ta wani abun ba saboda har yanzu ba'a hayyacin ta take ba... A b'angaren su Hajja Kubra kuwa ,an dawo daga Germany ,sun k'ara gogewa sun yi kyau abun su iskanci da rashin mutunci kuwa se abunda ya qaru. Wanda yasan su da idan ya gansu yanzu ze tabbatar da akwai tarin canje-canje. Da dawowar su ko wacce sashen ta ta nufa, kubra bata lura da sauye-sauyen dake sashen taba ,kai tsaye wanka ta fad'a ta sakarwa kanta ruwa ,ta dad'e a band'aki kafin ta fito ,rigar bacci kawai ta iya saka wa ta kwanta nan da nan bacci ya kwashe ta ,ba ita ta farka ba se yamma... Bayan ta tashi ne take tunanin ko ina su auta suka je ne ,Dan taji bata jiyo motsin suba. Tab'e baki tayi tare da cewa "k'ila kuma ya kai su kano".. Da haka taci gaba da gudanar da al-amuran ta... A b'angaren Khaltum kuwa ta kammala duk wani shirin ta tsaf na karb'ar girki a Daren ranar, a yayin da kubra ita ma ta gama shirin ta na zuwa tunkarar daddy duk da cewar ita ba girkin take da niyyar karb'a ba amma kuma tana kewar mijin ta ,tana so ta gan shi... Da daddare Lubabatu na zaune a parloun daddy tana kallo ,khaltum ta banko k'ofar ta shiga. Lubabatu dake zaune taso wa tayi a tunanin ta ko daddy ne amma se taga akasin hakan. Da wani irin d'an iskan kallo khaltum tabi Lubabatu ,yayin da itama take maida mata da martanin ke kuma daga ina??? Cike da tsiwa Lubabatu tace " Ke kuma malama daga ina? Kin shigo wa mutane ba sallama ba komai ko an gaya miki nan choci ce?"" Wani irin azababben mari khaltum ta kwasawa Lubabatu tare da cewa "Ni sa'ar kice daza ki dinga gaya mun duk kalamin daya zo bakin ki? Ko kuwa ba'a koya miki tarbiyya da iya magana bane daga gida? Banza shashasha. Ni ba wurin ki nazo ba wajen me gidan nazo, ki bari zan dawo ta kan ki".. Khaltum na gama fad'ar haka taja wani dogon tsaki tare da nufar hanyar bedroom d'in daddy ,shiga tayi ta dudduba seda ta tabbatar lallai baya nan sannan tazo ta wuce Lubabatu dake tsaye tare da banka k'ofar... Wani irin shu'umin murmushi Lubabatu tayi tare da cewa " lallai kuwa wannan matar baki San wa kika Mara ba ,Ashe kuwa zaki yi Dana sanin mari na da kika yi a yau ,Dan ni Lubabatu kabewar kan dutse ce ban fito ba seda na shirya. Wi k'aramar kura a kashe ki a d'au alhaki ,a barki ki girma ki kar mutum. Wannan duk kirari na ne, Bana barin bashi. Amma muje zuwa da sannu zan sa ki kwashe kashin ki a hannu. Banza sakariya kawai"... Wani gajeran tsaki taja sannan ta koma ta zauna ta had'e k'afa d'aya kan d'aya tana girza kai tare yin k'wafa... Kai tsaye Khaltum sashen Kubra ta wuce a kan stairs taci karo da kubran tana sauko wa. Kubra ganin data yi ran Khaltum a b'ace yasa ta tambaye ta "Yaya?" Nan Khaltum ke sheda mata duk yadda suka yi da Lubabatu a k'arshe ta k'ara da cewa "Har cewa tayi ba ni ba ko ke baki isa ba"... Wani d'an tak'aitaccen murmushin gefen baki kubra tayi ,tare da cewa " Ina ba dai ni ba. Ta dai yi dake Dan inaga kun fi zama kai d'aya " Da mamaki Khaltum tace "Ban gane me kike nufi ba?". Kubra tace " zaki gane a gaba". Wasa-wasa kusan kwana ukku daddy be koma gida ba ,yana asibiti tare da yaran shi yana kula dasu. Babu yadda Haj Jamil beyi akan ya koma gida ba amma yak'i. Ganin har kusan rana na hud'u daddy be dawo ba yasa kubra ta kira shi a waya, amma be d'aga ba, Khaltum ma ta kira shi yafi sau nawa amma yak'i d'auka... A washe gari ne Haajar ta farfad'o ,dan seda aka mata d'inki tsabar k'aruwan data yi. Amma Haseena kam se abunda Allah yayi... MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [8/10, 8:13 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA TALATIN DA HUD'U_ *___________________________* _Alhamdulillahi Haajar ta samu sauqi sosai ,dan kusan Yanzu ita ke kula da Haseena. Tun bayan abunda ya faru Haajar ta d'auke wa Daddy ,bata wani yi masa magana sosai se can baka rasa Ba, shima se idan maganar ta kama na dole ne kawai take yi masa. Ba kad'an ba hakan ya damu daddy ,gashi Hajj Jamil ma kwana biyu be zo asibitin ba balle daddy ya samu damar sanar dashi halin da ake ciki. Wasa wasa har kusan sati biyu Hajj Jamil be shigo ba ,tun abun baya damun daddy har ya soma hasashen abubuwa da dama. Dan Yanzu ya gano dalilin daya sa Haajar take share shi da kuma rashin zuwan Hajj Jamil, tabbas akan abunda ya faru ne ,yasan abun da d'aci ,amma ya kamata su gane ba yada lefi a ciki, shima ba'a son ranshi hakan ya faru ba, Dan shi da anbi ta tashi tun a wancan lokacin sedai idan b'arayin kashe shi zasu yi su kashe shi ,amma baze tab'a yiwa 'yar mutane fyad'e ba._ Sosai daddy ya shiga damuwa ,Dan ko kiran Hajj Jamil yayi a waya baya d'auka. Idan ma ya matsa masa da kira se dai ya turo masa message akan cewa 'yana aiki daga baya ze kira shi' kuma baze kira d'in ba. Daddy yayi ta k'ok'arin zuwa gida Neman sa a gida amma baya samun sa ,duk zuwan daze yi sedai Tukur me gadi yace masa yanzu ya fita ko ya dad'e da fita. Haka dai daddy yaci gaba da bibiyar Hajj Jamil. Gashi a Yanzu ba yada wani buri daya wuce yaga ya auri Haajar ,kuma hajj Jamil shine kad'ai Wanda ze taimaka masa ya samu auren Haajar cikin sauqi ,sedai baya tunanin hakan ze yiwu musamman da wannan abun ya faru tsakanin shi da Haajar... Sau da dama daddy na k'ok'arin ganin ya tambayi Haajar ko tana waya da hajj Jamil amma babu dama Dan baya samun fuskar hakan. Kawo yanzu zuciyar daddy kamar zata tarwatse da tsabagen tunani daya masa yawa. Ga dai tunanin Haajar daya hana shi sukuni ,ga rashin jin Hajj Jamil da baya yi ,a gefe d'aya kuma ga rashin lafiyar haseena, abubuwa sun taru sun tsaya masa a rai Wanda abinci ma dak'yar yake samun nutsuwar cin sa. Saboda wannan matsalar yasa ko gidan shi ya kasa koma wa ,gaba d'aya sedai ya tattara ya koma hotel da zama ba tare da sanin kowa ba. Kullum hakan siyo abinci ya kawo musu asibiti amma rashin sake masa da Haajar bata yi yasa gaba d'aya baya samun walwalar sake wa a asibitin ,duk wani abunda suke buqata yana k'ok'arin yi musu. Sannu a hankali Haseena ta fara samun sauqi cikin iyawar ubangiji. Bayan sati uku jikin ta yayi sauqi sosai Dan ba abunda bata yi ,sedai lafiyar ba kamar da ba. Bayan sati d'aya aka sallami Haseena. Dr. Zaidu ya buqaci Haajar akan ta kira daddy yazo yana so yayi magana dashi. "Ba nida kati a waya Dr. Amma idan ba damuwa me ze hana kai ka kira shi!" Haajar ta bashi amsa Dr. Zaidu yace "to ba damuwa zan yi k'ok'ari in neme shi. Muje office d'ina inaso inyi magana dake". Ba musu tace masa " toh" Bayan sunje office d'in sun zauna Dr. Zaidu ya kira daddy a waya ya sheda masa yana Neman sa. Ya kuwa yi sa'a daddy na kusa da asibitin ,ba b'ata lokaci se gashi ya k'araso. "To ya jikin naki yanzu?" Dr. Zaidu ya tambayi Haajar Fuske a sake ta amsa masa da "Alhamdulillahi naji sauqi sosai ni ai yanzu" Dr. Zaidu yace "masha Allah. Haka nake son ji ai. Ciwon a jikin ki yake amma ni ke jin rad'ad'in". Murmushi me qayatarwa Haajar ta saki tare da cewa "Ka dai ji Dr.da wani dad'in baki. Ta iya Wanda ke ciwo daban ,me jin zafin ciwon daban? Ai Abu ne Wanda baze yu ba". Shima Dr.zaidun dariya yake yi a lokaci d'aya yana fad'in " Ai dama baki sani ba? To idan baki tab'a ji ko gani ba ,to ai yau kinji ko"... "Aikam naji wannan tatsuniyar" Haajar ta bashi amsa tana da fara'a a fuskar ta Dr. Zaidu yace "Ina ba kiji tatsuniya ba ,za dai kiji. Dan har gida zan zo in baki tatsuniya me dad'in saurare Wanda kunnuwan ki basu tab'a jin irin suba"... Dariya maganar yaba Haajar ,tace " To Allah ya kaimu" Cikin raha suke ta tattaba hira. A haka daddy yayi sallama ya shigo office d'in. Wani irin takaici ne ya tokare masa mak'oshi lokacin daya ga Haajar a office d'in Dr. Zaidu se faman murmushi take masa ,wato shine ba zata iya yi wa murmushi ba ,amma ta zo ta zauna tana wani washe wa wani k'ato baki se kace mijin ta. Nan take yaji hausin su ya kama shi, a lokaci d'aya kuma yanayin shi ya sauya, idanuwan shi suka canza launi. Daga Haajar d'in har Dr. Zaidu idanu suka zuba masa. Takaicin kallon da suke masa ne ya sake kama shi. Dr. Zaidu fad'ad'a fara'ar dake fuskar shi yayi tare da cewa "Hajj Misbahu barka da k'arasowa. Bismillah". Kamar daddy baze tanka shi ba ,se kuma ya dake ya k'arasa ya zauna. Dr. Zaidu yace " Ka ganni da mutuniyar ko muna d'an tab'a hira? Ai wato ita d'in ce akwai iya zantuttuka masu dad'i " Dr.Zaidu ya fad'a zuciyar shi d'aya, Dan shi har cikin ran shi son Haajar yake yi. Murmushi Haajar d'in tayi tare da cewa "Nagode Dr." Wani irin kallo daddy ya bita dashi ,daya sa ta had'e girar sama Dana k'asa tare da kauda kan ta gefe d'aya. Zuciyar Daddy ne ya dad'a k'una cike da b'acin rai yace "Daddy kace inzo ,kuma nazo kayi shiru baka ce komai ba? Ina da ayukka a gaba na" Yanayin yadda daddy yayi magana ba k'aramin basu mamaki yayi ba, musamman Dr. Zaidu dabe tab'a ganin sa a irin wannan yanayin ba. Ganin haka yasa ya kauda wasa gefe tare da zare gilashin dake manne a idon shi yace "Hakane! Da ma akan ciwon Haseena ne!" Nan dai Dr.zaidu ya fad'a musu qa'idodi da dokoki had'id'a hanyoyin da zasu bi Dan gudun kar haseena ta shiga wani matsalar. A yadda ya shada musu kuma ,rayuwar ta na tsakanin rayuwa da mutuwa matuqar basu iya kiyaye wannan dokokin ba. Wasu magunguna masu tsadar gaske ya bada yace "wannan suna maganin da zata dinga amfani dasu ,akwai nasha k'arfe shida na safe ,akwai na sha biyu na rana ,akwai na shida na yamma sannan akwai na sha biyu na dare. Ko wanne kuma ana buqatar a kiyaye lokacin shan shi. Rashin kiyaye hakan kuma bazan iya cewa ga abunda ze faru ba ,Dan se abunda Allah yayi amma hakan ba k'aramin barazana ne ga rayuwar taba." Godia sosai Haajar tayi wa Dr. Zaidu ,tare da karb'an magungunan. Daddy yace "mun gode" ya fad'a a tak'aice tare da mik'ewa ya fita daga office d'in... Kai tsaye mota ya wuce ,yana jiran fitowar su. Haajar kuwa da Dr. Zaidu tare suka shiga d'akin da Haseena dasu suxee ke ciki ya taya su kwashe kaya. Auta se murna take zasu tafi gida ,Dan ta gaji da zaman asibitin ,haseena ma murna tayi sosai Dan har ga Allah ta jinyatu. Had'a komai da komai suxee tayi a jaka. Dr. Zaidu ya rik'o musu wasu daga cikin kayayyakin har mota sune tafe suna hira. Dr. Na cewa ze yi kewar su ,Dan zaman su a asibitin ba kad'an ba ya saba dasu sosai... Seda suka saka komai a mota. Dr. Zaidu dubi Haajar yace "A gaskiya zanyi kewa sosai Haajar. Da ma zaki taimaka mun koda da numbern waya ne kinga ai se mu dinga gaisawa kuma in dinga jin ya jikin Haseena"... Murmushi Haajar tayi tare da cewa "to ba damuwa. Ai se in baka lambar!" Nan ta karanto masa lambar ya saka ,tare da cewa ze kira ta idan sun isa gida. Allah ya kiyaye ya yi musu sannan ya koma ciki. Suxee da Auta ne suka shiga gidan gaba ,a inda Haajar da Haseena kuma suka shiga gidan baya... Wani irin fizgar motar daddy yayi ,Wanda seda yasa Haajar buga kai da kujerar direba dake gaban ta ,ba Dan ta rik'e haseena ba ita ma da se kan ta ya bugi kujerar. Wanda har seda auta tace "A'aaah Daddy" ,suxee ko bin daddy tayi da kallo da bema San tana yi ba. Fanfala gudu ya shiga yi a hanya kamar Wanda ze tashi sama, be taka burki ko inaba se k'ofar gidan shi, Wanda shima se a yau ya dawo gidan tun bayan faruwar abun. Da motar kubra suka ci karo ,ita da Khaltum da alama fita zasu yi ,amma ganin motar daddy yasa suka fasa fitar tare da karya motar suka koma ciki... MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [8/11, 7:09 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA TALATIN DA BIYAR_ *____________________________* _Wajen da aka ta nada Dan ajiye matoci nan daddy ya yi parking motar shi. Suxee ce ta fara fitowa tare da Auta, ka fin Haajar ta bud'e gidan baya ta fito sannan ta zagayo ta bud'e wa Haseena d'ayan k'ofar ta fito..._ Haajar da Suxee ne suka kwashe kayan zuwa cikin gida. Tun da suka fito daga mota Kubra dake zaune a motar ta ta sauke gilashin mota tana bin su da ido d'aya bayan d'aya. Tana wurin har lokacin da su Auta suka shige sashen ta ,daddy ya juya ya fita. Gaba d'aya kubra ta kasa gane komai. A yanayin da ta gan su ,ta tabbatar da akwai abunda ya faru ,ga shi duk sun rame sun yi duhu ,musamman ma Haseena dake tafiyar kamar Mara lafiya, ga Haajar da ta gani a tare da su ,duk da bata San ko wacece ba. Ta dad'e a wajen tana tunani iri-iri. "To me ya same su?" Ta tambayi kan ta ,ganin ba zata samu amsar tambayar ta a wurin kowa ba se a wurin yaran yasa ya fasa fitar. Bud'e marfin motar tayi ta fito. Da mamaki Khaltum ta bita da kallo tare da cewa "Hajja kubra ina zuwa haka? Naga cewa fita zamu yi kuma jiran mu ake yi?" Kubra bata ce mata komai ba ,ta fito tayi tafiyar ta. Wani guntun tsaki Khaltum taja tare da cewa "kya ji da shi". Ganin kubra na nema ta b'ata mata lokaci yasa ita ma ta fito daga motar ta koma ciki... Suna shiga Haajar ta kunna na'urar ruwan zafi ta band'aki Dan su samu suyi wanka. Kayan jikin ta ta rage ,Auta ta dube ta tare da cewa " Anty Haajar ni zaki fara yiwa"... Haseena dake zaune tace "Dalla ji ki k'atuwa dake se an miki wanka ,ke har yanzu ba zaki koyi wanka dake ba". Auta tace " to ai ni idan nayi da kaina bana fita ne ,amma idan Anty Haajar tayi mun ina fita sosai". Haseena tace "see you! U're getting to 9yrs amma har yanzu ke baki San kin girma ba"... Auta tace " to ai ni har yanzu k'arama ce Yaya haseena ba irin ki ba k'atotuwa" Ta sowa Haseena tayi zata kamo ta tana fad'in "Nice ma k'atuwa? Wallahi idan na kama ki zaki gane shayi ruwa ne" Haajar da ke ta faman yi musu dariya. Ganin haseena ta Neman tashi yasa tayi saurin maida ta zaune tare da cewa "Haba Haseena! Lafiyar jikin ki ba fa kamar da bane, Dole se kin kula sosai". Murmushi haseena tayi tare da koma wa ta zauna. Suxee tace " Ah to dai gara ki tuna mata idan ta manta Anty Haajar. Yanzu kam ke da Auta se gani se hange. Amma fa shigar miki zanyi ,dan bazan bari auta ta k'arasa mana ke ba, muna son ki". Murmushi Haajar tayi tare da cewa "Auta muje in yi miki wanka kinji. K'yale su zan ga me tab'a ki a gaban ido ne ,se dai ayi idan ba na kusa"... Tsalle Auta ta shiga yi tana fad'in" yeeeh Anty Haajar! " ta fad'a tare da yi wa su haseena gwalo. Wani guntun tsaki haseena taja tace "Ji ta fa Dan Allah! Kwatakwata Auta bata San ta fara girma ba. Zallar wauta ne da yarinta ke damun ta. Bansan yaushe za ta yi hankali ba wallahi" Dariya Suxee dake gyara musu kaya tayi tana fad'in "Ai Auta Autar ce. Allah dai ya raya ta musha biki" Haka suka ci gaba da tab'a hirar su cikin nuna qauna irin na 'yan uwan taka... Sallama kubra tayi kamar wata mutuniyar azziki ta shigo d'akin su Suxee, lokacin Haajar na band'aki tana wa Auta wanka. Tun da suka amsa mata sallama ko wacce ta d'auke kan ta. Duban su Kubra tayi tare da cewa "Ba Ku gan ni bane?" "Mun gan ki" Suxee ta bata amsa a tak'aice Mamaki ne ya kama Kubra, Dan idan akwai Wanda ya kamata ya yi mata hakan be wuce Haseena ba Dan ita ce me fitsarar cikin su ,amma kuma yau se ga Suxee. Duk da halin ko in kulan da suke nuna mata ya mata ciwo ,amma se ta share tare da zama a gefen gado kusa da inda haseena ke zaune ,shafo gefen fuskar ta tayi tare da cewa "me yake damun kine haseena naga duk kin rame ?" Kayan dake kusa da haseena Suxee tazo ta kwashe ,nan magungunan Haseenan suka fad'o k'asa. Haseena tace "Yaya Suxee magani ne" ta fad'a tare da nuna mata. Kafin suxee ta d'auka Kubra ta kai hannu ta d'auko tana dudduba magungunan. Kallon haseena ta sake yi tare da dafa kafad'ar ta tace "Haseena ba ki da lafiya ne? Me yake damun ki haka?" Kwab'e hannun ta haseena tayi daga kafad'ar ta rai a b'ace tace "Menene damuwar ki dani da har zaki damu da lafiya ta?" Kubra ji tayi ba dad'i a ranta ,amma ta danne tare da sake da fa kafad'ar haseena a karo na biyu tace "Wani irin magana kike yi haka Haseena? Na damu daku mana ,ni fa mahaifiyar Ku ce!" Wani irin murmushin takaici haseena tayi tare da cewa "Na riga na manta da wannan tuntuni ,ni ba ni da wata uwa. Amma nagode da kika tunanin da hakan ,amma inaso ki sauke hannun ki daga kafad'a ta tun kafin in manta da cewa ke ce kika haife ni. Ina kuma baki shawaran ki manta da cewa kin tab'a zama uwa ko kina da wasu 'ya'ya kamar yadda mu ma tuni muka manta da cewa muna da uwa irin ki a duniya..." Ba kad'an ba maganganun Haseena ya tab'a Kubra matuqa. A karo na farko da ta fara jin cewa bata kyauta wa rayuwar 'ya'yan ta ba ,amma son zuciyar ta ya hana ta ganin lefin abunda ta ke aikata wa. A sanyaye kubra ta tashi ta zata fita. Haseena tace "Du be ta Dan Allah! Tana yi kamar ba ta da hannu a duk abubuwan da suke faruwa da mu. Wacece silar tarwatsewar rayuwar mu Dana mahaifin mu idan ba ita ba!" Haseena ta fad'a cikin b'acin rai. Nan take hawaye suka fara sauko mata. Da sauri Suxee ta ajiye kayan da ta ke gyarawa ta matso ta dafa ta tana share mata hawaye tare da cewa "Relax Haseena! Kinsan ba wata isash-shiyar lafiya kike dashi ba. Yau fa aka sallamo ki daga asibiti. Be kamata ace har kin fara ta da hankalin ki haka ba. Babban burin mu a yanzu be wuce muga kin samu lafiya ba"... " Bazan tab'a samun lafiya ba matuqar ina ganin waccar matar!!! Matuqar tana ci gaba da kiran kan ta mahaifiya ta!!! Yaya suxee waccan matar da kike gani ba kowa bace silar faruwar abunda ya faru dani fa ce ita ,itace ummul abasin faruwar komai. Na tsane ta bana son ganin ta, wallahi idan aka yi wasa ni ce ajalin ta ,idan kuwa hakan bata faru ba ,to ita zata zama sanadiyyar nawa ajalin. Yaya suxee na tsane ta ,kice ta fita daga nan bana son ganin ta" Haseena ta k'arasa maganan tare da fashewa da wani marayan kuka ,a lokaci d'aya ta fad'a jikin Suxee tana ci gaba da rera kukan ta me ban tausayi. Suxee ita ma nan da nan hawaye suka fara sauko mata na tausayin kan su... Rai a matuqar b'ace Kubra ta juyo tare da cewa "Kin fita a hankalin ki ne? Me..." "Ya isa haka Dan Allah." Suxee ta katse Kubra ,sannan taci gaba da cewa " Ya isa! Wasan kwaikwayon ya isa haka. Dan Allah ki tafi. Kin zo ganin mu ko ? To mun gode da ziyara Allah ya ba da lada. Ki tafi pls ki bar mu da abunda muke ji ,tun kafin ki janyo mana wata masifar bayan wacce muka shiga"... Suxee ta fad'a hawaye na sauko mata. Zuciyar Kubra ta shiga k'una ,iya b'acin rai ran ta ya b'aci. A fusace ta fita hawaye na sauko wa daga idanuwan ta. Da gudu ta haura sama ,ba ta ko lura da Khaltum dake lab'e a wurin ba ,da alama taji duk abun da ya wakana tsakanin Kubra da 'ya'yan ta... Wani irin dariya Khaltum ta yi na makirci. Tare da d'aukar alwashin gano bakin zaren... MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [8/11, 9:14 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA TALATIN DA SHIDA_ *_____________________________* _Kubra kai tsaye d'akin ta nufa ,tana zuwa ta fa d'a kan gano tare da fashewa da wani sabon kuka me tattare da takaici da bak'in ciki. A rayuwa bata tab'a tunanin rana me kama da wannan za ta zo mata ba. Ace yau 'ya'yan ta na cikin ta ne suke furta mata Kalmar tsana da k'iyayya har suna furta k'ila su ne ajalin ta. Wannan Abu ba k'aramin tab'a kubra ya yi ba. Dan yinin ranar ko ina ba ta iya zuwa ba ,a d'aki ta wuni..._ Ganin haka yasa Khaltum ta zo sashen ,a kan gado ta samu kubra tayi rufda ciki ,da alama wani gajeren bacci ne ma ya kwashe ta ba tare da ta sani ba. D'an bubbuga gadon Khaltum tayi. Firgigit Kubra ta farka. Daga gefen gado Khaltum ta samu ta zauna tare da tambayar Kubra abun da ke damun ta "Ya na gan ki haka ne hajj Kubra? Ba ki da lafiya ne? Tun d'azu ina ta jiran ki har na gaji da jira na koma ciki. Yanzu ma gani nayi shirun yayi yawa nace bari in leqo inji ko lafiya. A karo na farko da kika fa sa zuwa chasu ,nasan ko menene lallai babban dalili"... Khaltum ta fad'a kamar ba ta ji komai ba. Wani nannauyan ajiyan zuciya Kubra ta sauke tare da cewa " Khaltum ina so in gyara tsakani na da 'ya'ya na!!! Ina so in ba su kula wa na tsakanin uwa da 'ya'ya... Khaltum ina son yara na ,bazan iya jure ganin su cikin wani hali ba... Ba zan tab'a yafe wa kaina ba idan wani abun ya same su ta sanadiyya ta ,balle ace wani na da hannu a cikin b'ata musu..." Wani kallon mamaki Khaltum ta bi Kubra da shi kafin tace "Me hakan ke nufi kenan? Ya na nufin zamu da ne shaqatawa da shar holiya? Kin San hakan ba k'aramin asara bane gare mu. Ki manta da wannan ,mu mori rayuwar mu. Naga cewar yaran lafiyar su qalau, kuma mahaifin su na kula da su ,me yasa zaki damu kan ki?"... " Khaltum ba zaki tab'a gane abun da nake nufi ba ,ba zaki tab'a gane irin soyayyar dake tsakanin uwa da 'ya'ya bane. Da zaki shiga zuciya ta kiji irin zugin da nake ji a yanzu da baki fad'i cewa in manta da su ba. Ko da yake ta ina ma zaki San me nake ji bayan ba uwa bace ke??? Ta ina zaki san abunda nake ji a yanzu bayan baki san darajar 'ya'ya ba. Da ace kin tab'a d'aukan ciki ko da so d'aya ne ,ko baki haife cikin ba ki kayi b'ari ina ga zaki fi gane d'acin dake rai na a yanzu. Ban ma ga amfanin zama ina gaya miki wannan ba Dan be shafe ki ba ,kuma ba ki da maganin da zaki mun. Uwa ya kamata in fad'a wa wacce tasan darajar 'ya'ya ,wacce ta tab'a d'aukan ciki ta haihuwa amma ba ke ba"... [8/11, 8:29 PM] SIDIYA...✍️: Ba kad'an ba kalaman Kubra ya yi matuqar k'onawa Khaltum rai. Dan ta fahimci akwai suka da habaici a cikin maganganun Kubra. Wato me Kubra ke so tace mata? Tana nufin ita juya ce ko kuwa? Tana nufin ita bata San zafin haihuwa ba shiyasa bata San darajar 'ya'ya ba? Lallai ya kamata ki farka daga dogon baccin da kika yi Khaltum' Khaltum ke ta faman sak'e-sak'e a ran ta. Tab'e baki ta yi tare da cewa "Wannan haka ne kam. Amma ga wannan ina ga idan kika sha ze rage miki rad'ad'in abunda kike ji a yanzu, nasan zaki ji dad'in shi"... Khaltum ta k'arasa fad'a tare da mik'e wa Kubra wani syrup. Ba musu kubra ta karb'a kwalban maganin nan ta d'aga ta shanye se dai ta aje kwalba ta shanye tas... Nan kubra ta fara sambatu iri iri akan tana so ta kasance da 'ya'yan ta. Wannan ya k'ara tabbatar wa da Khaltum cewa lallai kubra ta fara damuwa akan yaran ta ,ta San kuma komai ze iya faruwa daga wannan lokacin. Tashi tayi ta koma sashen ta. Ranar bata iya yin bacci ba ,kwana tayi tunanin yadda zata b'ullowa al-amarin, kafin safe ta yanke wa kan ta hukunci.... Kusan sati d'aya Kubra bata lek'o koda k'ofar sashen ta ba. Har wani rama tayi. Amma da yake fitar a jinin ta yake bayan sati d'aya da faruwar abun. Wata rana da la'asar tana zaune taji fitar ta tsikaro ta ,tana tunanin yadda za'ayi ta fita kawai se ga kiran Hajja Fati ta gaya mata akwai chasu. Dan haka kubra ta gama shirin ta tsaf na zuwa wannan chasun. Bayan ta gama shirya wa ta biya ta sashen Khaltum akan ta sanar da ita fitan ko za ta shirya su je tare. Daga farkon dusan sashen Khaltum d'in ta fara jiyo k'amshin girki. K'arasawa tayi ciki tare da zama kan d'aya daga cikin manyan kushin d'in da ke makeken parloun... Khaltum ce ta fito rik'e da wasu manyan kuloli a hannun ta ,tana ta aikin jera wa ,taci ado matakin k'arshe, tana ta Ku d'ai-d'aya kamar bata son taka k'asa. Har tazo ta wuce ta gaban kubra ba Dan bata gan ta ba. Kubra bata kawo komai a ranta ba. Da fara shimfid'e akan fuskar tace "Wannan wanka haka yau kuma Khaltum ,ko dai bak'i za muyi ne a gidan ,naji se k'amshin girki ne ke tashi." Wani irin murmushi Khaltum take yi. Dawowa tayi ta zauna kusa da kujerar da Kubra ke zaune suna kallon juna ,tace "Aikuwa kin ga se aiki nake ta fama da shi. Da wani abun ne?" "Eh wallahi Hajja Fati ce ta kira ni akan akwai chasu a NANAYE CLUB ,shine nace bari in zo in gaya miki ki shirya mu je" inji kubra Khaltum tace "Ayyah! Gaskiya zan kuwa so in halarci wannan chasun dan nasan ba makawa ze ba da citta. Se dai kash! Gaskiya ina da wani d'an uzuri da ze katange ni daga fita yau"... Kubra tace "Haba dai! Ke d'in kuma? Tukunna ma wasu bak'i ne za'a yi haka da har zaki fasa fita saboda su. Ke da bakya son bak'i" Kubra ta fad'a cike da tsokana Wani irin dariya Khaltum tayi tare da cewa "Kai Anty Kubra" Hab'a kubra ta rik'e tare da cewa "Yau kuma wani salo ki ka tashi da shi ne? Wai Anty Kubra ,wallahi ko dad'i be yi ba ,dama kin koma yadda kika sa ba ,Dan ya fi dad'i" Khaltum tace "Ai kuwa da zaki karb'i sabon canjin sunan da ya fi. Dan daga yau sunan ki kenan" Kubra tace "ko me yasa?" Khaltum tace "Ko kin manta ke kishiya ta ce? Ke fa uwar gida na ce ,to ai ya zama dole na baki girma. To bari ma in baki labari ,ni ba bak'in da zan yi girki zan karb'a yau. Saboda haka wannan shirin duk na Alhajin Allah ne"... Wani guntun tsaki Kubra ta ja tare da cewa " Dan Allah malama wasar ya isa haka ,kije ki d'auko mayafin ki ina jiran ki a mota"... Kubra ta fad'a tare da mik'e wa ta juya za ta fita... "Da ma zaki yadda da abunda na fad'a miki da ya fiye miki. Dan kuwa ni ba wani chasun da zan je gaskiya a yau, ba ma yau kad'ai ba ,daga rana me kamar na yau na dena zuwa wani Abu wai shi chasu"... Cak kubra ta ja ta tsaya. Juyowa tayi cike da tarin mamaki tace " To wai saboda me?" "Bakomai!!!" Khaltum ta bata amsa a tak'aice sannan taci gaba da cewa "Na yanke hukuncin daga rana me kamar ta yau ,na dena duk wani shashanci da nake yi ,na dawo na karb'i matsayi na na cikakkiyar matar aure ,Zan kuma zauna in kula da gida na da mijina ,,ina ga ta nan ne kawai zan iya zama uwa har in iya fahimtar duk wani matsala da damuwa da duk wata uwa take ciki"... " wai da gaske ki ke ko da wasa?"" Kubra ta tambaye ta D'aure fuska Khaltum ta yi kafin tace "Kamar ya da wasa? Wallahi da gaske nake miki. Aure na na karb'a hannu bibbiyu. Zan yi rayuwar aure cikin farin ciki da walwala kamar yadda ko wacce matar auren ke yi. Ni ma ina so in ga jini na. 'Ya'ya nake da sha'awar Inga na Haifa. Ni ma ina so in ga masu kira na da mama kamar yadda ke ma kika samu. To da ga wannan lokacin zamu iya ci gaba da duk wani sharholiya da muke yi amma a yanzu gaskiya komai ya dakata in dai dani ne, ke dai ban hana ki ba idan kinji zaki iya ga hanya ,dama a harkar na same ki ,idan yaso ni se in kula mana da gida da kuma mai Gidan..." Wani irin shu'umin murmushi kubra tayi tare da tafa hannu, tace "Wow!!! Gaskiya kin burge ni" k'arasowa tayi har inda Khaltum ke tsaye tace "Ni dama nasan rana me kamar na yau ze zo ,nasan wannan lokacin ze zo ,shiyasa na yi wa toka hanci,,,nayi maganin abun tun kafin yazo yafi k'arfi na. Bazan hana ki zaman aure ba Khaltum ,ga ki ga gida. Amma ki sani GIDAN MISBAHU gida na ne ,kuma ni kad'ai ce matar da zan Haifa masa 'ya'ya"... "K'arye ki ke yi wallahi. Kina zaune zaki ga yadda zan cika GIDAN MISBAHU da 'ya'ya ,Dan idan na fara zazzaga masa yara se na tabbatar na zazzage duk abun da ke mahaifa ta sannan zan tsaya. Oh saboda kin je kin juya mahaifa ba zaki sake haihuwa ba shiyasa ni ma ki ke tunanin nima zan zauna bazan haihu ba? To tun wuri idan ma mafarki ki ke ki farka"... Wani irin kafirin dariya kubra ta fashe da shi har da su dafe ciki. Da mamaki Khaltum ke bin Kubra da ido, Dan a tunanin ta idan ta gaya wa kubra haka zata had'iye zuciya ta mutu ,amma se ta ga sab'anin hakan... Dariya Kubra ke yi ba qaqqautawa ,har se da Khaltum ta fara tsora ta da dariyar... Se da Kubra tayi dariyar ta me isar ta sannan ta tsagaita tace " Ke duk a bahagon tunanin ki zaki haihu a GIDAN MISBAHU??? To wallahi kin makara. Dan kuma haihuwa ba ma a GIDAN MISBAHU kad'ai ba ,haihuwa in dai ta d'aukar ciki ne ki haife se dai ki gani a TV ko ki ji a labarai, amma ba dai ke ba. Ke saboda ma ki cire shakku ina so ki je asibiti na tabbata likitan ze gaya miki ni idan juya mahaifa nayi to ke babu ma mahaifar a cikin ki,,, kin kuwa San ana d'aukar ciki da juyayyen mahaifa amma har abada wacce ba ta da mahaifa ba zata tab'a d'aukar ciki ba. Idan kuma kin mu sa zaki iya zuwa duk asibitin da kike ganin sun k'ware za su tabbatar mi ki da hakan. Na kuma San gwaji ba ya k'arya"... Tana gama fad'ar hakan ya fice war ta. "K'arya ki ke wallahi ,ba ki isa ba. Haihuwa kuma kamar na yi na gama. Aikin banza kawai"... Ta ja wani dogon tsaki. Haka Khaltum ta yi ta bambami tana masifa... MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [8/12, 8:42 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA TALATIN DA BAKWAI_ *_____________________________* _A daren ranar bayan khaltum ta gama da kubra , sai da su ka yi hayaniya da lubabatu a sashen daddy. Duk wani haushin kubra se da khaltum ta sauke shi akan lubabatu, dan ma dai lubabatun ba kanwar lasa bace. Faɗa su ka yi sosai akan khaltum tace ita zata karɓa girki a daren ranar ,lubabatu kuma ta nuna sam bata san wannan zancen ba. K'arshe faɗan har se da ya kai su hadda doke-doke ,ko wacce ta fitar wa 'yar uwar ta jini. Wanda su ke faɗan akan shi kuma baya ma ta tasu ,dan ko kwana bai yi a gidan ba. Wannan abu ba k'aramin k'ara bak'anta musu rayuwa ya yi ba. Asuban farko ko waccen su ta kwashi tarkacen ta ta koma sashen ta cike da haushin er uwar ta..._ Har tsawon sati ɗaya daddy be sake waiwayo gidan shi ba ,amma duk wani abun da ke wakana ya na samun labari ta hanyar Suxee. Ranar wata safiyar Asabar asabar Dr. Zaidu ya kira Haajar akan ya na so yazo su gaisa ,ya kuma sa ke duba jikin Haseena. Haajar bata musa masa ba ,tayi masa kwatance dan a tunanin ta ko bai san gidan bane. Da yamma bayan sallar la'asariyya sai ga kiran Dr. Zaidu ya sheda mata cewar yazo yana bakin gate. Haajar ta yi mamaki sosai yadda aka yi ya gane gidan duk da unguwar ba ɓoyayyen unguwa bace a garin sakkwato... Hijabin ta ta saka har k'asa taja hannun Auta ta rakata. Dr.Zaidu na ganin ta ya sakar mata wani irin murmushi mai ɗauke da ma'anoni iri daban-daban. Ita ma Haajar ɗin maida masa martani tayi, a haka har ta k'arasa bakin motar shi. Sallama tayi masa cikin muryar ta mai daɗin sauraro ,shima ya amsa ta cike da shauk'i... "Sannu da zuwa Dr." Haajar ta faɗa fuske a sake Dr. Zaidu k'ara faɗaɗa fara'ar dake ɗauke a fuskar shi yayi tare da amsa mata. Haajar tace "ya akayi ka gane gidan ,ko dama kasan gidan ne??" murmushi Dr.zaidu ya yi tare da cewa "A'ah bansan gidan ba. kawai dai kinsan barin masoyi baya nisa ne. Bugun zuciyar ki nabi ya yi min iso har zuwa wajen ki".. Dariya Haajar tayi tare da cewa "Kai dai ba ka rabo da abun dariya". taci gaba da cewa "ba za ka shiga ciki bane ,ka tsaya a waje?" "A'ah! ai nan ma yayi. Asibiti zan je an kira ni akwai aiki ,nace bari in biyo mu gaisa". cewar Dr. zaidu Haajar tace "gaskiya kuwa ka kyauta. Mun gode sosai" Dr.zaidu yace "Haba sai kace wani abu. ya jikin Haseena ,fatar ta na samun sauqi sosai ,kuma kuna kula da shan maganin ta akan lokaci??" Haajar tace "Jiki Alhamdulillah. Magani kuma tana sha akan lokaci". Dr.zaidu yace " masha Allahu. hakan na da kyau. ki gaishe mun ita dakyau" "za ta ji" haajar ta bashi amsa. Da haka su ka yi sallama ya wuce ita kuma ta koma ciki... Duk wani motsi na su, daddy da ke gefe cikin wata mota me bak'in gilashi ya na kallon su, Wanda ba'a iya hango Wanda ke ciki sai dai na ciki yaga na waje,,,, zuciyar daddy har wani tafasa take saboda wani irin kishin Haajar da ke fizgar shi ,a gefe d'aya kuma wani irin haushin Dr.Zaidu ne ya kama shi ,musamman lokacin daya ga Haajar na masa murmushi, ji yayi kamar yabi takan su da mota ya taka su ,ko ya rage jin rad'ad'ad'i da zugin da zuciyar sa ke masa. Kan shi ya had'a da sitiyarin motar ,ya dad'e a haka a hankali ya fara samun nutsuwa ,hankalin shi ya dawo jikin shi ,kafin ya k'arasa cikin gidan... A b'angaren Khaltum kuwa tun lokacin da Kubra ta gaya mata cewar babu mahaifa a jikin ta ta kasa samun natsuwa. Ko rufe ido tayi maganganun Kubra ne kad'ai ke yi mata yawa a k'wak'walwar kai. Gaba ki d'aya ta kasa samun kwanciyar hankali ,gashi ba ta da Wanda zata kira ya ba ta shawara. Sai a lokacin ta tuno da rabon da ta kira mahaifiyar ta har ta manta ,kuma ta sha ganin kiran ta a watannin da suka wuce amma ba ta d'auka, k'arshe ma sai dai ta katse kiran ,ba Dan komai ba sai Dan ganin da take yi kamar ta samu duniya a hannun ta. Jin dad'in duniya ya sa ta manta da komai da kuma kowa na ta ,ba ta sauraren kowa ,ba kuma ta da lokacin komai sai sha'anin gaban ta sharholiya. Sai a yanzu take da nasanin duk wasu abubuwan da suka faru a baya... Daga k'arshe ta yanke shawarar ta je asibiti wajen k'wararren likita ,ko zata cire shakkun dake zuciyar ta. Domin ta fi kowa sanin wacece kubra da kuma shu'umancin ta ,ta San kubra tantiriyar gaske ce matakin farko babu abunda baza ta iya aikata wa ba Dan ta cimma burin ta... Da wannan shawarar Khaltum ta yanke cewa za ta je asibiti ,duk da ba wai ta yadda da kalaman Kubra bane ,ta San da ran ta da lafiyar ta ba yadda za'a yi ace an cire mata mahaifa ba tare da sanin ta ba... Washe gari da safe Khaltum ta shirya ta je asibiti. Kusan asibiti uku tana zuwa amma sakamakon iri d'aya ne shine ba zata tab'a haihuwa ba ,saboda babu mahaifar da d'a ze iya kwanciya a cikin ta balle har ta haife sa. Daga baya ma suka gano cewa ta tab'a samun ciki ta cire ,wannan Abu yayi matuqar d'aure wa Khaltum kai. Duk da irin jawaban da ta samu daga wurin likitoci daban-daban ,hakan be sa ta gama gamsuwa ba ,haka tayi ta yawo duk wani asibitin da ta ji ance sun k'ware wurin duba mata se Khaltum ta je ,amma maganar d'aya ce bata canza ba. Wannan al-amari ba k'aramin tayarwa Khaltum yayi da hankali ba... Ta ci kuka kamar ba gobe ,idanuwan ta kamar za su fad'o k'asa Dan tsabar kukan da ta darza. Tana dawo gida sashen ta ta wuce ,ta fara watsi da duk wani abun da ya zo gaban ta. Tana kuka tana fad'in "Me nayi miki haka Kubra??? Wani irin laifi na miki da zaki mun wannan sakayyar??? Kubra kin cuce ni ,kin cuce ni,,, bazan tab'a ya fe miki ba,,, ko da zan tafi da zani d'aya se naga bayan ki ,,,,sai na d'au fansa akan ki,,, idan kuwa Kika ga ban zama ajalin ki ba ,to lallai ni ba 'yar halak bace..." Haka Khaltum ta yi ta sambatu iri-iri. Cikin d'an k'ank'anin lokaci ta fita a hayyacin ta ,idan ka ganta jiya ka ganta a yanzu ba zaka tab'a cewa Khaltum d'in daka sani bane. Wayar ta ta d'auko ta kira mahaifiyar ta ko zata ji dad'i a ranta. Sai da kiran ya kusa yanke wa sannan Hajiya khairi ta d'auka. Wani matsananci Kuka Khaltum ta fashe da shi tana fad'in "Hajiya kubra ta cuce ni,,, kubra ta min kisan zaune,,, ta gama da rayuwa ta"... Hajiya khairi tace " wai me kubran ta yi miki?" Khaltum na kuka ta zayyanawa Mahaifiyar ta duk abunda ya faru.... A mamakin Khaltum sai jin tayi Hajiya khairi ta fashe da dariya tare da cewa "ba kiga komai ba khaltum. Wallahi so nayi ace kubran ta kashe ki gaba d'aya kowa ma ya huta. Mutuniyar banza kawai""" Hajiya khairi na gama fad'ar haka taja wani dogon tsaki tare da yanke kiran... Wani irin ihu khaltum tayi ,Cike da tashin hankali ta yi jifa da wayar hannun ta ,se da wayar ta fashe ,a lokaci d'aya ta sake fashe wa da wani marayan kuka. Haka ta kwana a zaune tana aikin Abu d'aya. Can cikin dare ta fara jiyo hayaniya sama-sama. Kamar dai ba zata fito ba ,Dan abunda ya ishe ta ya ishe ta ,sai kuma ta ji hayaniyar yayi yawa Dan haka ta leqo ta ga meke faruwa... Wuta ne ke tashi daga sashen daddy. Dukkan ma'aikatan gidan sun taru a wajen suna ta aikin kashe wutar ,amma wutar kamar dad'a hura ta suke yi. Lubabatu se ihu take tana kururuwa ,wannan ne ya k'ara janyo hankalin mutane da dama zuwa wurin. Daddy baya nan d'aya daga cikin ma'aikatan gidan ne ya kira shi a waya ya sanar mishi da abunda ke faruwa, cikin mintunan da basu Gaza biyar zuwa goma ba sai gashi. Kubra ma bata nan ,sai su Haajar ne da basu San wainar da ake toya wa ba. K'arar motar ruwa ta kashe wuta ne ya sa suka leko su ga abunda ke faruwa. Cikin tsananin tashin hankali suka k'arasa wajen. Mutane sai rirrik'e daddy suke yi dake ihun "Dukiya ta!!! Jama'a Ku taimake ni!!! Duk Wani abunda na mallaka yana ciki!!! Ku taimake ni!!!"" Haka aka yi ta rik'e shi ,a cikin masu rik'o shi hadda Haajar dake ta aikin kuka. Duk rashin imanin ka idan ka ga daddy a wannan ranar Dole ka tausaya masa. A haka yana ji yana gani komai da komai ya k'one k'urmumus ,sai wuraren asuba aka yi nasarar kashe wutar ,lokacin komai da komai na sashen daddy ya koma gawayi.... MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [8/13, 8:58 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* *INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN...ALLAH YA YI WA MAHAIFIYAR AUFANA RASUWA. D'AYA DAGA CIKIN MARUBUTAN QUNGIYAR MU TA INTELLIGENT. HAQIQA RASHIN MAHAIFIYA BABBAN RASHI NE DA YA FI KO WANI RASHI D'ACI A WANNAN DUNIYA. ALLAH YA JIQANTA DA RAHAMA YA KUMA KYAUTATA MAKWANCIN TA. AMEEN.😭😭👏* _BABI NA TALATIN DA TAKWAS_ *____________________________* _Haqiqa wannan al-amari na gobara ba k'aramin rikita daddy da duk wani masoyin shi ya yi ba fiye da yadda mai karatu ke tunani. Wannan na nufin duk wani wahala da daddy ya sha sama shekaru aru-aru ya tafi a banza. Dukiyar daya dad'e ya na tarawa yau rana d'aya ta qone qurmumus. Ka ma daga takaddun manyan gidajen shi ,takaddun manyan filayen shi ,takaddun kamfanonin shi ,kai hadda na kwantiragin shi komai ya qone. Lallai dole daddy ya shiga rud'ani da tashin hankali Mara misaltuwa. Domin kuwa kariyar azziki babban masifa ne ,Wanda ya zo mana a hadisi ingantacce cewa Annabi s.a.w yace "A TAUSAYA WA DUK WANDA KARIYAR AZZIKI YA SA MA"..._ Tun a washe garin ranar da abun ya faru Hajj Jamil ya samu labari. Dan haka be yi qasa a guiwa ba wajen zuwa yi wa daddy Jaje. Nan da nan gari ya d'auka, kasancewar daddy babban mutum ne. Nan fa k'ananan maganganu suka dinga tashi ,wasu suce " ije aka yi wa daddy saboda d'aukaka shi da Allah ya yi...wasu kuma suce da sa hannun abokan kasuwancin shi...kai wasu ma cewa suke da sa hannun uwar gidan shi wato Kubra... Haka dai maganganu suka yi ta yawo lungu da sako ,sakkwato da kewaye... Har tsawon sati biyu da faruwar abun mutane kai kawo suke a gidan daddy wajen yi masa jaje. Yayin da matakan tsaro suka ba da k'aimi wajen tuhumar duk wani Wanda aka San abokin hammayar daddy ne. Daga k'arshe daddy yace ya fawwala wa Allah komai na shi, saboda haka a dakatar da binciken da ake yi Dan kar a d'au haqqin mutane da da ma. Wata d'aya da faruwar wannan iftila'i wani masifar ya sake tunkaro wa. Dan kuwa Khaltum na nan akan bakan ta na ganin ta d'au fansa kan abunda kubra ta yi mata... Wata rana Haajar, Suxee da Auta sun fita tare da daddy ,an je kai Haajar asibiti kasancewar ba ta jin dad'i. Haseena kuma tana gida tana bacci ko da suka tafi ganin hakan ma yasa basu tashe taba suka tafiyar su Dan ba dad'e wa zasu yi ba...Bayani Haajar tayi wa likitan akan duk abunda take ji. Ya basu gwaji na fitsari dana jini ,bayan an yi ,aka ce su dawo gobe Dan karb'an sakamakon. Da haka suka juyo suka dawo gida. A garden daddy ya tsaya tare da auta. Haajar tace bari ta k'arasa ciki ta kwanta Dan wani jiri da take ji. Tare da suxee suka k'arasa... Duk wani motsi na su akan idon Khaltum su ke yin shi. Sai da ta tabbatar ta ga shigar su sannan tabi bayan su. A tunanin ta ko Suxee da Haseena ne ,Dan bata ma San da Haajar a gidan ba. Khaltum ce ta fito ta nufi sashen kubra. Sai da ta tabbatar ta kulle duk wani k'ofa da window na ciki da na waje, sannan ta haura sama ,inda ta tabbatar za ta samu kubra... A kwance ta samu kubra ta jingina da kujera ,idanuwan ta a lumshe ,k'arar sauti na tashi a hankali. A gefe kuma ga lemu me sanyi a kofin glass da alama ta gama sha ne ta ajiye... Jin kamar alamun tsayuwar mutum akan ta yasa ta bud'e idanuwan ta. A hankali ta sauke su akan Khaltum dake tsaye tana qare mata kallo tsaf. Tashi zaune kubra tayi ta zauna daidai kafin tace "Sannu da zuwa! Se kuma kika tsaya a tsaye sai kace wata baquwa? Ki zauna mana" ta fad'a tana nuna mata wurin zama Khaltum da idanuwan ta ya cika da hawaye tace "Kubra ba zama ya kawo ni ba. Ina so ki gaya mun ta yadda kika saka aka cire mun mahaifa ,da kuma lokacin da aka yi bansani ba ,Dan nasan ba ke ce za ki yi da kan ki ba ,saka wa za ki yi ayi." Wani irin guntun murmushi kubra ta yi tare da cewa "Na fuskanci kin d'au zafi da yawa. Amma ga wannan kisha ko zaki ji sanyi a ran ki." Ta k'arasa maganan tare da mik'a mata ragowar lemun dake Kofi a kusa da ita. Kau da kai Khaltum ta yi gefe tare da cewa "Ba na buqata. Ki amsa min tambaya ta kawai". Baki kubra ta tab'e tare da cewa " Gaggawar me kike yi? Da kin kwantar da hankalin ki ma har d'akin ki zan zo in gaya miki yadda komai ya wakana. Khaltum ban so tsiya ya had'a mu. Ke kika ja wa kan ki. Dan naji lokacin da kike waya da wata qawar ki a qasar Germany cewa idan har kika samu da ma zaki kawar da ni. Ni ko se naga duk zaman amanar da nake dake Ashe ke ba da zuciya d'aya kike zauna dani ba. Daga wannan lokacin na shirya komai da wata qawata da ke aiki a babban asibitin Germany ,na baki wata k'waya me k'arfi kika sha Dan in d'auke miki hankali ,na kuma Nasara k'wayar ta yi miki cikin sauqi ,na d'auke ki cikin mota na kai ki asibitin na kuma fad'a musu yadda nake so ayi ,cikin minti talatin akayi komai aka gama. Satin mu d'aya a asibitin ba tare da kin sani ba sakamakon allurori da ake miki masu qarfin gaske. Kinji yadda na tsara komai. Ni Kubra kuma kowa yaci tuwo dani miya sha ,bana yafe wa duk Wanda na yadda dashi yake k'ok'arin cin Amanata. Idan akwai Wanda na kama ta in d'aga wa k'afa be wuce Hajja Fati ba ,nasan kinsan yadda take a wuri na ,amma taci Amanata yanzu haka na turo wa Mijin ta videon iskancin da tayi da babban aminin shi ,da duk wani shiri da suke yi na ganin sun raba shi da kujerar daya ke kai na sarauta. Na tabbata komai ya dagule mata kawo yanzu. Idan wannan ne ya kawo ki zaki iya tafiya..." Kubra ta fad'a tare da d'aukar kofin lemun nan ta kai bakin ta... Da sauri ta janye kofin lemun daga bakin ta ,tare da shaqar iska Dan ta tabbatar da k'amshin da take ji. "Wannan kamar warin gass nake ji?"" Kubra ta fad'a tare da waiga wa.. Khaltum dake shawaye tace "ba wai bane. Warin gas ki ke ji. Idan kinsan me za ki aikata to baki San me za'a aikata miki ba Kubra. Fad'an wasa shi ake yi wa matsaya ,amma fad'ar gaske kuwa kwana ake yi ana yi. Ni Khaltum jinjirar d'an tsako ce me kwarjini a idon d'an angulla. Gonar sama mai wuyar kai taki... Tabbas kin samu Nasara a karo na farko ,amma ina me baki albishir da cewa kin yi na farko kuma kin yi d'an Autan k'arshe. Ni ni kad'ai kika yi wa amma daga ke har 'ya'yan ki da kike magana akan su wannan ita ce ranar Ku ta k'arshe a duniya... Kubra furzar da lemun dake bakin ta tayi tare da cewa " Me kike shirin aikata mana haka?" "Kashe Ku Zan yi. Wannan warin gas d'in da kike ji ,tukunyar gas d'in ki ce na bud'e ,nasan zuwa yanzu ya karad'e ko ina dako ina. Na fi son ayi mutuwar kasko wallahi d'a kwance uwa kwance. Kamar yadda na d'au alwashi ,nima nafi son in rasa rai na matuqar buri na ze ciki..." Cike da tsaro kubra ta mik'e tsaye tana zaro ido tare da cewa "kin kuwa San me kike yi Khaltum? Rai fa zaki kashe? Menene amfanin hakan? Wallahi Allah baze bar ki ba. Wallahi wuta zaki je" "Dalla malama dakata!!" Khaltum ta katse ta, sannan taci gaba da cewa "ke har kinsan Allah. Nasan ke abunda kika aikata mun aljannah zaki ce tunda a gidan uban ki ake raba ta. Muguwa kawai me zuciyar 'yan wuta. Nafi son tun a duniya wutar Allah ta fara kama ki kafin kije ki taradda babban azabar ki." Jin haka yasa kubra rugawa ta gudu ta nufe hanyar fita ,tare da ihun a taimake ta. Se dai bata yi sa'a ba ,dan duk k'ofar data je a kulle gam take jin ta. Ganin haka yasa ta saduda ,ta dawo ta zube k'asa kan guiwar ta kusa da Khaltum tana rok'on ta akan tayi hakuri tayi mata rai ,wallahi ba zata sake ba. Khaltum na kuka tace "Lokacin Neman afuwa ya k'are miki kubra. Yanzu lokacin girbar abunda kika shuka ne. " tana gama fad'in haka ta kunna ashanar dake hannun ta ,kubra na ihu tana Neman taimako haka Khaltum ta cilla wutar ashanan nan. Nan take wuta ta fara ci ,ko ina da ko ina ya ka ma a lokaci d'aya. Wuta ne yake ce a sashen kubra sosai. Nan danan hankalin mutanen ciki Dana wajen gida ya dawo nan. Dummmm! Kake ji kamar ta ya ta fashe. Wannan k'arar ne yasa daddy dake garden ya ankaro. Da sauri ya taso Dan ganin me ke faruwa. Kafin ya k'araso sai mutane ya gani suna shigowa ,ga gate an bud'e motar kashe wuta na shigo wa. Ai da gudu shima ya isa. A hankali hayaqi ya fara zagaye d'akin qasa da su haajar ke kwance ,tari suka fara ita da haseena ,Suxee dake band'aki da sauri ta fito Dan ganin meke faruwa. Aifa nan taga hayaqi ,ko gaban ta bata gani sosai ,tari ta fara yi sosai. Tana k'ok'arin kiran sunan Haajar Dana suxee... Da lalube har ta isa bakin gadon, ta lalubo hannun Haajar ,ba tare da tana ganin gaban ta ba saboda hayaqin daya yi yawa a d'akin. K'ok'arin kiran junan su suke yi ,yayin da mutanen waje ke k'ok'arin fasa k'ofar Dan shiga ceton su. Daddy se fad'in yake " 'ya'yana na ciki Ku taimake ni,,,Ku taimake ni 'ya'ya na. Wannan Wani irin musiba ba ne??? A karo na farko dukiya ta yanzu kuma 'ya'yana... Na shiga uku ni MISBAHU na ga ta kaina... Ihun Sunan Haajar ya fara yi kafin ya shiga kiran sunayen su suxee... A wannan karon daddy kusan zautuwa yayi. Dan yana ji yana gani wuta na ci ga 'ya'yan shi a ciki. K'arshe fad'a wa yayi da shi aka yi ta k'ok'arin k'ofar baya. Amma ba alamun k'ofar zata bud'e... MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [8/15, 7:27 AM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA TALATIN DA TARA_ *_________________________________* _Da k'yar masu k'ok'arin ceton rayuwar iyalin daddy suka yi nasarar fasa k'ofar baya, a lokacin har wutar ta fara ruzga gini. Sama suka nufa 'kofar da suke iya jiyo ihun Kubra. Sun yi iya bakin k'ok'arin su wajen bud'e k'ofar amma ina hakan bai yiwu ba. Dan khaltum ta datse ko ina da ko ina ,bayan makulli sai da ta saka hadda mab'allin kwad'o ,hakan yayi tasiri da kuma wutar dake ci a wannan lokacin. Ganin da suka yi wutar sai dad'a ruruwa take yi ga shi basu iya Ciro ko da mutum d'aya ba ,yasa suka bar wannan k'ofar Dan dole, suka koma ta k'ofar da su Haajar ke ciki._ Sai da suka yi da gaske kafin suka yi nasarar b'alle k'ofar. Da taimakon Allah suka iya Ciro mutum biyu daga ciki da ba iya tantance ko su waye ba ,sakamakon rud'ani da kuma yanayin tashin hankalin da ake ciki... Ana fito wa dasu daidai lokacin da motar asibiti ta k'arasa. Kai tsaye asibiti aka wuce dasu Dan ba su agajin gaggawa. Sannan suka koma a karo na biyu dan sake ceto sauran mutanen da ke ciki. Sai dai ina ,,,a wannan karon ba hanyar shiga, Dan kuwa wutar ta kama ko ina da ko ina. Wani daga cikin su me suna Auwal ne ya ke k'ok'arin ganin ko ta halin yaya ya kutsa dan ceton rai. A daidai lokacin da ya kai jiki ze shiga ciki ,wata Katanga dake famar ci da wuta ta ruguzo masa sai akan k'afa, da sauri sauran mutanen dake wajen suka k'araso suka d'auke shi. Yayin da masu kashe wuta wato (fire service) ke iya k'ok'arin su na ganin sun kashe wutar... Su na ji su na gani haka wuta taci gaba da ci. Jim kad'an suka jiyo wani k'ara tussss ,alamar kayan cikin mutum ya fashe. Duk Wanda ke wurin sai da ya razana ,wasu daga ciki har zubarda k'walla suke yi dan tsabar tausayi. Ba jima wa suka sake jiyo irin wannan sautin alamar kayan cikin wani ya sake fashewa. Cike da gigita daddy yayi kukan kura yana so ya fad'a ciki ,yana fad'in "rayukan 'ya'yana!! Allah ka taimake ni!!! Ku ban ni in shiga in ciro yarana! Kuna kallo wuta na cin iyalina!!!" Haka daddy ya dinga sambatu iri daban-daban. Kusan duk wanda ke wurin sai da ya tausaya mass. K'arar sautin fashewar kayan cikin mutum suka sake jiyo wa a karo na uku. A wannan karon daddy yanke jiki yayi ya fad'i, sai da aka kwashe shi a k'asa sumamme se asibiti... Wannan al-amari ba kad'an ba yayi masifar tayar wa mutane da hankali. Har kusan yamma kafin aka samu nasarar kashe wutar da ke ciki. Dak'yar aka yi nasarar zaqulo gawawwakin su ,dan kusan sun k'one qurmusus. A irin qonewar da su ka yi ,ba na tunanin ko rayuwa suka yi za su yi wani amfani a duniya ,mutuwar dai itace Hutu a gare su... Gawar mutum uku aka fitar ,Wanda ba'a iya tantance su waye da waye ba. Nan da nan gari ya d'auka. Hajj jamil shine Wanda yayi ruwa yayi tsaki akan mamatan. Washe gari da safe aka sallata gawawwakin aka kai su gidan su na gaskiya. A nan sai dai muce Allah ya jiqan wa'ayanda suka Riga mu gidan gaskiya... Kwanan daddy uku a asibiti be San Inda kan shi yake ba. Hajj jamil ne ya kira hajiyar daddy ya sanar mata. Ba shiri hajiya ta taho sakkwato hijab a baibai... Hajj jamil ne ke kula da daddy yayin da Hajiyar daddy ke kula da sauran majiyatan ,da basu qone ba ,sai dai jikata da suka yi had'ida qananan raunuka... A rana ta hud'u daddy ya farfad'o. Kuka sosai ya ke na rashin 'ya'yan shi. Dan shi duk a tunanin shi gaba ki d'aya ba'a fidda kowa ba. Dan idon shi ya riga ya rufe ,ba ze iya tantance lokacin da aka fito da wasu ba balle har ya iya Sanin ko su waye daga cikin su... Hak'uri Hajj jamil ya shiga ba shi tare da yi masa nasihohi akan qaddara, ya d'ora da cewa "wannan itace taka qaddarar MISBAHU,,, ba kuma dan Allah baya son ka bane yayi maka haka. Kar kayi mamakin wani tanadi ya maka Wanda yafi Wanda ya karb'a daga wajen ka"...haka hajj jamil ya dinga rarrashin daddy. Daddy na kuka yace " ka banni inyi kuka jamilu. Na rasa komai da kowa nawa. Ba ni da kowa ba nida kowa. Wannan wani irin musiba ce??? Wani kalar baqar qaddara ce ke bibiyata haka??? Me na aikata Dana cancani irin wannan tashin hankalin??? Gidana ya dawo tamkar kushewa" Hajj jamil na hawaye yace "Ka dena fad'ar haka MISBAHU. Baka rasa komai da kowa ba tunda ka na da Allah. Ya kuma San dakai. Shine kuma ze Isar maka ga dukkan al-amurran ka...MISBAHU kar ka manta Allah s.w.t Idan ka ga kayi dariya ni na saka ka ,idan kuma kaga kayi kuka to ni ne na saka ka shi ma...idan allah ya saka ka dariya ba wanda ya isa ya sa ka kuka ,idan kuma ya saka ka kuka to wallahi ba wanda ya isa ya saka ka dariya. Wannan shine karantarwa ta aqida... Allah dakan shi yace a cikin littafin shi mai girma "WA ANNAHU HUWA ADHAKA WA ABKA" Wato Allah shine me dariyantarwa, kuma shine me kukantarwa. Saboda haka ka yi tawakkali da Allah sai ya kaga ya Isar maka ga dukkan al-amurran ka..." Wannan nasiha ba kad'an ba ya shigi Daddy. Hajiya da ke gefe ita ma ta karb'e shi ,sai abunda Allah be bata ikon fad'a wa daddy ba na Kalmar nasiha da rarrashi. Daga k'arshe tace "MISBAHU baka tab'a baqanta mun ba ,ban tab'a rik'e ka a raina koda na sakan d'aya ba. A koda yaushe Addu'a ta da albarka ta na tare da kai. Ba zaka tab'a ganin ba daidai ba ,insha Allahu lafiya zaka gama..." Wannan Kalma ba kad'an ba ya sake kwantar wa da Daddy hankali. Satin daddy biyu aka sallame shi daga asibiti. Ranar da aka sallame shi ,Hajj Jamil yace yazo ya raka shi yana so ze dubo wani a cikin asibitin. Ba musu daddy yabi bayan shi. Sallama suka yi tare da shiga d'akin majinyatan. Haajar ce akan gado daya ,daya gadon kuma dake gefe Suxee. Ga hajiya a zaune akan kujera tare da auta. Da mamaki daddy ke bin su da kallo ,murza yayi yana so ya tabbatar da abunda yake gani. Ganin kamar yana shakku yasa Hajj Jamil ya janyo hannun shi suka zauna daga gefe kan gadon da Suxee ke kwance. Cike da al'ajabi daddy yace "Haajar,,, Hajiya k'arama da ma Baku mutu ba?""... Murmushi Haajar tayi tare da cewa " Allah ya raya mu Daddy ". Dariya maganar ta ya bama kowa. Suxee tace " Daddy ya jikin ka?" Tsabar farin ciki yasa daddy ya ma kasa amsa ta. Se bin su yake da ido kamar yau ya fara ganin su. Hannu ya d'aga sama tare da godewa Allah, ya kuma sake gasgata maganganun Hajj Jamil ,ga shi yanzu Allah ya dawo masa da wasu daga cikin ahalin shi a lokacin daya fi buqatar su... Hajiya tace "ka gani dai ko? Dama mun Bari ka samu sauqi ne tukunna kazo ka gan su. Amma haqiqanin gaskiya da aka ce maka kowa na ka ya mutu ba gaskiya bane ,Allah ya fitar maka da wasu daga ciki. Ka ga shi Allah ba'a yanke rai da rahmar sa. A koda yaushe kuma Rahma da ni'imar sa kewaye take da bayin shi salihai"... Jinjina kai daddy yayi cikin zuciyar shi ya sake godewa Allah. A fili ya furta " Lallai Allah ne abun godiya"... Suna zaune likita ya zo ya kawo takaddar sallama nasu Haajar tare da magungunan su. Had'ida sheda musu cewa Haajar ta dawo sati na sama a sake duba ta. Hajj Jamil ya tambaya ko da wani matsalar ne? Likita ya mik'a mi shi sakamakon gwajin da aka yi wa Haajar. Karb'a Hajj Jamil yayi bayan ya karanta ya saka a aljihu... Gaba d'aya suka d'unguma a mota zuwa gidan Hajj Jamil. Haajar na ganin an d'au hanyar da ba na gidan daddy ba ,tace wa Hajj Jamil dake toqa motar "Abbu sameer ina kuma za mu je?" Ba tare da ya juyo ba yace "Gida na zamu je mana". Girgiza kai tayi tare da cewa " A'ah Dan Allah! Ina so muje gidan daddy akwai abunda nake so in d'auka". Gaban daddy ne ya yanke ya fad'i lokacin daya ji Haajar ta ce aje gidan shi. Ba kad'an ba ya tsani yaji wani labari akan gidan balle har ace wani Abu ya sake kai shi gidan... Hajj Jamil be k'i ta tata ba ya karya motar zuwa gidan daddy... MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [8/17, 3:30 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA ARBA'IN_ *____________________* Har sun kai k'ofar gida barrister Kabir ya yi wa Hajj jamil waya akan yana babban asibiti ,Wanda shi ne mai bincike akan case d'in gobarar gidan daddy ,komai na tafiya ne a k'ark'ashin kulawar Hajj Jamil. Hajj jamil yace masa ya same shi a gidan daddy yanzu... Parking ya yi a k'ofar gida tare da kashe motar. Dikkan su suka fito suka shiga gidan a tare. Tunanin wani sashen za su suka fara yi. Hajj yace su nufi sashen bak'i Dan shi ne kad'ai a gyare, kuma anan zauna lokacin da al-amarin nan ya faru saboda zuwan jama'a ,wasu ya sauke su anan wasu kuma ya kai su masauqin bak'i. Gaba d'ayan su can suka nufa kai tsaye banda Haajar ,da ta zagaya ta bayan gidan da alama ma gidan gona ta nufa. Lubabatu na jin zuwan su ,nan da nan ta isa sashen Har ta na fad'uwa. Kuka ta rushe musu da shi tare da jajanta musu kan abunda ya faru. Wani irin kallo kowa ke bin ta da shi Wanda ya sa ta sha jinin jikin ta, da mamaki kowa ke jinjina rashin kunya da ta ido irin na lubabatu... A ce duk abubuwan nan da suka faru ,duk sintirin nan da aka yi ta tayi na asibiti babu ita ba labarin ta ,ba zuwa ba aike. Ai ko itace hajiya suwaiba uwar Daddy zata rarrashi zuciyar ta tazo idan ma tace duk rad'ad'in abun ne bai gama sakin ta ba... Haka kowa dai ya share ta idan ta kamo wancan batu ta saki ta kamo wannan duk na borin kunya. Babu Wanda yace mata ci kan ki. Gara ma hajiya har ta iya amsa gaisuwar ta. Mik'ewa tayi tare da cewa "bari in kawo muku ruwa". Tana gama fad'ar haka ta mik'e tabar parlourn. Auta ce tace " Ni hajiya bacci nake ji" hajiya tace "to muje ciki, daga nan ma na yi alwala Dan na ji kamar an fara kiran sallah". Hajj jamil yace " mu ma bari muje mu yi sallan hajiya ,mu na dawo wa yanzu" hajiya tace "to Ku dawo lafiya jameelu" daga nan daddy suka fita zuwa masallacin da ke cikin gidan shi ,a cewar Hajj jamil idan suka fita masallacin waje mutane za su yi ta zuwa mu su jaje ,kuma yanzu ya fi buqatar daddy ya samu Hutu kamar yadda likita ya jaddada masa... Fitowar su ya yi daidai da isowar Barrister Kabir. A tare suka shiba masallaci bayan sun fito sun jima suna tattaunawa kafin suka k'araso Dan Barr Kabir ya yiwa hajiya jajen abunda ya faru... Hajiya na d'aki kan sallaye ,suxee ta shigo tace mata "Hajiya kizo anyi bak'o" shafa addu'a hajiya ta yi tare da cewa "To ga ni nan zuwa". Ta fad'a tare da miqe wa ta nufi parlourn. Barr dake zaune kan kujera mazaunin mutum d'aya ,yana ganin hajiya ta fito ,har k'asa ya zuqunna yana gaishe ta, tare da jajanta mata kan abun da ya faru. Barr Kabir ba tun yau ya san hajiya ba ,da kuma tarin alkhairan da hajiya ta yi masa a rayuwa, Dan karatun da ya je yayo game da shari'a a qasar waje Allah ne sanadi hajiya ce sanadi ,Dan ita ta biya masa komai da komai ba tare ma da daddy ya sa ni ba. Wannan na d'aya daga cikin abunda yasa ba zai taba iya mantawa da hajiya ba. Auren sa na farko ma hajiya ce ta nema masa ta kuma yi masa komai duk a sanadiyyar zaman shi abokin daddy na k'uruciya kuma an yi zaman mutunci da iyayen shi lokacin da suke raye. Wanda Allah ya yiwa matar tashi rasuwa wajen haihuwa ,bayan ta Haifa masa 'ya mace wacce taci sunan hajiyar daddy suna kiran ta da HAJIYEYE. Zaman lafiya da soyayyar da Barr Kabir yayi da marigayiyar matar shi yasa ya kasa k'ara aure sama da shekaru bakwai ,kullum jiya iya yau ,hajiya ta yi masa fad'a amma koda yaushe maganar Barr Kabir shine shi fa a ganin shi ba ze tab'a samun wacce zata maye masa gurbin matar sa ba. Daga k'arshe ma da hajiya ta matsa masa ,sai ya ce ta sake nemo masa ,in dai ita ce zata nemo masa ya yi mata alqawarin ze yi aure Dan ba yada shakku ko haufi akan zab'in hajiya. Tun daga wannan lokacin hajiya ta sarara masa ,Dan a cewar ta ita ma sai ta yi bincike mai tsawo akan wacce zata samo masa ,Dan qaunar da ke yiwa Barr Kabir yasa bata son duk wani abun da ze zo ya kawo wa rayuwar shi cikas. Ta na kuma son shi da qaruwa kamar yadda take son Daddy da abun da ta Haifa da abun alkhairi. Wannan kuma na cikin karamci irin na hajiya ,duk Wanda ze zauna tare da ita to fa lallai ne yasan kirkin ta. Bayan sun gama gaisawa ,nan suka shiga tattauna abun da ya faru ,da kuma yadda ya shirya case d'in ganin sun samo bakin zaren. Suna zaune Lubabatu tayo sallama kamar wata mutuniyar azziki hannun ta d'auke da tiren lemu. Har gaban hajiya taje ta aje mata ,ta juya zata fita Barr dake bin ta da ido ya dakatar da ita. Gaban lubabatu ne ya yanke ya fad'i ainun. Hannu Barr Kabir ya sa a aljihun gaban rigar shi ya d'auko wayar sa. D'an danne danne yayi a wayar ,wani folder ya shiga da ke d'auke da hotunan lubabatun. Sake duban ta yayi ya kuma mai da kan shi kan wayar ya duba dakyau ya ga lallai itace ba wa ta bace. Ita dai lubabatu sai kallon shi take yi ta na so ta gane inda tasan wannan fuskar amma ta kasa tunowa. Tashi Barr Kabir ya yi yazo har inda lubabatu ke tsaye ,ya dinga zagaye ta yana qare mata kallo Sama da qasa ,Wanda ya sa lubabatu tsarguwa. Kowa ya zuba wa sarautar Allah ido yaga me ke shirin faruwa. Barr Kabir yace "kin yi kama da wata matar marigayi Alh sambo". Dummm! Gaban lubabatu ya yanke ya fad'i ,tabbas tasan ko waye ya mata farin sani musamman da ya ambato mata sunan Alh sambo. Zufa ne ya shiga tsiyayo mata ,kan kace me jikin lubabatu ya fara karkarwa. Murmushi Barr Kabir yayi kafin yaci gaba da cewa "ko da yake duniya ta fa d'i ba lallai ya zama ke ba ,ina ga dai kamar Ku ce ta yi yawa. Girgiza kai lubabatu ta shiga yi cike da sarqewar murya tace " umm...ummm ba ni bace". Ta na gama fadin haka ta yi hanyar waje da gudu. Sai dai a rashin sa'a sai jin tayi taci karo da mutum. 'Yan sanda ne sai dai ba'a kayan aiki su ke ba. Saboda kar su ja hankalin mutane, wanda Barr Kabir ne ya tura mu su adireshin unguwan da layin. Cafke ta suka yi ta na ta kokarin ta k'wace ,tare da cewa "Ku sake ni in tafi ,ba ni na kashe shiba wallahi Ku sake ni" Barr Kabir yace "da ma wa ya ce kin kashe shi ai yana nan da rai ba mutuwa yayi ba. Hannu lubabatu ta Dora akai tare kurma ihu tana fadin " na shiga uku na lalace" Barr yace "ba ki shiga ba za dai ki shiga" yana gama fadin haka yace su tafi da ita. MUJE ZUWA💃🏻 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [8/17, 3:30 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA ARBA'IN DA D'AYA_ *_______________________________* Ba su kai ga fita da ita ba Sai ga Haajar ta shigo ,wacce sun shigowar su ta fice bata San wainar da ake toya wa ba. Hannun ta rik'e da wani buhu duk ya yi datti ,ba kuma Wanda yasan me ke ciki sai ita data shigo da shi. Tace wa 'yan sandan "Ku dakata tukunna". K'arasawa ciki ta yi , sai da ta k'arasa tsakar parlourn in da kowa ze iya hango ta ,sannan ta zuqunna tare da zaro abun da ke cikin wannan buhun. Da sauri daddy ya mik'e tsaye yana bin abun da haajar ta Ciro a buhun. " wannan ba akwatin takaddu na bane?" Daddy fad'a tare da nuna akwatin. Haajar tace "ka sake dubawa dakyau dai ka gani. Ta fad'a tare da mik'a masa akwatin. Karb'a ya yi tare da zama a lokaci d'aya ya bud'e akwatin ya shiga duba takaddun da ke ciki... Da ido daddy ya bi ta, cike da matsuwar son jin k'arin bayanin In da ta samo akwatin bayan a idon shi komai ya k'one na sashen shi. Haajar ta fara da cewa " daddy nasan za ka yi mamakin yadda aka yi na samu wannan akwatin? To ba abun mamaki bane ,ba kuma tantama wannan akwatin dukiyar ka ne Allah ya dawo maka da shi Wanda babu abunda ya samu matsala. Sai zan so Ku saurare ni Dan jin a inda na samo da kuma yadda aka yi na samu akwatin". Kowa natsuwa ya yi yana sauraron haajar. Wani ajiyan zuciya ta sauke kafin ta shiga ba su labari Tun daga lokacin da lubabatu ta turo musu 'yan fashi da makami akan azo aci zarafin su... Shirin ta akan sace akwatin dukiyar daddy da ta yi sannan ta k'ona d'akin saboda ta kauda hankalin kowa,,, da yadda ita haajar d'in ta wargaza wa lubabatu shiri ta hanyar canza akwatin da wasu takaddun na bugi,,, ta d'ora da cewa "Tun lokacin da marigayiya Haseena ta gaya mun cewa ba ta yadda da wannnan mutumin dake zuwa gidan nan a matsayin k'anin lubabatu ba ,na sanya ido akan su ,na ke kuma kula da shige da fitan su. Na dinga bibiyar ta ,har lokacin da suka shirya sace maka dukiya. A wannan Daren ta d'auki akwatin ta kai gidan gona ,ta yi rami mai zurfi ta saka a ciki ,ba tare da tunanin me ze ya dawo ba. Bayan tabar wurin na b'atar mata da hankali ta hanyar musaya akwatin da irin sa. A washe gari ta kunna wuta a d'akin sannan ta fito tana kururuwar a taimake ta. Wannan ta Ku da ta yi yasa tayi wasa da hankulan mu. Gobarar da ta sake tashi a b'angaren kubra ma duk ita ce ta haddsa shi. Saboda ta ji duk irin sab'anin da Khaltum da Kshri suka sa mu a lokacin da kubra ta je sashen khaltum suna maida wa juna magana..." Nan Haajar ta zayyana musu duk irin abun da ta ji na sab'anin da su kubra su ka sa mu ,Tun daga zuwan su Germany har dawowar su. Daga nan ta ci gaba da cewa "Bayan Khaltum ta ji komai ,daga wannan lokacin sai ta fara tunanin duk wata hanya da zata bi Dan d'aukar fansa akan kubra. A nan lubabatu ta yi amfani da damar ta ,ta zuba wa khaltum magani a abun sha ta kai mata ,sannan ta zayyana mata duk yadda zata yi Dan d'aukar fansa. Idon khaltum ya rufe a wannan lokacin saboda haka sai ta yi tunanin ko lubabatu na so ta taimaka mata ne ,ba tare da ta yi shawara da kowa ba ta je ta aiwatar da duk yadda lubabatu ta tsara. Dalilin faruwar gobar na biyu kenan, Wanda yaci rayuka ,amma khaltum ba ta mutu ba a yanzu haka tana babban asibiti ana kula da ita. A ranar da gobar zata shi, ba nida lafiya daddy yace in shirya ya kai ni asibiti. Allah ya jiqan haseena ita ta fara shiga band'aki ta ga ruwan famfun baya zuwa ,da ta gayamun sai na fito na zagaya ta baya da niyyar in duba. Bayan na duba ruwan zan koma ciki. A ta wajen ajiye motoci naga wannan mutumin da lubabatu ke kira da qanin ta ,ya karb'a k'yallen da baba lawan ke goge mota sannan ya aike shi ,bayan baba lawan ya tafi aiken da a yi masa. Se da ya waiga ya ga ba Wanda ke ganin sa ,ya zuqunna ya sacce d'an bakin wannan motar da baba lawan ke gogewa da alama yasan da ita za'a fita, ya na gama wa ya yi wa lubabatu waya ta fito ,duk ina tsaye da baya ba tare da sun ganni ba, bansan dai me suka tattauna ba amma na ga ta bashi wani envelop da alama kud'i ne a ciki ,daga nan kowannen su ya kama gaban shi. Ita ta koma ciki shi kuma yayi tafiyar shi. Yana fita na yiwa 'yan sanda waya tare da yi musu kwatancen shi suka kama shi da kuma abunda take k'ok'arin aikatawa suka ka ma shi. Da mu ka fito za mu fita ,na cewa daddy kar mu shiga wannan motar mu shiga d'ayan. Ya yi mamaki ,ya tambaye ni ko lafiya ,nace masa lafiya qalau kawai dai sanyin A/c nne ba na so. Duk da ba wata hujja na ba da ba daddy ya biye min a tunanin shi ko duk zafin zazzab'in ne. A wannan ranar shirin lubabatu na k'arshe shi ne ta salwantar da rayukan mu gaba d'aya. A d'ayan b'angaren kuma ga gobarar da za ta tashi za'a yi marus ,a wayi gari ba kowa a gidan sai ita. Daga nan ta shirya 'yar k'aramar wasa na akan idan komai ya wakana kamar yadda ta tsara ,za ta yi haukar k'arya Wanda mutane za su yi tunanin ko duk iftila'in da ya faru ne ya tab'a mata k'wak'wal. Da ga nan bayan ta warke komai na daddy zai zama na mallakin ta."... Kowa da ke wajen kusan daskarewa ya yi Dan jin wannan al-ajabi. "Abu sai kace shirin film cewar Hajiya... Ta ku Haajar ta yi har inda lubabatu ke tsaye rik'e a hannun matakan tsaro tace "Wannan wasar ya k'are daga yau. Cin mutuncin da kike ganin kin mun kuma dama a wurin ki yake haka. A zahiri kuma ni matar daddy kamar yadda kike matar shi ,a yanzu haka kuma ina d'auke da cikin shi sanadiyyar abun da ya faru. Ke kuwa kina ji kina gani za'a fitar da ke daga cikin gidan nan, ba ma cikin gidan daddy kadai ba hatta rayuwar shi kin fita kenan fitar da babu dawowa har abada da yaddar Allah..." Mai da duban ta tayi gun Barr tace "za Ku iya tafi da ita. Idan wancan case din ba bamu da masaniya akai tuhuma ce to ga Wanda kuke da tabbaci akai". Ihu lubabatu ta shiga kurmawa ba qaqqautawa ,tana fadin " Wallahi sharri take mun ban aikata ba ,wannan kawai an hada ne Dan a rabani da mijina saboda anga yana so na. Barr dake tsaye yace "wancan ma ba tuhuma bane ,saboda yanzu mun kai shekara goma muna cigiyar ta Allah be sa mun gan ta ba sai yau. Muna kuma da izinin kamata mu danqa ta hannun hukuma duk lokacin da muka yi ido hudu da ita. Zamu tafi ita, idan komai ya daidaita zan dawo Ku ji komai". Barr yace wa matakan tsaro Ku tafi da ita. Ihu lubabatu ke yi tana fadin " Ku taimake in. Na shiga uku tun ban mutu ba ga matambaya sun iso min. Alhaji kana gani za'a tafi dani ka yi musu magana kar ka bari su tafi dani". Jin zata Tara musu jama'a yasa su ka rufe mata baki da wani k'yalle tare da ficewa da ita... Suxee da hajiya sai kuka su ke yi. Suxee na kukan rashin 'yar uwar ta haseena da baqin cikin irin mutuwar da tayi. A b'angare daya kuma tana takaicin irin turbar da mahaifiyar su ta mutu a kai. Gaba daya tausayin kan su ya kama ta a lokaci daya taji son Haajar ya qara shigar ta. Hajiya ita ma kukan rashin jikar ta take ,da tausayin d'an ta irin jarabtar da Allah ya yi masa na mata ,ace mata uku babu ta Allah a cikin su. Da badan Allah ya kawo musu Haajar a rayuwar su ba da yanzu labari ya sauya. Duk da wannan shi ne karo na farko da hajiya ta ga Haajar ba k'aramin kwanta mata ta yi ba ,musamman yanzu da ta ji irin tarin alkhairan da ta yi a d'an zaman ta a gidan yasa ta ji ta a ran ta fiye da yadda ya ji son ta a farko. Hajj Jamil dake gefe mamakin duniya ya hana shi magana. Duk wani abunda Haajar ke yi tana sanar mishi amma Sam ba yada masaniya akan abubuwan da ta zayyana a yanzu. "wato Haajar ta wuce duk yadda nake tunani?"" Ya fad'a a k'asan ran shi ,a fili kuma ajiyan zuciya ya sauke tare da cewa "Godia ya kama ta mu yi wa Allah ,ga me faruwar wa'yannan abubuwa. Abunda ya faru ya riga ya faru ba ma fatar makamancin wannan ya sake faruwa ,sai dai mu ce Allah ya tsare gaba ya kuma k'ara tsare mana imanin mu... Zuwa yanzu komai ya faru ya wuce ,mun ji komai. Abu daya da ya rage shine misbahu in gabatar maka da Haajar a matsayin matar ka. Tun lokacin da ka kwanta a asibiti ,na fad'a mata komai a kan ka saboda yadda naga ta damu dakai, ta kuma amince akan tana son ka zata aure ka. Daga wannan lokacin naje na nema maka auren ta a wajen mahaifin ta yaya na Dr. Sheikh Imam Ali asadussunnah, ya kuma amince da duk baya nan dana Je masa da shi. Ban baro jigawa ba sai da aka d'aura auren ka da ita. Tun lokacin Haajar ta dawo gidan nan da zama ,ta zo ne a matsayin matar ka. Kuma ita ta buqaci da a b'oye maka har zuwa wani lokaci saboda a samu daidaito, saboda kuma ka nemi soyayyar ta da kan ka ,ba Dan wani ko wata ya had'a Ku ba. Kamar yadda ka ji ta fad'a a yanzu cewa tana da juna biyu ,haka zancen yake. Duk abunda ya faru bana qasa a guiwa wajen sanar da hajiya. Tasan komai akan auren ka da Haajar, Dan har ma na tab'a had'a su a waya suka gaisa. Ko ba haka ba hajiya?" Hajiya ta amsa da "wannan haka yake" Daddy da tsoron Allah ya taru ya tsaya masa a zuci ,mamaki ,tsoro da alajabi ne ya hana shi furta ko da kalma daya. Jinjina kai ya shiga yi a hankali ya furta "Ikon Allah"... Ba tare da ya sake cewa komai ba ,Dan shi gaba d'aya ganin abubuwan da suka faru yake kamar a mafarki. Ba tare da ya sake furta kalma d'aya ba hajj jamil ya rufe taron da addu'a. Hajiya ma addu'a tayi musu sosai na samun zaman lafiya mai d'aure wa a rayuwar auren su. A gefe d'aya kuma ta yi Haajar godia bi sa namijin k'ok'arin da tayi ,a cewar hajiya ba mace ko namiji yayi irin wannan k'ok'arin yaci a jinjina mishi. Suxee in banda kuka ba abunda take yi. Hajiya da Haajar sai aikin lallashin ta suke yi. Sai da Hajj jamil ya saka baki kafin ta sassauta kukan da take yi... Da daddare Hajj jamil ya yo musu take away gaba d'ayan su.A ranar Hajiya tare suka kwana ,ita Haajar, auta da kuma suxee. Bayan sati d'aya... MUJE ZUWA💃🏻 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [8/18, 9:58 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA ARBA'IN DA BIYU_ *____________________________* Bayan sati d'aya... Komai ya fara daidai ta. _GIDAN MISBAHU_ ya fara farfad'o wa daga dogon hutun da ya je na farin ciki da kwanciyar hankali. Sosai Haajar ta samu karb'uwa a wajen daddy, ta kuma ba shi had'in kai wajen gudanar da rayuwa mai inganci. Hajiyar daddy ta so ta koma ,amma Haajar ta yi ta lallashin ta akan ta hak'ura ta zauna tare da su a garin sakkwato. Ba Dan Hajiya ta so ba amma Dan dole ta hak'ura ta zauna ,saboda kwarjini da kuma k'imar Haajar da take gani ,a cewar ta kuma babu abunda Haajar zata ne ma a wajen ta ta gaza yi mata shi matuqar abun nan bai fi k'arfin ta ba. Sashen bak'i aka gyara wa Hajiya. Ita kuma Haajar aka gyara mata sashen da ke gefen sashen da hajiya ke ciki. Sosai Haajar ke kula da duk wani buqatun hajiya da ma na gidan gaba d'aya. Ko da yaushe indai daddy ya fita to dikkan su suna tare da hajiya ana hirarrakin barkwanci ,wannan yasa Haajar ta k'ara samun karb'uwa a wajen hajiya ,take kuma yi mata gata irin na uwa da 'ya ,musamman da ta samu labarin cewa mahaifiyar Haajar d'in ta rasu. Hasalima ba ta wani San dad'in uwa ba ,tun tana k'arama Allah ya yiwa mahaifiyar ta ta rasuwa. Sashen kubra da Khaltum kuwa rushe su daddy yasa akayi Dan baya son yana gani ko tuno duk wani abunda ya dangance su. A gefe d'aya kuma yana matuqar kewar kubra. Dan duk wani abunda take yi masa ,sanyin halin shi da hak'urin shi bai sa ya manta da zamantakewar su ba ,duk da ko bai tab'a jin dad'in zama da ita ba koda na sakan d'aya. Amma duk lokacin daya kalli Suxee da Auta ,fuskar kubra yake gani k'arara a tare da su. Wannan yasa ya ka sa mantawa da ita gaba d'aya, amma Dan ta khaltum da lubabatu da ma ba zab'in ran shi bane ,Dan haka baya wani tuna cewa zamantakewa ta aure ta tab'a had'a su. A b'angaren lubabatu kuwa ,tun lokacin da ta shiga hannun hukuma take cin bak'ar wuya. Dan safe ,rana, dare azabtar da ita suke yi har lokacin da ta amsa lefin ta. Saboda an same ta dumu-dumu da laifin kashe mijin ta Alh sambo. Alh sambo shine mijin lubabatu na farko. Mutum ne hamshak'i mai azziki, Wanda ya tara 'ya'ya tsakanin maza da mata har su goma sha tara. Bayan mahaifiyar su ta rasu ya auri lubabatu. A wannan lokacin ita kuma lubabatu bata son shi ,Dan haka Bayan an yi auren ta koma juya shi ta yadda ran ta ke so, shi kuwa ya dinga biye mata a duk yadda tace to hakan za'ayi ,saboda son da yake mata. Wata rana ta sa Allh sambo ya tattara 'ya'yan nan nashi su goma sha Tara ya kai su kotu akan ai masa farar takadda da su ,babu shi babu su shi ba uban su bane. Wannan al-amari ba kad'an ba ya d'aga wa mutane hankali ,Dan duk Wanda ya ji ma cewa yake ba'a hayyacin shi yake ba. Inda Allah ma ya taimaki 'ya'yan ba yara bane. Daga chairman na lokal gobmen se 'yan kasuwa da sauran su. Autar cikin su itace sa'ar lubabatun wannan ze tabbatar wa mai karatu Alh sambo dattijo ne mai tarin 'ya'ya da jikoki. Bayan wannan al-amari ya faru kwatam wata rana aka wayi gari lubabatu ta kashe zuba wa Alh sambo guba a fura ya sha ya mutu, ta kuma tattara dukiyar shi gaba d'aya ta gudu, bata tsaya ko ina ba sai k'asar Ghana... Wannan Abu shi ne sanadiyyar daya haddasawa mahaifin lubabatu ciwon sashe ,Wanda har sai da ya zama ajalin shi. Mahaifiyar ta kuwa bak'in ciki ya sa ta tattara kayan ta tabar k'asar. Duk irin abubuwan da suka yi ta faruwa lubabatu ba ta sake waiwayo gida ba sama da shekaru goma. A can k'asar Ghana ta sake yin wani aure ,inda ta auri wani bawan Allah mai suna malam Alasan. Ko da aure shi yana da matar shi d'aya mai suna Wasila da 'ya'yan su bakwai. Wata rana 'yar hatsaniya ta had'u da malam Alasan. Lubabatu ta faki dare dama ranar girkin ta ne ,ta kwankwantse masa Al'aura, ta haura ta bar k'asar. Daga nan ta dad'e ba ta sake waiwayo gidan Nigeria ba ,sai bayan wani lokaci ta dawo kano da zama. Inda take zaune tare da wasu dattijawa ,bayan k'aryar da ta shata musu na cewa ta yi hatsari ne ta manta komai na rayuwar ta. Tun da suka ji haka suka rik'i lubabatu tamkar 'yar da suka Haifa ,da ma ba suba haihuwa ba. Daga wannan lokacin lubabatu ta zama tamkar 'ya a wurin wa'yannan bawan Allah. Inda anan ne Hajiya Gwaggo ta gan ta taji kuma ta kwanta mata ,har ta yi sha'awar ta had'a auren su Daddy. Lokacin da Hajiya khairi mahaifiyar Khaltum ta ji abun da ya faru da 'yar ta tilo, ba kad'an ba ta yi kukan bak'in ciki da nadamar irin turbar da ta d'ora 'yar ta ta akai ba ,mugun hali irin na ta ya sa mahaifin Khaltum ya ji ba zai iya ci gaba da zama da ita ba tun a wancan lokacin ya rabu da ita. Ya so ya karb'i Khaltum amma hajiya khairi ta hana shi saboda ita kad'ai ce 'yar shi a duniya k'arshe ma daya matsa kotu ta doka shi inda ta zuba kud'i aka mata farar takadda da mahaifin Khaltum akan babu shi babu Khaltum sakamakon sharrin da Hajiya khairi ta yi masa akan yana Neman ran su ne ita da 'yar ta. Tun daga wannan lokacin bai sake Neman su ba ,ya dad'e yana jinya sakamakon abun da ya faru da kuma irin son da yake wa Hajiya khairi da 'yar shi Khaltum. Sai da dangin shi suka yi da gaske kafin ya samu abun ya fita a ran shi ,daga baya ya sake aure ,ya kuma ta ra zuri'a da wannan matar da ya sake aure. Ko so d'aya kuma Hajiya khairi bata tab'a tunanin tura Khaltum wajen mahaifin ta ba. Yanzu da wannan al-amarin ya faru Hajiya khairi ta yi nadama iya nadama ,in da ta d'ora wa kan ta laifin duk wani abun da ya faru da Khaltum a rayuwa. Lokacin da labarin wannan abun ya isa wajen dangin mahaifin Khaltum iya Allah wadai sun yi da halayen Hajiya khairi ,a gefe d'aya kuma suna tausayin Khaltum dan duk wani abunda take yi mahaifiyar ta ce ke sanya ta. A yanzu haka ita ke zaune da Khaltum a babban asibiti Wanda iya wuya ne ace Khaltum zata sake wata rayuwar a wannan duniyar. Sakamakon k'onewar da tayi ,abun har ya tab'a k'wak'walwar ta dan kusan bata iya gane waye a kan ta. Sai dai da yake rayuwar a hannun ubangiji ta ke takan yu Allah ya yi ikon shi akan ta. Ranar da daddare Haajar da daddy suna zaune a sashen shi. Take masa magana akan ya kamata su je su gano Khaltum. Wannan batu yayi matuqar b'ata ran daddy. Ya nuna akan ba inda za su. Washe gari Haajar ta samu Hajiya ta ke fad'a mata akan ta yi wa daddy magana kan ya kamata su je su gano jikin Khaltum. Ta nuna wa hajiya akan har yanzu khaltum matar daddy ce tun da bai sake ta ba, saboda haka bai kamata ya manta da haqqin ta dake rataye a wuyan shi ba. Ba ta kuma so allah ya kama shi da wannan laigin. Jin haka yasa Hajiya ta k'ara yabawa Haajar tare da qara tabbatar da Lallai yanzu daddy ya yi aure. Hajiya ta yi wa daddy fad'a akan batun ta kuma nuna masa hakkin Khaltum dake kan shi ,sarai daddy yasan wannan aikin Haajar ne ,badan ya so ba haka ya hak'ura akan su je d'in. Washe gari gaba d'ayan su suka shirya dan zuwa dubo Khaltum. Wanda a ranar mahaifin khaltum shi da iyalan shi suma suka zo duba khaltum d'in. Dak'yar aka bari su daddy suka shiga inda Khaltum take. Mahaifiyar ta na kan dadduma tana Neman gafarar Allah kan abubuwan da ta aikata. Lokacin da hajiya khairi ta gan su ba kad'an ba ta ji kunyar had'a ido da su. Musamman hajiya da ta yadda da ita fiye da tunanin mai karatu ,Wanda yaddar da ta yi mata ne yasa har ta yi sha'awar su had'a jini. Shine lokacin da Hajiya ta had'a auren daddy da Khaltum d'in. Duk Wanda yaga Khaltum a wannan halin da ta take ciki a yanzu sai ya tausaya mata matuqa. Ga ta a kwance da ita da gawa ba su da banbanci ,ba um ba u'um. Hajiya khairi na kuka ta shiga Neman yafiyar hajiya akan abubuwan da suka faru. Duk da hajiya na takaicin sanin hajiya khairi da ta yi. Be hana ta yafe mata ba. K'anwar mahaifin Khaltum da aka zo tare da ita ne ta dinga maidawa Hajiya khairi da martanin abubuwan da suka faru. Hajiyar daddy ta yi ta mata fad'a akan ya kamata su yadda da qaddara komai ya wuce. Mahaifin Khaltum har hawaye sai da ya zubar lokacin da ya halin da 'yar shi ke ciki. Da Hajiya khairi ta nema yafiyar sa ko kad'an bai yi qasa a guiwa ba wajen yafe ta ba saboda 'yar shi. Dikkan su suna zaune kowa sai sannu yake wa Khaltum da bata San suna yi ba. A hankali Khaltum ta bud'e idon ta ta zuba su kan k'ofar shigowa. Hannu take k'ok'arin d'agawa tana nuna k'ofar ,amma ba su ga kowa ba. Jini ne ya shiga fito ma ta hanci da baki, a gefe d'aya kuma tana ci gaba da nuna k'ofa. Da sauri Haajar ta je ta kira likitocin da ke kula da ita. Amma kafin su k'araso rai yayi halin shi. Dan kuwa Allah ya yiwa Khaltum rasuwa. Hajiya khairi ta yi kuka kamar ba gobe. Kowa sai da ya tausaya mata. A ranar da jimamin abun su hajiya su ka koma gida. Washe gari aka wuce aka wuce da gawar Khaltum Dan ayi mata sutura akai ta gidan ta na gaskiya, Wanda tare da mahaifin Khaltum d'in aka wuce... MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [8/20, 12:19 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA ARBA'IN DA UKU_ *___________________________* Washe gari da yamma su Haajar na zaune a sashen Hajiya su na ta qara ji manta al-amarin da ya faru jiya a asibiti, sai ga wani al-amarin ya sake zuwa. Dan kuwa Barr Kabir ne ya zo musu da labarin cewa an yanke wa Lubabatu kisa ta hanyar rataya ,sakamakon kisan kai da ta yi har so biyu ta kuma yi yunqurin sake aikwatar da wani a karo na uku ,wannan ne yasa babu wani hukunci da alqalin ya ga yafi cancanta da Lubabatu bisa ga doka sama da rataye ta ,a hakan mai wai an yi mata da sauqi ne. Wannan labari shi ma ba kad'an ba ya sake d'aga hankalin su hajiya ,Haajar hadda zubar da 'yar k'walla saboda tausayi. Barr tambayar Hajiya ya yi akan ina Daddy? Hajiya tace "ai tun lokacin da komai ya warware Daddy ba ya zama Dan yanzu ma harkokin kasuwancin sai dad'a bud'e masa suke yi". Abu mai San yi Haajar ta kawo wa Barr tace wa hajiya " ni zan je in kwanta kai na ne ke d'an mun ciwo ". Hajiya tace " to Allah yasa kaffara ne. Ki tabbatar kin sha magani kafin ki kwantan. Tukunna ma kin ci abinci?" D'an sosa k'eya Haajar ta yi tare da cewa "Na sha shayi d'azu hajiya" hajiya tace "to ai ka ji shashanci. Wai shayi? Naga shayi ai ruwa ne ba abinci ba. Mutum yasan ba shi kad'ai ba amma sai sakaci. To maza kije ki nema abinci ki ci kafin ki fara aikin baccin". Murmushi Haajar ta yi tace " To insha Allahu zan ci hajiya". Hajiya tace "to ai shikenan. Sai kin fito" daga haka Haajar ta yi sallama da Barr ta wuce sashen ta. Kusan duk lokacin da Haajar za ta ji abunda ya d'aga mata hankali sai kan ta ya yi ciwo Wanda idan ba bacci ta samu ba bata samun sauqi, ita kuma da haka laulayin yazo mata. Barr kafe Suxee da ido ya yi, da ke kwance tana aikin daddanna waya. Hajiya tace "tashi Hajiya k'arama ki canza mana tasha zuwa sunnah tv saboda k'aratowar magriba." Ta shi suxee ta yi ta canza tasha kamar yadda Hajiya tace sannan ta dawo ta kwanta. Barr yace "Hajiya na ji kince Hajiya k'arama? Ba dai ita bata wannan ta girma haka?" Murmushi Hajiya ta yi irin na su na manya tace "Yo kai da kabiru da wautar ka da wacece?" Yace "wallahi Hajiya ban d'auka ita bace ,saboda nasan ai ke d'in ta mutane ce ba'a raba ki da jama'a. Na ga ta girma ne sosai". Hajiya tace " Lallai kuwa ga ta nan dai. An gama makaranta tuni ,banda Hajiya Gwaggo ma ta hana da yanzu ta yi nisa a karatun jami'a. Ina ga ko dan ba'a k'asar ka ke zaune bane tun wancan lokacin shiyasa ,kuma kaga ba Ku tab'a had'u wa a kano waje na ba. Lokacin da zasu zo sai sun tafi da jimawa kai kuma sai ka zo." Da mamaki Barr yace "wannan haka yake. Amma kuwa na ji kunya ,mutum da jinin shi ace ya kasa gane shi". Iya Murmushi kawai Hajiya ta yi. Barr yace " To ai ita d'in ne ma naga bata fiye magana ba". Hajiya tace "Ai haka ta ke Hajiya k'arama ba ta wani fiye magana ba musamman ma idan ba ta San mutum ba. Da dai marigayiya Haseena ce idan ka zo sai ka gaji da surutu" Barr yace "Allah sarki. Allah ya gafarta mata yasa ta huta. Hajiya ta amsa da " ameen". Daga haka tace "bari in shiga daga ciki kafin lokacin sallah ya k'arato." Har k'asa Barr ya zuqunna yace "a fito lafiya hajiya". Hajiya ta shige ,shi kuma ya koma ya zauna. Sun dad'e a zaune tsakanin shi da Suxee ba Wanda yace wa kowa komai ,ganin haka yasa ya kauda shirun da d'an d'auko wa Suxee hira. Sama sama dai suka d'an dinga hira anan har yake gaya mata yadda alaqar shi ta ke da Hajiya. Sai a lokacin ne ma suxee ta d'an sakar masa fuska. Ranar anan Barr ya ci abincin dare ,ya ta jiran daddy ya dawo su gaisa amma bai dawo da wuri ba ,ganin dare na yi yasa ya yi musu sallama ya tafi. Wani daren asabar Haajar na zaune tare da daddy suna hira. Ya na bata labarin irin ci gaban da ya samu a harkar kasuwancin shi cikin d'an k'ank'anin lokaci, Wanda duk ya ta'allaqa samun nasarorin akan Haajar. Haajar ta nuna jin dad'in ta ma matuqa game da yabon da ta samu a wajen daddy tare da yi masa fatar samun nasorin da ya fi wannan. Wani abunda mai karatu bai sani ba shine. Tun bayan lokacin da wancan al-amarin ya faru ,daddy bai sake kusantar Haajar ba, ba kuma Wani abun bane daban ,tsabar nauyin Haajar d'in yake ji ,ya ke kuma ganin idan ya nema ta kamar bai kyauta ba sakamakon abunda ya faru tsakani shi da ita a baya. Dukda kuwa yaji cewar a wancan lokacin duk Haajar d'in na a matsayin matar shi, amma ya kasa yafe wa kan shi. Tun Haajar na tunanin ko akwai wata matsalar ce a k'asa Wanda bata San da shi ba da yasa daddy ya k'i Neman ta a shimfid'a, har ta gano ba komai kawai nauyin ta daddy ke ji ba kuma Dan baya sha'awar ta ba ,kawai yana kai zuciyar shi nisa ne. Ganin haka yasa Haajar ta shirya tsaf Dan k'arawa kan ta daraja da k'ima a idon mijin ta. Washe gari da daddare bayan ta yi sallama da su Hajiya ta dawo sashen ta. Ta sake yin wani sabon girkin da ta San mijin ta ya fi son shi sama da kowani abinci. Bayan ta gama ta ci ado matakin k'arshe ,sannan ta zauna tana jiran dawowar farin cikin ta. Sai wuraren goma na dare daddy ya shigo gida. Sashen hajiya ya fara zuwa ya taradda sun yi bacci, bai yi k'ok'arin ta shin su ba. Ya wuce zuwa sashen Haajar. Tun farkon shigar shi ya ga wasu sababbin sauyi. Da wani irin k'amshi mai matuqar sanyaya ruhi ya fara cin karo. Haajar ce ta fito cikin wasu k'ananan kaya Riga da wando masu matuqar d'aukar hankalin mai kallon ta. Wannan ya k'ara tabbatar wa daddy da cewa yau d'in na musamman ne. Wani salo na mai tafiyar da nutsuwa ta dinga yi masa. Ruwan wanka ta fara had'a nasa ,ta taimaka masa ya cire kayan sa. Daddy shi dai sai bin ta da ido ya ke yi yana kallon ikon Allah, Haajar d'in ce duk ta canza masa yau d'in kamar ba ita ba. Wani abun mamakin ma bai wuce ta yaga alamar cewa tare take son suyi wankan ba. Dan bai tab'a ganin tsaraicin ta ba. Kullo band'akin tare da zare kayan da ke jikin ta d'aya bayan d'aya. Zaro ido daddy ya shiga yi yana mazurai kamar yau ne rana ta farko daya fara ganin tsaraicin mace. Kusan sumar tsaye ya yi lokacin da ya yi tozali da kyaky-kyawar surar jikin Haajar mai matuqar rikitarwa. Salo ta dinga yi masa ko a wajen wankan ,da k'yar daddy ya iya k'arfin halin had'i yawun sa. Bayan sun fito ba shi wuri ta yi ya kimtsa ita kuma ta koma d'ayan d'akin ta shiryo cikin wasu kayan bacci masu masifar kyau ,Wanda kusan da su da babu ba suda banbanci. Abinci ta fara gaba to wa daddy. Da kanta ta dinga ba shi a baki ,daddy kuwa dak'yar abincin ke wuce masa a mak'oshi Dan kusan ma ko gard'in abincin baya ji saboda abun da yake gaban sa ya kauda duk wani d'and'ano dake bakin sa. Bai wani ci sosai ba sakamakon ya k'agu. Haajar kuwa da ta ga yana bakin hanya ,sai ruwan shagwab'a take zuba masa tana wani narke masa a jiki. Wannan yanayi da daddy ke ciki a yau sai yake jin kamar kar ya wuce. Iya soyayya, salo da k'arshen kissa da kisisi na irin na mu na manta wajen Jan hankalin namiji sai da Haajar ta baje shi a wannan Daren. Daga nan ta ja su sai d'akin baccin su da ta k'awata da nau'in furai launin jajaye, ga wasu k'yandura a aka kunna suna fidda d'oruwar wuta. K'awa irin na masoya. Tsarin ya yi matuqar burge Daddy Wanda har sai da ya furta "ya yi kyau". A wannan Daren saida Haajar ta tabbatar wa da daddy ita d'in ta musamman ce kamar yadda komai na ta yake na daban ko a cikin mata. Dan kusan ma sai ya ji ya fi jin ta gam fiye da wancan lokacin da ya yi mata shigar gangancin. Duk wani gudunmawa Haajar ta ba shi a wannan Daren Dan su mori rayuwar su yadda ya kamata. Ba kad'an ba daddy ya murji Haajar son ran shi ba gajiya balle k'orafi. Kusan wannan dare na daga cikin dare mafi soyuwa ga wa'yannan masoya. Albarka sai kalan Wanda daddy ya manta ne bai saka wa Haajar ba a wannan Daren. Tun dare suke Abu d'aya, har wuraren asuba ,sannan su ka hak'ura ba Dan sun gaji da shak'ar d'umin junan su ba. Washe gari tun bayan da su daddy su ka yi sallar asuba ,suka koma bacci ,ba su suka farka ba sai sha biyu na rana. Hajiya da suxee tun suna jiran fitowar su har suka cire rai. Su kan su masoyan irin baccin da su kayi ya d'aure musu kai. Sai yanzu daddy ya k'ara tabbatar da abunda Hajj Jamil yake gaya masa na cewa matuqar yana tare da abunda ya ke so ,ya kuma samu yadda yake so, to ba shakka zai iya mantawa da komai". Wanka suka yi suka shirya cikin wata had'ad'd'iyar shadda mai tsada da taji aikin wuta. A tare suka nufa shashen Hajiya. Haajar sai sunne kai k'asa take yi ,Dan gani take Hajiya zata gano abunda ya faru tsakanin su. Ba ta san tun lokacin da hajiya ta ga yanayin shigar su ba ,da kuma irin farin cikin da Daddy ke ciki a yau ,ya tabbatar mata da komai. Iya murmushin ta kawai ta yi irin na su na manya tare da saka musu albarka. MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA....✍️ [8/22, 10:23 AM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA ARBA'IN DA HUD'U_ *____________________________* Tun daga wannan lokacin Barr babu ranar da baya zuwa gidan daddy ba Dan kowa ba sai saboda Suxee. Dan shi har ga Allah yanayin nutsuwar ta da hankalin ta yasa ta yi matuqar kwanta masa a rai. Ya na ta Neman hanyar da ze yi ya sanar da Hajiya Dan yasan ina ce zata tsaya masa har abun nan ya yiwu. Bai San Hajiya mace bace mai matuqar karantar yanayin mutum ,ko ince ya Sani mantawa ya yi. Tun yana b'oye-b'oyen har ya fito garan da garan ya gayawa Suxee abunda ke ran shi. Bata nuna masa komai ba Dan haka ya lashi takobin Neman soyayyar ta ta duk yadda zai iya. A b'angare d'aya kuma ga Hajj Jamil da tun ba yau ba yake masifar qaunar Suxee, Wanda kusan za mu iya cewa tun tana k'arama yake d'awainiya da son ta ,har kawo yanzu da ta girma, Wanda daddy ba yada masaniyar hakan. In da matsalar ta ke kuma ko so d'aya bai tab'a furtawa suxeen cewa yana qaunar ta ba. Ba Dan komai ba Sai Dan Hajj Jamil mutum ne mai matuqar zurfin ciki da kawaici. Yana ganin kamar bai kyauta ba idan har ya ce zai auri 'yar daddy. Badan komai ba saidan daddy babban aminin shi ne na har abada Wanda ba ya da tamkar shi ,sannan kuma yana tare da daddy ne tun kafin ya auri Mahaifiyar Suxee wato kubra. Da wannan yake ganin ya zama wajibi ya lallashi zuciyar shi Dan ba ya so ya aikata wannan abun kunyar. Idan da kara ai Suxee 'yar shi ce, ko daddy baya raye shi zai zama uban ta, a gefe d'aya kuma idan ya tuna halaccin abun a addinance sai ya ji baze iya hak'ura ba ko nan da can. Ga shi a yanzu qaunar ta dad'a mamaye ko wani lungu da saqo na kafatanin jikin shi ta ke dad'a yi. Wasu lokuttan idan ya zauna sai ya ga zuciyar shi bata yi masa adalci ba ,ta rasa wacce za ta so sai 'yar shi , 'yar babban aminin shi. Duk da cewa ko a shekaru daddy ya girme masa nisa ba kusa ba. Sai dai ita soyayya ba ruwan ta da wannan. Halittar Allah ce da ke ratsa duk Wanda ta so a kuma lokacin da ta ga dama. Takan iya wa mutum mummunan kamu musamman idan Wanda ta yi wa wannan illar ya yi mata gurguwar fahimta. Son da hajj Jamil ke yiwa Suxee har ya kai ya kawo idan ya ganta baya iya samun sukuni ,zuciyar shi ta dinga bugawa kenan ,ji yake kamar ya ta shi yaje ya rungumo ta ,amma ba dama. Baya tab'a samun sukuni har sai ya d'aga daga inda take. Wannan dalilin ne ma yasa shi ya rage zuwa gidan daddy Dan dole ba Dan ya so ba, ga Hajiya ko da yaushe tambayar sa take akan mai yasa ya rage zuwa kamar da ,a tunanin ta gidan daddy ai kamar na shi ne ,ga shi shi Matar shi ba mazauniya bace, wannan yasa Hajiya ke yawan yi masa fad'a akan ya dena zama shi kad'ai saboda kad'aici ,ka da wani ciwon yaje ya kama shi. Amma kuma duk randa abun ya tsikaro shi na son ganin Suxee ya zame masa wajibi sai ya je gidan ,ko da baze mata magana ba. Yau ma hakanne ya faru. Bayan ya dawo daga harkokin sa na kasuwanci kai tsaye gidan daddy ya nufa, tun bayan la'asar har kusan bayan isha yana tare da Hajiya su na ta hira. Rashin wurgawar Suxee ya sa duk ya shiga damuwa, sai waige-waige ya ke yaga ko zai gan ta ,amma shiru babu alamar ta. Har Hajiya ta d'ago shi tace masa ko wani abun yake nema? Amma sai yace a'ah. Yayin da ita kuma Suxee ta ke sashen Haajar tana bata labarin Barr Kabir da yadda yake matuqar qaunar ta. Wato wani abunda Haajar ta fahimta game da Suxee shine; Suxee na matuqar son mai nuna mata kulawa. Wannan ne yasa Barr bai sha wahala sosai wurin Neman soyayyar ta ba. Duk da cewar ita din tana da miskilanci amma hakan ba ya hana ta nuna jin d'ad'in ta a fili ga duk Wanda ya b'ata lokacin shi akan ta musamman ta fannin soyayya. Bayan ta gama zayyanawa Haajar komai ,Haajar ta fahimci cewa lallai fa Suxee ta fa d'a tarkon so kuma mai tsanani. Tace mata "Ni shawarar da zan baki shine ,ki yi a hankali Dan na fahimci ke baquwa ce ta wannan fannin. Ya na da kyau ki iya bambamce tsakanin SO da kuma QAUNA ,wannan ne zai taimaka miki wajen gane waya kamata ki so da kuma mai son ki na gaskiya." Nan Haajar ta ci gaba da ankarar da ita tare da yi mata 'yan nasihohi kan yadda zata kula da kan ta. Su na cikin hirar ne sai ga Barr ya kira ta a waya ya ce mata ya xo ya na sashen Hajiya. Tace "to ga ninan zuwa" tana gama fad'ar haka ta yanke kiran. Murmushi Haajar tayi tare da tambayar ta "shine? Suxee na murmushi Tace "Eh Shi ne". Ita ma Haajar murmushin ta yi tare da cewa " to motar soyayya! Jira ni in d'auko hijabi na a rage mun hanya". Dariya maganar Haajar din ya ba ma Suxee tace "Kai Anty Haajar. Ni d'in ce kuma motar soyayya?" Haajar tace "ai kin ma wuce mota ,sai da tashar motar". Dikkan su dariya suke yi ,da haka suka k'araso zuwa sashen Hajiya... Da sallama d'auke a bakunan su suka shiga parlour-n. Mutanen dake ciki suka amsa musu da "Wa'alaikumusallamu". Tun daga nisa Barr ke sakar wa Suxee murmushin qauna. Ita ma bata b'oye farin cikin ta na ganin shi ba. Da haka har suka k'araso suka zauna. Haajar tace " Lah Abbu sameer! Yaushe ka zo?" Hajiya tace "wa? Wai Jamilu? Ai ya dad'e anan muna ta hira abun mu". Haajar tace " shine baka kira mu munzo anyi da mu ba" Haajar ta fad'a cike da tsokana. Yace "Wa ke nan 'yan nan? Wannan hira ai ta girme ki ,Dan ta manya ce. D'a na ganawa da uwar shi, wa ya gayyato bare kuma?" Zaro ido Haajar d'in ta yi tare da cewa "Cabdi jam! Wai ma bare. To Allah yasan yanzu na fika fawa a wajen Hajiya." Hajj Jamil yace "haba wa yarinya ,tukunna dai. Sai dai ki fi daddy amma ba ni ba" cike da raha Haajar ta koma kan kujerar da Hajiyan ke zaune tana ta famar yi musu dariya ta maqalqale Hajiya tare da shagwab'ewa tana fad'in "wai Hajiya ta kin ji ya fi ni fawa?" Hajiya na dariya tace "k'yale shi 'ya ta ,yanzu kuma ai ke ce sarauniyar fadar sauran kuma sai dai su zo a fadawan ki". Cike da jin dad'i Haajar ta sake rumgume Hajiya tana fad'in " dakyau Hajiya ta. Allah ya qara lafiya da Nisan kwana. Ka dai ji ko Abbu sameer?" Hajj Jamil yace "ke Dan uban ki ni ki sake mana tsohuwar mu. Ji yadda ki ka maqalqale mana ita kamar za'a mai da ki ciki" Haajar sake mannewa Hajiya tayi. Hajj Jamil yace "au ba da Hausa nake magana ba". Ta sowa yake shirin yi yayo kanta, Hajiya tace " A'ah haba Jamilu. Ya zaka zo har gidan 'ya ta kana Neman ka takura mata? To ka fita mun a ido kaji na gaya maka. Idan ba haka kuma ka tashi ka tafi mun gode da ziyarar, da ma ai ka canza sheqa. Ina jin ma yau ma makuwa ka yi ba nan kaso zuwa ba". Dariya Haajar ta dinga yi wa hajj Jamil hadda su gwalo. Hajj Jamil yace "gaskiya sai na yi da gaske ,Dan baze yiwu ace wannan yarinyar mai kama da maqota na Neman k'wace mun fada ba". Hajiya tace " to sai ka bada himma". Dikkan su dake parlourn sai dariya suke musu. Sai a lokacin Haajar suka gaisa da Barr. Suxee kuma ta gaida hajj Jamil. Suna cikin haka daddy ya shigo. Ganin duk yadda suke raha yasa yace "Yau kuma wani albishir Ku ka samu ne haka?" Hajj yace "Ina fa albishir. Matar ka na Neman ta k'wace min fada a wurin Hajiya kuma bata isa ba." Daddy yace "yo isa kuma na nawa. Ni kaina nan inajin ka kusa jin ance Hajiya ta zane ni da bulala akan Haajar". Hajj Jamil yace " kace kai ma ba barin ka ta yi ba?" Daddy na dariya yace "Ai kuma sai kayi. Gata nan ka tambaye ta". Hajiya tace " kwayi kwa gaji Ku bari. 'Ya ta kuma li'ilafi quraishun." Hajj Jamil yace "lah! Ka ji Hajiya na Nema ta yi mana baki". Dikkan su suka saka dariya. Har kusan goma na dare su na nan su na ta shan hira cikin raha abun gwanin sha'awa ,Dan idan ka gan su a yadda su ke zaune ba zaka ce ba 'ya'yan Hajiya bane su. Daddy ne ya fara miqewa yace shi dai zai shige Dan ya fara jin bacci. Da haka ya yi musu sallama ya yi ficewar shi. Matar shi na ganin haka itama ta miqe ta bi bayan shi. Ya rage daga Hajiya, Suxee, hajj Jamil sai kuma Barr, Dan auta ta dad'e da yin bacci tun shigowar hajj Jamil. Barr yau d'in gaba d'aya ji yake an takura masa ,ga shi dare ya yi amma bai samu damar ganawa da masoyiyar sa ba. Ganin lokacin tafiyar shi ya kusa ,kuma matuqar ba shi ne ya kira suxee ba yasan ba zuwa za ta yi ba. Miqewa ya yi tare da cewa " Hajiya ni ma fa jirgi na zai d'aga. Dan na fara jin bacci". Hajiya tace "gaskiya kam ya kamata kaje ka d'an huta. " sai da safe ya yi musu tare da miqewa hajj Jamil hannu suka yi saida safe. Sannan ya dubi suxee da ke zaune kamar babu ita a wajen yace "biyo ni ki amso wa Auta chocolate d'in da na siyo mata, da safe ki ba ta. Saura kuma ki sha mata Abu". Murmushi kawai suxee ta yi Dan ta San mai hakan ke nufi. Shi ya fara yin gaba sannan ta bi bayan shi sad'af-sad'af... Hajj Jamil sai bin su yake da ido ,Dan tun lokacin da Barr ya zo ,har ya kira suxee a waya ,ba jimawa sai ga ta tazo duk idon shi na kai. Ya kauda kai ne kawai ya yi kamar bai Su na yi ba. Gaba d'aya ya kasa samun sukuni Dan haka shi ma ya yi wa Hajiya saida safe ya fito. Waige waige ya shiga yi yaga ta inda zai hango su kamar ance ya waiga hagun shi ,ya hango Suxee a zaune cikin motar Barr mazaunin driver, ta sako qafafun ta a waje ,yayin da shi kuma Barr ke tsaye ya rik'e marfin k'ofar da suxee ke zaune. Kai da ka hango kasan suna cikin farin ciki da jin dad'in hirar su. Ran hajj Jamil ne ya b'aci over. Wani irin haushi da takaici ya tokare masa maqoshi. Tunanin yadda zai b'ata musu wannan zaman ya fara yi. K'arasawa ya yi har inda suke tsaye. Suxee na ganin shi ta miqe da sauri tare da duqar da kanta k'asa. Barr yace "Ah kai ma ka fito kenan?" Hajj da yake jin kamar zai yi aman zuciya yace "Eh wallahi." Barr yace "To Allah ya ba mu alkhairi" wani baqin cikin ne ya qara taruwa ya tsaya masa a qahon zuci. Kamar kar yace komai sai kuma yace "Dama cewa na yi ko za ka d'an ajiye ni idan ba damuwa. Motar tawa ce tad'an samu matsala dak'yar na samu na qaraso nan yau. Sai gobe zan turo bakanike yazo ya duba". Ba tare da Barr ya kawo komai a ransa ba yace " To ba damuwa". Sannan ya maida duban shi wurin suxee yace "muje in raka ki ciki'". Ba musu ta shige gaba shi kuma yana biye da ita a baya a haka har sai da ya kaita k'ofar sashen Hajiya da ya San shiga kawai zata yi yace " saida safe ko?" Tace "Allah ya kaimu". Kiss ya yi a tafin hannun shi tare da aikata mata. Da sauri suxee ta shige ciki cike da jin kunya. Duk abun nan da suke Hajj Jamil na kallon su ba tare da sun Sani ba. Ran shi yayi qololuwan b'aci. Dan ko da Barr ya aje shi ko godia bai iya masa ba. Kawai shigewar sa ya yi gida... Daren ranar Haajar ta yi wani mummanan mafarki akan Kubra. Wai ga su nan a jeji tana gudu kubra na bin ta da gudu da wani mummunan siffa. Addu'o'i ta dinga jerowa sai kalan Wanda ta manta, daga haka Kubran ta b'ace bata sake bin ta ba. Wannan mafarki ya yi matuqar firgita Kubra. Daddy da ke kwance a kusa da ita da sauri ya tashi yana k'ok'arin kunna wutar d'akin. A firgice Haajar ta farka ,duk ta yi zufa. Tsanan tashin hankalin da ta shiga ya haifar mata da gocewar jini. A Daren daddy ya kaita asibiti ba tare da ya gayawa kowa ba. Sai dai kafin ma su kai asibitin Allah ya yi na shi ikon ,Dan kuwa cikin da ke jikin Haajar ya zube... MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [8/23, 6:58 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA ARBA'IN DA BIYAR_ *____________________________* Wannan al-amari bai yiwa daddy dad'i ba ko kad'an ,dan kusan har ya fi Haajar d'in damuwa. Yadda daddy ya shiga tashin hankali kai idan ka gani za ka d'auka wannan shine karo na farko da za'a yi masa haihuwa, badan komai ba Sai saboda tsananin Kaunar da yake yi wa Haajar d'in. Haajar ta sha wahala sosai. Ta zubarda jini matuqa ,wannan ne yasa aka buqaci da dole Sai an yi Mata k'arin jini, banda wankin Mara da aka yi mata. Jinin daddy aka iba aka sa ma ta. Hajiya ce ta koma asibitin tana kula da ita ,kwanan su hud'u ta ji sauqi Alhamdulillahi ,aka sallame su suka dawo gida. Mutanen azziki Sai zuwa yi mata sannu suke yi. Hajj jamil ma ya zo gaishe ta ,bayan sun samu sarari ne Haajar ke fad'a masa irin mafarkin da ya yi. Ya jima yana jimanta abun kafin ya yi Mata addu'an Allah ya tsare gaba ,yace kuma ta qara dagewa da addu'o'i. Bayan hajj jamil ya koma gidan shi ya kira yayan shi mahaifin Haajar ya shaida masa abubuwan da suke faruwa ,Sai dai an yi rashin sa'a mahaifin Haajar d'in baya qasar gaba d'aya yaje taron qaddamar da wata gidauniya ta taimakawa nakasassu kan harkan lafiya. Ya kuma shaida masa zai d'an d'auki lokaci a can d'in ,a qalla wata biyar ko shida. Hajj jamil bai ji dad'i ba ,Dan yasan da ace yayan na shi na qasar ,to shakka babu zai bada gudunmawar shi ,musamman da Allah ya yi shi mai tarin baiwa da hikimomi iri daban-daban. Ya na da k'warewa akan duk wata harka na jinnu da sauran su. Wannan ne yasa hajj jamil ya haqura ya bari har Sai ya dawo. Dan babu abunda za su iya babu shi. Wata d'aya da faruwar hakan ,Haajar ta sake samun juna biyu. Murna agun daddy ba ka ma hannun yaro. Tarairaya kuma Sai kalar Wanda ya manta. Haka hajiy ma ta ke kula da ita sosai. A gefe d'aya kuma soyayyar Suxee da Barr dad'a qarfi ta ke. A kwana a tashi cikin Haajar ya kai watanni ukku. Ta yi kyau sosai ta qara haske. Wata rana da daddare daddy yawo da rana ya taradda Haajar d'in na bacci. Ganin yadda take baccin hankali kwance yasa bai yi yunqurin tashin ta ba. Zuqunnawa ya yi Sai tin fuskar ta ya sumbaci gefen kuncin ta. Ya d'auki abunda zai d'auka sannan ya fice. Suxee ce ta nufo sashen da fara'a d'auke a fuskar ta. Ta zo ta ba Haajar labarin yadda ta yi da Barr akan yana so ya turo. Yanayin yadda taga Haajar d'in ya yi masifar tayar mata da hankali. A sume ta ga Haajar d'in dirsashen a k'asa ga jini na mata zuba ba girma ba azziki. Da gudu ta koma sashen Hajiya ta fad'o mata. Hankalin Hajiya idan ya yi dubu ya tashi, ba shiri ta biyo bayan suxee suka zo sashen Haajar d'in. Anan hankalin ta ya sake ta shi ganin yadda jini ke yiwa Haajar d'in zuba kai kace an yanka rago ne. Rud'ewa Hajiya ta yi nan da nan ta fara kuka ,tace wa suxee "ma za ki kira daddy ki sanar da shi halin da ake ciki. Suxee ita ma hawayen take ,da sauri ta d'aga waya ta kira daddy ta sanar da shi halin da ake ciki. Ba'a fi minti goma ba Sai ga shi ya iso hankalin shi a tashe. Haka ya ciccib'e ta ya sab'a ta a kafad'a ,jinin duk ya b'ata masa jiki yana gudu Hajiya na bin shi a baya. Mota ya bud'e ya saka ta gidan baya. Hajiya ta shiga tare da ita ,Sai addu'o'i ta ke tofawa Haajar d'in. Suxee na gida saboda auta shi yasa ba ta bi su ba ,Sai kuku take yi tana addu'ar Allah ya ta shi kafad'un Haajar. Dan gani take yi rasa Haajar d'in zata yi kamar yadda ta rasa 'yar uwar ta haseena. Ranar kasa cin komai ta yi ,Sai aikin hawaye da ta kasa tsayar da su. Ba jimawa Barr ya je gidan ,a nan suxee ke fad'a masa Haajar ba tada lafiya an kai ta asibiti. Tambayar ta ya yi a ina asibitin ya ke? Ta fad'a masa sunan asbitin da suke zuwa. Ko zama Barr bai yi ba ya ka ma hanyar zuwa asibitin. A asitin kuwa, farkon abunda aka fara nema shi ne jini. Ba halin ibar jinin daddy Sobada jinin shi ya hau a wannan lokacin. Hajj jamil daddy ya kira Dan dama jinin su iri d'aya ne za kuma su iya ba ma kowa. Leda biyu aka d'iba daga jikin Hajj jamil, kuma ledan jini biyar ake da buqatar a saka wa Haajar a wannan lokacin. Barr na zuwa ya taradda halin da ake ciki. Yace shi ma zai bada jinin. Bayan an gwada shi aka ga cewar shi ma zai iya ba ma kowa jini ,aka kuma yi masa wani gwajin aka gane baya d'auke da wani cutar da ze hana d'aukar jini a jikin shi. Nan ya kwanta aka d'iba leda ukun da ake da buqata ,yayin da aka jona mata wancan na farkon nan da nan Leda biyun ta k'are. Kusan dikkan su anan suka kwana. Sai washe gari hajj jamil yace wa Hajiya ta koma gida ko Dan su suxee su tabar su anan. Ba Dan ta so ba haka Barr ya dawo da ita gida ,sannan shi kuma ya koma asibitin. Ganin da Hajj jamil ya yi na cewar akwai buqatar daddy yabar asibitin ,Dan shakka babu idan yana ganin Haajar a wannan halin babu abunda zai hana hawan jinin shi kaiwa 280. Saboda haka ya yanke shawarar yi kiran yayar shi da ke bin mishi a waya wacce ke jigawa Anty zuwaira ,da mijin ta ya rasu. Kud'in mota ya tura mata. Ba b'ata lokaci Anty zuwaira ta had'o inata-inata ta biyo hanya. Sai yamma liqis sannan ya iso. Hajj jamil da kan shi yaje ya d'auko ta a tasha ,ya wuce da ita gidan daddy wurin Hajiya ,da ma ya sanar wa Hajiya da zuwan ta. Bayan ta yi wanka ta yi sallah ta ci abinci ,ta shirya Hajj jamil ya dawo ya d'auke ta yakai ta asibitin. Ranar Anty zuwaira ce ta kwana da Haajar a asibiti. Yayin da daddy ko kad'an bai so hakan ba. Yasan ko ya tafi ba ze iya gudanar da komai ba. Abinci ma yaqi ci tun jiya. Haka dai Hajj jamil ya lallashe shi suka dawo gida. Yace wa Anty zuwaira idan akwai buqatar wani abun ta kira shi a waya. Tace masa "toh". Gaba d'aya yanayin yadda Anty zuwaira ta ga Haajar d'in ta ji abun duk ba dad'i. Yadda dai aka gaya mata ciwon kwana d'aya ne ,amma idan ka kalle ta sai ka zaci ko ta yi wata ta na jinya. Ta rame ta fed'e ta yi fari tass alamar rashin jini. Kusan kwanan Haajar hud'u bata farka ba. Kullum kuma su daddy Suna asibitin ba sa koma wa gida dai dare. Ranar da Haajar za ta farka ,ta farka a gigice duk Wanda zai tunkaro ta sai ka je tana fad'in "kar ki zo nan,,,mai nai miki?,,,Ku taimake ni" sambatu dai iri-iri Wanda kai da ka gani ka san ba na lafiya bane. Wannan Abu ya sake d'agawa su daddy hankali. Anty zuwaira ce ta yi wa Hajiya bayani akan lallai ya kamata a maida Haajar gida ,Dan ta fuskanci wannan ciwon ba na asibiti bane ,saboda wasu zantuttuka da Haajar d'in ke sakowa cikin dare. Hajiya tace itama gaskiya a yadda taga Haajar ta farka ta lura da hakan. Ta ma fi tunanin ko shafar aljannu ce. Duk yadda aka so a fahimtar da daddy ina ya kasa fahimtar su sai ma cewa da yake yi "Ni fa matata bata wani aljannu ,saboda me za Ku d'ora mata ciwon iska? Babu abunda ya had'a ta da iska. Kawai rashin lafiya ce. Kuma ko zan k'arar da dukiyata baki d'aya sai na nemo wa matata lafiya." Ganin kamar daddy ya hau da yawa yasa kowa ya zura masa ido. Kusan kwanan Haajar ashirin da d'aya a asibiti babu wani abun ci gaba. Kullum sai ruwa da jini da ake sanya mata, idan aka sanya mata jini yau ko da za'a duba gobe za'a ga kamar ba'a sanya ba. Su kan su malaman asibitin abun yana d'aure musu kai. Ga shi daddy ya k'i sauraren kowa akan a maida Haajar gida ayi na Hausa. Daga k'arshe Hajiya da ta abun na nema ya ci tura da kanta ta sa aka rubuta wa musu takaddar sallama. Da daddy zai yi magana tace masa "Kan naji kan na gani. Wannan umurni ne ba shawara ba". Ba Dan daddy ya so ba haka ya hak'ura aka maida Haajar d'in gida. Kwanan su biyu da komawa gida sai ga Abu na Nema ya fi na da. Dan Haajar matuqar aka bar ta ba kowa a kusa da ita to fa ta fara cin na kare kenan tana nema ta fita. Abun da ya sake K'ullewa ahalin gidan kai. Kowa abun da yake kawowa a ran shi Haajar ta had'u da shafar aljannu ne. Hajj jamil ya sake kiran Dr Imam mahaifin Haajar ya shaida masa halin da ake ciki. Ba Dan ya kammala abunda ya je yi a qasar da yaje ba ,haka yabar komai ya kamo hanyar dawowa gida Nigeria saboda yadda Hajj jamil ya zayyana masa ciwon babu sauqi sai a wurin Allah. Kwanan shi biyu kafin ya iso Nigeria ,sai da ya kwana a jigawa ya d'auko duk wani maganin da zai buqata, sannan ya hawo jirgi safe zuwa sakkwato. Hajj jamil ne ya je ya d'auko shi ya kawo shi gidan daddy. A mutunce su ka gaggaisa. Babu Wanda bai yaba da dattakon Dr. Imam ba. Mutum ne mai matuqar karamci. Sai a yanzu Hajiya ta gane inda Haajar ta yi gadon mutunci. Sai da ya huta sannan aka kai shi sashen Haajar d'in. Ba qaramin tausaya mata ya yi ba. Ba dan ya na da qarfin hali ba, babu abunda zai hana bai yi mata kuka ba ,musamman yadda soyayyar Haajar take a cikin ran shi. Kaf a 'ya'yan shi babu Wanda yafi so sama da Haajar. Hajiya ,hajj jamil ,Anty zuwaira ne a zazaune sun zuba wa sarautar Allah ido. Daddy da ke gefe kamar a jikin shi ciwon yake Dr. Yace a d'aure masa ita da igiya. Kowa ya shiga zaro ido. Hajj jamil yace "Abbu Yusuf mai yasa ba za'a rik'e ta ba sai an d'aure ta?" Murmushi Dr. Iman ya yi tare da cewa "wannan aikin ba na mutum bane Jamilu. Kai dai Ku d'aure ta. Daddy ko motsi bai yi daga inda yake ba ,saboda tsabar tausayin Matar shi da yake ji. Ba Dan ma mahaifin ta bane shakka babu bazai bari a maida masa da mata kamar mahaukaciya ba. Da taimkon Dr. Imam hajj jamil ya samu nasarar d'aure Haajar d'in ,shi ma sai da ya zuba mata wani ruwan magani akai sannan. Sai wani zaro ido take yi tana fad'in " Kai kuma waye? Ka sake ni nace. Ba zaka sake ni ba? Sai na kashe ka mutumin banza". Sai kuma ta fashe da kuka tace "Me nayi miki? Kar ki kashe ni" can sai ka ji ta fashe da wani irin ihu Mara dad'in sauti... Karatun qurni Dr. Imam ya fara yi na Neman yaddar Allah kan aikin da ze yi. Haajar sai wani dariya ta ke yi tana zage-zage. Wani kundi Dr. Imam ya d'auko ya bud'e. Haajar na ganin shi ta fara ihu tana kururuwa. Duk Wanda ke wurin sai da ya zubar mata da hawaye. Wani magani Dr. Imam ya je ya bud'e bakin ta ya zuba mata. Sannan ya doki tsakiyar kan ta da qarfi tare da take qafar ta na hagu. Shak'e mata wuya ya yi a lokaci d'aya yana ci gaba da karanto alqur'ani. Shak'ar da Ya yiwa Haajar kowa sai da ya d'auka mutuwa za ta yi a yadda take kakari. Zuwa can sai ga shi tayi wani irin amai baqiqirin na sare saren zare. Kundin nan Dr. Imam ya ajiye a gaban ta ,ya danna yatsanta a ciki. Nan da nan hannun ya kama da wuta. Wani haske ne ya mamaye inda Haajar d'in ke tsaye. Can sai ga Haajar ta fad'i a gefe ga kuma wata siffa mai kama da Kubra sak an fitar a gefe. Duk Wanda ke wurin sai da ya girgiza. Nan Dr. Imam ya shiga yi wa wannan sifa tambayoyi ita kuma tana bashi amsa cikin wani yare Mara dad'in saurare da ba Wanda ke iya gane mai take cewa sai shi kad'ai. Hannun ta d'aya ya dad'a dannawa a cikin kundin, tana ihu tana qarawa a haka dai da jikin ta ya k'one gaba d'aya, daga k'arshe sai ga wani haske na bartsi. Daga nan ta watse. Dr. Imam ya yi hamdala tare da komawa ya zauna. Wani magani ya had'a San nan ya dawo kan Haajar da ke kwance kamar gawa. Tsakiyar kanta ya bud'e ya zuba wani magani na gari sannan ya fara yi mata yayyafi da wani ruwan magani da ke cikin kwalba fari. Ya dad'e a zaune kusa da ita yana karanto mata ayoyin waraka daga ubangiji. Kusan mintuna ashirin sai ga Haajar ta mik'e kamar ba ita ba tare da yin salati. Mamaki tayi yadda taga an tattaru akan ta. Ga mahaifin ta zaune kusa da ita. Tace "Me ke faruwa ne? Dan Allah Ku gaya mun" Ruwan zamzam da aka yi wa addu'o'in shifa mahaifin ta ya d'auka ya bata. Da ido ta ni shi alamar mai zata yi da shi yace "ki karb'a ki sha" ba musu ta karb'a ta shanye tas.. Sannan yace a bata d'ankwali ta d'aura a kanta. Wani zufa ne ya shiga tsatsafo wa Haajar ta ko ina ,sharkaf ta yi kamar wacce aka tsamo da teku. Nan Dr. Imam ya ce a kunna mata na'urar sanyi Wanda kafin ya fara aiki ya ce a kashe. Hajiya da kanta ta tashi ta kunna panka da kuma na'urar sanyi ,nan da nan iska da sanyi ya karad'e ko ina a parlourn. Sai wani ajiyar zuciya Haajar d'in ke saukewa kamar wacce tayi gudun tsere. Shima Dr. Imam ajiyar zuciyar ya sauke tare da zaro k'yallen goge zufa ya goge zufan fuskar shi ,sannan ya soma da hamdala tare da yiwa annabi salati, kafin ya d'ora da cewa "Dukkan godia ya tabbata ga Allah. Na San dikkan Ku kun ga abunda ya faru a yanzu ,za kuma kuyi mamakin wani irin nau'in al-amara ne wannan?" Hajiya tace "wannan gaskiya ne" Dr. Imam yaci gaba da cewa "Ciwon nan da Haajar d'in ake ta sanya mata jini alal haqiqa ba ita ake sanya wa jinin ba ,saboda masu shanye shi daban. Idan kuma da za'a yi shekarun annabi Nuhu A.S ana sanya mata jini ko makamancin wannan ba za Ku tab'a ganin ci gaba ba, sai dai ma daga k'arshe Ku rasata ma'ana ta mutu ,saboda jinin jikin ta da ake zuqa daga wani wurin daban. Wannan siffar da na fiddo daga jikin ta nasan kunsan ta?" Hajiya tace "shakka babu wannan Abokiyar zaman Haajar ce data mutu a gobarar da akayi a gidan ba da jimawa ba". Dr. Imam yace " to ta mutu ne amma kuruwar ta na nan na yawo. Ta kuma lashi takobin hana wannan ahali zaman lafiya. To amma da yake Allah ke yi ba wanin shi ba. Wannan kundi da kuka gani ,kundi ne na k'ona rauhanai. Saboda haka na nayi nasarar k'ona kuruwar wannan baiwar Allah da ke cikin jikin Haajar. Ba'anan matsalar take ba. Wannan ba ita bace asalin ruhin. Kuma muddin ba'a Nema ta asalin an k'ona ta ba ,to fa akwai gagaruwar matsala. Saboda haka na yi mata tambayoyi tun kafin na qona ta. Ta kuma gayamin inda za'a samu wannan babban kundin ,da an d'auko shi aka k'ona komai zai zama tarihi da izinin Allah." Wani irin ajiyar zuciya Hajiya ta sauke tare da cewa "To yanzu a ina za'a samu wannan kundi malam?" Sunan wani daji Dr. Imam ya fad'a mai matuqar hatsarin gaske. Wanda ba lallai ka shiga wannan dajin ka dawo ba ,idan kuwa ka dawo to ba shakka zaka iya tab'uwar hankali. Ya kuma shaida musu akan lallai lallai Haajar d'in ake buqatar da ta je da kanta. "Kai ina!" Inji daddy "bazan tab'a barin Haajar ta je wannan wurin ba". Dr. Imam yace " Wannan itace mafitar mu ta k'arshe ,idan ba haka kuruwar zata dawo ,kuma idan ta dawo to dawowar bazai wa kowa kyau ba". Shiru kowa ya yi yana jimanta al-amarin. Kafin Dr. Imam yaci gaba da cewa "Zan shirya komai a Daren yau insha Allahu rabbi." Daga haka yace a rufe sashen Haajar d'in kowa da kowa ya koma sashen Hajiya. Haka kuwa aka yi. Misalin k'arfe sha biyu na dare babu Wanda ya iya runtsawa banda suxee da auta da basu San wainar da ake toya wa ba. Wata farar mata ce ta shigo su Dr. Na zaune. Dr.imam yace ta zauna. Bayan ta zauna suka tattauna da shi cikin harshen larabci. Suna gama magana daddy yace wa Haajar "ki yi wa baquwa ta rakiya". Ba musu Haajar ta bi bayan wannan farar mata ,ita kuma Matar ta rik'e hannun Haajar suka fita. Bayan sun fita daddy ya dubi Dr. Imam tare da cewa "Wannan wacece da suka fita da Haajar?" Gyara zama Dr. Imam ya yi tare da cewa "Wannan da kuke gani ba mutum bace aljana ce, Sunan ta maimunatu. Maimunata aljanar zuri'a ta ce ta amana." Cike da tashin hankali daddy yace "ina kuma zata kai Haajar?" Dr. Imam yace "dajin da fad'a muku za'a d'auko wannan kundin. Da taimakon Allah da taimakon maimunatu Haajar zata kai ga wannan kundi". A gigice daddy ya fita da gudu yana kiran suna Haajar! Dr. Imam yace " da'ace zaka dawo ka kwantar da hankalin ka da ya fiye maka kwanciyar hankali. Dan babu Haajar take so a wurin mu yanzu sama da addu'a." Kuka daddy ya fashe da shi ya na mai ci gaba da kiran sunan Haajar d'in babu qaqqautawa Sai da ya bawa kowa tausayi. Aiki Dr. Imam ya shiga yi tuk'uru. Dan kusan saida ya yi saukar alqur'ani. Su Hajiya kuwa alwala suka yi suka duqufa sallah har garin Allah ya waye. Banda daddy dake zaune cunkus kamar wani Mara lakka ,tun yana kukan mai sauti har ya koma sai dai hawaye kawai ke yi masa zuba. MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [8/24, 12:09 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA ARBA'IN DA SHIDA_ *____________________________* Har wuraren shida na safe babu Haajar babu alamar ta. Gaba d'aya ahalin gidan sun shiga damuwa ainun. Shida da rabi, Dr. Imam ya fito wajen sashen da suke ciki. A bakin k'ofa ya ga Haajar d'in a yashe ta yi wani irin baqi ta sauya kala kamar ba ita ba. Koma wa ciki ya yi ya yiwa daddy magana akan yazo ya d'auko matar shi. Da sauri daddy ya miqe yana fad'in "Ina take?" Ganin kwance a qasa a k'ofar shiga ya sa yayo saurin yowa kanta ba shiri ,ya shiga jijjiga ta yana kiran sunan ta. Dr. Imam yace "ka shigo da ita ciki". Daga haka ya yi shigewar shi. Ba shiri daddy ya sunkuci Haajar d'in ya bi bayan Dr. Imam. A tsakar d'aki Dr. Imam yace ya ajiye ta. D'ankwalin dake k'ulle a jikin zanin ta ya kwanto tare da warware k'ullin ya furta " Alhamdulillahi! Wannan shi ne kundin da ake da buqata". K'ok'arin k'ona kundin ya shige yi da ayoyin Allah. Nan take wannan kundin ya ka ma da wuta ,wani bak'in hayak'i na tashi. Sai da ya cinye tas sannan ya yiwa Haajar d'in yayyafin ruwan magani. A zabure ta tashi zata ruga a guje ,ya rik'o ta, Tare da ci gaba da karanto mata ayoyin waraka daga ubangiji. Sambatu Haajar d'in ta shiga yi kamar wata zararriya. Addu'o'i sosai Dr. Imam ya dinga yi mata, daga haka wani irin nannauyan bacci ya yi awon gaba da ita. Ya sake furta "Alhamdulillahi! Sauqi ya samu daga Allah! Yanzu ta samu bacci. Sannan wannan baccin idan zata kai sati d'aya tana yin sa kar a tashe ta ,sai lokacin da ta farka da kanta. Kar kuma Ku damu, babu abunda zai sake faruwa da izinin Allah. Za kuma Ku iya ci gaba da sabgogin ku". Hajiya tace " Insha Allahu za mu yi k'ok'arin kiyaye wa. Sannu da aiki malam, Allah ya saka maka da alkhairi. Da ba Dan kazo ba bansan yadda za mu yi da wannan rikitaccen al-amarin ba mai kama da al-mara. Duk da cewar Haajar 'yar ka ce ,amma mu ka yi wa wannan taimakon, Dan Haajar wata jigo ce daga cikin wannan ahali da ba zamu tab'a qaunatar abunda zai same ta na rashin dad'i ba. Mun gode sosai". Dr. Imam yace "Allah ya tsare gaba". D'akin Hajiya aka maida Haajar d'in. Sai a lokacin kowa ya samu kwanciyar hankali. Hajj jamil jan Daddy ya yi suka tafi gidan shi ,a can suka yi bacci , ba su suka farka ba sai wuraren sha biyu na rana. Anty zuwaira ma zuwa tayi ta kwanta. Dr. Imam kuwa labari ya shiga baiwa Hajiya, kan abunda ya faru da kuma dalilin faruwar abun ,ya tabbatar mata cewa asalin tushen gurb'acewar rayuwar Kubra akwai sanya hannun mahaifiyar ta ,Wanda tun farko aka gina rayukkan akan b'ata da sagba ta miyagun jinnu, Wanda shi ne dalilin da yasa ko bayan ta mutu ta dawo a matsayin kuruwa. Wannan kundin kuma da aka k'ona shi ne asalin rayuwar Kubra... Ya faffad'awa Hajiya maganganu da dama na firgi ,al-ajabi da kuma ban tsoro. Hajiya ta yi ta mamakin dama hakan na faruwa a wannan duniyar ta mu? Dr. Imam ya tabbatar mata da akwai abunda ma ya fi wannan d'aure kai idan ta ji shi... Kusan kwanan Haajar uku ,ko k'wak'k'waran motsi ba ta yi ba. Wanda kowa ya damu da hakan. A gefe d'aya kuma mahaifin ta na ci gaba da yi mata addu'o'i da taimakon magungunan musulunci da yake da k'warewa akan su. Sai a rana ta biyar sannan Allah ya yi mata farkawa. Farin ciki ya dawo sabo. Kar ma daddy ka ji labari, Dan har rumgume ta ya yi Dan murna, ya ma manta cewar akwai mahaifiyar shi da mahaifin Haajar d'in a wurin. Nasihohi sosai Dr. Imam ya yi musu. Ya kuma ba da magungunan da Haajar d'in za ta ci gaba da amfani da su. Washe gari Dr. Imam ya yi musu sallama ya tafi. Haajar hadda kukan ta ,Dan sosai take kewar mahaifin na ta. Ya sha gaya mata a baya cewa duk soyayyar nan da yake mata ,za'a yi wani lokacin da wani ko wasu sun fi shi buqatar ta'. Shakka ba bu wannan lokacin ne. Bai tafi ba sai da ya yi mata nasihohi sosai itama, ya kuma k'ara gaya mata yadda mijin ta da ahalin shi ke matuqar Kaunar ta. Gargad'i Dr.Imam ya yi mata akan komai wuya wannan ahali sune abokan rayuwar tana duniya... Kusan har aka yi sati Haajar bata gama dawowa yadda take ba, gaba d'aya jin ta take kamar ba ita ba. Daddy musamman ya shirya walima Dan yiwa Allah godia. Satin Anty zuwaira biyu ,ta koma gida jigawa a inda daddy da Hajiya suka cika ta da tarin abun alkhairi... Bayan wata d'aya. Komai ya lafa ,rayuwa ta dawo musu sabuwa. Haajar ta sake samun wani cikin. Kowa sai murna ya ke yi. A b'angaren d'aya kuma an so a saka ranar bikin Suxee da Barr Kabir ,duba da yadda soyayyar su tayi k'arfi. Haajar ta nema alfarman da a bari idan Allah ya sauke ta lafiya. Hajiya tace "duk yadda take so hakan za'ayi. Dan itace uwar amarya kuma uwar biki". Wannan batu ya yiwa Haajar d'in dad'i. Sannu da hankali cikin ta sai girma yake yi. Ta k'ara kyau ta yi haske gwanin sha'awa. Kulawa da tarairaya kuwa daga wurin daddy sai Wanda ya manta ,wannan ne ya k'ara bata damar murje gwad'arta take zuba masa zallar shagwab'a tare da nuna masa so da qauna a koda yaushe. A b'angaren d'aya kuma Matar hajj jamil Hajiya zaliha ta dawo daga wurin aikin ta da take yi a wata qasa, Bayan tafiya na dogon zango da ta yi na tsawon watanni tara zuwa goma. Wanda a Qa'ida duk bayan wata biyar ta ke dagowa gida, tare da d'anta d'aya mai suna SAMEER. Abun ya yi matuqar d'aure Mata kai yadda ta dawo wannan karon Hajj jamil baya d'aukin ta ko kad'an kamar yadda ya saba. Hasalima ko kad'an bai nuna alamun jin dad'in ganin ta ba. A tunanin ta ko dad'ewar da ta yi ne bata dawo ba ya sanya ya ke fushi da ita, bata San abunda ya ishe shi bane ya ishe shi. Shi damuwar shi d'aya ne akan auren Suxee da Barr Kabir. Hajiya zaliha mace ce ta tsara daidai gwargwado da ta San abunda ya kamata ,tana da duk wani kwalitis d'in da namiji ke buqata, amma a zahiri bansan mai yasa ta fifita aikin ta sama da bautar auren ta ba, aikin ma a wata uwa duniya. Ta yi ta k'ok'arin ganin ta tambayi hajj jamil abunda ke damun shi. Hajj jamil mutum ne da baya tab'a iya b'oye damuwar sa idan ka tambaye shi. Ko kalma d'aya bai rage mata ba akan yadda yake matuqar son Suxee ,farin cikin shi shine ya ga ya auro ta tazo gidan shi a matsayin Matar shi ta sunnah. Hajiya zaliha ba ta gane wacce suxeen yake magana akai ba ,sai da ta sake tambayar shi, ya tabbatar ma ta da Suxee 'yar daddy da ta sa ni. Iya tashin hankali Hajiya zaliha ta shiga tashin hankali, Dan bata tab'a tunanin irin rana mai kama wannan zai zo mata ba. Ta yi kuka kamar ba gobe musamman yadda ta ga mijin ta ya susuce akan son 'yar aminin shi. 'Yar da idan da kara yace ya ba da ita ,ta badu kenan. Sosai tayi kaico da irin halin da ta sanya mijin ta a ciki ,ta yadda duk wani abun da zai je ya dawo laifin ta ne. Ta San bata kyauta wa mijin ta, d'anta da rayuwar auren ta ba ,kai hadda rayuwar ta kacokam. Ta yi matuqar tausaya wa mijin na ta da ita kanta. Gafarar ubangiji ta shiga nema ba dare ba rana ,Dan tasan matuqar ta mutu a haka ta shakka babu aljannah ko a gidan ubanta ake raba ta sai dai a raba babu ita. Da yake tana da rabo, watsar da duk wani rud'in duniya ta yi ,aikin ma tace ta aje ,ta dawo ta rumgumi auren da mijin ta hannu bibbiyu. Ta fara basa kulawar da a da can bata basa makamancin sa ba. Ta je ta cire tsarin iyalin da ta yi, a cewar ta bata son haihuwa da yawa ,Dan idan ta tara 'ya'ya za su hana ta aiki.. Ita dai aiki... Sosai ta ke iya bakin k'ok'arin ta na ganin ta kula da mijin ta. Hajj jamil ya ji dad'i sosai yadda Hajiya zaliha ta sauya lokaci d'aya, sai dai fa a gefe wutar son Haajar ne kawai ke dad'a ruruwa a zuciyar shi. Ranar hutun k'arshen mako wato weekend Hajj jamil da Matar shi Hajiya zaliha tare da d'an su suka je gidan daddy. Fad'a sosai tare da nasihohi mai shiga jiki Hajiyar daddy ta dinga yi ma ta. Hajiya zaliha hadda hawayen ta. Ta yi wa Hajiya alqawarin insha Allahu za ta gyara. Yadda Haajar ke tafiyar da rayuwar ta yayi matuqar burge Hajiya zaliha ,wannan ya sa Hajiya zaliha ta so su had'a k'awance duk da cewar za ta girmi Haajar d'in. Kuma Haajar 'yar yayan mijin ta ne. Sai dai da yake babu wata shaquwa mai qarfi tsakanin su. Amma ta tabbata girman huhun goro ba shi bane. Saboda haka suka sha hirar yaushe rabo da Haajar. Har dare su Hajiya zaliha su na gidan daddy kafin su ka tafi. Tun daga ranar Hajiya zaliha ta samu wurin zuwa dan ta maida Haajar tamkar qawarta. Bayan sati d'aya sati biyu haka takan zo su sha hira sosai da Haajar. Shakka babu Hajj jamil ya ga amfanin zaman Matar shi da Haajar. Dan ba iya rayuwar su komai ya canza ba ,hatta a shimfid'a ya ji bambamcin na daban. Bayan wata tara Haajar ta haifo santala santalan 'ya'yan ta mace da namiji. Namijin kama yake da daddy sak macen kuma kama ta ke da marigayiya Haseena. Murna a wurin wannan ahali abun Sai Wanda ya gani. Tun randa aka haihun Hajiya zaliha kullum ta na gidan ta na yiwa Haajar d'awainiya. Saura kwana biyu biki ,dangi na kusa da na nisa suka halatto ,da ma ga shi an dad'e ba'a yi sha'ani a gidan daddy ba. Musamman dangin Haajar d'in da wasu daga ciki sai dai suka ji labarin d'aurin auren. Yayyin ta da k'annen ta rankatakaf babu Wanda aka baro ,tare da Matar mahaifin su da ta zamo tamkar uwa a gare su. Kai! Haajar ranar ina ruwa ta tsoma kan ta Dan murna. Daga b'angaren daddy ma anga gayyar mutanen kano da kewaye. Hajiya zaliha ma ba'a barta a baya ba wurin yo tata gayyata. Ranar suna namijin yaci sunan Hajj jamil ana masa laqani da Hassan d'in shi, macen kuma taci sunan marigayiya Haseena ana kiran ta da hussaina. Taro ya yi taro anci ansha ,mai jego da 'ya'yan ta sun yi shiga daban-daban gwanin ban sha'awa. Duk Wanda ya zo taron suna da abun azziki yake tafiya. Banda kyaututtuka da zunzurutun kud'i da jariran suka samu daga wurin abokan su daddy. Hajj jamil kuwa kamar shi aka yi wa haihuwa ,Dan kusan komai shi ya yi. Barr Kabir ma sai da ya yiwa yaran kyautar naira dubu d'ari tare da akwatin kayan jarirai biyu. Hajiya ma ba'a barta a baya ba ,Dan kyauta ta yi Haajar d'in na musamman. Hatta Dr. Imam mahaifin Haajar sai da ya yo aike. Kai lissafa tarin alkhairan da Haajar da yaran ta suka sa mu b'ata lokaci na. Dan idan za mu kwana mu wuni ba zamu gama lissafe adadin abubuwan azzikin ba. Bayan su na mutane na ta watsewa. Ranar da 'yan uwan Haajar za su tafi ,kyauta daddy ya musu ba ni da kyauta ba. Sun ji dad'i matuqa sun kuma yaba da irin mijin ta Haajar ta samu. Bayan kowa ya gama tafiya. Haajar Sai da ta nemi inda za ta ajiye kayan yaran ,dan tsabar sun mata yawa. Uban gayyar kuwa wato daddy ,kyutar gidan gonar shi sukutum ya yiwa yaran shi. Haajar ba ta so ba Dan gani take abun ya yi yawa. Ga wa'yancan ga kuma wannan. Hadda k'wallan ta Dan farin ciki. Account Daddy ya bud'ewa yaran ya zuba musu duk kud'ad'en da suka samu. Haajar ta tambaye sa akan ya za'ayi da su yace ta yi amfani da su idan ta na da buqata Dan shi dai idan bai qara musu ba bazai karb'a sisi ba. Shawartar shi Haajar ta yi akan to ko ta bud'e gidauniya na taimakawa gajiyayyu da nakasassu. Daddy yace wannan shawara ce mai kyau. Hakan kuwa aka yi. Kafin kace me sunan Haajar da tallafin ta ya zaga sakkwato da kewaye. Bayan sun yi arba'in. Suka shirya Dan zuwa gano Hajiya Gwaggo da ta dad'e a kwance ba tada lafiya. Gaba d'ayan su suka tafi. Yadda su ka samu Hajiya gwaggo kam rai hannun Allah. Washe garin zuwan su wata tsohuwa mai suna TANI ta zo gidan. Hannun ta d'aya a shanye. Aka tambaye ta wa take nema? Tace Hajiya Gwaggo. Nan aka kaita taga yadda jikin Hajiya gwaggon ya yi. Matar nan ta fashe da kuka. Nan ta soma basu labarin abunda ya wuce shekaru aru-aru. Ga Hajiya sakina a zaune kishiyar Hajiya Gwaggo ,ga hajiyar daddy da daddyn kan shi ,ga wasu daga cikin 'ya'yan Hajiya sakina. Haajar ma na daga gefe a zaune. Matar mai suna TANI tace "Tun suna 'yan mata sun gina rayuwar su akan Neman duniya da son zuciya ita da Hajiya Gwaggo. Ba su da aiki sai shiga malamai. A haka har suka yi aure. Ko da mijin Hajiya Gwaggo zai auro Hajiya sakina babu inda ba su shiga ba Dan su hana wannan auren ,amma duk inda suka shiga sai a ce musu wannan aure ba fa shi. A haka aka zo aka yi auren har Hajiya sakina ta fara haihuwa. Duk lokacin da Hajiya sakina ta samu ciki sai sun je an yi musu duba. Har lokacin da ta samu cikin mahaifin daddy aka fad'a musu cewa namiji za'a haifa, kuma mai arziki. Nan fa muka dinga k'ulla tuggu akan yadda za mu zubar da cikin amma Allah ya yi sai abunda ke cikin nan ya ta ka doran k'asa. To dama a lokacin Hajiya Gwaggon itama tana da ciki. Allah kuma yasa lokacin haihuwar su yazo rana d'aya. Mu ka yi amfani da wannan damar muka canza 'ya'yan. A inda muka d'auke d'an Hajiya sakina wato mahaifin daddy mu ka sauya shi da 'yar Hajiya Gwaggon Dan ace ita ta haifa. Ashe da ma 'yar da muka sauya wa muka ba Hajiya sakina ba mai zama bace, Dan tun kafin a yi suna Allah ya yi Mata rasuwa. Hajiya Gwaggo kuma ta ci gaba da rik'e d'an Hajiya sakina a matsayin na ta." Tsohuwar nan ta sake fashewa da kuka. Tace "Na ga jarabawar rayuwa da mugayen qaddarori da bazan so ace na mutu a ciki ba. Duk Wanda muka zalunta na yi ta k'ok'arin ganin na nema inda yake na ba shi hakuri. Nan ma kusan sama da shekaru goma ina Neman gidan amma Allah bai sa na gane gidan ba Sai yau." Tsohuwar na kuka tana Neman gafarar su. Hajiya sakina tace ta yafe mata ta ta shi ta tafi. Hajiya Gwaggo ko hawaye ne ya shiga wanke mata fuska ,tana so ta nemi yafiyar su amma ba dama ciwo ya ci qarfin ta. Hajiya sakina na hawaye tace wallahi ta yafe mata har ga Allah ta kuma gargad'e su akan ba ta yadda a fitar da zancen ba. Tun da har Wanda ake yi Dan shi ya mutu. Ranar kowa da abun ya kwana a rai. Abu sai kace wasan kwaikwayo. Washe gari kiran sallar farko na asubahi Hajiya Gwaggo ta amsa kiran ubangiji. Hajiya sakina ta yi kuka kamar ba gobe ,Dan ita har ga ba ta tab'a rik'e Hajiya Gwaggo a ran ta ba. Tana kuma matuqar qaunar ta har cikin zuciyar ta ,musamman jiya da ta ji ance ta riqe d'an da ta haifa. Abunda ta yadda da shi shine ,babu Wanda zai so naka har ya rik'e face masoyin ka... MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [8/26, 7:29 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA ARBA'IN DA BAKWAI_ *____________________________* Misalin k'arfe Tara da safe aka yi jana'izar Hajiya Gwaggo aka kai ta makwancin ta. Kusan duk Wanda ya bud'e baki Allah wadai yake da halayyar Hajiya Gwaggo. Banda Hajiya sakina da ke ta faman kuka tana fad'in ta yafewa Hajiya Gwaggo duk abunda ta yi mata duniya da lahira. A gefe d'aya kuma ahalin gidan sai k'ara jimanta lamarin suke yi wai Hajiya Gwaggo ba ita ce ta haifi Baba Alhaji ba mahaifin Daddy,,, kai wannan Abu da d'aure kai yake. Ran da aka yi addu'an uku jama'a suka fara watsewa, yayinda wasu daga cikin ahalin wannan gida ke jin dad'in mutuwar Hajiya Gwaggo, a cewar wasu daga ciki ,ta gallaza musu ta addaba musu, su da gidan mahaifin su amma ba su da saqat. 'Ya'yan Hajiya sakina sai murna suke yi na kasancewar daddy d'an d'an uwan su ne. Suka zauna suka tattauna akan yadda za su k'arfafa zumuncin su, a ka saida magana cewa za'a dinga had'uwa anan gida duk bayan wata uku lokacin 'ya'yan su dake makaranta sun samu hutu, ya ka ma zama hud'u kenan a shekara. Wannan batu ya yi wa kowa dad'i. Daga su Haajar ba su baro ba sai da aka sanya ranar auren Suxee da Barr Kabir nan da wata uku me kamawa. Aka sanya na wasu 'yan matan wa'yan da 'ya'yar daddy wata biyu bayan bikin Suxee. Ba'a tashi daga taron ba saida Hajiya sakina ta yi musu wasu 'yan nasihohi masu ratsa jiki. Kusan dikkanin su da farin ciki suka watse cike da d'aukin junan su. Daga haka kowa ya watse, ciki yadda su daddy. Rayuwa ta dawo musu sabuwa. Sannu a hankali 'ya'yan Haajar sai wayo suke yi. Bayan sun dawo kano ba Dad'e wa ba, Haajar ta fara shirin ta na zuwa gida Jigawa Dan dubo 'yan uwanta. Tare da suxee ta tafi, a yayin daddy ya ba su driver sannan ya cika su da kayan arzuka a cewar shi su yi tsara. Ya kum shaida masa ze biyo bayan su shima ya gaida ahalin ta. Kwanan su Haajar biyu da tafiya Daddy ya shirya shima ya tafi. Babu Wanda bai ji dad'in zuwan su ba. Dan kusan lungu da sak'o na 'yan uwan Haajar babu inda daddy be sa Ankai shi ba ,duk inda yaje kuma sai ya yi musu kyauta ta ban mamaki. Kowa sai San barka yake yi da irin mijin ta Haajar ta samu. A yayin da shima daddy ke jin dad'in irin karrmawa irin na 'yan uwan Haajar. Dr. Imam ma yaji dad'in zuwan su, dukda cewar yana shirye-shiryen barin k'asar ne, zuwan su ne ya d'an dakatar da shi. Satin daddy d'aya ya juya. Haajar kuwa tunda taje Matar mahaifinta ke d'awainiyar gyaranta ciki da waje. A cewar ta bata samu damar yi mata na aure ba ,Dan haka take iya bakin k'ok'arin ta na ganin ta ranka mata. Kusan duk wani had'i da Haajar d'in za ta sha ko tayi amfani da shi tare da Suxee suka sha ,dukda cewa suxeen bata son amfani da wasu daga ciki, daga tace wannan ba dad'i ,,sai tace wannan bauri. Haajar tace "kya dai ji da shi. Wata rana ina zaune zaki zo nema" suxee tace "cabdi. Aiko Anty Haajar ba rana." Dariya kawai Haajar tayi tare da cewa "To Allah ya kaimu". Kusan satin su uku a Jigawa sannan suka dawo dawo gida cike da tsaraba. A kwana a tashi kwanaki tafiya suke yi. Yanzu saura wata d'aya da kwanaki bikin Suxee. Haajar ta shiga gyaran amarya ba dare ba rana. Dan kusan yanzu sun rage zuwa sashen Hajiya ,aka yi sa'a kuma daddy yayi tafiya. Kullum da irin sabon tsumin da Haajar ke yiwa Suxee. Banda gyaran jiki da ake yi kullum safe. Ita da kanta suxee ta ji canji a jikin ta. Ga wani qiba data k'ara fatar nan kau sai shek'i take yi. Saura sati uku bikin Suxee. Haajar ta zaunar da ita ta fara shimfid'a mata darussa zamantakewar aure ta yadda zata rik'e mutuncin gidan ta ba boka ba malam. Haajar ta soma da cewa "MIJI ABOKIN RAYUWA MACE ABOKIYAR RAYUWA Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah madaukin sarki wanda ya shar'anta aure kuma ya sanyashi ya zama bauta ga bayi,Tsira da amincin Allah su tabbata ga uban dakinmu Annabi muhammad ﷺ da iyalan gidansa da sahabbansa da wadanda suka bisu da kyautatawa har izuwa ranar sakamako. wasu daga cikin fa'idoji da kuma al'fano da yake tattare da yin aure. KAD'AN DAGA CIKIN FA'IDOJIN AURE Aure Bautar Allah ne kuma sunnah ne na Annabi ﷺ da sauran Annabawan Allah, Babu wani Annabi daga cikin Annabawan Allah face ya kasance yana da aure. Aure Hanyane na Samun zuri'a ta ýaýa wadanda zasu bautawa Allah sannan kuma Annabi yayi Alfahari dasu a ranar alkiyama. Aure Hanyane na samun nutsuwa da kwanciyar hankali da jin dadin rayuwa. Aure Hanyane na kiyaye ido daga kallace kallacen haram kuma hanyane na kange Al'aura daga fadawa zinace zinace. Aure Hanyane na kare mutuncin yaron da za'a haifa,domin duk yaron da aka haifeshi ba ta hanyar Aure ba, to yaron zai rayu cikin qunci da tsangwama. WAI SHIN MENENE NI'IMA A JIKIN MACE? Ni'ima dai wasu sinadarai ne da suke taruwa wajen jiyar da dadin ma'aurata ko basu cikakken gamsuwa lokacin Saduwa. Alamomin cikakken ni'ima sun had'a da: 1- jin ki cikin danshi 2- kasancewa cikin d'umin farji 3- Fitowan ruwa lokacin jima'i 4- Cikowar gaba da jinki a matse 5- Gamsar da miji da rikicewan salo lokacin saduwa koda baya sambatu 6- mace mai cikakken ni'ima takan ji sha'awa lokaci lokaci 1- Mace zata rika jinta cikin danshi ko tafiya kike zaki ji santsi santsi a jikinki sannan in kinje fitsari wajen tsarki zaki ga ruwa mai dan yauki ko yauki sosai a haraban farjin kina wankowa. ko kiga alamun shi a pant dinki ,kuma ruwan zaki gan shi fari kaman ruwa ko ki ganshi ruwan madara ,ya danganta dai. Amman duk ruwan da zaki gani wanda baida yauki wani daban ko kaman koko to na cuta ne Dan haka mata ku kula ,mu san wani kalan ruwa muke fitar wa daga jikinmu. Sannan akwai wani ruwa dake fita daga jikin mace wanda ba ni'ima bane kuma ba infection bane. Nasan zaku ce wani ruwa kenen??? Idan mace suka yi jima'i da mijinta da daddare to washegari zata ga maniyyi yana dan fita kadan kadan, kuma shi baida yauki sosai wasu har sai washegari ma maniyyin ke gama fita, musamman idan mijin ya zubarda maniyyin shi sosai. Kila kuna observing haka idan baki lura ki fara sa ido zaki gani. 2- Mace ta kasance cikin dumi alama ne na ni'ima dumin hq mace na tsimakawa matuka wajen gamsar da maigida yana tickling high arousal wajen sex yana taimakawa wajen sa bananan maigida ya kara kauri da tsawo ba'aso cikin farji ya kasance da sanyi yana tsinka ni'ima kuma yana rage kuzarin namiji wajen saduwa. Ta yanda zaki gane kina da dumin gaba ko hannunki kika dan jingina ta kasan ki zakiji da dumi. idan farjin ki ba ya da dumi ba zakiji ba... ABUBUWAN DAKE SA D'UMIN FARJI 1-Tsarki da ruwan dumi koda yaushe 2-Sa pant akai akai amma banda dare 3- Yawan had'e kafan ki in kina zaune 4-Tsugunno kan rushi ko baki sa komai ba. 5-Lulluba da ko zanin gado ne lokacin saduwa... Sai kuma nature. AKWAI ABUBUWA DAKE RAGE DUMIN FARJI 1-tsarki da ruwan sanyi 2-Rashin sanya pant 2-Yawan wawan zama 3-Rashin lulluba lokacin jima'i ko kuma kunna fanka ko Ac 4-Saka yatsa a farji 5-Yawo ba takalmi a tsakar gida BA KYAU, QUGU KO MANYAN NONO BANE D'AND'ANO Mutane da dama sun dauka mace mai kiba ko mai kyau ko mai kugu ko me manyan brs itace mai ni ima to gaskiya abin ba haka bane.. Allah ya halicci mata kala kala kuma kowacce da irin baiwar da yayi mata wata za ka ga bata da kiba amma kullum kamar korama take wata kuma tanada kiba amma kullum tana bushe. Wasu matan idan su na da ni'ima zasu rinka zubarda wani ruwa mai kamshi sannan kullum suna cikin shauki da sha awar jima'i, amma shi wannan ruwan akwai wanda yake fitowa na cuta ,ya danganta da kalarsa to amma mace wanda bata da ni ima bata cika sha awar jima'i ba amma idan namiji kuma ya nemeta tafishi zumudi.... DAN QARIN SHA'AWA INGATACCIYA DA NI'IMA MAI DOREWA 1- ki samu kankana mai kyau kifere samanta kawai seki caccaka cikinta sannan ki samu kwakwa kallo daya ki gurzata ki zuba aciki duk da ruwan saiki saka garin dabino da garin kanumfari saiki rufe kibarshi ya yini saiki zuba madara peak da zuma ki gaurayayshi sosai seki shanyeshi duka in bazaki iya sha atakeba zaki iya rabawa biyu. 2- kisamu aya d'anye da dabino kicire kwallayen saiki samu danyen zogale da kwakwa da kanunfari da kankana inzaki samu kisa cukwui aciki seki markadasu bayan kin markada seki zuba nonon rakumi da mazar kwaila kisha. SIRRIN BUSHEWAR FARJI yar'uwa ga dama ta samu, idan kina fama da bushewar farji, a koda yaushe to sai ki sami man zaitun da man habbatussauda, sai ki hada su wajen daya, ki dinga shafawa a cikin farjinki insha Allah Zaki ga biyan bukata, domin kowace cuta tana da magani, sai dai in baki nema ba, amma in kika nema Zaki samu. MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA ARBA'IN DA TAKWAS_ *____________________________* Haajar taci gaba da cewa "TATTALIN MIJI : Yar uwa ki bude kunnenki gawani sirri. Mi samu busheshiyar kubewarki cokali uku ki matse lemon tsami aciki da madara kizauna ki shanye ki dibi kadan ki hada da dakeken bagaruwa kiyi matsi dashi na awa daya sai ki wanke. Yana saukar da ni'ima sosai. Ana so ko da yaushe idan mijinki zai kusance ki yaji ki a matse kike, ba'a son lokacin da miji zai kusanci matarsa ya wuce siririf. Don haka ya ke da kyau mace ta rika kula da gabanta kar ya bude. Abubuwan da ke matse mace suna da yawa misali Bagaruwan hausa.....ana dafa ta da ganyen magarya ko ita kadai a rika wanke gaba dashi ko ki zuba a baho ki zauna a ciki da d'umi kamar na 30mins a kalla sau biyu a sati. Kanunfari ana dafa shi a sha da zuma da zafi zafi, ko ki jika ya kwana da safe ki tace kisha da madara da zuma. Ana kuma dafa ta a zauna a ciki da dumin ta ko a rika tsarki da ruwan ko kuma a zuba kanunfari a garwashi a tsugunna shi ma sau 2 a sati. Kwallon mangwaro idan kika fasa zaki ga dan ciki fari haka, ana busar dashi a daka a kwaba da zuma arika matsi da shi bayan isha'I idan zaki kwanta bacci ki wanke ko kuma ki dafa dan cikin da bagaruwa ki wuni tsarki dashi ko ki zauna a ciki shima a kalla so3 a sati. Almiski fari ko ja ki daka kanunfari ki tankad'e yai laushi sai ki kwaba da miskin da man zaitun, yawaita amfani dashi na matse mace sosai kuma kullum farjin ki cikin kamshi....yana gyara macen da ta haihu sosai musamman da jinin haihuwa ya dauke ki fara amfani dashi har ki yi ar'bain... MEKIKE NEMA BAYAN SO WAJEN MAIGIDA??? Yar'uwata kigwada wannan zakisha mamaki indai NI'IMA ne saidai kifadama wani. 1.Ki nemi Dabino wanda ba busasshe ba (lubiya) da Kankana mai yashi. kici dabinon sosai sai ki sha kankana daga baya. ki yi haka kamar bayan La'asar. 2. Kisami man Hulba da pure madara kota shanu ko peak ta ruwa sai ki hada ki aje yayi 1hr kafin ki kwanta, idan zaki kwanta sai kisha sai ki tsaya kamar 3mins saiki kwanta. 3. Kisami lalle kofi1, kisa a ruwa ki dafa sai kijuye kisa a baho kizauna Wallahi kam zaki matse. Ban da tsarki da Sabulu saboda yana causing cancer agabanki. Musamman detol dominshi yana kashe kwayoyine agaban macce damasu amfani da marar amfani..kisami KALTUFA(brown venigar) kirinka tsarki dashi. ABUBUWAN DAKE SA MACE TAFITA DAGA ZUCIYAR MIJINTA 1.RIKO Riko shine idan an aikatamata wani laifi kabar abin aranka batare da kayafe ba. Uwargida kada kizamo mai riko domin hakan ba karamin janyo miki matsala zaiyi ba, musamman idan mijinki nada saurin fushi . Saboda haka idan abu yafaru mudinga hakuri domin mata ansanmu da hakuri da juriya idan akai abu to dazaran ya wuce to amaida komi ba komi bane domin aljannarmu tana karkashin su sai sun daga zamu samu. Mata mudinga hakuri a duk lamuran mu sai muga mundace. 2. YAWON MITA Yar'uwa kar ki zamo cikin mata masu yawan mita a gurin miji. Abu baya wucewa ayita dawo da magana baya wanan zai haddasamaki matsala domin zaki fita ranshi. Idan abu yawuce to ayi hakuri abarshi adaina tuna baya. 3. FUSHI Uwargida kar ki zamo mai yawan fushi ko nunama miji kincika fushi. Kar ki manta Allah da kansa "yace yanatare da masu hakuri"shin bakison Allah yazamto yana tare dake kowane lokaci?. Yar'uwa kisama ranki hakuri fushi banaki bane domin karkashin wani , kowa yace zomu zauna zomu sab'ane. Hakuri shine ribarmu. 4.RASHIN IYA GIRKI Da anxo maganar girki sai in ji tsoro tare da jin kunya. Wlh samun yar aiki ba gata bane. Ina gatan yake kina can kwance yar aiki na saye zuciyar mijinki da dad'ad'an abinci? yar'uwa mutashi tsaye mukoyi girki kodan saye zuciyar miji. Domin namiji nason matar da ta iya girki. Za ki ga namiji na gayyato abokanai zuwa gidan shi don suci abinci saboda yasan bazata bashi kunya ba, amma idan baki iyaba fa zai fara tunanin kara aure. Sai mun gyara sosai. 5. QAZANTA Uwargida ayi tsafta kodon lfyr jikinki, karki manta tsafta nadaga cikin addini. Yar'uwa idan ba tsaftar yazakiyi ibada? Sanan kisani tsafta nasa miji yasoki sanan yaji bayada kamarki zakiga kowane lokaci yana manne dake yana shakar kamshinki Idan kuwa bakida tsafta da yabaki kudin cefane baki k'ara ganin shi sai dare domin koya dawo ba abinda zaigani sai bacin rai, har ki dinga cewa ya daina sonki, aa ba daina son ki yayi ba, kazantarki ce tajawo maki. Sanan kisani kazanta itama mabudin kara aure ce. Pls kozakiyi chatting yazamto kin gyara ko ina, sanan ya zamto kema kingyara jikinki da na yaranki, kuma idan mai gidan yadawo abashi kulawa a ajiye komai. 6.KULA DA SHINFIDAR MIJI Mata muna sakaci wajen bawa miji hakkinsa. kinaso amma kitsaya gulma wai jan aji ina ajin yake bayan yagama saninki lungu lungu ba inda baisaniba ajikinki, to wallahi ki gyara ki dinga bashi hakkin shi yadda yakamata wanan shi zaisa mijinki yasoki kuma ki mallakeshi. Abubuwa guda 4 dasuke matuqar janhankalin namiji yaso matarsa so matsananci. 1. tsafta: kowanna namiji yana matuqar son tsafta ,kuma kowanna namiji yatsani qazanta koda shi qazamine dazarar mace tazama me tsabta hakan zaizama abun yabo agun mijinta da qaramata kima agunsa .tsafta na sa maqota ma da yan uwanki mata suso abun da kikataba ,hakanan qazanta nasa kowa yatsanaki ballantana mijinki ma. 2. iya kwalliya: kwalliya na maida mace babba kamar budurwa hakama rashin kwalliya namai da mace kamar dodanniya ,ita mace batada wani kyau azahirinta inbatayi kwalliya ba ,sautarin rashin kwalliya nasa wasu mazan subar matansu kyawawa a gida suje neman munana a kwararo saboda sun iya kwalliya, dan haka yar uwa kikoyi kwalliya a gidan mijinki bawai sai zaki gidan biki ba. Dan haka ki tsaya kikoyi yadda akeyin kwalliya mekyau ba wacce zata maidake kamar dodanniyaba alhalin komai mijin na siyo miki. 3. iya girki: kowannan namiji yana alfahari da girkin matarsa yakan zuzutata akan ta iya girki koda bahakabane ,dazarar kin iya girki zakina gani mijinki na gaiyato abokansa kala kala hakan kuma naburgeshi ,na fasa masa kai .amma dazarar baki iya girkiba shima bazai naci ba sosai ballantana ma yagaiyato wasu abokansa. Dan haka lallai kizama me iya girki kala kala dan kula da mijinki. 4. kula da haqqin kwanciya: shima wannan na daga cikin abu mafi girma dake sa mace mallake miji wato bashi haqqinsa na kwanciya aduk sadda yabuqata.hakanan kuma hana mai gida haqqinsa na kwanciya nasa miji yatsaneki ko ma yakoreki bayan fushin Allah. Hadadden Maganin Sanyi ( Infection): Insha Allah 1. Alamomin Ciwon Sanyin Maza: - Saurin Inzali - Kankancewar Gaba - Daukewar Shaawa - Kurajen Gaba - Kaikaiyin Matse Matsi - Yawan Zafin Fitsari - Yawan Gajiya da Ciwon Mara. 2. Alamomin Ciwon Sanyi na Mata ( Women infection): Gushewar Shaawa Fitar Farin Ruwa Yawon ciwon Mara Jin Zafi Lokacin Jima'i Sanya Warin Gaba Daukewar Niima Wannan Matsala ta Sanyi Gaskiyar Magana ita ke haifar da rashin jituwa tsakanin Ma'aurata da yawa aure na mutuwa batare da an san daliliba, Gaskiyar al'amarin shine duk wadda yake da Sanyi cikin daya Miji ko Mata to kowanne cikin su nada Sanyi. Matukar mutum yanaso ya magance wannan matsala to Wajibine suyi family treatment na wannan matsala. HADIN ZUM Zuma Hulba Habbatus sauda ki samu zumar ki, ki hada da garin habbatus sauda da hulba ki kwaba sosai sai ki sha safe da yamma ni'ima kam ba'a cewa komai zaki ga abun mamaki. BAGARUWA Ki samu bagaruwa ki nika ta tayi laushi sosai sai ki samu zuma da almiski ki kwaba sai ki dinga matsi dashi zaki sha mamaki yar uwa ta. HULBA DA GANYEN MAGARYA Ki tafasa su sai ki dinga zama a ciki kiyi kamar minti goma ko sha biyar a ciki yana matse gaban mace sosai kuma babu illa sannan kuma yana maganin infection. GANYEN NA'A NA' Ki dinga tsuguno da shi yana hana warin gaba da kuma infection. DABINO DA KANUNFARI Ki b'are dabino ki samu kanunfari sai ki jika su a gora ko roba ki bari su jiku sosai sai ki dinga sha safe da yamma wannan hadi yana saukar da ni'ima sosai. DALILIN DA SUKE HANA WASU MATAN SHA'AWAR JIMA'I : A lokacin da wasu matan shaawarsu na son yin jima'i ya fi karfin mazajen su, akwai kuma wasu matan da mazajen su na fama dasu ne saboda yadda basuda sha'awar yin jima'i Sam. Irin waɗannan matayen a kullum suna samun matsala da mazajen nasu wanda hakan yasa wasu masu irin wannan matsalar suke dauka ko an musu asiri ne ko kuma dai su na dauke da wata cutar ne. Eh to ana iya samun duka biyu, sai dai kuma akasarin mata masu wannan matsalar babu wata cuta ko asiri da aka musu domin a dauke musu sha'awar su. Ana samun wasu mata da haka nan halittar su yake na basu da sha'awar yin jima'i kamar yadda ake samun wasu matan masu tsananin sha'awa. Sai dai kuma kamar yadda masu illimin jima'i suka gano. Kashi 1 ne kawai cikin 100 na matan da ba a cika samun su da sha'awar jima'i ba. Don haka akasarin mata masu fama da irin wannan matsalar da akwai wasu dalilai da suke hanasu sha'awar jima'i kamar haka: 1. Rashin son mijin da suke aure. Mace ba kamar namiji bane. Idan har bata son mijin da aka aura mata duk yadda zai taba ta sam bazata ji wani sha'awar ya motsa mata ba. Shi kuwa namiji ko baya son mace muddin har zai amince ta taɓa shi, tana iya motsa masa sha'awar sa har ma ya biya mata bukatar ta. Don haka idan kina da wannan matsalar sai ki duba shi mijin da kike aurensa ko akwai soyayya a tsakaninku. Mace idan tana son mijinta wata ko muryar sa ko da tunaninsa ta yi sha'awar ta zai iya motsawa. 2. Rashin Kwanciyar Hankali - Bama ga mata ko maza ba, muddin hankalin su ba a kwance yake ba to babu da wasu sha'awar yin jima'i da matansu. Hakan wannan matsalar ma take da mata. Muddin mace bata da natsuwa akwai wani muhimmin abunda ke damun ta kuma ya tsaya mata a rai, nan take sha'awarta yake daukewa. 3. Shan Miyagun Kwayoyi- suma suna daukewa mace sha'awar ta na jima’i.Haka shima yawan shan taba sigari. Duk macen da take mu'amala da miyagu kwayoyi kuma sama da rabin lokacinta tana buge. Irin waɗannan matan basu da wani sha'awar jima'i a tare dasu. Shi yasa ko yan matan da suke yawan shan kodin zina bai damesu ba. Su dai suyi dip kawai. Idan ma ta kama zasu yi jima'i suna yi ne domin shi mai bukatar ya gamsu amma ba dominsu ba. 4. Cuta - Akwai cuttutuka irin na hawan jini, ko ciwon shuga cuttutuka ne da suke daukewa mace sha'awar ta na jima'i muddin yayi kamari a jikin ta. Kamin har sha'awar su ya dawo sai sun samu sauki. Haka ma ciwon mata na fibroid shima yana daukewa Mata sha'awar su ta jima’I. 5. Shekaru- Karancin shekaru da kuma yawan shekaru na hana mace sha'awa. Akwai matan da ake aurar dasu da karancin shekaru irin waɗannan suna yin jima'i ne kawai amma ba wai domin suna sha'awa ba. Haka nan matar da shekarunta suka ja ita ma sha'awanta na iya daukewa. Waɗannan sune wasu daga cikin abubuwan da suke haddasawa mata daukewar shaawarsu na jima'i. YADDA ZAKI BURGE MIJINKI -Garin Nahal_ babban cokali 2. -Garin yayan bagaruwa Qarin cokali 2._ -Garin kanimfari cokali 1._ -Garin almiski ko ruwan almiski._ Zaki kwabasu gaba daya, yayin da zakije gun mai gidanki sai kiyi turarensu ki tsuguna ya shiga gabanki, Insha Allah maganar burgewa gun mai gida kin gama dashi ko harararki ake daga sanan an daina. SINADARAN TABBATUWAR NI'IMA DA ZAMA CIKAKKIYAR MOWAR GIDA. wannan wata irin tsaraba ce ta musamman gare ki uwar gida . sassaken baure. ruwan rake. 'ya'yan zogale. ruwan zuma. ruwan dabino. Ki daka sassaken baure ko ki barshi a sassaken sa, ki zuba ruwa cikin kofi daya, mai girman ( jug ) idan gari ne sai ki sa cokali biyar idan sassaken ne sai ki kin tabbata kamar yadda idan kin daka zai ba ki cokali biyar din, ki Dora a wuta ya tafasa kamar awa guda, sannan ki sauke idan ya kwanta sai ki tace, sai ki zuba markadadden ruwan kankana kofi daya, ruwan rake ma kofi daya ruwan dabino ma kofi daya, zuma Rabin kofi garin ganyen zogale cokali biyu, sai ki Dora a kan wuta Yayi ta dahuwa sai ya dahu sosai , zai yi kauri amma ba kitif ba, idan ya huce sai ki dinga shan Rabin kofi safe da yamma Wanna yan dadewa a jiki, Zaki ban labari. DAUKEWAR NI'IMA BAYAN HAIHUWA sassaken kankana sassaken baure ya'yan zogale idon zakara asuwaki mata ganyen kafi suga. Ki hada ki dake ki tankade yayi laushi sossai ki dinga zuba cikin cokali abinci daya cikin madarar shanu kofi daya ko cikin madarar ruwa gwangwani daya kina sha safe da yamma. : JAN HANKALI GA MATA MASU BUSHEWAR FARJI Sirin bushewar farji yar'uwa ga dama ta samu, idan kina fama da bushewar farji, a koda yaushe to sai ki sami man zaitun da man habbatussauda, sai ki hada su waje daya, ki dinga shafawa a cikin farjinki insha Allah Zaki ga biyan bukata, domin kowace cuta tana da magani, sai dai in baki nema ba, amma in kika nema Zaki samu. Allah ta'ala yasa mudace. QARIN NI'IMA Ya'yan kankana Danyar gyada Dabino Alkama Garin kumasoriyya 'Ya'yan zogale Ki dakesu suyi laushi ki rinka shan karamin cokali da madara ta ruwa safe da yamma, kuma shima mijin zai iya sha. QARIN NI'IMA Ki nemi ridi, ki daka ki tankade ki nemi madara ta ruwa ki hada ki gauraya kisha sai an gwada akan san na kwarai. QARIN NI'IMA Dabino Dankalin hausa Kwakwa Mazarkwaila Madara peak milk 1 Kanunfari Kicire kwallon dabino saiki jika ki fere dankali kiyanka kanana ,kixuba kijika maxarkwaila tajiku kixuba kiyanka kwakwa kanana kixuba saikiyi blending dinshi duka saiki tace kisaka a fridge yayi sanyi ki wuni kina sha. HADIN TANTABARA('YAN SHILA) Bayani akan hadin tantabara ba sobon abubane kusan kowacce mace tasan amfaninsa domin akwai tabbacin yana hada dankon soyayya tsakanin miji da mata bayan ni ima da dandano yana saka gaban mace ya ciko wannan an dade ana amfani dashi kuma yana aiki idan kinason koya to ga yanda zakiyi Da farko dai ga abubuwanda ake bukata ki nema 1️.Za ki samu Tanbaru guda biyu amma yaya ba iyayeba (Mace da Namiji) 2️.Habbatus-Sauda (Cokali biyu) 3️.Garin Raihan (Cokali hudu 4️.Ridi (Cokali uku) 5️.'Ya’yan Zogale (shima cokali uku) Duk wadannan anaso kidakasu su zama gari saiki ajiye bayan kin fara dafa wannan tantabarun sama sama saiki tace ruwan sannan ki zuba wannan garin saiki saka duk wani kayan hadi da kikeso sannan ki zuba ruwa kadan ki mayar kan wuta ki barshi ya dahu sosai sannan ki sauke. kuma dukkansu akeso ki cinye ke kadai ki jarraba wannan ko amarya ko uwargida. HADIN KAZA NA AMARYA DA UWARGIDA Hadin Kazar Amare Yanzu za mu yi bayanin sirrin dafa kazar Amare wanda idan har mace tayi kafin Aurenta da kamar sati 1 zataga amfaninsa. Irin wannan ne idan baki San sirrin ba zakije ki saya da tsada. Koda yake wasu qiwuya ke hanasu had'awa da Kansu. To ga sirrin Yadda ake : Anaso kisamu bushashen ganyen magarya da kanunfari da idon zakara duk ki hadasu waje daya ki dakasu ki tankade su zama gari to idan kika samu: Budurwar kaza, kika gyarata saiki zuba wannan garin acikin tukunyar sannan zaki iya zuba kayan miya yanda kikeso. Bayan ta dafu saiki cinye gaba daya. Yana saka Farjin mace ya kumbura ya ciko da Ni'ima, kuma yana karawa mace dàn dàno... MAGANIN K'AIK'AYIN FARJI KO KURAJE KO WARIN GABA Yawanci Ciwon Sanyi Na mata ne ya fi haddasa irin wadannan matsalolin. 1. Ganyen lalle Wanda bai zama gari ba 2. Yayan Hulbah 3. Tafarnuwa Guda 3 a 6are busashshen 6awonta 4. Kaninfari (Qudnuful)/clove chokali uku 5. Ganyen magarya ko garinsa 6. Ruwan khal tuffah ko white khal ko malt khal, Amma an fi son khal tuffah (Apple Veneger)/cedar Za a hadasu wuri Daya a dafa Su Su tafasa sai a sauke a juye a baho, in ya Dan huce yadda bazai cutar ba sai a Dan zuba ruwan khal din daidai gwargwado sai a shiga Ciki a zauna tsawon mintuna goma ko 15 sai a fito, kuma YAKAMATA a ce kin aske Gashin gabanki ta yadda ruwan zafin Zai sami damar penetrating in to ur Virgina's hole. Sannan ki bubbude cinyoyi Sbd ruwan ya shige ya ratsa, in kika fito sai ki zubar da ruwan da yamma ma sai ki kara Hada Wani ki dafa ki kara aikata haka, inshaaAllahu indai kaikayin Gaba ne ko zazzagiwar farji inshaaAllahu Zaki dace, sannan me fama da Warin Gaba ma Zata Iya amfani da wannan Hadin, haka me jin Zafi lokacin jima'i. MATSALAR BUSHEWAR GABA NA MATA DA KUMA KARANCIN NI'IMA (VAGINAL DRYNESS AND LOW SEXUAL PLEASURE) DA KUMA HANYAR MAGANCE MATSALAR A SAUKAKE Idan muka ce ni'ima to muna magana ne akan sha'awa waton (libido) a Turance kenan. Tana taruwa ne ga matan da suka balaga, masu koshin lafiya, walau budarwa ce ko kuma matar aure. Sha'awa halittace wacce ta banbanta daga wata mace zuwa wata macen. A lokacin da mace take jin sha'awa haka kawai ko sanda take karanta wani labari ko tinanin wani abu dake motsa sha'awa ko a yayin da ake gabatar da wasanni (fore play) kafin saduwa to idan dai har tana da ni'ima to zata ji duk ta jike dan wasu fararen ruwane masu yauqi zasu rinka fito mata. A lokacin ta riga ta kamu kenan wannan ne ake kira Natural lubrication ko Vaginal wet wanda idan har za a sadu da ita a lokacin to a shirye take. A hakika shima mai gidan zai yi matukar gamsuwa da ita. Bazata ji zafi ko ciwo ba saboda ta jika sosai ta yanda bata bukatar ayi amfani da wani vaseline ko ointment. To wadannan ruwan masu yauqi dake fitowa mace a sanda sha'awarta ta motsa to ita ke nuna alamun tana da ni'ima. Wasu matan sun fi wasu yawan sha'awa da samun ni'imar jiki dan yanayin halitta da lafiya, da ma abincin da suke ci ya sha banban. Wasu matan tun fil azal suna da ni'ima mai tarin gaske. Amma daga baya takan gushe sai su rasa sanin dalili. Hakan zai sa su tsunduma suyi ta neman kayan mata suna cusawa kansu abubuwa masu cutarwa duk da sunan ni'imarsu ta dawo. matsaloli da dama kan faru a sanadin haka. Akoi matsaloli da rashin lafiyoyi da dama dake haifar da gushewar ni'ima ga mata, wadanda suke bukatar bincike a maimakon haka mata da dama sukan yanke hukuncin cewa ai ciwon sanyi ne ke gare su alhali wata matsala ce ta daban. Akwai matan da basu da ni'ima a koyaushe gabansu a bushe yake ba wata ni'ima ko jin sha'awa. wasu matan sai sun shafa vaseline kamin a iya saduwa dasu. Hakan kan haifar da rashin samun gamsuwa musamman ga maigidan. Cushe cushen da mata ke yi da sunan matsi yana daya daga cikin abinda ke zuqe ni'imar mace ya haifar mata da bushewar gaba Musamman in abinda suke cusawar bai dace da Farjinsu ba, misali amfani da ruwan bagaruwa wacce tana matse fata amma kuma tana zuqe damshin dake ga wurin gaban mace, zai matse amma kuma zai kasance a bushe.To miye fa'idar yin haka kenan ? Maigida na saduwa dake amma yana jin kamar ana zoza mashi katako. wasu cushe cushen na haifar da cutukan gaba da kuraje da kaikayin gaba da irin wani wari wanda ke kanki sai ki rasa wanne irin wari ne? Dan an dauki wani abun na daban an tura a inda bai dace ba. Akwai magani Natural fruits da mata zasu iya rinka amfani dasu dan su karawa kansu shawa da ni'ima kai hattama da koshin lafiya. Kamarsu kankana ,ayaba, gwanda abarba, lemu ,timatir ,rake, dabino, kwakwa, dafaffiyar gyada, zuma ,nono, zogale, ridi, ruman cukwi(Nonon Rakumi), inabi, tuffa, zaitun, tafarnuwa, albasa, da dai Sauransu Wallahi wadannan duka sun fi duk wani cushe cushe ko kayan sha na mata da kuke gani amfani da kuma saukin saye. Zaki iya cin ayaba da dabino a yau. Gobe sai ki canza ki nemi kankana ki sha, jibi ki nemi dafaffiyar gyada ki ci, gata ki nemi zogale da albasa da quli quli kiyi datu/Kwadanta ki ci. sai kiga kina ta canzawa lokaci zuwa lokaci. Wallahi ina baki tabbaci idan kinka rike haka to ba wai ni'ima ba ko lafiya da fatar jikinki zaki ga tana canzawa. Amma an rungumi kayan maiqo da kayan zaqi da kayan yaji kawai ake ci dare da rana ana ta faman shan kayan mata da cushe cushe amma a banza dan ba sune abinda jiki keda bukata dasu ba ai dole shawa ta ja baya. Haka kuma zaki iya hada wadannan dan karin ni'ima da gamsarda mai gidanki. Amma akwai bukatar a kiyaye da tsabta. mata a daina cusa duk wani magani a cikin gaba wanda Bai dace da farji ba, farjin mace kaman ido yake baya son bako. A dinga tsarki da ruwan dumi amma banda sanya sabulu. A daina sanya pant da bai bushe ba. Idan an wanke to a rinka shanyawa har sai ya bushe. A ringa yi ana canza shi akai akai. Banda yin musanya da fatar za a kula. Ga wannan hadin sai a jarraba za a iya daukar daya ko biyu daga ciki ayi amfani dasu. 1-Qwai (Egg) da albasa da timatir, sai a soya amma kada a bari suyar ta kone. Banda sanya maggi da gishiri da yawa.zaki iya sakawa amma dan kadan ake so. Namiji zai iya ci hakan zai kara mashi da yawan ruwan maniyi. Za a iya neman garin dabino da ruwan kwakwa sai a dama a rinka shan cokali biyu manya chokali safe da yamma. KARIN NI' IMA═ "Yan mata ya kamata kusan mene yake kone muku fadamarku kafin jika lambunku da ruwan taimako! Kisani babbar lillah ce kice ke baki da sanyi ajikin ki wannan abinda bazaiyuba ne sannan baki shan magani da neman sa wannan jahilci ne anan inaso ince sanyi shine musabbabin kowace chuta ajikin dan Adam haka annabi ya fada hk km binkicen kowane sashi na binkeci ya nuna. Saidai sanyi ya rabu izuwa kasu dayawa dan bazan ace ga adadinsaba amma sanannu guda 2 ne wato sanyi na maza dana mata ackn 2 akwai kashe kashe misali sanyin mara sanyin daji sanyin laka sanyin hakori sanyin qashi sanyin dubura. Sanyi yana da siffa kala kala ya danganta da larurar data kawoshi mu anan zamu dau sanyin mara wanda shi ke kawo bushewar niimar mata. Abubuwan dayake janyo sanyin Mara ~1 samu daga miji mai namijin sanyi ~2 yin tsarki da ruwa me sanyi ~3 zama a inda danshi ko raba take ~4 yawan shan abu me sanyi sosai ~5 rashin kula da al'aura ~6 sanya yatsa ackn fari ~7 gada daga mahaifa ~8 yawan zama a turbaya ~9 yawan tayarwa da kai sha'awa ~10 rashin abinci me gina jiki Wadannan sune abubuwanda samuwar su duka ko mafi yawa dg ckn su yakan jawo gushewar ni'ima_ magani ~Kankana Kaninfari ~Zuma ~Tafarnuwa Wannan hadin bashi da bukatar a hada da yawa daidai yanda za a iya sha za ayi kuma sau daya ake sha a rana har tsawan sati 2 wato kwana 14 Za a sami kankana ynd ake da bukata ko a yanka ko burgeta a blander duk dayane sai asami dakakken kaninfari chukali daya na yara azuba sanan zuma karamar roba a zuba duka ack sannan tafarnuwa danya adaka guda 4 in qananuce in babbace kwalli 2 ko 3 ta isa faffasata za ayi ta dandaku sai azuba a bashi kamar minti bakwai 7 sai asha kenan za a iya hadawa bayan angama cin abinci sai ashanye gaba daya. In akabi doka to za a zauna lfy Allah kasa mudace! MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [8/26, 7:29 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA ARABA'IN DA TARA_ *____________________________* GYARAN JIKIN AMARE DA UWARGIDA Amfanin Garin Hulba Don Gyaran Jiki Gyaran Fuska. Za ki samu garin hulbar ki dama da madara da zuma ya damu sosai sai ki shafa a fuskar ki, ki barshi kamar minti talatin kafin ki yi wanka, fuskar ki zata yi sheki zai kashe miki pinples ya gyara miki fuska. BAMBAMCIN MACE MAI DADI DA MARASHI: Maza da yawa suna tafka muhawara akan shi mata suna da bambamcin dadi a wajen jima'i kodai dukkaninsu haka suke. Wasu sunce duk abun iri daya ne. Wasu kuma suce sam da akwai bambamci. Gaskiya ne mata sun bambamta a dãɗi na jima'i. Sai dai kuma wannan dãɗin ba abune da ake haifar mace mai dãɗi ko mara dadi ba. Ita macen ce take maida kanta mai dadi ko ta zama mara dadi. Akwai wasu mahimman abubuwan da suke sa mace tayi dadi ko kuma akasin hakan. Waɗannan abubuwan idan mace ta sansu, ta iya su kuma tana yinsu dole ne mijinta yace tana da dadi. Idan kuwa bata yinsu bata sansu ba to irin waɗannan matan ne maza suke kira da suna jaka. Sai dai kuma ba duka abubuwan dake sa mace dadi ake samu daga gareta ba. Akwai wasu daga shi mijin nata suke wanda idan babu su a gare shi to babu dãɗin da zai ji duk lokacin da zai yi jima'i da matarsa. Ga wasu abubuwan da suka bambamta mace mai dãɗi da marashi. 1: Soyayya - Duk yadda mace take muddin babu soyayyarta a zuciyar mijinta ba zai taba jin dãɗin ta ba ko sau nawa zai kwanta da ita. Don haka danƙon soyayya a tsakanin ma'aurata yana kara sawa namiji yaji dãɗin matarsa a lokacin jima'i. 2: Shauƙi: a lokacin da namiji ya kamu da sauƙin son yin jima'i da matarsa a wannan lokacin yana samu jin dadi na musamman idan yana saduwa da matarsa. Ba kamar lokacin da bai da sha'awar yi ba amma aka nemi yayi. A lokacin da namiji da kansa yake cikin bukatar matarsa a wannan lokacin idan zai yi jima'i da ita yafi jin dãɗin ta. 3: Tsafta-duk yadda miji yake son matarsa kuma yake da shaukin son yi jima'i da ita idan batada tsafta zai dai biya bukatarsa ne amma ba wai saboda yana jin dadi ba. Matan da suke barin gaban su babu tsafta ko bakin su, hamata da sauran lungunan jikunansu babu tsafta. Irin waɗannan matan namiji ba zai taba jin dãɗin yin jima'i dasu ba sai dai kawai ya biya bukatarsa amma ba domin yaji dãɗin ta ba. Ita mace mai tsafta bayaga dãɗi da take sawa mijinta yaji, ta kan kuma sashi a kullum yaji ya kamu da son yin jima'i da ita. 4 :Ni'Ima- ba kowace mace take da ni'ima ba. Wasu matan gaban su a bushe yake karas. Wasu kuwa a jike yake cakaf. Yawan ni'imar gaban mace yana karawa namiji jin dãɗin ta sosai a lõkacin da yake saduwa da ita. Wannan yasa maza da dama suke danganta mace mai yawan ruwa a gabanta itace mai dadi. Shi dai ni'imar gaban mace ba wai halitta bace wanda za ace wata an halicce ta dashi wata kuwa haka Allah Ya yita kandas. Duk mace tana iya samarwa kanta ni'ima idan tana bukatar yin hakan. Saboda akwai abinci da abubuwan sha da suke sa mace ta samu ni'ima da kuma masu kara mata idan tana dashi. A lokacinda namiji yake saduwa da mace mai ni'ima wannan ruwan gaban nata yana kara taimakawa wajen samun sauƙin shige da fita da azzakarin sa ke yi cikin farjin matarsa. Wanda hakan yake samar masa da wani dadi na musamman a lokacin jima'i. Sabanin macen da gabanta yake bushe. Wanda maimakon ta samar da ɗaɗin tana ma iya jin ciwo a gabanta kuma ta jiwa mijin nata shima. Mazan da matan su suke da bushenshen farji fatar jikin azzakarin su yana iya sullubewa ya daye saboda rashin samun ruwan da zai rika taimakamawa wajen shiga da fita. Wanda ita ma gabanta zai iya yin jini kuma ta rika jin zafi idan ana saduwa da ita saboda rashin ni'ima a jikin ta. Don haka mace mai ni'ima tafi mara shi dadi a jima'ince. 5. Iyawa- Macen data iya jima'i na kwarai ta kuma saki jiki tafi sabuwar shiga 'yar koyo dadi a jima'ince. Domin ba wai kawai a zura azzakari cikin farjin mace bane kaɗai zai samarwa maigida dãɗi dake kunshe cikin jima'i. Da akwai wasu sinadarori da ake hadawa dasu kamin mace ta samarwa mijinta hakikanin jin dãɗin jima'i. Waɗannan abubuwan kuwa suna hada kamar haka: I: Iya wasannin motsa sha'awa. Macen data iya wasanni da mijinta ba zata taba yin daidai da wacce bata iya ba. Don haka muddin mace ta san abubuwan da mijinta yake son a masa a lokacinsu na wassanin motsa sha'awa dole ne a wannan jima'in ta jiyar dashi dadi. Ii: Iya yanayin kwanciyar jima'i - dole mace ta iya yin yanayin kwanciya na jima'i daban daban idan har ta son mijinta ya rika jin dãɗin ta. Kowani namiji yana da yanayin daya fi so matarsa ta masa a lokacin jima'i. Muddin kuma bazaki iya masa wannan ba babu yadda za ayi yaji dadinki. Iii: Tsukewa da sakewa- akwai wasu mata yadda aka shege su haka nan suke sakin gaban su ba tare da sun daidaita shi yadda azzakari zai iya samun daidaito a cikinsu. Macen da take da faffadar farji, yana da kyau a lokacin da maigida ya shigeta ta tsuke farjinta yadda zai matsai azzakarin mijin a ciki. Haka kuma idan karamar gaba ce da ita sai tayi kokarin kara bude kafafuwanta domin baiwa azzakari damar gudanarwa. Wannan yanayin na tsukewa ko matsai farji a lokacin jima'i, yana samar da ɗaɗin na musamman ga namiji. Ba kamar macen da zata saki komai yadda yake ba. Iiii: Sumbatu: Yana matukar karawa maza jin dãɗin jima'i sosai amma akasarim mata basu da masaniyar hakan. Sumbatu musamman na kwarzanta mai gida ko masa koke koke na kissa da furta wasu kalamai na batsa suna da matukar tasiri a lokacin jima'i. Domin suna samar da jin dadi na musamman a yayi jima'i. Ba mace ta yi gum bata cewa koma ba. Iiiii: Tallafawa. A lokacin jima'i ba wai namiji bane kadai mace zata bari yana gwatso ba. A duk irin yanayin kwanciyar da zai baiwa mace damar ta motsa jikinta, to idan zata tallafawa maigida wannan ma yakan samar da jin dãɗi maimakon mace bata motsi na yi kamar gawa. Waɗannan sune wasu mahimman abubuwan da zan iya kawo su a fili da suke sa namiji yaji dãɗin jima'i da matarsa. Kuma sune suka bambamta mace mai dãɗi da mara dãɗi. RASHIN GAMSAR DA UWARGIDA / AMARYA INA MAFITA A kullum na duniya maza ma'aurata suna saduwa da matansu, sai dai kuma abun tambaya anan shine, maza nawa ne suke iya gamsar da matayen nasu a lokacin da sukayi kwanciyar ta jima'i? Maza nawane magidanta suke da illimin sanin yadda zasu gamsar da matansu..? Ko munki ko munso babu yadda zamu kaucewa magana a kan jima'i domin shine ginsheken zaman aure kuma yana cikin manyan lamuran da kan iya sa a samu zaman lafiyan ma'urata ko akasin hakan. Yana da kyau da kuma mahimancin maza su fahimci cewa, duk wata mace tana sha'awar ganin cewa mijinta yana matukar gamsar da ita yayin da suka yi kwanciya ta jima'i. Sai dai kuma abun ban haushi maza da dama suna dauka cewa gamsar da mace a jima'ince shine saduwa da mace da karfi ko kuma da mugunta ko jigatata shine zai iya gamsar da mace. Mafiya yawan maza basu da illimin sanin cewa mace takan dauki lokaci mai tsawo kamin ta kawo, kai duk da yake da akwai wasu matan da suke yinsa cikin karamin lokaci. Don hakane yake da kyau maza su gabatar da wasanni ga mace kamin su afkamata. Kamin mace ta kamu, dole ne sai an tattabamata wasu wurare ta hanyar sumbata, wasa da nonuwanta, gabanta da makamantan su. A wannan lokacin ne mace jinin jikinta yake bin ko ina a jikinta daga nan kuma sha'awa ya motsomata harta nemi bukatar mijinta. Mundin namiji ya jefa matarsa cikin wannan yanayi zai ji dadin yin jima'i da ita haka kuma ita kanta matan bazata yi koken rashin gamsuwa bayan an gama ba. maza masu murza matayensu a lokacin wasannin motsa sha'awa, mazane da suke sa matansu gamsuwa da zuwan kai cikin sauki kuma akai akai. Kada kayi gaggawar shigar matarka, ka tabbatar ka dauki lokacin kamar mintuna 25 zuwa 30 kana wasa da ita har sai lokacinda tayi laushi da kanta tana bukatar ka shigeta. Mata da dama dai sukanyi sha'awar gani mazansu ne ke tubesu da kansu a lokacin da ake tsaka da wasan, yadda kuma a yayin wasan kana tube mata kayan dake jikinta daya bayan daya kamin kashiga wasa da muhimman wuraren dake motsa mata sha'awa. Da yake bazan yi bayani dalla-dalla na yadda ake wasa da mace da kuma wuraren da ake wasan dasu ba a wannan fagen, yanada kyau maza su fahimci cewa ko wace mace da inda ke tayar mata da sha'awarta. Wata da zaran an soma shan bakinta sha'awata ya motsa, wata kuma wasa da gabanta, wata murza kan nonuwanta watama kunnenta kawai za'a taba ta fara d'iga, dole ne kowani magidanci ya fahimci meke tayarwa matarsa sha'awa a lokacin wasanni. Mahimmancin wasa da mace kamin soma jima'i shine, zai sata ta soma fitar da ruwa wanda ruwan yana taimakawa shigar azzakari cikin farjin mace da sauki. Haka kuma yana taimakawa mace tayi zuwan kai cikin sauki ba tare da ta dau lokaci ba. Girman azzakari, ko tsayinta bashi ne abu mafi mahimmanci ba a wajen mace, abun da kawai yake sa mace ta samu zuwan kai da kuma gamsuwa a yayin jima'i, shine yadda aka motsa mata sha'awarta a lokacin da ake wasa da ita shine abunda yake sata nan take ta samu zuwan kai da kuma gamsuwa irinta jima'i. Babu saduwar jima'i mafi dadi wajen mace irin tayi zuwan kai lokaci guda da mijinta, wanda bincike ya nuna cewa maza 100, 30 ne kawai suke iya yin zuwan kai lokacin guda da matansu, hakan kuma yana samuwa ne ganin yadda suka lakanci jima'i da matan nasu. Shi dai zuwan kan 'ya mace, shine kololuwarn jindadin kwanciyar jima'inta, kuma shine yake jawo gamsuwarta a jima'ince, don haka da zaran wasu matan sun samu gamsuwa to sha'awarsu ta jima'i kuma ta kare a wannen lokacin, duk kuwa da wasu matan da ake samunsu suna iya zuwan kai kamar sau biyu zuwa biyar a kwanciyar jima'i guda, hakan yana danganta ne da irin halittan macen da kuma yadda mijinta yake sarrafata a jima'ince. Shi dai zuwan kai 'yan mace ba kamar na miji bane, domin shi namiji idan yayi zuwan kai abune da ake iya ganinsa a zahiri saboda yadda maniyi yake fita daga azzakarinsa. Wasu na daukar cewa, ruwan dake fita daga gaban mace a lokacin saduwa da ita Ruwa iri biyu ne yake fita a gaban mace a lokacin da ake wasa da ita wani ruwa mai yauki ne yake soma fitowa, wanda yake alamta cewa ta soma kamuwa kenan, haka kuma idan ana saduwa da ita kuma da akwai wani farin ruwa wanda yafi kama da madara shima yana fita daga gabanta, shima wannan bashi ne alaman mace tayi zuwan kai ba. A lokacin da mace tazo kawowa, a wannan lokacin kamanninta sukan canza, numfashinta yana yawan bugawa da sauri, haka kuma jinin jikinta guduwarsa na karuwa sosai haka kuma jijiyuyin jikinta zasu kara bayyana yayin da zata yi wani kara ko kuka ko fadan wata kalmar dabata sanshi ba a yayi zuwan kan nata, haka kuma mata da dama suna kankame mazajensu a lokacin da suke zuwan kan. Da akwai yanayin kwanciya na jima'i da yake taimakawa mata domin yin zuwan kai cikin sauki a lokacin jima'i, sai dai kuma ganin babu dama da zamu kawo komai da komai a wannan anan nake baiwa ma'aurata su nemi ilimin jima'i Sai dai kuma kamin wannan lokacin, ya kamata maza su fahimci cewa da akwai illa ga duk namijin da bazai iya gamsar da matarsa ba a jima'ince, don haka ne nake bada shawara ga maza su nemi sanin illimin yadda zasu iya sarrafa mata MATSALOLIN MA'AURATA KAN SOYAYYA: Akwai wasu abubuwa da suke canja soyayya bayan aure sai ka ga an sami canje-canje, da ana soyayya kamar a hadiya juna amma da zarar anyi aure bayan lokuta kadan sai ka ga soyayya ta canja. Akwai dalilai da suke kawo hakan gasu kamar haka: 1.Rashin yin aure dan Allah ko kuma an gina soyayya akan karya ko anyi aure dan samun wani abun duniya sai kuma aka rasa. Sai ka ga ana canjawa juna fuska. 2. Rashin abubuwa guda 5, akwai wasu abubuwa guda biyar sune manyan bukatu na dan-adam ba a dakin aure ba koda a gidan kurkuku yake yana bukatar abubuwa 5 a duk inda yake dole ne a samawa mace su in ko ta rasa su to baza ta iya zaman aure ba kuma yanzu soyayya zata canja zuwa mummunan yanayi. Gasu kamar haka: -Samarwa mata da abunci -Bata suttura -Kula da lafiyar ta -Bata tsaro -Samarwa mata da mahalli. Abunci, suttura, muhalli, tsaro da lafiya su zama dole a kulawa mace su da zarar an rasa su sai kaji ana kace nace tsakanin ango da amarya. Masu iya magana suka ce abu uku basu haduwa a azauna lafiya, suka ce ango da amarya da kuma yunwa. 3. Gina aure akan sha’awa. Da zarar an gama rayuwar angwanci karsashin sha’awa ta gushe sai ka ga an canjawa juna fuska. 4. Wasu canje janje da suke shafar mace bayan tayi aure. wato kamar lokacin hailar mace kan jin dan damuwa da kunci, hakan kanshafi zamantaker aure. (samunciki da goyo )suma kan takurawa mace ta ji damuwa har hakan ya shafi zamantakewar ta ta aure. 5. Rashin bawa samari da ‘yanmata cikakken bayani da sirrin rayuwar aure tunkafin suyi aure. 6. Rashin daukar aure amatsayin ibada. 7. Rashin kwanciyar hankali,imma daga ‘yan’uwan miji ,uwar miji. Kashj 95% na matsalolin ma aurata bayan aure wadan nan matsalolin ne na sama. Taya za a magance su? Kada ayi aure har sai an cika sharudan shari’ah kamar samun sana’a,iya samar da mahalli, abunci, suttura, lafiya, tsaro. Yin aure dan Allah da daukarsa a matsayin ibada kamar sallah, azumi. Bawai zaman hutuba dole ne a ware cibiya ta musamman mai wayarwa samari da ‘yanmata kai akan harkar zamantakewa akan hakkin ma’aurata da yadda zamantakewa take. Yana da kyau maza su san cewa mata masu ciki ko haila suna dan samun canji a jikin su dan haka ana hakuri da su a lolacin. Wace ce Mace? Mace dai ta kasance tamkar wani furen fulawa. Wanda idanun mutum suke sha’awar kallo a koda yaushe, ita fulawa ta kasance abu ce mai kamshi. Haka bayan kyawun kallo, tana da bukatar kasancewa a cikin inuwa, domin idan aka sanya ta a rana za tayi yaushi. To tamkar haka mace kan kasance a wajen sanyaya zuciya, da sanya farin ciki a zuciyar abokin rayuwarta. Wannan kuma tun ran gini tun ran zane, domin kuwa mace, tun tana ‘yar karamar yarinya ta kasance mai kokarin son yin hidima ga wani, domin hatta wasanta na yarinta ba ya wuce na kula da jaririyarta (‘yar baby), ta kara ce, ko ta roba. Tare kuma da son taya mahaifiyarta aikin gida. Kuma a gaba haka za ta kasance har bayan ta girma tayi aure inda take zama rumfa, kuma ta zama garkuwa ga dukkan mutanen gida ta hanyar sadaukar da rayuwarta domin ta faranta masu da haskaka masu hanyar rayuwa. Wannan ya ta’allaka tun daga mijinta da ‘ya’yanta da dangin mijinta da makotansu. Za ta kasance cikin hidimarsu ta yadda takan kasance tamkar wata baiwa wadda ita ba ta ma san wani abu jin dadi ba. Haka za ta rika gudanar da hidima ga iyalinta, kowa ya riga ta kwantawa domin yin bacci, kuma ta riga kowa tashi don ta share masu fagen fara rayuwa a wannan sabuwar rana. Da irin haka kuruciyarta za ta tafi cikin hidimar gyaran al’ummarta, kyawunta da kuruciyarta da karfinta da komi nata a hankali haka za su gushe amma ba ta damu ba, manufarta daya ce rak wato sanya wa kowa farin cikin rayuwa da mika su zuwa ga ingantacciyar rayuwa har su kai ga burinsu. Mace duk a cikin wannan tashi fadin da take yi abu daya kawai take nema wato shi ne a nuna mata kauna da soyayya ta gaskiya ba tare da an ci amanarta ba ta kowace fuska. Allah sarki, mace ke nan, baiwar Allah. Sai dai hakan yana gagara a wajen da yawan mu maza. Yayin da wasun mu suka dauke ta wata abu kawai ta biyan bukata, wacce ba ta da wani gata da daraja illa kawai ta biya wa mutane bukatunsu, ta gusar musu da sha’awarsu. Wannan ya yi kama da yadda aka dauki mace a zamanin jahiliya. Yayin da su kuma Turawan yanzu suka dauki mace a matsayin wacce za ta kure kyawun fuskarta, ta bude adonta da wasu daga cikin ni’momin da Allah ya yi a gareta, kawai domin jama’a su gani su yi dariya, su ji dadi, akan haka suka mai da ita ‘yar aikin banki, ko kuma yar aikin shaguna, ko ‘yar fim. Koma mai watsa shirye-shirye a cikin tashoshin talabijin, ko ta watsa daddadar muryarta a cikin rediyo jama’a suna saurare. Ko ma ta koma wacce za a saka hotunanta a cikin abubuwan sayarwa, ta rika kwaye tsiraicinta tana fitinar al’umma da kyawun surarta, tana sayen fushin Allah ga kanta da sauran mutanen duniya. Su manufarsu kawai ita ce, domin ta janyo musu kasuwa ga abin da suke sayarwa, ita kuma ta nemarwa kanta mummunan karshe tun a nan duniya. Wacce za ta hadu da azabar Allah a gobe kiyama, ta kasance daga cikin makamashin Wuta. Allah ya tsaremu. Yayin da shi kuma addinin gaskiya na Musulunci tun farkon zuwansa ya karrama ta, ya ‘yantar da ita, ya ba ta hakkinta tamkar namiji wajen samun sakamako a kan wahalhalunta tun ma a nan duniya. Mata ku gode wa Allah a kan zuwan addinin Musulunci, kuma ku gode wa Allah idan har ya hallicce ku Musulmai, ku bi Allah, ku bi sunnar Annabinsa, ku yi koyi da iyayen Muminai domin ku shimfida rayuwa ingantacciya. Kuma ku samar da ‘ya’ya na gari, ku ba su tarbiya ta gari, a karshe su zama jama’a ta gari, a samu shuwagabbani na gari da ma’aikata na gari, ko ‘yan kasuwa na gari, ko malamai na gari. Kun ga dalilin ku sai a samu al’umma ta gari. Allahu Akbar!Mace ta gari ta sa duniya duk ta zama ta gari. Su kuma maza ku lura da yadda addininmu ya karrama mace, ya ba ta girma da daraja, wanda shi ne dalilin da ya sanya muka dauke ta da daraja. Mu yi nazarin rayuwar Annabawa, da salihan bayin Allah, yadda suka yi zamantakewarsu da matansu suka yi hakuri da su suka faranta musu rayuwa, suka nuna musu soyayya ta gaskiya ta tsakani da Allah. Idan muka yi nazarin a kan wadannan abubuwan za ku sauke nauyin da Allah ya dora muku a kan mata. Kuma idan aka tambaye Ku a kan abubuwan kiwon mu wadanda mata suna cikin su, to, a nan za mu bayar da amsa muna masu farin ciki da jin dadi. Annabin (S.A.W.) ya ce, dukan ku masu kiwo ne, kuma za a tambaye ku a kan abin da aka ba ku kiwo a kansa. Lallai magabatan mu sun yi adalci wajen nuna girman ‘ya mace, kuma sun nuna matsayin ta da sadaukarwar ta. A karshe, Allah ya sa mu kasance masu riko da gaskiya ba son ran mu ba. RAYUWAR AURE [GABOBIN JIMA'I NA MACE] GABOBIN JIMA'I NA MACE 1 DUMBARU BIYU MANYA: dumbaru manya wata tsokar nama ce mai kauri da dan tudu, wadda gashin gaba yake tsira a kanta 2 DUMBARU BIYU KANANA: su wadannan suna gefe manya dunbaru ne daga ciki, suna kankancewa su rika kare wa a hankali har su hade da yar fatar da take tsakanin kofar farji da kofar bahaya 3 BELI: beli shine wasu wasu suke cewa dan tsaka shi kasancewa ne a tsakiyar farji mace gaba da shi daga kasa kofar farji take. Beli yana gugar kan zakari a lokacin da yake kan hanyarsa ta shiga kofar farji, wanda hakan yana kara takalo sha'awar namiji kuma ya dadawa saduwar jima'i armashi Beli shine sashe da yafi jin tabi a jikin mace haka kuma suma dunbaru kanana suna da irin wannan jin tabin amma ba kamar na beli ba. Abin da ake nufi da jin"tabi" shine: idan ya shafi wani wuri a jikin mutum zaiji tsigar jikinsa duk ta tashi yaji kuma ya kamu sosai da sha'awar jima'i sabanin wasu wuraren dasu in an taba su ko ji ma mutum ba zai yi ba. Misali, duk namiji da aka shafa wa zakari ko dan kan nononsa zaiji ya kamu da sha'awa sosai nan take, haka kuma duk macen da aka shafi farjinta dole ne ta ji ta kamu sosai. sabanin idan aka shafi hannunta ko hannunsa ko da dai in an dade ana shafa zai kamu ko ta kamu amma ba kamar idan an shafi wuri mai jin tabi sosai ba. kuma shi "jin tabi"karfinsa ya bambanta daga wuri zuwa wuri, a jikin mutum. MISALI; a wajen namiji kan zakarinsa yafi ko 'ina a jikinsa jin tabi haka kuma jikin zakari yafi kan mara jin tabi haka mara kuma yafi kan nono, haka dai har zuwa karshe. A wurin mace kuma beli yafi kananan dunbaru jin tabi, su kuma sun fi manyan dunbaru manyan dunbaru kuma sun fi maranta jin tabi, haka dai har zuwa inda sam ma shi ba yaji tabin. Ana samun wasu mata da ake yanke wa dunbarunsu kanana biyun da wani bangare na beli, koma duk biyun da sunan ka ciya yin jima'i saboda wadannan sassa biyu, suna daga cikin manya-manya gabobin motsa ko kuma tsokar sha'awar jima'i. BELI; yana mikewa kamar yadda zakari namiji ke mikewa idan kuma ya mike, yana fin tsawonsa na kafin ya mike, har sau daya da rabi kuma shi beli ya dan dago sama kadan, ya dan matsi kofar farji, saboda a samu saukin gogayya tsakaninsa da zakarin namiji akwai wani ruwa, mai maiko-maiko da yake nasowa daga tsakanin fatar beli. Idan ba a tsaftace shi yana daskarewa a kan belin, wani lokacin ma yana zama kamar bawo-bawo. Kuma mafi yawancin warin da ake ji farjin mata na yi, yana samo asali ne daga wannan maiko-maiko da yake nasowa daga beli. Amma idan ya zama bai yi yawa ba, har ya zama wari to kanshin yana kara ta da hankalin maza. Saboda haka, ya kamata mata su rika tsaftace wannan maiko-maiko na beli a ko da yaushe. ZAKARI : tsawon zakari in yana zaune lafiya bai cika wace"centmeter"9-10 ba. Amma idan ya mika yakan kai"centmeter" 10-16. Wannan shine tsaka-tsaki amma ana samun wanda yafi haka ko wanda ya gaza haka abin ya bambanta daga wani namiji zuwa wani. Wurin da yafi ko'ina jin dadin tabi, a jikin zakari shine kansa. Musamman can kololuwar inda yayi tsini-tsini, wato wajen kaciya, a yayin da zakari yake a kwance, ba zai iya yin aikinsa ba yayin jima'i amma idan ya mike, a sannan ne zai iya yin aikinsa har maniyi ya shiga farji, idan zakari ya mike yakan danyi kasa-kasa daga baya, saboda yayi daidai da tankarewar farji da karkatawarsa zuwa gaba kadan domin ya cika farji sosai. A wurin wasu mazaje tunanin jima'i ko kuma ganin jima'in ko ganin wasu bangarori na mace, wani lokacin ma ko na namiji ya isa ya sanya zakarinsu ya mike wadannan sune mazaje masu cikakkiyar lafiya amma wasu zakarin nasu, baya mikewa sai mace ta kama shi ta mulmula MANIYI; ruwa ne fari mai kama da madara kuma yana da yauki da danko. Yana fitowa ne daga zakari namiji idan ya kai kololuwar sha'awa yana fara samuwa ne a jikin namiji, tun yana saurayi har tsufa, haka kuma yana da wasu 'ya'ya a cikinsa wadanda sune ke zama 'yan tayi daga karshe su wadanan ya'yan na maniyyi suna da kai da kuma wuya da jela wadda da ita ne suke yin iyo cikin ruwan maniyyi, idan namiji ya zuba shi a farji mace , har su kai ga kwan ita mace. daga karshe yana da kyau mu san cewa duk 'ya'yan maniyyi da namiji ya zuba wa mace, dukkansu mutuwa sukeyi, sai daya ne kawai yake saura ya hadu da kwan mace, ya zama halittar mutum A kowanne jima'i kuwa namiji yana zuba wa mace tsakanin 'ya'yan mani miliyan dari biyu zuwa miliyan dari biyar amma duk sauran da suka mutu suna fita ne da fitsari ta farji mace. JIMA'I: dukkan nau'o'in shafe-shafe, da saduwa tsakanin namiji da mace, jima'i yana farawa a lokacin da namiji ya shigar da zakarinsa cikin farji. DAN QARIN SHA'AWA INGATACCIYA DA NI'IMA MAI DOREWA kisamu kankana mai kyau kifere samanta kawai seki caccaka cikinta sannan ki samu kwakwa kallo daya ki gurzata ki zuba aciki duk da ruwan saiki saka garin dabino da garin kanumfari saiki rufe kibarshi ya yini saiki zuba madara peak da zuma ki gaurayayshi sosai seki shanyeshi duka in bazaki iya sha atakeba zaki iya rabawa biyu. . kisamu aya danye da dabino kicire kwallayen saiki samu danyen zogale da kwakwa da kanunfari da kankana inzaki samu kisa cukwui aciki seki markadasu bayan kin markada seki zuba nonon rakumi da mazar kwaila kisha. JAN HANKALI GA MAI MATSALAR BUSHEWAR FARJI SIRRIN BUSHEWAR FARJI. _ar'uwa ga dama ta samu, idan kina fama da bushewar farji, a koda yaushe to sai ki sami man zaitun da man habbatussauda, sai ki hada su wajen daya, ki dinga shafawa a cikin farjinki insha Allah Zaki ga biyan bukata, domin kowace cuta tana da magani, sai dai in baki nema ba, amma in kika nema Zaki samu. Allah ta'ala yasa mudace. ZUCIYAR ZAKARA Nasan abin zai bawa mata mamaki da tsoro, toh baza ki sha mamaki da tsoro bama sai kin aikata kinga sakamakon sa. Wato zaki samu Rikakken zakaran kazar Hausa ne sai ki yanka shi da nufin kin bawa Allah jinin, Sai ki gyara wannan zakaran ki cire zuciyar Zakarar ki shanyata a rana a gu me tsafta yadda zata yi saurin bushewa, naman kuma ko ki ci ke ba yara ko ki sadakar duk dai yadda kk o Idan zuciyar zakaran nan ta Bushe, sai ki dakata a cikin turmin da ba yaji ko wani Abu me kama da haka, ki dakata ta dawo gari, sai ki nemi zumarki Farar saka me kyau, ki tabbatar Zuma ce ta gsky ba ta choge ba, sai ki kwa6a ki dinga lakuta kina matsi na awa uku sai ki wanke, kina iya kwa6awa ko da man zaitun in zumar zata baki wahala, in baki samu man zaitun bama zaki iya kwa6awa da Baby Oil, Amma fa gaskiya da Zuma yafi bada Ma'ana, in har bata samu bane to sai ayi da wanchan. Idan kika kwa6a zaki lakuta da yatsarki manuniya ,da fadin bismillahi Wa Rafa'anahu Makanan Aliyya ki Ambaci sunansa sau 3 sai ki matse kawai, baza ki wanke ba sai bayan awa uku, toh daga nan kin matse kan gogan naki, Hmmm zaki ga sokonci a gado, idan mafadacine kuma zakiga ya rageyawan fada da gaddama, idan marowacine me hanun "yan Dambe kuma zai ware miki hannunsa, idan me 6oye kowanne sirrinsa ne baya Barin ki San komai toh zai fara su6utar baki, yana gayamiki abinda zaki sha mamaki da ya gayamiki domin bai saba fadan sirrinsa ko shawara da ke ba. Nidai kullum fatana zaman Kauna da soyayya tsakanin mata da miji, ba gaba ba Cuta ba cutarwa, Ubangiji Allah ya dawwamar da matayen Aure zaman Farinciki a gidajen mazajensu." MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SADIYA...✍️ [8/28, 11:27 AM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA HAMSIN_ *_____________________* Haajar tace "to kin dai ji? Wannan a tak'aice kenan." Sannan ta d'ora da yi mata fatar alkhairi da rayuwa mai inganci a rayuwar auren ta. Wani irin nannuyan ajiyan zuciya suxee ta sake tare da cewa "wai duk wannan godon sharhin a tak'aice kenan anty Haajar?" Haajar tace "eh mana! Ai sai dai mu taqaita amma ba wai mu gama ba" suxee tace "cabdi. Lallai ma Anty. Ni kam ai ba dika na iya rik'e komai ba. Sai dai duk ranar da bangane wani abun ba in kira ki a waya kimin bayani" Haajar tace "oh! Saboda ni kuma banda aikin yi sai na gyara auren Barr. Na wa mijin fa?" Suxee na dariya tace "kai Anty Haajar. Ai Ku kun tsufa" Haajar tace "furfura ce ta cika mana kai da k'yeya Dan tsufa". Dikkan su suka saka dariya. Daga nan suka fara kewar junan su. Tashi Haajar tayi ta d'auko dafaffen 'yan shila guda biyu data dafawa suxeen na yau. Dan kusan tun saura wata d'aya bikin a sati Sau biyu take dafa mata, yau idan aka dafa 'yan shila to idan za'a sake yi budurwar kaza zata dafa mata. Kusan yanzu shine abincin suxeen, Dan ba ta iya cinye d'aya lokaci d'aya sai dai a kwana biyu. Saura sati d'aya bikin biki ya kama ka'in da na'in. Su Haajar ba zama wai an saci d'an b'arawo, Dan ita daddy ya mallakawa komai na bikin ,ya bata wadatattun kud'in da yasan za su iya ayi komai cikin wadata. Haajar d'in ce zaune a sashen Hajiya su na ta tattauna yadda tsare-tsaren bikin ze kasance. Haajar tace " cabdi! Aikuwa kudin hannu na sun kusa k'are wa bari inje in samu daddy tun kafin ya fita". Daga haka ta mik'e zata fita. Hajiya tace kin ga dawo ki sallami wa'yannan bayin Allan. Dan yunwa suke ji ta fad'a tana nuna su Hassan dake kwance a gefen ta suna wasa. Haajar tace "Hajiya wallahi kk d'azu sai da na basu suka sha. Kawai tsabar ba za su bar ni in sake bane". Hajiya tace " dawo dai ki ba su. Idan aka bakki da shi ya zaki yi da shi? Ke kan ki kaya zai zama miki." Haajar ta dawo tana fad'in "Allah idan Ku ka sha yanzu sai bayan biki ko zaku sake shan wani" Hajiya tace "da haka ai to da yaye su kika yi sai ki huta. Naga yaran nan ma ba su wani damu da shan mamma ba ,kina gani fa yadda suke shan madara ,to da ke suke zuk'a haka ya kenan?" Haajar tace "Cabdi! Hajiya ai sedai madarar". Zama tayi ta basu sannan ta ajiyewa Hajiya su suna ta faman wasar su. Dan yaran ko kad'an ba suda fitina. Ga shi yanzu har zama suke yi sun k'ara wayo sosai. A d'aki ta samu daddy kwance a kan gado yana danne-danne a na'urar shi mai k'wak'walwa. Tausa masa k'afa ta fara yi tana fad'in " Sannu da aiki mijin Haajar " murmushi daddy yayi tare da waigowa ya dube ta sannan yace "yauwa Matar daddy". Hayewa tayi kan gadon tayi filo da bayan shi tare da cewa " gaskiya ina matuqar kewar mijina" daddy ya kamar jira yake yace "ai duk yadda kike kewa ta baki kaini ba" tace "inji wa? Ai ina ganin ma na fi ka" yace "shiyasa na ga kina guduna ai a 'yan kwanakin nan. Ina gefe an maida ni hoto" dariya Haajar tayi tare da cewa "Lah! Ka ji daddy wai an maida ka hoto. Ni ba wani gudun ka da nake yi kawai dai sha'anin biki ne. Amma idan aka gama hankali ya kwanta ai se a cigaba daga inda aka tsaya". Waro ido daddy yayi yace "yanzu kina nufin har sai bayan biki sannan zan dawo miji? Dan dai kam yanzu dani da fanko bamu da banbanci". Dariya Haajar ke yi masa tace "ni dai ba wannan ba. A ajiye wannan batu a gefe" yace "to fad'i Wanda ya kawo ki" Haajar tace "da ma Dan Allah kud'i zaka d'an k'ara mana ko ba yawa idan dakwai" yace "ni nasan abunda ze kawo ki daban dama. To babu" Haajar tace "haba Daddy" yace "to da Baku San yadda ake Neman kud'in ba sai iya iya kashewa kawai kuka yi?" Haajar tace "eh mana mu da muke da gidan kud'i. Alhaji Misbahu sukutum. Allah dai yaja kwana" ta fad'a cike da tsokana. Daddy yace "Aiko sisi bazan ba da ba. Ke ni kin ganni nan ma bando ko sisi sai d'ari biyar da hamsin" ya zaro a aljihu tare da nuna Mata. Dariya Haajar ke yi tace "kai daddy kaji tsoron Allah" yace "to tunda baki yadda ba ai shikenan. Kin ga ni aramin dubu biyu ma Insha fetur d'in mota" tace "Allah daddy account d'ina yayi k'asa sosai." Yace "ai nafi kowa Sani uwar biki. Aiki ya gan ku kuwa" tace "yanzu me za'a samu a nan?" Yace "d'ari biyu da hamsin ga ta. Dan bazan ma iya ba Ku d'ari biyar d'in ba duka" Haajar tace "Allah yasan indai d'ari biyu da hamsin mun yafe. A dai lalubo mana masu d'an kauri" yace "ke kin fa San gwamnati ta hana aikin banza. Kawai ban gishiri in baki manjà za'ayi" tace "kamar ya kenan?" Janyo ta daddy yayi suna kallon juna tare da sumbatar gefen fuskar ta. Haajar tace "ka rufa min asiri daddy ,ba yanzu ba Dan Allah. Dan maman sameer (Matar Hajj jamil) tana hanya da ita za mu fita " daddy yace "to ai shikenan tunda haka kika zab'a. Ta shi kije sai kun dawo" tace "to kud'in fa?" Yace "babu. Indai ba za'ayi yadda nace ba". Marairaice masa Haajar tayi ta dinga magiya Dan ta Riga ta gano logon sa. Mik'ewa tayi zata fita daddy yayi saurin fizgo ta. Yace " au tafiyan kuma za ki yi baki bani komai ba?" Tace "to ni wani abun ka bani" daddy yace "wallahi ni na fiku uzuri. Dan Allah a duba lamarina" k'ok'arin tashi Haajar ta farayi. Ganin da daddy yayi ba fa zata ba shi had'in kai ba yasa ya danne ta ,ihu ta fara masa tana fad'in "daddy yau kuma fyad'e Zaka yi?" Yace "wuce nan. Ai da matata zanyi ,saboda haka ban yi abun fad'i ba". Ganin tana nema ta Tara masa jama'a yasa ya tushe mata baki ta hanyar sanya bakin shi cikin na ta ,ya fara mata wani salo mai kashe jiki. Cikin d'an k'ank'anin lokaci ya fara fita a hayyacin shi. Wasanni ya Shiga yi mata iri daban-daban har sai da ya tabbata ta fara karb'an sak'onni Dan dole. A tak'aice ce dai daddy Sai da ya sauke abunda ke damun shi na tsawon lokaci sannan ya sararawa Haajar. Sai santi daddy ke yi yana yabawa da sabon canjin daya ji. Dan kusan tunda Haajar ta fara gyara bata had'a gado da daddy ba ,ga sha'anin biki ga shi kuma baya dawowa da wuri ,sai ma yawan tafiye-tafiye da yake yi. Bayan k'ura ta lafa. Daddy ke cewa "ai dole a guje ni wannan irin zak'i haka. Kai amma fa an dad'e ana cuta ta Allah" ita dai Haajar bata raba shi dako qala ba. Ta shi tayi ta yi saurin yin wanka, ta maida kayan ta. Sannan ta duba wayar ta. Kusan missed calls goma ta gani. Zaro ido ta shiga yi tana fad'in "ai shikenan ka b'ata mun record." ATM d'in shi ya bata ta sa hannu ta k'arba tare yi masa godia. Kashe Mata ido d'aya yayi yana cewa "wallahi ko kad'an ban gaji ba. Ko za'aje second round ne? Dan ni gaba d'aya ma an tada min da kwad'ayi" da gudu Haajar ta bar d'akin tana fad'in "yanzu kam k'walelen ka malam". Dariya daddy ya dinga yi ,nan take ya dinga jin wani irin farin ciki na ziyarto shi. Da farko gaba d'aya kasala yake ji Dan ya kasa k'arasa aikin dake gaban shi. Bayan yayi wanka ya dawo ya ci gaba nan take ya gama daddy yace " oh nan matsalar take kenan?" Murmushi yayi tare da shafo k'asan kanshi yana tuno abunda ya faru yanzu. Koma wa yayi ya kwanta yana kallon sama sai faman murmushi yake yi musamman idan ya tuno yadda yaji Haajar d'in yau kamar ya lashi zuma. Haka ya yi fama shi kad'ai. Hotunan ta ya d'auko ya fara kallo a waya, ya na ta murmushi tare da furta "zaki Sani ne ai ,zamu had'u." Da haka wani irin dad'ad'd'en bacci yayi awon gaban da shi. Da sauri Haajar ta k'arasa sashen Hajiya sai k'asa take da kai. A nan ta samu Hajiya ,suxee da Matar hajj jamil sai hira suke yi. Hajiya zaliha tace "ke kuwa kasuwa kike je haka?" Haajar tace " me kike gani?" Tace "to naga ina shigowa Hajiya ke cemin kinje sashen ki wurin daddy yanzu zaki dawo amma shiru-shiru kake ji kamar an aiki bawa garin su". Yak'e Haajar tayi tare da cewa " Baya nan ne koda naje yayi bak'u. Dole sai da ya sallami bak'on sannan na samu na ganshi muka yi magana" Suxee tace "ai ko da nace. Nima na ga kin dad'e". Hajiya tace " to ai shikenan ,tunda gata yanzu ta zo Sai Ku tashi Ku tafi yamma na yi ,Dan Ku dawo da wuri". Gaba d'aya Haajar a tsarge take. Hijabin ta kawai ya sanya sannan tayi gaba tana cewa "Hajiya mun tafi" Hajiya tace "A dawo lafiya". Nan suka fice. Ba su suka dawo ba dai takwas na dare. Tun daga ranar Haajar bata sake bari daddy ya rutse ta ba. Ga gidan na su ya cika da jama'a tinjim ,dangi na kusa dana nisa kowa kawo jiki yake yi banda gudunmawa da ake ta kawowa, kasancewar biki saura kwana uku. Washe gari aka je aka yiwa amarya jere a k'erarran gidan ta da ke k'ofar nasarawa. Gidan amarya Masha Allah abun sai Wanda ya gani. Daren biki babu wanda ya iya runtsawa, duk ana zazzaune a sashen Hajiya ba bu abunda ake yi sai hira kake ji yana tashi, da dariya ,duk wanda ka gani kasan yana cike da farin ciki. K'anwar baban daddy mai suna Anty Asiya tace " To Haajar maganar abinci fa?" Haajar tace "An gama wannan maganar. Dan ba a gida za'ayi komai ba sai dai d'an abunda ba'a rasa ba. Duk na sa a yi a wani gidan abinci kawowa kawai za'ayi idan lokaci yayi". Asiya tace " to ai shikenan ma ,hakan yayi kyau". Haka dai suka ci gaba da tattaunawa kan sha'anin bikin. Suxee na uwar d'akan Hajiya tana waya da Barr cike da so da qauna. Yana gaya mata yadda yayi matuqar kewar ta, Dan tun lokacin da za'a fara gyarata Haajar ta yi masa magana da kanta akan fa shi da amarya suxee sai dai ko a waya ,ko kuma idan an kai masa ita. Gara ma ranar da aka kawo lefen ta ya samu ganin ta ,shi d'in ma satar jiki tayi ba Wanda ya Sani ta fita suka gaisa sama-sama. Ba yadda ya iya Dan dole ya hak'ura da zuwa ba Dan ya so ba. Ko wani sak'o yake so ya bata sai dai ya aiko wata k'awarta ta family kuma 'yar uwarta mai suna fanna ita take zuwa ta amso ta kawo mata. Gyaran da Suxee tasha yasa duk a cikin kwana kin nan bata iya wani dogon bacci ,kai yadda taga safe haka take ganin dare. Dan wani wutar sha'awa dake fizgar ta. Ina ganin wannan abun ma na d'aya daga cikin abunda yasa Haajar ta dakatar da Barr Kabir daga zuwa gidan, Dan tasan k'arfin abubuwan da take baiwa suxeen da kuma lura da tayi na cewa suxee bata da wuyar tafiya... Da daddaren tela ya yiwa Haajar waya akan ga d'ikin su ya kammala. Dama kamar yasan shi take jira, ta yi ta kiran wayar shi tsawon kwana biyu wayar shi a kashe ,ga shi hatta kayan da amarya zata saka yana wajen shi. Hak'uri ya ba Haajar tare da bata uzuri. Haajar tace ba komai. Ta cika masa ragowar kud'in shi sannan ta amso d'inkin ta koma cikin gida. a parloun Hajiya ta baje d'inkunan. Sai da ta fara zare nata Dana amarya da na hajiya zaliha da ta bada da kuma sauran 'yan uwanta da suma gaya mata za su zo bikin, dama ita Hajiya da auta tuni aka kawo musu nasu, sannan tace ga wa sauran 'yan uwa ga ankon data sanya a d'inka musu riga da sket na kwaddebuwa atamfa mai kyau da tsada. Kowa ya gwada Wanda ze yi daidai da jikin shi. Ai fa nan parlour ya kwacema da murna. Nan fa aka shiga gwaje-gwajen kaya ,sai godia suke mata da San barka. Tace duk Wanda basu samu ba su jira zuwa da safe za'a kawo wasu kayan, Dan tela biyu ta baiwa d'inkunan Dan a samu a gama cikin lokaci. Wannan abu yaiwa kowa dad'i musamman wa'yanda basu saka da kan su a lissafi ba ,sai suka ga Haajar bata ware su ba. Washe gari musamman Haajar ta d'auko mai kwalliya ta biyata dan a fito da amarya. Da safe misalin k'arfe takwas amarya tayi wankan ta na farko ,dama gashi tasha lalle da kitso. Ta fito cikin wata atamfa ruwan ganye mai ratsin fari, a inda takalmin k'afar ta da pos d'in hannun ta had'ida mayafin ta duk ya zama fari. Sarka da d'ankunnen dake wayar ta had'ida awarwaro da zobban dake hannun ta duk na gwal ne da Barr Kabir ya sanyo mata a lefe. Ba k'aramin kyau tayi ba duk inda ta wurga sai d'aukar ido take yi tana zuba wani mayataccen k'amshi. Guda kake ji ya kace ma ko ina da ko ina. Ga mak'awan gargajiya da suka doko sammako daga can wajen shigowa gida ,ganga suka shiga kid'awa suna wake daddy da kuma Haajar sai kace su ake yi wa biki. Sai da Haajar ta aiko tace amarya za su wak'e mata sannan suka canza salon gagangar su. Da daddaren tela ya yiwa Haajar waya akan ga d'ikin su ya kammala. Dama kamar yasan shi take jira, ta yi ta kiran wayar shi tsawon kwana biyu wayar shi a kashe ,ga shi hatta kayan da amarya zata saka yana wajen shi. Hak'uri ya ba Haajar tare da bata uzuri. Haajar tace ba komai. Ta cika masa ragowar kud'in shi sannan ta amso d'inkin ta koma cikin gida. a parloun Hajiya ta baje d'inkunan. Sai da ta fara zare nata Dana amarya da na hajiya zaliha da ta bada da kuma sauran 'yan uwanta da suma gaya mata za su zo bikin, dama ita Hajiya da auta tuni aka kawo musu nasu, sannan tace ga wa sauran 'yan uwa ga ankon data sanya a d'inka musu riga da sket na kwaddebuwa atamfa mai kyau da tsada. Kowa ya gwada Wanda ze yi daidai da jikin shi. Ai fa nan parlour ya kwacema da murna. Nan fa aka shiga gwaje-gwajen kaya ,sai godia suke mata da San barka. Tace duk Wanda basu samu ba su jira zuwa da safe za'a kawo wasu kayan, Dan tela biyu ta baiwa d'inkunan Dan a samu a gama cikin lokaci. Wannan abu yaiwa kowa dad'i musamman wa'yanda basu saka da kan su a lissafi ba ,sai suka ga Haajar bata ware su ba. Washe gari musamman Haajar ta d'auko mai kwalliya ta biyata dan a fito da amarya. Da safe misalin k'arfe takwas amarya tayi wankan ta na farko ,dama gashi tasha lalle da kitso. Ta fito cikin wata atamfa ruwan ganye mai ratsin fari, a inda takalmin k'afar ta da pos d'in hannun ta had'ida mayafin ta duk ya zama fari. Sarka da d'ankunnen dake wayar ta had'ida awarwaro da zobban dake hannun ta duk na gwal ne da Barr Kabir ya sanyo mata a lefe. Ba k'aramin kyau tayi ba duk inda ta wurga sai d'aukar ido take yi tana zuba wani mayataccen k'amshi. Guda kake ji ya kace ma ko ina da ko ina. Ga mak'awan gargajiya da suka doko sammako daga can wajen shigowa gida ,ganga suka shiga kid'awa suna wake daddy da kuma Haajar sai kace su ake yi wa biki. Sai da Haajar ta aiko tace amarya za su wak'e mata sannan suka canza salon gagangar su. Zuwa sha biyu amarya ta sake canza kala inda ta fito cikin wata dakakkiyar shada mai tsada d'inkin doguwar riga daya amshi jikin ta. Haajar ba ta yi wanka ba sai da ta tabbatar ta gama shirya komai ,masu abinci sun gama sun kawo tare da ma'aikatan su da za su yi aikin zuba abincin. D'aki daya aka ware sai da aka cika shi da ruwa da kuma lemummuka. Sai da Haajar ta yi sallar azahar lokacin ana shirye-shiryen zuwa d'aurin aure sannan ta yi wanka. Ganin lokaci na k'urewa yasa tabar na ta shirin taje Dan ta shirya mijinta. Cikin wata arniyar farar shadda daddy ya shirya d'inkin babban riga wanda anko ne suka yi shida aminin shi hajj jamil. Misalta muku irin kyawun da daddy yayi b'ata lokaci ne Dan wallahi idan ka gan shi a wannan rana kai ka zata shi za'a je d'aurowa auren. Haajar ma saida tace "kai masha Allah! Ashe dai mijina kyakykyawan gaske ne? Wannan haka haka sai kace Kaine angon" daddy na dariya yace "to aini kullum ma ango na Dan yanzu ma da za'a bani dama Dana tabbatar miki da hakan" Haajar tace "to ank'i a baka daman" dariya yasa tare da cewa "matsoraciya" itama dariyar take yi tace "na dai ji". Nan fa soyayya ta dawo sabuwa Dan gaba d'aya Haajar ji take yi kamar kar daddy ya fita ya zauna tayi ta kallon shi ,ta kasa d'auke idon shi akanta. Yace " malama wannan kallon fa? Duk salon ki shanye dad'in gani na Amaryar da zan kawo ta rasa gane komai ko? Kinfa San ni mijin mace hud'u ne?" Haajar na dariya tace "Ah haba ai kuma Matan ka na aljannah d'an birni". Yace " allah ko?" Tace "yo wace zata wani so ka duk ka tsofe ka yi laushi ,me zata tadda ni din dai". Dariya dikkan su saka daddy yace " zaki yi baya ni ne ai idan na dawo ja'ira". Da haka daddy ya fito sakamakon hajj jamil daya yi masa akan yana jiran shi. Sai da ya fara shiga ya gaisa da su Hajiya. Taubasan shi sai tsokanar shi suke yi. Sannan yayi ficewar shi. Kwalliya aka tsantsarawa Haajar ta shirya cikin atamfa super Holland launin d'orawa da fari, d'inkin riga da sket pisis, Kai idan ka ganta kace ma ita ce Amaryar Dan tsabar kwawun da tayi. Fitowar ta yayi daidai da zuwan masu kid'an k'waryan data gayyato. Har ma sun fara k'ida mutane na rawa. Sai cigiyar ta suke ta lasifika suna fad'in "ina uwar amarya uwar gida a gidan alhaji Misbahu?" Kowa yayi wanka ya shirya ,tare da Hajiya zaliha da muqaraban ta suka sauko. Nan aka fara fito da abinci da abun sha ana kakkaiwa jama'a ,abinci sai kalan Wanda kake so. Ta sa aka warewa Hajiya da muqarabanta na su daban aka kai musu. Seda ta tabbata komai na tafiya da daidai sannan taje ta tutse suxee taci abinci dak'yar sannan ta sake canzo kaya suka fita fage. Suna tattaka rawa ga ruwan liqi da dake tashi. Aifa nan biki ya dawo kan su ,tsakanin Haajar da su idan ba wai ka San su ba ba lallai bane ka iya tantance wacece Amaryar daga ciki. Awa d'aya da fara kid'an k'warya suka sake komawa suka canzo shiga suka dawo. Mutane sai ido suke bin su da shi. A aka har aka dawo d'aurin aure ,su daddy suka wuce walimar da suka shirya na bayan d'aurin aure, wanda ya tara dandazon al-ummah. Wasu ma sai a ranar suka san daddy nada budurwar 'ya mace. Anci an sha a wurin walimar,wanda Hajj jamil ne ya shirya komai ,shine kuma mai kula da bak'in su. Sai wuraren la'asar suka yo gidan daddy da gayyar su. Gidan cindim yake da jama'a Dan se ka yi da gaske ma kafin ka samu wurin da zaka wuce. Mamaki ne ya kama daddy lokacin daya hango Haajar a tsakar fili tana takawa. Ba k'aramin kyau tayi masa ba. Sab'ewa su hajj jamil yayi ya kutsa har tsakar filin ya shiga yi mata lik'i, nan fa kallo ya koma sama. Yana mata liqi tana masa. Abokan su daddy suka dinga tambayar hajj jamil ko ita ce 'yar daddy?. Hajj jamil yace musu a'ah Matar shi ce. Nan fa aka shiga aka dinga musu liqi. Kafin daga baya suka fito zuwa sashen Hajiya. Har yamma ana ta shan sha'ani. Sai shida na yamma Haajar ta sallami masu k'idan k'warya saboda za su fara shirye-shiyen zuwa wurin dinna bayan magriba. Misalin k'arfe takwas suka gama shirin su na zuwa dinna. Amarya tasha kyau ita da angonta. Haajar ma sai da taja daddy ,Hajiya zaliha kuma tare da hajj jamil. Komai ya tafi gwanin sha'awa. Duk Wanda yaje sai ya fito da tsaraban kayan biki kama daga jaka ,memo ,ankicip, kofin tangaras nashan shayi, kayan mak'ulashe da sauran su, Wanda duk Haajar ce ta dau nauyin komai. Abun yayi matuqar k'ayatarwa. An shash-sha hotuna. Haajar Sai da ta keb'e mai hoto d'aya dake ta faman d'aukar su hoto ida da daddy ba tare daya Sani ba. Misalin k'arfe goma sha d'aya na dare aka tashi daga dinner. Kai tsaye gida suka nufa. Suna isa 'yan biko na zuwa. Ruwan lallen da aka jik'awa suxee aka bata taje ya ti wanka. Sannan ta fito. Haajar da kanta ta shirya ta cikin wata exclusive atamfa sannan ta d'ora mata alkyabba akai. Sashen Hajiya aka kaita su ka yi Mata nasihohi sannan aka kaita wurin su daddy, hajj jamil ne ya mata fad'a sosai shi dai daddy tun da yace "Allah ya sanyawa auren albarka" bai sake cewa komai ba. Suxee ta yi kuka kamar ba gobe, Haajar ma hadda hawayen ta. Daga nan aka wuce da amarya gidan ta. Haajar ta wuce mata da duk wani abun da zata buqata kafin gobe. Ko da suka dawo kai amarya kusan d'aya saura na dare. Lokacin duk ana zaune ana dudduba hotunan dinnan wa'yanda suka d'ad'd'auko da waya. Anan sai dai muce Allah ya bada zaman lafiya suxee da Barr Kabir... MUJE ZUWA💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [8/31, 3:27 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* _BABI NA HAMSIN DA D'AYA_ *_____________________________* Washe gari misalin qarfe goma na safe su Haajar su ka fara shirye-shiryen zuwa gidan amarya ,saboda walimar da za'a yi yau a can gidan amaryar sha biyu na rana, wanda karantarwa ta sunnah manzo S.A.W yazo mana da shi ,wato walima bayan aure. Daga gida suka yi komai da za'a rabawa 'yan walimar, sannan suka d'auki duk wani abunda yayi saura na amarya Dan awuce mata da shi. Misalin sha d'aya su Haajar suka fara wucewa kafin wasu 'yan uwa suka ce zasu biyo bayan su idan lokaci yayi. Koda suka je Barr Kabir baya nan ,suxee ce kawai. Ta gyara ko ina da ko ina a gidan ta sanya turaren wuta sai k'amshi ke tashi. Tana ganin su Haajar ta fara murna hadda guntun hawayen ta ,Dan daga jiya zuwa yau ji take kamar ta shekara ne bata gidan su, sosai take kewar kowa nata. Gaggaisawa suka shiga yi ,bayan sun zauna suxee taje ta kakkawo musu abun sha. Haajar ta wuce uwar d'aki ,suxee ba ganin haka tabi bayan ta. Yanayin tafiyar suxee kawai Haajar ta gani ta gano cewa wani abun ya faru. Ba tare da suxee ta kula ba Haajar ta kafe ta da ido ,suxee na ganowa ta fashe da kuka tare da rumgume Haajar. Tausayin suxee ne ya kama Haajar, ta shiga bubbuga bayan ta alamar lallashi. Cikin muryar kuka suxee tace "Anya Anty Haajar zan yi zaman aure kuwa? Ba kiji yadda nake ji ba ,duk abubuwan da nake yi k'arfin hali ne wallahi saboda abunda kika gayamin cewa kar in bari kowa ya gane abunda ya faru tsakani na da mijina. Amma Anty Haajar yadda nake jin labari ba haka na gani ba. Wasu daga cikin qawaye na sunce min sai bayan sati d'aya ko sati biyu da auren su mazajen su ke kusantar su ,amma ni duba ki gani fa jiya-jiya. Kika kuma cemin ba zafi bayan ba haka bane". Suxee ta qarashe maganan tare da fashewa da wani sabon kuku. Abun yaso ya bama Haajar dariya amma sai ta dake tare da ci gaba da bata hak'uri " Hajiya k'arama ki dena kukan nan, ko so kike wani ya shigo ya gane wani abun ya faru ,bakisan wannan sirrin ki bane? Ko ni bai kamata ki gayamun ba". Girgiza kai suxee tayi tare da share hawayen ta sannan tace "A'ah Anty Haajar. Ni a matsayin mahaifiya na d'auke ki ,bana tunanin zan iya b'oye miki komai. To idan ban gaya miki ba wa kike so ingayawa damuwa ta?" Haajar tace "hakane! To amma ki dena kuka. Sannan da kike zancen wai qawayen ki na gaya mi sai anyi sati ko sati biyu kafin mazan su su kusance su, angaya miki hadisi ne ko ayar allah? Babu wani nafsi daya ce haka, hasalima a karantarwa ta sunnah anfi son randa aka kawo mace mijin ta ya kusance ta shine maqasudin wannan walimar ta bayan aure. Idan kika ga miji ya d'aga wa matar shi qafa wannan ra'ayin shine da ganin damar shi, saboda haka ya kamata ki lura dakyau" Nasihohi sosai Haajar ta sake yiwa Haajar kan yadda zata tafiyar da rayuwar auren ta ,musamman ta fannin shimfid'ar mijin ta ,dan abunda Haajar ta lura da shi a maganganun suxee alama ce ta Barr mai yawan buqatar mace ne ,musamman yadda ya jima be yi auren nan ba ,ga shi ta lura suxee nada raki Wanda ze iya kawo mata naqasu a zamantakewar ta da mijin ta. Fad'a tayi mata sosai ,sannan ta bata wasu abubuwan da zata yi amfani dasu , ta had'a mata ruwan magarya da sassak'en b'aure mai zafi ta zauna. So biyu tana canza mata ruwan sannan tace tayi wanka ta fito ta shirya ,lokacin wacce zata mata kwalliya ta Kira tana hanya. Masu sanya rumfar walimar kuma suna harabar gidan suna aikin su. Gyara mata ko ina Haajar tayi ,ta jera mata jayan ta a sip ,sannan duk wasu muhimman abubuwan da suxee zata buqata ta ajiye mata su a kusa-kusa kamar kayan hakin maye ,drowa d'aya ta mata. Seda akayi sallar azahar sannan me kwalliya tazo ,lokacin mutane sun fara taruwa. D'an light make-up aka yi wa suxee. Ta shirya cikin wani material purple mai kyau da tsada, tare da d'ora alkyabba akai. Bayan angama Haajar ta dube ta tare da cewa "kai masha Allah Mrs Kabir kinyi kyau sosai." Suxee tace "nagode Mrs Misbahu". Dariya suka sa. Suxee tace " to Anty Haajar kizo a miki kwalliyar mana" Haajar tace "wa ni? Ai Kema kinsan ban damu da irin kwalliyar nan ba ,nafi gane in Shafa hoda in mits-tsika mai a baki kawai ya ishe ni". Fanna mai kwalliya tace " ai kinsan su kyawawa daban suke ,kwalliya bata wani dame su ba." Dariya suka yi Haajar tace "kin dai ga kyawawan gaske nan a gaban ki" ta nuna suxee. Suxee tace "kai Anty Haajar abun hadda zolaya?" Dariya Haajar tayi tare da cewa "ai kowace mace ma kyakykyawa ce saidai idan bata samu gyara ba". Fanna tace " hakane kam". Se da suka yi sallan azahar sannan aka fara shirye-shiryen walima. Misalin k'arfe biyu na rana ancika. Malama khadija itace wacce zata gabatar da nasiha a walimar. Tana zuwa walima yakan kama. Nasihohi sosai malama khadija tayi tare da tsakuro musu wasu daga cikin magungunan da zasu iya had'a wa da kan su ba tare da sun cutata ba. Sannan tayi tsawatarwa game da wuta da aljannah. Haqiqa ta fad'akar ,kowa yaji dad'in zuwa walimar. Sai la'asar taron ya fara watsewa ,duk Wanda zai tafi kuma da tsaraba yake tafiya ,na turaren wuta, kayan snacks da abun sha Wanda Haajar ce duk tayi wannan hidimar. Bayan la'asar duk mutane sun gama watsewa sai su Haajar kad'ai suka rage. Sai da suka gyara mata duk inda aka b'ata suka baza turaren wuta. Haajar ta sake dafawa suxee ruwan sassaken b'aure ta zauna sannan tasa tayi wanka ta canza kaya ,wani had'ad'd'en gumba na aya Wanda yaji kwakwa ,da dabino Haajar ta had'a wa suxee da madara tace "maza ki kafa kai ki shanye".bayan ta shanye ta tsiyaya mata tsumi Kofi d'aya shima ta shanye ,sannan tace " ya isa haka. Karki dinga shan abubuwa ya miki yawa, Dan suna da k'arfi zaki iya buguwa idan kika cika". Suxee tace "ai naji Anty Haajar, Dan har yanzu ban dena jin shi a mak'oshi na ba." K'arfe biyar su Haajar suka yiwa suxee sallama suka koma gida... Sai da akayi sati sannan Haajar ta dena aikawa su suxee abinci. Bayan sati d'aya aka kai hajiya gidan suxee ta wuni mata ,sai yamma daddy ya tura driver ya d'auko ta. Bayan sati biyu da zuwan hajiya suxee da Barr Kabir suka kawo ziyara gidan daddy. Kowa yayi murnan ganin su ,suxee tayi kyau abunda ya k'ara haske tayi 'yar k'iba ,haka shima Barr. Tun rana sai dare suka musu sallama suka tafi. Tun bayan biki Hajiya zaliha Matar hajj jamil bata sake komawa gidan Haajar ba ,Haajar ce ma suna hira da daddy wata rana da daddare take cewa ya kamata taje ta dubo maman sameer gobe. Washe gari da daddy zai fita ya aijye ta a gidan ,yace idan ya dawo da yamma zai biyo ya d'auke ta. Hajiya zaliha tayi murna sosai da ganin Haajar. Haajar tace "ya naga duk kin rame lafiya kuwa?" Hajiya zaliha tace "ina fa lafiya ,tun bayan biki nake nan banda lafiya" Haajar tace "ya salama! Ko ince ,amma wllh banda labari kuma Abbu sameer na zuwa gidan mu amma ban ji a bakin shi ba" Hajiya zaliha tace "aikin San halin shi ko yasan Abu indai ba tambayar shi kayi ba ,ba lallai ya fad'i ba." Haajar tace "to amma meyake damun ki haka? Kin rame sosai, Kodai ta samu ne?" Haajar ta fad'a cike da tsokana. Hajiya zaliha tace "kedai bari. Shi d'in ne fa, sai wahalar dani yake yi". Murna sosai Haajar tayi tare da yiwa Allah hamdala. Tace " Ashe dai biki bai qare mana ba? Kai amma naji dad'i sosai. Allah ya raba lafiya, ya bada rayayye ko rayayye mai albarka". Hajiya zaliha ta amsa da "ameen". Kusan Haajar ce tayi mata aikin gidan ranar. Sun sha hira sosai ,sai yamma liqis an ma kusa kiran sallan magrib daddy yazo d'aukan ta. A mota take bashi labarin Hajiya zaliha nada juna biyu ,shima daddy yayi murna sosai kai kace Matar shi ce aka ce tana d'auke da cikin. Tsokanar Haajar ya shiga yi akan cewa suma ya kamata ace sun d'au harman na biyu. Haajar tace " haba dai! Dan Allah kayi hak'uri ranka ya dad'e. Su Hassan fa ko yaye su ban yi ba" daddy yace "to idan kuma Allah ya kawo kuma fa?" Haajar tace "wannan kuma ba yadda zan yi" yace "to Dan haka wannan ma ba yadda zaki yi da shi na jikin ki" zaro ido Haajar ta shiga yi tare da cewa "menene kuma a jikin nawa daddy?" Dariyar mugunta daddy ya mata tare da cewa "ciki mana" Haajar tace "na shiga uku. Dama ina da wani cikin bayan na cin tuwo ne?" Ganin duk yadda ta rud'e yasa daddy cewa "ke wasa nake miki fa ,duk kin bi kin wani firgice. Da akwai keda yake jikin ki ai zaki sani" ajiyar zuciya Haajar ta sauke tare da dafe k'irji tace "haba! Yanzu naji zance". Dariya daddy ya shiga yi mata. Nan suka saki zancen suka d'auko wani, a haka har suka k'arasa gida. Bayan sati biyu da zuwan Haajar gidan Hajj jamil. Take cewa daddy tana so taje asibiti a duba ta. Daddy yace mata saboda me? Dan shi dai lafiya qalau ya ganta. Tace masa baccin da take yi ne yayi yawa ,ko da yaushe bacci kamar 'yar k'waya, se yawan kasala da take fama da shi. Daddy k'in yadda yayi aje asibitin ,haka ya dinga mata kwana-kwana ,har sai da cikin ya kai wata uku lokacin ya fara fitowa. A lokacin ba yadda Haajar ta iya amma kuma bata murna da cikin saboda a cewaf ta su Hassan ba suyi k'waren dahar zata yi musu qanne ba. Tunda Hajiya ta sani sai tace Haajar ta dinga basu nono so d'aya a rana ,dama ba wani damuwa sukayi da nonon ba sosai ,da haka har suka dena sha suka koma shan madara zallah. A b'angaren suxee ma tana can d'auke da ciki wata biyu. Murna a wurin su Haajar ba kama hannun yaro. Allah ya taimaki Haajar ko kafin watan haihuwar ta ya tsaya su Hassan sun iya tafiya suna gudun su ko ina ,ga yaran da jikin girma Dan idan ba an gaya maka cewar basu shekara biyu ba ba ganewa zaka yi ba, baki ne dai babu. Matar hajj jamil ce ta fara haihuwa ,ta samu mace ,murna a wurin daddy da hajj jamil abun sai Wanda ya gani. Daddy ne yayi komai na sha'anin suna, ranar suna yarinyar taci sunan Hajiyar daddy wato suwaiba ,ana mata laqani da Aslamiyya ,duk da shi hajj jamil suxee yayi wa kara ba Hajiya ba ,saboda qaunar da yake mata har yanzu babu abunda ya ragu. Kowa yaji dad'in karar da yiwa Hajiya ,Hajiya ma ta taka rawar gani sosai Dan ita aka yiwa takwara. Da farko ma ta d'auka ko sunan mahaifiyar shi zai saka, da ta yi masa magana sai yake ce mata ,ba yada ra'ayin hakan ne kawai ,iyayen ma da ba sanin su yayi ba ,Dan an haife shi da kwana tara mahaifiyar shi ta rasu a wurin dangin ta ya taso ,shekarar shi biyu da wata shida kuma Allah ya yiwa mahaifin shi rasuwa ,a wurin kakannin shi ya taso ,bayan sun rasu ne ya dawo hannun kawun shi da zama. Kunga kuwa ina wata shaquwa? Hajiya ce take zuwa gidan hajj jamil tana yiwa Hajiya zaliha duk wani abunda ya kamata har bayan suna ,Dan Haajar kam tayi nauyi ,ranar suna ma dak'yar ta samu taje ,shima tana zaune wuri d'aya bata iya tab'uka komai ba. Wata d'aya da haihuwan Hajiya zaliha Haajar ita ma ta haihu inda aka sake samun 'yan biyu ,sai dai wannan karon duk mata ne. Ranar suna Hassana taci sunan mahaifiyar Haajar Halimatus sa'adiya ana mata laqani da Ummi ,hussaina kuma taci sunan Kubra ana mata laqani da Amna. Haajar tayi hakan ne saboda suxee. Dukda daddy bai so ba ,amma ta nuna masa bata yadda za'ayi ya k'yamaci Kubra Dan ko duk yadda yaki yaso jinin ta na yawo a jinin shi ,ga kuma 'ya'yan ta nan na ci gaba da rayuwa a doron duniya. Ba Dan yaso ba haka ya hak'ura, Dan Haajar ba dai iya magana cikin hikima ba ,Hajiya ma taji dad'in abunda Haajar tayi sosai ,suxee ko hadda kukan ta da taji an saka sunan mahaifiyar ta. Cikin suxee ya girma ,wannan ne yasa aka tura mata auta Dan ta taya ta wasu aikace-aikacen ,tunda daddy yace kar ta dawo gida har sai Allah ya sauke ta lafiya... Kwana arba'in da biyar tsakinin haihuwar Haajar. Suxee itama Allah ya sauke ta lafiya ya bata santalelen d'an ta namiji mai kama da Barr Kabir Sak kamar an tsaga kara. Ranar suna yaro yaci suna Mahmud. Kusan tare Haajar da suxee suka yi jego... MUJE ZUWA 💃 TAKU HAR KULLUM SIDIYA...✍️ [9/1, 3:04 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠 🏠🏠🏠🏠🏠🏠 🏠🏠🏠🏠 🏠🏠 🏠 *_🏠(base on true life story)_*🏠 *_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_* (On ward together) *MALLAKAR:* *SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️* 🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚 _BABI NA HAMSIN DA BIYU_ *____________________________* Bayan suxee tayi arba'in ,Haajar ta rok'i daddy akan tana so ya bar su suje suga dangi itada suxee da kuma auta ,bai gaddama yace Allah ya kiyaye hanya, sai dai ya musu fad'a saboda jariran yara da suke da su ,har ma yace ze had'a su da 'yar taya raino Dan kar abun ya musu yawa. Su Haajar suka shirya tsaf, saida suka fara zuwa kano wurin Hajiya sakina ,Hajiya sakina tayi murna da ganin su matuqa, gidan yayyin baban daddy ma duk sai da suka zaga gidajen wa'yanda ke aure a nan jahar kano. Duk Wanda yagan su sai ya ji dad'i ,abun azziki kuwa sun samo su ,su turarukan wuta ne ,humra ,zannuwan gado ba'a magana ,kowa so yake aje idan gidan shi, idan aka je kuma baya barin su su fita hannun rabbana. Haqiqa dangin daddy masu karamci ne ,Dan iya kara su Haajar sun gan shi. Satin su d'aya a kano zuwa wuce jigawa gidan su Haajar, nan ma fa kar kaso kaga yadda jama'a ke sintirin zuwa gaishe su. Nan ma saida suka yi sati biyu ,kafin suka fara shirin tafiya. Daren da zasu tafi Haajar ke tambayar suxee inda dangin Kubra suke? Suxee ta dad'e tana jimanta tambayar ,kafin ta sauke wani guntun ajiyar zuciya tace "A gaskiya Anty Haajar idan nace miki ga inda suke na yi k'arya. Dangin mahaifin ta ne dai kam sunan nan a katsina ,an tab'a zuwa dani tun ina qarama ,amma idan nace miki zan gane wurin yanzu gaskiya na fad'i ne kawai Dan inji dad'in baki na". Haajar ta jimanta maganan kafin tace " to wai Dan me baku San su ba? Ba'a kai Ku ne?" Suxee tace "wacce ma ta zama musu dole ba zuwan take ba ,Dan tunda nake da mummy so d'aya naga taje katsina shine zuwan da aka yi dani da kuma Haseena lokacin ba'a haifi Auta ba. Sannan idan suka zo wurinta wulaqanta su take yi tana ganin kamar Allah ya fifita sama da su ,gani take kowa d'an cin azziki ne ,ganin haka yasa ka kanta yace duk Wanda ya sake takawa zuwa wurin ta Allah ya isa ,ba da miyon bakin shi ba, ya kuma yi mata mummunan fata. Allah ya jiqan Haseena da gafara ,,ta yiwa Mummy fad'an akan ita idan ba zata je ba mu tasa akai mu ,amma taqi. Ita ala dole ubanta mai kud'in da Dan ba na yanzu ba ,kuma tana auren 1 in town billionaire." Haajar ta dad'e tana jinjina magana kafin daga bisani tace "to yanzu baki San Wanda zamu iya samun labarin inda suke ba a katsinan?" Suxee tace "gaskiya bansani ba. Amma meze hana ki kira Hajiya inaga ita zata iya Sani, tunda mijin ta abokin Baban mummy ne lokacin yana da rai." Da wannan Haajar ta yanke shawarar kiran Hajiya ta tambaye ta. Da har ta bari sai zuwa da safe ,sai kuma ta duba agogo taga 11 saura na dare ,tasan Hajiya tayi bacci a wannan lokacin amma ba ta da wani zab'in daya wuce ta kira ta. Wayar ta ta d'auko tare sa kamo lambar Hajiya, sai sa kiran ya kusa tsinkewa sannan Hajiya ta d'aga, Haajar tayi sallama ,Hajiya ta amsa cikin muryar bacci tare da cewa "lafiya kuwa Haajar naga kiran ki da daddare?" Haajar tace "bakomai wallahi Hajiya. Kiyi hak'uri na tashe ki daga bacci. Dama so nake in d'an tambaye ki?" Hajiya tace "alhmdllh tunda ba wata matsalar bace. To inajin ki" nan Haajar d'in ke tambayar ta akan ko tasan inda dangin mahaifin Kubra suke a katsina? Hajiya ma jin maganar tayi kamar daga sama, amma tunda ta yadda da Haajar bata da wani sauran shakku akan ta, nan tayi mata kwatance ,ta kuma gaya mata sunan Wanda zasu tambaya idan sun je garin Rinjim. Haajar tayiwa Hajiya godia sannan ta yanke kiran... A akwati d'aya suka shirya kayan su ,suka bar sauran anan ,haajar tace sai idan sun dawo su biyo tanan dan kar su yita yawo da kaya. Washe gari suka shirya tunda sassafe suka kama hanyar katsina, Auta na bacci bata ma San sun tafi ba. Basu wani sha wahala ba suka isa garin Rinjim. Nan Haajar tayi tambayar sunan Wanda Hajiya tace su tambaya idan sunje garin wato MALAM NA ALLAH. Sanannen mutum ne kuma babban Malami ne a garin Rinjim. Cikin ikon Allah basu wani sha wahalar da suke tunani ba aka kai su gidan. Gidan gidan k'asa ne ,daka gani kasan irin ginin da ne ,daga cikin gidan idan ka shiga kai da ka gani kasan anyi kud'i a gidan ko yanayin tsarin kawai ka duba. Ko ina a share tsaf ,da alama masu gidan Nada tsafta. Sallama suka yi ,shiru ba Wanda ya amsa ,suka sake yi a karo na biyu ,nan ma shiru ,suxee tace "anya kwatancen nan daidai ne ma kuwa?" Haajar ta sake yin sallama ,sai ga wata tsohuwa ta fito, tace "sannun Ku yara! Wa kuke nema?" Haajar ta sunkuya ta gaishe ta ,sannan ta fad'a mata wurin malam suka zo. Tsohuwar nan tace "daga ina za'a ce masa?" Haajar tace "kice masa daga sakkwato". Nan wannan dattijuwa ta koma ciki dan sanarwa malam zuwan bak'in... Mintuna biyar da shigar tsohuwar nan sai ga wani dattijo ya fito yana duban k'ofar shigowa ,da fara'a ya tarbe su kamar yasan su yana fad'in "lale maraba da bak'i". K'arasawa suka yi suka kwashi gaisuwa ,sun san ko ba'a fad'a ba shine Malam Na Allah. Ciki ya shiga dasu yasa aka yi musu shimfid'a ,aka kawo musu fura mai sanyi damun kindirmo zallah. Haajar tasha sosai tayiwa Allah godia sannan itama suxee tasha. Nan take garin Ringim ya d'auka ,malam yayi bak'i ,aifa sai zuwa gaishe da su Haajar ake yi. Abun yata basu mamaki ,bayan sun yi sallar azahar malam ya dawo ,suka sake gaisawa ,Haajar tace " malam baka tambaye mu mu su waye ba?" Murmushi dattijon nan yayi tare da cewa "Haba jikata! Kun fa ce daga sakkwato kuke? To ai ko baku fad'a ba nasan ko Ku su waye ,ga kama nan. Wannan ko ba'a fad'i ba nasan jinin Hadiza ne" ya fad'a tare da nuna suxee dake zaune. Mamaki ne ya cika cikin Haajar. Aifa nan malam ya dinga basu tarihi ,da labaran ban dariya. Su Haajar sun yi matuqar jin dad'in kasancewa da shi. Haajar tace "Baba amma kunsan kuwa Allah ya yiwa Kubra rasuwa?" Murmushi malam ya sake yi Wanda yayi nasarar bayyana jajayen hak'oran shi yace "K'warai kuwa mun Sani jikata." Haajar tace "baba to amma meyasa Baku je ta'aziyya ba?" Malam yace "Allah ya gafarta Mata ya kuma yafe mata". Mun yi mata addu'a daga nan ,karki damu. Ganin kamar baya son maganar yasa Haajar ta bar shi suka d'auko wani. Bayan magriba bayan malam ya dawo daga sallah ,ya aika aka kira masa Haajar. Ya tambaye ta game da labarin kubra, Haajar bata b'oye masa komai ba ,ta fad'a masa cewa ita matar daddy ce ta kuma sanar da shi duk abunda ya faru Wanda aka yi tana nan dama Wanda hajj jamil ya bata labarin anyi kafin zuwan ta. Har zuwa mutuwar kubra da dawowar kuruwan ta jikinta... Malam ya girgiza Kai yace "kaico!!!kaico!!! Albasa bata yi halin ruwa ba. Bazan dena tir da Allah wadai da jinin Hadiza ba Dan ita tazo ta yad'a mana gurb'ataccen jini a zuri'ar mu." Haajar ta tambaya wacece Hadiza? Dan tasan sunan kubra ne. Malam yace mata "mahaifiyar kubra itace me wannan sunan Wanda a wurinta kubra taci wannan sunan." Nan malam ya fara bama Haajar tarihi tun kafin d'an shi ya auro mamar kubra. Da tarihin tsafin ta. Malam yace har yakai ya kawo saida aka raba shi da d'an shi daya Haifa ,daga k'arshe yaji labarin mutuwar sa ,daya tsananta addu'a sai ya gano Ashe abun tsafi aka sadaukar wa jinin d'an shi. Daga baya itama mutuwar ta bai yi kyau ba ,Dan mafi munan mutuwa tayi Wanda har yakai ya kawo tana fizgar naman jikin ta tana ci. Malam yace kubra ita kad'ai ce 'ya a wurin Hadiza ,kuma itama a binciken shi ya gano cewa ta sadaukar wa tsafi da ita tun kafin ajali ya riske ta. Malam ya tabbatar wa Haajar cewa gawar kubra ne kawai a makwancita amma a zahirin gaskiya kuruwar ta nacan ana tsafi da ita. D'aukar fansan data mutu da shi yasa kuruwar ta ke fitowa tana rab'ar Haajar ,Wanda daga baya da mahaifin Haajar ta gano haka ,sai ya yanke shawarar daya bar kuruwar aci gaba da tsafi da shi gara ya k'onata ta koma kabarin ta. Haajar tayi mamakin jin ance mahaifin ta yasan komai. Malam ya qara da cewa "hikimar k'ona wannan kuruwar shine Dan kada rayuwa da yawa su salwanta. Wannan ya ishi mutane ishara ,kubra ta mutu lokacin da take cikin jin dad'in duniya, ta qullaci d'aukar fansa ba tare da sanin cewa itama abun tsafin mahaifiyar ta neman fansa a kanta ta ba. Mafi munin mutuwa bai wuce ace an raba mahad'in rayuwar ka da gangan jikin ka ba ,wato acire kuruwar ka ana aikin tsafi da shi." Yace "to kinga Allah kenan buwayi gagara misali Wanda ba'a saka shi ba hana shi ,kuma shi keda iko akan komai da kowa. Fata dai Allah ya mana k'arshe mai kyau" Haajar da take jin maganganun malam kamar almara ta amsa da "Ameen". Ta jima suna hira da malam kafin ta koma cikin gida inda ake sauke su. Washe gari malam yasa aka zaga da su Haajar wurin ragowar dangin shi, suxee ta basu hak'uri a maimakon kubra ,sannan tayi musu alqawarin ci gaba da zumunci. Kowa yaji dad'in hakan. Haajar tayi musu alkhairi mai tarin yawa, Kwanan su uku suka koma jigawa. Washe gari daddy ya aiko da mota suka koma can gida sakkwato. Da suxee zata koma gidan ta, kamfani d'aya daddy ya bama mahmud a matsayin kyauta, kowa yaji dad'i matuwa. Bayan shekara biyu Haajar ta sake haihuwar d'anta namiji aka sanya sunan mahaifin daddy ana kiran shi da Abba. Lokacin su Hassan sun fara zuwa makaranta. Suxee ma ta sake haihuwa ta haifi mace Barr Kabir ya yiwa Haajar takwara ,su na kiran ta da Anty. Daga k'arshe aikin Barr Kabir ya koma bangaladash gaba d'aya, ya d'auki Matar shi da 'ya'yan shi suka koma can da zama, duk hutun k'arshen shekara suke dawowa ganin gida, wani lokacin kuma daddy ya kwashe iyalan shi gaba d'aya suje kai musu ziyara. Lokacin da auta ta kammala makaratar sakandire d'inta ,ta samu admission a Bangladesh wato babban birnin india inda su suxee ke zaune. A hannun su daddy ya damqa amanar shukra. Hajj jamil ma Matar shi ta sake haihuwa ,aka sanya Aisha. Tun daga wannan lokacin ,farin ciki da alkhairin Allah yaci gaba sauka a *GIDAN MISBAHU* ,rayuwa ta dawo musu sabuwa ,kowa na qaunar d'an uwan sa... *BAYAN SHEKARA GOMA SHA BIYAR* Auta shukra tayi aure a can bangaladash ,ta auri wani abokin aikin Barr Kabir har ma Allah ya azurta su da yara uku mata biyu namiji d'aya. A b'angaren daddy 'ya'yan shi tara ,Hassan da hussaina sun gama secondary school d'in su ,Hassan ha samu admission a k'asar paris a inda sameer babban d'an Hajj jamil ke aiki, hussaina kuma ta samu a jami'ar d'an fodiyo dake nan jahar sakkwato itada Suxee k'arama 'yar hajj jamil da suke sa'anni,,, su Amna da ummi kuma na shirye-shiryen gama sakandire ,yayin da Abba ke aji uku a sakandire, Abdul-Ahad na aji biyu a sakandire, sai Abdul-jalil dake aji d'aya ,Husnat da Auta Hafsat kuma na primary... Hajj jamil shi kuma 'ya'yan shi shida, sameer, suxee ,Aisha, mukhtar, Ali sai Auta Asma'u. Suxee ma yaranta shida, Mahmud, Anty, Hassan da hussaini, khadija da kuma Hamida. Zumunci yaci gaba tsakanin daddy da hajj jamil Dan yanzu haka ana shirye-shiryen bikin d'an hajj jamil sameer da kuma hussaina 'yar gidan daddy. Sai kuma Hassan Dan gidan daddy da Aisha er gidan hajj jamil Wannan had'i yayiwa kowa dad'i... A cikin wa'yannan shekarun kuma an yi rashe-rashe ,Dan kuwa Hajiya sakina ta rasu ,yayar daddy Hajiya bara ta rasu itama, malam na Allah kakan kubra shima ya rasu. Anan sai dai muce Allah ya jiqan wa'yanda suka Riga mu gidan gaskiya. Bayan bikin su hussaina ,daddy na zaune yadda iyali suka dabaibaye shi, ga 'ya'ya ga jikoki. Murmushi daddy yayi tare da cewa _Bayan wuya sai dad'i_... *_____TAMMAT__________________________* ALHAMDULILLAHI ALA KULLI HALIN. GODIYA TA TABBATA GA ALLAH MAI KOWA MAI KOWA WANDA CIKIN IYAWAR SA DA YADDAR SA YA BANI IKON FARA WANNAN LITTAFI MAI SUNA GIDAN MISBAHU ,A YAU KUMA ALLAH YA NUFA NA KAMMALA WANNAN LITTAFI, FATAR ALLAH YA YAFE MIN KURAKUREN DAKE CIKI ,ABUNDA NAYI DAIDAI KUMA ALLAH YA BANI LADAN SHI. MASOYA NA MASU BIBIYAR WANNAN LITTAFI INA MIK'A SAQON GAISUWA TA GARE KU ,DA ADDU'AR ALLAH YABAR QAUNA. NAGODE SOSAI DA SOYAYYAR DA KU KE NUNA MIN.😘💖💖 SAI KUN JI NI A SABON LITTAFI NA INSHA ALLAHU RABBI MAI SUNA... TAKU HAR KULLUM💃 SIDIYA...✍️09064458468