𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_Ɗan ɗano daga Zafafa biyar😋😋_* .........Kwanakin mako uku kenan da shuɗewar komai amma komai ya kasa mantuwa a zukatansu. Kuzari ya samu rauni kamar yanda dukkan karsashi ya gujema gangar jiki. Duniya ta masu ƙunci, ƙunci irin wanda har ƙarshen numfashi da wahala su manta. Farin cikinsu ya zama fansar damuwar wasu, wasun da kansu kawai suka sani basa kallon na ƙasa da su. Da ace ƙarfin iko a hanun kowanne ruhi yake a zahirin rayuwa, da ita ce zata zama mace ta farko a duniya mai ƙarfin ikon da zai girgiza zukatan kowaɗanne irin azzalumai. Kafin shuɗewar makwanni uku masu ɗauke da kundun baƙin ciki rayuwar ahalin Mal. Zayyan tamkar dutsen lu'u-lu'u suke a cikin tsakkiyar zinare. Ba magana ake akan dukiya ba, dan tana a cikin jerin abu mafi rauni da suke ɗauka ko amsa sunan ko kallo farin ciki. ana magana ne akan kammaluwar ahali masu matuƙar ƙaunar juna zunzurutu mara gauraye. Masu kuka a yayin zubar hawayen ɗayansu, masu dariya a yayin farin cikin ɗayansu, masu jiyya a yayin ciwon ɗayansu, masu zama komai a lokacin da komai yake abu ɗaya a hanunsu. 𝕽𝖚𝖒𝖆𝖓 babbar ƙasace a tsakkiyar wani babban tsibiri a wani ƙarni daya shuɗe kafin yau, ƙasace mai yawan arziƙin zinare yankin nahiyar Africa. Ƙasar Ruman nada babbar Daular mulki data ƙunshi manyan sarakuna masu ɗunbin tarihi kala-kala da labaransu bazai taɓa kasancewa shuɗaɗɗe ba a duniya. Ba arziƙin zinare ne kawai suke da shi ba, sunada nau'i-nau'in kayan itatuwa da wajajen noma harma da kiwon dabbobi da akan fita da su ƙasashe daban-daban ko'a shigo cikin ƙasar a saya. Al'ummar wannan ƙasa sun kasance wasu irin ƙyawawan mutane masu kwarjini da cikar haiba, sai dai duk da ƙyawun da mafi rinjayensu ke da shi hakan bazai hana a samu masu ƙarancin ƙyawun ba. Sunada yawan addinai da ƙabilu tamkar kowacce ƙasa, sai dai mafi rinjayen ƙabila sune masu yara yaren rumanci, sannan addinin musulinci yafi kowanne addini ƙarfi da rinjaye. Abu mafi mamaki a ƙasar ta Ruman shine, duk da ƙarfi da rinjayen da addinin musulinci ya samu suna girmama al'adunsu na kaka da kakani musamman ƙarfin iko. Ƙarfin iko nada matuƙar tasiri a ƙasar Ruman ainun, hakama al'adu da girman masautunsu na taka rawar ganin hana dukkan abinda turawa suka zo musu da shi taka rawar gaban hantsi a garesu bayan ilimin boko, duk da suma sun shiga cikin ƙangi na mulkin mallakar turawan a ƙarnin daya shuɗe. Babu wani mulki dake da tasiri sama dana sarautunsu tun a farkon ƙarnikan baya har zuwa yau ɗin nan da suke rayuwa bisa mulkin mallakar sarakunan dake mulkin mallakar su. 𝕯𝖆𝖚𝖑𝖆𝖗 𝕽𝖚𝖒𝖆𝖓 itace babbar masarauta da dukkan masarautu ke ƙarƙashin ikonta bama su talakawa kaɗai ba. Itace tamkar fadar shugaban ƙasa a wasu ƙasashe. A maimakon mulkin siyasa, su 𝐃𝐀𝐔𝐋𝐀𝐑 𝐑𝐔𝐌𝐀𝐍 itace babbar masarauta mai faɗa aji akan komai da kowa na ƙasar Ruman, komai yana tabbatuwa ko akasinsa da ƙarfin ikon sarki mai mulki a kujerar wannan daula. Bama gasu talakawa ba, babu wata masarauta a cikin kasar Ruman data isa koda ɗaga murya a bayan idon Daular Ruman saboda karfin ikon mulkin 𝐒𝐡𝐚𝐡𝐚𝐧-𝐬𝐡𝐚𝐧 (King of kings). Ƙarfin mulkin wannan Daula yakai a duk faɗi da ƙasar Ruman ke dashi babu wani mahaluki da zai iya faɗar siffa kai tsaye ko kamanni na sarkin da duk zai mulki daular ruman tun zamanin ƙarnikan baya, saboda tsantsar girmamawa da akema sarakunan wannan Daula ko iya ɗaga kai a musu kallon ƙurulla na kusa babu maiyi, daga nesa kuwa fuskokinsu ababen kwarjinine irin na masu mulki da a ranar wasan al'ada na kowanne shekara ake iya ganinsu a zahiri daga nesa bisa keken doki. A tsari da ƙa'idar daular ruman dukan yarima mai jiran gado daya shiga shekaru bakwai na girma za'a ɗaukesa kowa ya daina ganinsa, a sirrance zaiyi ilimin zamani dana addini dama duk wata rayuwarsa irin ta kowa. Bayan cikar shekarun girma a garesa za'a fara bayyanasa ga sarakunan sauran masarautu cikin shigar da ƙwayar idonsa kawai zasu iya gani. Nuna yarima mai jiran gado ga sauran masarautu na nufin alamar mahaifinsa zaiyi murabus kenan ya ɗaurasa a karagar mulki basai bayan ransa ba. Sarkin kuma da baya buƙatar hakan bazai taɓa bayyana yarima ba ga kowa har sai bayan mutuwarsa. 𝐓𝐚𝐣𝐰𝐚𝐫 𝐇𝐚𝐲𝐬𝐚𝐦 𝐢𝐛𝐧 𝐀𝐛𝐝𝐮𝐥𝐥-𝐌𝐚𝐣𝐞𝐞𝐝 shine sarkin daular ruman daya shuɗe aka ɗora ɗansa ɗaya tilo bisa karaga. Shi kaɗai ya haifa a duniya, shine kawai magajinsa sai mata huɗu da saɗaka daya bari. A yanda tarihi yazo ba'a taɓa 𝐒𝐡𝐚𝐡𝐚𝐧-𝐬𝐡𝐚𝐧 mai ƙarfin iko da daularsa ta gagari duk wani jar fata nunawa yatsa ba kamarsa, ya shimfiɗa mulki a Ruman dama yankin Africa gaba ɗaya, izzarsa da ƙarfin mulkinsa yasa ba masarautun Ruman kawai ba, dukkan masarautun Africa na biye da shi da girmamawa da tsoro mai ƙarfi. Ya tara arziƙi mai ban tsoro da ban mamaki, ya kuma shimfiɗa ayyuka da ba Ruman kawai ba, Africa gaba ɗaya bazasu iya mantawa ba. Kaf ƙasashen jajayen fata masu faɗa aji na tsoro da shakkar 𝐓𝐚𝐣𝐰𝐚𝐫 𝐇𝐚𝐲𝐬𝐚𝐦 𝐢𝐛𝐧 𝐀𝐛𝐝𝐮𝐥𝐥-𝐌𝐚𝐣𝐞𝐞𝐝. Sarki Haysam ya raini ɗansa ɗaya tilo tamkar sauran shuɗaɗɗun sarakuna koma fiye da su, dan saɓanin sauran yarima da tarihinsu ya shuɗe shi wannan yariman tun a shekara uku na haihuwarsa babu wanda ya sake ganinsa kojin labarin inda yake rayuwa. Sai dai a kullum akanji sunansa a bakin Tajwar Haysam fiye da sau goma, ambaton sunansa shine mafi yawan magana dake fita a bakin Tajwar. Hakan kan saka razani da tabbatuwar shi wannan yarima zai kasance na daban a dukkan sarakunan da suka shuɗe kenan. Tabbas hasashen mutanen ƙasar ruman ya rabbata, dan kuwa dai kam da gaske 𝐓𝐚𝐣𝐰𝐚𝐫 𝐄𝐬𝐡𝐚𝐚𝐧 𝐢𝐛𝐧 𝐇𝐚𝐲𝐬𝐚𝐦 𝐀𝐛𝐝𝐮𝐥𝐥-𝐦𝐚𝐣𝐞𝐞𝐝 ya zama sarki na daban a cikin dubban sarakuna, tare da labari mai ban tsoro da razani fiye dana mahaifinsa. Kamar yanda ƙa'idar daular ruman take bayan cikar shekara talatin da biyar yarima Eshaan ya bayyana a ƙasar haihuwarsa ta Ruman, sai dai kamar kowane yarima na baya babu mai iya ganin fuska ko suffarsa ta ainahi, hatta da idanunsa ma shi babu wanda zai iya ganin koda ƙwayar cikinsu sakamakon glass dake sakaye da su. Bayan gama bayyanashi ga masarautu da wata ɗaya kacal Tajwar Haysam bin Abdul-Majeed yay murabus aka ɗaura yarima mai jiran gado bisa kujerar mulkin daular ruman tare da auren mata huɗu galla-galla daga mabanbanta masarautu masu ƙarfin faɗa aji a kasar ruman. Kwanan 𝐓𝐚𝐣𝐰𝐚𝐫 𝐄𝐬𝐡𝐚𝐚𝐧 bakwai akan karagar mulki Tajwar mai murabus Haysam bin Abdul-Majeed ya kwanta jiyya, jiyya ce data girgiza kowa ta kuma bada mamaki, dan kuwa kwanansa ɗaya tak yace ga garinku nan. Kwatanta tashin hankalin da ƙasar Ruman ta shigama a lokacin bazai lissafu ba. Ƙura bata lafa ba mutuwar ɗaya daga matan 𝐓𝐚𝐣𝐰𝐚𝐫 𝐄𝐬𝐡𝐚𝐚𝐧 ta sake bayyana, kwana ɗaya da mutuwarta watama ta sake mutuwa a washe gari amare suka rage saura biyu. Al'amari ya fara saka zukatan jama'a hasashen da babu damar cewa komai. Wata biyu tsakani ɗayar matar ta uku ta sake mutuwa saura ɗaya. Tofa babbar magana. Abu mafi girgiza zukata shine mutuwar ɗayar data rage a shigar sabon wata. Kenan matan Tajwar 𝐓𝐚𝐣𝐰𝐚𝐫 𝐄𝐬𝐡𝐚𝐚𝐧 da mahaifinsa sun gama mutuwa kaf a cikar wataninsa uku da hawa karagar mulkinsa da kuma aurensa. Abun ya taɓa zukata aynun, sai dai babu wanda ya iya ko tari saboda tsoro. Sai dai abu mafi tsayawa arai a cikar wata na shidda aka sake ɗaura auren 𝐓𝐚𝐣𝐰𝐚𝐫 𝐄𝐬𝐡𝐚𝐚𝐧 𝐢𝐛𝐧 𝐇𝐚𝐲𝐬𝐚𝐦 𝐀𝐛𝐝𝐮𝐥𝐥-𝐦𝐚𝐣𝐞𝐞𝐝 da wasu matan biyu daga gidajen masarautun kasar ruman. Labarin bai canja ba, dan kuwa suma sun mutu ɗaya bayan ɗaya kafin cikar shekararsa guda da hawa mulkin. Abin al'ajabi aka kuma sake aura masa wasu biyun daga wasu masarautun, suma ɗin dai kamar ƙiftawar ido nasu labarin ya shuɗe a cikin shekara ɗaya. Haka aka sake ɗaurama Tajwar Eshan aure da wasu mata daga mabanbanta masarautu da tsoro bazai barsu hana auran ƴaƴansu ba, haka kuma suka mutu suma ya kasance duk ya auri yarinyar kowace masarauta goma da suke da su. Zuwa yanzu ba shakka da tsoron ɗaga murya bane kawai a zukatan mutanen ƙasar Ruman, hatta numfashi suna yinsane tamkar ɓerayen dake a ƙarƙashin tsaron maguna. A tunaninku yaya sautin fitar numfashin zai kasance?😭. ★★_________★★ Sunanta shine 𝕱𝖆𝖗𝖊𝖊𝖉𝖆𝖍 na yanka, sai dai iyayeta da dukan jama'a na mata alkunya da 𝑰𝒇𝒇𝒂𝒉. Su huɗu iyayensu suka haifa, itace auta a cikinsu. Hanash! Shine namiji babba. Arfa! ita ke bi masa, Fariha! Itace ta uku, sai ita auta 𝑰𝒇𝒇𝒂𝒉. Sunan mahaifinsu Zayyan!, amma suna kiransa Babiy, mahaifiyarsu Jamaima! Suna kiranta Ummu. Ƙasar Ruman ƙasarsu ce ta gado tun iyaye da kakanni, nan kaɗai suka sani, anan kuma kaɗai suke rayuwa. Kamar yanda na faɗa muku a tun farko ƙasar Ruman ƙasace mai tarin arziƙi nau-i daban-daban da ake kaikawo da su a cikin ƙasa da wajenta, tun daga kan zinare, noma, kiwo, ƴaƴan itatuwa dama wasu daban lissafo ba. Sai dai duk da wannan tarin arziƙi da ALLAH ya basu hakan bai hana kasancewar wasu a cikin matsayin talakawa ba. Kamar dai su 𝑰𝒇𝒇𝒂𝒉, mahaifinsu talaka ne mai rufin asirin ALLAH. Manomi kuma makiyayi, a nomansa harda noman zuma yakeyi. Dukkan wani nau'in zuma zaka samesa a hannunsa, wannan yasa yake mu'amula da daular ƙasar Ruman. Duk da ba masu arziƙi bane su mahaifinsu mutumne mai tsantseni da taka tsantsan, sannan ya tsaya tsayin daka wajen ganin sun samu ilimin addini dana zamani irin na yara ƴan gata. Gidansu gidane mai ban sha'awa da birgewa a ɓangaren mu'amulantar juna mai cike da soyayya da ƙauna. Basu da wani buri sai na faranta ran juna, a koda yaushe zaka samesu cikin nishaɗi dan talaucinsu bai taɓa kasancewa damuwa ga rayuwarsu ba ko nakasu ga farin cikinsu. Idan ɗaya na ciwo sukan kasance tamkar su duka suke ciwon, idan ɗaya na farin ciki sukan kasance su duka cikin farin ciki. Sune abokai kuma kawayen junansu harda iyayensu. Sunada tarin burika na rayuwa dana kai da kai, wasu a rubuce, wasu a ƙayyade a cikin zuciya, wasu a bayyane, wasu a adane a ƙasan zukata. wasu sun cika, wasu ƙaddarorinsu masu ɗaci da saka zubar hawaye dake gudana a halin yanzun sun yanke igiyar kaiwa ga samun cikarsu. Labarin sauyawar tasu, da yankewar tasu ya farane daga wata rana dake dai-dai da cikar sauran kwanaki huɗu na zagayowar bikin al'ada da ƙasar Ruman ke gudanarwa. Ranar da tarihinsu bazai iya gogewa ba, zukata bazasu iya mantawa ba, lissafin faruwarsu da shuɗewarsu bazai taɓa daina maimaita kansa ba koda a bayan rai ne.😭 A kowane karshen wata Babiy ke kai zuma tulu uku daular ruman, amma a duk bikin shekara na al'ada tulu goma yake kaiwa dan shi kaɗai ne yardajje a manoman zuma da sarki ke iya amfani da zumar dake zuwa daga hanunsa tun zamannin Tajwar Haysam. Koda ya mutu kuma 𝐓𝐚𝐣𝐰𝐚𝐫 𝐄𝐬𝐡𝐚𝐚𝐧 bai daina amsa ba. Sai dai kuma duk da wannan yarda a kullum zagaye suke da tsaro ta fannoni daban-daban duk a dalilin zumar da Babiy kan samarwa Tajwar. A ranar data rage sauran cika kwanaki huɗu na bikin al'ada rashin jin daɗin jiki ya saka Babiy bama Hanash damar tafiya dasu duka cikin ƙaton gidan gonat da yake noman zuma domin ɗurasu a sabbin tulunan da za'akai daular ruman. Da'ace yasan anjimarsa ko ƙaddararsa data ahalinsa da bazai taɓa barin wannan lokaci zuwa ba koda a mafarki. Sai dai kash, ƙaddara ta riga fata inji masu iya magana. Cike da farin ciki suka fita, dan kuwa a shekara sau uku kacal Babiy ke barinsu shiga cikin lambunsa. Ba lambun kawai ba, hatta fita koda ta zuwa makarantace suna yintane cikin shiga mai lulluɓe dukkan kamanni, domin kuwa ƴaƴan nasa na ɗauke da wani irin sirrin ƙyawu mai ɗaukar hankalin duk wanda zaiyi tozali da su, dan haka kullum cikin shigar larabawa suke harda niƙabi, idanunsu kawai ake iya gani da tafukan hanunsu, a yau kam sai suka fita a asalinsu batare da sanin iyayensu ba duk da kuwa suna dai sanye da abayoyin, sai dai babu niƙabin. Su kansu da'ace sun san abinda ke biye da rayuwarsu da zasu ninka niƙabi kan niƙabi ne har sama da sau sittin idan zai nisanta zuwan almakashin daya datse walwalin zinaren farin cikin zukatansu. Sun isa lambu sun gudanar da ayyukan da Babiy ya umarcesu cike da farin ciki da nishaɗi, suka tsinko tarin ƴaƴan itatuwa kowa da nasa da burin abinda zaiyi dashi a ranar bikin al'ada dake tunkarosu. shigarsu gida dai-dai da isowar tambura da bushe-bushen algaitu masu ban mamaki da al'ajab a cikin kunnuwansu dama dukkan sauran talakawan gari, dan abune da ba'a sabaji ba sai a wasu lokuta na gittawar Tajwar daga can kan hanya bawai a cikin anguwa kamar hakan ba...........✍ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +22799643131 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_2_* ...........Cikin ƙarfin hali Babiy ya zabura hanyar soro domin dubawa duk da halin ciwo da yake ciki. Baya yaja da sauri saboda cin karo da suka kusayi da tawagar jama'ar Daular Ruman dake ƙoƙarin shigowa suma. Kansa ya rissinar alamar girmamawa a garesu. Hanash da Ummu ma a kusan tare suka zabura. Cike da girmamawa mai haɗe da matsanancin tsoro Babiy ya zube bisa gwuyawunsa. Hakan da su Ummu sukaga yayi ya sasu zubewar suma tare da risinar da kawunansu, jikkunansu na matuƙar tsuma dan abune da ba'a taɓa gani kojin labarin faruwarsa a tarihin ƙasar Ruman ba. Babban mutum dake jagorantar tawagar ya tsaida idanunsa akan Babiy. “Ya kai wannan talaka dake a ƙarƙashin mulkin daular ruman, munzo da babbar magana ne gareka bisa umarnin daular ruman”. Ƙasa Babiy ya ƙarayi da kansa, tare da haɗe hannayensa waje guda. “Ina mai matuƙar farin cikin ganinku tare dani, ni mai biyayyane ga kowanne umarninku”. Duk da maganar Babiy ta musu daɗi babu alamar hakan a fuskokinsu. Ya miƙe cikin rawar jiki zuwa ɗakin Ummu. Mintuna kaɗan ya dawo da babbar tabarma sabuwa ƙal data saya domin auren Arfa zai shimfiɗa a gabansu. Dakatar da shi Shugaban tawagar tasu yayi cikin ɗaga hannu. *_“Munzo nan ne domin isar da saƙo ba zama ba ya kai wannan talaka dake a ƙarƙashin daular ruman. Umarni a gareka daga daular ruman, taga iri a gidanka kuma tana buƙata. Muna mai tayaka farin cikin zama ɗaya daga cikin surukan tarihin daular ruman”_*. A matuƙar firgice Babiy da iyalansa duka suka ɗago cikin zabura da matasanancin rikicewa. Sai dai basu da ikon koda motsa bakunansu balle neman ƙarin bayani. Kasancewar ba amsa dama suke buƙata ba mutumin ya janye idanunsa daga Babiy ya maida kansu Arfa da suka ƙanƙame hannayen junansu. “Wacece babba a cikinku?!”. Kalamai huɗu masu ƙarfin razani da neman fasa zukatan mai saurare da har abada bazasu bar amsa sauti cikin zuciya da ɓargonsu ba suka fita daga bakin ɗaya daga firɗa-firɗan samudawan dake zagaye da mutumin. Babu wanda ya iya motsawa a cikinsu, dan kuwa sake dulmiya suke a cikin duhuwa..... Saukar sautin wata zabgegiyar bulala mai adon jikin zakanya a jikinta ya sakasu zallo baki ɗaya. Babiy ya zube a ƙasa saboda azaba na raɗaɗin shigar wannan bahaguwar bulala a jikinsa, ganin basamuden mutumin dake riƙe da bulalar ya sake ɗagawa zai zuba masa Arfa ta miƙe tana mai fashewa da kuka jikinta na karkarwa tace.. “Nice!”. Cikin daka tsawa basamuden hadimin yaba Fariha da Iffah umarnin suma su ɗago. Ɗagowa sukai jikkunansu na karkarwa ga hawayen tausayin mahaifinsu ya wanke musu fuskoki. Idanu ya zuba musu kusan na sakan goma, kafin ya janye ya maida ga shugaban tawagar tasu.... “Zancenta nakan gaskiya ALLAH ya ƙara maka lafiya”. ya faɗa cikin girmamawa ga shugaban tawagar tasu. Shugaban ya gyaɗa kansa shima idanunsa akan Arfa “Mahaifinta da ɗan uwanta zasu zama waliyyanta”. Ya faɗa cike da cika umarni yana mai nufar hanyar fita batare da wani ƙarin bayani ba...... Har aka tafi da Hanash da Babiy babu abinda su Fariha suka fahimta, balle ma Iffah da kallon kowa kawai take. Kukan Ummu ne ya dawo da su hankalinsu, gaba ɗayansu sukai kanta. Ummu dake kuka kamar ranta zai fita ta haɗasu su duka ukun ta rungume jikinta na wani irin rawa...... ★★_______★★ Tafiyarsu da kamar awanni uku Babiy da Hanash suka dawo gida da doki ɗaya da tarin kayayyaki, sai rakuma guda uku. Fuskokinsu cike suke da firgici mai tsayawa a zukatan masu kallo. Ba abinda sukazo da shi bane a gabansu Ummu, burinsu susan mike faruwa? Kawai. Basu samu amsa ba daga garesu har bayan shuɗewar wasu awanni, kafin Babiy ya basu amsa cikin dakewa.... “Na bada aurenta ga *_Shahan-shan_*, bamu baro ba sai da aka ɗaura musu aure, wannan raƙuman da dokin sadakinta ne”. Ya ƙare maganar idonsa akan Arfa. Tamkar saukar aradu mai tarnatsa haka furucin ya isa cikin kunnuwansu, Ummu tai baya zata faɗi Babiy ya riƙota, kansa yake girgiza mata alamar kartace komai, suma yaran ya juyo garesu yay musu nuni da shiru ya jata suka shige ɗaki. Umarnin mahaifinsu shine mafi girman biyayyarsu garesa matsayinsu na waɗanda ke rayuwa a ƙarƙashinsa, badan sun so ba suka zaɓi shiru, sai dai shirun nasu bai hanasu haɗe kai a ɗaki suyi kuka ba su ukun. Kuka irin wanda za'a kira kuka a duk idaniyar da zubar hawaye ke kwaranya na rashin lissafin ƙididdiga. Mintuna sun shuɗe, hakama awannin da suka ƙarasa kalmashe wannan yinin. Bayan sallar magrib saiga motoci da tawagar hadimai tare da wasu hamshaƙan mata huɗu wai sunzo ɗaukar Amarya Arfa. Kuka suke tamkar ransu zai fita, haka sunaji suna gani suda iyayensu aka shirya Arfa cikin shiga ta alfarma aka wuce da ita Daular Ruman. Dare ya riski zukatansu cike da damuwa, yayinda sai ɓarawo mafi iya satane ya samu nasarar sama musu nutsuwar wucin gadi wato barci. Sun wayi gari kunnuwansu a buɗe na jiran jin labarin mutuwar ƴar uwarsu, sai dai babu wani alamar hakan har sake shuɗewar kwanakin zuwan ranar bikin al'ada. Babu fashi aka gudanar da bikin al'ada na ƙarshen kowace shekara. Sai dai su a zuri'arsu babu wanda ya leƙa koda ƙofar gida. Anyi an gama, kamar kowace shekara an samu rashin rayuka a wasanni daban-daban, da kuma haɗarin mota dana mashina suma a tituna daban-daban saboda cinkoson jama'a dalilin garin shine babban birni da Daular Ruman ke ciki. Bikin al'adar ƙasar ruman kuma yana ɗaya daga cikin biki mai tsananin ƙayatarwa da mutane daban-daban suke halarta daga sassan duniya ta ko ina. Shahan-shan ya fito zagaye tamkar kowace shekara cikin shiga ta alfarma, bashi a karan kansa ba hatta keken dokinsa ma abin kallo ne, sai dai a wannan karon ma babu wanda zaice ga kamanin Tajwar Eshaan ibn Haysam Abdull-majeed ɗin. ★ A haka lokaci ya ƙara turawar da kwanaki suka zama watanni kusan uku. Shuru na waɗannan watanni bai sama musu wata nutsuwa ba, dan a kallon farko da mai gani zaima gidansu zai san akwai matsala tattare dasu. Komai ya sauya, sauyawa irin wadda ƙaddara ta shigo cikin tarihinsu. Babu mai walwala a cikinsu, komai na ƙarfin hali sukeyi, abinci ya gagara ciyuwa yanda ya kamata a koda yaushe garesu, sai cin ƴaƴan itatuwa, tunkan a sanar musu alamominsu sun tabbatar da zaman makokinsu. A haka duhun wani dare na cika watanni uku da kwana uku da auren Arfa ya sake riskarsu, suka sake zama ƙarƙashin mulkin mallakar ɓarawo mafi iya sata koda shiri ko babu wato (barci). Daren da yazo ma Iffah da wasu irin munanan mafarkai masu firgici daban tsoron. Har rige-rigen fitowa suke daga ɗakunan barcinsu sakamakon fitar sautin razananniyar ƙarar data karaɗe gidan mai ban tashin hankali. Su duka huɗun suka rufu a kanta kowa na ambaton sunanta da kai hannu jikinta. Duk da sanyi da akeyi jike take sharkaf da zufa ga illahirin jikin nata daya ɗauka zafi. Ummu ta rungumeta tana mai sakin hawayen da ke kwance a cikin idanunta. Ta riga ta farka dan haka itama ta ƙanƙame Ummun tana fashewa da nata kukan. Ba yau ne karan farko da Iffah ke shiga irin wannan tsoron ba sakamakon firgici a mafarki, sai dai na kwanakin nan yafi razanarwa da saka ruɗani a zukatansu. Babiy ya kai hannu ya shafa yalwataccen gashin kanta, murya a raunane yake ambatar sunanta.. Kanta ta ɗago a hankali fuskata sharɓan da hawaye, ta dubi mahaifin nasu da Yayansu Hanash da Fariha, sassanyar ajiyar zuciya ta sauke tare da haɗiye sauran kukan tana tashi zaune daga jikin Ummu ta share hawayen dake jiƙe da fuskarta. Matsawa tai jikin mahaifinsu tana mai kamo hanunsa. “Babiy inajin tsoro, matuƙar tsoro a wannan mafarkin fiye dana kullum. Babiy itama Nina Arfa kashemana ita zasuyi kamar sauran matan daya aura?, itama zamu rasata na gani a mafarki na...” Da sauri Hanash da dukkan rauninsa ya bayyana a fuskarsa ya shiga girgiza mata kansa cikin aro jarumta. “Mafarki ba gaskiya bane Iffah, ki kwantar da hankalinki Arfa na cikin ƙoshin lafiya tamkar mu insha ALLAHU...” “Amma Akh Hanash nawa yasha zama gaskiya, a daren da Nina Arfa zata bar gidan nan irin wannan mafarkin nayi a kanta, yau ma shine na maimaita da ita babu banbanci a cikinsa na rantse maka”. Har ƙasan zukata zancen nata ya dake su, ganin bayyanar rauni a fuskokinsu ya saka Babiy yin murmushin ƙarfin hali yana shafa kanta. “Shaiɗanu zasu iya dawo miki da makamancin sa ai Ibnati, dan haka ki kwantar da hankalinki Arfa na lafiya a gidan aurenta”. Bazata cigaba dayin jayayya da su ba, amma tana cikin matsanancin damuwa tamkar yanda take hango tasu akan fuskokinsu. Maimakon komawarsu barci sai duk suka miƙe zuwa tsakar gida, alwala suka ɗauro, suka koma can runfar dake matsayin falon iyayensu suka fara salla da miƙa kukansu ga UBANGIJIN talikai da fatan hana tabbatuwar abinda zukatansu ke cikin tsananin fargaba. Haka suka kasance har sallar asubahi gaban mahaliccinmu, bayan idar da sallar asubahi maimakon kwanciya sai suka riski kansu a zaman jugum-jigum na jiran tsammani. Har fitowar rana babu wani yunƙuri daga ɗayansu. Sai ko ga isowar abinda suke fargabar ya riskesu ya iso garesun. Shigar bugun gidan a cikin kunnuwansu ta sakasu miƙewa a zabure gaba ɗaya kuma a lokaci ɗaya, kowanne cikin rawar jiki da fidda tsammani. Babiy ne yay jarumtar ƙarasawa ga soro cikin jan ƙafa. Tunda yay tozali da hadiman masarauta zuciyarsa tai wata irin masifar wulƙitawa..... “Kun kasheta itama ko?!”. Da shi da hadiman suka riski muryarta a cikin kunnensu a bazata. Sam babu tsoro ko shakka irin wadda akema duk wani mai alaƙa da masarauta a ƙasar cikin idanunta a yau. Sun soye sunyi jazur irin na tashin hankali. A harzuƙe cikin hadiman ɗaya ya daka mata tsawa da faɗin, “Hattara ɗiyar talakawa, bakin rijiya ba wajen wasan yaro bane”. “Idan yaron ya kasance rago ba!!”. Ta bashi amsa itama a tsawace. Shimfiɗeɗiyar bulalar hanunsa ya ɗaga zai zuba mata Babiy ya kare cikin rawar jiki yana mai zubewa ƙasa a kan gwiyawunsa. Sosai a zaba ta ratsashi, ya rimtse idanu cikin aro dakiya da jarumtar dole, “A gafarceta ita ɗin yarinyace masu nasara”. Ya faɗa cikin rawar murya saboda azabar tasirin shigar bulalar. Ƙasa Iffah takai durƙushe gaban Babiy tana mai fashewa da kuka, kafin ta ɗago ta dubesu zatayi magana Babiy yasa hannu ya rufe mata baki jikinsa na tsuma. Jikin nata itama tsumar yakeyi, sai dai ita bana tsoro bane na tsananin baƙin ciki ne da bushewar zuciya. So take ta amayar da abinda ke bakinta an hanata. Batare da hadiman sun sake bi takantaba suma suka isar da saƙon dake tafe da su. “Kasancewarka mai biyayya da bin umarnin masarauta a karo na biyu an sake baka damar halartar jana'izar ɗiyarka kai da zuri'ar ka. Mun barka lafiya”. Innalillahi wa-inna'ilaihirraji'un. Babiy ya shiga ambata, kusan a tare Ummu da Fariha suka saki razananniyar ƙara wadda ta jawo hankalin maƙwafta da mutanen dake tsaitsaye a ƙofar gida tun wucewar hadiman masarauta. Dan sun san dai labarin gizo bazai wuce na ƙoƙi ba........ *_WASA FARI GIRKI_* Dole ne zuri'ar mal. Zayyan su ambaci rasuwar Arfa da kalmar WASA FARIN GIRKI a jerin zaren ƙaddarar da ta kutso a rayuwarsu mai ɗauke da almakashin da ya datse farin cikinsu. Sun rasata tamkar labarin hikayoyin marubuta ko wasan kwaikwayo na film. Ta tafi tafiyar da bazasu sake ganita ba, tafiyar da babu wanda aka bawa damar yin cikkakkiyar sallama da ita a cikinsu hatta mahaifansu. Ta shuɗe a ƙaddararsu tamkar yanda ruwan damuna kan tafi da duk wani yayin dakan tare masa hanya a lokacin wucewa. Komai ya faru tamkar ba'aiba. Babu mai iya koda tari balle bin ba'asi. Iyakarsu kukan idanu dana zuci wanda muryarsu kan tsayane kawai iya filin gidansu ko katanga basu isa bari ta haura ba. A yau ma dai Babiy da Hanash ne sukaje domin jana'izarta. Suko aka barsu da amsar gaisuwa a cikin gida wadda mutanensu talakawa na zuwa musu itane a ɗarare....... Kwanaki sun cikagaba da shuɗawa tamkar ba'ai komai ba, yayinda ɗayar matar Tajwar da aka aura masa tare da Arfa itama dai ta mutu bayan wasu watanni. Bayan su Arfa ba'a sake jin Tajwar yayi wani aure ba, sai dai mutane na raɗeraɗin a duk randa aka kaisu domin ziyartar turakarsa babu fashi gawarsuce take fitowa. Hakan yasa kowa ke danganta mutuwar matan da tsafi yakeyi dasu. Wata huɗu da sati ɗaya cif tarihi ya sake maimaita kansa, dan kuwa Fariha ta sake faɗowa a jerin matan da aka ɗaurama Tajwar Eshaan ibn Haysam Abdul-majeed aure da su. Batare da wani shawara ba a safiyar alhamis suna zaune kira ya riski Babiy daga masarauta, babu wanda bai shiga tsoro da firgici ba a cikinsu, sai dai babu wanda ya isa hana hakan a duk faɗin ruman. Sunaji suna gani babiy yay shiri ya amsa kiran. Tafiyarsa da awanin da basu gaza biyar ba sai ga hadiman masarauta sunzo sunma Fariha ɗaukar amarya itama babu wani bayani daga garesu. Ranar dai kam Iffah bata gazaba kojin tsoro wajen gwada musu hauka, dan bata bari an fita da Fariha ba har sai da basamuden nan ya zabga mata bulalar dorinar hanunsa data sakata zubewa, bata tashi dawowa hayyacinta ba sai bayan wucewarsu da kusan awa guda. Zuwa lokacin har Babiy ya dawo. Kamar dai Arfa itama Fariha an ɗaura mata aure da sarkin da kowa yake masa inkiya da fir'aunan wannan ƙarnin. Sai dai a ɓoye wannan suna ke fita a bakunan talakawan gari irinsu Iffah. Sakamakon bulalar da aka zabga ma Iffah bayanta yay mugun fashewa har akan mazaunanta, ga wani raɗaɗi mai azaba na ratsata har ta kasa riƙewa sai da ta saki ƙara. Babiy da Ummu suka rufu a kanta, hawaye suke suna jeramata sannu, Hanash na gefe zaune idanunsa jajur alamar tsananin ɓacin ran da babu ƙarfin ɗaukar mataki...... Tayi jiyya ta kwanaki uku, wajen ya warke, daga haka kwanaki suka cigaba da tafiya, inda a cikar watanni biyu itama Fariha mutuwarta ta riskesu tamkar ba'ayita ba. Sun sake rasa Fariha a dalilin auren Tajwar Eshaan ibn Haysam Abdul-majeed........✍😭 *_Hummmm!!😕🤌🏻_* *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +22799643131 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafarta ma iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_3_* _____________ _*MAAB LUXURY HOME!!* Sabuwar duniyar hamshakan mata da ƴaƴan gata.💞_ _*GIDAN* ƙawa da ƙawata gidajen da suka cika gida._ _*SABUWAR DUNIYAR* Amare da uwargidan data amsa sunanta ƴar gaban goshi._ _*MAAB LUXURY HOME* wata duniya ce ta ƙawa da ƙawata gidajenmu da kayan ƙyale-kyale na burgewa da ɗaukar hankalin duk wani mai kallo_. _*SUNYI FICE* Fice irin na ɗaya a cikin tsara, sune na farkon fari, a farin da za'a kira fari a kowace irin duniya._ _*A GAREMU* ba sitturu na alfarma da kawa ne kawai ke tabbatar da mu hamshakai ba. Sai mun haɗa da ƙawata gidajenmu da kayan MAAB LUXURY HOME zamu kasance cikakkun ƴan gata ababen kallo da nunawa sa'a koda a cikin dubun da sukafi dubu._ _*MAAB LUXURY HOME* sun takaita mana dukkan wahalar nema ko order a kasashen ketare ta hanyar wadatamu da galla-gallan kayayyakin adon gidajenmu_ _*MAAB LUXURY HOME.* Duniyar kayan Kitchen da decoration din gida na keta raini._ _*INA UWARGIDA INA AMARYA!!?* Ku ziyarci shagon mu dake No 22 Ahmadu Bello Way, Kano state. Ko kuyi order daga shafin mu na Instagram @maabluxuryhome. Ko Facebook @maabluxuryhome. Ko Ku nememu a lambar waya *08034631010*._ *_Mai azama shi za'a kira dana farkon fari😉. Bara nai sauri nawa suzo hannuna kafin a kwashe😁⛹🏼‍♀️⛹🏼‍♀️⛹🏼‍♀️._* ______________ .........A wannan gaɓar haukane kawai ya rage wannan ahali suyi, dan duk dauriyar Babiy ya kasa danne raɗaɗi da zafin da yakeji. Itako Iffah kalaman dake fita a bakinta kausasa sun saka kowa ke ɗaukar tama zare kawai. Daga ƙarshe maganin barci aka ɗura mata. Bata tashi farkawa ba sai a ƙauyen da kakanninsu ke rayuwa. Wato iyayen Ummu. Rayuwa a ƙauyen Jumna a gareta tamkar mai gushewar hankali ya zame mata. Domin bata gane komai sai sambatu da kalamun ɗaura ɗammarar ɗaukar fansa ga duk ahalin Daular Ruman. Ba ƙaramin dagewa da jajircewa kakannisu da su Babiy sukai ba a kanta wajen ganin ta samu lafiya ta dawo hayyacinta. A cikin watanni takwas ta rasa yayunta guda biyu, wannan babban tarihine da bazai gogu a zuciya da ruhinta ba har karshen rayuwarta. Bayan jiyyar watanni kusan uku ta dawo hayyacinta. Sai dai ta daina fira'a da kowa, an daina ganin dariyarta ko farin cikinta. Babu abinda ke'a ranta sai buri da ƙudirin ɗaukar fansa. Tama kanta alƙawarin ita da hannunta zata kashe *_Tajwar Eshaan ibn Haysam Abdull-majeed_*. Bayan nan idan itama an kasheta burinta ya cika na kawar da azzalumin sarki mai mulki irin na fir'auna a ƙasarta a cikin al'ummarta.... *_(Babbar magana. Tayaya wannan buri naki zai cika Iffah😱? Sarki mai cikakken iko irin Tajwar Eshaan, mai amsa sunan Shahan-shan da ko fuskarsa babu wanda ya iya sani a cikin kasar Ruman har yanzun. Anya kuwa....? To mudaije zuwa wai mahaukaci ya sai kura😬🤧🚴🏼)_* ★★★ “Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un” bakinta ke ambata cikin firgici da rawar jiki sakamakon farkawar da tayi daga mummunan mafarkin daya risketa a cikin barcinta. Ta dafe kanta dake wata irin sarawa na ciwo tamkar ana mata luguden taɓaren daka a tsakkiyarsa, gaba ɗaya jikinta ya jiƙe da zufa tamkar tayi wanka. Kusan watanni biyar kafin mutuwar ƴan uwanta da fara canjawar salon mafarkainta saɓanin na baya, abu mafi tsoratarwa kuma kusan mafarki ɗaya ne ke maimaita kansa a kowane barcinta idan ta kwanta. Sai dai mafi tashin hankalin a yau yayi kamanceceniya da na wasu dare da tarihi bazai taɓa mantawa da shi ba a cikin rayuwarsu ita da ahalinta. “Nina Arfa! Nina Fariha!”. Ta ambata a zahiri zuciyata na ƙara ƙarfin gudu, yayinda hawaye suka shiga rige-rigen sauka a kumatunta. Tabbas irin wannan mafarkin tayi a daren da suka rasa Arfa, hakama daren mutuwar fariha. Yau kuma gashi ta maimaitashi akan kanta. Itama kenan zasu rasata?. Kai ta shiga girgizawa wani kuka masu ƙarfi na sake tahomata, hannu tasa ta toshe bakinta gudun kar sautinsa ya kai ga kunnen kakanninta. Sai dai aikin gama ya gama. Dan kuwa muryar kakanta takeji jikin ƙofar ɗakin nata a hankali yana ambatar sunanta. Da sauri ta shiga goge hawayen, kafin ta tashi daga shimfiɗar barcin nata wadda karan gado ne da katifar rimi. Mayafi ta ɗauka ta yanama jikinta, ta ƙarasa ga ƙofar ta buɗe... “Kina lafiya kuwa ɗiyar nan?”. Ya faɗa cikin kafeta da idanu. Kanta dake rissine ta jinjina masa, cikin son danne kukan dake yunƙuromata ta bashi amsa. “Ina lafiya Kaka”. Jin shiru bai sake cewa komai ba ta ɗago ta dubesa a karon farko. Shima dai kallon nata yakeyi tamkar mai nazari. Sake maida idonta tai ƙasa, hawayen da take faman riƙewa suka ɓalle mata da gudu. Bata san ta ambaci “Kaka nima zasu kashe muku ni ko?. Inaji a jikina nima zaku iya rasani nan kusa tamkar yanda muka rasa su Nina Arfa”. Rawar da jikinta ta fara ta sata zubewa a gabansa kuka na ƙwace mata. Kusan minti biyu baice da ita komai ba, ita kuma ta kasa tsaida kukan.. Jin saukar hanunsa saman kafaɗarta ya sata haɗiye kukan, ya ɗagota tsaye yana ɗan murmushi dake sake bayyana tsufansa. Gefen mayafin jikinta ya kama ya shiga goge mata hawayen. “Fareedatu! Ki kwantar da hankalinki, insha ALLAHU babu abinda zai faru da ke, mafarki ai ba gaskiya bane ba. Suma su Arfa kwanansu ne ya ƙare, koba komai kuma sun rasu a gidan aurensu. Wannan kawai ya ishemu farin ciki”. Kanta ta jinjina masa tana sauke ajiyar zuciya a jajjere. Ya cigaba da shafa kanta a hankali har zuwa wani ɗan lokaci. “Kije kiyi addu'a ki kwanta abinki da safe zamuyi magana”. A hankali tace, “Kaka ina son zuwa naga su Ummu gobe to dan ALLAH”. Da sauri ya girgizamata kansa. “A'a bazai yuwu ba Iffah, iyayenki sun kawoki nan ne domin kuɓutar dake, taya kike tunanin zan barki komawa cikin daular Ruman?. Tun ina ƙanƙanin yaro nake bauta wa masarautar Ruman, bayan mutuwar mahaifina na cigaba da bautar saƙa kayan doki a garesu kamar yanda mahaifina ya barmin gado, a haka na haifi ƙanin mahaifiyarku shima ya mayeni, gashi har girma ya riskesa shima yana bauta musu. Mun rasa ɗan uwan mahaifiyarku a yaƙin kare daular Ruman, mun rasa Arfa, da Fariha. Ke ɗaya da kika rage mana da yayanki wajen mahaifiyarku kuma sai muyi wasa da rayuwarki? Bazai yuwuba jeki kwanta...” Batare daya sake bata damar yin magana ba ya juya ya koma bayan ya jamata murfin kofar. Da kallo kawai ta bisa hawaye na silalo mata. Duk yanda taso komawa barcin bayan tafiyarsa hakan ya gagara, zuciyarta ta kasa fita da ga ƙangin fargaba, da gaske tanajin matuƙar tsoro bayan rasa Fariha da Arfa da sukai watanni ƙalilan da suka shuɗe itama su rasata, tanaji zuciyar ahalinta bazata iya ɗauka ba idan itama suka rasatan. Wasu zafafan hawaye suka sake silalo mata masu raɗaɗi da saka ƙuna a ƙirji...... ★★★ “Iffah! Iffah!!.....” Sautin ƙwala kiran sunanta daga muryar kakarsu da suke kira Iyyani ya sakata fitowa daga banɗaki data zagaya domin yin fitsari. Turus ta tsaya tare da haɗiye maganar da zatayi tana mai kallon ɗan-uwanta Hanash dake zaune gefen kakar tasu a ƙarƙashin bishiyar ɗoruwa da take a tsakar gidan. Murmushin da yakemata ta maida masa, kafin ta ajiye butar hannunta ta ƙarasa garesa. Dab da shi ta zauna tana mai ɗan rungumesa ta gefe da faɗin, “Ina kewarku Akhi”. Murmushinsa ya sake faɗaɗa yana mai kallon fuskarta. Ya kai hannu ya shafi yalwataccen gashin kanta da mayafin ya zame mai tsaho da santsi. “Muma muna kewarki Little angel. Gidan duk ya sake zama mana babu daɗi”. Yanda maganar tasa ta ƙare cikin rauni itama sai idonta ya cika da ƙwalla. Amma sai ta dannesu da murmushin mai ɗaci tana kaɗa kanta kawai. “Tashi ki bashi ruwa mana, k haka ake tarbar baƙo a garinku”. Baki ta ɗan tura gaba da kallon Iyyani mai maganar, tayi hakane danta katse raunin data hanga a fuskokinsu. Ta miƙe tana bata amsa cike da shagwaɓa. “Iyyani laifinkine fa, ban taɓa ganin matar da bata tattalin mai gida ba irinki, dole Yayana ya miki kishiya”. Daƙuwa tamata cikin gatsina fuska. “Ungo naki nan Fareedah, yo bandama lalacewa mizanyi da wannan faratun mai kama da jar tsada tuzurin banza”. Hanash ya tsuke fuska yana kallon Iyyani. Murmushi Iffah tayi tun kafin ya faɗi abinda ke bakinsa. Dan dama inhar suka haɗu da Iyyani sai ta hasalashi take jin daɗi shi da Arfa akan ƙinyin aure, duk da bawani shekarune da shi ba, dan ashirin da shida ne kawai, Arfa nada ashirin da uku, Fariha nada ashirin da ɗaya. Iffah nada goma sha takwas.... Iffah ta dire masa abinci da ruwa ta sake kaiwa zaune kusa da shi sannan ta dubesa. “Akhi yasu Babiy suke?”. Ya nisa a hankali bayan ya dire moɗar ruwan daya sha. “Duka lafiya suke. Suna gaisheki ke da su kaka. Duk da suma dai nan da kwana kusa zamu ma dawo nan ɗin muma. Yanzu haka nazo duba can tsohon gidanmu ne dan asan gyaran da za'ai masa”. Sosai ta kafesa da ido ita da Iyyani. Kafin cikin ƙarfin hali Iffah tai magana. “Amma Yaya su Babiy basa ganin rayuwa zata mana wahala anan sakamakon bamu sababa sam. Sannan ayyukansu dake acan miye makomarsu? Da karatunmu muma?. Abinda ya faru ya riga ya faru, tunda hannayenmu bazasu iya maidosu ba, mi zaisa zukatanmu bazasu cigaba da haƙuri ba. Barowarmu cikin Daular ruman tamkar munji tsorone, ko sake sakin rayuwarmu a hanun waɗanda kansu kawai suka sani.......” “Tsoro halak ne Iffah. Bama muba mafi yawan masu yara mata sunata barin daular ruman a yanzu domin tseratar da ƴaƴansu daga auren jeka nayika. Karatun ƴammata yana neman tsayawa cak, kowace na tsoron fitowa ta zama nama a hanun hadiman daular ruman. a yanda lissafin yake a yanzu an rasa mata goma sha huɗu fa, a tunaninki kafin ƙarewar wannan shekarar ba'a rasa fin hakaba duk da bawai ya cigaba da auren bane.” Wasu hawayene masu ɗaci da ƙuna suka silalo ma Iffah, tai saurin saka gefen mayafinta ta share tana murmushin takaici. “Niko a ganina gudu bashine mafita ba, muryoyinmu ya kama mu ɗaga wa duniya kowa yasan halin da muke ciki, idan har a ƙasar Ruman babu wani sama da nasa mulkin ai a sauran ƙasashen duniya akwai wanda suka fisa...” “Humm Iffah ke yarinya ce har yanzu.” “Sosai kuwa Hanash. Shiyyasa bata gane komai sai abinda yanzu take zuwa da shi”. “Humm Iyyani kenan”. Iffah ta faɗa a yanayin jin raɗaɗi a maƙoshinta. Su duka kallonta sukai, sai dai ta ɗauke kanta gefe tamkar bata gansu ba. Daga haka babu wanda ya sake cewa komai har tsahon wani lokaci. Iyyani ce ta canja hirar da wani abu daban har Hanash ya kammala. Tare da shi suka fita wajen duba tsohon gidan da kakaninsu da suka haifi Babiy ne suka rayu a ciki, dan sudai tunda suka taso a cikin birinin daular ruman suka san kansu duk da a ɗan gefen gari suke acan ɗin ma. Sai dai su shigo cikin ƙauyen Jumna a matsayin duba kakannin nasu. zuwa yanzu su duk sun rasu, shiyyasa gidan ya kasance babu kowa. Duk ma ya rusa ya fita hayyacinsa dan ginine na jar laka tamkar yanda duka gidajen ƙauyen suke. Sun ɗan jima acan suka dawo, sun iske kaka ya dawo shima daga fitar da yay tun ta safe gona ɗebo sassaƙe-sassaƙen magunguna. Ƙara zaman tattaunawa sukayi iya su uku, ita dai Iffah bata cewa komai. Daga ƙarshe ma tashi tai ta shige ɗakin kwananta. Bata sake fitowa ba sai da kaka ya neme ta. Sassaƙe-Sassaƙen magungunan daya ɗibo ɗazun ne a gabansa, kowanne ya ɗauresa daban-daban. Ya turamata babban robar da suke ciki... “Zaki fara amfani da su Iffah, bana son kiyi wasa dan ALLAH. Waɗannan kuma hayaƙine, a kowacce duhun magriba ki tabbatar kinyi turarensu, wannan kuma a ruwan wanka ne, da kin idar da sallar asuba ki zubasu cikin ruwa kaɗan ki cire kayanki ki tabbatar duk jikinki ya samu”. “Tofa kaka wannan ɗin kuma duk na miye?”. Iffah ta tambaya cikin nuna mamaki. Idanu ya tsiramata na kusan mintuna uku tamkar mai nazari, sai kuma ya ɗauke kansa da wani yanayi mai wahalar fassara. “Faruwar ƙaddararmu bashi ke nuna baza'a sake jarabtarmu ba. Idan jiya ta shuɗe da ɗaci zata iya yuwuwa yau ɗinmu da dariya zata kasance, sai dai sanin mike a gobenmu al'amarine mai girman gaske, damin gaibunmu ce ita ALLAH ne kaɗai masanin mi zaizo.” Kallon juna sukai ita da Hanash, Iffah ta ɗan ɗage kafaɗa cikin yanayin ban fahinta ba, shima sai ya kaɗamata idanu alamar shima hakan take. Atare suka maida dubansu ga kaka. Amma sai ya kauda kansa alamar baya buƙatar kowacce irin tambaya daga garesu. Iffah ta jinjina kai kawai alamar ko'oho. Sai kuma ta miƙe tana mai faɗin, “Ni dama fa na yanke shawarar zanbi Akhi mu koma. Tunda dai naji sauƙi gara naje na koma makaranta anata wuceni a darasi”. Ba karamin waro idanu Hanash yay ba, zaiyi magana kaka ya dakatar da shi ta hanyar yin murmushi da kaɗa kansa. “Ita rayuwa rubutacciya ce tunkan halitta, an rubutatane da alƙalamin da ba'a goge rubutunsa, babu wani hannu daya isa gogeta koda da ƙarfin iko. Dole ne sai anyi hakan, ko muna so ko bama so mashin nan sai ya isa inda aka aikashi. Domin ita *KIBIYAR AJALI! SULKE BAYA TARETA SAI TA GITTA*”. A rikice Hanash ya tari numfashinsa. “Kaka bana gane dunƙulallun zantukan nan naka, ka fito fili dan ALLAH ka sanar mana mi kake son faɗa...” “Hanash! Lokacin faɗar baiyiba ai, nima kurman baƙin kawai na gani, fassarar sai UBANGIJI”. Sosai Hanash ya sake tsare fuskar kaka da idanu, kamar yanda itama Iffah tai tsai tana kallon nasa. Su dukansu sun jima da sanin kaka mutum ne hatsabibi, dan kuwa mahaifinsa gawurtaccen masanine da azamaninsa akan kallesa tamkar matsafi ko wani mai gani har hanji, sai dai kasancewar bai ajiye buzu ya zauna akan iya wannan al'amarin ba yasa ake shakkar faɗa, yana bada taimako na magani akan abubuwa daban-daban musamman harkar aljanu komai ƙarfinsu da shaiɗancinsu. Sannan yana sana'arsa ta saƙa kayan kwalliyar doki. Kaka ya gaji abubuwa da dama a garesa, sai dai shi ya watsar da harkar bada maganin dan shima dai a karan kansa yana ta'allaƙa sanin mahaifin nasa da bokancin, duk da dai bai fito fili ya bayyana hakan ba kuwa, amma rashin maida hankali akan abinda ya shafi hakan zaisa ka zargi ko haka ɗinne. Akwai kayan aiki na mahaifinsa da yawa a killace a wani waje da shi kaɗai ya sani, kuma tun bayan mutuwarsa shi ya tattare su ya killace su............✍ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +22799643131 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_4_* _______________ _*MAAB LUXURY HOME!!* Sabuwar duniyar hamshakan mata da ƴaƴan gata.💞_ _*GIDAN* ƙawa da ƙawata gidajen da suka cika gida._ _*SABUWAR DUNIYAR* Amare da uwargidan data amsa sunanta ƴar gaban goshi._ _*MAAB LUXURY HOME* wata duniya ce ta ƙawa da ƙawata gidajenmu da kayan ƙyale-kyale na burgewa da ɗaukar hankalin duk wani mai kallo_. _*SUNYI FICE* Fice irin na ɗaya a cikin tsara, sune na farkon fari, a farin da za'a kira fari a kowace irin duniya._ _*A GAREMU* ba sitturu na alfarma da kawa ne kawai ke tabbatar da mu hamshakai ba. Sai mun haɗa da ƙawata gidajenmu da kayan MAAB LUXURY HOME zamu kasance cikakkun ƴan gata ababen kallo da nunawa sa'a koda a cikin dubun da sukafi dubu._ _*MAAB LUXURY HOME* sun takaita mana dukkan wahalar nema ko order a kasashen ketare ta hanyar wadatamu da galla-gallan kayayyakin adon gidajenmu_ _*MAAB LUXURY HOME.* Duniyar kayan Kitchen da decoration din gida na keta raini._ _*INA UWARGIDA INA AMARYA!!?* Ku ziyarci shagon mu dake No 22 Ahmadu Bello Way, Kano state. Ko kuyi order daga shafin mu na Instagram @maabluxuryhome. Ko Facebook @maabluxuryhome. Ko Ku nememu a lambar waya *08034631010*._ *_Mai azama shi za'a kira dana farkon fari😉. Bara nai sauri nawa suzo hannuna kafin a kwashe😁⛹🏼‍♀️⛹🏼‍♀️⛹🏼‍♀️._* ________________ .........Iffah tayi mamaki da kaka ya bari salin alin tabi Hanash washe gari, duk da Iyyani taso borewa ita. Amma wasu lafuza daga cuɗaɗɗun kalamansa ya sata yin shiru ta bisu da addu'a. Kaka yayma Iffah gargaɗi matuƙa akan abubuwan daya bata, ya kuma tabbatar mata ko guda ɗaya taƙiyi zaiji hakan a jikinsa. A hankali ta murza awarwarayen hannunta da shine ya sakamata, ta sake lumshe idanunta da sakin ajiyar zuciya. Haka kawai takejin awarwarayen da girma da kuma banbanci da irin wanda take sakawa a baya domin kwalliya, ko miye dalili oho. Daga Ummu har Babiy a tsorace suke kallon Iffah da Hanash da suka shigo. Hanash ya girgiza musu kansa cikin sauri yana faɗin, “Wlhy ba laifina bane Babiy. Itace ta bore akan saita biyoni, kaka kuma ya bata goyon baya. Dan a cewarsa _(Babu wani nisa dake bada tazarar gujema ƙaddara. A wani ajin jarabawar data biyoka ma gara kai ka tunkareta. Dan ba kowane kogo bane ke zama kogo ga ma'abocin gudun ceton rai)._ Babiy na kasa fassarawa, akoda yaushe cirkuɗaɗɗun kalamai daga bakin Kaka masu tsaurine da wahalar fahimta. Dan ALLAH idan kun sani ku fassara mana”. Maimakon amsa daga Babiy baya sukaga yayi tamkar zai faɗi, sai dai cikin sa'a ya dafe gini tare da dafe kansa alamar hajijiya. Ummu ma ƙasa takai zaune jikinta na rawa, hakan sai ya ƙara firgitasu. Da sauri duk sukai kansu suna mai tambayarsu suna lafiya kuwa?. Da kai kawai suka amsa musu, Babiy harda ƙoƙarin ƙaƙaro murmushi. Cikin son kwantar musu da hankali yake kallonsu. “Kunga karku sakama zukatanku wata damuwa, ba maganar Baba bace ba, kawai dai bana jin daɗine kwana biyun nan dama”. Jimm sukai alamar tunani, sai dai kuma babu damar yin musu ko ƙin aminta da cewar tasa. Hanash ya taimaka masa suka koma cikin runfa, Iffah kuma tana riƙe da Ummu.. ★★★ Washe gari batare da sun sani ba Babiy yay sammakon yin tafiya zuwa ƙauyen Jumna. Ya samu tarba daga surukan nasa ko ta girmamawa.... Ƙyaƙyƙyawan tsohon da Tattarowar fatarsa ta tsufa bai hana bayyanar ƙyawun cikar halittarsa ba ya sake kallon dattijon gabansa a karo na babu adadadi. Murmushi ya saki a karon farko, cikin karyar da kai da ƙanƙan da idanu ya kai hannu bisa kafaɗar dattijon. Numfashi yaja kakkaura da juyowa alamar dawowa hayyaci. Ya maida kansa ƙasa ya sunkiyar saboda girmamawa ta surukuta dake a tsakaninsu na tsahon shekaru. “Humm Muhammadu Zayyanu!”. Tsohon ya kira sunan tamkar mai sake bita a ranar da aka raɗa ga mai shi. Ɗago idanu ya sakeyi a karo na biyu sai kuma ya risinar tare da amsawa da “Na'am Baba”. “Tun isowarka magana nake gani shimfiɗe a fuskarka amma bakinka ya kasa furtawa, ko wani abu ya sami Hanash da ƴar uwarsa ne a hanyarsu ta komawa gida jiya?”. “A'a baba ko ɗaya, lafiya lau sukaje cikin ƙoshin lafiya kuma, sai dai.....” Sai kuma yay shiru ya kasa ƙarasawa. Kaka dake kallonsa yay ɗan murmushi, “Sai dai baku so komawar Iffah ba ko?”. “Hakane baba. Domin kuwa babu abinda ya canja a daular Ruman, muna jin tsoron rasata itama kamar ƴan uwanta, duk da bamu da tabbacin zasu sake waiwayrnmu, sai dai kalamanka sun sakamu a ruɗani har muka kasa rumtse idanu a daren jiya domin yin barc......” “Hana ido barci bashi ke nufin damar iya sauya abinda bakai ka rubuta ba. Muhammadu Zayyanu! Da ace ƙaddararmu a hannayenmu take da kaf mutane bazasu zana zaman duniya ba a littafinsu musamman idan sun san koda daɗin busawar iskar dake cikin aljanna ce. Karka damu kanka da sanin sirrin cikin dutsen da ko'a kallo abin firgitarwa ne. Mumini yakan kasance mai azumtar yini daga UBANGIJI, ya kuma sallaci duhun dare daga UBANGIJI domin yaye damuwa ko samuwar nutsuwa a duniyarsa. Gaibu daga ALLAH take, zahirin da yaso mu sani kawai yake iya nuna mana ta isharar rayuwa ko canjawar tunanin zuciyo yi”. Nannauyan numfashi yaja ya fesar tare da jinjina kai, bawai kwanciyar hankalin da yazo nema ya samu ba, sai dai rashin zaɓi ko bakin zaren kamawa ya sashi fahimtar tsohon na masa nuni da shiru ne kawai a zubama sarautar ALLAH ido dan shine kawai gagara misali..... _________________ ★Kwanaki biyu kenan da dawowar Iffah gida, inda dawowar tata ta zame mata tamkar wani famin ciwo a jikinta. Dan a kullum takanyi hawaye sama da sau babu adadi akan rashin ƴan uwanta guda biyu. Komai ta kalla nasu yakan dawo mata da jiyansune mai cike da farin ciki da babu tunanin yankewa. Duk halin da take a ciki Ummu da Babiy na hankalce da ita, tausayi take basu matuƙa, wani lokacin Ummu har hawaye takan share itama. Yau ma tamkar kullum tun bayan dawowarta tai shirin makaranta ta fice badan hankalin su Ummu ya kwanta ba. Kawai dai dan ta dagene akan komawar. Sun bartane ko komawar zaisa ta sake samun nutsuwa da farin cikin da ko'a fuskarta yanzu baka hangosa. Sanye take cikin skirt golden yellow da t-shirt fara da suka kasance Uniform ɗinsu, sai hijjab fari ƙarami shima ta ɗora niƙab ta yanda ƙwayar idanunta kawai ake iya gani. Bayanta goye da school bag. A nutse take tafiya kanta a ƙasa tamkar bata son taka ƙasar har ta iso bakin titi, tsayuwar da batafi ta mintuna uku ba ta samu abin hawa kamar sauran ɗalibai daketa ɓillowa a kowane kusurwa. Makarantarsu babbar makarantace mai ɗauke da ɗalibai masu hazaƙa, domin kuwa an tattarosu ne daga mabanbanta makarantu aka kawo nan saboda hazaƙarsu. Kowa bata kulaba ta shige aji tai zamanta, saɓanin da da kowa yasan Iffah mai tsiwa da surutu, gata ba'a kadata a himma. Kauɗinta yasa mafi yawan malamai saninta ga kuma ƙoƙari. Amma tunda ta dawo yanzu ta canjama kowa, magana ma saita zo har a tashi batai da wani ba. Kamar yanda malaman sukai mata uziri haka ɗaliban ma sukai mata, dan kowa yasan tana cikin yanayin da uzirin kawai tafi buƙata. Duk wanda ya shigo yakan miƙa mata hannu su gaisa, itama babu musu take miƙawa tare da amsa sallamar da sukai mata. A haka har duk ɗaliban ajin suka kammala shigowa malamin farko ya shigo musu. Da farko ta nutsu wajen fara fahimtar darasin da yake musu, a hankali kuma tunaninta ya fara janyewa zuwa ga abinda taketa faman shiryawa da zuciyarta a kwanakin nan har malamin ya kammala ya fita babu abinda ta ɗauka. Haka na bayansa suka cigaba da shigowa basu darasi daban-daban, wani hankalinta na kai wani harya fita babu abinda zatace ta saurara. Ana tashi tana a ɗalibai sahun farko da suka fara fitowa, jitai kawai tana sha'awar yin tattaki da ƙafafunta yau, dan haka bata tsaya neman abun hawa ba ta miƙo titi da ƙafa ta fara tafiya kamar wasu tsirarun ɗalibai irinta da gidajensu ke kusa da makarantar. Tafiya tayi mai nisa sosai batare da nuna alamun gajiyawa ba, harta kusa isowa roundabout ɗin daya raba hanyar gidansu da ainahin titin hanyar masarauta daular ruman. Daga roundabout ɗin ana iya hango ƙaton tambarin ƙosashen zaki da akayisa da gold na tambarin Masarauta. Iffah taja wani kakkauran tsaki da ɗauke kanta zuciyarta na mata zafi. Harta kusa tsallakawa ta hango wata tsohuwa dake riƙe da wani yaro da Uniform a jikinsa da alama titin take so su tsallaka amma sunata inda-inda. Karan farko murmushi ya suɓuce mata ganin yanda yaron ke jan hanun tsohuwar sai sun tafi kamar zasu tsallaka saita fisgo yaron su dawo baya tana masifa. Sallama tai musu, tsohuwar ta amsa mata. Ta gaisheta da girmamawa tare da faɗin, “Ammi kuna so ku tsalla ne?”. Amsawa tsohuwar tai da “Eh Ibnati ”. Iffah ta sake murmusawa daga cikin niƙab ɗinta, kafin takai hannu ta riƙo na tsohuwar dake riƙe da yaron ita kuma. Suna gab da kaiwa tsakkiya yaron ya fisge hanunsa ya koma baya da gudu yana faɗin yabar abunsa a baya. Tsohuwar zata fisge itama tana masifa da kiran yaron ya dawo Iffah ta riƙeta gam suka karasa tsallakawa. “Ammi yi haƙuri barsa naje zan sake tsallako miki da shi. Rufe bakin Iffah yay dai-dai da taka wani bahagon birkin daya bada sautin ƙuuuuuu!!!. Sai sautin fitar ƙara mai razanarwa ta biyo bayansa. Wani irin zabura Iffah tai na juyowa dan ƙarar har tsakkiyar kanta ta jita. Ai batama san sanda ta yaye niƙab ɗin fuskarta ba da waro manyan ƙyawawan idanunta waje gaba ɗaya ba tana mai ambaton sunan ALLAH ganin yaron nan tsaye cak a tsakkiyar titi hancin wata mota gab da shi allamar kaɗan ya hana ayi ɗanyen aiki. Kusan a tare suka isa kansa ita da tsohuwar data fashe da kuka da ƙwala kiran sunan yaron a matuƙar firgice. Iffah da jikinta ke ɓari ta riƙo yaron jikinta tana duddubashi da sauke ajiyar zuciya a jajjere, ganin babu ko ƙwarzane a jikin nasa. Saurin sakin yaron tai ga tsohuwar tasha gaban motar ranta a ɓace ganin mai motar ko fitowa baiyiba ya ɗan leƙone kawai, ganin baima yaron komaiba ya maida kansa yanama ƙoƙarin barin wajen. A fusace ta buɗe murfin, ba saurayin daya kasance drivern motar ba hatta wanda ke gefensa hankalinsa akan lap-top dake saman cinyarsa sai da ya ɗago suka zuba mata idanu. Gaba ɗayansu ta haɗa ta dallama harara da manyan idanunta masu matuƙar haske tamkar madara. “Kai malam baka san darajar mutane bane?....” Zazzaƙar muryarta mai taushi da nutsuwa a cikinta ta daki kunnuwansu cikin faɗa babu ko ɗigon tsoro a tare da ita. Batare data damu da yanda suka zuba mata ido ba ta murguɗa musu bakinta da sake dalla musu harara ta cigaba da masifarta, “Ka kusan bige yaro amma tsabar kanka ba'a daidai yake ba shine koka fito kaga yaya yake ma saboda ku masu kuɗin nan ɗaukar talaka kuke baida banbanci da titin da kuke gurza tayoyin banzayen motocinku da kuka saya da kuɗinmu”. “Kai!”. Drivern ya faɗa da maɗaukakin mamaki Iffah. Harara ta sake dalla masa da zira hannunta ta zare key ɗin motar daya riga ya kashe tun ɓuɗe musu murfin da tayi. “K! K! Dalla bani key kajimun fitsararriyar yarinya kinga mun taɓashi ne?”. “Anƙi a bakun, wlhy duk sai kun fito kun dubashi kun bama kakarsa haƙuri zan baku key ɗin nan, inba hakaba sai dai mu kwana anan.” Hannu saurayin ya kai da nufin warto key ɗin taja baya, sai dai duk da haka saida yaɗan taɓa skirt ɗinta kaɗan. Cikin matsanancin ɓacin rai ta jinjina yatsarta a kan fuskar matashin tamkar zata tsone masa ido. “Idan hanunka ya sake gigin taɓa koda hijjab ɗin jikina ne sai na karyashi, Sannan koda Shahanshan ne yay wannan aikin bai isa barin wajen nan ba balle kai shashasha driver”. “K!!”. Na gefensa ya faɗa cikin matuƙar waro idanu. A karan farko wanda ke hakimce zaune a sit ɗin bayansu lap-top a cinyarsa da tarin takardu a gefe da gefensa ya ɗago ƙyawawan idanunsa dake tattare da matsananciyar gajiya da ƙosawa yana yamutsa fuska. Baya ganin yarinyar, sai dai duk abinda take faɗa raɗam a kunensa zazzaƙar muryarta ke sauka. Baiko kalla yaran nasa ba ya sauke Lap-top ɗin dake cinyar tasa tare da kai hannu ya buɗe murfin. A tare suka zabura, sai dai kafin suyi wani yunƙuri harya fita a motar. Dolo suka fito suma da sauri...........✍ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +22799643131 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_5_* _________________ _*MAAB LUXURY HOME!!* Sabuwar duniyar hamshakan mata da ƴaƴan gata.💞_ _*GIDAN* ƙawa da ƙawata gidajen da suka cika gida._ _*SABUWAR DUNIYAR* Amare da uwargidan data amsa sunanta ƴar gaban goshi._ _*MAAB LUXURY HOME* wata duniya ce ta ƙawa da ƙawata gidajenmu da kayan ƙyale-kyale na burgewa da ɗaukar hankalin duk wani mai kallo_. _*SUNYI FICE* Fice irin na ɗaya a cikin tsara, sune na farkon fari, a farin da za'a kira fari a kowace irin duniya._ _*A GAREMU* ba sitturu na alfarma da kawa ne kawai ke tabbatar da mu hamshakai ba. Sai mun haɗa da ƙawata gidajenmu da kayan MAAB LUXURY HOME zamu kasance cikakkun ƴan gata ababen kallo da nunawa sa'a koda a cikin dubun da sukafi dubu._ _*MAAB LUXURY HOME* sun takaita mana dukkan wahalar nema ko order a kasashen ketare ta hanyar wadatamu da galla-gallan kayayyakin adon gidajenmu_ _*MAAB LUXURY HOME.* Duniyar kayan Kitchen da decoration din gida na keta raini._ _*INA UWARGIDA INA AMARYA!!?* Ku ziyarci shagon mu dake No 22 Ahmadu Bello Way, Kano state. Ko kuyi order daga shafin mu na Instagram @maabluxuryhome. Ko Facebook @maabluxuryhome. Ko Ku nememu a lambar waya *08034631010*._ *_Mai azama shi za'a kira dana farkon fari😉. Bara nai sauri nawa suzo hannuna kafin a kwashe😁⛹🏼‍♀️⛹🏼‍♀️⛹🏼‍♀️._* __________________ ........Kama hanun yaron da Iffah tai da nufin subar wajen duk da key ɗin motar mutanen har yanzu na'a hanunta yay dai-dai da isowar wani nutsatstsen taku mai tafiya da sassanyan ƙamshin turare tamkar shi kaɗai iska ke tsintowa tana busawa a hancinan mutane. Kamar wani magic wajen yay tsitt na wasu sakkani, tsirarun mutanen da suka taru a wajen tun furuwar abun duk suka zuba masa idanu. Ita kanta hajiya Iffah mai masifar ƙirjintane yay wata irin harbawa lokacin da mutumin ya sauke nasa lulu idanun cikin tsakkiyar nata. Da ƙyar ta iya fisgar su daga cikin nasa tana ɗan murguɗa baki da sauke niƙaf ɗinta cike da dakiya. Idanun nasa ya janye daga kanta shima da matsawa gaban yaron ya kai tsigunne dai-dai tsayinsa dan ya fara ɗauka yarinyar nan aljanace ma dai kawai. Cikin sassanyar muryarsa mai zurfi da nutsuwa ya motsa lips ɗinsa kaɗan tamkar an fisgo maganar. “Kana lafiya?”. Kai yaron ya gyaɗa masa. Ya ɗan ɗage gira da motsa bakinsa kamar zai taɓe. “Uhhm! minene sunanka?”. “Amjed”. Yaron ya faɗa cike da kwarin gwiwa. A hankali ya sake kaɗa fararen idanunsa tare da jinjina masa👍🏻 ya saki wani sassanyan murmushi a karon farko da jan kumatun yaron. “Oh my Friend! nice name. Kana sona da aboki?”. Da sauri yaron ya jinjina kai yana washe baki. Idanunsa ya ɗan sake fiddowa suka ƙara girma tare da ƙara sakin murmushi. Ya riƙo hannu yaron alamar suyi musabaha. Al'amarin ya birge mutane da yawa, duk da babu wanda yasan wanene shi, amma ko makaho ya kalla wannan mutumi yasan babban mutum ne. Suit ɗin dake jikinsa farare tas ma kawai abin kallone. Balle shi a karan kansa daya kasance ƙyaƙyƙyawan gasken fatarsa da gogewarta har ɗaukar idanun mai kallo take. Ga wani ƙamshi na musamman mai saka nutsuwa ga mai shaƙa, yanayin kamewarsa da cikakkiyar isa irin ta manyan mutane ke ƙara kawata kwarjininsa da cikar kamala ga duk mai kallonsa. A karo na biyu suka sake haɗa ido da Iffah dai-dai ya gama gaida kakar yaron nan da keta faman washe baki da jera masa godiya dan kuɗine dunkulallu sabbi ƙal ya damƙa a hanun Amjed. Harara ta balla masa da janye idanunta da sauri saboda wani abu mai tsananin sanyi taji yana tafiya daga ƙafafunta har saman kanta. Cike da takunsa na nutsuwa da ƙasaita shima ya juya ya bar wajen kai kace akan dole yake taka ƙasar saboda takun zaratan maza masu cikakkiyar isa da lafiya ce tattare da tafiyar tasa. Iffah ta jefama ɗaya daga cikin samarin nan biyu key ɗin motar, dan ɗayan ya tafi da hanzari ya buɗema ogansu ne. Dai-dai zai shiga ta ballama wanda ta jefama key ɗin harara da faɗin, “Daga yau ko daga nesa kuka hangoni to ku canja hanya koda a jirgi kuke kuwa”. Shigar maganar tata a cikin kunensa dai-dai zai shiga motar da aka buɗe masa ya ɗan ɗago idonsa, sai dai wadda ya ɗago da nufin kallar da mamakinta ke cin ransa tuni ta nufi barin wajen tamkar ba ita ta haɗa dabar wajen ba... Suna ƙoƙarin shan shataletalen titin idanunsa ya sake sauka a kanta ta miƙe titi tana tafiyarta a nutse, sai dai fuskarta a rufe take da niƙab data saki tun bayan haɗa idonsu na farko.... 🤔Wannan ƴa ta Babiy wataran sai ta saka an mata dukan sakwara a titi in har bata canja hali ba😬🚴🏼. ★★......★ “Badai a ƙasa kika tahoba auta? Na ganki a gajiye tamkar an koroki”. Zubewa tai a taburmar da Ummu ke zaune, tare da ɗora kanta a cinyarta tana ƙara narke fuska. “ALLAH a ƙasa na taho Ummu. Haka kawai naji ina son na taho a ƙafan”. “Ai gashi nan duk kin gajiyar da kanki, dama keba wata isashshiyar lafiya ba. Tashi kiɗan watsa ruwa dan sai warin rana kikeyi”. “Kai Ummu warin rana fa?”. Tai maganar a shagwaɓe da kamo rigarta ta kai hancinta. Miƙewa tai tana tura baki gaba da faɗin, “ALLAH Ummu kinso dai yarfanine amma ƙamshin ma turare nakeyi”. Murmushi kawai Ummu tai da girgiza kanta, ita kuma ta shige ɗaki sai faman cika baki take da iska a dole taji haushi..... ★Da daddare suna zaune a tsakar gida cikin hasken farin wata daya raba Hanash na koyama Iffah aikin makaranta. Daga gefensu Ummu da Babiy ne zaune yana cin abinci. Hira suke jefi-jefi akan kayan lambunsa da zai fidda a ƙarshen satin nan ga ƴan kasuwa. Iffah tai karaf jin Babiy yace zuma batayi kirki ba wannan karon bazata wuce tulu biyu ba. “Babiy sai a bar mana mu shanye kawai a gida. Kaga dama Ummu zatamin alkakin saukar islamiyyarmu nan da wata biyu”. Murmushi Babiy yayi, “Zanso haka Ibnati, sai dai bazai yuwuba dan dukanta zan kaita masarauta ne”. Take murmushin fuskar Iffah ya ɗauke baki ɗaya. Kamar zatai magana sai kuma tai shiru ta maida kanta ga aikinta kamar bataji ba. Shima Babiy sai bai sake cewa komai ba akan zumar suka cigaba da maganarsu da Hanash da Ummu dake saka baki jefi-jefi..... Tun wannan magana babu wanda ya sake tada zancen zumar nan. Babiy da Hanash suka duƙufa tattare kayan lambu da za'a fitar. Yayinda Iffah ta cigaba da zuwa makarantarta a zahiri kamar babu wata damuwa tattare da ita. Sai dai kuma a baɗini tun randa akai maganar kai zuma daular ruman zuciyarta sam bata huta ba. A duk motsinta cikin ƙullawa da kwancewa take game da babban burinta na ɗaukar fansa. Wanda tasan bata da wata hanyar yin hakan sai ta wannan zuma da Babiy ke kaiwa masarauta. Kuma tasha jin cewa Tajwar ne ke shanta kawai. Har ana saura kwana biyu bata samu wata mafitaba akan ƙudirinta, dan haka tana zuwa makaranta taja wata ƙawarta da kafin yanzu da ta canja suke sabgarsu da rashinji tare gefe. Ikram da taji farin cikin ƙawarta ta fara dawowa yanda take babu musu ta bita suka koma can ƙarƙashin wata bishiya suka zauna. “Ko kefa Iffah, ALLAH bana jin daɗin yanda kike shareni yanzu sam. Dan ALLAH ki manta da komai mu cigaba da yima su Akia Arfa addu'a”. “Humm”. kawai Iffah tace da ɗan laɓe fuska. “Kinga ni ba wannan yasa na kiraki ba, tambayarki nake so nayi?”. “To ALLAH yasa na sani”. Cewar Ikram tana gyara zama. “Kinma sani, kwanaki bakin bani labarin sister ɗin mamanku tasha zuma taita ciwon ciki ba, kafin aje asibiti har hanjinta ya kakkatse?”. “Yes anyi haka, bayan kwana huɗu ma ta rasu ai. Sai daga baya aka gane ashe saurayintane ya zuba mata wani magani a ciki. Sai dai har yanzu ma ana shari'an, dan a binciken likitoci sudai sunce basuga komai ba, abokinsa kuma da suka ƙulla tare ne ya tona masa asiri, ya kuma rantse sun zuba ɗin dan tare suka sayo maganin”. Iffah dake saurarenta tace, “Anya kuwa ba abokin na masa sharri bane?”. “To mudai bamu san dai-daiba sai ALLAH. Grand mother ɗinmu ma ita tace dan ALLAH abar shari'ar tunda UBANGIJI mafi sani ne. Idan anje garesa shi ya rarrabe ƙarya da gaskiya”. “Uhm gaskiya kam tayi magana mai ƙyau. To amma ni abinda ya bani mamaki, shiko wannan wane kalar maganine haka da har za'ace likitoci sun kasa ganewa, bayan kuma gashi sunce ya kakkatsa mata hanjinta da kansu.” “K nifa abinda na fahimta kamar an sayesu ne likitocin, kin sanfa ɗan manyan mutanene yaron. Amma abokin nasa ya faɗi sunan maganin sai dai na manta”. “Komaima zai iya faruwa indai shegun manyan ƙasar nannne, kansu kawai suka sani azzalumai. Amma ina son nasan sunan maganin dan ina son nai bincike a kansa ma ni wlhy.” “Kedai kawai wani abun adai rufesa kawai. Uhm kina nan da shegen son bincike-binciken nan naki, anya Iffah idan ALLAH ya cika miki burinki na zama ƴar jarida bazaki addabemuba? Dan na kula har hurumin aikin jami'an tsaro zaki dinga shiga tsabar bin kwaf-kwaf ɗinki”. “Ƴar sa ido naji, nidai kafin a tashi ki tuno sunan maganin inba hakaba zanta addabarkine”. Ikram tai dariya tana miƙewa. “Indai wannan ne zanyi ƙoƙari. Maganin ma fa ba wani na kirki bane ba ance ana zubama ƙananun ƙwari ne dakan damu mutane a cikin gida a ruwa haka ko abinci, dan basajin warinsa sam ko ami aka zuba sai kiga sunsha ruwa da shi ko abinci.” “To kinga koda ba bincikeba ai zai mana amfani, dama mu da muke cikin lambu kullum cikin ganin macizai dama halittu masu cutarwa iri-iri dake iya zama a cikin gida haka.” “Eh gaskiya kuma hakane, zai ko taimaka muku insha ALLAHU”. Kafin a tashi kuwa Ikram ta cika alƙawarin samowa Iffah sunan magani. Takoyi farin ciki har haƙwaranta na bayyana wajen murmushi irin wanda ta jima batayiba a rayuwarta. Iya kuɗin motarta ne kawai a jikinta. Dan haka ta gama tsara ƙaryar da zatai ta samu kuɗin sayen maganin idan ta koma gida. Koda ta koma gida tun kafin takai zaune ta sanarma Ummu ai an basu wani Assignment mai wahalar gaske. Gashi bata da littafin dazai taimaka mata tayi har sai ta saya. Ganin yanda tai maganar a serious yasa Ummu yimata murmushin kwantar da hankali. “Karki damu in har ana saidawa anjima sai Hanash ya fita ya saya miki kema, ko kuma ki bincika a kayan karatun su Arfa ƙila ki samu ai”. “Ummu basu dashi sam, dan kwanaki ma da malaminmu yay maganarsa sannan suna nan ai. Kinga da suna dashi ai da sun bani”. “Uhm hakane kuma kam. To ki bari Hanash ɗin ya dawo sai ya dubo miki”. “Ummu ni kawai ki bani yanzu da nayi wanka sai naje da kaina na dubo. Ƙilama daga nan na ƙara ilimi”. “Kai Iffah kin cika fitina, kin dai san ba son yawan fitarnan taki muke ba ai”. “Na sani Ummu, insha ALLAHU babu abinda zai faru addu'arku na biye dani, kuma ina suturce jikina idan zan fita”. Badan hankalin Ummu ya kwanta ba ta yarda tabar Iffah ta fita. dan ta dage akan gobe ake buƙatar sukai Assignment ɗin, idan tace zata jira sai Hanash ya dawo dare zaiyi tunta sunje babbar kasuwar cinikayyar ƙarshen watane ta daular ruman kai kayan lambu. Kamar kullum tai shirinta tsaf tare da rufe duk jikinta sai idanunta kawai da ake gani. Sosai ash color na abayar jikin nata mai adon duwatsu blue masu sheƙi sukai mata ƙyau duk da ba'a iya ganin fuskarta. Cikin nutsuwarta take takunta tamkar wata tarwaɗa. Dan Iffah tun tana yarinya irin yaran nanne masu shegen iyayi da kauɗi. Tun a shekarun baya mutane kance za'ai kallon ƴammata a wajen nan, dan tafi yayunta son kyale-ƙyale da tsantseni irin na ƴan gayun mata masu ji da kansu. Da ƙafa tazo har titi duk da akwai ɗan tafiya a tsakaninsu. Ta tare abin hawa tare da sanar masa inda zai kaita. A ƙofar katon kantin da ake saida duk wani nau'in magani daya shafi gona dana kauda mugayen halittu masu cutarwa ga mutane dakan shiga cikin gida ya sauketa. Ta biyashi kuɗinsa sannan ta shige. Kanta tsaye ta miƙa takardar data riga ta rubuta sunan maganin dan karta manta. Aka faɗa mata kuɗin ta biya suka bata. Wani irin farin ciki takeji a ranta, tunin karta koma gida babu littafi ta zama abar tuhuma ya sata cema mai abin hawan data hawo ya kaita babban shagon littatafai. Koda suka isa cewa tai ya jirata yanzu zata fito su wuce. Gargaɗi ya mata akan kuɗintafa ya ƙaru, tace babu damuwa tana shigewa. Ganin babu yawan mutane a shagon duk da ƙatone sosai ba kuma wajen da za'ai hayaniyar da zaka san adadin mutanen wajen bane yasata ɗage niƙab ɗinta yanda zataga komai da ƙyau. Kowanne littatafai da sashensu a rubuce kuma yanda bazakasha wahalar nema ba, maimakon ta nufi inda zataga irin nata kai tsaye saita fara zagaye. Sai da ta gama kewaye-kewayenta tamkar ta manta da wanda ta ajiye a waje kafin ta tsaida hankalinta ga inda zataga littafin daya dace ta ɗauka. Surutun yara takeji kaɗan-kaɗan ta bayan inda take, ta ɗan dudduba taga babu ta inda zata leƙasu sai ta haƙura cikin taɓe baki takai hannu kan wani littafi zata ɗauka. Daga can ɓangaren ma dai-dai an kai hannu akan littafin za'a ɗauka dan duk kanta ɗaya ce, littatafan ne kawai suka rufe wanda ke can baya ganin na nan. Iffah taja, daga can ma aka ja, jin za'a fisge saboda an fita ƙarfi dama tsaho dan ita harda su ɗiɗɗishe saita fisga itama a ɗan fusace saboda gani take wani keson raina mata hankali. Ta cikin ɗan space ɗin data cire littafin ita da shi suka zubama juna idanu, haka kawai taji tsigar jikinta ta tashi duk da ita bama wani ganesa tai da ƙyau ba saboda space ɗin bawai ya buɗe da ƙyau bane. Kamilalliyar fuskarsa da dama babu wani walwala a cikinta ya ƙara tsukewa dan shiko sarai ya ganeta...........✍ ★ Shin wanene wai wannan dake neman zamema Iffah ɗan kaɗafi?. ★To wai mima zatayi da maganin data saya ne?. ★ Ko Iffah zataci nasarar cika ƙudirinta?. ★Idan taci nasarar minene zai biyo baya?. ★Mike kashe matan Tajwar Eshaan ibn Haysam Abdull-majeed ne?. ★Shi kansa Tajwar Eshaan ɗin wanene shi?. ★Yaya yake? Taya zamu san ainahinsa?. *_Duka amsoshin nan na'a cikin gundarin labarin littafin DAUƊAR GORA. Masu iya magana kance (CIKI KA SHATA). To waima miye ma'anar kalmar Dauɗar gora ciki ka shatan ne?🤗. Kumuje zuwa kudai, karku bari a baku labari masoya🤸🏼, dan cakwakiya iya cakwakiya. Kundai san minene gidan sarauta, balle irin wannan na DAULAR RUMAN da Tajwar ɗinta ke amsa suna Shahan-shan. Ma'ana (King of Kings🤴🏻). Bafa cakwakiyar kawai bace, akwai tsumammiyar soyayya mai fasa zuciya😋._* Dawa?. A ina?. Taya?. _Duk amsar na cikin *DAUƊAR GORA CIKI KA SHATA🤗* dake a ɗaya daga cikin littatafai biyar na *ZAFAFANKU* abin alfaharinku. Kundai sansu kun san aikinsu babu wasa babu jan rai a cikinsa balle shiririta. Zamu gamsar da ku da salon labaranmu a wannan karon fiye dana baya insha ALLAHU. Kudai kawai ku kasance da zafafan naku biyar zakuce nina faɗa muku😋😁._ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +22799643131 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_6_* ________________ _*MAAB LUXURY HOME!!* Sabuwar duniyar hamshakan mata da ƴaƴan gata.💞_ _*GIDAN* ƙawa da ƙawata gidajen da suka cika gida._ _*SABUWAR DUNIYAR* Amare da uwargidan data amsa sunanta ƴar gaban goshi._ _*MAAB LUXURY HOME* wata duniya ce ta ƙawa da ƙawata gidajenmu da kayan ƙyale-kyale na burgewa da ɗaukar hankalin duk wani mai kallo_. _*SUNYI FICE* Fice irin na ɗaya a cikin tsara, sune na farkon fari, a farin da za'a kira fari a kowace irin duniya._ _*A GAREMU* ba sitturu na alfarma da kawa ne kawai ke tabbatar da mu hamshakai ba. Sai mun haɗa da ƙawata gidajenmu da kayan MAAB LUXURY HOME zamu kasance cikakkun ƴan gata ababen kallo da nunawa sa'a koda a cikin dubun da sukafi dubu._ _*MAAB LUXURY HOME* sun takaita mana dukkan wahalar nema ko order a kasashen ketare ta hanyar wadatamu da galla-gallan kayayyakin adon gidajenmu_ _*MAAB LUXURY HOME.* Duniyar kayan Kitchen da decoration din gida na keta raini._ _*INA UWARGIDA INA AMARYA!!?* Ku ziyarci shagon mu dake No 22 Ahmadu Bello Way, Kano state. Ko kuyi order daga shafin mu na Instagram @maabluxuryhome. Ko Facebook @maabluxuryhome. Ko Ku nememu a lambar waya *08034631010*._ *_Mai azama shi za'a kira dana farkon fari😉. Bara nai sauri nawa suzo hannuna kafin a kwashe😁⛹🏼‍♀️⛹🏼‍♀️⛹🏼‍♀️._* ___________________ ........Baki ta murguɗa da juya idanunta farare tas tamkar madara cikin nasa da ya kafeta da su. “Inma kai mayene to wlhy bazan ciyu ba, Babiy kullum addu'a yake min shi da Ummu”. Tana gama faɗa tabar wajen. Yaransa na waccan ranar ne dai yau ma a tare da shi. Kuma suma sarai kalaman Iffah da bazasu manta muryarta da wuri ba ta shiga cikin kunnuwansu. Dama sune suke dubama yaran dake tare da su books ɗin, shi ko yana biye da su ne kawai da binsu da idanu. Ɗaya daga cikin yaranne ya nuna littafin da Iffah ta ɗauka, su kuma kasancewar suna ɗakkoma sauranne sai shi da kansa yay yunƙurin ɗakkowa kafin su suyi hakan. Yunƙurin zagayowa wajen Iffah ɗaya daga cikin yaransa yayi, dan yay alƙawarin yau sai ya daddala mata mari, amma sai ya dakatar da shi ta hanyar yima ɗayan alamar ya tsayar da shi da ido. Da sauri wancan da shima yake jin kamar suje su haɗu su faffasa mata baki ya kira sunan wancan. “Azaan!”. Cak ya tsaya tare da rumtse ido da cije baki dan yasan dai ogane zaisa Fakhir ɗin ya dakatar da shi. Gashi harya hango Iffah dake gaban mai biyan kuɗi. Dole ya haƙura badan yaso ba, amma yaci alwashin duk randa suka sake haɗuwa da yarinyar can babu oga sai ya mata karyawar gasashshiyar masara danta tabbatar itace zata gujema haɗuwarsu ba su ba kamar yanda ta faɗa. Iffah dai tuni ta biya kuɗin littafi daya cinye mata duka kuɗinta babu ko na bawa mai Mototaxi (napep). Sai mita take a ranta Littafin yayi tsada, koda ta fito ta iske mai Mototaxi ya cika yayi taf. Tana isowa inda yake hannu kawai ya miƙa mata alamar ta bashi kuɗinsa ya wuce. Fuska ta ƙyaɓe ta cikin niƙab ɗinta tana wani kif-kif da idanunta da kawai yake gani. “Oh oh kaiko duk daɗin asara ai ta jira samu ko? Idan mukaje inda zani nace maka bazan biyaka bane?”. A fusace yana mai dalla mata harara yace, “Na fasa kaiki, dalla malama bani kuɗina kije ki hau wata. Kuma har na zaman danai anan sai kin haɗamun”. “Lallai sannu shugaban ɓarayin Ruman. Saboda Babiy yamun baki ko? Idan kaga zaka ɗaukeni muje na baka kuɗinka ka daukeni, in kuma zaka zauna wage baki kana ihu ne na tare wata na hau ka biyoni a baya dan bani da shi anan sai naje gida”. “Baki da hankali”. Mai Mototaxi ya faɗa a matuƙar fusace yana fitowa. Harga ALLAH Iffah ta tsorata, dan tasan wannan mai zubin samudawan ƙarnin farkon fyaɗa daya zai bazar da itane a titin nan sai dai a kaima su Ummu gawarta. Amma tsabar ƙarfin hali sai faman fiki-fiki take da idanu da faɗin, “To sai kayi duk abinda ma zakayi mana”. “Hakama kika ce?”. Ya faɗa yana matsota. Jikinta taja baya tana wani zazzaro masa manyan idanunta masu matuƙar sheƙi tamkar ta tara ruwan hawaye a ciki, “Idan hanunka ya taɓa koda abayar jikina sai na ɓallashi! Idan kuma ka isa ka gwada”. “Kan uban can kayyasa, ke yarinyar nan kin san wanene ni kuwa? To dan ALLAH gwada ɓallamin hanun nagani”. Ya faɗa yana yo kanta da gaske. Securitys ɗin dake a bakin bookshop ɗinne sukai saurin taresa, dama dai ganinsu yasa Iffah wannan hura hancin, ganin ta samu yanda takeso baki ya ƙara buɗewa ta buɗe baki zata cigaba da tsiwa idanunta suka sauka a kan mutumin nan. Yanayin takunsa na isa da ƙasaita kawai saka rawa a zuciyar Iffah yake, sai dai kasancewarta yarinya mai ƙarfin halin tsiya da rashin son a ga gazawarta yasa baka isa ganin wannan tsoron ba a kan fuskarta. Janye idanunta tayi tamkar bata gansa ba, shima sai ya cigaba da takowa tamkar bai ganta ɗin ba yaransa da tawagar yara kusan goma sha biyar biye da su. Kamar waccan ranar yau ma sanye yake cikin suit da sukai matuƙar fidda ƙyawun halittarsa ta tsayayyen mutum, saɓanin ranar na yau baƙaƙe ne, sai dai sunyi matuƙar dacewa da lallausar farar fatarsa mai matuƙar sheƙi da ɗaukar idon mai kallo. Ga mayataccen ƙamshinsa irin na ranar mai saka zuciyar mai shaƙa raunana da nutsuwa. Harya gotasu zai wuce a binsa sai kuma ya tsaya cak, hannayensa duk biyu ya zuba a aljihun wandonsa tare da juyowa. Ita ya fara kallo, sai kuma ya janye lulu idanunsa masu tabbatar da kwarjininsa da kamewarsa ga duk wanda ya kallesu ya maida kan securitys ɗin nan dake riƙe da mai Mototaxi ɗin har yanzu. Azaan daya fahimci mi ogan nasu ke nufi yay saurin faɗin “ku sakesa” duk da har cikin rai baiso hakan ba. Babu musu suka sakesa, shiko sai huci yake idonsa akan Iffah data juyar da kai gefe irin bata sanma mi'ake ɗin nan ba. Hanunsa ɗaya ya zare daga cikin aljihunsa ya ɗan ɗaga rigar suit ɗin tasa. Kuɗine masu yawa ya zaro ya miƙama mai Mototaxi ɗin. Cikin rawar jiki ya kai rissine kamar gwiwarsa zata taɓa ƙasa ya amsa yana godiya kamar zai haɗiye harshensa. Kansa kawai ya ɗauke zai juya suka sake haɗa ido da Iffah. Baki ta tura gaba tana fiki-fiki da idanu da sake ɗauke kanta... Takaici kamar ya kashe su Azaan. Babu wanda a cikinsu bai harari Iffah ba kafin subi bayan ogansu da tuni yabar wajen. Mai Mototaxi da bakinsa ke washe uwa gonar audiga ya kalla Iffah. “A to hajjaju taho na kaiki koda karshen Daular Ruman ne ma”. Wata banzar harara ta balla masa da jan tsaki tabar wajen. Cike da takunta na nutsuwa ta gitta motarsu dake ƙoƙarin barin wajen. Azzan yay ƙaramar ƙwafa, a ransa yana raya shine zai zama sanadin nakasa yarinyar nan kuwa wataran. Mai gayya mai aiki kam da gaba ɗaya zuciyarsa ta gama tabbatar masa yarinyar nan aljanar ce idanunsa ya lumshe a hankali yana mai ƙara gyara zamansa na ƙasaita tamkar ba'a mota yake ba.... Tunda ta samu wata Mototaxi ɗin ta shiga zuciyarta ta tafi tunani. A karan farko take tambayar kanta waye wai wannan mutumin a garin nan?, da ganinsa dai kasan ɗan masu farcen susu ne ko shi a karan kansa ne mai farcen susar. A ƙasan zuciyarta taji tana buƙatar sanin shi ɗin wanene badan wani abu nasa ya birgeta ba. Hasalima haka kawai haushinsa takeji tun akan bige yaron nan da suka kusa yi a waccan ranar da ƙoƙarin guduwa da sukai. Ko kuma ma dai aljanin ne?, dan inba aljani ba taya zata dinga ganinsa duk inda taje gashi har karo biyu.. Tasha ji a bakin mutane ana faɗin ita ɗin ƙyaƙyaƙyawa ce, tafi kowa ƙyau a gidansu, amma ƙyawun wannan bawa da dirarriyar halittar jiki data fuska mai cike da kwantaccen gashi tamkar shiya zaɓama kansa komai sai dai aljanin kam..... Isowarsu anguwarsu ya sata ture tunanin ta nunama mai Mototaxi inda zasu ƙarasa ta amso masa kuɗinsa. Cikin sa'a suna isa ƙofar gidansu sai ga Babiy da Hanash suma an saukesu da alama yanzun ne suke dawowa. Su suka biya mai Mototaxi ɗin kafin su shige cikin gidan bakinta washe tana jera musu sannu da zuwa... Labarin alkairin da aka samu na kayan da suka kai kasuwa su Babiy ke basu ita da Ummu, amma ita rabin hankalinta naga abinda take yunƙurin yine kawai. Ta matuƙar ƙagara ai kiran sallar magrib su Babiy su fice masallaci Ummu ta shiga ɗaki. Ana kwaɗa kiran salla kuwa itace farkon miƙewa yin haramar alwala. Hakan da tai baisa wani yaji daban ba dan kowa yasan Iffah da himmar yin salla. Komi take aka kira salla, ko'a ina take inhar wajen zaiyi ibada zata ajiye abinda takeyi kuwa tayi sallar. Wannan halin nata na ƙara sakama iyayenta da ƴan uwanta sonta, dan tunsu Arfa na raye ma sukansu Ummu takan zaburar dasu akan halin Iffah ɗin na kiyaye ibada da ƙoƙarin yinta akan lokaci. Koda ta shiga ɗakin bayan tayi alwala bakin gadonsu takai zaune dan tana fashin salla ne, sai da taji tsakar gidan yayi tsitt sannan ta ɗan leƙo, babu kowa kuwa Ummu ta shige su Hanash sun fita massallaci. Da sanɗa ta fito ledar maganinta na ɗazu da taketa ɓoyo riƙe a hanunta. Wuff ta afka ɗakin Babiy, cikin sa'a bata wani sha wahalar ganin tulunan da aka cika da zuma ba sabbi ƙal. Ta saki murmushi dajin kamar tai ihu dan farin cikin da takeji a zuciyarta. Amma sai ta kanne cikin rawar jiki da ɗan yin leƙe-leƙe irin na mai tsoron a kamasa yana laifi tana ƙoƙarin buɗe kwalbar. A tulun farko ta zuba kusan rabi, sai kuma ta dakata bisa shawarar zuciyarta akan ta zuba duka tunda bata da tabbacin dukansu Tajwar ɗinne zaiyi amfani da su. Ƙaramin sandan data shigo da shi tasa ta motsa da ƙyau har saida ta tabbatar ya gauraye sannan ta sakama ɗaya, tana tsaka da juyawa ta tsinkayo muryar Ummu na kiranta. Ido ta rumtse da sauri tana ambatar sunan ALLAH, da hanzari ta shiga rufe roban sauran maganin saboda jin kamar Ummu na nufi ɗakin, cikin riga ta saƙa maganin da sandar sannan taɗan leƙo. Can ta hango Ummu ta nufi kitchen ɗinsu, aiko tai wuff ta fito ta faɗa ɗakinsu. Ummu data juyo saboda jin kamar motsi ta sake ƙwala mata kira. Yanzu kam amsawa tai da fitowa tana gyara mayafin abayarta. “Yi haƙuri Ummu ina karatune”. “Shine kuma bazaki mun ko gyaran murya ba zaki barni ina wage baki”. “Kiyi haƙuri to Ummuna”. Ummu ta fito daga kitchen ɗin tana gyara mayafin jikinta itama. “Jeki ki cigaba da karatunki dama motsi naji kamar, amma fara duba kosu Hanash sun bar mana ƙofa buɗe ne”. Da to Iffah ta amsa tana nufar hanyar soro da sauke ajiyar zuciya... Tana shiga ɗaki wani uban tsalle tai ta dirga saman gadonsu dan farin ciki. Mulmula take tana dariya irin wadda ta jima batayi ba, wauta da ƙuruciyarta tafi hango mata nasararta na ɗaukar fansar ƴan uwanta fiye da tunanin idan wani abu ya faru Babiy ne na farkon wanda za'a tuhuma kasancewar zumar daga hanunsa ta fito. Haka Iffah ta ƙarasa wannan dare cike da zumiɗin ganin wayewar gari Babiy ya kai zuma masarauta. Bayan ta idar da salla yau ko fama da ita Ummu batai ba akan shirin tafiya makaranta, a da kuwa saita tasota daƙyar kasancewarta mai son barcin safen tsiya da tayi salla take komawa barci. Babiy kansa saida yay mamakin wannan sammakon tashi nata yau, Hanash kam kasa haƙuri yay saida yay magana. Sai cewa tai ai sunada program ne a makaranta yau... Koda taje makaramtar ma dai bawai ta nutsu bane, rabin hankalinta ne kawai ga duk malamin daya kasance da su har aka tashi. ★A ɓangaren Babiy kam duk da tabon da masarauta daular ruman ta bar masa a zuciya bai taɓaji koda wani zai bari ya cutar da su ta hanyarsa ba ko shi ya aikata hakan ta damar dake hanunsa na kai musu zuma. Tsaf yay shirinsa kasancewar yau juma'a ce ya ɗiba tulunan zumar nan guda uku ya nufi daular ruman. Idan yaje ba kaitsaye yake ɗaukar zumar nan ya kai ga Tajwar ba, dan ganin Tajwar kam babban abune da sai wanda ya cika ya tumbatsa keda wannan damar. Akwai wanda keda alhakin amsarta shi ya isar da ita inda ya dace har ta isa ga sashen Tajwar ɗin. Bayan ƴan bincike a kansa na kullum da basa ƙarewa ya shiga daular ruman iya ƙofa ta biyu. Dattijo da kamanni da suturar jikinsa kawai ta isa tabbatar maka da shima wanine ya iso ga Babiy bayan zaman jiran kusan mintuna goma da yayi. Cikin girmamawa Babiy ya gaidashi duk da zasu iya zama kusan sa'anni da shi. Shiko ya amsa yana hura hanci irin na masu dama ta mulki a hannu. Umarni ya bama Babiy akan ya ɗanɗana zumar, Babiy da yasan babu wani abu na razani ko shiga dogon tunani kafin ɗanɗanawar kansa tsaye ya kai hannu ya ɗauka cokali dake bisa tire a hanun hadimin dake biye da dattijon nan. Tunda dama haka ba sabon abu bane garesa duk sanda ya kawo sai ya ɗanɗana ɗin. Tulun farko ya kwancema baki kasancewar a ɗaure bakin yake da ganyen ayaba, yasa cokalin nan ya ɗibo zumar da bismillah ya nufi bakinsa.........✍ *_😬😬😬Iffahhhhhh!!!!🙆🏻._* *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +2290165991 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_7_* .........Haniniya da ƙarar takun sawayen wani farin ingarman doki ta saka Babiy sakin cokalin da yake shirin kaiwa bakinsa ya miƙe domin ceton kansa kamar yanda Dattijo nan da hadiman dake tare da su suma sukai nasu waje. Tuni tulunan zumar uku da Babiy ya kawo sukai nasu gefe suma, gaba ɗaya zumar ta kelaye a wajen. Cikin daka tsawa dattijon nan ke duban hadiman da suka biyo dokin domin kama shi... “Wane mara hankalinne yay sakacin daya kunce?”. Su dukansu jikunnansu rawa yake, cikin ƙarfin hali shugaban hadiman dake kula da barga ya zube ƙasa yana mai girgiza kansa. “ALLAH ya ƙara maka tsahon rai an gama masa wankane za'a maidashi na rantse maka”. Dattijon ya cije baki mai nuna alamar takaici, “Na baku mintuna goma kacal ku madashi shashashu kawai”. Miƙewa hadimin dattijon yayi cike da girmamwa dan dama sauran sunata ƙoƙarin ganin sun kama dokin ne, bama su kaɗai ba hadiman da yawa sun ƙaru saboda bahagon dokine da babu ma iya controling nashi sai Tajwar Eshaan. Horarran doki ne daga horonsa, da abinsa ya dawo ƙasar ruman, dokin yafi kowanne doki tsananin ƙarfi a masarautar. Shiyyasa idan har sukai sakaci ya ɓalle kowa sai ya jigata kafin a kamashi da ƙyar, kafinma kamashin sai an samu wanda sukaji raunika da yawa. Akwai randa irin haka ta taɓa faruwa baƙaramin jigata mutane yay ba harda masu karaya a hadimai, kuma duk iya wahala da jigata babu wanda ya iya kama dokin har duhun magriba yayi dan da yamma al'amarin ya faru. Kowa yayi laushi an rasa in za'a kama sai ga Tajwar Eshaan ya fito sallar magrib, abu mafi ban mamaki daya saka masarautar yin shiru na sakanni uku kiran sunan dokin kawai yay sai gashi gabansa, ya girgiza jikinsa tare da yin haniniya sannan ya koma kan ƙafafunsa ya tsaya cak tamkar bashiketa jigata mutane da hargitsa wajen ba. Wannan abun mamaki ya saka dukan hadiman da suka zube saman gwiyawunsu kawunansu a ƙasa a lokacin kasa haƙuri sai da suka saci kallon dokin dama Tajwar Eshan ɗin da hirami daya yafa a kansa ya rufe rabin fuskarsa..... ★★★★ A ɓangaren Iffah gaba ɗaya idanunta sun kasa barin ƙofa, babban burinta kawai dawowar Babiy taji zuma ta isa hanun Shahanshan. Sai dai shiru kakeji har akai sallar juma'a bai shigoba. Ko abinci babu yanda Ummu batai da ita tai zaman ci ba amma taƙi, Hanash ma sai da ya mata maganar tazo suci kamar yanda sukanyi duk juma'a tunma su Fariha nada rai amma tace batajin yunwa. Ƙyaleta sukai dan sun kasa gane minene ya hanata nutsuwa waje ɗaya. Babiy bai shigo gida ba sai bayan sallar la'asar. Azabure Ummu ta miƙe tana kallonsa. “Innalillahi wa inna'ilaihirraji'un. Abu Hanash haɗari kayi?”. Kai Babiy ya girgiza mata yana kaiwa zaune da ƙyar. “Ke dai bani ruwa na fara sha”. Kafinma ya rufe baki Iffah da itama jikinta ke rawa ta kawo masa ruwan, dai-dai nan Hanash ya fito daga ɗakinsa cikin shirin fita ƙwallo. Shima a ruɗe yay kan Babiy ɗin yana jera masa tambaya. Babiy ya ajiye kofin ruwan yana mai kallonsu gaba ɗaya. “Kunga ku kwantar da hankalinku babu abinda ya faru daga masarauta ne. Wani bahagon dokine fa ya kunce al'amarin tamkar yaƙi, hatta da zumar dana kai ba'a mora komai a cikinta ba ma”. Ummu da Hanash suka shiga jera salati, yayinda Iffah taji wani ƙududun baƙin ciki ya tokare mata maƙoshi, hakan na nufin bataci nasara ba sai ma Babiy daya dawo da raunika. Jitake kamar taga Tajwar Eshaan gabanta ta shaƙesa da hannayenta har sai ya bar duniya saboda tsabar tsanarsa. Har Hanash ya gama yima Babiy dressing ciwukan batace komai ba, daga ƙarshe ma ɗaki ta shige ta shiga faman kaikawo na tunanin abu na gaba. Dan tayi alƙawarin bazata taɓ haƙuraba sai ta kai *_Tajwar Eshaan ibn Haysam Abdull-majeed_* ƙasa zata samu salama game da rasa ƴan uwanta. Sam a wannan dare Iffah bata wani isashen barci ba saboda ƙullawa da kwancewa aka shiri na gaba. Abinda ta gama ƙullama zuciyarta yasata shirin fita a gidan da hantsi da dalilin cewar zataje wajen Ikram duba mamanta bata da lafiya bazata jima ba. Ummu tayi kamar bazata barta ba amma taita mata magiya harta amince da sharaɗin karta jima, kuma dolene ta rufe duk jikinta. Ta yarda da hakan saboda tana son fitar. A gurguje tai shirin fitar, tare da lalubo wayar Arfa a cikin kayansu. Koda ta haɗa batteryn ta kunna tayi sa'a tanada caji, dan haka ta loda number da take buƙatar kira tana mai addu'ar ALLAH yasa akwai kuɗi ma. Addu'ar tata bata amsu ba, dan haka ta tura wayar cikin jikinta bayan ta kashe sannan ta fito tai sallama da Ummu ta fita bayan ta amsa kuɗin taxi. Sai da ta fito daga cikin anguwarsu gaba ɗaya sannan ta tsaya ta sai kati, koda ta loda sai ta sake gwada kiran lambar ɗazun. Cikin sa'a kuwa aka ɗauka, jimm sukai su duka kafin ta katse shirun da sallama. Daga can aka amsa a noƙe alamar rashin sanin dawa ake tare. Fahimtar hakan ta saka Iffah bashi amsa tunkan yay tambayar. “Sir! Kana magana da Fareedah bint Zayy......” “Serious?”. Ya faɗa cikin katseta da alamar zabura tun kan ta ƙarasa faɗa. Baki ta ƙyaɓe a ƙasan zuciya tana jan tsuka, a zahiri kam sai ta saki murmushin da har sautinsa ya kai cikin kunnensa. Cike da sake ƙanƙan da kai tace “Tabbaci Sir. Ina buƙatar muhaɗune yanzu yaya za'ayi?”. “Kai! Iffah! Ke ɗin dai?...” “Bazan samu damarba ko......?” Cikin sauri ya katseta. “No ba nufina kenan ba, kawai na shiga al'ajab ne. Amma bara na ajiye tantamar tawa gefe dai. Inaga zanzo na sameki gida kawai...” “A'a sir”. “Miyasa?”. “Ba buƙatar hakan, mu haɗu kawai”. Jimm yayi na tunani, sai kuma ya sauke numfashi. “Okay! okay inaga bara na tura miki adireshin inda nake a yanzu haka sai mu haɗu nan in ba damuwa ko”. “Ya dai kasance babu abinda zai shafi mutuncina a wajen sir”. “Wannan shike ƙara samun naji ke ta daban ce Iffah”. Baki ta sake ƙyabewa. Amsa garesa kuma tace “humm” kawai. ★ Kallon baki da hankali mai haɗi da tsoro tun daga ƙarƙashin zuciya yake mata tun bayan gama masa dogon jawabin da tayi. Tasan zataga fiye da hakan ga kowa bama shi kawai ba, dan haka bataji komai ba sai ma murmushi data sakar masa. Bata san mi yake tattaunawa da zuciyarsa ba, amma tanaji a ranta yana auna shekarunta da maganganun da kowa zai auna da wautarta ne kawai. Ilai kuwa sai ta tsinkayi muryarsa da irin amsar datai tunanin samu. “Nikam Iffah shekarunki nawa?”. “Ashirin a kwashe biyu sir”. Ta faɗa tamkar bata fahimci alaƙar tambayar tasa ba. Kansa ya jinjina da cije lips nashi, kansa tsaye yace “Nama tunaninki mai kama da mafarki uziri. Amma zan baki shawara data dace da waɗanan shekarun naki na ƙuruciya. Ƙoƙarin ya kamata kiyi wajen cinye jarabawar share fagen shiga jami'a da ke tunkaroki kamar yanda nasan burinki. Tunaninki kuma ya zam tamkar baki taɓa yinsa ba, sannan na kasance na farko kuma na ƙarshe da kika faɗawa. Hakanne zai baki damar cigaba da ƙyaƙyƙyawar rayuwar da kika fara da ke da ahalinki har nima na cigaba da saka rasan samunki matsayin uwar ƴaƴana wata rana dan ALLAH Iffah”. Ya ƙare maganar da haɗe hannaye alamar roƙo.🙏🏻 “Ƙyaƙyƙyawar rayuwa ta daɗe da yankewa a cikin rayuwata data ahalina. kuma irinta nake hangowa da son daƙilewa ga ƴan baya ciki harda ƴaƴan da kaima a karan kanka zaka iya haifa wataran Sir. Sannan wannan tsoron da nake gani yanzu a cikin idanunka shine zai tabbatar da hakan, koda ni bana raye kai zaka rayu ka tuna. Nagode da saurarena da kayi sir”. Da sauri yasha gabanta kasancewar ta riga ta miƙe. Tai takwaf-takwaf da fuska tana mai tsaresa da manyan idanunta da tuni hasken cikinsu ya koma launin ja. “Ki fahimceni Fareedah, koba komai na fiki shekaru, na fiki ilimin sanin rayuwa dama sirrikan dake zagaye da lungu da saƙo na ƙasar Ruman....” “Na sani sir, tabbas na sani shiyyasa ma na fara nemanka. Sai dai nima kayi haƙuri, dan babu shawararka ɗaya data shiga cikin wannan kan nawa, saboda abinda ke cikinsa tamkar kundin littafin da aka rubuta labari daki-daki ne, kaga dole zaizo feji bayan feji. Kuma duk abinda ya shiga ciki bazai taɓa goguwa ba sai ta hanya ɗaya tak! Mutuwa!. Mutuwa ce kawai zata goge wannan yunƙurin insha ALLAH. Na barka lafiya”. Sororo ya bita da kallo harta tare mototaxi ta shiga, ji yay ta ƙara masa girma a ido, girma bana shekaru kawai ba na wata ilhamar kwarjini da cikar mutuntaka. In har yara irinta da ayanzu suka fara rayuwa zasuyi irin wannan tunani akan al'ummarsu mi manya kakaninsa, iyayensa, yayunsa dama sa'aninsa sukeyi ne su? Shin basa ganin abinda take gani ne? Ko kuwa da gaske tsoron data ambata ta gani a cikin idanun nasane a idon kowa?. Kenan hatta da sauran sarakunan ƙasar da mafi yawan cikinsu sun rasa ƴaƴansu suma cikin tsoron suke? Anya maganar mutane ba tabbatacciya bace akan danganta Shahanshan na daular ruman da magajin fir'auna daya shuɗe batare da labarinsa ya gushe ba?. Iffah! Iffah!! Da gasken gaske ke tadabance kamar yanda nasha faɗa a aji aduk sanda kika bada amsar data danganci darasi...... ★★★ Kwanaki uku kenan da Iffah ta tunkari malaminta batare da nasara ko ƙwarin gwiwa daga garesa ba. Sai dai hakan baisa taji ta sare ba ko haƙura da ƙudirinta. Koda ace nata ajalin take tunkara tayi alƙawarin sai tabi kadin jinin ƴan uwanta guda biyu. Koda ace bata da ƙarfin ikon ruguza mulkin sarkin dake kama da mulki irin na fir'auna zata tabbatar sai kuwwar gunjin kukanta ta fita a duniya, koba komai tanada yaƙinin a bayanta zata samu masu share mata hawaye insha ALLAHU. Hanyar da tabi a farko ita kaɗaice hanyar da tasan tanada ita wajen bi ta samu nasara cikin sauƙi. Sai gashi kuma ba'a dace ba. Gashi tabi ta biyu itama, sai dai anƙi buɗemata ƙofar saboda tsoro da ƙarfin tasirin mulkin azzalumin, a yanzu haka tunaninta hanya ta uku koda itama bazata samu nasarar ba. Zata kuma cigaba da bin hanyoyin koda zasu ninka dubu sau dubu har sai ta dace. Nannauyan numfashin data zuƙa ta fesar, tare da gyara kwanciyata ta jawo wayar Arfa da har yanzu bata bari wani a gidansu yasan da tana amfani da ita ba. Ido sosai ta tsurama wayar, tabbas ba gizo bane tarin missed call ne daga malaminta. Taruwarsu da rashin jin sanda suka shigo wayar kuma nada nasaba da kasancewarta a silent. Tayi kamar zata share amma sai ta kasa hakan. Dan a yanzu shine kawai madubin da take kallo matsayin damar dake a hanunta ta isa ga abinda take so da wurwuri. Cikin sa'a tana kokarin kiransa sai ga kiran nasa ya sake shigowa. A dakile ta amsa tare da masa sallama murya a cuɗe. “Kiyi haƙuri”. Kalmar farko data fara fita a bakinsa. Iffah taja numfashi mai nauyi tare da haɗiyewa muƙut. “Sir bakamun laifin komaiba nikam”. Ta faɗa tamkar komai baima faruba. “Humm” ya faɗa shima, sai kuma ya ɗora da faɗin “Ina son mu haɗu”. “Babu dalilin hakan sir”. “Akwai Fareedah, kar kiyi taurin kai”. “Koba komai kai ɗin malamina ne ai, mi zaisa na maka taurin kai?. Iya gaskiyata nake faɗa maka”. “A cikin gaskiyar taki harda haƙura da samun abokina”. Zumbur ta miƙe zaune tamkar wadda aka kwantsamawa a radu a tsakkiyar kunne. “Sirrrrr!.....” “Na amince zan haɗaki da shi”. Ya katseta da sauri. Jitai tamkar ta sandara ihu ko zaifi fahimtar farin cikin dake a tare da ita, amma sai tai ƙoƙarin gimtsewa. “Sir ba dole sai shi kawai bane zaiyi aikin, harma na samu wan....” “Fareedahhh!”. Ya faɗa da wani yanayi a muryarsa. Ajiyar zuciya ta sauke a ƙasan maƙoshi. Sai kuma ta lumshe idanu tamkar tana a gabansa tace, “Shikenan ka turamun adireshi. Sai dai inda bazai taɓa mutuncina ba”. Murmushi yayi mai sauti, tare da faɗa kamar yanda ya saba tun acan baya. “Fareedah ke ta dabance ƙwarai da gaskeeee”. Baki taɗan laɓe batare da tace komai ba ta yanke wayar..........✍ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +2290165991 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_8_* ..........Zaune takai a kujerar dake duban tasa tana mai kallon agogon hanunanta. Ya saki murmushi cikin kafeta da idanu. “Daga zuwa sai duba agogo?”. “Hakan dolene Sir, domin ko lokacin islamiyya zan cinye anan. Kaga kenan sai da tsantseni”. “Okay”. Ya faɗa yana gyara zamansa. “Ba buƙatar maimaita abinda ya faru baya, na gaba kawai yanzu shine zanyi iya ƙoƙarin ganin na haɗu da abokin nawa koda ta waya ne, kin san aikin nan nasu yana hanasu samun isashen lokaci matuƙa kasancewarsu manya dake tare da babbar kafar yaɗa labarai mai aiki da kamar duniya gaba ɗaya. Ke yanzu a gareki miye shirinki?”. Kafaɗa Iffah ta ɗan ɗage cikin jan iska da hurowa. “Kusan dukan shirina a kammale yake, burina kawai nasamu yin hira da African Aye👁️‍🗨”. “Indai hakane haɗuwa da abokina kawai ya rage mana, fatana dai bayan ni kar wanda yasan wannan hatta a gidanku, inba hakaba zamu iya shiga haɗarin da har burin rayuwarmu ma bazai cikaba bayan wannan. Nikuma zanyi duk yanda zanyi insha ALLAHU wajen hana wannan sirrin fita daga gareni....” “Shi abokinka ɗin fa?”. “Baki da matsala da shi domin shi aikinsa ne”. Kai ta jinjina masa fuskata cike da murmushi. Sai kuma ta rissinar da idanunta alamar jin kunyarsa saboda kallon daya kafeta da shi. Kunyar nada nasaba da tuna yanda ta dinga wancakalar da shi da manufarsa a sanda yake malaminta. Sai gashi shine na farko data fara tunkara da matsalata a yanzu duk da kuwa tana kallonta a kan matsalar data shafi kowa na ƙasar Ruman ne. Sautin murmushinsa ya sakata ɗagowa ta ɗan kallesa, sai kuma ta sake kauda kanta gefe itama tana murmushin. “Hummm!” Ya faɗa yana miƙewa. Itama miƙewar tayi batare data yarda sun sake haɗa ido ba. “Kije gida zamuyi waya”. “Nagode sir, ALLAH ya tsare gabanka da bayanka”. Jin sautin murmushinsa ya tabbatar mata jin daɗinsa, amma sai tai gaba da sassarfa tunkan ya sake cewa komai........ ★__________________★ *_DAULAR RUMAN (MASARAUTA)_* Katafaren ɗaki mai ɗauke da ƙayatattun kayan more rayuwa, kwance take bisa lafiyayyen gado da dukkan nau'in shimfiɗunsa suka kasance na alfarma. Sautin dariyar dake tashi cikin kunnuwanta tamkar mafarki ya sata buɗe idanu, cikin tsumar jiki ta ture lallausan bargon da take ciki, tamkar walƙiya ta dire ƙasan lafiyayyen kafet ɗin dake malale gaban gadon tai kneel down tamkar mai neman gafara, kanta a risine alamar nuna tsantsar girmamawa..... Tamkar shirin film ko labaran almara tsohuwa tukuf sanye cikin jajayen kaya ta bayyana bisa baƙar kujerar ƙarfe mai ɗauke da adon gold a cikin ɗakin. Baƙace matuƙa mai tsananin muni da jajayen idanu, yanda ta zauna ƙafa a harɗe kai ka ɗauka itace Shahanshan ɗin..... “Lafiya da tsahon rai su ƙara kasancewa a rayuwar *_Uwa_* mai share kukan masu kuka”. Hamshaƙiyar matar ta faɗa cikin tsantsar girmamawa ga tsohuwar dake harɗe saman kujerar tata tamkar sarauniyar ingila. Cike da isa da ƙasaita tsohuwar taja wani kakkauran numfashi da sake faɗaɗa girman ƙofofin hancinta ta hanyar hurashi, ƙara harɗe ƙafafunta tai tana mai motsa yatsun hanunta, idanunta jajaye kafe akan matar. Cike da isa da ƙasaita mai ɗauke da rashin daɗin muryarta ta tsufa ta fara magana. “Ta-ƙurya kin kusa cin nasara wajen cika sharaɗi na biyu akan alƙawarinmu. Na tayaki murna, saura sharaɗinki na ƙarshe, mafi wahala a cikinsu”. Ƙasa ta ƙarayi da kanta cike da girmamawa a gareta, da dukkan ƙarfin zuciyarta ta furta, “Kece madubin nasarata Uwa!, duk inda akaga naje da jagorancinki na isa. Yanda na cika na farko shima na biyu zan cika sa, nayi alƙawarin cika na ƙarshe ma fiye da yanda kike tsammani.....” Jajayen idanunta masu kama da garwashin wutar gidan biredi ta ɗago tana kallon ƙyaƙyƙyawar kuma hamshaƙiyar matar dake gurfane a gabanta. Ta ƙyalƙyale da wata dariya mara daɗin saurare ga kunen kowa, sai kuma ta gimtse tamkar ba ita tayi ba tana zaro manyan jajayen idanunta kamar na dodanni. “Ta-ƙurya nasan zaki iya, sai dai akwai wani babban ƙalubale dake tunkaro cikar nasararki ta biyu, kuma gab yake da cimmawa, idan baki gaggauta datsesa ba, zakiyi biyu babu”. A razane ta ɗago tana kallonta cikeda bushewar zuciya, sai kuma ta maida kanta da sauri ta rissinar “A gafarceni Uwa, a kawar da ko miye mai son yima cikar burina kutse. Na rantse da ALLAH daya halicceni, koda cikin yankin ahalina ne bana buƙatar numfashinsa Uwa!!”. Dariya ta sake ƙyalƙyalewa da shi sai kuma ta gimtse fuska. Kanta ta shiga girgiza mata da dukkan isa. “Ta-ƙurya wannan karon akwai banbanci da koyaushe, dama na taɓa faɗa miki bayan cikar nasararki ta farko akwai ƙalubale dana gani akan cikar ta biyu, sai dai ba'a buɗe mun komaiba a wancan lokacin, alamar haka na nuna ƙarfin taurarin mai yunƙurin, amma a daren jiya dana tsananta bincike akan mafarkinki na gano wani yanki da ƙyar. Ƴar shilar suda na ƙoƙarin yin cara irin ta gawurtattun zakaru a kunnen bututu da taimakon wata zuciya mai son kusantar tata.” “A taimakeni a kawar mun dasu gaba ɗayansu Uwa. Ko a bani damar kawar da su da kaina”. “Hhhhhhh!!!! Ƙaddarar ƴar shilar bata mutuwa bace cikin sauƙi. Tana kuma da ƙarfin taurarin da zata iya cin nasarar dusashe naki”. Bugawar da ƙirjinta yayi ta zata zuciyarta ce zata fito ta bakinta dan tsabar razana. Ta kafeta da idanu cikin wani irin yanayi mai wahalar fassara. Sai kuma tai saurin maida kanta ƙasa ta rissinar tana faɗin, “A gafarceni Uwa”. Wani irin kakkauran numfashi mai cike da gargaɗi tsohuwar taja, cike da ƙasaita tana yamutse mummunar fuskarta ta cigaba da faɗin, “Zamu iya samun mafita sai dai akwai ruɗani a cikinta. Har zuwa yanzu kuma ban samu buɗewar ruɗanin ba kai tsaye. Dan haka kina da zaɓi biyu. Kodai ki ƙara yin duk yanda zakiyi igiya ta ƙullu tsakanin Malik-alMuluk da wannan ƴar shila muyi duk yanda zamuyi tazama cikamakin aikinmu na biyu, ko kuma ki barta ta cimma burinta.......” Idanunta da suka kaɗa jajur tai ƙoƙarin ɗagowa, sai dai ta maidasu da sauri zuwa ƙasa. “Uwa amma kin faɗamin na cinye jarabawa ta biyu da zarar ya aura cika makin matansa shine matakan nasarata, yanzu haka akwai su su biyu da suka rage ɗauke da aurensa a kansu, zasu miƙasu garesa a karshen watannin nan kamar yanda na samu tabbaci. Taya zamu shigo da wata bayan aikin ya cika. A yanzu ya rage kawai samun cikar burina na ƙarshe ne a kansa. Miye dalilin shigowar wannan yarinyar abinda bai shafeta ba? Mizai hana ai mata wani hukuncin daya dace da ita?...” Hannu ta ɗaga mata cikin tarar numfashi da ƴar hasala-hasala, da kakkausar murya tana mai nunata da ɗanyatsa “Amma har yanzu ban sanar dake wadda ta dace ba, kuma damun san cutarwace na umarninmu gareki bazamu ce ta shigo ba”. “Hakane Uwa, a gafarce ni. Sai dai Mahaifiyar Zak.......”. Ta faɗa da alamun shiga tashin hankali mai girma, amma kallon da Uwa ta watso amata ya hanata ƙarasawa. Bata tanka mata ba, sai dai yanayinta ya nuna a hasale take, dan cikin kaushin murya da zunzurutun jin zafi ta kaɗa ƙahon hanunta mai kama da kwarkwaron gidan dodon koɗi. A take haske ya gilma, sai ga farar takarda a hanunta. “Ƴar shila burinta shine ɗaukar fansa, domin biyu a cikin masu ɗakin Malik-alMuluk da suka shuɗe jininta ne. Burinta shine bin kadin jininsu ta hanyar bayyanama duniya ko kawar da shi. Bayyanawar tata kafin cikar burinki faɗuwarki ne, a yanzu haka kuma ta haɗu da mai taimaka matan harma sun gama magana”. Sosai zuciyarta ta ƙara harzuƙowa. Amma sai batace komai ba saboda ganin Uwa a hasale take da ita. Cikin yin ƙara ƙasa da kai tace, “Da ace bayan cikar burina ne kauɗi da ƙudirin ɗaukar fansar wannan yarinya ya shigo haske ne ga cikar burina. Dan zata ƙarasamin aikin ƙarshe da zanyi. Amma tunda ta shigo a tsakkiyar labarina dolene ta fuskanci hukuncin daya dace da ita. Idan ita bazata mutun ba shi a kawar min da shi mana Uwa”. “Hakan mai sauƙi ne, sai dai shima babu buƙatar mutuwarsa, dan zai iya mana amfani a gaba. Sannan shi rabata da shi shine mafi ƙololuwar hukuncinsa. Dan haka daga nan zuwa safiyar kowace juma'a ta ƙarshen shekarar nan ki tabbatar an zarga igiya tsakaninta da Malik-alMuluk, a dakatar da kai masa matan da suka rage a kaita garesa bayan tarewa, dan da ita zamu cigaba da amfani har samuwar cikar burinmu ga kowa!!.” Da sauri ta ɗago kai jin muryar nayin nesa da ita, sai dai kafin ta iya furta wani abu Uwa ta ɓace daga ɗakin tamkar guntun girgijen hadari a tsakkiyar fararen gizagizai. Zumbur ta miƙe tana mai dafe kanta dake sara mata, wani irin tuƙuƙi da ƙaiƙayin mai zafafa ruhi zuciyarta ke mata. Sai dai sanin wacece Uwa ya sata jin ɗan sassauci kaɗan, amma ruɗani mai ɗauke da abubuwa masu matuƙar yawan gaske da fassarasu a ɗauka shekara dubu bisa dubu ba'a kammala ba na neman danne wancan ƙwarin gwiwar. Taya ruhin ƴaƴan sarakunan ƙasar Ruman basu bata matsala ba sai ƴar talakawa ƙasƙantattu? Dolene yarinyar nan ta ɗanɗana kuɗarta na hukuncin shiga gonar daba tata ba ƙwarai da gaske, sai tayi wasa da ita a tsakkiyar titi wasa irin na ɓera a hanun mage, dan ko ita Malikat bata isaba..... (Tofa masu karatu, ita kuma wannan wacece ita? Iffah fa ta taro match ɗin da babu players. Kumuje zuwa dai muga yaya wasan zai kaya🚴🏼...) ★__________________★ *_IFFAH_* A ɗan firgice ta buɗe idanunta tare da tura hannu ƙarƙashin filon data tada kai ta sake danne wayar dake faman ɓurari cike da tsoron kar Ummu ta jiyo, dan tasan Babiy da Hanash basa gidan. Ajiyar zuciya ta sauke mai matuƙar ƙarfi da zaro wayar, cikin rawar jiki ta dannata a silent. Tamkar jira kiran ya sake shigowa kuwa. Idanunta masu matuƙar girma da haske ta waro sosai ganin mai kiran, ai batama bari tayi ring na biyu ba taa ɗaga tare da kaiwa kunnenta tana direwa a gadon. “Kina jina?”. Aka faɗa daga can. Kanta ta jinjina masa tamkar tana gabansa dai-dai tana leƙawa tsakar gidansu. Daga can gefen da Babiy ke kiwon tsuntsaye ta hango Ummu, dan haka ta sauke ajiyar numfashi da fara magana cikin raɗa. “Ina jinka Sir! Ta samu ne?”. “Babu lokacin dogon magana Iffah, kiyi ƙoƙari daga nan zuwa awa ɗaya ki sameni, dan kuwa mun tsinta dami a kala Ajmal ya shigo Ruman, kuma a yanzu haka mun gama magana da shi sai dai ban sanar masa ainahin zancen ba, ya kuma buƙaci haɗuwa dake.....” “Ya ALLAH! Alhmdllhi. Naji daɗi matuƙa wlhy Sir. Insha ALLAHU duk yanda zanyi kuwa zan fito ka saurare ni”. “Okay”. Kawai ya faɗa yana mai yanke wayar. Itama shiri ta shiga faman yi a gaggauce, tare da tattare takardun dukkan bayanai data tattara waje ɗaya. Bakinta ɗauke da addu'ar samun nasarar amincewar Ummu abisa ƙaryar data shirya akan fitar ta fito. Daga inda Ummu take tako zubomata ido na alamar tuhuma. Gareta ta ƙarasa cikin danne komai da karsashin data aro. “Ummu kiran gaggawa na samu daga Ikram. Inaga dai abinda muka jima muna jirane ya fito”. “Amma Iffah....” “Ummu dan ALLAH kar kice a'a”. Iffah tai saurin tarar numfashinta cike da marairaicewa. “Ni ba hanaki zanyiba, sai dai wannan yawan fitar taki a kwanakin nan bana zuwa makaranta ba ya fara damuna Iffah. Shin kin manta halin da muka shiga da wanda zamu iya shiga a yanzu? Ina jin tsoro wlhy, matuƙar tsoro a duk sanda kika fita koda makaranta ne”. Sosai tausayin Ummu ya sake mamaye zuciyar Iffah, ta haɗiye hawayen da suka taru mata a ido tana ƙaƙaro murmushi. “Insha ALLAHU Ummu babu abinda zai faru, wanda ya farun ma a baya bazamu taɓa mu yafe ba. Fita ta kuma ta daina baki tsoro, tunda kinga duk sanda zan fitan ina suturta dukkan jikina”. “Shike nan ALLAH ya tsareki, dan ALLAH kiyi maza ki dawo kafin Abbin ku ya dawo gidan nan ko ɗan uwanki”. “Insha ALLAHU Ummuna”. Iffah ta faɗa tana rungumeta. Shafa kanta Ummu tai tana murmushin ƙarfin hali itama, dan ba wani zuciyarta ta samu nutsuwa bane ita dai, ta bartane kawai saboda tace fitar ta shafi karatunta. Amma zata cigaba da rakata da addu'a harta dawo.........✍ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +22 90165991 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_9_* ...........Kasancewar wajene daba kowa ke shiga ba anyhow yasa sai da Iffah tai kiran Sir Fawzan bayan saukarta a bakin gate. Umarnin bama security ɗin wajen wayar ya bata. Bayan yayi magana da security ɗin suka bata damar shigewa batare data san miya faɗa musu ba. Tafiya take a nutse tana ɗan kallon wajen da tsarinsa. Dan babban garden ne mai cike da ababen kallo da ni'imtattun korayen ciyayi da ƙawatatun filawoyi. Ta taɓa shiga sau biyu a dalilin taron makarantarsu ta Islamiyya da aka gudanar a wajen. Ya riga ya faɗa mata inda zata samesa, dan haka kanta tsaye take nufar wajen ranta fes da nishaɗi tamkar ance mata ga wuƙa ga maƙoshin Tajwar Eshaan ta yanka. Sai da taje kusan ƙarshen garden ɗin ta tsaya, sai kuma ta shiga canki in canka na number wajen daya bata kasancewar akwai rukuni-rukuni na ɓoyayyun wajen hutawa da manyan mutane sukafi tu'ammali da su idan basa buƙatar wata hayaniya. Cikin ɗan ɗage kafaɗa ta nufi na farkon da zuciyarta tafi karkata. Ƙawatuwar wajen takai mai kallo shagala harya iya manta abinda ya kawoshi, kamshin firanni da wani iska mai busawa a hankali kaɗai na dabanne. Jitai kamar da shakku na shigowarta wajen, amma sai ta dannesa a ƙasan zuciya ta cigaba da takawa tamkar mai sanɗa tana leƙe-leƙe. Ta isa kusan tsakkiya zuciyarta ta shiga gargaɗinta ganin babu alamar akwai mutum mai numfashi a wajen, cak ta tsaya tare da ciro wayarta domin neman sir Fawzan. “Ya ALLAHU”. Ta faɗa jin ana sanar mata bata da kati kona sisi a wayar. Kamar zatai kuka ta sauketa daga kunenta tana ɗan ƙara danne-danne da cigaba da takawa a hankali batare data san mike a gabanta ba. Kaɗowar iska da sassanyan ƙamshin turare mai daɗin gaske ya sakata tsayawa cak ƙirjinta na harbawa da ƙarfi. Fararen idanunta ta janye daga kan wayar tare da ɗago kanta gaba ɗaya, a kan mutumin dake kishingiɗe bisa wani lallausan jan darduma daya haɗu da kalar korayen ciyayi ya bada ƙyaƙyƙyawan tsari ta sauke. Rabin jikinsa akan tum-tum yake. Kansa a risine yana kallon lap-top ƙirar kamfanin apple dake akan wani ƙaramin tum-tum ɗin itama. Gefensa kaɗan wani ƙyaƙyƙyawan bowl ne fari na tangaran, sai butar shayi kalar golden akan tray dake tabbatar da set ne dan harda ƙananun cups nashan shayi. Sanye yake da ƙananun kaya farare tas da suka fidda ainahin suffarsa ta masu ta'amalli da ƙarafuna, gashi sun sake fidda ainahin hasken fatarsa da sheƙinta irin na masu jin daɗi. Duk da tana a gab da shi aikinsa yake hankali kwance baiko nuna alamar yasan da zuwanta ba. “Mi kake buƙata?”. Sassaanyar muryarsa mai zurfi da kamewa ta daki kunenta da alamar akwai wanda yay tsammani ba ita ba. Ƙirjinta ne ya sake harbawa har tanaji kamar jininta daya tsinke na neman biyo hudojin gashin fatarta ya fito. Bata da niyyar cewa komai, gata tsaye tamkar an dasata ta gagara ɗaga ko ƙafa ɗaya tabar wajen duk da haka zuciyarta tafi buƙatar da tayi. Jin shiru ba'a amsa masa ba, ga tsaiwar mutum yanaji har yanzu a gabansa ya sashi ɗago lulu idanunsa masu haske da baiwar bakin ƙwayar tsakkiyarsu ya sauke a kanta. Komai tsayawa yay daga garesa, kamar yanda Iffah ma hatta kaɗawar iskar wajen ta tsaya mata cak... Fuskarsa dake a kame da kwarjini ya sake tsumewa yana sassauta girman idanunsa tamkar mai son lumshesu da gayya. A fisge, tamkar an jawo furucin daga bakin Iffah ta yamutsa fuskarta da ƙanƙance manyan fararen idanunta da tun a kallon farko ta kaudasu da ga kansa alamar kunya irin ta mace, “Idan ma kai aljanine wlhy nafi ƙarfinka. Wace irin jaraba ce duk inda nai saina ganka”. Ta ƙare maganar da hura bakinta. Kamar yanda bai motsa daga yanda yake ba haka bai ce mata komai ba, bai kuma janye idanunsa a kanta ba har yanzu. A zuciyar Iffah fa ta fara tsorata dajin tabbacin mutumin nan fa ƙila aljani ne. Amma sai taga idan ta nuna tsoronsa fa zai ma iya kasheta, saboda a yanzu haka ma ƙarfin hali take, tana matuƙar jin kaifi da tasirin idanunsa a dukkan ɓargon jikinta da jijiyoyi da gudanar jini. Amma sai ta dake a ƙasan ranta tana karanto addu'ar neman tsari da aljanu. Kusan tunani iri ɗaya ne a zukatansu. Dan shima dai zuciyarsa ta ƙara yarda wannan abar aljana ce kawai, yana ganin kuma ya kamata yasan miyasa take bibiyarsa ne?. Nisan data fara masa a idonsa ya fahimci tabar wajen, ilai kuwa can ya hangota tana tafiya cikin sassarfa ta nufi ƙofa. Cin karo data kusan yi da mutum ya sata ja gefe da sauri. Ɗaya daga cikin matasan datai masa gani biyu da su ne, cikin nuna alamar mamaki da tsuke fuska yake kallonta. Harara ta balla masa ta ƙyaɓe fuska da raɓashi ta wuce, danji take ƙafafunta tamkar ba'a kansu take takun ba..... “Fareedah!”. Da sauri ta juyo jin muryar Sir Fawzan daya sauke numfashi da dafe kansa na tabbacin ya jima yana nemanta. “Ina kika shigane wai? Tun ɗazun sai faman zagaye garden ɗin nan nake ni da securitys nemanki, ga wayarki ma taƙi shiga sam”. Maimakon ta bashi amsa sai ta zube a kujerar dake a kusa da ita ragwaf. A wahale tace “Sir ka bani ruwa nasha Please”. Sosai yanayinta ya sake neman firgitashi, amma fahimtar ruwan tafi buƙata ba tambaya ba ya sashi barin wajen da ɗan hanzari. Mintuna ƙalilan ya dawo da robar ruwa. Miƙa mata yay bayan ya ɓalle murfin. Tunda ta kafa kai bata koja numfashi ba sai da ta sha fin rabi, ta sauke robar tare da dafe goshinta tana sauke ajiyar zuciya a jajjere. Lokaci ya bata sosai ta samu nutsuwa kafin ya kai zaune a kujerar dake facing ɗinta. “Fareedah miya faru wai? Ina kika shiga? Duk kin tadamin hankali saboda security sun tabbatar min kin shigo”. A hankali ta ɗago manyan idanunta da launin farinsu ya sirka ta zuba masa. Sai kuma ta janye da sauri tana girgiza kanta dan fuskar mutumin nan kawai ta gani a tare da shi saboda ta sakama ranta aljani ne. Idanunta rumtse tare da yakice tunanin ta sake buɗesu akansa. “Sir lokaci ya ƙure ina abokin naka?”. Ya fahimci bata son bashi amsa, sai kawai ya girgiza mata kai. “Rashin ganinki ya sakani a ruɗanin da har ya kira waya ban sani ba, sai daga baya na lura na kirashi shima kuma bai ɗaga ba”. “Ya ALLAH, shike nan itama wannan damar ta kufce min!”. “Bazamuce haka ba sai munji ta bakinsa, a yau ne dai kawai nake ganin bazai yuwu ba gaskiya, kodan ke a karan kanki ma. Kinga saura baifi mintuna arba'in ayi magrib ba. Kije gida, insha ALLAHU zanbi duk hanyar data dace domin ganin kin haɗu da shi”. Kallonsa take kamar zatai kuka. Sai dai saka zantukansa a ma'aunin hankali ya sata kasa cewa komai. “Kiyi haƙuri”. Ya faɗa cikin sake sanyaya murya yana mata wani lallausan kallo. Kauda nata idon tai daga kansa, taja iska ta fesar da jinjina masa kanta kawai. Dan ta tabbatar inhar tai magana kuka ne zai iya ƙwace mata ma..... *_MASARAUTA_* Gurfane take a gaban Uwa kamar yanda dokar take ga duk wanda ke binta. Duk da matsayinta da girmanta a cikin daular ruman a gaban uwa ita ba komai bace face mai neman biyan buƙata (Wa'iyazubillah). Kamar ko yaushe tsohuwar da suke kira uwa sanye take cikin jajayen kaya, sai dai saɓanin waccan ranar yau inuwarta kawai ake iya gani a jikin bangon ɗakin. Amma abin mamaki babu tsoro ko wata shakkar hakan a idanun hamshaƙiyar matar. Inuwar uwa ta kece da mumunar dariyarta mara daɗin saurare, kai kace za'a iya jinta a duk faɗin masarautar, sai dai abin mamaki iya ita ɗin kawai take jinta. Sai da tayi mai isarta kafin ta tsagaita tamkar ba'ita tayin ba. “Ta-ƙurya alƙawarina ya cika, zaku iya tunkarar kowa a yanzu da maganar auren Malik-alMuluk babu mai musa miki hatta Malikat da shi a karan kansa balle duk wani mai faɗa masa yaji. Sai dai akwai banbanci a wannan karon da baya. Hhhhhhhh!!”. “Umarninki shine abin jira Uwa mai share kukan mai kuka”. “Hhhhh Ta-ƙurya shiyyasa bana baƙin cikin taimakonki, zan kuma cigaba da taimakonki kiyita na sara keda duk mabiyanki. Ragamar kasancewar gida a hanun wasunki bashine zai sa su zama masu ƙarfin ikoba sama da naki. Ki shiga ki fita a haɗa gagarumin aure na bajinta tsakanin wannan yarinya da Malik-alMuluk. Hakan zaisa su shagaltu da tunanin komai ya canja musamman shafe watanni tara da Zawjata-almilki da suka rage suka kwashe gidan nan batare da ko ciwon kai ba. Ina son ki nuna bajinta irin wadda ko Malikat bazata yiba, Daular ruman zata cigaba da kasancewa a tafin hanunki a baɗini koda a zahiri kinada wanda suke nuna sunfi ƙarfinki. Ranar mako zata zama ranar sa'a Hhhhhhhh!!!”. Sautin dariyar ya cigaba da nesa da kunuwanta har inuwar uwa ta ɓace. Nannauyan numfashi ta sauke tare da murmushi mai nuna tsantsar farin ciki. Ta dubi ƙyaƙyƙyawan farin tafin hanunta da jini keta kaikawo tana sake maimaita kasantuwar daular ruman a tafin hanunta da uwa ta ambata mata. Tabbas ita ɗin mai sa'a ce, sa'ar da zata iya nunata a gaban duk wasu sa'ointa koma wanda suka ɗarata. Fatanta kawai ALLAH ya kaita ranar cikar burinta gaba ɗaya domin tabbatarma kowa dake cikin Ruman ma ba daular ruman kawai ba *Saka ƙwan kaza bashi ke nufin mallakar akurki ita ɗaya ba* sannan zuwan *mai guri bashi ke tabbatarda naɗewar mai tabarma ba*....... ★★_______★ Kwanaki biyu kenan Iffah bata sake neman sir Fawzan ɗinta ba, ta kuma kashe wayarta ta yanda shima koya nemeta bazai sametan ba. Ita tasan dalilin zaɓar yin hakan, duk da yanayinta ya nuna tana da damuwa dan babu walwala tattare da ita sam tun baro garden ɗin da tayi. Yau ma data kasance bazataje makaranta ba kamar yanda ta saba ta tashi taya Ummu aiki, sai dai yanda take komai kamar mara laka a jiki yasa Ummu nutsuwa a nazartar ta.. “Wai lafiyarki kuwa Iffah? Tun dawowar fitar da kikai shekaran jiya duk kin wani canja. Ko jikin naki ne?”. “A'a Ummu, kawai dai kaina na ɗan mun ciwo ne ƙasa-ƙasa. Amma na san barci ne da bai isheni ba”. “Barci kuma? To miya hanaki barcin?”. In'ina ta fara na rashin sanin abinda zata faɗa. Sai kuma tai ƙasa da kanta ganin yanda Ummu ta kafeta da idanu. Ummu mace ce mai yawan tsantseni wajen tarbiyyar ƴaƴanta. Komai tana binsa a sannu babu garaje ko gaggawar akan tafida yaranta tun kafin sukai haka, shiyyasa cikin sauki take iya sanin matsalolinsu da saurin fahimtar sabuwar hanya da suka ɗauka saɓanin wadda ta sansu da shi. Yanzu ma dai ɗauke kai tai ga Iffah ta cigaba da hidimar gabanta batare data sake magana ba. Daga baya ma saita ƙirƙiri jan Iffah da sabuwar hira da bata da alaƙa data farko. Tun Iffah na ɗararewa har ta saki jikinta... ★Washe gari ta ɗan danne kaso sittin cikin dari na damuwarta dan kar Ummu ta hanata zuwa makaranta. Sai dai koda taje makarantar ma dai zaune kawai ta kasance badan ta nutsu a fahimtar komai ba har aka tashi. Kanta tsaye ta fito domin samun abin hawa a bakin gate kamar sauran ɗalibai. Da ƙyar ta samu tare da wasu da suke kusan a anguwarsu, sai dai zasu rigata fara sauka... A hankali wata baƙar mota dake fake ɗan nesa da makarantar tasu ta fara bin bayan mai Mototaxi ɗin da sam shi hankalinsa baima kai ba. Haka suma su Iffah babu wanda ya kula da motar. Da mai motar ya fahimci zasu zargesa sai ya canja salon bin nasu. A haka har aka sauke abokan tafiyarta. Motar ta cigaba da binsu har titin anguwarsu, anan aka dakata har mai Mototaxi ɗin ya shiga ya kai Iffah ya juyo zai fita suka tsaidashi..........✍ _To ke kuma baƙar mota daga ina🙆🏻?._ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 90165991 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_10_* ........Kamar wasa Iffah na shigowa gida ta zube kwance tana rawar sanyi, ga jikinta ya ɗauka matsanancin zafi. Ummu bata kawo komai a ranta ba game da ciwon Iffah sai tunanin ranar da ake ƙwallawa ce ta washeta. Da ƙyar ta tilastata tai wanka, taci abinci kaɗan ta ajiye. Maganin zazzaɓi Ummu ta bata tasha, daga haka ta koma ta kwanta ranar ko Islamiyya bataje ba. Da dare firgita data dingayi saboda munanan mafarkai ya sa kusan kowa bai rintsa ba a gidan sai gab da asuba. Da barci yaɗan figeta saita tashi a firgice har sai sun rufeta da addu'oi take samun nutsuwa ta sake komawa barci. Al'amarin ya tsayama kowa a rai, sai dai ganin ta tashi ragal da asuba tai salla sai sukaita mamaki. Dan bazaka taɓa tsammanin itace a daren jiya ba. Da safe koda tace zataje makaranta hanata Babiy yayi, acewarsa ma asibiti zasuje da Hanash. Kasancewar Iffah da rashin son asibiti sai ta turje akan itafa ta warke, dama jiyan rana ce (ta fake da abinda Ummu tace). Ganin harda ƴan kwallanta Babiy yace to inhar zazzaɓi ya sake dawowa a yinin yau dole suje asibitin nan. Da sauri tace ta yarda. Bayan wucewar Babiy tai ta ɗan ƙarfafa kanta harda taya Ummu aiki, duk da yanda takejin yanayinta babu daɗi haka tai ƙudirin shirin Islamiyya idan lokaci yayi, tana ɗaki kwance bayan idar da sallar azhar sai ga kiran malaminta Fawzan, wayar kawai ta tsurama ido tamkar bazata ɗauka ba harta katse, wani kiran ya sake shigowa shima harya katse bata ɗaga ba. Duk da zumuɗin son ganin kiran nashi da take ciki a kusan kwanaki uku sai taji hanunta ya mata nauyin ɗagawa a yanzu daya kira... Shigowar saƙo ya katse mata tunani, ta kai hannu kan wayar ta ɗauka kamar mai tsoro... _“Fareedah ga dama ta biyu ta sake samuwa, Idan kinga saƙona kiyi ƙoƙarin fitowa kafin Four”._ A zabure ta miƙe jikinta na tsuma ta hau shirin Islamiyya, tare da tattare dukkan takardun bayanan da take ta faman adanawa harma da waɗanda ta ƙara haɗawa a kwanaki ukun nan. “Ummu zan wuce Islamiyya”. Ta faɗa lokacin da take ƙoƙarin saka takalmi a ƙafarta Ummu na tsakar gida tana alwalar sallar la'asar. “Ke da baki da lafiya auta”. “Ummu naji sauƙi wlhy, kinga saukarmu ya kusa babu buƙatar na fara wasa ai. Malam nata mana gargaɗin hak......” Sauran maganar ya maƙale a harshenta sakamakon tashin sautin busa mai nuni da isowar jama'ar masarautar Daular Ruman. Tamkar an daki kan Iffah da guduma haka taji wani dummm! A cikin kunnenta har suka ƙarasa shigowa cikin gidansu jinta bai dawo ba. (Shin tsoro ne? Ko firgici?) bata san wanene ya risketa ba...... Taɓata da Ummu tayine ya sata jan kakkauran numfashi tare da kallonta. Jikin Ummu ne ke rawa, idanunta kam tuni sun tara ƙwalla. Iffah ta shiga girgiza mata kai alamar kar tai kuka, ta sake damƙe hanunta cikin nata tare da maida kallonta garesu rai ɓace, dan ta ɗauka alwashin a wannan karon komi sukazo da shi sun tara sun samu, sai dai a kasheta... “Mi kukazo yimana a gida kuma? Ko kun dawo muma ku idasa kashemu tamkar yanda kuka halaka min ƴan uwana da tsafink......” Da sauri Ummu ta danne mata baki da tafin hannunta tun kan ta ƙarasa faɗa. Kai take girgizamata cikin rawar jiki. Da ace ba Ummu bace babu abinda zai hanata ta ture hanunta ta ƙarasa abinda ta fara faɗa ko zata samu salama a ranta. Sai dai kuma bazata iya ba, dan haka ta shiga yima Ummu alamar roƙo da magiyar ta barta amma taƙi yin hakan... Basamuden nan ne na kullum mai riƙe da bulala ya daka mata tsawa. Da sauri Ummu ta sakemata baki, sai dai ta jawota jikinta ta ƙanƙame. Iffah jitai zuciyata ta ƙara hautsunowa, a matuƙar zabure ta sake buɗe baki zatayi magana ya dakatar da ita... “Ke ƴar talakawa lura da inda kike. Bakin rijiya ba wajen wasan makaho bane. Idan taƙamarki tsageranci tamkar ƙiftawar ido za'a sauke miki shi, a kuma shafe babinku daga ke har iyayen naki a doron ƙasa”. Hasala iya hasala Iffah tayi, Kukan da Ummu ta fashe da shi ya hanata cewa komai ta juya gareta jikinta na rawar shiga tsananin ɓacin rai, kanta take juyamata alamar karntace komai..... “Umm....” “A'a Iffah! Ina umartarki karki ce komai”. “Kibarta tace ɗinma yanzu harshenta ya zama datsatstse a gabanki.” Kafin Ummu dake girgiza kai tace komai Babiy ya shigo tamkar an jehoshi, da alama dai wanine ya sanar masa da zuwan jama'ar masarauta gidan nasa. Ko sau ɗaya basu bashi damar cewa komaiba suka isar masa da saƙon kira daga daular ruman. “Innalillahi.....” Iffah ta shiga ambata ita da Ummu, dan sunaji a ransu tarihine dai yake ƙoƙarin maimaita kansa, hawaye masu tsananin ƙuna da ɗaci na gangarowa bisa ƙyaƙyƙyawar fuskata Babiy da shima dai yasan labarin gizo bazai wuce ƙoƙi ba. A gaban idonsu aka wuce da Babiy Daular Ruman a karo na uku, tare da barin wasu dakaru a ƙofar gida ta hanyar hana duk wani mai yunƙurin fita daga gidan. Haɗe kai kawai Iffah da Ummu sukai suna kuka, dan shi kaɗai suke da damar yi ɗin.. ★Bayan cikar awanni biyu da tafiyar Babiy sai gashi ya dawo, dawowa irin wadda ya saba a duk lokacin da makamancin kira irin wannan ya samesa daga daular Ruman. Yanda ya kafe Iffah da idanunsa dake zubda hawaye ya saka Ummu zubewa ƙasa cikin kuka. “Abu Hanash itama zamu rasata ko? Itama ka ɗaura mata aure da Tajwar.....?” Hawayene masu ɗumi da ƙuna suka ziraro a idanun Babiy, ya girgizama Ummu kansa a hankali alamar a'a, tare da girgiza kan nasa kuma alamar tayi shiru. Hawayen nata ta share kamar yanda ya buƙata, sai dai jikinta bai bar tsuma ba. Kamar yanda Iffah data kafesa da idanu bata iya ko ƙyaftawa ba. Ummu ta sake gyara zamanta da fuskantar Babiy da ƙyau.... “Idan ba abinda muke tunani bane to minene ya faru?”. “Ki kwantar da hankalinki babu komai f.....” “Bazan taɓa yarda babu komai ba. Sai dai idan kana so ka rufeni ne. Hakan kuma shine mafi ƙololuwar kuskuren da banajin zan iya yin afuwa gareka a kanshi. Dan inaji a jikina zuwanka masarauta nada nasaba da rayuwar yarinyata data rage min, idan har zuciyarka ta iya ɓoyewa ƙwayoyin idanunka basu lulluɓe komai ba, garama ka sanar min”. Babiy ya fahimci idon Ummu ya rufe ta manta Iffah na wajen, dan haka ya cigaba da ƙoƙarin ganin ya kufcema faɗar abinda yazo da shi har sai sun keɓe amma ta dage akan itafa ya faɗa mata a yanzu. So yake ya buɗe ido amma bashi da sauran ƙarfin zuciya a yanzu, dan haka a sanyaye ya rumtse idanunsa da launinsu yay matuƙar komawa ja. “Ba'a ɗaura mata aure da shi ba. Sai dai....” ya kasa ƙarasawa. “......Sai dai me? Dan ALLAH ka faɗa min”. Ummu ta faɗa tana mai sake fashe masa da kuka mai matuƙar sake ɗaga masa hankali. Miƙewa yay yunƙurin yi tai saurin riƙe masa ƙafa. Babiy ji yake shima kamar ya fashe da kuka ya huta kawai. Ya dawo ya durƙusa gaban Ummu tare da riƙo mata hannu, “Akan abinda suka faɗa munada mafita tunda yasha ban-ban dana baya Jumaima. Dan haka na gama yanke shawarar zamu bar garin nan dama ƙasar gaba ɗaya a daren yau insha ALLAH. Dan sun buƙaci izinin neman auren Iffah ne a gareni, sun kuma bani damar zuwa nai shawara daga nan har zuwa ƙarshen makon nan”. Kafin Ummu ta samu damar cewa wani abu sulalewa da faɗuwar Iffah a lokaci guda ta riski kunnuwansu. A tare suka zabura kanta jikunansu na matuƙar rawa da tsuma. Ummu ta fashe da kuka dai-dai tana ɗago Iffah dake wanwar a ƙasa taga ta koma yaraf alamar babu rai a tare da ita..... .....Sosai kukan Iffah ya sake ɗaga hankalin Babiy. Dan tunda aka zuba mata ruwa ta farfaɗo ta haɗe kai da gwiwa. Suma idanu kawai suka zuba mata suna hawayen zuci, rikicin yana a kantane kawai, amma sune suka fita jin raɗaɗin a zuciya saboda ita akwai ƙuruciya tare da ita. A ganinsu bai zama lallai ma tana hange irin wanda su suke matane ba. Kusan mintuna talatin suna a haka, kafin Babiy yay ƙarfin halin miƙewa suma yay musu umarnin su tashi su koma ciki. Sai da taimakon Ummu Iffah ta iya miƙewa, har sun kusa shiga ɗakin ta tsaya, ɗagowa tai ta dubi Ummu ta juya ta dubi Baby hawaye na sauka da gudu bisa ƙyaƙyƙyawar fuskarta. “Bazamu gudu ba Babiy, zan aure shi....” Kaɗan ya rage Babiy yaci uban tuntuɓe saboda firgitaccen furicin Iffah mai kamanceceniya da gawurtaciyar sautin saukar aradu cikin tsakkiyar duhuwar dare. Ummu ma dai da taima Iffah sakin bazata ƙirji ta dafe dukanin idanunta na firfitowa..... Iffah ta share hawayenta da sakin murmushi a karo na farko. “Ummu! Babiy! ku kwantar da hankalinku, kar kuma ku ɗauka ba'a cikin hayyacina nake ba. Nasan burinku shine ku kuɓutar dani daga mutuwa, sai dai kuma a duk inda zanje ku sani tana tare da nine. Wannan azzalumin ba guje masa ya kamata ayi ba, tunkararsa ya kamata ayi. Kamar yanda kaka ya faɗa, a wasu lokutan gujema ƙaddara ba mafita bace sake kirawowa kai halaka ne. Amma tunkararta gaba da gaba ƙarfafa imani ne sannan jarumtace. Shin idan mun gudu kunada tabbacin zamu iya tsere musu bayan ƙasar a hanunsu take? Sannan idan mun tafi ina zamuje bayan babu inda muka sani sama da ƙasar Ruman. Fir'auna ma da yay nasa zamanin mulkin da ko kama kafarsa wannan shaiɗanin baiyiba UBANGIJI maida ANNABI MUSA (A.S) yay cikin gidansa ya rayu bisa ƙudirarsa da tabbatar masa shine mai iko akan kowa da komai. Azzalumin nan ba gudun masa ya kamata ayi ba, daƙilesa ya kamata ayi, domin idan ni kun kuɓutar dani, su sauran iyayen da zasu iya fuskantar makamancin halin da kuke ciki fa bayanku?. Babiy zanyi biyayya kamar yanda ƴan uwana sukayi, kuma ku sani da iznin ALLAH nice zan kashes........” Cikin rawar jiki Ummu ta zaburo tare da toshe bakin Iffah. Sai faman waigen bayansu take domin sanin dakarun Daular Ruman na ƙofa gidan har su biyar. Babiy ma gaba ɗaya kalaman Iffah sun sake rikitashi. Sai dai kafin wani cikinsu ya samu damar cewa wani abu ta shige cikin ɗakin. Idanu suka tsirama juna shi da Ummu harna tsahon mintina biyu, kafin Babiy yay ƙarfin halin janyewa yana mai jan nannauyan numfashi da barin wajen ya shige ɗakinsa. Da ƙyar itama Ummu ta sauke numfashin, har zatabi bayan Iffah sai kuma ta fasa ta nufi ɗakin Babiy ɗin itama. Shigowarta dai-dai dayin sallamarsa waya manne a kunensa. Zaune takai a bakin gadon dake ɗakin dan inba haka ba zata iya zubewa ƙasa saboda yamutsawa da jininta ke mata. Jin sunan Baba da Babiy ya ambatane ya sata maida hankali garesa itama. Komai sai da Babiy ya zayyanema Kaka kafin yay shiru alanar saurarensa. Daga can Baba yaja nannauyan numfashi bayan gama sauraren surukin nasa mijin ƴarsa tilo data rage masa a raye. Sai kuma yay murmushin ƙarfin hali mai sautin daya isa har cikin kunnen Babiy. “Ni ma ina goyon bayan maganar Fareedatu. Da ace wani rai nada ikon hana tabbatuwar wasu daƙiƙu na gaban rayuwarsa masu tafe da ƙaddara da mutane da yawa sunyi rigakafi kafin cikar adadin waɗan nan daƙiƙu Muhammadu Zayyanu. Amma inaso ku tuna muɗin talakawansu ne, masu rayuwa a ƙarƙashin mulkinsu, bamu da wani ƙarfin iko akan hukuncinsu garemu ko kan ƴaƴanmu. Dan haka ku bita da addu'a kawai itama.” Tamkar yana gabansa ya jinjina masa kansa, tare da ƙoƙarin danne hawayen da yake na zuciya da ƙunarsu gara ace a zahiri suke zuba bisa ƙyaƙyƙyawar fuskarsa. “Shikenan Baba, amma furucin Iffah ya girgizani, ina tsoron kar zuciya ta ingizata tai yunƙurin aikatawa. Kisa fa! Koda bata aikata ba fitar wannan furucin zuwa kunen wani bayan mu ba ƙaramar magana bace” “Kar komai ya dameka Muhammad Zayyan. Ta faɗane kawai saboda raɗaɗi da takeji da kuma ƙuruciya, kai dai ka sanar dasu ka amsa daga nan zuwa kwanaki uku. Zan zo a amsa kuɗin auren da ni dama wasu a cikin zuri'an ka insha ALLAHU.........✍ ALLAH sarki Iffah kin bani tausayi🥲 *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 90165991 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_11_* ..........Iffah taci kuka matuƙa da ko maƙiyinta ya dubeta sai ya tausaya mata. Sai dai kuma iya juyawa su Babiy sun mata akan su gudu ta kafe akan itafa ta yarda zata aura *_Tajwar Eshaan ibn Haysam Abdull-Majeed_*. Sosai hankalinsu yake ƙara tashi da tirjewarta. Gashi gaba ɗaya ta bikice musu ko isashen lafiya babu a tare da ita. A cikin wannan halin Babiy ya sake samun saƙon kira daga masarauta. Yana shirin tafiya sai ga Kaka. Duk sunyi matuƙar mamakin zuwan nasa, dan abune mai wahalar gaske a garesa zuwa inba da wani dalili ba. Sun tarbesa kamar yanda suka saba matsayinsa na uba. Bayan gama gaisawa ya kai dubansa ga Iffah dake kwance cikin bargo duk ta rame ta sake komawa fayau da ita, dama tun rasa ƴan uwanta ɗan jikinta ya zube, dan sam ba siririya bace. Iffah nada jiki murjajje daba za'ace mata siririya ba kuma babu mai sakata a sahun masu ƙiba. Duk da shekarunta har yanzu sunada ƙaranci ALLAH ya bata jiki na manyan mata da'a yanzu komanta yake ciff dai-dai da halittarta. Kaka ya ɗauke idanunsa a hankali tare da maidasu ga Babiy. “Muhammadu Zayyanu ka sakama ranka nutsuwa ka cire batun barin gidan dan bashine mafita ba. Hasalima tun randa ka amsa kiran masarauta wannan gidan zagaye yake da dakarun daular ruman harta inda baka zata ba. Ko'a tunaninka zasu tunkareka da wannan maganar su baka damar kanka sannan su koma gefe da tunanin kai bazakayi wani yunƙuri ba”. Daga Babiy har Ummu da Hanash kallon tsoro da mamaki sukema Kaka. Ya ɗan jinjina kansa alamar tabbatarwa. “Karku damu da yanda akai nasan wannan, kai dai kawai kaje ga kiran da sukai maka. Karka kuma nuna wani ja'inja kace ka amince musu suzo neman auren”. Kuka Ummu ta fashe da shi tana kallon mahaifin nata. Yay ɗan murmushi da ɗauke kansa tamkar bai fahimci mitake nufi ba. Ganin haka Hanash da idanunsa sukai jajur cikin cinkushewar harshe yace, “Amma kaka miyasa ka zaɓa itama mu sake rasata? Wlhy nayi alƙawarin in har itama ta salwanta sai na salwantar da ran Shahan-shan da wannan hanun nawa wajen ɗaukar fansa koda nima za ai gunduwa gunduwa da naman jikina!!”. “Ba kai ne zaka salwantar da ruhinsa ba, ni nan Fareedah bint Zayyan nice zan karya ƙarfin ikon azzalumi da hannuna, zan masa shaƙa irin wadda har sai ya mutu yana mai kallon tsakkiyar cikin ƙwayar idanuna Hanash Akhi”. Su duka zuba mata idanu sukayi, dan a yanda take maganar babu alamar tana a cikin hayyacinta. Babiy zaiyi magana Kaka ya girgiza masa kai alamar kar yace komai yaje kawai.... ★Kamar yanda Kaka ya umarci Babiy ya amsa kiran masarauta kasancewar a wannan karon an bashi damar zuwa ne shi kaɗai batare da dakaru sun taho da shi ba. A yanda ya samu tarba zai tabbatar maka dama a jirace ake da zuwansa. Kamar ko yaushe a wannan karon ma baiga Tajwar ba, amma dai a karon farko na tarihin rayuwarsa an kaisa har cikin fadar Shahan-shan. Inda yaga tsantsar dukiya da ainahin karagar mulki ta Shahan-shan da akayita da zallar zinare. Hakan ba'abin mamaki bane ba, saboda girman Shahan-shan koda da diamonds akai kujerar mulkinsa bazai zama wani babban al'amari ba, sannan zinare arziƙin ƙasar su ta ruman ne da bare ma kanzo ya ci balle su ƴan ƙasa musamman Shahan-shan. Karo na farko da Babiy yaga karramawa daga dattijan daular ƙasar ruman. Waɗan da ko'a mafarki bai taɓa tunanin gani ba dan su ɗin ma ba'abune mai sauƙi ga duk wani talaka ganinsu ba kai tsaye haka. Duk da a birkicen da yake ALLAH sai ya saka masa nutsuwar yi musu bayani babu ko rawar harshe a tare da shi. Sun masa godiya da tabbacin a gobe idan ALLAH ya kaimu masu neman aure zasu zo. Karramawar da sukai masa ta matuƙar basa mamaki da tsayawa a ransa, sai dai ta wani gefe na zuciya ya tabbatar da sabuwar hanyar yaudarace kawai. Cikin danƙareriyar mota aka maidasa har gida badan yaso haka ba, yayi shiru ne kawai domin bin unarnin mahaifin matarsa, dan duk da bai taɓa ambatawa ba ga kowa ya jima da tsanar duk wani abu daya shafi masarautar daular ruman.. ★A wannan dare Babiy yayi zaman kuka irin wanda ake kira kuka a zahiri da baɗinin rayuwa. Har yanaji bazai iya cigaba da yima kaka biyayya ba shikam, zai ɗauke Iffah su gudu daga ruman koda daga shi sai ita ne. Sai dai wani ɓangare na zuciyarsa na tunatar da shi maganar Kaka, yasan gaskiya ya faɗa, dan daular ruman bazata zuba ido na barinsa sakakai ba. Ajiyayyun dakarun dake a ƙofar gidansa ma kawai tabbaci ne.... A ɓangaren Ummu ma bata runtsa ba, sai dai saɓanin Babiy ita kwana tai tsaye tana gayama UBANGIJI damuwarsu da roƙonsa kariya da kuɓuta ga yarinyarta. Shi kuwa Hanash kwana yay ƙulla ta yanda zai halaka Tajwar Eshaan ibn Haysam Abdul-majeed da kansa. Hakama Iffah nata shirin nada alaƙa dana Hanash. Ta gama yankema kanta koda zata mutu itama sai dai su mutu tare da Tajwar Eshaan. In yaso a binne gawarta a tsakiyyar ruman matsayin tarihin da za'a dinga tunawa....... *_WASHE GARI_* Washe gari data kasance safiyar laraba da misalin ƙarfe biyar na yamma sai ga manyan baƙi daga masarauta ruman. Baƙi masu ban mamaki, dan kuwa wasu manya ne a cikin dattijai masu faɗa aji a daular ruman. Sannan iyaye ga Shahan-shan ta ɓangaren jini makusanta sosai ga mahaifinsa. Tamburan masarauta da ɗunbin tawagar hadimai da jibga-jibgan motoci da suka ƙoshi ne suka tabbatarma da jama'ar anguwa dama maƙwaftan anguwar wace tawagace. Tuni mutane suka fara ƴar rige-rigen fitowa daga gidajensu bama idanunsu abinci. Sun tarbesu bisa jagoranci Kaka daya tsara komai tare da shimfiɗa kakkauran gargaɗi ga su Babiy. Bayan an musu masauki a cikin lambun Babiy ta ɓangaren garden ɗin da yayi domin farin ciki ga iyalansa aka cika musu gabansu da ƴaƴan itatuwa duk da babu tunanin ko zasu ci. Babiy, Kaka, da wasu dattijai biyu, ɗaya ta ɓangaren Babiy, ɗaya ta ɓangaren Ummu ɗan uwa ga kaka kenan suka zauna da su. Sun miƙa gaisuwa a garesu cikin mutuntawa da nuna tabbacin su ɗin masu ƙarfin iko ne a garesu talakawan ƙasan ruman. Hakan yayima dattijan matuƙar daɗi da yabama su Kaka. Dan haka suma suka nuna mutuntawa a garesu da basu ƙarfi matsayin waɗanda sukazo neman iri wajensu. Hakan ya ɗan bama su kaka mamaki amma sai babu wanda ya nuna. Sun gabatar da buƙatarsu, tare da bada duk wani abu na al'adar aure da ƙasar ruman ta tanada ninki wanda akanyi sau goma. Hakan sai ya ƙara firgita Babiy da bashi tabbacin yanda za'a salwantar da rayuwar ƴarsa ɗaya tilo data rage masa zai zama ƙololuwar girma fiye da ƴan uwanta kenan. To inbaice hakaba mizaice, dan dukiyar da suka kawo kawai tamafi ƙarfin ma sayen Iffah idan sayarwar zaiyi. Bai samu damar cewa wani abu ba, yadai cigaba da kukan zucinsa yabar su Kaka dayin abinda ya dace. A wannan zama aka ƙarƙare komai har ranar ɗaurin aure dama inda za'a ɗaura auren. Daga haka sukai addu'a suka tafi bayan an shigo da tarin kayayyakin da sukazo da shi. Daga Babiy har Ummu tagumi kawai sukai suna kallon kayan da aka baza a tsakar gida. Hakama Hanash da dattijan nan guda biyu da sai gobe zasu koma tare da kaka. Kaka kuwa na gefe zaune abinsa tamkar baima san mike faruwa ba a gidan. Yayinda Iffah ke can ƙuryar ɗakin Ummu kwance cikin zazzaɓi data yini da shi..... Washe gari su kaka suka wuce batare daya sake cewa uffan ga su Babiy ba akan komai. Yadai gargaɗi Babiy akan karya kuskura yace zai yi wani yunƙuri. Ya kuma sakasu killace dukkan kayan da aka kawo daga masarauta..... ★★★_______★ Tamkar da gayya cikin kanƙanin lokaci gari ya ɗauka Shahan-shan zai yi aure, alamu kuma sun nuna ana shiryama auren da shiri na musamman duk da amaryar bata kasance ƴar kowa ba. Hasalima ahalinta nada tabon Shahan-shan a dalilin salwantar ƴaƴansu biyu kafin ita. Dukkanin waɗan nan ƙananun magana na faruwane a bakunan mutane da ƙaramar murya, yayinda a kafafen ƴaɗa labarai da fejikan yaɗa zumunta babu mai iya ɗaga murya yayin faɗa sai fatan alkairi kawai. Mutane sun sake samun tabbacin wannan aure na musammne daya sha banban dana baya sakamakon fara shelarsa a kafafen yaɗa labarai domin gayyatar manya-manyan ƙasar kamar kowane Tajwar da jama'ar majalissarsa da talakawan garinsa. Da yanda ake wasu ƴan gyare-gyare a daular ruman wai duk na tarbar zuwan ranar ɗaurin aure ne. Humm abin faɗa taf bakunan mutane sai dai babu damar faɗar. Idan kuma suke ganin zasu sami wani ƙarin bayani an toshesa dan babu mai ikon shiga gidan Babiy a halin yanzu kasancewar zagaye yake da dakaru tako ina, acewarsu suna bama *_Zawjata-almilki_* tsaro ne. A cikin gidan kuma babu mai fita hatta da Hanash dake zuwa babbar makaranta... A haka kwanakin biki da suka rage suka cigaba da shurawa batare da wadda ake iƙirarin zama amaryar ta sake tada kai ta dubi wani abu daya shafi auren nata ba koda da kallo. Ta dake matuƙa tamkar ba itaba, hatta da ciwon dake cinta a tsaitsaye taki bada damar da su Ummu zasu fahimta. Ta ƙeƙashe idanunta ƙam ta hana hawaye zuba daga cikinsu. Ta tattare gaba ɗaya hankalinta ta maida ga rubuce-rubuce da babu wanda ya fahimci na minene a gidan, dan bata bari kowa ya duba mata shi. Sai dai ga duk mai hankali a duba ɗaya da zai mata zai fahimci tana cikin matsananciyar damuwa, mai busar da zuciyar mai ita da zai iya aikata komai da zai iya zama komai akan komai.. Kamar ko yaushe yau ma bayan ta kammala ayyukan gidan da take taimakawa Ummu da su ɗaki ta koma tana kukan zuci daya zame mata abokin rayuwa. A idaniyarta kam babu alamar ɗigon hawaye, sai dai raɗaɗin wanda ke kwaranya a zuciya ya maida launin idanunta sirkin ja har kana iya ganin jijiyoyi a cikinsa. Duƙufe take akan littafinta tanata rubutu da sakin ajiyar zuciya akai-akai. Ummu data shigo ɗakin takai zaune a kusa da ita tana mai tsurawa rubutun idanu na wasu sakanni. “Ibnati!”. Karan farko Iffah ta ɗago ta kalla Ummu duk da tun shigowarta ta jita sarai. Wani irin miskilin murmushi ta saki tare da maida kanta a hankali ta duƙar.. “Kina ganin laifinmu ko?”. Cak ta tsaya da rubutun data cigaba, sai kuma ta saki murmushi. Tsahon sakkani uku kafin ta ɗago ta dubi Ummu. Ta ɗan girgiza kanta da ajiye biron hanunta. “Ummuna idan har zanyi zargin wani akan wannan al'amarin to kaina ya dace na zarga. Ku ɗin nagartattun iyayene abin alfaharin kowane irin ɗa. Ni ya dace nazo muku da wannan maganar, domin nice na saka zukatanku a damuwa da ɗunbin fargaba. Na tabbata a kowane sakan, a kowane minti, a kowane awa, a kowane kwana na waɗan nan kwanakin kunayinsa ne cike da fargabar shuɗewarsu da gabatowar su. Kuyi haƙuri ku ƙara haƙuri ku gafarceni. Koda baku faɗamin ba, baku faɗama duniya ba nasan irin raɗaɗin da kukeji a zukatanku domin nima makamancinsa nakeji. Sai dai ina muku albishir Ummuna, koda zakuyi kuka a wannan gaɓar bazakuyi irin na baya ba. Na muku alƙawarin kukan ku zai kasance tare da dariyarkune a lokaci guda. Dan ruhina sai ya amso muku diyyar su Nina Arfa kafin yabar gangar jikina. A duk randa saƙon mutuwata zai riskeku insha ALLAHU zai riskekune tare da na mutuwar azzalumai. Dan haka ina roƙonku kar kuyi baƙin ciki a wannan karon, zaku sadaukar da ruhin da zaije muku yaƙin neman ƴancin kai ne ku da al'ummar ƙasar ruman.....” Kai Ummu ta shiga jujjuyawa hawaye na kwaranya a idanunta, “Ibnat...” “Na roƙeki kar kice komai Ummuna, albarkarki itace mafi ƙololuwar buƙata ga ruhin daya daɗe da zama cikin tahin gawa. Ƙaddarata rubutacciya ce tun daga alƙalamin da idan yay rubutu babu wani duster dake iya gogesa”...........✍ ALLAH sarki Iffah, ALLAH ya baki damar yaƙi irin wanda ya dace da fatanki na alkairi🙏🏻😭 *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 90165991 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_12_* .........Kalaman Iffah sun zama mafi ƙololuwar zama famin gyambo a zukatan Ummu da Babiy harma da Hanash. Sun zanu da zanen da zuciya ta killace koda tunasu zai zama mai raɗaɗi a cikinta. Sun karɓa domin karɓar ta zama tilas a garesu saboda rashin murya da ƙarfin iko da suka rasa a hannayensu. Sun cigaba da kuka saboda kukan shine kawai mafita a garesu. A haka kwanaki suka cigaba da tafiya da raunin zukatansu har zuwan ranar juma'ar da masu ƙarfin iko suka tsaida matsayin ranar ɗaurin auren ƴarsu. Bayyana ko misalta kasancewar wannan dare da wayewarsa ma ɓata lokacine game da halin da ahalin malam Zayyan suka tsinci kawunansu. Babu wani alamomin biki daga ɓangarensu sai ma zaman makoki. Dan bayan Iyyani da Kaka da wasu dattijai da basu gaza biyar ba a cikin zuri'arsu babu wanda ya halacci wannan makahon aure hatta da maƙwaftansu. Bisa tilastawar Kaka Babiy da Hanash sukai shirin halartar massallaci yin sallar juma'a da riskar abinda zuciyoyi ke tsananin ƙuna a kansa. Sun tafi sun bar Ummu da Iyyani da tazo itama a yanayi mai ban tausayi. Amarya Iffah kam idanunta ma babu wanda ya gani a wannan safiya abinci ma Iyyani ta bita da shi har ɗaki.... *_TAFARU TA ƘARE_* Bayan gushewar wasu awanni, masu tafiya da ƙarfin bugun zuciya busa irin ta sarakai da tashin tambura ya karaɗe cikin birnin Daular Ruman dake cike da manyan baƙi tako ina. Dan kuwa sarakuna goma cif na ƙasar Ruman duk sun halarta duk da suma akwai raɗaɗin rasa ƴaƴayensu a zukatansu har yanzu. Koda yake wasu a ciki sun bada ne da kwaɗayi na burin zamowar ƴaƴan nasu zama matan Shahanshan, suna ganin hakan wani ɗaukaka ce a garesu da samun wasu damammaki...... Iffah dake kwance a ɗaki zuciyarta a bushe, idanunta dake zubda hawaye a ɗazun a soye ta jiyo bayanin ɗaura aurenta da Tajwar Eshaan ibn Haysam Abdull-Majieed daga bakin su Kaka. Wani irin dimmm taji a cikin kunnuwanta tamkar ɗaukewar wutar lantarki daga tashar gidan redio, ta koma ita ba wadda ta suma ba, ba kuma wadda ke a raye ba tsabar tsintar kai a wani hali. Ta jima a haka kafin ta dawo hankalinta kwakwalwata ta fara tantance abinda taji ɗin. Kenan abinda ya faru da yan uwanta a wasu watanni da suka shuɗe itama shine ya faru da ita yau? Itama zata mutu mutuwar rashin gata da ƴanci a hanun azzalumin mai mulkin Ruman da jama'ar cikinta. Daga yau za'a koma ƙirga mintuna da daƙiƙun mutuwarta da suka rage mata, daga yau tayi bankwana da Ummu, da Babiy, da Hanash Akhi da su Kaka. Anya kuwa zata iya? Anya kuwa sadaukarwar nan ta dace da rubutattun burukanta? Anya kuwa zata iya jurewa? Kai ina bazai yuwu ba. (Mizai hanasa yuwuwa? Bayan zakije inda ko kuwwa kikai babu maijin muryarki?) wata zuciya acan gefe ta ayyana mata. A karo na farko hawaye masu zafi da raɗaɗi suka silalo bisa kumatunta da gudu. “Dole ma na jure, jurewa irin wadda a duk faɗin duniya labarina zai karaɗesa a lokacin dana hukunta Tajwar Eshaan ibn Haysam ibn Abdul-majeed”. Ta faɗa cike da ƙwarin gwiwa na tabbatar da burin mai ɗaukar fansa. Batare data goge hawayen dake cigaba da rige-rigen zubo mata ba ta sauka a gadon tana tangaɗin jiri. Wayar data maida ta ajiye da ƙudirin ta daina amfani da ita ta lalubo, haɗata tai ta kunna, sai dai tai ɗan jimm namai nazari kafin ta fara rubuta saƙo. Minti biyu bayan turawa kira ya shigo. Numfashi ta fesar, sai kuma ta saki murmushin takaici jin abinda aka faɗa daga can. “Sir bamu da lokacin tattauna wannan a yanzu”. “Na sani Fareedah, sai dai inajin matuƙar tsoro, tsoro irin wanda ko'a ido aka kalla an san tsoro ne. Nasan na rasaki na har abada a yanzu”. Murmushin takaici ya suɓuce ma fuskarta, sai dai ta hana hawayen da suka ciko mata ido zubowa. “Wannan shine tsoron dana gudar maka fuskanta tun farko dama duk jama'ar Ruman. Amma bazan gajiya ba, plan A dama yaƙin sunƙuru ne, plan B mafi haɗari amma da yaƙinin nasara”. “Ta yaya Fareedah? Kin san kuwa waye Shahanshan? Kin san minene girman ikonsa?.....” “Na sani mana tunda nima a ƙasar aka haifeni. Sannan na zama cikin ahalin da sukafi ɗanɗana ɗacin girman ikon nasa da zalunci. Karka damu da haɗari sir, taimako ɗaya zakamun a wannan plan ɗin wanda babu wani abu da zai shafeka da iznin ALLAH”. “Amma Fareed....” “Please sir”. Kakkauran numfashi yaja ya fesar cike da ƙarfin halin son danne rauninsa a gareta. “Okay ina jinki”. “Ka bani number abokinka”. “Fareedah mi kuma ya rage?”. “Abubuwa masu yawa da amfani, hasalima yanzu ne za'a fara wasan na gaskiya”. “Karki taurin kai”. “Na jima da zama mai busashiyar zuciya”. “Ki fahimceni”. “Ko kaina ma bana iya fahimta sir”. “Bana son na rasaki Fareedah”. “Iyayena sun jima da haƙurin rasa ni, kamar yanda na jima da sadaukar da kaina”. “Miyasa kike da taurin kai Fareedah”. “Shine izzata, ƙarfin gwiwa ta wajen tunkarar maƙiyi na”. Wani irin cije lips yayi daga can, hawayen da tun randa labarin auren wadda ya fara so yake kuma kan so yazo masa da wanda yafi ƙarfinsa suke kwaranya ya kasa sharesu suka shiga rige-rigen zubowa daga idanunsa, yasan ta ƙare kuma, abinda ya rage kawai ƙyautatama masoyiyarsa koda hakan zai kasance sadaukarwa ta ƙarshe da zaiyi a rayuwarsa. “Na barki lafiya, ki kasance cikin aminci da kariyar UBANGIJI”. Ya faɗa harshensa a sarƙe da yanke wayar a lokaci guda. Wasu irin zafafan hawaye ne suka shiga gudu a fuskar Iffah, bata san tana son Sir Fawzan ba sai a yanzu. A yanzun da kowa zai iya kiransa ƙurarren lokaci a rayuwarta. Zata cigaba da masa fatan alkairin samun madadinta koma wadda ta fita, jin kamar motsin ana tunkaro ɗakin yasata saurin kwanciya taja bargo har saman kanta.... ★★........ “Muhammad Zayyan!”. Kaka ya kira Babiy tamkar yana gabansa cikin matsanancin damuwa da firgici na zahiri dake kan fuskarsa. Ɗago kansa dake sunkuye yay a hankali shima tamkar yana a gaban Kakan. Hakan ya bayyana jajayen idanunsa da damuwa ta rinar. Sun rabu ne tun a wajen ɗaurin aure basu dawo nan gidan ba suka wuce Jumna. “Na'am Baba”. “Kayi haƙuri. Karku zama masu baƙin ciki kai da matarka. Ku zama masu juriya da karɓar ƙaddara rubutacciya daga UBANGIJI. Nasan akwai raɗaɗi, nima kuma makamancin irinsa nakeji a ƙirjina. Sai dai bazan gaji da faɗa maka *_Kibiyar ajali sulke baya tareta sai ta gitta ba_* kamar yanda babu wata duster data isa goge abinda alƙalamin ƙaddara ya rubuta. Mu mun wuce yanzu, dan mungama namu ku ya rage kuyi naku mu barma UBANGIJI sauran, dan dama duka nasa ne. Iyyani itace zata shiryata kafin isowarsu ɗaukarta, nau'in turaren da yake a cikin gidanka kawai nake buƙatar fitar ƙamshinsa daga jikinta. Ta kuma sha iya adadin madara datake gidanka kawai daga yanzun har zuwa wayewar gari. Ta kwana a ɗakin daba shi aka ajiyeta ba. Karta karɓa daga wanda zuciyarta tai rawa a kansa. Ta zama ƴar kallo a takun farko, ta zama kurma a shigar farko, ta zama mai rauni a tawagar farko, tasa a ranta kariyar UBANGIJI na tare da ita. Na barku lafiya”. Ummu ta juya ta kalla Babiy dake riƙe da wayar a hannu tamkar dasashen gunkin da akai ado dashi domin tunawa a tarihi. “Lafiya kuwa? Baba ma baida wata mafita ko? Shiyyasa yaƙi dawowa tanan ya wuce gida?”. Idanu ya cigaba da tsura mata tsahon wasu sakanni harta fara kuka, ya ciza leɓensa na ƙasa yana mai haɗiye abinda ya tokare masa maƙoshi. Gefenta ya kai zaune, tamkar mai bitar karatu ya shiga maimaita kalaman baba a zahiri _“Iyyani za ta shiryata kafin isowarsu ɗaukarta, nau'in turaren da yake a cikin gidanka kawai nake buƙatar fitar ƙamshinsa daga jikinta. Ta kuma sha iya adadin madara datake gidank.......”_ Kallonsa Ummu tai da share hawayenta a lokaci guda, cikin rashin fahimta tace, “Mi kake son faɗa?”. Kansa shima ya girgiza mata. “Ba dagani bane ba, Baba ne. Amma na kasa fahimtar komai Jamaima. Ko ke kin fahimta?”. Har zatace a'a sai kuma tai ɗan jimm idanunta masu girma da su Iffah suka gada a kansa. Itama maimaita kalaman tayi kamar yanda ya faɗa har sau uku, “Idanfa har na fahimta, Baba yana nufin _Iyyani ta shirya Iffah da kanata, idan sunzo da wani turare karmu bari tai amfani da shi, sannan ko taje can an bata wani abu kar taci......, Kaga kenan daga nan mu saka mata turaren, sannan mu bata abinci taci cikinta ya cika. Mu kuma......” Numfashi ya ja daga hancinsa a hankali ya saukar a ƙirjinsa, itama ta sauke numfashin mai haɗe da zubar hawaye sakamakon dakatar da ita da yay da hannu alamar ya fahimta ba sai ta ƙarasa ba. duk da bawai nauyin da zuciyarsa tayi ya ragu bane, ya dai samu sassauci daga kalaman Baba duk da basu san manufarsuba kai tsaye. Sai dai bin umarninsa a garesu tilas ne....... ★ Tsaf Iyyani ta shirya Iffah dake faman zubda hawaye har yanzu cikin shiga ta alfarma kamar yanda Kaka ya bada umarni. Wata haɗaɗɗiyar riga ce da akanga irinta kawai a jikin hamshaƙan matan gidan sarauta na ƙasar ruman mai kama da alƙyabba da ita kanta Iyyani bata taɓa sanin a kwaita a gidansu ba Kaka ya kawo yace a saka mata. Duk da shirine bana daɗin rai ba tayi ƙyau matuƙa. Ga wasu nau'in sirrika na ƙamshi na tashi daga jikinta har suna hawa kai. Tsaff Ummu da kanta ta shirya mata wasu abubuwa masu muhimmanci nata duk da sun san zama ne na taƙaitaccen lokaci ga ƴar tasu mace tilo data rage yanzu. Daga Babiy har Ummu zama sukai suna mata nasiha, nasihar kuma gaba ɗayanta tafi ƙarfine akan addu'a, ta kula da addininta, azkar, karatun alkur'ani kar tai sakaci da su. Babiy da kansa ya ɗakko wayar Fariha ya bata yace ta ɓoye kozasuna rinƙa jinta, baima san ta Arfa ma na hanunta ba. Isowar jama'ar daular ruman ta katse zaman nasu. Inda mayan matan da suka shigo gidan tare da rakkiyar tawagar hadimai suka buƙaci a basu amarya da ruwa mai ɗumi su shiryata. Kan Babiy a ƙasa ya basu amsa da “A shirye take domin cika umarninku”. Sosai mamaki ya bayyana a fuskokinsu dajin kalaman Babiy da kuma fitowar Iffah da Iyyani ta riƙo suka fito. Baki ɗaya daga cikinsu ta buɗe zatai magana wata ta girgiza mata kai alamar kartace komai. Badan taso ba tai shiru, sai dai ta juya ta fita tana mai danna wayar hanunta da alama wani take ƙoƙarin kira. Babiy da kansa ya kama hanun Iffah tare da akwatin kayanta ƙarami har ƙofar gida gaban motar da aka tabbatar masa itace ta ɗaukar amarya.. Da gayya Iffah tai gaba zata kifa suna gab da fita a soron kamar tayi tuntuɓe da rigar jikinta dake jan ƙasa. Da sauri hadimai mazan dake tare da su sukai mata runfa da bayansu dan kar wanda yaganta, dan kofar gidan dama cike yake da jama'a, cikin sauri ta gefenta mai sanye da baƙar abaya harda niƙaf tai ƙoƙarin yin kamar zata tarota suka duƙe tare, a hankali ta ɗan ɗago suka haɗa ido, matar dake ƙoƙarin taimaka mata ɗin tai saurin kautar da nata da sukai jajur tare da ɗaukar littafin da Iffah ta saki ƙasa yayin da take kaiwa sunkuye. Miƙewa matar tai, itama Iffah ta ɗauka envelope ɗin da matar ta saki ƙasa dai-dai Babiy na ɗagota. Da baya-baya Sir Fawzan da yay ɓaddabamin shigar mata cikin baƙar abaya da niƙab kamar hadiman masarauta ya dinga jan jikinsa cikin mutane ƴan kallo har ya sulale gaba ɗaya a wajen..... *_DAULAR RUMAN_* Wannan ne karo na farko da Iffah ta shigo cikin masarautar daular Ruman. Duk da a cikin mota suke kuma har yanzu hawaye basu daina zirara daga idaniyarta zuwa fiskarta ba hakan bai hanata tsarkake sunan UBANGIJI ba, yayin da motocin da suke a ciki suka gama keta katafaren gate ɗin farko zuwa cikin masarautar mai matuƙar girma da hasashe ko kintace bazai iya bayyanawa ba kai tsaye sai al'amarin ya sake girmama zuciyata........✍ Tabɗi jan🙆🏻 Ga aure dai ya ɗauru tsakanin Tajwar Eshaan Bin Haysam Abdull-Majeed. Da Fareedah Bint Zayyan. Shin itama zata mutunne kamar sauran matansa ko zata tsira? Wacece Uwa? Wacece Ta-ƙurya? Wanene shi kansa Tajwar Eshaan da ƴan ƙasar Ruman baki ɗaya kema kallon Fir'aunan wannan ƙarnin?. Miye dalilin mutuwar matan Tajwar? Shike kashesu? Ko akwai lauje cikin naɗi a kashesun?. amsoshinku duk suna a cikakken littafin nan na DAUƊAR GORA CIKI KA SHATA, dan cakwakiyarfa yanzune ma zata fara😉🤗. *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 90165991 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_13_* .........Ta ko'ina bayine masu hidima ga wannan basarakiyar daula. Yo basarakiya mana, dan itace masarauta dake mulkin ƴan ƙasa dama sarakunan ƙasar baki ɗaya. Sun sake wuce gate na biyu inda anan ɗin ma dai katafaren wajene da misaltasa babban aikine ga mai hasashe. Ta ko'ina hadimai ne ke kaiwa da komowa maza da mata. Ga wasu irin gine-gine na alfarma da ɗaukar hankalin mai kallo tamkar ba'a cikin ƙasar Ruman ba. dogayen gine-gine ne da abaya sai dai su hangosu daga nesa tamkar yanda suke iya kallon jirgi yayinda yake keta giza-gizai. Ga wasu irin korayen shukoki tako ina tare da shimfiɗaɗen lafiyayyen titi da za'a iya rantsewa yafi kowanne titi dake a cikin ƙasar Ruman. Kasancewarta farin shiga a ganin wannan shimfiɗaɗɗiyar daula saita fara tunanin anyama kuwa a duniyar mutane take? Kokuwa dai mafarki takeyi ne? Dan sam inda take yafi kama da anguwanin ƙasashen turawan da a tv ne kawai suke iya ganinsu cikin film ko labarai da makamantansu... Har motocin suka samu wajen tsayawa aka fito da ita sam ba'a hayyacinta take ba, bawai ƙawatuwa da tarin ƙyale-ƙyalen da aka zubane kawai ke ɗibar hankalinta ba, akwai wani ɓoyayyen tunani acan ƙasan ruhinta da ƙahon zuciyarta mai alaƙa da tabbatar da abinda mutane ke faɗa akan Daular Ruman ɗin...... Saukar sautin busar sarewa mai zaƙi da daɗin saurare da ya fara tashi a cikin daular Ruman ya sauka cikin kunnenta tare da katse tunaninta ya maidota hayyacinta. Wannan saƙone dake isa zuwa kunnen duk wanda ke a cikin masarautar cewar an iso da _Zawjata almilki_. Tsawon lokaci sautin na tashi har sai da saƙon ya isa ga kunen kowan da ake buƙata. Daga Iffah dai bata san ma'anarsa ba, dan haka bata ɗaukesa komai ba. Sai ma share hawayen fuskarta data cigaba dayi, dan har yanzu fuskar tata na lulluɓe ne da hular ƙawatacciyar rigar jikinta da zamu iya kira alƙyaba. Sai dai zuciyarta cike take da alwashi mai ban tsoro ga duk wanda zai iya jinsa a kunne. Ta sadaukar zata mutu, amma ba ita kaɗai ba harda Shahan-shan na Daular Ruman, idan an hanata damar bayyanama duniya a ƙwato musu ƴancinsu, sai ya mutu aga wanda zai cigaba da kashesu. A karan farko ta saki murmushi mai ƙayatarwa, irin murmushin data jima batayiba kuwa........ Babu wanda ta ɗaga kai ta ko kalla a cikinsu har suka gama bushe-bushen algaitunsu dana sarewa. Cikin girmamawa ɗaya daga cikin matan da suka ɗakkota ta matso gab da ita. “Ran Zawjata-almilki ya daɗe, nan shine sashen Malikat Bushirat. Mahaifiya ga Zakin wannan daula Shahan-shan, Uwa ga duk wani ɗan ƙasar ruman”. A karo na farko Iffah ta ɗan ɗago idanu ta dubeta kaɗan daga cikin alƙyabar, kanta a ƙasa yake ita a dole bazata iya ko haɗa ido da ita ba domin girmamawa. komai batace da ita ba, sai dai ta dubi katafaren ginin da ya tabbatar mata da maganar matar. Idanunta ta maida ta risinar kawai batare data nuna alamar tama jita ba. Abin mamaki bai nema tsaida bugawar zuciyar Iffah ba sai da suka shiga wannan katafaren gini, bayi sai zubewa suke akan gwiyawunsu tamkar wasu masu neman gafara ko kuma Tajwar Eshaan ɗinne da kansa. Zaman faɗa muku daula da dukiyar dake a wannan sashe ma ai ɓata lokacine, dan haka na baku damar ƙiyastama zukatanku kawai.... (Lol😉😋😆) ★Karan farko na tarihi, karan farko na rayuwa, yau ga Iffah gaban *_Malikat Busheerat_*. Mace ta biyu ga tsohon Tajwar Haysam ibn Abdull-Majeed. Mahaifiya ga Tajwar Eshaan ibn Haysam Abdill-Majeed Shahan-shan na wannan ƙarni. Hamshaƙiyar mace mai tsananin ƙyau tamkar itace ta zaɓama kanta ƙyaƙyƙyawar surar jikinta da zubin halittar ta. A kallo ɗaya da Iffah tai mata daga cikin hular alƙyabar jikinta ta kasa sake ɗaga idanu ta ƙara saboda kwarjininta. Ta tabbatar ta isa a kirata _Malikat_ (Sarauniya), Uwa ga fir'aunan sarki kuma. Kishingiɗe take a ɗaya daga ƙayatattun kujerun katafaren falon daya amsa sunansa daular duniya, wanda kafin isowarsu cikinsa sun wuce manyan faluka da suma suka amsa suna daular duniya bama ta ruman ba kawai. A gefe da gefenta wasu matanne cikin shiga ta alfarma suma har su huɗu, sai hadimai dake zagaye da ita kowanne da hidimar da yake a gareta cikin matsanancin taka tsan-tsan da kai. Dan ko wadda ke tare da ita suna shigowa zubewa ƙasa sukai jikinsu har tsuma yake yi, ita Iffah har tsoroma suka bata tare da mamaki mai girma na wannan ƙarfin iko. Iffah dai na tsaye har sai da ɗaya daga cikin matan nan dake tare da Malikat ta miƙe ta kamota ta zaunar ƙasa bisa lallausan carpet ɗin dake a falon saitin Malikat Bushirat da har yanzu tana a kishingiɗenta kuma ko sau ɗaya bata ɗago ta kalla kowaba tunda suka shigo. Kusan minti biyu falon yay tsitt babu wanda ya sake koda motsin kirki, sai ƙarar na'urar sanyi dake tashi kaɗan-kaɗan da wani ƙamshi na musamman. (To masu karatu inhar Malikat na'a haka, yaya shi kuma Tajwar ɗin zai kasance kenan akan izza da mulki?🤔.) Iffah da shirun ya isheta kaɗan ta ɗago idanunta ta cikin hula ta saci kallonsu. Sai taga su duka har Malikat ɗin ashe ita suka zubama idanu. Haka kawai tasha jinin jikinta, dan kallone bana a santa ba, kallone dake buƙatar nutsuwa kafin a bashi fassara. Kaɗan taja numfashin dake neman maƙale mata a maƙoshi da ƙara yin ƙasa da kanta hular ta sake rufe fuskarta ruff. A hankali, cikin son ɓoye rauninta da hawayen dake neman kwace mata ta furta “Barka da yamma ranki ya daɗe”. “Malikat ta amsa miki, tare da maraba a gareki”. Ɗaya daga cikin matan ta amsa a maimakon Malikat da har yanzu batako motsa daga kishingiɗar da tayi ba. Sai dai ta ɗago ƙyawawan idanunta farare tas ta sake zubasu akan Iffah, idanun ta juya a hankali ta dubi ɗaya daga cikin matan nan dai dake kusa da ita. “An gama ranki ya daɗe”. Matar ta faɗa da girmamawa alamar ta fahimci mi take nufi. Tsam ta miƙe zuwa inda Iffah take, ta kai hannayenta biyu ta kama hular alƙyabbar tai baya da ita, ƙyaƙyƙyawar fuskar Iffah datai jajur saboda kukan da tasha abinka da farar fata ta bayyana. Idanu Iffah ta rumtse sakamakon jin al'amarin a bazata, ga wani irin harbawa da ƙirjinta yayi har sai da ta ambaci (Hasbinallahu wa-ni'imal wakil) a zuciyarta sannan taji numfashinta da yay sama yay ƙasa a lokaci guda ya daidaita. Kaf hadiman ƙasa sukai da kansu, dan haramunne a garesu kallon fuskar *_Zawjata-almilki_* kai tsaye. Yayinda Malikat Bushirat ta motsa a karo na farko daga kishingiɗar da tai idanunta akan Iffah. Kusan kallon mintuna biyu tai mata kafin ta janye idanun cike da ƙasaitar masu isa, yatsun hanunta ta ɗan murza suka bada sautin (ɗass! Ɗass!!!) har sau biyu. Tamkar ƙiftawar ido hadimar dake tsaye riƙe da wani ƙasaitaccen bowl kalar gold da adon stones masu ɗaukar ido ta iso gaban Iffah da kanta ke ƙasa har yanzu tana ambaton ALLAH a zuciyarta ta zube tamkar mai neman gafara. Kanta a ƙasa alamar bazata iya kallon Iffah ba ta miƙa mata bowl ɗin hannu biyu bayan wata a cikin sauran hadiman ta matso da sauri ita kuma ta janye farin ƙyalle da aka yana a saman bowl ɗin tare da murfinsa, tatacciyar madara fara tas ta bayyana. Cikin rawar murya da tsantseni hadimar ta furta, “Ya Zawjata-almilki! Wannan madara ce mai daraja daga hannun Malikat domin nuna maraba da zuwa a gareki cikin DAULAR RUMAN”. Shiru Iffah bata da alamar motsawa, har hakan ya bama duk wanda ke gurin mamaki har Malikat Bushirat. Tsahon sakanni goma kafin ta ɗago. Manyan idanunta da sukaci kuka har suka gode ALLAH ta zubama bowl ɗin tare da hadimar dake gurfane a gabanta tamkar mai neman gafara. Kanta ta girgiza a hankali tare da sake maidashi ta risinar. Cikin motsa laɓɓanta a hankali tace, “Wannan karamci abin alfaharine a gareni da nuna tsantsar godiya ga Uwa gareni dama ƙasar Ruman baki ɗaya. Sai dai ina mai neman afuwar jinkirtamin shan wannan madara sakamakon azumtar wannan yini da nakeyi batare da nasan yau zata kasance rana mafi daraja da alfarma a gareni ba”. Kalaman Iffah da tasirinsu tamkar saƙar ƙudan zumace cikin kuttu a zukatan duk wani mai numfashi dake a wannan falo. A zahiri da baɗini kuma babu wanda mamaki bai bayyana akan fuskarsa ba, saboda abune da bai taɓa faruwaba a cikin daular ruman. Malikat Bushirat tai ƙyauta a jinkirta amsa tare da biyo jinkirin da sharhin da babu gargada akan harshen mai furtashi. Wannan abu yakai a kalla Iffah a sake kallonta dan ko ƴaƴan gidajen sarauta goma cif da aka kawo daular a irin matsayinta basu samu ƙwarin gwiwar ƙin shan irin wannan madara ba. Hasalima kowaccensu da rawar jiki take amsa ta shanye tas ta bada bowl ɗin tana mai gurfana a gaban Malikat domin yin godiya. Ba'a matsayi kuma kawai ba hatta a shekaru Iffah itace mafi ƙanƙanta a cikin Zawjata-almilki goma sha huɗu da aka kawo gidan. Ɗaya daga cikin matance ta zabura idanunta dake nuna ɓacin rai akan Iffah. Sai dai abin mamaki Malikat Bushirat da idanunta ke kan Iffah ko ƙyaftawa babu ta ɗaga mata hannu alamar ta zauna tare da sakin wani ƙasaitaccen murmushi. Nuni tai akan a rufe madarar. Ruf aka maidata yanda take hadimar ta miƙe daga gaban Iffah da tunda ta sake maida kanta ta rissinar bata ƙara ko motsawa ba. A karo na farko Malikat ta motsa laɓɓanta, cike da izza da ƙasaita irin ta manyan masu mulki. “A kaita masaukinta”. Ƙasaitacciyar muryarta ta ratsa zuciyar Iffah tare da girgiza gaɓɓanta cikin ikon harbawar jini. Sunan ALLAH ta ƙara tsarkakewa a zuciyarta dan tabbas Malikat ta cika Malikat ɗin babu tantama. Saboda muryar tata kanta barazanace ga duk mai yunƙurin kawoma girmanta wargi da saka tsantseni a zuciyar duk wani talaka dake a ƙarƙashin mulkinta. “Ki huta lafiya, cikin aminci da farin ciki”. Iffah ta faɗa cikin risinar da kanta alamar girmamawa lokacin da take miƙewa bisa taimakon ɗaya daga cikin matan nan. Yin hakan ya sake saka zukatansu a mamaki, ita kanta Malikat Bushirat da kallon ƙasan ido ta bisu har suka fice. A ƙasan ranta tana mai jin farin cikin samuwar Zawjata-almilki data dace da gudan jininta tilo kuma Shahan-shan na ƙasar Ruman gaba ɗaya. A ganinta lokacine daya dace tai yaƙi da maƙiyanta masu yaƙar Zakinta a yanzu dake zagaye da su..... ★★Kamar yanda Malikat Bushirat ta bada umarni amarya Iffah (Zawjata-almilki) an isa da ita sashenta dake gab da sashen matan Tajwar Eshaan su biyu da har yau suke raye, sannan kuma kusa da katafaren sashen Tajwar Eshaan da yafi kowanne gini ɗaukar hankali da kayan kyale-ƙyale da tsagwaren dukiya a cikin Daular Ruman harma da tsantsar tsaro... Sashen Iffah ya kasance shima sashe dake ɗauke da nau'in kayan more rayuwa da a kallo ɗaya mai karatu zai tabbatar da sai dai Zawjata-almilki ɗince kawai kam ta dace da zama a cikinsa. Kamar yanda al'adar take anyi rakkiyar Iffah dake kan keken doki tare da busar sarewa mai daɗin saurare har zuwa sashen nata. Iya masu hurumin shiga kawai suka shiga har cikin bedroom da suka kira matsayin master bedroom nata. Sai dai suna fita ta miƙe daga zaman ɗofanar da tai a gefen gadon, cikin ambaton sunan ALLAH da zubar hawaye ta jaye hular alƙyabar ta ta ƙarema ɗakin kallo na tsahon mintuna uku. Komai batace ba ta ɗauka akwatinta da aka shigo da shi ta fito a ɗakin tare da jawo ƙofar. Bata wani tsaya kallon falon data fito ba, sai dai tabi kowace kusurwa na cikinsa domin lissafa adadin ƙofofin dake a cikin. Ƙofar da lissafinta ya tabbatar mata ta nufa, cikin ɗan jimami da tausayin kai ta murɗa ƙofar mai kalar ruwan gold. Ɗakin ta shiga bayan ta leƙa kanta cikinsa. Shima ɗin dai a ƙayace yake da komai na alfarma. Sai dai komai nasa ya banbanta da kalar na wancan ɗakin. Amma shima duk abinda ke cikinsa royal ne irin kayan da suka dace da gidan hamshaƙan masarautu kamar Daular Ruman. Ajiyar zuciya ta sauke bata samun nutsuwa ba, sai ta son rage nauyi mai danƙarewa a ƙirji kawai har numfashi ya gaza samun damar fita yanda ake buƙata. Jikkar ta ajiye tare da zama bakin gadon ta rushe da sabon kuka.........✍ _To ko burin Malikat Bushirat zai cika kuwa? Kokuwa dai itama Iffah zata suɓucema ƙwarin gwiwar tata tamkar Zawjata-almilki na baya da suka shuɗe ta hanyar kisan da har yanzu ba'a san wanene sanadinsa ba?. Idan Shahan-shan ne da kansa yaya Malikat zata kasance a wannan yaƙin kenan? Dan masu iya magana kance fa DAUƊAR GORA CIKI KA SHATA.._ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 90165991 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_14_* .........Wannan dare darene na tarihin da har abadan Iffah bazata taɓa mantawa da shi ba. Badan wani abu ya faru bayan wanda ya faruba, wanda ya farunne bazai taɓa zama shiɗaɗɗe a zuciyarta ba. Kwana ɗaya tak ta kasance cikin ɗimuwa da tsananin kewar ahalinta. Wanda ta riga ta gama sallamawa ta rabu dasu kenan har gaban abada. Sai dai bayan mutuwarta suzo jana'izarta batare da ko kan gawarta an barsu matsawa ba. Sam babu wani barci koda ɓarawo da yaci galabar ɗaukarta a wannan dare. Hakama abincin da aka biyo bayanta da shi na buɗa bakin azumin da tace batacisa ba. Kuka taci ta ƙoshi har kusan rabawar dare kafin ta miƙe zuwa bayi tayo alwala ta nutsu gaba ɗayanta gaban UBANGIJIN talikai maji roƙon bayinsa. Duk da tsananin tsoro da take a ciki na kasancewa ita kaɗai a katafaren sashen haka ta dinga jarumtar son dannewa a zahiri. Sai dai duk ƙanƙantar motsi yakan saka zuciyarta harbawa da tunanin anzo kashetane. Tana idar da sallar asubahi barci yafa ce ya shirya, dan duk yanda take faman turesa da son ƙin yinsa sai da yakaita ƙasa, dole takai kwance kan lafiyayyen kafet ɗin dake gaban gadon kafin ƙiftawar ido ta fara sauke numfashi.... Barci sosai Iffah tasha na tsahon lokaci mai tsayi da har sai da aka tadata ta fahimci hakan. Ƙyawawan idanunta dake cike da barci ta buɗe da ƙyar akan matar dake tsaye a gabanta kanta a rissine. Babbar mace ce mai shekaru sosai, sai dai shigarta ta tabbatar da cewa ita ɗin bakomai bace sai hadima a masarautar. Amma kuma da alama hadima ce mai babban muƙami da matsayi.... “Barka da safiya ya Zawjata-almilki”. Ta katse tunanin Iffah ta hanyar gaisheta. Yunƙurawa tai ta tashi zaune idonta na a kanta, kanta ta gyaɗa da faɗin, “Mama ina kwana”. Dan shekarun girma na matar ya wuce ta zauna saita gaisheta. Sosai ta ga ruɗewa da kiɗima a idanun matar. Cikin yin waige-waige na tsoron kar wani yaji ta zube ƙasa da rawar harshe. “Ranki ya daɗe na roƙeki dan ALLAH wannan sunan yabar fita a bakinki. Kece uwa a garemu, ke kika cancanta mu kira da sunan bani ƙasƙantacciyar baiwa mai miki hidima ba. Sunana shine Diwa, zaki iya kiran Ama (baiwa), ni shugabar hadimai masu kula da tsaftar sashen Malikat ce. An kawo miki abin karin kumallone tare da wanda zasu shiryaki da hadiman da zasu kasance masu hidima a gareki”. Idanu kawai Iffah ta tsura mata cike da tausayawa. Sai dai komai bata iya cewa ba ta kauda idanunta zuciyarta na ƙuna na raɗaɗin ƙasƙancin da su talakawan ruman ke fuskanta a ƙarƙashin waɗannan masarautu. Hadima Diwa miƙewa tai da sauri ta fita. Mintuna kaɗan sai gata ta dawo tare da wasu mata guda biyu. “Ranki ya daɗe, waɗannan matan sune zasu shiryaki a yanzu”. Yanzun ma iyakarta ɗago ido ta kallesu kawai, sai dai batayi musu ba wajen basu damar fara aikinsu. Amma a zuciyarta ta cigaba da yin addu'a sakamakon harbawa da ƙirjinta keyi da sauri-sauri tamkar mai tsoron tunkarar wani abu. Tsaf suka kwance kitson dake kanta, dogon gashinta da mafi yawan ƴan ƙasar ta Ruman keda ya bayyana. “ALLAH ya ƙara miƙi tsahon rai da lafiya, wannan lokacine na wanka”. Komai Iffah batace musu ba ta miƙe, dan tanabin huɗubar Kaka ne daki-daki. Da zata shiga bayi dakatar da su tai daga ƙoƙarin binta da suke. Hadima Diwa dake gurfane gefe tai saurin faɗin, “Ranki ya daɗe ki basu dama dan ALLAH, dan zasu nuna miki yanda zaki amfani da kayan wankan da aka shirya dominki a ciki, su kuma gyara miki kai kawai su fito”. “Karki damu zanyi da kaina”. Ta faɗa tana mai shigewa kafin ma ta sake cewa wani abu, sai dai bakinta ɗauke yake da addu'a. Wani irin harbawa zuciyarta tayi, tareda sarawar kai lokacin da take sanya ƙafa cikin toilet ɗin sai kace ba dashi tai amfani ba da asubahi, yanzu kuma da su Diwa suka shikago sun gyarasa da ajiye kayan wankan da suka shigo da shi tare da matan, hannu takai saman kanta tana karanto addu'a bayan ta shiga toilet da tayi sannan ta ƙarasa shiga. Shi kansa bayin abin kallone a yanzu fiye da ɗazun, dan yanzu an ƙawatashine da wasu irin fure da candles ta gefen jakuzzie ɗin. Sai wasu nau'inkan ruwan turare da aka ajiye domin tai amfani da shi, sam zuciyarta taƙi aminta da hakan, atake ta dinga ɗaga tasoshin da suke a ciki tana maidasu gefe guda ta hau wankanta tana mai zubda hawayen tausayin kanta dana iyayenta da batasan halin da suke ba a yanzun suma.... Koda ta fito da tunanin samun matan data bari sai taci karo da akasin haka. Domin kuwa wayam ɗakin babu kowa, sai ƙamshi mai daɗi na turaren wuta da aka ajiye ke tashi. Numfashi ta sauke a hankali, badan samun nutsuwa na abinda ke gudana ba. Sai dan samun sassaucin nauyin da zuciyarta tai mata. Kusan mintuna biyar da fitowarta ta gagara tsinana komai, hasalima bata san ta ina zata fara ba. Knocking ƙofar da neman izinin shigowa ya sakata ɗaga idanunta manya takai dubanta, kafin ta bada izinin shigowa tana mai janye idanun nata. Hadima Diwa ta shigo sallama kanta a ƙasa, tun'a bakin ƙofa ta zube bisa gwiyawunta. Cike da tsantseni irin na tsakanin yaro da uban gidansa murya cike da rauni tace, “Ya Zawjata-almilki! Yanzu lokacine na shiryawarki da taimakon waɗan nan mata”. Ta ƙare maganar da nuna bayanta. Iffah dake saurarenta tare da zuba mata ido kallonta ta kai bayan nata, kamar zatai magana sai kuma ta fasa. Tai ɗan shiru na wasu sakanni tamkar mai tunani kafin taja numfashi. “Ai zan iya shirya kaina su barshi kawai”. Ƙasa Diwa ta sake yi da kanta da sake gurfana ƙasa sosai. “Ki gafarceni ya Zawjata-almilki. An basu umarnine, saɓawa kuma a garesu tamkar bijirewa ne?”. Tsantsar tausayinsu da takaici mai gimtse maƙoshi ya sake baibaye Iffah, ta nisa tare da haɗiye abinda ya tokare ƙirjinta tana mai jin-jina kai wa hadima Diwa kawai. Tamkar ƙyaftawar ido matan suka shigo su biyu. Suma dai kallonsu kawai Iffah take cike da tausaya wa. dan cike da girmamawa a gareta suka zube gwiyawunsu a ƙasa domin gaisuwa a gareta kasancewar bana ɗazun bane. “Dan ALLAH ku miƙe”. Ta faɗa cikin wani irin yanayi daya saka matan ɗan ɗagowa suka dubeta. Su ɗin ababen tausayine, amma sai sukaji itace suke tausayi fiye da kansu. Umarninta sukabi duk suka miƙe ɗin, suna maiji da kallonta da matuƙar girma a idanunsu duk da ƙanƙantar ta, dan kuwa itace mafi ƙarancin girma a cikin Zawjata-almilki da aka kawo daular ruman. Sun mata shiri irin na Zawjata-almilki data isa a kirata da wannan sunan. Dan ƙwalliyar tata ta dace da halittar ƙyaƙyƙyawar surar jikinta da ƙyawunta. Ta cancanci a kirata Malikat Fareedah bayan Zawjata-almilki duk da ƙanƙantar shekarunta. Saboda duk da damuwar dake shimfiɗe a ƙyaƙyƙyawar fuskarta hakan bai hana bayyanar fitar kwalliyar ƙawata kwarjininta da cikar haiba ba. Su kansu hadiman dake zagaye da ita sai faman satar kallonta suke. Bawai dan tafi duk sauran Zawjata-almilki da suka shuɗe ƙyawu ba, kawai natan ya matuƙar ƙayatar dasu ne batare da sun san dalili ba. Ita a karan kanta kallon kanta take dajin tamkar ba ita ɗin bace, bawai dan ƙyale-ƙyalen gold da diamonds da aka ƙawata adon jikin nata da shi ba. Hasalima sune abu na farko da takejin tsantsenin gani a jikinta. Hadima Diwa data sake neman izinin shigowa ta shigo a gabanta ta sake zubewa tana mai satar kallonta itama. Cikin jinjina girma irin na UBANGIJI mai halittar abinda yaso a yanda yaso ta isar da saƙonta kamar haka.... “Ya Zawjata-almilki! Yanzu shine lokacin karin kumallonki”. Iffah da takurar ta fara gundurarta ta saurin tarar numfashinta, “Bana buƙatar cin komai nikam Mama”. Tamkar hadima Diwa zatai kuka, muryarta har rawa take wajen faɗin, “Ki gafarceni ranki ya daɗe. Wannan suna bai dace da niba, jinsa a harshenki zai tabbatar da hukunci mai tsanani a gareni. Hakama rashin cin abincinki a yanzu”. (Ya rabba). Iffah ta ambata a zuciyarta cike da takaici dajin sake tsanar Tajwar Eshaan dama duk mai faɗa aji na masarautar. Bata sake magana ba ta miƙe suka fito da hadima Diwa. Dan matan da suka mata kwalliya tuni sun fice su. Babu kowa a ƙaramin falon da Diwa tai mata jagora, inda aka shirya abinci kala-kala kai kace su goma zasu cisa. Ita a rantama tunani tai ko tare da Tajwar Eshaan ɗinne ma. Sai da taga har takai zaune Diwa na ƙoƙarin fara haɗa mata abincin ta tabbatar domin ita kawai akayi kenan. Komai batace ba, har Diwa ta gama buɗe abincin duka alamar taga wanda take buƙata kenan. Komai kallo ɗaya tai masa ta ɗauke kanta, da ga ƙarshe ta nuna mata dafaffiyar madara kaɗai. Diwa tai jimm kamar mai tunani, sai kuma ta saci kallon Iffah ɗin tai saurin maida kanta ƙasa. Iffah da duk ke kallonta ta ƙasan ido ta cigaba da nazarinta harta kammala zuba mata madarar. Gabanta tazo ta ajiye, harta yunƙura zata miƙe ta dakatar da ita. “Bani zan sha ba ai mama naki ne”. A wani irin matuƙar hargitse Diwa ta ɗago tana duban ta, jikinta har wani karkarwa yake. “R....ran...ki ya daɗe w...w..wan nan ai ba hurumina bane”. Iffah data kafeta da idanu ko ƙyaftawa batayi ta janyesu a hankali tana mai miƙewa abinta batare da tace komai ba. Da sauri Diwa ta ƙara gurfana a gabanta tana hurwa. “Ranki ya daɗe dan ALLAH karkice bazakici komai ba, dan komai anan umarnine”. Bata zauna ɗin ba, ba kuma tace komai ba. Sai ma ɗakin da suka fito data nufa zuciyarta cike da nauyi. Batafi zaman mintuna biyarba wasu mata da batako musu kallo biyu ba suka iso da wata hamshaƙiyar riga mai kamar alƙyabba daga Malikat. Tare da umarnin tafiya da ita. Batai musu ba, dan a nata tunanin Malikat Bushirat suke nufi, sai dai zuciyarta ta kasa nutsuwa. Addu'a ta shiga ambato a zuciyarta har suka kammala saka mata ƙawatacciyar rigar alƙyabar mai tsananin ado da ɗaukar idanu, zasu kunna mata turaren wuta da suka shigo da shi a burner tai saurin dakatar da su. Kallon juna sukai, kafin ɗaya tai saurin faɗin cikin ƙanƙan da kai, “Ya Zawjata-almilki wannan umarnine daga Malikat”. Yamutsa fuska Iffah tai tana mai kallonta, kallo irin na wannan bata san wacece autar Babiy ba ta ɗauke kai. A karon farko tun shigowarta gidan tai magana da harshen ƙarfin zuciya ta ajiye rauninta a gefe. “Ni kuma wannan umarnina ne bana buƙata. Sai kumuje umarni na gaba”. Babu wanda a cikinsu baiji yayi sumar wucin gadi ba. Sai dai wani irin kwarjininta da jin shakkarta ya gama ɗarsuwa a zukatansu lokaci guda.. Iffah dake jin jininta na wani irin tsitstsinkewa ta sake dubansu da niyyar magana, tamkar wadda aka jefa da narkakken ƙarfe taji yafff! A ƙirjinta. Da sauri ta dafe ƙirjin tana mai rumtse idanunta. Rawar da jikinta ya farayi ya sata zubewa ƙasa tana mai ƙoƙarin ambaton sunan ALLAH, amma hakan ya gagara, dan tamkar an naɗe zuciyartane da harshenta a lokaci guda...... Har rige-rigen fita hadiman nan sukeyi jikinsu na matuƙar rawa. Diwa dake zaune a falo tana jiran fitowarsu ta miƙe da sauri tana tambayar lafiya? Babu wanda ya saurareta a cikinsu suka fice. Hankalintane ya tashi, tai kamar zata bisu sai kuma ta fasa ta nufi ɗakin da Iffah take. Wani irin mugun bugawa ƙirjinta yay damm. Innalillahi..... ta shiga ambata dayin kan Iffah dake ta faman juye-juye a ƙasa, cikin ƙanƙanin lokaci ta jiƙe sharkaf da zufa tamkar an watsa mata ruwa koma an tsamota a ciki. Harta kusa kai hannu kanta sai kuma taja baya da sauri cikin tsoro. Ina bai kamataba, matsayinta na hadima hanunta ya taɓa Zawjata-almilki. A daburce tai waje da nufin isar da saƙo ga Malikat Bushirat duk da bata da tabbacin samun iso cikin sauƙi........✍ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 90165991 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_16_* ........Cikin ƙanƙanin lokaci labarin abinda ke faruwa da Zawjata-almilki ta uku ya gama gauraye daular ruman. A take ko'ina yay tsit sai ƙus-ƙus da maganar ido kawai. Sauran Zawjata-almilki kuwa guda biyu dake gidan dama kafin kawo Iffah tuni sun sake shiga tsantsar tashin hankalin da yafi wanda suke ciki. Su dai dama rayuwa suke cikin jiran tsammanin isowar mutuwarsu. Ko lokacin da aka sanar musu sake ɗaura auren Tajwar da wata matar tsantsar tausayin kansune kawai ya baibayesu, yanzu kam jin halin da matar da aka kawo jiya take ciki ya tabbatar musu suma mutuwarsu tunkarosu take sakeyi kenan....... Duk wata tuhumar data dace akan hadima Jaza da sauran hadimai biyu da sukaje ɗakin Iffah suma da aka gano anyi amma sunƙi faɗar gaskiyar wanda ya sakasu, sai cewa suke Diwa ce. Yayinda Diwa ke rantsuwa da ALLAH tana kuka akan ƙarya suke mata ita bata san komai ba. Iya jigatuwa sun jigatu har takai numfashi da ƙyar sukeyi saboda azabartawar da ake musu. Sanin rayuwarsu akafi buƙata a yanzu sama da mutuwarsu yasa hadiman kurkukun dake a cikin daular ruman tsagaita musu. Amintaccen hadimin Malikat Bushirat ya koma ya sanar mata halin da ake ciki. Shiru kamar bazatace komaiba. Sai kuma ta dubi Jasrah da har yanzu ke tare da ita ta ɗauke kanta. Jasrah data fahimci mi ƴar uwar tata ke nufi takai dubanta ga hadimin. “Ghazi! A cigaba da tsaurara musu tsaro har zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu”. “ALLAH ya ƙara miki lafiya an gama”. Ya faɗa da tsantsar girmamawa yana mai rissinawa da gyara takobin hanunsa ya fice....... *_ZAWJATA-ALMILKI_* Tun Iffah na iya motsa jikinta da furta kalmar bakinta har hakan ya gagara numfashinta ya fara neman barin jikinta. Ga dai masu magani mata rufe a kanta mazan na daga waje suna haɗo duk abinda ya dace amma babu alamar wani canji sai ma ƙwaɓewa da komai ke nemanyi. Tun ana ƙirga awannin iya shawo kan matsalar har komai ya fara firgita kowa. Daular ruman tayi tsitt babu mai ƙwaƙwaran motsi a cikinta. Sautin fitar kiran salla ma dan ya zama dolene. Koda aka idar da salla ma sake komawa zaman jigum-jigum akayi domin kuwa abinda bai taɓa faruwa a tarihin masarautar bane ya faru. Tajwar Eshaan bai fito sallar zuhur ba yau. Hakama da la'asar. Magrib ma ta shiga babu wanda yaji motsinsa. Zuwa lokacin kuma akan Iffah an zubama sarautar ALLAH idone wadda ta girma ta ɗaukaka. Dan kuwa tana a shimfiɗene jiki duk ya ɗashe tamkar wadda ta ƙone gurin yay ja kafin ya tashi. Kaɗan-kaɗan numfashinta ke fita wanda shine kawai ya tabbatar da tana a raye bata mutu ba. Masu magani kowa yayi iya iyawarsa sun koma gefe ana jiran ikon ALLAH kuma. Ana idar da sallar la'asar Malikat Bushirat ta bada izinin maida Iffah sashenta..... Kamar yanda Malikat Bushirat ta bada umarni an maida Iffah sashenta, a kuma cikin ɗakin barcinta da babu wani mahaluki daya taɓa shiga bayan Tajwar Eshaan da Jasrah. Hakan ya bama dukkan hadiman sashen mamaki da tabbatar da lallai wannan Zawjata-almilki ɗin tana da wata daraja ta musamman ga Malikat. Dan kaf Zawjata-almilki da suka rasa rayuwukansu a gidan babu wanda ya iya ganin makamancin damuwar Malikat Bushirat irin ta yau. Ƙarin tabbaci har hawaye sai da ta share na tsagwaron tausayin Iffah. Lallai halin da Iffah ke ciki ta cancanci duk mai imani ya zubda mata hawaye, dan sauran Zawjata-almilki na baya mutuwarsu kawai akeji bayan kaisu turakarsa. Amma ita ko kaitanma ba'ayiba, a kwana ɗaya tak da tai a gidan batare da an kammala gagarumin taron bikin da aka shirya ba dominta gata a halin da gara mutuwa da shi... Bayan idar da sallar isha'i Malikat Bushirat na hakimce a katafaren falonta na uku Malikat Ashwaq ta iso da tawagar hadimanta duba Iffah. Malikat Ashwaq itace mace ta farko ga marigayi Tajwar Haysam ibn Abdull-majeed. Hamshaƙiyar mace ce data isa take kuma amsa suna Malikat. A ƙa'idar Daular ruman matar data haifi yarima mai jiran gado a cikin matan sarkice kawai ake kira da Malikat. Mafi yawanci kuma ana samu ne daga matan farko. Sai dai ga Tajwar Haysam hakan bata faru ba. Dan matarsa ta farko Ameera Ashwaq bata taɓa haihuwa ba kamar sauran matansa, tadai taɓa ɓarin ciki na wata huɗu daga shi kuma bata ƙara ba. A zahiri mace ce isashiya mai baza mulkin da yafi na kowace mace a gidan bayan malikat Bushirat, amma kuma bata da damuwa sam. Ƙaryarka kace ga wani mugun halinta na zahiri saboda tasan kanta. Rana ɗaya aka ɗaura aurenta dana Malikat Bushirat matsayin Zawjata-almilki. Amma itace uwargida. Duk da mulkinta Malikat Bushirat ta fita, ta kuma fita zafi da nuna kishi a zahiri dan sam ita bata da haƙuri, hakan yasa ake matuƙar jin tsoronta fiye da kowace Zawjata-almilki, dan Malikat Bushirat ba kanwar lasa bace ƙwarai da gaske, sai dai mace ce mai son ƙyautatama wanda yay mata da na ƙasa da ita, hakan ya taimaka mata samun soyayyar hadiman gidan. Haihuwar Miran (Yarima) mai jiran gado Eshaan tasa dole sunan Malikat ya koma kan Malikat Bushirat. Wato Sarauniya Bushirat kenan. Amma duk da haka sai Mahaifiyar Tajwar Haysam mai suna Malikat Haseena ta bada umarnin cigaba da kiran Ashwaq da suna Malikat Ashwaq. Hakan ya ƙona ran Malikat Bushirat, sai dai babu yanda zatayi. Amma ta sake tsananta kishin da takema Malikat Ashwaq ɗin fiye da da, yayinda ita kuma Malikat Ashwaq ke nuna tamkar babu komai a zahiri, amma a baɗini hummm.... Koda ta shigo Malikat Bushirat bata nuna tasan da shigowar tata ba. Sai dai ta ɗagama hadimanta yatsu biyu da ya sakasu rige-rigen fara barin falon. Zaune Malikat Ashwaq takai bisa ɗaya daga cikin kujerun falon tanama nata hadiman nuni dasu fita suma. Da sauri suma duk suka fice aka barsu su biyu kawai. A hankali Malikat Ashwaq ta ɗan sakin murmushi daya danne zafin yarfin da Malikat Bushirat ɗin tai mata, ita ta fara gaisheta da tambayar ya mai jiki?. A daƙile Malikat Bishirat da tai kamar zata basar ta amsa mata cike da isa. Nanma Malikat Ashwaq dai murmushi kawai tayi da haɗiye ɓacin ranta. Sosai ta nuna tausayi akan Iffah ta kuma mata doguwar addu'a da bada shawarar mizai hana a kira likita ma ya duba ta ko wani abune daban da wanda ake tunani. Karan farko Malikat Bushirat ta ɗakko manyan idanunta tai mata kallon tsakkiyar ido. Cikin yamutsa fuska taja numfashi da fesarwa, “Haihuwar magajin Daular ruman daga tsatson Malikat Bushirat rubutacciyar ƙaddara ce da duk yaƙi da gwagwarmayar masu son daƙile hakan. A baya basuci nasara ba, Taya suke tunanin samunta a yanzu kan _Saifulmulk_ ɗi na?. Kamar yanda aka haifesa daga matsayin gudan jinin Shahan-shan, Tajwar Haysam ibn Abdul-majeed. Shima haka za'a samar da Ɗa daga gudan jininsa da izinin UBANGIJI masu lissafi su fara...” Muƙutt Malikat Ashwaq ta haɗiye yawun dake neman kufce mata, a zahiri kuwa murmushi ta saki da ɗan girgiza kanta. Batare da tace komai ba tai yunƙurin miƙewa domin barin ɗakin tana mai ƙoƙarin danne zuciyarta dake yunƙurowa. Har tayi taku biyu sai kuma ta tsaya, batare data juyi ba ta saki murmushi. “Idan dai har Eshaan ya kasance gudan jinin Shahan-shan ne babu gauraye, muma irin wannan fatanne a bakunanmu garesa kasancewarmu uwaye a wajensa. Fatan alkairi da samuwar lafiya ga Zawjata-almilki.....” Har tsakkiyar kai kalaman ƙarshe na Malikat Ashwaq suka daki zuciyar Malikat Bushirat, sai dai kafin ta samu wani damar fassarasu sallamar Ameera Danish-Ara da suka kusan kiciɓus da Malikat Ashwaq ya dakatar da ita. Itace mata ta uku ga Tajwar Haysam. itama da tata tawagar hadiman. Kallon juna sukai da Malikat Ashwaq, Ameera Danish-Ara ta saki wani malalacin murmushi a kaikaice. Sai kuma ta matso cikin girmamawa ta gaishe da Malikat Ashwaq ɗin datai mata kallo guda ta ɗauke kanta. Amsa mata tai cike da ƙasaita, kafin ta matsa ta bata hanya ta shige, itama ta fice tawagarta biye da ita. Saɓanin Malikat Ashwaq ita ta samu tarba daga malikat Bushirat. Dan duk da take mata itama ga Tajwar kuma Malikat Bushirat kishiya a gareta hakan bai hanata risinawa ta gaidata ba da matuƙar girmamawa tana mai tambayar jikin Iffah. Malikat Bushirat dake kishingiɗe har yanzu a yanda Malikat Ashwaq ta barta ta amsa mata da sassauci mai haɗe da jimami. Cike da makirci Ameera Danish-Ara ke nuna tsantsar tausayin Iffah tana mai yin ALLAH wadai ga duk mai hannu akan waɗan nan al'amura. Malikat Bushirat taɗan jinjina kai irin na ƙasaitattun mata da yamutsa fuska kaɗan, a saman lips ta furta, “Nagode”. A kaikaice Amera Danish-Ara ta ɗan saƙi murmushi tare da harararta ta ƙasan ido. A zahiri kuwa zamanta ta gyara tare da risinar da kanta. “Wannan abunda ya shafemune ai gaba ɗaya ranki ya daɗe. Domin Zaki ɗammu ne, fatammu dai ALLAH ya warware waɗannan al'amura cikin sauƙi”. Har cikin zuciya Malikat Bushirat taji daɗin kalaman Amera Danish-Ara, dan haka a lips ta amsa da “amin” tana mai sauke ajiyar zuciya, dan bata cika samun damuwa da ita a gidanba tunma sunada ƙuruciya. Amera Danish-Ara mace ce mai tsananin kissa da ba lallai a lokaci guda ka iya gano wacece ita ba. Duk da kasancewar ita Zawjata-almilki ce a daular ruman zakasha mamakin irin girman da take bama Malikat Ashwaq da Malikat Bushirat a gidan a zahiri tunda ta shigo. Kai hatta da Amera Haifah dake amarya kuma ƙarama a cikinsu ita bata taɓa bari saɓani ya shiga tsakaninsu ba a zahiri. Wannan halin nata yasa sanda surukarsu Malikat Haseena ke da lafiyar ƙafa take sonta da janta a jiki fiye da su Malikat Bushirat. Wani lokacin har kwatance take musu da halin Amera Danish-Ara ɗin wai suyi koyi ta fisu dattako. A yanzu haka da take zaune babu lafiyar ƙafa Ameera Danish-Ara ɗin tafi kowa sintirin zuwa dubata da mata hidima a zahirance, duk da itama Malikat Bushirat na kamantawa sai dai babu ruwanta da sai wani ya gani yace tayi. Shiru falon ya ɗauka na wasu mintuna, Amera Danish-Ara na son taga Iffah babu fuska ga Malikat Bushirat, dole ta miƙe cikin ƴan kame-kame tana tambayar ko Amera Haifah tazo kuwa?. Kallon ƙasan ido Malikat Bushirat tai mata tana ƙara tsuke fuska, dan ita duk yanda take da zafi babu wanda zaice ga ranar data zauna maganar wani a cikinsu koda da su Jasrah ne kuwa. A ganinta idan tai hakan sunma isa kenan a wajenta. Murmushin yaƙe Amera Danish-Ara tayi cike da basarwa. Sai dai ƙasƙantaccen kallon da Malikat Bushirat tai mata ya matuƙar sokar mata zuciya. Taɗan risina da faɗin, “Na barki lafiya ranki ya daɗe”. Kai kawai Malikat Bushirat ta jinjina mata batare data ko ɗago ba. Amera Danish-Ara ta cije baki da ficewa hadimanta dake jiranta daga falo na biyu suka take mata baya. Sam Amera Danish-Ara bata gaban Malikat Bushirat, kalaman Malikat Ashwaq ne keta faman mata kaikawo a zuciya musamman na ƙarshe. (Fatan alkairi da samuwar lafiya ga Zawjata-almilki) waɗan kalamai bakwai a cikin tarin kalaman Malikat Ashwaq sunfi komi tsayawa Malikat Bushirat a zuciya. Dan kuwa tana fassarasu ne da wani abu daban ne. Haka manyan mutanen masarautar suka cigaba da shigowa duba Iffah daga sassa daban-daban na gidan. wasu iyaye ne, wasu yayu, wasu ƴaƴa harma da kakanni maza da mata duk da basu samun damar shiga ciki iyakarsu wajen Malikat Bushirat. Bata damu kanta ba sai da dare yaja. Koda hadimanta suka dawo sallamarsu tai dan tafi buƙatar kaɗaici a yanzu saboda son ƙara tunani akan kalaman Malikat Ashwaq da suka gagara haɗiyuwa a gareta. Da kuma nazartar kowa daya shigo sashen nata domin duba Iffah. Tun tana a zaune har takai ta miƙe tsaye hannayenta goye da bayanta tana faman kaikawo tamkar mai safa da marwa..........✍ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 90165991 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_17_* ...........Dare yayi nisa, bakajin motsin kowa a daular ruman sai sassanyar iskar dake kaɗa bishiyoyi kaɗan-kaɗan. Sai kuma Hadiman da ake kira Ghazi a masarautar ne kawai ke faman kaikawo domin bada tsaro ta kowacce kusurwa ta gidan musamman a sashen Tajwar Eshaan. Iffah dake kwance samɓal a katafaran gadon alfarma na Malikat Bushirat idanunta a rufe kai kace batama numfashine ta fara zabura a hankali kamar wadda ake mintsini. Jasrah ce kawai tare da ita a ɗakin, tana daga gefe barci ya ɗan figeta mai cike da wani irin mummunan mafarki. Wata gigitacciyar ƙara da Iffah ta fassa tare da girgizar data saka gadon shima rinƙa girgizawa yasa Jasrah farkawa a kiɗime. Tsalle tai gefe jikinta na rawa ganin yanda Iffah da gadon ke girgiza, hatta shi kansa ɗakin ji Jasrah keyi na mata rawa shida fitulun da suka haskesa, dan sai daukewa suke suna kawowa. Wani irin tari Iffah ta farayi mai tahowa da aman jini ta baka ta hancinta harda ta kunne. Jasrah ta fara ƙwala kiran sunan Malikat Bushirat a matuƙar firgice tana sake manne jikinta da bango hanunta na laluben ƙofa amma ta kasa buɗeta... Malikat Bushirat da dama ba barci take ba saboda tsabar damuwa ta buɗe idanunta a hankali jin sautin muryar Jasrah tamkar a sararin samaniya tana yawo. Cigaba da jin sautin ya sata miƙewa zaune ta sauka a gadon baki ɗaya. Babu wani hadimi dake da damar shigowa sashen ɗakunan barcinta sai masu gyarawa kawai suma da safe ne, hakan ya sata ɗora abaya kawai a saman kayan barcinta ta fito.... Jasrah da ta gama fita hayyacinta gaba ɗaya ta faɗa jikin Malikat Bushirat, rungume ƴar uwar tata tayi, a hankali ta shiga hura mata iska a kunne tana bubbuga bayanta. Jasrah da ƴar nutsuwa ta fara zuwa mata tai lamo tana sauke numfarfashi a jajjere, sai kuma ta ɗago a hankali hawaye wanke da fuskarta... “Mike faruwa?”. Malikat ta faɗa a hankali. Ɗakin Jasrah tabi da kallo, kafin ta fara mata bayanin komai har yanzu hawayenta sun kasa tsayawa. Sosai hankalin Malikat ya ƙara tashi, sai dai kamewarta yasa ba lallai ka fahimta a kan fuskarta ba. Cikin takunta na ƙasaita ta isa gaban gadon inda Iffah take. Kwance take samɓal tamkar ba itace ta gama buge-buge ba yanzun. Idanu ta tsura mata a karan farko, yarinya ce ƙarama sosai kuma ƙyaƙyƙyawa matuƙa, duk da halin ciwo da take ciki da canjawar fatar jikinta ƙyawunta da kwarjininta basu gushe ba, tausayinta mai tsanani da ƙaunarta suka sake ratsa zuciyarta. Zaune ta kai gefen gadon ta kai hannu ta shafa yalwataccen gashin Iffah daya gama bajewa a kan filon. “Ibnati kiyi haƙuri zaki samu lafiya bazasu taɓa samun galaba ba kinji”. Iffah da sarai take jin maganar Malikat dan ba barci take ba azaba ce kawai ke ratsata tai murmushin ƙarfin hali a zuciyarta, a karan farko taji ƙaunar matar a ranta da sake ganin kima da girmanta....... ★★_______★★ “Sun jiƙa mana aiki! Sun ɓata mana shiri! Ya ƙwace mana damarmu wadda sake samun samuwarta a garemu cikin sauƙi haka zata iya zame mana mai wahala!!”. Kakkausar muryar Uwa mai matuƙar rashin daɗin saurare ta fara karaɗe ɗakin cikin amon sauti mai tashi sama. A firgice ta miƙe a zabure tare da zube gwuyawunta ƙasa jikinta na tsuma dan dama zaune take ido biyu tana jiran tsammani. “A gafarce ni uwa ba laifina bane, ni kaina ina cikin damuwar tangarɗar da aka samu”. “Bana buƙatar jin komai daga gareki Taƙurya. Domin sakacinki ne ya jawo hakan. Nasha faɗa miki ki san suwa zaki bama aikin da ke bazaki iya yinsa kai tsaye ba. Su kuma waɗan can sakarkarun barinsu sukai wayewar gari tamkar rasa sauran damar data rage miki ne....” Ɗan zabura tayi da nufin cewa wani abu, sai dai tamkar walƙiya Uwa ta ɓace a ɗakin. Hakan na nufin ranta a ɓace yake. Itama kanta ta dafe nata ran na suya da ƙara girmamar baƙin cikinta. Miyasa kowa bai bata matsala ba sai wannan ƴar shilar yarinyar da bata wuce sauron gidanta ba da feshi ɗaya take kawar da shi. Zuciyarta ta fara raya mata Uwa kodai tsoron yarinyar nan takeyi, yo inba tsoro ba taya zata dinga wani gewaye-gewaye bayan bai wuce da ƙyaftawar ido kawai ta shafe babin rayuwarta ba. Dama mutum na gagarar aljani ne banda ta fara maidata susu...... WASHE GARI.. Duk wanda ya kwana ya tashi a masarauta a yau ya tashi ne da tashin hankalin da yafi na jiya sakamakon mawuyacin yanayin da Iffah ta wayi gari. Dole tun gabatowar sallar asuba aka maidata cikin clinic ɗin dake a masarautar saboda ɓallewar jini ta kowane sashe na jikinta. Da farko aman jini ta fara, sai kuma ta hancinta, sai gashi ta ido da kunne harda ma ramin cibiyarta. Hankalin Jasrah da Malikat dake tare da ita ya kai matuƙar ƙololuwar tashi. Duk da kowa yasan ciwo ne bana asibiti ba haka likitoci suka rufu a kanta domin ƙoƙarin ganin sun tsaida jinin amma abu na neman gagara. Har kusan goma na safe a gogon ƙasar babu wani cigaba, jikin Iffah ma ya fara saki alamar jininta yayi ƙasa matuƙa.... ★★... “Bari-Hamshira! Inaga ya kamata a bama masu maganin dake waje dama suma suzo su gwada sa'arsu tunda ba'a dace dana cikin masarauta ba.” Malikat da damuwar duniya ta tattaro a kanta yau ko fadarta bata iya fitaba tana cikin ɗakin barcinta har zuwa yanzu ta ɗago idanunta dake jajur ta sauke akan ƙanwarta ta uku mai suna Zaimah, cikin nuna sallamawa ta jinjina kanta. “Wannan ma shawara ce mai ƙyau Akia, ruɗewa tasa sam wannan tunanin bai zomin ba. A sanar da Ghazi su faɗama Baba Yaro. Sai dai komai ya kasance cikin sirri da amana dan kar maƙiyanmu suyi amfani da wannan damar wajen ruguza ɗan sauran ƙwarin gwiwar mu akan wannan yarinya”. Kai Zaimah ta jinjina mata, sai kuma ta miƙe da hanzari domin isar da umarnin..... *_ƘAUYEN JUMNA_* Tafiya saurayin yake tamkar zai tashi sama dan gaggawa, wani lokacin har tuntuɓe yakanci sai dai kafin ya kai ƙasa yay azamar taro kansa ta hanyar dafe duk abinda ke kusa da shi. Wurjanjan ya isa ƙofar gidan Dattijon da kowa yafi sani da suna Abu Huzaifah ya kwaɗa sallama da iya ƙarfin muryarsa har sau huɗu babu ko jiran a amsa masa. Dattijo Abu Huzaifah Da mukafi sani da Kaka ya dakata da ga ɗinkin kwalliyar doki daya duƙufa yi ya dago suka kalla juna da Iyyani dake shara a tsakar gidan. “Kamarfa sallama naji Abu Jamaima a ƙofar gidan nan” Kafaɗa yaɗan rausayar gefe da ajiye zungureriyar allurar da yake ɗinkin da ita. Kafin ya ce wani abu aka ƙara zungura sallamar a jajjere tamkar yaƙi. Kansa ya ƙara jijjigawa ya miƙe dajan tsaki. “Kai wasu dai mutanen sam basu da lissafi, irin wannan ai saka ɗauka tashin hankali ne”. Kaka ya faɗa cikin mita yana gyara takalmansa. Iyyani da takaici ya ƙulle itama ta bisa da kallo harya fice a soron gidan... “Ayyub! dama kai ne kake ƙwaɗa irin wannan sallama haka? Lafiya dai ko?”. “Da sauƙi dai Baba, amma amin afuwa bani da wani zaɓi bayan hakan. Saƙone daga Baba yaro”. Ya ƙare maganar da miƙama Kaka takardar hanunsa. Kaka ya amsa takardar yana ɗan juyata, sai kuma ya nuna hanyar shiga da faɗin, “Kaga shigo daga ciki”. A tare suka shiga cikin gidan, Kaka ya buɗe takarda yana dubawa, yayinda Iyyani ta kawoma baƙo dake gaisheta ruwa. Kaka ya ɗan murmusa bayan gama karanta takarda tare da girgiza kansa. “Ayyub naga saƙo, sai dai kuma inaga basai naje da kaina ba. Zan baka saƙo ka kai masa nima. Ita kuma ALLAH ya bata lafiya yasa ya zama kaffara a gareta”. Ɗan jimm Ayyub yayi, sai dai kafin yace wani abu Kaka ya miƙe. Ɗakinsa ya shiga, kusan mintuna ashirin sai gashi ya fito da wata jakkar fata. “Kayi maza ka kai masa wannan. Kace kuma ina gaishesa”. Cike da girmamawa Ayyub ya amsa da faɗin “Angama Baba. A huta lafiya”. Kai kawai Kaka ya jinjina masa yana murmushi. Sai da ya rakasa har ƙofar gida sannan ya dawo. Iyyani da duk ta shiga damuwa ko zama baiyiba ta jeho masa tambaya, dan tasan ma'anar wannan murmushin nasa bana farin ciki bane, yakan yisane a lokacin da wani abu ke masa ƙuna a zuciya. “Itama sun taɓata ko?”. Bai bata amsa ba sai da ya zauna. Ya jawo allurarsa zai cigaba da ɗinkinsa. “Dama ai bazasu barta haka ba saboda wasu dalilai”. “Dalilai kuma? Nami to?”. “Kinga sarkin tambaya bani zaren cen dana manta kan bunu”. Iyyani tasan tambayarce baya son amsa mata, dan haka taja bakinta tai shiru bayan ta kawo masa zaren. Sai dai sam zuciyarta babu nutsuwa...... ★★.MASARAUTA.★★ Bayan sallar azhar Ayyub ya iso masarauta. Zuwa yanzun har an fara raɗe raɗin mutuwar Iffah, duk da kuwa ya tadda masu maganin da suka isa suka tumbatsa da matuƙar yawa an tarasu kowa nata gwada ƙoƙarinsa da baiwar da ALLAH ya basa. Baba Yayaroya furzar da nannauyan numfashi bayan ya amshi saƙon kaka a hanun Ayyub “Dama nasan da wuya Dattijo ya zo”. “Amma duk da haka ka aika masa Baba?”. “Ya cancanci a aika masan”. “To amma miyasa yaƙi zuwa? Bayan kuma alamu sun nuna kai tsaye ma yasan abinda ke faruwa anan ɗin”. Baba ya tsurama ɗan nasa ido na wasu sakanni, sai kuma ya girgiza kansa. “Ba lallai sani irin wanda kake tunani yayi ba. Dan nidai nasan baida wata alaƙa da abinda ke faruwa anan. Sai dai ya sani ta dalilin baiwar da ALLAH ya masa duk da shi yana gudunta ne”. “Amma Baba....” “Kaga Ayyub wannan ba lokacin tambayoyi bane. Bara naje muga ko za'a dace anan.” Da kallo Ayyub yabi mahaifin nasa. Sai dai ƙasan ransa fal tambayoyine da yasan samun amsarsu zaiyi wuya a lokacin da yake buƙata. Yasan mahaifinsa gawurtaccen masanin magani ne irin na gargajiya dama na gusar da junnu. Shahararsa tasa Daular Ruman ɗaukarsa da bashi matsayin (Mai magani a gonar yaro) amma ya rasa minene dalilinsa na bama wancan dattijon girma mai tsanani duk da shi kowa bai sanshi ba sai da sunan mai ɗinka kayan doki..... *_ZAWJATA-ALMILKI_* Zuwa yanzu numfashin Iffah ma yana fitane da taimakon na'urori, yayinda jinin dake fita a jikinta har yanzu yake fita ta kunenta. Na ido da hanci da baki ne kawai likitoci suka samu nasarar tsaidawa. Baba yaro shine shugaba na masu maganin, dan haka ake basa damar shiga kai maganin da duk aka bayar dan ai mata amma da taimakon Jasrah kai tsaye. Yanzu ɗinma dai hakance ta kasance. Bayan neman iso aka bashi iznin shiga inda Iffah take, sai dai babu mai iya ganinta kasancewar zagaye take da glass..... *_SHAHAN-SHAN_* Bani kaɗai ba, nasan duk masu karatu tambayarsu zata rinjayane akan wai shin duk abin nan dake faruwa ina _Shahan-shan_ yake ne a matsayinsa na shugaba ga ƙasar ruman baki ɗaya bama daular ruman ba?. To amsar itace yana nan a cikin masarautar, sai dai kuma tun a yammacin jiya bayan dawowa daga sallar juma'a babu wanda ya sakejin motsinsa. Duk da dama fitarsa a zahiri ta zuwa massallaci ce kawai. Yana kuma da ƙofar dake kaisa har massallaci daga sashensa batare daya fito wani ya gansa kai tsaye a masarautar ba. Shiyyasa har zuwa yanzu wanda suka san fuskarsa ko'a cikin masarautar ma ƙalilanne musamman a cikin hadimai. Duk abinda ke faruwa a masarautar kuma kowa nada yaƙinin ya sani, sai dai ba'an miyasa ya zaɓi yin shiru ba. Kamar jiya yau ma labari yajema Malikat Bushirat akan Shahan-shan bai fito sallaba har ta asubahi. A yanzu kam hankalinta ya tashi ba kamar a jiya ba data ɗauka dan yana fushi da auren da yaso bijiremawa ne. A take ta bada umarnin shirya mata zama da shi. Dan ita a karan kanta na uwa garesa bata da hurumin ganinsa a duk sanda taso ko kai tsaye bisa doka da al'adar masarauta da ƙarfin iko na Shahan-shan. Sai zuwa ɗaya tak na kowanne wata da yakanyi kawai na zahiri. Amma duk da haka Tajwar Eshaan kan saci jiki wani lokacin ya kawo mata ziyarar tsakkiyar dare cikin ɓadda kama batare da wani ya taɓa fahimtaba har yanzu a cikin masarautar. Shiri ta farayi duk da batada tabbacin samun damar ganin nasa a yanzu, sai dai sanin duk ƴan majalissar fada na'a masarautar yau yasa bata fidda tsammani ba. Cikin sa'a kuwa cikin abinda baifi mintuna ashirin ba Ghazi ya zo ya isar mata da sakon ƙarɓuwar buƙatarta. Dan dama suma ƴan majalisar fadan nada buƙatar samun wanda zai duba shi, hakan kuma bamai yuwuwa bane dan ita dake amsa suna mahaifiyarsa da Malikat Haseena (Kakarsa) da matansa ne kawai ke da wannan hurumin saboda an tabbatar tun jiya baiko zo falo na uku ba. Sannan duk abincin da mai dafa masa ya shirya tun daga kan na daren jiya har safiyar yau da rana haka yake zuwa ya kwashesa ba'a taɓa ba. Cikin shiri na alfarma da rakkiyar tawagar hadimai maza da mata Malikat Bushirat ta doshi sashen Tajwar Eshaan ibn Haysam Abdull-majeed.........✍ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 90165991 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_18_* ..........Tuni labari ya kai kunnuwan sauran matan gidan musamman Malikat Ashwaq da Ameera Danish-Ara da Ameera Haifah cewar Malikat Bushirat ta ziyarci Shahan-shan saboda rashin jin motsinsa. Hakama wasu a cikin matan manyan masu faɗa aji a gidan harma da mazan, wasu iyaye, wasu ƴaƴa, wasu jikoki. Hakan yasa aka kafa gungu-gungu na cigaba da tattaunawa tare da sukar cewar yasan tsiyar daya aikata ai shiyyasa ya ɓoye kansa. Kokuma dodon tsafin nasa ne ya bashi wannan umarnin naƙin fitowa har sai yarinyar mutane ta mutu... Wasu kuwa murmushine kawai nasu dan su kaɗai suka san kansu. Yayinda wasu ke tausayama Tajwar Eshaan ɗin da ganin abubuwa ne suka masa zafi da yawa dan suna kallon komai a matsayin makirci da mafi yawa akafi dangantashi da matan ubansa, da kuma ƴan uwan mahaifin nasa na jini masu zawarcin son hawa wannan kujera... (To koma dai miye ALLAHU shine mafi sani). Duk inda ta gitta hadimai zubewa suke akan gwuyawunsu suna miƙa gaisuwa. Ko sau ɗaya bata ɗaga ido ta kalla kowa ba, sai hadimanta ne ke amsawa duk wanda yay gaisuwar. Tun'a harabar shiga sashen dukkanin hadimanta suka dakata. Sashen Shahan-shan shine mafi ƙyawu da ƙawatuwa na ƙyale-ƙyale a daular ruman. Gini ne da kusan zamuce an yisa da zallar gilashi. Yanada hawa huɗu dan haka sai da lifter. Zaman lissafin dukiya da daular da aka zuba a cikinsa da kuma ainahin fadar da Shahan-shan ke zaman fadanci ma ɓata lokacine. A lokuta da dama duk abinda ke faruwa a cikin masarauta Tajwar na kallo daga cikin sashensa musamman idan a hawa na ƙarshe yake, hatta da wajen masarauta yana iya hangowa. Hadiman dake tsaron sashen matsayin sojoji suka maye gurbinsu wajen take mata baya har falon farko. Anan ɗin ma hadiman zubewa suka dingayi ƙasa kawunansu a risine domin girmamawa a gareta har zuwa falon farko. Wanda suka rakota ciki suka dakata, na falon farkon dake a hawa na ɗaya suka take mata baya har zuwa falo na biyu a hawa na biyu, suma iyakarsu nan, wanda suke a falo na biyu sukai mata rakkiya har zuwa falo na uku dake a hawa na uku. Anan soja ɗaya ne, shine amintacce da yake iya haurawa har zuwa falo na huɗu hawa na huɗu a falon dake can. Anan ma akwai hadimi ƙwara ɗaya sai masu dafa masa abinci su biyu suma. Sune amintattun na ƙarshe dake iya zuwa hawa na can ƙarshe na huɗu kenan, suke iya ganin Tajwar kai tsaye kuma, suke iya sanin a wane ɗaki ya kwana, suke iya shiga ɗakin barcinsa suyi gyara ko kai abinda yake buƙata, ko isar da wani saƙo. Bayan gaisuwa a gareta Ghazi ya nema afuwa da bashi damar zuwa nema mata iso ga Tajwar. Hannu kawai ta iya ɗaga masa. Mintuna da basu wuce huɗu da shigar tasa ba ya dawo ya zube a gabanta. “ALLAH ya ƙara miki lafiya da tsahon rai mai amfani, shugaba ya bada damar shiga dake har ciki”. Shiru tai kamar bazata motsa ba, dan a duk sanda ta kama zasu gana anan sashensa yakan fito ne su haɗu a wannan falon ko ƙaramin falon hutawarsa dake a hawa na uku. Wannan kuwa a ƙa'ida ko matarsa bata shigarsa, dan haka jin wannan amasa yasata fahimtar akwai matsalar da gaske. Bayan buɗe mata ƙofa Ghazi yaja da baya. Cikin takunta na ƙasaita da isa ta ƙarasa shiga cikin matsakaicin falon mai fidda wani irin ƙamshi da wadataccen sanyin na'urar ac. Rashin girman falon ba komai bane, haɗuwarsa da tsaruwarsa ce mafi ɗaukar hankalin mai kallo. Dan an ƙawatashine da wasu irin tausasan tumtum na ainahin sarakan asali, dardumar falon kanta abin kallo ce, komai ya tsaru dai-dai da tsaruwar manyan mutane. A hankali takai zaune tana mai sauke ajiyar zuciya, sosai takejin matuƙar kewar gudan jinin nata, sai dai tsarin masarautar tasu ya tilasta mata haƙura akan dole tamkar kowace uwa ta Tajwar irinta da akai a cikin wannan daula.... Motsin buɗe ƙofa da ƙamshin turarensa mai rige-rigen isowa hancinta da sautin takumsa ya sata ɗago ƙyawawan idanunta ta sauke a kansa. A hankali ya cigaba da takowa cikin ƙasaita da nutsuwa har ya ƙaraso gareta. Daga tsayen da yake ya ɗan risinar da kansa alamar girmamawa. “Amincin ALLAH ya tabbata a gareki *_Ammie!_*”. Nutsatstsiyar muryarsa mai zurfi da rashin hayaniya ta fita a fisge, dan yanda ya motsa lips ɗinsa a hankali zama ka iya ɗauka bashi yay maganar ba. A hankali ta sauke ajiyar zuciya mai haɗe da nannauyan numfashi ta jinjina kanta da lumshe idanunta ta buɗe a kansa alamar amsawa. A nutse ya kai zaune a gefenta, yay zama irin na ƙasaita da kame kai da kuma girmamawa a gareta matsayin mahaifiya. Hanunta ta ɗaura bisa tattausar sumar dake kansa kwance, tare da ɗan ranƙwafawa ta sumbaci goshinsa da yay zafi zau alamar baida lafiya. Lumsassun idanunsa da ƙanƙancewarsu ya hanata ganin hasken cikinsu ya buɗe, ya motsa lips ɗinsa kaɗan alamar murmushi a gareta. Murmushin ta saki itama a karo na farko da gyara zamanta na ƙasaita. “Kaima amincin ALLAH ya tabbata a gareka *Bugun zuciyar Ammie'n sa*”. Ɗan luuu yay da idanunsa ya lumshesu tare da sake buɗewa a kanta da ɗan risinar da kai na girmamawa. Sai kuma ya kamo hanunta data janye a saman sumar kansa ya sumbata. Ajiyar zuciya ta sake saukewa mai kauri da jin ƙarin ƙaunar tilon gudan jinin nata da maƙiya suka sako a gaba. Tana matuƙar ƙishirwar rashin ganinsa a kusa da ita ko yaushe, sai dai babu yanda ta'iyane..... “Ammie kina lafiya?”. Ya katse mata tunanin da take neman yin nisa a ciki. Numfashi ta ɗan fisga ta fesar alamar dawowa. Sai kuma ta girgiza kanta da raunana fuskarta. “Kasancewarka lafiya itace tawa Saiful-mulk”. A karo na biyu ya saki murmushi yana ɗan jinjina kansa shima, sai kuma ya ɗago ya ɗan kalleta ya kauda kai. “Ina lafiya Ammie”. “Ni ba haka na gani a cikin idanunka ba *_Negar_*”. Baice komaiba kusan minti ɗaya, hakan ya fahintar da ita bazai ce ɗin ba, tai murmushi kawai tana kaɗa kanta. Ta yarda jinin mulki gaskiya ne, dan tana ganinsa yana yawo a cikin gudan jininta. Duk ƙasaita da miskilanci irin na Tajwar Haysam da ita kanta da ake faɗi Eshaan ɗinta ya takasu ya shanye. Irin miskalayen mutanen nan ne shi masu matukar ban mamaki da wuyar sha'ani, dan kai tsaye baka isa gane ainahinsu ba balle farin cikinsu ko damuwarsu kai tsaye, a matsayinta na mahaifiya a garesa da ake ganin yafi sakewa da ita fiye da kowa sukanyi zaman awa guda bai firta jimlar magana sau goma ba, murmushi kam ita da Malikat Haseenah kawai ke gani daga garesa sai mahaifinsa kafin yabar duniya...... Lurar da yay tayi nisa a tunani ya sashi kai hannunsa cikin ƙyaƙyƙyawan bowl ɗin da aka cuɗa dabino da zuba ya ɗakko tsagin dabino ɗaya daya naɗi zuma yay luntsum, ya tare da ɗayan hanunsa ya kai bakinta. A hankali taja numfashi ta sauke alamar dawowa. Babu musu ta matso tare da buɗe bakin ya saka mata. Sai da ta cinye a nutse tana mai kallonsa da murmushi sannan itama ta ɗauka kamar yanda ya bata ta bashi har sau uku. Tasan yunwa yake ji, amma yaƙi cin komai saboda damuwa. Tun yana yaro haka yake, a duk sanda sukaje dubashi a inda ya girma ita da Tajwar Haysam ta wannan hanyar take gane yanada damuwa, ko kuma yana fushi. Dan in har yana jin yunwa yaƙi cin abinci suka matsa masa akan yaci zai ɗiba abincin ya saka a bakinsu, sukuma hakan da yayi zai nusashesu zama su bashi da kansu har sai ya ƙoshi. Tissue tasa ta goge masa bakinsa idonta dake kansa na cika da ƙwalla. “Kanajin yuwa Negar?”. Gajeren murmushisa ya sakar mata da kauda kansa gefe maimakon amsar data buƙaci ji daga garesa. Itama bata sake cewa komaiba, sai wayar landline dake gefensa ta ɗauka. (Inba akan Tajwar Eshaan ba waya isa ganin Malikat Bushirat a haka😑). Cikin ƙanƙanin lokaci aka iso da abinda ta buƙata. Shi dai kallonta yake a harɗe kamar yanda itama take zaune a harɗen. Abincine na musamman, wanda tasan shine mafi soyuwa a garesa... “Idan kana zama da yunwa bazan yafema kaina ba”. Idanunsa yay kamar zai rufe sai kuma ya buɗe a kanta. Ƙasaita jininsa ce, kamewa da tsumewa nagartarsa ce. Kwarjini da cikar haiba mutuncinsa ne. Miskilanci gadonsa ne. inba ita ɗin bama wake ganin murmushin kojin furucin bakinsa, dan babu abu mafi wahala da girma ga Tajwar Eshaan kamar magana. Dariya kam ko'ita a karan kanta zata iya rantsuwa bata taɓa gani ba tunda ba'a gabanta ya tashi ba, sai lokaci-lokaci suke zuwa su gansa. Abincin ta haɗa masa a gabansa da kanta, babu musu kuwa ya amsa tausasan idanunsa na kallonta da jin ƙaunarta kamar kowane ɗa akan mahaifiyarsa. Tsahon mintuna yana tsakurar abincin cike da ƙasaita kamar wani magani, kafin ya ɗauka tissue ya goge bakinsa da janye jikinsa da ga kwanikan alamar ya ƙoshi..... “Ya take yanzun?”. Tambayar da take son jin tun ɗazu daga bakinsa ta fito tamkar an fisgota. Idanunta ta ɗan kafe kansa, amma sai ya kauda kai gefe kamar bashi ya buƙaci ji ba. Taja numfashi ta fesar, itama batare data sake cewa komai ba ta cigaba da nazartar sa. Kusan mintuna uku tsakani sannan ta nisa... “Ban san mikafi buƙatar ji ba. Sauƙin ko akasin sa. Amma dai zan iya cewa muna jiran ikon UBANGIJI ne”. Shiru babu alamar zai sake cewa komai, itama bata sake cewar ba. Kansa ya ɗan risinar gefe bayan ɗan kallon gefen idanu da yay mata. Miƙewa Malikat Bushirat tayi, ya bita da kallo harta isa bakin ƙofa sai kuma ta juyo, “Ina jin tsoron ace alaƙar da maƙiyanmu ke alaƙantawa da kai ta zam haka take Saiful-mulk” Kansa ya ɗauke gefe, itama sai ta ɗauke nata kan daga garesa tana danne lips ɗinta da haƙori. Shiru kusan na minti ɗaya, ita bata fitaba ita bata juyo ba, shi kuma bai amsa mata ba bai kuma motsa ba, sai kawai ta buɗe ƙofar zata fice. “A huta lafiya”. Ya faɗa dai-dai tana ficewa. Bayan kusan minti uku da fitarta ya furzar da nannauyar iska, miƙewa yay hannayensa goye da bayansa ya fara tattaki zuwa gaban window ta saitin inda zai iya hangota. Dai-dai kuwa hadimanta dake zaman jiranta na zagayeta. Duk da nisan da sukema idanunsa bai bar wajen ba har sai da yaga ta shige sashenta da tawagar hadimanta.. Wani irin ƙasaitaccen murmushi ya saki da lumshe idanu, sai kuma ya buɗe cike da isa yana mai barin windown ya shige ƙofar daya fito ɗazun.... Lafiyayyen bedroom ne mai ɗauke da kayan more rayuwa irin nasu na manya. Ƙamshi dai kam ba'a magana dan Tajwar Eshaan ko gonar turare haka ta gansa ta bari saboda yanda yake wanka da shi a duk motsinsa, son ƙamshi da zama cikinsa tamkar al'adarsu ce data zama dole ga talaka da mai kuɗi, sai dai banbancin tsada da ƙamshi ya banbanta maka wanene tare da kai. Amma dai-dai da banɗakin jinin Ruman ko shagon sai da kaya a kasuwa ka shiga saika san kazo ƙasar ƙamshi, duniya ta sansu da wannan tun shekaru aru-aru, dan suna a sahun farko na ƙasashen dake yin turare, yana kuma ɗaya daga cikin tattalin arziƙinsu dake shigar musu da kuɗi da bayyanasu a ko'ina suka shiga a duniya. Zaune ya kai a kujerar dake ɗan gefe ta jikin window, ya kai bayansa kwance a kujerar, tare da kwantar da kansa ya kalli sama ya lumshe idanunsa. Daga ƙasa ƙafafunsa a harɗe, hannayensa duk biyu akan hanun kujerar ya ɗan fara lila kansa. Sai da ya ɗauki tsahon mintuna ashirin a haka dan zakama iya ɗauka barci yake yi kafin ya buɗe idanunsa da suka kaɗa sukai jajur, zaune ya tashi da ƙyau, ya kai hannu drawer'n dake gefen kujerar ya buɗe, ƙaramar waya ƙirar nokia ya ɗakko. Danne-danne yay tare da kaiwa kunnensa yana wani yamutsa fuska. Bugu ɗaya kuwa aka ɗaga daga can, cikin bada umarni da ƙarfin ikon ya furta.. “A kawar da ukun bana buƙatarsu. Haɗuwa, da lokaci zaizo a saƙo”. Ya janye wayar daga kunnensa da dafe kansa yana cizar lips ɗinsa a lokaci guda fuskarsa babu alamar ɗigon wasa ko sassauci a cikinta sai razani mai ban tsoro da saka firgicin ga duk wanda zai iya ganinsa a hakan...........✍ (Tofa! Tajwar......🤔 bara dai nai shiru🤫). *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 90165991 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_19_* ..........Shigar Malikat Bushirat sashen Tajwar da yanayin data fito ya sake zama wasu ƙananun maganganu a masarautar, musamman ga masu ikon faɗa aji. Dan ta ko'ina suna da masu leƙen asiri a cikin hadimai da masu tsaron gidan kamar yanda itama Malikat ɗin ke dasu a kowanne sashe. Ga hadimai dai babu damar yin faɗa da kuwwa sai ƴar ƙus-ƙus, ƙus-ƙus ɗin ma sai ka samu wanda kafi yarda da shi kuɗan zanta gudun karka faɗa tarko. ★★...... Tun barowarta sashen Tajwar ta kasa zaune ta kasa tsaye. Abubuwane birjik ke faman mata kaikawo a zuciya. A karo na farko kenan da zuciyarta ta fara rawa akan al'amarin dake faruwa tun daga randa aka ɗora tilon ɗanta karagar mulkin kujerar Shahan-shan. Anya kuwa ba'akwai lauje cikin naɗi ba a wannan al'amarin?. Sannan ba zaton wuta a maƙera sukema komai ba alhalin yana a masaƙa?. Ta rumtse idanunta da sukai matuƙar ja da ƙarfi, saboda zuciyarta ke hasaso abun, amma ƙirjinta ne keci da wutar ƙunar dangantashi da abinda tafi so fiye da komai a duniya. Sai dai ya zatai, hakan kamar dole ne a gareta kodan rashin samun wani bakin zare har yanzu.... Kalmar bakin zare data faɗo a tunaninta ce ta sata buɗe idanu da sauri, sai kuma ta jawo ɗaya daga cikin wayoyinta da dan tsumar jiki tana gyara zama. Danne-danne tai tare da kaiwa kunnemta. Daga can akai sallama tun kafin ita tayi. A taƙaice ta amsa da faɗin, “Jasrah ina buƙatar hadiman nan yanzun nan”. “An gama Akia”. Jasrah ta amsa mata da girmamawa. Mikewa tai itama ta hau shirin fita fadarta. Sai dai komai tana yinsa ne a tsanake amma yanayinta tattare da matsananciyar damuwa. Fitowarta dai-dai da shigowar Ghazi, ya zube ƙasa yana mai miƙa gaisuwa a gareta. Hannu kawai ta daga masa bayan ta kai zaune. Jasrah ma dake zaman jiran fitowar tata tai mata sannu da fitowa. Kai ta jinjina mata da maida hankalinta ga Ghazi dake gurfane kansa a risine. Itama Jasrah hankalinta ta maida kansa. “Ghazi ya naganka kai ɗaya?”. “Ranki ya daɗe an samu matsala ne”. “Matsala kuma? Kamar ya kenan?”. Ɗan jimm yay na jimamin faɗar abinda ke bakinsa. Sanin Malikat Bushirat bata buƙatar kawane-kwane a magana ya sashi girgiza kansa idanunsa na canja kala zuwa ja sosai. “Ranki ya daɗe gawar uku daga cikinsu kawai muka samu, tare da hadiman dake tsaron inda aka killace sun su duka biyun. Diwa da ta rage ma bana zaton zata kai labari, kuma da alama yanzu-yanzu aka aikata ta hanyar madarar da aka basu matsayin abincin rana. Ba ƙaramar zabura Jasrah tai ba, yayinda Malikat ta rumtse idanu da sauri ƙirjinta yay wata irin harbawa da ƙarfi tamkar zai buɗe dan firgici. Amma a zahiri miskilancinta da ƙasaitar mulki bazai taɓa haska maka komai ba daga yanayin nata..... ★Kamar yanda labarin mutuwar hadiman nan ya isa kunnen Malikat Bushirat haka ya karaɗe kunen kowa a masarautar. Yayinda likitoci suka rufu akan Diwa da itama gab take da rasa tata rayuwar. Wasu kuma sun duƙufa ne akan binciken madarar da suka sha ta ƙarshe duk da kowa ya san daga cikinta ne akama zuba musu ko minene....... *_ZAWJATA-ALMILKI_* Yayinda ake tsaka da jimamin rasa hadiman da sukai sanadin shigar Iffah a mawuyacin halin da take ciki, ita kuma waraka ALLAH ya saukar a gareta bayan duƙufar Baba yaro akanta da maganin da aka amso a wajen Kaka. Tun a mata hayaƙin farko jinin dake fita a jikinta ya tsaya. Hakan ya basu hope ɗin cigaba da bin dokokin da kaka ya kafa na maganin daki-daki har ALLAH yasa aka dace ta kawo wani nannauyan numfashi da ambaton sunan ALLAH. “Ruwa!”. Shine abinda ta ambata na biyu. Cikin sauri Daneen Ammarah ƙanwa ta biyu ga marigayi Tajwar Haysam da ayanzu ke tare da ita ta zabura da kanta ta ɗauka ɗaya daga cikin bottle water dake a ɗakin ta ɓalle murfin ta kafa mata a baki. Cikin mawuyacin hali Iffah take zuƙar ruwar, sai dai kasancewar shine abinda tafi buƙata a ƙanƙanin lokaci ta shanye sa tas. Yumma da itama dai uwa ce gasu Daneen Ammarah ɗin, sannan matsayin Kaka ga Tajwar Eshaan dan ƙanwace ga Malikat Haseena ta sake ɓalle wani ta zuba a hanunta ta shafa a goshin Iffah dake jiƙe sharkaf da gumi. Ajiyar zuciya ta sake ja a hankali tare da buɗe idanunta da sukai mata matuƙar nauyi. Kaɗan ta buɗe ta maida ta rufe. Alhmdllh suka shiga ambata da mata sannu, yayinda Daneen Ammarah cike da zumuɗi tai kiran Malikat Bushirat. Ita ta fara sanar mawa kafin mahaifiyarsu Malikat Haseena duk da tana cikin halin ciwon ƙafa da bata iya ko miƙewa sai da taimakon wheelchair dama ga tsufa..... Cikin abinda baifi mintuna goma ba ɗakin da Iffah ke kwance ya cika da wasu a manyan masarauta. A fuska dai suna nuna farin cikin farkawar tata ne, amma a ƙasan zuciya mafi yawansu kowa da irin tasa manufar. Malikat Bushirat kuwa harda hawayen farin cikinta, farkawar yarinyar da a kallon farko ta gama shiga ranta ya goge mata sauran damuwar abinda ya faru game da kashe Hadiman da aka aika suka aikata sherin daya jawo komai. A take Malikat Bushirat ta bada ƙyauta mai tsoka ga Baba yaro. Hakama wasu a cikin manyan sun masa ƙyautar. Daneen Ammara ce ta biyu, itama kuma ta bada mai tsoka daya bama kowa mamaki. Ana ƙoƙari daukar Iffah zuwa sashen Malikat Bushirat kamar yanda ta buƙata sai ga saƙo da ga Malikat Haseena cewar akai Zawjata-almilki sashenta. Take fuskokin mutane da yawa ya canja a wajen, saɓanin ta Malikat Bushirat data nuna tsantsar farin ciki da jin ƙaunar surukar tata. Dan dama zuciyarta cike take da fargabar sake kasancewar Iffah babu tsaro. Duk da sashenta ma bazai iya zama kanwar lasa ba ga wani mahaluki a zahiri, sai dai yaƙin sunƙuru. To amma idan ta danganta da abinda zuciyarta ke rawa a kai komawar Iffah sashenta kamar an gudu ba'a tsira bane. Sashen Malikat Haseena kuwa sunyi imanin ko ifiritu da kansa zaiji tsoron gittawa kai tsaye balle wani shiryayye dake a masarautar.... Rashin ƙarfin jiki da rashin dai-daiton tunani yasa Iffah ba fahimtar komai take ba, hasalima tun yunƙurin farko bata sake gwada buɗe idanunta ba suna a lumshe. Sai dai tana jin komai dake gudana har ɗaukarta da akai akan keken asibitin zuwa waje. A mota a ka sakata Daneen Ammarah tare da ita. Sai Malikat Bushirat da tabi bayansu a tata motar da ake tuƙata. Ganin haka sauran ƴan son ganin ƙwaf suma duk suka bisu can dan babu mai fatar yin laifi ga Malikat Haseena....... *_GIDAN BABIY_* Tun bayan barin Iffah gidan ɗan sauran kakkaɓin farin ciki da ƙwarin gwiwar da su Fareeha suka barsu da shi ya ida kakkaɓewa. Ummu bata da aiki sai kuka. A kwana uku kawai duk ta rame saboda ko abinci bata ci yanda ya kamata. Hanash kam ba'a magana dan makamancin irin ciwon Iffah na damuwa ne ke neman bugarsa (Depression). Shi kansa Babiy dake dauriya duk ya zuƙe a tsaye wani lokaci har yi yake kamar zai faɗi. Komai ya tsaya musu cak, kunnuwansu ne kawai a buɗe na jiran kiran jana'izar tilon ƴarsu mace data rage. Dan gushewar kwana uku bai sa sun saka ran ta tsallake ba. Suna tsaka da wannan zaman jigum-jigum akai sallama da Babiy ƙofar gida. Kamar bazai fita ba sai kuma ya miƙe cikin ƙarfin hali ya zura takalma ya fita. Ɗan turus yayi idanunsa kafe akan wanda yay sallamar da shi... Abu Moosa da shima ke kallonsa ya iso gabansa da ƙyar yana tangaɗi. Riƙesa Babiy yay da sauri da faɗin, “Subahanallahi Abu Moosa!”. Bai iya ya amsa masa ba saboda halin da yake ciki. Riƙesa da ƙyau Babiy yay suka shiga ciki yana jera masa sannu. Zai zaunar da shi a soro ya girgiza masa kai cike da ƙarfin hali. “Kamin alfarma mu shiga ciki”. Ya faɗa da ƙyar tamkar numfashinsa zai rabu da gangar jikinsa. Cikin sauri Babiy ya cigaba da riƙesa suka shiga cikin gidan, shigowarsu yasa Ummu miƙewa da sauri ta ɗakko tabarma ta shimfiɗa a ƙasan bishiyar dake tsakar gidan... “Ku bani ruwa dan ALLAH”. Abu Moosa Ya sake faɗa da ƙyar yana fisgar numfashi. Ruwan Ummu ta kawo masa, dai-dai da fitowar Hanash daga ɗaki saboda jin maganganu na tashi a gidan nasu. Da ƙyar ya iya maƙwarwa uku saboda numfashinsa fisga yake. Babiy ya ajiye ruwan da sake tallafosa jikinsa. “Abu Moosa mike faruwa ne haka? Daga ina kake?”. Da ƙyar ya iya ɗaga idanunsa dake zubar da hawaye ya kalla Babiy. Sai kuma ya girgiza kan yana jan numfashi da shashsheka. “Abu Hanash ka gafarceni dan ALLAH, nasan wannan yana cikin numfashin bankwana da nakeyi”. “Babu abinda kamun nikam, dan ALLAH kuma ka daina faɗar wannan magana bara mu kaika asibiti”. Riƙo hanun Babiy dake yunƙurin tashi yay yana girgiza masa kai da ƙyar. “Babu buƙatar hakan, domin ban cancanci kwatankwacin wannan adalcin daga gareka ba, kayi haƙuri ka zauna ka saurari abinda zan faɗa maka da yafi kaini asibiti muhimmanci, nasan kuma insha ALLAHU zai maka amfani da kuɓutar da yarinyarka dama sauran yaran da zasu iya biyo baya a makamancin halin data tsinci kanta”. Numfashin dake neman kufce masa yaja da ƙyar kafin ya cigaba da faɗin, “Abu Hanash ka gafarce ni nine nai sanadin shigar ƴaƴanka wannan halin, dan nine nai shunensu ga masarauta”. Da ga Babiy har Ummu da Hanash wani irin zabura sukai mai bugawa da bugun ƙirji. Ya cigaba da faɗin, “Nayi hakane dan son zuciya da shegen son abin duniya. Sai hassadarka data daɗe a zuciyata saboda sana'armu ta kasance iri ɗaya, ada tare ake amsar zumar mu a masarauta amma daga baya aka koma amsar taka kawai saboda gaskiyarka da rashin algus. Maimakon na gyara nima na zama mutumin kirki kamarka sai na kasa hakan, shaiɗan ya dinga tunzurani akan kayi sammu ne shiyyasa. Tun daga wancan lokaci naketa ƙulla hanyoyin ganin bayanka a matsayin ɗaukar fansa, sai dai duk wadda na ƙulla sai ALLAH ya kuɓutar da kai, hakan ya cigaba da ƙaramin tsanarka, dan haka na cigaba da kutsa kaina cikin masarauta dan kawai naga na ɓataka an wulaƙantaka, nan ma banci nasara ba dai. Kwatsam sai aka samu canji gwamnati, ni kuma nai amfani da wannan dama wajen sake cusa kaina cikin tsakkiyar masarauta harna samu nasarar amsuwa, nasan komai game da mutuwar Zawjata-almilki, dan ina gaba-gaba a hadiman da ke aiki ga masu aikatawar”. Yaja numfashinsa da ke fisga da ƙyar. “Lokacin da aka sakamu aikin binciken yara mata guda biyu masu hankali dan a aurama Tajwar naji a raina lokacin nasarata a kanka ya yi, dan haka na bada sunanka da adireshin gidanka. An ɗauka tsahon kwanaki ana bibiyar yaranka da kai kanka kafin azo gareka. Ko bayan mutuwar ta farko ni na ƙara ƙulla aka sake dawowa ta biyu dan burina kawai naga na durƙusar da kai ƙasa. Ka gafarceni Abu Hanash dan nayi nasara, sai dai ramin muguntar dana gina daga ƙarshe ni na afka ciki......” Babiy da hawaye suka gama wanke masa fuska ya share yana duban Abu Moosa “Kenan kai ne ka ƙulla na uku ma?”. “Wlhy a'a bani da alaƙa da wannan, hasalima ban san ƴar wajenka bace sai ranar da aka kawo kuɗin aure”. “Waye ya kashe min ƴaƴa? Kai kuma miya faru da kai?”.......✍ 🤔Ikon ALLAH, wannan duniya ina zaki kaimu, baka damu da kowa ba amma kana barcine da rashin barcin wasu, kana ci ne da rashin cin abincin wasu. Kana numfashi ne da burin ƙaruwar na wasu. Kana farin ciki da gushewar farin cikin wasu. Kana shiga tarkon wahala da dariyar bakunan wasu. Ya ALLAHU ka ɗoramu akan maƙiyammu, ka hanemu yin hassada da zaluntar wani koda ace shi ɗin ya zaluncemu. ALLAH sarki Babiy namu🤦🏻 *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 90165991 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_20_* ........Abu Moosa dake sonyin magana ya dafe ƙirjinsa da numfashi ke kokawar kufcewa, tari ne ya suɓuce masa sai ga jini. Hankalin Babiy da Ummu ya tashi, amma Hanash ko'a jikinsa. Da ƙyar tarin ya lafa, Babiy dake riƙe da shi yace, “Kayi haƙuri muje asibiti, aman jini fa kake yi”. Murmushi yay mai ciwo da kaɗa ma Babiy kansa da ƙyar. “Abu Hanash zuwa asibiti bazai canja komai ba, dan gubar da aka shayar da ni bata da makari a ko'ina sai a wajensu.” “Ya ALLAH! Guba kuma?” “Wannan shine hukuncin daya dace da masu irin halina ai karka damu, kai dai kawai ka saurareni zan gaya maka ta hanyar da zaka kuɓutar da yarinyarka, ina fatan hakan ya zamar min aikin alkairin dazan samu sassauci a kabarina”. Babiy zai yi magana ya dakatar da shi. “Ka saurareni kawa Ab.....” ya kasa ƙarasawa saboda sabon tarin daya sake sarƙesa. Sosai Babiy ya rikice ya shiga ƙwala kiran Hanash duk da yana a kusa da shi. Hanash dake jin tamkar yasa wuƙa ya ƙarasa numfashin wanan shegen tsoho ya amsa da ƙyar. “Kaga kamashi maza muje asibiti”. “K...k...karku wahal da kan.. Ku. ka saurareni kawai”. Abu Moosa ya tari numfashinsu da ƙyar yana dafe ƙircinsa da tari ke yunƙurowa. Babiy ya buɗe baki zai yi magana cikin taresa shima sai kawai sukaga yarab alamar rai yayi halinsa. Salati suka ɗauka a tare, wanda yay dai-dai da shigowar jami'an tsaro dake na ƴan sanda a ƙasar, bayansu wata mata ce ke rusar kuka... “Ranka ya daɗe dama na faɗa muku, na faɗa muku mutumin nan baya ƙaunar mijina, yanzu kun gani da idonku gashi nan ya kashe mini shi, dama kullum yana faɗa min neman rayuwarsa yake yi, ashe dai shine ɗin zai zama ajalinsa.....” ta zube ƙasa tana cigaba da kuka harda kururuwa....... Hankali tashe su Babiy ke kallon wannan mata da jami'an tsaron, ba shigowarce ta tada hankalinsu ba da farko, dan tunaninsu ya basu duk wanda ya bama Abu Moosa guba shine yasa suka biyo sa. Furicin wannan mata da kai tsaye Babiy ya gane matar Abu Moosa ce ya firgitar dasu. Cikin ƙarfin hali Babiy yace, “Yallaɓai taya daga taimako kuma zan zama mai kisa? Abu Moosa abokina ne tun ƙuruciya kowa ya sani, ban kashesa a da da muke tare ba sai yanzu da a ƙalla nama kai shekara biyar kenan ban sakashi a idona ba sai yanzu dana gansa ayam cikin gidana babu zato.....” “......Shiyyasa akaga gawarsa a cikin gidanka yanzu daka samu damar ganin nasa ko?”. Jami'in ya tari numfashin Babiy da sauri yana wani makirin murmushin ƙeta... “Allahumma ajirni fi musibati wa'akhlifni khairin minha” Babiy ya faɗa a zahiri gumi na karyo masa. Duban jami'in yay zaiyi magana matar ta taresa tana cigaba da kukanta mai cike da bori.... “Ƙarya yake wlhy yallaɓai, shekaran jiya jiyan nan sai da yaje har gidanmu ya faffaɗa masa magana mara daɗi da tabbatar masa shine ajalinsa, idan ya ƙaryata ai munada shaidar hakan”. Hanash da zuciyarsa tazo ta tokare maƙoshi a hasale yayo kan matar, wata shegiyar shaƙa yakai mata saiga idanunta tamkar zasu fito waje. “K! baƙar matsiyaciya, dan kawai anga gawar mutum a waje sai ya tabbatar masu wajen suka kashe shi!!”. Idanuta ta rumtse da ƙarfi jikinta na ɓari, ta fara kakarin azaba dan da gaske ta shaƙu. Tuni jami'an tsaron duk sukai kansu da ƙoƙarin ɓanɓare hanun Hanash a wuyanta amma sun kasa. Ummu kuka ta sanya, yayinda Babiy keta kiran sunan Hanash da faɗin ya saketa amma sam babu alamar yana ma jinsa. Da ƙyar aka iya ɓanɓare Hanash, ta zube gefe tana sauke nunfashi da ƙyar hanunta riƙe da wuyanta. Sai da suka bata ruwan da suka fita suka ɗakko a mota da sauri tasha ta samu dai-daiton numfashi. Cike da gadara ogan tawagar ya bama yaransa umarnin kama Babiy da Hanash. Sosai Ummu ke kuka da roƙonsu amma babu wanda ya saurareta, har ƙofar gidansu daya cika da mutane tun isowar jami'an tsaron ta biyosu amma kamarma basu san tanayi ba. Haka aka saka Babiy da Hanash a mota, sai gawar Abu Moosa a Ambulance da sukazo da ita (Alamar akwai dai lauje cikin naɗi kenan. Inba hakaba miye na zuwa da Ambulance ɗin?🤔). Matan anguwar ne suka rufu kan Ummu data yanke jiki ta faɗi bayan wucewar motocin. Amma koda suka zuba mata ruwa bata farfaɗo ba. Hankalinsu ne ya sake tashi, makwafcinsu ya bada umarnin a sakata a motarsa a kaita asibiti. Da taimakon matan aka sakata a mota, matarsa da wata mata dake anguwar itama mijinta ya rasu suka shiga. Sai lokacinne mutane suka samu bakin magana. Wasu na nuna tausayawa ga wannan ahali, wasu na jin farin ciki badan sun taɓa musu komaiba, sai dan kawai dalilin hassada na rashin dalili. A asibiti kam har an amshesu za'a fara dubata sai sukaga Doctor ɗin ya dakata sakamakon kiran wayarsa da akayi. Kansa ya girgiza musu ya nufi barin ɗakin yana sanar musu yanada uziri. Hankali tashe makwafcin nan nasu da ake kira Abu Zainab ya shiga roƙonsa amma bai sauraresu ba. Sun fara neman taikon Nurses suma sai zuƙewa suke saboda gargaɗin da Doctor yay musu. Al'amarin kamar wasa anƙi taɓa Ummu, dole suka ɗauketa suka bar asibitin zuwa wani, sai dai acan ɗin ma har an amshesu aka koresu. Basu gajiyaba suna kuka suka nufi privet ko acan za'a dace tunda aikin kuɗine. Anan sun amsheta, amma sun sara musu maƙudan kuɗaɗe kafin su taɓata, acewarsu dokarsu kenan. Matar nan da mijinta ya rasu ta fashe da kuka tana girgiza kai. “Suma basa son su amshemu ne kawai, shiyyasa suke mana kora da hali. Inba kora da hali ba ai banajin Abu Hanash ya mallaki koda kwatar waɗan nan kuɗaɗen da suka ambata inba dai kaddararsa zai saida ba”. “Hakane Umm Yazeed maganarki nakan gaskiya, kuma tabbas na fara ji a jikina akwai lauje cikin naɗi a wannan lamarin, da alama hanasu amsarmu akeyi”. Abu Zainab ya faɗa ransa a ɓace. Matar Abu Zainab dake share hawayen itama ta ce, “Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un. Wannan wace irin masiface haka? Mi bayin ALLAH nan suka tarema wani da zafi haka?”. “Sanin gaibu sai ALLAH, inaga inada mafita ɗaya, mu ɗauketa mu maidata gida sai a sanar da ƴan uwansu ko? Tunda mudai munyi iya ƙoƙarin mu...” “Da hakan kukai tun farko da baku wahal da kanku ba”. Wata murya ta faɗa a bayansu. Da sauri suka juya su duka, sai dai bayan mutumin kawai suka iya gani. Da gudu Abu Zainab ya bisa, amma kafin yaƙarasa garesan harya shige mota sai ƙura ya bulesa da shi....... (🤔????) *_MASARAUTA_* Babban ɗaki na musamman aka warema Iffah a sashen Malikat Haseena. Tare da amintattun hadimai biyar da zasu dinga mata hidima. Sai Ghazi biyar suma da zasu dinga bata tsaro duk da dama sashen zagaye yake da masu tsaron, amma an ware biyar ɗinne na musamman domin kula da duk wani motsin shiga da fitar mutane da zai shafi Iffah. Hakan ya sake saka Malikat Bushirat a farin ciki matuƙa. Yayinda sabanin haka ya bayyana a fuskokin munafukai, sai dai wasu sunyi jarumtar dannewa baƙin cikin nacin zukatansu tamkar wutar daji. Malikat Haseena data zartar da hukuncin batama nuna tasan sunai ba. Ita kuwa Daneen Ammarah damar nutsuwar nazartarsu ta samu ɗaya bayan ɗaya dalilin wani ɓoyayyen al'amari dake ajiye a zuciyarta tsahon shekaru. Daneen Ammarah ta kasance ɗaya daga cikin ƴaƴan Malikat Haseena da Tajwar Abdul-majeed Ibn Aliy. Su huɗu suka haifa. Tajwar Haysam shine babba, (sarkin daya shuɗe kuma mahaifin sarkin yanzun). Sai Daneen Waheeda tana auren wani babban sarki a yankin larabawa. Sai Daneen Ammarah, itama tayi aure sai dai auren bai jimaba sakamakon wani ɓoyayyen al'amari dake tattare da ita, wannan ne sanadin dawowarta gida take zaune kusan shekara goma sha tara kenan bata kuma sake wani auren ba. Ƴar uwarta da mahaifiyarsu Malikat Haseena da marigayi Tajwar Haysam da mahaifinsu daya bar duniya da tabon damuwar ƙaddarar ɗiyar tasa ne kawai sukasan wannan sirrin, al'amarin ya sameta tun tana ƙarama dan bata wuce shekara 14 ba, shiyyasa ta jima batayi aure ba, bayan ta samu tai auren kuma bata jimaba suka rabu da mijin dan auren baifi wata takwas ba ma. Manyan masarauta sunta ƙananan magana akan hakan da fassara al'amarin na Daneen Ammarah ta siga daban-daban amma su Malikat Haseena sukai biris dasu. Sai auta Miran Nayyar nada shekara bakwai ALLAH yay masa rasuwa. Bazamuce Iffah tayi garau ba kam a wannan yini. Dan har yanzu ko idanunta bata iya ɗagawa ta kalla kowa. Sai dai daidaituwar fitar numfashinta ya saka nutsuwa a zuciyar kowa. Koba komai dai an samu sassauci ai. Daneen Ammarah itace da kanta ta gogema Iffah jiki ta canja mata kaya, itace kuma da kanta tai zaman bata abinci daya kasance mai ruwa-ruwa. Daga haka aka ƙara bata magungunan da duk suka dace da gyara mata kwanciya a lafiyayyen gadon da yaji shimfiɗu na alfarma. Wani irin barcine mai daɗi yay awon gaba da ita, cikin ƙanƙanin lokaci ta fara sauke numfashi. Daneen Ammarah dake kallonta cike da tausayawa da jin wani ɓoyayyen al'amari akan yarinyar ta sauke numfashi ahankali da mata addu'ar samun lafiya da fatan ya zama kaffara a gareta....... ★★.... ★.... ★★..... Duk wani nau'in kiranye ga uwa ta yisa tun lokacin da labarin abinda ya faru da yarinyar can sakamakon saka riga ya risketa, tabbas sune suka bada riga, amma abinda ya faru da yarinyar bashine ya kamata ya faru ba akan rigar, dan shirinsu sam bashi da alaƙa da halin da take a ciki yanzun. Hakan na nufin kenan bayansu akwai wasu masu shiri akan yarinyar kenan?. In dai har hakane kuwa to su ɗin su wanene? Minene tasu manufar kuma?. Wannan amsar take buƙatar ji a wajen Uwa, sai dai har zuwa duhun dare babu alamar zata ziyarce ta. Tun zuciyarta na raya mata ta jira har ta fara jin ita taje gareta mana kawai. Amma tuna zuwa ga Uwa babban al'amari ne mai wahalar yiwuwa gareta yasa ta kasa iya cigaba da tabuka komai har dare ya cigaba da tsalawa masarautar ta ɗauki shiru tamkar babu wani mahaluki mai sauran numfashi. Ta cigaba da kaikawo a cikin wannan shiru, tare da ƙara gwada dabaru kala-kala na kiranye ga Uwa. Dai-dai lokacin da take sarewa, gaɓɓanta ke nuna gajiyawa mummunan sautin dariyar Uwa mara daɗin saurare a kunnuwa ta fara mata kaikawo tamkar tana yawo cikin iska. Ƙasa ta zube akan gwuyawunta tana mai jan nannauyan numfashi dajin sanyi a ranta. Tarwai Uwa ta bayyana a gabanta, akan kujerar baƙin karfenta mai adon gwal sanye cikin jajayen kaya kamar koyaushe. Mummunar fuskarta a matuƙar tsuke take babu alamar itace ta gama dariyar dataita amsa kuwa a mintocin da suka shuɗe..... “Barka da isowa Uwa mai share kukan masu kuka. Uwa ina cikin matuƙar ruɗani, dan aikinmu yasha banban da wanda ya bayyana ga ƴar shilar suda. Kamar yanda na riski yinin jiya a cikin ruɗani, haka na kasance a duhun dare batare da na rintsa ba, na kuma sake wayar gari da ƙishirwar ganinki a yinin yau har zuwa iyanzu da daren ke ƙoƙarin zama dare biyu da faruwar komai?. Shin kuskuren daga garemu ne? Kokuwa kece kika canja aikin ya koma hakan? Ko akwai wasu masu irin shirinmu ne a wannan daula batare da mun san dasu ba? Minene manufarsu su? Wane buri kuma suke da shirin cimmawa?. Uwa ki taimakeni nasan wannan amsoshi in ba hakaba zuciyata na gab da tarwatsewa ne”. “Bazan gaji da tuna miki akwai ƙalubale zagaye da cikar matakin aykinki na biyu ba, kuma wannan ƴar shila na tare da kaddarar ƙalubalenne, sai dai na miki alkawarin tsayuwar daka akan hana faruwar nasarar da zatazo in har bataki bace ba. Tabbas aikin ba namu bane, kuma rigar da aka kai mata ta sanya ba tamu bace itama. Na gano hakane a daren jiya bayan mutuwar waɗan can hadiman da kuma samun lafiyar ƴar shilar.. Hakane ya sani duƙufa bincike tuƙuru domin gano daga ina matsalar take?, wanene ya shirya aikin laɓewa bayan namu? Har yaci nasarar kuɓutar da ita da tarkon makircin sa cikin sauƙi haka?......” “Uwa kin gano kenan?”. Ta-kurya ta tari numfashinta cike da zalamar son jin amsa........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 90165991 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_21_* ________________________ _Innalillahi wa-inna ilaihirraji'un. A madadin ɗaukacin ɗalibai na G.G.A.S.S D/Z. Muna miƙa saƙon ta'aziyyar ga ƴan uwanmu da iyayenmu da yayyenmu na rasa Uwa abin alfaharin duk wani ɗa na gari da mukai *Hajiya Ai'sha Ahmad Tukur* tsohuwar principal ɗinmu. Ya rabbi ka gafarta mata, ka yafe mata kurakuranta. Ka bama iyalanta da mu haƙurin rashinta. Mu data bama tarbiyya a wani bigire na rayuwa, ALLAH yasa muyi koyi da ƙyawawan halayenta managarta. Dan ita ɗin abin alfaharinmu ce da bazamu taɓa iya mantawa ba😭, zamu tunata, zamu cigaba da tunawa da ita, zakuma mu tunatar dana bayanmu kyawawan halayenta da alkairinta. (ALLAH ya gafarta mata.😭🙏🏻)_ ________________________ ...........“Ina kan ƙoƙarin yin hakan yawaitar kiranyanki ya katse ni, amma tabbas wanda ya aikata yana a cikin wannan daula ne, yana kuma da babban shirin daya kamata mu sani tun a yanzu. Ina kuma ji a jikina babban yaƙine da kema ya shafeki, kuma za'a cigaba da amfani da yarinyar ne wajen tabbatar da shi in har tana cikin masarautar nan”. “Shiyyasa tun farko nace a kawar da ita Uwa, dan babu wani amfani da wannan yarinyar zatamin face cigaba da ɗagamin hankali, gashi kuma har tana neman zama tafinta a al'amurana dake gab da kammala bayan gumurzun yaƙin da naci na tsahon shekaru a baya kafin zuwa lokacin tattara ganima”. “Abinda kike ƙoƙarin yi shine mafi girman kuskure da zai rusa dukkan nasarorinki Ta-kurya. Domin yunƙurin kashe wannan ƴar shilar da kike tamkar kashe rayuwarki ne baki ɗaya. Tun farko na faɗa miki kasheta kai tsaye bashine mafitar ba, ba kuma shine ƙarshen daƙile yunƙurinta ba ita a karan kanta. Hasalima a yanzu rayuwarta mukafi buƙata, zamu jefata ne matsayin dutse ɗaya dazai wargaza tsuntsaye biyu. An wargaza mana shirin mu na farko a kanta, dan haka zamu tafi na biyu. Yaƙinki a yanzu shine kiyi duk yanda zaki ta baro wancan sashen daga nan zuwa cikar kwanaki bakwai. Zakiyi yanka na baƙar babbar dabba a daren goma sha uku, zakuma ki dawo da rigar data sanya. Kiyi duk wani ƙoƙarin da zai hana kusancinta da Ajlaan a turaka. Dan maganar kaita turakarsa ta rushe kuma zamu sake sabon salo ne domin kama tsuntsu mai wayo.......” “An gama Uwa mai share kukan masu kuka. Sai dai dawo da rigar nan zai zama abu mai wahala kasancewar tana a hanun Mamma (Malikat Haseena) ne a yanzu haka”. “Wannan umarni ne Ta-ƙurya”. “Zanyi iya ƙoƙarina Uwa. Sai kuma maganar mutuwar Hadiman can, Shahanshan da kansa ya saka kwamitin bincike masu tsauri da basu taɓa ƙetare nasarar cika umarnin da'aka basu ba. Kinga akwai matsala kenan tunda waɗan can sun laɓe ne a jikin aikinmu suka zartar da nasu, sannan suka kashe hadiman tamkar yanda muka shirya kafin mu mu aiwatar da hakan”. Wata irin mahaukaciyar dariya mai amsa kuwwa Uwa ta shiga ƙyalkyalawa, sai da ta ɗauka tsahon lokaci tanayi kafin ta tsagaita ta tsuke fuska tamkar ba itace tayin ba. Har ta ƙurya ta fidda ran samun amsa sai kuma Uwa ta sake ƙyalkyalewa da dariya tana ambaton “Ajlan! Ajlan!! Ajlan!!!” ta ƙara kwashewa da dariya tana mai disashewa a idanun Ta-kurya da zuciyarta ta kasa fassara ma'ana ko dalilin dariyar ta uwa... 🤔Ko miye naku tunanin a wannan gaɓar kuma masu karatu???. ★... ★.★.★ ★... *_GIDAN BABIY_* Sun dawo har yanzu da ɗan sauran mutane maƙwafta da aketa ɗan ƙus-ƙus akan lamarin. Cikin ƙanƙanin lokaci aka baibaye motar, waɗanda suka shige gidaje suka fara fitowa. A yanayin da aka fidda Ummu mafi yawansu sunma ɗauka dai bata da rai, dan kuwa da gaske babu alamar rai tare da itan. Kuka da salatin da mafi yawan mutane suka ɗauka na tunanin ta mutun ne yasa Abu Zainab saurin dakatar da su. “Dan ALLAH kowa ya kwantar da hankalinsa. Umm-Arfa ba mutuwa tai ba”. Badan hankalin su ya kwantaba sukai shiru, sai dai dama kukan na wasu na munafurci ne dai. Matane suka kamata aka shiga da ita, a tabarmar da suka samu tsakar gida suka shimfiɗeta. Cikin sa'a Abu Zainab yaci karo da wayar Babiy dake yashe a ƙasa. Da alama sanda jami'an nan zasu fita da shine ta faɗi. Jikinsa har tsuma yake a duba contact ɗin wayar, cikin sa'a ya samo number da akai saving da Baba. Baya raba ɗayan biyu mai sunan nada babban matsayin baban a wajen Babiy ɗin, dan haka ya danna masa kira kai tsaye, sai dai harta tsinke ba'a ɗaga ba. Sake kiran yay yana addu'ar dacewa sai ko gashi an ɗaga... ★A lokacin da kiran Abu Zainab ya riski su kaka ta hanyar wayar Babiy ba'a ƙaramin tashin hankali suka tsinci kansu ba shi da Iyyani. Duk da kasancewar yamma tayi kuma yasan a yau dole ne sai ya dangana da daular ruman dole ya bazama neman wani yaro mai mota a ƙauyen nasu dake jigila a ko yaushe, cikin sa'a ya samesa ya dawo kenan ma ko gida bai shiga ba. Amma saboda mutuncinsa da ake gani yana masa bayani babu musu ya amsa masa suka ɗauka hanya harda Iyyani daketa faman sharar hawayen da suka kasa tsaya mata. Ana sallar isha'i suka iso cikin daular ruman. Basu sami mutane ba a gidan kamar ɗazun, sai Umm Yazeed da matar Abu Zainab dake dai tare da ita har yanzun. Zuwa yanzu Ummu ta farfaɗo, sai dai taƙi magana da kowa sai hawaye da taketa faman zirarwa ta gefen ido, ga numfashinta baya fita normal kamar na kowa, tana fitar da shine da fisgosa a wahale sannan a fiffisge. Kuka Iyyani ta sake fashe da shi da rungume Ummu a jikinta tana kiran sunanta. Kaka kam tsaye yay kawai zuciyarsa na harbawa da ƙuna. Suna a haka Abu Zainab ya dawo, dama sallar isha'i yaje. Cikin girmamawa ya gaida kaka, shima ya amsa masa da kulawa da godiya. Ya ɗan murmusa kansa a risine. “Ai ba komai baba yiwa kai ne. Sannan mun zama ɗaya ai mu da Abu Hanash. Ko mu irin haka ta faru da mu zai tsaya tsayin dakane a kan komai. Ruɗanin halin da Umm Arfa ke ciki yasa su bamu bibiyesu musan miya faru ba har yanzu gaskiya. Dan munata yawo a asibitoci amma sunƙi amsarta, ga jikin nata kuma yana buƙatar a duba mata shi, shiyyasa yanzu dana idar da sallar magrib naje na samo ɗan uwana dake aikin asibiti gashi muna tare, sai dai ba wani babban likita bane dai....” Kai kawai Kaka ya jinjina masa da faɗin, “ALLAH ya saka muku da alkairi, haka ake fatan zaman makwaftaka, domin ita makwaftaka tanada ƙarfin da zata iya fin ƴan uwantaka muhimmanci ma a wani ɓangaren. Yanzu gashi abu ya samesu, kafin mu muzo kun basu ɗauki, da bakwa zaman lafiya kuma hakan bazai yuwuba. Dan haka duk wani mutum na ƙwarai daya san kansa ya dace ya rayu da maƙwafcinsa lafiya da ƙaunar juna”. “Hakane Baba, ALLAH ya saka da alkairi. Bara na shigo da shi”. Murmushi Kaka yayi da jinjina masa kai. Koda suka shigo tare da ɗan uwan nasa shima ya gaida Kaka da girmamawa, hakama Iyyani da har yanzu ke faman sharar hawaye tana tofama Ummu addu'a. Damar duba Ummun Kaka ya bashi dan haka ya shiga aikinsa. Ya tabbatar musu jinin Ummu ya hau matuƙa, amma zai mata allurar barci ta samu nutsuwa dan barinta a ido biyu akwai haɗari komai zai iya faruwa. Sai da suka maida Ummu ɗaki sannan ya saka mata ruwa da allurai aciki, cikin sa'a kuwa babu jimawa barci yay awan gaba da ita. Sosai Kaka yay musu godiya da sanya albarka, dan ko sisi ɗan uwan nasa bai amsaba ma....... ★★.... ★.... ★★..... An wayi gari da samun canji sosai a yanayin Iffah, dan zuwa yau kam Alhmdllh. Sai dai jikinta dake wani irin saɓa saikace wata macijiya. Sai kuma rauni data tsinci kanta a ciki sakamakon mummunan mafarkin datai akan su Babiy daya haddasa mata matsanancin faɗuwar gaba da akai-akai. Gata dai iya gata tana gani wajen tsohuwa Malikat Haseena duk da bata da lafiyar ƙafa sai a wheelchair take komai. Hakama Daneen Ammarah tsaye take kan Iffah, yanda take kula da ita yasa Iffah jin ƙaunarta batare data san dalili ba, ganinta take tamkar Ummu. Yanda ake tsaye kanta da gata da kulawa yasa ko damar yin ƙwaƙwaran tunani bata da shi, dan da tayi shiru Daneen Ammarah zata nuna damuwa taita jera mata tambayar mike damunta? Ko tamanin wani abu ne a jikinta har yanzu?. Dole take sassauta damuwarta, sai dai tayi matuƙar dagewa wajen ambaton UBANGIJI kamar yanda Babiy da Ummu suka dinga jaddada mata a nasiharsu ta ƙarshe gareta. Labarin mutuwar hadiman da suka kai mata rigar nan ta saka yazo kunenta itama, sai dai jin sanadin mutuwar tasu ya tsaya mata a rai matuƙa, harma ta rasa yaya zata fassara al'amarin... Bayan idar da sallar isha'i tana zaune tayi tagumi gaba ɗaya hankalinta ya tattara ga tunanin iyayenta da mummunan mafarkin daren jiya a kansu Daneen Ammarah ta shigo hadimai uku biye da ita. A bakin gadon takai zaune tare da kai hannu ta janye tagumin da Iffah tai. Nannauyan nunfashi ta sauke da ɗan ɗagowa ta kalla Daneen Ammarah ɗin, sai kuma ta maida kanta ta risinar da mata sannu da zuwa. Daneen Ammarah dake kallonta cikin damuwa taja numfashi ta fesar batare data amsa ba. Dai-dai nan Hadiman da suke tare suka zube gaban Iffah bayan sun ajiye kayan hanunsu. Gaisheta suke da tsantsar girmamawar da ko iya ɗaga kawunansu basayi su dubi sashen da take. Sam Iffah batajin daɗin yanda suke matan saboda bata sababa, a ranta gani take kamar ƙasƙancine. Hannu Daneen Ammarah ta kaɗa musu alamar suje, zumut suka miƙe tamkar ƙyaftawar ido suka fice. Iffah ta bisu da kallo cike da jin raɗaɗi a zuciyarta. “Ibnati!”. “Na'am Mamy!”. Iffah ta amsa cike da girmamawa ga Daneen Ammarah. Sosai sunan da Iffah ke kiranta da shi ke raunanata da sake jin ƙaunar yarinyar, dan a bakin mutum ɗaya tak take jinsa kafin ita. Taja numfashi da haɗiye hawayen da suka cika mata ido ta maye gurbinsu da murmushi. “Ibnati bana son cigaba da ganin damuwar nan a fuskarki, ki kwantar da hankalinki insha ALLAHU babu abinda zai sake samunki. Wanda ma ya sameki ki ɗauka kaddararkice kinji, amma inaji a jikina insha ALLAH kece mabuɗin nasararmu, ke ce hasken da zata haska mana duhun da muke a ciki a Daular nan kinji”. Kai Iffah ta jinjina a hankali, haka kawai take jin matuƙar nutsuwar kasancewa da wannan baiwar ALLAH, sam batajin irin zafi da tsanar da takema duk wani mai alaƙa da masarauta a kanta. Kallonta take tamkar wata katanga ta wani babban al'amari dake tunkarota. “Mamy bana tare da damuwa in har kina a kusa dani, duk abinda ya sameni kuma dama ALLAH ya ƙaddara sai ya sameni koda banzo nan ba. Ina tunanin su Ummu ne da jin tsananin kewarsu saboda mummunan mafarkin danai akansu jiya, ina tsoron kar wani abu ya samesu ne suma?”. Cike da jin tausayita Daneen Ammarah ta shafa kanta, “Duk ɗa na gari dolene ya kasance cikin kewa a lokacin da yay nesa da ahalinsa, da ace inada dama da a yau sai na kaiki kinga su Ummunki. Amma dokar masarauta ce Zawjata-almilki tana fitane kawai bisa ƙwaƙwaran dalili, zuwa gidansu kuwa tana yinsa ne sau biyu tak a shekara, ɗaya a sirrance, ɗaya a bayyane tare da rakkiyar hadimai. Shiko mafarki ai na gaskiya bane Ibnati, MANZANNI ne kawai idan suka yisa yake gaskiya a garesu, amma mu namu yakanzo da wasu sigogi ciki harda sheɗanu”. A hankali hawaye suka silalo a kumatun Iffah, bawai lokacin ziyarar bane yay mata nisa, rashin tabbacin kaiwa lokacin ziyararne ya sata zubar hawaye. Ita dake zaman jiran ƙaddarar mutuwarta taya zatai tunanin zuwan waɗan can damarmaki guda biyu na ganin su Babiy, maganar mafarki kam ta san gaskiya Mamyn ta faɗa, itama kuma ba tana dangantashi da zama tabbaci bane, kawai tana matuƙar jin tsoron faruwar wani abu ne a dalilin mafarkanta na baya.... Ganin hawayen Iffah ya matuƙar tada hankalin Daneen Ammarah, a rikice ta shiga tambayarta kamar yanda ta saba in har ta ganta a makamancin damuwar nan. Hannu Iffah tasa ta share hawayen nata da ƙirƙiro murmushi. “Mamy ki kwantar da hankalinki hawayen sunzo ne kawai da kansu babu dalili”. “Haba Ibnati, dama ana kuka babu dalili ne? Ko baki faɗaba nasan kinada dalilan yin kuka, amma idan kika zama mai haƙuri da juriya wataran ke zakiyi dariya a gaban waɗanda suka cancanta suyi kuka.” (ALLAH ya tabbatar da wannan ranar) Iffah ta faɗa a zuciyarta, a zahiri kam sai ta goge hawayen tana murmushi. Hakan yasa Daneen Ammarah yin murmushin itama, kafin kuma ta mike tsaye da kama Iffah suka koma kan dardumar da aka shirya abinci acan gefe na ɗakin, dan ɗakine ƙaton gaske mai dauke da komai na jin daɗin duniya. Tare sukaci abincin, Daneen Ammarah har tana bama Iffah wani lokacin a baki, jitake inama Iffah ɗiyartace, dan da'ace tana gidan aurenta har yanzu ɗiyarta ta fari zata iya kasancewa dai-dai da shekarun Iffah ne. Kulawar Daneen Ammarah ta sake saka sassauci a zuciyar Iffah harta ɗan saki jikinta. Bayan sun kammala ta sakata shiga bayi tai wankan maganin da take amfani da shi, data fitoma da kanta tai mata hayaƙin turare. Iffah ta hau gado ta zauna, Daneen Ammarah a gefenta da littafin tarihin annabawa acewarta zata dinga karantama Iffah har sai taga tayi barci domin ɗebe mata kewa. “Yauwa Ibnati kin shirya dai ko?”. Fuskar Iffah da ɗan murmushi tace, “Eh Mamy na” “Masha ALLAHU ashe dai Habibty na tare dani”. Hannu Iffah tasa ta rufe fuska tana murmushi, itama dai Daneen Ammarah murmushin take. Ta fara buɗe littafin. Iffah dake kallonta tai dauriyar finciko ɗaya daga ɗunmbin tabayoyin dake cin ranta ganin zata fara karatun... “Mamy dan ALLAH na tambayeki wani abu?”. “Oh Ibnati tambayeni mana kanki ma tsaye kuwa.” Iffah ta jinjina kanta da sauke ajiyar zuciya..........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 90165991 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_22_* .......Iffah ta jinjina kanta da sauke ajiyar zuciya, “Immm Mamy dama...” sai kuma tai shiru dalilin gargaɗin da zuciyarta ke mata tunda har yanzu fa Bama wai tasan matsayin Daneen Ammarah ɗin bane a masarautar. “Dama mi? Kinga karkiji komai kimin duk tambayar da kike buƙata, insha ALLAH zan kasance mai baki amsa, idan kuma bata dace ba zan baki shawara kodan nan gaba”. Kai Iffah ta jinjina “Dama dan ALLAH zance ne yanzu mutuwar su hadiman can shikenan ta tafi a banza baza'ai wani bincike a gano ba?”. Kallo na kusan sakan biyar Daneen Ammarah taima Iffah da har tama ɗauka tai laifi, amma sai taji taja numfashi da maida kanta kan littafin hanunta. “Mutuwarsu bazai tafi a banza ba saboda dalili mai ƙarfi Ibnati. Dan duk wanda ya kashesu yana gudun tonuwar asirinsa ne akan cutar da ke da akai yunkurin yi. A yanzu haka Shahanshan ya saka kwamitin bincike, muna fatan kuma ta wannan hanyar za'a gano koma wanene ya saka ki a halin da kika tsinci kanki. Kuma dama kema ana jiran ƙara samun lafiyarki ne aji ko akwai wani abu da kika sani, ko kuma bayan su ukun can da ɗayar da aka samu nasarar ceto ranta ko akwai wasu..” Da sauri Iffah ta dubeta. “Mamy akwai wadda bata mutu ba dama?”. “Eh akwai amintacciyar hadimar Umm-Jasrah (haka take kiran Malikat Bushirat) mai suna Diwa. Ita an kaita asibiti kafin gubar da suka sha ta karasa katsa ƴan hanjinta. Alhmdllh kuma an dace dan yanzu haka tana kan shan magani, tana kuma zagaye da tsatstsauran tsaro” “ALLAH ya ƙara bata lafiya, sai dai kuma banajin tanada hannu a cikin al'amarin Mamy, dan da ganinta mutiniyar kirki ce”. “Gane mutanen kirki ba'a ido yake ba Ibnati musamman a wannan masarautar da kowa kansa kawai ya sani, a mafi yawan lokuta ma ba'a gane maƙiyi da halayya. Akwai rikitattun abubuwa dake a matuƙar cuɗe a wannan Daular da gani da ido bazai wadaci mai kallo ba, dan haka nakeso ki nutsu kisa hankalinki waje ɗaya kafin ki koma sashenki ki koyi abubuwa da yawa na salon mulki da tsarin matsayinki na Zawjata-almilki. Saboda kunada matuƙar tasiri da girma a tsarin ƙarfin iko na masarauta da kaikawon talakawan ƙasan ruman. Fatana kuma kece Malikat a cikin Zawjata-almilki insha ALLAHU”. Sam Iffah bata fahimci komai ba ga kalaman Daneen Ammarah, amma sai bata sake cewa komai ba dan a ganinta tana buƙatar samun lokacin yin nazari na musamman a kansu kafin ta fahimcesu dallah-dallah....... ★★... ★... ★★.... Ana idar da sallar asuba drivern daya kawo su Kaka jiya dan hanashi komawa yay saboda dare ya ɗauka Iyyani da Ummu suka wuce. Kaka da Abu Zainab kuma sukai shirin fara neman inda zasu samo Babiy da Hanash. Dai-dai suna shiga mota kaka ya dubi Abu Zainab da ɗan murmushin ƙarfin hali a fuskarsa, “To Zakariyya kai ne ɗan gari, yanzu ta ina zamu fara kenan?”. Numfashi Abu Zainab ya furzar, tare da yin ɗan jimm alamar tunani, “E to Baba banace ba dai, dan al'amari nada wuya, saboda bamu da tabbacin waɗan nan jami'ai daga wane station suke. Amma ni yanzu a nawa shawaran ina ganin kamar mu nema gidan shi marigayi ɗin, tunda matarsa ita ta kawo jami'an tasan daga ina suke”. “Hakane, wannan ma shawara ce mai kyau, sai dai inda gizo ke saƙar kai koka san ina gidan Dawood ɗin yake? Dan ni dai rabona da shi ma kusan shekara biyar kenan tun suna tare da Muhammad Zayyan”. “Ito baba banace ba, dan kusan nima hakan dai take, amma bayan tashinsa daga anguwarmu nasan inda ya koma, sai dai bani da tabbacin ko har yanzu acan ɗin yake zaune tunda ba wani huɗɗa muke ba gaskiya, dama dalilin Abu Hanash ɗinne ake gaisawa sai kuma idan wani zama na anguwa ya haɗa kafin ya tashi kenan. Amma yanzu dai bara mu tafi can ɗin kawai rana ma nayi”. Cikin ƙanƙanin lokaci suka iso anguwar, kasancewar ma ta cika ba kamar da ba da kyar suka iya samo gidan. Duk da jikinsu ya ɗanyi sanyi ganin ƙofar gidan babu alamar anyi wani abu daya shafi mutuwa Abu Zainab yay sallama har sau uku. Ana huɗun wani mutum ya fito. Cikin binsu da kallon rashin sani ya basu hannu suka gaisa. Abu Zainab da shima dai jikinsa yay sanyi ya ce, “Kayi haƙuri nasan baka sammu ba. Muma dai munzo nan ɗinne neman wani bawan ALLAH daya zauna anan shekara kusan huɗu haka baya. Sunansa Dawood, amma ana masa alkunya da Abu Moosa. Matarsa ɗaya bashi kuma da yaro ko ɗaya”. “ALLAH sarki, gaskiya ban sanshi ba, dan nima dai ban wuce shekara biyu da tarewa anan ɗin ba. Na kuma sayi gidanne a hanun wani mutum Ibrahim Askari”. Abu Zainab zai sake magana Kaka ya girgiza masa kai alamar kar yace komai. Godiya sukai masa da sallama suka wuce. “Baba ban san miyasa ka dakatar dani ba. Dama zan tambayesa ne ko zai faɗa mana inda zamu samu shi Ibrahim Askari ɗinne”. Numfashi Kaka yaja ya fesar, “Dalilin da yasa na dakatar da kai kenan. Kasan shi al'amari irin wannan yana buƙatar kasan dawa zakai maganar abu na gaba. Inaji a jikina waɗanda suka haddasa tushen wannan matsalar dole suma zasu kasance suna bin bayanmu domin toshe duk wata hanyar da zamu iya bi. Dalili kuwa shine ina kallon lauje ne cikin naɗi akan al'amarin”. “Eh gaskiya hakane kuma Baba. To amma in har hakane mizai hana mu nema lauya, sai nake ganin cikin sauƙi shi zai iya binciko mana inda suke ma, kuma koma minene sai yazo cikin sauƙi tunda ana magana ne akan abinda ya shafi shari'a ko kuwa?”. “Itama wannan babbar shawara ce a mahangar hankali Zakariyya, sai dai shi lauyan ne matsala musanma irin mu wanda muke bukata. Mai gaskiya da amana”. “In dai dan wannan ne babu damuwa insha ALLAHU, akwai yayan matata data rasu, kwararren lauyane kuma mai nagarta da nasan zakaso aikinsa kuma zai taimakemu kasancewarsa babba. A yanzu dai nasan bazamu samesa a gidansa ba. Bara kawai muje ofishinsa”... ★★..... ★... ★★..... Kamar yanda Iffan ta nema alfarma a wajen Daneen Ammarah akan ɗakko mata akwatinta da aka kawo ta gidan dashi ya iso gareta. Taji matuƙar sanyi a ranta da farin ciki. Hadimar data kawo na fita ta buɗe akwatin ta shiga dubawa. Alhamdullah komai yana nan yanda yake, hatta takardar da malam Fawzan ya bata ɗinnan itama tana a inda ta ɓoye ta. Tana idar da sallar azhar littafin data sako a kayan nata kawai ta ɗauka da biro ta fara rubutu. Anutse take rubuta komai daya faru daki-daki tun daga barowarta gida har zuwa shigowarta cikin masarautar, abinda ya faru da ita dama wanda ke kan faruwa bayan warkewarta. Da zarar taji motsi koda ma Daneen Ammarah ne sai ta boye, a haka ta kwashe kaf yinin har zuwa dare tana abu ɗaya. Da daddare bayan kammala shirin barci maimakon kwanciya zaman karatun Alkur'ani tayi, koda Daneen Ammarah ta shigo ta sameta a hakan bata katseta ba. Tasa Hadimar dake biye da ita ajiye mata madarar da suka shigo da ita. Daga haka ta fice taja mata ƙofar da nufin ta dawo zuwa anjima, dan yanzu tana son zuwa ta duba Malikat Haseena ne da yai batajin daɗi. Iffah na ganin ta fice ta sauke ajiyar zuciya, addu'a tai ta rufe Alkur'anin ta mike, kofar taje ta sanyama key bayan ta leƙa babu kowa a corridor ɗin. Ta ɗan jingina da ƙofar tana mai ambaton “Alhamdullah” da sakin ɓoyayyen murmushi. Cikin sassarfa tabar jikin ƙofar zuwa ga akwatinta, ta buɗe tare da ɗakko wayar Arfa da takardar da Malam Fawzan ya bata. Number da aka rubuta ta kwashe a wayar, ta haye tsakkiyar gadon ta kwanta tare da jan lallausan bargon ta shige ciki har kanta sannan tai dailing number. Gaba ɗaya a kage take da zumuɗin a ɗauka. Dan haka take bin sautin shigar kiran da zuciyarta. Sai dai harta yanke ba'a ɗaga ɗin ba. Kira ta sake yi, nan ma dai shiru, bata gajiya ba ta cigaba da kira har fin sau goma kafin a ɗaga a karo kusan na goma sha biyar. Nannauyar ajiyar zuciya ta sauke tamkar wadda aka tsamo daga cikin ƙanƙara. Sai kuma tai saurin faɗin, “Assalamu alaikum”. “Wa'ake nema?”. Aka faɗa daga can maimakon amsa sallamar tata. Da lafiya lafiya ne sai tayi mitar ƙin amsa sallamar, amma sai tai saurin faɗin, “Sir Ajmaal”. “Wa'ake nema?”. Aka sake maimaita mata tambayar. Zuciyarta ta ɗan fara zabura amma sai ta danne ta sake maimaitawa itama. “Sir Ajmaal”. “Wa'ake nema?”. Still aka sake faɗa kamar dai ba'ama jita ba. Wayar ta janye a kunenta ta tashi zaune ta ɗauka takardar, number dai dake a jikice dai-dai batai mistake ba. Sake maida wayar tai kunne aranta tana faɗin (bara naga ƙarshen ku dai) ta sake amsawa da “Sir Ajmaal”. “Kin saɓa lamba”. Aka bata amsa da yanke wayar lokaci guda batare da anjira cewar ta ba...... ★★..... ★... ★★..... Kasancewar Abu Zainab suruki ga barrister cikin sauƙi suka samu ganinsa ta hanyar kiran waya. Har office yasa masinjansa daya fita yay musu iso ya shiga da su. Ganin lafiyayyen office ɗin nasa dama hukumar tasu ya sake tabbatar ma da Kaka babbane gaskiya. Sun gaisa cikin nuna sanayya shi da Abu Zainab. Ya kuma gaida Kaka da girmamawa kasancewar tsoho dama zai iya haifarsa. Basu saurari lemo da aka kawo musu ba Abu Zainab ya shiga masa bayani dalla-dalla. Sai da ya gama tsaf Barrister Abdallah dake rubuta wa ya ajiye biron yana jinjina kansa. Kaka ya fuskanta cikin son ƙarin bayani.... “Baba kaima kasan shi Dawood ɗin kenan?”. “Tabbas na sanshi yaro. Hasalima ga gidan mahaifin shi Muhammad Zayyanu gana mahaifin Dawood. Sannan ta ɓangaren mahaifiyata ma munada alaƙar jini da mahaifin nasa. Shine kuma yay sanadin zuwan Muhammad Zayyanu garin nan, shi kuma Muhammad Zayyanu ya koya masa noman zuma daya gada ga mahaifinsa”. “Eh lallai sanayya ce babba kam. Sai dai kuma inaga ya kamata nasan miya rabasu? Dan yanzu hujjojin hanunmu sune zasu taimaka mana wajen kubutar da su saboda wannan case ne babba kuma da alama shiryayye” “To nidai kai tsaye banace ga abinda ya zama sanadin rabuwar kawunan nasu ba. Dan shi Muhammad Zayyanu mutum ne mai zurfin ciki da rashin kwaramniya. Amma dai lokacin da naga bana ganinsu tare na tambayesa ko akwai matsala? Shi da abokin nasa. Sai ya sanar min shi dai a saninsa bai masa komai ba ya janye daga jikinsa, ya kuma bisa ya bisa babu adadi danya faɗa masa amma yaƙi, daga karshe ma ya tattare kayansa da iyalinsa sukabar anguwar, bai kuma sake ganinsa ba har watanni sunja a lokacin. Na bashi shawarar ya ƙara nemansa dai, da muka sake haɗuwa na tambayesa sai yace ai yama bincika yabar gari. Iyakar abinda na sani kenan gaskiya”. “Shi kuma Dawood ɗin baka sake ganinsa ba kaima?”. “Eh to gaskiya ban sake ganinsa ba. Dan ko'a rasuwar mahaifinsa sai wai-wai mukaji yazo yay gaisuwa ya tafi kawai. Daga nan kuma dai bamu sake jin ɗuriyar tasa ba dan dama mahaifiyarsa bata raye tuni”. Barrister dake faman kaɗa kai ya sake ajiye bironsa. “Uhhm yanzu to inaga mataki na biyu shine musan wane station suke. Ko kuma inda ita matar tasa take”. Cikin damuwa Abu Zainab yace, “Munje inda muke tunanin samun nata bamu sameta ba. Sai dai an ambata mana sunan wanda ya saida gidan ga wanda ke ciki yanzu”. “Miye sunan”. “Ibrahim Askari”. “Badamuwa kuje abunku, insha ALLAHU daga nan zuwa gobe za'a nema mana Ibrahim Askari ɗin. Suma kuma zan ɗan bincika ta hanyar jami'an dana sani a mabanbanta station na garin nan”. Sosai kaka ya dinga ma barrister godiya. Hakama Abu Zainab. Shi dai faɗa musu yake karsu damu. Aje a cigaba da addu'a komai zai zama labari insha ALLAHU...... ★★..... ★★.... ★★..... Iffah kamar zatai kuka ta ƙara dailing number amma sai ma aka sanar mata switch up. Wani irin zafi da lugude ƙirjinta ya shiga yi, ta shiga neman number Malam Fawzan cikin rawar jiki tunda dai shine ya bata number..........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 90165991 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_23_* ........Itama ɗin dai switch up. Wasu zafafan hawaye suka silalo a kumatun ta. Ƙoƙarin sake kiran waccan number ta gwadayi knoking ƙofar da akai ya katseta. Da sauri ta yanke kiran da kashe wayar ma baki ɗaya ta ɗaga gadon ta tusasu har da takardar gaba ɗaya sannan ta sauka dan tasan bazai wuce Daneen Ammarah ba... “Ibnati baki barci ba kenan?”. Kan Iffah a ƙasa tai ɗan murmushi. “Yanzu zanyi Mamy karatu na kammala”. “Masha ALLAH, ya kamata ki kwanta to dare yaja, nima zuwa zanje na kwanta”. “To Mamy ALLAH ya tashemu lafiya”. Koda Daneen Ammarah ta wuce Iffah ba kwanciyar tai ba, sake ɗakko wayar tayi ta cigaba da neman wancan layin da a yanzu ake cemata not available saɓanin switch up na ɗazun. Hakama number Malam Fawzan har yanzun. Daga ƙarshe dai barci ɓarawo gwanin iya sata ne ya saceta akan dole ta haƙura, sai da asuba ta tsinta wayar a ƙasa yashe.... Yau dai kam ta ƙudiri niyyar fita gaida tsohuwa Malikat Haseena da kanta, tunda dai jikinta Alhamdullah hatta saɓar ma sai inda ba'a rasa bane bai gama ba. Bayan hadimar dake gyara ɗakin ta kammala ta fita key ta sama ƙofar sannan ta shiga wanka. Dan duk da tausayin hadiman da takeji a yanzu batajin zata sake yarda da waninsu. Ta fito tana tsaka da shiryawa cikin ɗaya daga kayanta na gida akai knoking. Karasa saka abayar tayi sannan taje ta buɗe, a tare suka sakarma juna murmushi, tai ƙasa da kanta tana faɗin, “Barka da safiya Mamy”. Daneen Ammarah takai hannu ta taɓa kanta da faɗin, “Kin tashi lafiya?”. “Alhamdullah”. “Haka ake so. Ga kayanki nan na amfanin yau, mun zaɓi yin hakane saboda gudun abinda zai iya zuwa ya dawo Ibnati, amma insha ALLAH kayanki na amfani na gab da kammaluwa, saiki shirya ni zanje sashen Umm Jasrah. Ki tabbatar kinci abinci sosai yanzu zan dawo ba jimawa zanyi ba”. “Adawo lafiya Mamy a gaisheta”. “Zataji, amma ki tabbatar kin canja waɗan nan kayan”. Kai kawai Iffah ta jinjina mata. Amma a ranta tana mamakin minene aibun abayar tata? Tana cikin sabbin kayantama da take matuƙar ji da su. Shigowar hadimai biyu da kayayyaki ya katse mata mitar tata, sai dai batace komai ba bayan amsa musu gaisuwa. Fita ɗayar tai aka barta da wadda tafi yawan kasancewa da ita, tazo gabanta ta zube kanta a rissine. “Ya Zawjata-almilki bisa umarninki za'a shirya kayan”. Karo na biyu Iffah ta amsa neman izini da umarni ga hadimai a gidan. “Ba yanzu ba, zaki mun rakkiya ga Mamma ne, ki jirani a waje”. “Umarninki shi nake zaman jira ya Zawjata-almilki”. Hadimar na fita ta taka inda kayan suke tana dubawa. Tunda ta samu lafiya kullum da safe za'a kawo mata kaya kala uku, washe gari za'a kwashesu koda daya kawai ta saka a sake ajiye mata wasu. Da farko ta ɗauka ko haka tsarin masarautar yake. Sai a yau bayanin Daneen Ammarah yasa ta fahimci ita akema hakan saboda tsaro. Waɗanda ranta yafi kwantawa da su ta dauka ta saka. Ta koyi ƙyau sosai musamman da suka kasance bakake da adon stones masu sheƙi da ɗaukar idanu. Ga farar fatarta data koma ja ƙaɗan saboda saɓar datai tamkar ta larabawa ta sake fitowa. Ɓoyayyun turarenta na wajen Kaka ta ɗakko ta saka, wani irin ƙamshi mai daɗi da saka zuciya nutsuwa ya fara ratsa ɗakin... Sosai murmushi ya bayyana a fuskar tsohuwa Malikat Haseena saboda ganin Iffah akan kafafunta, takuma ji daɗin wannan ziyarar bazata data kawo mata duk da kuwa suna a sashe ɗaya ne. Iffah data kai zaune gefenta bisa tattausar dardumar da aka ƙawata falon da shi ta risinar da kai tana gaisheta da tambayarta yaya jiki?. “Alhamdullahi ƴar albarka. Yaya naki jikin?”. Malikat Haseena ta amsa da kulawa har yanzu murmushi ƙawace da fuskarta. “Naji sauƙi ai Mamma” (kamar yanda taji Daneen Ammarah na kiranta. “To Alhamdullah ALLAH ya ƙara kiyaye gaba”. Da amin duk hadiman wajen suka amsa. Malikat Haseena sallamar duk Hadiman tayi, tare da bada umarnin a shirya mata breakfast da Iffah. Hakan ya bama hadiman mamaki sosai, dan duk wanda Malikat Haseena zata buƙaci zaman cin abinci da shi ba karamin mai sa'a bane ba. Cikin ƙanƙanin lokaci kuwa aka kammala shirya komai, ita dai Iffah na kallon ikon ALLAH da tsagwaron mulki wajen wannan tsohuwa. A ranta kam tunani take shin wai idan haka matan suke waishi babban dodon nasu yaya za'a gansa kenan?. Bisa umarnin Malikat Haseena Iffah ta mike suka nufi wajen da aka shirya abincin. Zamansu dai-dai da shigowar amintacciyar hadimar Malikat ɗin ɗauke da wani ƙaramin kwano... Shigar ƙamshin turaren Iffah hancin Hadima Banou ya saka jikinta fara tsuma. Hanunta na ɗan rawa ta sunkiya zata ajiye kwanon suka haɗa ido da Iffah. Zabura tayi da sauri ta miƙe kanta a sunkuye. Iffah ma dake jin jikinta na wani irin yamutsawa ta sake kallonta da kyau, haka kawai matar batai mata ba, gata wata irin doguwar mace gandaƙaiƙai kamar namiji babu wani fasalin mata tattare da ita... Malikat Haseena da rawar jikin Hadimar ya bata mamaki itama ta tsura mata idanu. Sai dai mulki da kasaita baisa ta tanka ba. Hadima Banou dake jin kamar ta zura a guje saboda yanda take jin jikinta ta zube ƙasa, cikin rawar hannu ta fara yunƙurin haɗama Malikat Haseena abinci.. Iffah dake mata kallon nazari ta dakatar da ita. “Kinga jeki kawai”. Ai kafin ma ta rufe baki tuni ta mike zaram kamar wadda ke akan wuta. Iffah da gaba ɗaya abin ya gama ɗaure kanta ta fara haɗama Malikat Haseena abincin da kanta. Itako Malikat Haseena komai bata kawo a ranta ba game da yanayin Amintacciyar hadimar tata, saboda takan ganta a wasu yanayi daya fima hakan, dan haka ta jima da sakata a jerin masu aljanu... Hadima Banou na fita a falon ta sauke wani irin nannauyar ajiyar zuciya da kai hannu ta yarce gumin dayay sharkaf a goshinta kamar wadda ta tiƙi surfen gero. Gaba ɗaya manyan idanunta masu saka tsigar jikin mutane tashi sunyi jazur. Gefe ta koma ta zauna a ranta tana fatan ALLAH yasa har Iffah ta tafi Malikat Haseena bazata nemeta ba. A ganinta ma tai zamanta anan koda an nemetan ai sai an ganta. Wannan shawarar data yankema ranta ya sata cigaba da zama a wajen har lokacin jikinta bai gama komawa dai-dai ba.... Gaba ɗaya Iffah kasa sakewa taci abincin tai saboda kunya, ganin haka cikin hikima Malikat Haseena ta cigaba da ɗan jan ta da hira domin jan ra'ayinta, itako tana amsa mata a kunyace da tsakurar abincin. Suna a haka Daneen Ammarah ta shigo, itama dai ta nuna jin daɗinta na ganin Iffah ɗin tare da jin kaunarrta har cikin rai. Zama tai itama aka ɗora cin abincin da ita suna yar hira jefe-jefi da Malikat Haseena. Iffahn dai nata saurare kawai, sai kuma murmushi. Rabin hankalinta kam nacan wajen tunanin hadima banou da yanayin ta.... ★★.... ★.. ★★.... Kamar yanda Barrister yayma su kaka alƙawari ya samo Ibrahim Askari ta hanyar mutumin nan da suka fara zuwa wajensa. Fuskarsa cike da murmushi yake dubansu, dan tun yana can ya sanarma Abu Zainab su haɗu a office. Sai gashi kafin ya iso ma su har sun iso. Ko cikakkiyar gaisuwa basuyi ba ya fara musu bayani. “Alhamdulh an samo Ibrahim Askari, ya kuma bani cikakken adireshin Dawood ɗin, hasalima yace shiyya sayar masa da gidan daya koma ɗin. Ga adireshin gidan ya bani”. Sosai farin ciki ya bayyana a fuskar Kaka. Ya dinga jerama Barrister addu'a da fatan alkairi. Shima dai Abu Zainab yayi masa godiya, tare da ɗorawa da faɗin, “Barrister yanzu mune zamuje can ɗin? Kokuwa kai ne?”. “Mu duka babu wanda zai je Zakariyya”. Kallonsa sukai su duka, ya jinjina musu kansa da buɗe wani littafi a gefensa ya yago takarda, ɗan rubutu yay da sake ɗagowa ya dubesu. “Kamar yanda na faɗa muku mu duka babu wanda zaije. Domin ita Shari'a takanzo saɓanin hankali. Sannan bamu san nasu shiri ba, zasu iya amfani da duk wani yunkurinmu a yanzu. Dan haka nayi abinda ya dace bayan barina wajen Ibrahim Askari. Akwai wani babban police dana sani kai tsaye naje garesa, nakumayi sa'asar samunsa. Nayi magana dashi da rokonsa ya bincika mana inda zamu iya samun su, Alhamdullah kuma ya amsa, yanzu haka kiransa nake jira kamar yanda yaymin alkawarin kafin cikar awa ɗaya”. Anan ɗin ma dai farin ciki ne a fuskokin su Kaka, sai faman sauke ajiyar zuciya sukeyi..... ★... ★★.... ★.... Zamu iya cewa gaba ɗaya yinin yau Iffah ta kare shine a neman number Malaminta Fawzan da abokinsa Ajmaal. Amma abin mamaki har yamma amsa ɗaya ce layukansu not available. Gaba ɗaya tayi firingai-firingai na damuwa, duk yanda take ƙoƙarin ɓoyewa da danne hawayenta sai da suka zubo bayan ta idar da salla. Bakomai yasata shiga damuwar akan son samunsu ba sai rashin samun number Babiy da Hanash da batai ba suma. Tana son jin wani abu game da ahalinta, dan yawan faduwar gaban da take da mummunan mafarki yasa tanaji a jikinta akwai matsala. Tama rasa wane tunani zatayi, har text message ta turama Malam Fawzan akan ya taimaketa ya duba mata iyayenta amma shiru kakeji, bama tada tabbacin ya gani ko bai gani ba. Kuka taci sosai a wajen kafin ta mike tana share hawaye bisa shawarar zuciyarta. Wayar ta sake ɗauka ta sake tura sakon data turama Malam Fawzan a layin Ajmaal abokin nasa. Tana fatan ɗaya daga cikinsu yaga saƙon koda bata samu sauran biyan bukatarta ba. Jikin window ta koma ta tsaya tana mai shaƙar iskar dake busowa mai daɗi, kamar ance kalla gefe ta hango Hadima Banou can jikin filawoyin saitin ɗakin Malikat Haseena tsugunne kamar tana tona rami, sai faman waige-waige take alamar rashin gaskiya. Da farko tsura mata idanu Iffah tai, sai kuma ta zabura bisa umarnin zuciyarta. Sai da ta tabbatar wani baiga sanda ta fito a dakinta ba sannan ta fice, kasancewar ta naɗe har fuskarta da ɗan kwalin abayar jikinta yasa babu wanda ya ganeta, balle abayar jikin nata ɗaya daga cikin natane na gida data canja bayan barowarta wajen Malikat Haseena. Da ƙyar ta gane hanyar dazata ɓulla bayan, dai-dai Hadima Banou na ƙoƙarin maida kasar data tone alamar harta saka abinda zata saka. Sauri-sauri takeyi harta kammala, ta ɗago da nufin barin wajen taja ta tsaya a kiɗime ganin mutum tsaye a bayanta. Amma kasancewar ta mai shegen tsurin ido sai ta dake a zahiri tana kallon Iffah da har yanzu bata janye mayafin data yane har fuskar ba.... “K! Ubanwa ya kawoki nan?”. Ta faɗa da zaton cikin hadimai ne irinta. A hankali iffah ta karasa takowa gabanta, tare da janye mayafin ta saka idanunta cikin nata jajaye marasa ƙyan gani. Sosai hadima banou ta rikice har rawar jikinta ya bayyana. Iffah ta janye idanunta daga kanta ta maida akan ramin, “Mi kika binne?”. “Ranki ya daɗe babu komai, w... W... Wani magani ne kawai da nake son yin amfani da shi.....” “.....Shine kika shuka shi anan cikin rashin gaskiya? Wacece ke? Mi kike kullawa”. Tambayoyin sunma Banou yawa da tsauri wajen bada amsa, a take ta sake gigicewa duk da tana ƙoƙarin ƙirƙirar jarumtar dole. Wuceta Iffah tai zuwa wajen ramin, ta tsugunna da daukar iccen datai tonan da shi ta shiga sake tone kasar da Bismillah. Firrr wani abu kamar tsintsuwa ya fito a ramin yay sama. Iffah ta mike da sauri ta bisa da kallo harya bace. Juyawa tai da sauri inda Banou take, dai-dai ko tayi shirin silalewa tabar wajen ta dakatar da ita. Ƙasa tai da kanta jikinta na matukar rawa, Iffah ta kare mata kallo sama da kasa na wasu sakkani, sai kuma ta girgiza kai. “Wani asirinne haka bizne tsuntsuwa da ranta saboda son zuciya? Ko wani ya sakaki biznewar saboda ya isa? Kokuwa ke ɗin kina a cikin jinsin Mayu ne? Dan a cikin ukun nan dana lissafa dole ne a samu ɗaya tattare da ke tsohuwa”. Kuka Banou ta fashe da shi gwuyawunta a ƙasa. “Ranki ya daɗe ban fahimci abinda kike nufi ba, nifa magani na shuka ki yarda dani”. “Uhhm wato magani kika shuka, tsohuwa kalleni da kyau ki ganni banyi kama da wanda akema rufa ido ba, amma zan baki lokaci kije, zan nemeki a lokacin daya dace. Idan kika hangi gudu baki da wajen iya ɓoye min, idan cutar dani ne zagaye nake da kariyar UBANGIJINA, idan yunkurin salwantar da rayuwarkine idona biye yake dake tako ina. Shawara ya rage gamai shiga rijiya”. Da wani irin mummunan kallo hadima banou tabi bayanta da shi, ta cije baki da rumtse jajayen idanunta da karfi.........✍️ 🤔 Wannan ƴa ta Babiy ƙarfin halinta da tarar aradu sun mata yawa. Dole dai sai ta kai kanta inda za'a lamushete oh ni Balki😜. *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 90165991 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_24_* ..........Komai daya faru tsakanin Iffah da Hadima Banou akan idon Daneen Ammarah ne, dan itama tayi yunƙurin fitowar ne ganin Banou na tono a bayan windown Mamman sai ta hango Iffah na tahowa. Kasancewar ta ganta da rigar jikinta a ɗazun yasa kai tsaye ta ganeta. Da farko gabantane ya fara faɗuwa da tunani iri-iri, shiyyasa ta tsaya domin ganema idanunta. Sai dai kalaman Iffah da yanayin Hadima Banou ɗin ya sata shiga ruɗanin tunani. Idan har zata auna da hankalinta matsayin babba itama Iffah taga Hadima Banou ne shiyyasa ta fito, a yanayin Banou kuma ya nuna akwai wani ɓoyayyen al'amari na rashin gaskiya tattare da ita. To amma su maiyasa a tsahon shekaru basu taɓa ganin wannan fuskar ta Banou ɗin ba? Wacece Iffah? Anya kuwa ba akwai abinda ya kamata ta sani dangane da yarinyar nan ba?...... ★Iffah da al'amarin wannan masarauta ya fara ruɗama tunani tana shiga ɗakin dake matsayin nata yanzu ta murza key. A jikin ƙofar ta jingina da lumshe idanunta tana sauke numfashi. Ita kanta taga ƙarfin halinta yau, dan zata iya rantsewa bata san a ina ta samo wannan jarumtar ba. Idanun ta buɗe tare da riƙe ƙugu ta karyar da kai alamar nazari. In fa har ta canka dai-dai tabbas wannan hadimar mayya ce. Dan bata manta da wani labari da Iyyani ta taɓa basu ba na mayya yar Danƙo datai zamani a kauyen jumna shekarun baya. Babu banbanci da abinda taga matar nan tayi yanzu, dan da alama kurwar wani ta laso tazo ta boye a wajen. “Bahun ubancan, eh da gaske dai ashe lamushe ƴaƴan mutane ake a masarautar nan tunda ga alama harda su bayi an barbaɗa musu muguwar tambaya. Shi baƙin babban dodon nasu nacinye mutanen gari su kuma bayi nacinye junansu a cikin gida”. Tai maganar a fili cikin ƙankance idanu na alamar tunzuruwa... Murmushi Daneen Ammarah dake bakin ƙofa tsaye ta saki, dan nutsuwar da zuciyarta ta kasa mata ya sata biyo bayan Iffah, har ta kai hannu zatai knoking sai kuma ta fasa da tunanin inhar Iffah nada wani mugun nufi a kansu to baro can zata samu wani abun take aikatawa a yanzu. Dan haka ta ɗan kara kunenta kaɗan jikin ƙofar, cikin Sa'a kuwa ta jiyo mi Iffah ta faɗa saboda yanda tai maganar da ɗan zafi sai ta fita da ɗan karfi kaɗan. Ƙofar ta fasa bugawa ta koma ɗakinta da baya. Itama dai ƙofar tata ta sanyama key duk da tasan babu wanda zai shigo mata. Kai tsaye wadrob ɗin ta ta nufa, a cikin wani akwatin ƙarfe karami mai ƙyau ta fiddo waya bayan ta danna madannan sirri ya buɗe. Wayar ta shiga ƙoƙarin kunnawa tana mai rufo windows ɗin ɗakin nata. Sai da tai danne-danne kusan na mintuna biyu alamar text ta tura. Kira ne ya shigo, sai a ring ɗin karshe ta ɗaga, batare da jiran wani gaisuwa daga wancan ba cikin bada umarni tace, “Daga yanzu zuwa safiyar gobe idan ALLAH ya kaimu ina buƙatar sanin komai akan Zawjata-almilk ta uku. Idan nace komai yana nufin komai da komai”. Kitt ta yanke kiran tana wani irin murmushi tun kan ma ta samu amsar data bukaci sani. Wayar ta kashe gaba ɗaya ta sake maidata inda ta dakkota...... (🤔Wai su kowa da tasa manufar ne????) *_MALIKAT BUSHIRAT_* Zaune take hakimce kamar ko yaushe cikin kwalliya mai matukar ɗaukar idanu. Ga wani sihirtaccen ƙamshi mai ratsa zuciyar duk wani mai shaƙa na tashi. Shi kansa falon kamshinsa na musamman ne. Gefenta na dama Jasrah ce itama cikin kwalliyar, zuwanta kenan sashen sakamakon aiken data samu daga ƴar uwar tata. (Itama dai Jasrah anan cikin masarautar take aure, tana kuma auren ƙanin marigayi Tajwar Haysam ne da suke uba ɗaya. Dan kamar yanda Tajwar Haysam suke su huɗu a ɗakinsu suna kuma da ƴan uba har su kusan tara, sai dai mata sunfi yawa a ciki. Su tarannan kuma ƴaƴan mata uku ne. Mijin Jasrah shine babba a cikin ƴaƴan amaryar Tajwar Haysam da ake kira Ameera Aasfah a masarautar. Mace ce mai kirki da sanin ya kamata, jininsu kuma yay matuƙar haɗuwa da Malikat Haseena. Dan idan ka gansu bazaka taɓa ɗauka kishiyoyi bane a sanda tana raye. Yaranta biyune ita kacal, Miran Arshaan shine babba, shine kuma ɗa na takwas a wajen Tajwar Abdul-majeed, a maza kuma na uku, shine mijin Jasrah a yanzu, sai ƙanwarsa Daneen Fu'ada, a yanzu haka tana aure itama. Ƙaunar dake tsakanin Malikat Haseena da Ameera Aasfah yasa shaƙuwa sosai a tsakanin ƴaƴansu, hakan yasa Tajwar Haysam ke kallon Miran Arshaan tamkar ƙaninsa Miran Nayyar daya rasa, shine ma da kansa ya aura masa Jasrah. Wannan kenan, ALLAH yasa kun gane🥱). “Akia kince nazo amma kin kasa cewa komai? Wani abun ya sake faruwa ne?”. Numfashi Malikat Bushirat ta sauke a hankali tana kallon ƴar uwar tata da takema kallo tamkar first born ɗin ta. Kamar bazatai magana ba sai kuma ta nisa cike da kasaita. “Komai bai sake faruwa ba, sai dai ina gudun sake faruwar. Sanin kanki ne Jasrah ba lallai kosu waye su haƙura ba dan yarinyar nan ta kuɓuta a yanzun, sannan ma bayan ita akwai sauran yaran biyu da har yanzu fargaba ta hanamu kaisu turakar Saifulmalik. Kin san kuma rashin kai su zuwa nan da ɗan lokaci sai kinji an fara kace-nace”. “Hakane Akia. Amma ke mikike son cewa?”. “Zancen dai ɗaya ne shine inajin tsoro, na biyu kuma da gaske yarinyar nan ta shiga raina fiye da duk matan da aka kawo gidan nan matsayin Zawjata-almilk”. “Wlhy nima har cikin rai yarinyar ta shiga raina. Gata da tarbiyya daga ganinta, sannan itace mafi ƙanƙanta a duk matan na Son”. “Wannan yana ɗaya daga cikin abinda ya sake jan hankalina a kanta Jasrah, shiyyasa yanzu da wani tunani yazo min nace bara nai shawara da ke. Shin kina ganin naima Mamma (Malikat Haseena) magana gobe idan ALLAH ya kaimu da Saifulmalik zaije gaisheta a kusanta shi da yarinyar nan suga juna? Sai nake ganin hakan zai canja wani babban al'amari da masu mana yankan baya ke ƙullawa. Tunda kinga dai duk matansa sai an kaisu turaka yake da damar ganinsu kamar yanda kowa yasan dokar kenan ga duk Zawjata-almilk tun ƙarnin baya”. “Eh gaskiya kuma wannan tunani ne mai ƙyau Akia inhar Mamma zata amince ɗin. Dan Kinga muma a karan kammu wata hanya ce da zamu fuskanci wani abu akan shi kansa..” “Wannan gaskiya ne. Dan da gaske Jasrah a yanzu har shi kansa zuciyata rawa take ga al'amarinsa, dan abinda ke faruwa dole ne kowa ya zama abin zargi har mu kammu, ke nama takaice miki zance ni kaina yanzu ban yarda da kaina ba”. Murmushi Jasrah tai har haƙoranta na bayyana. Tace, “Kai Akia kinada abin dariya wlhy wani lokacin. To inke baki yarda da kanki ba mu kuma dawa zamu yarda kenan?. Kawai dai inaji a jikina koma minene ya kusa zuwa ƙarshe ta silar yarinyar nan tunda har ALLAH ya fara nuna musu iyakarsu suka gaza cin nasara a harin farko da suka kai mata. Yanzu dai bamu da lokaci, ki tattauna da Mamma ɗin kawai. Hukuncin data yanke sai mu karɓa kawai”. Malikat Bushirat ta jinjina kai kaunar ƴar uwar tata na sake ratsata. Koba komai idan ta tattauna da ita takanji sanyi a ranta....... ★★.... ★.... ★★..... “Wai nikam ɗazu ina ƙoƙarin shiga fada naga kamar motarki ta gitta, kinje wani waje ne?”. Shayin da take ƙoƙarin zuba masa ta karasa tare da miƙa masa. Sai da ya amsa ta koma ta zauna tana mai ɗan ɗage kafaɗunta. “Kaima kasan fita ta bata wuce wajen Akia ai Abu Harith, wlhy itace fa tai min kiran gaggawa shine ka ganni na fitan. Amma lafiya kuwa har irin wannan lokacin kuna a fada?”. “Uhm to lafiya lau za'ace, anyi baƙin bazata ne kawai ga Shahan-shan ya rigada ya shige kuma. Dole mu mukai zaman tarbarsu. Amma kiran gaggawa wata matsalar ne ta sake faruwa? Ko jikin Zawjata-almilk ɗinne dai?”. “No akan dai wadda ake cikine. Jikinta kuma Alhamdullah, idan ma ka ganta yanzu bazakace wani abu ya faru ba. Kawai dai Akia ce ke ganin ya kamata idan Shahan-shan yaje gaida Mamma gobe idan ALLAH ya kaimu Zawjata-almilk ta ziyarcesa ko hakan zai kawo wani sauyi kan abinda har yanzu muka kasa sanin kansa”. “Amma baƙwa ganin hakan wani ganganci ne? Sannan dokace fa Shahan-shan baya ganin matansa sai a turaka”. “Eh muma mun duba wannan ɗin, dan haka ma bamu wani yanke shawara ba akace sai an sanarma Mamma. Amma kai ya kake gani akan hakan. Abu Harith wlhy Akia na bani tausayi matuƙa, a yanzu har takai da kanta itama zarginsa take shi yake ɓarnar nan”. “Ya ALLAH wannan wace irin magana ce haka? Miyasa zatai irin wannan tunanin akan ɗanta. Bana jin Eshaan zai taɓa aikata makamancin hakan. Kawai dai akwai abinda yake ba daidai ba”. “Sosai kuwa. Amma insha ALLAHU ta sanadin yarinyar nan kowa sai yaci ƙaniyarsa. Dan haka kawai nakeji a jikina ita ɗin haske ce a wannan daula. Tunda har gashi ta karya tarihin farko na azzalumai”. “Haka muke fata, dan muma an tattauna akan hakan sosai jiya da yau a fada. Kusanma issue ɗin da ake kai kenan kawai yanzu a majalissa. Sai na kisan hadiman can”. “To ALLAH ya dafa mana mu da ku, ya kaimu ranar da zamu ga iyakar wannan al'amari”. “Amin my meera”. Yay maganar da wani salon kashe ido mai cike da soyayya da kaunarta. Murmushi tayi itama tana miƙewa, “Bara na kimtsa kafin ka kammala ko”. Kai ya gyaɗa mata idanunsa narke a kanta.. Tana juya baya ya bita da wani irin matsiyacin kallo mai ma'anoni da yawan gaske yana tsuke fuska da jan tsaki...... 🤦Jasrah kamar yanda ƴar uwarki ta faɗa miki kowa ba abin yarda bane yanzu🧐. ★★.... ★★..... Kamar yanda Malikat Bushirat suka tattauna da Jasrah batai ƙasa a gwiwa ba tana idar da sallar asuba ta fita daga sashenta cikin badda kama zuwa sashen Malikat Haseena. Kasancewar ta sanarma Daneen Ammarah tare suka nufi ɗakin Malikat Haseena ɗin. Itama tasan da zuwan Malikat Bushirat ɗin. Dan haka basu ɓata lokaci ba suka fara tattaunawa dan ta samu ta koma kafin gari yay haske. Da farko dai malikat Haseena ta kakkawo musu dokokin masarautar masu tsari dangane da haɗa Shahan-shan da Zawjata-almilk kai tsaye ba'a turakarsa ba. Sai dai bayanin da sukai mata da nusar da ita abinda suke son tabbatarwa yasa itama ta amince. Sai dai da sharaɗin komi ya biyo bayan hakan laifinsu zata gani. Cike da yaƙinin fatan karma wani abu ya faru suka amince. Dan haka tai musu sallama ta koma. Daneen Ammarah da tunaninta nada banbanci da na Malikat Bushirat akan wannan haɗuwa tai murmushi a ranta tana mai addu'ar samun nasara. Domin wannan yaƙi kamar natane ita kaɗai sakamakon itace kawai tasan ɓoyayyen sirrin daba kowa ya sani ba sai UBANGIJIN talikai. Fatanta shine komai yazam yana gangarowane ga faɗan karshe akan maƙiya koda ita zata rasa rayuwartane a yayin gumurzun... (Daneen Ammarah kin fara bani tsoro fa🧐😞). *_SHAHAN-SHAN_* Yau ɗin ce dai ta kasance rana da yake zuwa gaishe da kakarsa Malikat Haseenah. Irin wannan rana kuma tana zuwane sau ɗaya a kowanne wata. Sai dai idan ita ke buƙatar ganinsa ta samesa a sashensa. Amma a kowane wata yanada ranaku biyu na ziyartar kakar tasa da mahaifiyarsa. Malikat Haseena yake fara dubawa a farkon wata, Malikat Bushirat a tsakkiyar wata. Duk da fitace ta dare da ba lallai kowa ya gansa ba ya kasance cikin shiri mai ɓoye ainahinsa, ga wani ƙamshi na isassun da suka isa na tashi tattare da shi. Takunsa da ƙarfin izzarsa ya isa tabbatar maka eh lallai Shahan-shan ne da kansa. Ƙasaita jinin jikinsa ce, kamewa da isa adonsa ce, kwarjini da nutsuwa halittarsa ce.... Duk da farkon dare ne dan kwata-kwata ƙarfe takwas ne, amma masarautar tayi tsit kowa ya nutsu a inda ya dace saboda sanin wannan rana ce da Shahan-shan ke fitowa zuwa sashen Malikat Bushirat. Babu wani Hadimi dake kai kawo sai Ghazi da masu tsaro da suka tsare ko'ina fiye da kullum. Hakama sauran jama'a in ba babba mai faɗa aji ba babu wanda keda hurumin wani kaikawo a irin wannan daren dake zuwa a wannan rana saboda fitowar Shahan-shan...........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 90165991 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_25_* .......Turus Jasrah tayi ganin babu Abu Harith a inda ta barsa. Sai kuma ta nufi ɗakin barcinsa da tunanin koya shige. Nan ɗin ma dai babu alamarsa har cikin bathroom. Batare data kawo komai a ranta ba ta ɗan ɗage kafaɗa ta fito. ★Shi kuwa da tun bayan ficewarta ta ɗazun da kamar mintuna uku ya fice cikin ɓadda kama ya nufi sashen Miran Jasim. (Miran Jasim ɗane a wajen Ameera Banafsha, matar Tajwar Abdul-majeed ta biyu, shine ɗa na huɗu a wajensa, a maza kuma na biyu. Miran Arshaan ke bi masa. Sam babu jituwa tsakanin Ameera Banafsha da Malikat Haseena, ko mutuwar Miran Nayyar an dangantata da Ameera Banafsha a wancan lokacin. Sai dai da yake yaƙin sunkuru ne tsakanin matan biyu duniya bata san da haka ba. Burin Miran Jasim shine mulkar kujerar Shahan-shan tun yana ƙarami kamar yanda mahaifiyarsa ta horesa a kai, dan haka tayi matuƙar gwabza ɓoyayyen yaƙi akan marigayi Tajwar Haysam akan haihuwa har ALLAH ya bashi Tajwar Eshaan. Haihuwar Tajwar Eshaan wata ɗimuwace a nasararsu, saboda haka sun aikata abubuwa da yawan gaske na ganin bai kai ga matsayin da yake a yanzu ba ciki harda karkato da hankalin Miran Arshaan babban ɗa ga Ameera Aasfah amintacciya a wajen Malikat Haseena miji kuma ga Jasrah. Miran Arshaan sam bai biyo ƙyawawan halayen mahaifiyarsa ba, munafuki ne shima kuma yanada boyayyan nasa sirrin duk da riƙo irin na uwa da Malikat Haseena tai masa bayan rasuwar mahaifiyarsa, shiyyasa ya yarda ya haɗa kai da Miran Jasim domin kauda Tajwar Eshaan. Amma kaico UBANGIJI shi mai bawa wanda yaso ne, dan gashi dai Tajwar Eshaan ya zama Shahan-shan a daular ruman. Amma hakan baisa sun bar ƙulla-ƙulla na ganin cikar burinsu ba. ALLAH yasa kun gane🥲). Miran Jasim da dama tsumayen isowar Miran Arshaan ɗin yake ya miƙe daga zaman ƙasaitar da yay a katafaren falonsa da ya jiku da kayan more rayuwa. Juna suka tsirama ido cikin nazari dan bayan ƙullin tsakaninsu kowa nada ɓoyayyen sirri na akan ɗan uwansa. Miran Jasim ne ya fara kauda kansa ya maida hannayensa baya ya goya ya tako a sannu har tsakkiyar falon. Hakan yasa shima Miran Arshaan ɗin ƙarasa shiga suka tsaya gab da juna. “Arshaan Akh Barka da isowa”. Kai Miran Arshaan ya jinjina masa, sai kuma shima ya maida hannayensa ya goya a bayansa tare da ɗan takawa ya koma ta gefensa yana fiskantar window. Murmushi Miran Jasim yayi tare da juyowa yana kallonsa. Shima ya ɗan taka ya sake komawa gabansa. “Arshaan Akh kayi shiru, bayan kuma naga magana mai muhimmanci a cikin idanunka kamar yanda ka sanar dani ta waya”. Huci Miran Arshaan ya furzar, sai kuma ya ɗago suna kallon juna shi da Miran Jasim ɗin. “Jasim Akh akwai damuwa ne. Yanzu nakeji wajen Zawjata. A ziyarar Yaron can ta yau wajen kakarsa akwai shirya ganawa tsakaninsa da yarinyar da shashashar matar can da ban san amfaninta garemu ba tasa muka aura masa”. “What! Waye yay wannan ƙullin?”. “Bana tunanin kana buƙatar tambaya dan kasan wace gadararriyar ce zata iya yanke wannan hukuncin. Na gaji da ganin matar can a raye.” Murmushi Miran Jasim yayi da cije lips. Cikin ɗacin murya ya ce, “Ba Bushirat bace ta cancanci mutuwa. Waccan tsohuwar ce Arshaan Akh. Sai dai kuma su duka bazasu mutu yanzu ba”. “To sai yaushe?”. “Sai sunyi kuka akan gawar wancan shashashan yaron kamar yanda sukai kuka akan ta ubansa”. Karan farko Miran Arshaan ya saki murmushi. Sai kuma ya warware hanunsa da ɗage kafaɗa. “Hakan ma shiri ne mai ƙayatarwa. Yaya batun uban yarinyar da ɗan uwanta? Dan sun sami Barrister Abdullah Aas a yanzu haka”. Da sauri Miran Jasim ya kallesa. “Miyasa ban san wannan ba?”. “Saboda bashi da muhimmanci dan na gama musu talala”. “Arshaan kasan kuwa wanene Barrister Aas?”. “Duk yanda saninsa zai iya bani tsoro ai bai kai razanin sanin muɗin su wanene ba a garesa nake ji?”. “Ba ina maka magana bane akan ƙarfin iko”. “Mi kake son na sani?”. “Ba lokacin sanin tarihi bane. Kawai kayi duk yanda zakai na ganin ya dakata, su kuma a canja musu wajen zama”. “Wai miyasa muke bukatarsu a raye?”. “Saboda sune makamin da zamu juya yarinyar a ƙarƙashin ikon mu yanda muke so”. “Kenan bamu da buƙatar matar hadimin can itama, dan ta gama mana aikinmu”. “Matsalarta mai sauƙi ce. Daƙile Barrister Abdallah Aas ce mafi muhimmanci daga daren yau zuwa yinin gobe. Sai dai ina son a masa talala ta hanyar sanin inda suke kafin ya tsinta kansa a ramin damisa in har baiji gargaɗin farko ba”. Miran Arshaan ya lumshe idanu da sakin siririyar dariya idonsa akan Miran Jasim. Shima dariyar yayi da masa jinjina....... ★... ★★.... ★.... A sashen Malikat Haseenah ma an gama shirya komai na tarbarsa, tun daga kan abincin da yake ci tare da kakar tasa har zuwa tsaftar sashen ma a yau ta kasance ta musamman duk da a kullum a tsaftace yake. An shirya kalolin abinci da ƙamshinsu tun duhun magrib ya cika ko'ina na sashen har maƙwafta ma na iya jiyowa. Abincine da Daneen Ammara ta girka sa da kanta saboda kar a cutar da shi ta hanyar girkawar, sai taimakon ƙanwar Malikat Haseenah da suke kira Yumma. Gab da ƙofar fadar Malikat Haseena lafiyayyar motar da yake ciki ta tsaya, cikin rawar jiki ɗaya daga cikin Hadiman ya buɗe masa, sauran kuwa tuni sun zube ƙasa kan gwiyawunsu kawunansu a ƙasa domin girmamawa a garesa. Yaja fin mintuna biyu bai fito ba duk da an buɗe masa, sai da ya mula dan kansa sannan ya ziro ƙafarsa fara tas dake a cikin ƙyaƙyƙyawan blue ɗin takalmi mai tsananin taushi da ɗaukar ido da zai iya birge duk wani mai kallo, half cover irin na masu sarauta, kusan sakan biyar a tsakani sannan ya ƙara zuro ɗayar cike da ƙasaita. Tashin ƙamshin turarensa da takun sawayensa ya tabbatar ma Malikat Haseenah isowarsa. Da hannu taima dukkan amintattun hadimanta dake zagaye da ita nunin su fice. Har rige-rigen bin ƙofar da zata kaisu falon farko dazai fiddasu ta ainahin ƙofar sashen nata suke. A nutse tsohuwar ta ɗago idanunta ta sauke a ƙofar dai-dai shigowarsa. Tar-tar yake kallonta a cikin hasken ƙwan lantarkin daya haske falon kamar yanda itama take kallon ƙyakyawar fuskarsa dake a tsuke. Tai murmushi da jan numfashi ta fesar a hankali lokacin da yake isowa gabanta. Farin hannunta da fatar ta gama tattarewa saboda tsufa ya ɗan rissina ya kamo tare da kai tausasan lips ɗinsa ya sumbata. “Amincin ALLAH da yardarsa su tabbata ga managarcin tushe mai cike da tsaftatacciyar yabanya”. Idanunta ta lumshe a hankali da sakin murmushi a lokaci guda, sai kuma ta buɗesu tare da buɗe masa hannayenta. Rungumeta yay shima yana sakin ƙasaitaccen murmushi a karo na farko. Tsahon sakan talatin suna a haka kafin su saki juna ya dago amma bai ɗaga daga ranƙwafen ba. Hannunta ta ɗaura saman tausasashiyar sumarsa da a kallo guda zaka tabbatar da kuɗaɗen da take lashewa bazasu kasance na wasa ba. “Aminci da yardar UBANGIJI ta kasance tare da kai kaima farar yabanya abin alfaharina”. Idanunsa ya ɗan ƙankance da jinjina kansa yana murmushin da ita kawai ke iya ganinsa kai tsaye a fuskarsa kamar haka, sai ko Malikat Bushirat. Daga haka ya miƙe da ƙyau ya zauna ƙasan tattausar dardumar da aka shirya musu abinci, zama yay irin zaman sarakai da suka isa suka tumbatsa. Idanunsa ya zubama kakar tasa da murmushi ya gagara barin fuskarta, dan duk wannan ranar tanajinta rana ta musamman ne a gareta, sakamakon tuna mata da mijinta da ɗanta da takeyi da kuma tsananin ƙaunar jikan nata a yanzu. “Nannah Kina lafiya?”. “A zahiri dai lafiya nake, amma a baɗini cike nake da kewarka da ƙishirwar son ganinka a idaniyata Hafeedi”. “Uhhm!” ya faɗa da ɗan lumshe idanunsa ya buɗe a lokaci guda. “To ki koma sashena mana, in har da gaske ne kina mun irin wannan buƙatar a kusa da ke”. Yay maganar da yanayin zolaya, sai dai fuskar a kame take babu alamar hakan tattare da shi. Itama murmushi tai batare da tace komai ba dai-dai tana miƙa masa kofin data zuba madara. “Kwana biyu mike faruwa da kai?”. Yaja wasu sakanni kafin ya girgiza mata kansa alamar babu komai. Idanu ta cigaba da tsura masa har hakan ya ɗan sakashi tsarguwa ya kauda kansa gefe. Itama ɗauke natan tai gefe cikin rashin bama yanda yay ɗin muhimmanci. Sun kwashe kusan mintuna uku a yanayin shiru kafin shi ya katse hakan. “Mamy fa?”. Yay maganar a fisge tamkar yinta ya zama tilas ne a garesa. Ita ɗin ma a ƙasaitancen ta bashi amsa da “Suna zuwa”. Idanunsa masu girma da haske ya tsira mata. Kanta ta ɗauke gefe dan tasan kalmar (Suna zuwa) ɗin ce yake nemawa amsa.. Shima janye nasa idanun yay cike da basarwa da ƙasaitarsa ya ɗauka kofin data zuba masa madara...... A dai-dai nan Daneen Ammarah ta shigo da sallama hanunta riƙe dana Iffah dake cikin ƙyaƙyƙyawar doguwar rigar abaya baƙa datai matuƙar amsar jikinta, Shirine na musamman da Daneen Ammarah ta zauna domin yinsa gareta da kanta. Cikin ƙanƙanin lokaci sirrintaccen ƙamshin jikinta ya shiga rige-rigen isa hancin Malikat Haseena da mai gayya mai aiki. Shaƙar ƙamshin turaren da zaton Daneen Ammarah ce kawai mai shigowar ya sashi ɗago idanunsa, cikin Sa'a kuwa ya sauke su a kanta. Murmushi Daneen Ammarah da suka haɗa ido ta sakar masa, yayinda shi kuma fuskarsa ke nuna tsananin ƙaunar da yake mata a zahiri. Haka itama Malikat Haseena murmushi ne ƙawace a fuskarta idonta akan Iffah da kanta ke rissine taƙi kallon komai. Ƙara riƙe hanun Iffah Daneen Ammarah tai da ƙyau kamar za'a ƙwace mata suka cigaba da takowa a nutse. Malikat Haseena taima Daneen Ammarah nuni ta zaunar da Iffah a kusa da ita, sai ya zam suna facing juna da Tajwar Eshaan, sannan kuma a tsakkiyar su shi da Malikat Haseena ɗin.. Gaba ɗaya ya tattara hankalinsa ga Daneen Ammarah tamkar baiga tana tare da wata ba, “Amincin ALLAH da rahamarsa su tabbata ga Mamy na!”. Ya faɗa akan laɓɓansa kamar bashi yay maganar ba, dan ko Iffah da Malikat Haseena ba jinsa sukai ba sai ita Daneen Ammarah da takai zaune kusa da shi. itama ta sake sakin murmushi da kaɗa masa kanta. “Tare da kai Abni, Amincin ALLAH da rahama da kariyarsa su tabbata a gareka. Ina fatan kana cikin ƙoshin lafiya da nutsuwar zuciya?”. Kansa kawai ya kaɗa mata, sai kuma ya ɗan ɓata fuska. Murmushi ta sake saki da maida idanunta kan Iffah da Malikat Haseena kema magana. “Hafed-ti! An hanaki barci ko?”. A hankali Iffah da ƙirjinta ke faman harbawa da sauri-sauri ta girgizama Malikat Haseena da tai maganar kanta. Cikin sanyin murya da sauƙaƙa fitar sautinta ta ce, “A'a Mamma ai bamma kwanta ba”. “Masha ALLAH yaya jikin naki?”. “Alhamdulillahi Mamma, Aminci ALLAH ya tabbata a gareki a wannan lokaci”. “Amin. tare dake kema Negar”. Iffah ta ɗan murmusa har yanzu kanta a rissine. Daneen Ammarah dake kallonsu da murmushi ta janye idanunta ta maida ga Shahan-shan daya sake ɗauke kansa tamkar bai san mike faruwa ba ma. “Ibnati!”. Ta kira sunan Iffah a tausashe kamar yanda ta saba. “Na'am Mamy”. Itama ta amsa mata kamar yanda ta saba. Sai dai ta kasa iya ɗago kanta, dan duk da bata san wanene ba gaba ɗaya kwarjininsa ya cika falon har tanajinta a matuƙar matse kamar ta tsilla da gudu kozata samu nutsuwa.... “Ga yaro na”. Ta faɗa cikin sigar son ɓiye mata ainahin wanene ɗin. Iffah da bata damu da son sanin gaskiyar zancen Daneen Ammarah ɗin ba ta amsa da alamar raunin murya a tare da ita. “Amincin ALLAH ya tabbata a gareka. Barka da wannan lokaci”. Shiru babu alamar zai amsa mata, ran Iffah ya sosu dan a rayuwa ta mugun tsanar wulaƙanci, duk yanda taso ta danne sai ta kasa, a karan farko tun shigowarsu falon ta ɗago idanu cike da jin zafi, dai-dai ya ɗan ɗago shima zai kai kofin madara bakinsa idanunsu suka rufta cikin na juna... Zabura Iffah tayi da ware manyan idanunta, yayinda shima yay ɗan tsai yana kallonta na sakanin da basu gaza biyar ba, sai kuma ya janye abinsa cikin halin ko'in kula ko fahimtar yanayin data shiga ya sake gyara zaman ƙasaitarsa.......✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 90165991 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_26_* ........“Ya rabbi. Aljanin can dai”. Harshen Iffah da zuciyarta ke bugawa da sauri-sauri ya suɓuce wajen faɗa batare data shirya hakan ba..Malikat Haseena da furucin Iffah ya shiga kunnuwansu a bazata duk suka ɗago suka kalleta. “Ibnati! Aljani kuma a ina?”. Cewar Daneen Ammarah a mamakance”. Yawu Iffah ta haɗiya da ƙyar, sai kuma ta girgiza kanta da sauri tana ƙaƙaro murmushi. “M... M.. Mamy bance komai ba”. Tai ƙoƙarin kare kanta da rawar harshe. Magana Daneen Ammarah tai ƙoƙarin sake yi Malikat Haseena ta ƙyafta mata idanu. Dole ta haɗiye ta maye gurbinta da murmushin son basarwa. Jikin Iffah tsuma yake, amma tanata ƙoƙarin son hana fitowar hakan ta hanyar matse kanta waje guda da ambaton sunayen ALLAH a jajjere ko zata farka a ruɗanin da takema kallon gizo ko tabbacin abinda take tsoro wato Aljanin can ya cigaba da bibiyarta. Daneen Ammarah na ƙoƙarin haɗama Tajwar Eshaan abinci Malikat Haseena ta girgiza mata kai da yi mata nuni da Iffah ta wutsiya ido. Amsa mata tai cikin lumshe idanu da buɗesu akan Iffah. “Ibnati”. A ɗan zabure Iffah ta ɗago ta dubeta. Itama da idanu tai mata nuni da abincin. Sam Iffah ba fahimtar Yaren nan nasu ta cika yi ba kai tsaye, dan haka tai ɗan tsamm tana kallon Daneen Ammarah ɗin har sai da ta furta mata da baki. Numfashi ta sauke a hankali bana samun nutsuwa ba, na sake shiga ɗimuwa da kaikawon bugun zuciya, a saɓule ta motsa ta miƙe dan tayi ɗan nisa da shi, ta bayan Malikat Haseena ta zagaya ta koma kusa da shi ta durƙusa. Ta gefen ido ta ɗan sake kallonsa cike da taraddadi, cikin sauri ta kauda idanun dan abinda ta gani ɗazun ne dai ta sake gani, ta jawo numfashin dake neman kufce ma ƙirjinta da ƙyar.... “Ki haɗa masa waɗan nan”. Daneen Ammarah ta katseta ta hanyar nuna mata abinda ke cikin kwanikan gabansa.. Da ƙyar ta iya amsa mata da to, sannan ta kame jikinta dake rawa, ta ɗan duƙo zata ɗauka abu ƙamshin turaren da bazai taɓa ɓace mata ba ya daki hancinta, da alama wanda take shaƙar ne tun ɗazun ya dannesa saboda ba'ayi amfani da shi ba a yanzu ko kuma wani abu da ban. Da sauri ta ɗan ja jikinta baya jininta na tsinkewa, yanzu kam duk yanda taso dannewa sai da halin da take ciki yaso bayyana.... “Hafed-ti! Ko jikin ne?”. Malikat Haseena ta jeho mata tambayar da har shi kansa sai da ya ɗan kallesu ta gefen ido. Kanta ta girgiza mata tana ƙoƙarin danne abinda ke neman fin ƙarfinta na ruɗani. “Ina cikin godiyar ALLAH Mamma”. Murmushi Malikat ɗin tayi cikin cigaba da nazartar ta harta kammala. Sosai kanta ke juya mata, dan haka ta koma mazauninta da jan jiki tamkar ta tsala ihu ko hakan zai bayyanama kowa a wane hali take ne... Ko sau ɗaya Iffah ta kasa kai abincin bakinta, sai faman juya spoon take da satar kallon yanda yake tsakurar nasa abincin shima cike da ƙasaita. Lura da bata ci yasa Daneen Ammarah mata magana. Sai kawai tai murmushi da ɗan ɗiba kaɗan takai bakinta, juyashi take a hankali kamar mai tauna magani, dai-dai shi kuma ya ajiye nasa cokalin zai ciri tissue suka haɗa ido a karo na biyu. Da ƙarfin zuciya taso janye nata amma yaƙi bata damar hakan, sai ma jan nashi da yay cike da salo kamar zai lumshe ya sake buɗe su a tsakkiyar ƙwayar nata. Ƙwarewa tai tsabar lamarin yazo mata a bazata.. Daneen Ammarah da Malikat Haseena suka zabura kanta baki ɗaya, da kyar ta iya buɗe baki ta amshi ruwan da Malikat ta saka mata a baki, yayinda Daneen Ammarah ke faman shafa bayanta tana jera mata sannu.. A dukkan bidirin da ake idan dutse ya motsa Tajwar Eshaan ya motsa. Har tarin ma ya lafama Iffah ta samu daidaiton numfashi. Koda ganganci bata sake yunƙurin duban sashen da yake ba har lokacin tafiyarsa yay, duk yanda taso zamewa a masa rakkiya da taga Daneen Ammarah da Malikat Haseena na shirin yi hakan bai yiwu ba, dole ta bisu har waje. Tana ta faman ɗauke kanta amma tamkar wani sihiri sai da suka haɗa ido dai-dai zai shiga motar da aka buɗe masa. Wani irin karsashi da ƙwarin gwiwarta ne a bazata suka dawo jikinta, ta yamutse fuska da tsuke baki ta fincike nata.. Yayinda shi kuma ya ɗan motsa bakinsa tamkar mai son yin murmushi ko magana.... (🤔???) ★★..... Ruɗani, mamaki, al'ajabi sun taru sun hana Iffah runtsawa a wannan dare. Kanta ya gama kullewa dangane da abinda duk suka faru ɗazun. Shin mutumin nan aljanin ne da gaske? Kokuwa wani abu daban da bata sani ba. Babu abinda ke mata kaikawo a zuciya sai haɗuwarsu ta baya har sau uku, kenan idan lissafin ta yayi dai-dai shiɗin jikan gidan nan ne tunda Daneen Ammarah ta kirasa da ɗanta, kamar yanda Malikat Haseena ta kirasa da jikanta. Shiyyasa yake komai cike da ƙasaita da izzar da ko Shahan-shan ɗin da kansa iyakar wadda zaiyi kenan ai. Ita kam al'amarin wannan gida ya fara birkita mata lissafi. A lissafin ta dai Daneen Ammarah aka haifa a gidan nan, Hakan na nufin ta rabu da mahaifinsa ne? Kokuwa a cikin gidan itama take auren? Dan ita dai tunda tazo anan take ganinta babu alamar tana da wani miji ko gidan zama bayan nan ɗin.. “Ya rabbi” ta faɗa a fili tana mai jan nannauyan numfashi ta fesar..... *_WASHE GARI_* A ɓangaren Malikat Haseena ma yanda Iffan ta kusan raba dare tana juya al'amura a ranta haka itama ta raba dare wasiwasi akan abinda ta fahimta da wanda ta nazarta. Data kasa cigaba da riƙe abinda ke mata kaikawo tana idar da sallar asubahi ta bukaci ganin Daneen Ammarah. A ɗan rikice ta shigo da tunanin ko ta kwana babu lafiya ne. Ganinta zaune sumul ya sata sauke ajiyar zuciya takai zaune kusa da ita. “Wlhy Mamma hankalina har ya tashi, nayi zaton ko kin kwana babu lafiya ne”. Ɗan murmushi tai batare datace mata komai ba. Sai dai ta miƙa mata maganin da ake shafa mata a kafafu. Amsa tai babu musu ta fara shafa mata itama tana murmushin. “Ammarah mi kika fahimta?”. Ta jeho tambayar tata kai tsaye ga Daneen Ammarah. Cikin rashin fahimta Daneen Ammarah ta ɗago. “Mamma akan mi?”. “Haɗuwar Malik da Zawjata-almilk”. “Mammah har kin sakani dariya, Miya kawo wannan maganar kuma?”. “Ke dai amsa mini ita”. “Ban san mi kike son sani ba Mammah, amma nidai nasararmu da dacewarsu matsayin ma'aurata na hanga tattare da su”. Murmushi Malikat Haseena ta saki da kauda kanta. “Ni kuma ba hakan kawai na hanga ba”. Idanu Daneen Ammarah ta tsura mata batare da tace komai ba. Malikat Haseena datai shiru itama kamar bazata cigaba da cewa wani abu ba ta nisa. “A nazarin danai musu tamkar akwai sanayya tsakaninsu kafin haɗuwar jiya”. “Sanayya kuma Mammah? Idan da na fahimta sun san juna kenan kike nufi?”. “Haka”. “Haba Mammah a ina to zasu san juna? Karki manta Abni ba fita yake ba. Ƙaddara ma yana fita, wanda ke zagaye da tsaro ta ina sani da mu'amula mai ƙarfi irin wadda kike hasashe zasu ƙullu tsakaninsa da yarinya mai matsayinta. Karfa ki manta ko'a cikin gidan nan ba kowa ya san fuskarsa ba balle talakawan dake rayuwa a waje”. “Wannan shine abinda ya ɗaure kaina nima. Sai dai azuciyata na faɗamin akwai abinda yake ba daidai ba da saninmu tabbas”. “Kamar mi kenan Mammah?”. “Nima amsar da nake nema kenan”. Babu wanda ya iya sake cewa komai sukai shiru kowa da abinda yake tattaunawa da zuciyarsa...... ★★..... ★★.... ★★..... Alhamdullah Barrister yaci nasarar gano inda su Babiy suke, sai dai ba'a jiya ba kamar yanda ya faɗama su kaka har suka zauna zaman jira sai da sukaga yamma tayi babu wani bayani sannan suka haƙura suka wuce. Bai ɓata lokaci ba kuwa yay kiran Abu Zainab ya sanar masa. Shima cike da zumuɗi ya nufi gidan Babiy domin sanar ma Kaka. Sai dai kuma ya tarar yaje masallaci kasancewar lokacin sallar zuhur yayi. Dole ya shanye zumuɗin nasa shima ya tafi masallacin. Bayan an idar da salla ƙofar masallaci ya fito ya tsaya yana kallon duk mai fitowa. Daga can ciki kuwa Kaka dake a cikin mutanen da suke sahun farko sai a karshe suka sami damar miƙewa suma. Ya ɗaga zai miƙe mutumin dake a kusa da shi ya bashi hannu alamar suyi musabaha. Babu musu ya miƙa masa nasa yana ɗan murmushi. Mutumin da shima murmushin yake ya tsaida kwayoyin idanunsa a tsakkiyar na kaka, hakan yasa shima Kaka cigaba da kallonsa dan ya fahimci akwai wani abu.... “Nasan kasan girman alkairi tsoho. To karka yarda ka maida shi da sharri ga wanda yay maka. Dan haka ina baka shawarar hana waɗan can mutanen biyu cigaba da shiga abinda bai shafesu ba. Inba hakaba kuwa kai da su kuna gab da zuwa inda surukinka da jikanka suke yanzu. Na Barka lafiya”. Mutumin ya kare maganar da zare hanunsa a cikin na Kaka ya miƙe. Da kallo kawai kaka ya bisa harya ɓacema ganinsa. Kafin yaja numfashi ya fesar tare da miƙewa zuciyarsa na faman kaikawo tamkar zata fito. Koda ya fito da Abu Zainab ya fara cin karo, ya tsira masa ido na wasu sakanni kafin ya karasa garesa. Abu Zainab da shima ya hangosa cike da zumuɗi ya tarbesa, ko gaisawa basuyi ba ya rankwafa dai-dai kunnen kaka ya gwargwaɗa masa saƙon Barrister... Murmushi kaka ya saki na ƙarfin hali, sai kuma ya jinjina kansa da ambaton Alhamdullah a hankali. Abu Zainab da bai gama fahimtar yanayin kakan ba cike da zumuɗi yace, “Baba muje Barrister na jiranmu yanzu haka”. Idanu kaka ya tsira masa tamkar zai ce a'a. zuciyarsa na tuna masa girman alkairinsu garesa, tabbas bazai so saka rayuwarsu a gariri su da iyalansu ba, idan ma yaga wani zai zama sanadi zai bada karfinsa wajen karesu. Kalaman wancan mutumin sun sake tabbatar masa akwai lauje cikin naɗi game da kama su Babiy, hakama ƙin amsar Ummu a asibiti waccan ranar. Hakan na nufin kuma duk kaikawon da suke ana biye da su....... “Baba kaga gashi ma yana kirana”. Abu Zainab ya katse masa tunani. Ɓoyayyar ajiyar zuciya ya sauke, yanda Abu Zainab ya ƙagu ya sashi fahimtar bashi da isasshen lokacin tunani, zai bari sai ya samu nutsuwa ya bi hanyar data dace badan masu kurarin sunfi ƙarfinsa ba. Sai dan kawai baya son bin wata hanya daya jima da kyamatarta a ransa, amma da su ko inda yake basu isa tunkara ba balle jininsa..... *_BARRISTER_* Barrister Abdallah Aas ya ajiye wayar daya janye manne a kunensa alamar waya ya gama. Kallonsa ya maida ga sakatarensa dake ƙoƙarin ficewa saboda ganin yana waya. “Suhail”. Ya dakatar da shi ta hanyar kiran sunansa. Amsawa yay tare da juyowa cikin girmamawa. “Akwai damuwa ne?”. “A'a Sir. Wani mutum ne dai ke buƙatar ganinka. Nayi ƙoƙarin fahimtar da shi kanada uziri amma bai saurareni ba”. Ɗan jimm yay kamar mai nazari, sai kuma ya huro iska da kaɗa kai. “Okay ba damuwa shigo da shi kawai na gansa kona minti goma ne dan zan fita ne”. “Okay Sir”. A yanayin da mutumin ya shigo ya saka Barrister tsira masa ido, yakai zaune tun kan a bashi izini yana cigaba da bin office ɗin da kallo tamkar mai irge kayan cikinsa. Sai kuma ya juya ga Barrister tamkar wanda aka bama umarni ya miƙa masa hannu. Kamar Barrister zai noƙe sai kuma ya miƙa masa shima. “Am sorry Barrister nasan baka Sanni ba. Na kuma shigo kai tsaye batare da neman damarka ba” ya saki murmushi da cigaba da maganarsa batare da ya bama Barrister ɗin damar cewa wani abu ba. “Kar sani na ya zama damuwar abinda ya kamata ka sani dangane da ni, mafi muhimmanci kawai kasan miya kawo ni”. Ya kai ƙarshen maganar da ɗakko jakkar daya shigo da ita ya ajiye saman tebirin Barrister. “Waɗan nan kuɗaɗene da zasu isheka tsahon wani lokaci kana amfana, ina son ka manta da zancen aikin da surikinka ya kawo maka, idan son samu ne ma daga yau ka dakatar da shi shiga abinda bai shafesa ba”. “Duk akan wane dalili zanyi hakan?” Barrister da ɓacin ransa ke yunkurowa ya faɗa cikin son dannewa. “Ba dalilin ya kamata ka sani ba. Ƙin bin shawarar ne matsalarka Barrister”. Cikin bayyanar fushin Barrister gaba ɗaya akan fuska ya yunkuro zaiyi magana ring ɗin wayarsa ya dakatar da shi hakan. Atare suka kalli wayar sannan suka kalla juna. Wayar mutumin ya nuna da sakin murmushi, “Bismillah”. Barrister yaja ƙaramin tsaki da hararsa tare da kai hannu akan wayar dake cigaba da ɓurari.........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 90165991 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_27_* .......“Assalamu alaikum”. Ya faɗa a daƙile saboda rashin sanin wanene. A maimakon amsa masa sallamarsa aka ambaci sunansa tamkar a lokacin ake raɗa masa shi. “Barrister Abdallah Ibn Adam Aas! Kar kayi taurin kai, dan zaka iya rasa kanka dama waɗan da kake yunƙurin taimakawar. Ni umarni nake baka ba shawara ba kamar shi, domin hatta iyalanka ba zasu tsira ba daga tarko na”.. Ɗan zabura Barrister yay tamkar wanda cinnaka ya ciza. Daga can aka cigaba da magana cike da isa. “Suna hanyar zuwa gareka, ya rage naka tun yanzu ka raba gari da su, ka kuma gargaɗi surikinka. Na barka lafiya”. Yana kokarin yin magana ƙitt aka yanke kiran. Ciro wayar yay da sauri daga kunensa, ganin ta yanke yay ƙoƙarin kiran number... Mutumin dake tare da shi ya miƙe yana dariya. “Barrister shawara karma ka wahal da kanka dan basake samunsa zakai ba har abada in har a wannan layin ne. Na barka lafiya”. Da ƙyar Barrister ya kwato numfashinsa gab da mutumin zai fice. Cikin jarumtarsa ya dakatar da shi a ɗan tsawace. “Ni kurari ko gizago basa firgitani ai. Dawowa ka ɗauka trash bag ɗinka zai fi maka alkairi fiye daka barta anan ta zamewa rayuwarka BAYA DA ƘURA. wannan shawara ce”. Har cikin rai maganganun Barrister sun sokesa. Amma kasancewar sa ɗan hannu a iya bariki sai ya saki murmushi. Batare da yace komai ba yay salute ɗin Barrister dake masa kallon ƙasƙanci yay ficewarsa. Baya Kaka da Abu Zainab dake yunƙurin shigowa office ɗin suka ja dan kaɗan ya rage suyi gware. Suna masa sallama bai ko amsa su ba yay musu kallon ƙasa da sama yay wucewarsa. Basu damu ba, dan daga ganinsa kaga babban mutum. Barrister da aka bari da juyawar kai ya amsa musu sallama cike da son danne ɓacin ran dake a fuskarsa. Sun gaisa da mutuntawa kamar yanda suka saba. Fuskar Kaka da ɗan murmushi ya ce, “Ashe kuma an dace da sanin inda suke?”. Murmushin ƙarfin hali Barrister yayi da jinjina kansa, ya jawo wani file dake gefensa. “Nima banyi tunanin abin zai zo mana da sauƙi haka ba Baba. Amma Alhamdullah addu'a bata faɗuwa ƙasa banza. Inaga muyi azamar zuwa ma kar'a samu wani tazgaro kuma kasan halin ƙasar tamu”. Daga Kaka har Abu Zainab sunyi na'am da hakan. Duk suka miƙe babu ɓata lokaci suka fice kowa da abinda ke masa kai kawo a cikin rai musamman Kaka da Barrister..... *_MASARAUTA. (MALIKAT BUSHIRAT_* Cikin zumuɗin son jin yaya haɗuwar Shahan-shan da Zawjata-almilk ta kasance a jiya Malikat Bushirat tai shirin ziyartar sashen Malikat Haseena a yau. A ƴan rakkiyarta har da Jasrah dake son sake duba jikin Iffah. Tuni ƴan leƙen asirin cikin hadimai sun kwasa zuwa sassan iyayen gijinsu kuwa. Dan wannan ya zama kamar al'ada a masarautar kowane ɗan leƙen asiri kan kai wa uwargijiyarsa ko uban gidansa duk wani motsin wani babba a daular. Ta wannan hanyar ne a mafi yawan lokuta abubuwa ke yaɗuwa kunnen duk wani mai faɗa aji na gidan musamman abinda ya kasance na sirri. Malikat Bushirat ta samu tarba ta girmamawa ga surukar tasu a fadarta. Tuni hadimai sun cika gabansu da kayan motsa baki. Kasancewar ganawar ta shafi wani yanki na ɓoyayyen sirrinsu duk wani hadimi aka sallamesa. Katafaren falon ya kasance daga Malikat Haseena sai Malikat Bushirat da Jasrah sai Daneen Ammarah. Tattaunawar ta jasu tsahon lokaci kafin Malikat Haseena ta aika amintacciyar hadimarta Banou kiran Iffah.... ★Sam Iffah dake cikin wani yanayi na tsananin faɗuwar gaba da sanyin gaɓɓai sakamakon mummunan mafarkin da tai akan su Babiy a barcin zuhur daya figeta bata san mi ake ba saboda bata fita ko'inaba yau iyakarta ɗakinta. Yanzu hakama da aka idar da sallar la'asar tana tsumayen Daneen Ammarah ne kamar yanda ta saba, dan duk yinin yau ma basu haɗu ba tun bayan idar da sallar asuba dai data fita ta gaishesu kamar yanda ta saba ita da Malikat Haseena. Hadimai dai sun kawo abinci tare da saƙon gaisuwa daga Daneen Ammarah ɗin ɗazun da rana akan cewar tana nan tafe. Malikat Haseenah ma kullum da kanta takan zo ta duba ta, kasancewarta tsohuwa mai dattako da iya zama da mutane tuni ta shige zuciyar Iffah itama, dan duk da bata da sakewa da yawan fara'a har dan jan Iffah take da hira. Sallayar datai sallar ta linke har yanzu jikinta a sanyaye ga damuwa fal ranta akan iyayenta, acan ƙasan zuciyarta takeji akwai wani mummunan abu dake sake tunkarota koma ya riga ya iso garetan ta hanyar iyayenta batare data sani ba. Yanayin ɗan zafi da ake ya sata yaye mayafin abayan data naɗe kanta da shi ta ajiye, ɗaurarren dogon baƙin gashinta dake reto a tsakkiya ya bayyana. Abincin da aka shirya mata tun ɗazun da bata ci ba ta nufa, ta bubbuɗe taga komai, batama jin cin komai har yanzun, dan haka ta tsiyayyi madara kawai da shanta tamkar al'adar ƴan ƙasar ne. Tana buƙatar fara canja kayanta zuwa marasa nauyi, dan haka ta ajiye kofin madarar a bedside drawer. Toilet ta fara shiga ta fito sannan ta shirya cikin wata yar yololuwar rigar mara nauyi mai zubin shimi. Iyakar rigar gwiwar ta ne, gata kalar fari da adon jajayen firanni. Ta matuƙar haskata da fidda ƙuruciyarta tamkar ƴar budurwar balarabiya. Turarrukan da Daneen Ammarah ta tule mata ta zaɓa kusan kala uku ta fesama jikinta. Cikin nutsatstsen takunta ta dawo saman gadon tana mai kallon fatar hanunta dake jajir saboda saɓar da tayi. “ALLAH dai ya isana wlhy” ta faɗa cike da halin tsiwarta tana jan bargo ta rufa iya cinyoyinta bayan ta jingina jikinta da fuskar gadon. Littafin da take rubuce-rubucenta na duk abinda ya faru ta ɗauka ta buɗe ko zata ji sassaucin tunane-tunen da zuciyarta ke mata marasa daɗi akan iyayenta, dan sam mafarkin nan yaƙi barin ranta koda na sakan ɗaya... A zahiri rubutun tai shirin fawara, dan yanda ta tsurama littafin ido da riƙe biron da nutsuwa matuƙa zai saka ka hasashen haka. Sai dai sam ko kalma biyu ta kasa rubutawa tamkar ma an mata wankin ƙwaƙwalwa komai ya gudu, hasalima nisan da tai a tunani yasa bibbiyu take ganin rubutun baya da tayi.... Knoking ƙofar da akai ya sata jan numfashi ta fesar, sai kuma taja mayafin dake gefenta ta yane jikinta har saman kanta tare da amsawa da “Yes! Kowaye ya shigo”. A ɗarare hadima banou ta shigo, tsananin tsoron Iffah shimfiɗe akan fuskarta ya kasa boyuwa. Daga bakin ƙofar ta zube muryarta na ɗan rawa kamar yanda jikinta ke tsuma. “Amincin ALLAH da lafiya su tabbata ga Zawjata-almilk”. Harara Iffah dake kallonta ta zabga mata. “Ina tare da masu lashe kurwar mutane irinku lafiyar zata tabbata a gareni? mtsoww!! Malama faɗi abinda ya kawoki bana son gulma”. Ƙasa Banou ta sakeyi da kanta muryarta na rawa, dan harga ALLAH tana shakkar wannan yarinya da ko magana gatsau take yinta babu alamar shakku tattare da ita. “Uhm uhm dama Malikat ce take buƙatar ganinki”. Hannu kawai Iffah ta ɗaga mata, dan har cikin rai ta tsani matar nan matuka. Sai da ta miƙe zata buɗe ƙofa sannan tai magana a gadarance. “Ki jirani a ƙofa, saura kuma kafin na fito ki lashe mun hadimai azzalumar bamza”. Da rawar jiki data harshe Banou tace, “Hakan bazata faru ba ranki ya daɗe”. “Uhm munafuka kamar gaske”. Iffah ta faɗa tana sauka a gadon cikin mita...... ★Tunda suka shigo ko sau ɗaya Iffah bata iya ɗaga kai ta kalla ko ɗaya a cikinsu ba. Saɓanin su da duk suka zuba mata ido cike da jin ƙaunarta a rayukansu. Cike da nutsuwarta ta karasa garesu, maimakon kujera da duk suke zaune sai ta kai ƙasan lallausan dardumar... “Haba Ibnati tashi ki hau sama mana”. Jasrah tai yunƙurin dakatar da ita. Kai Iffah ta girgiza da ɗan murmushi a fuskarta, “A'a nanma ya isa”. Cike da sha'awa da jin daɗi duk suke dubanta. Ta juya ta gaishe da Malikat Haseena, da fara'a da kulawa ta amsa mata tana mai sanya mata albarka. Cikin jin daɗi ta juya gasu Malikat Bushirat ta gaidasu suma. Suma da kulawar suka amsa mata, dan duk ƙasaita da jin kan Malikat Bushirat sai ta tsinci kanta da murmushi da sauƙaƙawa akan yarinyar saboda kwarjini da tai mata. Shiru na wasu ƴan sakkani ya biyo baya, kafin Daneen Ammarah ta katse shirun ta hanyar kiran sunan Iffah. Ta amsa mata da girmamawa sai dai bata iya ta ɗago kanta ba. Daneen Ammarah ta sake kiran sunanta da faɗin, “Kinga ɗago ki kallemu”. Da ƙyar ta iya dauriyar bin umarninta. Dan duk rashin jin Iffah tana da wani hali na girmama duk mai nuna mata ƙauna koda bai cancanta ga sauran mutane ba. “Ibnati nasan nan zuwa yanzu duk kin sammu ko?”. “Eh Mamy”. “Amma baki san matsayinmu ba?”. Nanma tace “Eh Mamy”. “To Alhamdullah yau duk zaki sani. Ina son ki bani dukkan hankalinki nan ki kuma saurare ni yanda ya kamata”. Ta jin jina mata kai. “Kamar yanda nasan kikaji Mamma a garemu mahaifiya ce, itace ta haifi Hama (Suruki) ɗin ki, da ni dama wasu biyu da zaki sani anan gaba sai dai ɗaya ya rasu”. “ALLAH ya gafarta masa”. Ta faɗa cike da rauni. A tare suka amsa mata da Amin. Daneen Ammarah ta ciga da faɗin, “Wannan da kike jin ana kira Malikat Bushirat itace Hamah (Suruka) ɗinki data haifi Shahan-shan na yanzu kuma mijinki da yazo nan jiya......” A razane Iffan ta waro idanu ƙirjinta na wani irin harbawa kamar zai wantsalo. Cikin subutar baki ta ce, “Shahan-shan! Na jiy.....” sai kuma tai shiru ta haɗiye sauran maganar saboda tuna a inda take... “Kin sanshi ne kafin jiya?”. Malikat Haseena dake nazartarta ta jeho mata tambayar a bazata. Da sauri Iffah da zufa ta jiƙema dukkan jiki, ta girgiza kanta. Kasancewar ta gwanar wayo tai saurin faɗin, “Mamma ina mamaki ne dai, ban zaci ganin Shahan-shan ɗin nada sauƙi kamar haka ba”. Kusan a tare suka saki murmushi saboda hango tsantsar ƙuruciya a maganar tata. Sai dai malikat Haseena tsaf ta gama karantar Iffah waskewa tai. Amma kasancewar ta tsohuwa mai dattako sai ta dake itama ta shiga jerin ƴan murmushin.. Daneen Ammarah ta cigaba da faɗin, “Wannan ƙanwa ce ga Malikat Bushirat, Khaalah (Aunt) ga mijinki. Na baki ne a dunƙule iyamu da muke anan saboda muhimmancin abinda zakiji a yanzu”. Kai Iffah ta jinjina mata da alamun gamsuwa. Jasrah ta cigaba daga inda Daneen Ammarah ta tsaya. “Ibnati dalilin miki wannan dogon sharhin a kammu shine fara aikinki matsayin Zawjata-almilk a wannan masarauta. Alhamdullah tunda kinji sauƙi zaki koma sashenki kamar sauran Zawjata-almilk guda biyu, sai dai zaki samu horo daga wasu amintattunmu matsayinki na Zawjata-almilk. Mun zaɓeki ne saboda nutsuwarki da tarbiyyarki. Basai mun zaman sharhi akan abinda ya faru ba a baya kasancewar kema ƴar kasa ce kin san komai na dangane da mutuwar matan Shahan-shan da suka gabata.” Iffah ta haɗiye kududun baƙin cikin daya tokare mata maƙoshi akan famin rasa ƴan uwanta da tai da ƙyar ta jinjina kanta. Malikat Bushirat ta amshe da cigaba da faɗin, “Ibnati kece zaki zama mutum ta farko a rayuwa da zan nema alfarma a gareta, hakan kuma ta faru ne saboda jinki da nake a cikin raina da kallon da duk muke miki anan matsayin wani haske da insha ALLAH zai haska mana duhun da muke ciki. Muna son ki shiga jikin Saiful-malik domin binciko mana ainahin minene matsalar, saboda dukkan waɗan can matan da aka rasa daga kaisu turakarsa ne ake samun matsalar. Mun miki alƙawarin baki dukkan kariyar da bazamu bari ki cutu ba....” (Kariyar UBANGIJINA zata kasance tare da Ni). Iffah ta ayyana a zuciyarta. Malikat Haseena ce ta cigaba da faɗin, “Zamu fara ne da matakai da hanyoyin dinga haɗuwarku daga nan zuwa wani lokaci, fatanmu ki zama mai saka ido a dukkan wani motsinsa, a karan kansa, da duk wasu wanda zasu mu'amulancesa har a cikin hadimai. Kiyi takan tsantsan, dan mutum ne shi mai wayo matuƙa, sannan mai wahalar sha'ani da fahimta. Ba'a gane mi yake nufi ko minene a ransa akan fuskarsa, kar ki yarda ki bashi wata damar da zai iya zargi a kanki. Fatanmu dai ki zama jaruma a dukkan al'amuransa dama na kowa dake a wannan masarauta, duk abinda kikaci karo da shi ba dai-dai ba kiyi maza ki sanar da ɗaya daga cikinmu”. Zantukan nasu ya saka zuciyar Iffah dinga tsalle-tsalle a kan dalilai biyu.......✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_28_* ........Na farko ji a ranta UBANGIJI ya amsa mata addu'ar ta akan burin data shigo da shi Daular ruman. Na biyu minene dalilin waɗan nan mutane na buɗe mata cikinsu?. Na ƙarshe da yafi kowanne razani da ban mamaki a ƙwaƙwalwarta dama suma sun san shike aikata kisan kenan? Amma suka zaɓi yin shiru saboda ba ƴaƴansu ake halakawa ba kokuwa suma tsoronsa sukeji? A ɗan ƙaramin tunaninta tanaga zasu iya yin amfani da ƙwanji wajen sanin mi Shahan-shan ɗin ke aikatawa musamman Malikat Haseena da Malikat Bushirat. Amma miyasa suka zaɓi yin amfani da ita? Kodai sun gama gane manufarta ne a kansa.....? “Ibnati!”. Daneen Ammarah ta katseta daga nisan da tai a tunani ta hanyar kiran sunanta da taɓata. Firgigit kuwa ta kawo ajiyar zuciya. “Karki kasance a dogon nazari, manufarmu ta sakaki a wannan sabgar tana da nasaba ne da dalilai biyu. Na farko juriyarki ta bamu ƙwarin gwiwar kallonki a jaruma. Na biyu jinki wata abu mai muhimmanci da muke fatan nasara ta dalilinta kodan tsallake tarkon masu aikata wannan ɓarna da kika tsallake a harin farko da muke jin shine lagon da aka dinga ɗanawa a farko wajen salwantar da rayukan da suka gabata....” “Mamy nima zata yuwu bana tsallake bane dan nafi ƙarfinsu, maybe na tsallake ne saboda tsayawarku da fatanku akan ganin na tsallake ɗin. Amma tabbas zan iya sadaukarwa, zan kuma iya bin umarninku badan inajin ƙarfina ya kai ba sai dan kun isa ku bani umarni”. Su dukansu kalamanta sunyi wani tasiri na musamman a zukatansu tare da ƙawatata a cikin idanunsu. A wani gefen sunyi amanna irinta ɗansu ya dace ya samu tun farko, dan ƙarfin gwiwarta sunyi dai-dai da Zawjata-almilk da akafi buƙata ga kowane Shahan-shan. Sannan Malikat da sukema kansu fata. “ALLAH yay miki albarka”. Suka faɗa kusan a tare su duka huɗun. A kan laɓɓanta ta amsa da amin. Sun cigaba da tattaunawar da gaba ɗaya ta saka Iffah cikin ƙagara, ƙagara mai nasaba da shiga ruɗanin wani furici daga Daneen Ammarah. Wai jiya Shahan-shan ne wanda ya ziyarcesu a wannan falon, tana buƙatar samun filin tunani dan zuciyarta da ƙwaƙwalwarta fa gaba ɗaya sun kulle, ruɗani ya gama mamaye duk wani hangenta da dama bai wuce iya tsayin ƙafafunta da shekarunta ba.... ★★.... A hankali ta maida ƙofar ta rufe tare da jingina a jikinta ta lumshe ido da sauke numfashi tamkar mai kokawar jawosa. Shin murna zatayi a wannan gaɓar ko kuwa shiga ruɗani?. Idan ance Shahan-shan ne a jiya ta yarda, shi kuma wanda tai gamo da shi a mabanbanta wajeje kafin shigowarta masarauta wanene shi?. Wannan tambaya tafi kowace tambaya girma da girgiza zuciyarta a duk abubuwan dake cin ranta. “Kai nifa nama ruɗe wlhy”. Ta faɗa a zahiri tana zamewa cikin sarewa ta zube ƙasa. Ta jima a wajen cikin halin shiru da ambaton hasbinallahu wa ni'imal wakil ko zata samu dai-daiton komawa cikin hankali dan da gaske komai na halittarta mai motsi ya raunana da rauni mafi ban tsoro da shiga ruɗani. Tsahon lokaci ta kwashe a wajen tana kokawa da raunin zuciyarta da rashin ƙarfin gudanar jini. Fahimtar wancan tunanin na buƙatar lokaci ya sata turesa ta maida hankali akan tattaunawarsu da su Malikat. Tabbas wannan shine babban ƙudirinta dayin ƙundunbalar juriya na tunkarar rayuwar da bata da tabbacin tsallakewa. Duk da tasan anfi ƙarfinta, dama duk wani mai ƙarfi da take kallon ƙarfinta ta zaɓi fuskantar mutum mafi girman iko da tsaro domin ɗaukar fansa. A kwanakin da suka gabata na kasancewarta cikin wannan daula ta fara fidda ran samun cikar burinta saboda dalilai masu yawa. Ciki harda rashin samun koda ƙanƙanuwar ƙofar sanin minene ma daular ruman ɗin ta ƙunsa balle Shahan-shan da kansa. Sai gashi a yau cikin sauƙi an buƙaci kaita inda zuciyarta ta fara raya mata zuwansa ba ƙaramin tsalle bane da ba'a da tabbacin fita idan an shiga, aka kuma sanar mata wani yanki na sirrin daular ruman mai girman gaske da ko na ciki basu san da shi ba ƙila. “Anya babu wani abu a ran mutanen nan saɓanin abinda suka faɗa?” bakinta ya furta a zahiri cikin sake dulmiya a ruɗani. (Koda akwaisa yardar ki dasu ce zata baki ilimin sanin hakan) zuciyarta ta faɗa cikin ƙarfafata da ture raunin dake neman rinjayarta.... Knoking ƙofar daya wanzu a dai-dai lokacin ya sata jan numfashi a sauƙaƙe. Da ƙyar ta iya miƙewa daga zaman daɓaron da tayi ta buɗe. Daneen Ammarah ta sakar mata murmushi. Cikin yaƙe ta mayar mata da murtani da matsawa ta bata hanya. Rissinawa hadimar da suke tare tai ta gaisheta, hannu kawai ta ɗaga mata alamar amsawa tana bin ledar hanunta da kallo...... ★★.... ★.... ★★..... Kamar yanda aka sanar da Barrister kai tsaye station ɗin da akace su Babiy suke suka nufa. Kasancewarsa babba kuma sananne basusha wahalar ganin ogan station ɗin ba kai tsaye. Sunyi gaisuwa irin tasu ta manyan ma'aikata, su kai kuma gaisuwar girmama juna da su Kaka. Barrister ya gabatar da kansa, ya kuma gabatar da abinda suke tafe da shi harda hoton su Babiy domin sauƙaƙawa. Jami'in yay shiru yana kallon hotunan kamar mai hasashe, sai kuma ya ɗago ya kalla Barrister “Gaskiya banajin akwai waɗan nan mutanen a wannan station ɗin Barrister”. Barrister daya fahimci matsala ce ke neman shigowa yay ɗan murmushi da muskuta zamansa. “Yallaɓai adai sake dubawa, zata iya yuwuwa ko akwaisu ɗin baka da labarin hakan. Amma tabbas suna a wannan station ɗin. A matsayina na Barrister ba nazo nan dan a bani belinsu bane ba, duk da nasan basu da hannu a abinda ake zarginsu. Nazo ne dan na gana da su, sannan a miƙasu kotu saboda nasan dai ita matar data saka aka kawosu nan burinta a kwatar mata hakkin mijinta”. “Iya gaskiyata nake faɗa maka Barrister babu waɗan nan mutanen a wannan station ɗin. Amma mizai hana ku sami ita matar na tabbata tunda tare da ita akaje tasan wane station ne”. Barrister yay shiru yana kallonsa cike da nazari. Hakama Kaka da Abu Zainab. Kusan minti biyu shiru babu wanda ya motsa, kafin Barrister ya miƙe yana ɗan murmushi ya bashi hannu. Suma su Abu Zainab miƙewar sukai... Da kallo ya bisu har suka gama ficewa, ya kai hannu kan wayarsa dake saman desk ɗin sa yana wani murmushi. A bugu biyu aka ɗauka wayar daya kira. Sallama kawai yay da faɗin, “Kamar yanda kai hasashe ranka ya daɗe yanzu suka bar office ɗina”. Shiru yana sauraren mi'ake faɗa daga can, sai kuma yay murmushi da amsawa da “Angama ranka ya daɗe”. Daga haka ya ajiye wayar yana wata ƴar iskar dariya... Abu Zainab daya kasa fahimtar komai saɓanin Kaka da Barrister dake hangen wani abu dalilin kashedi da akai musu kafin zuwansu nan dama ya katse shirun da motar ta ɗauka ta hanyar nisawa. “Anya kuwa wannan jami'in akwai gaskiya a maganarsa Barrister. Kagafa yanda yake ƙyaf-ƙyaf da idanu kamar tsohon ɗan jari hujja. Nifa wannan al'amari ya fara bani tsoro wlhy”. Barrister da zuciyarsa ke kai kawo ya fesar da huci, “Kana tunanin yaƙi faɗa mana gaskiya ne Zakariyya?”. “Fuskarsa ta nuna hakan ai Barrister, ko kuwa Kaka?”. Kaka da shima dai yake aune-aunensa a rai ya girgiza kansa. “Zata iya yuwuwa gaskiyar ya faɗa, sai dai kumin wani taimako ɗaya dazai warware mana gaskiyar tasa ko saɓaninta, bayan nan zan sanar muku abinda ya faru kafin zuwanmu nan”. Barrister da shima abinda ke'a ransa kenan ya ɗan juyo ya kalla kaka ta madubi, “Muna jinka Baba”. “Muyi gaggawar isa gidan Dawood”. “Shawara mai ƙyau Baba”. Barrister ya faɗa yana juya motar hanyar da zata kaisa gidan Abu Moosa. ★★... ★★... ★★... “Mamy kuma duka wayar da lap-top ɗinne nawa?”. Iffah ta faɗa da mamaki. Murmushi Daneen Ammarah tayi, “Ibnati wannan ai ba komai bane ba, sannan ko baki faɗa ba kina buƙatar su tare da ke kodan ki dinga jin motsin gida. Na biyu kuma wannan aikin da zaki fara kowa yasan mai haɗari ne, dolene ki kasance da waya a duk inda kike a masarautar nan. Da zarar Kinga abinda zuciyarki bata kwanta da shi ba a cikin mu huɗun zaki iya kiran kowa ki sanar masa. Lap-top kuwa ni naga ya dace na kawo miki ita domin ɗebe kewa. Amma kiyi taka tsantsan ki kuma kula sosai, dan samun waɗan nan na nufin zaki iya mu'amula da kowa musamman a yanar gizo batare da kin samu tabbacin wanene ɗin ba”. “Haka ne Mamy, insha ALLAH zan kiyaye. Nagode sosai ALLAH ya saka da alkairi”. “Karki damu kin cancanta ne ai”. ★Iffah ta daka tsallen murna bayan ficewar Daneen Ammarah, harda ƴar rawarta. Duk wani tunani da kaikawon da zuciyarta ke mata akan Shahan-shan zuwan wannan waya da lap-top ya kauda mata shi. Domin a ganinta dama biyu ce tazo mata a lokaci guda kuma zata damata ta yanda dole sai Shahan-shan ya shata. Yanzu dai abu na farko da zata fara shine malam Fawzan. Ta tura masa saƙo bayan nemansa da tai shi da abokinsa wayar Arfa dake hanunta ta mutu ba caji, tana buƙatar tasan ko yaga saƙon? Ya kuma iyayenta suke?. Samun wayar da caji yasa tun a daren ta haɗata, duk da taga akwai sim card batai amfani da shi ba ta cire na Arfa ta sanya. Tamkar jira saƙon Malam Fawzan ne ya fara shigowa, jikinta har tsuma yake wajen buɗewa. Batako kai ƙarshen karantawa ba kira ya shigo. Gabanta ne ya faɗi ganin baƙuwar lamba, amma tsabar ƙarfin hali sai ta ɗaga. “Sir!”. Ta faɗa cikin gwalalo idanu da nufar ƙofa da sauri ta saka key. Daga can aka amsa mata da “Na'am Fareedah. Ina kika shiga haka? Tun bayan ganin saƙonki na kasa samunki, har zuciyata ta karaya da ko wani ya gano ki ne?”. “Babu wanda ya gano ni Sir, akasi aka samu wayar ta mutu, na kuma rasa ta yanda zanyi cajinta dan na manta da cajan a gida”. “Ayya. Kin ganni akoda yaushe cikin gwada wayarki nake koza'a dace. Saboda ke na samar da wannan layin na sirri. Yanzu ma gwadawa kawai nake amma banyi tunanin samunki ba sam”. Iffah ta share hawayen da suka silalo mata tana ɗan murmushi. “Nagode Sir, koda banyi nasara ba bazan taɓa mantawa da kai ba. Ina fatan ka bincika min su Ummu. Dan sam na kasa samun kwanciyar hankali na rashin jin su”. Ɗan jimm yay kamar mai tattaro abin faɗa, sai kuma yay ɗan murmushin basarwa. “Suna lafiya dan har gida naje, sai dai ban samu shiga ba kasancewar suna tare da tsaron dakarun masarautar har yanzu. Amma nayi ƙoƙari mun haɗu da Hanash....” “Amma miyasa wayoyinsu basayi?”. Ta katsesa a ƙagauce. Da ƙyar ya iya tattaro abin faɗa a wannan gaɓar ma. “Shi Babiy wayarsa ta samu matsala ne. Hanash kuwa network ne dan yace min shima yasha nemanki amma baya samunki”. “Bani da lafiya ne, ba koyaushe kuma wayar ke kunne ba. Amma yanzu zan sake nemansa insha ALLAHU dan ina matuƙar bukatar son naji muryoyinsu kozan samu nutsuwa”. “Hakan yana da ƙyau. ALLAH kuma ya ƙara lafiya. Kinyi waya da abokina kuwa?”.. “Eh nayi, amma kamar yanda na sanar maka a text message an ɗaga amma ana mun wani shirmen banza. Daga ƙarshe ma akace wai na saɓa lamba”. Karan farko malam Fawzan yay ƴar dariya. “Taku ne kawai irin na masu iyawa. Amma a yanzu na tabbatar zai saurareki”. Iffah ta ɗan taɓe baki kamar tana gabansa. “Ni ALLAH harna ɗauka ko ka yaudareni ne ka bani number daba itaba ma”. “Iffah koda abin wasa kikazo da shi bazan masa riƙon banza ba balle wannan mai matuƙar muhimmanci da ma'ana. Yanzu dai ina fatan wayar taki akwai caji?”. “Ai bama waccan bace, sabuwa fil aka bani a kwali yau harda lap-top”. Jimm yay na wasu ƴan sakkani. Sai kuma ya cire wayar a kunnensa ya duba. Tuna ashema shine ya kirata ya sashi sake maidawa. “Amma baƙya zargin akwai wani dalili a baki wayar? Mutanen nan fa sunada haɗari sosai Iffah. Bazan ɓoye miki ba inajin tsoron ƙarfin ikonsu”. “Nice zan baka wannan labarin Sir kasancewata a cikinsu yanzu. Sai dai kuma wanda suka bani wayar yanki ne na mutanen kirkin cikinsu. Kasan a ko ina akwai ƙyakykyawa akwai kuma mummuna”. Tsaf ta kwashe yanda sukai ta sanar masa saboda ta matuƙar yarda da shi. Shine kuma takema kallon wanda zai taimaka mata a wannan yaƙin kamar yanda tai fata. Ya jimanta al'amarin matuƙa, ta wata fuskar kuma yayi murnar ganin hanyar samun nasararsu ce tazo. “Lallai mun samu hanya ta jifan tsuntsu biyu da dutse ɗaya Iffah. Sai dai dole kiyi taka tsantsan da waɗan nan wayoyin. Ki buɗe account da duk kike ɓuƙata da layin da suka sanya miki, shi kuma wannan nakin watsap kawai zaki buɗe da shi, sai dai karki barsa akan wayar, da kuma kinyi magana da Ajmaal da shi ki goge watsap ɗin ki cire layin sai zaku ƙara ki maida. Akoda yaushe wayarki ta kasance da security na idanunki bana wayar ba. Dan inada tabbacin suma zasu saka ido a kanki. A daren nan ki buɗe watsap ɗin ki sake ma Ajmaal magana”. “Nahode Sir, insha ALLAHU zan yi duk yanda kace”.........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_29_* .........Barrister na ƙoƙarin shiga layin gidan Abu Moosa wata baƙar mota na ficewa. Babu wanda ya damu da ganinta a cikinsu, suka ƙarasa kutsa kai har ƙofar gidansa. Ganin gidan rufe daga nesa baisa sun kawo wani abu a ransu ba duk suka fita. Abu Zainab ne ya ƙarasa har jikin ƙofar. Kansa tsaye ya kai hannu ya fara knoking, amma har tsahon mintuna biyu babu alamar motsin mutum. Juyowa yay ya ɗan kalli su Kaka dake kallonsa. Cikin sarewa ya girgiza musu kai. “Banajin fa akwai mutum a gidan nan, dan babu wani motsi”. “Kara dai bugawa”. Cewar Barrister cikin bashi ƙwarin gwiwa. Kai Abu Zainab ya kaɗa ya cigaba da bugawa, maimakon a buɗe nan sai ƙofar makwaftansu ce ta buɗe. Wani matashin saurayi ya fito. Abu Zainab ya maida hankalinsa garesa suka gaisa. Kafinma ya tambaya saurayin ya bashi amsa. “Ai banajin akwai kowa gidan nan. Saboda yanzu babu jimawa matar gidan aka ɗauke a mota harda ƙaton akwati”. Da mamaki Abu Zainab ya ce, “Kana nufin yanzun?”. “Eh, dan banajin sunma rufa minti goma. Ta kuma yima mahaifiyata sallama akan zata koma garinsu ne. Harma mukayi mamakin hakan ganin duka rasuwar mijinta bai wuce kwanaki goma sha biyar ba”. Godiya Abu Zainab yay masa jiki a saɓule ya koma gasu Kaka. “Waifa kunji babu jimawa tabar anguwar nan. A yanda tacema makwaftansu ma ta koma garinsu ne”. “Garinsu kuma?”. “Haka dai yace. Nifa na fara tsorata da lamarin nan, dan tabbas akwai abinda ke ɓoye da bamu sanshi ba”. Tsakanin Kaka da Barrister babu wanda ya iya cewa komai.... *_MASARAUTA (JASRAH)_* “Wai ni naga sai faman moso kike, kinma kasa bani labarin yanda kukai da Akia akan zancenmu na jiya. Kuma naga wucewarku ke da ita ɗazun zuwa sashin Mamma (Malikat Haseena)”. Cike da zolaya ta ɗan hararesa. “Ko kuma dai ƴan leƙen asirinku sun sanar maka ba”. “Leƙen asiri kuma? Haba sai kace dai ku. Kudai matan masarautar nan ne dai da baƙwa iya rayuwa sai dai ƴan leƙen asiri. Amma mu maza miya haɗamu da wani leƙen asiri kamar marasa aikin yi”. Ta ɗan dara kaɗan da taɓe baki. “Muma ɗin ba kowa ne yake hakan ba kamar yanda kuke zargi. Niko waya dameni a daular nan dahar zan damu da saka wani bibiyarsa. Ko lamarin Zaki addu'a ce tamu a garesa kawai”. “To ALLAH yasa hakan. Yaya zaman naku ya kasance?”. “Zama an samu nasara. Dan inama Akia bayani a take ta amince, ta kumace muje sashen Mamma itama muji ta bakinta. Alhamdullah sai aka dace itama zancen ya ƙayatar da ita. Na taƙaice maka zance a yanzu haka ma mun zauna da ita yarinyar. Insha ALLAHU zuwa gobe ma zata koma sashenta. Sai dai abu ɗaya ne fa Mamma bata amince da shi ba”. “Minene shi?”. “Sake kai wata Zawjata-almilk turakarsa. Acewarta za'a ƙara jinkirtawa aga abinda yarinyar zata samo. Sannan za'a sakema duka Zawjata-almilk ɗin sabon horo akan kasancewar su Zawjata-almilk a wannan karon”. (Wata sabuwa kenan, wannan tsinanniyar tsohuwar ko) ya ambata a zuciyarsa. A fili kam fuskarsa ya kawata da sabon murmushi da faɗin, “Woow wannan tsarin yayi, shiyyasa Mamma ke daɗa birgeni. Hakan ma wani mataki ne da zai taimakemu matuƙa. ALLAH kuma yasa mu dace”. “Amin dai Abu Harith. Dan gaskiya a wannan gaɓar ina tsoron a ce abinda ya faru ya sake maimaita kansa. Saboda zuwa yanzu hankalin manyan ƙasashen duniya ya fara dawowa kan ƙasar ruman. Dan ma ana shakkarmu ne da tuni wani zancen ake ba wannan ɗin ba. ALLAH dai ka bayyana gaskiya ka kuma wanke wanda ake neman disashewa saboda son zuciya”. “Amin Meera. Amma ko yanzu ɗin ma akwai abinda baku sani ba. Shahan-shan na ɓoyewa ne kawai dan karya tashi hankalin kowa. A wata mai kamawa shugabannin manyan ƙasashe bakwai na africa zasu kawo ziyara ƙasar ruman. Bisa jagorancin shugaban ƙasar Nijeriya, bama raba ɗayan biyu akan wannan al'amarin ne kuma”. “Ya Arrahaman”. Jasrah ta faɗa a tsorace. “Ki kwantar da hankalinki, dan ALLAH kuma kar kowa yasan wannan, dan na sanar miki ne kema saboda na yarda da ke”. Badan hankalin nata ya kwanta ba ta jin jina masa kanta kawai. Cigaba da kwantar mata da hankali yay cikin kwantar da murya har barci ɓarawo ya kwashe ta. Sai da ya tabbatar barcinta yayi nisa sannan ya zare jikinsa cikin sanɗa ya fice zuwa ɗayan ɗakin dake jikin wanda suke kwance da waya a hannunsa...... *_ZAWJATA-ALMILK_* Dukan matakin shawarar da Sir Fawzan ya bata shi tabi, dan tunda sukai bankwana da Daneen Ammarah tai shirin barci ta sakama ƙofarta key. Ta fara da buɗe Watsap, sannan ta lalubo number Ajmaal. Cikin sa'a kuwa yana online, wani farin ciki ne ya ratsata. Taja kakkauran numfashi da godema ALLAH. _Assalamu alaikum_ Ta fara turawa da fatan samun amsa zuciyarta na harbawa da sauri-sauri. Tsahon mintuna kusan goma babu alamar zama a buɗe saƙon. Sake tura sallamar tayi a karo na biyu. Ta dasama wayar ido kamar mai irgan fitan numfashinta. Kamar a mafarki taga an buɗe, tai kasare tana jiran taga an amsa sai dai shiru har kusan wasu mintuna goman. A yanzu kam zuciyarta ta sosu, dan duk yanda take buƙatar abu ga mutum ta tsani a wulakantata. Ta cije lips da ƙarfi tana danne fushin dake son mata tasiri. _Wa'alaikissalam_. Aka amsa mata a bazata. Nannauyar iska ta furzar, itama ta buɗe saƙon ta share. Da ƙyar ta iya danne zuciyarta mintuna bakwai suka cika. _Sunana Fareedah bint Zayyan_. Tsahon mintuna kusan goma yanzu ma sannan aka buɗe. _Na sani_. Tai shiru tana kallon amsar, sai kuma taja tsaki na takaici. A fili ta furta, “Aikin banza. Ka sani shine baka san aikinka ba mtsoww!!”. Sharewa tai, ta rubuta masa. _Kwanaki na kira, amma akaimun tarbar da har yau ina mamakinta. Shin dama manyan ƴan jarida haka suke da wulaƙanta bukatar marasa ƙarfi?_ Tsahon minti ashirin da buɗe saƙon babu alamar za'a amsata. Hakan yay mata ciwo matuƙa. Sir Fawzan ta kira, bugu biyu kuwa ya ɗaga. A ɗan rikice yace, “Iffah baki ganin akwai matsala yawan kiran nan? Masarauta fa ba irin ko'ina bane sunada hanyoyin tsaro ɓoyayyu ciki harda cctv”. “Hakane Sir, amma nima dole ce ta sakani kiran. Anya kuwa wannan abokin naka da gaske ɗan jaridar ne? Sam baya ɗaukar al'amarina da muhimmanci, duk ɗan jarida na kwarai zaka samesa da zumuɗi akan labari, musamman ma irin nawa daya kasance babba”. “Miya faru? Bai amsa saƙonki ba ne?”. “Ya amsa. Amma yanamun yanga. Harna fara jin gundira a huɗɗa da shi”. “Karki saurin karaya, amma nayi mamaki dan masan Ajmaal ba mutum bane mai irin wannan siffar wlhy. Inaga dai akwai aikin da yake yi a wannan gaɓar shiyyasa. Kin san su abubuwan nasu da yawa. Kin san kuwa yanda ya ƙagu akan son jinki, dan ɗazun na fara ƙyara masa abinda ke ranki kaɗan”. Ta ɗanji sassauci daga haushinsa. Taja ajiyar zuciya a fili da faɗin, “Shike nan bara na koma”. Sallama yay mata ya yanke wayar. _Am sorry na haɗa wani aikin ne da saurarenki. Yanzu ina jinki_. Da wannan saƙon taci karo bayan yanke wayar. Sanyi ta ƙaraji a ranta. Cikin ɗan karsashi ta maida amsa. _Ayya kayi jaƙuri na maka gurguwar fahimta._ _Babu damuwa_ Aka amsa mata cikin ƴan sakanni. Cike da karfin gwiwa ta rubuta. _Nasan abokinka ya fara maka bayani akan nemanka da nake ido rufe._ _Hakane. A yanzu haka ma munyi dashi zai bani wani yankin rubutunki dake hanunsa._ _Alhamdullahi. A yanzuma akwai cigaban wancan rubutun a hannuna nima. Sai dai ban san ta hanyar da zai zo garesa ba ko gareka_. _Wannan mai sauƙine ai. Zaki iya turamin shi tanan_ _Wai! Amma typing ɗin zaimun wahala gaskiya_. _Karki damu ki ɗauki hoto_ Cike da zumuɗi ta miƙe. Gado ta ɗaga ta ɗakko notebook ɗinta, a take ta ɗauka hoton duka rubutun ta tura masa. _Gashi, insha ALLAHU duk bayan kwanaki uku zaka iya ganin saƙona_ _Masha ALLAH hakan yayi, sai dai a maimakon kwana uku mizai hana muyi mako-mako. Dan wani abun da zai zo yana buƙatar bin diddigi da faɗaɗa bincike mu tanan a garemu._ _Yanda kace haka za'ayi. Ni dai fatana ka kasance ɗan jarida mai gaskiya da riƙon amanar kimar ƙasarsa. ALLAH shine shaidata na baku dukkan yarda kai da Sir Fawzan. Idan akasin nasarata ya biyo bayan yunƙurina ku zan zarga. Duk kuma yarinyar data samu kanta a irin halin da ƴan uwana da ni muka kasance kuma zaku amsa sunan azzalumai ne kamar yanda Shahan-shan ɗin ke amsawa a yanzu. Ku kuma dinga tunawa da mala'iku tare da ku masu rubutawa daga ayyukanku na zahiri da baɗini. ALLAH ya cigaba da tsare ƙasar ruman. Idan kanada wata tambaya zaka iya tura min text message na Barka lafiya_. Bata jira amsa daga garesa ba ta fita gaba ɗaya. Watsap ɗin ta goge ta kashe wayar gaba ɗayama tana sakin ajiyar zuciya a jajjere. Sai takejin wani kaso na damuwarta da nauyin zuciyarta ya ragu kaɗan. A wani gefe kuma kamannin mutumin can da wanda ta gani a jiya matsayin Shahan-shan ne ke ta faman mata kaikawo babu alamar zai barta ta huta...... ★★.... “★★” .....★ “Lafiyarki da tsahon zamani su da ɗa tabbatuwa uwa mai share kukan masu kuka”. Ta-kurya dake kai gwuyawunta ƙasa ta faɗa sakamakon zuwan Uwa gareta a bazata. Kamar ko yaushe, cikin shigarta ta jajayen kaya, ta gyara zaman ƙasaitar ta. Ƙoƙon dake hanunta ta miƙama ta ƙurya. Hannu biyu ta karɓa, ta kafa kai ta shanye abinda ke ciki. “Tukuycin cika umarninmu na yanka babbar baƙar dabba da kikai ne. Azamarki da himmarki zaisa bazaki taɓa nema daga garemu ba ki rasa Ta-kurya (Wa'iyazubillah 😭). “Nagode uwa mai share kukan masu kuka”. Murmushin daya sake munana fuskarta ta saki tana ƙara kalmashe ƙafafu a kujerarta. “Karki damu ke mai nasara ce. Minene makomar ayyukan da muka barki da su?”. “Ina kan yunƙurin ƙarasawa. Na kuma samu ƙyaƙyƙyawan labari a majiya mai ƙarfi yarinyar zata koma sashenta. Sai dai akwai zaman sirri dasu Uwar masu gida sukai wanda babu wanda yasan misuka tattauna. Ina dai ƙyautata zaton duk akan komawar yarinyar ne”. “Kar tattaunawarsu ta dameki. Tabbatar da ƴan leƙen asirinki cikin hadimanta shine aikinki na gaba. Dan kunada yawa masu wannan burin kema kin sani basai na sanar miki ba. Ina kuma tunatar dake rigar can dake a sashen Uwar masu gida. Da zaran ta tare ki kasance ɗaya daga cikin masu janta a jiki. Yardarta gareki ne zai bamu damar amfani da ita wajen cikar burinmu”. “Na gode da kasancewar ki haske mai haskamin duk wani surƙuƙin da zai iya zamemin duhuwa uwa”. “Biyayyarki garemu ita ce tushen share kukanki Ta-kurya. Dan haka bazamu taɓa barin kiyi kuka ba maƙiyanki suyi dariya ba. Sai dai su suyi kuka ke ki kasance cikin dariya a kullum bisa nasararsu. Karki shagala ƴar shilar suda nada taurin kai, Karki zama cikin jerin mutane masu raina allura ta zame musu garma. Muna son tasha madarar nan a ƙalla sau uku daga gareki da zaran ta tare a sashenta”. Ta ƙare maganar da miƙama ta ƙurya ƙoƙon da bata san daga ina ya fito ba. Dan ganinsa kawai tai a hannunta tamkar ƙyaftawar idanu. Hannu biyu tasa a wajen amsa tana jera mata kirari da godiya. A hankali ta fara disashewa a idanunta tamkar baƙin hadarin da masha ruwa (Bakan gizo) ya shanye cikin sakanni. Ta-ƙurya ta sauke nannauyan ajiyar zuciya. Sai kuma ta miƙe da ƙoƙon da Uwa ta bata. A guri na musamman da na'urar sanyi ke aiki ta ajiye madaran, murmushin jin cigaba da tabbatuwar nasararta na cigaba da ƙawata ƙyaƙykywar fuskarta. Ji take a ranta yanzu ne fa za'a fara wasan na gaskiya. Dan dama idan aski yazo gaban goshi masu iya magana kwance yafi raɗaɗi da zafi. Ta jima bata samu irin wannan damar ga uwa ba a ɗan tsakanin nan da mafi yawan lokuta sukafi ganawa cikin ɓacin rai da rabuwa da ɓacin ran. Amma a yau yanda uwa ta ziyarceta ya sakata jin karsashi da ƙarin kwarin gwiwar cigaba da ruguza duk wanda ya cigaba da yunƙurin shiga gaban nasararta.......✍️ “Humm masu karatu, da gaske fa yanzu ne za'a fara wasan na gaskiya. Ga dai Iffah zata koma ɗakinta. Komawar dake cike da burikan wasu dake zagaye da ita. Buri kuma irin wanda ke kamanceceniya da juna ta fuskar wanzuwa. Manufa kuma kowa da irin tasa. Ita kanta Iffah da nata ƙudirin karku manta. Shin wanene zaiyi nasara ne? Yaya batun su Babiy kuma? Dan maimakon haske komai ƙara cuɗewa yake. Kaka zaiyi wani yunkuri a alamarin kokuwa Barrister zai janye bisa gargaɗin da akai masa shima?. Kumuje zuwa dai dan ba'a fara komai ba sai yanzu😉🥱”. *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_30_* ........Kamar yanda su Malikat Haseena suka faɗa a yau aka tashi da gyaran sashen Iffah, sai dai abinda ya Bama kowa mamaki ba inda aka fara kaita bane. Ɗaya daga cikin sabbin sashen da babu wanda ya taɓa rayuwa a cikinsu ne a masarautar. Hasalima an jima ana gutsiri tsomar dalilin gininsu da Tajwar Eshaan yasa ayi batare da ansan dalilinsa ba. Ba kayan ƙawata gida kawai aka zubama sashen ba, harda tarin sitturu da kayan ado na sakawar Iffah. A karan kanta kuma masu gyaran jiki na musamman ne suka duƙufa kanta a yinin wannan rana. Da dare ta samu hutawa. Washe gari aka cigaba da mata gyaran da ita kanta sai da zuciyarta ta fara shiga wasi-wasi. Koda yake dama a ciki take. Dan gaba ɗaya kwanakin nan aikinta kawai shine nazari da fasalta abubuwa masu yawa a rai da takasa gane bakin zarensu sam. Sai dai shawarar malam Fawzan ta waccan ranar ta ƙara mata ƙwarin gwiwa da maidota a hayyacinta da matsayin shigowarta daular ruman..... Tsahon kwanaki uku ta gyaru ta ƙara ƙyau tamkar ba'ita tayi fama da jiyya na a kwanakin baya. Ƙamshin dake fita a jikinta ma kawai ya isa ai kiransa na musamman. Ita a karan kanta har gizago canjawar tata ke mata. Jikinta ya murje ta ƙara girma da cika ido tamkar ba autar Ummu da Babiy ba. Ga wani jin kai da takejin ta ƙara masu neman kere shekarunta. Babu shakka kuma hakan nada nasaba da girman da ake bata. Masarauta da jama'ar cikinta zance ya yaɗu yau za'a maida Zawjata-almilk sabon sashenta tunda ta samu sauƙi. Shaidar haka kuma nada nasaba da walimar da Malikat Haseena suka shirya, acewarsu ta aure ce da ba'aiba sanadin abinda ya faru za'ayi yanzu. Shirya wannan walima ya kawo ƙananun magana matuƙa, dan kuɗi aka kashe tamkar za'a sake wani sabon auren. Abin mamaki sauran mata biyu kafin Iffah ga Tajwar Eshaan sai al'amarin ya sosa musu zuciya duk da har yanzu zaune suke batare da ko Tajwar ɗin sun san kalarsa ba. Sam Iffah bata san da wani taron walima ba, sai da aka kammala mata shiri cikin wasu ƙawatattun kaya masu tsananin ɗaukar ido da tabbatar da ita amarya ta gaskiya mai amsa sunan Zawjata-almilk kanta ya fara ɗaurewa. A ganinta in har shigace ta iya rakata sashenta baici ace ta ƙawatu har haka ba kodan kasancewar dare ne ma. Kai mutanen nan fa sun fara caja mata ƙwaƙwalwa, ta faraji a ƙasan ranta akwai manufa. Amma dai koma minene zata jure har zuwa lokacin samun ƴancin kanta na komawa sashen nata dan ta shiryawa kowa talalarsa. A kwanakin baya ta kwantar da kai ne ga kowa domin fahimtar manufar wasu koda kalilanne a cikinsu. Alhamdullah kuma ta dace, dan koba komai ta gama samun yardar Daneen Ammarah da masu gayya da aiki Malikat Haseena da Malikat Bushirat. Duk da dai tasan kada mage ba yankata bane. Amma koba komai raina allura yakan sa ta zama garma ga wanda yay sakaci ai. Taji ba daɗi da barin ɗakin data rayu tsahon kwanaki cike da kewa. Koba komai bazata manta da rayuwar kusan sati uku da tayi a cikinsa ba. Ta koyi ilimi da yawa, harma da darasi data ɓoye matsayin sirrinta. Da wannan tunanin a ranta har aka iso babban ɗakin taro na cikin masarautar, wanda ya ƙunshi duk wani babba mai faɗa aji. Al'ajab ya kama Iffah, amma ta dake zuciyarta na sake tauri na nan dalilin ɓoye mata wannan zaman da akai. Amma a zahiri rashin ƙarfin cewa yasata yin luff kamar yanda ta kasance a kwanakin da suka gabata na samun lafiyarta. Daneen Ammarah data kasance mata ƴar jagora kasancewar fuskarta a sakaye take ta kaita har mazaunin da aka tanada dan ita a cikin ƙaton falon bisa tattausar dardumar da aka shirya walimar. Kamar yanda al'adar take, abinci aka fara ci yayinda Iffah ta gagara kai ko ruwan madara bakinta. Yanda tayi ɗin ya sake burge su Malikat Bushirat, suna ji a ransu sun dace da irin surukar da suke fata. Bayan anci ansha kowa ya nutsu. An fara buɗe taron da addu'a, tare da saƙon maraba ga sabuwar Zawjata-almilk, harma da fatan kasancewar ta abinda kowa ke fata. Kowa dai ya amsa da amin a zahiri, a baɗini kam sanin sirrin wasu sai ALLAH. A mataki na biyu shine zagayawa da Zawjata-almilk takai gaisuwa ga duk wanda ke wajen, kasancewar kakanni ne makusanta da iyaye, da yayye. A yanzu dai kam da taimakon Jasrah ta motsa, bayan ta janye hular rigar alkyabbar jikinta data hana kowa kallon ainahinta a tun farko. Duk da Iffah taji ta takura, hakan wata damace a gareta na sanin dukkan masu faɗa ajin, zai kuma zama jagoran abinda zai taimakawa nata ƙudirin. Idanunta suka cika da hawaye, a lokacin da take durƙushe gaban Malikat Haseena matsayin bankwana. Tanajin tsohuwar a ranta, ta kuma samu wani kebantaccen ilimin zamantakewa da ita. Ta saka mata albarka tare da yaba ƙyawawan halayenta da jinjinama iyayenta tarbiyyar da sukai mata. Ta ƙare da fatan alkairi da samun zuri'a mai albarka tsakaninta da Shahan-shan. Waɗan nan zantika sun zama abin kaiwa da komawa a zukatan manyan masarauta. Dan kowa na ganin kamar wata isharace Malikat Haseena ta isar cewar ta karɓi Iffah ɗari bisa ɗari matsayin Zawjata-almilk fiye dana baya da suka gabata. Iffah a karan kanta taji tausayin tsohuwar bisa ƙudirinta na shigowa daular ruman data tabbatar yasha banban da fatan da Malikat Haseena tayi gareta a yau gaban duk wanda ya isa a ƙasar ruman ma ba daular ruman ɗin kawai ba. Har yanzu har gobe da jibi tana akan bakanta na ɗaukar fansar rasa ƴan uwanta. Abin harinta kuma ɗaya ne tal shine Tajwar Eshaan, inma da wanda zasu biyo bayansa sai ta gama da babban dodon nasu. Ta samu ƙwarin gwiwar hakanne da tabbacin jin sai an kai matan turakarsa ake fiddosu babu rai. Sai kuma bincike da shaƙiƙansa guda huɗu sukai yunƙurin ɗaurata a yanzu haka. Kenan babu buƙatar wasi-wasi koma minene shike ƙullasa... Malikat Bushirat ma tayi irin makamancin addu'ar Malikat Haseena ne ga surukar tata. Ta ƙara da faɗin ita ɗiya takejin ta samu ba Suruka kawai ba, tana kuma fatan ta kasance kibiyar ajali ga masu ƙudirin sharri a ciki da wajen daular ruman. Tabbas maganar Malikat Bushirat tafi ta Malikat Haseena ɗumama zukatan wasu, yayinda mugun ƙudirinsu akan Iffah ya ƙara hauhawar farashi a zukatansu, amma duk sai suka ɓoye suma sukai mata irin tarbar data ɓoye dukkan ainahinsu. Dan Miran Jasim ma da akazo kansa har ƙyauta ta musamman ya gabatar ga Zawjata-almilk. Iffah data kasance cikin ladabi da ƙawata harshenta gaban kowa yayin miƙa gaisuwarta duk da ƙarancin shekarunta kaifin basirarta da wayonta ya bata damar nazari da adana cewar kowa a wajen da fuskar daya tarbeta ta hanyar kallonsu a ƙyalkyalin jikin rigarta datai matuƙar taimaka mata harta ambata godiya ga Malikat Haseena data zaɓa mata rigar domin sakawa a yanzun. Ba kalaman kawai ta riƙe ba da fuskokinsu da suka fita tartar bisa taimakon hasken kwayayen wutar lantarki. Harda sunayensu sun kasance kamar wani zane akan dutse cikin ƙwaƙwalwarta da zuciyarta. Ƙarfe goma da kusan mintuna talatin taron ya tashi na dare, aka fara fita da Zawjata-almilk da kowa ke tunanin sashenta za'a kaita kai tsaye. Sai kuma hakan ya bambanta da tunaninsu a lokacin da Malikat Haseena tabi bayansu akan wheelchair ɗinta matsayin maiyin wannan rakkiya. Abu ne da ba'a taɓa gani ba a masarautar. Dan hatta Malikat Bushirat da Daneen Ammarah sun sake jinjina wannan soyayya mai ƙarfi data shiga tsakanin Malikat Haseena da Iffah. Sai dai hakan ya musu daɗi, musamman Malikat Bushirat da take ganin hakan matsayin ƙarin sanin wanene Shahan-shan a zuciyar Malikat Haseena ga maƙiyanta. A lokacin da kowa ke fitowa daga falon da walimar ta gudana bayan gama sallamar sai da safe gagarumin labari da ɗumi-ɗuminsa shine cin karo da motar data ɗauka Malikat Haseena da Iffah a ciki ƙofar sashen Shahan-shan. A wannan karo hatta da Malikat Bushirat da Daneen Ammarah sai da sukai turus dan shirine da sam basu san da shi ba. A take suka koma ƴar kallo a tsakaninsu, cikin tambayar juna yaya akai haka kuma? Da idanu. Rashin amsa da mai basu amsar ya sasu shanye komai...... ★★.... ★... ★★..... Komai ya tsaya cak a ɓangaren su Kaka a kwanakin nan da suka gabata dangane da neman inda su Babiy suke. Barrister ya sake bin duk hanyar da yake da yaƙinin samu koda na ƙarfin iko ne amma sai ya risketa a toshe. Zuwa yanzu kam su duka ukun sun fahimci komai shiri ne bisa la'akari da labarin da suka bama juna na gargaɗin da akai musu. Sai dai abu mafi ɗaure kai da ban mamaki, wanene mai shirin? A wane dalili yay shirin kuma? Miyasa zaiyi shirin akansu Babiy ɗin?. Waɗan nan tambayoyi sune suka zama abun tattaunawa tsakanin Kaka da Barrister dama Abu Zainab daya saudaukar da dukkan lokacinsa domin ganin komai ya daidaita. Bisa shawarar Barrister Kaka yay shirin komawa Jimna, dan a cewarsa suna buƙatar bada ƙafa kodan harar rayukansu da aka farayi suma. Saboda a kwanaki biyun da suka gabata da ƙyar Barrister yasha a hanun wasu tankunan mai da suka sakashi tsakkiya bisa titi lokacin da yake tashi aiki. Haka yaron Abu Zainab a jiya anyi wuff da shi daga hanyarsu ta zuwa makaranta a cikin ƴan uwansa. Ba kuma a sakesa ba sai a daren jiya bayan sallar isha'i lokacin kowa ya gama jigata da nema da hasashen inda ya shiga. Rubutacciyar wasiƙar da aka haɗosa da shi yayin maidosa ya basu tabbacin daga inda tsiyar take. Kaka ya kammala kulle ko'ina na gidan sannan yay sammala da su Abu Zainab tare da godiya ya ɗauki hanyar inda zai samu motar ƙauyen Jumna. Harya sauka a mototaxi aka dakatar da shi, da mamaki yake duban mai mototaxi ɗin dake miƙa masa ƙaramar jakkar hannunsa. “Baba kayi mantuwa, ALLAH yasa na farga da wuri”. Kafin Kaka ya samu damar cewa wani abu saurayin ya ajiye jakkar gabansa ya koma cikin mototaxi ɗin da baiko waiwayo ya dubi Kaka dake yunƙurin dakatar da shi ba. “Kar kai jayayya tsoho, ka ɗauka dan naka ne”. Aka faɗa ta bayansa dai-dai yana kaiwa duƙe zai ajiye jakar. Ɗagowa kaka yayi, sai dai bayan mutumin kawai ya gani sai ƙurar motarsa. Ran Kaka ya sosu, har fuskarsa ta nuna haka. Alamar ƙosawa da wasan kwaikwayon waɗan nan mutane ya fara tunzura kawaicinsa da son bin doka a yanda tazo. Amma ya fuskanci burinsu kawai su kaisa maƙurar da sai ya gwada ƙwanjinsa akansu. Yay ƙwafa tare da ɗaukar jakar....... ★ “Boss ya ɗauka fa”. Wani matashin saurayi siriri dake zaune cikin taxi nesa kaɗan da Kaka ya faɗa yana ɗan kai hannu a kunensa ya dafe bluetooth ɗin dake manne a ciki. “Tabbas akwai alamar ɓacin rai tattare da shi a yau, dan fuskarsa harta kasa ɓoyewa”. Saurayin ya sake faɗa da alamar amsawa wanda ya kira da Boss ɗin a farko idonsa ƙyam akan Kaka da har yanzu ke tsaye jikin wata mota. Kai ya gyaɗa alamar an sake masa magana daga wayar, sai kuma ya gyara baƙar facing cap ɗin kansa da faɗin, “Eh da alama bai samu motar garin nasu bane. Amma gani ina tunkararsa, komi kenan zan cigaba da riƙe wayar dan kaji komai”. Kaka na shirin ɗaukar jakar da mai mototaxi ya barsa da ita zai bar wajen saurayin ya katsesa ta hanyar masa sallama. A ɗan daƙile ya amsa dan ransa babu daɗi har yanzun. A yanda ya kafe saurayin da idanunsa masu kaifi duk sai yaji ya tsargu. Ya haɗiye yawu da ƙyar cikin ɗan harɗewar harshe yace, “Baba tafiya ne?”. Kaka dake nazartarsa ya ƙyabe baki cikin masa kallon sama da ƙasa yace, “Kaima nasun ne?”. Sai da gaban saurayin ya faɗi, amma yay jarumtar ƙwaɓe fuska da faɗin, “Nasuwa kuma Baba? Ni fa mai taxi ne, na hangokane kawai na iso”. Kaka ya cigaba da masa kallon nazari, sai kuma ya furzar da isaka da kauda kansa yana kallon mutanen daketa faman kai kawo a titin cikin son watsar da lamarin saurayin... “Bar wajen kamar kayi fushi”. Aka faɗa daga cikin bluetooth ɗin dake manne a kunensa........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_31_* .......Takun da baifi uku ba Kaka ya juyo ya bisa da kallo, kamar a bazata saurayin ya tsinkayi muryarsa na faɗin, “Jumna zanje”. Yi yay tamkar bai jisa ba. Hakan yasa Kaka sake ɗaga murya amma ya cigaba da sharesa shima. Yana ƙoƙarin shiga motarsa Kaka daya biyosa a baya yace, “Haba ɗan nan baka jini bane?”. “Sarai na jika Baba. Na fahimci ba tafiyar zakai ba, ba kuma hurimina bane tilastaka”. A karan farko kaka ya saki murmushi. “ALLAH sarki, to ayima tsoho haƙuri ɗana”. “Baba kamin laifin komai ba ALLAH, ai aikina ne. Dama naji kana sanarma wancan ne ni kuma hanyatace shiyyasa ma naje gareka. Zanje ƙauyen Yamanu ne dama”. “A Alhamdullah, lallai hanyarmu ɗaya Bara na ɗakko kayana.” Mutum biyu kawai saurayin ya ƙara ɗauka bayan kaka suka ɗauki hanya. Hakan baisa kaka ya ji wani zargi game da shi ba. Sai ma hira da suka dingayi kai kace sun san juna. Bayan sauke mutum biyun daya ɗakko har ƙofar gida ya kai Kaka. Yaji matuƙar jin daɗin wannan karamci dan haka yay masa tayin shiga ciki yasha ruwa. Saurayin ya ɗan nuna tirjewa amma Kaka ya janye ra'ayinsa a dole ya bisa suka shiga, sai dai dama a ransa hakan yake fata. Ummu na zaune a tsakar gida ita da Iyyani, ta rame matuƙa tayi duhu irin na wanda ya shiga damuwa. Tamkar an sare gwiyawun Kaka ya ƙarasa shiga idanunsa akan Ummu data tsurama bayansa ido. Iyyani ma jiki a sanyaye ta miƙe dan tasan komai tunda kullum sai sunyi waya da Kaka. Itace tai ƙarfin halin masa sannu da zuwa. Ya amsa a sanyaye yana waiga bayansa. “Yaro shigo mana”. Kaka ya faɗa domin samawa Ummu nutsuwa. Da sallama saurayin ya shiga. Ummu tai ƙasa da kanta a hankali. Bayan sun gama zama a tabarmar da Iyyani ta shimfiɗa musu saurayin ya fara gaishe da Ummu. Bata amsa ba, hakan ya sakashi shan jinin jikinsa yay shiru a sanyaye. Iyyani data sake kawo musu ruwa ce ta amsa masa da “Bata magana yaro”. “ALLAH sarki” ya faɗa cikin sauke ajiyar zuciya ita ya gaisheta. Da kulawa ta amsa masa dukkan hankalinta a kan Kaka dake kallon Ummu tamkar ya samu television. Ummu da hawaye suka cikama ido ta miƙe a hankali, ɗaki ta shige duk suka bita da kallo. Kaka baice komai ba hakama Iyyani data zarce kitchen sai gata da kwanon abinci....... ★★... ★★★ ....★ Tamkar raƙumi da akala haka Iffah ke tafiya bisa jagorancin Malikat Haseenat. Kasancewar dare ne babu yawaitar hadimai masu hidima. Sai dai masu tsaro tako ina kai kace zasu iya kare ran wanda suke tsaye a dalilinsa daga ziyartar mutuwa. Tsirarun hadiman da suka samu nata zubewa kwasar gaisuwa, Malikat Haseenat ce kawai ke iya jinsu da ganinsu. Iffah dake ta faman sauke ajiyar zuciya da al'ajabin dukiyar dake narke a wannan gini ji take komai ya ƙwace mata. Ta kasa fasalta komai ta kasa auna komai a ma'aunin rinjayen aikin zuciya dana ƙwaƙwalwa.... “Bismillah”. Malikat Haseenat ta katse mata ɗimuwar da take ciki ta hanyar nuna mata ɗaya daga cikin kujerun katafaren falon mai cike da abubuwan da bazasu lissafu ba. Da gaske Iffah bazata ma iya tantance yanda akai ƙafarta tazo nan ɗin ba. Komai Malikat Haseenat batace ba, dan ta gama karance ɗimuwar dake jagorantar fitar numfashin Iffah. Amintattun Hadiman dake a falon na uku suka zube gaban Malikat Haseenat kawunansu a ƙasa. Hannu kawai ta iya ɗaga musu. Babu buƙatar sai ta faɗa abinda tazo dan shi, shugaban hadiman dake a wannan falon ya miƙe zuwa ga landline domin isar da saƙon zuwanta... “Tsahon rai da lafiya su tabbata ga Uwa a garemu, shugaban na tsumayen isarku a falon sama”. Shiru malikat Haseenat batace komai ba. Yayinda Iffah da zuciyarta ke luguden ke saurarensu cikin juyewar tunaninta da har yanzu bai dawo dai-dai ba. Kusan mintuna uku Malikat Haseenat taima Iffah nuni data miƙe, ita kuma ta birka wheelchair ɗinta suka shiga lifter. Mintuna biyu ne kacal suka iso da su katafaren falon da yafi kowane falo ƙawatuwa a kaf daular ma da sashen kawai ba. Iffah tai ƙoƙarin danne harbawar ƙirjinta sakamakon tozali da wanda ke zaune a falon cikin zama na ƙasaita da izzar masu mulki. Tafiya take tamkar hawainiya saboda tsabar kasala da sanyin gaɓɓai. Zuwa yanzu wannan fuskar bata aljani take fassarata ba, neman ƙarin bayani take a kanta a dalilin ganinta a waje biyu da basu da alaƙa da juna a zahirin rayuwa... Tajwar Eshaan da ke kishingiɗe bisa ƙayataccen kujera mai kama da wani madaidaicin gado gabansa butar shayi ce da ƙaramin kofin da alamu suka nuna yasha ko zai sha, idanunsa ya janye daga kan television da yake kallo ya ɗan waigo garesu. Akan Iffah dake tafiya tamkar hawainiya ya fara saukewa, fuskarta a sakaye take, hanunta dake riƙe da rigar jikinta ne ta ƙasa kawai a bayyane. Janye wa yay ya maida ga Malikat Haseenat. Ta ɗan hararesa da salon kulawa da nuna damuwa. Idanun ya janye a sannu daga kanta itama yana sakin kasaitaccen murmushi.... Harya gama gaisawa da kakar tasa a yanda yake kishingiɗe batare da ya motsa ba Iffah na tsaye ƙyam tamkar an dasata. Malikat Haseenat ta maida kallonta gareta tare da ambatar sunanta. A dake Iffah ta amsa dan tayi alƙawari ma kanta bazata taɓa barin rauninta sake bayyana ga kowa ba a yanzun. Kafinma Malikat ta sake cewa wani abu tai ƙasa a hankali, cikin rashin ƙwarin jiki ta zube ƙasan lallausan carpet ɗin da ko jikin zomo bazai nuna masa laushi ba. Ƙamshi ko ba'a magana dan ko'anan ake shukashi iyaka kenan. “Amincin ALLAH ya tabbata a gareka”. Ta faɗa badan har zuciyarta abinda take son faɗar kenan ba. Sai dai kwarjininsa daya mamaye falon da duk girmansa take jinta a matse yaƙi bata damar fitar jin zafinsa dake a ƙasan zuciyarta a zahiri. Kamar a waccan ranar yau ma bai amsa ba, babu ma alamar yajita tattare da shi. Daga cikin hular alkyabbar jikinta ta cije lips ɗinta da masifar ƙarfi tamkar zata hudasu da haƙori..... “Ai ma Zawjata-almilk rakkiya ɗakin da Tajwar zaiyi barci a yau”. Furucin Malikat Haseenat ga hadiman dake rakuɓe gefe zube a ƙasa kawunansu rissine tun shugowarsu ya nema sarƙe numfashin Iffah da Tajwar Eshaan a lokaci guda. Babu wanda Malikat Haseenat ta kalla a cikinsu sai ɗaya daga cikin Hadiman ce da suke girki ta miƙe da rawar jiki zuwa inda Iffah take. Dole ta mike dan a furucin Malikat Haseenat babu wasa ko ɗaukar turjiya ga kowannensu.... Shiru falon babu wanda ya sake ƙwaƙwƙwaran motsi har hadimar data raka Iffah iyakar ƙofar ɗakin ta dawo Malikat Haseenat ta sallamesu. Da ga shi sai ita suka rage, dan haka ya kafeta da idanunsa. Kai Malikat Haseenat ta ɗauke gefe tamkar bata gansa ba ko fahimtar kallon. “Anan zata zauna, sai ka zaɓi inda kake buƙatar ta kasance har tsahon sati ɗaya, dan zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu masu mata hidima zasu kasance tare da ita. Na damƙa amanarta a hannunka, ina kuma fatan ta kasance ƙarƙashin kariyar UBANGIJI. Fatan alkairi da shiga sabuwar rayuwa, tare da tayaka murnar sabon aure. Na barku cikin amincin ALLAH”. Da alama gushewar numfashi da rikicin wannan tsohuwa ya gama daskarar da jinin Shahan-shan. Dan harta fice a falon ko gashin idonsa bai ƙyafta ba, kai kace wani butun butumine aka dasa a wajen domin tarihi....... (🤔Tsohuwar nan kuwa na lafiya? Zata kai mana Iffah har ƙuryar Dodon Mayu🥱🤦). ★★... ★★.... Duk da dare ne gaba ɗaya masarautar ta ɗauki ɗumi bisa wannan bahagon hukunci na Malikat Haseenat. Basu da al'amarin yazoma a bazata ba, hatta Malikat Bushirat da Daneen Ammarah da Jasrah da akai zaman da su komai ya musu cak. Abinda suka sani kawai komawar Iffah sashenta, bawai kaita turakar Shahan-shan ba. Miyasa Malikat Haseenat ta canja lissafin a kan kansu suma?. Wannan itace tambayar daketa musu kaikawo su duka. “Ni kam dai a wannan gaɓar na kasa gane komai wlhy Akia. Shin minene dalilin Mamma nayin haka? Miyasa lissafin ya canja daga yanda muka tsara gaba ɗaya?”. Kamar malikat Bushirat bazata tanka har ta kai ta kawo kusan sau uku kafin ta dubi Jasrah mai maganar. “Kaina ya kulle Jasrah”. Ta faɗa a takaice da kaiwa zaune bakin gadon ta dafe kanta. “Ya ALLAH! Wlhy zuciyata ta fara kai ni ga hasashen wani abu daban?”. Jasrah ta sake faɗa tana dafe nata kan itama. ★ A ɓangaren Daneen Ammarah ma dai a rikicen take. Sai dai ita nata lissafin yasha banban da nasu Malikat Haseenat. Daga ɗakin taro bedroom ɗin Malikat Haseenat ta wuce zaman jiranta. A zaman da bai wuce mintuna arba'in ba kuwa sai gata. Kallo ɗaya taimata ta ɗauke kai. Hadimar dake biye da ita ta ajiye madarar hanunta da zubewa ƙasa tana gaida Daneen Ammarah. Hannu kawai ta ɗaga mata.... “Na matuƙar gajiya, kwanciya kawai nafi buƙata”. Malikat Haseenat ta faɗa tana wulla kekenta hanyar bathroom ɗinta batare data sake kallon Daneen Ammarah ba. Da kallo ta bita cikin shakku da shan jinin jiki. Dan duk da a dunƙule tai magana tana nufin bata bukatarta a ɗakin kenan. Jiki a sanyaye ta miƙe ta fice zuciyarta na faman tsalle-tsalle... Duk yanda taso kwanciya ta kasa hakan, fargaba da tausayin Iffah ne ke matukar ɗawainiya da ita. Har cikin zuciya bata son rasa yarinyar dan ta matuƙar shiga ranta. Soyayya take mata irin ta ƴa da uwa. Ita kanta har takanyi mamakin yanda takejin Iffah a rai matuƙa, amma tasan wannan ƙaunar daga ALLAH ne kawai. Wayar dake a hannunta ta ƙara rumtsewa, ta gwada kiran Iffah ya kai sau huɗu kenan amma tana fasawa, so take taji lafiyarta ko zata samu ƴar nutsuwa, amma wata zuciya na gargaɗarta da kalmar rashin dacewa.... ★★..... “Mi wannan tsohuwar ke nufi wai shin? Ko itace abin neman mu kamar yanda barbushi ya sanar mana?”. Miran Arshaan yaja numfashi ya fesar, kamar bazaice komai ba sai kuma ya kafe Miran Jasim da kallo yana girgiza kai. “Wlhy kaina ya kwance Jasim Akhi. Na kasa gane komai a wannan gaɓar, abinda na sani kawai shine mutuwar yarinyar nan a wannan gaɓar tamkar mutuwar cikar birinmu ce, dan na gama ɗora dukkan hope ɗinmu a kantane. Bai kamata ta mutu a yanzu ba har sai ta ƙarasa mana aikin da muka kwashi tsahon shekaru muna ginawa”. “Miye mafita?”. Cewar Miran Jasim a firgice, dan zantukan Arshaan ɗin kamar sun zaburar da shi ne abinda ke gabansu. Kai tsaye Miran Arshaan yace, “Ziyartar Barbushi a wannan daren, kafin waccan sankaran matar da ban san amfaninta a tafiyarmu ba tazo ta ishemu da tsarin banza”. “Hakan yayi mun, babu amfanin ɓata lokaci kaje kayi shiri”. Kai Miran Arshaan ya gyaɗa masa, tare da mikewa ya fice. Da banzan kallo Miran Jasim ya bisa, cikin ƙanƙance idanu da wani shu'umin murmushi a fuskarsa “Ba matar can bace kawai abin banza a cikinmu, har da kai Arshaan, daka gama mun amfani zan kawar da kai, dan ni kaɗai nake son mulkar daular ruman batare da ɗan uba ko ɗaya ba da zai zame min abokin gaba, nasan idan har na barka kaima zaka zamemin maƙiyi dan burinka wannan kujerar ne na sani shashasha”... (🥱Waɗan nan mutane dai to bara nayi shiru dai🤫) *_ZAWJATA-ALMILK_* Duk da akwai wani ɗan ɓurɓushin tsoro a ƙasan zuciyar Iffah ta matuƙar dakewa da addu'a ta shiga ɗakin bayan ta gama ƙarema bangon dogon corridor ɗin da suka biyo kallo, ta jinjina kai cikin jin matuƙar ƙuna da tausayin talakawan ƙasan ruman baki ɗaya. Tayi imanin akwai dubbunan mutane dake barci akan titi cikin yinwa da ƙishirwa da yawa. Amma abin mamaki yau ga bangon ɗakin barcin Shahan-shan yasha ado da zinari matsayin fenti, “Taya ma imani zai zauna a zuciyar mutanen nan har su ɗauka rai wani abun mai daraja?” ta faɗa a zahiri idanunta na cika da ƙwallar baƙin ciki da ƙara jin tsanar Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed..........✍️ (😭Hikenan Iffahr mu an shigo ɗakin mutuwa😱🙆). Ko miye dalilin Malikat Haseenat na kai Iffah turakar Shahan-shan kai tsaye haka? Miye dalilinta na canja abinda suka tattauna da su Malikat Bushirat? Shin ko dai malikat Haseenat ce T....😱🤫🤭?. Yaya zata kasance tsakanin Iffah da Shahan-shan ne? Ta wani ɓangaren abinda ke kashe Zawjata-almilk kuna ganin zai ƙyale rayuwar Iffah a wannan dare kuwa?. Gadai wasu ɓoyayyun maƙiya na sake fitowa. Irinsu Miran Arshaan (mijin Jasrah kuma ƙani ga Tajwar Haysam) da Miran Jasim (shima ƙani ga Tajwar Haysam). Shin wacece wai matar nan da suketa a ambata batare da sunanta ba?. Hhhh tabbas yanzu ne wasan zai fara. Sai ku shirya ku sake shiri dan sai a yanzu ne muka kalmashe bakin shimfiɗar labarin dake cikin littafin DAUƊAR GORA... Wasan na asali yanzu ne filin yinsa ya kammala. Masoya sai mu antaya kawai😉🥱🏇🏇🏇🏇. *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽 _𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_32_* ........Ni'imtaccen ƙamshin dake tashi a katafaren ɗakin ta zuƙa ta fesar da cigaba da bin komai daki-daki. Ɗaki kam ya cika a kirasa ɗaki ga masu arziƙin dake ɗaukar duniya gidan zama. Sai dai ta gama ayyanawa a ranta babu wani ƙyale-ƙyale da zatai sakacin da zai ruɗeta har ya dakatar mata da ƙudirinta data fara taka tsanin nasararsa a yau insha ALLAH. Ta saki kasaitaccen murmushi da ware hannayenta iskar na'urar ac ta busota tare da ƙamshi, idanunta ta lumshe ta buɗe tare da tsuke fuska. Cikin wani kakkausan sauti daya bambanta da nata na baya ta furta. “Yanzu ne za'a fara wasan na gaskiya. Dodon matsafa MATAN ƘWARAI bisa kanka!!”... (🥱 Iffahn mu irin wannan alwashi haka🤔 kinfa fara bani tsoro😱🏇). ★★... Tun wucewar Malikat Haseenat ya bar falon shima. Tsaye yake jikin windown ƙaramin falonsa na hutawa da babu mai shigarsa sai shi ɗaya tak da amintacen hadiminsa mai gyarasa. Dan a doka ma hatta matarsa bata da hurumin shiga wannan falon a tsari da ƙa'idar masarautar. Hasken daya ƙawata cikin masarautar ya bashi damar iya ganin abubuwan dake kusa daga inda yake, sai dai kuma a zahiri idanun nasa ne kawai ke kallon zuciyarsa sam ba'a nan take ba. Ya kwashe tsahon lokaci a wajen kafin ya warware hannayensa dake goye a bayansa ya furzar da numfashi. Ƙofar ɗakin barci ƙwaya ɗaya dake a falon ya nufa. Shima tsaf yake tamkar anan yake zaman din-din-din. A maimakon kwanciya anan ɗin ma zaune yakai cikin kujerar dake ajiye a gefe domin hutawa kawai. Tun agogon ɗakin na juya sakanni da mintuna har ya koma awanni yana zaune idanunsa lumshe, ya kwantar da bayansa a makarin kujerar dake ɗan juyawa a hankali. A kallon fuska baka isa gane yanayinsa ba balle ka samu damar masa fassara. Bugawar agogon ɗakin mai nuni da cikar ƙarfe biyu dai-dai ta sakashi buɗe idanunsa da ƙarancin hasken ɗakin ya hana damar iya tantance launinsu a yanzu. Agogon ya tsurama ido tamkar mai lissafa daƙiƙun da suka cigaba da motsawa..... A ɓangaren Iffah wannan lokaci na dai-dai da kai goshinta ƙasa domin yima UBANGIJI suduja a karo na babu adadi. Tun bayan kammala lissafe-lissafenta da ƙidaye-ƙidaye ta zanzare rigar jikinta, ƙaramin akwatinta ta buɗe babu alamar damuwa tattare da ita ta sauya kayanta zuwa abaya. Daga haka ta nufi bayi bakinta ƙunshe da tarin addu'oin da taketa yi tun shigowarta ɗakin. A karan farko data buɗe fanfo da nufin yin alwala saɓanin zubar ruwa sai taci karo da jan abu tamkar jini. Tabbas taji firgici, amma sai tai yaƙi da rauninta wajen cigaba da addu'a da son daidaita harbawar da zuciyarta keyi da sauri-sauri. Tamkar almara kalar jan ya ɓace a idanunta ainahin ruwa ya maye gurbinsa. Numfashi taja ta fesar zuciyarta na tabbatar mata ta ƙara dakewa. Tsaf ta ɗaura alwalarta kuwa ta miƙe, tana ƙoƙarin gyara ɗan kwalinta taji tamkar an gitta ta bayanta. Anan ɗinma dai zuciyarta ta tsinke, amma sai ta cigaba da ambaton sunan ALLAH ta basar. Bata damu da nan wanin abin salla ba, dan tsaftar dardumar da aka ƙawata ɗakin da ita ya gamsar da ita. Mayafinta ta naɗa tai nagartacciyar tsayuwar salla domin fuskantar UBANGIJIN talikai mai jin kukan wanda ma basu fara kukan ba, mai bada kariya ga wanda ya yarda babu abin dogaro sama da shi... Taja tsahon lokaci a sujidar tana mai zubda hawaye da ƙaskantar da kai ga mai gani a duk inda ka ɓuya. Bayan ta sallame tai zaman karatun Alkur'ani a cikin wayarta dan batajin zata samu Alkur'ani a wannan ɗakin da ƙyaleƙyalen cikinsa ya tabbatar mata zamowa fadar aljanu ba komai bane. Sai da ta gama karance baƙara har zuwa inda suka tsaya a makaranta sannan tai addu'a mai tsawo itama. Sosai taji wata iriyar nutsuwa na ratsa dukkan jikinta, ta sauke ajiyar zuciya da miƙewa. Hankalinta kwance ta haye katafaren lafiyayyen gadon da Shahan-shan ne kawai ya taɓa hawansa a tarihi. Nanma zama tai tai addu'ar barci ya shafe jikinta ta gyara lausasan filos ɗin da aka ƙawata adon gadon da su ta kwanta tana sauke ajiyar zuciya. Barci mai daɗi ya fara fisgar idanunta a sannu-sannu sai gata tana sauke numfashi....... ★★...... ★★..... ★★....... Bayan wucewar saurayin da Kaka ya shimfiɗama sha tara na arziƙi gidan yay shiru. Kamar yanda bai cema Iyyani komai ba itama batace ba, tsahon wasu mintuna sannan ya miƙe ya shiga ɗakinsa. Tashi Iyyani tai ta bisa, dan ta fahimci maganarce baya buƙatar ayi sam.. A ɗakin ma baice mata komai ba har tsahon wani lokaci, ganin haka ta katse shirun da faɗin, “A haɗa maka ruwan wanka?”. Batare da ya bar abinda yake ba ya jinjina mata kai. Fita tai jiki a sanyaye, babu jimawa ta koma ta sanar masa an haɗa. “ALLAH yay miki albarka”. Ya faɗa kamar yanda ya saba. Ta ɗan ji sanyi a ranta, dan haka ta amsa da “Amin tare da kai” cikin sauke ajiyar zuciya.... “Ai bakaci wani abincin kirki ba”. Iyyani ta faɗa idonta akan kwanikan gaban Kaka da ya gama cin abincin data kawo masa bayan fitowarsa wanka. Kai ya jinjina mata da sakin murmushi a karan farko tun bayan shigowarsa gidan. “Alhamdulillahi wanda naci ya wadatar dani”. Kai kawai ta jinjina masa jikinta na ƙara sanyaya. Duk wanda zai sam mijinta a bayanta yake, ta san murmushin sa ba yana nufin farin ciki bane na tsantsar damuwa ce..... “Yaya jikinta?”. Ya katse tunaninta da abinda taketa zumuɗin san ji a bakinsa. “Alhamdulillahi da sauƙi”. “ALLAH ya ƙara afuwa. Bara na ganta”. Ummu na zaune shiru ta tsurama waje ɗaya idanu suka shiga. Har suka kai zaune gefenta babu alamar tana san da zuwan nasu. Kaka ya kafa mata idanu na wasu sakanni sai kuma ya kauda kai. Taɓata Iyyani tayi, ta kawo nannauyan numfashi da ɗan zabura na ganinsu a ɗakin dan da gaske bata san da shigowar tasu ba. Kaka ta kalla idanunta na cikowa da ƙwalla, sai kuma ta duƙar da kai ta fara gaishesa. A hankali ya nisa kafin ya amsa a taƙaice kamar yanda tai gaisuwar. “Jumaimah!”. Ya kira ainahin sunanta. “Na'am Baba”. Ta amsa akan laɓɓanta. “Damuwa ko ƙuntata kai bata sauya ƙaddarar bawa. Juriya da tsantsar jarumta baya hana ƙaddarar zuwa. Haƙilo ko nuna ƙarfin iko baya ture ta a lokacin da aka so. Rauni ko rashin tawwakali bazai dawo maka da abinda dama can ba naka bane ba. Haƙuri shike samar da komai koda kuwa a zahiri yafi ƙarfin ƙarfinka”. “Hakane Baba”. Ta faɗa cikin rawar murya. Murmushi ya saki da matsawa kusa da ita sosai. Ɗa a gaban iyayensa baya girma koda ace yayi furfura a saman kai. Kaka ya riƙo hanun Ummu cikin nasa, ɗayan kuma ya shafa kanta. “ALLAH yayi miki albarka. Yasa ƙaddarar su ta zama kaffara a garemu baki ɗaya.” “Baba mun rasa su suma ko?”. Ummu dake dubansa idanu cike da ƙwalla ta faɗa. Murmushin ya sake sakar mata. Sai kuma ya girgiza kansa da kwanto da kanta bisa kafaɗarsa. “Bamu rasa su ba, ba kuma mu fidda rai da samunsu ba”. A hankali hawayen da suka kasa fita a idonta tsahon kwanaki suka fara sauka a kafaɗarsa....... ★★.... ★★.... ★★..... Mummunan mafarkin da ALLAH ya bata ikon cin galaba a cikinsa ta farka a zabure, cikin amincin UBANGIJI harshenta ya ambato addu'ar tashi daga barci kamar yanda musulinci ya ɗoramu akai. Ajiyar zuciya ta sauke da saka gefen bargon data lulluɓa ta yarce gumin da yay ma goshinta jalab, sai kuma ta sake lumshe idanu jin sautin kiran salla da take ƙyautata zaton a masallacin cikin masarautar ne. Hasken ɗakin ta kai hannu ta ƙara, ta bi ko'ina na cikinsa da kallo tamkar zataga munanan halittun data gani a cikinsa a mafarki. Rashin ganin komai a zahiri ya bata ƙarin gwiwar sakkowa a gadon ta nufi toilet. Bata damu da rashin ganin Tajwar Eshaan a ɗakin ba duk da taji Malikat Haseenat ta ambata nan ɗin matsayin ɗakin barcinsa na daren jiya. Ƙarancin shekarunta da wautarta yasa bata ɗauki tsallakewar komai ba. Abinda kawai zuciyarta ke mata kaikawo a rai shine ta tsallake daren na jiya dai koma yaya ne, ta tsallake tarihin mutuwa a daren kwana turakar dodon matsafa. Dalilin tsallakewar, ko barinta da yay da ranta ne bata sani ba, ba kuma tasan tayaya ya kamata ta sani ba. Abinda kawai take da damar yi shine buɗe kunne da idanuwa taga mizai biyo baya ga kowa da kowa. A yanzu ɗin ma tayi zaton ganin jinin kamar jiya dai, sai dai babu alamar hakan har ta kammala uzirinta tayo alwala ta fito. Tana idar da salla wani irin nannauyan barci ya dinga fisgar idanunta. Dakewa tai cikin dauriya tai zaman yin azkar, da ƙyar ta iya kammalawa barci yay mata baban fisga a wajen dole takai kwance tana ambaton sunan ALLAH. A hankali ta fara sauke numfashi alamar barcin nata mai nauyi ne.... ★★.... ★★..... A cikin masarauta tako ina an gama baza kunnuwan jin fito da gawar Zawjata-almilk. Hatta da Malikat Haseena bata tare da nutsuwarta gaba ɗaya. Tun ana ƙirga sakanni a bayan sallar asubahi har aka koma mintuna, mintuna suka koma awanni babu wani labari. A take aka koma ƴar ƙus-ƙus tun daga kan hadimai har manyan masu faɗa ajin masarautar. Yayinda suma Hadiman sashen Shahan-shan suke zaune jigum-jigum na jiran tsumayen abinda kowa keda tabbacin zai kasance. bakunansu cike yake taf da abubuwan faɗa akan abinda suka wayi gari da shi mai matuƙar rikitarwa da zai maimaita faruwa bayan ya faru ga duk wata Zawjata-almilk data kwana ta tashi a wannan sashen. Duk ɗunbin yawan abin cewar iyakarsa zukatansu dan ko'a tsakaninsu bai faɗuwa balle gulmantawa a waje saboda tako ina camara ce zagaye da su..... *_★MALIKAT BUSHIRAT★_* Ba'a safiyar yau ba, ita tun ma a daren jiya tai hanun riga da nutsuwa. Gaba ɗaya a daren ko sau ɗaya bata iya ta rintsa ba. A maimakon barci ma idanunta akan sashen Shahan-shan da kowa ke iya gani daga nasa sashen a cikin masarautar suka kwashe mafi yawan awannin daren na jiya. Tayi yunƙurin kiransa amma wayar a kashe, hakanne ya sake ɗaga mata hankali da jin zafin wannan hukunci na Malikat Haseenat a karo na farko. A ganinta ganganci ne miƙa nagartacciyar yariya irin Iffah hannun gudan jinin nata bayan Mamma tasan minene makomar yin hakan ga rayuwar yarinyar. Duk jarumtarta a duk sanda ta tuna zuwa safiya gawar yarinyar ce zata fito takanji ƙwalla sun cika idonta. Amma takan danne ta hanasu fitowa har garin ALLAH ya kammala wayewa... Tun idar da sallar asubahi bata iya ta motsa ba, ƙirjinta ne ke matuƙar bugawa da jiran tsammanin mummunan labari..... *_★DANEEN AMMARAH★_* A ɓangaren Daneen Ammarah itama a kwatankwacin irin halin da Malikat Bushirat ta kwana ta tashi take ciki. Dan ita kwana tayi ma tana hawaye. Har ƙarƙashin zuciya takejin matsanancin ƙaunar Iffah. Tana jin yarinyar a matsayin cikon wani gurbi data rasa irin na kowace uwa mai shekarunta. Sai gashi Mamma da ta fara bata tsoro a daren jiya ta rusashi da maye gurbinsa da fargaba mai matuƙar tsanani da razani. Wani mutum saɓanin jininta bai taɓa mamaye zuciyarta da ƙauna mai ƙarfin haka ba kamar yanda yarinyar tayi mata. Sosai take jinta a rai da jinin jikinta. Itama dai tun daga sallar asuba bata sake iya kataɓus ba tai zaman jiran tsammani irin na duk wanda ya kwana ya tashi a cikin masarautar....... ★★... ★★.... ★★.... Harya gota ɗakin cikin shiga ta blue ɗin jallabiya mai tsananin ƙyau da ƙyalli mai ɗaukar ido da nuna taushinta a zahiri dake nuna daga masallaci yake ya tsaya cak. Kamar bazai motsa ba sai kuma ya juya kansa a sannu yana kallon ɗakin. Kallon kusan minti ɗaya da wasu sakanni ya motsa gaɓɓansa cikin takunsa na izza da kame kai ya tura kai ciki. Da farko rashin lura da ita ya sakashi yin tsamm, sai dai fuskarsa ta nuna dakewa kamar koyaushe. Ya ɗaga ƙafa da niyyar juyawa ya fita idanunsa suka sauka a kanta. Yay tsai yana kallonta na tsahon mintuna kusan huɗu tamkar mai rarrabe ita ɗin ce ko wata? Dan a kallo ɗaya zaka fahimci salla ta idar a wajen barci yay awon gaba da ita. Ya ɗan furzar da numfashi da kauda kansa gefe ya sake bin ɗakin da kallo kai kace baƙonsa ne har ya sake direwa akan fuskar Iffah dake ta barcinta numfashinta na fita a hankali.........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_33_* .........Ƙarfe takwas da rabi dai-dai agogon ƙasar ɗaya daga cikin amintattun Hadiman dake gyara ɗakunan barcin na Tajwar ta iso cikin faɗuwar gaba hanunta ɗauke da akwati da aka kawo yanzun nan daga sashen Malikat Haseenat matsayin kayan da Iffah zatai amfani da shi. Zuciyarta har wani zallo take na fargabar abinda take da tabbacin tozali da shi kamar yanda sukayi a baya ga sauran Zawjata-almilk da suka shuɗe. Ta tura ƙofar cikin sanɗa tana mai ambaton sallama da rawar harshe badan tana tunanin samun amsa ba. Ganin Iffah kwance a saman gado, lulluɓe da lallausan bargo baisa taji ƙwarin gwiwa ba. Tai yunƙurin ajiye akwatin hanunta, cak ta tsaya dukkanin idanunta na fitowa waje dan firgici ko sumar tsaye sakamakon juyi da Iffah tai alamar gyara kwanciya. Akwatin ta saki ƙasa ta shiga jan jikinta dake ɓari baya-baya harta dangane da ƙofa gab..... Iffah dake ƙoƙarin gyara bargo idanunta rufe ta buɗesu da sauri saboda jin ƙarar bigewar hadimar. Da mamakin jinta kamar a gado ya sata shashshafa hannunta. (Tabbas gadonne) ta ayyana a zuciyarta tana sake buɗe idanunta da ƙyau tana mai yunƙurin tashi zaune. Tuni hadimar nan ta sake firgicewa, da lalube ta murɗa handle ɗin ƙofar ta fita a guje. Kallon ƙofar Iffah tayi, sai dai hadimar ta gama ficewa bayanta kawai ta ɗan gani kaɗan da wulgawar mayafinta. da sauri ta yaye bargon da bata san ya akai yazo jikinta ba. Ta dire ƙasa mamakin duniya na cigaba da dabaibaye ta. “Wacece wadda ta fita? Mi tazo yi? Wai ta yaya ma na dawo saman gadon nan bayan a ƙasa na kwanta?”. Ta shiga jerama kanta tambayoyin da bata san inda zata samu amsarsu ba. Sai kuma ta ɗan kamo rigar jikinta ta kai hancinta. “Ya ALLAH, da gaske fa wannan mayataccen ƙamshin a jikina ne?”. Ta sake faɗa a fili tana sake shinshinar rigar...... A ɓangaren jama'ar masarauta dake a zaman jigum-jigum kam fitar hadimar nan ya isar da saƙon Zawjata-almilk na raye. Da farko duk wanda zancen yaje kunensa ɗaukewar numfashi na wucin gadi ne ke riskarsa, sai kuma rashin gaskatawa a zahiri ya biyo baya. Hatta da Malikat Bushirat da Daneen Ammarah yanayi da ruɗanin jin hakan bai tsallakesu ba suma. A kusan tare suka ɗauka wayoyinsu domin neman Iffah ko zasu samu jin gaskiyar zance. Cikin Sa'a kuwa ta Daneen Ammarah ta fara shiga.... Iffah na zaune har yanzu cikin ɗaurewar kai akan wanda ya maidata saman gado da wulƙawar fitar wadda bata sani ba wayarta ta katseta. Numfashi taja ta fesar da ɗan ƙarfi tana kai hannu akan wayar. *_Mamy_* ta gani rubuce ɓaro-ɓaro. Ganin zata katse tai ƙarfin halin ɗagawa ta kai kunne tana faɗin, “Assalamu alaikum. Amincin UBANGIJI da rahamar sa su yalwatu a gareki Mamy barka da safiya”. A matuƙar razani da motsuwar zuciya Daneen Ammarah taja numfashin dake neman ƙwace mata. “Ibnati!”. Ta ambata cikin son tabbatarwa. “Na'am Mamy”. Iffah ta amsa kanta tsaye babu alamar irin fargabar dake harshen Daneen Ammarah ɗin a tattare da ita. Dan ita wanda ya ɗauketa daga ƙasa ya maida saman gado da fitar macen data ganine kawai damuwarta a yanzu. Daneen Ammarah da taji al'amarin tamkar a mafarki ta lumshe ido hawaye na silalo mata saman ƙyakykywar fuskarta a hankali. Ƙasa takai durƙushe tana mai godema UBANGIJI ta hayar kai goshinta ƙasa tai sujjadar shukur... Iffah da mamaki ta cigaba da ambaton “Hallo Mamy! Mamy kina jina kuwa?”. Shiru babu alamar za'a amsa. Yanke wayar tai da yunƙurin sake kira a zatonta matsalar network ce sai ga kiran Malikat Bushirat ya shigo shima. Ɗan jimm tai tana kallon wayar, sai kuma ta ɗaga takai kunne da sallama nan ma. Malikat Bushirat da idanunta ke cikowa da ƙwalla sakamakon jin muryar Iffah tar-tar a kunenta ta kai zaune tana ambaton sunan ALLAH. Iffah na son tambaya tana jin nauyi, sai kawai tai shiru tana sauraren kalmomin godiya ga ALLAH da Malikat Bushirat ɗin ke ambata daga can. (Ya rabbi! Wai mike faruwa ne haka?) Ta ayyana a zuciyarta da al'ajabi. Knocking ƙofa da akai ta hanyar danna alerm a dai-dai lokacin ya katse tunanin nata. Ta kai dubanta ga kofar babu alamar zata tanka har aka sake danna alerm ɗin sannan tai ƙarfin halin amsawa da bada umarnin shigowa tana gyara mayafin data yanama kanta.. Hadimar ɗazun ce dai ta shigo ɗauke da ƙaramin tray mai ɗauke da butar shayi. Kanta a ƙasa ta ajiye a inda ya dace tana mai zubewa ƙasa durkushe. “Amincin ALLAH da tsahon rai mai albarka su kasance tare da Zawjata-almilk Barka da safiya”. Iffah da ke kallonta ta amsa cikin motsa lips ɗinta kaɗan. Sabo da hakan yasa hadimar bata damu da rashin amsawar Iffah ba. Cikin sake rissinar da kai tace, “Ya Zawjata-almilk yanzu lokacin wankanki ne, bayan nan karin kummalo na jiranki tare da Shugabana”. Yanzu ɗin ma kamar Iffah bazata amsa ba sai kuma ta jinjina kanta. “Kije abinki zan fito”. “Umarninki shine abin jirana. Amma a gafarceni zan haɗa ruwan”. “Kije abinki zan yi komai da kaina”. Babu yanda hafimar ta iya dole ta miƙe domin bin umarni shine kawai huruminsu. Da kallo iffah ta bita abubuwa masu yawan gaske na son fara mata kutse a ƙwaƙwalwa da zuciya. Ƙwarin gwiwar da take bama kanta akan turesu ya sata miƙewa ta nufin toilet tana mai ambaton addu'ai a bakinta saboda tuna abinda taci karo da shi a daren jiya a toilet ɗin. Ko'ina tsaf, kuma cikin ƙamshi irin na daren jiya. Sai da ta ƙarema komai kallo fiye da jiya kafin ta ɗage kafaɗa irin na koma miye ta shirya masa. Tsabagen rigima da wuce wuri ko tsageranci za'ace ta haɗa ruwanta mai ɗumi da zuba duk wani nau'in turaren wanka da aka jera domin Shahan-shan ta shige cikin kwamin wankan tai luf. Sai da taji ko'ina nata ya miƙe yanda take buƙata sannan ta fita a ruwan domin fara wanka... Tsaf ta kammala shirinta cikin doguwar rigar material sky blue da akaima ɗinkin daya fidda ainahin halittarta tamkar ƴar tsanar roba. Rigar ta zauna mata ɗas, siririn mayafin da aka haɗa rigar da shi ta naɗa tamkar yanda larabawa keyi, ta ɗakko after dress shara-shara mai kamar alƙyabba ta ɗora a sama kalar blue sosai. Ta ɗanji babu daɗi na rashin turarurrukanta tare da ita, dan ko waɗan nan kayan ganinsu kawai tai, cikin ɗan taɓe baki da ɗage kafaɗa a zahiri ta dinga kwasar turarrukan da taci karo da su a ɗakin cikin wani ƙyaƙykyawan glass dake kusa da mirror ta dinga zazzagama jikinta har sai da ta gamsu ƙarfin kamshin zai kai duk inda mai rai ke numfashi a sashen sannan ta haƙura. Idanunta ƙyam a mirrorn ta saki ƙayataccen murmushi da kanne ido ɗaya a fili ta furta “Irin wannan haɗuwa haka autar Ummu”. Tai salute ɗin kanta.... Sautin ƙarar takun takalman ƙafarta da mayataccen ƙamshin tiraren da shi kaɗai aka sani da shi ya sashi tsayawa cak daga ƙoƙarin kai hannu a abincin da aka gama haɗawa gabansa. Fararen idanunsa tar-tar tamkar madara ya ɗago ya sauke a kanta. Hakama hadiman dake a tsaye ta gefe da gefensa kawunansu a ƙasa cikin yanayin mutuwar tsaye data rikesu suka zube ƙasa kan gwiyawunsu illahirin jikkunansu na ƙyarma akan dalilai guda biyu. Na farko ganin tabbatar da wadda suka gama fidda rai da jiran tsammanin ganin an shigo fidda gawarta tamkar Zawjata-almilk na baya dai na raye ɗin kamar yanda Hadimar ta gano. Na biyu ƙamshin turaren jikinta da ga mutum ɗaya tak ake iya jinsa a duk faɗin ƙasar ruman ma bawai a daular ruman ba... Tamkar Iffah bata fahimci halin da suke a ciki ba ta ƙaraso cikin katafaren falon batare data dubi ko ɗaya a cikinsu ba balle mai gayya mai aikin. Cikin sauri ɗaya daga cikin hadiman ya miƙe ya gyara mata kujera, zaune ta kai tana mai dubansa a karo na farko. Tuni shi kuma ya maida kansa ga abinda yake yi tamkar bai san da zuwan tan ba. Ta taɓe baki da juya idanunta ta maida ga hadimar dake ƙoƙarin fara haɗa mata abincin. Nunin abinda take buƙata tai mata da ɗan yatsa. Hadimar na kammalawa ta koma cikin ƴan uwanta ta tsaya itama kanta a rirrine. Gaba ɗaya jinta take a takure, kwarjininsa ya cika ko'ina a falon. Cikin dakewa da kaucewa gizago sa ta ɗan ɗago ta ɗan saci kallonsa da nufin gaishesa idanunta suka shige cikin nasa da ya ɗago da nufin kallon nata... “Who are you?” Ya fara faɗa cikin basarwa yana kaɗa idanusa da har yanzu ke cikin nata tamkar bashi yay maganar ba. Badan a idanunta tausasan lips ɗinsa suka motsa wajen ambaton wacece itan ba zata iya gaddamar hakan. Kaifin idanunsa sun neman sage duk wani ƙwarin gwiwarta. Ƙoƙarin fara sassauta nata idanun tai yunƙurin yi cikin ƙanƙance su sannu a hankali. Shima sai ya kankance nasa kamar yanda takeyi, fuskarsa na sake tsukewa babu alamar sassauci tattare da ita. Nata ta fisga da ƙarfi ta lumshe su, sai kuma ta buɗe a kansa tana mai sake tsuke tata fuskar itama, bazata iya jure salon nasa ba dake neman ƙone ƙudirinta, dan haka ta kauda kanta gefe babu alamar zata bashi amsar da yay yunƙurin ji daga garetan.. “Barka da safiya”. Ta faɗa a ƙoƙarinta na basar da tambayarsa ta farko. Bai motsa ba, babu alamar kuma zai amsa ta. Hakan sai ya sake sukar zuciyarta harta ɗan saci kallonsa, da sauri ta kauda idanunta, dan da gaske fuskarsa ruguza mata lissafi take, da gasken gaske shi ƙyaƙyƙyawa ne, irin ƙyawun dako a cikin ƙasar tasu ake yabawa da shi, koda yake batai mamakin hakan ba, dan Malikat Bushirat ba'a magana, duk da girma ya fara zuwa gareta tsantsar ƙyawunta a bayyane yake. Hakama Malikat Haseena dake matsayin kakarsa data haifi babansa tunda ita dai bataga baban nasaba ko'a hoto har yanzun, amma zubin Malikat Haseena dana Daneen Ammarah ya tabbatar mata shima ɗin dai zai kasance ƙyaƙyƙywan ne...... “What is your goal in life?”. Kalmomi guda shida suka katse mata tunani a bazata. Ta kallesa tana ƙoƙarin danne mamakinta kan waɗan nan tambayoyi da yake faman yanko mata kai tsaye. Ganin yanda ya zuba mata ƙasaitattun idanunsa masu firgita mara gaskiya ta janye nata tana yamutse fuska. (Damarki ce wannan) wata zuciya ta ayyana mata. Cike da gamsuwa ta sake kauda kai gefe dan har yanzu tanajin kaifin idanunsa a kanta. “Ni ban kasance kowa ba sai talakar dake a ƙarƙashin mulkinka ranka ya daɗe. Abinda nake son cimmawa kuwa a rayuwata irin abinda shugaba ke fatan cimmawa ga talakawan ƙasarsa ta hanyar mulkarsu da fuska biyu ne”. Yanda tai maganar kanta tsaye babu ko ɗar ya sashi jin mamakinta. (Tabbas wannan abar ba mutum bace) zuciyarsa ta tabbatar masa. A zahiri sai ya ɗauke kansa cike da basarwa. Shiru babu alamar zai sake tankawa har Iffah tama fidda rai ta cigaba da tsakurar abincinta kamar yanda yakeyi shima. “Wasa da rayuwarki kuskurene ga ƙarfin halinki, ƙin kasancewar ki tarihi a wannan safiyar bashi ke tabbatar miki nasarar tsallakewa ba”. A yanzun kam zantukansa sun zama masu matuƙar tasiri a fitarsu da saurarensu gareta, jin bazata iya dannewa ba ta amsa batare data ɗago ta kallesa ba, “Hakane shugabana, sai dai fa _Fate is some thing undeniable”_ Ya basar babu alamar yanzu ma zai amsa, shayin sa ya kai baki cike da ƙasaita. Itama sai bata sake cewa komai ba ta cigaba da cin abincin tana mai kallonsa ta gefen ido, sannu-sannu tabi sautin motsa plate ɗin gabansa da kallo har kan lallausan farar fatan hanunsa masu ɗauke da tsaftatattun fararen dogayen farce, baya tai ƙoƙarin jan jikinta batare data yarda idanunta sun wuce kallon hanun nasa ba. Yanda ya basar da ita ɗin kuma sai yay matuƙar sukar zuciyarta, dan bata buƙatar tattaunawar tasu ta tsaya iya haka. Amma sai bata yarda fuskarta ta nunaba. Sai ma mamakin ƙasaita da tsantsar izzar wannan bawa da zuciyarta ke faman yi. A wani ɓangaren ita kanta dakewa kawai take, amma kwarjininsa da gizago na firgita ta matuƙa. Tana ƙara tsarkake sunan ALLAH akan yarda da jinin mulki gaskiya ne. Duk da ta shigo daular ruman da wani ƙudiri a ranta hakan bazai hanata girmamashi ba, koda ace tayima yunƙurin hakan kwarjinsa bazai bata damar yin saɓanin girmamawar da kowa ke masan ba. So take taji tsanarsa a ranta kamar yanda takeji kafin ganin wannan fuskar matsayin shi amma zuciyarta taƙi bata haɗin kai. Numfashi taja a hankali ta fesar a ƙasan maƙoshinta. “Kokawa da ƙaddara a fuskar iyawa na nufin faɗuwa! Kinga ko what you get is, what you have?”. Ya faɗa cikin katse mata tunani dai-dai yana ɗagowa.......✍️ “Fareedatu kibar danginmu su tsinkayi yini da kwana cikin sallama, Banda taro dutsen zuma inake ina kace nace da dodon may...🥱🏇”. *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_34_* ........(Mi wannan mutumin ke ƙullawa?). Ta faɗa a zuciya batare data motsa ba. (Keda ke neman kusanci da shi dama miye matsalarki da koma mi yake nufi) wata zuciyarta ta sake ayyana mata. tamkar wadda aka zaburar sunan Arfa da Fariha ya fara amsa kuwwa a zuciyarta har tana jinsa yana tashi bisa sararin samaniya. Kaifafan idanunsa masu nuna tsaurinsa ya zuba mata ganin ta basar da shi itama. Kusan mintuna uku babu alamar zata tankama zancen nasa har ya fara jin haushi. Ta taɓe baki da kauda kanta gefe, cike da dakewa ta furta, “Da gizago na tsorata ƙwarin gwiwata da bazan amincewa shigowa ramin zakin da ɗanyen nama shine abincinsa ba. Karka damu a kaina ranka ya daɗe, dan a wannan gaɓar *_cuta ce ta ɗakko cuta, ɓarawo ya ɗakko akwatin maciji”._* Fuska ya ɗan motsa kamar zaiyi murmushi, sai kuma ya basar. “Bana haɗa ƙwanji da mage duk da kamaninta na yanayi da nawa matsayina na ZAKI har a hallaya. Ki kama kanki dan kina buƙatar rayuwa mai tsaho wajen moran ƙuruciyarki”. Ya faɗa da muryarsa mai zurfi da ƙasaita yana miƙewa ya zagayeta ya wuce abinsa. Shiru bata motsa ba har ta gama jin ɓacewar sautin takunsa a wajen, ta ɗan cije bakinta “Zaki zako ka magantu fiye da haka”. Ta faɗa a fili cike da kwaikwayo salon maganarsa tana sakin wani lallausan murmushi da kai kofin shayi a bakinta, duk da zafinsa ta rumtse ido ta kwankwaɗe abinta sannan ta juya taima hadiman dake tsaye har yanzu kallo ɗaya ta ɗauke kanta batare da damuwar komai ba, dan tasan basuji komai ɗin ba da suka tattauna. A yanda suke maganar ma wani sai ya ɗauka wani zancen soyayya ne ya haɗasu. Komai batacema kowa ba itama ta miƙe tabar wajen, duk suka bita da kallon ƙasan ido kowa da abinda yake ayyanawa a zuciyarsa. A tafiyar tata tana ɗan kalle-kalle taci karo da camara, komai bataji a ranta ba, dan tayi tsammanin hakan tun farko, saboda babu yanda za'ai sashen mutum mai ƙarfin iko kamar Tajwar ace babu wani tsaro makamancin hakan koma fiye da hakan. Da ƙyar ta iya gane ɗakin data kwana. Tana shiga ta zube a kujera da sauke nauyayan numfashi, ɗakin da akaima gyara ɗan gaske tabi da idanu, sai taga ma kamar ba'a cikinsa ta kwana ba, ganin akwatin kayanta kawai ya tabbatar mata da shi ɗin ne. Tunani mai ƙarfin gaske ta faɗa kusan kashi uku zuwa huɗu musamman akan kawota da Malikat Haseena tayi, mi tsohuwar ke nufi da haka bayan su suka sanar mata an rasa matan baya ne a dalilin kawosu turakar Shahan-shan ɗin. Sai kuma akan Tajwar Eshaan ɗin, na farko waccan fuskar data gani a waje kafin shigowarta masarautar matsayin matarsa. Na biyu wannan fuskar ta yanzu da bata da banbanci da waccan ɗin, na uku hanyar da ya kamata ta cigaba da bi domin sanin ainahin wanene Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed a baɗini da zahirin rayuwa. Domin da gasken gaske tana a cikin ruɗani akan fuskokin nan biyu data gani a mabanbanta muhallai. Su ƴan biyu ne? Kokuwa shi ɗinne ke ɓadda kama yana fita?. Abu na uku kuma abinda ya faru a daren jiya da sai a yanzu yake bata matuƙar mamaki, tun a jiyan bawai ta ajiyesa a gefe bane dan bashi da muhimmanci ga haɗarin da tasan ta kawo kanta ciki, kawai dai bata san dalilin da yasa bataji ko ɗar ba a zuciyarta na tsoro, kuma har yanzu batajin tsoron sam, dama kuma tun asali bata da tsoron. Dan Iffah irin mutanen nan ne masu ƙesashiyar zuciya mai iya tunkarar komai koda yanada haɗari a garesu, tanada naci da zama kaifi ɗaya akan zimma da cimma buri duk da ƙarancin shekarunta. Na ƙarshe tattaunawarsu ta yanzu da shi da girman kalaman da yay amfani wajen jifanta da su. Ta ɗan murmusa da cije lips ɗinta tana mai lumshe idanu a hankali...... ★★.... ★★..... Zuwa yanzu tako ina maganar tsallakewar Iffah ce ke kaikawo a cikin masarautar. Kowa ya nutsu wajen tattauna abinda ke bakinsa da abokin maganarsa. Wasu jin daɗine game da hakan, wasu ko baƙin cikine a ransu, dan mutuwar Zawjata-almilk ɗin kamar wani makamine a hannayensu na dukan nasarar Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed ɗin. Tsallakewar Iffah kuma zai kasance kamar damar ƙalubalantarsa da suka riƙe ya kuɓuce musu kenan. Ita kuma yarinyar kimarta da nunawa duniya tafi ƙarfin masu ƙarfin zai yi tasiri a zukatan jama'a..... ★Komai dake faruwa yana isa da shiga a kunnen manyan masu faɗa aji ta bangaren iko da kusanci da Tajwar Eshaan ɗin. Wato Malikat Haseenat da Malikat Bushirat. Sai dai sunyi biris babu alamar zasu tofa nasu akan hakan bayan bayyanar farin cikinsu akan fuskokinsu daya gaza boyuwa ga kowa. Dan a dalilin wannan al'amari Malikat Bushirat har ƴafiya tayi ga wasu firsinoni dake a cikin kurkukun masarautar akan wasu laifuka nasu da basu kai sun kawo ba. A cikin sunne kuma aka sallami harda Diwa a dalilin bincike daya tabbatar da bata da hannu game da abinda ya faru ga Iffah a waccan ranar. ★A ɓangaren Malikat Haseenat kuwa maimakon bama abinda ke zuwama kunenta muhimmanci hankalinta ta maida wajen tantance hadiman da zasu koma aiki a karkashin Iffah ne bisa taimakon Daneen Ammarah da farin cikinta itama yake a bayyane. Dan itama dai har kyaututtuka na musamman yau ta bada ga hadimai tare da sakawa a tattaro mata dukkan malaman masarautar zuwa sashen Iffah da bukatar suyi saukar Alkur'ani mai girma. Ta kuma miƙe da karfin jikinta wajen shirya lunch na musamman ga Tajwar Eshaan da amarya Iffah Zawjata-almilk... *_★BARRISTER★_* Abubuwan da suka faru sun sakashi dakatawa a zahirance bisa shawarar Kaka. Sai dai yana cigaba da gudanar da wani binciken sirri dan yayma kansa alƙawarin binciko duk mai hannu akan wannan al'amarin nasu Babiy da ma inda aka ɓoye su. Kamar yau ma tun jijjifin safiya ya fito daga gida. Kai tsaye hanyar jihar Hubab ya nufa inda bincikensa ya tabbatar masa nanne ainahin jihar da matar Abu Moosa ta fito. Jihar Hubab makwafciyar Dahab city ce (Daular ruman kenan) dan haka a cikin ƙanƙanin lokaci ya isa. Bai tsaya sanyaba ya ɗauka hanyar ainahin kauyensu kuma. Kasancewar anan ma hanyace shimfidaɗɗiya a kanƙanin lokaci ya isa. Da farko ya sha wahalar binciken inda gidansu yake, sai da yay dabarar nuna hotonta sannan. Kusan mintuna goma bayan isar da saƙon tanada baƙo gareta ta fito cikin irin shigarsu. Tayi ɗan tsamm alamar shan jinin jikinta kafin ta ƙaraso a yanayin son basarwa. Barrister shi ya fara gaidata, tare da sanar mata sunansa. Lokaci ɗaya ruɗani ya bayyana akan fuskarta ta shiga waige-waige irin na rashin gaskiya da ƙoƙarin ja baya daga garesa... “Bawan ALLAH ina baka shawara ka taimaki kanka ka bar ƙauyen nan, babu wani abu da zaka iya ji a gareni dan ban san komai ba”. A fusace Barrister yay tsalle gabanta yana huci. “Baki san komai ba amma akaje da ke har gida aka kamasu. Karki sha mamakin bayan sanin inda kike har wasu abubuwa na sani a kanki Mss Farishta. Rashin bani haɗin kai kuma na nufin na tonasu kowa yasan ke ɗin wacece har ma da dalilin auren Dawood, sani kankine wannan babban koma baya ne a gareki kuma harma da zuri'arki”. Yayu ta haɗiya masu kauri tana kallon Barrister, sai kuma ta sake wawwaigawa tabbacin dai akwai abinda take shakka. “Naji Barrister zan baka dukkan bayanan da kake buƙata, amma ina roƙonka kabar wajen nan, idan ma zai yuwu kauyen nan gaba ɗaya nake son ka bari. Wlhy na maka alkawarin zan zo na sameka na kuma faɗa maka komai da kake buƙata harma wanda baka sani ba”. “Miyasa bazan sani ba a yanzu?”. “Saboda zamanka anan yana da matuƙar haɗari”. “Taya zan tabbatar da zaki zo ɗin?”. “Na baka dama kabi duk hanyar da zata bibiyi al'amarina”. Kafaɗarsa ya ɗan ɗage sama da faɗin, “Okay inaga bana bukatar hakan, kije kawai ni na san ta hanyar daya dace na bibiyekin. Amma yaushe ne zamu haɗun?”. “Inasha ALLAH a daren yau ka sameni a ƙauyen Jumna”. “Garin su Abu Hanash da Dawood kenan?”. “Insha ALLAH”. Tafiya yake zuciyarsa na faman masa kaikawo akan haɗuwar tasa da Farishta (matar Abu Moosa datazo har gida da ƴan sanda aka kama su Babiy. ALLAH yasa kun gane🥱). Duk da yasan zata iya ƙin aikata abinda ta faɗa na haɗuwar tasu a garin Jimna ya zaɓi barinta su haɗun can bisa lumana. A cikin Hubab ya tsaya yaci abinci tare da sallar azhar. Ya fito masallaci idanunsa suka sake sauka akan wata mota da tun fitowarsa ƙauyen su Farishta ya lura da ita tana biye da shi, sai dai duk da ya ganta suna tafiya kafaɗa da kafaɗa bai kawo komai a zuciyarsa ba. Janyewa yay cike da rashin bama abin muhimmanci ya shige motarsa da zummar zai cigaba da tafiya kawai yaga an zagaye motarsa da bindigu....... ★★★.... ★★.... ★... A firgice ta farka a ɗan barcin daya figeta bayan ta idar da sallar azhar. Ta dafe kanta dake sara mata. Irin mafarkin da tai da dare ne dai babu banbanci. Huci ta furzar da faɗin, “Wace madara ce haka? Tabbas kodaga ina zata fito babu alkairi a cikinta tunda har mafarkin nan ya sake maimaita min kansa. Ya ALLAH”. Ta furta a fili zuciyarta duk babu daɗi, dan zuwa yanzu Iffah ta fahimci wani ɓoyayyen al'amari game da ita, tabbas in har zatai mafarki taita kuma maimaita irinsa sai wani abu ya biyo bayansa mai taɓa zuciya, ta gane hakanne a ɗan zamanta cikin masarautar nan, sai kuma auna abubuwan da suka faru a baya kafin yau ɗin. Sai dai tana ƙoƙarin ƙin gasktama kanta hakan dan kar zuciyarta ta shagala kan abinda zai sakata kaucema umarnin mahaliccinta kuma. Ga kanta jingim kamar yanda yakeyi a duk lokacin datai mafarki makamancin haka, sai zufa data jiƙeta sharkaf tamkar wadda tai wanka. Shigowar saƙo a wayarta da ke gefenta ya sakata tsurama wayar ido na kusan mintuna biyu, kamar wadda aka zaburar wani abu data shafa'a kuma sai ta jawo wayar. Data ta kunna a take tai downloading WhatsApp app..., Bayan ta kammala dai-daita komai tai searching number Sir Fawzan da zuciyarta ke ayyana mata ta fara nema, cikin rashin sa'a taga kusan kwana uku ma baya online ta hanyar lastsin ɗinsa. Duk da hakan bai mata daɗi ba batai wani yunƙurin kiransa ba ta maida akalarta kan number abokinsa Ajmaal. Cikin sa'a shikam dai yana online. Sallama tai masa a taƙaice ta tura, sai dai har kusan mintuna biyu babu reply (yana aiki) zuciyarta ta ayyana mata. Aminta da hakan ya sata cigaba da ajiye masa saƙo kawai a kan duk abinda ya sake faruwa bayan wanda ta tura masa ranar. Daga karshe ta aika masa da roƙon ya bincika mata iyayenta dan har yanzu hankalinta ya kasa kwanciya dangane da su. Ta haɗa masa da adireshin gidansu, da faɗin (In har kaci amanata ko yaudarata na barka da mahaliccin rana da wata yay maka hukunci da alhakin dukkan al'amuran ƙasar ruman da zalincin mulkin wannan shaiɗanin dodo ke tafin hanunsa). Daga haka ta fito shima Sir Fawzan ɗin ta tura masa gajeran saƙo ta goge WhatsApp ɗin gaba ɗayansa ta ajiye wayar. Da ɗan layin nauyin jikin dake tare da ita ta miƙe, tana ƙoƙarin shiga toilet taji kamar an gitta mata ta baya. Idanunta ta ɗan rumtse sai kuma ta waigo. Komai babu dai a zahiri dan haka ta kaɗa kanta kawai ta shige bakinta da addu'a.... Fitowarta kenan bayan ta watsa ruwa alerm ɗin ƙofar yay ƙara alamar ana knocking. Sai da ta zira doguwar rigar abaya data ɗakko cikin kayanta sannan ta ƙarasa ƙofar ta buɗe. Hadimar dake tsaye ta zube ƙasa cikin girmamawa tana kwasar gaisuwa. Amsa mata Iffah tai, zuciyarta babu daɗi akan yanda suke ƙasƙantar da kansu, ta amsa cikin sauƙin muryarta dake a sanyaye sakamakon mafarkin da duk ya sakar mata kasala.. “Wani abu ya faru ne?”. Ta tare hadimar tunkan tace komai. Kai ta gyaɗa mata tana sake rissinar da kanta. “A gafarceni ya Zawjata-almilk. Dama abinci ne aka kawo daga sashen mai Babban ɗaki”. Iffah tai ɗan jim tana hasashen wace kuma mai babban ɗaki? Kamar hadimar ta fahimta tai saurin mata fashin baƙi da “Malikat mai babban ɗaki”. (Malikat Haseenat) shine abinda zuciyarta ta ayyana mata. Ta kaɗa kanta da faɗin, “Okay ba damuwa zan fito”. Daga haka ta maida ƙofar ta rufe. Ciki ta koma, sai dai maimakon zama sai ta koma kaikawo kamar mai Safa da marwa abubuwa masu yawa na faman mata kaikawo. Ta jima a haka sosai kafin ta sake kimtsa jikinta cikin wata tsadadiyar abaya mai adon stones dake ta ƙyalli da ɗaukar idanu. (Wannan yana cikin horon Daneen Ammarah data tabbatar mata koda wasa karta zauna da kazamar shiga ko fitowa da ga ɗaki a raguwar kwalliya. Dolene inhar zata bar cikin ɗakinta ta tabbatar komai na jikinta ya isa a kalleta da shi. A tsarin masarautar hakan ba fariyya bane mutunta kaine ga kowa. A kuma ɗan zaman Iffah cikinsu ta fahimci hakan sarai). A yanzu ma kamar ɗazun turarrukan sa ta baza har ƙamshinsu na rige-rigen fita kafin ita ta fita. Ta fito cikin takunta na nutsuwa da ƙasaita kamar wata budurwar macen ɗawisu (🥱😉lol)..........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_35_* ........Hadiman sashin gaba ɗaya kamshin turaren da sukaji ya sakasu tunanin Tajwar Eshaan da bai jima da shigowa ba daga fada ne ya sake fitowa. Sai kuma sukaga saɓanin haka lokacin da Iffah ke ƙarasowa cikin katafaren falon mai ɗauke da duk wani nau'in kayan more rayuwa irin na wanda suka isa. A kujerar da ko ba'a faɗaba tsarin zubinta ya isa tabbatar ma mai kallo Shahan-shan ne kawai ke zamanta ta kai zaune da bismillah a bakinta. Ƙafa ɗaya kan ɗaya ta harɗe fiye da salon sarauniyar Ingila tana kallonsu. Cikin rawar harshe dajin kwarjininta ya cike falon tsaf suka shiga zubewa suna gaisheta. Yatsu biyu ta ɗaga musu cike da ƙasaita batare data amsa ba dan haka kawai yanayin da ta tashi da shi taji bata buƙatar magana. Basu iya sun motsa ba har ta gama zuƙar iska da fesarwa tamkar mai lissafin kaɗawarta sannan ta dubesu, sai kuma ta maida ga tarin abincin da aka shirya yanzu akan wata lallausar darduma saɓanin na ɗazun akan teburin cin abinci. Akan farin tambulan na gilashi mai ɗauke da madara fara ƙal-ƙal ta sauke idanun nata (mafarkina ya zama gaskiya kenan ko saɓaninsa) zuciyarta ta ayyana har lokacin idanunta tsaye akan tambulan ɗin.. Hadiman da basu fahimci ma'anar kallon da takema kayan abincinba cike da girmamawa a gareta ɗaya ke faɗin, “Ya Zawjata-almilk abincine daga saken mai babban ɗaki, an shiryashi ne matsayin liyafa gareki ke da shugaba”. A hankali Iffah ta janye idanunta daga wajen ta maida kan hadimar na tsahon wasu sakkani, acan ƙasan zuciyarta kuwa nanata sunan Malikat Haseenat take tamkar mai bitar karatun hadda. Batare da tace komai ba kuma sai ta kaɗa kanta. Shiru ya sake biyo baya kafin Iffah ta katseshi da duban hadiman da har yanzu dai ke tsaye da alama zaman jiransu sukeyi kenan, dan ta fahimci idan zaici abinci haka suke zagayesa. Kanta ta kauda da faɗin, “Maleek fa?”. Kai tsaye duk suka fahimci wa take nufi, tunda dai duk sun san minene ma'anar kalmar Malik ɗin. Cikin tsantsan da kai ɗaya daga ciki ta amsa mata da “Yanzu ya shigo daga fada”. Bata amsa ba, sai ɗan jimm da tai na tunani akan ambatar fada da hadimar tayi, amma a zahiri ta basar abinta. ★Kasancewar saƙon haɗa liyafar cin abincin na Malikat Haseenat da tai akan iya shi da wadda ake kira matar tasa ya riskesa tunma kafin Iffah, dan kusan shine ma yay sanadin barowarsa fada duk da Aaminsa Miran Jasim (Aami. Kawunsa)ya buƙaci zaman tattaunawa da shi. Badan son ransa ba ya kimtsa ya fito cikin shiga mai sauƙi ta zaman gida. Kamshinsa da takun sawayensa dake tabbatar da girman ikonsa tuni ya iso a kunne da hancin Iffah dama hadiman dake zagaye da ita. Tuni hadiman duk sun zube bisa gwiwunsu kawuna a ƙasa dan kallon shugaban nasu kai tsaye haramunne garesu bisa al'adar masarautar, idanma hakan ta faru gaban Ghazi zaka iya fuskantar tsatstsauran hukunci a dalilin hakan. Akanta dake harɗe kan kujerar da bayan shi babu wani mahaluki daya iya kwatanta zama kanta ya fara sauke ƙasaittun idanunsa. Dai-dai itama ta ɗago nata sakamakon jin takun sawayensa da zubewar hadiman. Cikin ido suka kalla juna, hakan yay matuƙar tsikarar zuciyar Iffah da abinda take faman hasashe da neman tabbaci a kwanakin nan ya tabbata ɗin yau a idanunta. Dan tabbas shigar jikinsa ta yanzu ta sake tabbatar mata da waccan fuskar... Shine ya fara janye nasa kausasan idanun batare data iya tsinto komai a cikinsu ba. Kamewa da gagara fassara abinda ke kan fuskarsa kuma ya taka rawar gani wajen ɓoye ainahinsa. Sai ma kallonsa da ya maida kan ƙaton agogon dake kafe a falon cike da basarwa kai kace bai ganta bane. Ita madai basar da shi ɗin tayi kamar ma bata san da fitowar tasa ba, sai zuciyarta dake faman kai kawo a ƙirjinta cikin sauri-sauri. So take ta gaskata shi ɗinne kota ƙaryata amma zuciyarta taƙi bata haɗin kan karkata akan ko ɗaya a cikinsu. Sai ma neman jefata a ruɗani takeyi...... *_BARRISTER_* Duk yanda Barrister yaso sanin suwaye su? Mi kuma yay musu basu saurareshi ba suka turasa cikin jibgegiyar baƙar motarsu, yayinda ɗaya daga cikinsu kuma ya shiga motar Barrister ɗin ya fiddo komai na ciki a cikin wata ƙatuwar jakka suka bar wajen.. Suna ɗan matsawa a wajen wani abu mai masifar ƙara ya ziyarci kunnuwan kowa. A take aka fara gudun ceton rai dan duk wanda yasan bomb yasan shine a yanzun ma. “Innalillahi wa inna'illaihirraji'un”. Barrister ya faɗa idonsa nabin motarsa da tai sama ta shiga dawowa pieces ƙasa alamar dai bomb ɗin daga cikinta ya tashi. Duk da ya firgita da mutanen yay jarumtar dubansu fuska a dake. “Ku su waye? Miyasa kuka aikata min haka?”. Babu wanda ya tanka masa a cikinsu, kamarma basu jisa ba sukayi. Hakan sai ya ƙara tada hankalin Barrister, dan ya fahimci ya shiga hannun mugayen mutanen nan kenan. Yunƙurowa yayi da nufin ƙara magana suka jefa masa handkherciff a fuska, daga haka bai sake sanin inda yake ba sai buɗe idanu yay ya gansa a wani ɗaki da bai san inane ba... Gaba ɗaya jihar Hubab da ƙasar Ruman a rikice ake akan tashin wannan bomb, dan abune da bai taɓa faruwa da su ba. Jami'an tsaro sun iso akan lokaci, sai dai Alhamdullah ba'a samu asarar rai ko ɗaya ba daga mutanen gari, amma ana tunanin harda drivern motar al'amarin ya rutsa saboda babu wanda ya lura da sanda mutanen nan suka ƙwamushe Barrister ɗin kasancewar komai sun yisa ne cikin ƙwarewa... Jami'an tsaro da ƴan jarida tuni sun iso wajen akan lokaci, hakama jama'ar gari masu jarumta sun zagaye wajen domin ganema idanunsu. Babu gawar direban motar a duk iya bincike da jami'an tsaro sukayi, dan basu ga wani alamar sassan jikin mutum ba ko ɗan yatsa, hakan sai ya ɗaure musu kai dan mutanen da abun ya faru a idonsu sun tabbatar sunga lokacin da mai motar ya ajiye ta a wajen ya shiga masallaci, koda aka fito kuma mutane da yawa sun tabbatar sunga lokacin daya nufi motar wasu ma sunce har ya shiga. Wannan zance ya sake ɗaukar hankalin jama'a kowa yana faɗar albarkacin bakinsa akan al'amarin... Isowar wasu samari wajen kusan dai-dai da tashin bomb ɗin, kallon juna sukai da sakin dariya a tare suna tafawa. Sai da sukai mai isarsu drivern dake jan motar ya ɗauka waya. Nuni yay musu da suyi shiru. Take motar tai tsit kuwa. Ya ɗan rissina cike da girmamawa tamkar yana a gabansa ne yana kwasar gaisuwa, bai damu da a yanda aka amsa masa a daƙile ba ya cigaba da faɗin, “An rufe babinsa ranka ya daɗe”. Murmushi yayi alamar an amsasa da magana mai daɗi daga can. Sai kuma ya sauke wayar da juyawa yana kallon ƴan uwansa ya kashe musu ido. Dariya suka shiga kwasa a yanzun ma, bayan sanyi wadda suka gamsu sun wadata sannan suka fita suma suma shige cikin taron mutanen dake wajen dan jin mi'ake tattaunawa..... ★★★..... MASARAUTA ★..... Sai da ya kai zaune a inda aka shirya tarin abincin da kusan minti biyu sannan ta motsa itama dalilin maganar da Hadimai sukai mata. Bata musa ba ta miƙe zuwa inda yaken cikin takunta na nutsuwa da wasu ke ɗauka yanga ko makamancin hakan. Zama tai irin nasa na ƙasaita sai dai da alama ita kanta bata fahimci tayi hakan ba ma. Tsaurin idonta ya sakashi dubanta ta gefen ido batare da alamar hakan ta bayyana a yanayinsa ba. Tuni hadiman suka ƙaraso domin shirya abincin garesu. Iffah batai yunƙurin hanasu ba, dan a ganinta dole ta nutsu ta fara fahimtar yanda ake masa komai kafin ta karɓa wannan tsarin shima. Ta ɗan bi madarar da hadimar ta ɗauka, har yanzu zuciyarta na mata wasiwasi akan madarar batare data san dalili ba... “Bar nan”. Ta faɗa dai-dai Hadimar na yunƙurin zuba madarar a ƙaramin cup na glass daya gama haɗuwa. Cikin mamaki hadimar ta sake risinar da kai domin girmamawa ga Iffah tana faɗin, “Ya Zawjata-almilk madara na ɗaya daga cikin abinda shugaba yafi buƙatar amfani da shi a irin wannan lokacin”. Kai tsaye babu ko ɗar tattare da Iffah tace, “Na yau dai bazai sha ba. A ɗaukesa anan”. Tsoro ne ya bayyana sosai a fuskar hadimar, gashi bata da damar ko satar kallon sashin da Tajwar ɗin yake balle ta fahimci karatun tasa fuskar. A ɗan ɗar-ɗar na rashin madafa ta ajiye tambulan ɗin a gefe ta ƙarasa aikinta. Duk da abinda ake yi a gaban Tajwar Eshaan ne, yanaji kuma yana gani. amma tsabar miskilanci da ƙarfin iko irin na masu ƙasa a hannu bai ko motsa ba balle bada wata alama akan abinda Iffah tayi ya bashi mamaki, ko ya ɗimautashi, koya birgesa, koya bashi haushi. Ko ɗaya babu mai iya tsinta a yanayinsa. Iffah ma dai bata yarda ta dubesa ba balle ta tsinta komai a tattare da shi ɗin. Sai ma wani kallon da taima hadiman ya tabbatar musu bata bukatarsu a wajen. Dan haka tuni suka ɓace tamkar ƙyaftawar ido. Ya ɗan ja wasu mintuna zaune batare da ya taɓa komai ba, Iffah ta ɗan laɓe baki, acan ƙasan maƙoshi ta furta “Ranka ya daɗe barka da wannan lokaci”. A hankali ya ɗago ya zuba mata idanunsa, a mamakinsa bashi take kalloba ma. Kuma ya tabbatar itace tai maganar ba wani ba dai. Sake tsukewar fuskarsa mai cike da gizago da motsa hanunsa dake kan spoon ya tilasta Iffah ɗan ɗagowa garesa. Sai kuma ta tsaya cak tare da ɗago birkitattun idanunta da ƙyau. Cikin nasa dake kallonta suka shige tamkar ya tsara hakan da gayya. Muƙut ta haɗiye yawu da ƙoƙarin kame rauninta dake neman bayyana a fili ta kauda kai gefe.. Shima nasan ya janye a ƙasaitance ya fara cakulal abincin kamar mai cin magani batare da ya amsa mata gaisuwar tata ba. Hakan da yay ya sosa zuciyar Iffah, dan haka ta kumbura fuska lips ɗinta suka shiga motsawa alamar akwai magana a bakinta sai dai babu damar faɗa... ★★.... ★.... Tun bayan tabbatar da madarar ta shiga jerin abincin liyafar da aka shiryawa Shahan-shan da Zawjata-almilk ta kasa zaune ta kasa tsaye, bukatarta kawai taji sakamakon da take buƙata ga amintacciyar hadimarta akan lokaci. Sai dai kuma shiru kakeji wai malam yaci shirwa har lokacin da labarin tashin nakiya a jihar Hubab ya iso cikin masarautar. Ba wannan ne a gabanta ba, dan haka cikin jan tsaki ta kashe television ɗin a harzuƙe. Idanunta ta sake maidawa kan agogon falon tanaji kamar tai tsalle ta ganta a sashen Tajwar Eshaan ɗin ayita ta ƙare. Dan yanzu a duniyar nan gani take bata da babban maƙiyya sama da yarinyar nan datai mugun shige mata hanci amma ta gagara fyatota ta huta a dalilin gargaɗin Uwa data kasa gane manufarsa har yanzu. Sai dai yarda da Uwa ɗin ya tilasta mata bin komai ɗin a sannu. Zata iya rantsuwa tunda ta san kanta bata taɓa cin karo da abinda ya kiɗima zuciyarta ba irin saƙon Zawjata-almilk na raye bayan ta kwana a turakar Shahan-shan kuma. Ba ita kawai ba, hatta Uwa hakan ya kiɗimata da sake tabbatar da yaƙine na gaske tsakaninsu da wannan yarinyar kenan. Dan haka batai wani magana mai tsaho da Ta-kurya ba bayan bata umarnin a isar da madarar data bata ga Iffah ta ɓace cikin tsanani ɓacin rai daya ƙara birkita dukkan tunanin Ta-kurya ɗin a yanzu har ta kasa zaune ta kasa tsaye sakamakon hakan........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_36_* ........Isowar labarin tashin nakiya a jihar Hubab ya matuƙar tada hankalin duk wani mai faɗa a ji a daular ruman. Dan abune da bai taɓa faruwa ba a kasar ta ruman. Amma abin mamaki ga Tajwar Eshaan ba hakan bane, dan babu wani alamar damuwa ko nuna kaɗuwa da lamarin. Kallo ɗaya yayma akwatin talabijin ma ya ɗauke kai kamar ba'a ƙasar da yake mulka matsayin shugan kowa da kowa al'amarin ya faru ba. A karan farko wani abu da tun shigowar Iffah masarauta bataji akansa ba ya tsikari zuciyarta sakamakon ganin halin da ya nuna akan wannan al'amari da duk wanda ya kwana ya tashi a ƙasar ta ruman bazai ce bai shiga ruɗani ba. Duk da ance ba'ai asarar rai ko ɗaya ba taji kamar ta tashi ta shaƙure wuyan Shahan-shan ɗin ta huta da ganin wannan azzalumin shugaba da kansa kawai ya sani sai ahalinsa. “Mi hakan ke nufi?”. Ta faɗa tana faman kai kawo a ruɗe itama duk da a labarin an sanar da ba'a samu asarar rai ko ɗaya ba sai dai dukiya. Abu mafi caja ƙwaƙwalwa ga kowa ma ba ita kaɗai ba shine jin wai wanda ya dasa bomb ɗin ya tsere Bayan wasu sun tabbatar da sunga fuskarsa da shigarsa motar, musamman ma wasu samari huɗu da suka tanbatar da tare suke da wannan mota tun daga ƙauyen Lufana da alama mutumin daga can ya fito. Tabbas sai tayi ajalin wannan mutumin a zuciyarta zataji salama. Dan a ganinta idan yau ya tashi kowa bai rasa ransa ba na gobe kuma fa? A wannan gaɓar ta fara zargin anya wannan sarkin bada wata manufa dama ya dawo ya karɓa mulkin mahaifinsa ba? Dan alamu sun fara nuna uban nasa ma shine ya kasheshi. “Lokaci yayi da zan fara aikina gadan-gadan”. Ta faɗa a zahiri cikin tabbatarma kanta da yanayin ɗaukar alwashi.... (Muma kam muna bayanki Iffah, dan muna son sanin mike zuciyar wannan bahagon sarki haka mai wahalar fahimta😉🥱🏇). ★★★ A babban zauren majalisan manyan masu faɗa aji na daular ruman kuwa na can yana neman hargitsewa dangane da faruwar wannan al'amari. Kowa faɗar albarkacin bakinsa yake a duk yanda zuciyarsa ta ayyana masa musamman masu sukar mulkin Tajwar Eshaan a fakaice. Duk wannan kace nace da akeyi Tajwar Eshaan ɗin na zaune cikinsu amma uffan bai tofa ba har suka ci suka tsire. Sai da suka lafa dan kansu da kuma maganar Miran Arshaan cikin ɓacin rai a garesu sannan Tajwar Eshaan ɗin ya buɗe idanunsa dake a lumshe ya gama ƙare musu kallo ɗaya bayan ɗaya.. Akan Miran Arshaan dake cigaba da faɗa rai ɓace kan kausasan maganganu nasu ga ɗan ɗan uwansa kuma sarkinsu a yau basu dace ba ya sauke idanunsa. Cikin muryarsa mai zurfi da ƙasaita ya fara magana a gadarance kuma a fisge... “Barsu Aami. Waninsu bazai canja komai ba, kamar yanda bazai tirsasa Eshaan yin komai ba. Abinda kawai nake son ku sani, Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed guguwace data gama turniƙeku, kuma babu ruwan kogin da zai iya shayar da ita ruwan da zata lafa. Ku daina bama kanku wahala ƙasar ruman da jama'ar cikinta a rubuce suke tsakkiyar tafin hannuna. Idan na murza kwafsanku kawai duniya zata gani a cikin guguwata, idan na matsa, jininku ne zai dinga ɗiga a ƙarƙashin sawun ƙafata na ringa bi ina takawa matsayin kwalta, ya rage naku ku zauna a inda na baku zaɓi ko ku zaɓo mummunan ƙaddararku da kanku tun lokacin ɓacewarku a doron ƙasa baiyi ba”. Yana gama faɗa ya miƙe cike da takun Izza da kasaita ya bar falon. Da kallo duk suka bishi ran wasunsu na ƙuna, zukatansu kam tamkar zasu kifo ƙasa dan firgici. Cikin dauriya da nuna jarumta wani ƙyamusashen dattijo da tsufansa ya fara bayyana a cikinsu yay ƙwafa rai ɓace da kausasa murya. “Lallai wannan yaron ya cika ya tumbatsa kuwa. Wai kenan haka zamu cigaba da zama yaro ƙarami na tafka kuskure da mulkin zalunci yana kuma takamu a yanda ya gadama. Akaf tarihin mulkin daular ruman ba'a taɓa tsageran yaro kamar wannan ba, amma ubansa ya ɗaura shi matsayin Shahan-shan bayan babu mai makamancin shekarunsa daya taɓa zama a wannan matsayin. lokaci yayi da zamuyi bore wajen tsigesa kafin ya gama halaka ƙasar baki ɗaya tunda naga shi ran ɗan adam ba'a bakin komai yake garesa ba. wama ya sani ko shine yasa a dasa nakiyar kamar yanda ya kashe ubansa da ƴaƴan mutane da aka aura masa. Koda yake minene ma na tantama tunda ga amsa ya bamu da bakinsa cewar ƙasar da ƴan ƙasar duk a tafin hannunsa muke”. A zahiri dai kowa yay tsitt yana sauraren dattijon, amma a zukatan wasunsu farin cikine fal da zantukan wannan tsoho ga Tajwar Eshaan ɗin da mafi yawansu shakkarsa ta gama zagaye tunaninsu duk da kuwa kusan duk sun haifesa dan babu wani sa'ansa, dan har yanzu tun ƴan majalissar mulkin mahaifinsa ne bai canja ba. Dattijon na rufe baki Miran Jasim ya miƙe rai a ɓace shima. Dattijon ya watsama wani mummunan kallo da faɗin, “A lallai ka cika dattijon banza dan bazan kalleka matsayin Aami ɗinmu ba yau kam. Mun godema ALLAH daya fara nuna mana ku a zahiri, ai bamu san ɗan ɗan uwanmu ya kai muku har haka a zuciya ba sai yanzu. To ku sani duk ma mai irin wannan tunanin ya makaro, Eshaan kuma a gareku sai gani sai hange sai hararar nesa, dan badai mutum ba ku rubuta ku aje”. Ya kare maganar yana ɗan ƙyaftama Miran Arshaan daya saki baki tsabar al'ajabin ɗan uwan nasa da kasa fahimtar inda ya dosa. Cikin sauri ya kaɗan kansa da amshe zancen a fusace shima yana miƙewa. “Aam ai ban san haka kakeba wlhy sai a yau, ashe zaka zama na farko a jerin wanda zasu soki jinin Haysam Akhi kuma ɗan uwanka mahaifinmu dan ƙasa ta rufe idanunsu? To bazamu ce da ku komaiba a yanzu, amma kusani duk wanda yake da wannan ƙudirin a ransa jininmu fansa ne ga kare Eshaan tako wace fuska. Mun barku lafiya”. Waɗan nan zantuka na Miran Jasim da Miran Arshaan sun matuƙar saka ruɗani a zukatan duk wanda ke a wannan zauren taron. A take wasu suka shiga barranta kansu ga wannan magana ta dattijon Aamin sun ganin waɗanda ma ya dace suyi hanƙoro da kwarema Tajwar Eshaan ɗin baya saboda kwaɗayin kujerar da yake kai tunda suma sunada hakki a kanta na tare da shi su kuma a wa. Anan fa rikici ya kaure aka tashi baram-baram.... ★★ “Nikam na kasa fahimtar dalilin ka nayin hakan”. Miran Arshaan ya faɗa bayan fitowarsu daga zauren tattaunawar. Wani shegen murmushi Miran Jasim ya saki cike da basarwa. Sai da sukai nisa da sashen Tajwar Eshaan gaba ɗaya sannan yay wata ƴar dariya batare daya kalla Miran Arshaan ɗin ba. Shimfiɗa kenan daga cikin plan b, harinmu na gaba shine ƙulla alaƙa da yarinyar nan, dan na san yanzu abinda zatai yinƙurin farawa shine bincike akan wanene shi”. “Wai ya akai duk kake sanin hakan?”. Miran Arshaan ya tambaya cikin mamaki. Dariya Miran Jasim yayi sosai da faɗin, “Arshaan Akhi har yanzu kai ɗin yaro ne. Waya gaya maka mai nema yana zaman jiran tsammani. Tashi yake da ƙwanji da zuciya wajen samowa ai. Karka damu da inda na sani, kai dai kawai ka tabbatar littatafan nan da mukai magana kwanaki an kaisu books room an ajiye a daren yau, dan bana raba ɗayan biyu zuwa gobe zata iya bukatarsu”. Cikin halin ko'in kula Miran Arshaan ya ɗage kafaɗu da tabe baki, sai dai acan ƙasan ransa dariya yake dan shima akwai nasa shirin akan hakan tun randa sukai maganar...... ★★ Duk da fuskarsa mai tsananin ɓoye sirrin zuciyace a yau ɓacin ransa sai da ya bayyana. Huci kawai yake faman furzarwa a kai-akai. Dan daga ɗakin meeting ɗin nasu da ba'a samu damar tattauna abinda ya dace ba kai tsaye sama yay can ƙarshen rufin ginin sashen nasa da aka gyara domin hutawa kawai. Ko gaisuwar hadiman dake tsare da ƙofar shiga wajen baiyi ba. Ya jima yana faman kai kawo hannayensa zube cikin aljihun farin wandonsa. Bakajin komai tattare da shi sai shaƙa da furzar da numfashi. Sai da ya ɗan samu nutsuwar da yake bukata ya zaro waya dake cikin aljihunsa. Kira yay, bugu ɗaya kuwa aka ɗaga, batare daya amsa gaisuwar da ake masa ba a kausashe ya furta. “A sakaya min shi, inda babu wani mahaluki da zai taɓa hasashe a kansa”. Yana gama faɗa ya yanke kiran cikin sake tsuke fuska da zuƙa ya fesar..... (Anya kuwa....?? 🤭bakina kanen kafa ta dai🏇). ★★ A ɓangaren Iffah tana tsaka da kai kawonta da ƙullawa da warwarewa itama wani tunani ya sata tsayawa cak. Miƙewa tai cikin gamsuwa, sai kuma ta koma ta zauna bisa wani tunanin da yazo a bayan wanda ya sata mikewar. A kallo ɗaya zaka fahimci tana cikin yanayin da duk wani ɗan ƙasar zaka iya ganin ya shiga sakamakon wannan baƙon al'amari daya shigo musu. Da farko bai lura da ita ba saboda idonsa rufe yake da ɓacin rai har lokacin, sai da ya kai zaune yay ƙoƙarin lumshe ido sai kuma ya buɗesu a kanta dai-dai itama ta kallesan mamakin yanayinsa na yanzun kuma fes a fuskarta. Ita ta fara janye nata shima sai ya furzar da huci mai zafi yana maida nasa ya lumshe kamar yanda yayi a farko. Falon ya ɗauka shiru babu alamar wani zai tanka sai karar na'urorin ac dana tv da har yanzu ake cigaba da nuna al'amarin da yanda hankulan jama'a ke tashe. Kiran sallar la'asar ne ya katse zaman shirun nasu. Iffah ta fara yunƙurawa ta tashi batare da ta ko sake kallonsa ba dan da gaske har cikin rai haushinsa takeji yau. Da kallon ƙasan ido ya bita harta ɓacema ganinsa. Ya ɗan sauke ɓoyayyar ajiyar zuciya da maida idanunsa ya rufe. Sai da Iffah tai kusan mintuna huɗu da barin wajen sannan ya mike shima har yanzu da alamar ɓacin rai tattare da shi.... ★★★.... Bayan Iffah ta idar da salla kamar yanda ta tsara tai shirinta tsaf cikin wata doguwar riga mai tsananin ɗaukar idon duk wanda zai iya kallonta. Kamshin data gaje batare da umarnin mai shi ba ta baza tamkar tayi ɓarinsa a jikinta. A cikin dukkanin shirinta babu bijirema umarnin waɗan da tazo wannan matakin a dalilinsu, dan haka kai tsaye tai kiran number Daneen Ammarah. Ana ɗagawa tai sallama cikin sauƙaƙa murya mai nuna ladabi. Daga can Daneen Ammarah ta amsa cike da zumuɗi da nuna jin daɗinta da wannan kira. “Shahrbano ce da kanta haka?”. Murmushi Iffah tai mai bayyana haƙora jin sunan da Daneen Ammarah ta kirata da shi. Ta girgiza kai tamkar tana a gabanta. “Mamy zakisa a tsire ni a tsakkiyar daular ruman fa”. Dariya sosai maganar ta bama Daneen Ammarah. Dan haka ta dara sosai kafin ta tsagaita. “Waya isa ya tsire Ibnati kuma Shahrbano duk faɗin ƙasar ruman. Babu mai wannan power ɗin Ibnati, ko maƙiya sun san kin gagara sai kallo daga nesa, dan kowa ya tabbatar a yanzu ke ɗin ce _Lady of the city_”. Komai Iffah bata iya tace ba, sai dai Daneen Ammarah na iya jiyo sautin murmushinta harta gama kwarzantata. “Mamy dama na kiraki ne na shaida miki ina ɗan son na fito zama waje ɗayan ya isheni, daga nan sai na ɗan leƙama ɗakin karatu kozan samo abin ɗebe kewa”. “Hakan kam yana da ƙyau Ibnati. Dan haka ki shirya kawai, hadimanki na sashenki za'a sanar da su su tsumayi fitowarki”. “Nagode Mamy, ALLAH ya ƙara miki lafiya da tsohon rai mai amfani da albarka”. Cikin jin daɗi Daneen Ammarah ta amsa da Amin tana mai saka mata albarka itama. A yau kam Iffah ta ƙara tabbatar da tsantsar ƙarfin ikon mulkin wannan daula. Dan tunda ta baro hawa na ƙarshe hadiman sashin na Shahan-shan ke faman zubewa gabanta batare da dubi da ƙanƙantar shekarunta ba, matsayinta kawai suke kalla. Duk sai taji zuciyarta babu daɗi ganin kusan duk shekarunsu zai iya kaiwa dai-dai dana Hanash, wasu ma sun girme masa. (Nace Iffah danma Tajwar Eshaan yayi sauyi ne da matasa kikaga hakan, da har sa'an kaka da Babiy sai kin gani kuwa). Kamar yanda Daneen Ammarah ta faɗa tako samu hadiman na zaman jiranta. Ta gane hakanne ta hanyar zuwa da sukai suka zube a gabanta da sanar mata matsayinsu. Batare da damuwa ba duk ta bisu da kallo, su biyar ne cif kuma duk yara ƴammata matasa, za'a iya samun sa'aninta dama wanda suka girme mata kamar su Fariha. “Ina buƙatar zuwa books room ne akwai wani tsari akan hakan?”. Da sauri ƴar babbar dake ta gabanta sosai ta girgiza kai. “Ga Zawjata-almilk babu wani dokar yin hakan ALLAH ya ƙara miki lafiya”. “Okay zamu iya tafiya”. Iffah ta amsa mata kai tsaye. Hadima ɗaya ce tai gaba sosai Iffah na biye da ita cikin takunta na nutsuwa da wasu kan iya gani su fassara da abinda zuciyarsu ta basu. Bayanta Hadimai huɗu na biye da ita cikin taka tsantsan da nuna girma da ƙarfin ikonta a bayyane...........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_37_* .........Duk ta inda suka gitta kwarjininta dake ɓoye shekarunta kansa a bata girma irin wanda ya dace ga Zawjata-almilk da suka isa a masarautar. Hadimai kam sai zubewa suke bisa gwiwunsu sakamakon sanarwar da ɗan kazagin da Iffah bata farga da shi ba sai da suka fara tafiya taji shelanta tahowarta da yake yi. A yau kam ta ƙara jinjinama girman wannan katafariyar masarauta mai abubuwan kallo matuƙa. Sai dai ga mai kallo bazai taɓa fahimtar hakanba a yanda take faman basarwa kai kace ita ɗin tun fil'azal jinin sarauta ce. Ba wani nisa bane zuwa books room ɗin, hakan ya sakasu isowa cikin ƙanƙanin lokaci dan ma tafiya ce ta ƙasaita.... Cikin ƙankanin lokaci labarin fitowar Zawjata-almilk ya karaɗe masarautar. Hadimai ƴan leƙen asiri dake watse ta ko'ina sun gama kai labari ga iyayen gidansu. Da yawa mamaki ya kamasu tare da gane lallai yarinyar tazo da tsageranci. Inba tsageranci ba wace Zawjata-almilk ce ta taɓa fitowa bayan kaita turakar Shahan-shan da kwana ɗaya kacal. Wasu kuma kai tsaye fassara wannan fita suke da gatsali, acewarsu Iffah nason tabbatar musu tafi ƙarfin iyawarsu, ƙarfin ikon su kuma ba komai bane dan ta gagaresu. ★Malikat Bushirat kanta isowar wannan labari a kunenta sai da tai wani tsamm na nuna mamaki, sai dai bata ce uffan ba kasancewarta mace mai tsananin jin kai da izza. Tana son Iffah, kuma ƙarfin halin yarinyar na kawatar da ita. Sai dai hakan ba yana nufin zata dama damawarta ne a yanda taso ba ko ƙetare tsarin zama a masarautar musamman ga Zawjata-almilk irinta da ƙa'ida komai sai da umarnin Malikat zatayi sa. (Kamar dai ita dake mahaifiya ga Tajwar Eshaan. A ƙa'ida dole komi Iffah zatayi sai ta nema izinin mahaifiyarsa kafin ta aiwatar). Jin al'amarin ya cigaba da caccakar zuciyarta ta sallami duk hadimanta. Kamar ƙiftawar ido suka ɓace kuwa. Rai a ɓace ta ɗaga waya tai kiran Jasrah da ita bama tasan wainar da ake toyawa a masarautar ba kasancewar a ɗan tsakanin nan tana fama da laulayin ciki ne sama-sama. Duk da a halin rashin jin daɗi da take ciki bazata iya ƙin amsa kiran ƴar uwar tata da takema kallon uwa a yanzu ba. Haka ta kimtsa cikin dauriya ta nufi sashen Malikat Bushirat ɗin. A tsaye ta sameta cikin yanayin ɓacin rai da ya kasa ɓoyuwa a kan fuskarta. Sai duk taji itama nata ran a jagule... “Akia kina lafiya kuwa? Miya ɓata miki rai haka har fuskarki ta kasa ɓoye wa?”. Malikat Bushirat ta zuƙa kakkaurar iska ta fesar tana mai kallon ƴar uwar tata. Cikin ɗacin murya tace, “Yarinyar nan ce”. “Yarinya kuma? Wace yarinya kenan?”. Kamar bazata tanka ba, tai taku ɗaya zuwa uku batare data dubi Jasrah ba tace, “Zawjata-almilk. Da alama tana buƙatar sai an saita mata zama da tuna mata nan daular ruman ce ba getto eria ɗin data rayu ba. Komai muna yinsa da ƙa'ida bisa umarnin na gaba”. “Kiyi haƙuri Akia. Amma na kasa fahimtar miya kawo wannan maganar, wace kuma Zawjata-almilk ce a cikin yaran? Dan nasan dai kinfi kowa so da ƙaunar wadda ke tare da shi a halin yanzu”. “Ina sonta bashi zai bata lasisin shimfiɗa abinda ta gadama na a saman nawa ƙarfin ikon ba. Yanzu labari ya iso gareni ta fito daga sashen Saiful-malik zuwa books room tare da hadimai”. “Tofa, ita kuma da wannan tazo? Mu muna murnar samunta matsayin wadda zata share kukanmu amma zata fara da haka?. To amma fa Akia wani hanzari ba gudu ba. Shin baki ganin salon yarinyar a wani mahangar nasara ce a garemu. Na farko dai babu wanda yasan ta fito ne batare da umarninki ba. Na biyu koba komai ta sake jaddada isar da saƙonmu akan maƙiya. Na uku salonta tamkar barazana ce ga duk wani shu'umi dake rayuwa a wannan masarautar. Inaga bai kamata ki damu ba, dan a wani ɓangaren ma kamar mune masu laifi, karki manta Mammah ta mikata sashen Abni batare da bin ƙa'idojin da ake kai Zawjata-almilk turakarsa ba. Sannan inada tabbacin ba'a sanar da ita komai game da tsarin komai ba fa, sai aikin da muka faɗa mata zatayi a garemu”. A hankali Malikat Bushirat ta saki wata nannauyar ajiyar zuciya. Cikin kwantar da murya ta ce, “Hakane kumafa Jasrah, kin tunatar da ni abinda ya ɓacemin har idona ya rufe. Sai yanzu na fahimci lallai wannan fitar tata ma da alama tanada manufa akan umarnin aikinmu. Duk Mamma ce da wannan kwamacalar da muka kasa fahimtar manufarta a kai, nayi niyyar zuwa sashen nata ma naji dalili baƙin nan na ɗazun suka cinyemin lokaci. Amma munyi magana da Ammarah zuwa anjima zanje ko cikin ɓadda kama ne”. “Hakan yayi, dan koni ina son sanin yaya akai hakan ta kasance. Duk da dai Alhamdullah yarinyar ta kuɓuta. Amma mun kwana a fargaba ai dan ko barci jiya banajin waninmu yayi wlhy. Hatta da Abu Harith kwana yay tunani”. Murmushi Malikat Bushirat tayi, dan har cikin ranta tana ƙaunar ƙanin mijin nata kuma mijin ƙanwarta, tare da yaba ƙoƙarin sa akan kulawa da kaunar da yake nunawa ga gudan jinin nata tilo da har wasu ke jin zafinsa a gidan bisa hakan..... ★★.... Katafaren ɗakin daya kasance mai cika ido ga Iffah tsarinsa ya matuƙar ƙawatar da ita. Ta samu jagorancin shiga lungu da saƙo na cikinsa bisa taimakon masu kula da ɗakin. Inda a zagayen nasu suke nuna mata abubuwan tarihi na tun farkon ƙarnin kafa Daular ruman ɗin da suka shuɗe cike da girmamawa a gareta. Tafiya kam mabuɗin ilimice haƙƙun dan Iffah ta ilmantu da abinda yafi wanda ta sani ƙalilan a baya dangane da tarihin daular ta ruman da akan tsakura musu a darasin makarantu. Shugaban masu kula da sashen ya matuƙar nuna jin daɗinsa da bata shawarwari kan tsarin zama mai nazarin tarihi data ambata dan abune daba kasafai ake ganinsa ga matan cikin masarautar ba. Akwai wadda ma bata taɓa taka ƙafarta cikin ɗakin litattafan ba. Amma ita gata ƙaramar yarinya da rayuwarta ke kamar akan ɗar-ɗar abinda ta fara nuna sha'awa na farko akansa kenan. Shine ya fara zaɓa mata books daya ga ya dace ta fara dubawa, hakan yasa ta basar da waɗanda ta shigo nema kai tsaye, dan a ganinta bin shawarar tasa zaifi bata fiye da abinda take buƙata ɗin. Shugaban da shekaru sunyi matuƙar ja a garesa yaji daɗin amsar shawarar tasa da tayi, dan yasan duk da zai iya haifarta matsayinta ya bata ikon yin duk yanda taso a sama da shi... A cikin farin cikin daya goge duk wani damuwarta a wannan yini ta fito hadimanta na take mata baya ɗauke da ɗirka-ɗirkan littafan da ta ɗebo. A yanzu ɗin ma dai tako ina hadimai faman zubewa suke domin girmamawa a gareta harta isa sashenta data basu umarnin su kaita saɓanin sashen Shahan-shan daya kamata ace ta koma tunda a ƙa'ida sati guda zatayi kamar yanda Malikat Haseena ta sanar da Tajwar Eshaan. Iffah kam da ba zama akai aka faɗa mata komai na ƙa'idojin ba haka kawai taji bata bukatar komawa zaman takura da zuciyarta ta ayyana mata rashin amfaninsa. Shi dai wanda aka kaita dominsa ko kallo bata ishesa ba, hasalima baya kallonta da suffar da suka miƙata garesan kai tsaye. Yo dole ta faɗi haka, tunda wane mijin ƙwarai ne zai jefama matarsa kalmar tambaya ta ita (wacece?) Bayan da saninsa aka kai sadakinsa domin aurota. Bazata iya ɗaukar waɗan nan abubuwan ba, dan bama abinda ya kawota nan ɗin ba kenan tun fil'azal. A ganinta kuma ba sai dole an kaita garesa an ƙaskantar da ita ba, zatabi hanyoyin daya dace na haɗuwa da shi har lokacin da zata cika ɓoyayyen burinta.... Da wannan tunanin suka ƙarasa sabon sashen nata. Tabbas ta jinjinama ƙoƙarin su, dan ko makaho ya laluba yasan wannan sashen yayma wanda aka kaita fintinkau a komai duk da shima wancan ɗin dai ba baya bane a tsaruwar. Ta ɗan sauke numfashi da kaiwa zaune bisa ɗaya daga cikin lumbutsa-lumbutsan kujerun da aka shirya falon da su bakinta ɗauke da bismillah. Suma dai hadiman nata bayan sun ajiye litattafan a saman Centre table a gabanta suka zube. Taja tsahon mintuna goma tana mai nazarinsu kafin ta ɗan sauke numfashi da miƙewa. “Ina buƙatar zama da duk wanda zai kasance da Ni a wannan sashen zuwa anjima”. Cike da girmamawa duk suka amsa mata kawunansu a ƙasa. Ta ƙara jan numfashi ta fesar batare data farga da salon izzar da yay kutse ga al'amarin ta na yanzu ba ta kai dubanta ga agogon falon. “Muna da sauran lokaci yanzu da zai ishemu zagaya sashen kafin na shige salla”. Anan ma sun amsa mata ɗinne da girmamawa. Batare da ta sake cewa komai ba tai gaba duk suka miƙe suna take mata baya. A yanzu ma dai wadda ta jagorancesu zuwa books room ce ke mata bayanin sashen da tsarinsa yanda ya kamata. Cike da gamsuwa batare data furta komai ba koda so ɗaya take gyaɗa mata kai. Sashen ya ƙunsa abubuwa masu yawa da zaman lissafinsa zai zama ɓata lokaci da cinye mana page, bayan sun kammala zaga ko'ina Iffah ta shiga bedroom ɗin da zuciyarta tafi aminta da shi matsayin master bedroom ɗin ta. Mamaki ya kamata lokacin da taci karo da guntuwar takarda a saman duvet ɗin saman gadon. _Ibnati wannan ɗakin ki tabbar ya kasance ɗakin sirrinki, shiyyasa nasa a shirya miji duk wani abu na buƙatar ki._ takardar ta ɗan juya tana mai jan numfashi da fesarwa. Sai kuma ta saki murmushi dan ta fahimci saƙon na Daneen Ammarah ne. Wayarta ta ɗauka a ɗan gaggauce ta aika mata saƙo. Sannan ta nufi bayi gabatar da al'wala....... *_★★SHAHAN-SHAN★★_* Tun bayan faruwar komai daya shige ɗaya daga cikin ɗakunan barcinsa bai sake fitowa ba sai yanzu a cikin shirin zuwa Masallaci. Sau ɗaya ya ɗagama hadiman dake zube ƙasa a dalilin fitowarsa hannu ya fice. Da kallon ƙasan ido duk suka bisa, kowa da abinda zuciyarsa ke ayyana masa game da shi... Bayan idar da sallar isha'i bai samu damar shigowa ba yay zaman ganawa da Aamin sa su biyu da suka buƙaci hakan. (Miran Jasim da Miran Arshaan). Miran Arshaan shi yafi jansa a jiki tun fil'azal, sannan kuma kamar yafi kusanci garesa ta bangarorin biyu kasancewarsa miji ga Khaalti (Aunt) ɗinsa da yake kallo tamkar yaya. Shima dai Miran Jasim ɗin bai taɓa nuna masa wani abu mara kyau ba a zahirin rayuwa, a komai ma da zai taso yakan bada ƙarfinsa wajen karesu ne ga kowa koda a fada ne. Waɗannan hallayya tasu ya sashi ɗaukar yarda ya basu har yakan iya tattauna wasu abubuwa da suka shafi mulkinsa, sai dai abinda duk ya shafesa a karan kansa duk yanda zasu so sani baya taɓa basu fuskar hakan dan ko'a zahiri kowa na masa kallon mutum mai wuyar sha'ani, bahagon mai bauɗaɗɗen hali da zurfin ciki ne. Bayan ficewar hadimin daya gama hidimar zuba shayi a gaban kowannensu ya fice Miran Jasim ya fara katse shirun dan yasan in zasu kwashe awa ɗaya a wajen Tajwar Eshaan bazai sake tofa komai ba bayan gaisuwar da yay musu. “Abni nasan zakai mamakin wannan zaman namu, sai dai a dubi da abinda ya faru ɗazun ba abin mamaki bane. Abinda ya faru ɗazun ya matuƙar Kona mana zuciya, dan bazamu taɓa so a aibantaka ba muna ji muna gani kodan amanar da Haysam Akhi ya barmana taka. Akwai wasu abubuwan da yawa daya kamata dama mu tattauna da kai kafin wannan ɗin, amma a yanzu kamar wannan ɗin ne importent”. “Hakane Jasim Akhi”. Miran Arshaan ya karɓe fuskarsa na nuna tsantsar damuwa. Ya cigaba da faɗin, Abni lokaci yayi da nake ganin ya dace wasu a cikin iyayen nan namu dake zaman fadanci ya kamata su huta ƴaƴayensu su karɓesu. Duba da kai matashi ne, a koda yaushe ra'ayinka da hangenka zai cigaba da zama banbanci ne da nasun. Koda yake su a gare sun ma ba haka bane, dan haka mahaifinka yasha gwagwarmaya matuƙa da su a yayin nasa mulkin. Amma kai mi kake gani akan hakan?”. Shiru babu alamar Tajwar Eshaan zai tanka, sai ma cigaba da kurɓar shayinsa yake cike da ƙasaita idanunsa akan television dake aiki a falon..........✍️ *AYYIRIRIRI AHAYYE CHAS 💃🏼💃🏼💃🏼 sunan wata waƙa wai ita LUWAI* _Ana tayi muna tayi manyan mata dai da gaske sun dage sai sun zama kalar gaban mota kalar camera tare da gudummawar Mg's skin care Hajia ta kina ina ake ta wannan harkar arziƙin mata nata glowing suna faranta zuciyar mazajensu da laushi da santsin fatar su ke kina nan kina fama jiki duk kirci😱😱?_ Ah haba madam yunƙuro ayi tafiyar nan dake ki shiga ki wataya acikin shahararrun matan nan da ko'ina ake fatan gani dan an daɗe ana jin su watau *team glow by Mg's* Macen da ta isa itace mace karki bari ki zama cikin irin muna matan nan da suka rako mata duniya kuna tafe da mijinki yana kallon wata har miyau na zuba tsabar haɗuwarta da kyan fatarta Mg's skin care sune sirrin duk wata macen da ta isa a ɗaga kai a kira da suna mace wacce ba'a jin kunyar shiga taro da ita daga nan har villah kizo/kuzo mu haɗe a wannan ƙasaitacciyar tafiyar ta Mg's skin care domin sune na gaban gaba sune suka ciri tuta indai a harkar gyaran skin ce hajiata kiyi wani fresh kiyi smooth wow🥰🥰🥰kina tafe kina walwali idan fa kina amfani da *Mg's skin care* ba kya buƙatar ko wanne irin mai product ɗinmu katt ne duk matsalar fatarki muna da maganinta uhmm inata miki labari nace ba sister shin meye matsalarki ta gaban goshin ƴallaɓai? Acne?, pimples? spot?, strech marks?, sunburn?. to hutas bi'izinilLah muna da maganin matsalarki kina ganin mata a tiktok fuska luwai lumus kice dama ni ko? to in dai kina tare da *Mg's* matsalarki tazo ƙarshe bama cika baki gaskiya itace takenmu haka nan kuma siyen nagari mai da kuɗi gida *MG's skin care gagarabadau* Price ɗinmu daidaitacce ne sannan kuma dai dai da aljihunku *Soap price:4k* maiso yy mgn 08062991549 07046881166 07067210195 Call 08064532391 Instagram:glow_with_mgs Facebook: mg's skincare Masu bukatar cream Shima munadashi harda ma complete set nagyaranjiki Small 12k Medium 14k Babba 20k *BE PART OF THE GLOW TEAM KARKU BARI A BAKU LABARI* *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_38_* ........Duk da yanda zukatansu ke suya da tsagwaron salon wulaƙanci da raini da suke jifansa da shi game da wannan halin nasa da babu komai a cikinsa sai tsantsar miskilanci da kasancewar jinin mulki da ke yawo a jikinsa basu bari fuskokinsu sun nuna ba har ya gama shan ƙamahinsa da basarwarsa ya tanka. “Amfanin kasancewarsu cikinmu yafi rashin amfanin muhimmanci Aam. A lokuta da dama nafi son zama da maƙiyi fiye da masoyi saboda dalilai biyu”. Wani irin kallo suke masa har fuskokinsu na barazanar bayyana sirrin zukatansu. Miran Arshaan yay saurin katsesa da faɗin, “Abni wace irin magana ce wannan? Kakuwa san illar hakan da kakeyi?”. Miran Jasim dake masa kallon gefen ido cikin takaici yake masifa a zuciyarsa. (Shifa wannan wawa ne baima iya jin ƙarshen zance sam). A zahiri kam kallonsa ya sauke ga Tajwar Eshaan da yay biris tamkar bashi ya ɗakko zancen ba. “Ihm kaga Abni ƙarasa, zata iya yuwuwa naka hangen gaskiyar cikinsa rinjaye ne ga namu. Domin kowa da irin yanda UBANGIJI ke fahimtar da shi abu”. Tajwar Eshaan da bai ko motsa ba ga zancen Amin nasa sai da ya shaƙi iska iya buƙatarsa kafin ya ɗan ɗage kafaɗu a yanayin ko'in kula. “Ku manta kawai muje kan magana ta gaba. Wataran zamu ƙarasa wannan ɗin”. Sosai takaici ya maƙure musu maƙoshi su dukansu. Sai dai Miran Jasim har Miran Arshaan yake jin takaici kasancewar shine sanadin katse zancen. Suma shiru sukai kamar bazasuce komai ba a wannan gaɓar. Kafin Miran Jasim ya nisa. “Abu na gaba shine farin cikin tsallakewar matarka. Alhamdullah addu'oin mu sun karɓu, ALLAH yasa ta kasance uwa ga ƴaƴan da zaka haifa masu albarka”. A maimakon amsawa da Amin daga garesa ƙasaitaccen murmushinsa mai ƙara bayyana ƙyawun da ALLAH ya azurtashi da shine ya saki kaɗan yana mai kauda kansa gefe babu alamar zaice wani abu. Suma basu nuna alamar sun damu da sai yace ɗin ba Miran Jasim ya cigaba da faɗin, “Ya kamata a zauna da Tajwar na jihar Hubab da shugaban tsaro akan waccan matsalar itama. Kar muyi sakaci dayin biris da wannan maganar dan bamu san minene manufa ko dalilin faruwar komai ba. Abu mafi ruɗanin shine makamancin haka bai taɓa faruwa a ƙasar ruman ba sai dai muji a wasu ƙasashe har ma mu bada shawara da gudun mawar ganin sun samu zaman lafiya. Idan haka kuma ta fara faruwa a garemu lallai maƙiyanmu na barazana akan nasararmu kenan”. Nan ɗin ma dai kamar bazai tanka ba sai kuma ya dubi Miran Jasim ɗin da alama zancen ya shigesa. “Na baku damar yin duk yanda ya dace Aam”. A take fuskokinsu suka nuna jin daɗin wannan girma daya basu. Sanin halinsa yasa daga haka sukai masa sallama. Har sun miƙe Miran Arshaan yace “Af niko kaga na shafa'a da wannan batun. Abni baka ganin yayi kusa kuwa ace fitar Zawjata-almilk har cikin books room? Yakamata ace tayi haƙurin cigaba da killace kanta kodan maƙiyan da bamu san ta inda suke shirya sabon shiri ba, dan yayi wuri ace mun shagala da tsallakewar ta ta a nawa ɗan hangen. Ai ƙoƙari a tsawata mata ALLAH ya cigaba da kare mana ku ku duka dai”. Miran Jasim ya amsa da Amin yana jinjina kai alamar tabbatar da maganar, sai dai ganin Tajwar Eshaan bashi da alamar cewa wani abu suka fice abinsu. Koda suka fitan ya jima bai motsa a yanda yake ba, da alama dai maganar tasu ta ƙarshe ce ke masa kaikawo. Hasashen kam sai ya zama gaskiya dan akan lips ɗinsa daya motsa kaɗan ya ambaci, “Yarinyar nan ko”. Daga haka ya shanye sauran a cikinsa.... ★★.... ★.... Kamar yanda ta faɗa bayan sallar isha'i ta fito cikin abaya fara tas. Duk da dare ne ƙamshinta da kwarjininta mai ɓoye ƙarancin shekarunta na tare da ita. Fuskarta ɗauke da murmushi mai bayyana haƙora take amsa gaisuwar hadiman da tuni sun kammala taruwa bisa umarninta. Ɗaya bayan ɗaya ta basu damar gabatar mata da kansu da matsayin ayyukansu. Har suka gama batace komai ba tana dai nazarinsu ne. Haka kawai take jin bai kamata ta yarda da kowa ba a wannan gaɓar, dan duk da tausayinsu dake nuƙurƙusar zuciyarta tayi imanin akwai masu gurɓatacciyar zuciya a cikinsu kamar yanda Daneen Ammarah ta karanta mata komai. “Okay duk naji bayanan ku, sai dai kuma Ni zan canja tsarin aikin da bama kowa abinda nake ganin zai fi dacewa da kasancewar tare da ni. Bazan roƙi kowa ba a cikinku cewar ya kasance mai gaskiya da riƙe amana, sai dai zan tabbatar muku zan iya hukunci ga kowa idan na kamashi da waɗan nan abubuwan biyu. Dan na matuƙar tsanar mai wannan halayar koda a sama dani yake. Zan kuma iya aikata harma abinda mutum baiyi zatoba akan hakan.....” ɗaya bayan ɗaya ta rarrabasu ga ayyukan saɓanin yanda aka turosu suyi, salon nata ya matuƙar girgizasu a take kuma tasirin gizagonta ya shigesu, har suke ambaton tsarin da gaba kura baya sayaƙi kenan, dan kuwa dai kamar yanda Iffah tai hasashe mafiya yawan cikinsu zasu kasance da itane bisa umarnin iyayen gidansu na ɓoye bisa ɗabi'ar tura ƴan leƙen asiri da manyan masarautar suka tasirantu a kansa. Bayan ta sallamesu akan aikinsu zai fara daga gobe ne ta tattare littafanta da kanta tai ciki da su. Sai da ta tabbatar ta ƙarema ɗakin kallo yanda ya kamata fiye da ɗazu bisa zargin za'a iya saka mata camara kamar yanda Ajmaal ya tabbar mata. Babu alamar akwai abinda take zargin dan haka ta ɗauka wayarta. A maimakon WhatsApp yau a text message ta tura masa saƙo, daga ƙarshe ta ƙara roƙonsa bincika mata lafiyar iyayenta dan zuwa yanzu zuciyarta na tabbatar mata akwai abinda Sir Fawzan ya faɗa mata ba dai-dai ba ko yake ɓoye mata. Dan kullum takan gwada number Hanash da Babiy sama da sau babu adadi amma babu alamar zata samesu. Ga mafarkinta a kansu duk kusan bayan kwana biyu cikin maimaita kansa yake gareta. Bawai tayi imani da hakan bane, kawai dai zuciyarta takan rinjayu da tsoro akan mafarki musamman idan ta auna da abubuwan da suka tabbata akan wasu mafarkai da sukai wa riƙon wasarere ita da iyayenta a baya....... *_★MALIKAT HASEENAT★_* Kamar yanda labarin fitar Iffah yaje kunnen kowa a masarautar itama yaje nata kunnen, sai dai saɓanin malikat Bushirat ita murmushi tayi batare data furta komai ba akan zancen. Rashin cewar tata ya Bama Hadimar damar ƙarasa mata zancen akan Iffah kuma ta koma sashenta bayan barowarta books room. Anan kam idanu Malikat Haseenat ta tsurama hadimar Tata tamkar zataga fuskar Iffah a jikinta ne. Sai kuma ta janye da wani ɗan murmushi a fuskarta ta maida ga hadima Banou. “A haɗa abincin karin kumallo da Zawjata-almilk ta uku”. Cikin tashin hankalin wannan umarni na Malikat Haseenat kamar Banou zata fasa kuka ta jinjina kai, har hakan ya bama malikat Haseenat mamaki, sai dai batayi magana ba kasancewar tasan shirmen Banou fiye da haka. Itama dai tana zaune da itane batare da tasan dalili ba, amma wasu lokuta takanji yanayi mai wahalar fassara koda a kallon hadimar tata ne amintacciya a bangaren girka mata abinci... 7 *_BARRISTER_* “Su waye ku? Miyasa kuka kawoni nan? Mina muku?”. Barrister ya faɗa yana mai bin zaratan samarin da kallo harma da ɗakin da suka kawoshi mai ƙarancin haske gashi a ɗaɗɗaure a kujera. Fahimtar bazasu bashi amsa ko ɗaya ba daya bukata ya sashi cigaba da magana a hasale. Dan shi mutum ne mai saurin fushi musamman akan gaskiya da mai gaskiya. Baya son zalunci shiyyasa ko baka da ƙarfi zai tsaya maka akan haƙƙinka in har ka kasance mai gaskiya. “Idan ma akan case ɗin nan ne kuke ganin sakayeni ko ɓadda rayuwata zai baku damar yin yanda kuke so akan bayin ALLAH da basujiba basu gani ba ku sani ni bamai hukunci bane. ALLAH shine mai hukunta kowa, zai kuma iya kawo wanda ya fini ƙarfi ya cece su”. Yanzu ɗinma dai babu alamar wani a cikinsu zai tanka masa. Idanunsa ya rumtse zuciyarsa na masa ƙuna. Bashi da wani buri yanzu a duniya sama da yasan asalin tushen wannan case ɗin nasu Babiy, yayi alƙawarin tsayawa da ƙarfinsa dana aljihunsa insha ALLAHU. Har dare babu wani haske daya samu dan har lokacin yana a ɗaure, sai da aka kira sallar magriba ne suka bashi dama yay salla harda isha'i. Hakan ya ɗan sassauta masa zuciya, dan koba komai damar yin salla da suka bashi yaji a ransa masu sassauci ne. Abinci suka kawo masa basu sake ɗauresa ba, sai dai yaƙi yako kallesa hakan yasa suka sake zuwa kusan ƙarfe tara agogon ƙasar suka sake ɗauresa sukai ficewarsu da kullesa ta baya. Babu irin tunani da takaici da baijiba amma ya cigaba da ambaton sunan ALLAH dan yasan shine kaɗai zai kuɓutar da shi a wannan gaɓar. Kusan ƙarfe sha ɗaya gyangyaɗi naɗan kwasarsa yaji ana ƙoƙarin buɗe ƙofar, idanunsa ya buɗe duk da baya iya ganin mai shigowa saboda ƙarancin hasken ɗakin. A ɗan hasken ya fahimci yanzu mutumin uku suka shigo, wanda ke gaba kuma da alama ogansu ne dan yanda ya shigo da takun izza cikin ɗakin. Da sauri suka ajiye masa kujera ya zauna yana mai facing ɗin Barrister yay wani irin zaman ƙasaita yana ƙarema Barrister ɗin kallo ta cikin glasses ɗin daya toshe idanunsa.... “Miyasa kuka dauresa?”. Ya faɗa a kausashe. Kame-kame yaran nasa suka fara kowa na ƙoƙarin kare kansa. Yaja tsakin daya sakasu nutsuwar dole yana mai faɗin, “Ku kwance sa”. Bayan an kwance Barrister ya sake bada umarnin a bashi abinci da ruwa. Barrister dai kallonsa kawai yake da mamakin wannan izza tasa. Baiyi niyyar cin wani abu ba dan haka yay saurin faɗin, “Bana buƙatar wani abinci. Kusanar min kawai dalilin da yasa kuka kawoni nan da kuma inda nake dan ALLAH”. Har Barrister ya fidda rai ga samun amsa yaji an karɓama zancensa a kausashe. “Barrister Abdallah Aas ba shiririta ta kawoni nan ba. Dan na baro abubuwan da suka fika muhimmanci nazo nan. Duk da rayuwarka ce ba sanin inda kake ko sanin mu su wanene ba matsalarka. Dalilin kawoka nan kawai zaka iya sani, damar hakan kuma na hanunka ta hanyar bin umarninmu”. Haka kawai kwarjinin wannan mutum da ko fuskarsa Barrister baya gani da ƙyau yay matuƙar mamayesa, duk da yanaji a ransa ba alkairi yasa suka kawosa nan ba sai yaji bazai iya jayayya da shi ba. Cikin sanyin jiki ya fara cin abincin, yaci kusan lauma bakwai yasha ruwa duk suna a ɗakin. “Na gama”. Ya faɗa cikin sanyin murya. “Good for you”. Aka bashi amsa cikin halin ko'in kula. Sai kuma yay shiru kamar baida abin faɗa kafin yaja numfashi cike da isa ya fesar. “Lokacina ƙurarrene dan haka bani da lokacin cigaba da ɓatashi a rikeka nan. Aiki zakamun baka da kuma zaɓin cewa e ko a'a. Nasan kasan Barrister Akeem Ibn Behnam”. “Hakane, dan abokina ne ma ranka ya daɗe”. Barrister ya amsa mishi da kalmar giramamawa a ƙarshe batare da yasan dalili ba. Kawai dai yana jin matuƙar girman wannan mutum da ko a murya yasan ya girme masa. Cikin yaransa ɗaya ya cigaba da faɗin, “Sanin hakan yasa aikin ya wajaba a kanka. Akwai aikin da Barrister Akeem ɗin keyima wasu mutane, Boss naso ka maye gurbinsa....” “Tayaya hakan zata faru, bayan su sun san wanda suke huɗɗa da shi”. Barrister yay saurin katse mai maganar. “Ai mun fika sanin hakan shiyyasa muka zaɓeka. A yanzu Barrister Akeem na hanunmu kamar yanda kake a hanunmu, munada hanyoyin bi wajen canjaka ka koma shi bisa dalilan da kaima kasani, yayinda su a wajensu kai ka mutu a yanzu, zuri'arka kuma basu san inda kake ba. Zakai aikinne na kwanakin da basu gaza goma ba, idan sun zarta hakan kuma kai kaso”. “Kun sani a duhu wlhy, Barrister Akeem fa wani babban jigone a rayuwata, muna taimakama juna matuƙa taya kuke tunanin zanci amanarsa ta hanyar yin amfani da kammanin da mukeyi ace na masa kutse akan aikinsa bayan haka cin amana ne?”. “Wannan damuwarka ne. Aikinmu zai fara daga gobe”. Ogan nasu ya faɗa cikin kausasa harshe yana miƙewa. “Ranka ya daɗe dan ALLAH ka saurare ni”. Barrister ya faɗa cikin rauni. Sai dai baiko nuna alamar yama jisa ba yay ficewarsa yaransa biye da shi..........✍️ 🤔????. Nama rasa abin faɗa. *AYYIRIRIRI AHAYYE CHAS 💃🏼💃🏼💃🏼 sunan wata waƙa wai ita LUWAI* _Ana tayi muna tayi manyan mata dai da gaske sun dage sai sun zama kalar gaban mota kalar camera tare da gudummawar Mg's skin care Hajia ta kina ina ake ta wannan harkar arziƙin mata nata glowing suna faranta zuciyar mazajensu da laushi da santsin fatar su ke kina nan kina fama jiki duk kirci😱😱?_ Ah haba madam yunƙuro ayi tafiyar nan dake ki shiga ki wataya acikin shahararrun matan nan da ko'ina ake fatan gani dan an daɗe ana jin su watau *team glow by Mg's* Macen da ta isa itace mace karki bari ki zama cikin irin muna matan nan da suka rako mata duniya kuna tafe da mijinki yana kallon wata har miyau na zuba tsabar haɗuwarta da kyan fatarta Mg's skin care sune sirrin duk wata macen da ta isa a ɗaga kai a kira da suna mace wacce ba'a jin kunyar shiga taro da ita daga nan har villah kizo/kuzo mu haɗe a wannan ƙasaitacciyar tafiyar ta Mg's skin care domin sune na gaban gaba sune suka ciri tuta indai a harkar gyaran skin ce hajiata kiyi wani fresh kiyi smooth wow🥰🥰🥰kina tafe kina walwali idan fa kina amfani da *Mg's skin care* ba kya buƙatar ko wanne irin mai product ɗinmu katt ne duk matsalar fatarki muna da maganinta uhmm inata miki labari nace ba sister shin meye matsalarki ta gaban goshin ƴallaɓai? Acne?, pimples? spot?, strech marks?, sunburn?. to hutas bi'izinilLah muna da maganin matsalarki kina ganin mata a tiktok fuska luwai lumus kice dama ni ko? to in dai kina tare da *Mg's* matsalarki tazo ƙarshe bama cika baki gaskiya itace takenmu haka nan kuma siyen nagari mai da kuɗi gida *MG's skin care gagarabadau* Price ɗinmu daidaitacce ne sannan kuma dai dai da aljihunku *Soap price:4k* maiso yy mgn 08062991549 07046881166 07067210195 Call 08064532391 Instagram:glow_with_mgs Facebook: mg's skincare Masu bukatar cream Shima munadashi harda ma complete set nagyaranjiki Small 12k Medium 14k Babba 20k *BE PART OF THE GLOW TEAM KARKU BARI A BAKU LABARI* *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_39_* ........A ɓangaren Iffah kam bayan sallamar Hadimanta data ƙudiri nutsuwa wajen fahimtarsu a tsanake itama ciki ta shige. Kamar yanda ta saba sai da ta gudanar da duk wani al'adan rayuwarta kafin barci. Ta haye sabon katafaren gadon nata bakinta da addu'a. Manya-manyan littafan dake jere a bideside drawer ɗinta data kwaso a books room ta kalla cikin nazari har idonta ya sauka kan wanda ya kamata ta fara dubawa. Sai da taja lalausan bargon dake a saman gadon ta ɗan rufe kafafunta zuwa cinya ta gyara zamanta da ƙyau ta buɗe littafin da bismillah. A nutse kuma daki-daki ta fara nazartar littafin da ƙoƙarin dinga fahimtarsa yanda ya kamata da irin fahimtar dai-dai nata tunanin. Taja wani tsahon lokaci a nazartar littafin barci gwanin iya sata ya cigaba da rinjayar idanunta. Haka badan taso ba ta kife book ɗin a gefen ta zame ta kwanta tana hamma. Da ƙyar ta kammala haɗa addu'ar barci...... ★★..... ★..... “Uwa komai ya rikicemun wlhy, narasa ina zan kama. Ki taimakeni kar yaƙin dana sha a baya ya zama wahalar banza akan cikar burina”. Ta-kurya ce mai maganar cikin tsananin tashin hankali da susucewa game da rashin mutuwar Iffah kamar na sauran matan baya”. Uwa dake hakimce duk tana saurarenta ta nisa tana mai girgiza kanta da sake tsuke mummunar fuskarta. “Ƴar shilar nan bata isa ja dani ba Ta-kurya, kin Sanni kin san aikina kin kuma san mizan iyayi. Ya kamata ki nutsu tsaf akan bayanin danai miki tun a baya. Tabbas mutuwarta zata iya zame mana mai wahala a lokacin da muke buƙata, shiyyasa naji takaicin suɓucewar waccan damar da muka samu a farko. Gashi kema sakacinki yasa har zuwa yanzu kin gagara kawo mana rigar dake sashen mai Babban ɗaki ko zamu iya kamo bakin wancan zaren dan zuwa yanzu na fahimci akwai masu irin manufarmu akan yarinyar kamar yanda na sanar miki. An kuma mana karan tsaye na kaita sashen Ajlaan ta hanyar ƙin bin dokokin kaita turakarsa, kin san kuma mu munbi matakanne wajen ɗana tarko akan waɗan ca har mukai na sara, sun shammacemu sun kaita ne, sai dai abinda basu sani ba hakan bazai taba tseratar da itaba a tarkonmu na gaba da kuma mutuwarta” “Uwa ba sakaci bane, a yanzu haka hadimar dana saka wannan aikin tana gab da kammala min shi. Ni yanzu tashin hankalina shine cikar lokacin kalmashe bakin zaren burina na biyu dake ƙara nisa. Har yanzu da buƙatar cikamakon aikin fa kafin na tsallaka na uku da shine cikar gaba ɗayan nasarata akan wannan yaƙin. Uwa ya kamata kiyi wani abu. Idan ita wannan yarinyar mutuwar tata bazai yuwu ba ta wannan silar inaga mu ajiye batunta gefe a haɗe wannan bakin zaren”. “Kema kinzo da magana mai ƙyau kam ta ƙurya. Kuma inaganin ya kamata cikin Zawjata-almilk biyu da suka rage ɗaya zata zama cikamakin ayyukanmu na biyu. Kinga sai mu haɗa aikinmu na uku dana ƴar shilar sudan can, amma duk da haka a kwana bakwai da zatai bazamu daina gwada sa'ar mu ba dai”. “Haka shine dai-dai uwa mai share kukan masu kuka. Madubin rayuwar duk wani mai buƙatar kallon ƙarshen ƙyawun nasararsa.” “Nasara takice Ta-kurya tunda har kina tare damu. Sai dai maganar yarinyar can dole ki haɗa da kirsa a yanzu kamar yanda kika saba wajen nasarar haɗa dukkan auren Ajlaan ta hanyar mai Babban ɗaki a yanda kika so. Ki kusanta kanki da yarinyar itama sosai”. “Indai wannan ne angama Uwa”. “Na barki lafiya”. Uwa ta faɗa tana mai ɓacema ganinta a sannu-sannu harta daina ganinta. Ajiyar zuciya mai nauyi ta sauke ranta duk babu daɗi. Dan zuciyarta kam ta fara ayyana mata ƙarfin ikon uwa ya fara sanyi. Dole ne ta nema sabon mai taimakonta duk da bazata taɓa mantawa da gudunmawar da uwa ta bata ba harta kawo wannan matsayin a wannan daula ta ruman da ayanzu take kamar mai juyata ta ƙarƙashin ƙasa da zahiri a yanda take so. Amma ga karamar yarinya da bata wuce kiyashin da take murjewa a ƙasan tsinin takalminta batare data sani ba tana neman zamewa rayuwarta wata ƙadangaren bakin tulu a gabar cikar babban burinta na ƙarshe...... ★★★..... ★★.... ★.... A ɗan firgice Iffah da kiran sallar asubahi ya farkar take kallon kanta da inda take a yanzu. Cikin shiga razani mai ban tsoro ta diro a gadon daya kasance saɓanin inda ta kwanta a daren na jiya. Kamar wadda ake ingizawa ta fice a ɗakin cikin sassarfa. Tabbas sashen Tajwar Eshaan ne dai take. “Taya haka zata kasance?”. Ta faɗa cikin bugun zuciya. Sai kuma ta fara tunanin kodai mafarki take yine. Hannu takai ta ɗan mari fuskarta. Sai dai babu abinda ya canja daga wanda idonta ke gane mata a yanzu. Dan lallai da gaske a sashen Shahan-shan ɗin dai take. “Ya ALLAH mike faruwa da ni ne haka wai. Taya zan kwanta a sashen da ba wannan ba na kuma buɗe ido na gannni? Jiya an ɗaukeni daga ƙasa an maida saman gado na share, amma shine yau kuma za'a ɗakkoni daga wani sashe zuwa wani daban. Anya ba matsafan gidan nan ke son min wasa da hankali na ba?”. Wannan tunani na karshe ya sata saurin kama rigarta ta shinshina. Tabbas irin dai ƙamshin turaren jiya ne da karfinsa harya danne nata. “Ya Arrahaman” ta sake faɗa tana mai juyawa ta shiga kallon ɗakin da sauri. A kan tarin kayan turarruka da idonta ya sauka a kai ta nufa, ta buɗe gilashin da suke ciki kamar dai nacan ɗakin ta fara shinshinasu ɗaya bayan ɗaya. Sai dai abin mamaki babu wanda ƙamshinsa yay kama da wanda takeji a jikinta. (Dole ne ma na gano, kuma ta wannan ƙamshin insha ALLAH). Ta ayyana a zuciyarta cike da alwashin hakan. Alwala taje ta dauro jin makara na neman riskarta. Bayan ta idarne kuma ta sake nutsuwa wajen ƙarema ɗakin kallo yanda ya kamata. sai yanzu ma ta gane ba inda ta kwana a jiya bane wani ne daban. Sai dai shima wannan ɗin ya matuƙar haɗuwa fiye ma da wancan ɗin. Saɓanin wancan da tsarin komai na cikinsa ke fari anan kuwa komai blue ne, ga wani ƙamshi na fitina na tashi kamar dai wancan. Abu mafi ban mamaki nan ɗin dai duk da ya nuna ana tsaftaceshi a hargitse yake kamar anyi dambe a cikinsa. Ita kanta dama a shigarsa toilet har mamakin yanda taga kanta a birkice tai, dan tasan dai tsaf ta kwanta kuma bata buge-buge a barcin. Son yin salla a kan lokaci ya sakata bata maida hankali ba sai yanzu data idar ta samu nutsuwa. Tayi tunanin gyara ɗakin da fita binciken turaren nan na jikinta da alama ya tabbatar mata mai shi ke son wasa da tunaninta, sai dai wata zuciyarta ta bata shawarar ajiye waɗan nan batun ta sake kwanciya irin ta jiya tai likimo kozata samu bakin zaren ta hanyar shigowar wanda take zargin kamar jiya. Ta gamsu da hakan tako kwanta, sai dai tsahon kusan awa ɗaya babu wani wanda ya zo ɗakin, babu ma alamar wani ɗin zai zo harta tashi akan dole ta kimtsa ɗakin ta shiga wanka. Kayan data samu a lokacin gyaran ɗakin ta sanya babu ko ɗar a ranta. Tayi ƙyau sosai, ta kuma sake baza turarurrukansa a jikinta kamar jiya sannan ta fice a sannan kusan ƙarfe bakwai da rabi... Da ƙyar yau ma ta iya gano ɗakin data kwana a shekaran jiya, cikin Sa'a kuma ta samesa a buɗe. Shiga tai da sallama duk da bata zaton samun kowa a ciki. Tsaf yake kamar batai bidiri cikinsa ba jiya, an canja zanin gadon ga kamshi na tashi mai daɗi da sanyin ac. A yanda hadiman suka nuna sun ɗan yi shock da ganinta ya ɗan sakata a mamaki, amma sai ta dake babu alamar hakan gareta ta nufi ɗaya daga cikin kujerun falon tai zaman ƙasaita da ita kanta bata farga da yinsa. Hadiman da duk ganinta ya sakasu a firgici suka iso gabanta suka zube domin miƙa gaisuwa. Rayukansu kam cike da mamaki dan kowa dai yasan a jiya ba sashen ta kwana ba, tun fitar yamma da tai bata sake dawowa ba har suka rufe waje suka kwanta. Tun bayan idar da salla asuba kuma suka fito balle suce koda safen nan ta dawo. A fisge ta amsa gaisuwarsu tana mai sauke manyan fararen idanunta akan ƙyaƙyƙywan tray ɗin dake ajiye a table ɗin gaban kujerar data zauna a jiya wadda koda ba'a faɗa mata matsayin kujerar ba tasan ta zaman Shahan-shan ce. Ɗan juyiwa tai ta dubi hadiman da har sun fara miƙewa. Ta jeho musu tambaya da faɗin, “Wannan fa?”. Cikin sauri mai sanye da kayan kuku ta amsa da “Shayi na farko da Shugaba ke sha bayan gama motsa jiki”... “Kayan haɗin sa?”. Ta tambaya a takaice. Nanma da tsumar jiki ta lissafa mata. Iffah ta yamutsa fuska da sake harɗe ƙafafu. “A canja minsu da tatattun kayan itatuwa da ganyen koren shayi”. Cikin tsoro duk suka dubeta, ta sake tsuke fuska da musu alamar gargaɗi da hannunta. Kamar ƙyaftawar ido kukun ta ɓace a wajen. Cikin abinda bai fi mintuna goma sha biyu ba aka dawo da wani sabon haɗin shayin. Miƙewa Iffah tai da nuna hanya alamar ta kaita inda yake. Anan ma ba karamin tsoro bane ya bayyana a idanun hadimar har ma da sauran ƴan uwanta, amma tsayayyun idanunta masu ƙarfi fiye da girman shekarunta ya hana hadimar iya furtawa a baki. Kai tsaye hanyar dake acan gefe ta nufa, sai dai suna zuwa ta dubi Iffah a mariraice sai kuma ta duƙar da kai. “Tsahon rai da amincin UBANGIJI su zama kariya ga Zawjata-almilk, wlhy bani da hurumin tsallake wannan iyakar”. (Kinyi mai wuyar) cewar Iffah a zuciya. A zahiri kam hannu ta miƙa ta amshi tray ɗin batare da tace uffan ba. Cikin rawar jiki hadimar ta buɗe mata ƙofar gilashin dake a wajen, Iffah ta ɗan tsirama steps na bene daya bayyana alamar shi zatabi kusan na sakan ashirin kafin ta maida ga hadimar da kanta ke duƙe, “Zaki iya komawa bakin aikinki”. Kamar dama umarnin take jira, cike da sassarfa tabar wajen ƙwaƙwalwarta fal mamakin wannan baiwa har zufa na taruwa a goshinta. ★Ba karamin sake jinjinama al'amarin wannan masarauta Iffah tai ba, dan tana ɗaura kafarta a step na farko na'ura ta fara shelanta kasancewarta a wajen. Abu mafi bata mamakin kalmar sunan da na'urar ta ambaceta da shi. Kafin ta sami damar wani waige-waige lifter data kwasota ta direta a wata ƙofar da hadimai biyu ke tsaye hannunsu riƙe da manyan bindugu. Tayi mamakin ganin yanda suka rissinar da kawuna sunka fara gaisheta. (Shin sun yarda da zancen na'urar ne? Kokuwa sun santa a matsayin Zawjata-almilk ɗin ne dama?). Da wannan tambayar da babu mai bata amsa ta cigaba da takawa a hankali kasancewar sun buɗe mata ƙofar wajen. Iska mai daɗi dake busawa ta sanyin safiya ta fara cin karo, ta zuƙa a hankali tana mai lumshe idanunta. Sai kuma ta buɗesu a sannu, a lokaci ɗaya bugawar zuciya da tsinkewar jini suka nema sarƙe numfashinta, neman daburcewa take sakamakon abinda tai tozali da shi. Babu shiri ta maida idanunta ta rumtse tana mai ambaton sunan ALLAH akan wannan mummunan gani da tai. To mummunan gani mana, dan tunda take a rayuwarta bata taɓa tozali da namiji a irin wannan yanayin da idonta ya gane mata ba.. Ji take kawai ta zura da gudu ta koma, sai dai hadiman dake bayanta fa? Wane irin kallo zasu mata bayan na'ura ta gama fallasata a garesu. Tabbas nuna gazawarta na nufin faɗuwarta, faɗuwarta a matakin farko kuwa na nufin rushewar gaba ɗaya nasararta. Da karfi taja numfashi mai kauri ta haɗiye, kamar zatai kuka ta sake buɗe idanun a hankali, sai dai koda wasa bata yarda ta kalla gaban nata ba..... Shigar ƙamshin turarensa da bayan shi babu wani mai irinsa da sautin takun takalman ƙafarta ya sashi juya sharɓeɓen takobin dake a hanunsa cike da gwanancewa ya karci ƙasa ya gocema Aamin nasa da suke wasan tare ya juyashi zuwa hannunsa na haggu saɓanin na dama sai gashi akan wuyan Iffah da numfashinta yay wata irin mummunan fisga. “Who are yo.....?”. Yay yunƙurin faɗa cikin alamun bayyanar fushi mai haɗi da isa da ƙasaita, sai dai kalmar ta gagara ƙarasa fita a harshen nasa dalilin tozali da abinda bashi yay tsammanin gani ba. Tar-tar fuskokinsu suka bayyana akan takobin mai matuƙar ƙyalli da sheƙi da kai tsaye za'a iya kiranta faɗama jini na wuce........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_40_* ..........Tsam Iffah ta ƙara damƙe trayn hanunta jin rawar jikinta na neman fitowa, “Barka da safiya ranka ya daɗe”. Ta faɗa cikin ƙarfin hali da jarumtar saka idanunta cikin tsakkiyar nasa da ke tsaye a kanta har yanzu ƙyam. Sai dai duk ƙwaƙwƙwafin mutum bazai iya gane abinda ke a cikinsu ba balle akan fuskarsa mai cike da gizago akoda yaushe. Ganin bai amsa ba, bai kuma daina kallon tsakkiyar idanunta da ayanzu take ƙoƙarin janyewa a nasa ba, bai kuma janye takobin da kallonta kawai zai iya tada tsigar jikin mutum daga wuyanta ba ya sata ɗan shammatarsa ta goce makoshinta da ga tsinin takobin daya ɗaura matan, sai dai a yanda ya wani lumshe idanu da sauke takobin yasata tabbatar da ya bartane kawai. Gaba tai yunƙurin yi, da yima hadiman da suka iso wajen yanzu nan kallon gefen ido a kaikaice ta saki wani lallausan murmushi mai ma'anoni da yawa a zahiri. A kuma ƙasan ranta ko ɗar babu. Duk wannan abun Miran Arshaan fa na tsaye a wajen ne yana ƙarema Iffah kallo a kaikaice cike da mamakin ƙarfin halin yarinyar, dan tunda yake a wannan masarauta bayan shi babu wani mahaluki daya taɓa zuwa wannan wajen sai Shahan-shan da hadiman dake kula da wajen. Amma a yau sai ga yarinya ƙarama da babu alamar tsoro a cikin idanunta a wajen. Sai kuma yanda tayi kamar bata gansa ba yay matuƙar ƙona masa rai amma ya dake dan yana buƙatar ganin ƙarshen wasan.... Wajen duk da filine na karshen ginin (rufinsa kenan) ya ƙawatu da abubuwa kashi-kashi na more rayuwa. Ga wani ƙamashin furanni da aka ƙawata waje dana fresh air masu narkar da jinin mutum da sanya kasala. Da sauri ɗaya daga cikin hadiman da suka shigo wajen da abubuwa a hanunsu ya ƙarasa ga Tajwar Eshaan dake murza goshinsa kansa a ɗan rissine ƙasa. A gabansa ya dirƙushe yana mai miƙa masa kufan takobin hanunsa da babu tantama anyi adon jikinsa da gold ne. Takobin ya ɗaura masa kan dogon trayn da kufan yake. Hadimin ya miƙe da sauri yana ja da baya. Na biyu ya iso da sauri shima, sai dai saɓanin na farko shi bayansa ya koma yana warware farar rigar hanunsa mai maɗauri. Hannayensa ya ware da ɗan kai idanunsa inda Iffah ke tsaye tana tsiyaya shayi a karamin kofi, ya wani irin ɗage kafaɗu da juya rigar cike da salo ta rufe jikinsa tare da zarge igiyoyin biyu akan damammen cikinsa. Hadimi na uku ya iso shima ya durƙushe hanunsa dauke da ƙaramin farin towel. Nan ma dai ɗauka yay ya rataya a kafaɗa bayan ya ɗan tsane zufan daya taru masa a gefen wuya da goshi alamar dai jininsa a tsinke yake a lokacin. A yanda hadiman suka sani daga haka hanyar da zata maidashi bedroom ɗin daya kwana yake bi, acan zai samu shayinsa na ƙa'ida mai dafawa ta kai, bayan yasha zai shiga wanka kafin ya fito inda aka shirya masa karin kummalo. Sai dai saɓanin yau yana ɗaga ƙafa domin barin wajen bayan ya dubi Aamin nasa ya rissinar da kai kaɗan na alamar sallama da girmamawa a garesa Iffah dake faman baza ƙamshin da ga Shahan-shan ɗin kawai suka sansa ta isowa wajen ɗauke da ƙaramin kofin shayi dake tururi fari tar na glass. Da sauri duk hadiman suka juya bayansu, dan kallon abinda zai iya biyo bayan wanda suka gani ɗin haramunne a garesu. Iffah dake taku a nutse kamar wata hawainiya takalmanta da ba wani tsinin kirkine da su ba na bada sautin isar da saƙon tahowar tata ta iso gabansa.. Ƙin yarda tai koda wasa su haɗa idanu. Idanunsa da kallonsu ke canjawa ya sauke akan kofin shayin da take miƙo masan. Shiru babu alamar zai amsa, har hanunta na ƙoƙarin fara yin dayi. Sai da ta fara ambatar sunan ALLAH kafin ta ɗago fuskarta a dake, “Ƙin sha na nufin rauni da muhimmancin Zawjata-almilk a gareka. Ko kuwa cigaba da tabbatarma duniya abinda suka sani shine gaskiya ranka ya daɗe”. Yanda lips ɗinta da suka sha pink lipstick ke motsawa ya zubama ido, sai dai maimakon mata sharhi akan zancenta kamar yanda taso yau gefe ya ɗan maida kansa da amsar shayin kamar wanda ya shiga halin tarkon kasala. Karan farko ta sakar masa wani lallausan murmushi da faɗin, “Thanks”. Basarwa yay ta hanyar ɗan duban gefensa a takaice ya furta, “Aami”. Da sauri Iffah ta duba wajen tamkar sai yanzu ne taga Miran Arshaan ɗin, “Ya salam”. Ta faɗa a zahiri da nufarsa ta zube ƙasa domin miƙa gaisuwa a garesa. Ya ɗan murmusa zuciyarsa taf da al'ajabin wannan figigiyar yarinya da da auren wuri yayi ya haifa wanda suka fita nesa ba kusa ba. Cike da salonsa na fuska biyu ya amsa yana mai ƙare mata kallo ta ƙasan ido. Iffah daba kula da hakan tai ba cike da girmamawa ta miƙe da faɗin, “Uncle bara a baka shayin kaima”. “Zan so kasanwa na farko da zai ci abu daga hanunki Ibnati”. Jin daɗin kalamansa yasa Iffah sakin murmushi da ɗan rissinawa ta furta, “Na gode Aam”. Shima dai shayin ta kawo masa, nan ma yay mata godiya da sanya albarka yana ɗan duban sashen da Tajwar yake tsaye dafe da ƙarfen da aka zagaye wajen ta bakin ginin yake ya tsurama cikin masarautar idanu yana ɗan kai shayin bakinsa tamkar bai san abinda ke gudana a wajen ba. A hankali ya taka inda yake shima yana shan nasa. “Yanzu ne daular ruman ta tabbatar da samuwar Zawjata-almilk”. Sarai Tajwar Eshaan ya jisa. Amma halinsa na ƙasaita da mafi yawan iyayen nasa suke ambato da girman kai yasa yay tamkar baiji ɗin ba. Sai ma juyawa da yay bayan wasu sakkani ya dubi Aamin nasa cikin tausasashiyar muryarsa mara hayaniya da kamewa ya furta. “A huta gajiya”. Ya bar wajen. Ga mamakin duk wanda ke'a wajen gaban Iffah dake ɗan nisa da su ya isa. A bazata taji tattausan tafin hanunsa da yay sanyi ƙalau sakamakon iskar wajen a cikin nata. Da sauri ta rumtse idanu tana mai ambaton sunan ALLAH a zuciyarta da ɗan dubamsa. Ba ita yake kallo ba, sai ma fara takawar da yay wanda ya tilastata binsa tamkar raƙumi da akala. Batare da sun luraba takun sawayensu na sauka da ɗagawa a tare sakamakon shima tafiyar izza da ƙasaita irin na masu mulki yasa baida garaje a tafiya tamkar wani mace. Anan ɗin ma dai tana sanya ƙafarta na'ura ta sanar da ita wacece, haka shima. Da sauri hadimin dake a ƙofar ya zube yana kwasar gaisuwa. Hannu kawai ya ɗaga masa yay gaba abinsa har lokacin hannunsa na cikin nata ya riƙe gam kamar wanda aka bama amanar riƙon nata dan karta suɓuce...... ★★..... ★★...... A ɓangaren Barrister kamar yanda mutanen can suka sanar masa hakance ta faru. Sunyi amfani da kamannin da mutane suka daɗe da sanin sunayi, wanda shine ma tushen zamowarsu abokai, aikinsu kuma ya maidasu aminai. Sai dai muryarsu ta banbanta da wasu abubuwa na ɗi'ar yau da kullum. Akan wannan ne mutanen suka bashi training na dole dalilin barazana da sukai masa akan iyalinsa dama kashe Barrister Akeem ɗin da yake gudun cin amana. Bayan kimtsawarsa da shiga irin ta Barrister Akeem da bashi wasu bayanai akan aikin da zai musun suka bashi key ɗin motar Barrister Akeem. Sun sanar masa dukkan motsinsa akan idonsu ne, kuskure ɗaya akan ganganci fansar rayuwar ɗaya daga cikin ahalinsa ne kona Barrister Akeem. Dole Barrister ya kwantar da hankalinsa dan ya fahimci mutanen sunfi ƙarfinsa, gashi koba komai yana buƙatar kuɓuta kodan tarin ayyukan dake gabansa musamman akan aikin da ayanzu ya tasa a gaba da alƙawarin cika alƙawari. Su da kansu suka bashi address ɗin inda zaije, yayinda ya hau titi kuma sai ya fahimci suna biye da shi a mashina wasu a mota. Ya ɗan rumtse idanu da jan kakkauran numfashi ya fesar lokacin da ya gama dai-daita parking a inda suka umarcesa zuwa. Sai da ya karanto addu'ar neman ɗauki ga ALLAH sannan ya fito riƙe da brefcase ɗin Barrister Akeem a hannu. Ƙaton gidan ya ɗan ƙarema kallo kafin ya nufi inda suke sanar masa yabi ta hanyar bluetooth ɗin kunnensa. Kansa kawai yaɗan gyaɗa tamkar yana gabansu ya nufi ƙofar...... ★★★....... ★★..... A cikin masarauta kam kusan ƙarfe tara da wasu mintuna labari mai razanarwa na rashin ganin Sayeed Khairul-Bashar (Aami gasu Miran Arshaan. Kaka kuma ga Tajwar Eshaan. Shine wanda yay maganar jiya a ɗakin tattaunawa bayan tashin Tajwar Eshaan). Zancen rashin ganin nasa ya fito ne daga iyalansa, da farko an ɗauka yana cikin masarautar ne dan sun tabbatar daga sallar asuba bai dawo ba. Amma ganin har lokacin shigarsa gida ya wuce ƴaƴansa kuma sun bincika a inda suke tunanin ganinsa amma babu shi sai suka fitar da maganar. A take sojojin gidan masu bada tsaro dama hadimai suka bazu lungu da saƙo amma babu alamar hakan. Anbi diddigin wasu daga cikin cctv footage amma fitowarsa kawai aka gani daga sashen nasa babu komawarsa. Hakan ya matuƙar bama kowa mamaki da ɗaure kai. Dan ta ko'ina masu tsaron ƙofofi sun tabbatar basuga fitarsaba sukam. Gashi kuma an duba lungu da saƙo na gidan amma babu wata alamarsa..... ★★...... Lokacin da labarin rashin ganin Sayeed Khairul-Bashar ya iso kunnen Miran Jasim da Miran Arshaan dake tare kallon juna sukai, sai kuma duk suka kauda kawuna suna murmushi. Cikin son basar da zancen Miran Jasim ya cigaba da magana kan zancen da Miran Arshaan ya kawo masa dangane da Iffah “Lallai wannan yarinyar hatsabibiya ce, aini tun isowar labarin kasancewarta raye a safiyar jiya al'amarin ta kemun kai kawo. Zancen ka na yanzu kuma ya sake tabbatar min da shirinta ta shigo masarautar nan.” “To ai ta tara ta samu, dan dama mu irinta muke nema”. Cewar Miran Arshaan yana ɗan murmushi. Miran Jasim ya jinjina kai shima yana murmushin nasa na izza da ƙasaita. “Hakane kam ta kawo kanta inda ake jirace da zuwanta. Dan kam zamu sauke ƙuruciyar dake izata a tunanin yin rawa da bazarta dake ɗawainiya da ita. Zata ƙarasa mana aikinmu cikin sauƙi batare da ita kanta tasan a cikin tarko take ba”. Nan ma murmushi Miran Arshaan yay idonsa akan ɗan uwan nasa. “Zuwa yaushe aikinmu zai fara?”. Miran Jasim ya ɗan ɗage kafaɗa da taɓe baki. “Bazai ɗauka lokaci ba. Sai dai muna bukatar wani point ne dole”. “Wanda yake hannunmu fa?”. Cewar Miran Arshaan da mamaki. “Kai wannan bashi da wani ƙarfin da zaiyi tasiri ita a gareta, duk da dai zai iya zama kamar share mana fage ne. Zaren da nake ganin zamu ja ya kaimu gareta ɗaya ne, duk da dai har yanzu babu wani shaida dangane da tsallakewarta itama. Amma zamu yi amfani da damar, a wannan karonma matarka ce zata mana aikin”. “A wannan gaɓar fa ya kamata mu canja salo, Jasrah nada matuƙar wayo, kar yawan bugar cikinta fa yasa ta fara fahimtar wani abu”. “Sai idan kaine ka bada ƙofar hakan Arshaan. Shekara nawa muna amfani da itan bata fahimtaba sai yanzu. Ka dai kawai ka kasance mai lura”. Kai kawai Miran Arshaan ya jinjina batare daya ce komai ba...... ★★★...... Suna yin ɗan nesa kaɗan da masu tsaron ƙofar Iffah ta zare hannunta da sauri tana ɓata fuska. Bai ko juyo ya kalleta ba balle ya nuna alamar yasan mitayi yay gaba abinsa cikin takunsa na nutsuwa da tsantsar ƙasaita tamkar baya son taka kafafun nasa. Da ƴar hararar ƙasan ido ta bisa tana ƙunƙuni a zuciyarta. (A haka dai kamar na wani limamin masallacin Saudiyya, sai dai zuciyar ko kafiran farkon ƙarni haka suka gansa suka barsa. Wanda duk zai iya salwantar da rai yay barci lafiya babu ko ɗar ai ya dace ka kirasa da duk sunan daya zo maka a rai dan ya cancanci haka). “Ni zanyi maganinka da izinin ALLAH”. Ta faɗa a zahiri fuskarta na nuna gaskiyar ɗacin da zuciyarta ke mata.......✍️ 🥱Bazamu hanaki ba Iffahn mu🏇😉. *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_41_* .......Shiru yay yana kallon inda ya saba iske shayinsa, wayam babu komai, ya kai zaune a kujerar cikin alamun gajiyawa, a gefe kuma tsaurin idon yarinyar da ƙarfin halinta na masa kaikawo. Shan wannan shayin ya zame masa jiki da in bai sha ɗin ba sam bama yajin daɗi, har ma yakan tsinta kansa a wani yanayi da shi kaɗai ya barma kansa matsayin sirri duk da abun na matuƙar damunsa. Har yayi yunƙurin dauriyar sharewa tunda ya ɗan sha wani amma jin abinda yake gudun na taso masa ya sashi furzar da zazzafar iska, babu shiri ya danna alerm ɗin dake isar da saƙon kira ga amintattun hadimansa. Cikin mintunan da basu wuce uku ba ko sai ga ɗaya daga cikin su ya iso. A gabansa ya zube cikin tsumar jiki yana mai ambaton... “ALLAH ya ƙara ma Shugabana tsahon rai da ingantacciyar lafiya, umarninka shine abin jirana”. A zuciya ya amsa da Amin, a zahiri kam babu alamar zai tanka kamarma bashi ya bukaci ganin hadimin ba. Tsahon mintuna uku ƙasaita da izza irinta saraki na dawainiya da shi kafin ya motsa lips ɗinsa a hankali cikin bada umarni. “Miya hana a kawo shayi?”. Hadimin ya ƙara ƙasa da kai jikinsa na ɗan rawa. “Umarni ne daga Zawjata-almilk”. (Umarni?!) Ya maimaita kalmar a zuciyarsa cikin ƙara ƙanƙance idanunsa. (Shi kam ya zaiyi da yarinyar nan ne? Mai kama da alja.....) Ya sake ayyanawa a zuciyarsa batare da ya ƙarasa ba. Sai kuma ya kalla hadimin ya ɗauke kai. “Ina buƙatar waninsa”. Da sauri hadimin ya ƙara gurfana yana amsa masa ransa fal mamaki da al'ajabin wannan sabon al'amari. Fuskarsa gwanace wajen shanye sirrin dake bayyane, amma yanda ya yatsinata da lumshe idanu a yanzu zai tabbatar maka akwai magana tattare da shi..... ★★ Duk yanda taso nuna halin ko'in kula kan abinda ya farun yanzu hakan ya gagara. Dan mayataccen ƙamshin turarensa daya bambanta da wanda ta saka duk da suma nasa ɗinne ya mugun addabarta. Takai hanunta kan hanci yafi sau biyar, sai ta shinshina sai kuma ta janye tana laɓe baki. Hakan kuma bai hana anjima ta sake maidawar ta shinshina. Daga ƙarshe da taga abin na neman zama mata ɗan kaɗafi sai ta faɗa toilet ta wanke hanun da sabulu, amma dan mayata yaƙi ya daina sai da ta ɗauka ɗaya a cikin turarrukan datai amfani da su na ɗakin tasa a hannun sannan ta daina ji. Littafinta ta ɗauka domin cigaba da nazari, sai kuma ta tsaya cak, wani tunani ne yazo mata a zuciya, dan haka ta miƙe zaraf tana ɗaukar wayarta data gani tare da littafin alamar duk ma wanda ya kawota tare da su ya kawotan. Kamar yanda ta saba idan zasuyi magana tai dawnlording sabon WhatsApp app, sai da ta daidaita komai sannan ta lalubosa. Baya online gashi kuma tana buƙatar yau suyi magana ne bawai saƙo take son ajiye masa ba. Sai hakan ya sata jin babu daɗi har walwalarta ta ɓace. “Kona masa flashing?”. Ta faɗa cikin sigar tambayar kanta. Kan ta daga alamar gamsuwa, ta fito a watsap ɗin. A karo na farko tai dailing number ɗin cikin shakku. Harta katse ba'a ɗaga ba, damuwarta ta kara bayyana. Harta sake komawa watsap ɗin ta fito ta sake danna kiran. A hankali ta sauke ajiyar zuciya har ana iya jinta daga can. Tai sallama cikin yar muryarta dake nuna zumuɗin jin an ɗaga, sai dai ba'a amsa mata ba gashi kuma tanajin alamar ana saurarenta. Danne takaicinta tai ta sake sallamar, nan ma shiru dai babu ma alamar za'a amsa. Cikin suɓutar baki taja tsoki da faɗin. “Nifa a rayuwa na tsani walakanci wlhy, shiyyasa komai nafi yarda naima kaina. Yanzu haka wani ɗan iyan dake ƙarƙashin sa ya ɗaga kiran kamar waccan ranar dana fara kira, ƴan hana ruwa gudu kenan. Nima badan ƙaddarar faɗawa hannun wannan Dodon ba da yanzu ina can ina karatuna na jaridar a daina yarfani. Kai insha ALLAHU kafin naga bayan a azzalumin nan ko sau ɗaya ne sai na hau kujerar karagar mulkin nan nayi tankaɗe da rairaya cikin duk ƴan jaridar ƙasar nan da jami'an tsaro aikin banza......” Jin kamar sautin fitar murmushi a kunenta ya sata saurin ciro wayar ta kalla. Dai-dai ana yanke wayar. Ido ta kwalalo waje da dafe bakin. Sai kuma ta janye da faɗin, “Kai kamarfa daga cikin wayar ne sautin nan ya fito wlhy. Kai ina”. Ta sake faɗa tana ɗan wawwaigawa babu dai alamar wani a ɗakin sai itan kaɗai. “Oh ni Iffah anya bakin nan nawa bazai yankani ba wataran, yanzu hakama shine yazo ya amshi wayar inata zuba ban sani ba”. Tai tagumi cikin takaicin kanta. Kamar kuma wadda aka ɗan zabura sai ta sake ɗaukar wayar. Cikin sa'a tai tozali da ganinsa online har an amsa mata sallamarta ma. Sai kuma ta shiga kokwanton tayi magana ko kawai ta share. Wata zuciya ta amsa mata da (Kema kin san bashi bane ya ɗaga miki waya. Ki basar kawai). Da alama ta gamsu da shawarar, dan haka ta saki murmushi da buɗe saƙon. “Sorry kin kirani bana kusa yarona ya amsa”. Amsar data samu kenan bayan sallamarta da aka amsa. Har cikin rai taji daɗi, dan haka a fili ta furta “Alhamdullah dama naji haka a jikina”. Shi kuma ta bashi amsa da “Babu damuwa Sir”. “kina da fahimta Shahrbano”. “Bankai nan ba😣”. Ta bashi amsa da emojin yamutse fuska. Sharewa yay da faɗin, “Ta samu ne?”. Itama sai ta share da bashi amsa da. “Kusan haka. Sai dai a wannan gaɓar lamarin akwai ban tsoro Sir Ajmaal. Da gaske mutanen nan matsafa ne kuma suna aiki da aljanu”. “Ya arrahaman! Kamar ya? Har kimsa na tsorata fa”. “Tab tunma kan na faɗa kenan. To kama cire dan wlhy ba aljanu ba ko bataliyar ifiritai ce sai naga bayan mutumin nan. Wai fa jiya da dare nabar sashen nasa na koma inda sukace nawa kawai yau na wayi gari na ganni an sake maidoni sashen Dodon nan. Ɗakin dana kwana kuwa duk da haɗuwarsa na rantse maka a harmutse kamar anci dambe”. “Dambe fa?”. Ya share zancen farko ya amsa na ƙarshe. “Wlhy kuwa Sir! Sai dai fa ni wannan bai damenba. So nake nasan ta yaya aka ɗakkoni aka maido ni inda ba nan na kwanta ba”. “Kina da gaskiya dan akwai alamar tambaya kam. Amma ke yanzu wane mataki kika ɗauka?”. “Komai banyiba har yanzu, nadai fara bincika irin kamshin da naji jikina nayi, inma shine ya aika aljanunsa suka ɗakkoni dan ya kashe ni”. “🤭”. Ya bata amsa da emojin rufe baki alamar tare dariya. “😞Bafa abin dariya bane wannan, abin a dubane. Idan kuma aka halakani kafin ƙwato muku ƴancinku ku kukayi asara Sir Ajmaal”. “Eh gaskiya hakane kuma ranki ya daɗe. Yanzu dai ƙarasa bani labarin dan in san ina zan kama. Saboda na gama shirye-shiryen buɗe wani sashe na shiri na musamman akan wannan case ɗin, sai dai komai zai kasance cikin hikima”. “Aiko da naji daɗi Sir, dan gara kam a fara kafin ma na mutu na dinga ji. Dama inason maka zancen wancan tashin bomb ɗin, ko ka san mutumin nan ko damuwa bai nuna ba akan lamarin tsabar bai ɗauki rai bakin komai ba. Wlhy naji kamar na shaƙesa a jiyan kowama ya huta dan takaici”. “Wai da gaske kike zancen nan ranki ya daɗe?” “Wlhy kuwa babu wasa. Ni ka daina kirana da wannan sunan bana so”. “Kiyi haƙuri kin cancanta ne ai. Zawjata-almilk guda ai ba abin wasan mu bace. Nima dai tsaurin ido yasa har nake iya zaman tattaunawa da ke”. “🙄😏”. Ta tura masa tana kashe data ɗinta. Daga can Ajmaal ya ƙurama emojis ɗin ido yana mai ƙoƙarin danne dariyarsa amma hakan ya gagara, dole yay faffaɗan murmushi har haƙoransa na bayyana yana ayyana (ƙuruciya daɗi) a zuciyarsa. Ganin ta kashe datan shima sai ya kashe kawai dan yana son sai ya nutsu yay zaman nazari akan abinda suka tattauna ɗin..... ★★..... KAUYEN JUMNA ★...... Alhamdullah dawowar Kaka da tsayuwar daka akan lafiyar Ummu yasa jikinta ƙarayin sauƙi har tana ɗan yin magana. Wani lokacin ma idan suna ƴar hira takan ɗan saka bakinta musamman idan akan Iffah ne da a mafi yawan lokuta take faɗo musu a zukata. Bawai halin da suka shiga kansu Babiy ya mantar da su ita bane, a koda yaushe tana manne a rayukansu, suna kuma binta da addu'a da cigaba da baza kunnen saƙon mutuwarta kamar ƴaƴansu na baya. Duk da dai ga Iffahn na nan shafe wata na uku kenan a daular ruman ɗin. Yau ma kamar kullum Ummu da Iyyani na a tsakar gida suna aiki wanda kusan Ummu ce keyinsa duk da bana kirki bane. Kaka ya fita tun ɗazun wajen jana'izar mutuwa da akayi ta wani tsoho. Sauri-sauri Ummu ke ƙarasa aikin saboda rana ta ɗaga gata da zafi sosai kasancewar su yankinsu akwai sahara, danma suna ɗan samun sassauci dalilin ruwa ne zagaye da ƙasar tasu. Sai dai kuma zaman Dahab City (Daular ruman) kamar a tsakkiyar ƙasar ta ruman yasa su sunfi samun zafin yashin fiye da sanyin ruwan daya mamaye wasu jahohin dake a gaɓarsa sosai. Sallamar da akayi ta saka Ummu amsawa tana mai duban ƙofar gidan, Iyyani ta fito tana faɗin, “Inaga mutanen Abbunku ne da basa ƙarewa. Gashi kuma bai dawo ba har yanzu ko yaya zamuyi kenan?”. “Nima shi nake tunani Iyyani, kona leƙa na gani tunda ba'a sani ba ko baƙon mai muhimmanci ne?”. Har Iyyani ta buɗe baki zata bama Ummu amsa sallamar Kaka ta katseta. “To Alhamdullah gamashi nan”. Iyyani ta faɗa tana kallon Ummu. Cikin fara'a kaka ya shigo, hakan yasa bayan sun masa sannu Iyyani ke tambayarsa ko lafiya?. Fuskar tasa da murmushi har sannan ya ce “Bani abun zama kedai yaron nan ne Zakariyya makwafcin su Jumimah”. Ya kare maganar da kallon inda Ummu take. “Ah Masha ALLAH, ALLAH yasa muji alkairi to”. Iyyani ta faɗa tana ɗakko masa abinda ya buƙata har da ruwan sha ma a kofi....... ★★★.... ★★..... ★..... Iffah kam dake ta faman tsuke fuska ita a dole taji haushi ta jawo rigar ɗazun ta maida a saman gown ɗinta ta fice. Isowarta falon dai-dai isar da sakon Tajwar Eshaan akan sake dafa masa shayi a bakin hadimin nan ga masu dafa abinci. Kai tsaye mamaki ya bayyana ƙarara a kan fuskarta. Amma sai ta dake babu alamarsa a zahiri taima hadiman wani kallo ta ɗauke kai. Ba ƙaramin razana da ganinta a cikin kicin masu girkin sukai ba. Dan hakan zai iya zamar musu rasa aikinsu. Sai dai yanda tai kicin-kicin da fuska ya sasu kama kansu, kwarjininta da gizagonta na kere yawan shekarunta. Jikinsu har rawa yake lokacin data buƙaci ganin kayan shayin da Tajwar ɗin ke amfani da su. Daki-daki take binsu da kallo cike da nazari, sai da ta gama tsaf kafin ta juya garesu fuska a tsume. “Idan ina buƙatar wasu bayan waɗan nan a yanzun fa?”. Cikin mamaki da tsoro suka sanar mata za'a kawo da gaggawa. “Ina buƙatar zama da mai kawowar”. Ta faɗa a gadarance da juyawa ta fara haɗa kalar shayi da salon dabararta batare da tayi amfani da wanda ake dafa masan ba. Wannan duk cikin shirinta ne na son ƙuntata ma zuciyar Tajwar Eshaan a cewarta. Cikin lokaci ƙalilan ta gama kasancewar ba wani mai yawa bane, ta juyesa a haɗaɗɗen butar shayi tare da haɗa komai na buƙata tai ƙoƙarin ɗauka. Da sauri hadima ɗaya ta miƙe ta amsheta. Bata musaba wajen bata dan dama ba sanin inda zata samesan tai ba. Hadimar tai tsaye a dai-dai ƙofar ƙaramin falon alamar iyakar ta kenan. Iffah ta fahimci haka, sai kawai ta amsa batare da tace komai ba. Ba tsoro ko shakkar haɗuwa da shi take ba, abinda zai farunne idan ta shiga kawai take tunani. Tsahon minti biyu kafin tai ƙundunbalar shiga dan a ganinta wannan wata dama ce ta biyu a gareta, cikin takunta na nutsuwa da dakewarta ta tura kai bayan ƙofar gilashin ta zuge da kanta batare data tabata ba.........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_42_* .........Kasancewar Barrister Akeem ba baƙo bane na shigowa gidan masu hidima a gidan suka dinga gaidashi. Amsa musu Barrister Abdallah ya dingayi da fara'a da kuma muryar Barrister Akeem data zama yana kwaikwaya a yanzu kamar yanda aka horar da shi. Ya iso katafaren falon da yaji komai na more rayuwar duniya, ga kamshi na tashi irin wanda aka san duk wani jinin ƙasar ruman da shi. Cikin girmamawa ya kai zaune fuskarsa da murmushi ya shiga gaida babban mutum ɗin dake zaune a falon cikin shigar kayan ƙasar na alfarma. Da ƴar sakin fuska mutumin ya amsa masa da faɗin, “Barrister sai yau ake ganinka? Bayan kuma tun jiya nasa a sanar maka na dawo ƙasar”. “Amun afuwa ranka ya daɗe, an ɗan samu wani tazgarone daya riƙeni a dalilin zaman da Boss namu ya kira, nayi zaton zamu tashi akan lokaci harna iso nan ɗin sai hakan bata yiwu ba, ganin dare yayi kawai na wuce gidan dan nasan kana bukatar hutu”. “Hakane kam. Yaya aikin naku?”. “Alhamdullh ranka ya daɗe munata bubbugawa”. Murmushi mutumin yayi, sai kuma ya ɗan gyara zamansa da zuƙar shisha ɗin hanunsa yana gyaɗa kai. Shiru ya biyo baya kasancewar ɗaya daga cikin masu masa hidima ya kawo ma Barrister shayi. Sai da ya kammala ya fice mutumin ya ajiye marikin shisha ɗin da fesar da uban hayaƙin daya tara a bakinsa. “Barrister dama ina maka wani neman gaggawa ne akan abokinka mai shegen taurin kai Barrister Abdallah Aas”. “Tofa oga ya ƙara yin wani laifi ne?”. “Kusan haka kam, dan akwai wani case na aminina dake a rufe sai ƙoƙarin ganin ya buɗosa yake yi. An masa gargaɗi kusan sau uku amma bai ji ba har sai da yajama kansa aka kauda shi kasan mutumin na ka da taurin kai”. “Kauda shi kuma ranka ya daɗe?”. Barrister ya faɗa cikin nuna rudanin as shine Barrister Akeem. Murmushi mutumin yayi irin nasu na manya yana ɗage kafaɗa alamar ko'a jikinsa. “To in basu kaudashi ba mi kake so suyi Barrister?. Yana da taurin kai ne gaskiya. Nasan dai kaji zancen tashin bomb ɗin can na jihar Hubab..?” “Yes Yes ranka ya daɗe, ai kowa ma dake ƙasar nan yaji wannan baƙon al'amari mai tada hankali tunda bai taɓa faruwa ba a wannan ƙasa tamu......” “To ga abokinka kam yaja ya faru, dan an tada wannan bomb ɗinne da shi kasancewar a cikin motarsa aka sakashi”. A matuƙar razane Barrister ya furta “What! Ranka ya daɗe abokin nawa?”. “Kaga kwantar min da hankalinka wannan ba wani abu bane. Sakamakonsa ya amsa a hannunsa. Kaga ko anan gaba masu shirin taurin kai irin nasa sai su kiyaye. Ba wannan ne abin damuwa bisa maƙasudin kiranka nan ba. Muna son ne ka maye gurbinsa a wancan case ɗin ne domin kwaso mana dukkan wasu bayanai da ya haɗa. Mun zaɓoka ne saboda kamaninku ɗaya, har yanzu kuma babu wanda yasan da shi bomb ɗin ya tashi. Kafin masu bincike su gama gano motarsa ce wadda bomb ɗin ya tashi a ciki muke bukatar ka kamla komai”. “Amma ranka ya daɗe......” Hannu ya ɗaga masa da sauri. “Karkace komai Barrister, nasan zafin rasashi kakeji, ina maka ta'aziyyar hakan. Sai dai ka sani, wanda ya ɓatar da shi kaima zai iya ɓaddaka kai da duk a halinka wannan yafi shan shayi sauƙi a garesa. Dan haka ka kula. Akwai saƙo na kafin alkalami a motar ka mu yini lafiya🙏”. Hakan da yay na nufin ya sallamesa. Barrister Abdallah ya miƙe jiki a sanyaye. Gaba ɗaya tunaninsa ya rabu da zuciya da kwakwalwarsa. A yanzu kam ya gagara fahimtar komai gaskiya. Shin idan har waɗan nan ɗin sune mugaye a garesa, waɗan da kuma su yake bibiya a case ɗin su Babiy to sukuma waɗan da suka sakashi wannan aikin fa? Kenan fa kuɓutar da shi sukai a waccan ranar ko mi abinda sukai ɗin ke nufi? Ya ALLAH mike shirin faruwa da ni ni Abdallah?. Ya tambayi kansa batare da yasan ina zai kama ba har ya ƙaraso jikin motarsa ya shiga. Da ƙyar ya iya tuƙin zuwa waje, yana hawa titi ɗan nesa da gidan aka dakatar da shi akan cewar yay parking ta cikin bluetooth ɗin kunnensa. Hakan ba karamin taimako bane a garesa, dan a yanda yake jinsa tabbas zai iya kife kansa a titin ma gaba ɗaya........ ★★.... ★★..... Babu kowa a ɗakin sai wani irin ƙamshi mai matuƙar saka jiki kasala da sanyin ac. Iffah ta lumshe manyan idanunta tana ambaton sunan ALLAH da sake buɗesu. (Kai kai kai duniya fa na inda take) ta ayyana a zuciya tana dire tray ɗin hannunta saman wani ɗan table dake gaban ƙyaƙyƙyawar kukera ta hutawa. (Dama ce fa wannan) ta zabura dalilin wancan furucin da zuciyarta ta ayyana. “Tabbas dama ce kam”. Ta maimaita a fili tana ɗan waige-waige a nutse cikin hikima kuma ɗan gudun kar ya zam akwai camara a ɗakin kamar yanda aka bazasu ta waje ko'ina a sashen. Adai iya dubanta babu kamar sauran ɗakunan data kwana, dan haka ta cire takalmanta cikin sanɗa ta nufi ƙofar toilet da zuciyarta ke raya mata yana ciki. Tabbas yana cikin kuwa dan jin motsin ruwa. Ta daga hannayenta sama alamar Alhamdullah sannan ta baro wajen. Da ma'ajiyar turarrukan sa ta fara, sai da ta gama ɗagasu ɗaya bayan ɗaya ta shinshina. Sam babu alamar irin wancan, cikin damuwa ta maida ta rufe badan zuciyarta ta wankesa da zargiba har yanzu. Dan ta gama haƙƙaƙewa aljanun tsafinsa ya tura suka ɗakkota a daren na jiya dan ya cika burinsa. Amma ALLAH ya hanashi sa'a shiyyasama taga ɗakin kaca-kaca kamar anyi dambe a cikinsa. Da alama sun gusar mata da hankaline shiyyasama bataji sanda aka ɗakkotan daga can ɗin ba. Harta juya zata fita zuciyarta ta sake nata shawarar ta ɗan sake duddubawa ko zataga wani shaida da suke buƙata akansa. Cikin yanayin dai ɗan tsoro-tsoro na mara gaskiyar dake gudun a kamasa take ɗan buɗe-buɗen ta, sai dai abin mamaki idan ka cire turarrukan data gama dubawa, da wasu tarin books a cikin wata ƙyakykywan show glass, babu wani abu a ɗakin bayan kayan gado da na ƙawata adon ɗakin kuma. Sai kuma kayan barci kala-kala a cikin wani dogon gilashi shima alamar matsayin wadrub, sai dai kasancewar zallar gilashi komai ana gani fes dan duk rataye suke a jikin hanger ma. Iffah da gaba ɗaya kanta ya kulle na mamakin ina kayan da yake sakawa? Da takalma? Su agogo dama duk wani nau'in kayan da yake ado dasu fa?. Dan acan ma sauran ɗakunan da ta kwana iya irin abinda ke anan ɗin kawai ta gani. Lallai dole akwai abinda yake buƙatar tayi nazari a kansa kenan? (Minene to?) Zuciyarta ta ayyana mata tare da katse tunaninta sakamakon jin wani masifaffen kamshin shower gel da tsumammun turarrukan wanka ƴan asali da bata taɓa shaƙar irinsu ba. A ɗan firgice ta juyo, sai kuma ta sake juyawa da sauri tana mai rumtse idanunta da faɗin, “Wayyo ni Iffah” ta nufi ƙofar fita da matuƙar sassarfa tamkar zata kifa dan hatta da tsumar jikinta a bayyane take.. Shiko da komai ya faru dominsa babu alamar hakan ya damesa. Dan ko kallon inda take baiba tunda ya fito. Babu ma alamar yasan da ita a ɗakin tattare da shi. Amma abin mamaki sai gashi ya zauna a kujerar da table ɗin ke tare da ita, wanda kuma anan ne Iffah ta ajiye shayin nasa. banbancin ɗanɗano da wanda ya saba sha kamar ɗazun ya sakashi yin tsamm da tsurama shiyin ido tamkar a cikinsa yake neman amsar sanin yaya hakan wai ke faruwa?. A zahiri ko babu wani abu a fuskarsa sai ma glowing da take irin na mai lafiyayyar fatar data jiƙu da hutu da jin daɗi. Yatsunsa biyu ya ɗan kai saman goshinsa ya murza kusan tsahon sakanni arba'in, kafin kuma ya janye yana mai ajiye kofin ya miƙe batare da ya sha ba. Ta can wajen gilashin da kayan barcinsa suke ya taka, hannunsa ya daura akan gilashin sai gashi gaba ɗayan drawer ɗin ta zuge a hankali ƙofa ta bayyana. Takawa yay ya shige, ta maida kanta ta zuge........ (😏😏an wani rufe dan kar na gani, to Iffahn mu zata gano mana ai ehe🚶😞). ★★..... Da gaske dai ɓatan Sayeed Khairul-Bashar ya tabbata a cikin masarauta. Dan Iya duk wani bincike babu wata alama ta yana a cikin gidan. Iyalansa sai kuka suke duk sun hargitsa masarautar. (Kamar yanda kukaji a baya Sayeed Khairul-Bashar Aami ne a wajen su Tajwar Haysam, Miran Arshaan, Miran Jasim da dai sauransu. Kaka kenan a wajen Tajwar Eshaan shi kuma. Sayeed Khairul-Bashar da Tajwar Abdul-majeed kakan Tajwar Eshaan ƴan uba ne suma. Kamar yanda a yanzu Tajwar Eshaan ke shan gwagwarmaya a hannun su Miran Jasim haka mahaifinsa Tajwar Haysam yasha wannan wahalar a hannun Aamin nasu irin su Sayeed Khairul-Bashar. Sai dai ko kusa basu ci galaba ba dan Tajwar Haysam ma dai kaifi ɗaya ne kuma tsayayyen mutum kamar yanda kuke ganin Tajwar Eshaan a yanzun. Wannan rashin nasarar tasu akan Tajwar Abdul-majeed da ɗansa Tajwar Haysam ce ta dawo kan Tajwar Eshaan a yanzu, sai dai kuma da alama bazai taɓa ya raga musu ba. A gefe kuma su Miran Jasim na amfani da wannan damar wajen dama garinsu akan Tajwar Eshaan... ALLAH ya sa kun gane ni dai ba ruwana🥱🚶) Duk bidirin da ake Tajwar Eshaan bai sani ba, dan yau ya fita fada ne a makare. Koda ya isa fada kuma aka kawo zancen da farko bai ɗauka abin na gaske bane, dan haka cikin halin ko'in kula irin nasa ya nuna musu maybe yayi fitar da kowa baya buƙatar ya sani ne. A bashi lokaci a gani. A cikin wasu ƴan majalissar tasa wasu sun gamsu da wannan jawabi, harma aka fiddashi waje dan hankulan mutane su kwanta. Sai dai a wani gefen kuma jawabin Shahan-shan ɗin tamkar samun wani makamine na dukansa da shi ga maƙiyansa na ɓoye dana zahiri, sai dai sun danne a yanzu basuce komai ba suna jiran lokaci........ ★★..... BARRISTER ★★..... Ruɗanin da Barrister yake ciki ya wuce duk yanda mai hasashe zaiyi tunani. Gashi tunda suka maidashi gidan suka sake kullesa a ɗakin babu wanda ya waiwayesa har duhun magriba ya kawo, bayan idar da sallar isha'i ne aka kawo masa abinci. Dan haka ya fuskanci mai kawo abincin da alamar yar yanzu zuciyarsa ta kasa tsayawa waje ɗaya. “Dan ALLAH ina son magana da ogan ku Akhi. Ina da abubuwan tattaunawa da shi masu yawan gaske da muhimmanci”. Kamar bazai tanka masa ba sai kuma ya amsa shi da faɗin, “Boss baya nan, ganinsa kuma abune bamai sauƙi ba dan bana jin ma yana ƙasar. Karka damu idan yana buƙatar magana da kai zai zo da kansa basai ka nema hakan ba”. Daga haka yay ficewarsa. Jiki a sanyaye Barrister ya bisa da kallo harya maida ƙofar zai rufe yay saurin faɗin, “Na roƙeka kota wayane ka haɗamu, da gaske maganar da zanyi da shi nada matuƙar muhimmanci, da kuma buƙatar yinta da gaggawa”. Jimm saurayin yay yana kallon Barrister ɗin daga inda yake, sai kuma ya ɗan rausayar da kansa da faɗin, “Okay duk yanda mukai zan dawo”. “Nagode sosai”. Baifi mintuna biyar da fita ba sai gashi, har lokacin Barrister na zaune a inda ya barsa. Ya miƙa masa wayar hannunsa. Cikin jin daɗi Barrister ya amsa. Shi ya fara sallama da gaisuwa batare da la'akari daya girmi boss ɗin nasu ba. Amsa masa akai daga can a taƙaice, nan ma bai nuna ya damu ba cikin tashin hankali ya fara maganar dake cimasa rai.. “Alhmdullah na cika umarninku, sai dai sakamakon dana samo ya matuƙar rikita tunani na. Dan wannan case ɗin case ɗin da nake yine, kuma a dalilinsa naje ƙauyen Lufana. Yanzu kuma sun bani aiki akan kaina, Ina cikin ruɗani sosai, dan na gagara fahimtar manufarku ku da su, shiyyasa gaba ɗaya ruɗani ya kasa barina na fahimci abinda ya dace na fahimta....” “Karka damu kanka da son sai ka fahimta Barrister. Kai dai kai musu aikin da suka buƙata, basu bayanai akan naka da case ɗin kawai”. “Idan nai haka zan saka rayuwar bayin ALLAH ne a haɗari, wlhy mutanen na mutanen kirki ne komai an shiryashi garesu ne bisa wata manufa. Ina matuƙar jin tausayinsu, an rabasu da ƴaƴansu har uku, an kuma biyo ta wata hanyar rusasu da shine nake son ma san dalili, yanzu kuma ace nine da hannuna zan miƙasu, idan nai hakan bazan taɓa yafema kaina ba”. “Baka da wani zaɓi bayan hakan Barrister. Idan kuma ka shirya rasa iyalanka ne fine”. Kitt aka yanke wayar. Barrister dake jin hajijiya na ɗan kwasarsa ya dafe bango da sauri yana mai ambaton sunan ALLAH domin neman ɗauki.........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_43_* ..........Yau kwanaki huɗu kenan da rashin ganin Sayyid Khairul-Bashar, kwana shidda kuma cur da kai Iffah sashen Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed. Sosai masarautar a harmutse take, yayinda ƙananun magana da rikice-rikice ke neman tashi a dalilin fitar zantukan da Sayeed Khairul-Bashar ɗin yayi kan Tajwar Eshaan a daren da za'a rasashi. Nan fa kowa ya shiga yima al'amarin fashin baƙi da ga ɓangaren masu faɗa ajin gidan, wanda kai tsaye kusan mafi yawansu sun karkata zarginsu ne da kalaman da Tajwar Eshaan yayi shi kuma.. Duk abinda ke faruwa sarai yana isa kunensa, sai dai abin mamaki yayi biris kamar yanda ya saba. Yayinda shirun nasa ke ƙara wutar al'amarin matuƙa a tsakanin ahalin gidan baki ɗaya. Rashin daɗin maganganun da ke neman kawo bore ga mulkin Shahan-shan ɗin kai tsaye ne ya tada hankalin Malikat Bushirat matuƙa ta nema ganawa da ɗan nata, dan tun ana yi iya su ahali har abu ya zagaye masarauta yana neman fara fita waje. Bayan mintinan da basu gaza talatin ba amsa daga Tajwar Eshaan ta dawo ga Malikat Bushirat cewar baya buƙatar ganawa da kowa. Ranta ya matuƙar ɓaci da wannan amsa, dan take ta kori dukkan hadimanta ta shiga Safa da marwa. Tasan kota kirashi bazai ɗaga ba, kuma tunda yace bai buƙatar ganawa da kowan ta san halinsa har zuciya baya bukatar hakan. A kaikawon nata Iffah ta faɗo mata a rai, babu ɓata lokaci a karo na biyu ta bukaci ganinta duk da kuwa sune sukai mata katanga da sake baro sashen Tajwar Eshaan tun a waccan fitar acewarsu har sai ta cika kwanakin bakwai ciff. Iffah na zaune a ƴar barandar da takan sha iska da nazarin littattafan data maida hankali saƙon na Malikat Bushirat ya risketa, ta ɗanji mamaki, amma sai ta shanye a ranta kawai, dan tun washe garin kwananta na biyu Malikat Haseenat ta kirata a waya da kanta ta sanar mata karta sake cewa zata baro sashen Tajwar ɗin har sai kwanakin bakwai sun cika. Haƙuri ta bada bisa kuskurenta, daga ranar kuma ta haƙura duk da a takure take matuƙa da zaman, ganin ranta zaita ɓaci ma a banza sai ta maida hankalinta ga nazarin littattafan nan data ɗibo a books room, ko shi Tajwar Eshaan ɗin ma sai ta ƙulla wasan ɓuya da shi, dan tun faruwar tashin bomb ɗin nan ta riƙesa a rai, sai kuma maganar ɓatan Sayeed Khairul-Bashar da a yanzu aketa dangantashi da shi ya ƙara tabbatar mata da shi mutumin banza ne.... Cikin ƙanƙanin lokaci ta kimtsa, ta saka kamshin data maida nata ta ƙarfi da yaji. Tana fitowa daga sashen ta samu hadimanta na jiranta. Gaisuwarsu ta amsa a yau kam da kulawa, kafin ta shiga motar da zasuje sashen Malikat Bushirat ɗin a ciki duk da bawani uban nisa bane, amma akwai tazara gaskiya. Sojan daya buɗe mata yay salute ɗinta kafin ya maida ƙofar ya rufe, da sauri suma hadiman suka shiga ɗayar motar bayanta. A tafiyar da bata gaza mintuna biyar zuwa bakwai ba suka iso, anan ɗin ma dai buɗe mata akai, yayinda hadimai ke faman zubewa ƙasa bisa gwiyawunsu. Hannu kawai Iffah ke ɗaga musu da sakewa. Tausayinsu da sake jin zafin wannan mulkin iko na kasarsu a ranta. Tun a falo na farko tabar hadimanta, inda amintacciyar hadimar Malikat Bushirat ta karasa mata iso har inda take. “Barka da yamma Mah-mah”. Iffah ta faɗa cikin girmamawa ga Malikat Bushirat dake hakimce fuska babu walwala. Hannu kawai ta ɗaga mata, daga haka falon yayi shiru. Sai da ta gama shan kamshinta kafin ta tashi zaune da ƙyau idonta akan Iffah da ta rissinar da kai . “Ibnati kin san miyasa na kiraki?”. “A'a Mah-mah”. Iffah ta amsata da sauri. Cikin ɗacin murya Malikat Bushirat ta cigaba da faɗin, “Akan mijinki ne, nasan duk abinda ke faruwa a Masarautar nan kin sani kema”. “Hakane Mah-mah, amma sai nake ganin kamar ba haka bane, kawai dai wasu ne ke son ɓata masa suna”. Har cikin rai kamalan Iffah sun saka Malikat Bushirat jin sanyi a rai, sai zuciyarta na rawa dan zuwa yanzu al'amarin ɗan nata da gaske tsoro yake bata. Yayinda ita ko Iffah ta faɗi hakanne da manufar wayon da ALLAH ya bata domin son fahimtar abinda take son sani. Malikat Bushirat ta katse mata tunani da faɗin, “Hakan zai iya zama gaskiya, sai dai bazamu saki jiki ba dan da gaske al'amarin mijinki na bani tsoro. A yanzu haka na bukaci ganinsa amma shi yace bai buƙatar ganin kowa”. Da mamaki Iffah ta ɗan ɗago ta dubeta, a ranta kam jinjina rashin mutuncin sa take, a tunaninta ai ko kowa bai tsiraba mahaifiyarsa ta tsira. “Mah-mah kuma shi ɗinne ya faɗa?”. A karan farko Malikat Bushirat tai murmushin takaici. “Kar kiji ko tantama akan hakan Ibnati. Dan duk yanda kike tunaninsa ya wuce nan ɗin. A yanzu dai tunda ya nuna bai buƙatar ganin kowan bazai gani ɗin ba. Shiyyasa na kiraki nan dan kimin wani taimako na haɗani da shi ta waya”. Yawu Iffah ta haɗiye muƙut, dan itama dai a karan kanta kwanaki huɗu kenan bata sanyashi a ido ba. Tayaya kuma zata haɗasu a waya. To wanda ma ya nuna kai tsaye bazai haɗu da ita matsayin mahaifiyarsa ba ita kuma ƴar karere taya zatai hakan?. Amma bara ta amsa mata kawai, dan koba komai itama tana buƙatar jin gaskiyar lamarin ai....... ★★....... Har lokacin kwanciya barci Iffah bata samu wata makamar riƙewa na tunkarar Tajwar Eshaan ba. Hasalima bata da tabbacin a inda zata samesa. Tambayar hadimai kuma tamkar gazawace a gareta matsayinta na Zawjata-almilk. Kusan ƙarfe ɗayan dare tana tsaka da kai kawonta da faman jan tsaki saƙo ya shigo wayarta. Kamar zata share sai kuma ta ɗauka dan koba komai kullum a cikin tsumayen ji daga su Babiy take. Mamaki ya sata buɗe saƙon da hanzari ganin Malikat Bushirat. _Ina alfahari da kasancewar ki tare da gudan jinina Ibnati. ALLAH yay miki albarka, yanda kika zama sanadin yaye damuwata kema ALLAH ya yaye miki taki yanzu na gama waya da shi_. “What!!”. Iffah ta faɗa cikin ɗan zabura tana sakin wayar akan carpet. To mi hakan ke nufi? Ita da batama gansa ba taya har yay kiran mahaifiyar tasa da har ta gamsu itace sanadi. “Anya mutumin nan kuwa ba ifiritin aljani bane?”. Ta faɗa a zahiri tana waige-waige a ɗakin da tunanin ko dai akwai camara, to inma camara ɗin ce itada sukai magana a sashen Malikat Bushirat ma ta ina camara ɗin zatai tasiri kenan... Har waye war gari babu nutsuwata tattare da Iffah akan wannan al'amarin, dan ko barcin kirki batayi ba sam. Sai dai tuna a'a yau zata bar sashen ya saka mata ɗan jin sassauci ka ɗan a zuciyarta. Tana ko idar da sallar asubahi ta taattara kayanta waje guda tsaf tana jiran gari ya ƙara haske ta kama gabanta duk da kuwa wata zuciyar na bata shawarar take akan zuwa Tajwar Eshaan wai ko zata fahimci wata gaskiya saɓanin wadda zuciyarta ke tabbatar mata. Amma dai ta dake dan tana buƙatar damar keɓance kanta ko zata samu nutsuwa. A bisa al'adar masarautar kamar yanda ake kai Zawjata-almilk turakar Shahan-shan haka ake zuwa a ɗakkota cikin tattali da giramamawa tare da manyan ƙyaututtuka a randa ta cika kwanaki bakwai cif. Kowa ya ɗauka tunda an kai Iffah ba bisa ƙa'ida ba baza'ai wannan al'ada ba gareta musamman yanda tama karya doka a kwana ɗaya ta fito. Ga kuma a yanda masarautar take harmutse kwana biyun nan. Amma sai Malikat Haseena ta bama kowa mamaki ta hanyar haɗa komai na al'ada da akeyi, tare da mukulllin zabgegiyar mota ƙirar zamani da masu hidima har guda goma, da tarin turarurruka na musamman, Daneen Ammarah da tsaffin dake da hurumin gudanar da al'adar a masarautar suka yima sashen Tajwar Eshaan tsinke cikin busar sarewa mai tabbatar da isar da saƙon manufar al'amarin. Tofa wannan fa shine an tsokalo tsuliyar dodo. Dan kuma masu rajin faɗa aji tuni sun sake buɗe shafin caccakar Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed da kakar tasa Malikat Haseena kan basu damu da ɓatan Sayeed Khairul-Bashar ba. Ko kuma ma dai sun san komai ɗin da gaske. Wannan al'ada ta sake saka jikin Iffah mutuwa da shiga ɗunbin mamaki na gaske, har aka maidata sashinta babu alamar tana cikin cikakken tunaninta ma. Bin dai kowa take da ido tamkar gunkiyar da aka ƙirƙira domin tarihi... ★Ashe duk wan can ƙarami ne a abin mamaki da Malikat Haseena ta tanada a yau ɗin. Dan ƙarfe tara na dare da kanta kamar yanda tayi akan Iffah ta sake jagorantar rakiyar ɗaya cikin biyun Zawjata-almilk dake gidan tun kafin zuwan Iffah. Duk da bata haɗu da Tajwar Eshaan ba yau bata dawo da ita ba kuma dan acewarta zai ma gaji ne itama ya kulata idan ya gama zaman kulle kansa a ɗakin kamar yanda zukatansu ke basu sakamakon sanin hakan al'adarsa ce a duk sanda ransa ke ɓace. A wannan gaɓar kam kowa ya saki jiki waccan matsalar ta shuɗe tunda ga Iffah tai kwanakinta lafiya ta fito. Maimakon shiga fargabar rasata itama sai kowa ya ɓige da ƙananun magana akan rashin dacewar hakan. Yau ɗin ma dai malikat Haseenat tayi kunnen uwar shegu da su, yayinda Malikat Bushirat da Daneen Ammarah suka shiga halin mamaki da hukuncin na Malikat Haseenat a karo na biyu saɓanin dukkan shirye-shiryen su. A wannan karon kam sun yanke ƙuirin tun kararta suji ba'asi, sai dai sun barma safiya komai.... ★★ Surutai akan ɗimuwar da aka wayi gari da shi a masarautar ne ya farkar da Iffah dake fashin salla ɗan barcin daya figeta, dama da ƙyar ta yisa sakamakon kwana da tai neman Sir Fawzan da Sir Ajmaal a waya amma bata samesu a online ba hakama a kira. Sai abinda ta karanta da yay matuƙar tada hankalinta a ɗaya daga cikin littafan da take nazarta akan Tajwar Eshaan. “Tabbas babu lafiya” ta faɗa a zahiri tana miƙewa zumbur. Har ta nufi ƙofa ta dawo da sauri, toilet ta shiga a gurguje ta watsa ruwa ta fito. Sama-sama ta kimtsa jikinta ta fito. Hadiman ta da alamun sanyin jiki ya bayyana a agaresu suka dinga zubewa gaisheta. Maimakon amsa ta jefa musu tambayar da ruɗani ya bayyana kansa a cikin idanunsu da jikkunansu lokaci ɗaya. “Mike faruwa a masarautar nan? Da alama babu lafiya?”. Duk sun rikice babu alamar wani zai amsa mata. Sai kaɗuwa suke kamar masu jin sanyi. Halin da take ciki ya assasa mata jin zafin hakan ta daka musu tsawa. Sake firgicewa sukai, sai dai wajibi ne a gare su bin umarninta, dan haka cikin ƙarfin hali wadda ke matsayin amintatta a gareta ta sanar mata cewar an wayi gari da rashin Zawjata-almilk ne ta farko da jiya ta kwana turakar Shahan-shan sai Sayeed Khairul-Bashar shima da aka samu gawarsa a wani ɗaki cikin masarautar. Iffah da bata san da hakan ba ta ƙame ƙam alamar sumar tsaye ta wucin gadi ce ta risketa. Sai kuma hajijiya ta fara juya mata falon da hadiman, a hankali duhu ya dinga lulluɓe idanunta data kafa musu tabbacin bata cikin hayyacinta..........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_44_* ..........A hankali ta shiga ƙoƙarin buɗe idanunta da takejin sun mata matukar nauyi, sai kuma ta yunƙura ta tashi da ƙyar tana mai bin ɗakin da kallo. Dishi-dishi take ganin amintacciyar hadimar tata dake rukuɓe gefe ta zabga tagumi, _(An wayi gari da rashin Zawjata-almilk ne ta farko da jiya ta kwana turakar Shahan-shan sai Sayeed Khairul-Bashar shima da aka samu gawarsa a wani ɗaki cikin masarautar.)_ kalaman hadimar na ɗazun suka shiga dawo mata tiryan-tiryan a zuciya. Da karfi ta rumtse idanun nata da sukai jajur, ga kanta dake matuƙar sara mata kamar zai rabe biyu. Amma haka ta yunƙura ta sauka a gadon cikin ƙarfin hali da jarumta, dan idan batai amfani da wannan lokacin ba tabbas damarta ta kuɓuce mata kenan, batajin kuma zata sake samun wata cikin sauƙi. Zumbur hadimar ta miƙe itama tana mata sannu, bata iya amsa ta ba, sai nuni da tai mata ta je. Jiki a sanyaye ta fice, ita kuma ta jawo mayafi ya naɗama jikinta. Hadimanta dake falon farko duk suka miƙe, hannu ta ɗaga musu alamar bata buƙatar rakkiyar ta fice ita kaɗai dan babu yanda zasuyi. Da gaske masarautar a hargitse take matuƙa, duk da ba wannan ne karo na farko da aka rasa Zawjata-almilk ba, sai dai haɗi da mutuwar Sayyid Khairul-Bashar ta sake girmama ta Zawjata-almilk ɗin itama a wannan karon, da kuma tsallakewar Iffah da aka fara kaiwa babu abinda ya sameta. Cikin dabara da amfani da harmutsewar gidan tai amfani wajen kutsa kai sashen Shahan-shan. Zuwa yanzu fuskarta ba ɓoyayyar fuska bace ga masu tsaron sashen, dan haka babu wanda ya dakatar da ita sai ma gaisuwar girmamawa da suke miƙa mata duk da ganin nata ya basu mamaki. Su kansu hadimai masu girka abincin Tajwar Eshaan ɗin data samu a falo na uku saɓanin na karshe da ta san suna zama ganinta ya girgizasu, musamman daya kasance har yanzu ba'a fita da gawar Zawjata-almilk ɗin ba. Hasalima babu wanda yaga Shahan-shan har yanzu balle jin motsinsa. Kamar yanda tun a ƙasa bata tanka gaisuwar kowa ba anan ɗin ma bata kulasu ba dan ganinsu ya tabbatar mata anan abun ya faru kenan, ita wannan Zawjata-almilk ɗin a ɗakunan barcin falo na uku aka ajiyeta. Duk da bata san ya suke ba babu ko ɗar tattare da ita ta shige abinta inda take kyautata zaton ɗakunan barcin nan ɗin suke. Ido rufe take bin ɗakunan ɗaya bayan ɗaya, sai dai har kusan uku duk a rufe suke, bata gajiya ba ta cigaba sai a na biyar ta samu a buɗe. Cikin rawar jiki ta afka ɗakin, yayi kaca-kaca tamkar anyi dambe a cikinsa, dan wasu abubuwan ma duk gasu anan a fashe ƙasa, sai ɗigo-ɗigon jini ta wasu wajajen da dama. Idanunta suka sauka akan ƙyaƙyƙyawar budurwar da a shekaru zata iya zama sa'ar Arfa shimfiɗe a ƙasa ta jikin gado. Yanda gashinta da jikinta ke a birkice zai tabbatar maka da ta jigata matuƙa kafin ta rasa ranta, dan hanunta na dama dake kaca-kaca da jini riƙe yake da wata kwalbar filawar doco... Alamar ta riƙe domin kare kanta, amma duk da haka sai da akaci galaba a kanta. Iffah da jikinta ke karkarwa ta durƙushe hawaye na rige-rigen sakko mata, dan ji take kamar Fariha da Arfa ne take kallo kwance. Ta jima tana kuka akan gawar kafin ta zabura sakamakon maganganu da takejin suna tunkaro ɗakin, zumbur ta muƙe ta fara daukar video recording ɗin ɗakin har gawar, sai kuma ta ɗauka hoton gawar ta kowacce kusurwa. Jin shigowar za'ai da gaske tai saurin fara neman wajen ɓuya.... Miran Jasim, tare da Miran Arshaan, shugaban jami'an tsaron masarauta, Daneen Ammarah sai Malikat Bushirat da a wannan karon ta kasa haƙuri itama suka shigo. Sai da suka gama bin ɗakin kaf da kallo kafin su ƙarasa kan gawar. Shiru babu wanda ya iya magana a cikinsu har tsahon wasu mintuna kafin shugaban jami'an ya nisa. “Exactly kisan irin na baya ne dai babu wani banbanci gaskiya, da alama kuma tayi ƙoƙarin kare kanta itama shine dalilin kasancewar ɗakin a haka harma da wannan jinin”. “Wannan lamari daban mamaki yake, taya za'ai kisa amma babu wani alamar yanda akayisan, a wannan karon kodai za'a canja likita ne? Dan dole dole akwai abinda yake a ɓoye. Yarinyar nan itace ta goma sha biyar da aka rasa, kisan kuma iri ɗaya babu wani bambanci sai kace abun tsafi”. “Haba haba wane irin kuma tsafi? Jasim Akh. Dole dai akwai abinda bamu sani ba ɗin kam gaskiya”. “Zancena nakan hanya Ukhti Ammarah. Idan ba aikin tsafi ba mi zamu kira wannan al'amarin ne? Bagashi ita waccan da yake ta gagara ko kuma wani abu daban ta tsira babu abinda ya sameta ko ciwon kai ba”. “Inaga yanzu duk ba lokacin yin wannan maganar bane, ayi abinda ya dace, a wannan karon kuma ya kamata Abni yace wani abu bawai ya cigaba da yin shiru ba kamar yanda ya saba”. “Maganarka nakan hanya Miran Arshaan”. Miran Jasim ya faɗa cikin son sake tabbatar wa. Shiru Daneen Ammarah da Malikat Bushirat basu tanka ba, hakama jami'in yanata cigaba da zagaye ɗakin alamar nazari.. duk wannan al'amari Iffah na maƙure a maɓoyarta tana sauraren komai hannunta danne kan bakinta kar kukan da take ya fito har su farga da ita. Koda suka gama abinda suke bayan shigowar doctor da fitar da gawar kasa fitowa tai, sai dai ta zame ƙasa da sake fashewa da wani irin kuka mai ban tausayin dan mutuwar yayunta biyu ta dawo mata ne a rai sabu a yau ganin ta hanyar da suma suka rasasu a zahiri gabanta...... “Kuka bashi zai kuɓutar dake ba kema...” A razane Iffah ta buɗe idanunta dake kaca-kaca da hawaye gasu jajur. Miran Jasim da tun ɗazun ya lura da ƙafar Iffah amma ya basar har sai da suka fice yayo sau da baya ne a gabanta. Duk da so ɗaya ta taɓa ganinsa ranar liyafar cin abinci da aka kawota nan hakan baisa ta shaida fuskarba a ɗan fisge. Kai ya jinjina mata cikin ɗage kafaɗu “Yanda ya kashe na baya kema babu tantama hakance zata kasance. Karki ga ya ƙyaleki zata iya yuwuwa shirinki na musamman ne. Amma in har kin shirya kuɓuta daga tarkon sa ni mai iya taimaka miki ne”. Iffah dai kallonsa take kamar gunkiya, sai hawayen da suka kasa tsaya mata ne kawai ke tabbatar da ita a mai numfashi. Bai nuna ya damu da yanayin nata ba ya cigaba da faɗin. “Ni sunana Jasim Ibn Abdull-Majeed Aliy. Ƙani ga mahaifin mijikin kenan. Nasan kina buƙatar sanin abubuwa masu yawa akansa amma kinƙi samun kowacce irin dama saboda iyayensa dake zagaye da ke. Duk yanda kike zaton abin ko tsammani ya wuce nan, Malikat Haseena da Malikat Bushirat da kike gani sun san komai game da mutuwar matansa, hasalima da taimakonsu komai ke gudana, zaki iya lura da hakan a yanzu ta yanda duk muka nuna damuwa amma su ko'a jikinsu. Abinda zai tabbatar miki da sun sani kuwa duba da abinda kika ganema idonki ne, taya za'a kashe mutum amma a kasa gane hakan, sannan kuma a sake kawo masa gobe ta mutu hakan baisa an dakata ba. Waɗan nan likitoci da jami'an da kike gani duk an siyesu ne, shiyyasa suke pretending cewar basu san komai ba ko basu gane komai ba. Koda yake su a zahiri bazasuga komai ɗin ba, dan ana kashesu ne ta hanyar tsafi domin ƙarama ƙarfin mulkinsa iko.....” yaja numfashi tare da fesarwa idonsa a kanta yana nazartar yanayin tasirin da maganarsa ke samu a wajenta. Da alama akwai nasara dan haka ya cigaba da faɗin, “Mu ajiye wannan, dan bashi da amfanin cigaba da faɗa miki. Ko kin san mahaifinki da ɗan uwanki ma anyi amfani da jininsu a maimakon naki shiyyasa ke kika tsira saɓanin wannan”. Zabura Iffah tai jikinta na rawa. Sai dai ta kasa faɗin abinda ke son fita a bakinta. Ya ɗaga mata hannu da faɗin, “Kinga kwantar da hankalinki, amshi wannan ki kalla. Idan kin kammala sai ki yankema zancena hukunci. Amma ki sani tabbas ta hanyar da aka halaka iyayen nan naki da ita ake bi wajen halaka waɗan nan matan nasa shiyyasa likitoci basa gane komai na barki lafiya..” Harya ɓacema ganinta Iffah bata iya ta motsa ba, sai dai rawar jikinta da karkarwa a bayyane take. Jin kamar motsin mutane ya sata ɗaukar flash ɗin daya ajiye mata ta sake ɓoye wa. Jami'in ɗazunne ya dawo ɗakin, a wannan karon sun ɗauka hotunan komai a ɗakin da ɗan sake bibbincikawa dan tare yake da yara biyu jami'ai suma. Dole Iffah ta sake lafewa har suka fice sannan itama ta fito. ★ A yanzu kam masarautar a harmutse take fiye da ɗazun, hakan ya sake bama Iffah damar komawa sashenta cikin matuƙar tashin hankalin abinda ya faru da zantukan wannan mutumi. Kulle kanta tai a ɗaku ido rufe ta saka flash ɗin a jikin laptop ɗinta da bawani amfani dake da shi ba. Abin tamkar wani film video ya fara da shigar Babiy riƙe da Abu Moosa cikin gidansu a waccan ranar, shimfiɗa tabarmar Ummu da bayanin Abu Moosa da bai kammala ba har mutuwarsa. Zuwan matar Abu Moosa da jami'an tsaro abinda Hanash yay mata da tafiya dasu. Daga nan ya yanke. Da sauri tai playing na gaba. A yanzu kam su Babiy ne a mawuyacin hali duk sun rame sunyi baƙi a cikin wani ɗaki. Kan Babiy a saman cinyar Hanash alamar babu lafiya tare da shi, Hanash nata faman shafa masa ruwa a fuska yana kuka. Sautin dariya ne ya fara tashi a ɗakin, kafin shigowar wani mutum da iya jikinsa kawai ake gani babu fuska. A take su Hanash suka zabura yayinda sautin dariya ke tashi da tafa hannayen mutumin. Bayan anyi dariyar mai tsawo aka tsagaita, ƙirjinta yay wata irin bugawa jin muryar Shahan-shan. “A tunaninku bayan samun tagomashi a jinin yaronku ƴan baiwa zan haƙura ne. Ina bazai yuwuba, dan a kaf yaran dana halaka jinin ƴaƴankune na farko daya bani fiye da nasarar da nake buƙata, shiyyasa na fara bibiyar ta uku daku kanku saboda bincikena ya nuna min daga jinin ubansu ne”. Hhhhhhh! Hhhhh!! Kune nasarata ahalin Zayyan. Kune nasarata dole ne kuma na samu hhhhhhh!!!”. Kuka Hanash keyi da roƙonsa amma babu alamar zai sauraresa. Sai ma wani irin salon siddabaru da yakeyi da hanunsa a take ɗakin ya turniƙe da hayaƙi, sai kuma wata irin guguwa mai ƙarfi ta nannaɗe hayaƙin a tsakkiyar ɗakin. Su Babiy dai tuni sun maƙure a bango. Sai kuma suka shiga ihu ganin guguwar ta zama wani irin maciji daya kusa cinye kashi ɗaya bisa ukun ɗakin, sara ya fara kaima su Babiy da suka dunƙule waje ɗaya shi da Hanash, kafin macijin ya kafa kansa a wuyar Hanash dake ƙanƙama Babiy. Tuni duhu ya gama mamaye jikin Iffah dake karkarwa, ta rufe laptop dan zuwa yanzu ma kukan ya kafe ƙaf a idanunta. Sai wani irin mahaukacin ja da sukayi kai kace wuta aka haɗa a cikinsu. Tun tana iya jin surutan masarautar har ta daina jin komai. Daga haka sai farkawa tai ta ganta a gadon asibiti Daneen Ammarah tare da ita.. Gaba ɗaya ta tsani komai daya shafi Tajwar Eshaan. Dan haka tun buɗe idon farko da tai ta ga wadda ke tare da ita bata sake yarda ta buɗe ba. Hakan yasa Daneen Ammarah bata san ta farka ba. Dama itama kuma tayi matuƙar nisa ne a cikin tunani a kallo ɗaya ma zaka fahimci bata tare da nutsuwarta. Ga wata ƴar rama ta yini ɗaya sakamakon tashin hankalin da ake ciki tattare da ita. Dan tun kai gawar Zawjata-almilk da Sayeed Khairul-Bashar makwanci ba daular ruman kawai ba gaba ɗaya ƙasar ruman a harmutse take. Yau wasu a cikin talakawa sunyi ƙarfin halin fitowa zanga-zanga a wasu jahohin suna kiranyen Shahan-shan ya sauka ko su ɗauka doka a hanunsu. Fitsari daya takura Iffah ne ya tilastata tashi har Daneen Ammarah ta farga. Da sauri takai hannu ta riƙota tana mata sannu, dauriya kawai Iffah tai na dannewa dan tunanin datai a ɗan farkawar nan Tata zuciyarta ta bata shawarar ɓoye sirrin ranta domin samun cikar burinta. Dan tayi alkawarin a wannan karon sai ta halaka Shahan-shan, ta riga ta ƙuna bata tsoron mutuwa. In har burinta ya cika danta mutu ba komai bane a gareta a yanzu ma tafi buƙatar mutuwar fiye da rayuwa tunda har ta rasa sauran ahalinta kuma miya rage mata. “Ya akai na zo nan Mamy?”. Ta faɗa cikin danne komai dake ɓoye a ranta. Daneen Ammarah da farin cikin farkawar Iffah ya sata sakin murmushi yaƙe da ita kuma Iffah ta fassara da wani abu daban ta amsa mata da faɗin, “Sakamakon abinda muke tunanin ya rikeki aka sameki a sume shine aka kawoki asibiti, amma Alhamdullah tunda gaki kin farka”. Maimakon ta amsa mata wannan zancen sai ta jefa mata tambaya. “Mamy da gaske ta mutu ko?”. Take idanun Daneen Ammarah suka cika da hawaye. Cikin ɗaci tace, “Sun kasheta Ibnati, sun sami damar da suke buƙata akansa. Gaba ɗaya ƙasa ta harmutse da bore akansa kamar yanda dama suke son cimma buri”. Iffah ta ɗan lumshe ido ta buɗe zuciyarta na karajin tsanar Daneen Ammarah ɗin da mamakin salon yaudararsu, amma a zahiri sai itama ta marairaice fuska. “Mamy ban fahimta ba?”. Hawaye Daneen Ammarah ta share, “Ibnati a yau ruman baki ɗaya a harmutse take, talakawa nata zanga-zanga a wasu jahohin akan sai Abni yayi murabus a kujerar Shahan-shan inba hakaba zasu ɗauki mataki. Gashi tunda abin nan ya faru babu wanda yaga idonsa ya kulle kansa a ɗaki anyi-anyi ya buɗe yaƙi”. Iffah ta rumtse idanu da karfi tana taune lips ɗinta, yayinda take faɗi a zuciyarta da kakkausar murya. (Ni zan ƙarasa musu aikin da kawo musu ƙarshen matsalarsu. Dan ba murabus kawai ya cancanci yi ba mutuwa gaba ɗaya yabar duniyar ya cancanta da shi ba kujerar Shahan-shan da ƙasar ruman kawai ba)..........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_45_* ........Daneen Ammarah dake tunanin yanayin ma Iffah tashin hankaline kawai sai ta shiga rarrashinta. Dole Iffah ta cigaba da pretending da matsawa a sallameta taji sauƙi. Daneen Ammarah na rakata sashen ta wuce dan jikin Malikat Haseena ma dai babu daɗi sam. Dama Daneen Ammarah ɗin ta zauna da Iffah ne domin saka ido kar wani ya cuta mata itama. Hakan yama Iffah daɗi, dan ya bata damar nutsuwa a kallon videon data ɗauka ɗazun. Sosai tai zooming gawar Zawjata-almilk tana kai bin jikinta ta inda yake a waje daki-daki. Wata irin zabura tai ganin abinda take ma ɗin kuwa a saitin wuyan gawar ta gefen kunenta na haggu. Wato alamar ɗigon sarin maciji har biyu. Innalillahi wa inna'ilaihirraji'un take ambata wata irin zufan na keto mata, dan kuwa tabbas zancen mutumin can ya zama gaskiya. Amma duk da haka tana buƙatar sake tabbatar wa. Cikin rawar da jikinta ke mata ta shiga laluben number ɗin Sir Fawzan. Bugu ɗaya kuwa ya amsa kasancewar dama a jirace yake da kiran, dan ya nemeta amma bai samu ba. Yaci kuka har ya godema ALLAH dan zatonsa ma ita suka rasa. Cikin rawar murya ya ambaci sunanta duk da yaji muryarta. Amsawa tai da kuka, bata jira cewarsa ba tace, “Sir kaji tsoron ALLAH ka sanarmin gaskiya akan iyayena. Na rokeka karka ɓoyemun komai”. Zufa ce ta shiga karyo masa tako ina, dan baiyi tunanin jin wannan tambayar bazatanba a bakinta. Shirunsa ya sake tada hankalin Iffah, ta cigaba da masa magiyar da dole ya faɗa mata gaskiyar data buƙata. “Tabbas na ɓoye miki Iffah, amma tun bayan barinki gida baifi da kwanaki ba aka rasa ɗan uwanki da Babiy sakamakon......” Ya zayyane mata labari tiryan-tiryan kamar yanda ya bincika. Babu kuma banbanci da abinda ta gani a wancan video ɗin na farko. Ya kare da faɗin, “Wlhy har yanzu akan binciken inda aka kaisu ake amma babu labarinsu. Nima kuma a yanzu haka ina yin nawa ta ƙarƙashin ƙasa amma har yanzu ban samu wani bakin zaren ba....” Kukan data fashe masa da shi ne ya katsesa daga jawabin nasa. “Ba zaku gansu ba, ba zamu ƙara ganinsu ba, sun rabani da su kamar yanda suka rabamu da ƴan uwana. Wlhy nima sai na kasheshi kamar yanda ya kashesu. Na rantse bazan barsa ba, bazan taɓa barinsa ba. Yanda ya halakasu da macijin tsafi sai na halakashi da dafin maciji na gaskiya. Shima sai ya ɗanɗa......” kuka ya sarƙeta ta kasa cigaba da magana... Cikin tashin hankali daga can Sir Fawzan ke faɗin, “Iffah ban gane ba. Dan ALLAH ki daina kuka kimun bayani, kaina ya kulle dan ALLAH kiyi shiru kinji, wlhy na miki alkawarin taimaka miki akan koma minene, koda kuwa nima zan rasa rayuwata ne.....”. “Babu wannan lokacin sir, bani da shi. Kai dai kawai ina zan samu dafin maciji mai haɗarin gaske?”. “Ya ALLAHU! dan ALLAH ki faɗamin mike faruwa? a yanda zan fahimceki”. “Idan bazaka samamin abinda nake buƙata ba na Barka lafiya”. Yana hello-hello bata sauraresa ba ta yanke wayar, koda ya sake kira bata ɗauka ba, da taga zai dameta ma sai ta jefa shi a black list. Kaikawo ta cigaba dayi a ɗakin tana kuka. Komai ya cakuɗe mata, zuciyarta ta gama ƙeƙashewa da bushewa. Ta sallama duk wani ɗan sauran rangwamenta. Abinda kawai idonta da zuciyarta ke gani gawa huɗu ta ahalinta kwance duk a dalilin mutum ɗaya tak, lokaci yayi da zatai abinda ya kawota itama dan bai cancanci cigaba da rayuwa ba mutumin nan sam, tayi alkawarin tare zasu mutu, amma sai ta kasheshi ta kuma bayyanama duniya wanene shi. Yanda taci kuka ta fita hayyacinta dole ta bama duk wani tausayi, da ƙyar ta iya zaman rubuta komai da ya rage, ta tattare ga Ajmaal, a ganinta ta gama tattare dukan abinda ya dace ta tattare masa. Hatta ƙudirinta na kawar da Shahan-shan ta hanyar dafin maciji bata ɓoye masa ba. Ta kwashe videos ɗin dake wayar zuwa wayarta ta turama Ajmaal ɗin, takumayi gajeren video da kalaman masu girgiza zuciya har biyu. Ɗaya na Ummu da su Kaka ta roƙa ya bamawa, ɗaya kuma na al'ummar ƙasar ruman ne baki ɗaya. Shima tai masa godiya da fatan alheri da nasara har ƙarshen rayuwa....... ★★..... BARRISTER ★★..... Barrister dake jin kamar ya ƙwaɗa wayar da ƙasa ya rumtseta a hannunsa da masifar ƙarfi, a karo na farko wasu zafafan hawaye suke silalo masa. Jarumar zuciyarsa zugasa take kada ya yarda ya amince koda zai rasa rayuwarsa, yayinda wani ɓangaren kuma ke haska masa iyalansa da yafi so fiye da komai a duniya a halin yanzun. Wannan shine tashin hankalin mafi ƙololuwar girma daya taɓa cin karo da shi a rayuwarsa.... Washe gari da safe wujiga-wujiga ya wayi gari, amma hakan bai saka ko gezau ga mutanen ba. Sai ma duk wani details daya shafi case ɗin da suka dire masa. Mamaki da tsoronsu ya sake mamayesa ganin duk wani abinda ke hannunsa ne. Kuma ya adanasu ne a mabanbanta wajeje. Akwai wanda a gidansa suke, akwai wanda a office suke, akwai na mota ma. Amma abin mamaki gasu duk a gabansa sun tattaro sun kawo masa. Tabbas ya sadaƙar, dan mutanen nan hatsabibaine na innanaha. In har zasu iya hakan a kankanin lokaci bayaji idan ya bijire musu iyalansa zasu tsira kuwa.... “Barrister baka da lokacin dogon tunani, ka shirya dan a yau oga ke son ka tattaro masa duk bayanin da yake buƙata a wajen mutanen can. Ciki har da sanin su wanene ainahin masu aikin, da inda suka ɓoye Abu Hanash da ɗansa”. Karan farko Barrister ya dubeshi a razane, har ƙoƙarin taune harshe yake wajen faɗin, “Kana nufin dama baku bane ke riƙe da su Abu Hanash ɗin...?” Saurayin yay ɗan waige-waige alamar baya son wani yaji, cikin raɗa-raɗa yace, “Bamu bane Barrister. Muma kuɓutar da su muke son yi har ma da kai kanka. Sai dai ban san miyasa oga bai son ka sani ba ya zaɓi baka aikin a kife”. Ba ƙaramin zabura Barrister yay ba jikinsa har rawa yake ya matsa gab da saurayin. “Dan ALLAH kada ka yaudareni ka faɗa min gaskiya”. Da sauri saurayin ke masa nuni da yay ƙasa da murya kar wani yaji, “Barrister wlhy kaji na rantse maka abinda na faɗa maka shine gaskiya. Na kuma sanar maka ne saboda ka bani tausayi. Amma iyalanka kansu suna zagaye da tsaro ta yanda wani bazai taɓa iya samun damar cutar da su ba, kai kanka kusan sati uku fa muna tare da kai batare daka sani ba. Oga ba azzalumi bane ba, amma ban san miyasa bai son kasan taimakonku zaiyi ba. ya kamata kaima ai ka gane hakan tun farko musamman aikin daya baka ɗin, taya wanda zai cutar da kai zai kuɓutar da kai?, taya wanda zai cutar da kai zai ɗauraka akan hanyar abinda kake nema ya baka bakin zarensa haka cikin sauƙi?”. “Hakane wlhy ɗan uwa hakane. Kaina ne ya kulle a ruɗani nake gaba ɗaya. Nagode nagode yanzu kam ka bani ƙwarin gwiwa, insha ALLAHU kuma sai na bada mamaki. Dan a wannan gaɓar sai su Abu Hanash sun fita da izinin UBANGIJI, zan kuma gano koma wanene da hannu a kan ɓoyesu”. “ALLAH ya baka nasara. Ni bara naje kar wani ya fahimci ina anan har yanzu”. Kai kawai Barrister ya ɗaga masa yana murmushi. Wannan tattaunawa ce ta bama Barrister duk wani ƙarfi da sabuwar himma na musamman, a yanzu kama baka iya ganin komai sai murmushi tare da shi, lokacin da aka kawo masa abincin rana ya buƙaci takarda da abin rubutu. Takardu aka kawo masa bama takarda ba, hakan ko ya masa daɗi, dan ya kwashe sauran wannan yinin da dare wajen tsara duk abinda ya dace. Washe gari har ya fisu zumuɗin son fita ma, sauran da basu san miya faru ba canjawar Barrister ɗin taita basu mamaki..... ★★... KAUYEN JUMNA ★★.... Tun kammala bayanin Abu Zainab ga su Kaka jikkunansu duk yay sanyi, Ummu ma hawaye takeyi, Barrister shine hope ɗin su a yanzu bayan UBANGIJI masanin abinda ke fili da ɓoye. Gashi a dalilinsu an rasashi. Idan har aka cutar da shi ta dalilinsu bazasu yafema kawunansu ba. Kaka dai jinjina kai kawai yake amma komai ya kasa cewa, sai Iyyani ce cikin ƙarfin hali da sharar ƙwalla ta dubi Abu Zainab da damuwa ke shimfiɗe a fuskarsa. “Zakariyya kuyi haƙuri dan ALLAH, mun jefa rayuwarku a haɗari, ya ALLAH ka bayyana Abdullahi da gaggawa”. Ɗan murmushin yaƙe Abu Zainab yayi, cikin danne abinda ke masa kaikawo yace, “A'a mama ai mutum baya taɓa wuce ƙaddararsa, kuma har yanzu bamu tabbatar ba ko akan wannan case ɗin bane muka rasa shin, dan Barrister da kike ganinsa nan shima hatsabibin kansa ne, gaskiyarsa da tsayuwa akan ganin tabbatar da ita yasa yanada maƙiya da yawa akan cases daban-daban hatta a cikin abokan aikinsa ma. Kinga kuwa zama ta iya yiwuwa ba'akan wannan ɗin bane.....” “Dole ya zama akan wannan ne” Kaka ya faɗa cikin katse Abu Zainab. Duk kallonsu suka maida a kansa. Ya jinjina kai batare da ya kallesu ba. “Ban san gaibu ba, amma inaji a jikina akan su Muhammad Zayyanu ne, sai dai kuma tabbas koma a ina yake har yanzu yana raye insha ALLAHU. Inajin wannan ƙwarin gwiwar ne a zuciyata”. Ba ƙaramin mamaki kalaman kakan suka basu ba, sai dai kowa ya gagara cewa komai sun dai zuba masa ido. Kusan mintuna biyu gidan shiru kafin kaka ya miƙe, babu jimawa ya dawo da jakka a hanunsa. Su dai duk suna kallonsa kawai. Takardar daya zaro ya miƙama Abu Zainab. “Ungo duba wannan”. Da sauri Abu Zainab ya amsa ya fara karantawa. Bakinsa cike da magana ya ɗago yana duban kaka da ke kallonsa. “Baba wannan kuma fa?”. Murmushi Kaka yayi da kauda kansa kamar bazaice komai ba. Sai kuma ya ɗan taɓe baki da fara basu labarin yanda duk a kai a randa zai dawo. Ya ɗora da faɗin, “Saurayin daya kawoni gidan nan zuciyata ta bani ba haka nan ya kawoni ba....” “Amma baba shine ka amince harma da nuna masa gida?”. Kaka yay ƴar dariyarsu ta manya. “Zakariyya kenan, to idan baka iya kama ɓarawo ba ai shi sai ya kamaka. Ka ganni nan barni kawai inda ka ganni. Idan na nuna nasan yanada manufa a kaina tun farko kamar yanda naso nuna masa a tasha ai bazan san sirrin zuciyarsa ba. Amma dana bashi dama fa? Yanzu a tafin hannuna yake, kuma jirace nake da zuwansa dan na tabbatar zai dawo, na masa talalar da tabbas sai ya dawo da izinin UBANGIJI”. Abu Zainab kam a yau Kaka ya fara bashi tsoro. Sai dai ya danne bai yarda ya nuna ba. Kaka ma ya fahimci haka amma ya kanne, sai jakkar ya tura ma Abu Zainab yana faɗin, “Wannan sune kuɗin dake tare da takardar”. Nan ma dai da mamaki Abu Zainab ke kallon kuɗin, kuɗine masu yawa sabbi ƙal sai ƙamshi suke na sabunta. “Baba waɗan nan mutanen kuwa anya....” Kaka yay murmushi mai bayyana haƙora. Sai kuma ya ɗan kalli sashen da Ummu ke zaune. Tuni ta tashi batare da sun farga ba har Iyyani..........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_46_* ..........Lokacin da kaka yayi ma Abu Zainab rakkiya sukejin halin da ƙasar ke ciki, dan shima Abu Zainab kasancewar fitowar sassafe yayi sannan komai bai fasu ba. Hankalinsu yayi matuƙar tashi dan basu san wacece a cikin matan sarkin ta rasu ba. “Zakariyya zama bai ganni ba, dole ne mu wuce tare kenan, kayi haƙuri kaɗan jirani anan ina zuwa”. Kaka bai jira cewar Abu Zainab ba ya koma gida da sauri, koda su Iyyani sukaga a yanayin da ya shigo suma hankalinsu ya tashi, amma tambayar duniya yaƙi ce musu komai kan abinda ya farun, sai cemusu da yay shima zaije Daular ruman ne.”. jin wannan furucin nasa yasa jikin Ummu fara rawa, a hankali ta zube ƙasa dan zuciyarta ta gama bata kodai ta rasa Iffah ko su Babiy. Dama yau kusan gabbanin asuba tayi mafarkin Iffah na kuka da kiranta tazo ta ceceta, sai kawai ma zuciyarta tafi karkata akan Uffan.. Su Kaka sun iso daular ruman a harmutse, dan ƴan zanga-zanga nata da ɗa karuwa harma abin na bama mutane mamaki. Yayinda jami'an tsaro tuni sun fito ta kowane titi na masarauta sun tare. Da ƙyar suka samu ƙarasawa gida, kasancewar ana aikowa gidan domin halartar jana'iza yasa Kaka yay tunanin wannan ma indai Iffahr ce zasu aiko. Dan haka suka shiga tambayar ƴan anguwa amma kowa na tabbatar musu babu wanda yazo. Hankalin Kaka ya tashi fiye da farko, dan kuwa dai bayan wannan hanyar babu wata mai sauƙi da zai iya ji sai abokinsa dogon yaro da ke cikin masarauta. A yanda kuma garin yake hakan abune mai wahala a garesa kenan...... ★ BARRISTER ★ Yanayin da aka wayi gari a ƙasar bai hana su Barrister fitowa ba, sai ma lokacin shi yasan abinda ke faruwar, al'amarin ya taɓa masa zuciya, dan ta wani fannin case ɗinsa tamkar kacokal yanada alaƙa mai ƙarfi ne da abinda ke faruwar. Har yaji yana tsoron ace yarinyar ce ma ta rasa ran nata. Dan dole dai ya daure ya isa inda ya nufa. A yau dai bai samu Sayyid Faizul-Anwar a falon ba, sai dai kasancewar an san da zuwansa ya samu tarbar data dace. Bayan zaman kusan mintuna arba'in Sayeed ya fito cikin shigar jallabiya, cikin girmamawa Barrister ya gaidashi, ya amsa masa da kulawa shima yana masa barka da zuwa. Suna tsaka da gaisuwar cikin yaran Sayeed ya shigo ya isar da saƙon zuwan wasu baƙin. Damar shigo da su ya bada dan yasan da zuwansu, daga haka ya maida hankalinsa kan Barrister. Barrister yayi matuƙar mamakin ganin baƙin, sai dai ya danne hakan dalilin kallon da suke masa matsayin Barrister Akeem. Gaisuwa sukai ta mutunta juna, har suna tsokanarsa da cewa shine idonsu na gari. Murmushi yayi yana rissinar da kai alamar girmamawa. “Kar kuji komai ranka ya daɗe, a komai muna tare da ku kuma zamu kare mutuncin ku”. Sosai suka nuna jin daɗi da zancensa. Nan suka shiga kwarzantashi. Shi dai nasa murmushi ne a zahiri, a kasan rai kuma yana matuƙar mamakin abokinsa da ɓoyayyun ayyukansa. Dan bai taɓa tunanin Barrister Akeem zai iya irin waɗan nan ayyuka ba..... “Barriter ina alkawarin mu?”. Sayeed Faizul-Anwar ya katse masa tunani. Ajiyar zuciya yaja a ɓoye, sai kuma ya muskuta yana murmushi da taɓa bag ɗin daya shigo da ita. “Ranka ya daɗe komai yazo hannu fiye ma da yanda kuke buƙata. Sai dai kafin mukai ga nan ina son nace wani abu saboda wasu dalilai”. “Faɗi kanka tsaye Barrister baka da damuwa akan hakan”. “Nagode ranka ya daɗe. Bawani abu bane mai girma akan dai shi wannan case ɗinne. Komai dai gashi na gani anan kuma na tattaro, sai dai yanda aka bani aikin a dunƙule ina ganin ya kamata nace wani abu duk da dai naga komai a kansa, amma saboda nasan inda duk ya kamata na toshe a ramukan da zasu iya yunƙurin buɗewa koma su buɗe ɗin yasa nake son bada shawara bisa wani hangena”. Shiru kamar bazasu ce komaiba. Sai dai sun maida dubansu ga Sayeed Faizul-Anwar, kai ya gyaɗa musu alamar tabbatar da babu matsala, dan haka kusan a tare suka sauke numfashi, kafin ɗaya a ciki ya shiga faɗin. “Barrister mun yarda da kai, sai dai ka sani koda baka san komai akan case ɗin nan ba bazamu taɓa bari wani rami a buɗe mana ba koya buɗe maka, zamu kasance a bayanka a kowanne lungu da saƙo na ƙasar nan.” “Nagode da wannan karamci”. Barrister ya faɗa da girmamawa. “Baka da damuwa Barrister ka cancanta ne.” Murmushi ya sake saki tare da mikewa ya kai jakar gabansu, cike da farin ciki suka buɗe suna mai fiddo duk takardun ciki. Bayan sun ɗan dudduba su suka ɗago fuskoki cike da murmushi suna yabama Barrister namijin ƙoƙarin sa. Shi dai nashi murmushi ne kawai. Ɗaya daga cikin baƙin da ake kira da Sayeed Harun Al-rashid, babban mutum ne a ƙasar ta ruman, dan riƙƙaƙen ɗan kasuwa ne na gwal da kowa ya sani kasancewar sunansa yayi matuƙar shura a wannan harkar data zama babban tattalin arzikin su na ƙasar, dan Ruman kam bata san iya arziƙin gwal da ALLAH yay mata ba, shiyyasa duk wani riƙƙaƙen ɗan kasuwa zaka samu gwal ɗin ne mafi rinjayen makaminsa kamar dai Sayeed Harun Al-rashid. Ta wani gefen kuma yana riƙe da sarauta sai dai yafi bama kasuwancin muhimmanci matuƙa. Zamansa ya gyara sosai yana fuskantar Barrister. “Barrister yanzu mi kake son ka sani?”. “Ranka ya daɗe ba komai bane dama sai akan waɗan da naga case ɗin ya karkata. Na duba dukkan bayanan Barrister Abdallah Aas, sai dai a yanda na fahimta kamar ya gano inda su mutanen dake hannun naku suke, dan kafin ma ya rasa ransa kamar ya fito da ga ƙauyen Lufana ne wajen matar marigayin, abinda nake son cewa anan ina tsoron yazam bayan Barrister ɗin akwai wanda yasan wannan sirrin. In kuwa hakan ta kasance zaman mutanen a station ɗin dana fahimci kun ɓoyesu zai zama barazana ke nan koda anan gaba”. Kusan a tare sukai murmushi, Sayeed Harun Al-rashid ya muskuta zamansa cikin nuna damuwa da zancen Barrister. “Maganar ka nakan hanya Barrister shiyyasa tun kafin yau muka gama maganin duk abinda kake gudun. Tun daga farkon wannan case ɗin idanunmu akan komai suke, dan haka ka kwantar da hankalinka. Su kuma tuni basa a police station ɗin, dama mun kai ajiyar su ne domin ɓadda kama bayan kwanaki kuma muka ɗauke su, amma kai a yanzu mi kake son cewa?”. Anzo dai-dai gaɓar da Barrister keson azo, dan haka ya ɗan murmusa yana mai ƙara bama kansa nutsuwa. “Alhmdullh kun fahimci inda nake buƙatar akai ranka ya daɗe. Abinda nake son cewa kai tsaye shine ayi duk yanda za'ai cikin kwanaki biyun nan abar ƙasar ruman da mutanen gaba ɗaya”. “Eh maganarka abin dubawa ce kam, amma kuma mizai hana kawai a ɓaddasu a wuce wajen, dan abinda ya zama dalilin zuwansu hanunmun ma an sameshi cikin sauƙi yanzu haka”. Barrister yay ɗan jimm dan bai fahimta ba, amma sai ya dake bai sake musu wata tambaya ba gudun karsu zargi wani abu. Sai dai ya cigaba da faɗin, “Ɓaddasu bashine mafitaba ranka ya daɗe, dan a ɗan bincike da nayifa akwai babbar matsala game da mutuwar Barrister Aas”. Babu wanda zancen bai daka ba a acikinsu, Sayeed Faizul-Anwar daya kafe Barrister da ido yay saurin faɗin, “Barrister bamu fahimce ka ba, mi kake son cewa?” “Ranka ya daɗe yanzu zan fahimtar da ku. Idan har kun saurari dukkan labaran dake yawo har yanzu babu wani tabbaci na samun alamar sassan mutum a cikin motar Abdallah, wannan shine yaja hankalina tun a ranar farko bayan nabar nan na fara nazari da bincike. Tabbas Abdallah na raye, sai dai ya ɓoye kansa domin bada ƙafa. Na sanshi nasan mizai iya fiye da tunaninku. Shiyyasa nake ganin kashe mutanen a yanzu bashine mafita ba, muyi nesa da su da ƙasar nan ta yanda babu inda zasuji ɗuriyarmu, sai kuma mu samo wasu a madadinsu a buɗe shari'ar ta yanda zamu ƙona Barrister Abdallah Aas da ransa batare daya farga ba”. Dukansu gumi suke na tashin hanakali, sai dai babu wanda ya iya cewa komai har zuwa wani tsahon lokaci. Sayeed Harun Al-rashid ya nisa yana mai share ɗan gumin daya taru masa a goshi. Ƙyaƙyƙyawar fuskarsa fara tas gaba ɗaya ta ƙwaɓe alamar rashin damuwa. “Zartar da hukunci bazai yuwu yanzu ba Barrister, amma kaje zuwa anjima zakaji komai ta waya”. “Babu damuwa ranka ya daɗe”. Barrister ya faɗa cikin jimami shima, sai dai acan ƙasan ransa dariya yakeyi, yayinda wani gefe na zuciyarsa ke tabbatar masa akwai wani babba mai alaƙa da case ɗin bayan su, shiyyasa bazasu iya zartar da hukuncin ba kai tsaye. Yau ma dai an rakosa da kuɗi masu yawa har mota....... ★★... BAYAN KWANA BIYU ★★.... A kwanaki biyun nan abubuwa da yawa sun faru tako wane ɓangare, sai dai marasa daɗi sunfi masu daɗin rinjaye. Zuwa yanzu dai da gaske ƙasar ruman da jama'arta suke basa buƙatar Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed matsayin Shahan-shan. Dan tun tsirarun mutane na zanga-zanga a wasu jahohi takai yanzu ƙasar ma gaba ɗaya ta ɗauka. Abu mafi ban mamaki harda wasu a manyan ƙasar na nuna goyon baya ga talakawa, ciki kuwa harda wasu Tajwar na jihohi. Yayinda ta wani gefen kuma hankalin wasu manyan ƙasashen duniya ya fara dawowa kan zanga-zangar dama dalilin yinta. Babban abinda ke tunzura jama'a shine biris daga Shahan-shan, yayinda kuma a cikin gida hankalin ƴan majalissar sa ya rabu kaso biyu, wasu na goyen bayan ya saukan wasu na buƙatar karya sauka dan shine kawai ya cancanta da kujerar a ganinsu. A talakawan ma bai rasa tsirarun masoya ba, sai dai basu da ƙarfin ja da masu boren shiyyasa suka koma gefe sukai shiru matsayin masu kallo da ido. *_IFFAH!_* A kwanaki biyun nan yanda Daular ruman ke a hargitse haka Iffah ke a hargitse. Kuka kam idanunta har sun daina fidda ruwan hawaye. Cikin ƙanƙanin lokaci tayi wata irin rama mai ban tausayi. Haukan da iyalan Sayeed Khairul-Bashar keyi a masarautar da wanda jama'a keyi a waje sai ta ɗaukesa wasan yara. Idan su da suka rasa uba kawai zasu harmutsa masarautar haka ina ga ita data rasa ahalinta duka, a ganinta ita ya cancanci ta hargitse ƙasar ruman baki ɗaya ma ai. Sai dai yanda ƴan zanga-zanga ke daɗa ƙaruwa na saka mata farin ciki, dan abin ban mamaki har wasu a cikin Tajwar na jihohi suma sun ƙara tunzura wuta da bada goyon baya akan saukar Shahan-shan ɗin, hankalin ƙasashe kuma ya fara dawowa ƙasar ruman, da alama dai dama a jirace kowa yake da wannan damar. Hakan na sake tunzura ƙwarin gwiwar ƙudirinta. Wutar wannan al'amari na ƙara ruruwane dalilin shirun Tajwar Eshaan. Babu shi babu cewarsa, harma wasu sun fara tunanin anya kuwa yana cikin masarautar ma ko?.... Duk wannan bai damu Iffah ba a yanzu, hankalinta gaba ɗaya ya tattara ne akan ta ina zata samo dafin maciji. Bata da wani amintacce a cikin masarautar, a waje kam sir Fawzan ne kawai, shima kuma zuwa yanzu ta fara shakku akansa saboda tana ganin ya ɓoye mata abinda ya faru da su Babiy ne bisa wata manufa. Idan tace zata fita a sulale daga masarautar taya kuma zata dawo cikinta? Wannan ƙalubalen keta faman mata kaikawo harya gagara samun mafita a kwanaki biyun nan. Tana a bangarenta bata ganin kowa kowa baya ganinta, waɗan da zasu iya ganinta hankalinsu a tashe yake dan kai tsaye su abin ya shafa, shirunsu kuma sai ya bama Iffah damar fassarashi da abinda zuciyarta ta gama tabbatar mata, dan haka itama a yanzu ta haƙƙaƙe bata da lokacinsu. Kamar yanda ta tsara bayan sallar la'asar ta shirya tsaf cikin abaya data amshi jikinta, dan ma ta rame ga idanunta da suka ɗan kuklumburo amalar taci kuka bana wasa ba. Duk da masarautar a harmutse take haka ta keta cikinta hadimanta na take mata baya har sashen marigayi Sayeed Khairul-Bashar. Tayi matuƙar mamakin tarbar data samu dan batai zaton irinta ba, sai dai abinda bata sani ba shine su kallon tausayi suke mata da tabbatar da itama bawai ta tsira bane a hannun azzalumin. Dan malamin duba da matar Sayeed Khairul-Bashar ɗin ta ziyarta tun lokacin daya ɓata kafin aga gawarsa ya tabbatar mata akwai ƙulli mai girma da Shahan-shan keyi game da rayuwar Iffah shiyyasa itama bata mutu ba a sanda aka kaita sashenshi. A ranar bata ɓoyema ƴaƴanta komai akan zancen nan data jiyo ba, sun kuma yi niyyar samun Iffah har sashenta da batun washe gari aka tashi da wannan tashin hankali. Wannan shine dalilinsu na mata tarbar data bata mamaki. Ita kuma kasancewar zuciyarta a kusa take tana musu ta'aziyya tana share hawaye da handkherciff. Sai hakan ya ƙara mata kima a idon iyalansa. Yayinda ƴan uwansu kuma da basu san komai na ke jin zafin ganin Iffahr da fassarashi matsayin leƙen wani asiri dan a yanzu wasu a cikin ahalin masarautar su kuma suna ma Iffah kallon wata ƴar kaɗafin Tajwar Eshaan ce tunda har ta tsira daga kisan gillarsa..........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_47_* .........Kamar yanda Iffah tai tunani labarin zuwanta sashen Sayeed Khairul-Bashar ta'aziyya har ya isa kunnen surukarta dama na jikin Tajwar Eshaan irinsu malikat Haseenat da su Daneen Ammarah. Dan tana fitowa kiran Daneen Ammarah ya shigo wayarta. Bata ɗaga ba, aka kuma sake kira nan ma dai ta share kamar bataji ba. Sai da ta koma sashenta da kusan mintuna goma sannan tai kiran Daneen Ammarah ɗin back. A bugu biyu ta ɗaga, Iffah ta taɓe baki cikin rashin damuwa tai sallama da fara gaishe ta. Da kulawa Daneen Ammarah ta amsa. Iffah na jiran jin ta mata batun fitarta sai Daneen Ammarah ta jeho mata tambayar da bata da alaƙa ma da fitar. “Ibnati na kiraki ne akan Abni, shirunsa na tadamin hankali matuƙa, gashi yana ƙara harzuƙa mutane ƙasa, kinga dai yanda ƙasar nan ke sake rikicewa. Mu dukanmu mun nemesa a waya amma bamata shiga, na fara zargin anya ma yana cikin masarautar nan?”. Murmushin takaici Iffah tayi, amma a zahiri sai ta danne ta fara magana cikin kwantar da murya. “Wannan shine tunani na nima Mamy, sai dai ban san yanda zanyi ba ganin ku manya bakuce komai ba.” “Shirun na dole ne Ibnati, bazaki gane babbar sarƙaƙiyar dake cikin masarautar nan ba ne. Amma tabbas akwai matsala, akwai kuma gagarumin al'amarin dake ɓoye amma yana son bayyana kansa a wannan gaɓar.....” Cikin zumuɗi Iffah tace, “Mamy minene shi dan ALLAH?”. “Humm Fareedah kinyi ƙarama da yawa ba yanzu ba. Ke dai kawai abinda nake so da ke shine ki taimaka ki bincika min idan Abni yana a gidan nan...” “To Mamy, amma dai zaiyi wuya tunda kunce idan yana cikin damuwa kulle kansa yakeyi baya kuma sauraren kowa. Sai nake ganin ni taya zai saurare ni”. Murmushi Daneen Ammarah tayi mai sauti. “Rashin saurarenmu bashi ke nufin kema bazai saurareki ba Ibnati. Ke dai gwada sa'arki mu gani”. Iffah dai ta jita ne kawai, amma sai bata sake musawa ba sukai sallama..... ★★.... ★..... Miran Jasim ya sauke wayar dake a kunnensa bayan gama sauraren abokin wayar tasa, yanda fuskarsa ta canja daga farin cikin dake shimfiɗe a kanta kafin wayar yasa Miran Arshaan sake maida hankalinsa garesa. “Wani abu ya sake faruwa ne?”. “Zai dai faru”. Cewar Miran Jasim ɗin a fusace yana miƙewa. Miran Arshaan da maganar ta dakesa ya miƙe zumbur shima. “Ban gane mi kake son cewa ba Jasim Akh?”. Kamar bazai tanka masa ba sai kuma yaja kakkauran tsaki. “Harun Al-rashid ne dai akan waccan maganar banzar ta ranar, duk yabi ya tashi hankalinsa yana cigaba da damuna nima, tun abin bai tasiri a raina ba har ya fara, wai Barrister da suka bama aikin can kan ɗan iskan can ne ke cigaba da musu bayani dai kan Barrister Abdallah bai mutu ba dai da gaske.” “Wai suna nufin shi ya tabbatar da hakan kenan?”. “Abinda ke cazamun kai kenan, na rasa wane shirme ne kuma hakan? Taya wanda bomb ya tashi da shi ace bai mutu ba?”. “To amma fa kuma maganarsu fa abin a duba ce Jasim Akh. Dan koni naji shakku a randa bomb ɗin nan ya tashi amma jami'an tsaro suka tabbatar babu wani alamar an rasa rai......” “Amma shine kai shiru?!”. Miran Jasim ya katsesa a zafafe. “Mi kake so nayi bayan wanda nayi to? ina son ka tuna tun a ranar na kawo maka wannan zancen amma ka nuna min cewar zata iya yuwuwa ƙarfin tashin nakiyar ya cillashi wani waje ne shiyyasa basu gansa ba. A kuma shekaran jiya da suka kawo maganar na kuma ƙoƙarin maka nuni ka kalli zancensu a shirme”. Shima Miran Arshaan ɗin ya karɓa masa a nasa zafin. Shiru Miran Jasim yayi da dafe kansa yana murza goshinsa dan ya tuna tabbas anyi hakan. Amma wannan aikin na cikin gida da rashin sanin mi Tajwar Eshaan ke ciki ya ɗauke hankalinsa bai nutsu yayi nazari kan batunba kasancewar akwai abubuwa da yawa da bawai yana buɗema Miran Arshaan ɗin bane, kamar yanda shima Miran Arshaan ɗin ba komai yake yarda ya buɗe ma Miran Jasim ɗin ba. Sai dai a yanzu dukansu sun fahimci yin kuskure, dan haka kowanne ya ajiye ɓoyayyar manufarsa suka fuskanci juna. “Ni ina ganin in har an yarda da aikin Barrister ɗin nan shawararsa ba abar yardawa bace. Sannan dole ne fa mu gaggauta ganawa da yarinyar can in ba hakaba aikinmu zai iya buɗewa. Dan idan ya kasance Barrister Aas na raye bazai samu ɗaki bane ya kulle kansa domin hutu kaima ka sani”. Miran Jasim ya gyaɗa kai da faɗin, “Hakane maganarka na kan gaskiya. Yanzu minene abinyi?”. “Abinyi ɗaya ne bama Barrister Akeem damar shigewa gaba kafin kwana biyun nan na cikar aikinmu abar ƙasar nan da mutanen. Bayan ka haye karagar mulki shi kuma shegen duk inda yake zamu nemishi ne ya ɗan-ɗana kuɗarsa”. “Ina sake godema ALLAH da kasancewar ka kusa da ni, dan kana farkar da ni a duk sanda kaina ya shiga duhuwa ɗan uwana”. Murmushi Miran Arshaan ya saki a zahiri, a zuciya kam faɗi yake, (Banza ka gama cusamin ƙayar a rumbu na rufeta da ɗan boto ina daga kwance). Ɗaukar wayar Miran Jasim dai-dai da kammala wayar Iffah da Daneen Ammarah daga can...... ★★..... Tana ajiye wayar wani kiran ya sake shigowa, kamar zata share dan bata san number ɗin ba sai kuma dai ta ɗauka da tunanin ko Sir Ajmaal ne kasancewar a saƙonta na ƙarshe ta roƙesa idan ya gani ya kirata. Daga can aka amsa sallamarta kai tsaye, hakan ya sata Ciro wayar a kunenta ta kalla tamkar mai son gano muryar. Miran Jasim da kamar yana ganinta yay gyaran murya, hakan ya sata sake maida wayar. “Kina magana da Jasim Ibn Abdull-Majeed Aliy”. Kai tsaye Iffah ta ganesa, dan haka ta fara gaidashi da girmamawa. Hakan ya masa daɗi, dan yanda yake amsa mata da kulawa zai baka tabbaci. Shiru ne ya ɗan biyo bayan gaisuwar, kafin ya katsesa da faɗin, “Ibnati inata zaman jiran ji daga gareki amma shiru. Ko baki amince da abinda kika gani bane ba dai?”. Iffah da ke jin an taɓo mata inda ke mata ƙaiƙayi hawaye suka shiga rige-rigen sakko mata. Hannu tasa ta sharesu da ɗan jan hanci. “Ba yarda ne banyiba ranka ya daɗe, kawai dai zuciyata na kaikawo ne na son sanin dalilinka na yin hakan a gareni. Idan ban manta ba kai fa Ammi ne garesa, mizaisa ka zaɓeni sama da shi? A barshi ma zaka iya hakan kasancewar ka mai gaskiya ko ƙyamar abinda yake. Amma miyasa su na baya da aka rasa bakuyi wani yunƙuri ba sai ni a kaina bayan akwai ƴaƴan Tajwar mafi rinjaye a cikin wanda ya halaka?”. (Kaga ibilishiyar yarinya) ya ayyana a zuciyarsa. A zahiri kam sai yay gyaran murya cike da dattako yana kallon Miran Arshaan da shima ke sauraren komai. “Wato Ibnati duk yanda zan miki bayani a wayar nan ba lallai ki fahimta ba. Amma zan tura miki lokaci da adireshi mu haɗu zai fi”. Jimmm Iffah tayi kamar mai shakku, sai kuma ta nisa cikin gyaɗa kai tace, “Okay babu damuwa ina jira”. Daga haka sukai sallama kowa ransa na masa kaikawo... ★★.... Cikin ƴar dariya Miran Arshaan yace, “Amma shegiyar yarinyar nan fa da zata samu dama a masarautar nan ba ƙaramin hatsabibiya za'ai ba. Kaji murya cauy-cauy bata ko tsallaken kalma ga shegen wayo”. “Shiyyasa dolene tana kammala aikin nan a kaudata kawai, ai tunda har tana da ƙarfin halin shigowa masarautar nan da ƙudiri irin na kashe Shahan-shan dama nasan zamuga fiye da hakan tattare da ita. Irin waɗan nan yaran masu taurin zuciya a cikin mata basu da yawa, amma kuma kasancewar su mata ga mai mulki ba karamin ƙara samun power bane. Badan-badan ba babu abinda zai hanani tabbatar da ita abokiyar tafiyata. Dama yarinyar ga shegen ƙyau da ƙira tamkar ita ta zana kanta...” Ƙaramar dariya Miran Arshaan yay idonsa akan ɗan uwan nasa. “Wato dai Jasim Akh har yanzu bazaka canja ba, na ɗauka tuni ka jingine batun son matan nan naka kodan kujerar da ke gab da zama taka”. “Bazaka gane bane Arshaan Akh”. Miran Jasim ya faɗa yana tasa ƴar dariyar shima da komawa jikin kujera ya lafe ƙyaƙyƙyawar surar Iffah da bata wuce sa'ar autarsa ba na masa kaikawo. Shima dai Miran Arshaan ɗin hakance a ransa, dan tun randa suka haɗu da Iffah a wajen wasan takobi da Tajwar Eshaan yarinyar ta kasa barin ransa. Duk da dai shi yanzu kam ya ɗan rage bin mata tun aurensa da Jasrah. Humm masu karatu Bara na ɗan tsakura muku wata gulma dai karna wuce. (A baya ƙiyayyar ƴan ɗakin su Miran Jasim da Miran Arshaan a bayyane take fiye data ƴan ɗakinsu Tajwar Haysam (mahaifin Tajwar Eshaan kenan) amma a wasu shekaru bayan hawa mulkin Tajwar Haysam sai aka wayi gari sun ɗinke, ƙiyayyar da sukema juna ta koma ta ƙarƙashin ƙasa. Wannan haɗin kai nasu kuwa ya samo asaline a dalilin kasancewar halinsu da yazo ɗaya. Awani lokacin bikin al'ada kamar yanda duk suka saba sun baza yaransu samo musu yara matasan ƴammata masu jini a jika da basu gaza sha bakwai zuwa ashirin ba. Karku ɗauka da yardar yaran wai ake kai musu su, ko ɗaya, ta karfin tsiya za'a ɗaukeki bayan an shaƙa miki abu ko an yaudareki, bazaki tashi tsintar kanki ba sai a ɓoyayyen gurin da in zaki kwana dubu ihu babu mai jinki. Idan sun gama lalata rayuwar yaran kuma a jefar da su. Alokacin da labarin yaje ga Tajwar Haysam hankalinsa ya tashi, dan a shekarar an samu gawar yara ƴammata kusan biyar da waɗan da aka jikata, iya bincike kuma na jami'an tsaro ba'a sami komai ba. Da shekara ta dawo kuwa yasa tsatstsauran tsaro akan kaikawon mata fiye da maza, aka kuma sake sabon tsarin yanda bikin al'ada zai kasance. Ransu Miran Jasim ya ɓaci matuƙa, dan ƙarshe sai a yaran masarauta suka huce haushinsu ƴaƴan talakawa sun gagara ɗauka. Duk da ba tare suke aikatawa ba sai shirunsu yazo ɗaya a lokacin, har ya kasance yaransu dake sato musu ƴammatan sunyi haɗaka akan yarinya rigima ta kaure, kowanne ya sanarma ogansa, a zafafe Miran Jasim da Miran Jasim suka buƙaci sanin juna kowanne da tunanin shike da ƙarfin iko, sunko haɗun a yanayin da hantar kowanne ta kaɗu dan mamaki, amma ƙwallafa rai da kowannensu yayi akan yarinyar ya sasu amincewa juna yin tarayya da ita a tare Wa'iyazubillah 😭🤦. Haka suka haɗu suka lalata rayuwar yarinyar daga ƙarshe ta rasa ranta, a cikin masarautar suka bizneta har a yau kuma babu wanda ya san hakan sai ɗauka da ake yarinyar ta ɓata ne a taron bikin al'ada. Wannan shine sanadin zamowarsu inuwa ɗaya dan wannan ya basu ƙofar dinga kawoma juna mata, sai dai Miran Jasim yafi Miran Arshaan ƙwarewa a harkar, dan shi har order mata yomasa ake daga wasu ƙasashen ma🤦). Wanda ya gane na tayasa murna, wanda bai ganeba ya tsallake kawai😂🥱. ★★ BARRISTER ★★ Kamar yanda su Barrister ke zaman tsammani a yau sai ga kira daga Sayeed Harun Al-rashid, sun tattauna sosai ciki harda yarjewar fita da su Babiy zuwa wata ƙasa da kuma tsananta bincike wajen gani maɓoyar Barrister Abdallah Aas kamar yanda Barrister suka tsara musu. Abu mafi saka Barrister a ƙololuwar farin ciki shine damƙa fita da su Babiy ɗin a hannunsa, amma a zahiri sai ya nuna hakan ba aikinsa bane, shifa ya bada shawara ne kawai. A ɓangaren su sun nuna masa sufa sun yarda da shine, bayan shi kuma bazasu iya bama wani aikin ba gudun abinda zai je ya dawo. Bayan dai ɗan cigaba da tirjewa da ga ƙarshe Barrister ya amsa. Hakan ya musu daɗi suma, dan a nasu ɓangaren sun bashi aikinne domin ƙullama rayuwarsa, acewarsu koda ta tashi salin alin zasu zare hanunsu su barsa a ciki. Barrister da ya gama fahimtar su da ƙudirinsu duk da basu fito sun faɗa ba yay murmushi yana mai girgiza kansa da mamakin mutanen wannan duniya mai cike da rikici. “Son kai shine tushen rugujewar kawunan mu a wannan duniyar. Mai mulki kansa kawai ya sani. Mai arziƙi kansa kawai ya sani. Talaka kansa kawai ya sani. Mai ilimi kansa kawai ya sani. Jahili kansa kawai ya sani. Iyaye kansu kawai suka sani. Matasa kansu kawai suka sani. Yaro kansa kawai ya sani. Kowa akan buƙatarsa kansa kawai yake iya kallo. Duk shaƙuwa irin ta ma'aurata akan son kansu kowanne zai iya aikata komai. Duk shaƙuwa irin ta ɗa da iyaye akan son kansu zasu iya komai. A wannan duniyar yanzu samun cikakken amini sai an tona, ka gama yarda da mutum amma akan son kansa zai iya komai. Son kai dai! Son kai dai ya rabbi. Ƴan uwa son kai fa na kawo abubuwa da yawan gaske. Yana gina hassada a zuciya, ƙyashi, zalunci, raunana imani, ƙarya, munafunci, kai komai ma wlhy, hatta shirka tana iya shiga a cikin son kai batare da mun sani ba. Ya rabbi ka ganar damu gaskiya tun kan ta nisanta a kunnuwanmu da idanunmu.......✍️ (Wannan zance haka yake Barrister, ALLAH dai ka shiryar damu🤦). *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_48_* ...........Babu kwanciyar hankali gasu Kaka, dan har yanzu basu sami bakin zaren jin komai ba game da wadda aka rasa a cikin matan Shahan-shan. Ga tashin hankalin ɓatan Barrister dan sun je har gidansa amma a rufe alamar iyalansa ma dai basa nan. Acewar makwafta kuma dai anzo an kwashesune a cikin dare, yau kusan kwanaki takwas kenan. A lissafinsu kuma ya kama randa Barrister ya ɓata kenan. Zuciyar kaka ingizashi take kan abubuwa masu yawan gaske amma yana gocewa, dan duk tsanani yayi alƙawarin dogaro ga ALLAH majiɓincin al'amuran bayi a kowane tsanani da sauƙi. Kwanansa ɗaya ya juya ƙauyen Jumna, dan yasan ya baro su Iyyani a tashin hankali. Ilai kuwa koda ya koma sai ya samesu a birkice, dan suma dai zuwa yanzu labarin halin da ƙasar ke ciki ya isa har kunnuwansu. Ummu tayi kuka har hawaye sun daina zuba. Ta gama sadakarwa ta rasa autarta itama. Dama ta jima da fidda rai ga su Babiy tuni. Kaka rasa ma mizai ce da su yayi, dan shima dai nasa kan a zafafe yake. Sai kawai ya shige ɗakinsa ya rufe kansa yana mai safa da marwa....... ★★..... BARRISTER ★★...... Da taimakon masu tsaronsa bisa umarnin ogansu da tun a ganin farko da yay masa bai sake ganinsa ba sai ta waya tun a yammacin ranar suka fara tattara abubuwan da zai basu kariya wajen fita da su Babiy duk da basu zo hanunsu ba har yanzu. Sai dai a daren ranar su Sayeed Harun Al-rashid sukai alkawarin danƙasu hannun Barrister, duk da ya nuna musu shifa yana jin tsoro su bari komai ya kammala sannan suka nuna masa suna tare da shi da kuma tsaro na musamman duk da kuwa ƙarya ne a baɗini. Zancen kam nasu ya tabbata, dan a daren ranar ƙarfe kusan tara na dare aka damƙa Babiy da Hanash a hannun Barrister Abdallah Aas matsayin Barrister Akeem da zukatansu su suka ɗauka. Daga gani kasan sun jigata matuƙa, sun rame sosai sunyi duhu. Ga rashin ƙarfin jiki da zaman waje ɗaya harma da ƙarancin abinci dana iska mai ƙyau. Hankalin Barrister ya tashi matuƙa, ya dinga share hawayen tausayinsu. Ya sake tabbatar da mutanen nan da suka kamashi mutanen kirki ne a yau, dan ana iso da su Babiy hanunsu sai ga likitoci, dan-da-nan suka duƙufa kansu da kulawa kai kace dama a shirye suke da hakan....... ★★..... MASARAUTA ★★..... Duk da ƙarancin shekarunta ALLAH ya bata basira irinta masu hangen nesa. Tun bayan gama wayarta da Miran Jasim zuciyarta bata aminta da yarda su gana fuska da fuska ba. Dan haka ana idar da sallar magrib ta tura masa saƙo kamar haka duk da ita ba sallar zatai ba tana fashi. _Na amince mu tattauna, sai dai bata haɗuwa ba, muyi magana ta video call._ Miran Jasim ya karanta saƙon yafi sau ashirin, takaici kam ba'a magana ga ɗunbin mamakin basirar ƴar ficikar yarinyar. A take ransa duk ya jagule, ga boka Barbushi ya tabbatar masa haɗuwa da yarinyar fuska da fuska yafi fa'ida. Dan kwarjininsa da suddabaran da ya basu zai sakamata tsoronsa mai tsanani ya dinga yanda yaso da ita har zuwa sanda itama zasu ɓaddata bayan ta cika musu aikinsu. Gashi yanzu guri ya ƙure, bazai yiwu masa ba zuwa ga Barbushi ɗin dan zai iya rasa wannan damar da bokan nasu ya tabbatar musu itace ranarsu mafi Sa'a akan yarinyar kasancewar tana fashin salla, tana kuma cikin ruɗanin da ba komai yake iya banbancewa yanda ya kamata ba zasu iya sarrafata a duk yanda sukaso musamman akan Shahan-shan. Duk da sallar isha'i data gama gabatowa haka ya miƙe ya fice a masallacin bayan yayma Miran Arshaan alama da ido. Bai jima da fita ba kuwa yabi bayansa.... “ALLAH yasa dai lafiya na ganka duk a wani birkice?”. Miran Jasim ya sauke idonsa akan Miran Arshaan mai maganar yana mai jan tsaki. “Wane kwanciyar hankaline da ni inba gani nai komai ya daidaita ba Arshaan. Yanzu ma ƴar iskar yarinyar nan ce wai fa ta turamin text message bata yarda mu haɗu fuska da fuska ba sai dai video call”. “What! Waini wace irin hatsabibiyar yarinya ce wannan? Nama fahimci kallon sa'aninta take mana”. “Ka barta karka damu, zata yabama aya zaƙinta ta dai gama mana aikinmu. Anan zata gane ko wanda ya ajiyeta a gidan bai isa ba balle ita karamar halitta. Ni yanzu damuwata ma shine Barbushi ya tabbar mana da wannan ranar ta sa'a, haɗuwarmu kuma fuska da fuska wani babban cigabane garemu.” “Komai ya kwaɓe kam, sai dai ni a wannan gaɓar ina masa kallon mai sauƙi. Kaga dai a yanzu bamu da isashen lokacin komawa wajen Barbushi, na biyu barin wannan damar ta wuce a garemu kuskure ne. Dan haka kawai mubita a yanda take so ɗin, da sassafe mu nufi Barbushi”. Ajiyar zuciya mai nauyi Miran Jasim ya sauke domin gamsuwa da zancen Miran Arshaan ɗin, daga haka basu koma masallacin ba sukai zaman kulla yanda zasu tunkari Iffah bayan sun tura mata saƙon amincewa ayi video call ɗin. *_10:30pm_* Ƙarfe goma da rabi na dare agogon ƙasar Iffah zaune gaban laptop ɗin ta, sanye take cikin suturar ta mai sirrinta jiki, iya zagayen ƙyaƙykywar fuskarta kawai ake iya gani. Tayi fayau ga mai kallo baka iya ganin komai sai damuwa da tsantsar ƙuruciyarta. Cikin girmamawa ta gaida dattijan guda biyu dake a fuskar lap-top ɗin tata. Miran Jasim da Miran Arshaan suka amsa mata da kulawa da nuna tausayawa tsantsa a fuskokinsu. Ita dai idanunta a rissine, dan tun kallo ɗaya datai musu bata sake yarda ta ƙara ba. Miran Jasim yay ƴar gyaran murya da fara magana bayan gaisuwar tasu. “Ibnati mu mun sauke nauyin dake kammu naki, abinda kika yanke kawai muke buƙatar ji domin tsallakar da rayuwarki data ƴan baya. Dan a yanzu mun shirya tsaf ba tsafi ba ko bataliyar ifiritai Eshaan zai sauke a kammu domin danne cewarmu bazamu taɓa yin shiru ba”. Iffah ta jinjina kai a hankali da faɗin, “Uncles naji daɗin hakan, kuma tun farko dama haka ya kamata ku kasance, duk da dai nasan bai zama lallai kuji irin zafin da iyayenmu sukaji ba. Amma a yanzu daya fara taɓaku gashi kun zaburo. Duk da haka bazamu ƙi karɓar taimakonku ba, dan a yanzu bani da wani abu dana tsana sama da shi, a shirye nake kuma na zama ajalinsa koda nima zan rasa nawa ranne. Sai dai ina son dan ALLAH uncle ka faɗamin gaskiya taya ka samu wannan videon? Ta ya kuma kasan na cikin videon nada alaƙa da ni ne? Miyasa kuke son taimaka mini? Miyasa duk da kun san yana kan rashin dai-dai baku taɓa wani yunƙuri ba a baya sai yanzu?”. Kallon juna Miran Arshaan da Miran Jasim sukai kowanne ransa na susa da mamakin tsaurin idon wannan yarinya da sukema kallon hatsabibiya. Amma a zahiri sai Miran Jasim yaja ajiyar zuciya ya fesar cikin ƙoƙarin danne razanin da tambayoyinta suke neman jefasa. “Ibnati duk wannan ai na abin mamaki bane da har zai saka miki shakku, amma tunda kina son sani yanzu zakiji komai. Wannan video ɗin da kike gani na samosa ne a system ɗin Eshaan, bakuna shi kaɗai bane ba. Akwai ire-irensa da yawa harma dana yanda aka hallaka matansa na baya. Ina haɗasu ne domin miƙasa kotu a kwatarma masu hakki hakkinsu duk da ina fargabar ƙarfin iko irin na Shahan-shan bazai bari a hukunta shin ba kasancewar komai sai da say ɗinsa ke gudana a ƙasar ruman baki ɗaya. Sanin alaƙarki da wannan video kuwa ta samune duk a dalilin bibiyar tasa, sai dai bamu tabbatar ke bace ba sai a ranar da kika samesa tare da Arshaan Akh suna wasan takkubba. Sannan kasa tunkararsa a baya Ibnati bazaki gane ba, ƙarfin ikon Shahan-shan fa bana wasa bane ga kowa....” “Tabbas hakane” Miran Arshaan ya amshe zancen. Batare daya jira cewar Iffah ba ya cigaba da faɗin, “Idan baki manta ba bayan kin basa shayi ya koma gefene yana kallo cikin masarauta, nima kina bani kuma na koma kusa da shi ina mai yabama tarbiyyarki da tabbatar masa yayi dace mace tagari data dace da shi a yanzu. Buɗar bakinsa sai ya sake tsaki da faɗin, “Tukunna dai, ai shi har yanzu matar da zai rayu da ita bata iso ba. Naji mamaki harna tambayesa ba'asin hakan amma sai bai tankani ba kin sanshi da girman kai. Zancen ya tsaya min a rai nazo na sami Jasim Akh da maganar, shine fa ya duƙufa bincike harya samu ganawa da kakanki da ke a ƙauyen Jumna”. Sosai Iffah ta zabura da jin sun gana da kaka harta ɗago ido ta na kallonsu. Tabbas sihiri gaskiya ne, kuma yakanci kowama tunda har yaci ma'aikin ALLAH. A take wani abu mai sanyi ya dinga shiga jikin Iffah tamkar ana kwararashi cikin jininta. Hawaye ne suka silalo a idonta ta buɗe baki a hankali ta furta “Tabbas zan kashesa da hannuna, zan kashesa da dafin maciji na gaskiya kamar yanda yake halaka mutane dana tsafi. Nayi alkawarin yanda ya wargaza min ahali nima sai na wargaza rayuwarsa..” Miran Arshaan da Miran Jasim suka kalli juna sukai murmushi. “Zako mu baki dukkan gudunmawar da kike buƙata Ibnati. Tare da kariya ta musamman ga duk wanda zai iya kawo miki hari, balle ma a yanzu abinda zakiyi sai dai ya ƙara kawo miki ɗaukaka dan irinki ƙasar ruman ke nema. Mi kike buƙata a yanzu?”. Kai tsaye ta amsa da cewar, “Dafin maciji mai matuƙar haɗari”. “Zako ki sami na macizai ma ba maciji kawai ba. Ki saurari saƙo zuwa safiyar gobe. Mun barki lafiya”. Wani irin kuka mai taɓa zuciya Iffah ta saki, a hankali ta zame takai kwance kanta da yay mata nauyi na sara mata. Gaba ɗaya duniyar tai mata dummm bata gane komai, burinta kawai shine ta ɓatar da Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed. Gawarsa kawai tafi bukatar gani kwance a ƙasa fiye da komai. So take taga ahalinsa na kuka fiye da wanda sukai a dalilin rasa ƴan uwansu saboda son kansa. Haka ta kwana a wani irin bahagon yanayin da bazata iya koda tunawa ba. Ita bamai barci ba ita ba ido biyu ba, ita ba matacciya ba ita ba mai rai ba gadai tanan. Duk da tana fashin salla ana kiran salla ta miƙe, bayi ta shiga ta tsaftace jikinta duk da babu wani ƙazanta tattare da ita, tana ƙoƙarin naɗe gashinta daya ɗan warware takeji kamar magana a ƙofar ɗakin nata. Cikin shakku ta gyara rigar wankar jikinta ta nufi ƙofa ta buɗe. Da mamaki take kallon amintacciyar hadimarta mai suna Abal dake a durƙushe hanunta ɗauke da ƙyakywan bowl. Da sauri Abal takai ƙasa tana gaidata. Batare da Iffah ta amsa ba ta ɗaga bakinta da yay mata nauyi da ƙyar tace, “Lafiya.....?” “Lafiya Lau ya Zawjata-almilk. Saƙone daga sashen mai Babban ɗaki”. Hakan ya ɗan saka Iffah a shakku da mamaki, amma sai bakinta yay mata nauyi bata iya ta sake cewa komai ba ta amshi tambulan ɗin mai ɗauke da sabuwar madara fara ƙal. Idanu Iffah ta tsurama madarar wani shawa'ar shanta na fusgarta. Amma sai ta dake ta ajiye ta da nufin sai ta gama kimtsawa tasha ko kaɗanne kaffin ta sake komawa barci. Harta nufi kayan data fiddo zata saka kira ya shigo wayarta. Ruɗewa tai dan abune da bai taɓa faruwa da ita ba, kofa sallar asubahi ba ayi ba. Kamar wadda ake ingizawa da remote ta ɗauka wayar, ganin Miran Jasim ta amsa da tsumar jiki tana gaisheshi kai kace yana a gabanta ne. Bai amsata ba, sai ma umarni daya bata cikin kakkausar murya saɓanin wadda yake mata magana da ita a baya. “Wannan madara ce mai ɗauke da dafin macizai masu haɗarin gaske har guda biyar, daga yanzu zuwa ƙarfe takwas na safiya ina buƙatar jin kukan mutuwa. Kukan mutuwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed nake buƙatar ji har gadon barci na ta dalilinki”. “An gama ranka ya daɗe”. Iffah ta amsa da rawar murya hawaye na ciko mata ido ga girmamawa har tana rissinawa kamar tana a gabamsa.........✍️ *_🤦ALLAH sarki Iffah baki shike yanka wuya. Kin ɗauka niyya badan zuciyarki zata iya ba a zahiri, gashi masu babban burin sharri zasuyi jifa da hannayenki batare da kin san illar hakan ba a gareki._* *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_49_* .........Tunda al'amarin nan ya faru babu wanda zai ce yaji koda motsinsa a masarautar hatta hadiman dake zagaye da sashen nasa. Har masu dafa abinci da amintacen hadiminsa dakan iya ganinsa ko kai masa saƙo ma ba ganin nasa suke ba. Abinci kuwa yanda suka shirya haka suke kwashesa. Amma hakan baisa sun gajiya ba kasancewar aikinsu ne. Yau ma kamar kullum sun tsaftato ko'ina sun kuma bajesa da ƙamshi mai taɓa kuzarin mai shaƙa. Bayan an haɗa abincinsa da duk a kwanakin nan yanda ake shiryashi haka suke zuwa su kwashe duk suka koma hawa na uku da shine dai wajen zamansu, sai amintacen hadiminsa da kawai ke da lasisin zama a hawa na karshen ne yay zaman gadin abincin gudun samun matsala duk da babu wani mahaluki a zahiri daya isa ketowa har nan ya saka wani abin cutarwa da ake tsoro. Kusan ƙarfe takwas abinda hadimin bai zaton gani ko tsammani ba yay matuƙar kidimashi. Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed ne da suka kwashe kusan kwanaki takwas batare da sanyashi a idonsu ba ke tunkaro falon cikin takun ƙasaita da izza. Cikin rawar jiki da ruɗani hadimin ya zube a ƙasa bakinsa har rawa yake wajen miƙa gaisuwa. Kamar yanda ya saba kai kawai ya ɗan jinjina batare da damuwa da hadimin ya gani ko bai gani ba ya gittashi ya wuce. Hadimin ya ɗan lumshe ido da zuƙar daddaɗan kamshin shugaban nasa yana mai sauke ajiyar zuciya a ƙasan maƙoshi. Tajwar Eshaan da baima san yanayi ba a hankali ya kai zaune cikin kujera ya harɗe ƙafafu cikin salon zama irin na sarakan da suka isa. Sai a lokacin hadimin ya zaburo ya sake zubewa gabansa. “Ya shugabana ko ana bukatar shayi?”. Kansa kawai ya ɗan jinjina alamar eh yana kauda fuskar sa gefe. Da sauri hadimin da ke satar kallonsa ta gefen ido ya miƙe, haɗaɗɗen daning table ɗin mai cike da kayan breakfast ya nufa, cikin abinda baifi mintuna biyu ba ya dawo ɗauke da ƙaramin tray da butar shayi a samansa. A ɗan tebirin gaban kukerar da yake zaune ya ajiye. Ya tsiyaya shayin a ƙaramin kofin. Baya yaja sosai kansa a ƙasa cikin ƙanƙan da kai yace, “An kammala ya shugabana”. Baiyi magana ba, bai kuma motsa ba har bayan wasu mintunan biyu. Bayan ya kai shayin bakinsa kusan sau biyu ya ɗan dubi hadimin dake tsaye kai a risine ya sake kauda kai. Maganace a bakinsa, amma sai da ya sake jan wasu sakkani kafin ya furta ta a fisge. “Mike faruwa a daular ruman?”. Tambaya mafi rikitarwa, mamaki, al'ajabi harma da ruɗaki ga duk wanda ya jita a bakin da ba'ayi tunani ko tsammani ba ce ta riski hadimin. Falon ya shiga waw-wai-gawa cikin tsumar jiki. Tabbas shine dai akaima tambayar ba wani ba. Sai duk ya sake ruɗewa ba shiri ya zube ƙasa akan guyawunsa. “Kariyar UBANGIJI da ingantacciyar lafiya su kasance ga shugabana, abubuwa da yawa sun faru marasa daɗin faɗi da sauraren ji. Sai dai ban san wanne ake bukatar na isar ba”. Tamkar ma bashine ya buƙaci jin ba, tsahon wasu mintuna da zasu iya kai huɗu ya sake amsawa ciki-ciki. “Komai”. Kai hadimin ya jinjina yana mai sake ƙan-ƙan da kai, ya fara zayyano komai tiryan-tiryan tun daga randa aka ɗauke Iffah sashen har zuwa yau ɗin nan da yake gabansa. Ya kare da faɗin, “Idan na faɗi abinda ba shi shugabana ke buƙatar ji ba ina mai neman afuwa”. Idan gunki ya motsa bayan ƙare abinda ya buƙaci ji to ya motsa. Hadimin dama dai baya tsammanin samun sharhi ko tambaya ko fashin baƙi daga abinda ya faɗa, dan haka yaja bakinsa yay shiru yana ɗan satar kallonsa ta gefen ido. Ba yau ya fara ganin Tajwar Eshaan ɗin ya danna wani abu a gefen kujerar da yake zama computer ta bayyana ba kamar yanda yayi a yanzu, sai dai a iya hasashensa da dube-dube idan yana gyaran saman ya kasa gano komai...... ★★... KAUYEN JUMNA ★★ Hukuncin da kaka ya yanke, sakamakon tashin hankalin da suka kwana a ciki shi da Ummu da Iyyani tun da sassafe suka fito da nufin komawa gidan Babiy na daular ruman gaba ɗayansu. Kaka ya gama shirya tunkarar kowa gaba-da-gaba a yanzu, dan haka babu ko ɗar tattare da shi. Saurayin nan na kwanaki dake ƙoƙarin shigowa layin gidansu yay saurin taka birki idanunsa a kansu. Tabbatar da su ɗinne dai ke tafe a ƙafa ya sashi ɗaukar wayarsa da sauri-sauri ya latso wata lamba. Sai da tana gab da tsinkewa aka ɗaga, da ƙyar ya iya haɗa haruffan sallama bai jira an amsa masa ba ya ɗora da faɗin, “Oga abin mamaki gasu nan suna fitowa da alama ma garin zasu bari”. “Woow interesting”. Aka faɗa daga can cikin nuna ci da birgewa. Sai kuma aka ɗora da faɗin, “Maza ka juya ka koma kan ainahin hanya kafin su isa. Ka tabbatar nan da mintunan da basu wuce hamsin ba na gansu a gabana”. “An gama boss”. Saurayin ya faɗa da tsantsar girmamawa. Sam su Kaka dake tafiya hankalinsu bai kai kan motarba saboda Ummu dake tafiya a wahale, idan ma ta taka ɗaya biyu sai sun tsaya ta huta kafin su cigaba. Yayi jira na kusan mintuna goma sha ɗaya kafin su iso inda tuni ya iso shi yay fakin. Da sauri ya fito daga lungun daya laɓe hanunsa riƙe da leda yana ɗan cillawa yana ƴar wakarsa. Kamar wani shiri sai ko idon Kaka dake ma Ummu nasiha ta daure su ƙarasa akan wannan saurayi. Yay ɗan jimm alamar shan jinin jiki, sai kuma ganin yanda saurayin ya gittasu babu alamar ya gansa ya sashi zabura. “Ƴan samari na ce ba...?” Kamar saurayin bazai kula ba sai kuma ya juyo a ɗan yatsine yana faɗin, “Kace mi....?” sai kuma ya ƙi ƙarasawa da nuna alamar shock kamar gaske. “Ya ALLAHU wa nake gaji haka kamar Baba?”. Kaka ya sauke ajiyar zuciya da jin shakkunsa gaba ɗaya ya gudu yay ɗan murmushi. “Kaga ja'iri ni ne ɗin dai, yaushe haka a gari babu labari?”. Kai a sunkuye saurayin ya shafa ƙeya yana murmushi. “Afuwa kaka uziri ne ya ciyoni har nai ƙudirin shallakeku a karo na biyu batare dana leƙa ba. Yanzu haka ma nan jirana ake saƙo na amsa anan ɗin fatana na kai Dahab (Daular ruman) kafin cikar awa ɗaya da rabi”. Cikin jin daɗi Kaka yace, “Kai Alhamdullah da wannan zance. Ka ganmu muma can ɗin muka nufa a she da rabon ba sai mun sha wahala ba na jiran mota ma”. Saurayin ya ɗago irin da mamakin nan, irin sai yanzu ya lura da su iyyanin nan. Gaishesu ya fara da ban haƙurin bai lura da su ba ne wai. Iyyani ta amsa masa da kulawa tana faɗin babu komai. “Idan hakane Baba ai ku shiga kawai mu wuce, gaisuwar ma a karasata a hanya”. “Af, e to kaima kayi zance na gaskiya. Amma ai zamu dakushe maka uzrinka”. “Ai babu komai baba, sahun giwa ya isa take na raƙumi”. Fuskokinsu ɗauke da murmushi duk suka shiga, Iyyani da Ummu a baya. Kaka ya shiga ta gefensa. Sai da ya tabbatar sun hau hanya ya gyara zaman norse mask ɗin fuskarsa da ƙyau, handkherciff ɗin gefensa ya matsar jikin ac kamar zai goge ya danna ac'n motar ya ƙure. A take ya busa tare abinda ke jikin handkherciff ɗin gasu Iyyani da kaka suka shaƙa har suna sakin ajiyar zukata kusan a jere. Kashewa yay da sauri yana faɗin, “Af kajini da karambani zansa Baba mura”. Nauyin da kawunansu ya fara musu ya hanasu damar magana duk suka dafe kai kusan a tare, kaka ne ke ƙarfin halin cewa wani abu amma ya kasa, su Ummu kam tuni sunyi luuu jikin kujera alamar barci ya bugar da su. Kakan ma yay luuu a tasa kujerar. Nannauyan numfashi saurayin ya sauke da ɗan juyawa ya dubesu ta mirror. Tabbatar da sun suma yanda yake buƙata ya sashi janye Norse mask ɗin fuskasa da sakin murmushi ya latse wayarsa. Ana ɗagawa bai jira komai ba ya furta, “Done! boss”. “Proud of you”. Aka bashi amsa a taƙaice da ga can da latse wayar...... (Ta faru ta ƙare🤦😱) ★★.... ★★.... ★★..... Tajwar Eshaan da bai sake bi takan hadimin ba kam hankalinsa gaba ɗaya ya tattara ne ga computer ɗin gabansa a yanda yake harɗe. Cikin nutsuwa yake sarrafata a take saƙonnin da yake buƙatar gani suka bayyana kansu. Hannu ya kai ya sake daidaita gilashin idanunsa da ɗan yamutsa fuska ganin dogon text message ɗin daya buɗo... Dai-dai nan takunta da ƙyamshin sassanyan turarenta ya fara rige-rigen isowa hancinsa tun kafin bayyanarta. Wani irin harbawa daya tilastashi ɗaga ƙwayoyin idanunsa kaɗan ta cikin gilashin yay sai ko suka sauka akanta. Sanye take cikin shirinta da baza'a kirasa mai matuƙar ƙawa ba, ba kuma mai ƙasƙantarwa ba. Babu ko ɗigon kwalliya a fuskarta, ƙamshin turarenta ma a yau ƙasa-ƙasa ake iya jinsa. A zahiri zaka ɗauka yanayin da masarautar ke cikine ya sata kasancewa haka, sai dai a haƙiƙanin gaskiya komai a sukurkurce yake gareta. Duk wanda ya san alwashinta akan Tajwar Eshaan zai kalla wannan lokaci ne matsayin na farinciki a gareta domin ta kusanto hanyar cikar nasararta, sai dai zuciyarta danƙare take da wani irin ruɗani da ƙunci. Amma ta kasa dakatar da kanta, komai yana sarrafa kansa tare da ita ne tamkar wadda ake sarrafawa da na'urar remote. Yanda ta ɗanyi turus kamar wadda ta firgita da ganinsa ne ya sashi maida idanun nasa ƙasa cike da basarwa ga screen ɗin computer ɗin kai kace baima san da ko motsinta ba a wajen. Da ƙyar Iffah ta iya jan numfashi, yayinda bugun da zuciyarta ke faman yi tsananinsa ya ƙara hauhawa. Sai dai mi, bata iya jin zata dakata duk da wani irin rauni da kasala dake cigaba da mamayeta. Tamkar wata hawainiya haka ta cigaba da takowa da sanɗa har inda yake, ta ɗan rissino ta gabansa ta dire tambulan ɗin hannunta a tebirin gaban nasa batare da tayi magana ba. Amintaccen hadimin nasa da al'amarin ya zame masa kamar wani sabon abu, yay saurin dawowa hayyacinsa cikin rawar harshe ya fara miƙa gaisuwa gareta. Hannu kawai ta iya ɗaga masa a kasalance dai-dai tana kaiwa a kujerar dake gefen Tajwar Eshaan zaune. Dole ya miƙe da sauri ya fice a falon, dan cigaba da zamansa haramunne. Iffah dake jin kamar ta fasa kuka a dai-dai wannan gaɓar ta ɗaga idanunta da girmansu a yau gaba ɗaya ya shanye da ƙyar ta saukesu akan Shahan-shan da yay tamkar bai san da wani mahaluki mai numfashi a falon ba bayan shi. “Bar... ka da sa.. fi... ya”. Ta faɗa a rarrabe tamkar mai koyon magana. Da gaske yau ƴan izzar ne a kasan, dan haka bai nuna alamar yaji ba, dan bai ko motsa ba balle ɗauke ido akan abinda ke gabansa har kusan tsahon mintuna biyu kafin ya ɗaga mata hannu da ƙyar ya cigaba da abinda ke gabansa. A ƙalla da a ainahin Iffahr ta take salon nasa zai soke ta, bakuma zata iya haƙuri ba sai ta maida murtani. Amma abin mamaki sai ta miƙe jiki a saɓule ta nufi daning babu jimawa ta dawo da glass cup. Da kallon ƙasan ido ya bita zuciyarsa da jijiyoyin jikinsa na wani irin tsitstsinkewa tamkar suna masa ishara da abinda ke tinkarosa. A karo na farko takai durƙushe gabansa, tare da buɗe tambulan ɗin data shigo da shi mai ɗauke da tatacciyar madara dake gauraye da dafin macizai daban-daban har kala biyar. Jikinta rawa yake, har shi kansa sai da ya lura da hakan ta kallon gefen ido da yake mata. Madarar da bata wuce rabin kofi ba ta miƙa masa tana mai rumtse idanunta wasu hawaye da ƙarfinsu ya zame mata nauyi a ƙirji na gangarowa da gudun tsiya bisa ƙyakykyawar fuskarta. Cak ya tsaya daga abinda ya keyi, duk da bai juyo gaba ɗayansa yana kallonta ba, hankalinsa kaf ya koma gareta. Kusan a tare zuciyarsa da jininsa ke tsitstsinkewa. Bashi da bukatar shan madara a wannan gaɓar dan a nasa tsarin da rana ko dare kawai yake shan madara. Sauran lokuta shayi ne mafi rinjaye da ruwa. Amma a yanzu duk da bahagon yanayin da yake jin jikinsa, da wanda yaga yarinyar a ciki sai ya kasa nuna bazai sha ba, tamkar shima ana ingizashi da remote ɗinne ya kai tattausan hannunsa saman nata a karo na biyu. Zabura tayi kamar wadda ke son dawowa hayyacinta sai kuma ta koma laƙwas tare da buɗe idanunta da sukai jazur ta sauke a kansa. Kallon cikin ido sukai ma juna na kusan tsahon minti ɗaya cirr batare da ɗaya su ya motsa ba abinda bai taɓa faruwa da su ba. Shi ya fara janye nasa a kasalance tare da hanunsa da ya zaro kofin daga cikin nata... A yanzun ma firgigit tayi tamkar wadda ta farka a barci harda ɗan zabura ta kai hannu kamar zata riƙo kofin sai dai abin mamaki shi har ya kaisa kan baki...........✍️ (🤦Da zaka iya jina daga tawa duniyar da nace karka sha😭). *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_Part 1 End_* *_(50)_* ........Dire kofin da ke empty a hanun Tajwar Eshaan dai-dai da komawar Iffah daɓas zaune ƙasan lallausan kafet ɗin kamar wadda aka zarema dukkan numfashi. Ta matse jikinta tana mai ƙoƙarin riƙe tsumar da takeyi tare da miƙewa zumut. Ya kafeta da ido lips ɗinsa na ɗan motsawa alamar son cewa wani abu amma jin kai da ƙasaita ya hanashi yin hakan. Sai kawai yay ƙoƙarin janyewa cike da basarwa amma hakan ya gagara. Shi kansa bai san yaya akai ba, bai san tayaya ba kawai ya samu kansa ne da riƙo hannunta. A tare suka rumtse ido bisa mabanbanta dalilai. Karan farko na fara tasirin dafin macizan da suka gama gauraye jininsa ya matsota a hankali garesa. Babu zato Iffah tajita saman jikinsa da ke fitar da wani irin sirrintaccen ƙamshi mai karya zuciya. Numfashinta ne ya fisga da ƙarfi kamar mai cutar Asthma, ta buɗe ido da sauri dan gaba ɗaya hankalinta ya dawo jikinta. Zumbur ta mike jikinta na wani irin kaɗawa ta fara jan ƙafafunta da baya-baya siraran hawaye da batasan na minene ba na rige-rigen sakkowa. Cikin son danne tashin hankalin dake cigaba da gauraye jijiyoyi da tsokar jikinsa ya ɗago idanunsa da launinsu har ya fara canjawa ya zuba mata, gab taci tuntuɓe da centre table, kaifin idanunsa da tasirin su gareta a wannan gaɓar ya sata zubewa gaba ɗayanta akan tebirin... Wata irin zufa ce ta fara keto masa a dukkan ƙofifin gashinsa, yayinda tun yana iya ganin Iffah a kusa da shi har ta fara masa nisa. (Tabbas a kwai matsala) ya ayyana a zuciyarsa yana mikewa da ƙyar. Da kallo ta bishi zuciyarta na wani irin mahaukacin bugu tamkar zata buntsiro ta bakinta. Ganin ya shige ta miƙe itama cikin sassarfa, harta nufi ƙofa ta dakata, tamkar an janyo idanunta suka sauka kan computer ɗinsa, janyewa tai dan burinta tabar sashen kawai amma sai zuciyarta ta dinga ingizata ga computer ɗin. Bayanta ta ɗan waw-wai-gawa irin dai na rashin gaskiya kafin ta koma da baya ta zauna a kujerar tasa ta dasama rubutun fuskar computer ɗin ido. A karan farko ƙirjinta yay wani irin masifar motsawa. Tsabar kaɗuwa batama san takai hannu ga computer ɗin ba har rawar jikinta na bayyana. Babu tantama saƙon data turama Ajmaal ne na karshe, kaɗan ya rage zuciyar Iffah ta ɓaro waje a wannan gaɓar, babu shiri ta fara sama dukkan saƙonin data tura masa ne babu ko ɗaya daya goge, kowanne kuma babu canji a date ɗin data tura ne. Ai babu shiri ta fito ta shiga settings ɗinsa na WhatsApp. A Profile ɗinsa, dp pic.. ɗinsa, da komai na dai Ajmaal ɗin data sani ne... “Allahumma ajirni fi musibati wa'akhlifni khairin minha”. Iffah ta ambata a karon farko numfashinta na barazanar barin gangar jikinta, computer ɗin tai ƙoƙarin singumowa gaba ɗaya dan maidata cinyarta akai rashin sa'a ta danna abinda bata sani ba kamar ƙiftawar ido suuu ta shige cikin table ɗin. Ƙwaƙwalwarta neman bugawa tayi tsabar rikicewa, ta shiga leƙe-leƙe a wajen sai dai babu abinda ta gane. Babu shiri ta zabura hanyar da Tajwar Eshaan ya bi tana haɗa hanya..... A ɓangaren Tajwar Eshaan kam da kyar ya iya kai kansa ɗaki, dan jefa kafar kawai yake batare da yasan inda yake takawa ba. A ƙasan lallausan carpet ɗin ɗakin ya zube yana mai jingina jikinsa da yay sharkaf da zufa jikin gado, duk wata addu'ar da tazo bakinsa ambata yake, a haka Iffah data gano ɗakin da ƙyar ta shigo a ɗimauce. Idanunsa dake a lumshe ya buɗe a hankali suka sauka a kanta. Dukkan ƙarfin halinsa da jarumta ya tattaro ya adana tashin hankalin da ke tattare da shi. A ɓangaren ta itama ruɗanin da take ciki ya bada gudunmawa wajen makantar da ita yanayinsa, cikin rawar harshe idanunta dake tsiyayar hawaye a kansa ta durƙushe ɗan nesa da shi. “Dan ALLAH na roƙeka ka faɗamin wanene kai? Miye alaƙar ka da Ajmaal?!”. Babu alamar zai tanka mata, sai dai idanunsa dake sake rinewa jajur na tsaye a kanta ƙyam. Tsahon wasu mintuna ya lumshe su da sake buɗe su a kanta yana cije lips ɗinsa. Ya kauda fuskarsa cike da ƙarfin hali, da son saisaita muryarsa, a maimakon ta samu amsar tambayarta sai saɓaninta ya fito da ga garesa. “Ki canja madarar da kika bani da wadda ke akan dining. Hatta kofin da na sha daga cikinsa karki bari”. Ya ƙare faɗa a wahale cikin cije baki da rumtse idanunsa. (Iffah ki nutsu karki tonama kanki asiri) zuciyarta ta ayyana mata. Idanunta ta rumtse da karfi tana gyaɗa kai kamar wadda ake faɗamawa a cikin kunne. Sai kuma ta shiga goge hawayen nata da maida kallonta garesa a yanayin son kare kai. “Ni ba batun madara na tambaye ka ba. Wanene Ajmaal?!!!”. Ta faɗa a matuƙar tsawace. Birkitattun idanunsa ya rumtse da ƙarfi dan sam baya son hayaniya, balle ma a irin wannan halin da yake ciki a yanzu. Ya buɗesu kanta shima a fusace har sai da kallon cikinsu ya sakata zabura. Shima cikin tsawar da fisgar numfashi ya ce, “Babu abinda zai amfanar da ke a jin amsoshin da kike buƙata a yanzu. Kije kiyi abinda nace!! Kije!!!!”. Ba ƙaramin firgici Iffah ta shiga da yanayin nasa ba. A zabure kuwa ta miƙe, batama san taya ta nufi ƙofa ba ganin kanta kawai tai a falo, harta nufi ƙofar lifter ta dawo da baya, tambulan ɗin madarar ta ɗauka, ta nufi dining wajen wanke hannu ta juyeta, kofin ta ɗauraye jikinta nata ƙyarma, gaba ɗaya ta nema jarumtarta ta rasa, sai da ta tabbatar ya fita ta dawo kan dining ɗin inda aka shirya break fast, madarar dake a jiye a wani tambulan ta ɗaga ta juye a wanda ta wanke ɗin, ta sake komawa ta wanke wannan, sai kuma ta rasa ina zata ɓoyesa kamar yanda zuciyarta ke bata shawara. Da kyar ta samu nutsuwar samun wajen makalasa, ta dawo harta sake nufar hanyar fita ta sake dawowa da baya, kofin da ya sha madarar ne, shima ɗauka tai ta wanke ta zuba sabuwar madarar ta kauraya ta maida inda ya sha. Sake nufar ƙofa tayi sai kuma ta sake dawowa ta nufi ɗakin dai da ka ganta kasan tana a cikin halin ɗimuwa.... A ɓangaren Tajwar Eshaan kam tana fita tari ya sarkesa, jin saukar abu a tafin hannunsa da yake tare bakin ya sashi saurin kallon hannun. “Jini..” ya ambata a hankali saman lips, sai kuma ya saki wani irin wahalallen murmushi da mai da kansa ya kwantar jikin gadon yana ambaton “Sunci nasara, sun sami nasara ta dalilinki *_My Sohaa_*....” tari ya kuma sarƙesa a hankali, sai dai murmushin na nan maƙale a fuskarsa har yanzu, sai faman lumshe idanunsa da suka birkice yake yana ƙoƙarin buɗesu da ƙyar fuskar Iffah da hawayenta ne tsaye ƙyam a cikinsu. Ba mutuwa yake tsoro ba a yanzu, baya da ƙurar da zai barta a ciki, ya tabbatar itace zata sha wahala, wahala irin wadda ba ita yay mata tanadi ba. Hakanne ya zaburar da shi, yaja jikinsa da ke saki gaba ɗaya da ƙyar zuwa telephone.. Ana ɗagawa ya fara magana cikin son ɓoye yanayin da yake ciki. “Duk wani cctv footage na safiyar yau zuwa yanzu na sashe na ka kwashe sa, amana ko kai na haramta maka ganinsa ka ajiyesa gareni, idan kuma na rasa raina ka damƙashi ga Zawja Fareedah....” Bai bada damar cewa komai ba ya yanke kiran, da ƙyar ya maida akalar wani zuwa Malikat Bushirat.... *_MALIKAT BUSHIRAT_* Yanayin tashin hankalin da masarautar ke ciki koma a ace ƙasar baki ɗaya dan yau mutanen da suka fito zanga-zanga akan murabus ɗin Tajwar Eshaan sunfi na kullum yasa ko fita batayi. A kallo ɗaya zaka iya ƙirga damuwarta saman ƙyakykywar fuskarta data koɗe matuƙa a cikin kwanaki ukun nan. Tayi duk wani ƙoƙarin ta iya iyawa domin ganin gudan jininta amma al'amarin ya gagara. Kuka bata san iya adadin da tayi ba ba kuma ta san wanda zatayi a gaba ba, dan anzo gaɓar da ko'a mafarki bata taɓa sakata a lissafin ƙaddararta ba..... Shigowar kira a landline ɗin ɗakin barcin nata ya sata zabura dan yazo mata ne a bazata, dole ta ambaceshi da bazata dan Tajwar Eshaan ne kawai ke da wannan hurumin. Har tuntuɓe taci amma bata damuba ta caɓi kan wayar tunkan ta karasa gareta da ƙyau. Rawar jikinta dana harshe na faruwa ne a lokaci guda, sai dai muryar data doki tsakkiyar dodon kunnenta ta saka numfashinta tsaiwar wucin gadi.... “Ammie!...” Aka faɗa da ƙyar cikin kuma rawar harshe mai fidda sautin nakasashshiyar murya mai tabbatar da amon razani ga mai saurare. “Saiful-malik!!...” Ta ambata itama tare da fisgar numfashinta dake kaikawo a iya maƙoshinta zuwa cikin baki kawai. Shi bai sauka a huhu ba, bai kuma fita ta hanci ba. Bata ma san ta saki wayar ba ta fice... “Ya ALLAH Akia!...” Jasrah dake shigowa ta faɗa da sauri tana riƙo Malikat Bushirat da gaba ɗaya idonta ya rufe da ruɗani. Son ƙwacewa take tana ambaton “Eshaan.. Jasrah Eshaan.. Eshaan zasu kashe min shi”. Sam Jasrah bata fahimci inda ƴar uwar tata ta dosa ba, dan haka tai saurin katseta da faɗin, “Na shiga uku Akia dan ALLAH nutsu kimin bayani, mi ya dakesa?”. Ina Malikat Bushirat ta kasa amsata, dan numfashinta ma har ya fara fisga. Bata haɗa soyayyar Tajwar Eshaan da komai ba a duniya. Tana masa wani irin makahon so mai wahalar fahimta. Duk yanda Jasrah taso tanƙwarata ta kasa, sunan Eshaan kawai take ambata da son fisgewa ta fita. Bazai yiwu ta barta ta fita a haka ba, dan haka tai saurin danna ƙofar bedroom ɗin da ƙafa. Hankaɗata Malikat Bushirat tayi, duk da taji zafi dama gata ba wani ƙwarin jikin take ji ba amma haka ta daure ta murza key. Da ƙyar ta iya zarewa ta sake riƙo Malikat Bushirat tana mai fashewa da kuka. “Akia dan ALLAH ki sanar min, fitarki a haka ba itace mafita ba, idan ma akan masu zanga-zanga ɗin nan ne ki kwantar da hankalinki jami'an tsaro bazasu barsu su ɓalla koda gate na farko ba........” “Jasrah ki fahimceni.....!!!” Malikat Bushirat ta katseta cikin ƙaraji sai kuma ta fashe da kuka. Tabbas babu lafiya, ƴar uwarta a haka lallai akwai matsala. Har taune harshe take wajen ambaton, “Zan fahimceki faɗamin ko a taƙaice ne Akia dan ALLAH”. Da ƙyar Malikat Bushirat ta sanar mata a dunƙule, nan fa hankalin Jasrah ya tashi itama babu shiri ta zabura ta buɗe ƙofar...... ★★.... Suɓucewar kan wayar a hannun Tajwar Eshaan dai-dai da sake faɗowar Iffah ɗakin a birkice. Gaba ɗaya ma ta mance matsayinsa da nata, tai kansa babu alamar hankalinta na tare da gangar jikinta. Tana zubewa gabansa yana faɗowa jikinta hannunsa dafe da kansa yana ambaton “Ammie...” a hankali, ga wata irin zufar da tai masa sharkaf kai kace wanka yay a lokacin. “Na shiga uku ni Fhareedah!”. Da Iffah ta faɗa cikin kuka ya saka shi ɗago idanunsa dake matukar jazur zattashin hankali. Akanta ya tsaidasu a wani irin bahagon yanayi, ya lumshesu da ƙyar ya sake buɗewa a kanta. Lips ɗinsa da suka koma jajur saɓanin pink a da suna motsa a hankali ya saki wani wahalallen murmushi da har Iffah ta koma ga ALLAH bazata taɓa mantawa ba, dan ya zauna a allon zuciyarta tamkar rubutu akan dutse. kafin idon nasa ya koma ya lumshe gaba ɗaya tattausan hanunsa na dama saƙale cikin nata da bata san sanda ya riƙo ba...........✍️ *_ALHAMDULLAHI!!🙏_* Ina godiga ga ALLAH daya bani ikon kawo ƙarshen littafin DAUƊAR GORA CIKI KA SHATA kashi na farƙo. Ina roƙon UBANGIJI ya bani tsahon rai da lafiya ni da ku har zuwa bayan salla da zan ɗora kashi na biyu insha ALLAHU. Ina mai baku haƙuri da ƙari saman haƙuri da tangarɗa da jinkiri da aka samu duk da Alhamdullah ban taɓa fashin posting ba, sai dai labarin yayi tafiyar hawainiya saboda yanayi, hakan ta samune dalilin babban dalili daya shafi uzirin rayuwata. Insha ALLAHU bayan salla zakuga canji ayi haƙuri amin afuwa dan ALLAH yau da gobe kenan kun san Bilyn taku ba haka takeba a da.🙏🥲. Himmm!! Ban san ma mizan ce mukuba daga ƙarshe, amma ku sani DAUƊAR GORA part 2 zai zama na musamman ne da salo mai..... (🤭hummm badai sai nace komai ba..) ★Yaya kuke tunanin rayuwar Iffah zata kasance ne?. ★Mizai faru da Tajwar Eshaan zai mutu ne kokuwa?. ★Waye saurayin daya kwamushe su Kaka?. ★Taya Tajwar Eshaan ya zama Ajmaal?. ★Wacece ta ƙurya?. ★Miran Jasim da Miran Arshaan zasu ci nasara?. ★Anya ƴan ƙasar ruman akwai mai iya kwantar da fushinsu a wannan gaɓar?. ★Yaya makomar su Babiy da Barrister?. Kai tambayoyin da yawa suke karna cikaku da zance Ni ban baku cigaba ba. Kudai kawai muyi addu'ar ALLAH ya kaimu a gama azumi lafiya. Ya rabbi kasa muyi karɓaɓɓiyar ibada. Ina ƙaunarku masoya, zan cigaba da ƙaunarku kuma. Duk wanda ya soni domin ALLAH shima ALLAH ya soshi haka😭🙏😍😍🤩🥰😘. Taku Bilyn Abdull ce😉👍😄. *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (001) ........A matuƙar razane Iffah ta shiga girgiza Tajwar Eshaan jikinta na rawa, gaba ɗaya ta daburce jin jikinsa ya saki ma gaba ɗaya a kanta, hannu ta kai saitin hancinsa, ƙirjinta ya sake girgiza tamkar zuciyarta zata ɓallo daga cikinsa ta faɗi. Cikin fita hayyaci ta cigaba da ɗan girgiza kafaɗunsa dake jikinta da faɗin, “Karka min haka, dan ALLAH ka tashi, ka tashi ka faɗamin, ka faɗamin wanene kai, wanene Ajmaal? Minene alaƙarka da shi? Idan ka mutu nima wlhy mutuwa zanyi... wayyo Ummu wayyo Babiy na shiga ukuna....” kuka ta fashe da shi mai tsuma rai tana mai ɗaura goshinta kan nasa da cigaba da ambaton “Innalillahi wa'inna ilaihiraji'un! Shike nan ni Fhareedah, shike nan na kasheshi Ummu, Ummu na kashshi na shiga ukunaaaaa!!”. A tare Miran Jasim da Miran Arshaan dake shigowa suka ɗauki salati, yayinda Malikat Bushirat da kalaman Iffah sukai matuƙar cakar ƙirjinta tamkar saukar mashi juwa ke neman zubar da ita a ƙasa, cikin sauri Daneen Ammarah dake bayanta ta riƙota itama jikinta na rawar. Jasrah dake bayansu kam tuni tayi kukan kura akan Iffah da ruɗani ya hanata sanin shigowarsu duk da salatin da su Miran Jasim ke faman jerawa har yanzu. A birkice ta janyo Iffah baya ta shaƙeta, faɗi take itama sai ta kasheta, sai ta rabata da numfashinta. Ganin Jasrah na neman yin kisa da gaske Daneen Ammarah tai saurin zaunar da Malikat Bushirat a kujera ta nufesu. Da ƙyar ta iya ɓangare Iffah da taimakon Miran Arshaan da sai da yaga Daneen Ammarah ta zaburo sannan shima ya zabura. Yaraf Iffah ta zube ƙasa tana jan numfashi da ƙyar, yayinda Jasrah ke cigaba da zabura cikin kuka akan ita sai fa ta kashe Iffah. Ƙoƙarin tanƙwarata Miran Arshaan yake yi amma sai ta sake kufce masa. A wannan karon kam da ƙyar Daneen Ammarah ta ɓanɓare Jasrah ta hanyar sauke mata mari itama. Ɗifff kowa ya ɗauke wuta a ɗakin sai kakarin wahalar da Iffah keyi, dai-dai nan kuma Sayeed Aashiq Ali ya iso da likitoci, kasanwarsa uba a gare su a tsawace ya basu umarnin duk su fice. A kaikaice Miran Jasim da Miran Arshaan suka dalla masa harara kafin su fice, Daneen Ammarah ta taimakawa Malikat Bushirat da bata tofa ko kanzil ba har yanzu, Miran Arshaan kuma ya kama Jasrah. Iffah kasa tashi tayi dan da gaske ta shaƙu, dole sai da aka taimaka mata itama. Da ƙyar aka iya ɓanɓare hannun dake cikin na Tajwar Eshaan har yanzu tana kuka kamar ranta zai fita. Sashenta aka maidata, tare da sake zagaye sashen Shahan-shan ɗin da tsaro na musamman. Likitansa da wasu ƙwararrun likitoci biyu dake a kansa domin ceto rayuwarsa tuni bincikensu ya gano musu dafin macizai da guba da ya sha. Sun sami nasarar kashe kaifin dafin macizan, sai dai sun tabbatar da gubar ta fara ma jikinsa illa, idan kuma ba'a gaggauta yin wani abu ba zai iya rasa ransa duk da a yanzu ma dai sai abinda ALLAH yayi. Hankalin su Malikat Bushirat da gaba ɗaya ta gama fita a hayyacinta ya sake tashi, dan gani suke ma Tajwar Eshaan ya rasu ne likitocin na ɓoyewa ne kawai. Saboda duk wanda ya ga a halin da aka samesa bazai taba sakankancewa zai rayu ba. Malikat Haseena tsohuwa mai ƙarfin hali da jarumta, duk da yanayin da nata jikin yake bata gaza nuna ƙoƙarin ta ba. Da taimakon Daneen Ammarah aka maida Iffah dake matsanancin kuka tamkar wadda ta zautu sashenta, suna shiga ta riƙo kafaɗunta cikin tashin hankali tana mai girgiza ta, “Ibnati kice min ba haka bane kar zuciyata ta buga, dan ALLAH ki faɗa mana gaskiya miya samesa, minene ya faru?”. Babu alamar Iffah zata kare kanta, sai ma wani irin karkarwa da jikinta ya farayi hawaye na rige-rigen sakkowa a kumatunta. Sai ma kawai ta tafi luuu ta zube ƙasa.... ★A firgice Iffah ta farka daga barcin da likita ya sakata na dole. Dan tun bayan shafa mata ruwa ta farfaɗo yanda take kuka da surutai sai tai kamar wadda ta zautu. Daneen Ammarah da ke kallon al'amarin nata matsayin ruɗani ne suka saka doctor danƙara mata allurar barci gudun kar wani abu ya samu brain ɗin ta. Saurin riƙota tai cikin muryarta data sha kuka ta shaƙe take faɗin, “Ibnati kwantar da hankalinki...” “Mamy hankalina bazai taɓa kwanciya ba. Dan ALLAH a wane hali yake? Ya rasa ransa ko? Ku kaini na sake ganinsa karki ce a'a dan ALLAH Mamy”. Duk wanda ya ga yanda Iffah ke jero waɗan nan tambayoyi yasan har yanzu a birkice take, dan tuni hawaye sun sake ma fuskarta kaca-kaca. Riƙota Daneen Ammarah tai ta rungume itama tana nata hawayen... A tsawace Jasrah data faɗo musu babu zato ta bama jami'an dake a bakin ƙofar izinin shigowa ɗakin. Daneen Ammarah tai saurin dakatar da ita itama a ɗan zafafe. “Jasrah!! Ki dawo cikin hankalinki, idan kin manta bara na tuna miki. Ita ɗin Zawjata-almilk ce, ba hadimar daular ruman ba, ba ɗakin barcinta ba koda falonta haramunne shigarsu.....” Itama Jasrah cikin rufewar idon ta tari numfashin Daneen Ammarah “Nima idan kin manta bara na tunatar dake Daneen Ammarah. Ada wannan abar ke amsa sunan da kike tunanin zai bata waccan darajar da kariya, a yanzu ko sunanta ƴar ta'adda, mai kisan kai, kisan kan ma na Shahan-shan.....” “Kin tabbatar da ita ta aikata?”. Ta katseta itama a fusace.. “Mikike buƙatar ji bayan wanda kunnuwanmu sukaji? Da wanda idanunmu suka gani?”. Rikici ne yake neman ɓarkewa a tsakaninsu, kowanne na ƙoƙarin ganin ya tabbatar da gaskiyarsa akan Iffah. Abune da bai taɓa faruwa ba, dan akwai girmamawa tsakaninsu musamman kasancewar shekarun Daneen Ammarah sama dana Jasrah. A yanda suke a fusace su duka ya sake hargitsa kan Iffah da gaba ɗaya ta daina gane komai, sai ma hajijiya da ke neman son sake zubar da ita a ƙasa tai nasarar jingina da bango..... ★.... A ɓangaren al'ummar ƙasar ruman kam dake faman zanga-zanga jin abinda ke faruwa hankali ya rabu gida biyu, wasu sun yarda harda shiga jimami. Wasu ko na kallon abin ta fiskar yaudara ne kawai Tajwar Eshaan ɗin na son ƙetare ƙasar ne saboda baya son yin murabus. Wasu kuma sun kasance ƴan babu manufa ne kawai. Ƙasa ta ɗauki ka-ce-na-ce tako'ina har wani bayajin zancen wani, haka ma kafofin yaɗa labarai da social media. Duk yanda suka so jin bakin likitocin da suka dubashin hakan bai yiwu ba, sai dai an sami hatsabibin da ya haɗa guntun bidiyon cewar Shahan-shan babu lafiya kai babu ma alamar yana raye. Wannan video shi yay rugugin amsa kuwa cikin ƙankanin lokaci a kowace kafar ƴaɗa labarai na ƙasar. Duk da ɗan jaridan abinda yay kuskure ne sai wannan bidiyo ya zama tamkar alkairi, dan kuwa ya sauya labarin Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed daga azzalumin da bai son yayi murabus zuwa abin tausayi da fara tunanin anya kuwa babu wani abu a ƙasa da mutane ya kamata su sani?. Cikin ƙankanin lokaci bakin ƴan jarida da masu rajin faɗa aji suka fara fashin baƙi akan al'amarin, daga sauran talakawan ƙasa ma kowa nata faɗin al'barkacin bakinsa, wasu ɓangarori na mutane kuma suka fara binsa da addu'ar fatan alkairi da samun lafiya.. ★★..... Al'amarin fa tamkar wasa ƙaramar magana ta zama babba. Tabbas a yanda su Miran Jasim sukai shiri na gaske akan Iffah bata da wata mafita ta kowanne mahanga, sun kuma tsaya tsayin daka wajen nuna ƙarfin iko da tabbatar da Miran Jasim matsayin magajin kujerar Tajwar Eshaan har lokacin da ALLAH zai bashi lafiya shine zai cigaba da jan ragamar mulkin sarautar Shahan-shan. Wannan damar dake a hanunsu sukai amfani wajen damawa aka miƙa Iffah zuwa cikin kurkukun masarauta. A gefe kuma masarautar ta ɗauki ɗumi fiye da na sanda ake zanga-zanga kan murabus ɗin Tajwar Eshaan. Kowa faɗin albarkacin bakinsa yake, masu goyon bayan Iffah da ganin ta ƙarasa musu abinda suke burin gani, da masu zaginta da ganin gangancinta, da masu yima su Malikat Haseena ALLAH ya ƙara a cewarsu sun fifita lamarin Iffah fiye da Zawjata-almilk na baya da suka rasa ransu. Surutai dai kala-kala sai wanda kunnenka yaso ji. Dan har zuwa dare babu alamar masarautar zata lafa sai ma fita gari da maganar ta farayi har wasu kafafen yaɗa labarai sun fara tsegunta zancen a kaikaice..... ★...........★ Zuwa safiya daular ruman ta gama cika tako ina da sarakuna na jihohi dan labari ya gama karaɗe ko'ina. Dole amintaccen likitan Tajwar Eshaan da suka kwana kansa ya tattauna da manema labarai dan kwantar da hankalin mutane bisa umarnin Malikat Haseenat. Ya tabbatar da Tajwar Eshaan ɗin na raye, an kuma sami nasarar daƙile dafin macizan da aka shayar da shi a cikin madarar da bincikensu ya tabbatar musu. Sai dai zai cigaba da karɓar magani zuwa wasu ƴan kwanakin da zasu iya ji daga garesa. Hankali ya ɗan kwanta kaɗan, nanfa aka shiga jera masa addu'oin samun lafiya tamkar ba suke zanga-zanga yay murabus ba. Sai dai kuma ga wasu hankalinsu ya sake tashi ne. Dan Wannan sauyi da aka samu saɓanin abinda sukai hasashen faruwa ya matuƙar tada hankalinsu. Saboda tun da Malikat Haseena ta bada umarnin sanar da ƴan ƙasa halin da Tajwar Eshaan ɗin ke ciki Miran Jasim da Miran Arshaan suka kasa zaune suka kasa tsaye. Sunbi wasu hanyoyi ta ƙarƙashin ƙasa domin daƙile fitar zancen ga al'ummar ƙasar ta ruman sai dai hakan ya gagara, dan Malikat Haseenat ta tsaya tsayin daka tare da rufe idonta wajen ƙin ganin komai sai ƙoƙarin wanke Shahan-shan ɗin ga talakawansa... ★★...... “Dole ne mu gaggauta sake salo muma, dan a wannan gaɓar idan har muka bar shaiɗanin yaron nan ya tsallake to mufa bazamu tsallake ba”. Miran Jasim ne mai maganar hankali tashe yana faman kai kawo. Cikin gamsuwa Miran Arshaan ya amsashi da faɗin, “Kafin hakan dole ne mu fara kauda yarinyar nan. Dan barinta itama tamkar kashe maciji ne bamu sare kansa ba. Dan na tabbata zuwa yanzu ta dawo hankalinta kamar yanda Barbushi ya tabbatar mana abinda yay mata bazai jima a jikinta ba. Kaga kuwa a ƙalla yanzu muna da kusan awanni takwas da faruwar komai, na kula kuma tsohuwar can son dawo da martabar jikanta take yi kawai ta amfani da wannan ciwon”. “Haka ne, kaima kayi magana mai ƙyau. Amma kasheta a wannan gaɓar bazai yiwu ba, dan in har muka aikata hakan zai ƙara tabbatar ma mutane abinda tsohuwar ke son a duba, kuma zai sake ɗaukaka darajar jikan nata dan na kula hankulansu ya fara dawowa kansa duk da ƙoƙarin da mukai na munana shi a zukatansu. Na rasa mi wannan matsiyacin yaron ya taka haka? Haka shima fa ubansa ya dinga wajiga rayukanmu”. Ƙwafa Miran Arshaan yayi mai haɗe da cije lips. Cikin takaici da nuna jin zafi yace, “Lokaci yayi da zamuyi yaƙi na gaske wajen shafe babin duk wanda yay ƙoƙarin cigaba da kasancewa a gaban nasarar mu. Ba Eshaan kawai ba, hatta tsohuwar can da uwarsa lokacin kasancewar su larihi yayi”. Wani banzan murmushi Miran Jasim ya saki yana mai kallon Miran Arshaan ɗin, a zuciyarsa kam faɗi yake (Har da kai a cikin wannan lissafin Akhi. Dan bazan taɓa hawa karagar mulki da wani maƙiyi shaƙiƙi ba) a zahiri kam sai ya ɗan bubbuga kafaɗar ɗan uwan nasa murmushi kwance a fuskarsa. “Shiyyasa bazan taɓa daina alfahari da kai ba”. Murmushi shima Miran Arshaan ɗin yayi, a tashi zuciyar yana ayyana (Kwanaki kawai zakai na ɗan-ɗanar mulkin da ka kwashe tsahon rayuwarka kanayi, dan bazan taɓa bari ka wuce kwanan wata ɗaya ba. Ni kaɗai na dace da cancantar zama magajin daular ruman) a zahiri kam kaɗa kansa yayi har da ɗan risinar da kai alamar girmamawa yana murmushi.........✍️ Hummmm. barkanmu da sake dawowa filin daga ƴan uwa. Barkanmu da salla kuma. Ya ibada? ALLAH ya sa muna cikin bayin da aka ƴanta, ya yafe mana kurakuranmu. Ya biya mana buƙatunmu na alkairi. UBANGIJI ka sadamu da rahamominka marasa yankewa. Fatan alkairi a gareku baki ɗaya🥰😍😘🙏. *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (002) ........Murmushi ta saki mai sanyi bayan gama sauraren dogon bayanin nasu, ta ɗan muskuta zamanta na ƙasaita cike da ƙarfin hali da sake bayyanar rauninta na tsufa da halin rashin ƙarfin jiki da jiyyar kwana biyu ta haddasa mata. Malikat Haseenat kenan tare da manyan masu faɗa ajin masarauta da suka buƙaci zama da ita akan lamarin Iffah da suke buƙatar shiga kotu domin yanke mata hukunci dai-dai da abinda ta aikata bisa tunzurawar Miran Arshaan da Miran Jasim. Cikin dattakonta da ƙasaita ta sake jan numfashi a karo na biyu idanunta akan su Miran Jasim, sai kuma ta ɗan kaudasu tana jinjina kai. “Bazan hana ko dakatarwa ba akan gurfanar da mai laifi irin Zawjata-almilk. Sai dai a nawa adalcin ina bada ƙwarin gwiwa da shawara ga masu zaman shari'ar bin komai a sannu da yin ƙwaƙwƙwaran bincike. Sashen Shahan-shan dai zagaye yake da ƙyamarori, hakama madarar da aka tabbatar ya sha tana buƙatar musan daga ina ta fito, shi kansa dafin data zuba waya samar mata da shi har ya shigo cikin masarautar nan?. Abu na ƙarshe shine bata tsaro na musamman da saka idanu a dukkan abinda zata ci. Dan in har wani abu ya sami yarinyar nan batare da gaskiya ta fito ba a tabbata hukunci zai koma hannuna, kuma zan iya zartar da shi akan kowa. Idan nace kowa ina nufin kowa ma koda nice a karan kaina”. Babu wanda ya iya tari a falon sai jinjina kawuna kawai suke. Yayinda Malikat Haseenat bata sake tofa komai ba sai ma ƙoƙarin barin falon da tai ta hanyar gara wheelchair ɗinta da remote ɗin jikinta (nace kaga ƴan gatan duniya lols😉). Da kallo suma kawai suka bita babu alamar wani zai ce har lokacin. Sai dai zukatan wasu tamkar zasu kama da wuta dan baƙin cikinta, ji suke kamar subi dare wajen mata yankan rago su zubar da jinin banza. Wasu ko gamsuwa sukai da bayanin nata, dan dama sunbi wannan ayarin ne kawai saboda rashin ƙarfin cewarsu, amma da za'a basu zaɓi sunfi buƙatar ayi haƙuri ma har Shahan-shan ya ƙarasa samun lafiyar da kowa ke fata..... ★★★..... Kusan a tare suka iso falon kowa ransa a dagule. Sai faman huci suke kamar wasu zakuna. Tamkar basuga juna ba suka fara kaikawo kamar masu safa da marwa. Sunyi haka ya kai sau hur-huɗu kafin Miran Arshaan ya dakata cikin ƙunar zuciya ya furta, “A wannan gaɓar maciji muka kashe bamu sare kansa ba. Kauda wannan yaron a bayan rayuwar wannan tsohuwar sunansa BAYA DA ƘURA....” “...Idan har barin wadda rayuwa ta zame mata saura ƙiris a zahirance zai amsa suna baya da ƙura to cigaba da numfashin waccan yarinyar sunansa BAYA DA TARNAƘI”. Miran Jasim ya katsesa a zafafe shima. Tsaye sukai sunama juna kallon kallo. Kafin Miran Arshaan ya katse shirun ta hanyar faɗin, “Tsuntsayen biyu jifa iri ɗaya suke buƙata. Inba haka ba a cikin ƙarfin iko za'a tabbatar da ƙarfafa mai rauni”. “Na tabbatar da hakan ta hanyar gani da ido, kunnena kuma sun jiye min tabbacin AKWAI WATA A ƘASA bayan tatsuniyar gizo da ƙoƙi”. “Miye mafita?!”. Cewar Miran Arshaan cikin tarar numfashin Miran Jasim. Miran Jasim ɗin ya kafesa da idanu yana sakin wani murmushi. “A wannan gaɓar jifar tsuntsu huɗu da dutsi ɗaya ne ba biyu ba”. Jimmm Miran Arshaan yay yana kallonsa, dan a saninsa da hasashensa tsuntsayen da ya kamata su jefa uku ne kawai ba huɗun ba. Sai dai kafin yace komai Miran Jasim ɗin ya katsesa da sake faɗin, “Tabbas huɗu ne, sai dai zamu fara kauda ukun kafin cikon na huɗun, dan haka dole ne a gobe mu ziyarci Barbushi”. Miran Arshaan zai yi magana sai kuma ya haɗiye, batare da ya ƙara tofa komai ba ya nufi hanyar fita yana faɗin, “Asuba ta gari”. Da wani mugun kallo Miran Jasim ya bisa, yayinda shima Miran Arshaan ɗin ya fice yana taunar lips tabbacin da nasa ƙudirin shima. (Nace “Hummm”). ★★..... Yau kwanakinta uku cif a cikin ɗakin da aka garkameta mai tsananin duhu da bata iya banbance dare da rana, sai ɗan hasken da kan leko ta window dake can sama karami na hasken rana ko wutar lantarki. Ta matuƙar zama wujiga-wujiga da fita a hayyacinta dalilin ƙin cin abincin da ake kawo mata sau ɗaya a kowane yini, sai madara. Tun a ranar farko ta gama fahimtar akwai babban ƙuli da ya kamata ta fara fahimta kafin zuwan wannan lokacin. Zuwa yanzu ta gama fahimtar su Miran Jasim sunyi amfani da ita ne, sunyi amfani da ita duk da itama da wannan ƙudirin a ranta. Sai dai kuma cika baki ne kawai, ta fahimci a hakanne a randa ƙaddarar dake tafiya da rayuwarta ta yanzu ta tabbata. Dole ta kira hakan da ƙaddara, dan inba ƙaddara ba babu ta yanda zata iya cutar da waninta mai bautar ALLAH da hanunta. Ƙwarai da gaske tanajin zafi, matuƙar zafi na rasa ƴan uwanta guda biyu a dalilin auren Shahan-shan. Hakan kuma shine ya zama sanadin komai na jin kangarewar zuciya da ƙudirin da babu tabbacin iya aiwatar da shi. Komai ya nema canja mata a lokacin da tai tozali da fuskarsa, bata san dalili ba ta dingajin kamar shi bazai iya kasancewa mai cutarwa ba, ta dinga jin dole akwai abinda yake ɓoye da ya kamata ta sani, sai dai a lokacin data gama shirinta tsaf akan hakan ƙaddara ta sake sauyata, komai ya nema rushewa a zuciyarta batare da riƙe wata makama mai ƙwaƙwarar hujja ba ta yanke hukunci ga wanda bata da wata hujja ko shaida akansa, wanda maimakon ya bada umarnin ɗaukar mataki a kanta ya nuna mata hanyar kuɓuta ta hanyar bata umarnin zubar da madarar da bata san yanda akai takaita gareshi ba. Amma kash, da alama ƙoƙarinsa na kubtar da ita bai tabbata ba. Dan gashi maƙiyansu da alamu suka nuna shirinsu bana yau bane sun gama cin nasara, nasara biyu a lokaci ɗaya, kaudashi da kaudata itama batare da ta san mi taci burin son sani ba. Sai ma sake tsunduma a duhuwa tayi. Dole ta kira gaɓar da suna duhuwa, dan tanada tambayoyi masu ɗunbin yawa akan kanta ma. Mafi girma a ciki sune taya Ajmaal ya zama Shahan-shan? Wake halaka matansa idan har ya kasance ba shi bane? Miyasa bai iya cewa komai bayan shine keda hakkin cewar? Da gaske ta rasa iyayensu suma da ɗan uwanta tilo daya rage kokuwa duk cikin shirin su Miran Arshaan ne?.... Shi kansa Sir Fawzan tana da bukatar sanin wani abu a kansa. Sai dai ta yaya? Ta wace hanya? Duk yanzu bata sani ba. Zafafan hawayen da a kwana ukun nan bata taɓa gwada sharewa ba suka sake zubowa masu zafi. Ta lumshe raunanan idanunta murmushi mai ciwo na suɓuce mata. Fuskarsa take kallo a kan allon zuciyarta a lokacin da yake sakar mata murmushin da har abada bazai taɓa zama mai gogewa ba a tarihinta. Siririyar dariya da tafin dake shiga kunnenta a bazata ya saka ɓacewar murmushin kan fuskar tata da buɗe lumsassun idanun nata lokaci guda.. Kanta ne ya sara da ƙarfi, da sauri ta maida su ta rumtse sakamakon hasken daya ratsasu mai kaifi, yau kwananta uku tana a cikin duhu, dolene karfin idanunta ya samu rauni a lokacin da aka samar da haske cikinsu. Duk yanda taso sake buɗewa ta kasa, dan har cikin kwakwalwarta taji shigar kaifin hasken na bazata. Ta cije lips a hankali tana mai ƙoƙarin ganin ta riƙe hawayenta da son danne tasirin raɗaɗin dariyar izgilancin da bata san daga wanda take fita ba. Sai dai zuciyarta na bata Miran Jasim ko Miran Arshaan ne. Bata da ƙarfin tashi daga kwancen da take, dan haka tai jarumtar sake buɗe idanun nata sannu a hankali a karo na biyu, zuciyarta na ambaton (Hasbinallahu wani'imal wakil). Da ƙyar ta iya tsaidasu akan Miran Jasim dake zaune ƙafa ɗaya kan ɗaya bisa kujerar da basai tayi wani tunani ba da ita aka shigo masa. Raɗaɗi idanun ke mata, gasu a kumbure jajur amma haka tai jarumtar cigaba da tsaidasu a kansa harya gaji dan kansa daga dariyar yay shiru.. _“Zawgatu al-ibn! (Daughter in-law) proud of you. Kin zama ta daban a cikin dubun da bazan so na manta ba. Duk da nima dai nasan ban cancanci ki manta ni ba ta sauƙi, na san na cancanci zama abin alfaharinki a yanzu. Cikin sauƙi na cika miki burinki, gaskiya na cancanci karɓar tukuyci na musamman. Koda yake kwantar da hankalinki bama sai kin bani komai ba, zamanki anan ma babban tukuyci ne. Zan sake faɗa “Ina al'fahari da ke”. Yay wata ƴar dariya mai ƙona zuciya dake shiga har ƙarƙashin zuciyar Iffah, amma kasancewar ta jarumar gaske mai ƙarfin zuciya sai batako motsa ba, raunanan idanunta kuma har lokacin suna a kansa duk da raɗaɗin azabar shigar haske dake ratsasu har yanzu. Dan kansa ya tsagaita da dariyar tare da gyara zamansa yana binta da wani shegen kallon ƙurulla har yana lasar lips ɗinsa kaɗan. “Bana son ki kalleni da irin kallon da nake da yaƙinin shine a allon zuciyarki Zawgatu al-ibn!. Ina son ki dai fahimci ni ɗin mutum ne mai son kansa, zan kuma iya kauda koda yatsan hannuna ne in har zai iya zame min cikas domin samun cikar burina”. Yay wata ƴar dariya a zahiri, a can ƙasan ransa kam kallon da Iffahr ke masa ko ƙiftawa babu yay masa tsaye a kan allon zuciya, amma kasancewar sa gwani sai ya shanye babu alamun hakan a kan fuskarsa. Sai ma miƙewa yay cike da kasaita, a gabanta yaje ya tsugunna tare da kai hannunsa fari sol zai shafa fuskarta. Cikin wata irin zabura da ƙarfin da Iffah bata san yay ragowa a jikinta ba taja da baya tana watsa masa wani mummunan kallo har hucinta na bayyana akan hancinta. Murmushin gefen baki yay da lumshe idanu, sai kuma ya janye hannun nasa cikin ɗage kafaɗa da son basarwa. Idanun ya sake lumshewa da buɗewa a kanta yana shu'umin murmushin dake sukar zuciyar Iffah matuƙa. “Hakan ma ya burgeni Zawgatu al-ibn”. Harara ta watsa masa kai kace idanun zasu faɗo, cikin kaushin muryar da ke fita da ƙyar ta fara magana a karo na farko cike da gargaɗi. “Kai fagalalle ka rubuta ka ajiye, a duk ranar da koda ɗan yatsan ka yay kuskuran taɓa jikina ni Fhareedah bint Zayyan na maka alƙawarin karyasa, karaya irin wadda har kabar duniya tabonta bazai goge a idanunka da zuciyarka ba. Iffah babban goro ce sai magogin ƙarfe”. Tabbas maganarta ta matuƙar sukarsa, ta kuma zauna daram bisa zuciyarsa tamkar rubutu akan dutse, amma a zahiri sai ya murmusa harda lasar lips a karo na biyu. “Immm bazance kinyi ƙarya ba kam, nima shaida ne ke ɗin babban goro ce, kuma tabbas sai ni magogin ƙarfe. Ina miki albishir daga yau ki fara takaba da irga kwanakin zamowarki babban goro ta magogin ƙarfe ni Shahan-shan na ƙasar ruman Tajwar Jasim ibn Abdul-majeed Aliy! Nayi alkawarin sai na maidake karuwar da zata zama a ƙololuwar abin kwatance a duniya duka bama ƙasar ruman kawai ba. Daga yanzu kisa a ranki ƙaddararki ta fara a hannuna hhhh!!!”. “hhahhaha!!!”. Itama Iffah ta fara dariyar kamar yanda yake yi, sai dai tata cike da ƙarfin haline kawai. Tsagaitawa yayi da tasa yana kallonta cike da mamakin da yake ƙoƙarin dannewa, sai dai kuma fuskarsa na ƙoƙarin fallasa shi. Ganin bata da alamar tsagaita dariyar tata ya miƙe cikin zafin rai.... “Alfahari da ƙaddara akan Fareedah rauni ne ai Aam! Dan ƙaddarar itace hasken fitilar nasarar Iffah. Ƙyaƙyƙyawan mafarki Uncle”. Ta ƙare maganar da cigaba da dariyar da tafi ta farko saka ƙuna a zuciya. Miran Jasim dake tsaye cak shi bai fitaba shi bai dawo ba yay wani irin cizar lips, sai kuma ya fice cikin zafin nama dan har ƙarƙashin ruhinsa dariyar Iffah ke shigarsa.. Sai da ta daina jin takun sawunsa gaba ɗaya da kulleta da aka sakeyi sannan ta tsagaita itama, a maimakon dariyar sai ta fashe da kuka mai tsuma zuciya. Ta tabbatar duk abinda Miran Jasim ya faɗa zai aikata mafiyinsa, sai dai ba tana kuka bane akan kanta, tana kuka ne a maimakon talakawan ƙasarta da Tajwar Eshaan bin Haysam Abdul-majeed. Tana kuka ne akan tsananin buƙatar son sanin zahirinsa da baɗininsa da su Miran Jasim suka zaburar da ita. Sai dai tasan guri ya ƙure, ƙurewa irin ta numfashi da ƙarewar rayuwa. Koda ace shi ya rayu ita bazata rayu ba, koda ace wasun sa na buƙatar ta rayu ita bata buƙatar rayuwar a halin yanzu.........✍️ (ALLAH sarki Iffah 😭🙏). *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (03) ......Kamar yanada Malikat Haseenat ta faɗa an sake tsaurara tsaro a ɗakin da Iffah take, bana dakaru kawai ba harda tarin jami'an tsaron da Shahan-shan kawai suke bama tsaro tako ina yayinda ta kasance cikin masu iya bibiyar komai kai tsaye. Shi kansa abincin da ake kai mata a yanzu ya kasance na musamman dake samun saka ido, dan a rana ta biyar da yunwa ta nema mata illa sai dai likita ya shiga ya dubata. Dan dole ta koma cin abincin sai dai bata wuce lauma uku ko kurɓa uku na madara take ta ajiyewa.. ....A ɓangaren masu faɗa ajin masarauta ana ta cigaba da tattara bayanan da suka kamata ta hanyar bincike. Sai dai tsaiko na farko da aka fara samu shine rasa cctv footage na sashen Tajwar Eshaan da ga asubahin randa al'amarin zai faru har zuwa lokacin isar su Daneen Ammarah da su Miran Jasim sashen. Sai wayar Iffah da itama aka nema ƙasa da sama aka rasa da lap-top ɗinta. Wannan al'amari ma ya kawo ka-ce-na-ce bana wasa ba har takai jami'an tsaro cafke mai kula da ɗakin tsaron aka garƙame. Amma kuma juyin duniya yace bai san yanda akai ba. Hakama hadiman sashen Iffah kaf ɗinsu an tattare, suma kuma sun rantse sun kuma basu san yanda akai wayar Iffah da lap-top ɗin sukai ɓatan dabo ba. Ba kuma suga wani ya shigo sashen ba. Waɗan nan abubuwa na rashin makamar tabbatar da Iffah akan laifin da kowa keda yaƙinin ta aikata ya kawo rabuwar kai da rikici babban akan mata hukunci. Yayinda su Miran Jasim suka sha jinin jikinsu, dan haka suka zama ɓangaren masu nuna kawai a kashe Iffahn. Ɗayan sashen kuma da suka haɗa da zuri'ar Sayeed Khairul-Bashar suka bore akan bincike na har sai an tabbatar a kuma ji dalilinta dan in ma har ta aikata to dole akwai saka hannun wasu a masarautar. Rikici ne bana wasa ba, dan har takai anyi wani zaman a karo na biyu amma sam babu masalaha daga kowane ɓangare. Ɓangaren kuma dake ganin kashe Iffahn shi yafi sauƙi sune ɓangare mafi ƙarfi dan da yawansu na jikin Tajwar Eshaan ɗin ne. Malikat Haseenat ce kawai ke nuna a dai cigaba da bincike kar a aikata aikin dana sani. Hakama Daneen Ammarah sam zuciyarta taƙi aminta Iffah zata aikata bisa raɗin kanta, idan ma har ita ta aikata ɗin kenan tunda har yanzu babu wata shaida dake nuna itace ɗin ta bashi madarar dan bayan ita suma masu dafa masa abinci da amintacen hadiminsa duk suna a rufe. Ƙulle-ƙullen su Miran Arshaan ne yasa dukan zargin yafi ƙarfi akan Iffah. A yanzu haka kuma sunyi kane-kane wajen sake rura al'amarin da nuna ɗaukar zafi fiye da kowa musamman Miran Jasim daya kasance mai riƙe da masarautar har zuwa samun lafiyar Tajwar Eshaan da ake fata... ★★.... ★..... Har cikar kwanakin mako babu wani cikakken masalaha akan al'amarin, sai ma ɗaukar zafi da kowane ɓangare suka sake yi. Iffah kuma taƙi taɓuwa bisa jajircewar Malikat Haseenat na sai fa anyi bincike. Wannan kafiya ta saka Miran Jasim da Miran Arshaan kasa zaune da tsaye. Barbushi kuma ya tabbatar musu in har fa Malikat Haseenat na numfashi bazasu taɓa samun yanda suke so cikin sauƙi ba. Dan haka ya basu zaɓi biyu. Kodai su gaggauta kasheta da hanunsu, ko kuma suyi ƙoƙarin tunzura Malikat Bushirat dayin amfani da ita kamar yanda sukayi da Iffah ta kawar musu da ita. Hankalinsu ya tashi, dan kashe Malikat Haseenat abu ne ba ƙarami ba musamman a wannan gaɓar da take taka wata rawa mai banbanci da tasu duk da tafisu kusanci da Tajwar Eshaan. Duk yanda suka tattauna da aunawa sun gafa wannan hanyar mai wahala ce a gare su, dan haka suka zaɓi nufar sashen Malikat Bushirat ɗin domin fuskantar ta kai tsaye. Fatansu zaman ya zame musu jifan tsuntsu biyu da dutsi ɗaya, dan tunda aka fara rikicin nan Malikat Bushirat taƙi tofa komai ma, ta tattare hankalinta kacokan akan ganin lafiyar Tajwar Eshaan da aka hana kowa gani a masarautar sai ita da Malikat Haseenat har zuwa yau da ake cika kwanaki tara da faruwar komai....... ★... MALIKAT BUSHIRAT ★... Yanda take magana cikin fitar ɗacin sauti tana kaikawo a fusace zai tabbatar maka ranta a ɓace yake ƙololuwa. Malikat Bushirat kenan da tun faruwar al'amarin nan babu wanda zaice yaji bakinta duk wannan sa toka sa ƙatsin da akeyi. A yanzu babban burinta bai wuce samun lafiyar tilon ɗan nata ba, batun hukunta wadda ta zama sanadin komai wato Iffah kuwa duk faɗi tashin da ake komai tana sane, sai dai bata shirya saka baki ba a yanzu acewarta akwai lokaci. A tsahon kwanakin nan dukkan wani motsin masarautar ruman a cikin kunenta yake fiye da masu kai kawon. Hauhawa da bunƙasar ɓacin ranta na yanzu kam yana da alaƙa ne da tattaunawar ta da su Miran Jasim, zaman nasu kuma kacokan ya alaƙantu ne ga hana hukunta Iffah da Malikat Haseenat tayi kai tsaye har sai anyi binciken da ta sharɗanta. Irin wannan fusatar ga Malikat Bushirat shine fatansu, dan haka suka dubi juna cikin son danne murmushin kan fuskokinsu. Zama suka gyara tare da sake buɗe sabon shafin abinda suka faro. Miran Arshaan ya sake marairaice fuska mai cike da tsantsar damuwa yana mai duban Malikat Bushirat.. “... Ni a ganina ɓacin rai ko damuwa bashi ne zai zame mana mafita ba. Mu zauna mu tattauna yanda abinda ya dace kafin lokaci ya ƙure. Ban san miyasa Mammah ta ɗauka al'amarin nan da rashin muhimmanci ba. A yanda nake ji a zuciyata da tuni labarin wata akeyi ba yarinyar nan ba. Dan banga dalilin da zaisa ace wai sai anyi bincike za'ai mata hukunci bayan komai data aikata a bayyane yake, wannan tamkar muna nuna rashin muhimmancin ran yaronmu ne ma ai.....” “Gaskiya kam Arshaan Akhi”. Miran Jasim ya tari numfashinsa da sauri, cikin nuna ɓacin rai shima ya cigaba da faɗin, “Ni kaina komai na kasa fahimta musamman akan ra'ayin Mammah. Sai nake ganin bata damu bane? Ko kuwa tafi son yarinyar sama da gudan jininta? Inba hakaba minene na waɗan nan sharaɗin marasa tushe? Bayan komai a bayyane yake. To gashi tace sai anyi bincike, amma dai-dai da cctv footage an nema an rasa tabbacin komai shiri ne. Inada yaƙinin komai sai dai yarinyar nan ta shirya kafin ta shigo masarautar nan. Dan binciken mu ya nuna ta aurensa ne dama domin ɗaukar fansar ƴan uwanta guda biyu, shiyyasa ta kwantar da kai ta shiga jikinsu musamman Mammah da Akia Ammarah da a yanzu suke nuna goyon bayansu kan cigaba da rayuwarta sai kace sun manta matsayin wanda taso halakawa a gare su...” Maganganunsu sake hargitsa Malikat Bushirat suke da tunzurata. Tuni jin zafin Malikat Haseenat da tsanar Daneen Ammarah ya sake bunƙasa a ranta. Dama kullum Jasrah cikin munana Daneen Ammarah ɗin take a wajenta yanzu bisa huɗubar Miran Arshaan, dan tafi kawo mata zancen duk motsinsu a masarautar fiye da kowa, musamman daya kasance ra'ayinsu ya babanta da nasu akan hukunta Iffah. Yanda take sake kumbura jira suke kawai suji tace wani abu, amma kasancewar ta mace mai bahagon hali dama fahimta ko uffan da suke so bata tofa ba, sai cika take dai tana batsewarta ita ɗaya. Duk yanda suka cigaba da fanfatan kuma batace ɗin ba har lokacin samun damar ganin Tajwar Eshaan yay a gareta, dan tunda abin ya faru suma ɗin basu samu ganinsa ba kasancewar akwai doka mai haɗe da babban tsaro akan ganin nasa ga duk wanda ya kwana ya tashi a daular ta ruman, su kansu bisa tsayawar Malikat Bushirat ɗinne da itama sau ɗaya take da hurumin ganinsa a rana zasu ganshi yau ɗin. Duk wani motsi da shiga da fitar jama'a a ƙarƙashin saka idon masu tsaron sashen yake a yanzun. Tako ina ka waiga cctv camaras ne. Su kansu ma'aikatan cikin sanya ido suke a kowane motsin tsakaninsu dan a yanzu kowa bai yarda da kowa ba ake. Sun sami tarba daga ƙwararren likitansa daya kasa ya tsare, yana hakane kuma bisa umarnin Malikat Bushirat ɗin. Cikin girmamawa ya gaidasu, batare da damuwa da yanda suka amsa masa cike da isa da ƙasaita ba ya jagorancesu zuwa ɗakin da aka warewa Tajwar Eshaan ɗin domin jiyya. Ɗakine tamkar asibiti, dan komai zaka samesa na aiki ingantattu da kowace ƙasa zata iya alfahari da shi. Dan ƙasar ruman na ɗaya daga cikin ƙasashe masu ƙwararrun likitoci da duniya ke alfahari da su tako wane fanni. Hakan yasa hatta shi kansa Shahan-shan dan yana ciwo bai ƙetare ƙasar haihuwarsa, kai sai ma dai su azo tasu ƙasar neman lafiyar saboda ingancin su.... Zaune yake a gadon marasa lafiyar bayansa jingine da tausasan filo da jikin gado da aka ɗago, duk da ya ɗanyi rama ƙyawun haibarsa da kwarjini na manne da cikar kamalar fuskarsa. Yayi fayau da shi da ƙara hasken daya bayyana bakin kwantacciyar sumar kansa data kumatunsa zuwa haɓa, light blue ɗin kayan jiyyar da suma suka ƙara fitar hasken fatar tasa tar-tar ga mai kallo sun masa ƙyau kamar ya saka ne domin ado. Sai manyan idanunsa da har yanzu fatarsu ke a ɗan kumbure alamar dai yana cikin halin jinya. Duk da jin an shigo bai motsa ba idanunsa nakan lap-top ɗin da yake sarrafawa cike da nutsuwa da ƙasaita. Daga Miran Arshaan har Miran Jasim sukai turus alamar mamaki, dan sam zukatansu basu ayyana musu samunsa a haka ba musamman yanda likitansa yaƙi cewa komai game da zungurar da ƴan jarida ke masa akan son sanin halin da Tajwar Eshaan ɗin yake a yanzu. Saboda tun washe garin da suka tattauna da ƴan jarida basu sake cewa komai ba akan yanayin jikin nasa. Malikat Bushirat da hankalinta gaba ɗaya ke akan gudan jinin nata ta ƙarasa garesa fuskarta ƙawace da murmushi. Sai da taja kujera ta zauna a gefensa kaɗan ya ɗan ɗago saboda shigar ƙamshin turarenta cikin hancinsa.....✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔. (04) .......Kai tsaye ya sauke kumburarrun fararen idanunsa dake a ɗan shanye kanta. “Barkan ki Ammie”. Ya faɗa a hankali fuskarsa da ɗan murmushi kaɗan tamkar an masa dole. “Barka My Niger”. Ta amsashi tata fuskar na sake faɗaɗa da murmushin tsantsar kulawa da soyayyar da take masa. Idanunsa ya lumshe ya sake buɗewa a kanta, dai-dai ta juya gasu Miran Jasim dake tsaye tamkar gunkinan da aka ajiye domin tarihi. Shima a karon farko ya ɗan juya nasa idanun zuwa garesu. Mara gaskiya ko'a ruwa gumi yake, haka kawai sai kaifafan idanun nasa da rauninsu ke a bayyane sukai tasiri garesu. Da ƙyar suka iya ƙoƙarin danne tsarguwarsu da bugun da zukatansu keyi a ƙirazansu. Kasancewarsa mutum mai kaifin tunani da saurin karantar yanayi tuni ya karancesu tsaf, ya risinar da idanun yana ƙoƙarin haɗiye murmushin dake neman suɓuce masa. Cike da basar da yanayin nasu ya marabcesu da sannu da zuwa. Sun saita kansu da ƙyar wajen amsawa fuskokinsu na ƙoƙarin bayyana damuwarsu mai ɗauke da tsantsar kulawa da takaici. Malikat Bushirat da gaba ɗaya hankalinta ke kan Tajwar Eshaan ba fahimtar yanayin nasu tai ba ta sake juyowa garesu tana murmushi mai faɗi da amsa gaisuwar ya jiki da sukai masa sai dai bai amsa ba ya basar kamar bai jiba. “Ai jinkin nasa Alhamdullah, duk da dai doctors ɗin sunce sai sun masa aiki nan da wasu kwanaki. A yanzu haka suna kan bashi magani dafin gubar na tattare kanta waje guda dan ta macizan dai anci nasarar daƙileta.” Zancen nata ya matuƙar dukansu a zuciya, sai dai ta wani gefen ya sakasu a farin ciki. Amma sai suka danne komai wajen nuna jimami da tsantsar takaici da damuwa. Tare da aibanta Iffah da tabbatar da sai sun saka dukan zuri'arta a nadama Bama ita kawai ba. Babban burinsu kawai ALLAH ya basa lafiya ya koma karagar mulki. Kalamansu sun sake tunzura fushin malikat Bushirat a bayyane, sai dai kuma batace komai ba kamar yanda shima Tajwar Eshaan ɗin bai tanka ba, hasalima tun fara zancen nasu ya ɗan kai dubansa ga likitansa dake a ɗakin shima, dan ƙa'idar zaman nasu a ɗakin sai da shi. Da idanu ya masa magana. Doctor Afif ya jinjina kansa da takowa gaban gadon ya janye ɗan tabir ɗin da aka saƙala ta samansa ya ɗaura lap-top ɗin da yake sarrafawa. Gefe ya maida shi ya kife fuskar laptop ɗin. Daga haka ya kwantar masa da gadon kaɗan da remote, shi kuma ya ɗan gyara kwanciyarsa ya maida idanunsa ya lumshe. Bai sake buɗesu ba balle ya tanka duk maganganunsu, duk da kuwa yana jinsu sarai.... ★★.... ★.... “Anya kuwa matsiyacin yaron nan ba akwai abinda yake ɓoyewa ba kuwa?”. Miran Arshaan ne ya faɗa cikin tashin hankali da kaikawo. Barowarsu daga sashen Tajwar Eshaan kenan, Malikat Bushirat ta nufi sashenta suma suka nufi na Miran Jasim dan akwai tazara a tsakaninsu da ita. Miran Jasim da shima irin abinda ke ran Miran Arshaan ɗin ne a zuciyarsa ya taune lips da masifar ƙarfi. “Akhi nima inajin hakan a raina, sai dai na kasa ɗaura dukan motsinsa a mizanin daya dace. Kaima kasan yaron nan hatsabibin kansa ne fiye da mahaifinsa, dole ne mu koma wajen Barbushi zuwa safiyar gobe dan muna buƙatar ganawa ta gaggawa da shi”. “Wannan shine dai-dai. Amma tilas tafiyarmu ta kasance tare da babban shiri, dan muna buƙatar gusar da yarintar can itama kafin mudawo garesa”. “Babu damuwa, dan yanda nake jina ko a yanzu akace nikam a shirye nake. Amma asubancin ma yayi”. Kamar yanda suka faɗa hakance ta kasance. Sai dai a daren sun gana da ɗaya daga cikin Doctors ɗin dake kula da Tajwar Eshaan ɗin, sun kuma jima suna tattaunawa da babu wanda yasan akan minene. Da safen suka sami damar sake shiga duba Tajwar Eshaan bisa jagorancin Malikat Bushirat da suka sake maƙalewa, sai dai sun samu ma yana barci. Dole sukai sallama da Malikat Bushirat ɗin dan ita a sashen take yini ma yanzu. Duk da sun so jin abinda ke bakinta basu sami damar ba. Dan mace ce mai zurfin cikin tsiya da zamu iya cewa Tajwar Eshaan ya gada a gareta ga miskilanci...... ★★...... ★..... A safiyar basu sami damar barin masarautar ba zuwa ga Barbushi kamar yanda sukaso saboda zuwan baƙi. Sarakunan ƙasar ruman gaba ɗaya ne suka sake zuwa domin ƙara duba jikin Tajwar Eshaan. Inda wannan dubiya ta bama al'ummar ƙasar ruman damar sanin yanayin jikin Shahan-shan ɗin. Dan Alhamdullah har fitowa yay falon da akai musu masauki. Yayi zaman kusan mintuna talatin da su, lokacin da yake miƙewa domin komawa kunnensa ya riski matsananciyar hayaniyar da ke ɗan tashi sama-sama kamar daga wajen masarautar. Da farko baiyi mamaki ba, dan tunanisa har yanzu waccan zanga-zangar ba'a dainata ba. Sai dai ya ɗan dakata daga yunƙurin barin falon ya kai dubansa Sayeed Fayzul-haq daya jagorancin shigowar sarakunan garesa. Cikin sauri ya matso garesa kansa a risine cike da girmamawa. “Amincin da kariyar UBANGIJI su cigaba da gadinka ya adalin shugabanmu ko ana bukatar wani abu ne?”. Shiru kamar bazai ce komai ba, sai kuma ya nisa a hankali tare da ɗan lumshe idanunsa ya sake buɗewa a kansa. A kan lips ɗinsa ya furta, “Akwai abinda ke faruwa ne bayan wanda na sani?”. “A sani na dai babu wani sabon abu, sai dai idan akan waccan hayaniyar ne ƴan jarida ne ke cike da nacin son sanin yanayin jikinka kamar yanda al'ummar ƙasar ruman ke ƙulafuci suma. Duk da kullum cikin jeren zuwa suke ƙofar masarauta dama, amma yau ganin baƙi suke tunanin zasu sami abinda suke so shine suka taru fiye da kullum. Shine jami'ai ke ƙoƙarin hana dukkan hanƙoramsu ta hanyar sake tsaurara tsaro”. “A tara taron manema labarai zanyi magana da su zuwa gobe Insha ALLAH”. A firgice, a razane, a kuma ɗimauce Sayeed Fayzul-haq ya ɗago batare da ya farga da abinda yay ɗin ba. Dan wata irin saukar tarnatsa kalaman Tajwar Eshaan ɗin da suka fita a bazata sukai a cikin kunensa. Tabbas bashi kaɗai ba ga duk wanda zaiji dolene al'amarin ya firgitar da shi, dan abune da bai taɓa faruwa ba kai tsaye kamar haka a ƙasar ruman. Koda Shahan-shan nada buƙatar ganawa da manema labarai sai dai ya wakilta waninsa bisa umarninsa ya tattauna da su da yawunsa. Amma duk da Tajwar Eshaan ɗin bai fito yace shine zai tattauna da su ɗin ba a yanzu Sayeed Fayzul-haq ya girgiza ƙwarai matuƙa. A cikin abinda bai wuce awa guda ba wannan saƙo na Tajwar Eshaan ya shiga karaɗe lungu da saƙo na ƙasar ruman da kewaye. Ko'ina ka leƙa zancen da ake kenan Tajwar Eshaan zai zauna da manema labarai a safiyar gobe insha ALLAHU. Kowa burinsa gari ya waye kawai, ba ƴan jaridar ba ba talakawan ba, hatta da manyan ƙasar ma masu manufofi daban-daban sun shiga jerin masu jiran. A daren shugabannin ƴan jarida na ƙasar ruman suka buƙaci zama na gaggawa, dan dolene su tattauna abinda ya dace kasancewar akwai tambayoyi fal zukatan al'ummar ƙasar ruman da ke son a amsa musu, kuma daga bakin Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed suke buƙatar ji duk da basu da tabbacin samu saboda abune mai matuƙar wahalar gaske kowa ya sani...... ★•••• ★••••• Hankali a tashe suka iso ga Barbushi. Duk da tsalawar dare da na duhuwar jejin babu alamar tsoron abin cutarwar tattare da su saboda bushewar zukata. Hasalima su ba abinda zai basu tsoro anan bane damuwarsu. Wanda ya wuni basu tsoro da zama cikin wasi-wasi na rashin makamar riƙewa ne matsalarsu. Boka Barbushi da ƙazanta da dattin kafirci yay ma fuskarsa da gangar jikinsa ƙawanya ya tuntsire da wata irin mahaukaciyar dariya da sai da ta ƙular da Miran Arshaan da Miran Jasim. Sai dai basu nuna ba balle damar cewa wani abu. Sai da yay mai isarsa kafin ya tsagaita da maida hankalinsa garesu. Basu da matsala akan faɗin abinda ya kawosu, dan sunyi imanin ya san komai hatta gaibu (wa'iyazubillah 😭🙏), sakamakon idan sun zo wajensa tun kan su faɗi abinda ya kawosun shike zayyane musu. A yanzun ma dai yana rufe bakinsa daga dariyar tasa ya fara zayyano musu.... “Sarƙa-sarƙar sarƙaƙiya ce mai cike da mugun ƙullin dake ɗaure da kowa. Babu mai iya gane tushen farawarta balle kamo bakin zaren ƙarshenta kasanwar anyi komai a cikin duhun da idanun kowa bazai gani ba ko wanene shi a hatsabibanci. Ina mai tabbatar muku shi ɗin hatsabibi ne ƙwarai da gaske. Kuma tabbas a yanzu ne aka fara wasan hhhhhhhh!!!! Hahahahahahaha!!!!...” Yanda mummunar daiyarsa ke amsa kuwwa a jejin haka sautin bugun zukatan Miran Jasim da Miran Arshaan ke bada nasu sautin a ƙirazansu. Hatta yawun dake gudana da kai kawo a bakunansu zuwa maƙoshi ya ƙame ƙaf. Hargitsatstsun idanunsu kawai suka iya zubawa boka Barbushi da ke kwasar dariya har yanzu. Cikin ƙarfin hali da tsawa-tsawa na fitar hayyaci Miran Jasim yay ƙoƙarin dakatar da shi a kausashe.. “Koma mi ya taka ko yake taƙama da shi mu bai damemu ba. Muna son a ƙarasa mana rayuwarsa a wannan dare, haka itama yarinyar ta hanyar uwarsa Malikat Bushirat, asirinta ya tonu duniya duk ta shaida itace ta kashe yarinyar kaga sai ya gana da ƴan jaridar da hujja. A haddasa babban rikici tsakaninsu da talakawan ƙasar nan harma da tsohuwar can da rayuwarta ta zame mana ƙadagaren bakin tulu. Mu kuma zamuyi amfani da wannan rikicin wajen kawar da Eshaan ɗin ta hanyar aikin da likitoci zasu masa, sai kawai ace bugun zuciya ne dalilin abinda ke faruwa..” “Hhahahaha!!! Hhhhh!!!” Barbushi ya shiga kwasar dariyar wulaƙanci sa mai tsananin bada amsa kuwa. “Ina son mugunta da mugu hhhhh!!. Ina son naga ana mugunta HHhH!!. Koba komai ƴan wuta sun sami ƙaruwa hhhhh!! (Wa'iyazubillah. Ya rabbi badan halinmu ba ka karemu daga nema a wajen waninka, ka tsaremu daga shirka da mushirikai🙏😭). Duk da kalamansa na ƙarshe basu ji ko gezau ba akan ƙudirinsu, duk da kuwa sunyi imanin UBANGIJI ya halicci (WUTA DA ALJANNA) babu kokwanton zai cikasu kuma kamar yanda ya alƙarwanta, sai dai son cikar burin duniya na ƙanƙanin lokaci ya rufe zukatansu da idanunsu, sun jima matuƙa tare da shi sai gabanin asubahi suka koma masarauta ta ɓarauniyar hanyar kamar yanda suka fita.... *_WASHE GARI_* Ƙarfe goma na safe ƴan jarida da taron al'ummar ƙasar ruman sun cika ƙofar masarautar Ruman cika mai ban mamaki kai kace Tajwar Eshaan ɗin zai fito ne ƙuru-ƙuru su gansa kamar yanda suka jima suna bege a rayuwarsu. Dole aka baza jami'an tsaro saboda gudun abinda zaije ya dawo.........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (05) ........Tun a jiyan Doctor Afif yaso fahimtar da Tajwar Eshaan haƙuri da wannan zama saboda jikinsa har yanzu bawai ya kasance yanda ake bukata bane ba. Hasalima ana shirye-shiryen masa aikin da ya rage ne daga nan zuwa kwana biyu. Kallonsa kawai Tajwar Eshaan yay har ya kammala masa bayanin cike da girmamawa kai a rissine. Bai ce da shi komai ba tsahon lokaci, sai daga baya ya ɗan girgiza kansa kawai iya amsar kenan. Dole doctor Afif ɗin ya haƙura gudun shiga hurumin daba nasa ba. Kamar yanda ya saba komansa kafin faruwar al'amarin haka ya gudanar a yau ma duk da rashin ƙarfin jiki dana ciwon dake sukarsa kaɗan-kaɗan. Sai dai kasancewar jarumin jarumai gwanin juriya da shanye kowane irin al'amari cike da ƙarfin hali ya shirya cikin ƙasaitaccen shirinsa mai firgitar da duk wanda ya ɗaura idanunsa a kansa shi ɗin wanene. Shirine da ya bayyanar da tsantsar ƙyawun da ALLAH ya bashi da cikar kamalar mulki mai tafiya da kwarjinin kasancewar sa cikakken mutum mai matuƙar zama barazana ga kowa. Ƙamshinsa matuƙar narka da zuciyar mai shaƙa yake a kowane motsinsa. Ya cika ɗawusun da al'ummar ƙasar sa ke kiransa wajen iya ado da zauna masa a jiki koma ya zarce. Dan tabbas ko'a cikin dubu baya boyuwa da lalube ma cankosa ake kasancewarsa ɗaya ƙwallin ƙwal Shahan-shan Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed da babu wani mai irin matsayinsa a ƙasar ruman da kewaye kaf. A lokaci ɗaya gaba ɗayan masarautar ta ɗauki tsitt kasancewar fitowarsa a zahirinsa cikin takun dake tabbatar ma ga duk wanda bai san wannan fuska a zahiri ba shi ɗinne dai da suke cike da ƙishirwar son gani. Cikin karkarwar jiki data zukata hadimai ke faman zubewa bisa kafafunsu zukatansu na neman wantsalowa ta bakunansu duk da a kallo ɗaya da suke masa basa sake iya daga kai yin gigin kallo na biyu. Baga hadiman kawai ba hatta da masu faɗa ajin masarautar ma wutar kawunansu gaba ɗaya ta gama ɗaukewa dan al'ajabi. Domin kuwa tun fitowarsa hadimansu ƴan leƙen asiri har ci da goshi suke wajen isar da tsegumi ga iyayen gidan nasu kan fitowar Shahan-shan Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed yau a zahirinsa ga kowa babu shamaki..... ★A yanda dokin ya cika bargar da haniniya da fisge-fisge ya matuƙar tada hankalin masu kula da su. Iya kokari yi suke na ganin sun dakatar da shi daga ballewa saboda saninsa amma hakan ya gagara. Da yay wata irin mahaukaciyar girgiza sai ga zaratan mazan su biyar a ƙasa wanwar. Darewa a ka dingayi duk inda ya keta a cikin masarautar, yayinda hankalin mafi yawan hadimai ya tashi sanin babu mai iya dakatar da shi sai mai shi...... Cak ya tsaya daga yunƙurin shiga motar da aka tanada domin zuwansa falon da zaiyi zaman tattaunawa da yan jaridar duk da kuwa a cikin masarautar ne. Ko'a cikin barci yaji takun waɗan nan kofatan bazai iya manta mai su ba. A zabure jami'ai Da Gazi dake zagaye da shi suka zabura domin dakatar da ingarman farin doki da ko ga mai kallo ya san ya wuce tara irin ta gaba-da-gaba. Amma domin kare shugabansu a gare su tunkararsa dole ne koda tasu lafiyar bazata samu kariya ba. Ai girgiza ɗaya yay ya zubar da kusan uku da suka tunkaresa, wasu na ƙoƙarin sake tunkararsa yay wata irin turjiya, ya kwafuci ƙasa ya sake ƙwafuta yay girgiza mai haɗe da haniniya sai gashi gaban Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed. Dole kowa ya dakata wajen ya ɗauki shiru na wucin gadi duk suna kallon ikon ALLAH. A hankali ya kai tattausan hannunsa a fuskar dokin ya shafa, haniniya ya sakeyi da ƙwafutar ƙasa ya girgiza jikinsa. Wannan al'amari ya matuƙar ƙayatar ga duk wanda ke wajen, duk da kuwa ba'a yau suka saba ganin irin haka ga dokin ba a duk lokacin da ya kasance tare da Tajwar Eshaan ɗin.. Cikin muryarsa mai tausasawa da tarin nutsuwa ya kema dokin magana yana shafasa a hankali fuskarsa da ƴar sakewa kaɗan sai dai ba murmushi ya ke ba. Hasalima sai mai lurane zai fahimci sassaucin fuskar tasa a zahiri. Ya kwashe tsahon mintuna huɗu da dokin, hakan ya bama duk wanda ke a wajen damar cigaba da satar kallonsa, wanda kuma aka kaima gulma na ƙoƙarin tururuwar fitowa da leƙe a maƙe. Cike da ƙasaitarsa ya damƙa dokin a hannun Sayeed Fayzul-haq, shi kuma ya shige motar da ke buɗe har yanzu. Da sauri hadimin ya maida ya rufe murfin kansa a rissine. Da ga haka motocin suka nufi inda za'ai zaman. ★Isar da saƙon shigowarsa katafaren falon ya saka duk wani mahaluki mai numfashi yin ƙasa da kansa. Daddaɗan ƙamshinsa shine abu mafi ɗaukar hankali a garesu da saka nutsuwar zuciya. Yayinda takun sawayensa masu tabbatar da ƙasaitarsa ke ɗauka da sauka da bugun zukatansu. A zahiri da baɗininsu cike suke da ɗokin kasancewa a tare da shi koda bazasuga fuskar tasa ba. Duk da kasancewar sa Shahan-shan mafi ƙarancin shekaru a cikin duk Shahan-shan da suka gabata a daular ruman kwarjininsa na razanar da su, dan ko makaho ya laluba zai bada amsar Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed cikin jerin jaruman maza zaratan gaske koda basu ganin ainahin zahirinsa kuwa. A hankali ya kai zaune saman kujerar da aka tanada dominsa cikin nutsuwarsa da sanyin da rashin ƙarfin jiki ya haddasa masa. Kallo ya dinga binsu da shi cike da nazarinsu kafin ya lumshe idanu da buɗewa yana jan ƙaramar iska ya fesar. Su Miran Jasim da ke biye da shi bayan an kai musu labarin fitowarsa babu shamakin da ke ɓoye zahirinsa suma duk zaman sukayi ransu yana ƙuna matuƙa, wasu kam ransu fari ƙal da abinda Tajwar Eshaan ɗin yayi. Kasancewar sun tsara abin a yanda sukazo bisa jagorancin wakilai ɗai-ɗai daga kowace jiha sai zaman ya kasance a tsare. Ko sau ɗaya a cikinsu babu wanda ya gwada iya ɗaga kansa ɗan kwarjininsa ya gama mamayesu tun kan su gansa, sai dai tabbatar da kammalawar zamansa ya sakasu sake gurfana gaishesa. An amsa musu da yawun Shahan-shan batare da shi yako motsa ba daga zaman ƙasaitar da yayi har sai da falon yay shiru. Umarnin da aka basu na shiryawa ya saka su miƙewa musamman masu gyara camaras da tabbatar da abin ɗaukar maganarsu ya zauna yanda ya kamata a inda aka jerasu reras gabansa kaɗan. Kaɗan ya rage zukatan wasu su wantsalo da gasken gaske. Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed a zahirinsa, wannan fuskar da suka jima da mafarki da kulafucin son gani a bayyane ce a zahiri babu shamaki yau. Duk da kowa yay masa kallo ɗaya baya sake maimaitawa a ransu ayyanawa suke dole ya dinga kasancewa a ɓoye kam duk da cewa hakan al'adarsu ce, dan zasu iya cewa shine na farko a tarihi cikin duk Shahan-shan da suka gabata daya bayyana fuskarsa a zahiri. Abune da bai taɓa faruwa ba. Mafi yawancin al'ummar ƙasar ruman ƙyawawane duniya ma ta shaida hakan, sai dai fa a yau kam sunga inda ƙyawu yake na zahiri, ƙyawu irin wanda ko'a ƙasar ruman ɗin zasu ambacesa da ƙyawu ɗan gaske da ba'a iya ɗauke ido a kallo ɗaya ga mai shi... Wannan firgici ba'a iya falon kawai ya kasance ba. A duk lungu da saƙo na ƙasar ruman ne dan tunda aka ɗora Camara ga Tajwar Eshaan komai ya koma live ga masu kallo da saurare kamar yanda ya bada umarni.. A karan farko ya motsa pink lips ɗinsa da kyar ya fara magana a hankali. “Inama duk wanda ya kasance anan fatan alkairi da godiyar amsa wannan gayyatar. Tare da duk al'ummar ƙasata baki ɗaya. Kakannina, Iyayena yau ga ɗanku. Yayuna ga ƙaninku, ƙannena ga Yayanku, ƴaƴana ga Abbun ku ba'a matsayin shugaban ku kawai ba. Zaune nake anan da suna Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed ba Shahan-shan ka ɗai ba. Zaune nake domin baku haƙuri, zaune nake anan domin roƙonku alfarmar zama lafiya, zaune nake anan domin baku damar bin hanyar data dace kubi dan ganin kun miƙani a duk inda kuka aminta da a tuhumeni bisa duk laifukan da kuke kallon nayisu gareku. Na yarda kuma na amince zan zama mai amsawa in har na aikata koda zai kasance ƙarshen numfashina kenan. Bakuma zan zargeku ba. Kuje, kuje daga yau na baku damar yanke hukunci, zan kasance mai jiranku. Zan kuma kasance mai biyayya ga shari'a, zan kuma damƙa wannan mulkin ga duk wanda kuke buƙata na biku da fatan alherin ya kasance alkairi ga ƙasar ruman baki ɗaya a bayana. Fatan alheri a gareku baki ɗaya, da roƙon afuwar gazawata akan ku. Nagode nagode da fatan alherin da kuka min a baya da ma wanda wasunku ke min har a yau👏”. Tabbas da akwai camara da zata iya ɗaukar ƙasar ruman baki ɗayanta a wannan lokaci da ansha kallon mamaki, da ansha kallon yanda komai ya tsaya cak tamkar ana juya ƙasar da na'urar remote. Kalmomi ne da gaba ɗaya bazasu gaza ɗari da hamsin ba, amma sun shiga al'umma fiye da zamansu guda dubu. Sunzo a wata siga da babu wanda ya taɓa zato ko tsammanin fitarsu daga bakin da suka fita. Abu na gaba mamakin ganin fuskar wanda ya ambatasu ga wasu mutane da ruɗani ya riska. Dole su kira al'amarin da ruɗani kasancewar sanin wannan fuskar a fuskar da basu taɓa zato ko tsammani ba. Motsin gaɓɓai basu fara bayyana ba a zahiri sai da ƙyaƙyƙyawar fuskarsa ta gushe daga allunan talabijin ɗinsu. A take amon sautika ya fara tashi a sigar furuci daban-daban wanda ya hargitse ƙasar baki ɗaya tako ina, har zuwa dare kuma babu alamar lafawarsa, dan tako ina sharhine ke kai kawo ga masu fashin baƙi akan kalaman Tajwar Eshaan ɗin, ata wani gefen kuwa wasu videos masu ban mamaki suke faman kaikawo a yanar gizo daga talakawan ƙasar game da fuskar da suka gani yau matsayin Shahan-shan ɗinsu. Sai dai abin farin cikin kowane furuci kan fitane da alkairansa batare da sun san shi ɗin wanene ba. Yayinda wasu kuma ke nuna irin shock da suka tsinci kansu na ganin fuskar a matsayin Shahan-shan ɗinsu.........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (06) ........Sir Fawzan na ɗaya da ga cikin waɗanda suka tsinta kansu a wannan razanin. Hakama Azaan da Fhakir da suka kasance yaransa da duk inda ya saka ƙafa a ɓoyayyen yanayinsa suna biye batare da sun san ainahin wanene shi ɗin ba. Ire-irensu nada yawa da Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed ya mu'amulanta ta fuskoki daban-daban na alkairinsa da bibiyar al'amarin al'ummar ƙasar tasa batare da sun sani ba sai a yau da ya bayyana kansa a zahirinsa garesu..... ★★..... A cikin masarauta wannan al'amari daya jagoranci motsin ƙasar a yau ya matuƙar sakasu a rudani da firgici, dan da gasken gaske Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed ya musu duka irin na bayan ƙeya na cikin duhuwar da ko zaka tsinke wuyanka dan waige bazaka iya hango wanda zai maka ba sai bayan yayi idan yaso. Hankula da damar gaske sun tashi, irin tashin da sukejin ko wuta aka nuna musu zasu iya jagorantar jefa Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed ɗin a yau. Shi mai mulki ne, mulkin kuma shine abin baƙin cikin mafi yawansu. Su da shi duk suna gwagwarmaya ne akan waɗanda yake mulka ne. Sai dai su ƙoƙarin wargaza kansu suke yi masa bore domin cikar burikansu, shi kuma son dunkulesu yake domin sauke nauyinsu da ALLAH ya daura masa duk da kasancewarsa mai shekarun da har yanzu basu cimma arba'in ba a duniya... Abinda zai sake birgeka ga wannan bawan ALLAH tun da ya gama fuskantar al'ummar sa babu wanda ya sake jin wani motsinsa a wannan dare sai likitocin da ke zagaye da shi, wanda a yau zasu masa aikin da ya rage insha ALLAHU kamar yanda ya buƙata...... ★★..... ★...... Duk jarumtarta da juriya a wannan gaɓar sai da nakasun ƙaddara ya kaita ƙasa. Ƙarancin cin abincinta da tsantsar damuwar da suka zame mata abokan rayuwa sun mata illa matuƙa. Ta fita a hayyacinta sosai tamkar ba Iffahr nan ba ƴar gayu mai bakin da kadata sai wanda ya gawurta. Duk da ƙarfinta ya ƙare, rashin yaƙinin cigaba da rayuwa bai sa ta sallama ba akan burin maida fansar ta ga su Miran Jasim. Babban burin da take fata a yanzu koda bayan ranta shine al'ummar ƙasar ruman su kasance masu tsananta bincike wajen sanin ainahin Tajwar Eshaan bin Haysam Abdul-majeed a zahirinsa da baɗininsa. Duhuwar ƙaddara da bin makauniyar hanya sun haska mata wasu muhimman abubuwa a wannan tafiyar, sai dai kash ita tata tazo ƙarshe, labarinta ya zama tarihi a gaɓar daya kamata ace itace mai rubuta tarihin abinda ya kasance burinta da sadakarwata. Ta saki wani murmushi mai wahalar fassara ga wanda ya santa sakamakon ƙamshin turaren data ɗauka tsahon mintuna tana shaƙa a dinɗaɗɗen ɗakin kurkukun da take da yaƙinin yafi na kowa matsi da tsauri, sannan ita kaɗai ce mutum mai numfashi a wajen sai ko dakarun da ke zagaye da ita da sunan tsaro.... (Kowanene Iffahn ta shin shino haka kuma? Ta hanyar turarensa, da alama dai wanda ta sani ne ko take hasashe🚶). Batai yunƙurin buɗe idanunta ba kamar yanda bata motsa ba. Ɗakin ya cigaba da zama shiru babu alamar wanda ke tare da itan zai tanka har tsahon wasu mintuna data fara jin gundira da kasancewar koma waye a tare da itan. Sai dai kuma da alama akwai wani farin ciki, dake kokawa da gargaɗin ba haka bane a tattare da yaƙininta. Kunya da tunanin idon da zata iya kallonsa in har ma shi ɗinne yasa taji bazata iya ɗagawa ta tabbatar ba. Duk da duhun ɗakin hasken dake leƙowa ta mitsitsin windown da wutar lantarkin waje ta hasko ya taimaka wajen ganin wanda ke zaunen. Sanye yake da kaya baƙaƙe hatta da yatsun hanunsa a cikin safar hannu suke. Fuskarsa kam na sakaye da norse mask daya sakaya ainahinsa, sai baƙin gilashi daya ɓoye idanunsa. Ga mutum mai hangen nesa da ilimin saurin ɗaukar haske kan abu zai kira kowanene da mace, dan ƙira da dirin jiki sam basuyi kama dana namiji ba duk da akwai maza masu ƙarancin girma ta ɗa namiji. Babu alamar damuwa da rashin ɗagowar Iffahr da ta tasa gaba ta na kallo, haka suke sake shanye adadin wasu mintunan babu alamar nuna gundira duk da kuwa tsakkiyar dare ne da shiru ɗin masarautar zai iya tabbatar maka da haka kai tsaye. Da alamar jiran cikar lokaci aka kai duba ga agogon dake a tsintsiyar hannu, batare da cewa komai ba akai saurin ɗaga yatsu biyu ga wanda ke baya tsaye da babu tantama shikam namiji ne. Cikin gyaɗa kawai ya zaro syringe dake jikinsa mai ɗauke da ruwan allura ya nufi Iffah da har yanzu bata ɗago ba, babu ma alamar zata ɗago ɗin. Zabura tayi da ƙoƙarin son sakin ƙara sakamakon jin saukar ƙarfen allura ta kusa da gefen wuyanta da ke tsakani da kafaɗa. Abinda aka manne bakinta da shi ya hana fitar ƙarar, cikin abinda kuma bai wuce mintuna uku ba sun fice dai-dai da shaƙar wani ɓoyayyen ƙamshi daya bambanta dana farkon data fara shaƙa data gama hasashen mai shi. Sai dai na yanzu ya sake tabbatar mata da an yaudareta da ƙamshin ne kawai ba Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed ɗin bane...... Kammala theatre ɗin Tajwar Eshaan dai-dai da fiddo Iffah da mintuna kaɗan baya aka farga da halin da take a ciki ta dalilin jami'an dake zagayata a kowane dare domin tabbatar da lafiyarta bisa umarnin Malikat Haseenat. Da farko su sunma zata ta mutu ne, ruɗewarsu da kururuwarsu taja hankalin jami'an dake zagaye da sauran ɗakunan masu laifin dan waɗanda ke zagaye da Iffar har su huɗe duk suna zube alamar akwai abinda aka shaƙa musu suma. Sunyi gaggawar sanar da halin da take a ciki, cikin ƙankanin lokaci ƙwararren likitan dake a clinic ɗin masarautar ya isa gareta, sai dai a take ya fahimci abin babban al'amari ne, dan haka shima ya tabbatar da dubata bazai yiwu ba anan. Kai tsaye Malikat Haseenat ta bada umarni ɗaukarta zuwa clinic ɗin. An isa da Iffah clinic hankali tashe, yayinda likitoci suka rufu a kanta, sai dai abin mamaki iya bincike har na kusan awanni biyar basu gano komai ba, gata kuma a sanƙare babu inda ke motsi a jikinta sai bugun zuciyarta da na fitar numfashi kawai. Hatta abincin da aka kai mata a daren ranar dana safiyar duk anyi bincike kansa babu komai da aka zuba wanda zargin kowa ya karkata akai. Tofa wannan al'amari yazo da wani sabon hargitsi da yafi na lokacin Tajwar Eshaan, dan fa a wannan karon zukatan jama'ar masarautar ma kansu da bakunansu sun fara karkata da wani abu daban mai nuni da (anya kuwa babu wata a ƙasa?). Wannan kalma tayi wata irin amsa kuwa ga mafi rinjayen al'ummar cikin masarautar da zuwa yanzu komai yaje ga kowa. Dama gasu a cikin wata ɗimuwar da aketa faman ka-ce-na-ce da babu alamar zai ƙare anan kusa... (🤔nifa gaskiya🥱, tom🤫 bara dai nayi shiru🤭). ★★..... An sake wayar gari dai cikin tashin hankalin yanayin da Iffahr ke ciki wanda hankulan mutane suka rabu biyu. Dan duk yanda ake ƙunshe maganar a iya masarauta a washe garin sai da tai amsa kuwwa matuƙa a kafafen ƴa labarai dama na social media fiye da tsammani. Anan ne fa kowa ya shiga ƙara tofa albarkacin bakinsa. Malikat Haseenat tsohuwar alkairi, duk da abinda Iffah ta aikata ga jikanta ta kasance a jerin farko na masu zuwa su dubata bisa jagorancin Daneen Ammarah. Hankalinta ya matuƙar tashi, a take tausayin nan nata da zinariyar zuciya suka motsa ta nema ganawa da likitocin dake tsaye akan Iffahr. Sunyi zaman tattaunawa na kusan awa ɗaya, ƴan son suji mi zaman ya ƙunsa tuni sun baza hadimansu ƴan leƙen asiri, sai dai kuma basu sami damar jin mi'aka tattauna ɗin ba, sai labarin zuwan ƙwararren likitan da ake da yaƙinin yana da ilimi akan al'amarin na Iffah daga ƙetare domin dubata tunda su likitocin na nan sun kasa fahimtar komai, dan hatta da likitoci uku ƙwararru da suka zo daga baya suma basu iya yin komai ba a kai. Cikin ƙanƙanin lokaci aka fara shirye-shirye zuwan doctor, abinka da masu ƙasa cikin abinda bai gaza awanni goma sha biyar ba komai ya kammala doctor ya iso. A wannan karon Daneen Ammarah ce tsaye kan komai, hakan sai ya bama Miran Jasim da Miran Arshaan damar kafa wasu ƴan ƙananun magana ga su Jasrah dangin Malikat Bushirat, acewarsu Daneen Ammarah ta nuna damuwa akan bare wadda ta shirya halaka musu jininsu, har takai wasu ma na danganta halin da Tajwar Eshaan ɗin ke ciki da ita har ma da Malikat Haseenat da wasu maganganun kan koma cikin kunenta amma tai kunnen uwar shegu.... ★★★....... Ƙwararrun likitoci kuma manya ne suka rufu kan Iffah na tsahon lokaci. A ranar dai basu cema kowa komai dan gane da al'amarin nata ba, sai dai Daneen Ammarah nata ƙoƙarin ganin ta kwantar da hankalin Malikat Haseenat dake kiransu akai-akai dan hankalin tsohuwar da gaske a tashe yake, tashin hankalin da kowa ya gagara bama fassarar dalilinsa a gareta. Duk da a wannan ranar basu sami damar sake ganinta ba hankalinsu ya ɗan kwanta da ganin jikin Tajwar Eshaan yayi ƙyau shi kuma Alhamdullah, dan zuwa dare a bisa jagorancin likitansa doctor Afif sun sami shiga ɗakin da yake. Duk da bai furta da baki ba alamu sun nuna yayi farin ciki da ganin Daneen Ammarah ɗin, haka itama har da hawayenta na farin ciki ta kumayi sujudar shukur na nuna godiyar ta ga ALLAH. Baiyi magana akan Iffah ba, itama kuma batai masa ba duk da tanada tabbacin komai dake faruwa a masarautar yana zuwa masa kasanwar tun a safiyar yau ɗin ya farka kuma likitoci sun tabbatar da nasarar da aka samu kan aikin da akai masan a daren na jiya.........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (07) ........Kwanaki biyu kenan ana jiran tsammanin farfaɗowarta amma shiru kake ji, tun likitocin na iya controlling ruɗanin su Daneen Ammarah su ma har karayarsu ta fara bayyana. Dukkan wasu salon dabaru irin nasu na ƙwararrun likitoci sunyi amma babu wani canji tattare da Iffah duk da bincikensu na baɗini ya tabbatar musu nasara. Zuwa dare da ke neman ƙulle adadin cikon kwanaki na uku ruɗanin likitocin ya sake bayyana da shi kansa uban ginsamin duk da basarwar tasa a yau dai sai da ya magantu. Dan cikin tashin hankali lokacin da Daneen Ammarah ta ziyarcesa take sanar masa har da kukanta, saboda ita a nata tunanin ma yanzu ko bai ma san a halin da Iffah ke ciki ba ne dai shiyyasa baiyi mata magana a kanta ba, itama kuma bata masa ba. Shiru kamar bazai tanka ba duk da hawayen da take faman sharewa na tsikarar zuciyarsa. “Calm dawn Mamy”. Ya faɗa cikin sanyinsa da ƙyar kai kacema ba daga bakinsa kalmomin uku suka fita ba. Daneen Ammarah da ke sharar hawaye ta shiga girgiza kanta kukan na sake ƙwace mata, “Abni ta ina hankali zai kwanta da wannan yanayin, ina tausayin yarinyar nan matuƙa. Ina tsoron wani ya sake samun damar cuta mata ta hanyar yahudawan nan da bamu da tabbacin riƙe amanarmu da ke hannunsu. Tana da ƙyawawan halaye ɓoyayyu da sai mai lura da nutsuwar fuskantar ta zai iya ganinsu a bayyane. Ita ɗin tamkar lu'u-lu'u ce a cikin zinare, Abni bana so mu rasata a gaɓar da ta cancanci a kalla a nuna tamkar jinjirin wata da kowa burinsa shine ganinsa. Bana son wasu suyi amfani da wannan damar wajen salwantar mana da ita a wannan gaɓar da idanunmu ba zasu kasance kanta na tsawon kowanne daƙiƙa ba....” Kansa ya ɗan kauda gefe kaɗan tare da lumshe idanunsa da wani irin salon ƙasaita irin na gawurtattun sarakunan da jinin mulki ke kaikawo a jininsu. A zahiri kam babu alamar wani yanayi a fuskarsa da zai iya bada wata ƙofar da wani zai iya fahimtar baɗininsa, hakama fuskarsa bata canja da ga yanda take ba. Babu alamar zai ce kamar yanda Daneen Ammarah tafi buƙata da ga garesa har tsahon wasu mintuna da ta gama fidda rai.... “Mamy bana son kuka”. Ya sake faɗa a fisge a yanayin motsa pink lips ɗinsa kaɗan tare da dai-daita buɗe lumsassun idanunsa a kanta yana mai riƙo yatsun hannunta uku na tsakkiya kasancewar tana zaune ne a kujerar gaban gadon jiyyar tasa gab. Kai Daneen Ammarah ta jinjina masa cike da rauni tana ƙarasa share hawayenta. Yanada abin faɗa fiye da wanda ya faɗa a bakinsa amma furtawarce mafi girman aiki a garesa. Sai kawai ya zaɓi ɗan yin luuu da idanunsa tamkar zai lumshe sai kuma ya buɗe tare da motsa kumatunsa kaɗan alamar murmushi. Duk da a iyakar lips ɗinsa ya tsaya hakan bai hana Daneen Ammarah maida masa murtani ba cike da jin ƙaunarsa matsayinsa na ɗan ɗan uwanta mafi soyuwa a ranta kuma shugabanta. Ƙwayoyin idanunsa ya juya ga Doctor da ke daga gefe, tazbihi kawai yake ma UBANGIJI da girmama jini irin na masu mulki da ƙasaitar Shahan-shan ɗin na su, har zuciyarsa na raya masa anya kuwa akwai wani sarki mai mulki da ƙasaitarsa zata iya kamo ƙafar ta Shahan-shan ɗin nasu Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed?. Rashin mai tayasa ya sashi haɗiye tarin gulmar dake ran nasa ya saci kallonsa ta ƙasan ido, sai akai sa'a dai-dai saukar idon Tajwar Eshaan ɗin a kansa. Da sauri ya maida nasa ya rissinar yana mai jin kaifi da tasirin na Shahan-shan ɗin a kansa. “ALLAH ya ƙara lafiya da tsohon rai mai albarka ko ana buƙatar wani abu ne?”. Ya faɗa cikin rawar harshe da kaifafan idanun Tajwar Eshaan suka haddasa masa. Kallon nasa ya cigaba da yi har na wasu tsahon sakanni da suka kusa ƙulla mintuna biyu kafin ya motsa lips ɗinsa kaɗan ya faɗi abinda ya ke ta juyawa a ransa tun ɗazun. “Zata iya kasancewa tare da mu anan?”. Cikin gyaɗa kai da sake risinar da shi Doctor Afif yay saurin faɗin, “Idan hakan shine buƙatar adalin sarki shugaban sarakunan ƙasar ruman da al'ummar cikinta ya tabbata abu mafi sauƙin zartarwa a bisa umarninsa”. Kansa kawai ya ɗauke ba tare da ya sake magana ba har doctor ya fice. Daneen Ammarah da fuskarta ke faɗaɗa da murmushi ta buɗe baki zatai magana, sai hakan yay dai-dai da ɗagowarsa gareta, har cikin rai yaji daɗin ganin murmushin a fuskarta, amma bazaka taɓa gane hakan a tashi fuskarba. Ya dai ɗan sake ƙasa-ƙasa da idanunsa masu yalwar cikar gashi da motsa lips ɗinsa a hankali ya furta... “Kinyi farin ciki?”. “Sosai sosai kuwa sweetheart. ALLAH ya albarkaci rayuwarka, ya cigaba da tsare min kai ga duk wani abin ƙi. Ya yalwata zuciyarka da imanin da baya yankewa da tsoron ALLAH. ALLAH ya ƙara maka lafiya adalin shugabanmu abin alfaharin ƙasar ruman da al'ummar cikinta....” “Mammyy!”. Ya faɗa da wani irin sanyi-sanyi da ke son bayyana shagwaɓarsa a fili duk da fuskarsa ta shanye komai ta ɓoye. Karan farko Daneen Ammarah ta saki ƴar siririyar dariya dan ganin Baby Eshaan ɗin ta na baya a zahiri. (Su baby Eshaan anji jiki😜🏃)... ★Cikin ƙankanin lokaci aka cika umarninsa ta hanyar saka gado a ɗakin dake jikin katafaren ɗakin jiyyar tasa da gilashi kawai ya rabasu da nashin da ya kasance na musamman a sashe na musamman tare da dukkanin kayan aikin kula da duk motsin mai jiyya da abinda irin tata jiyyar take buƙata. Yana zaune a irin zaman da yafi yi a gadon jiyyar tasa ƙafafu a miƙe an rufesu da farin lallausan duvet har zuwa ƙugunsa, bayansa jingine da filon daya zauna dai-dai yanda ake buƙatarsa da taimakon ɗaga gadon da akai irin na mai jiyya. Duk da yanayi na mai jiyya da fuskarsa ta nuna tana nan tar-tar da ita da hasken nan nasa mai ɗaukar ido kamar madara, hakama kwantaccen gashin daya zagaye fuskarsa baƙi siɗik na kwance a fuskar kai kace wani hamshaƙin gyara yake samu. Duk da kasancewarsa a asibiti mayataccen ƙamshinsa da nasa ne shi kaɗai babu wani mahaluki mai irinsa ya gama manne ɗakin da duk wani abu da ake sarrafawa. Alkur'ani ne a hannunsa yana karatu dan haka bai ko motsa ba har aka kammala gyara gadon da za'a ajiye Iffah itama aka gungurota a gado. Da taimakon likitoci biyu mata aka ɗagata daga gadon da suka turota suka maidata a gadon da aka kafa. Sharɓan take kwance idanu a rufe, ƙyaƙyƙyawar fuskarta ma'abociyar tsiwa da rashin barin sai ta kwana tayi wani fayau. Ta rame ga idon duk wanda ya santa duk da bata cikin hayyacinta, damma bargon da aka lulluɓeta da shi ya ɓoye ramar da tayi ta jiki. Har suka kammala komai suka fice bai motsa idanunsa da ga kan Alkur'anin ba, karatunsa yake a nutse cikin zuciya da tattara dukan hankalinsa kacokan. Sai da ya kai inda yake buƙatar kaiwar sannan ya dakata yana mai lumshe idanunsa da sakin jerarrun ajiyar zuciya, dan a duk sanda ya kusanci Alkur'ani ta hanyar karantasa ya kanjisa cikin wata tarin nutsuwa da mulki ko dukiya ko wata ɗaukakar duniya bata bama ɗan adam. Yakan shagaltu da wani sirri da mai karanta Alkur'ani ne kawai ke iya samunsa a duniya. Sannan dukan damuwa da nauyin zuciyarsa kan kwaranye ya dinga jinsa tamkar wani sabon mutum sabuwar haihuwa. Bayan jan tsahon mintinan da suka sake tabbatar da gamsuwar nutsuwar da gangar jikinsa da zuciyarsa ke buƙata ya sake sauke ajiyar zuciya da buɗe lumsassun idanun nasa inda zuciyarsa ke fisgarsa da umarnin da bazai iya bijirewa ba. Duk da gilashin da ya raba sun tsaf yake iya hangota kwance samɓal, illahirin jikinta da zahirinsa ke a bayyane zagaye da na'urori kala-kala da suka kasance sirrin aikin likitoci. Idanun ya sake lumshewa ya buɗe akan fuskarta dake fayau sai hasken data ƙara mai tsananin ɗaukar idon mai kallo. Tabbas akwai abin faɗa a lips ɗinsa, sai dai ƙasaita da ƙarfin jinin iko mai yawo a jijiyoyin jikinsa ya jagorancesa ga haɗiyesu kawai dan barin kaza cikin gashinta kamar yafi alkairi ga mai kiyo. ★.... ★★.... ★..... Tun isowar labarin abinda ya faru da Iffah a wancan daren take jin ranta fes, sai dai zuciyarta na son sanin wanda ya aikata koma miye dan ta tabbatar masoyinsu ne. Cikin zumuɗi tai yunƙurin kiran number ƴar uwarta domin ta sanar mata amma ta gagara samunta. Hakan bai mata daɗi ba, amma dai bata damu sosai ba dan tasan itama komai zaije gareta. Da wannan farin cikin ta kwana a wannan ranar har zuwa jiya da Iffah bata dawo hayyacinta ba. A yanzu kam cikin harzuƙa da ɓacin rai take neman Malikat Bushirat ɗin dalilin labarin sake zuwan Daneen Ammarah sashen Tajwar Eshaan a yau, amma babu alamar zata sameta, tana a cikin wannan ɓacin ran labarin maida Iffah sashen Tajwar Eshaan ya sake riskarta. Cikin tashin hankali ta wancakalar da wayar tayo waje, batare da jiran driver ba ta nufi sashen Malikat Bushirat ɗin.. Hadima Banou dake tafe a ɗan gaggauce dan cika umarnin aiken da Malikat Haseenat tai mata tabi Jasrah da ke fitowa a mota rai ɓace da kallo. A hankali ta lashe laɓɓanta tana mai haɗiyar yawu. Ta jima tana kawaici akan cikin nan na Jasrah saboda shakkar Iffah, amma a yau kam ga dama ta samu. Sake haɗiye tsinkakken yawunta tayi tana gyara tsaiwa. Gabb sukai karo da Jasrah da alamu suka nuna idonta rufe suke da ɓacin rai, itako Hadima Banou duk da tayi ne ta biyu sai ta zube ƙasa cikin rawar jiki tana neman afuwa da rantsuwar bata lura da tahowarta ba har da ƙoƙarin dafa ƙafafun ta, Sake ɓaci ran Jasrah yayi, cikin rufewar idon ta ɗaga hannu ta sauke mata lafiyayyen marin da ya saka sauran hadiman dake ɗan kai kawo shiga razani. Maruwa dai kam Hadima Banou ta maru, dan har sai da tayi ƴar a dunguren da duk wanda ke a wajen yaji tausayinta. Amma a gareta hakan ma nasara ce dan ta samu abinda take so. Fuuu Jasrah ta tsallaketa ta wuce zuwa cikin sashen Malikat Bushirat rai a ɓacin, sai dai cikin girmamawa hadiman ƴar uwar tata suka sanar mata saƙon data bari na bata buƙatar ganin kowa. Watsa musu mummunan kallo tai taja tsaki da shigewarta.........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (08) ........Fitowarta kenan da ga toilet da alamun wanka tayo dai-dai da shigowar Jasrah ɗakin. Malikat Bushirat ta zuba mata ƙyawawan idanunta kawai cike da mamakin ganin yanda ta ingizo ƙofar gashi ko sallama batai ba. Jasrah da gaba ɗaya idonta ke lulluɓe da tsantsar ɓacin rai ga dunƙulewa da ɗan cikinta yay waje guda ya ƙulle mata mara ta zube a kan gado yarab. Malikat Bushirat da har lokacin ke binta da kallo ta ƙaraso gareta da sassarfa tana ambaton sunanta. Bata iya ta amsa mata ba har ta ɗagota jikinta. “Jasrah! Are you ok?”. Ina Jasrah bata iya ta amsata ba saboda yanda mararta ta ƙulle tamau. Hankalin Malikat Bushirat yay ƙololuwar tashi ganin tana jan numfashi da ƙyar. Dole ta shimfiɗeta tai amfani da telephone wajen kiran clinic. Cikin ƙanƙanin lokaci doctor... ta iso, kamar an saita tana shigowa jini na ɓallema Jasrah.. ★★ Wannan hali da Jasrah ta tsinci kanta a ciki ya ɗauke hankalin Malikat Bushirat da ga sanin halin da ake ciki akan komawar Iffah sashen Tajwar Eshaan ɗin. Dan kamar wasa jini ya ɓalle mata har sai da cikin jikinta da sukai matuƙar ƙwallafawa rai ita da mijinta (Miran Arshaan) gaba ɗaya ya fita har itama ana neman rasata dan itama hadima Banou ɗin taso taɓata ALLAH dai ya sa tana da sauran kwana a gaba tasha da ƙyar sai dai a ranar kam a asibitin cikin masarautar ta kwana. Rasa cikin nan ya matuƙar ƙona ran Miran Arshaan da ita kanta Jasrahn da sai a washe gari ta dawo hankalinta har take faɗa musu dalilin shigarta wannan hali saboda likita tace musu ɓacin ran da take ciki ne ya janyo ɓarin. Sabuwar tsanar Iffah ce ta baibayesu tare da ɗaukar alwashin a sashen Shahan-shan ɗin da su malikat Haseenat ɗin suka kaita sai sun bita sun halakar da ita. Ita kanta malikat Haseenat ɗin sun ƙullaceta matuƙa dan a ganinsu ita ce sanadin komai. (basu san ita bama tasan anai ba😏). Bayan lafawar halin da Jasrah k ciki ba ƙaramin ɓacin rai Malikat Bushirat ta nuna ba akan jin an maida Iffah sashen Tajwar Eshaan bisa wai umarninsa, sai dai sam bata yarda ba acewarta Malikat Haseenat da Daneen Ammarah ne suka saka shi yin hakan. A wannan gaɓar dai kai tsaye kowa ya fahimci fushin nata gaba ɗaya ya dangana ne ga Malikat Haseenat. Dan a take ta saka a rufe mata likitocin da suke duba Iffah, acewarta sai sun faɗa mata wanda ya sakasu yin shirin. Iya gaskiyarsu sun rantse mata akan su babu ruwansu umarni kawai aka basu. abinda kuma ya samu Iffah gaskiya ne kuma bincikensu ne ya basu da iliminsu. Bata nuna alamun zata saurarensu ba ma balle yarda da abinda suke faɗa ɗin, sai ma sabon bincike data saka akan zaman Iffah kurkuku. Sai dai me hatta jami'an da Malikat Haseenat tasa suke tsaron Iffah sunƙi faɗar kowane sirri, hakan sai ya sake hargitsa mata lissafi ga kuma su Miran Arshaan na tunzurata a gefe da sake munana tsohuwa Malikat Haseenat da komai dake faruwa tana ji amma ko tari taƙiyi balle ta nuna tama san da abinda Malikat Bushirat ɗin keyi. Ta dai aika Yumma (ƙanwarta da take tare da ita) taje ta duba Jasrah a randa tai ɓari... ★★..... ★..... A hankali ya janye idanunsa da ga kallon inda taken cike da basarwa yana amsa sallamar Doctor Afif da ya shigo ɗakin akan lips. Dr Afif ya ƙaraso cikin ɗakin yana mai rissinawa ya gaishesa, da idanu ya amsa masa kawai alamar ƴan izzar na kusa. Shima Dr Afif ɗin bai damu ba, dan a ɗan zaman jiyyar nan har ya fara haddace magana da idon nan. Gaban gadon ya ƙarasa yana sake rissinawa a cikin girmamawa ya miƙa masa file ɗin hannunsa. “Wannan shine file ɗin dukkanin bayanan nata da likitocin suka tattara. Sai dai suna kan sake bincike akan rashin farfaɗowar tata kan lokaci da ya kamata ace tayi tun kwanaki biyu da suka wuce”. File ɗin ya amsa batare da yace komai ba, ya ɗan dudduba, sai kuma ya ɗago idanunsa ya sake zubasu kan Dr Afif ɗin. Sai da yaja wasu sakanni kafin ya iya furta abinda ke bakinsa da ƙyar. “Kai mi ka fahimta akan hakan?”. Tsaiwa Dr Afif ya gyara yana mai sake rissinar da kansa. “ALLAH ya ƙara maka lafiya da tsohon rai mai albarka ni ina ganin ko za'a sake neman wani ƙwararren likitanne akan al'amurin nata da ya fi waɗan nan ɗin ƙwarewa. A yanda suka san aikinsu bai kamata ma ace sun gagara gano wani ƙwaƙwƙwaran abu guda ɗaya ba har zuwa yanzun, dan dole akwai abinda akai mata, dan bazai yiwu ace ta kasance a wannan halin babu ƙwaƙwƙwaran dalili ba”. Ɗan murmushi Tajwar Eshaan ya saki a karo na farko, batare da ya cema doctor komai akan bayaninsa ba ya ziro fararen ƙafafunsa zuwa ƙasa. Slippers ɗin dake ajiye gaban gadon ya saka, murya a dake ya furta, “Zan ganta”. Da sauri Dr Afif yay gaba yana faɗin, “Bismillah ranka ya daɗe”. Gaba ɗaya suka fito a ɗakin da yake tasa jiyyar, shi yana gaba doctor na biye da shi, duk da a jikin ɗakin da yaken ne koma ace ɗakinne kawai aka raba da glass sai ya zam ƙofar shigar sai kayi kamar ɗan taku biyar zuwa shida ne. Anan ɗin ma ƙofar ta gilashi ce, doctor ya buɗe masa yana ɗan ja baya. Sai da ya fara shiga. Tsaye yay a bakin gadon batare da ya zauna a kujerar da Doctor ya gyara masa ba. Sai da ya fara kai dubansa kan na'urorin dake aiki a jikin nata, gadai bugun zuciyarta normal na'urar ta nuna, sai dai nunfashinta baya tare da ita a zahirance. Ɗauke idanun yay da ga na'urorin ya maida a kanta. Lumsassun idanunsa ya tsura mata. Har yanzu tana kwance a yanda yake hangota daga ɗakin jiyyarsa tun ɗazun, tayi wani irin fayau da ita ga uban haske data ƙara. Ƙoƙarin saita yanayinsa da ke neman fallasa kan fuskarsa yayi, batare da yace komai ba cike da basarwa yay wani irin shegen murmushin takaici mai nunin ma'anoni daban-daban da ya saka Doctor Afif yin suman tsaye dan mamaki. Shi baima san Dr Afif ɗin nayi ba, sai ma idanunsan da ya ɗan lumshe yana haɗiye murmushin ya taka a sannu gaban gadon sosai tamkar ba shi ba. Yatsunsa guda biyu ya kai kan jijiyar kanta da tai ruɗu-ruɗu kusan na minti ɗaya, kafin ya janye ransa a dagule ya dubi Doctor Afif. “A cire mata duk wata na'urar jikinta”. A ɗan firgice Dr Afif ya waro manyan idanunsa. Har lips ɗinsa na rawa wajen faɗin, “Ranka ya daɗe na'urorin mam sune ke taimakamana ganin ɗan sauran abinda ya rage yana aiki a tattare da ita. Cirewar zata iya zama haɗari a gareta. A gafarceni idan na shiga hurumin da ba nawa ba”. Kamar ma bai fahimci bayanin doctor ɗin ba ya sake furta, “Nace a cire”. Sake daburcewa Dr Afif yay, sai dai bashi da damar cigaba da jayayya duk da ya san bazai yuwu Iffah ta cigaba da rayuwa ba in har babu waɗannan na'urorin. Wayarsa ya ciro a aljihu yay kiran wata nurse da ke aiki a clinic ɗin masarautar, cikin ƙanƙanin lokaci sai gata tazo. Razana tai da ganin mai gayya mai aiki a ɗakin, tuni ta zube gwuyawunta a ƙasa tana kwasar gaisuwa cikin tsumar jiki. Da hannu yay ma Doctor nuni tai aikinta kawai batare da ko ya dubi sashen da take na. Cikin sauri Dr Afif ya ce ta miƙe, shine ya shiga nuna mata yanda zatai komai. Hannunta na ɗan rawa dan kasancewarsa a ɗakun kwarjininsa ya cika ko'ina. Abune kuma da zatace bai taɓa faruwa ba a rayuwarta duk da itama ɗin dai jinin gidan ce. Ta gama janye komai da ga jikin Iffah'r bisa umarnin Dr Afif batare da ya nemo Doctor ɗin da ke kula da ita ba. Shiko gogan na tsaye kamar wani soja idanunsa a kan duk yanda suke komai har aka kammala. Fita nurse ɗin tayi, shima doctor ya koma gefe yana son ganin ikon ALLAH. Kanta ya ɗan rissino a hankali ya kama duvet ɗin gadon ya sake gyara mata, batare da ya dubi Doctor Afif ba ya nufi ƙofar fita yana faɗin, “Ina buƙatar ganin Sayyid Fayzul-haq yanzu nan”. “Umarninka shine abin jirana”. Doctor ya faɗa da sauri yana buɗe masa ƙofa. ★A mintinan da basu ƙarasa goma ba Sayyid Fayzul-haq ya iso. Cike da girmamawa ya miƙa gaisuwa. Kai kawai ya ɗaga masa batare da ya janye idanunsa da ga kan system ɗin gabansa da yake sarrafawa ba, dan tun shigowarsa ɗakin ita yay zaman sarrafawa. Ɗakin ya cigaba da ɗaukar shiru na tsawon wasu mintuna kamar bashi yasa ai kirasa ba. Sai da ya mula dan kansa kafin ya buɗe baki da ƙyar batare da ya bar abinda yake ɗin ba. “Ina buƙatar ruwan zam-zam, da waɗan nan abubuwan”. Yay maganar yana masa nuni da takardar da ke gefensa batare da ya ɗago ɗin ba dai. “An gama, umarninka shine abin jirana. ALLAH ya ƙara maka lafiya da rayuwa mai albarka”. Sayeed ya faɗa yana matsawa kansa a rissine ya ɗauka takardar. Sai kuma yay masa sallama duk da yasan ba amsa zai samu ba ya fice da hanzarinsa domin gaggauta cika umarnin shugabansa. Cikin ƙanƙanin lokaci kuwa dukkan abinda ya buƙata aka kawosu.. Ya hana duk likitocin sake taɓata a wannan yinin, sai ma Daneen Ammarah da ya saka aka nemo masa. Tasha mamakin magungunan da ya nuna mata da ganin an cire duk wata na'urar da ke tare da Iffah'r, sai dai yanda ya tsuke fuska babu alamar wasa ya sata shanye duk abinda ke a ranta ta ɗauka abinda ya batan bisa umarnisa. Dan duk da kasancewarsa ɗan ɗan uwanta a yanzu shi ɗin shugaba ne, akwai gaɓar da kuma yake tafiyar da wasu al'amuran a tsakaninsu matsayin shugaba ɗin. Hakan baya damunta, dan kowa ya san ALLAH ne ya bashi, ba dan kuma ya kasƙantar da su a kansa bane ya fifitashi da jarabawar mulkin.........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (09) .........Yanda ya umarcetan haka tayi akan Iffah, dan dole ta kasance a tare da ita har zuwa lokacin da ya bukaci ta kai tare da itan. Komai dake faruwa kuma akan idanunsa ne, sai bayan wucewar Daneen Ammarah da kusan mintuna talatin ya ɗauka Alkur'aninsa ya fito cike da takun nan nasa na izza da ƙasaita ya nufi ɗakin. Zama yay a kujerar da ke gaban gadon shanyayyun idanunsa a kanta, ya mata kallo na wasu mintuna tamkar mai nazari kafin ya fesar da ɗan huci ya ɗauke kansa. Alkur'anin ya buɗe yana mai ƙara tabbatar da nutsuwarsa gaba ɗaya garesa sannan ya fara raira karatu cikin daddaɗar muryarsa da bama kowane harafi hakkinsa cikin ƙwararren larabci yanda ya kamata. Ya ɗauki tsahon lokaci yana karatun, kafin ya tsagaita ya rufe ya ajiye. Kujerar da yake zaunen ya sake matsarwa gab-gab da gadon, tamkar wanda baya so ya kai hanunsa kan bargon ya ɗan yaye kaɗan. Kauda idanunsa yay da ga kallon inda suka sauka ya maida a fuskarta, ɗan bakin tsiwar nan duk ya bushe. Ya ɗan ja wasu sakanni a kallon nata, sai kuma ya kaudar yana sake tsuke fuska ya fara karanto addu'oi yana tofa mata. Haka ya kasance tare da ita har gabannin asubahi, dan sai da katafaren agogon masarautar ya buga cikar ƙarfe uku dai-dai sannan ya bar ɗakin ya koma nasa. Dole ya kai kwance dan shima ba jikin nasa ya gama komawa normal bane, a yanzu hakan ma jiri-jirin da ya fara ji yana rinjayarsa ne ya sakashi haƙura ya dawo nan ɗin....... ★★... WASHE GARI ★★.... Ƙoƙarin rufe system ɗin gabansa yake dai-dai da shigowarta da sallama doctor Afif na take mata baya kasancewar hadimanta basu da hurin biyota har nan. A kallo ɗaya zaka fahimci ɓacin ran da ke shimfiɗe kan ƙyaƙyƙyawar fuskarta. Doctor Afif ya gyara mata kujerar da ke gaban gadon jiyyar Tajwar Eshaan ɗin, sai da ta zauna ya juya ya fice tare da zuge musu ƙofar gilashin duk da wajene da bana shiga kowa da kowa ba. A hankali ya ɗan risinar da idanunsa alamar girmamawarsa gareta, sai kuma ya motsa lips ɗinsa a tausashe ya furta “Amincin ALLAH ya tabbata a gareki ya Ammie-na”. Duk da ɓacin ran da ke zagaye da zuciyarta hakan bai hanata ɗan sakin murmushi ba, ta kai hannunta kan nasa ta riƙo, itama cikin sauƙaƙa harshe da nuna kulawa ta amsa. “Tare da kai Bin Haysam Abdul-majeed. Ya ƙarfin jikinka?”. Suna mafi soyuwa da yakan so ji da ga bakin mahaifiyarsa, sai dai kuma a duk sanda ya jisa da ƙarfin izzar harshenta ya kan saurin gane ɓacin ranta a bayyane. Ganin damuwarta kam shine abu mafi ƙona zuciyarsa dan shi karan kansa bai san irin tarin ƙaunar da yake ma mahaifiyar tasa ba. Kaɗan ya gyara kishingiɗar da yay har lokacin idanunsa na kanta, ya juya yatsunsa da ke riƙe da nata ya maida nasa a ciki, a sannu yake tausa mata gaɓɓansu da kulawa da lallashi batare da ya sake cewa komai ba. Tsahon mintuna suna a haka har ta fara sauke ajiyar zuciya alamar saukar fushin nata. Ganin ta koma kamar yanda yafi buƙatar ganinta ya ɗan sake mata murmushi. “Nafi buƙatar ganin murmushin akan ƙyaƙyƙyawar fuskar Ammie-na a kowace daƙiƙa ta numfashi na. Akasinsa kan ƙona zuciyata fiye da yanda wuta ke narkar da kitse.” Kalamansa koda a taƙaice suke zinarai ne a zuciyarta, shi ɗin yafi hasken diamond walwali da ƙyalli a cikin idanunta a duk sanda take dubansa, ta so abubuwa da yawa kafinsa ciki harda mahaifinsa sai dai shi tamkar shafine dake shafe dukanin fejin sauran fejikan baya a littafin rayuwarta. Kafin ka buɗe a bangonta shine, a shafin farko da shi take shimfiɗa, tsakkiya da ƙarshe shine mafi girma a ababen yabonta da ƙaunarta. Ta sake sakin murmushi zuciyarta na sake risina da ga fushin da ta baro sashenta a ciki. Malikat Bushirat wata irin mace ce da gane halinta sai wanda ya santa, tana da abubuwan ban mamaki ta na da kuma na ban tsoro harma dana ban sha'awa da suka kasance mafi rinjaye a yimata ado. Hamshaƙiyace ta gasken gaske dan ko'a cikin manyan matan dole a kirata *_ZAKANYA UWAR ZAKIN ƘASAR RUMAN_*. A yanzun ma halin dattakon nata ta nuna, ta hanyar shanye dukan tarin abubuwan bakin nata ta cigaba da bama ɗanta magajin mijinta mai amsa suna shugaban sarakunan ƙasarta kulawa har zuwa lokacin data gamsu zata iya magana da shi babu fushi a harshenta. Ta tsatstsaresa da idanunta masu kaifi irin na uwa, yayinda shi nashi ke a rissine gareta risina irin ta ɗa a gaban mahaifiya. “Na kasa gane komai da ga Mammah dangane da al'amarin yarinyar, a sanina ita ke fara hukunta duk wanda ya zaɓi cutar da kai koda da mummunar magana ne, kuma koda ni da na haifeka ce. Amma a wannan lokaci sai ta zaɓi bama mai son kawar da numfashinka kariya batare da fahimtar da ni kaina hujjarta akan hakan ba. Shin taya ake tunanin zan iya haɗa numfashi a ƙarƙashin runfa ɗaya da wadda ta shirya kawarmin da abinda bani da madadinsa ko samin madadinsan ba har abada? Taya ake tunanin zan iya kawaicin barinta da cigaba da kallonta a matsayin Zawgatu al-ibn duk da yunƙurinta na son ganinta ta tarwatsani da tai? Idan har igiyar aurenka da ke kanta ne katangar da ake iya min nuni da ita bango gareta ina son ka rusheta, ka yanketa, yankewa ta har abada ibn Haysam Abdul-majeed. Dan hakan shine kawai zai iya bani nutsuwa na manta da komai”. Da ɗan ƙarfi ya matse idanunsa yana mai sakin numfashi a harɗe, sai dai mai kallo da ido bai isa fassara kamilar fuskarsa ma'abociyar annuri da kwarjini ba hatta ita dake amsa sunan mahaifiya a garesa..... “Yanke hukunci cikin fushi da rashin haƙuri akan bincike ba itace ɗabi'ar shugaba nagartacce ba”. Daneen Ammarah ce dake tsaye mai maganar tana ƙoƙarin shigowa ɗakin, da alama ta ji dukkan kalaman Malikat Bushirat ɗin. Bai motsa ba, hakama bai buɗe idanun nasa ba harta ƙarasa shigowa garesu, sai dai ya sauke wata irin ɓoyayyar bahaguwar ajiyar zuciya acan cikin maƙoshinsa. Jin shiru ya ratsa ɗakin ya sashi buɗe idanun sannu-sannu. Dukansu cikin ɓacin rai suke kallon juna kowa najin ya isa yana kuma da ƙarfin iko akan yaƙin. Abune da babu wanda zai ce ya taɓa gani a tsakaninsu sai a wannan lokaci, ciki kuwa harda shi kansa. Daneen Ammarah ta sake katse yanayin nasu ta hanyar ɗora hannunta a kafaɗar malikat Bushirat da alamu suka nuna ta gama kaiwa maƙura a fusata.. “Úht!”. (sunan data kan kirata da shi wani lokacin) “Ban sanki da garaje ba, ban sanki da kasa fahimta ba, ban sanki da munana zato ba. Ban sanki da dagiya ba. Ina roƙonki ki danne, ki jure, ki zama mai ƙarfafa gwiwar mai ƙarfin da ba ƙarfin akafi son ya gwada ba kai tsaye, saboda amsa sunansa na shugaba. Bazan musa miki sunan Fareedah matsayin mai laifi ba, amma zan so ki kasance a yanda na sanki wajen tabbatar da gaskiya akan kowane ne kafin zartar da hukunci. Muma ba burinmu hana a hukunta ta ba, ko fifitata sama da gudan jininmu kuma shugabanmu ba, so muke kawai abi tsarin da ya dace da dokar shari'a da muke fata bayan ita za'a iya tono waɗan da ma suke aikata ɓarnar baya mai barinma gudan jininmu baƙin fenti da tabo a rayuwarsa da rayuwar mulkinsa. Ki fahimci Mammah ba fifita Fareedah take sama da abinda ta cancanci fuskanta bane, kariya take bata matsayinta na tamkar makamin da zai iya zama zaren da zai jamu ga duk ɓoyayyun masu laifin da muke fatan kamawa a cikin hannayenmu. Shin baki ji a ranki wanda suke aikata ta'asar baya nada nasaba da na yanzu ba? Baki ji a ranki yanke mata hukunci a kallonta ita kaɗai mai laifin tamkar basu ƙwarin gwiwar cigaba da aikatawar bane koda kuwa a yanzu basu da hannu kan abinda yarinyar ta aikata? Shin baki tunawa shi shugaba ne ba mai azaba ba?. Da yawan mutane gani suke sakacinsa da ƙin bama abu muhimmanci koda mai muhimmancin ne halayyarsa, sai dai yanda yake yi shine cikar zama cikakken duk wani shugaba. Shugaba da shanyewa aka sansa koda ɗacin na ƙona makoshinsa, da haɗiyewa aka sansa koda raɗaɗin na azabtar da hanjinsa, da ɓoyewa aka sansa koda girman al'amarin yafi girman zuciyarsa, da nazarta aka sansa koda ƙarfin yafi ƙarfin ɗaukar ƙwaƙwalwarsa. Ba ko yaushe yake ihu ba, ba ko yaushe ake gane ainahinsa ba, ba ko yaushe ake iya karantar zuciyarsa ba koda a ƙwayoyin idanunsa ne.....” ta ɗan ja numfashi ta fesar a hankali da cigaba da faɗin, “Idan har mu a karan kammu zamu kasa fahimtar kammu taya wanɗanda ke zagaye da mu zasu fahimcemu?. Idan har uwa zata iya shanye wa da daurewa akan halayyar ƴaƴanta da duk girman adadinsu bazasu haura ashirin ba mai zaisa shugaba mai mulkin ƙasa baki ɗaya kamar ruman za'a so ganin zahirinsa a dole dan kawai farin cikin wani ɓangare ko munanama wani ɓangare? Tayi laifi an yanke mata hukunci, daga baya gaskiya ta bayyana bata da laifi ko tursasata akayi ko wani dalili da zai iya wanketa koda ace ba shine yay hukuncin ba, to shi ne za'a kalla da tabon gazawa? Wa za'a munana? Wa za'a aibanta? Wa za'a munanama kima da mutunci? Amasar itace shugaban nan dai Umm-Jasrah. Dan ALLAH na roƙeki ki kwantar da hankalinki kar wasu su dinga amfani da fusata fushinki domin cikar nasu burin, ki cigaba da zama a yanda na sanki inba hakaba wasu zasuyi amfani da hannayenki wajen shafama kanki da kanki fentin da babu wani ruwan da zai wankeki ya wanke wanda ake son amfani da soyayyarsa a zuciyarki. Bayan ke uwa ce, kema ɗin shugaba ce.....” Har cikin rai da ɓargo zantukan Daneen Ammarah sun matuƙar ratsata, sai dai basu ruguje kaso ashirin cikin ɗari ɗin matsayin da take kallon Iffah da shi ba har a yanzun, amma taji ta kuma amince zama mai haƙurin bin matakin da ya dace ɗin wajen hukuntata, hakanne kawai zai bata salama kasancewar ta wadda bata ɗaukar ƙiyayya da sauƙi ga duk wanda ya nuna mata, hakama soyayya. (Hakan kuskure ne Malikat Bushirat, karka zafafa ƙiyayya, kar kuma ka zafafa soyayya dan wataran duk zasu iya canja kansu a gurbin juna), sai kuma ƙudirinta na biyu babu gudu babu ja da baya zata tabbatar da shi koda babu yardar kowa a daular ruman har shi kansa Tajwar Eshaan ɗin........✍️ (Nace, “Humm”) *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (10) ........Daneen Ammarah da dama sanin fushin malikat Bushirat ɗin kan al'amarin ya sata tada hankalinta ganin an kusanto da Iffah ga Tajwar Eshaan tai ɗan murmushi, tasan kalamanta sunyi tasiri, sai dai ba tasirin da zai iya ruguje abinda take son ganin ta ruguje ɗin ba (Wato ƙiyayyar Iffah a zuciyar Malikat Bushirat a yanzun). Kanta ta ɗan rausayar tare da kallon Tajwar Eshaan da yay kamar babu shi a ɗakin, dan idanunsa ma a lumshe suke kamar wanda barci ya ɗaukesa. Juyawa tai ta fice a binta itama zuciyarta cike da ƙudirin tsayuwar daka domin tabbatar da gaskiya da kuɓutar da yarinyar da takejinta har cikin ƙasan zuciyarta. Idanun ya buɗe kaɗan ya bita da kallo tamkar yanda itama Malikat Bushirat ɗin data gagara iya cewa komai ta bita da kallon.. *_“Hummm!! Bazan iya hakuri ba sai na tofa”_* “Idan nace Humm fa ina nufin Humm da gasken gaske. Idan har Iffah ta rayu yaya kuke tunanin a yanzu salon zamanta zai kasance da uwar mijin nata mai tsananin ƙarfin iko? haka koda an tabbatar da jagororin abinda ya faru ta dalilin nata. Masu karatu akwaifa cakwakiya, dan yanzu salon zai fara a ƙarƙashin abu uku ne, da zaku iya canko min su dana baku babbar ƙyauta😉😁🥱”. ★.... TA-ƘURYA ★..... “Na daɗe da faɗa miki wannan yarinyar hatsabibiya ce kar ki sakaci da rauninta na kasancewa mai ƙarancin shekaru ko ƙanƙanta sama da ƙarfin ikon ki ta-ƙurya?. A duniyar cikar buri raina abokin karo kuskure ne kuma ganganci ne da kan iya rusa duk wani ginin da aka faro komai tsahon shekarunsa.....” Ta-ƙurya da ke gurfane gaban Uwa cikin jin raɗaɗi a zuciya ta ɗago idanunta da launinsu ya koma jazur, cikin rufewar idon irin na mai ɓacin rai da manta wake a gabansa ta ce, “Mina gaza Uwa?! Minene ban bi ba a dukkanin sharuɗan ki a shekarun nan? Miyasa matsala bata kasance abokiyar gogayya ta ba sai a lokacin da zan girbi shukar dana ɓata tsahon shekaru wajen yimata barruwa? Miyasa? Miyasa?. Na ce miyasa hakan ne?!. Miyasa sai da na yarda na rasa komai domin samun abinda nake kallo komai a gareni sannan zaki hana mini? Ke ce kika ce karna taɓa kokwanto bazaki taɓa barin zubar waɗan nan hawayen da a yanzu suke kwaranya akan fuskanta ba da ga gareni. (Wa'iyazubillah 😭🙏). Miyasa? Miyasa a yanzu sabanin hakan nake gani? Yarinya ƙarama da bata wuce na murjeta da tsinin takalmina ba ta shigo rayuwata da barazanar yin kutse akan nasarata. Idan tafi ƙarfinki ne ki faɗa min danni batafi ƙarfi na ba, babu wata uwa data haifi ƴa ko ɗan dazai zama barazana akan cikar burina, in ko uwar ta haifosa har kuma ya kwatanta zan shafe babin zuri'arsa kaf da babu wani abinda za'a kalla a tuna su kuma. A yanzu kam zanyi yaƙin da hannayena dan bana buƙatar k......” “K!! Ta-ƙurya ki dawo cikin hankalinki, kalleni da ƙyau ki san a gaban wa kike? Uwar mugu nake bata sakarai ba. Banyi lalacewar da ke zaki ci tuwo a kaina ba koda kuwa tuwun na ƙasa ne mai sauƙin wawaso. Idan kuma zaki gwada ga fili ga mai doki”.. Cikin nuna halin ko gezau ta-ƙurya taja tsaki mai tsananin sauti dai-dai lokacin da Uwa ke ɓacewa daga idanunta rai a ɓace. Ta rakata da harara tana mai miƙewa da ga durƙuson da tai. Waya ta fusga cikin tsananin fusata ta hau danne-danne tana kai kawo a katafaren ɗakin... 🙆Tofa al'amarin babba ne tsakanin ta-ƙurya da uwa ta ta😱. Mu dai ƴan kallo ne😜. ★★..... ★..... Alhamdullah a daren yau likitoci suka sami nasarar dawowar Iffah dake cika kwanaki huɗu hayyacinta, zuwa safiya kam sai dai ace Alhamdullah duk da bawai tana a cikin ƙarfin jikinta bane ko warkewa sarai kamar yanda take a baya. Daneen Ammarah har da kukanta na farin ciki, bata ɓata lokaci ba wajen sanar ma Malikat Haseenat. (Alhamdullah) ta dinga jerawa itama tare da jin nutsuwa na saukar mata, dan tunda yarinyar nan ta tsinta kanta a halin nan hankalinta ya gagara kwanciya. Malikat Bushirat duk da labarin farkawar Iffah ya zo har kunenta ta hanyar doctor Afif batace komai ba hakama bata leƙa dubata ba, sai ma yazam a safiyar ranar har zuwa yamma bata leƙa sashen Tajwar Eshaan ɗin ba gaba ɗaya, ta dai kira waya domin jin cigaban lafiyar jikinsa. Shi ɗin ma dai bai shiga duba Iffahn ba sai yamma duk da kuwa jiyan ma a gaban idonsa ta farfaɗo, Sannan har yanzu jikinsa babu ƙarfi shima, dan da gaske gubar da suka haɗa da dafin macizan ta so masa illa ƙwarai da gaske tunda gashi ma har sai da akai masa aiki dalilin taɓa wani sashe na jikinsa data so tayi saboda ƙarfinta. Duk da ɗakunan jiyyar tasu na maƙwaftaka da juna a yau bamai iya ganin wani sakamako labulolin da aka zuge suka toshe gilashin da ya raba sun, koda babu labulen gilashin mai ƙarfine da babu mai jin maganar wani koda za'ayi da ƙarfi ne, sai dai zaka iya hango mutum fes. Har zuwa yanzu dai kayan jiyya ne a jikinsa sai dai a kullum yakan canja da wasu sabbi sau fiye da biyu, ya ɗan rame saboda yanda ciwon ya bugesa. Sai hakan ya sake fiddo hasken fatarsa mai launin tar-tar a cikin idanun mai kallo. Cikin jarumtarsa da ƙarfin hali yake tafe doctor Afif biye da shi a baya tare da Sayeed Fayzul-haq dake tsaye da ga bakin ƙofa dan zuwansa kenan. Cikin sauri Sayeed ya danna maɓallin ƙofar gilashin ta zuge kanta a hankali. Baya ya ɗan ja yana mai rissinar da kansa ga shugaban nasa mai matsayin gaske a garesa da bazaya iya musaltuwa ba. Izzarsa da ƙasaita na tattare da shi, dan tamkar itace jinin dake zagayawa a maimakon jininsa, ya ɗan ja iska ya fesar na wasu sakkani kafin ya cigaba da takawa a sannu ya shiga bakinsa ɗauke da sallama can ƙasan maƙoshi. .. Daneen Ammarah da ke zaune a gefenta tana ƙoƙarin bata shayi mai zafin gaske da Doctor ya bada umarnin bata ce ta ɗan waigo najin motsi, numfashi ta ɗan ja ƙaɗan tana mai sauke idanunta a kansa. Sai kuma ta miƙe dai-dai Iffah tana damƙe kofin shayin cikin hannunta duk da zafinsa da takeji sakamakon jin Daneen Ammarah ta ambaci “Abni”. Sosai zuciyarta ke harbawa da ƙarfin gaske, kusan tare da ɗaga sawunsa da saukewa cike da izzar da raunin ciwo bai rageta a gareshi ba sam. A tsumen da fuskarsa take ya tabbatar ma Daneen Ammarah a Shahan-shan ɗin sa ya shigo ba ɗanta ba, dan haka ta ɗan ja gefe a yanayin girmama darajar da ALLAH ya basa. Cikin sauri Sayeed Fayzul-haq ya gyara masa kujera yana mai ja baya kusa da Doctor ya rissinar da kansa. Duk abin nan dake faruwa yana tsaye kaifafan idanunsa masu matuƙar tasiri da tabbatar da girman da ALLAH ya bashi na mulki badan yafi saura ba na a kanta, kallo yake mata irin na ƙasan ido mai hana wanda akema sukuni koda bai san wanda ke masa ba. Sai da ya gaji dan kansa sannan ya kai zaune sannu a hankali ga kujerar da aka gyara masan... Iffah ta kasa sake iya motsi duk da azabar zafin shayin da raɗaɗin da ke ratsa mata hannu, sauƙinta ma ta ɗora shi ne bisa lallausan duvet ɗin da ƙafafunta ke ciki har zuwa cinyarta. So take kawai taji ta ɓata, ɓata irin wanda ta daɗe tana jin labarin masu layar zana nayi, ta kasa tantance ainahin abinda ke razanar da kasancewar sa gareta, shin tsoro ne ko matsananciyar kunyar kai ne?. Inama inama, inama daga halin data tsinci kanta bata sake farkawa ba balle su haɗu, inama an cigaba da barinta ta dawwama a kurkukun da bazata sake ganinsa ya ganta ba har abada. Tabbas har yanzu tana jin zafi, zafi mai haɗe da raɗaɗin rasa ƴan uwanta guda biyu, sai dai saɓanin yanda ta ɗauka abun a da akwai banbanci da yanda take kallonsa a yanzu... Sake maida idanun nasa da ya ɗan kauda daga kanta yayi, sai dai yanzu a kan kofin shayin da take faman damƙa ya sauke su, ya ɗanyi sama da su zuwa ƙirjinta da girman rigar asibitin ta sakaya, sake sama yay zuwa kan fuskarta da ke nuna ainahin yanayinta. Lumshesu yay da sake buɗewa cikin salon shanyesu matuƙa mai son nuna kasala a bayyane, sai dai tsaf ya shanye komai daga kan fuskarsa ya haɗiyema ransa yana mai furzar da iska kaɗan tare da gyaran muryar da ta sakata zabura alamar hakan yazo mata a bazata. Dubansa ya maida ga Daneen Ammarah da itama gyaran muryar tasa ya sakata ɗagawa kamar su doctor, sai dai maimakon shi bakinsa ya ce wani abu sai Sayeed Fayzul-haq ne yay saurin faɗin, “Ranki ya daɗe, adalin shugaba mai musanya sharri da alkairi na miƙo gaisuwar yaya jiki ga Zawjata-almilk. ALLAH ya ƙara mata lafiya da rayuwa mai albarka.” Daneen Ammarah ta ɗan nisa kaɗan da jinjina kanta tana mai gyara tsaiwa. “Zawjata-almilk na godiya da wannan karamci, tana mai fatan alkairi da addu'ar samun lafiya ga Shahan-shan shima”. Iffah da ke saurarensu cikin tsinkewar zuciya ta ɗan ɗago ido kaɗan da niyyar duban sa dan rashin gamsuwa da zancen Sayeed Fayzul-haq a maimakonsa, tasan bazai barta ba, dolene ta samu hukunci dai-dai da laifinta. Sake tsinkewa zuciyarta tai sakamakon shigar idanunta cikin nasa da ke mata kallon ƙasa-ƙasa da ta gagara iya bashi fassara, sai kawai taji jikinta ya fara ƙyarma. Bata san ta ya ba, bata san ya akai ba taji an riƙe kofin shayin hanunta da ke faman tangal-tangal zai kife a jikinta. A raunane, a kuma birkice ta sake ɗago manyan idanunta da ciwo ya sakasu raunana haɗe da kumburowa. Damar sarƙesu ya sake samu cikin shanyayyun nasa masu kaifi, sai kawai ta saki kuka, kuka irin wanda ta jima da son tayi, kuka irin wanda take buƙatar mai lallashi, kuka irin mai nuna tsananin bukatuwar ɗumin mahaifa ko shaƙiƙan ƴan uwa da zasu rungumeka su lallasheka. Cigaba yay da kallonta kawai shima zafin shayin na ratsa masa hannun da har ya fara gumi ga raɗaɗi na shigarsa. Baya son ji dan yana matuƙar sukarsa, sai dai bazai hanata ba dan yafi son tayisa har iya iyawar jin ta gamsu a karan kanta. Takoyi ɗin fiye ma da yanda yake buƙata, dan sai da ta kai har ya fara cije lips ɗinsa a tsakkiyar haƙora. Sai dai ƙasaita, izza da tsananin miskilanci mai samun jagorancin gudanar jinin mulki da ke tare da shi ya hanashi cewa da ita komai, koman da koda kuwa abinda ya shafi laifinta ne harta fara jan numfashi a suƙe mai alamar ƙoƙarin haɗiyewa........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (11) .........Doctor dai da Sayeed Fayzul-haq kawunansu a ƙasa mamaki na ratsa su, dan ba abinda sukai zaton gani ba kenan musamman idan akai la'akari da laifin Zawjata-almilk ɗin. Daneen Ammarah kam idanunta ta lumshe tana mai sakin murmushi da addu'a mai girma a ƙasan zuciyarta. Duk da tasan gane ainahin abinda ke cikin zuciyar wannan gwarzon nasu abune mai wahala, mutum ne miskili da ya gajesa wajen uwa da uba. Ga zurfin cikin tsiya uwa uba jinin mulki dake yawo a jikinsa. Sai dai hakan baya nufin taƙi son tabbatuwar abinda take fata ɗin.... “Wannan ya huce a canjashi da wani Mamy”. Ya faɗa a can ƙasan maƙoshi yana miƙewa tamkar bashi ne yay maganar ba. Da alama Daneen Ammarah ta fahimci abinda yake nufin, dan kallo ta bisa da shi mai tattare da ɗan murmushi har ya fice Sayeed Fayzul-haq da Doctor suka take masa baya. “Muna godiya da wannan karamci”. Ta faɗa dai-dai zai fice a ɗakin. A yanzun ma Sayeed ne ya amsa mata da tausasawa, yayinda shi ya fice abinsa. Daneen Ammarah ta sake sakin murmushi da zaunawa a gefen Iffah, kofin shayin ta amshe tana ƴar dariya. “Haba Ibnati, irin wannan rawar jiki haka! Ki kwantar da hankalinki insha ALLAHU babu abinda zai faru sai alkairi. Abni adalin shugaba ne mai son kwatanta adalci wa kowa koda kuma maƙiyinsa ne”. Kalmar ƙarshe da ƙarfi ta zabiri Iffah. Sai kawai ta sake fashewa da kuka tana mai jujjuya kanta lips ɗin ta na rawa. “Mamy nayi kuskure, kuskure irin wanda bazan iya yafema kaina b.....” “Ya isa haka”. Daneen Ammarah ta faɗa tana mai ɗora mata yatsa akan baki alamar tai shiru. Shirun kuwa tai sai dai hawayen basu bar zuba ba, ga jikinta na ɗan tsuma har sai da ta rungume ta cike da lallashi.. *_★.. TA-ƘURYA ..★_* Da ƙyar take shaƙar numfashi da fesarwa sakamakon warin da ƙarin harma da tsamin dake tashi a cikin kogon dutsen mai tsananin saka hautsinawar ciki. Cikin son danne aman da ke ta yunƙuro mata ta sake gyara mayafin dake jikinta ta ƙarashe zancenta da, “Ruƙuƙi mai cika aiki na yarda da dukkan al'amarin ka tunda ƙawata ta bani labarinka. Na yarda zaka iya ƙarashemin abinda uwa ta fara, na yarda zan ƙarasa samun cikar burina a gareka, ina son a kawar min da duk wanda yace zai min karan tsaye ko wanene shi a duniyar nan.....” (Wa'iyazubillah. Ya rabbi ka hanamu ɓata akan son zukatanmu😭👏) Wata irin basamudiyar dariya Boka Ruƙuƙi ya kece da ita, hakan ya bama hamami da ɗoyin bakinsa damar sake busowa a cikin hancin ta ƙurya da takejin cikinta na hautsinawa, tun a shigowarta kogon dutsen sihirtaccen ƙamshin turarenta mai narka zuciyar mai shaƙa tuni warin kogon dutsen ɗakin boka Ruƙuƙi ya disashe sa. Amma ta jure ta danne domin samun cikar burinta ya shafe kowanne ƙalubale da zai iya shafarta. Boka Ruƙuƙi ya gimtse fuska bayan ya gama kwasar dariyar tamkar bashi ba. Ya ƙara juya jajayen idanunsa da ke sake fidda munin fuskarsa yana mai girgiza ƙaton kansa. “Duk ƙasar ruman babu wani boka mai ƙarasa miki aikin da uwa ta fara. Ki ɓace, ki ɓace gareni butulu inba hakaba zan ruguza duk wanda tai jajircewar gina miki. Uwa uwar kowa ce mai share kukan masu kuka, butulu ki ɓace gareni, maza ki ɓace!!!!”. Ba ƙaramar gigitata tsawar tayi ba, tuni ta manta da matsayinta ta fito a matuƙar kiɗime har tana gware da dutsi ALLAH dai ya taimaketa kan bai fashe ba. Tana gama fitowa ta fara kwara amai, amai matuƙa tamkar zata amaryar da ƴan hanjinta. Kasancewar daji ne ga kuma dare ya tsala daga inda amintacen hadiminta ke jiranta ya dinga jiyo kakarin amanta. So yake yazo ya taimaka mata sai dai yana matuƙar jin tsoro, jin dai ta cigaba dayi yay ƙundunbalar nufarta cikin matuƙar sassarfa hannunsa ɗauke da gorar ruwa. Ƙasa ya zube duk da duhuwar da wajen ke da shi, cikin rawar jiki yake jera mata sannu da miƙa mata gorar ruwan. Amsa tai dan tana matuƙar buƙata, ta ɓalle murfin ta shiga sheƙama fuskarta batare da ta damu da yanda yake jiƙa har jikinta da tsadaddun kayanta ba. Sai da ta kusa juyesa tas kafin ta kuskure baki da sauran ta tsillar da robar tana sakin numfashi da ɗaɗɗaya. Batare da tace da hadimin ko ci kanka ba ta nufi motar da suka zo bayan ta maida norse mask ɗin fuskarta batare data bar hadimin ya ga ainahinta ba. Da gudu ya miƙe ya rigata isa, shi ya buɗe mata murfin har sai da ta shiga sannan ya nufi mazaunin driver... Daga nesa da masarautar ya tsaya a inda suka ɗauka motar, Ta-ƙurya dake a bayan motar ta jawo dukkan kayan ɓadda kamarta ta maida a jikinta, haka shima hadimin nata sannan suka fita a motar. Kamar yanda suka fita ta ɓarauniyar hanya da taimakon hadimintan haka suka koma cikin masarautar. Ta sauke bahaguwar ajiyar zuciya lokacin da take zubewa a saman ƙawataccen gadonta. Har yanzu kanta juya mata yake, har yanzu warin da ta shaƙo ya gagara barin hancinta. Ga matsanancin tashin hankali, taya ita kam zata lallashi uwa, bayan ɓacin rai ya rufe idanunta ta faffaɗa mata maganganu marasa da ɗi. Ta ina zata fara? Matsaloli sake yawa suke a rayuwarta.... ★★.... ★.... Samun lafiyar Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed ta saka razanin a zukatan wasu a cikin masarautar matuƙa. Dan da gasken gaske ba haka suka so ba. Ga soyayyar mutanen ƙasa tako ina bisa ɓoyayyun alkairansa da suka gano sanadin ganin fuskar a zahirin Shahan-shan ɗin su yanzu. A yanzu kam babu inda zakaje kaji ana zaginsa sai abinda ba'a rasa ba kasancewar duniya duk masoyanka sai ka samu maƙiya, hakama duk maƙiyanka sai ka samu masoya. Shari'ar farko da yay shirin fara gabatarwa itace kawo dai-daito tsakanin iyayensa. Sai dai kuma sam hakan yaƙi yiwuwa saboda Malikat Bushirat ta matuƙar ɗaukar zafi. Dan gaba ɗaya tana kallon Malikat Haseenat ne a mai son kanta da fifita bare sama da gudan jininta. Harzuƙar tata na hauhawa ne bisa jagorancin rura wutar da su Miran Jasim keyi ta bayan fage. Yayinda ita kuma Malikat Haseenat tai biris kamar ma bata san mike faruwa ba. Ta kuma tsaya tsayin daka wajen bama Iffah kariya da ƙara tsaurara tsaro na hana bama kowa hanyar iya cutar da ita. Al'amarin na ƙara rikitar da kowa dan an kasa gane bakin zaren takun saƙar tasu akan Iffah balle manufar kowanne. A randa doctor ya sallami Iffah dole aka maidata kurkuku, dan rikici neman tashi yayi a zaman fada tunanin wasu haka shine take-taken Tajwar Eshaan ɗin. Shi dai komai baice musu ba har suka gama cece kucensu. Sai a washe gari ya bada umarnin tsaida ranar da za'ai zaman shari'a. Dan a zahiri ba su Miran Arshaan bane kawai ke tada jijiyar wuya kan ganin anyi shari'ar, har Malikat Bushirat zungurarsa take yi matuƙa akan al'amarin. Acewarta in har bai gurfanar da Iffah ba ita zata ɗauka duk matakin da ya dace a kanta... ★.... *21/4/2022* Rana ce data kasance na zaman shari'a tsakanin Iffah da ahalin Tajwar Eshaan akan yunƙurin halaka ɗan su. Ƴan jarida sun so halartar wannan shari'a ƙwarai da gaske, hakama jama'ar gari. Sai dai hakan bata faru ba sakamakon cewar Shahan-shan wannan shari'a ce ta cikin gida. Ba haka su Miran Jasim suka so ba, sai dai basu ce komai ba dan kar nuna zaƙewarsu yay yawa ya harbosu dan sun san hatsabibi ne. A yanzun ma suna cikin taka tsantsan ne a duk wani motsinsu. Kasancewar shari'ar cikin gida ce kamar yanda Shahan-shan ya faɗa da kansa anyi zaman gudanar da ita ne a falonsa na biyu. Zaman ya kasance a iyakar waɗanda ya shafa, sai manyan masu faɗa aji a ɓangaren shari'a. Falon yay tsit kowa ya nutsu kawunansu a rissine duk da kasancewar duk iyayensa ne a wajen da kuma yayunsa, sai dai girman da ALLAH ya ɗaura masa na shugabancin da har suma suka kasance a ƙarƙashin sa ya tilasta musu biyayyar da girmama wannan girman koda basa so. A sannu ya ke binsu da ido ɗaya bayan ɗaya har idanunsa ya sauka a kanta ƙyam. (Miyasa kika fi yarda da zaɓa mana haka a lokacin da zaɓin ya fi rinjayen kasancewa a zaɓin wasu?) Ya ayyana a zuciyarsa cikin ɗan jansu idanunsa luuu, lumshesu yay tare da ɗan matsesu, sai kuma ya buɗe yana mai kauda kansa. Kusan tsahon mintuna biyu yaja isaka ya fesar yana mai ɗanyin gyaran murya da sake saita kansa. A nutse Sayeed Hanifud-Din ya fara da, “Alhmdullih kamar yanda na sani kuka sani yau ranar 21/4/2022 zamu fara sauraren wannan ƙara. Muna roƙon UBANGIJI ya bada ikon kamanta zartar da hukuncin adalci wajen bama mai hakki hakkinsa batare da san zuciya ba”. A tare aka amsa da amin har lokacin kawunansu dai a ƙasa. Ƙoƙarin hana idanunsa da ke fusga gareta yay. Sayeed Hanifud-Din ya cigaba da faɗin, Muna buƙatar sake ji da ga bakin masu ƙara. Muna fatan abinda ke a zukatansu ne zai fita a harsunansu, kuskuren hakan na nufin ɗaukar mataki takowace fuska da shari'a a ta koyar damu”. Kawuna suka shiga gyaɗawa da ambaton (Insha ALLAHU) alamar tabbatar da abinda ya bukata ne zai tabbatan. Miran Arshaan ya sake rissinar da kansa da gyara zama na tsantsar nutsuwa da duba ladabi. “Ni sunana Miran Arshaan ibn Abdul-majeed Aliy. Zan kasance mai wakiltar ahalina dangane da guba da Zawjata-almilk ta zuba ga ɗanmu a yunƙurinta na kasheshi ranar 21/2/2022. Muna roƙon adalin shugabanmu mai albarka daya yanke mata hukunci dai-dai da laifinta dan ya zama izina ga ƴan baya. Ngd.” Babu wanda ya motsa a falon, tsahon mintuna biyu Shahan-shan ya nisa yana mai ɗauke dubansa ga Miran Arshaan ya maida ga sauran ahalinsa. A karon farko ya motsa lips ɗinsa a hankali, “Ko masu ƙara nada sauran wani ƙarin bayanin bayan wannan?”. Kawunansu suka shiga girgiza wa alamar a'a. Komai baice ba ya ɗauke kansa ya maida ga Iffah da tun da aka shigo da su a falon bata ɗago ta kalla kowa ba. “Ko wadda ake tuhuma tana da ja akan abinda ake tuhumarta da shi? Ko abin cewa?”.........✍️ Miran Jasim Miran Arshaan kuyi takanku aradu ba ruwana😂🏃🏻‍♀️🏃🏻‍♀️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (12) .......Iffah da ke ƙoƙarin danne kukanta ta girgiza kanta alamar a'a. Idanunsa dake mata kallon ƙasa-ƙasa ya ɗauke ya maida ga Sayeed Hanifud-Din dake riƙe da takardar tuhume-tuhumen da akema Iffah. Miƙewa Sayeed.. yayi yana mai risinawar girmamawa ga Shahan-shan. Kafin ya sake gyara tsaiwarsa ya maida kan Iffah. “Ranki ya daɗe wannan kotu mai adalci na son ji daga bakinki dangane da waɗan nan laifuka da ake zargin kin aikata su. Shin kin aikata da gaske? Ko kuwa dai abin ba haka bane......” “Ba haka bane? Kenan ma ƙazafi mukai mata bayan da bakinta ta furt.....” Jasrah ce mai maganar rai ɓace. Sai dai muƙut ta haɗiye batare da ta ƙarasa faɗar ba sakamakon kallon da Tajwar Eshaan yay mata, dan a yanzu sarkinta ne shi ba ɗan yayarta ba. Idanun nasa ya juya kan Sayeed.. alamar ya cigaba. Sayeed ya sake rissinar da kansa da ɗan rankwafawa sannan ya sake maida hankalinsa ga Iffah. Tayi matuƙar jarumta da ƙoƙarin danne hawayen domin hanasu cigaba da zuba. Sai dai tanajin raɗaɗinsu a ƙarƙashin zuciyarta, har hucinsu na rige-rigen fita da numfashinta. Ta sani basai Jasrah tace komai ba, su dukansu zafinta sukeji, dan dukansu taga hakan a fuskokinsu, Daneen Ammarah ce mai ɗan sassauci, bakuma tada abinda za tace a kanta itakam..... “Kotu na sauraren Zawjata-almilk”. Sayeed Hanifud-Din ya faɗa a girmame duk da kuwa ya haifeta. Murmushin da ya bama kowa mamaki Iffah ta saki, tare da ɗago fuskarta a karo na farko yanda zata iya duban kowa. Sai dai bata aminta ta haɗa idonta da kowan ba. Tsaiwarta ta gyara idonta na kallon sashen su Miran Jasim ƙasa-ƙasa, murmushi ta sake saki a karo na biyu dan ganin yanda duk suka shiga yanayin firgici sai mazurai suke, duk da suna ƙoƙarin dannewa kuma. (Ku kwantar da hankalinku ai ba'a zo wajen ba) ta faɗa a zuciyarta tana ɗauke kanta. A zahiri kam natsuwarta ta sake tabbatarwa tana fuskantar kotu da ƙyau. “Ni Fareedah bint Zayyan zan fara da bada haƙuri kafin cewar da kowa ke buƙata da ga baki na. Nasan ko ba'a kawoni nan an gurfanar ba na can-can-ci acema bana numfashi a dalilin taɓa rayuwar mutum mai girman iko kamar Shahan-shan. Basai na wahal da Shari'a ba tabbas nice da kaina na bashi madarar da ya sha mai ɗauke da dafin macizai....” Babu wanda bai zaro idanu ba a mutanen falon dan mamakin ƙarfin halinta. Shiko uban gayyar da furucin nata yazo masa a bazata kafeta kawai yay da idanu zuciyarsa na matuƙar mamakin ƙarfin halin takife ɗin yarinyar... Cikin ɗan taɓe baki Iffah ta ɗage kafaɗu tamkar bataga yanayin da duk suka shigaba ta cigaba da faɗin. “Sai dai ba bashi madarar bace ya kamata ya zama abin mamaki ga wannan kotu mai adalci, sannan kuma ba itace ya dace ta zama abin tuhuma ba ko burin ganin an hukunta nin da kowa ke faman haƙilo da kai kawo sai kace kunajin tsoron numfashina barazanace gareku. Ni inda nice ku, tushen samuwar madarar zan maida hankali sani. Amma duk da haka ina so mai girma Shugabana da ku ahalinsa ku duƙufa wajen bincikowa, ba kuma dan inajin tsoro ko shakkar hukuncin da za'a min bane. Ba kuma dan zan kasa kama sunan wani bane wajen bayyana yanda akai madarar tazo hannuna ba. Ku da kanku nake son ku gano kafin ku sami dukkan amsoshin da kuke buƙata daga gareni dan ko numfashina zai tsaya sai na fesar da su ne tun daga tushe, ku kanku masu kisan Zawjata-almilk na baya sai ku shirya ranar tonon silili na tunkaro ku in har numfashina na harbawa daga gangar jikinna. Da ga ƙarshe ina roƙon wannan kotu mai adalci data sallami amintaccen hadimin shugabana tare da masu dafa masa abinci dan basu da laifin komai, su kuma masu ganin sun binne Iffah ne su shirya akwai sauran wasan dan ko filin ba'a share ba. Dan sai sun biya fansar jinin ƴan uwana uku da na iyayena koda zasu sami nasarar shafe nawa babin a doron wannan ƙasar”. (Fitinanniyar yarinyar nan zata sa su binne ni a tsakkiyar ƙasata) ya faɗa a zuciyarsa yana mai lumshe idanunsa da ke bin lips ɗinta da kallon ƙasa-ƙasa, murmushi da ke neman suɓuce masa ya haɗiye a zahiri acan ƙasan zuciyarsa kuwa yinsa yake. Wanda bai sani ba sai ya ɗauka idanun nasa a lumshe suke, ga fuskarsa cike da barazana mai saka ruɗani ga duk wanda zai iya dubansa saboda yanda ya ɗaureta tamau..... Kusan kowa sai da ya ɗauke numfashi a falon. Zukatansu kam na wata irin duka kamar ganguna, kalaman Iffah basu da banbanci da saukar nakiya a tsakkiyar kasuwar da bazaka iya banbance akan kanka ta fashe ba ko makwafcinka dan tsabar ruɗani. Cikin rashin yarda da kai aka shiga kallon kallo, kowa tsoron fara tankawa yake ko yin ƙwaƙwƙwaran motsin da zargi zai iya sauka a kansa. (Kun san mai kaza a aljihu fa baya jimirin asss). Malikat Ashwaq ta ɗan juya idanunta cikin ɓacin rai zatai magana da sauri Ameera Danish-Ara ta danne mata yatsun hannu tana mai haɗiyar yawu da ƙarfi. Shiru tai ta haɗiye abinda yake shirin suɓuce mata. Hakama Malikat Bushirat duk da kalaman Iffah sun daketa da ƙayatar da ita sai take jin kamar wani makircine yarinyar ke son ƙullawa domin kufcewa hukunci. Itama yunƙurawar tai zatai magana Daneen Ammarah ta girgiza mata kai da sauri. Sayeed Hanifud-Din da gaba ɗaya shima yay mutuwar tsaye da waɗan nan kalamai na Zawjata-almilk da babu ɗar ko shakku na tsoro a idanunta duk da raunin dake tattare da yanayinta, jiki a sanyaye ya maida dubansa ga Shahan-shan. Babu alamar zaice wani abu har tsawon wasu mintuna da tashin hankalin duk wani wanda ke a falon ke sake bayyana. Sai da ya mula dan kansa yay gyaran murya. Cike da nutsuwa da ƙasaitar data zama ado ga sanyinsa ya ɗan sake dubanta da kallon da ke tada mata tsigar jiki a duk sanda ya yinsa. (Kinfa kife fuska tunda kin ɓallo min ruwa) a zahiri kam sai ya sake gyara gilashin fuskarsa kaɗan. “A bisa baƙon al'amarin da ya shigo a wannan shari'a bisa furucin wadda ake tuhuma, zamu ɗage wannan zama har zuwa nan da kwanaki uku. Za'a sake tsaurara tsaro ga wadda ake tuhuma fiye da da. Roƙon sakin wasu bai karɓu ba. Idan kuma da mai buƙatar cewa wani abu kotu na saurarensa”. Shiru kowa ya kasa cewa komai, da alama wasu sun tsargu da tunanin cewar tasu zata iya zama talala musamman a sanin kaifin basira da sukaima Shahan-shan ɗin nasu. Hannun da yaga an ɗaga ya bi da kallo har ya sauke idanunsa kan kakar tasa, hakama duk wanda ke'a falon kallon nata yake. Malikat Haseenat ta jinjina kanta cike da dattako bayan kotu ta bata izinin maganar data nuna bukatar yi. A ladabce tai ƙasa da idanunta. “Muna godiya da wannan adalci na adalin shugabanmu, muna kuma roƙo a bisa adalcin wannan kotu ta bamu belin wadda ake tuhuma kodan kare lafiyarta da ranta da za'a iya nema a koda yaushe a dalilin furucin ta, babu yanda za'ai masu waɗan nan laifukan da ta ankarar su koma gefe su naɗe hannun zaman jiran a bankaɗosu batare da yunƙurin cuta mata ba”. Nanma shiru kamar bazai amsa ba, bayan shuɗewar wasu mintuna kuma sai ya motsa. “Kotu ta gamsu da roƙon, sai dai bazata iya bada belin wadda ake tuhuma ba har sai an samo wani haske koda ƙanƙani ne da ga abinda ta faɗa ɗin. Za'a iya sake nema a zama na gaba”. Daga haka ya miƙe abinsa cike da ƙasaita yana takun nan nasa na izza da bajinta. Dole kowa yay ƙasa da kansa har sai da ya fice sannan kowa ya ɗago. Iffah da ke jin ana kallonta ta ɗan ɗago kanta, ilai kuwa idanun Miran Arshaan da Miran Jasim ta gani na kallonta kamar zasu faɗo. Wani irin shegen makirin murmushi da ya nema wantsalo zukatansu waje ta saki tana mai kanne musu ido ɗaya da musu wani irin salo da yatsunta uku ta ɗauke kanta. Dan jam'ian dake tsare da ita sun zo tafiya da ita za'a maidata kurkuku. (Wannan ƴa ta Babiy dai to sai ta sa anyi farfesunta a daular ruman 🥲🚶) ★★★...... Har karo suke da juna yayin tafiya tsabar fita a hayyaci. Da ƙyar suka iya ƙarasa kai kansu falon Miran Jasim da ya zamar musu mahaɗar tattauna matsalolin su. “Tabbas kasheta zanyi, da hannuna kuma zan kashe matsiyaciyar yarinyar nan a yau”. “Da hakan mizai hana kaje kace masa kai ne kawai ka bada madarar”. Miran Jasim ya faɗa cikin tsananin ɓacin rai yana wurgama Miran Arshaan da yay maganar farko harara. Shima a harzuƙe ya dubesa. “To mi kake so muyi ko jira? Kai a tunaninka wannan yarinyar mai kama da agwagwar ƙwa-ƙwa ta ƙi bayyana sunanmu ne danta rufa asirinmu? To ka dawo hankalinka idan ma ya suɓuce maka ne. Dan tarko ta kafa mana, tarko na talala garesa da bama mu ba hatta iyayen da suka haifemu sai munyi dana sanin zuwansu wannan masarautar. Ban taɓa sanin tsagerancin ƴar iskar yarinyar nan ya kai haka ba.” Miran Jasim ya saki murmushi yana dafa kafaɗar Miran Arshaan. “Akwai abinda ta taka ne, amma zamu sauke mata shi ta yanda ya dace. Zamu tabbatar mata da mu iyayen iyayenta ne a wannan fanin na makirci. Ina son ka kwantar da hankalinka Akhi, ba ita ba, hatta shi mai yanke hukuncin anzo gaɓar da.....hhhhhh”. Ya ƙare da ƙyalkyalewa da dariya batare da ya ƙarasa ba........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (13) ..........Cikin kallon kai mahaukaci ne Miran Arshaan yaja guntun tsaki. “Na kwantar da hankali fa kace? A gaɓar da nake hango cikar 99days ɗina kake tunanin kwanciyar hankali a gareni. Jasim kanka kawai ka sani a hatsabibanci, dan haka kar kai sakaci da ɗan hakkin da ka raina, dan shike zama RAINA KAMA KAGA GAYYA. Da ganin idon wannan tsinanmiyar yarinyar kai ka san akwai abinda ta taka. Nama fara zargin shegen yaron nan ba yana tare da ita bane kuwa?”. Kalaman Miran Arshaan sun sanyaya jikin Miran Jasim da alama, dama can ƙarfin haline kawai. Yaja numfashi mai nauyi yana jinjina kansa. “Hakane Arshaan, amma ina son ka fahimta kasheta ma kai tsaye ba abune mai sauƙi ba. Dan bazasu taɓa iya sakaci da bata kariya ba kamar yanda munafukan tsohuwar can ta ambata. Damar da ke garemu kawai a yanzu shine komawa wajen Barbushi. Shine ya kamata ya mana wannan aikin”. Jiki a saɓule Miran Arshaan ya jinjina masa kai shima alamar gamsuwa..... ★★★....... Duk yanda yake yaƙi da murmushin a karo na babu adadi ya gagara nasarar dakatar da shi bayyana a kan ƙyaƙyƙyawar fuskarsa. Akan dole dai ya sakeshi tare da lumshe idanunsa. “Fitinanniya”. Ya faɗa a hankali da sake nutsa kansa cikin lallausar kujerar da yake zaune. *_(Kai malam baka san darajar mutane bane?....)_* Kalaman da suka zama na farko a haɗuwar farkon da bazai taɓa iya mantawa ba domin rubutattu ne a sashen da baya goge muhimman abubuwa suka dawo masa kamar yanzu take furtasu. *_(Ka kusan bige yaro amma tsabar kanka ba'a dai-dai yake ba shine koka fito kaga yaya yake ma saboda ku masu kuɗin nan ɗaukar talaka kuke baida banbanci da titin da kuke gurza tayoyin banzayen motocinku da kuka saya da kuɗinmu”). (“Anƙi a bakun, wlhy duk sai kun fito kun dubashi kun bama kakarsa haƙuri zan baku key ɗin nan, inba hakaba sai dai mu kwana anan.”)._* “Zaki iya”. Ya faɗa a hankali da ƙara sakin ɗan wani murmushin da kauda fuska kai kace bayan shi akwai wani a ɗakin. Ƙoƙarin ture komai yake sai dai hakan kamar da wahala dan komai kokawar sake maimaita kansa yake tamkar a yau ne ranar ke faruwa (Idan hanunka ya sake gigin taɓa koda hijjab ɗin jikina ne sai na karyashi, Sannan koda Shahan-shan ne yay wannan aikin bai isa barin wajen nan ba balle kai shashasha driver”) (“Daga yau ko daga nesa kuka hangoni to ku canja hanya koda a jirgi kuke kuwa”). Idanunsa ya lumshe da kai hannu ya shafi tattausar baƙar sumar kansa. Sai kuma ya miƙe cike da ƙasaita yana mai ɗan sakin murmushin gefen baki da faɗin, “Drama queen”. (☺️Da alama su Shanshani an shiga lambun fulawoyi🥱🚶) ★★...... ★.... “Mammah wlhy yarinyar nan ta fara bani tsoro nikam”. Daneen Ammarah ta faɗa da alamar tsoron da gaske a kan fuskarta. Murmushi Malikat Haseenat tayi har haƙoranta na bayyana. Sai kuma ta dubi Daneen Ammarah ɗin da ƙyau cikin ido. “Banda abin Ammarah minene abin tsoron anan to?...” “Mammah akwai wlhy, ki dubi fa furucin da yarinyar nan keyi, ni gaba ɗaya komai ma neman ƙwacemin yakeyi. Ga shi tun ɗazu nake neman sister (Daneen Waheeda. Ƴar uwarta dake aure a yankin larabawa) amma wayan yaƙi shiga.” Sosai Malikat Haseenat ta tsareta da idanu, sai kuma ta ɗan muskuta kamar mai son bada gargaɗi “Badai sanar mata zakiyi ba? Kirki ma fara wannan gamgancin, kin san dai halinta ko, fitinanniya ce ta gaske. Bata haɗa al'amarin duk wani jininta da kowa ba. Kuma kin san yanda ta nuna adawarta akan auran yarinyar nan da janta da mukai jikinmu tun farko saboda ƙin bata haɗin kai taƙi zuwa ko dubashi duk da labarin abinda ya samesa babu inda bai karaɗe ba”. A sanyaye Daneen Ammarah ta jinjina kanta. “Hakane kuma Mamma, kiyi haƙuri wlhy abinne duk ya ɗaure mun kai. Ita waccan (Malikat Bushirat) da zamu iya tattaunawa kuma an riga an birkita al'amarin ta da zuga gaba ɗaya. Amma gaskiya furucin yarinyar nan ya matuƙar gigitani. Mita sani haka akan abinda kowa bai sani ba? Ta yaya ma ta sani ɗin bayan bata da alaƙa da wannan masarautar a lokacin da abubuwan ke faruwa. Anya kuwa Iffah ba aljana bace Mamma”. Dariya sosai Malikat Haseenat keyi, sai da tai mai isarta ta tsagaita tana mai duban Daneen Ammarah da tai kasaƙe tana kallonta. “Babu wani aljana Ammarah. Mutumce kamar kowa. Kuma duk abinda kike tunanin ta sani ɗin a ɗan zaman nan nata ta fahimceshi. Ni kaina na san yarinyar hatsabibiya ce, sannan akwai wani ɓoyayyen al'amari tattare da ita mai girman gaske da ita kanta bana tunanin tasan akwaishi tare da ita”. “Mamma kema fa kin fara bani tsoro”. “To ko nima na zama aljanar?”. Malikat Haseenat ta faɗa cike da zolaya tana murmushi. “Wayyo Mamma ni dai bance ba kar kisa jikanki ya tsireni a tsakkiyar masarautar sa. Kinga tafiyata”. Da kallo kawai Malikat Haseenat ta bita tana murmushi. Tana matuƙar ƙaunar ɗiyar tata da tausayinta. Ammarah itace ɗiya mafi soyuwa a ranta. Dan ta haɗa abubuwa da yawa da ƴan uwanta basu da shi. Ga kuma ƙaddarar da ta sameta wadda har yanzu sun kasa fahimtar tushenta, duk da dai zuciyarsu na karkata musu wani abu daya shuɗe a rayuwarsu mara daɗin tunawa. Taja siririn tsaki da kauda al'amarin a ranta cike da ƙunar zuciya...... ★★..... Dariya take sosai mai haɗe da kuka. Dariyar na zuwa mata ne a dalilin tuno fuskokin Miran Jasim da Miran Arshaan a ɗazun, harma da na waɗanda bata san dalilin razanar tasu ba game da furucin nata. Kuka kuwa tana yinsa ne da sanin ko mi zatayi a yanzu ta dai riga ta rasa ahalinta, rasawa ta har abada. Sai dai koba komai tana jinta sakayau a yau, kai koda ace su Miran Jasim sun halakata a wannan daren bazatai baƙin ciki ba. Dan wannan ruɗanin da ta saka a zukatan manyan masu faɗa ajin masarautar zai zama rikici ne na har abada da zai cigaba da hanasu farin ciki. Sannan zai fargar da al'ummar ƙasar ruman son sanin wanene Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed da banbance abinda suke son sanin gaskiyarsa. Shima zai sakashi ya maganantu ga al'ummar tasa ko da babu haka a cikin kundin tsarin mulkin nasa. Zai saka tsoro kuma ga masu kashe masa matan da zai sake iya aura anan gaba. Ta jefa tsuntsu biyu da dutse ɗaya kenan, kuma harga ALLAH ta sako zance masu kashe masa mata ne badan tasan komai akan hakan ba, sai dai zuciyarta na zargin su Miran Jasim ɗin ma anan, dan tunda suka iya shirya kashe Tajwar Eshaan ɗin lallai zasu iya halaka matansa dan su goga masa baƙin fenti ko wani dalilinsu da ban. “Na barku da wannan a halin daular ruman”. Ta faɗa tana sake ƙyalƙyalewa da dariya a karo na babu adadi tun maidota ɗakin kurkukun. Masifaffen kamshin da ya daki hancinta da kai saƙo cikin ƙwaƙwalwarta kai tsaye ya sata haɗiye dariyar. Shiru tai zuciyarta dake ƙoƙarin ƙaryata ƙwaƙwalwar tata na kaikawo da sauri-sauri. Tabbas alamar tsayuwar mutum take ji a ɗakin, sai dai yaushe ya shigo? Ta ina kuma? Shine abu mafi ban mamaki. Cikin ƙoƙarin son kauda abinda brain ɗin ta ke son tabbatar mata duk da zuciyarta na ƙaryata wa ta ɗago kanta data tura cikin cinyoyi. Zabura ta ɗanyi idanunta na sake fitowa waje, sai kuma ta shiga waige-waige. Shi ɗinne dai a zaune, zama irin na ƙasaita da iko a cikin sabon ɗakin nata na kurku da aka canja mata a yau. Ga wani kwarjini da cikar haiba zagaye da ƙyaƙykyawar fuskarsa dake bayyana shekarunsa. Ko maƙiyinsa ya kallesa yasan ya iya tsara ado, adon da koda a ƙaramar sutura yayisa sai ya nuna kansa.... Ƙafarsa dake kan ɗaya ya sauke, hakan ya sakata dawowa hayyacinta tai saurin kauda kanta tana cure fuska waje guda ita a dole ba kallonsa take ba. Shima cikin nasa salon basarwar ya kauda nasa idanun dake mata kallon ƙasa-ƙasa yana mai miƙewa gaba ɗayansa. Hannayensa biyu duka ya zuba aljihu tare da yin ɗan taku ɗaya zuwa biyu tamkar namijin tantabarar da ke son birge matarsa, sai kuma ya juyo a sannu gareta ya sake sauke kaifafan idanun nasa a kanta. Cikin yanayin son lumshesu da sake buɗewa ya motsa lips ɗinsa cikin sautin ƙasan maƙoshi ya furta, “Wacece ke? Mi kike buƙata? Waya turoki a gareni ko ga ahalina? Dukiya? Mulki? Ko yin suna?”. Tabbas kalamansa sun mata zafi, sai dai kwarjininsa da wata kima da take kallonsa da shi a cikin idanunta sun hanata koda motsi. Shiru kusan na minti ɗaya taƙi ta tanka, sai can kamar wadda aka zaburar taja nannauyan numfashi da sake suƙe fuska tana mai fisgo jarumtarta a zahirance ta saki sassanyan murmushi. Da ƙyar ta iya riƙe rauninta wajen bashi amsa tana mai haɗiye murmushin. “Ni ba kowa bace. Bana buƙatar komai ga wani na sai UBANGIJI na. Farin cikin dunƙulallen ahalina zinare ko lu'u-lu'u da duk dukiyar da ƙasar ruman ke taƙama da ita bazai iya sayensa ba. Mulki baya cikin lissafina dan bai taɓa ko birge ni ba. Da suna nake buƙata akwai hanyar da tafi wannan da zan bi nayi duniya ta sanni ba ƙasata ba kawai ta ruman. Ni na turo kaina domin rama cuta ga macuci koda ace ya kasance k.....” Sai kuma ta haɗiye tana mai kauda kanta da ga kallon da yake mata. Jin babu alamar zai daina kallon nata ya sata sake juyowa garesa fuskarta a tsuke kamar yanda tasa take. Suɓul ɗan ƙarfin gwiwar da take da ya suɓuce kamar yanda takejin saurin kuzarinta na ida sabulewa da ga gangar jikinta shima. Idanu ta zuba masa a karo na biyu tamkar wata gaula ko shasha. A yanda take kallonsa da ƙamewarta ya sakashi cigaba da zuba mata idanun shima, sai dai duk da kallon nata ke ɗaukar wata siga da ban, shi tayar masa da tsigar jiki yake a sigar da shi tashi zuciyar ke amsa. Cikin son kauda abinda ke son masa kutsen ya fara takawa sannu-sannu kamar mai sanɗa har zuwa gabanta.. Ta tafi kam, tafiyar da mai kallo zai iya kira suman zaune dan tsayuwarsa gab da ita baisa ta motsa ba. Sannu a hankali ya tokare hannunsa ga ƙarfen ɗan gadon da ke a ɗakin, tare da rissinowa gareta fuskarsu gab-gab da juna ya zuƙa numfashinta ya fesa mata nasa da ya maidota hayyacinta, tsinin hancinsa kan nata tamkar zai haɗe lips ɗinsu da ya dai-daita, ƙyawawan idanunsa da suka ɗan canja launinsu tare da shanyewa kamar mai jin barci ƙyam akan nata da wani irin sassanyan kallo data kasa fassarawa. “Ko giwa ta faɗi tafi ƙarfin wawaso. Kina da kauɗi! Gaki da hayaƙi. Kar ki kaini bango na aikata abinda zuciyata ke raya min faaaa..”.........✍️ _🙄😏Mufa a daina shige mana ba wannan ya kawomu daular ruman ba, dan duk abun mutum sai mun masa hukunci ehe😌🚶. (Dangin Iffah'r mu koya kukace🥱)_ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (14) ........Zabura tai saboda yanda yaja (faaa) ɗin ƙarshe da wani salon busa mata numfashinsa mai ɗumi. Tare da waro idanunta waje tai baya gaba ɗayanta ta zube ruguf a gadon idanunta na kif-kif na shiga ruɗani. Sai kuma ta tura bakin gaba da ɓata fuska tamkar mai shirin fashewa da kuka. Idanunsa da ke a kanta ya sake shanyewa, a yanayin son basar da salon nata ya ɗan ƙara kusanta fuskokin su tamkar zai rungumeta har lips ɗinsu na gogar juna. A yanzun kam bata da zaɓin da ya wuce rumtse idanun da masifar ƙarfi, ƙoƙarin danne tsumar da jikinta keyi tayi ta hanyar son damƙo bedsheet ɗin gadon sai ta damƙo tattausan hanunsa. Da sauri ta janye nata zata yarfar ya sarƙe yatsunta cikin nasa ya matse da ƙarfin da har sai da tai zaburar da jikinsu ya manne da juna, cikin rawar baki da rashin sanin abin faɗa ta fara magana a sarƙe. “D... Dan ALLAH k.. kafin ka kashe ni ka faɗa min game da Ajmaal. Ka faɗamin game da Iyayena da aka ce ka kashe?”. Ta faɗa maimakon amsa masa tashi maganar tana mai sauke ajiyar zuciya da sauri-sauri saboda kusancin nasu ya yayi yawa. Ga ƙamshin mayen turarensa wani irin harmutsa mata lissafi yake har gashin jikinta na mimmiƙewa alamar tashin tsigar jiki. Lips ɗinsa ya motsa kaɗan tamkar zaiyi magana sai kawai jin saukar duminsu tai a kan nata, da masifar ƙarfi ta matse idonta da ƙanƙame illahirin jikinta da ya ɗauka karkarwa. Miya rage mata ita kam, kawai ta saki ihun da sai ya girgiza masarautar ko wani zai tai maketa daga ɗaurin goron da Shahan-shan ya mata, wannan salon nasa ya girmi kanta bazata iya ɗauka ba. Hannun tai ƙoƙarin janyewa a karo na biyu da lips ɗinta da ya ɗan ciza mai makon sumbatar da tai zato tamkar wadda ta ɗosana kan wuta tana mai fisgar numfashinta shima a sarƙe. Sosai abun ya so bashi dariya amma ya haɗiye kayansa yana ɗan janye jikinsa baya, dan ya fahimci zata ma iya sume masa. Aiko wata wawuyar ajiyar zuciya ta sauke ta miƙe zaune zumbur, cikin son kame rawar da jikinta keyi ta dunƙule kanta waje ɗaya. Ƙoƙarin haɗiye murmushin da ke neman suɓuce masa a zuciya yayi, a fuskarsa kam babu alamar hakan sai ma sake tsuke ta da yay fiye da farko. Jikinsa ya ɗan ja baya ya koma a kujerar da ya tashi ya sake zama yana mai harɗe hannayensa a ƙirjinsa da ɗaura ƙafa ɗaya kan ɗaya ya zuba mata idanu kawai. Tsahon kusan mintuna uku suna a haka kafin shi ya katse shirun ta hanyar gyaran murya. “Su waye su?”. Kaɗan ta ɗago tare da buɗe idanunta. A yanda taci karo da fuskarsa sai taji wani irin shakkarsa da kwarjinin sa ya sake baibaye numfashinta. Yana zaune a kame tamkar daɗa duniya tun shigowarsa bai motsa a yanda yake ba. Wani kallo data kasa bama fassara ya jefa mata ya kauda idanun. Itama sai ta ja iska ta karasa risinar da nata tana ɗan kallonsa ƙasa-ƙasa. “Saninsu kai tsaye da ga gareni ba shine ya dace ba *_Sultan_*, taka tsantsan da rayuwarka da sanya ido kan wanda duk suke zagaye da kai shine mai muhimmanci. Idan ni banci nasara a yau ba, su zasu iya ci watarana, duk da nima ba haƙura nai ba zan sake gwada sa'a ta a karo na biyu”. Ta ƙare maganar a salon juya manyan idanunta da yamutse fuskarta dake tsuke tana laɓe baki idanunta dake cike da hawaye a kansa. Sai kuma ta janye su ganin yanda ya tsareta da nasa. Bai iya ya motsa ba, kallonta kawai yake da ƙoƙarin danne abinda ke taso masa a kanta tun daga yatsan ƙafarsa har zuwa cikin tsakkiyar kansa. (Yarinyar nan ko) ya faɗa a zuciyarsa. A zahiri kam tsaf ya shanye komai daga kan fuskarsa ya haɗiyema ransa yana mai furzar da iska kaɗan tare da sake yin gyaran muryar da ta sakata sake ɗagowa dole, sai dai bata jure kallon nasa ba ta maida kanta ta rissinar. Shima ɗauke nasa yay daga kanta tare da miƙewa, ta ƙasan ido tabi takun sawayensa mai cike da izza da nutsuwa da kallo, sai da ya kai ƙofar fita gab ya dakata sai dai bai juyo ba, “Na baki dama ta biyu, in har kikaci nasarar kaudani a karo na biyu daga nan zuwa shekara ɗaya tukuycinki zama sarauniyar daular ruman bisa karagar mulkin Shahan-shan. Idan kika gaza hukuncinki zama uwar yarana biyar a ƙarƙashin ƙarfin iko ba soyayya ba....” “Bana yarda aci riba kaina bisa ƙarfin mulkin mallaka koda anfi ƙarfi na. Taya zakaci riba biyu a shekara ɗaya duk a kaina, Iffah ba tsuntsuwar da ake ajiyewa a gida domin ado bace”. Wani ɗan murmushin gefen baki yaso suɓuce masa amma sai bai bar hakan ba. A ransa ya furta (Ƴar barazana ce yarinyar nan) a zahiri kam sai yay ƙoƙarin ficewarsa maimakon bata amsa. Dan kansa har ya fara ciwo. In ba da iyayensa da Malikat Haseenat ba bayaji ya taɓa magana mai tsaho da wani a rayuwarsa kamar ta yau, shi kansa mamakin ma hakan yake, a rayuwarsa babu abu mafi bashi wahala kamar yin magana mai tsawo, shiyyasa yafi yarda da yaren kurma koda a fada ne... “Banfa yarda ba.... Soyayya kuwa ni bama ta taɓa zama abinda nake kallo da muhimmanci ba da har zanyi kwaɗayin yima wani bayan ta ahalina” Ya tsinkayi furucin nata yana ƙoƙarin ficewa. Yanzu kam sai da yay murmushin a zuciyarsa da sake jinjina ƙarfin halinta. Bai kuma juya ɗin ba yay tafiyarsa. Ta ɓarauniyar hanyar da ya fito ya koma sashensa, dan dama fita ce ta ɓadda kama. Turus ya ɗanyi da ganin Malikat Haseenat da bai zaton gani a irin wannan lokacin ba, kuma a falonsa da bazai iya tuna sanda ta shigo shi na ƙarshe ba. Basar da yanda take binsa da kallon tuhumar da ya gani a idanunta yay ya ƙarasa takowa gareta. Sai da ya kai zaune ya riƙo hanunta ya sumbata. Sannan ya furta “Idan amintacciya na buƙatar ganin gudan jininta shin ba umarni kawai zata bada ba ya isa gareta”. Murmushi ta saki a karo na farko, itama cikin nata salon girmamawar garesa duk da matsayinta kanta ta ɗan rausayar. “Idan uwa ta girmama ɗanta da ke amsa sunan shugabanta laifi ne Hafidi?”. Kansa ya girgiza yana ɗan murmushi a karo na farko. Ta san iya amsar kenan daga garesa. Dan haka cikin rashin nuna damuwa ta cigaba da faɗin, “Fita ce ta sirri, dan idanuna sun kasa rintsawa a wannan daren a dalilin furucin Zawjata-almilk”. Idanunsa ya ɗan motsa, kamar bazaice komai ba sai kuma ya nisa, “Jadda-ti miye abin hana barci a ciki? Faɗin akwai wanda ta ambata bayan mun san da su? ko kuwa furtawarta kasancewar bamu taɓa ji da ga bakin wani ba?. Shirmenta da son kare kanta da ga laifinta ne kawai ya sata furtawa itama, nasan tana da hujja kan wani ba.....” “Ina bazai yiwu ba Eshaan. Na jima da fahimtar wannan yarinyar nada wasu ɓoyayyun al'amura tattare da ita, sannan tana da ɗabi'ar zama kaifi.....” (Mai hatsarin gaske ma kuwa, dan tafi duk yanda kike tunaninta Jaddah) ya ayyana a zuciyarsa. A zahiri kam sai ya ɗan yamutsa fuska kaɗan, dan kansa ke ciwo. Can ƙasan maƙoshi ya ce, “Yanzu mi kike son ayi?”. “Karmu matsa mata da son sanin da wa sukai wannan aikin. Kamar yanda tace mu bincika da kammu muyi ƙoƙarin hakan, dan akwai wata hikima a zancen ta na bamu damar mu bincika ɗin”. “Yanda kikace haka za'ayi Jadda-ti. Sai dai kuma idan bamuyi bincike ba taya za'a yanke mata hukunci? Ni fa ƙara aka kawo min, dolene na hukunta mai laifi ko na wankesa akan gaskiyarsa”. Murmushi tayi mai ma'anoni da yawa da ita tasan dalilin kayanta. Taja numfashi ta fesar da ƙara damƙe hannunsa cikin nata. “Wannan sune siffofin adalin shugaba. Sai dai inaji a jikina a kwanaki ukun nan daka bada wani abu zai iya faruwa, dan duk masu hannu a ciki a yanzu hankalinsu ba'a kwance yake ba sam. Suna can neman hanyar ɗaukar mataki a kanta kafin cikar kwanaki uku harma da mu kammu”. Idanu ya tsira mata da mamakin jin kalamanta. Amma sai bai iya cewa komai ba. Itama bata sake cewar ba ta sumbaci hannunsa tana mai lumshe idanun da buɗewa alamar sallamar kenan. Shima nasan ya lumshe tare da rissinar da kansa ya buɗe a hankali fuskarsa da ɗan yanayin murmushi sai dai bayin yake ba. Sai dai ta kurema ganinsa sannan ya janye idanunsa da ke binta da kallo. Ya maida bayansa jikin kujera ya maida idanun ya lumshe... Duk yanda yake son hana tasirin kaikawonta a zuciya hakan ya gagara. Ƙarfin halinta, tsaurin ido da kauɗin zance na matuƙar zaburar da shi. Koda a tsoracan take sak take a zahirinta. Ba mata ba mazan ƙasar ruman gaba ɗaya shakkar masa magana suke kansu tsaye, amma ita tar idonta da muryarta ke fita garesa. Itace ta farko dake iya kallon cikin idonsa ta faɗi magana bayan mahaifinsa, amma ko Malikat Bushirat da Malikat Haseenat bejin tunda ya mallaki hankalin kansa sun taɓa hakan musamman a yanzu da yake matsayin Shahan-shan, suna masa magana da taushin harshe da kuma kimantawa, duk da kasancewar sa ɗa garesu. Amma ita duk da akwai girmamawar tattare da fitar sautinta garesa kai tsaye take babu alamar shakku, bata kuma iya ɓoye abinda ke ranta koda a inda tasan anfi ƙarfi ta ne. “Fitinanniya”. Ya furta a hankali kan tausasan lips ɗinsa yana mai miƙewa da wani irin makirin murmushi a kan ƙyaƙyƙyawar fuskarsa..........✍️ _🏃🏻‍♀️🏃🏻‍♀️🏃🏻‍♀️🏃🏻‍♀️wanga Shahan-shan ya fara bani olo_ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (15) ........“Wlhy gaba ɗaya kaina ya kulle Akia, shin yarinyar nan wani ƙulli ne take son yi dan ta kuɓutar da kanta saboda tasan babban burin kowa sanin mai kashe matan Abni ne? ko kuwa gaskiya take faɗa? Idan gaskiya take faɗa taya akai tasani mu a tsahon shekaru muka gagara ganowa? Anya kuwa shigowar yarinyar nan cikin masarautar nan tun farko bada wata ƙullalliya ba?”. Shiru babu alamar Malikat Bushirat zatace wani abu, hakan bai damu Jasrah ba ta cigaba da faɗin, “Al'amarin Mammah ya cigaba da bani tsoro a wannan gaɓar. Anya ba akwai abinda take ɓoye mana ba daya kamata mu sani?”. A karo na farko Malikat Bushirat ta ɗago ta dubi Jasrah. Sai kuma ta miƙe cikin yanayin ƴar zabira. “Kamar mi kike tunani?”. “Abubuwa da yawa Akia. Ciki harda halayyarta ta yanzu dake bayyanar da ita a mara gaskiya. Zuciyata na rayamun abubuwa da yawa fiye da yanda kike zato. Abin tambayar anan miyasa take goyawa yarinyar nan baya? Miyasa take son bata kariya? Bayan gudan jininta ta shirya halakawa? Ki duba kiga yanda taƙi bamu goyon baya akan shari'ar nan ita da Ammarah. Yarinyar nan ita aka fara kaiwa sashen Abni, kuma ita ta kaita, batai ko ciwon kai ba aka kai wata daga baya ta rasa ranta. Mi hakan ke nufi? Kaɗan daga cikin zarge-zargena kenan”. Kai kawai Malikat Bushirat ke jinjinawa alamar gamsuwa da bayanin Jasrah, dan itama wannan tunanin ya jima yana mata kaikawo a zuciya. Taƙi fiddashi ne saboda tuna halayen Malikat Haseenat ɗin masu yawa kafin yau, amma yanzu kam zuciyarta na mata rawa akan a bubuwa da yawan gaske...... ★★.... ★..... Barbushi dake kwasar dariya bayan gama sauraren Miran Jasim da Miran Arshaan ya tsagaita dan kansa ya tamke fuskar tamau kamar bashi ne yayi ba. “Ƙwarai kuna a tsaka mai wuya, tsakar da in har bakinta ya buɗe ta furta ƙarshenku yazo. Abu ɗaya zamuyi akanta, idan mun taki sa'a kun tsira. Idan akasin hakan ya kasance ku zargi kanku....” Komai basu iya sunce ba, dan zuciyarsu ta fara saka musu shakku akan gazawar Barbushi. Inba gazawa ba taya ƴar yarinya ƙarama zai dinga nuna kamar ta gagaresa. Bayan a da ya musu ayyuka manya da har a yanzu suke taka rawa da bazarsa. Ransu ɓace suka baro wajen nasa, zukatansu na matsanancin ƙuna, kowa kuma da abinda yake tattaunawa da ransa akan matakin ɗauka. Dan ko ana ha maza ha mata bazasu bar Iffah ta cigaba da numfashi ba a wannan gaɓar. Kai hatta da uban gayyar za'ai ƙurun-ƙus a wuce wajen dan sun gaji da gafara sa basuga ƙaho ba. In ba hakaba yarinyar nan zata ɓallo musu aiki.... ★★... TA-ƘURYA ★★... Tun zaman shari'ar nan ta kasa zaune ta kasa tsaye. Ta rasa makamar kamawa. A lissafi bayan boka Ruƙuƙi ta ziyarci manyan bokaye a ƙalla huɗu amma amsa guda suke bata bazasu iya mata aiki ba ta koma ga UWA. Tsabar takaici har kuka tayi, kuka irin wanda ake kira kuka data ɗauka tsahon shekarun da bazata iya tuna sanda tayi makamancin sa ba ma. Jin tsanar Iffah take fiye da komai yanzu a duniya. A kwanaki biyun nan da suka gabata bayan zaman shari'a ta yanke shawarar gwada kasheta amma duk hanyar da tabi sai ta sameta a toshe. Wannan ne ya sake ƙona mata rai da sake jin raɗaɗi mafi girma. (Ki ajiye komai ki sake komawa ga uwa, karki bari wahalarki ta wuce a banza) shawarar aminiyarta ta sake dawo mata a karo na babu adadi. Jagwab takai zaune, cikin don danne hawayen dake ƙoƙarin zubo mata tace, “Mike shirin faruwa da ni ne haka? Shirin dana ɗauka shekaru kusan arba'in inayi ne wata mitsitsiyar halitta zata zama sanadin rushemin, micece ita? Mi take takama da shi?” hawayen da take dannewar suka zubo saboda radaɗin da take ji. Bata da sauran zaɓi a yanzu face sake nemo UWA. Zumbur ta miƙe tamkar wadda aka tsikara. Ta lalubo kayan surkullen da take kiranyen uwa da su, da ƙyar ta gano robar da hayaƙi ke ciki ta bulbula a burner, take ɗakin ya harmutse har baka iya ganin komai, ita kanta numfashinta har wani fisgar yake tsabar ƙarfin hayaƙin. Idanunta ta rumtse tare da zubewa bisa gwiwunta ta fara hurwa na kiranye cikin yaren surkulle. Amma tsahon lokaci babu alamar uwa, har hayaƙin ya Kore, bata gajiya ba ta cigaba tana mai sake ninka rauninta (Wa'iyazubillah). Ta share tsahon awa guda tana abu ɗaya babu uwa babu alamar ta. Sai ranta ya ƙara sosuwa, ta dunƙule kanta waje ɗaya tana mai jin hawaye nason zubo mata. Amma ta hana hakan saboda taurin zuciya. Har karfe biyu na dare da masarautar ta nitsa bakajin motsin komai alamar anyi barci, in ma da wanda bai barcinba ya kasance a killace ƙarƙashin inuwar karamin motsi. Waya ta ɗauka tai danne-danne ta kai kunne, a bugu ɗaya aka amsa mata. Kafin ace komai da ga can cikin bada umarni ta furta, “Ki sashi ya jirani a garden”. Daga haka ta yanke kiran. A gurguje tai shiri cikin ɓadda kama ta fice, bazaka taɓa ɗauka mace bace, ta canja kammani cikin kayan jami'an dake aiki bada tsaro a masarautar. Dan haka babu wanda ya maida hankali kanta harta isa babban garden ɗin masarautar dake a ɓangaren kudanci. Wajen nada ƙarancin haske, sai kukan tsuntsaye da ake kiwo jefi-jefi. Da sauri ya fito da ga maboyarsa, ya zube a gabanta yana miƙa gaisuwa. Nuni tai masa ya miƙe batare da ta amsa masa ba. Mikewar yay, kansa a rissine, dan haramunne a garesa kallonta. Sai da ta gama ƙare masa kallo sama da ƙasa ta mika masa anvelope ɗin hannunta. “Daga daren yau zuwa safiyar gobe ina buƙatar jin kuka, ina buƙatar naji kukan mutuwar Zawjata-almilk. Idan aka samu kuskure kuwa kukan mutuwarka ahalinka zasuyi. A jefata a babban ruwan swimming pool na garden ɗin gabashi”. “Umarninki shine abin jirana da cikawa”. Ya faɗa da sauri cikin matuƙar girmamawa. Bata sake tankawa ba ta juya tabar wajen. Sai da ta ɓacema ganinsa ya iya ɗago kansa dake a risine yana sakin nannauyar ajiyar zuciya. Ba yau ya fara mata aiki ba, sai dai a shi kansa har yanzu bazai iya sanin ainahin wacece ba. Dan a koda yaushe cikin ɓadda kama take bashi umarni ko ta saka amintacciyar ta ta bashi, sai dai a duk lokacin da ita ta bashi da kanta ya san ba aiki bane ƙarami. Anvelope ɗin ya buɗe, ya wani zaro idanu da ganin makudan kuɗin da ke ciki miƙaƙƙu sababbi ƙal sai ƙamshin sabunta suke. Fuskarsa washe da murmushi ya sumbaci kuɗin, ransa fes da samunsu. Duk da dai yasan bazai cisu a banza ba, dan wannan aikin bazai taɓa zama mai sauƙi ba a garesa kasancewar matsanancin tsaron da kurkukun da Zawjata-almilk ke ciki, amma kodan waɗan nan taurarin dolene ya cika umarni....... ★★...... Ya kai mintuna goma yana kallon yanda masu tsaron kurkukun ke kaiwa da komowa, kowanne kuma da makami tare da shi. Ga haske ƙal tamkar rana dan ko allura ka yar ka duka ka ɗauka abinka batare da ka nema ba. Bugawar ƙaton agogon masarautar da ake iya gani tako wace kusurwar daular ta ruman ya sashi jan numfashi a sarƙe. Karfe uku dai-dai kenan, awa ɗaya garesa kacal na kammala wannan aikin. Dan huɗu nayi zaka fara jin motsin hadimai na tashi domin fara ayyukansu, musamman masu share-share da goge-goge. Zaman ɗammarar ƙugunsa ya gyara da ƙyau, hakama hular kansa kalar kayan jikinsa na ainahin amintattun jami'an dake cikin sashen Tajwar Eshaan. Ya ƙara saita kansa da ƙyau cikin dakewa ya tunkaresu hannunsa ɗauke da babbar jaka. Duk da sanin matsayin masu waɗan nan kayan a gidan gaba ɗaya sukai masa ca. Bai nuna razana ba duk da zuciyarsa na faman dukan dari-ɗari ne. Cikin sake matse kansa ya sara musu alamar girmamawa yana mai miƙa musu I'd card ɗinsa. “Umarnine da ga shugaba, zan sada kayan nan ga Zawjata-almilk domin sakasu a gobe idan zata fita, na kwashe na dattin dake tare da ita”. Kallonsa suke kawai suna sake kallon katin domin tantance shi ɗinne a hoton kokuwa. Sai dai hoton ya ɗanyi duhu, duk da kuma hasken wajen dai rana bazata taɓa zama ɗaya da hasken lantarki ba. A dake ya sake faɗin, “Ba tantancewar kaɗai ake buƙata ba. Ya kamata ku kira sashen shugaba domin tabbatarwa, wannan shine cikar aikin masu tsaro”. Kalamansa sun ɗanyi tasiri garesu, sai dai duk da haka wani ya tubure akan sai ya fara zuwa ya tabbatar bawai kiran waya ba. Dan ko ƙuda an tabbatar musu su kasance masu himma wajen hanashi gittawa zuwa inda Iffah take sai da ƙwaƙwƙwaran dalili. Tsabar ƙarfin hali na hadimin nan, babu ko nuna gezau ya bada goyon baya. Hakan ya ƙara saka sauran jin sun yarda da shi, sai dai wancan ɗin babu alamar hakan. Sai ma tabbatar musu da yay su cigaba da tsaresa zaije ya dawo”. Tsahon mintuna goma da tafiyarsa sai gashi ya dawo, batare da yace komai ba yay masa nuni da ya shiga. Wata irin wawuyar ajiyar zuciya ya saki da ɗan kashe ido wa jami'in da a yanzu yake ta faman sinne kai kamar wani munafuki. Sauran basu damuba dan su dama sun aminta tun dazun, dan haka ya wuce hankali kwance. Tana tsaka da ɓarawon barcin da ya sace ta bayan ta idar da sallar da take tsaiwar yi duk dare domin miƙa kukanta ga UBANGIJI taji kamar numfashinta na fita a fisge, firgigit ta farka da ƙoƙarin kai hannunta saman hancinta, sai dai aikin gama ya gama dan ya riga ya shaƙa mata abinda ke cikin handkherciff ɗin. Duk yanda taso sake yunƙurawa hakan ya gagara sai ma jikinta dake saki baki ɗaya. Daga haka bata sake sanin inda kanta yake ba. Jikinsa na ɗan ɓari ya sakata a babbar jakar hanun nasa tare da zuge zip ɗin. Bai tsaya ɓata lokaci ba ya saɓeta kasancewarsa ƙaƙƙarfan mutum babu alamar da zai tabbatar maka mutum ya ɗakko. Gashi dama Iffah ta rame sosai duk da dama ba wata mai jiki bace can. Sai dai kuma duk da hakan ƙarfin haline kawai irin na masu busashshiyar zuciya dan sumar da itan da yay jikinta duk ya saki ta sake nauyi. Sai da yay musu sallama da sanar da su ya kwaso kayan dattin wajenta ne bisa umarnin Tajwar Eshaan sannan ya wuce.........✍️ Hummm *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (16) ........Kamar yanda al'adar take duk wani hadimi da karfe huɗu tayi zai fara gudanar da aikinsa in har yana cikin hadimai masu kula da tsaftar masarautar. Musamman ma masu shara da tsaftace irinsu garden barga da sauransu. Yauma hakance ta kasance, hadiman duk sun tashi domin kama ayyukansu, kowa ƙoƙarinsa ya kammala kafin sallar asubahi. Swimming pool ɗin garden ɗin gabashi dake kamar ta bayan sashen Shahan-shan gab, babban swimming ne da masu aikin tsaftace ruwan cikinsa suka kasance har su huɗu, kowace kusurwa da mai gyarawa. Sukan saka raga domin tace duk wani datti daya shiga ciki, tare da sake ingantashi ya fita fes yana bada kalar blue mai ɗaukar ido ko daga nesa. Aikinsu suka fara a nutse, tare da yima juna magana jefi-jefi, can wanda ke a bangon yamma ya zabura tare da ƙwala ƙarar da tai amsa kuwwa zuwa kunnen duk hadiman dake aikinsu suma gab da wajen. A take ƴan uwansa sukayi kansa suna tambayar lafiya. Jikinsa na rawar karkarwa yay musu nuni da cikin swimming pool, kallonsu suka maida wajen zukatansu na dukan tara-tara, dan basu mance tsautsayin da ya taɓa faruwa ba da har yay sanadin rasa ran Miran Nayyar (ƙani ga Marigayi Tajwar Haysam). A tare suma suka zabura jikkunansu na sake shiga mazarin rawa. “Tabbas mutum ne mun shiga uku!!”. Wani ya faɗa a cikin sauran hadiman da ihun wancan ya jawo hankalinsu. Sake daburcewa duk sukayi, an rasa wanda zai yi hoɓɓosan kai agaji ko neman agajin, gashi motsin da suke gani anayi a cikin ruwan ya fara lafawa alamar wanda ke cikin yana sake ƙasa. Wani da yazo kusan a ƙarshe-ƙarshe ne ya zabura zai afka, da sauri wani ya rikoshi yana girgiza kansa. “Wannan bashine mafita ba, ayi azamar sanar da jami'ai gudun kar mu aikata kuskure tunda bamu san wanene ba. Duk wanda ya kai shekara arba'in da biyar baya anan yasan miya faru a dalilin irin wannan kuskuran”. Sun gamsu da jawabinsa, duk da wasu labari kawai sukaji dan sannan girmansu bai kai ba, wasu ma ba'a haifesu ba. Cikin ƙanƙanin lokaci jami'ai suka iso wajen, hakama mazan masarautar dake ƙoƙarin tafiya masallaci sallar asubahi. Rashin sanin wanene a ciki yasa shugaban jami'an ya hana a shiga kai tsaye, sai dai tuni an gama dasa na'urorin da zasu iya fiddo koma wanene. (Dan tun rasa Miran Nayyar da masarautar tayi Tajwar Abdul-majeed ya tanadar da na'urorin domin tsaro). Tayi ƙasa sosai ga swimming pool ɗin da girma sosai, cikinsa kuma anyi style kamar wani sashe-sashe da suffar ado. Hakan yasa akaja lokaci mai tsawo kafin a samu nasarar samota, zuwa lokacin har an idar da sallar asuba. Kasancewar tsirarun mutane da Tajwar Eshaan ne kawai suka sami damar yin sallar asubahin ya bada mamaki har Tajwar Eshaan ɗin yasa akai tambayar ko wani abu na faruwa ne haka?. Waɗanda suke a masallacin duk basu sani ba, dan haka suka tabbatar da babu komai, sai dai ko makarace ta kawo hakan. Baiji ya gamsu ba, amma sai bai musa ba ya miƙe ya fito Sayeed Fayzul-haq da ya zama kamar amintaccensa yanzu biye da shi. A falo Sayeed ya dakata, shi kuma ya nufi bedroom domin shiryawa ya shiga grm. Dai-dai nan kiran waya ya shigo ta landline. Tsayawa yay cak, dan duk kiran da zai iya shiga a wannan wayar direct dole mai muhimmanci ne da shi ya shafa, kuma kai tsaye ake bukatar magana da shi. Tana gab da tsinkewa ya juyo, idanunsa ya sauke akan sayeed, cike da ƙasaita yay masa nuni da wayar alamar ya ɗaga. Cikin bin umarni sayeed ya ɗaga wayar, shiru kusan na minti ɗaya ya janye a ɗan zabure yana kife wayar. “ALLAH ya ƙarama shugaban sarakuna da al'ummar ƙasar ruman baki ɗaya lafiya da tsohon rai mai albarka. Kirane da ga shugaban jami'an tsaro. An samu accident ne a cikin swimming pool ɗin babban garden, mace ce kuma, ana kyautata zaton bata cikin hadimai, gashi tana buƙatar taimakon gaggawa da basu da hurumin taɓata su”. Ƙirjinsa ne yay wata irin mummunar bugawa, mafarkinsa na gabanin asubahi da har yasa shi ƴar makara ya shiga maimaita kansa a kwanyarsa. Ƙoƙarin basarwa yay kamar yanda ya saba, sai dai zuciyarsa taƙi bashi goyon bayan bada umarnin waninsa yaje. Har ya daga ƙafarsa da niyyar cigaba da tafiya hakan ya gagara, idonsa ya rumtse da ɗan ƙarfi ya buɗe, batare da yace uffan ba ya nufi ɓoyayyar hanyar da zata sadashi da babban garden ɗin. Sosai mamaki ya kama Sayeed Fayzul-haq, sai dai bashi da hurumin tambaya dan haka ya take masa baya da sassarfa... ★Cikin rawar jiki hadiman wajen suka shiga zubewa bisa gwiwunsu ganin mai ruman ɗin ne fa da kansa. Yayinda jami'an suma duk suka risinar da kawuna. Taku yake a nutse cike da ƙasaitar da ke tabbatar da kasancewarsa bajimin namiji da ko a cikin jaruman gwarazo ne. A ƙirjinsa bugu yake kamar zai hantsilo waje, a zahirinsa kuwa babu mai iya fahimtar komai koda daga fuskarsa ne. A hankali matan da ke zagaye da ita suka dare, dan sune suka sanar cewar Zawjata-almilk ce, shugaban jami'ai ya faɗa a rufe ne saboda shakkar isar da saƙon kai tsaye ga Shahan-shan ɗin. Suma kawunansu duk a rissine suke, cikin rawar murya ɗaya daga cikin matan data kasance amintacciyar hadima mai ƴanci dake da alhakin kaiwa da komowar duk wani abinda ya shafi Shahan-shan da matansa ko makusancinsa (kamar jakadiya a ƙasar hausa) ta ƙarasa zubewa cikin gurfana, “ALLAH ya huci zuciyar shugaban sarakunan ƙasar ruman da al'ummar cikinta. Umarninka muke jira domin taɓa Zawjata-almilk, dan rayuwarta zata iya salwanta.....” Idanunsa da ke ma Iffah kallon ƙasa-ƙasa ya ɗan lumshe, cikin jarumtar son danne zillon da zuciyar ke masa ya ɗaga ƙafarsa da ƙyar yay taku ɗaya biyu da ya sake saka matan darewa cikin rawar jiki mamaki na neman halakasu ganin gadan-gadan Iffah ya nufa. Dai-dai yana ƙarasawa ɗaya da ga cikin jami'an wajen da yay wata irin zabura ya sunkuto ɗaya daga kujerun dake a wajen ya dire masa, da sauri aka ɗaura hiramin sayeed Fayzul-haq daya fincike a kansa. A hankali ya kai zaune shanyayyun idanunsa na sake tar-tar a kanta cikin ɗan hasken da garin ya fara. An lulluɓe jikinta da mayafi kasanwar kayanta dake jiƙe zai iya bayyana ainahinta, kallon kusan sakanni biyar yaja numfashi ya fesar yana mai kai yatsunsa biyu saman hancinta, babu alamar numfashi, ɗaukewa yay ya maida a jijiyar wuyanta, nan ma bata harbawa, cikin jarumta da zaburo da sanyin da ke sauka a jijiyoyin jikinsa ya ɗan ɗaga mayafin ya ciro hanunta. A kan tattausan nasa ya ɗaura yana mai ɗaura yatsansa akan jijiyar tsintsiyar hannun ya lumshe ido. Da sauri ya buɗe sai dai ga mai kallo bazai taɓa fahimta ba. Dan a nitse yake sarrafa hannunsa dake motsi kawai a jikin nasa. Shugaban jami'ai da Sayeed Fayzul-haq dake ɗan satar kallonsa kasancewar duk wani hadimi da sauran jami'an tun zamansa a kujerar duk sun juya bayansu suka ɗan waro ido ganin ya kusanta ƙyaƙyƙyawar fuskarsa da ta Iffah har hancinansu na gogar juna. Ya lumshe idanu tare da sauke tausasan lips ɗinsa kan nata, ai dole suma suka sake rissinar da kawunansu duk da sun san bawani abu zai yi ba illa bata taimakon gaggawa. Shiko da bai ma san sunayi ba da harshensa yay nasarar raba lips ɗinta da haƙoranta dage datse cikin na juna ya turashi cikin bakin nata, sai kuma ya kai yatsunsa biyu kan hancinta ya matse. Iskar bakinsa mai ƙarfi ya hura mata cike da salon ƙwarewarsa akan iya ruwa da ceton duk wanda ya samu accident a dalilinsa. Da wani irin ƙarfi ta zaburo ƙirjinta na ballaƙowa sai ruwan bakinta bulla a kan fuskarsa. Idanu ya lumshe a hankali yana mai sauke wata irin nannauyar ajiyar zuciya daga cikin maƙoshinsa da ɗan jan fuskarsa data wanke da ruwan bakinta. Cikin sauri Ama. Ta miƙama Sayeed ƙaramin towel cikin wanda ke hanunta, amsa yay ya matsa kusa da Tajwar Eshaan kansa a rissine ya miƙa masa. Bai motsa ba idonsa a kanta tana cigaba da amayo ruwan saboda ɗan danna ƙirjinta da ya cigaba dayi har tsawon kusan mintuna biyu, kafin ya miƙama sayeed hannu batare da ya juyi ba ya amsa. Kan fuskarsa ya kai ya tsane ruwan da tuni yama gangagare har wuyansa har ya ɗan jiƙa jallabiyar jikinsa mai tsananin ƙyau da ɗaukar idanun kai kallo. “Duvet”. Ya faɗa a hankali ganin jikinta ya fara karkarwa har ɗan gadon agajin gaggawar da aka daurata na ɗan jijigawa. A cikin ƙanƙanin lokaci aka kawo, yanzu ma da kansa ya rufa mata. Sannan ya miƙe gaba ɗayansa yana ɗan duban Sayeed. “A maidata gareni”. Ya faɗa can ƙasan maƙoshi tamkar bashine yay maganar ba yana ƙoƙarin barin wajen. Sai yanzu ya lura da cikar garden ɗin da duk masu faɗa ajin masarautar a wajen. Idonsa ne ya sauka kan Malikat Bushirat da Malikat Haseenat da ke kusan tare da juna. Dan Daneen Ammarah da Malikat Ashwaq ne suka ɗan shiga tsakaninsu. Ɗauke idanun nasa yay ya cigaba da takunsa na bajimta. Dan kowa a wajen kansa a rissine yake har su Malikat Bushirat ɗin kansu domin tabbatar da girman da ALLAH ya bashi na shugabanci.... A gaban idon kowa aka wuce da Iffah sashen Tajwar Eshaan ɗin tare da Doctor da zata sake bata taimakon gaggawa, a hankali ƙus-ƙus ya fara tashi a wajen kowa na jimanta al'amarin da jinjina faruwarsa kasancewar duk wanda ya kwana ya tashi a gidan yasan Iffah na kurkuku ne, kuma a yau za'ai zaman shari'a ta biyu, hakama abinda ta faɗa a zaman waccan shari'ar kowa ya jisa. Sai dalilin faruwar al'amarin yau ya saka zukata fara rarrabuwa a kan al'amarin ta, masu ganin a wancan zaman shari'ar ta faɗi waɗan can kalamanne danta kuɓutar da kanta ko sharri, sai a yanzu suke ganinfa akwai ƙamshin gaskiya tunda a karo na biyu kenan ana yunƙurin kasheta. Idan babu rami to miya kawo rami? Wannan shine tambayarsu...........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (17) ........Samun gawar ɗaya daga cikin jami'an dake tsare da Iffah, da ɗaya daga cikin na sashen Tajwar Eshaan ya sake tabbatar da akwai ƙullalliya. Dan alamomi na bayyane sun nuna an fara kashe jam'in sashen Tajwar Eshaan ɗin ne akai amfani da kayansa zuwa kurkuku, sai kuma gawar jami'in dake cikin masu tsaron Iffah da bayanin sauran jami'an ya tabbatar da koma miye a lokacin da yace zaije ya binciko gaskiyar zuwan jami'in da yace yazo kawoma Zawjata-almilk kaya ne. Sarƙa-sarƙar ta ɗaure kan mutane matuƙa da yanda tama faru, sai dai jami'an sun tabbatar da sai sun gano koma wanene anan kusa cike kuma da alwashi..... ★★.... ★.... Tunda akace ta farfaɗo hankalin duk masu hannu akan al'amarin ke'a tashe musamman ta-ƙurya da hadimin da yay aikin. Tashin hankalin ta-ƙurya rashin mutuwar Iffah ne, dan tanada hanyoyin da zatabi na ɓatar da hadimin cikin sauƙi, kai koda ta barsa da rayuwarsa ma bai san ita wacece ba. Amma kasancewar cigaba da rayuwar Iffah na nufin MATSALARTA na nan har yau da gobe dama ranar da bata san iyaka ba. Idan har tace kuma zata sake wani yinƙuri a yanzu akwai matsala, mafitarta ɗaya ce sake komawa ga UWA ɗin da take hangen ta gaza a baya. Wasu irin zafafan hawaye ne masu raɗaɗi suka shiga bin kumatunta, ɗuminsu kawai taji batare da tasan ta farasu ba. Hakan ya ƙara ƙona ranta dan akan ƴar yarinyar data raina hawayenta na zuba a karo na babu adadi, abinda bai taɓa faruwa da ita ba kasancewarta mai nasara ga duk abinda ta sanya gaba. Shawarar da zuciyarta ta bata akan sake kiranyen uwa ya sata miƙewa. Surkullen jiya ta shiga fara maimaitawa. Tsahon lokaci har ta fidda rai a yanzu ma sautin mummunar dariyar uwa ta fara karaɗe ɗakin. Dariya ta tsaho lokaci babu alamar za'a daina kafin uwa ta bayyana a gabanta. “Ashe k! ƙaramar mara kunyace ta-ƙurya. Ashe baki shirya yaƙin ba kika yanki filin yinsa ba! Ashe b......” “Tuba nake Uwa mai share kukan masu kuka. Nayi kuskure a gafarceni bazan sake ba. Ni mai biyayyace ga umarninki a koda yaushe. Wannan ma saɓanin fahimta aka samu”. Shiru kamar uwa bazata tanka ba, sai kuma ta hura mummunan hancinta dayin ƙwafa. “Dalilai biyu zasu sa na miki afuwa ta-ƙurya. Baki taɓa saɓama umarninmu ba sai a wannan karon. Na biyu darajar wannan masarautar da kike ci. Kije ki kalmashe bakin zaren aikinmu na ƙarshe, dan aikinki na gab da buɗewa. Ki kuma kiyayi kaima yarinyar nan hari kai tsaye, dan duk yanda kike tunanin zaki iya a kanta ta waɗan nan hanyoyin al'amarinta ya fi ƙarfin nan. A yanzu haka Ajlaan ya fara shinshinar ta. Kuma komai zai iya faruwa, dan muna a gaɓar da zai iya kashe ƙishinsa kanta a yanzun, babu makawa magajin kujerar daular ruman na kusanto duniya kenan.....” Zabura ta-ƙurya tai jikinta na matuƙar rawa, sai wani irin rawa da lips ɗin ta keyi suma tama gagara furta abinda ke bakinta tsabar shiga tashin hankali. Uwa ta miƙa mata hoto cikin bada umarni. “Itace muke buƙata ta zama uwar Miran mai jiran gado, ki gaggauta, ki gaggauta tabbatar da ita cikin masarautar nan matsayin Zawjata-almilk daga nan zuwa ƙanƙanin lokaci. Inba haka ba kiyi kuka da kanki ta-ƙurya! Kuyi kuka da kanki!! hahaha!! hahahah!! hhhhhh!!!!!”. Ta ɓace ɓat sautin mummunar dariyarta na amsa kuwwa cikin ɗakin kai kace duk masarautar za'a iya jinta... ★★.... “Wannan na sake tabbatar mana da ƙamshin gaskiya akan yarinyar nan Mammah”. Daneen Ammarah ta faɗa cikin sanyin murya da jimamin abinda ya faru ya haddasa mata. Numfashi mai nauyi Malikat Haseenat ta sauke, kamar bazatace komai ba sai kuma ta dubi ɗiyar tata. “Akwai al'amarin dake tare da yarinyar mai girma da ko iyayenta bana jin sun san da shi tattare da ita ba. Inaji a jikina a dalilinta komai na gab da buɗewa a wannan masarautar”. Cikin nuna mamaki Daneen Ammarah ta ce, “Babban al'amari kuma Mammah? Kamar wane iri kenan?”. A karo na farko Malikat Haseenat ta saki murmushi mai ƙayatarwa, batare da tace komai ba ta danna kekenta yay gaba. Da kallo Daneen Ammarah ta bita baki sake, ita kam wani lokacin Mammah na hargitsa mata tunani da sakata a wasiwasi gaskiya..... ★★.... “Idan har ya kasance bakai bane kamar yanda ka faɗa to wanene kenan? Dama da gaske kamar yanda muke zargi bayan mu akwai masu harar rayuwar yarinyar nan kenan akwai ɗin?”. “Ga alamun hakan ka gani. Sai ma nakega su ɗin sun fimu shiri. Sai dai abinda ke ɗauren kai su kuma miye nasu dalilin? Dan na hanga na hango a duk cikin wanda zasu iya aikata hakan burinsu zai kasance irin namu ne amma basu da hujjar yin hakan. Idan a matan mahaifinsa ne miye ribarsu tunda ba wasu ƴaƴane da su ba balle ace suna yaƙi irin namu ne? Anya kuwa ba iyalan Sayeed Khairul-Bashar bane ke son ɗaukar fansa?”. “Idan kuma zasu ɗauki fansa sai su ɗauka akan wadda ba'ita ta musu laifin ba?. Idan har sune rayuwarsa zasu hara bata matarsa ba. Kuma ai tun farkon shigowarta masarautar nan aka fara wannan wasan. Akwai dai wata a ƙasa daya kama mu sani mu kuma san mai wannan shirin dan dalilinsa mai ƙarfi ne.” Cikin gamsuwa Miran Jasim ke gyaɗama Miran Arshaan kai fuskarsa ɗauke da murmushi, dan koda basu suka aikata ba abinda ya farun ya musu daɗi har cikin rai yake jin farin ciki da nishaɗi.. ★..... Tunda Doctor ta gama dubata ta fice ya cigaba da tsaiwa akan ƙafafunsa lumsassun idanunsa da suka canja kala kaɗan na ɓacin rai ƙyam a kanta. Kallonta yake tamkar wata sabuwar halitta a rayuwarsa. Kallonta yake zuciyarsa na harbawa da sauri-sauri. Kallo yake mata irin na miyasa kika zaɓi shigowa rayuwata a haka?, bayan ba haka na so ki kasance ba. Ƙanƙance idanun ya sakeyi a kanta yana mai datse lips ɗinsa da haƙori har yanajin raɗaɗin hakan a karan kansa. Sannu a hankali ya fara kai kawo a ɗakin hannayensa duk biyu goye da bayansa. Sosai a wannan gaɓar fuskarsa ta nuna matsanancin fushi. Zuciyarsa ta fara kaiwa maƙura akan abubuwan dake faruwa a masarautar, ya fara jin bazai iya cigaba da jurewa akai gaɓar da yake buƙata ba tun farko. Kalaman wasiyyar mahaifinsa ne suka shiga dawo masa ɗaya bayan ɗaya. A yanzu kam idanun ya rumtse tare da kaiwa zaune cikin kujera. Zuciyarsa na gudu da sauri-sauri. Sosai yake jin ɗaci mai sosa zuciya. Hawayene suka cika masa ido domin shima mutum ne kamar kowa, zuciyarsa irin ta kowa ce, yanajin zafi, yanajin farin ciki. Sosai yake buƙatar son jinsa a jikin wani. Mahaifiya ko mata. Sai dai yasan hakan shine abu mafi wahala a gareshi bayan abubuwa masu yawa da ALLAH ya azurtashi da su. Yanada tarin dukiya daya nema da guminsa, mahaifinsa ya bar masa tarin dukiya da shi kansa bai san iyakarta ba. ALLAH ya bashi mulki, mulki mafi daraja sama da kowane shugaba da ke a ƙasar ruman. Ya azurtashi da ƙyawu irin wanda ko'a cikin ƙyawawa yasan zai zama abin kallo. Ya azurtashi da ilimi na boko dana addini da babu abinda zaice sai Alhamdullah. Sai dai ya tawaya ta ɓangaren mace, shi mutum ne mabuƙaci, ya daɗe da fahimtar hakan, amma ƙaddarorimsa sun nisanta shi da samun cikamakin waɗan nan ni'imomin da UBANGIJI ya mallaka masa. A hankali ya sauke lumsassun idanunsa kan Iffah zuciyarsa na kaikawo. (Abbie miyasa kace na kasance haka?) Ya ambata a zuciya cike da ƙunar da take masa mai raɗaɗi.. ★★...... Jigum-jigum aka yini a masarautar cike da jimamin abinda ya faru. Al'amarin ya fara ɗaure zuciyar kowa a yanayin da yake da wahalar fassara. Sai dai a zahiri babu mai iya cewa komai sai ƴar ƙus-ƙus kai da abokin maganarka. Har yamma Tajwar Eshaan na tare da Iffah, duk da damunsa da na'urar ɗumama ɗakin da aka kunna saboda ita keyi haka ya cigaba da zama a ɗakin. Hatta da fada da akai zaman fadanci da tunanin zai fito yace wani abu akan abinda ya faru bai fitan ba. Sallama a ɗakin yayi ta yau. Hakan ya fara ankarar da mutanen masarautar kenan duk lokacin daya killace kansa yaƙi fita yana fushi ne ko cikin damuwa. Dan yau dai kusan kowa a haka ya fassara rashin fitowar tasa. Su dai ke kiɗansu suna rawarsu, dan shi dai bai ce ba babu kuma alamar zai ce ɗin har yammaci. A hankali ta fara motsi dai-dai lokacin da yake zaune yana raira karatun Alkur'ani mai girma da wata irin sassanyar murya mai tsaushi da ratsa zuciyar mai saurare. A duk lokacin da ya samu kansa a irin wannan yanayi na damuwa mai ƙuna yafi buƙatar zama yayta karatun Alkur'ani sai ya samu nutsuwa. Da atshawa ta fara a jere har guda huɗu, hakan ya ankarar da shi farkawar tata. Amma tsabar ƙasaita da miskilanci baiko motsa ba ya cigaba da karatunsa har inda yaji zai tsaya dan kansa. Koda ya ajiye Alkur'anin ma bai juyo ɗin ba kai tsaye duk da atishawar da ta cigaba da jerawa a wahalce kuma a jajjere. A nutse ya miƙe babu alamar gaggawa ko garaje tattare da shi, sannu-sannu ya sauke manyan ƙyawawan fararen idanunsa kanta dai-dai ta sake yago tissue dake gefenta a bed side drawer ta toshe bakinta domin tare atshawan da ya sake taho mata. Kusan uku ta sake jerawa kafin ta ajiye tissue ɗin inda ta tara sauran cikin ƙanƙanin lokaci. Numfashi take saukewa a ɗan wahale kumburarrun idanunta na lumshewa da buɗewa.........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (18) .........A haka idanun nata suka kai garesa, zuba masa su tai a yanayin kallo na ƙasan ido, har ranta take jin bugun zuciyarta na harbawa da sauri-sauri. Ba yau ta fara ganinsa cikin ƙananan kaya ba idan yana sashensa a keɓe, amma sai taga yau ɗin kamar special ne. Baƙaƙen kayan sun masa ƙyau matuƙa da sake bayyana haskensa da ƙuruciyarsa kamar wani matashin saurayin da bai taɓa mallakar ko budurwa ba. Tsantsar ƙasaita da izzar mulki dake yawo a jininsa na ƙara masa wani irin kwarjini mai cika ido da barazana. A hankali ta ƙara ƙasa da kanta jin kamar yana nufota. Gareta ɗin ko ya iso fuskar nan ɗam-ɗam babu alamar yasan minene murmushi ma balle a kai ga dariya. Mug ɗin hanunsa da keta faman tururi da tashin ƙamshin haɗaɗɗen shayi na musamman ya ajiye a side drawer ɗin batare da yayi magana ba. Shayin ta ɗan kalla da sake maida kallonta gareshi cike da mamaki, dan ya ajiye baice komai ba ya bar wajen, bathroom ya shige, ta ɗan lumshe idanu batare data iya cewa komai ba. Babu abinda take buƙata sama da shayin a yanzu, dan haka ta ɗauka ta fara sha lokaci-lokaci tana atshawa ɗin a wahalce da duban hanyar bathroom ɗin. Tsahon mintuna biyar sai gashi ya fito yana faman sake tsuke face. Da sauri ta ɗauke idonta kamar bata gansaba itama, ta ajiye mug ɗin hanunta data kammala shanye shayin da ya zuba matan tana yaye duvet ɗin da take a ciki jin zufa na karyo mata tako ina a jikinta. Yunkurin sakkowa take a gadon dai-dai yana isowa gab da ita, hakan yasa ta dakata da miƙewar ta ɗan dubesa ta kauda kai. Idanu ya tsura mata kamar mai tunanin ta yanda zaice wani abu, kusan minti ɗaya ya ɗan yamutsa fuska cikin motsa lips da ƙyar yace, “ki shiga ruwa a bath....” ya haɗiye sauran a maƙoshi batare da ya ƙarasa ba. Sake ɗago ido tai ta kallesa, ganin nasa idanun a kanta sai ta tura baki kawai ta kauda fuska gefe sai kace wata ƴar yarinya. (Taɓara) ya ayyana a zuciyarsa shima yana ɓata fuskar. Ƴan jin kanne yau a kusa, wanda dama ita su ta sani a zahiri. Bama ta taɓa kallonsa a jerin mutane masu sauƙi ba. Batare da sake cewa uffan ba kawai taji ya ɗan duƙo kanta, zabura tai baya, sai dai kafin tai wani yunƙuri ya ɗagata cak kamar wata ƴar baby. Yo akansa micece wata Iffah. Tsayayyen namiji ne fa ingarma da duban damtsen hannunsa kawai ya iya saka mai tsoro zawayi a wando. Baka gane hakan sai yana sanye da ƙananun kaya. Gaba ɗaya ta waro idanunta sai cikin nasa, da sauri taso kauda natan ya hana hakan ta hanyar sarƙesu. Sai kawai taji zafin zazzaɓinta na ƙaruwa ma... “Ni dai ka daina kallona”. Furucin ya fito cikin suɓutar baki tana laɓe fuska kamar zatai kuka, dan da gaske idanun nan nasa tsoro suke bata. Ta ɗan so bashi dariya, sai dai a zahirinsa babu ko alamar hakan sai ma sake tsuke face ɗin da yay bai kuma janye idanun nasa ba. Sai ma tafiya da ya farayi da ita a hankali. Rumtse nata ta samu nasarar yi da ƙarfi dan gaba ɗaya jikinta yamutsawa yake har zuciyarta na zallo a cikin ƙirji. Zabura tai da buɗe idanun nata a lokaci guda jinta cikin ruwa mai ɗumi sosai. Taja ajiyar zuciya da faɗin, “Wayyo Ummuna”. Bai kulata ba ya ida ajiyeta a ruwan dake ta faman tashin ƙamshi na masifa, ga wani ɗumi mai ratsa ƙashi da ɓargo. Fuska a ƙwaɓe take duban kanta da yanda ya sakata ita da kayan gaba ɗaya cikin ruwan. Sai taji kamarma ta saki kuka kawai ta huta. Wannan wane irin kalar walaƙanci ne. Idan yace mata taje tai wanka kawai ai ya wadatar, amma yanzu gashi ya jiƙa mata kaya duka al'halin bata da yaƙinin wasu dan ta fahimci a sashensa take. Bai dai san tanai ba, dan tuni ma shi ya fice abinsa. Haka ta cire kayan a jiƙe ta ajiye a gefe, nutsa kanta ta sakeyi a ruwan tana mai lushe idanu kamshin ruwan da ɗuminsa na ratsata, ga yanda kumfar tai a sama ful-ful na wani irin ƙayatar da ita..... ★Ta jima a bayin kafin ta fito, sam batai tunanin samunsa a ɗakin ba. Dan haka ta fito kanta tsaye a zatonta ai zai fita ya bata waje tunda ya san wanka ta shiga. Sai da tazo tsakkiyar ɗakin tana ƙoƙarin sharce ruwan dake sakkowa daga jiƙaƙƙen kanta data wanke zuwa kan fuska ta tsaya turus. Da sauri ta juya bayanta kamar zata fasa ihu. ALLAH ma ya sota bathrobe ta sanyo ba towel ba. Ai da yau taji ƙarshen kunya a duniya. Babu alamar zai motsa a zaman ƙasaitar da yay cikin haɗaɗɗiyar kujerar da yake duk da yaji fitowar tata. Sai da ya mula dan kansa ya ɗan ɗago idanunsa ya dubeta kaɗan ya kauda kai. (Bata tausayama kamata) ya ayyana a zuciyarsa yana jan sirrin tsaki a can ƙasan maƙoshi. System ɗin dake a cinyarsa ya ajiye saman ɗan coffee table ɗin gabansa ya miƙe fuska a daƙile, ta gabanta ya raɓa ya wuce kamar bai ganta ba. Jitai kamar tasa ihu dan takaicinsa, sai dai kuma ta kasa motsawa da ga tsaiwar har ya sake dawowa. A bazata yanzun ma taji tattausan hanunsa kan dogon gashinta data naɗe dan ya tsane da wuri kasancewar ta jiƙesa lungu da saƙo dan wanki ta masa mai ƙyau. Warwaresa yay sannan ya ɗaura karamin towel ɗin hanunsa baby pink a kanta ya fara tsane mata ruwan. A yanzu kam ba mamaki ne ya kashe Iffah kawai ba har da suman wucin gadi tai na ɗunbin mamakinsa. Ita Iffah, ɗiyar Babiy da Ummu ne tsaye Shahan-shan ke mata hidima, Shahan-shan fa ba wai hadimin daular ruman ba. Shahan-shan gaba ɗaya, wanda ke amsa shugaban na ƙasarta baki ɗaya, shugaban kuma al'ummar ƙasar ruman baki ɗaya. Sarkin da duniya ke shakka da tsoron nunama koda ƙasarsa yatsa. Ɗan gata da iyayensa suka haifa shi ɗaya ƙwallin ƙwal a duniya. Shi ɗin nan dai da duniya ke kallo matsayin wani babban tauraro mai girman gaske. “Kai ya ALLAH anya ba mafarki nake ba?” (Idonki biyu) zuciyarta ta bata amsa da tabbatar da abinda takewa kokwanto. Ai kanta bai nema kwancewa ba sai da ya kama igiyar bathrobe ɗin jikinta ya kwance. A ɗan zabure ta riƙe hannunsa caraf cikin nata tana waro idanu. “Mi zakayi...?” kalmar ta fito a suɓuce daga bakinta. Wata irin dariya ce ta nema kufce masa ya danneta da ƙyar. Cikin ƙara kame fuska ya tsareta da idanun nan nasa masu kaifin tsiya, hanun nata ya ture zai ƙarasa kwancewa abinsa. Sai kawai ta daka uban tsalle ta faɗa masa a jiki “Ni wlhy ba ƴar iska bace, babu fa komai a c....” ta kasa ƙarasawa tana ƙara cikuykuyesa da ƙyau. Jikinsa rawa ya neman farayi saboda yanda ta ƙanƙamesa, tunda yake a rayuwarsa bayajin ya taɓa rungumar mace kamar haka. Gaba ɗaya abinda ya ɗauka tsahon shekaru yana dakon dannewa ya nema yunƙurowa. Ƙoƙarin janyeta yake tana sake ƙadandanesa a tunaninta so yake ya cire matan koda tsiya. (Ya arrahaman zata halakani) ya faɗa a zuciya yana mai rumtse idanunsa da masifar ƙarfi a zahiri. Cikin zafin nama ya finciketa da sauri yana ƙoƙarin riƙe rawar da jikin nasa ya fara. Cikin wata ƴar sassarfar da bata hana takunsa na ƙasaita fita a yanda yake ba ya bar wajen, a kujerar da ya tashi ya koma ya zube. Faɗi yake (shike nan ta buɗe aiki, Fitinanniyar yarinya zata halakani). Oho Fareedatu batama san yanai ba, dan tana samu ya jayetan daga jikinsa ta kwasa da gudu sai saman katafaren gadon da aka gyara tsaf kamar ba yanzu ta sauka akansa ba. Bata da nutsuwar tunanin yanda akai aka gyara ɗin ko wanda ya gyara taja lafiyayyen duvet ɗin ta naɗe jikinta dake faman kakkarwa. Dan jinta take kamar wadda ta jonu da lantarki. Shiru ɗakin kowa yay ɗif a cikinsu. Babu ko motsin ac dan bai kunna ba saboda ita, duk da yana buƙatarsa, sai dai ya kashe na'urar ɗúmama ɗakin dake aiki tun ɗazun saboda itan. Sai da ya ɗan saita kansa kaɗan kafin ya miƙe, batare da ya dubeta ba ya nufi hanyar fita. Ƙasa-ƙasa ta bishi da kallo, ganin ya tsaya tai saurin kauda kanta. Bai juyo ba sai dai yaji a jikinsa ana kallonsa, murya a shaƙe can ƙasan maƙoshi ya motsa lips ɗinsa kaɗan. “Ki canja wannan rigan”. Jitai kamar ana narkama jikinta ƙanƙara, ta wani lumshe idanunta dake faman yin mar-mar, sai kuma ta sauke ƙaƙƙarfar ajiyar zuciya dai-dai da rufe ƙofar da yay bayan ya fice. Jitai gaba ɗaya kanta yama tushe, ta gagara tunanin komai kamar yanda take buƙata, kamar wadda aka zabura ta miƙe, idanunta ne suka sauka kan wata ƙyaƙyƙyawar abaya mai ɗaukar idanu. Karasawa tai ta daga rigar, sai kuma ta ɗan waro idanu ganin b&p a ƙasa, “Kam babbar buta, duk shi ya ajiye wannan ma? OMG! Wannan Shahan-shan ɗin daular ruman ɗin ko”. Ta ƙare faɗa kamar zata fashe da kuka. Dan ji take duk ta daburce tsabar wata kunya da take ji na ratsata tamkar tana a gabansa.........✍️ _🥱🏇🏇🏇🏇Babu abun faɗa yau kam, nayi nan kar ace kuma..... To bara dai nai shiru kawai._ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (19) .......<<★★ TA-ƘURYA ★★>> _(Itace muke buƙata ta zama uwar Miran mai jiran gado, ki gaggauta, ki gaggauta tabbatar da ita cikin masarautar nan matsayin Zawjata-almilk daga nan zuwa mako huɗu. Inba haka ba kiyi kuka da kanki ta-ƙurya hahaha!!! hahaha! hhhhh!!!!)_ Zumbur ta miƙe daga ɗan barcin daya figeta, firgitattun kalaman uwa da tayi mata su a zahiri ne waccan ranar ke maimaita kansu yanzu a barcinta matsayin mafarki. Hannu takai ta yarce uban gumin da ya jiƙe mata goshi har yana zirarowa akan fuskarta. Tana a tsaka mai wuya, irin tsakan da bata taɓa shigaba a duk umarnin da uwa ta bata a baya. Maganar ƙulla auren nan bazai kasance ƙarami ba gareta a wannan karon, sakamakon zaman babu wanda ya yarda da ɗan uwansa da akeyi yanzu a masarautar ta ruman. Gaba ɗaya ta rasa ta inda zata ɓullowa al'amarin nan. Ji take komai ya sukurkurce mata, sai dai kuma bazata iya yarda da barin cikar burinta ba na tsawon shekaru da take ganin tazo gab da cimmawa. Dolene ma tai wani abu, sai dai salon zai banbanta dana baya koda kaɗanne, zatai irin ɓadda kamar data saba wajen ganin wannan auren ya ɗauru, dan ko zatai yawo tsirara bazata taɓa yarda Iffah ta zama Malikat ba, mai haihuwar magajin Shahan-shan never for ever hakan ta faru tana numfashi a doron duniya.... 🥱To ta-ƙurya bara mu gani ko zaki iya, mudai ƴan kallo ne😉. ★★... ★..... A hankali ta matse fuska sai kuma takai hannu kan shafaffen cikinta dake mata zafin yunwa. Rabonta da abinci tun yammacin jiya, dan ƙin cin abincin da aka kai mata da dare tai a kurkuku. Zamewa tai a hankali ta kwanta a gadon tana cigaba da matse fuska. Dubanta ta kai a karo na biyu kan kofin shayin da ya bata ta ɓalla masa harara kamar shi ya hanata abincin, sai kuma tai juyi ta maida fuskarta ɗayan side ɗin tana ƙara cure jikinta waje guda hanunnta na kan cikinta.. A hankali ya tura ƙofar ya shiga idanunsa da hankalinsa gaba ɗaya na kan wayar hanunsa mai shegen ƙyau da ɗaukar ido kamar wani glass. Ciki-ciki yay sallama a ƙasan maƙoshi, batare da nuna alamar tuna yabar wani a ɗakin ba ya nufi ƙyaƙyƙywar kujerar zamansa ta musamman ya kai zaune a ƙasaitance. Wani kalan zaman isa da izzar mulki yay har lokacin idonsa akan wayar da alamar serious abu yake yi. Sassanyan ƙamshin turarensa dake ratsa mata ƙofifin hanci ya sata buɗe idanunta sannu a hankali. Har sun canja kala alamar barci ya fara ɗaukarta. Juyowa tai sannu a hankali batare da tunanin shi ɗin bane da gaske, dan indai ƙamshin sa ne ya riga ya gama kama duk bedrooms ɗin da yake amfani da su tsabar yanda yake wanka da turare kamar ruwa. Akan ƙyaƙyƙyawar farar fuskarsa da hasken wayan ya ɗan haska baƙin sajen siɗik ɗin gashinsa na ƙyalli ta sauke, yanda akai masa gyaran fuskar da wani irin haɗaɗɗen style yay matuƙar ƙara masa ƙyau. Sai taji tana buƙatar cigaba da kallonsa kawai, wani abu data kasa banbancewa na tsikarar ƙasan zuciyarta. A jikinsa yaji ana kallonsa, dan haka ya tsaya cak da ga sarrafa wayar da yake faman yi cike da ƙwarewa. Sai dai bai ɗago ba har tsawon kusan minti ɗaya. Sai da yay bala'in shammatarta a bazata ya ɗago nasa kaifafan idanun sai cikin nata dake tsaye ƙyam a kansa. Da wani irin sauri ta fisge kanta gefe cike da pretending ta riƙe ciki tana murƙususu ita a dole bata da lafiya ma. Idanun nasa ya kaɗa kamar wani mai zuƙota ta cikinsu, sai kuma ya yamutse fuska da sake tsuketa ya ɗauke kansa shima. Ci gaba yay da sarrafa wayarsa batare da ya sake kallonta ba, hakan ya bata damar sake satan kallonsa ta ƙasan ido tana sake ƙaƙaro kukan ƙaryanta. lips ɗinsa ya ɗan ciza kaɗan batare da ya bar abinda yake ba a hankali can ƙasan maƙoshi ya furta, “What happend?”. Baki ta tura gaba kamar bazatace komai ba. Sai kuma cikin kuka-kuka da kai tsaye za'a kirashi na shagwaɓa tace, “Ni dai kayan cikina zasu naɗe, yunwa nakeji ga headache, ga ciwo jikina namun ko'ina da ina”. Ta ƙare maganar tana ƙara tura baki. (Yarinyar nan ko...) Ya faɗa a cikin ransa idanunsa na wani binta da kallon slowly kamar mai zooming ɗin ta a cikinsu. Dan can ƙasa-ƙasa yake mata kallon da ita sam ta ɗauka hankalinsa na kan wayar ne baya ganinta saboda ganin yanda yake cigaba da sarrafa wayarsa bai dakata ba. Babu alamar zai sake tanka mata har tsawon kusan mintuna huɗu data cika tai fam da haushinsa. Tsabar son ƙular da shi sai ta fashe da sabon kuka ta shiga wani murƙususun tana kiran “Wayyo cikina Ummu yunwa zata halaka miki ni, nima kasheni zaiyi kamar yanda ya kashe ku. Abbiy ka shirya tarbana gani nan a hanya inda kuke. Ni wlhy garama a kasheni da wannan azaba da akemun, wayyo wo wo wo!!”. Tamkar wani gunki haka ya cigaba da zuba mata ido yana kallon ikon God, shi kam bai taɓa ganin Fitinanniyar yarinya irin yarinyar nan ba a rayuwanshi. Sam batajin magana, ga shegen tsiwa kamar wata babyn roba mai battery. Da ƙyar ya iya ɗaga ƙafa inda take ganin bata da alamar barin kunensa ya huta, yay tsaye a kanta kamar wanda aka dasa, sai wani binta yake da kallon ƙasaita. “Mike ciyon?” ya faɗa a fisge kamar ba shine ya tambayeta yanzun nan ta bashi amsa ba. Ɗan zabura tai da jinsa gab da ita dan batai zato ba, ta yunƙura da sauri zata tashi ya maidata. Sai kuma ya kai zaune gefenta har jinkinsu na gogar juna. Sake zaburar taso yi ya sake maidata yana tsatstsareta da mayun idanunsa masu kaifi. “Ni dai ya warke barshi” ta faɗa da sauri tana ƙoƙarin ture hannunsa dake jikinta. Ko gezau baiyi ba, sai ma ɗorasa da yay saman kanta ya zare towel ɗin da ya naɗa mata tun ɗazun. Dogon gashinta mai alamar lema har yanzu dake faman ƙyalli ne ya bayyana, ya ɗan tsirama gashin ido na wasu sakkani kamar mai nazari, sai kuma ya janye yayo ƙasa da su kan fuskarta. Da sauri tai ƙoƙarin kauda fuskar, sai dai ya hana hakan ta hanyar taro fuskar tata cikin tafin hannunsa ya sarƙe idanunsa cikin idanunta ta ƙarfin tsiya. Wani irin tashi tsigar jikinta ta farayi, cikin rawar lips kamar zata saki kuka ta ce, “Nifa na warke nace”. Idanunsa ya lumshe da sake buɗewa a kanta yana kusanta fuskarsu gab-gab da juna. “Ban yarda ba”. Ya faɗa cikin raɗa-raɗa yana hura mata iskar bakinsa mai ƙamshin banana akan fuskar. Zuƙa tai ta lumshe idanun tana kame jikinta da ke son fara rawa. Da ɗan rawar lips ɗin ta sake furta, “Da gaske nake ciwon ya daina”. Yanda tai maganar a hankali cikin rauni kaɗan ya hana Shahan-shan sakin ihu, amma ya kanne cike da son nuna jarumta yana haɗe tsinin hancinsu waje guda. “Ni ban yarda ba, ki nuna na tausa miki bada zafi ba fa”. Da ƙarfi numfashin Iffah ya fisga tsabar shiga ruɗani, sai da ƙyar ta jawoshi ya koma ƙirjinta, sai dai rawar jikinta ta fara bayyana kanta. Jin saukar tattausan hannunsa bisa lallausar fatan gefen cikinta zuwa ƙugu da ya matsa ya sata furta “Wayyo Ummuna”. “Nima wayyo Ammie-na”. Ya faɗa cikin kwaikwayon ƴar muryarta yana sake tura hanun saman shafaffen cikinta. Da sauri tasa hannu biyu ta riƙe hannun tana tura baki, hakan ya bama lips ɗinsu damar haɗewa, sai tai azamar son kauda fuskar amma ya hana hakan. A bazata taji saukar lips ɗin nasa kan nata. A tare suka buɗe idanun da suka lumshe, sai dai ita zazzaro nata tayi saɓanin shi da ya tsareta da nasa cikin kallon data kasa bama fassara. Da wani salo ya kaɗa nasa alamar ta rufe natan, kamar wata gaula ko wadda yake juyawa da remote kuwa ta rufesu ruf jinin jikinta na hautsina mata. Dole ta ƙanƙame hannunsa dake kan cikinta har yanzu da masifar ƙarfi dan bata da zaɓin daya wuce haka bayan shi. Sai da yaso dan kansa ya janye lips ɗinsa suna mai sauke numfashi a jajjere kamar wanda sukai gudun gasa a ƙaton fili, cikin matuƙar dauriya ya kame nasa yanayin sai dai yaƙi yarda su haɗa ido sam. Itama ɗin dai ba kallon nasa take ba, hasalima bata da burin da ya wuce ta samu wajen ɓuya ko zata samu sassaucin halin da ya jefata na rashin tabbas. Tsahon wasu ƴan mintuna ɗakin ya cigaba da zama shiru, kafin shi ya katse hakan ta hanyar ɗagota gaba ɗayanta ya zaunar a kan gadon, hannunsa ya tura cikin gashinta, tai azamar rumtse idanunta da ƙarfi. Har yanzu akwai damshin da yake gudar mata shiga halin muran. A nutse ya miƙe tare da miƙar da ita, hannunta riƙe a cikin nasa suka isa gaban wadrub ɗin glass ɗin ɗakin nasa dake cike da kayan barci kawai. Ya ɗan danna wani maɓalli sai gata ta zuge ƙofa ta bayyana kanta. Saurin dubansa tai mamaki na barazanar halakata, shiko yay fuska abinsa kamarma bai ganta ba, sai ma janta da yay suka ƙarasa shiga. Ashe anan abun mamakin yake ba can ba, dan kuwa ɗakine babba zagaye da irin waccan wadrube na glass ɗin, kai kace wani shagon saida kaya ne mai zaman kansa. Duk wani nau'in sutura da kayan ado da yake sakama jikinsa ne anan, hatta da takalma sunada nasu sashen, agoguna masu ƙyau na diamond dasu azurfa dana manyan companys ne gasu nan ba'a magana. Bataji a ranta hakan mafarki bane ko bazai yiwu ba kasancewar sanin matsayinsa, Shahan-shan fa, ai ko abinda yafi haka ka gani bakayi mamaki ba. Shi dai ya fuske abinsa tamkar bai fahimceta ba, ya ƙarasa da ita gaban ƙaton mirror ɗin da ke ɗauke da nau'in kayan gyaran gashi kala-kala, ko mace albarka, saukar iskar ɗumin hair dryer ne ya maidota hayyacinta ta sauke nannauyan numfashi da ɗago idanunta ta dubi madubin.........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (20) .........Tar-tar take kallonsu a ciki yana busar mata da gashi a nutse fuskar kuma babu fara'a kota sisin kwabo. Kauda nata tai jikinta gaba ɗaya yay sanyi da al'amarinsa. Sotake tayi tunanin akansa dan ya gama birkita duk ginin da take kallonsa da shi a baya yau baki ɗaya, kaikawo kawai zuciyarta keyi. Ada zahirinsa take tunanin kallo, ashe ba haka bane, dan a yau ta kasa iya banbance zahirinsa na gaskiya. Ya rikita komai a lokacin daya kamata ace ta fahimci komai ɗin. Itafa gaskiya man kanta kawai ma ya tsiyaye tas.. _(Nima dai nawa ya tsiyaye ƴar koran taki Iffah. Shahan-shan yazo da babbar bidi'a fa gaskiya🥱🤣)._ ★★ MALIKAT BUSHIRAT ★★ Tun fara faruwar al'amuran nan yau ne zuciyarta ta ɗan fara mata wasi-wasi, a karan kanta sai take ji tana son sanin wanene ya shugabanci yarinyar domin halaka mata gudan jininta. Dan tabbas akwai ƙamashin gaskiyar lauje cikin naɗi. Ba komai ya sata farga ba a yau sai kallon zancen ido data ga yana gudana tsakanin Malikat Ashwaq da Ameera Haifah a ɗazun sanda aka wuce da Iffah. Sai kuma kallon da taga shi kansa Tajwar Eshaan ɗin ya musu su dukansu kasancewar suna tsaye duk a waje guda ne. Ita ta haifesa, duk da bata rayu da shi na tsawon lokaci a zaman kwana da yini ba, tasan halin ɗanta ciki da bai, ta masa sanin da ko da ido yay magana tana fahimtarsa. Lallai kallon yana da manufa, manufa irin wadda ya kamata ace ta sani. Manufa irin wadda ya kamata ace ta farka daga nannauyan barcin dake neman tasiri a idanunta. Ta jima tana zargin Malikat Ashwaq a duk abinda ke faruwa ga tilon ɗanta, sai dai a yau zuciyarta na gaya mata akwai wasu bayan itan, a wasun kuwa har Mamma (Malikat Haseenat) bata cire a ciki ba, dan akwanakin nan take-taken tsohuwar na rikita mata yardar data mata a baya. Nannauyar ajiyar zuciya ta sauke, gaba ɗaya ji take komai ya cinkushe mata, dole ne ma tana buƙatar yin nazari mai faɗi, ya kamata kuma ta gana da shi.... ★ Zaune yake harɗe a ɗaya daga cikin lafiyayyun kujerun falon. Tun dawowarsa da ga sallar la'asar ya yada zango anan. Laptop ce a coffee table ɗin gaban kujerar da yake yana sarrafata sannu a hankali. Sai mug na shayi dake ta faman tururi ƙamshinsa mai daɗi daya gauraya dana turarensa na tashi sannu a hankali. Sosai siririn farin gilashin idonsa ya sake masa ƙyau. A yanda gaba ɗaya ya tattara hankalinsa ga screen ɗin computer ɗin zai tabbatar maka abu mai matukar muhimmanci yake yi. Dan sai lokaci-lokaci ya kan ɗan ɗauka mug ɗin ya kai bakinsa ya maida ya ajiye duk hankalinsa na kan abinda yake yin. Sayeed Fayzul-haq dake shigowa ya sake maimaita sallamarsa cikin nutsuwarsa, a hankali ya motsa lips ɗinsa ya amsa batare da ya ɗago ba. Sayeed ya ɗan ranƙwafa yana kai gaisuwa duk da basu jima da rabuwa ba. Kansa kawai ya jinjina masa alamar amsawar kenan. “ALLAH ya ƙara maka lafiya da nisan kwana. Malikat ke neman izinin ganinka idan bata shiga lokacin da bai dace da ita ba”. Shiru ya ɗan tsaya daga sarrafa system ɗin, sai dai kuma bai dagoba har shurewar wasu sakanni da suka zama mintoci biyu. Maida yatsunsa yay kan keyboard ɗin kamar bazai ce komai ba sai kuma ya motsa lips ɗin kamar an masa dole ya furta, “Zata iya shigowa”. “Malikat na godiya, ALLAH ya cigaba da kare mana kai adalin shugabanmu. ALLAH ya gafartama magabata”. Duk da addu'ar ƙarshe ta masa daɗi a cikin rai bai motsa ba balle ya amsa. Har cikin ransa yana masifar jin maɗaukakin daɗi a duk lokacin da wani yay ma mahaifansa da suka kwanta dama addu'a.. ★Kallo yake mata irin na kewa da lumsassun idanunsa. Sai dai a zahirinsa baka isa fahimtar hakan ba kai tsaye. A hankali ya ɗan kauda idanunsa da ke binta da kallo yana rissinar da kansa dai-dai tana zama. Itama fuskarta da murmushi take dubansa saɓanin shi da tashi babu walwalar sosai. Sai dai ya motsa lips ɗinsa a hankali ya furta, “Barka da yamma Ammie.” Murmushi ta sake saki da ke sake fidda ƙyawun da ALLAH ya mata. “Ina fatan kana lafiya Niger?”. Maimakon amsa gajeren murmushin da ita kawai keda lasisin ganinsa ya ɗan saki yana kauda kansa, sai kuma ya sake maidowa yana mai zuba mata idanunsan nan masu kaifi. Dan ita kanta data haifesa a duk sanda ya tsareta da su tana jin tasirinsu sosai tattare da ita. Nata ta janye cike da ƙasaita ta furta, “Ya jikin Ibnati?”. Kamar bazaice komai ba sai kuma a fisge ya amsata. “Alhamdullah”. “Thanks God. ALLAH ya ƙara lafiya”. A zuciyarsa ya amsa amin ɗin. Bata damu ba ta cigaba da faɗin, “Abubuwa da yawa da ke faruwa suna sake rikitamun kai, sai dai basu ne suka kawoni ba a yanzu. Yaya maganar shari'ar da aka fara?”. “Tana nan Ammie, za kuma a ƙarasata”. Ya faɗa a hankali cikin taushin harshe. Ajiyar zuciya ta ɗan sauke sai kuma ta ambaci sunansa. Dara-daran idanunsa ya sake saukewa a kanta da ƙyau. Itama kallonsa take cike da so da ƙauna. “Ina son tattaunawa da kai mai muhimmanci, sai dai ba'a nan ba Bin Haysam Abdul-majeed”. Idanunsa ya lumshe ya buɗe a hankali, sunan data kirasa na ratsashi matuƙa, cike da girmamawa a gareta ya furta, “Ki yanke duk lokacin da kike buƙata ni mai jiran umarninki ne a koda yaushe”. Ƙasaitaccen murmushi ta saki ƙaunarsa na sake ratsata. Cikin gyaɗa kai ta furta, “ALLAH ya cigaba da karemun kai, ya lulluɓeka da tarin albarka da rahamominsa marasa yankewa. Duk sanda na yanke zaka jini na barka lafiya”. Kansa ya ɗan rissinar alamar girmamawa, kafin ya furta, “A huta lafiya”. ★★..... ★.... Bayan sallar magrib duk wani mai alaƙa da shari'ar ya kimtsa kansa a katafaren falon da akai wancan zaman farkon. Shine ƙarshen shigowa kamar a wancan zaman. Kan kowa rissine har ya zauna a inda aka tanada masa, tuni ƙamshinsa ya gama danne duk wani turare mai ƙarfi a wajen. Sai da ya gama binsu da kallo ɗaya bayan ɗaya ta ƙasan ido na tsawon wasu mintuna kafin ya mula dan kansa yay gyaran murya. Dake nutsuwa kowa yay da maida hankalinsa garesa. Nan ma ya sake jan wasu mintuna biyun kafin ya ɗaura da faɗin, “Naso yanke hukunci a zaman ƙarshe na Shari'ar nan a yau, sai dai masu hannu a al'amarin sun nuna mana su basa buƙatar hakan. Bazan tambayi dan mi akai yunƙurin kasheta ba a karo na biyu, sai dai zan sanar da duk wanda ya aikata ya sake shiri akan wanda yake da a baya. Kamar yanda kuka kawo ƙarar neman hakkin yunƙurin kisan jininku da tayi, nima zan shigar da ƙarar neman hakkin kashe min mata da akayi. Kamar yanda nai alƙawarin nema muku haƙƙinku matsayina na shugaba, itama zan nema mata nata hakkin Insha ALLAHU a matsayina na shugaba bayan ta samu lafiya”. Kan babbar buta kenan, ai ba wanda suka shigar da ƙarar ba hatta masu goyon bayan Iffah kalaman Tajwar Eshaan ɗin sai da sukai musu tsawar saukar aradu na wucin gadi. A hankali Malikat Haseenat ta saki wani ƙayataccen ɓoyayyen murmushi, a zahiri kam ta katse suman zaunen da jama'ar wajen sukai ta hanyar faɗin, “Hukuncinka adalcine ga kowa koda son zuciya ta rufe idanun kowa. ALLAH ya ƙarama Zawjata-almilk lafiya, ya tona asirin wanda sukai mata wannan aikin koda a cikinmu ne”. “Shugaba ya amsa tare da godiya ga Uwar masu gida abin al'faharin ƴaƴan ƙwarai. ALLAH ya ƙara miki lafiya da tsohon rai mai albarka baya goya marayu”. Wannan kalamai sun fito ne da ga bakin Sayeed Fayzul-haq mai yawun faɗa da yawun Tajwar Eshaan kasancewar yanzu tamkar amintaccensa yake. Babu dai wanda ya motsa a zahiri, dan tamkar duk sun tafi suman wucin gadi ne, hakan yasa ya cigaba da faɗin, “Wannan kotu mai adalci ta bada umarnin sakin Zawjata-almilk da alƙawarin bata kariya har zuwa sanda za'a yanke mata hukuncin daya dace da ita. Ta kuma saki amintattun hadiman da har yanzu bata kama da laifin komai ba, zakuma su cigaba da aikinsu da ga yau. Ta bada dama ga duk mai ƙorafi akan wannan hukunci ya faɗa a zama na gaba”. Tabbas sun gama yarda cewar Tajwar Eshaan tsohon makirin kansa ne. Sannan hatsabibancin da suke jifansa da shi fa sun tabbatar da shi ɗin a tattare da shi yau. Rai ɓace kusan kowa ya fita a falon bayan fitarsa, kowa bakinsa fal da magana sai dai babu damar yinta anan kuma gudun abinda zaije ya dawo... ★★...... Sam Iffah bata san wainar da ake toyawa ba, dan tun fita sallar la'asar da yay a ɗakin bayan ya tsareta ta ɗanci abincin da aka kawo bata sake ganinsa ba. Sai ma wani wahalallen zazzaɓi ne ya rufeta ruf. Da ƙyar ta iya tashi sallar magrib. Tayi ta a daddafe ta sake komawa saman gadon ta kwanta dan rawar sanyi jikinta ke mata. Bata iya tashi sallar isha'i ba tana cikin bargo. Sosai jikin nata ya ɗauka matsanancin zafi ga ciwon kai ga sanyi tana ji. Tun bata damu da ƙin shigowar tasa ba har ta fara addu'ar hakan, a haka wani wahalallen barci ya ɗauketa.........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (21) ........Har ya kammala shirin barcinsa zai kwanta zuciyarsa taƙi bashi haɗin kan hakan. Fuska ya ɗan yamutse kai kace bashi da ra'ayin abinda zuciyar tasa ke so. Sai dai a kallo ɗaya zaka fahimci tsabar miskilanci ke cinsa da ƙasaitar mulki. Cike da izzar dake bayyana takunsa a matsayinsa ya nufi ɗakin. A hankali ya tura ƙofan ya shiga bakinsa da sallama ƙasa-ƙasa. Kallon mamaki yake mata ganinta naɗe a cikin bargo, ga alamar ɗan rawa-rawa da jikinta ke mata da yake gani. Hannu ya kai ya ɗan janye bargon daga saman fuskarta. Aiko ta wani zabura, caraf ta damƙe hannunsa idanunta rufe ruf da alamar tana cikin mayen barcin dai bakinta na motsi cikin faɗa-faɗa take faɗin abinda baya ji. (Fitinatu har a cikin barcin ma ba'a kadata) ya faɗa a zuciyarsa yana lumshe ido da riƙota ganin da gaske fa faɗan take ga zafin hanunta dake kan nasa na ratsa fatar shi. Jikinta rawa yake sosai, dan mafarkin da tai ya matuƙar firgitata, ta daɗe batai irin mafarkan nan ba. Da farko mamakin yanda take ɗinne ya shiga, sai dai ganin abinfa na gaske ne sai hankalinsa ya tashi. Amma bazaka taɓa tantancewa ba a face ɗin sa. Kaɗan ya girgizata muryarsa a ƙasan maƙoshi ya furta “K!”. Ina batama san yanai ba, sai ƙoƙarin fisge jikinta da take kamar dai yanayin da takan shiga a duk lokacin da tai irin mafarkan. Jikinsa ya jawota sosai yana ɗan bubbuga fuskarta kaɗan-kaɗan, sai kuma ya sake faɗin, “Open your eyes. Iffah k!”. Karan farko daya taɓa ambatar sunanta, duk da bata a hayyacinta sai da taji fitar sautin sunan. Buɗe idanun tai a hankali jikinta na ɗan tsuma ta sauke a kansa, sai kuma taja nannauyan numfashi tana ɗan ƙara warosu domin tabbatar da shi ɗinne a zahiri ko har yanzu a mafarkin ne dai. A hankali ya mannata da ƙirjinsa ya rungume. Wani ajiyar zuciya ta sake ja mai ƴar shashshekar data saka tsigar jikinsa tashi. Sai kuma ta maida idanunta ta lumshe sannu a hankali ganin yanda ya tsareta da kaifafan nasa idanun. Lafewa tai a jikin nasa kamar wata mage, dan kanta ciwo yake matuƙa. Ba ƙaramin dauriya yay ba na zamanta jikinsa har tsahon mintuna uku, cikin son danne yanayin da ke neman halaka shi ya buɗe idanunsa da suka canja kala akan ƙyaƙyƙyawar fuskarta. Wani irin kallo yake binta da shi tun daga fuskarta har zuwa ƙafafunta, gaba ɗayanta naɗe take a jikinsa. Yanda ta naɗe ɗin ya bama abayarta mai sanyi damar lafewa a jikin nata ya fidda mata suranta da ƙyau. A kasalance ya lumshe idanunsa yana kauda kansa jin numfashinsa na wata rawa-rawa. Ga ɗumin jikinta na matuƙar ratsa nasa jikin. “What happend?”. Ya faɗa a cikin kunenta da wata irin shaƙaƙƙiyar murya da bata taɓa ji da ga garesa ba, gata acan ƙasan maƙoshi matuƙa. Yanda sautin ya ratsa kunenta har cikin ɓargonta da ƙwaƙwalwar ta ya sata rumtse idanunta da masifar ƙarfi tana wani ƙanƙamesa. Ihu kawai ya rage ya sakar mata ko zata gane a wane riski ta jefashi, amma sai ya danne cike da jarumta ya furzar da boyayyan huci. Cikin sigar tambaya ya sake faɗin, “Uhhuyim?”. Nan ma kamar bazata amsa ba sai kuma ta nisa tana sauke ajiyar zuciya. Kanta ta ɗan girgiza a hankali ta ce, “Mafarki”. “Mafarki?”. Ya maimaita akan lips ɗinsa yana ƙoƙarin saka idanunsa cikin nata kasancewar ta ɗago da ga jikin nasa. Kanta ta gyaɗa masa tana ɗan kauda idonta, dan tun abinda ya faru ɗazu a tsakaninsu sai ta tsinci kanta da jin matsananciyar kunyarsa. Yanzun ma dan kawai tana a firgice ne. Kamar zai ƙara magana sai kuma ya share, murya a shaƙe mai tabbatar da ya gaji da magana ya motsa lips ɗinsa a nutse kamar a fisge, “Kinyi salla?”. Kanta ta ke girgiza masa batare da ta yarda ta kallesan ba yanzu ma. Komai bai sake cewa ba ya miƙe kawai, kamar wanda ke'a yanayin sanyi jiki ya nufi hanyar bathroom. Da kallo ta bisa ƙasa-ƙasa, mummunan mafarkin da tayi a kansa na dawo mata. (Mafarki ba gaskiya ba ne) zuciyarta ta ayyana mata, hakan ya sata sauke ajiyar zuciya ta zame ta kwanta jin sanyi na ratsa mata gaɓoɓi. Bai wani jima sosai ba ya fito, bargon data rufa ya kama ya yaye, tai saurin riƙowa tana ɓata fuska da turo masa baki. “Ni dai sanyi nake ji”. Ido kawai ya tsirama lips ɗin nata batare da ya iya cewa komai ba, kafin ya ranƙwafa a kanta slowly ya ɗauke ta cak ɗinta cikin hannayensa. Ba ƙaramin waro masa manyan idanunta tai ba. Ya ɗan harareta yana kauda nasa. Itama kauda natan tai tana kumbura bakin gaba sosai. (Stubborn girl) ya faɗa a ransa, a zahiri kam fuskar ya sake tsukewa da kyau kai kace da ɗa duniya bai san miye murmushi ba. Yana direta yay fitowansa abinsa. Binsa tai da kallo, abubuwa masu yawa na mata yawo a zuciya game da shi.... Da ƙyar ta iya bin bango ta fito bayan idar da alwalar, yana zaune a cikin kujerar idonsa kan television ɗin ɗakin. Kaɗan ya ɗaga idanunsa ya kalleta ta ƙasa-ƙasa. Duk da yaga yanda take layi tsabar baƙin hali da ƙasaitar mulki ya hanashi tashi ya sake taimaka mata. Harta ƙaraso inda ya shimfiɗa sallayar kamar bai ma san da fitowarta ba. Kallonsa ta sata ta kauda kanta, sai kuma hakan da yay mata ya ƙona mata rai. Cikin jin haushi-haushinsa ta ɗan ƙarfafa kanta, gyalen daya ajiye mata ta ɗauka ta naɗa a kanta, kasancewar abayar jikinta babu ta inda ta tawaya ta kabbara sallarta cike da nutsuwar da ke tabbatar da ta samu wadataccen ilimin addini. Shi kansa yanda take sallar a nutsu duk da wani lokacin jiri kanyi kamar zai kadata sai yaji wata nutsuwa ta ratsashi. Wani kimar iyayenta da sake ganin darajarsu na mamaye sa. A zahiri kam bama zaka taɓa ɗauka hankalinsa a kanta yake ba. Fuskar nan tai ciɗin-ciɗin ko ɗan yankar kanun mutane sai haka😏. Tana idarwa ta zame a wajen ta kwanta hanunta dafe da kanta dake matsanancin sara mata, zuwa can kamar wadda aka zabura ta miƙe zumbur hanunta a baki, sai kuma ta nufi bathroom da ɗan gudu-gudu alamar amai. “OMG!”. Ya faɗa a hankali ƙasan maƙoshinsa jin tana kakarin amai. Bai motsa ba duk da yanda zuciyarsa ke bugawa da sauri-sauri, kusan mintuna biyu da wasu sakanni sai gata ta sake fitowa tana layi. Ga hawaye shaɓe-shaɓe a fuskar gwanin ban tausayi. Yanzu kam miƙewa yay da ƙyar ya nufeta, kamar jira dai-dai yana isowa gab da ita tai wani luuuu zatai baya ya tareta cikin zafin nama ta faɗo cikin hannunsa.. A hankali ta dinga jan ajiyar zuciya jin bata faɗin ba. Sai dai ta kasa buɗe idanunta da ke rufe ruf duk da tanajin alamun nasa kamar na binta da kallo. Kallon nata kuwa yake cike da kasala, sai kuma ya ɗan lumshe nasa idanun shima yana sake rungumota da ƙyau har yana jin saukar numfashinta a jikinsa. Yanda nunfashinta ke saukar masa a jiki sai yake jin tamkar shima hajijiyar na neman kwasarsa, gudun kar ai abin kunya ya ɗagata cak ya ajiye a saman gadon. Kafin ya zauna a kusa da ita yana mai tsura mata fararen idanunsa. Sun kai kusan mintuna biyu a haka, kafin ya katse shirun ɗakin ta hanyar motsa lips ɗinsa a hankali ya furta, “What again?”. Kanta ta nuna masa da gyar ta furta. “Kaina kamar zai fashe”. Sai ga hawaye sharr. Ita kanta bata san miyasa take jin karaya ba a gabansa ko ma shagwaɓa ne oho. Idanunsa ya zuba mata kawai yana bin hawayen da ke bin ƙyaƙyƙyawar fuskarta da gudu-gudu da kallo. Haka kawai sai yaji murmushi na suɓuce masa. Kansa ya kauda gefe yay murmushin sannan ya ɗan sake matsawa kusa da kan nata sosai. Numfashi ta ɗan ja a sanyaye jin saukar lallausan tafin hannunsa saman goshinta. Shi kansa yanda zafin kan ya ratsa hanun nasa sai da ya ɗan lumshe ido. Murya can ƙasan maƙoshi ya ce, “Ta nan ne?”. Kanta ta ɗan jinjina masa, sai kuma ta ɗaura nata hannun saman nasa ta ɗan matsar zuwa gefen kunenta idanunta na sake kawo ƙwalla ta ce, “Harda nan da ma duka”. A yanda tai maganar cikin shagwaɓa kamar wata ƴar baby yaji tsigar jikinsa na wani yamutsawa. Amma jarumin naku sai yay ƙoƙarin basarwa har da yamutsa fuska kaɗan ya furta, “K raguwa ne ko? Just ciwon kai ki ke ma kuka?”. Kamar ya tunzurata ta sake turo masa baki da son ture hannunsa da ke kanta. Ko gezau, dan haka tai yunƙurin juyawa. Nan ma sai da ya nema sakin murmushi amma ya fuske. Cikin wata murya da mai lura zai iya fahimtar shauƙin da yanayin da suke cikin ke bashi ya ɗan matso da jikinsa gab-gab da nata yana faɗin, “Kin cika ragwantaka ne ai. Na miki addu'a?”. Kamar zata sakar masa kuka ta ɗaga kan dan da gaske kan na mata ciwo ne sosai. Shiru bai sake magana ba ya kamota, kan nata ya ɗaura saman jikinsa. Sannan ya sake maida hanunsa saman goshin yana ɗan murza mata sannu a hankali yana mata addu'an. Idanun ta dinga lumshewa sannu-sannu itama, batare data farga ba barci mai nauyi yay awon gaba da ita. Bai daina addu'an da murza mata goshin ba, sai ma wani mayataccen kallo da yake mata idanunsa a shanye. Ya kwashe tsahon lokacin da bai fargaba a wajen zaune, dan tun kan da zafi har ya fara hucewa. Inda wani yace masa hakan zata faru tsakaninsa da wata ɗiya mace zai ƙaryata. Sai dai shi lissafin ƙaddara bai damu da wanda zai lissafa maka ba komai taka tsantsan ɗin ka akan nisanta kai ga abu.........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (22) ........Komai ya ƙara kwaɓema ta-ƙurya, ta rasa wace hanya ya kamata tabi dan ganin wannan aure ya ƙullu tsakanin Shahan-shan da yarinyar da sai a yau ta saka amintaccen bawanta bincike a kanta. A ɗan gefen ga jami'an gidan sun mugun duƙufa domin gano wanda yay tsaurin idon ɗaukar Zawjata-almilk daga kurkuku zuwa cikin pool har da kashe jami'an dake tsaronta. Da zafi-zafi suke aiki a wannan yini dan Tajwar Eshaan ya basu kwana biyu ne kacal. Sunko duƙufan matuƙa, domin umarnin mai gayya mai aiki ba abin wasa bane a garesu. Tasan amintaccen hadimin nata shi a karan kansa bai san ita ɗin wacece ba, dan bayan muryar da take masa magana da ita a duk sanda zata sakashi aiki babu abinda ya sani tattare da ita kuma. To ko muryar ma ai bada tata ta ainahi take masa maganar ba. Sai dai duk da wannan tsaron data tabbatar tana da shi bata kasa jin wani ɓurɓushin damuwa ba a ƙasan ranta game da tsananta binciken. Ga Uwa tai mata alƙawarin bazata taimaketa da komai ba a wannan gaɓar, acewarta shine hukuncinta. Ta tsani yarinyar nan, tsana irin wanda batajin ta taɓa yima wani mahaluki irinta a rayuwa. Bata taɓa fuskantar tangarɗa a aikinta ba sai da yarinyar ta shigo rayuwarta. Matsala bata taɓa shiga a aikinta ba sai da yarinyar ta shigo masarautar. Tabi hanyoyi da yawa domin ganin bayanta amma ko gezau. Ta rasa wane kalar shegen taurin kai yarinyar ke da shi. Ita zuciyarta ta fara bata ma anya yarinyar ba shugabar wata ƙungiyar asiri bace mai zaman kanta? Dan abubuwan da ke faruwa a kanta sun fara bata tsoro. Sai dai taci alwashin kota halin ƙaƙa ne sai ta shafe babin rayuwar yarinyar da kaf zuri'arta a duniya nan bada jimawa ba. Wannan alkawarin ta ne...... (Ni dai nace hummmm). ★★.... ★★.... Fuska cike da murmushi yake duban kayan surkullen da boka Barbushi ya basu. Cikin ƴar dariya-dariya ya dubi Miran Arshaan da shima a kallo ɗaya zaka fahimci nasa nishaɗin. “Idan ya isa shi hatsabibi ne a wannan karon ya tsallake mana, ai idan yasan wata bai san wata ba damu yake labarin da ga shi har ƴar iskar yarinyar tashi”. Ƴar dariyar shima Miran Arshaan ɗin yayi, cike da nishaɗi ya ce, “Sai dai uwarsa Bushirat kuwa ta haifi wani amma ba madadinsa ba. Tunda taƙamarsa taurin rai sai mu bisa ta hanyar da zai laushi ta dolen dole da ƙaniyarsa. Shegen yaro kamar jinin aljanu da ga shi har ƴar ƙaniyar yarinyar”. “Kona ifiritai ne wannan karon dai tasu ta ƙare. Dan haka a daren nan na yau zamu saka komai a inda ya dace kamar yanda Barbushi ya bada umarni. Dan ubansu badai sunƙi mutuwa ta sauƙi ba, to ga rayuwar yayita sai dai a cikin ƙunci da baƙin ciki da ga shi har duk wani mai iya jin zai bashi kariyar.” Dariya suka sheƙe da ita har da tafawa kamar wasu abokai. Kafin su miƙe cikin ɓadda kamar da suka gama shiryawa suka nufi fada yanda boka Barbushi ya basu umarni..... ★★... ★★.... Kamar yanda ta saba farkawa akan lokaci domin gudanar da sallar asubahi yau ma bata makara ba. Sai dai saɓanin ko yaushe yau a firgice ta farka. Da sauri-sauri ta ke karanto addu'ar tashi da ga barci tana faman waige-waige a ɗakin mummunan mafarkin da tai a daren jiya da ya sake maimaita kansa gareta yanzu na sake dawo mata. Sosai take jin zuciyarta na tsitstsinkewa, dole taja jikinta ta maƙure kanta a fuskar gadon tana mai naɗe jikinta da son riƙe rawar da yake yi bakinta na ambaton sunan ALLAH kamar yanda kaka ya horeta da daina ihu a duk sanda tai mafarki makamantan hakan saɓanin da da take ihun. Ta ɗauka tsahon mintuna shida kafin ta ɗan samu nutsuwa. Sai ajiyar zuciya da take faman saki a jajjere. Da alama ita ɗaya ta kwana a ɗakin batare da tasan sanda ya fice ba. Hanunta ta kai saman goshinta da zuwa yanzu Alhamdullah babu matsanancin ciwon kan nan data kwanta da shi. Sai ma ɗan sanyi-sanyi da damshin zufar data haɗa ya haddasa mata. Janyewa ta sake yi tana mai lumshe idanunta, haka kawai take jinta wata daban a yau kamar ba Iffahn Babiy da Ummu ba. Ko miye dalilin jin hakan bata sani ba. Kabbara salla da aka farayi ya sata miƙewa zumbur tana ture komai gefe. Gaba ɗaya jikinta babu ƙarfi, ga mafarkin da tai ya sake nunar mata da gaɓɓan jikin baki ɗaya. Haka dai ta ɗan watsa ruwa mai ɗumi ko zai saki sannan tayo alwala ta fito. Bayan ta gabatar da salla maimakon ta koma ta kwanta sai tai zaman karatun Alkur'ani ko zata samu nauyin da zuciyarta ta mata na kwana biyu ya ɗan rage... ★ Saɓanin ita shi ko rintsawar ma baiyi ba gaba ɗaya. Dan tun bayan barowarsa ɗakin da take yana zaune ne gaban laptop yana aikin da shi ya barma kansa sani. Har kusan uku yana zaune kafin ya tattara ya ajiye ya ɗauro alwala. Bai tashi a sallayar ba sai lokacin asubahi da zai wuce masallaci. A maimakon Gym da ya saba shiga ko yin wasan takobi a wasu ranakun sai ya nufi sashen Malikat Bushirat ta sirrintacciyar ƙofar dake kaisa sashen batare da kowa ya gansa ba idan yaso hakan. Jin nutsatstsiyar muryarsa nayin sallama a can ƙasan maƙoshi Jasrah da Malikat Bushirat suka dubi juna a yanayin mamaki. Cikin rashin aminta da abinda suka jin Malikat Bushirat ta bada umarnin shigowa. A maimakonsa shi ɗinne kuwa. Shi kam baiyi wani mamakin ganinsu taren ba duk da a yanzu aka idar da salla, dan yasan ɗunbin shaƙuwar dake tsakaninsu ta dabance. Maimakon zama a cikin kujera a hankali ya kai zaune kusa da Malikat Bushirat dake zaune kan sallaya har yanzun. Dan tana idar da salla Jasrah ta shigo mata. Gab-gab da ita yake zaune yana mai tanƙwashe ƙafafunsa tare da ɗaura kansa a kafaɗarta. Ajiyar zuciya ya sauke a hankali yana lumshe idanunsa. Malikat Bushirat da ke kallonsa cike da tausayawa sanin in har ta gansa a yanayin nan yana cikin damuwa ta kai hanunta kan tattausar sumarsa yalwatacciya ta shafa a hankali. Nan ma ajiyar zuciyar ya ɗan ƙara saukewa. Kafin ya motsa lips ɗinsa kaɗan ya furta “Barka da asuba ya Ammie-na”. “Ka tashi lafiya Saiful-malik”. Ta amsashi da kulawa tana sake tura yatsunta cikin sumar kansa a hankali. Kai kawai ya ɗan gyaɗa mata, sai kuma batare da ya dubi Jasrah da ke kallonsa ba ya ce, “Aunt good morning”. Murmushi ta saki jin yau kuma ita ake gaidawa. Itama ta amsashi da kulawa tana tasowa da ga inda take ta dawo ta ɗayan gefen Malikat Bushirat suka sakata tsakkiya ita da shi. Idanunsa ya ɗan buɗe kaɗan ya mata hararar wasa, a zahiri kam babu alamar ko murmushi a fuskarsa. Cikin fisgo maganar tasa da kamar an masa tilas yace, “Ammie kice ta tafi ta barni, ita kullum tana nane da ke tai auren ma baki huta ba”. Wani sassanyan murmushi Malikat Bushirat ta saki, dan yanda yay ɗin sai ya tuna mata da ƙuruciyarsa lokacin idan sunje dubashi harda Jasrah. Yata mita kenan Jasrah ta tafi tunda ita tana ganinta kullum har sai mahaifinsa ya shiga lallashinsa yake haƙura. Ita kanta Jasrah sai komai yake dawo mata, fuska ɗauke da murmushi tace, “Nikam babu inda zanje, sai dai kai ka koma inda ka fito ka barni da mamata”. Fuska ya ɗan kauda gefe yana sake tsuketa, amma baice komai ba. Ita kuma Jasrah ta cigaba da ɗan tsokanarsa kamar yanda takeyi a baya Malikat Bushirat na karesa tana musu dariya. Shi dai da ya fara takalo wasan bai sake ce musu ko kanzil ba. Bayan wasu ƴan mintuna Malikat Bushirat taci serious tana maida dukkan hankalinta kansa. Murya cike da kulawa ta ce, “Baka da lafiya ne?”. Kai ya juya mata alamar a'a. Sai kuma ya motsa lips ɗinsa kaɗan ya furta “Ina missing ɗinki ne my first luv”. Ji tai wani daɗi na ratsata, kanta na sake kumbura da alfaharin kasancewarta mahaifiya ga wannan ƙasaitaccen bajimin ƙyaƙyƙyawan sarkin. Ta sake shafa fuskarsa da kulawa matuƙa. “ALLAH yay maka albarka, ya cigaba da kulamin da kai da baka kariya”. “Amin”. Ya furta a saman lips, Jasrah kam a zahiri tana murmushi. Idanunsa ya maida kan Jasrah, fuskarsa babu alamar wasa ya furta “Mi kikeyi anan da safen nan kika bar mijinki?”. Murmushi ta masa ganin a serious yay maganar babu wasa a ciki. Tana ɗan wasa da yatsunta dan bazata iya kallonsa ba tai maganar dake bakinta duk da a shekaru itace sama da shi, sai dai ALLAH ya kwace girman ya bashi matsayinsa na namiji kuma sarkinta, a hankali ta ce, “Maganace mai muhimmanci ta kawoni”. Ta ƙare maganar tana ɗan ɗagowa ta dubi Malikat Bushirat. Shima kallonsa ya maida ga Ammien tasa. Malikat Bushirat ta sauke sassanyar ajiyar zuciya tana ɗan shafa kansa, “Magana ce muhimmiya Jasrah tazo da ita a kanka Saiful-malik”. Kaifafan idanunsa ya ɗan tsura ma Jasrahn ganin yaƙi yarda ta kallesa ya janye su ya sake maidawa ga Ammien sa. “Wani abu ya faru ne?”. Kai Malikat Bushirat ta girgiza masa, “Komai bai faruba, na baya ne dai da suka faru musamman akan abinda yarinyar nan ta aikata. Ba kowa ne zai fahimci irin abin da naji ba a lokacin da na fahimci zan iya rasa tilon ɗan dana mallaka a duniya. Amma sai na danne zuciyata wajen maida hankali na maka addu'ar samun lafiya fiye da ɗaukar mataki. Bani da jayayya akan hukuncinka, sai dai ƴar uwata tazo da shawarar dana gamsu da ita nima”........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (23) .......Kansa dake a kafaɗarta ya ɗago a hankali jin yanda take maganar a serious, sai dai baice komai ba. Itama batare data kallesa ba ta cigaba da faɗin, “A nawa ra'ayin ka rabu da yarinyar nan, sai dai bazan tirsasaka kan hakan ba zan jira har lokacin da za'a yanke mata hukunci bisa abinda ta aikata. Amma kamar yanda Jasrah ta faɗa ya kamata ka ƙara aure. Ina son ka samu farin ciki kaima kamar kowane namiji mai irin shekarunka. Ina son naga zuri'arka Eshaan. Na kuma shirya fito-na-fito da duk mai son daƙile waɗan nan zaren farin cikin namu ta hanyar kashe yaran da basu ji ba basu gani ba dan kawai kasancewarsu matanka. Nima a wannan karon na shirya, na shirya tarar kowa Eshaan...” Kuka mai tsuma zuciya ya sarƙe ta. Har cikin ransa yake jin kukan nata, sai dai babu alamar zaice wani abu. Jasrah da itama ke hawayen ta miƙe a hankali zuwa gabansa, zama tai ta kamo hanunsa cikin nata cike da kulawa ta kira sunansa. Ɗagowa yay a hankali ya zuba mata idanunsa da baka isa gane yanayin da yake ciki ba koda a cikinsu. Hawayen da ke cigaba da zubo mata ta share tana ɗan kauda idanunta zuwa ƙasa, dan kaifin nasa sun mata yawa. “Kayi haƙuri ka fahimcemu Abni, muna tsananin jin zafin abubuwan da ke faruwa da gaba ɗaya sun ta'allaka da kai ne matsayinka na shugaba sama da kowa na ƙasar nan. Lokaci yayi da zamu tashi yin fito na fito da kowa a wannan gaɓar. Ba zai yiwu mu cigaba da zuba ido ba kuma. Kafin yau mun tattara hope ɗin mu gaba ɗaya kan yarinyar nan, amma daga ƙarshe itama tai shirin halaka ka ma. Shiyyasa nai tunanin ya kamata a nema maka wata matar dan nasan kai dai baka da wannan lokacin, mu kuma Insha ALLAHU zamuyi duk shirin da ya dace don ganin mun kamo bakin zaren. Fatanmu mu dai kawai amincewar ka, dan wannan al'amarin baya buƙatar cigaba da zuba idanu kuma”. Uffan bashi da alamar cewa, bai kuma canja da ga kallon da yake musu ba a zahiri. Suma sai duk sukai shiru, dan sun san halinsa sarai.... ★★.... Bayan barowarsa daga sashen Malikat Bushirat ƙayataccen Gym ɗinsa mai ɗauke da nau'ikan machines na zamani ya nufa. Tuni hadimai masu tsaron wajen suka zube kan gwiyawunsu suna miƙa gaisuwa. Idanunsa kawai ya lumshe yay shigewarsa batare da yako kallesu ba. Da alama dai yau ƴan mulki ne bisa kai da miskilancin, ko kuwa maganar da yay da su Ammien tasa ne ke tsikarar masa rai oho dai. Sosai Gym ɗin ya ƙayatu ga mai kallo, dan hatta kaya motsa jikin an musu wadrube ne na musamman gasu nan iri-iri. Tattausar jallabiyar jikinsa ya cire ya ajiye, sannan ya fiddo set ɗaya na kayan ya ɗauka dogon wandon kawai ya saka. Sosai mutum ne buɗaɗɗe da baka gane hakan kai tsaye idan baya cikin riga. Cikin zafi-zafin da ke nuna kamar yana cikin fushi ya fara sarrafa machine ɗin gudun idanunsa a rufe ruf. Ya kwashe tsawon lokaci yanayi dan sai da yay sharkaf da zufa kafin ya kashe ya koma wajen ɗaga ƙananan ƙarfe irin na riƙewa a hannun nan ko kana daga zaune zaka ɗaga, duk da dai a zahiri kallon kitse akema rogo suna da matuƙar nauyi. Nan ma kusan mintuna goma sha biyar ya ajiye ya koma ɗaga ainahin ƙarfe daga kwance rigingine. Haka ya dinga caccanjawa har ya shafe tsahon awa biyu da wasu mintuna a ciki. Kafin yaja rigar wandon ya saka tare da ɗaukar goran ruwa ya kwankwaɗa yana sauke numfashi, dan shi ɗaya ke zuwa nan kawai bayan hadiman dake tsaren wajen. Ko amintaccen hadiminsa baya zuwa da shi. Kamar yanda aka saba ya samu shayinsa na ƙa'ida a ɗakin da ya kwana, dan masu aikin girka abincinsa sun cigaba da aikinsu tare da amintacen hadiminsa. Zaman shan shayin yay yana mai shaƙar daddaɗan kamshin da ɗakin keyi na gyaran da ya sha harya kammala. Da ga haka ya nufi bayi tsaftace jikinsa. Ya kwashe lokaci mai tsayi anan ma kafin ya fito ya shige inda kayansa suke domin shiryawa. Masha ALLAH na ambata lokacin da yake fitowa cikin wata irin shiga ta alfarma. Ga wani ni'imtaccen ƙamshi na musamman da ya sake gauraye ɗakin cikin ƙanƙanin lokaci. Dubansa ya kai ga agogon ɗakin yana ɗan ɓata fuska. Yana da buƙatar zuwa ya duba yaya ta kwana. Ga shi kuma ya makara, dan yanada shari'ar da zai gudanar a fada yau. Batare da ya yanke hukuncin abinda ya dace yay ba ya fito cike da takun nan nasa na izza da ƙasaita tamkar mai tafiya a saman iska tsabar yanda yake wani ɗaga ƙafafun da sauke su a nutse. Fuskar nan tsam babu alamar yama san minene yaran murmushi. Har ya nufi hanyar da zata sada shi kai tsaye da falo ya ɗan dakata, gajeren tsaki ya ja da juyowa sannu a hankali ya doshi ɗakin da Iffah ta kwana. Ƙamshinsa da sautin takun sawayensa da ke alamta isowarsa waje ya sata ɗan ɗago idanunta ta zubama ƙofar, sai kuma ta kauda da sauri ta cigaba da tsamar dabinon da aka zuba cikin zuma a wani ɗan farin bowl da ke a cinyarta. Kamar yanda yay sallamarsa ciki-ciki haka itama ta amsa masa can ƙasan maƙoshi batare da ta motsa da ga yanda take ba har ya iso tsakkiyar ɗakin. “Barka da safiya”. Ta faɗa kanta tsaye batare da ta ɗago ta kallesa ba, duk da kuwa tana matuƙar buƙatar hakan amma ta kwaɓi kanta. Maimakon amsa gaisuwar da tai masa sai ya jeho mata tambaya a bazata yana wani shanye idanunsa da ke binta da kallon ƙurilla. “Kina jin wani ciwon ne a yanzu?”. Idanunta ta ɗago sannu a hankali ta zubasu a kansa karo na farko. Gabanta yay wata irin mummunar faɗuwa ganin exactly kayan da tai mafarki da shi dai sune a jikinsa daren jiya da asubahin yau ne dai abin kamar wani almara. Sai dai kwarjinsa da wata barazanar cikar haiba ta cika mata idanun. Babu shiri ta maida nata ta rissinar zuciyarta na wani irin bugawa da sauri-sauri. Amma a zahiri ta wani sake tsuke fuskar ne kamar yanda tashi ke'a tsuke. Kanta ta girgiza masa maimakon amsa masa da baki. Sosai fitinar yarinyar nan ke bashi mamaki, a fuska bazaka taɓa tunanin halayyarta ba, dan tanada suffar mutane masu sanyin hali da rashin son yawan magana ma, sai dai inta buɗe baki ko kanari albarka ya kada ita. Rigimarta ta musamman ce sama da duk ta wani rigimamme da ya sani a tsayin rayuwarsa. Lips ɗinsa ya ɗan laɓe cike da sake tsuke fuska magana can ƙasan maƙoshi a fisge ya furta, “Akwai phone a side drawer, zaki iya magana da Mammy game da abubuwan buƙatarki, idan kuma zaki online shopping ne da kanki fine. Da akwai card tare da ita” ya ƙare maganar yana ɗan matsawa ga table ɗin dake ɗauke da takardun da bata san na minene ba ya ɗauka pen. Ɗan rubutu yay a takarda ya tako har gabanta ya ajiye batare da ya sake cewa komai ba ya juya zai bar ɗakin. “Jazakallahu khairan”. Ta faɗa a hankali, lumshe idanu yay batare da yace komai ba ya cigaba da tafiyarsa. Kamar wadda aka tsikara ta miƙe zumbur. Kaɗan ya rage tai tuntuɓe da lallausan carpet ɗin gaban gadon ALLAH dai ya bata sa'ar tsallakewa ta cimmasa. Yana ƙoƙarin ɗaura hannunsa kan handle ɗin ƙofar sai ganinta yay a gabansa kamar wata aljana. Mar-mar ta ɗan yi da idanunta tana motsa pink lips ɗinta a marairaice. “Indai fita ta wuce iya nan sashenka ka haƙura kar kayi Pleaseee”. Idanunsa ya tsura mata da wani irin kallo da ta kasa bama fassara, dole ta risinar da nata tana ɗan wasa da bazar veil ɗin abayar jikinta da tai mata matuƙar ƙyau kasancewar blue black. Itama dai tashi tai kawai ta ganta bata san daga ina ba, amma tasan dai shine ya ajiye kamar yanda ya ajiye mata jiya. Idanun ya sauke a hankali kan hanun nata fari tas da babu wani datti a ƙunbunan suma. Kamar bazai ce komai ba sai kuma ya sake maida idanunsa kan fuskarta a fisge ya furta, “Akan wane dalili?”. Baki ta ɗan turo kaɗan, ta ce, “Kawai”. “Kawai?”. Ya maimaita a sigar tambaya da wata irin muryar jinjina wautar ta. Kallonta ya cigaba da yi cike da nazari.. Tsintar kanta tai da jin ƙafafunta na rawa, dan idanunsa kaifafa da ya tsareta da su ji take suna sagar da ɗan sauran ƙwarin gwiwar tata. A hankali ta motsa da nufin barin wajen ya tareta da hannunsa. A marairaice ta ɗago tana dubansa kamar zata fasa kuka, sai kuma ta sake maida idanun ta risinar tana ɗan ƙara tura baki dan yaƙi daina kallon nata.. Idanun ya ɗan lumshe da sake buɗewa a kanta, a wata irin ƙaramar muryar da inba kusa da su kake bazaka taɓa sanin yana magana ba ya ce, “Kin san a gaban wa kike kuwa?”.......✍️ _😂Da alama ta manta Shahan-shan, sai ka tuna mata fa🏃🏃🏃🥱._ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (24) ........Kasa daurewa tai sai da ta ɗago ido ta ɗan kallesa, babu shiri ta sake maidawa da sauri. Amma gudun kar yaga gazawar tata sai cewa tai, “Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed. Shahan-shan ɗin ƙasar ruman mana”. Ta bashi amsa tana ƙwaɓe fuska babu ko gargada a harshenta balle muryarta.. Mutuwar tsaye yay na mamaki, ya lumshe idanunsa a hankali, shi yau shi Eshaan ƙaramar yarinyar nan ke ambaton sunansa babu ko gargada a harshenta ko nuna shakkarsa balle akai ga tsoro a gabansa ido cikin ido. Abune da bai taɓa jinsa ba sai a bakin mahaifiyarsa ko kakarsa. Suma ɗin akan jima baiji sun ambata ɗin ba. (Kai wannan yarinya zata halaka shi) “Kada fa kace nayi rashin kunya kasa a ɓatar da ni ban gama cika burina ba, tunda ai dai kai ka tambayeni ko”. Ta faɗa tana mai langaɓar da kai idanunta na ɗan cikowa da ƙwalla na shagwaɓa da katse masa tunani da muryar nan tata mai ingiza bugun zuciyarsa kamar tasan mi yake tunani. Komai baice mata ba, duk da yanda take kallonsa a kaikaice. Ya dai ɗan matsa gabanta yana cigaba da kallon ta kawai har tsawon wasu mintuna yanda tai kamar wata ƴar baby na bashi dariya a ƙasan zuciya. Sai kuma ya janye tare da ɗan matsawa da ga jikin nata da ya matso a zahiri babu ma alamar yasan minene murmushi. Aiko sai gata tana jan ajiyar zuciya. Basarwa yay kamar baijita ba. “Miye burin naki?”. Kalmar ta fito da ga harshensa a ɗan fisge tamkar wanda akaima dole. Batare da ta yarda ta kallesa ba ta ce, “Suna da yawa, muhimmai a cikinsu dai yanzu duk sun shafeka”. Wani kallo da ke nuna alamar ni ɗin yay mata. Tako ɗaga masa kanta idanunta na ɗan cikowa da hawaye tana ƙiƙƙifatasu. A raunane kamar ba ita ba ta ce, “Ina son sanin halin da Iyayena ke ciki duk da an sanar min ka halaka su. Ina son sanin wanene Ajmaal?. Ina son idasa tabbatar da masu fuska biyun daular ruman wa duniya koda ni bazan iya wanke kaina ga kowa ba”. Yanda yake kallonta kamar wata sabuwar halitta sai ka ɗauka idanun nasa sun kafe ne a kanta. A hankali ya ɗaga kafarsa yay ɗan taku ɗaya zuwa uku, a gabanta ya dakata gab-gab kamar zai haɗe jikinsu. Sai dai kuma baiyi hakan ba ya ɗan bar tazarar da bata wuce tsahon yatsa manuniya ba. Da sauri-sauri ƙirjinta ya hau dokawa ganin ya mata runfa, dan duk da kasancewar ta mai ɗan tsayi a gabansa ba komai bace duk da shima ba wani dogo bane na bala'i can, sai dai kuma dole a kira shi da dogon. Kamar yanda yake duban cikin idanunta haka itama ta ke dubansa, sai dai nata cike suke da ƙwalla ga tsumar da jikinta keyi ta kasa janyewa. Hannunsa ya dogare jikin lafiyayyar ƙofar mai tsananin ɗaukar ido, sai hakan ya sake bashi damar rufeta ruf har tana jin shaƙar numfashi ma na neman mata wahala tsabar yanda kwarjininsa ya cika mata ko'ina, har ji take kamar ma ɗakin ya musu kaɗanne. Rasa abin cewa ya sashi ɗaura yatsunsa biyu kan haɓarta ya ɗago fuskarta da ƙyau suna kallon juna, nasa ya sake lumshewa da sake buɗe wa a cikin natan cikin wani irin yanayi mai wahalar fassara ya furta. “Bayan kin cika waɗan nan sai me kuma?”. Yanda yay maganar yana mai sake sarƙe kaifafan idanun nasa cikin nata da ke tara ƙwallar da bata san dalili ba ya sata shiga jujjuya masa kanta a hankali idanunta na sake cikowa da ƙwalla dan jin kusancin nasu take kamar wani dabaibayi da ya fi ma zamanta a kurkuku. Lips ɗinta ta motsa a hankali, cikin raɗa-raɗa muryarta na ɗan rawa ta furta, “Yi maka hukunci akan laifukanka”. Da ƙyar ya iya haɗiye murmushin da ke ƙoƙarin yinƙuro masa. Sake matsar da fuskar tasa yay gab-gab da tata, hakan sai ya sake hauhawar bugun zuciyarta har yana iya jiyo yanda nunfashinta ke fita a sarƙe. Amma sai ya fuske abunsa ya cigaba da jujjuya nasa ƙwayoyin idon a nata cike da wani irin salon da ke neman fallasa sirrin da yake faman dannewa a ƙasan zuciyarsa. “Bayan hukuncin da kikai min na son kasheni duk bai isa ba *_Niazmina_*?”. Idanunta ta waro a matuƙar razane, tari mai ƙarfi ya sarƙeta, dan maganar tasa tazo mata a matuƙar bazata. Duk yanda yaso shanye dariyarsa a wannan karon hakan ya gagara har sai da lallausan murmushi ya suɓuce masa. Sai kawai ya jawota ya manna da jikinsa ya cigaba da yin abunsa dan ya kasa riƙewar.. (🥱Wato guy ɗin nan mugun ɗan latsi ne🚶🤭) ★Sosai take tarin har sai da ya janyeta suka koma bakin gado, shi dai murmushin sa kawai yake yana cigaba da shafa bayanta. Sai da ya ɗan lafa mata ya ɗauka tambulan ɗin ruwa da ke a side drawer ya tsiyaya kaɗan a ƙaramin cup. Ɗagota yay, batare da yayi magana ba ya ɗaura mata akan lips ɗinta. Da sauri ta shiga sha ƙwallar da ya cika idanunta da yay jajir na cigaba da sakkowa. Sai da ta shanye tas ya janye yana ƙara tsuke fuska kamar bashi ne ya gama murmushi ba yanzun. Ƙin yarda tai su haɗa ido, sai ma ta zame ta kwanta abunta ta juya masa baya. Shima komai bai sake ce mata ba yama miƙe. “Dan ALLAH kada kaje zasu cutar da kai, dan sun saka abu a ƙasan kujerar zamanka”. Shaƙaƙƙiyar muryarta da ke fita a dakushe saboda sarƙewar da tai ta sake ratsa dodon kunensa. Cak ya sake tsayawa tamkar wanda ake juyawa da remote, sai kuma ya ɗan waiwayo ya dubeta ganin abun nata serious ne. Tana a kwancen da take dai ta juyama ƙofar baya. Kallon kusan sakkani a shirin ya mata sai kuma ya juya ya cigaba da tafiyarsa batare da ya tanka ba. Idanu ta rumtse da ƙarfi jin ya fice a binsa. Ranta a dagule cikin kamar bori-bori ta shiga kaima gadon ƙananun duka da tittirza ƙafafunta tana fadin, “Ni dai na faɗa ma gaskiya ai, duk abinda ya sameka kai ka sani mi ma ya shafe ni”. (🥱Ato idan ya mutu bashi ya huta ba Iffah'r mu🤭🏃😜). ★Tsahon wasu mintuna bata iya ta tashi a kwancen da ya barta ba. Kokawa take da zuciyarta dake ingizata taje ta duba karfa ya fita ɗin. “In ma ya fita shi ya sani”. Ta faɗa a fili tana tura baki irin ko'a jikintan nam. Sai kuma can ƙasan zuciyarta ta ayyana mata (Idan ya mutu shikenan bazaki san gaskiyar rasa iyayenki da sanin waye Ajmaal ba fa kenan) zumbur ta miƙe kamar wadda aka tsikara, sauri-sauri ta fisgi mayafin abayarta ta yana a kai tana zira slippers. Ko sanda ta zauna a sashen bata san wannan ɗakin ba, amma ko gezau ta fito tana kalle-kalle. Da canki canka ta fito katafaren falon kamar wadda aka jeho. Da sauri Sayeed Fayzul-haq da ke zaune a ƙasa gefen ƙafafunsa da wasu tarkace marasa ƙyan gani ya ɗago, shiko hamshaƙin ko motsi bai yi ba idanunsa na kan waya da ke hanunsa. Ɓoyayyar ajiyar zuciya ta sauke da ɗan galla masa hararar ƙasan ido, sai dai kuma can ƙasan zuciyarta wani irin bugawa yake da sauri-sauri. Dan tabbas tarkacen gaban nasu irin abubuwan da ta gani ne a mafarkinta kamar yanda kayan da ya sanya sukai dai-dai da wanda ta gani sanye jikinsa a mafarkin. A ɗan daburce Sayeed Fayzul-haq ya sake maida kansa ya rissinar. Tunaninta ya katse cike da girmamawa ya ce, “ALLAH ya ƙarawa Zawjata-almilk lafiya da tsohon rai mai albarka. Barka da fitowa”. Jin al'amarin tai wani gin-girin-gin ganin dattijon da shi kansa Tajwar Eshaan ɗin zai girmesa nesa ma ba kusa ba amma yana gaisheta da wani sinne kai na tsantsar girmamawa. Kai ita kam wannan mulkin mallaka na masu mulki baya burgeta. Tajwar Eshaan ɗin da har yanzu bai nuna yasan da zuwanta wajen ba ta ɗan saci kallo, sai kuma ta ɗauke a kasalance ta buɗe baki tana gaishe da Sayeed Fayzul-haq. Bawon ALLAH duk sai ya rikice, duk da kasancewarsa shaƙiƙin a zuri'ar gidan ina shi ina Zawjata-almilk ta gaidashi. Komai bata sake cewa ba ta juya ta koma hanyar da ta fito. Da kallo ya bita ta ƙasan idon da tun ɗazun yake kallon nata dama. Harga ALLAH ta fara bashi tsoro. Dole yace tsoro, da farko ƙin ɗaukar abinda ta faɗa ɗin da muhimmanci yayi, amma sai zuciyarsa taƙi yarje masa hakan. Shine ya kira Sayeed Fayzul-haq akan a sallami shari'ar mutanen da ke jiransa sai nan da kwana biyu bisa wani uzirinsa. Cikin girmamawa Sayeed Fayzul-haq ɗin ke sanar masa ma ai ɗaya a ciki bai ƙara so ba har yanzu, dan sunama shirin tura dakaru nemosa ne kasancewar dama shine wanda ake ƙarar. A dakatar kawai ya bada umarni ya yanke wayar. Bayan tabbatar da fitar kowa Sayeed ya sake kira ya sanar masa. Shine ya bada umarnin a duba masa kujerar zaman nasa da tace an saka abu. Sai gashi kuwa a cikin abinda baifi mintuna ashirin ba Sayeed Fayzul-haq ɗin ya iso da tarkacen da aka samu ɗin, daka gani kuma kasan kayan surkulle ne.......✍️ _Tofa kowa sai yay takansa aljanancin Iffah da alama ya fara bayyana yau ɗin nan😂🏃🏃🏃🏃_ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (25) ........Kamar ko yaushe tana kishingiɗe amintacciyar hadimarta Jazaa na da ga gefenta tana yanka mata tupa. Magana take mata a hankali itako idanunta lumshe. Jazaa cikakkiyar ƴar leƙen asirinta ce a cikin gidan. Dan duk wani hadimi dake mata aiki Jazaa ya sani ba ita ba. Ita a karan kanta Jazaar ta ɗauka tsahon shekaru uku a sanda ta fara mata aiki bata isa faɗin ainahin wacece ita ba a cikin gidan. Dan takanzo mata ne da fuskoki daban-daban kafin ta bayyana mata ainahin fuskarta. Duk da kasancewar ta ba'a cikin hadiman gidan ba, kai ita bama a masarautar take ba UWA ce ta kawo mata ita ta razana a sanda ta san wacece itan. Amma har yau da suka kwashe tsahon shekaru tare bata taɓa iya ɗaga baki ta faɗama wani wacece ta-ƙurya ba, ta dai so gwada hakan sau ɗaya taci wahala dan daina ji da magana tayi baki ɗaya ta koma kurma. Sai da tai kusan shekara a haka sannan ji da maganarta ya dawo bayan tasha doguwar barazana. Duk wanda zai shaida makirci da tsantsar rashin imani irin na ta-ƙurya to lallai itace Jazaa. Kuma a hakan ma ba komai ta sani ba itama sai abinda taso ta sani kawai. “Bincike na ƙara nisa kan hadimi Israr Uwargijiya ta. Dan a yanzu haka ma naga baƙuwar fuska a cikin rukunin hadiman da Israr ke aiki. Inaji a jikina kuma ɗan leƙen asirine aka turo daga jami'an gidan nan”. Idanunta ta buɗe a hankali kan Jazaa. Kallo take mata mai kaifi da ya sakata sake gurfane gabanta kamar mai neman gafara. Cikin isa da kaushin harshe ta furta, “Ya jima yana mana aiki, kuma kowanne an samu nasara. Sai dai a gareni sabo da kaza bazai baya hanani yankata. Zan yanke masa hukuncin da ya dace da shi, dan dama na sanar masa in har aka samu matsala hukuncin zai zama dai-dai da irin na kowa. Bazan taɓa barin wani gaɓa da zai zame min matsala ba”. Yawu masu kauri Jazaa ta haɗiye. Zuciyarta sai bugu take da sauri-sauri. In dai har Israr bazai tsira da ga mummunan hukuncin uwargijiyar su ba kenan itama wataran idan tai kuskure zata iya fuskantar kowane irin hukunci. Ya ALLAH wannan wace irin rayuwace ta faɗo ciki mai ban tsoro. Wai shin mi matar nan take nema a duniya bayan wanda ALLAH ya azurtata da shi tari-tari da ita kanta bata san adadinsa ba?. Tsawar data ratsa kunenta ce ta sata zabura. Mikewa tai jikinta na rawa. “A gafarceni uwargijiyata”. Ta faɗa illahirin jikinta na tsuma. Sai kuma ta fice da sauri ta ɓarauniyar hanyar da ta ke shigowa da fita in har ganawa da uwargijiyar tata ya kama..... Ba ƙaramin tashin hankali wannan saƙo na Jazaa yazo mata da shi ba. Gaba ɗaya sai duk wani ɗan farin ciki data tashi da shi yau ta nemesa ta rasa. Tabbas dole ne hadimi Israr ya bar duniya a yau. Dan duk rintsi ita bata barin ƙurar da zata zame mata bi baya a bayanta koda kuwa ta wacece. Israr hadiminta ne na amana, ya matuƙar sanin abubuwa a kanta da in har aka kamashi duk da bai san ainahinta ba ayyukanta da yawa zasu kwaɓe. Wani irin lumshe idanu tai da mahaukacin zuƙar iska ta fesar, kafin tabar inda taken cikin sassarfa zuwa cikin bedroom ɗin ta, dan a yau dole ne tayi aikin nan da kanta. ★Duk yanda Jazaa taso haɗiye mummunan furucin Uwargijiyar tasu kan Israr ta kasa hakan, gaba ɗaya ta kasa samun nutsuwa. Ba yau ta saba jagorantar ai ma Uwargijiyar su aiki ba, idan aka samu kuskure kuma a sata da hanunnta ta shayar da mutum madarar mutuwa. Amma a wannan karon sai take ji bazata iya ba. Badan komai ba sai dan sanin irin bautar da Israr yay ga ta-ƙurya kamar yanda itama tayi koma take kanyi, duk haɗarin aiki aka sakashi sai ya zartar da shi koda zai cutu, dan kawai an samu akasi a wannan karon, akasin ma ba daga garesa bane tunda ya gudanar da umarnin data bashi sai a halakar da shi. Kai itakam zata samesa ta sanar da shi gaskiya (Ki kiyayi kanki) wata zuciya ta gargaɗe ta da sauri, tare da tuna mata wacece Ta-ƙurya idan ta manta... Ni dai nace, “Hummm” ★★... MALIKAT BUSHIRAT ★.... Kamar ko yaushe kishingiɗe take a katafaren falon nata da ya jiƙu matuƙa da nau'i-nau'in kayan more rayuwa. Yayinda hadimai uku ne ka ɗai ke tare da ita dan yau tace bata son hayaniya duk da dama basu isa yin hayaniyar ba gareta. A kallo ɗaya zaka iya fuskantar tana cikin damuwa, duk da ita ɗin ba wai mace bace mai fara'a tun fil azal. Ba komai ke mata kaikawo a rai ba sai tattaunawarsu ta ɗazun da Jasrah. Tabbas tana buƙatar yaronta ya ƙara aure, kodan ya samu nutsuwa irin ta kowane namiji irinsa. Sannan tana son yakice Iffah da ga jikinsa, dan tunda har ta iya gwada kashe mata yaro wataran zata iya cin nasara ai. Ba'a ƙaramin damuwa take da zaman yarinyar nan tare da shi ba gudun karta maimaita abinda ta fara, kallafa babu tsoro ko shakka tattare da ita take sanar da cewar ita ta bashi madarar ya sha, ta rasa gane wai Iffah mutum ce ko aljana. Ita kama bata taɓa cin karo da yarinya mai shekarunta da babu tsoro ko shakka tattare da ita ba. Taya ma zuciyarta zata iya nutsuwar barin Iffah tare da tilon ɗanta. Ita kam ta rasa ma wane irin kalar tunani ya kamata tayi. Gaskiya tana buƙatar zama da Malikat Haseenat a wannan karon, dan ita kam dai zuciyarta ta fara sakkowa da ga zafin da take ji nata. Tana buƙatar neman shawara ma akan abinda Jasrah tazo da shi, dan shi kansa Tajwar Eshaan ɗin bai ce komai ba akan batun ƙara auren da sukai masan ɗazun, harma Jasrah ta nuna jin haushin hakan duk da dai bata fito tace komai ba..... ★... MALIKAT HASEENAT ★... Tana zaune a keɓantaccen garden ɗinta tana tsakurar farfesun kayan ciki da ta saka hadima Banou tai mata saboda rashin daɗin baki da take fama da shi na mura da kwana biyu ke damunta ɗaya da ga cikin hadimanta tazo da saƙon neman iso da ga Malikat Bushirat. Ɗan jimmm tayi na mamaki, dan ko rabon da ko gaisheta Malikat Bushirat tazo yi a ƙalla ana neman wata kusan uku kenan, dan tun kafin faruwar rikicin da har yanzu ya gagara ƙarewa a masarautar ne. Murmushin ta ɗan saki mai sanyi da jinjina kanta cikin halin dattako. A ƙasaitance ta jinjinama hadimar kai alamar bada dama. Cikin abinda bai fi mintuna biyar ba sai ga Malikat Bushirat da Daneen Ammarah tare suna tunkaro ta. Kallo ɗaya ta musu ta ɗauke kanta, har ga ALLAH tana matuƙar ƙaunar Malikat Bushirat, tana mata so irin wanda takema ƴaƴan cikinta, bawai dan ta haifa mata jika bane, kawai dai yanda ta ɗauketa tamkar uwa yasa itama ta ke mata kallon ɗiya. Dan duk da kasancewar Malikat Ashwaq matsayin jininta Malikat Bushirat ta fiye mata ita sau dubu.... “Barka da hutawa Mamma”. Daneen Ammarah ta faɗa tana kaiwa zaune kusa da ita. Kai kawai malikat Haseenat ta jinjina mata, idanunta akan Malikat Bushirat da ta kasa zama ta kasa magana kanta a risine. Murmushi tayi mai ƙayatarwa ta kauda kanta batare da tace komai ba ta maida ga Hadima Banou dake tsaye da ga gefe kanta a rissine tana bin Malikat Bushirat da kallo, dan ita kaɗai tasan wane kalar abun daɗi take hangowa. “Bamu waje”. Ta faɗa a hankali cike da ƙasaitar ta. Da sauri hadima Banou ta amsata tana wucewar yawu taf da bakinta na kwaɗayi. Kwana biyu kenan tana neman mai ƙararren kwana bata dace ba, tayi alƙawarin sai ta maida asarar kwanakin da Iffah ta satayi na hanata laƙume kowa. Ganin Banou ta ɓace Malikat Haseenat ta maida kanta ga farfesunta batare data sake duban Daneen Ammarah da Malikat Bushirat ɗin ba. Hakan da tai na nufin tana fushi ɗin dai da gaske. Duk sai Malikat Bushirat kejin ta sake shiga ruɗani, duk da tasan Mammah ɗin dama zata iya yin fushin saboda mace ce da bata ɗaukar wargi, sai dai batai tsamanin kamar haka ba. A hankali ta kai zaune kan lallausan carpet ɗin da aka shimfiɗa saman korayen ciyayin wajen dake kwance luf-luf ko'a filin ƙwallon ƙafa albarka. Ƙafafunta ta tanƙwashe tana mai fuskantar ta da ƙyau, kanta a ƙasa ta riƙe kunnuwanta. “Nasan ni mai laifice ƙwarai da gaske Mammah, mai laifin data cancanci hukunci ga mahaifiya, amma ina mai neman afuwar bazan sake ba. Nima ku fahimceni ina kan gaskiya ta ne. Duk wata uwa irina zata yi abinda yafi wanda nayi a yayin da ta fahimci kota kama mai shirin halaka mata ɗa. Har yanzu inajin zafi, zafi matuƙa akan abinda ya faru, sai dai gani nazo gareki Mammah, dan ALLAH ki fahimtar dani abinda kike son na fahimta game da wannan al'amarin. Dan maybe ni nawa tunanin a wannan gaɓar ya tsuke ne waje ɗaya ta inda bana hangen komai sai laifin yarinyar nan kawai saboda ta taɓa abinda nafi so fiye da komai a wannan duniyar, Mammah wlhy zan iya fansar da numfashina akan Eshaan iya gaskiyata nake gaya miki”. Idanu kawai Malikat Haseenat ta zuba mata. Sai dai a cikin ranta tana ƙara jinjina kalaman ƙarshe na Malikat Bushirat ɗin. Eh tabbas itama tana son ƴaƴanta, sai dai ba makahon so ba irin wannan, a ganinta a duk lokacin da uwa zata iyama ɗanta irin wannan makahon son to bazata taɓa iya son wanin ɗanta ba kenan, bazata taɓa iya maida maraya nata ba, bazata taɓa iya dai-daita ƴaƴanta da wasu ƴaƴan masu kiranta da uwa ba kamar yanda ita a yanzu take kallonsu duk da matsayin matan ɗanta da suke. Amma sai kawai ta shanye batace komai ba tama cigaba da shan farfesunta. Daneen Ammarah da batace komai ba tun ɗazun ta ɗan ɗago tana kallon mahaifiyar tasu. Ta santa, ta san in tai fushi tana da wahalar tarowa, duk da kuma batace komai akam duk abinda Malikat Bushirat ɗin tayi a kwanakin nan ba ta san ranta ya ɓaci. murya ta sanyaya cike da lallashi ta ce, “Mammah kiyi haƙuri, insha ALLAH a yanzu mu masu biyayya ne ga dukkan umarninki. Ba zaki samemu a masu saɓawaba kuma”. Nan ma shiru kamar bazata ce komai ba, sai kuma ta ture bowl ɗin tana jan ajiyar zuciya, a nutse ta ja tissue ta goge bakinta kafin ta dubi Malikat Bushirat da kanta ke risine ita dai, dan a gaban uwa take nata mulkin dole ya zam mai risinawa........✍️ _(🥱gskiya itama tsohuwar nan akwai hegen mulki🏃)_ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (26) .........“Idan nace banji ciwo akan kuskurenki ba ƙarya zan miki. Amma tunda kin fahimta da kanki shike nan komai ya wuce. Akan abinda ya faru kuwa bazan hanaki jin zafi ba, dan kinyi abinda kowacce uwa zata iya yi har ni kai na. Sai dai kuma ni bazanyi haka kamar yanda ke ki kayi ɗin ba, saboda wasu dalilai nawa, wanda bai zama lallai ke a gareki su zama dalilan ba. Amma zan baku shawara matsayina na uwa. K shugaba ce, sannan kuma uwa. Shi shugaba an sanshi da haƙuri ne, kauda kai, jarumta, haɗiyewa komai ɗaci, shugaba kowa nashi ne, baya kuma taɓa kallon gudan jininsa kawai a matsayin ɗa sai ya haɗa da wanda ma bai haifa ba. Eh munji yarinyar tayi kuskure ƙwarai da gaske, kuskure kuma mafi girma da bai kamata ace an yafe mata cikin sauki ko sassauta mata ba. Sai dai a matsayinmu na wanda suka san ahalin da suke ciki ya kamata muyi wani nazari, sannan mu haɗiye dukkan zafin da muke ji koda ace yana ƙonamu. Domin ta hanyar wannan haɗiyewar ne kawai zamu iya sanin ainahin gaskiya. Ga duk mai hankali idan zai nutsu a shekarun yarinyar nan masu ƙaranci kai tsaye zai zamto aikin data aikata ba nata bane, anyi amfani da ita ne kawai domin samun cikar buri. Iffah yarinya ce da bata iya ɓoye abu, sannan akwai ƙuruciya a cikin al'amurran ta. Idan har ainahin mai wancan aiken zaiyi amfani da duk wannan yanayin nata, mu mezai hana bazamuyi amfani da fahimtar ta ba wajen gano koma wanene ta cikin sauƙi. Bushirat sam ban san lokacin da kika lalace haka ba, sai dai na fahimci a yanzu kina samun wasu ƴan kazagine da ke amfani da damuwarki wajen ingizaki. Bazance ki rabu da su ba, sai dai zan baki shawarar nutsuwar fahimtar manufofin su akan tunzurakin. Lokaci yayi da zaki farka, inba haka ba zakiyi nadama a gaɓar da nadamar bazata amfanar da ke komai ba face dana sani” Ba ƙaramin shiga jikinta kalaman Malikat Haseenat ɗin sukai ba. Sun ratsata matuƙa, ta kuma hankaltu da abinda take son nusasheta cikin hikima. Cike da girmamawa ta jinjina kanta, muryarta a raunane ta ce, “Nagode Mammah, nagode da kika farkar dani wannan nannauyan barcin da ya ɗaukeni. Kiyi haƙuri da duk abubuwan da suka faru, Insha ALLAHU kuma zaki sameni mai canjawa”. “ALLAH ya tabbatar da hakan”. Malikat Haseenat ta faɗa. A tare Daneen Ammarah da Malikat Bushirat suka amsa da Amin. Da haka wajen yay ɗan shiru, sai zuwa can kuma Malikat Bushirat ta sake nisawa. “Mammah sai kuma abu na biyu, duk da fadakarwarki ta farko ni dai ta janye min komai dake raina”. “Ki faɗi ko miye dan a yanzu mu duk wata hanyar mafita abin nemanmu ce”. Kai Malikat Bushirat ta jinjina, kafin ta cigaba da magana kanta a ƙasa. “Dama Jasrah ce ɗazun ta sameni akan batun......” tsaf ta zayyane mata komai a to z batare data rage ba. Hatta da zuwan Tajwar Eshaan ɗin na bazata da ƙin cewa komai da yay akan zancen. Ta ɗaura da faɗin, “Tun kafin tazo da wannan zancen ni dama inada burin hakan, sai dai bana nufin tirsasa masa. Amma dai yanzu ina son naji ta bakinki kema”. Wani ɗan murmushin manyance Malikat Haseenat tayi idanunta akan Malikat Bushirat ɗin. Sai kuma ta kauda kanta kamar bazatace komai ba. Kusan minti ɗaya sannan ta nisa da sake kallonta. “Hakan tunani ne mai ƙyau, sai dai ina son ku tuna abinda ya faru last ɗin nan. Mun sake rasa ɗaya a cikin matansa, ɗayar kuma saboda firgita ta tsinta kanta a halin ciwo da dole sai da muka maidata ga iyayenta. Yarinyar nan dai Iffah da aketa ɗauki ba daɗi a kanta itace ta gagara, gagarar tata kuma na mana ishara da tabbacin zarginmu, dan yarinyar tana zagaye da kariyar UBANGIJI ne, da kuma kwananta bai ƙare ba. Shiyyasa aketa bin wasu hanyoyi amma duk da haka ba'aci nasara ba. Idan munada wayo a wannan gaɓar hakan na nufin ita ɗin ba abinda zamu banzatar bace, Insha ALLAHU itace wadda ta dace da zama Zawjata-almilk da taɓata ga maƙiyanmu wani babban yaƙine da idan suka ce zasu ci gaba to kwanakinsun nan 99 da ake faɗa na ɓarawo na gab da cika”. A tare Daneen Ammarah da Malikat Bushirat suka kalleta, itako ta gyaɗa musu kai cike da tabbatarwa... ★... Kallon juna suma hadiman dake lafe cikin fulawoyin garden ɗin sukai dai-dai da na su Daneen Ammarah. Sai kuma suka miƙe cikin sanɗar da baza'a gansu ba zasu bar wajen. Daneen Ammarah ce ta ɗan shiga waige-waige, dan itakam ALLAH ya bata ƙarfin ji. Jin tabbas kamar fa motsin mutum ya sata miƙewa da ɗan hanzari, inda take jin motsin ta nufa. Da wani irin rawar jiki suka koma bayan wasu flowers masu duhu sosai suka lafe. Ganin babu alamar abinda take zargin ta baro wajen, sai dai zuciyarta na cigaba da tabbatar mata akwai wani bayansu a cikin garden ɗin. “Lafiya?”. Malikat Haseenat ta tambaya lokacin da Daneen Ammarah ke dawowa. Cikin nuna ƴar damuwa ta ce, “Wlhy Mammah kamar naji motsi ne. Sai dai kuma banga komai ba”. Magana Malikat Haseenat tai kamar zatayi, sai kuma ta haɗiye abunta. Sai ma duban Malikat Bushirat data miƙe tai da mata alamar ta zauna. Babu musu ta koma ta zauna badan taso ba. Dan itama dai zuciyarta na raya mata dole motsin da Daneen Ammarah ta ji ya kasance wani abu...... ★★.. ZAWJATA-ALMILK ★..... Harta nufi hanyar komawa ɗaki ta canja shawara, da baya ta dawo, hanyar da suka taɓa biyowa da shi randa ta samesa a can sama tare da Miran Arshaan ta nufa, haka kawai take son sake komawa wajen. Tana gab da isa ta ɗan tsaya a ƙofar da tun wancan karon taso sanin ita kuma ta miye, babu wani ko ɗar ta nufi ƙofar ta buɗe, sai taji ta buɗe babu gardama. Ƙaton Gym ne mai ɗauke da nau'i-nau'in machines na motsa jiki masu ƙayatarwa. “Uhyim” ta faɗa tana ɗan jinjina kanta da taɓe baki hannayenta duk biyu a ƙugu. Jitai har ma taji sha'awan motsa jikin, dan haka ta juya ta fita tana murmushi da faɗin, “Zan dawo gareku kuma”. Hadiman nan dai na wancan lokacin ta sake tararwa yau ma, cikin sauri duk suka zube suna gaisheta, yayinda na'ura ke yayata sunanta. Murmushi ta ɗan musu kawai ta wuce abinta, a ranta kam gulmar Tajwar Eshaan take dan tasan iyayinsa ne yasa aka saka wannan na'uran da in har zaka ƙetare ƙofan wajen sai ta sanar da ko kai waye ko kuma tsoro ne oho masa. “Ya rabba”. Ta faɗa a hankali tana mai lumshe idanu jin yanda iskar wajen ta wani buso mata. Sai kuma ta buɗe idanun ta kaisu ga sararin samaniya da ke ta faman haɗa giza-gizai alamar haɗuwar hadari. Da alama ruwa zai iya zubowa a koda yaushe insha ALLAHU. Iffah na matuƙar son yanayin damuna, dan koba komai tayi tsalle-tsallenta a ruwa ai. Cigaba da takawa tai murmushi na ƙara yalwatuwa a fuskarta har fararen haƙoranta na bayyana. Ƙyawawan idanunta na cigaba da bin wajen da kallo daki-daki cike da shauƙi. Inda ya tsaya ranar shi da Miran Arshaan ta ƙarasa, “Woow!!” ta faɗa tana wani irin ware idanunta ganin yanda take iya ganin masarautar baki ɗaya da ga wajen. Harma wajen masarautar ana hangowa da kaikawon motsoci dana mutane ɗai-ɗai. Ai bata taɓa tunanin haka wajen yake ba, da tuni ta maidashi wajen zamanta. Ɗan yayyafi aka fara a hankali, cike da nishaɗi ta rungume hannayenta tana sakin ƙayataccen murmushin dake sake bayyana ƙyawun da ALLAH ya azurtata da shi. Kamar da wasa ruwan ya fara ƙarfi, amma bata da alamar barin wajen kamar ma farin cikinta ƙaruwa yake, dan sam murmushi yaƙi barin face ɗinta, har ta kai ta fara ware hannayenta tana ɗan juyawa idanunta a lumshe tamkar mai hajijiya. Cak ta ɗauke wuta jin ta jingina da abu a yayin da take jujjuyawarta, sai kuma sassanyan ƙamshin turarensa ya shiga rige-rigen faɗawa hancinta. Sauri-sauri ta buɗe idanun tana juyowa, ganin shi ɗinne dai tsaye cikin sabuwar shiga yasa tayi kamar wadda ta ɗan firgita. Sai kuma ta haɗiye sauran murmushin fuskarta tana saukar da idanunta ƙasa saboda yanda ya tsareta da nasa idanun. “Baƙya tausayin kanki ko?”. Ya faɗa can ƙasan maƙoshi cikin sanyi sauti da ko ita ɗin ma dan suna gab da juna ne tajisa. Lips ɗinta ta ɗan shiga motsawa kamar zatai magana sai kuma ta kasa, ƙafafunta ta ɗaga da nufin barin wajen. Taku biyu ta tsaya cak tana mai rumtse idanunta jin ya riƙo hanunta. Kallon hannun nasa fari sol da ke riƙe da nata tai ta gefen ido, ga wasu dogayen farata farare tas-tas babu ɗigon datti tattare da su sai ma sheƙi da sukeyi, jitai tsigar jiki ta na wani irin tashi, a ɗan shagwaɓe ta ce, “Zanje ciki ne”. Maimakon ya saketa sai ya maidota a hankali ta dawo gabansa. Kallonta ya ke da ga sama har ƙasa, kallo irin na ƙurilla. Ji tai gaba ɗaya tana neman daburcewa, dan sam bata son kallo, balle ma irin nasa mai tada tsigar jiki. A hankali ya lumshe nasa yana ƙoƙarin danne murmushin da ke taso masa ya matsota ta koma jikinsa, babu yanda ta iya face lumshe nata idanun itama da ɗaura hannayenta kan ƙarfen wajen tai luf a jikin nasa tana shaƙar sassanyan ƙamshin sa da ita dai a rayuwarta shi kaɗai ta sani da shi. Nashi hannayen shima yasa a ƙarfen ya ɗaura kansa a kafaɗarta har lokacin idanunsa a lumshe yayyafin na sauka a kansu kaɗan-kaɗan, sai ya zam tana a tsakkiyarsa shi da ƙarfen..........✍️ 🥱🥱🤫😑🚶 *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (27) .......... “Kallo nada matuƙar ƙayatarwa da ga nan ba?”. Ya faɗa a hankali cikin kunenta. Sosai tsigar jikinta ta yamutsa, dan haka cikin matse idanunta da jikinta da ke jingine da nasa ta ce, “Uhhm” acan ƙasan maƙoshi itama. Murmushi ya sake saki da buɗe idanunsa, sai kuma a hankali ya ɗaura hannayensa kan nata da har yanzu ke'a kan ƙarfen. Itama buɗewar tai suka cigaba da kallon kaikawon mutane da mafi yawa suka kasance hadimai ne, sai daga can wajen masarautar kuma da kai kawon motoci yafi yawa. Yanda numfashinsa ke sauka a gefen wuyanta ba ƙaramin illata ta yake ba, tai dai jarumtar daurewa gudun kar aga gazawarta (Kun san dai mutuniyar tamu🥱😂). Jin ruwan na cigaba da sauka kansu dan ya ɗan fara ƙarfi ya sashi sauke sassanyar ajiyar zuciya da lumshe idanunsa ya sake buɗewa, sai kuma ya miƙe da ƙyau ya ja hanunta da ke cikin nasa har yanzun, kamar jira suna shiga ɗaya daga cikin rumfunan wajen ruwan ya kece mai ƙarfi. Hanunnta da take mutsu-mutsun cirewa a cikin nasa ya saki, cike da basarwa ya kai zaune a ɗaya daga kujerun cikin rumfar. Zama yay irin na ƙasaita, ga fuskar nan tamau a tsuke kamar bashi ba. Batare da ya sake kallon inda take tsaye ba ya danna wani ɗan maɓalli ta gefensa sai ga abu na sakkowa a gefe-gefen rumfar, ruf ya rufesu suka koma kamar cikin ɗaki, dan yana gama sauka har ƙasa sai ga haske da ya ƙarama wajen ƙyau da ɗaukar hankali.. Iffah bata ma san ta furta kalmar “Woow! Ya ALLAH”. Ba tsabar yanda abun yay matuƙar ƙayatar da ita. Sai kuma tai saurin ɗaura hanunnta kan baki tana ɗan satar kallon inda yake. Baima nuna yasan tanai ba, dan ya basar kamar ma bai san da zamanta wajen ba. Sai ma wani ƙara harɗe zamansa da yay yana lumshe idanunsa. Baki ta ɗan taɓe ta ɗauke kanta itama. Sosai ruwan ke sauka kamar ba ruwan farko ba, ga wani sanyi mai ratsa ɓargo duk da suna a rufe. Fara ƙudindine jiki Iffah tai tana ɗan yamutse fuska, sai dai duk da haka zuciyarta zungurarta take ta leƙa taga yanda ruwan ke zuba. Amma shakkar kasancewarsa a wajen ya hanata haka. “Sit”. Ya faɗa kamar ba daga bakinsa maganar ta fito ba. Da sauri ta buɗe idanunta da ke lumshe. Har yanzu yana a yanda yake. Kauda nata kan tai itama tana ɗan yamutse fuska. Sai kuma ta dubi kujerun, ji tai bazata iya musa masa ba, dan haka takai zaune tana ƙara ɗan matse jikinta dan sanyi takeji yana ratsata. Idanunsa ya ɗan buɗe a kanta sai kuma ya ɗauke. Cike da ƙasaita ya mike yana zare jacket ɗin jikinsa, ita dai kallonsa take ta ƙasan ido, jin ya zagaya bayanta ta maida kanta ta risinar. Sai kuma ta sake ɗagowa da sauri jin ya ɗora jacket ɗin a jikinta. Ajiyar zuciya ta sauke a hankali, tare da dafe rigar data ɗan zame ta ce, “Thanks”. Bai ce mata komai ba sai da ya koma ya zauna inda ya tashi sannan ya sake dubanta fuska babu alamar wasa ya tsareta da idanunsa masu kaifi, kasa jurewa tai tai ƙasa da nata tana bin ash color ɗin jacket ɗin nasa mai ƙyalli da ƙamahinta ya mamayeta da kallo. “Waya faɗa miki an saka abubuwan nan? Su waye suka saka kuma?”. Batai tunanin zai tuhumeta da sauri haka ba, dan haka ta ɗan ɗago ta dubesa. Idanunsa na kanta har yanzu, ga fuskar nan babu alamar yasan miye murmushi ma. Nata tai saurin maidawa ƙasa ta sake risinarwa dan kallon ya matuƙar ratsata. Kamar mai raɗa a hankali ta furta “A mafarki na gani”. Zaune ya tashi da ƙyau, Wani irin kallo yake mata tamkar idanunsa zasu faɗo. Jin kaifafan idanun nasa har yanzu a kanta ya sata saurin faɗin, “Da gaske a mafarki na gani, nima kuma banyi zaton abin zai tabbata ba, kawai dai zuciyata ce ta kasa nutsuwa akan lamarin. Dan duk sanda naita maimaita mafarki to daga baya sai abun kaga ya kasance a wasu lokutan”. (Ya arrahaman) ya faɗa a zuciyarsa dake faman bugawa da sauri-sauri. Kallo yake mata na kin ma rainamin hankali ko ke ba mutum bace halan, dan haka ya ƙara tsuke fuskar a zahiri. A ɗan kausashe ya furta “Who Are you Zawj? Miya kawoki gareni? Babu yanda za'ai wanda yay shirin kasheka ya dawo ya taimakeka kan yunƙurin wani mai ƙudiri irin nasa”. Yanzu kam ɗago idanunta tai ta ɗan kallesa dan tsabar shiga mamakin furucin nasa. Maidawa ta sake yi ta risinar tsigar jikinta na tashi saboda yanda kallon ya wani irin ratsata. Cikin wani irin sanyi da ɗan kaushi-kaushin muryar tunawa da ahalinta da suka tarwatse a dalilinsa bata san ya akai furucin ya fito ba ta ce, “FHAREEDAH BINT ZAYYAN!!”. Sai kuma tai shiru na wasu sakanni, kamar wadda aka tsikara ta ce, “Bani na kawo kaina gareka ba kai ne ka kawo kanka gareni Sultan. Mu huɗu iyayena suka haifa a duniya. “Hanash, Arfa, Fariha sai ni auta. A shekara ɗaya kafin yau gidanmu shine aljannarmu ta duniya, dan duk da muka kasance talakawa muna farin ciki irin wanda masu dukiya ba lallai sunayi ba. Cike muke da soyayyar juna, ƙauna, kulawa irin wadda ko tuntuɓe ɗayanmu yayi mu duka munajin ciwon a jikinmu ne. Duk wannan aljannar tamu ta sauya ne daga wani yammaci na ranar juma'a da bazamu taɓa mantawa ba. Ranar da zaran ƙaddara yay lilon da har Nina Arfa ta shiga a jerin ɗaya daga matanka.....” Hawayen da suka ciko mata ido suka sarƙeta ta kasa ƙara sawa. Wajen yay shiru sai saukar ajiyar zuciyarta a jajjere dana ruwan sama da ake ketawa tamkar ba ruwan farko ba, shikam yana zaune a harɗe baka isa iya tantance yanayinsa ba, a zahiri ma zakace idonsa a rufe suke, sai dai can ƙasa yake kallonta a wani irin yanayi da shi ya barma kansa sani. Hawayen da suka zubo mata ta share badan sun tsaya ba, ta cigaba da faɗin, “Komai ya rushe, komai ya canja, canjawar da har abada baya bazata dawo da shi ba. Na rasata, na rasa Fariha duk a dalilin aurenka, da ga ƙarshe na rasa Ummu da Babiy na rasa Hanash shima duk saboda kai fa. Komai ya ƙare, kamar ban taɓa mallakarsa ba, kamar ban taɓa zama mai ahali ba, kamar ma ban taɓa zama kowaba duk dai saboda kai fa. Inajin ciwo, ciwo matsananci mai ƙuna a kowane ɓargona da gunar jini na. Na kai gaɓar da bana baƙin ciki ko shakkar rasa numfashina nima a yanzu, dan abinda ya rage min kenan kuma bana jin yana da sauran amfani a gareni balle muhimmanci duk fa dai saboda kai. Nafi buƙatar na bisu nima, amma sai bayan na tabbatar da nunama duniya su waye su, wannan alwashi na ne duk da kasancewata mai rauni bazasu sha a banza ba sai dai mu rasa a tare ni da su duk da kasancewarsu a cikin ahali mafi girman daraja da kowa ke kallo a ƙasata....” nan ma kuka ya ƙara sarƙeta mai ƙarfi. A yanzun ma bai iya ko motsi ba binta kawai ya ke da kallo zuciyarsa na wani irin zallo da bai taɓa fuskanta da ga gareta ba. Zamewa tai daga saman kujerar da take zaune a hankali ta durƙusa gabansa, kanta a risine hannayenta a haɗe 🙏. “Ina roƙonka karka sakankance da ni, dan da gaske har yanzu zuciyata cike take da burin ɗaukar fansa. Ina kuma baka shawarar ka yanke min hukunci da gaggawa akan laifina kuma dai-dai da abinda na aikata, dan da gaske na shigo masarautar nan ne domin hukuntaka akan laifin da nake zargin kai kake aikata shi. Da shirin ɗaukar fansar jinin ƴan uwana na yarda da aurenka, da alƙawarin ɗan ɗana maka mutuwa kamar yanda na rasasu na shigo wannan masarautar. Kuma har yanzu ban gama tabbatar da babu hanunka a cikin ba. Ban kuma janye makamaina ba na son tabbatar da hakan. Sai dai ina rokonka kafin hukuncin ka sanar dani alaƙarka da Ajmaal dan ALLAH. Ka kuma janye kariyar da kake ƙoƙarin bani dan killaceni anan tamkar raunani ne. Burina fito-na-fito da su kamar yanda suka nuna min filin yaƙin na shirya. Na shirya tsaf da shirin bama kaina da kai kariya da ga duk wani sharrinsu koda daga baya kaima zan dawo na hukuntaka kamar yanda na shigo da ƙudirin yi duk da sun kasance jininka ne su ɗin”. Hannu ta sa ta share duk hawayenta tana sake miƙewa ta koma saman kujerar. “Kayi haƙuri da tsaurin idona haka nake. Koda ina so ko bana so haka zan cigaba da kasancewa domin hallayata ce wani yanayi bazai canja min ita ba, ita ɗin jinin jikina ce. Kallon cikin idonka na faɗa maka abinda yake gaskiyata bashi ke nufin baka da kima da daraja a idanuna ba. Kai ɗin shugabana ne, mai daraja da wata irin kimar da in wani mahaluki ya zageka a ƙetaran ƙasata ta ruman koda yafi ƙarfi na sai na daka tsalle wajen wanke fuskarsa da marin da sai na zubda haƙwaransa ƙasa a gaban duk wanda ya ke jin ya isar masa. Kayi a hankali Kanada maƙiya sosai kuma zagaye suke da kai tako ina, a cikinsu ma kuma har da ni nan da ke a gabanka yanzu Sultan. Duk ƙanƙantar maƙiyi kada kayi sakaci da shirinsa koda nice nan, dan allura ma da kake gani fa itama ƙarfece, idan har tsayawar numfashi a iya ƙirji baya nufin mutuwa kai tsaye to ka sani fa reza zata iya kisa irin na wuƙa har a gagara iya banbancewa jikin son a tabbatar. Dan haka kamar yanda na roƙeƙa kar sawayenka su wuce sashenka a yau, dan ALLAH kar kaje. Ina maka wannan roƙon ne a matsayin *_MATARKA_* ba shugaba da talakarsa ba, ba kuma ƙin fitar taka zai kareka da ga ƙaddarar ka bane ko hanasu cin nasara a kanka”........✍️ *_Shahan-shan da gaske fa kayi takanka dan da alama aljanar gaskiya aka aura maka batare da ka farga ba🙆, to nidai ba ruwana kuzo broza ɗinku na cikin haɗari ƴan DAUƊAR GORA.... CONVERSETION 🏃🏃🤔._* _Ga alakoro nan na raya gori😎😎_ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (28) ........Cak numfashinsa ya tsaya da ga kaikawon da yake a ƙirjinsa. Kalmar *_a matsayin MATARKA_* ɗin nan tafi kowacce matuƙar ratsasa har tsakkiyar kai fiye da komai data faɗa, duk da suma sauran kalaman nasa nada wani muhimmanci da nasu tasirin. Amma a zahiri bai ko motsa ba, yana dai kallonta ne a ƙasan ido kamar ya samu wani television. Shiru na tsawon wasu sakanni kamar masu sauraren saukar ruwan saman, sai kuma ya ɗago kaifafan idanunsa dai-dai da ɗago nata itama, cikin kallon ido cikin ido da wata sarƙaƙaƙƙiyar muryar da fitarta bai canja taushin ainahin muryarsa mai sanyi da nutsuwa ba ya furta, “Mi kika sani game da ni? A bayan burin da kika shigo da shi masarauta ta?”. Kamar bazata motsa ba sai kuma ta motsa lips ɗin ta a hankali. Daurewa tai bata nuna ko gezau ba, itama ta zuba nata idanun da yanayinsu ke wani irin canja kala-kala maisa tsigar jikinsa tashi cikin nasa da ƙyau. Tai ɗan murmushi mai sanyi da ya nema ɗauke fitar numfashinsa a baɗininsa, janyewa tai gefe kaɗan fuskarta har lokacin da murmushin, “Sanin wani abu game da kai abu ne mai wahalar gaske ga baƙon zaman wannan gidan. Sai dai kai da kanka ya kamata ka duƙufa sanin komai a kanka, idan kuma ka sani ka ke shanyewa ka tuna kai shugaba ne. Haƙƙoƙin biliyoyin mutane ne a ƙarƙashinka, idan ka tauye ɗaya da gangan sai ALLAH ya tambayeka koda da ƙwayar zarra ne, inaji a raina kai ba mutum bane irin mutanen da tunaninsu ke a takure waje guda, in har bakai kake aikata laifin da mafiya al'ummar ƙasar nan ke kallonka da shi ba na tabbata kasan masu aikata wasu a ciki koda kaɗan ne, dan inba haka ba banga dalilin da zaisa su dinga farautar rayuwarka ba irin haka a matsayinsu na makusantanka”. (Ya arrahaman) ya faɗa a zuciyarsa. Karo na farko ana faɗa masa gaskiyar da kowa ke shakkar tunkararsa a kanta hatta da wanda suke sama da shi a shekaru. Amma gashi yarinya ƙaramar da a haihuwar kaji ya haifeta yau tana jaddada masa shi ɗin wanene. Tsarge masa komai take a yanda ya jima yana buƙatar ji daga bakin wani koda mahaifiyarsa ne. Magana mafi dukan zuciyarsa itace ta ƙarshe. Ana farautar rayuwarsa kuma makusantansa. Yes ya jima da sanin wasu a makusantan sa na bibiyar rayuwarsa, kuma mahaifinsa ya fargar da shi hakan tun yana raye, amma a yau sai yaji kalmar daga bakinta ta sake girma matuƙa garesa. Kallonta yake cikin ido a wani irin yanayin da ke neman sarƙe fitar numfashinsa. Muryarsa a wani irin sanyaye ya furta, “Sune suka baki guba ki bani?”. Shiru kamar bazatace komai ba, sai kuma ta ɗago ta ɗan kallesa. (To Miya rage kuma? Ai bataga amfanin cigaba da ɓoye masa ba) dan haka kai tsaye kawai ta jinjina masa kanta. “Ni nasan baka buƙatar sai na maimaita komai, domin ban ɓoye komai a zamana gidan nan ga Ajmaal ba, hatta randa nake neman dafin macizai ido rufe na sanar masa, shiyyasa har yanzu zuciyata taƙi daina mamakin miyasa kasha madarar tunda har kaga saƙon kuma...” Wani murmushi ne ya nema suɓuce masa a hankali, sai dai bai yarda ya bayyana akan fuskarsa ba ya hadiye kayansa yana mai lumshe idanunsa da launinsu ya canja baki ɗaya. Kamar bazai tanka ba sai kuma ya sake buɗe idanunsa ya sauke a kanta cikin wani irin kasalallen kallo da ya tilastata rissinar da nata. “A ranar banga saƙonki ba dan bana cikin ƙasar nan”. Ɗagowa tai da sauri ta dubesa. Idanunta a ware cikin rawar harshe ta ce, “Kamar ya baka cikin ƙasar nan? Bayan matarka an mata kisan gilla a tsakanin, hakama tsohon da kowa ke tabbatar da jayayyar da yay da kai ce tasa ka ɓaddashi. Kana nufin kuma da gaske kai ne Ajmaal ɗin dai?”. Idanunsa ya lumshe ya buɗe a hankali, sai kuma ya miƙe a nutse zuwa gabanta, binsa take ita dai da idanunta da ke a waje gaba ɗaya kamar zasu faɗo har ya kai zaune a kujerar kusa da ita. Zamansa ya maida kafa ɗaya kan ɗaya idanun nan nasa masu kaifi shanye a kanta. Itama ta kasa daina kallonsa, dan gaba ɗaya kamar a rikice ma take. “Duk matar da aka kawo Masarautar nan da sunan tawa ni ke kaɗai na taɓa gani da idanuna, babu wacce ta taɓa rasa ranta ina a cikin masarautar nan kuma. Zaki san Ajmaal kamar yanda kike buƙata domin ina son muyi aiki tare”. Ya ɗan yi murmushin da ya nema ɗauke duka numfashinta batare da ya jira amasawarta ba ya cigaba, “Ki ɗauka anan tare kike da Ajmaal ba Shahan-shan Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed ba. Mi kike son sani?”. Da ƙyar ta iya haɗiye yawu da rawar jikinta, dan itakam kallon komai take kamar a mafarki. Hasalima ya ƙara birkitar mata da kai ne. Cikin rawar murya kamar mai in ina ta ce, “Cafa kai baka taɓa ganin fuskar su ba, suna mutuwa kuma baka cikin masarauta? Taya hankali zai ɗauki wannan maganar?”. “Ta yanda ya ɗauki zaman Tajwar Eshaan tare da ke anan babu wani shamaki mai shari'a”. Ya faɗa a hankali kamar ba daga shi kalaman suka fito ba. Yawu ta haɗiye da ƙyar tana ɗan tura baki jin ya kirata mai shari'a, sam zuciyarta tama ƙi yarda da wancan zancen nasa, “Ya akai ka zama abokin Sir Fawzan?”. Ta faɗa a hankali tamkar mai tsoron wani ya jita. Shiru babu alamar zai amsa mata idonsa na kallon ƙasa, dan dauriya kawai yake da surutun nan, da alama ita kuma kamar ma yanzu ya fara mata daɗi. Ya ɗan ja numfashi ya fesar a hankali, “A baɗini Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed abokin kowa ne a ƙasar ruman da sunan Ajmaal, dan haka shima Fawzan ya shigo ne kamar yanda kowa ke shigowa, a taƙaice dai na haɗu da shi ne a ƙasar Cuba, lokaci ina wani couse, abinda ya fara haɗamu so bawai sai an maimaita faɗarsa bane, kawai dai sanda nasan shi ɗan ƙasata ne naji farin ciki, na kuma nuna masa cewa nima asalina ɗan canne...” Yanda yake maganar da ɗaɗɗaya kuma kamar da ƙyar sai taji ya bata tausayi da dariya, ta daɗe da fahimtar magana abune mai wahalar gaske a gareshi. Kamar ko yasan mi take tunanin, sai gani tai ya miƙa mata waya yana ɗan murza goshinsa da ke sarawa. “Mu cigaba a rubuce kaina yana ciwo”. Dariya abun ya bata, tai murmushi idonta a kan wayar da yake miƙo matan. Kamar bazata amsa ba sai kuma ta amsa a zuciyarta tana faɗin (Miskilanci ma ai cuta ce gaskiya), a zahiri kam sai ta ɗan taɓe baki tana rubuta, “Miyasa randa na haɗu da kai a Eira garden ban ganku tare ba?, bayan kuma shi ya kirani ne dan na haɗu da Ajmaal?” ta mika masa wayar. Rubutun kawai ya tsirama ido harta fara ƙosawa, dan bashi da alamar zai bata amsa. Sai da ya gama shan ƙamshinsa sannan ya amsa a rubucen shima. “Dama banyi niyyar mu haɗun ba, dan ina son na fara sanin waye ke”. Sosai ta waro idanu tana kallonsa lokacin da ta gama karantawa. Bama ta san bakinta ya suɓuce wajen faɗin, “Saboda mi to?”. Shiru yay kawai ya tsira mata idanu, sai kuma ya ɗago a hankali ya zare wayar daga cikin hanunta. “Saboda yamun bayanin manufarki da kai tsaye ni ta shafa batare da shima ya san hakan ba” ta karanta. Sake kallonsa tai mamaki na bayyana a fuskarta. Nan ɗin ma bakinta ne ya suɓuce wajen faɗin, “Anya mutumin nan bada saka hanunka aka kawoni gidan nan ba?”. Wani irin lumshe idanu yay cike da salo ya sake buɗewa a kanta, sai kuma ya saki wani makirin murmushi yana kauda kansa. “Ka amsa min Please”. Ta faɗa tana matsowa karshen kujeran da ya maida zaman nasu gab har ƙafanta na gogan nashi. Nan ma babu alamar zai tanka matan tsahon wasu sakkani, kafin ya fiskanceta da kyau kaifafan idanunsa a kanta. “Idan na matso da makashina kusa da ni sai ya zama laifi?”. Zumbur ta miƙa tafukan hannayenta duk biyu akan fuskarta ta furta, “Ya arrahaman ka kasheni, wlhy ka gama dani. Na shiga uku ni Fhareedah wace irin MAKAUNIYAR ƘADDARA ce kuma wannan ɗin?”. Yanda take kaikawo da sambatun jikinta na rawa kaɗan ya rage ya kwashe da dariya. Amma ya danne da ƙyar, sai dai duk da haka sai da ya kauda kansa gefe yana murmushi. A mamakinsa sai yaji kawai ta fita a wajen da ɗan gudu-gudu. Sosai ya zaro idanunsa, sai kuma kawai ya saki murmushi mai faɗin da har haƙoransa na bayyana a bazata. Murmushin yake shi kaɗai yana faman kare baki idanunsa akan hanyar da tabi..... ★★..... ★.... A yanda hadiman leƙen asirin nata suka shigo yasa ta bama duk sauran hadiman dake zagaye da ita umarnin barinta. Jikkunansu har rawa suke suka fice, a yanda ta zuba musu ido yasa bama su tsaya wani jan jeni ba suka shiga sanar mata komai dan sun san bata buƙatar jan zance da tsaho. “ALLAH ya ƙara miki lafiya mai amfani uwargida shugabar matan wannan daula. A yau Malikat Bushirat ta baƙunci Uwar masu gida. A yanzu haka ma suna a garden ɗin ta tare har da Daneen...” Wani irin kallo take watsa musu da kai tsaye suka fahimci manufarta. Sake gurfana sukai a gabanta cike da girmamawa. “Kamar yanda ki ka fi buƙata mun kasance da su a wajen muma, duk da kaɗan ya rage Daneen ta ganemu”. Fuska ta yatsine alamar ba wannan take son ji ba. Fahimtar hakan ya sakasu cigaba da faɗin, “Sun tattauna abubuwa da yawa, sai dai gaba ɗaya a dunƙule sun ta'allaƙa ne a neman afuwar Uwar masu gida da Malikat tayi. Ta faɗi maganganu masu yawa itama na nuna fushi, sai dai da ga karshe ta sakko harta yafe mata abubuwan da suka farun da dorawa da bata shawara game da al'amarin Zawjata-almilk. Da ga ƙarshen zancen sun kuma dai ya ƙare akan son ƙarin auren Shugaban wannan daula....” A karan farko Malikat Ashwaq ta miƙe zaune sosai tana kallonsu. “Sai me ya faru?”. Ta faɗa kamar idanun nata zasu faɗo a kansu. “Babu alamar dai Uwar masu gida ta bada goyon baya, daga hakanne kuma Daneen ta fahimci motsin mu a wajen iyakar abinda muka ji kenan”. Hannu kawai ta ɗaga musu alamar suje. Suna ficewa itama ta miƙe, da ƴar sassarfa ta bar falon hutawar tata zuwa ɗakin barcinta mafi zama sirri gareta har kafafunta na neman harɗewa........✍️ _Tofa, Malikat Ashwaq yaya dai🥱🏃_ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (29) .........Bayan kamar mintuna ashirin da tafiyar Iffah sannan shima ya mike, zuwa lokacin ruwan ya tsagaita sai ɗan yaf-yaf da akeyi ga garin ya ɗauki wani irin sanyi mai ratsa ɓargon jiki. A hankali ya lumshe idanunsa ya buɗe a kan sararin samaniya da tai wani irin fayau, ga garin yay luf-luf ƙamshin ƙasa na ratsa hancinan mutane. A kan lips ya shiga furta addu'ar nan ta bayan saukar ruwan sama. *مُطِرْنَا بِفَضْلِ اللهِ وَرَحْمَتِهِ.* _Mutirna bifadlil-lahi warahmatih._ (An yi mana ruwa saboda falalar ALLAH da Rahamarsa). Kafin ya cigaba da tafiya cikin takun nan nasa na ƙasaita da izza tamkar mai irga steps.... ★★..... Tunda ta dawo ɗakin kaikawo kawai take faman yi hankali a tashe. Duk nacin son sanin wanene Ajmaal ɗin da takeyi bata kawo a ranta zai zama shi ɗin ne ba. Tunaninta kawai ya kama Ajmaal ɗin ne kodai wani abu da ba shi take zato ba yana mata yawo da hankali ne. Ji take komai ya kwance mata, komai ya ƙare mata. Ta sadaƙar dan tata ta riga ta ƙare kawai. Yaya akai hakan ta kasance, yanzu komai daya wakana tsakaninta da Ajmaal da Shahan-shan ɗin ne kenan? Kai ina impossible, taya hakan zai kasance ma? Miyasa sir Fawzan zai mata hakane? Miyasa? Miyasa ya rabbi shike nan ita kam. Yanda take yi dolene ya baka tausayi da dariya. Ƙululu taji cikinta ya murɗa kamar mai jin gudawa. Ta kai hannu ta matse cikin ƙirjinta kamar zai tarwatse dan tashin hankali da tsabar ruɗanin da take ciki..... “Nace na gama da ke ne?”. A wani irin haukace ta ɗago ta kalla ƙofar jin sassanyar muryarsa bazata a cikin kunneta, shi ɗinne dai tsaye hannayensa duka cikin aljihun wandon jikinsa. Sam bataji shigowarsa ba, koda yake a buɗe tabar ƙofar tsabar ruɗani. Tafiya ta farayi da baya-baya, jin zata ma iya sakin gudawar a wajen sai kawai ta sake kwasa da gudu tai hanyar toilet. Ta ɗauki tsawon mintunan da zuciyarta ke faɗa mata ƙilama ya gaji ya fita, sai dai wani sashe na gargaɗinta. Jin an fara kiran sallar azhar ta sauke ajiyar zuciya, ta san dai tabbas dolene ya fita ai yanzu. Alwala tayi, kai tsaye ta fito tana ayyanama ranta ta saka ma ƙofar key kawai. Da sauri taja birki ganinsa zaune a harɗe cikin zaman ƙasaitar nan tasa a saman kujerar ɗakin, sai kuma ta juya da sauri zata koma dan yayi wani ɗam-ɗam da fuska. “Zaki sha mamaki idan kika koma”. Kamar zata fasa ihu ta dubesa, sai kuma ta ɗauke kanta ƙwalla na cika idonta. (Shikenan Iffah kekam sai abinda ALLAH yayi, gaki dama ba uwa ba uba miya rage kuma? Kawai yasa a tsireki) a zuciyarta take sambatun tana cigaba da takowa sum-suma batare data yarda ta sake kallonsa ba. Miƙewa yay shima fuskar nan babu alamar fara'a, idonsa a kanta. A gabanta ya tsaya mayen ƙamshin turarensa na cigaba da addabarta, ga mamakin yanda yake abubuwa kamar ba Shahan-shan ɗin nan nasu da suke hange da ga nesa ba mai shegen isa da izza na ƙara bata mamaki da ɗaukar komai tamkar wani mafarki. Jinsa a kusa da ita sai kawai ta rumtse idanunta da ƙarfi tana jiran abinda zai biyo baya. “Na tafi?”. Ya faɗa a hankali yana wani shanye idanunsa ƙasa-ƙasa a kanta. Da wani irin sauri ta buɗe idanunta da ɗagowa ta kallesa tana sakin nannauyar ajiyar zuciya saboda shock da furicin nasa ya sakata. Sai kuma ta kaudar da kan gefe dan salon kallon nan nasa birkita ta yake. Muryarta can ƙasa-ƙasa ta jinjina masa kai. “Magana nake so”. Ya faɗa a fisge kamar wanda akaima tilas. Tsabar yanda take jin kusancin nasu kamar zata shiɗe a hankali ta ce, “Uhhm”. Ɗan sake matsawa yay gareta dab har tana iya jin saukar numfashinsa a kan fuskarta. Jin saukar yatsunsa kan haɓarta ruf ta rufe idanunta da ƙoƙarin riƙe rawar da jikinta ke neman farayi. Ya ɗan lumshe idanunsa dake yawo akan fuskar tata yana ƙoƙarin shanye murmushin dake taso masa. A bazata kawai taji saukar lallausan lips ɗinsa saman goshinta ya manna mata sumba mai lafiya da har sai da ta saki wata ajiyar zuciya mai ƙarfi. Batare da ya sake cewa komai ba ya ja da baya ya juya ya bar ɗakin fuskarsa shimfiɗe da murmushin da duk sonshi da basar da shi hakan ya gagara. A ransa rayawa yake (Damisar takarda ga tsoro ga ban tsoro) Da kallo ta bishi har ya fice, ta sauke ajiyar zuciya da kaiwa zaune jagwab kamar wadda tasha gudu ta gaji, sai faman matse jikinta take waje guda amma yaƙi daina tsumar dole ta kai kwance na wani ɗan lokaci, badan taji ƙarfi ba dai ta miƙe tai sallar ganin lokaci zai shige.... Duk yanda yaso dai-daita kansa hakan ya gagara. Tabbas ya yarda SO wani abune mai matuƙar kaifi. Duk yanda kaso ɓoyeshi da ƙin son bayyanashi hakan gagara yake. Duk matsayinka, duk girman shekarunka, sai ya kaika ƙasa. Shi shaida ne akan hakan, tunda gashi yana gani akan kansa. Gaba ɗaya idan yana a gaban mitsitsiyar yarinyar nan manta shi ɗin wanene ya ke da matsayinsa. Ya rasa wannan abu haka mai kama da kamar wata almara. A gurguje ya canja shiga da ɗaura alwala ya fita masallaci. Ya wani tsume kamar bashi ba, dan a Shahan-shan ɗin sa ya fita mai tsananin ƙasaita da izzar nan ga miskilancin tsiya. Bayan idar da salla bai shigo ba ya zarce fada, umarnin isar da saƙon tattaro masa wasu a cikin manyan masarautar ya bada. Cikin ƙanƙanin lokaci duk wanda sunansa ya fito a zaman saƙo ya riskesa. Kafin cikar wasu mintuna duk sun hallara. Duk da kasancewar yana a cikin fadar a wani matsakaicin falonsa yake zaune ba cikin ainahin fada inda karagar mulki take ba. Da ga shi sai amintaccen hadiminsa na amana da ako ina ka gansa shima zaka ganshi, idan ka cire ɗakin barcinsa kawai. Suma ɗin yana shiga kai abinda ake buƙata da kuma gyarawa. A zahiri zaka ɗauka hankalinsa kan television ɗin da ke aiki a falon suke, dan manyan kaifafan idanunsa na kanta ne. A gabansa ƙyaƙyƙyawar butar shayi ce irin ta hamshaƙan sarakai kalar golden mai tsananin ɗaukar idon mai kallo. Dan har wasu irin fararen stones aka jera jikinta da ya sake ƙayatar da ita. Sai dai hankalin nasa sam ba'a nan ɗin yake ba. Gaba ɗaya a tunanin zantukan Iffah ne na ɗazu. Dan shauƙin da yake ciki bawai ya mantar da shi bane ba. Ya dai tattarasu ne ya ajiye gefe domin basu nasu lokaci. Sallama Sayeed Fayzul-haq ta saka amintaccen Ghazi ɗinsa da ke gefensa tsaye ko gajiya bayayi amsawa. Sai kuma ya nufi ƙofar domin duba wanene. Shi dai bai motsa a yanda yake ba, kai kace ma bai san abinda ake ba. Minti ɗaya da wasu sakanni amintaccen nasa ya dawo, a gabansa ya zube murya cike da tsantsar girmamawa yace, “Kariyar UBANGIJI ta cigaba da kasancewa zagaye da adalin shugabanmu. Sayeed Fayzul-haq ne ke isar da saƙon kammalawar kasancewar kowa”. Shiru babu alamar zai tanka har kusan mintuna biyu, sai ka rantse baima jisa ba. Sai da ya mula dan kansa ya motsa lips da ƙyar. “Zasu iya shigowa”. “Umarninka shine abin jiran kowa”. Hadimin ya faɗa yana rissinar da kai sannan ya miƙe da sauri. Cikin abinda bai fi minti uku ba dattijai masu cikakkiyar kamala da nutsuwa suka dinga shigowa ɗaya bayan ɗaya a nutse. Duk wanda ya shigo sai ya miƙa gaisuwa kafin ya wuce ya zauna. Sayeed Fayzul-haq ne ƙarshe hannunsa ɗauke da ledar da aka zuba kayan surkullen nan. A gaban Tajwar Eshaan ɗin ya kai ya ajiye yana ɗan matsar da ƙyaƙyƙywar butar shayin nan kaɗan. Leda ɗin ya buɗe sannan ya ja da baya shima ya zauna. Yanzun ma sharewa yay tsahon wasu mintuna kamar bashine yasa a tarasu ba, kowa kuwa a cikinsu ya zubama ledar ido musamman Miran Arshaan da jikinsa har tsuma yake, sai dai yana ta faman taushe kansa. Tajwar Eshaan da ke nazartar kowa ta ƙasan ido ya motsa lips ɗinsa da ƙyar yana mai buɗe idanunsa masu saka mara gaskiya tsuma tar-tar a kansu da ƙyau. “Bana bukatar sanin wanda ya ajiye su balle dalilin ajiye sun. Sai dai zan gargaɗi mai ajiyewar da abu uku. Eshaan a koda yaushe yana zagaye ne a cikin kariyar UBANGIJINSA insha ALLAHU. A komai na ina amfani da zuciya ne fiye da ƙwanji na da ƙwaƙwalwa. A kuma duk sanda maƙiyi ya sokeni ta baya sunansa matsoraci a wajena, jarumi gaba-da-gaba yake zuwa filin daga in har ya cika sunansa jarumi. Saboda haka, idan har ya shirya na bashi tabbaci ɗan Haysam bin Abdul-majeed Aliy Qutb a shirye yake shima”. A take falon gaba ɗaya ya ɗauka kalmar neman afuwa da fatan hucewar zuciya ga Shahan-shan. A baɗini kam baka jin komai sai bugun zuciyoyi, yayinda ake ma juna ƴar kallon kallo, dan ba ƙaramin ratsasu kausasan kalaman Tajwar Eshaan ɗin suke ba, duk da a zahiri shi ya yisu ne cikin sanyin nan nasa mai amon nutsuwa da cikakkiyar ƙasaitar tabbatar da shi ɗin wanene. Ƙananun maganganu ne suka nema fara tashi kowa na ƙoƙarin son ganin ya kare kansa. Yi yay kamar bama jinsu ya ke ba, sai da Sayeed Fayzul-haq ya fargar da su sannan falon yay tsitt. Wani ɗan ƙyamusashen tsoho da suke kira Sayeed Tasadduq-Husain da fuskarsa ke nuna alamun ɓacin rai ya dubesu cikin ɗacin murya, a karo na farko da tun shigowarsa falon yay magana. Shima ɗin kamar Uncle ya ke a wajen Tajwar Eshaan, mutum ne mai tsananin tsage gaskiya a duk yanda tazo shiyyasa bai cika farin jini a wajen su ba, alokuta da dama idan yaga an dabaibaye rayuwar Tajwar Eshaan da yawa yakan nuna ɓacin ransa har ya faffaɗi maganganu masu ɗaci, to a yau ɗin ma tin ganin waɗan nan kayan sirkullen ɗazun ya nuna takaicinsa, hasalima shine ya ingiza Sayeed Fayzul-haq kan Tajwar Eshaan ya tarasu ayi maganar kar a wani rufe, gara wanda ya ajiye abubuwan ya san an san ya ajiye ɗin.........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (30) ..........“Ƙoƙarin kare kai bashi zai fidda kowanne mu ba, duk da bazai yiwu ace dukanmu anan ne muka aikata ɗin ba, sai dai dole duk ma wanda ya aikata a cikinmun yake dai. Shin wace irin rayuwa ce muke son ta cigaba da yaɗuwa a wannan zuri'ar tamu ne bayan kasancewar mu jini ɗaya?. Shin mi muke nema wanda UBANGIJI baiyi mana shi ba? Mi muke buƙata da ga siffofin shugaba na gari da ALLAH bai azurta bawan ALLAHn nan da shi ba da a kullum muke son nuna bore da hukuncin ALLAH? Ni na rasa gane mi duk mai ƙoƙarin assasa fitine-finen nan ke buƙata ba ko san zuwa. Shin mulkin yake so ne? Ko kuwa rayuwar wannan bawan ALLAH da'a kullum alkairinsa ke zagaye da mu..” takaici ya saka hawaye ziraro masa. Handkherciff yasa ya share tare da sake dubansu ya cigaba da faɗin, “Shike nan babu mai hana koma waye yin yanda ya ke so, sai dai ya sani a duk randa yazo hanunmu wlhy ko shi waye a cikinmu sai yayi dana sani da nadamar kasancewarsa cikin zuri'ar mu. Sannan tarihi zai masa tanadin da bazai taɓa goge sunansa ba a matsayin azzalumi mai fuska biyu a cikin zuri'ar mu. Wannan faɗan ba nashi bane namu ne, dan mu nan da mu akeyi ba da shi ba, dan haka duk wanda ya shirya bismillah muma mun shirya”. A zahirance duk nuna goyon baya a kan maganarsa sukai, sai dai a ransu ji suke kamar su shaƙo wuyan Sayeed Tasadduq-Husain ɗin. Yasan da hakan, shiyyasa ko kallo babu wanda ya ishesa a cikinsu, ya kuma ci dubu sai ceto. Miran Arshaan da gaba ɗaya ya ke jin kamar ya danne Sayeed Tasadduq-Husain a wajen ya masa yankan rago ya taushi zuciyarsa da ƙyar, dan wannan wata dama ce a garesa, rashin ganin Miran Jasim a wajen yay masa da ɗi, dan haka ya miƙe cike da dakewa da tsan-tsar iya makirci shima ya fuskancesu ya zuba kausasan kalamai, da ga ƙarshe ya rufe da faɗin, “In ma tsoro da kunya sun hana duk ma wanda ya aikata ɗin zuwa nan batare da mun farga ba to na tabbata akwai mabiyansa da irinsa anan ɗin, sai su isar da saƙonmu na tabbatar da duk randa mutum yazo hanunmu sai ya yabama aya zaƙinta a wannan masarauta kamar yanda Sayeed Tasadduq-Husain ya faɗa”. Kalamansa kam tabbas sun saka wasu fara hasaso abinda yake son dama ai hasashen, sai dai babu wanda ya furta a zahirance aka cigaba da tattaunawa. Ya ɗauka tsahon lokaci da su a falon suna tattaunawar, dan suna fitowa da ga zaman ma masallaci suka zarce sallar la'asar. Bayan an idar ya koma sashensa. Bai nema Iffah ba yanzun kam. Dan yana buƙatar ɗan hutawa saboda yau zai ɗanyi fitar dare ta sirri zuwa cikin gari. Sai dai koda ya shiga ɗakin ma sai yaji baida buƙatar kwanciyar saboda ransa a matuƙar ɓace ya ke har yanzun. Tashi yay ya canja kayansa cikin wasu fararen wando da riga tas na kamfanin *Nike* da sukai masa matuƙar ƙyau duk da ya sane badan kwalliya ba. Takalma ya ɗaura a ƙafarsa baƙaƙe ya ɗauka p-cap a hannu ya fito cikin takun nan nasa mai tabbatar da shi ɗinne dai ko da ga nesa. Cikin sauri amintaccensa ya miƙe ƙansa rissine, ba sai yace masa ga abinda yake buƙata ba, kai tsaye ya fahimci inda suka dosa. Kafin ya ƙaraso gareshi yay saurin ɗaga waya yay kiran sarkin barga. Ana ɗagawa yay saurin bashi umarnin shirya dokin amana da kowa ya san in ba shi ba Shahan-shan ɗin baya hawan kowanne doki a gidan. Wayar ya katse dan dai-dai da isowar Tajwar Eshaan ɗin, ganin ya nufi elevator batare da ko kallon inda yake yayi ba shima ya zabura. Cikin sauri ya danna floor 1 bayan ƙofar ta maida kanta ta zuge. Suna fitowa da ga lift ɗin ɓoyayyar hanyar da zata fiddasu batare da ko hadiman ƙasan sungansu ba ya nufa, amintaccensa biye da shi. A wani ƙaton fili suka fito, an gyara wajen da wani irin farin yashi mai matuƙar ɗaukar idon mai kallo da birgewa. Kasancewar ruwan saman da aka sha sai wajen ya sake bada wani yanayi mai matuƙar daɗi ga sassanyar iskar da bishiyoyin da aka ƙawata wajen na dabino na bayarwa. Da ga ɗan nesa da su Sarkin barga ke riƙe da ƙyaƙyƙyawan farin dokin da shi da kansa ya raɗa ma abinsa suna da ƙyautar ALLAH. Kamar yanda ɗabi'ar dokin take suna fitowa yay wata irin haniniya da girgiza kai kace ƙamshin Tajwar Eshaan ɗin yake ji ya shaida kasancewar sa a waje. Da wani irin gudun bajinta ya nufosu, yana isowa gabansa yay wata irin ƙwafutar ƙasa yay girgiza da haniniya, har gashin saman kansa zuwa wuya na wani tarwatsewa da haɗe kansa waje guda. A hankali Tajwar Eshaan ya lumshe idanunsa yana sakin sassanyan murmushi da mutane kan jima basu gani tare da shi ba sannan ya kai hannu ya shafi fuskar dokin yana masa magana ƙasa-ƙasa da ko Sarkin barga da amintaccen hadiminsa dake tsaye gefe kawuna a risine basa iya jinsa. Cikin wani irin salon da ke tabbatar da ƙwarewarsa a iya sarrafa dokin ya damƙi linzamin sa cikin action mai matuƙar ɗaukar hankali da bajinta ya ɗane saman sa. Cikin tabbatar da ƙwarewar da dokin ya samu a hanunsa yay wata irin haniniya da ƙwafutar ƙasa ya ɗiba hanya tamkar a filin polo. Rere suka fara ɗan gaske da sauran dokunan huɗu da aka sakakarma linzami batare da kowa a kansu ba. Duk wanda ya ga yanda yake sarrafa dokin basai an faɗaba ya san shi ɗin ƙwarren ɗan wasan polo ne kuma jarumin gaske. Dan cikin ƙanƙanin lokaci yay ma sauran dokunan da babu kowa ɗin fintinkau, har ya sake dawowa ya koma sannan su suka iso. Kaida gani kasan yana nishaɗi da wasan matuƙa. Sosai su sarkin barga ke murmushi da jinjina jarumta irin ta gwarzon Sarkin nasu. Ko'a cikin dubu shi ɗin na dabanne da kai tsaye za'a nuna a shaida. Dan suna da tabbacin da a lokacin yaƙi ne yazo babu abinda zai hana ya zama babban jarumin da tararsa a filin daga abin tsoro ne. Ya ɗauka tsahon lokaci yana wasan dokin har sai da yaji ya gamsu jininsa ya tashi fiye ma da yanda yake buƙata sannan yaja linzamin dokin ya dire bisa ƙasa cike da bajinta yana sauke numfashi ɗaya-ɗaya. Da sauri amintaccensa ya matsa garesa hannunsa ɗauke da ƙyaƙyƙyawan tray mai ɗauke da gorar ruwa da glass cup. Goran ruwan ya ɗauka batare da ya haɗa da cup ɗin ba, ya ɓalle murfin ya kai bakinsa. Yasha kusan fin rabi sannan ya juyo ya juye sauran akan fuskar dokin nasa yana ɗan murmushi. Haniniya dokin yayi mai nuni da isharar jin daɗin kasancewarsa da adalin ubangidan nasa. Shima sai ya kai hannu ya share masa ruwan yana murmushi. Ƙaramin towel Sarkin barga ya miƙo masa da sauri, bai musaba ya amsa ya goge hannunsa da wuyansa sannan ya kai shi ga fuskar dokin shima ya share masa ruwan da ƙyau. Yanda yake ma dokin da kansa dolene ka tabbatar akwai matuƙar shaƙuwa a tsakaninsu mai birgewa da ƙayatarwa. (Ko dabba ma ta san me bata kulawa da nuna ƙauna kenan☺️😘) ★★...... ★.... ★... Karo na biyu kenan da ta sake dawowa ɗakin ta samesa yana kai kawo rai a ɓace. So take taji miye damuwarsa, sai dai tana matuƙar shakkar hakan. Dan mijin nasu wani irin bahagon mutum ne da sam baida daɗin zama. Su dake tare da shine kuma kawai suka san hakan. Amma ga al'ummar masarautar kowa yabonsa yake, shiyyasa a lokuta da yawa idan suka kai ƙararsa ga Shahan-shan tun ma zamanin Tajwar Haysam sai kiga ana ganin laifinsu na gajen haƙuri da rashin godiyar UBANGIJI. Hayaƙin Shishar da ya bulbule ɗakin da shi ta ɗan saka hannu ta kore, dan shi kansa ma da ƙyar take iya hangosa. Ƙundunbalar shiga tayi dan so take ta sanar masa kiran da aka aiko ana masa da ga Shahan-shan, amma tsoro takeji ganin yanayin da yake ciki. Muryarta na ɗan rawa ta risina da ga tsakkiyar ɗakin tana shaƙar hayaƙin madadin iska da ƙyar. “Barka da wannan lokaci Abu Husam”. Cak ya tsaya da ga zuƙar Shishar, yay wani masifar bulbulo hayaƙin bakinsa da ya sake turniƙe ɗakin zuciyarsa na wani irin kumburowa da takaicin wace ƴar ƙunar baƙin waken ce a matan nasa data manta da dokarsa. Sai da hayaƙin ya lafa sannan ya iya ganinta da ƙyau, e ai ya sani sai ita ɗin, dan babu mai yawan shiga masa hanci kamarta. Tsawa ya daka mata yana miƙewa a fusace. “Buhaysah! Ban ce bana buƙatar ganin wani a sashe na ba da ga nan har sai idan nine na nema mutum?!!”. A ɗan firgice ta zabura baya, sai kuma ta shiga girgiza masa kai jikinta na ƙyarma. “Hakane, amma Ka gafarce ni Abu Husam, wlhy bada son raina na karya maka doka ba. Saƙone da ga Shahan-shan ana buƙatar ganinka. Naga kada kai laifi ne shiyyas....” “Tasss!!” Kakejin saukar wani lafiyayyen mari akan ƙyaƙyƙyawar fuskar ta. Dan mace ce zankaɗeɗiyar gaske dirarriya. Duk da shekaru sunja gareta ƙyawunta a bayyane yake gata ƴar gayu. Ba yau ta saba shan mari a wajensa ba, amma sai na yau ɗin yay mata ciwo fiye da ko yaushe. A hankali ta ɗaga jajayen idanunta ta kallesa, fuskarta na nuna alamar ɓacin rai, abune kuma da bai taɓa gani da ga gareta ba. “Abu Husam minene laifina anan da har na cancanci mari dan ALLAH?”.. “Ƙari kike buƙata kenan?”. Ya faɗa a zafafe da sake yunƙurowa zai sauke mata wani duk da jin wani shakkarta a yau ɗin da yaji ta shigesa.. Abin mamaki da firgici ga Miran Jasim, sai ga Buhaysah kam ta riƙe hannunsa caraf.........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (31) ..........Abune da bai taɓa faruwa ba a tsakaninsu, a tsahon shekarun da suka kwashe tare na aure talatin da ɗaya cif. Cikin ido take dubansa da wani irin kallo mai gigita zuciya “Jasim tsahon shekaru talatin da ɗaya kenan nake zaune a ƙarƙashin mulkin mallakarka. Nayi juriyar nayi kawaicin amma na fahimci kai ɗin gafalalle ne da baya gane komai a rayuwarsa sai son zuciyarsa. A da dai na haƙurce maka na shanye, amma a yanzu zan tabbatar maka dai-dai nake da kai asararre kawai da ya girma bai san ya girma ba!”. Ta yarfar da hannunsa gefe da wulla masa wani irin mugun kallo ta juya zata fice. Wata irin zabura yay da ga sumar wucin gadin mamakinta daya riskesa, ya wani shaƙo wuyan rigarta ta baya ya fizgita jikinsa na rawa. Kiyyyyy rigar ta shiga kecewa, hakan yasata yin gaba. Tsabar shi cikakken mugune yasa ƙafa ya taɗeta. Mummunar buguwar da ta sakata ƙwalla wahalalliyar ƙara tai a ƙasan wajen. Cikin rufewar idanu yasa ƙafar ya taka mata gadon baya sai ga ƙashi na bada sauti. A guje suka dinga rige-rigen shigowa dan ƙarar tata ta matuƙar ratsa kunnuwansu. Basu kaɗai ba hatta da hadiman dake musu hidima a sashen babu wanda zai ce baiji ƙarar baiwar ALLAHr nan ba. Ganinsu baisa ya dakata da dukanta ba. Cikin wata iriyar fusata babban ɗansa da itace mahaifiyarsa Husam yay wani irin kukan kura ya hankaɗashi baya sai da ya daki bango. Baiyi wata-wata ba kuma ya damƙi wuyan rigarsa ya shaƙeshi dan shima yaron tsageran kanshi ne. Kaf halin Miran Jasim ɗin ya kwaso, sai dai duk da haka yana bala'i bala'in son mahaifinsa. Ya jima da ciwon dukanta da mahaifinsa keyi duk da bata taɓa fitowa fili ta sanar masa ba. Tun yana yaro ko shatin yatsu ya gani a fuskarta ya tabbaya sai tace bakomai ko bigewa tayi. Sai bayan ya girama ne ya fahimci mahaifinsa ne ke marinta kamar yanda suma sauran matansa biyu ba tsira sukai ba. Rawa jikin sauran matan nasa ya shigayi, sun rasa ma wa zasu bama ɗauki, shi da Husam ya shaƙe ko Buhaysah da ke kwance tana madoɗowar azaba. Gwara kansa da bango da Husam yayi yana ƙaraji ya sa matan yin kansa da sauri suna kuka da roƙon Husam ɗin ya sakesa. Amma ina yaron nan ƙara gwara kan Miran Jasim yake yana kai masa naushi kamar ba mahaifinsa ba. Ga wani irin ƙarajin ɓacin rai yanayi mai haɗe da kuka. Sukam al'amarin nan yafi ƙarfinsu, hankali tashe suka shiga neman number Miran Arshaan amma ba'a daga ba. Har kira uku babu alamar za'a amsa dole suka maida akalar kiran ga Daneen Ammarah domin ta sanar da Mammah da Sayeed Fayzul-haq kasancewar sun san yana ɗan jin shakkarsu, dan daga Malikat Haseenat ɗin har Sayeed Fayzul-haq ɗin basa ɗaukar raini ko wasa a garesu dama masarautar kowa yasan haka. Wayar ta riski Sayeed ne lokacin da yake fitowa daga sashen Tajwar Eshaan bayan masa rakkiya daga sallar la'asar da suka idar. Itama Daneen Ammarah lokacin tana ƙoƙarin tashi da ga abin salla. Hankali tashe duk suka nufi sashen Miran Jasim ɗin har da Malikat Haseenat ɗin da aka saka a mota, dai-dai da shima Miran Arshaan ya nufi can dan shima yayi mamakin rashin ganinsa wajen tattaunawar da akayi duk da yasan dai ransa a ɓace yake matuƙa. Dan tun jin Tajwar Eshaan bai fito fada ba da safe ransu ke'a jagule. Yanzu kuma a wannan zaman ashe ma akansu ne akayisa duk da dai shi Tajwar Eshaan ɗin bai fito fili ya ambaci suna ba, amma duk da wannan sanin da yay akan Miran Jasim ɗin ya zaɓi yimasa zamba cikin aminci dan a ganinsa lokaci yayi da shima zai dakata da ga rakkiyar Miran Jasim ɗin ya fara yaƙin kansa... Da ƙayar aka ɓanɓare Husam da ga shaƙar da yay ma Miran Jasim, yaraf ya zube ƙasa hannunsa kan maƙoshinsa yana kakari. Idanunsa sunyi ruƙu-ruƙu tsabar yanda yaji shaƙar nan, ga kansa daya fashe saboda ƙuma masan daya dinga yi sai jini yake yi. A gefe ga Buhaysah da ke kukan wahala Husam ya je ya rungumeta yana kuka da alama dai yaji mata ciwo a baya koma ya karya ta ne oho. Malikat Haseenat da ta ɗan girgiza kanta da duban Sayeed. A matuƙar ruɗe Sayeed Fayzul-haq ya jinjina mata kai. Waya ya ciro yay kiran clinic ya bada umarnin a kawo ambulance ƙofar sashen Miran Jasim ɗin..... A gaggauce aka miƙa Miran Jasim da Buhaysah asibiti. Husam kuma Malikat Haseenat tasa Daneen Ammarah su wuce da shi sashenta, yaron sai kuka yake mai matuƙar cin rai da zai baka tausayi, dan duk wanda ya kalla mahaifiyarsa yasan akwai babbar matsala a bayan nan nata da mahaifinsa ya taka Jigum-jigum sauran matansa da yara suka zauna. Kowa ka gani cikin damuwa. Dan wannan abun kunya ne da in har ya fita koda a cikin masarautar ne bazasu taɓa jin daɗi ba. Mijinsu mugu ne, dan ba yau ya fara kai hannunsa kansu ba, sai dai in ka cire Tajwar Haysam da Malikat Haseenat da mahaifiyarsa Ameera Banafsha kafin ta mutu babu wanda yasan hakan. Ko ƴayansu Husam ɗinne kawai ya sani sai mai bi masa Faida data zama babbar budurwa, inda ma ALLAH ya bata miji da tuni tai aure. Koda yake ba mijin ta rasa ba, taƙi sauraren samarin ne saboda mutuwar son Tajwar Eshaan da takeyi tun dawowarsa ƙasar ruman. Hatta da mutuwar matansa bai taɓa saka Faida jin zata iya daina son sa ba. Randa ya bayyana fuskarsa ba ƙaramin hauka tayi ba, duk da kuwa itama ɗin ƙyaƙyƙyawa ce sosai, sai dai shi kuma baima san tanayi ba.. Abinda suke gudun dai kam sai da ya faru, dan tuni hadiman sashen nasu suka fara zare jiki kai gulma ga iyayen gidansu. Dan wannan al'adace ta masarautar. Mafi yawan hadiman kowane sashe zaka samesu ƴan leƙen asirin ɓangarori daban-daban ne, duk da iyayen gidansu kanji a ransu akwai ƴan leƙen asirin bazasu iya banbance su ko fitowa suce ga su ba balle su fiddasu a masu hidimar tasu. Hakan yasa dole kowa ya haƙura da kasancewa cikin taka tsantsan kawai. Fitar wannan magana kuma sai tai dai-dai da wadda ta fara yawo na sakama Tajwar Eshaan kayan tsafi a kujerar zamansa da maganar Miran Arshaan da kai tsaye aka fara fassarata da cewar da Miran Jasim ɗin yake. ga kuma abinda ya aikata yanzu na sake tabbatar da maganar Miran Arshaan ɗin akwai ƙamshin gaskiya kenan..... ★★.... ★.... Iffah kam da bata san mike faruwa ba rabonta da ganin Tajwar Eshaan tunda ya bar sashen ɗazun da azhar. Duk da dai itama barcinta ta sha bayan idar da sallar azhar ɗin. A makare ma tai sallar la'asar. Kaɗan ta tsakuri abincin da aka kawo mata har ɗaki. Sanin babu mai hawowa floor ɗin na ƙarshe sai shi da amintaccensa yasa ta ɗauka wayar da ya faɗa da card ɗin data gani ta fito katafaren falon da wani irin ƙamshi mai masifar daɗi ke tashi. Shiru babu kowa hatta da television a kashe suke, dan girman falon yasa kusan tv uku ne. Itama kallon bawani ya ɗaɗarata da ƙasa bane, barta dai da son bibiyar labarai saboda yanda take matuƙar ƙaunar aikin jarida. Shine burinta, kuma Insha ALLAHU sai ta cika shi in har ta cigaba da numfashi a doron duniya. Cikin ɗaya daga lafiyayyun kujerun ta shige tana mai bin haɗaɗɗen falon da kallo kamar yau ne ta fara shigarsa. Komai na ciki ka kalla kasan an narka dukiya mai ban mamaki, ya fita tsaf kamar ba'a duniyar mutane ake ba (😂to dama irin wanga falo kam ai sai duniyar novel🤣 lols). Baki ta ɗan taɓe tana ƙunƙunin da ita ta barma kanta sani, daga haka takai kwance ta fara sarrafa wayar domin yin online shopping ɗin da ya umarce ta, dan bata son takurama Mamy kunyarta ta ke ji, akan abin nan daya faru tana jin nauyin haɗuwa da mutane biyu, Malikat Haseenat da Daneen Ammarah, saboda yanda ta shayar da jininsu guba amma su goyon baya da son bata kariya ne burinsu, wannan al'amari na bata mamaki da ƙara sakata a kunyar gudun haduwa da su. Wasu kayan motsa jiki ne kalar pink sukai matuƙar fara ɗaukar hankalinta, ta shiga sakin murmushi tana yaba kayan a zuciyarta. Sai dai kuma ganin kuɗin da aka rubuta na sayensu ya sata zaro idanu waje. Sai kuma ta ɗan taɓe baki da ɗage kafaɗa tana ƙunƙuni wai ai dai kuɗin ma nasu ne su talakawan RUMAN, garama ta ci musu. Da wannan shawarar zuciyar tata ta dinga jidar kaya masu ƙyau da tsada tana ƴar dariyar muguntar yau sai tama asusun nasa wawason taron dangi zai gane ita Iffah bata wasan yara bace. (Ni dai nace hummmm 😂) Ganin magrib ta gabato ga ɗan sanyi-sanyi na ratsata ya tadata a falon ta koma ɗaki. Shigewarta babu jimawa ya shigo shi kuma da ga wajen hawan doki. Ɗan waige-waige ya shigayi a falon saboda jin ƙamshin turarenta. Ganin dai babu alamar mutum ma ya sashi fesar da numfashi cike da basarwa ya nufi ciki. Bai jima ba sosai ya sake fitowa cikin shirin tafiya masallaci. A kallo ɗaya da zakai mai zaka fahimci wanka kawai yayi ya fito. Sake ficewa yay gabatar da sallar magrib..... ★★..... Kamar yanda labarin abinda ke faruwa yaje kunnen kowa a masarautar haka itama ya isa nata kunnen. Dai-dai amintacciyar hadimarta na sanar mata Jasrah ta shigo a rikice. Malikat Bushirat da gaba ɗaya hankalinta yay masifar tashi jin wai an samu kayan sihiri a karagar mulkin Shahan-shan tabi Jasrah da ke shigowa itama a masifar tashin hankalin da kallo. Tsawa Jasrah ta dakama Hadimar, cikin rawar jiki ta tashi ta fice. Kafin ma hadimar ta gama ficewa ta fara magana a masifar tashin hankali hawaye na zubo mata. “Akia akwai matsala wlhy, ni dai wannan masifa ta isheni, kar mutanen nan suyi galabar halaka mana Eshaan. Kiga fa da ga wannan musiba sai wannan, ni wlhy gara ya sauka ya bar musu mulkin nan da dai mu rasa shi, dan ALLAH ki kirashi muji a wane hali yake, zuciyata ta kasa nutsuwa duk da Abu Harith ya sanar min bai zauna ba”. Cikin sake shiga tashin hankali Malikat Bushirat da ke sauke numfashi da ɗaɗɗaya idanunta a lumshe ta girgiza kanta, sai kuma ta buɗe idanun nata da ke jajur. Ita duk wannan surutun bashi take buƙata ba, yaronta take son gani, so take ta gansa da idanunta ta tabbatar da lafiyarsa ƙalau sannan koma miye da ke a ranta sai ta fitar. Dan wlhy a wannan gaɓar taci matuƙar alwashin in har wani abu ya sami ɗanta kamar wancan karon du da bai bar duniya ba azabar daya ɗan ɗana fansarta shine ran kowane shege. Duk kuma wanda yay yunƙurin shiga mata hanci koda Malikat Haseenat ce zata fyato ta. Ta shirya tsaf a wannan karon koda za'a babbakama DAULAR RUMAN gaba ɗaya wuta sai ta ƙwatoma ɗanta hakkinsa ga duk wani mai hannu a kan abinda ya faru bama Iffah kawai ba.........✍️ _Tofa ran manya ya kai ƙololuwa a ɓaci🧐._ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (32) .........Fitowarta kenan a wanka tana ƙoƙarin shirin barci dan sanyi-sanyin da garin ya ɗauka yasa tuni masarautar tai wani irin yin tsitt, duk da bawani dare ne yay ba. A bazata wayar landline ɗin ɗakin ta fara bada sautin dake nuna alamar kira ya shigo. Kamar wata mai son rarrabe gaskiyar hakan ko akasinta ta tsaya tana kallon wayar harta yanke. Wani kiranne ya sake shigowa. Da ƙyar ta iya saita kanta ta kai hannu ta ɗauka tare da kaiwa kunne tai shiru. Daga can ma shiru akai babu alamar za'a tanka har na wasu sakkani da suka kusa haɗa minti ɗaya. Cikin ɗan yanayin ƙufula-kufula da ƙosawa tace, “ALLAH zan yanke dan inada abinyi”. Ba'a tanka ɗin ba, sai dai kuma taji kamar alamar an ɗan motsa da ga can. bata fahimci motsin na miye ba, sai taji ta ƙara hawa sama. “Na kashe ne?”. Ta sake faɗa a ƙufule. (Fitinanniya komai masifa) ya faɗa a zuciyarsa yana ɗan sakin wani murmushin da shi da babu duk ɗaya, dan sai ma mai tsananin saka ido ne zai tabbatar da yayi. “Ki sameni a room 2. Idan kika ɓatamin lokaci kuma hummm...” Ya faɗa a can ƙasan maƙoshi batare da ya ƙarasa ba dai-dai tana shirin katse kiran. “Ya arrahaman Iffah kin kaɗe”. Ta faɗa a fili cikin waro ido tana sauke wayar da tunanin ya yanke. Sai dai sarai ya jita. Safa da marwa ta shiga yi kamar wata wadda ke'a cikin tashin hankalin rayuwa. Ita gaba ɗaya ma ta rasa mima take ji akan al'amurin ta na yanzu da bawan ALLAHn nan. Tsoro ne ko miye?. Itace fa Iffah ɗin nan maijin zata iya tunkarar kowa akan gaskiyarta. Mai ikirarin tabbatar da ɗaukar fansar ƴan uwanta kansa. Mai jin zata fuskancesa fuska da fuska batare da taji zata iya masa ragi a duk abinda ta shiryo masa ba. Sai gashi tun ba'aje ko'ina ba lissafinta ya rikice. Abubuwa suna neman canja kansu a canjin data kasa fahimta. Gargaɗinsa na ƙarshen umarni ya fara maimaita kansa cikin kunenta. Birki taja da ga kaikawon, fahimtar halinsa data farayi na in har ya faɗa sai ya cika ya sata saurin neman kaya ta saka a gurguje. Abaya ce mai matuƙar ƙyau red and black data haska farar fatarta sosai. Ita kanta bata san kiyasa sai da ta zaɓo ba kafin tasa duk da kayan barci tai niyyar sakawa da farkoa. Ga wani uban ƙamshin turarrukan sa data baza tare da wanda aka kawo mata cikin kayan online shopping ɗinta da tun ɗazun suka iso, kayan sunfa yi ƙyau babu na kushewa, amma kuma fa an ciri uban kuɗi da har sai da ta razana daga baya. Dan hakama yanzu duk takeji ta rikice da tunanin koma kuɗin data kashe masa ne zai mata faɗa a kai, ita wlhy bata san da gaske kuɗin kayan da suka rubuta a jikin kowanne zasu iya cirewan ba fa. Taku take a hankali kamar mai sanɗa ko wata budurwar hawainiya, babu abinda zuciyarta keyi sai dukan tamanin-tamanin. Idan yace ta biyasa kudinsa itako batama san yaya zatayi ba. Da ƙyar ta gano room two ɗin duk da bedrooms ɗin biyar ne kawai take tunani a wajen. Sauran ƙofofin bazata iya tabbatar dana minene ba tunda ba kowacce karambaninta ya taɓa kaita taɓawa ba bayan ta Gym a ɗazun. Taja wasu mintuna uku masu ƙyau a ƙofar kafin tai ƙundun balar ɗaura hanunnta a handle ɗin ta murɗa. Da sallama ciki-ciki ta shigo ɗakin da babu wani haske sosai, sai wani uban ƙamshi mai ratsa kwanya da uban sanyin ac kamar ba sanyi ake a garin ba. Hannunta na dama ta ɗan kai kan kafaɗarta ta haggu tana shafawa alamar sanyin ya ratsata. Can ta hangosa cikin ƙyaƙyƙyawar kujerar da ke gefe guda biyu, yana sanye cikin kayan barci farare tas da sukai masa ƙyau sosai, yanda hannun rigar ya kamashi sai ya fiddo murɗaɗɗen damtsensa da a kallo ɗaya zaka san yana samun isasshen motsa jiki. Lap-top ce a gabansa yana sarrafawa cike da ƙwarewa, sai butar shayi mai ƙyau da ƙaramin kofin da ke tabbatar da sha yake yi. Duk da motsin buɗe ƙofar tata da uban ƙamshin turarensa data bulbula ya zo hancinsa bai ko motsa ba balle ya nuna alamar yasan da zuwanta, aikinsa yake hankali kwance. Idanunta data zuba masa ta janye, a karo na farko ta fara jin tana son sanin wai mi yake yi a laptop da a koda yaushe zaka gansa yana sarrafawa. Ko waya takan daɗe bata ganta a hannunsa ba. Amma computer in har yana zaune to baka rabashi da ita. Ganin har tazo gaf da inda yake bai nuna alamar yaji shigowarta ba tai tunanin ko bai jitan bane. Sallamar ta sake maimaitawa ƙasa-ƙasa. Idanu ya ɗan lumshe kaɗan ya sake buɗewa saboda yanda sassanyar muryarta ta wani ratsashi. Da ƙyar ya iya danne abinda ke taso masa ya buɗe idanun akan lap-top ɗin ya cigaba da aikinsa batare da ya motsa ɗin ba dai. Haushi ne ya kama Iffah a karo na farko, ta san dai in har baiji sallamar farko ba babu yanda za'ai ace baiji ta yanzu ba. Idanunta ta juya kamar zata ɓalla masa harara dan takaici, amma bazata iya ba, sai kuma tai tunanin koma ta juya ta koma, nan ma tasan ko giyar kokino ta sha bazata iya hakan ba dai. Tsaiwar ta cigaba da yi batare data sake motsawa ba itama, sai bin ɗakin dai take da kallo. Duka bedroom ɗin data taɓa shiga a sashen nasa tasan sun haɗu matuƙa, sai dai fa wannan ɗin na musamman ne gaskiya. Dan kamar ma duk yafi waɗancan girma. Ƙatone na gaske, bayan katafaren gadon da zai iya cinye mutane goma tsaf akwai wadrobe na glass kamar yanda gadon ma take ganin kamar glass ɗinne. Hakama mirror da duk sauran tarkacen furnitures ɗin sun haɗu. Sai wasu rukunin haɗaɗɗun kujeru suma pitch and gold ɗin kamar yanda gadon yake... Kai ita fa idan tace ma zata cigaba da lissafi sai ta gaji, kawai dai ɗakin ya haɗu, komai na cikinsa pitch and golden ne da suka dace da kansu..... “Kin koma soja ne?”. Nutsatstsiyar muryarsa mai cike da kamewa da ƙasaita ta ratsa kunnuwanta a bazata. Kallonsa tai tana tunzura baki na haushi, yana a yanda yake tunda ta shigo, ɗan latsin ashe yasan da shigowar tata. A zahiri kam cikin muryar shagwaɓa-shagwaɓa haushi-haushi ta ce, “To ai ba'a bani wajen zaman ba”. Shiru kamar bazai tanka ba, sai kuma ya ɗago kamar wani mai ciwon wuya ya sauke idanun nasa masu haske da kaifi a kanta. Ƙasa tai da nata fuskarta har yanzu a ɗan shagwaɓe, bata sake gigin ɗagowa ba sum-sum taje kujerar gabansa ta zauna tai gefe da fuska. Ɗauke idanunsa kawai yay da ga kanta ya cigaba da abinda yake yi, sai da ya sake kwashe wasu cikakkun mintuna huɗun sannan ya ɗago a hankali yana ɗan firzar da iska. Ɗahowar tasa sai tai dai-dai da fara ring na landline ɗin gefensa. Ganin yay kamar baiji wayar ba ta ɗago ta kallesa, bashi da niyyar ɗaga wayar har ta tsinke, sai da a kira na biyu ya kai hannu ya ɗauka. Bayansa ya kwantar a jikin kujerar da kai wayar kunnensa yana lumshe ido. Maimakon amintaccensa da yay tunanin ji sai yaji muryar Malikat Bushirat tana sanar masa gata a falonsa.. kansa ya jinjina tamkar yana a gabanta, sai kuma ya buɗe baki da ƙyar yace, “To”. Daga haka ya miƙe yana kallon Iffah da ke binsa da kallo. “Muje” ya faɗa a taƙaice nan ma. Bata da zaɓin da ya wuce bin umarninsa, bakuma tada hurumin tambayar ina zasuje ko miya faru. Ta ɗaga kafa kawai a bazata taji lallausan hannunsa cikin nata, da sauri ta ɗago ta dubesa, sai dai shi sam bama ita ɗin ya ke kallo ba. Suna kusantar falon bugun zuciyarta na ƙara hauhawa. Da masifar sauri taja wani irin bahagon burki lokacin da suke ƙarasowa tsakkiyar falon tai ido biyu da Malikat Bushirat da ke zaune hakimce fuskar nan tata babu alamar ta taɓa sanin minene ma murmushi a duniya. Hannun nata ta zare a cikin nasa ta fara ja da baya-baya, cak ya tsaya a wajen tamkar wanda aka dasa, sai kuma ya basar batare da ya ko waiwaya ba ya cigaba da tafiyar nan tasa ta ƙasaita. Da sauri Malikat Bushirat da sam bata lura da Iffah ba ta miƙe, kafin ya ƙarasa isowa inda take ita ta miƙe zuwa garesa ta wani rungumesa. Idanunsa ya lumshe a hankali da sakin sassanyar ajiyar zuciya, dan abune da ya jima yana buƙata amma bai samu ba. Kusan sakan ashirin tana rungume da shi kafin ta ɗagoshi tana share hawaye, kallonsa ta ke cike da son tabbatar da babu abinda ya taɓa mata shi, dan duk duniya babu abinda take so da ƙauna sama da shi. Tana masa wani irin makahon so da ya zarta hankalin duk wani mai tunani... “Ammie”. Ya faɗa a hankali yana riƙo hanunta cikin nashi. Ɗayan kuma ya kaisa kan ƙyaƙyƙyawar fuskarta ya share mata hawaye hankalinsa duk a tashe, dan ganin hawaye a fuskar Ammien sa abune da bazai kasance ƙarami ba. Ya santa ya san mahaifiyarsa jaruma ce da ko'a cikin dubu zai faɗa babu wani ɗar. Sake rungumesa tai tana magana cikin ɗacin murya. “Wlhy da yau wani abu ya sameka kamar wancan karon babu abinda zai hanani ɗaukar mataki akan koma wanene, dan bazan yafe musu ba, na baya ma ba yafe musu nai ba Eshaan” sai kuma ta sake ɗagosa da sauri, takarda da biron data ajiye a kujerar data zauna ta ɗauka, ta kamo hanunsa shi dai yana binta da kallo, a cikin tafin hannun ta saka masa, babu alamar wasa ko sassauci akan fuskarta ta furta, “A matsayina na UWA mahaifiya a gareka bin Haysam Abdul-majeed, ina baka umarnin ka saki yarinyar nan, ka kuma janye duk wata garkuwar da kai mata...” Wani irin mummunan bugun zuciya mai kaɗawa da tashin hankali da bai taɓa cin karo da shi ba a rayuwarsa yaji yana taso masa, amma yay jarumtar shanye komai ya zubamata idanunsa a dake. Kamar zai yi magana sai kuma ya fasa, kamata yay ya zaunar a kujerar data taso, kafin shima ya kai zaune gefenta a hankali dan ji yake hajijiya na neman zubdashi ƙasa. Amma kasancewarsa gwanin kamewa ko'a fuska bazaka taɓa tantance komai da ga garesa ba..........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (33) ........Ruwan da ke ajiye kan table ɗin cikin jug ya ɗauka ya tsiyaya, cike da kulawa ya miƙa mata yana lumshe idanu da buɗewa. Kai ta girgiza masa zatai magana, shima ya girgiza masa nata alamar kartace komai. Ya ce, “please Ammie”. Ruwan ta amsa, kurɓa biyu tai masa ta ajiye tana sauke ajiyar zuciya, ta sake yunƙurowa zatai magana ya sake girgiza mata kai dai. “Please Ammie slow dawn ki faɗa min mike faruwa?”. “So nake ka saketa kawai, ka janye garkuwar da ka bata, na sani dama Saiful-malik yarinyar nan bazata taɓa barinka ba. Amma Mammah da kai da Ammarah duk kuka gagara fahimtata, to gashi tun ba'aje ko'ina ba ta sake aikatawa. Yanzu badan ALLAH ya sa shi Sayeed Fayzul-haq ɗin ya lura ba wani zancen ake ba wannan ba, bazan iya jure rasaka ba a duniya wlhy Eshaan, dan haka ni kawai ka saketa na gaji haka bazan iya ba..” “Wlhy Ammie ban aikata abinda kike zargina da shi ba”. A tare duk suka dubi inda maganar ke fitowa, Iffah ce tsaye kanta a ƙasa, amma duk da haka ana iya hango yanda fuskarta tai jage-jage da hawaye. Abinka da fara tai jajir musamman ma kan hancinta. Wani irin mugun kallo Malikat Bushirat ke jifanta da shi, sai kuma ta miƙe cike da takun izza ta nufeta. Ji kake tauuuu!! Ta ɗauke fuskar Iffah da mari lafiyayyu haggu da dama. “K! Har kinyi isar da ina magana da ɗana ki kasance a wajen? Wacece k!? Ƴar uban waye k!?”. Idanunsa ya rumtse da sauri jikinsa na wani irin yamutsawa, amma a zahiri zaune yake a dake yanda ta barsa ko kallonsu ma bayayi. Malikat Bushirat ta shaƙo Iffah da ko gezau batai a tsayen da take ba saboda taurin zuciya, duk da kuwa marin ya matuƙar ratsata dan zata iya rantsuwa ba'a taɓa mata mari mai azaba irin wannan ba. Yanda ta shaƙontanne yasa fuskarta ɗagowa, da wani irin gudu jini ya shiga fitowa a hancinta yana sauka har kan hannun Malikat Bushirat, hawayen fuskarta kuwa tsaf sun ɗauke, sai wani irin mugun jaa da idanun sukayi mai ban tsoro. Malikat Bushirat da idanunta suka riga suka rufe ta ƙare matse wuyan Iffah duk da ganin jinin tana zazzaro manyan idanunta da itama suka kaɗa sukai ja.. “Yau zan kasheki na kashe banza wofi, sai naga ubanda ya tsaya miki da har kike tunanin idanunki sunyi tsaurin halakamin yaro...” Wani irin kakarin azaba Iffah ta shigayi, ga idanunta sun fara juyewa, jinin hancinta ko sake gudu yake dan a tsinke yake (haɓo). Amma tsabar ƙarfin hali bakin bai mutu ba, jajayen idanunta da ke neman wulƙicewa ta zuba cikin na Malikat Bushirat tana sakin wani murmushin wahala. “A tunaninki kasheni ne zai canja komai? To kinyi kus...ku...ren fa... fahimtar hakan Ammie, dan masu san kashe ɗakin zagaye su...suke da ke. Idan kin kasheni ki ma... maciji kika kashe baki sare kanshi ba, ki rubuta ki ajiya ko gangar jikina ta daina numfashi sai ruhina ya dawo wannan masarautar ɗaukar fansar ruhin ƴan uwana......” Wani irin yarfar da ita Malikat Bushirat da jikinta ke rawa yayi, dan wani irin guguwar bala'i ta hango a cikin idanun Iffah masu matuƙar gigitarwa tamkar ba ainahin idanun yarinyar ba. Akan jikinsa Iffah ta faɗa, dan yarfar da ita da Malikat Bushirat tayi dai-dai da mikewarsa dama, sai dai kalaman Ammien sa da shaƙar da tai mata kawai suka shiga kunensa da idanunsa, baiji komai na da ga abinda Iffah ta faɗa ba ita. Hankalinsa ne yay bala'in tashi da ganin jinin da ke fita a hancin Iffah, yay saurin tarota jikinsa ganin jiri na neman zubar da ita. Sake harzuƙowa Malikat Bushirat tayi. “Please Ammie, Please! Please” ya faɗa da wata irin raunananniyar murya mai sage duk wani kuzarin mutum. Idanunta da suka gama juyewa gaba ɗaya ta watsa masa, tana mai nuna shi da ɗan yatsa a kausashe. “Na baka nanda awa ashirin da huɗu in bakabi umarnina ba zakasha mamaki Eshaan”. Fuuuu ta nufi Alevator batare da jiran amsarsa ba ta shige.... Hankalin Tajwar Eshaan gaba ɗaya sai ya rabu biyu. Furucin Amminen sa ga kuma jinin da ke zuba da ga hancin Iffah. Tsabar yanda ya rikice sai ya shiga laluben waya. Hannunsa Iffah da ke ƙoƙarin ganin jinin ya tsagaita ta riƙe dan ba yau ta fara haɓo ba. Kanta ta shiga girgiza masa tana magana da ƙyar dan ta shaƙu a wuyantan nan. “Karka kira kowa Sultan Please. Haɓo ne kawai ka samun ruwa a kaina in munyi sa'a zai tsaya”. Kansa ya jinjina mata kawai, dan duk da ruɗanin da yake a ciki babu abinda ya canja a nutsuwarsa da ƙasaitar nan. Wanda ma zai iya ganinsa a haka sai ya iya ɗauka ai baima wani damu ba. Ɗagata yay cak cikin hannayensa yana tafiya cikin takun nan nasa step by step babu wani gargada ko garaje a ciki. Ɗakin da suka fito ya koma da ita. Kai tsaye cikin haɗaɗɗen toilet ɗin ɗakin ya kaita, faɗa masa duk yanda Ummu ke mata idan tana haɓo tayi, cikin sa'a kuwa sai gashi ya tsaya. Sai dai ba ita ba hatta shima kayansa jinin duk ya ɗan taɓa, nashi ma sai yafi bayyana kasancewarsu masu haske. Dole ya cire rigar dan jini na ɗaya daga cikin abinda bai son gani, yanzu hakan ma tsigar jikinsa sai tashi take yi, dakewarsa ce kawai ta ɓoye hakan a zahiri. Gama cire rigar dai-dai da ɗagowar Iffah da ke son ce masa thanks you. Cikin sauri ta maida idanunta ƙasa ƙirjinta na wani irin harbawa, dan babu komai a cikin rigar, da ya ciren sai ya zam da ga shi sai dogon wandon pyjamas ɗin kawai ya rage. Koda wasa bata taɓa sanin mutumin nan haka yake a murɗe ba kamar wani ɗan wasan danbe ba, ita fa duk tsiwar nan tata haka kawai duk wani mai irin suffar nan tsoronsa ma takeji, shiyyasa bata kallon wristiling koda wasan wasa. Shiko da tun sanda ta maida kai ta duƙar ya fahimci inda ta dosa hanyar fita ya nufa, sai da ya je gab da ƙofa a maganar nan tasa kamar ta dole ƙasa-ƙasa ya furta “kiyi wanka” ya ƙarasa ficewa. Ta jima zaune maganar kiyi wankan na juya mata a rai, tana da buƙatar wankan, amma tana jin kunyar yinsa saboda sanin bata da kaya a nan. To amma tunda shine ya ce tayi tasan maybe ya ɗauka mata kamar wancan ranakun. Da wannan tunanin ta gamsu da yin wankan. Sai da kuma ta kammala ta duba babu bathrobe duk sai towels a bathroom ɗin. Kamar zatai kuka ganin duk basu da wani girma, da ga ƙarshe ta samu ɗan babba da ya kai mata gwiwa da ƙyar. Kamar mai shirin yin sata haka ta fito da sanɗa, ta saki wata wawuyar ajiyar zuciya ganin babu kowa a ɗakin, da ɗan hanzarinta ta ƙaraso cikin ɗakin tana dube-duben koya ajiye mata kayan, ganin dai babun tai ƙwalƙwal da idanu kamar zatai kuka. Zuciyarta na raya mata ta koma ɗakin da kayanta suke, ɗan ɗagowa tai firgigit dan jin motsi da tai har towel ɗin na neman suɓuce mata saboda tun asali ita fa bata iya ɗaure towel da ƙyau ba sai Arfa ta mata, shiyyasa tafi son babban towel da zata iya cikuyewa a hanunta ta riƙe. Cak ya tsaya sakamakon saukar idanunsa kan wani damɓareren tabon tawadar ALLAH a bayanta dake fari sol a ta ɓangaren kafaɗar damanta. Iffah da duk ta rikice da ganinsa tuni ta ɗane gadonsa taja lallausan duvet ɗin sa ta cikuykuye jikinta dake mazarin rawa. Babu abinda ta tsana kamar namiji ya gammata jikinta. Musamman ma shi da takema kallon wani abu da ban. Gwanin naku tuni ya basar da haɗiye komai kamar ma bai san da zamanta a ɗakin ba. Sai ma ƙarasa takowa da yay jikin gadon ya ajiye mata kayan da ke hannunsa ya kai zaune shima ya bata baya. Idanunsa ya rumtse zuciyarsa na wani irin harbawa da ganin ƙyaƙyƙyawar surarta da tabon nan na tawadar ALLAH da ke a bayanta. Buƙatar son sake gani yake dan tabbatar da abinda zuciyarsa ke cusa masa yana ƙaryatawa. Sai dai yasan haka gatsau gareta bazai yuwu ba, dan haka sai kawai yama miƙe ya fice a ɗakin domin bata damar shiryawa. Tsahon mintuna goma sha biyar ya ɗauka kafin ya sake dawowa ɗakin. Ta saka kayan sai dai tana zaune a kan gadon ta cusa kanta cikin ƙafafunta komai da ya faru na dawo mata tamkar mafarki. Dan tsantsar tsanarta data hango cikin idanun Malikat Bushirat yaƙi barin ranta sam. Tasan zata iya ganin fiyema da haka saboda abinda ta aikatama tilon ɗanta amma sai zuciyarta ke tabbatar mata akwai dai.... Motsin shigowarsa ta sata katse tunanin sai dai bata ɗago ba. Kallo ɗaya yay mata a cikin kayan nasa da sukai mata burum-burum duk da t-shirt ce fara da wando 3quater ya ɗauke kai. Bayan minti ɗaya da wasu ƴan sakkani taji motsin zamansa kusa da ita. Ɗagowa tai tana ƙoƙarin haɗiye hawayenta, dan wani kewar iyayenta da yan uwanta takeji. Shayin da ya ajiye a ɗan coffee table ɗin gaban gadon ya tura mata batare da ya ce komai ba. Ƙyakyƙyawan kofin ta bi da kallo, sai taji shayin ya burgeta dan tunda ta shigo ɗazun dama ƙamshin ya cika mata hanci. Ɗan ɗagowa tai, sai ko suka haɗa ido, ƙif-ƙif ta farayi da nata kamar zata sake sakar masa wani kukan da take ƙoƙarin haɗiyewa. “What?”. Ya faɗa ƙasa-ƙasa shanyayyun idanunsa na bin hawayen fuskar tata da kallo. Sake ƙwaɓe fuskar tayi a hankali ta furta, “Kai ne ai”. “Nai miye?”. Ya tambaya cikin ɗan waro idanunsa waje. “Ni bana son kallo”. Yanda ta faɗa tana tura baki da share hawayenta ba ƙaramin tunzurashi yay ba. Amma sai ya kanne yana ƙara ƙanƙance idanun nasa a kanta da motsa lips ɗinsa kaɗan yana binta da shegen kallon nan nasa. Sai kuma ya ɗan laɓe baki a fisge ya furta, “Sadakina na kalla ai”. Furucin nasa yazo mata a bazata, dakatawa tai daga ƙoƙarin kai kofin shayin bakinta ta dubesa da sauri domin tabbatar da shi ɗinne ya faɗa ko wani aljani. Bayan ita da shi ɗin dai babu wani a ɗakin, sannan kuma ya ƙi ɗauke idanun nasa da ga kanta, sai ma sake narkesu yake da wani salon kallo mai saka tsigar jiki tashi kamar mai jiran cewarta..........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (34) ..........Wani irin tashi tsigar jikinta ta shigayi da salon kallon nasa, yayinda bugun zuciyarta ke amsa kuwwa cikin ƙirjinsa. Numfashi ta ɗan ja a hankali ta maida idanunta ƙasa, batare da ta sake gigin ɗagowa ba dan haka yafi mata kwanciyar hankali. Ganin bazatace koman da yake buƙatar ji ba ya wani ɗauke kai gefe cikin son basar da shock ɗin da ya fahimci maganarsa ta jefata yana wani lumshe idanunsa. Sai kuma ya buɗe da sake juyowa ya ɗan ɗage gira sama, “Tunda bakin ya mutu mu cigaba da maganarmu ta ɗazun?, dan da gaske ina son muyi aiki tare”. Ƙin ɗagowa tai yanzun ma ta jin jina masa kai kawai alamar eh. Shiru ya ɗanyi na wani lokaci kamar mai tunanin abinda zai fa ɗa, sai kuma ya nisa da ƙyar ya furta, “Abinda ya faru ki ɗaukesa kamar bai faru ba, tana cikin fushine kawai. Duk abinda kike buƙatar sani da ga gareni na baki da ma”. Yanzu ma kanta ta jinjina masan tana wasa da yatsunta, ta fahimci akan mahaifiyarsa yake magana. Batare da ta dago ba ta ce, “Miyasa ka yarda da ni, bayan na sanar maka duk abinda ke raina game da kasancewa da kai? Har ma na aikata, na kuma amsa na aikata” Ɗan murmushi ya saki kaɗan yana mai bin yatsun kafarta da take wasa da su da kallo, sai kuma ya kauda kan gefe yana ɗan lumshe idanun da buɗewa. Kai daka ga yanayin nasa ka tabbatar bazai iya jure doguwar maganar ba, duk ma a takure yake da yawan surutun. Iffah da ke binsa ta kasan ido da kallo sai ta samu kanta da kasa daina kallonsa, a zuciyarta kam ayyanawa ta ke (murmushi yana masa ƙyau). Kamar ya fahimci mi take ayyanawar kuwa ya tsuke fuskar. Wayar da ya ajiye a gefensa ya ɗauka, yay ɗan rubutu ya ajiye gabanta. Rinannun idanunta ta sauke akan wayar. _“Ki faɗamin gaskiya ya akai kika san an saka abubuwan can na ɗazun?”._ Shayinta ta cigaba da sha kamar bazatace komai ba. Sai kuma taja ajiyar zuciya, cikin muryar nan tata dake shaƙe ta bashi amsa. “Kamar yanda na sanar maka a mafarki na gani. Iya gaskiyar kenan”. Bawai bai yarda da ita bane, dan ya fahimci ita tana cikin mutane marasa ɓoye abinda ke ransu koda kuwa laifi ne a kansu. Amma zuciyarsa rawa take da amsar tata kasancewar al'amarin bazai kama hankali ba, musamman ga irinshi da ba wani gama sanin abubuwa irin waɗan nan yay ba da ƙyau. Wayar ya sake ɗauka ya rubuta, “Miye alaƙar wanda kukai aikin farko da wannan?”. Wayar ta ajiye tana ɗan murmushi, “A baɗinin abinda na gani suna da alaƙa, a zahiri kam bani da shaidar tabbatar da hakan dan ni kaina ban yarda mafarki na zai zama gaskiya ba”. “Ina son na sansu”. “Bita kawai kake buƙata amma nasan ka sansu”. Jin yayi shiru ta sake nisawa da ajiye kofin. “Bayan nan mi kake son sani?”. Kansa ya jinjina mata alamar babu. Ta ƙara faɗin, “Ni zan iya tambaya?”. Nan ma kan ya jinjina mata alamar eh. “Kace baka san duk matan da aka aura maka ba sai ni, a ɗan gajeren labarin da naji kuma ance sai an kawosu sashen nan suke rasa ransu ai, bayan mutuwarsu ka taɓa ganin gawarsu?”. “Miyasa kike son sanin wannan?”. “Saboda kace zamuyi aiki tare”. “Wannan baya cikin aikinmu”. “Shine mafi muhimmanci ma acikin aikin da zamuyi tare, dan nafi alaƙa da shi fiye da wanda kake son alakantani da shi. Inaji a jikina mutuwar matanka bata da alaƙa da yunƙurin waɗan nan Uncle's ɗin naka. Su nasu yaƙin da banne da wannan”. Kallonta yake kamar idanunsa zasu zubo. Itako ta kauda kan gefe kamar ba daga bakinta lafuzzan suka fito ba. “Mi kike son faɗa?”. “Abinda ya dace ka faɗa kafin faɗata. Ni nasan kasan su wanene Uncle's ɗin ka da burinsu a kanka. Masu kashe matanka kawai kake buƙatar sani in har da haske bakai bane ba”. Tsabar yanda maganarta ta masa dirar mikiya a zuciya da brain bai ma san sanda ya juyo da ƙyau yana fuskantarta ba. Eh tabbas ya jima da sanin su wanene Miran Arshaan da Miran Jasim har da ma burinsu a kansa, tun kuma randa ta bashi guba yaji a ransa su ɗinne, hakama kisan matansa da su yake dangantawa, su kuma yake bibiya da son tabbatarwa. Amma magana mafi ɗaukar hankalinsa da ga gareta furucinta na ƙarshe. “Basu bane ba fa?”. Zancen zuciya ya fito fili batare da ya sani ba. Jajayen idanunta ta zuba masa kai tsaye, sai kuma ta saki murmushi mai ciwo. “Sultan ban shigo masarautar RUMAN domin kallon gine-ginen ƙawa da adon zinari ba. Idanuna a buɗe suke fiye da yanda na mage basa barci a cikin dare. A tunaninka na baka gubar da suka bani ne dan ka mutu?”. Ta juya idanunta da suka fara bashi tsoro ma shikam tana sakin ƙayataccen murmushi. “Lala-lala, madarar dana baka sam bata da alaƙa da wadda suka kawo na baka, wadda kuma na baka ɗin tun usil dama bata kisa bace” tai wata ƴar dariya mai ƙayatarwa. “Kayi haƙuri, su fa wawayen karatunsu karanta musu yake amfani suke da ni, basu san Fhareedah bint Zayyan bace ke amfani da su. Bari dai na taƙaice maka karna jaka da nisa. Ni da kaina na kawo kaina nan domin tabbatar da waye masheƙin ƴan uwana. Bani aka kawo domin bama kariya ba....” Gaba ɗaya Tajwar Eshaan yama kasa gane suma yayi ne? Ko kuwa ya zama butun butumi ne oho shi bai sani ba. Abinda kawai ya sani idanunsa nakan aljana zai kirata ko mima bai tantance ba. Iffah da ke wata ƴar dariya ƙasa-ƙasa ta yunƙura zata sauka a gadon ganin kamar ya zama gunki ne ma oho. Cak ta dakata jin an riƙota, maidota yay ta koma inda ta tashin yana binta da wani irin shegen kallo data kasa bama fassara. “Wacece ke!?”. Kalmar data iya fitowa a bakinsa kenan a cikin dubunan da ke masa kaikawo. Da gaske idanunsa razanata suke, dan haka ta kaudar da natan tana cigaba da murmushinta. “Nikam maimaita wacece ni ko bitar karatu ne ya kamata an haddace. Amma kayi haƙuri, Fhareedah bint Zayyan ce, mai jiƙaƙƙen shirin tarwatsa masarautar ruman kamar yanda suka tarwatsa min ahalina. Wlhy da gaske nake bana yafiya, in har nace sai nayi to sai nayi ɗin koda zan ƙarasa da bugun numfashina na ƙarshe.” “Kin san zan iya kasheki a cikin ɗakin nan na binne gawarki kamar ba'ayiki ba”. “Shiiii!!”. Ta faɗa a hankali da ɗaura yatsanta saman tausasan lips ɗinsa, cikin raɗa-raɗa da ƙyaƙykyafta idanunta cikin nasa dake neman tsaida numfashinsa ta furta, “Da hakan kake da tuni kayi, amma nasan kai ba mai kisa bane bin Haysam Abdul-majeed Qutb....” sai kuma ta saki murmushi tana lumshe idanunta da har yanzu basu washe da ga shaƙar da Malikat Bushirat ta mata ba, tare da yo ƙasa da yatsanta da ke kan lips ɗinsa a hankali tabi takan kakkauran wuyansa tayo ƙasa kan ƙirjinsa da tai matuƙar dannewa kafin ta taɓa ɗin, a saitin zuciyarsa ta tsaida ɗan yatsan da buɗe idanunta dake lumshe. “Wannan zuciyar zinariya ce mai hasken diamond dake bugawa da harbawar numfashin duk wani talakan ƙasata, ba ita kawai ba, kai a karan kanka ZINARE ne ESHAAN”. Ta ƙare faɗa tana mai daddaga yatsan nata akan saitin zuciyar tasa idanunta na cika da hawaye.... Ji kawai yay ɗan sauran ƙarfin da ya rage masa ya ƙarasa guduwa. Gaba ɗaya jikinsa da yay mata runfa shima ya ƙarasa saki. Miya rage kuma? Miya rage masa da zai faɗa akan wannan aljanar yarinyar yanzu kam? Taci nasara, kawai taci nasara..... 🥱 Iffah! Iffah! Anya ke ba aljanar da Shahan-shan ɗin yake ambata bace. Ni ma dai ƴar koran taki na sallama a wannan gaɓar.🚶 ★★..... ★.... “Ashe abin kunyar da wancan wawan yayan naka ya aikata mana kenan yau a gidan nan?. Wai shi sai yaushe zai san ya girma ne? A haka yake tunanin mulkar jama'a ko gidansa bai iya adalci ba mtsowww!!”. Fuska Miran Arshaan ya yatsine cike da rashin damuwar zagin da Ameera Haifah ɗin kema ɗan uwansa Miran Jasim. A hankali ya zuƙa karan haɗaɗɗiyar tabar da sai lokaci-lokaci yake ɗan sha shima ya fesar. “Kin kirani nan ne domin zagin wani ko yin abinda ya dace?”. Tsaki ta ɗan ja tana balla masa harara, “Naga kaima zagin nasa kake ai. Abinda ya dace ɗin kuma ai duk dai a kansa ne. Dan kasan tunda wannan tsohon munafukin Sayeed Fayzul-haq ya sani shi da tsohuwar can sai wannan maganar taje gaban wancan ɗan ALLAH bani in raya gorin (Tajwar Eshaan take nufi🤭), yana sani kuwa kowa kamar ya sani ne, ga shegen yaron nan da kaifin basirar tsiya matsiyacin wlhy zai iya bin ta hanyar ya gano abinda yake fafitikar son ganowa dare da rana. Wlhy na tsani yaron nan shi da uwarsa, dan duk abinda ubansa yamun a kansa zan rama har sai naga baya numfashi a duniya zan huta”. Saurin kallonta yay, Dan shi fa wannan tunanin ma baizo kansa ba yanzu tsabar abubuwa sun ma kansa yawa..........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (35) .........Karan sigarin hannunsa ya ajiye a ƙyakykyawan ƙaramin bowl ɗin gabansa na glass “Ya akai banyi wannan tunanin ba, ya ALLAH”. Yay maganar yana miƙewa hannunsa duka kan sumarsa ya shiga cakuɗata. Shi dama akwai ruɗewa idan abubuwa suka masa yawa. Harara Ameera Haifah ta balla masa tana faɗin, (Kai dama ai jaki ba komai kake fahimta ba, shegu biyu burina na cika na kawar da shegen yaron nan kuma bazaku sha ba ai, kubar ganin da taimakonku na shigo masarautar nan, bazaku sha da ga maidani abinda na za na yanzun). A zahiri kam sai ta saki murmushin yaudara. “Kaga zauna Shahan-shan ɗin gobe, kai daɗina da kai ruɗiyar masifa”. “Bazaki gane ba Haifah, duk yanda kike zato da tsammanin hatsabibanci shegen yaron nan ya wuce nan. Wlhy yace ubansa bai iya komai ba akan taurin kai da shegen kaifi”. “Duk kaifinsa da taurinsa mune ajalinsa shi da wannan ƴar iskar yarinyar mai bakin reza. Na rasa gidan ubanda suka samota sai kace ƴar ifiritan aljanu”. (Iffah 😂). “To dama micece inba ƴar ifiritan aljanun ba. Kina gani har yanzu iya bincikenmu mun gagara gano inda tsinannun mutanen nan suke. Wai mu Barrister Akeem zaici ma amana bayan mun yarda da shi”. “Nifa gaskiya bana tunanin haka, nasan waye Barrister Akeem batun yanzu ba, zaka tabbatar da yana da hujjar ɓoye kansa shima a duk randa ya bayyana kansa garemu. Ai tunda har ya bamu haɗin kan salwantar da iyalan Barrister Abdallah Aas da yake abokinsa dolene ya bada ƙafa. Kai dai mu cigaba da jiransa ɗin, Ni yanzu duk bama wannan ke gabana ba, wannan haukan yayan naka ne, sai kuma ita waccan kuna bibiyar lamarinta da gaske har yanzu shegen bakin nata na kulle dai ko?”. Nannauyan numfashi Miran Arshaan ya saki, “Boka Barbushi baya aiki ya warware sai in da kansa ya warwaresa, amma duk da haka Inaga zan jefa tsuntsu biyu da dutse ɗaya. Zan ziyarce a safiyar gobe da safe”. “Hakan ma yayi, ni bara na wuce dan naga asuba ma na gabatowa.” ɗan riƙota ya sakeyi yana wani ɗan murmushin da kai hancinsa jikinta, murya can ƙasan maƙoshi ya ce, “Ki ɗan ƙaramin lokaci mana, kwana nawa bamma sakaki a idona ba”. Baki ta ɗan taɓe da janye jikinta tana cigaba da maida kayanta. Cike da muryar yaudara tace, “Nima ina kewar taka ai, sai dai lokacin barina nan ɗin yayi. Kaje ga wawuyar matarka can nasan ta kasa barci saboda kai ƴar wahalar”. Haka kawai sai yaji zuciyarsa ta ɗan sosu da zagin da akaima Jasrahn yau, duk da ba yau ne karo na farko da Ameera Haifah ke zaginta ba. Baice komai ba ya koma ya kwanta yana ƙoƙarin sake kunna karan sigari. Itama tsaf ta gama kimtsawa cikin kayan ɓadda kamarta, gabansa tazo ta ɗan kamo hanunsa mai riƙe da sigarin ta zuƙa, a fuskarsa ta bulbula hayaƙin, hannu ya kai zai cafkota ta zille tana ƴar dariya ta fice.... (Humm, na san dai masu karatu basu mance wacece Ameera Haifah ba. Itace amaryar Tajwar Haysam mahaifin Tajwar Eshaan kenan. Bari na baku a buɗe. Ameera Haifah dai itace su Miran Arshaan ke yawan ambata da matar nan. Sun santa ko nace Miran Jasim ya santa tun kafin ta shigo masarautar. Dan karuwarsa ce, ko nace shine ya maidata karuwar🤦 . Dan da farko tazo neman taimakonsa ne ya shige mata gaba ta auri mahaifin Tajwar Eshaan marigayi Tajwar Haysam kenan saboda sonsa da take na masifa. Ita kuma ɗiyar wani shahararren mai kuɗi ne Anwarus-sadat, ƴar gata ce ta gaske a gidansu, ta fara son Tajwar Haysam ne lokacin data rako mahaifinta sukai masa gaisuwar salla. Tunda ta gansa ta rikice itafa sai shi, shiko bai taɓa bi takanta ba, a wajen mahaifinta ta amshi number sa, ta dinga takura masa da sakwanni shiko ya share. Iya haukacewa tayi kansa har mahaifinta ya tunkari Tajwar Haysam a lokacin amma ya bashi haƙuri kasancewar Ameera Haifah bata wuce sa'ar Tajwar Eshaan ba ma, acewarsa tayi ƙarama a duk cikin matansa, dan ko Ameera Danish-Ara ta girmeta sosai. Kamar ta haƙura sai kuma ta kasa a wata haɗuwa da sukai da Miran Jasim cikin jirgi, shi da ya ganta sonta yake a lokacin, sai dai kuma ita kafin ya furta sai tazo masa da batun yayansa, wannan abu yay masa zafi, amma da yake shegen kansa ne sai yay mata alƙawarin mallakar Tajwar Haysam amma ta yarda da shi. Masifaffen son ganin ta zama matar Shahan-shan Haysam ya sata amincewa. Kasancewarta ƴar gata babu ƙwaɓa a cikin gidansu ya fara lalata mata rayuwa. Tun kamar za'ai ɗaya a haƙura har ya maidata kamar wata matarsa😭, sai dai da ga ƙarshe yaci nasarar cika mata burinta na zama matar Shahan-shan Haysam da taimakon Miran Arshaan daya shige gaba wajen Malikat Haseenat kasancewar shi ɗan ɗakinta ne. Tunda Ameera Haifah ta auri Tajwar Haysam bata sake yarda da Miran Jasim ba duk da yana mata nacin hakan, ga shi kuma taƙi samun soyayyar Tajwar Haysam shi kuma, baya wulaƙantata amma kuma babu ruwansa da ita, dan takai kusan wata bakwai kafin ya yarda ya kusanceta dan gudun kar UBANGIJI ya kamashi da laifin tauye mata hakki. Duk matansa babu wadda bata kawo masa mutuncinta ba, hakan ya bada gudunmawar jin ya ƙara tsanar Ameera Haifah saboda yanda ya sameta. Da ga nan fa ya tattarata ya watsar ko kallo bata ishesa ba. Itako tarayya da ita da yay sau ɗayan nan taji ta sake haukacewa a kansa. Zamansu sam babu daɗi a tsahon shekara bakwai da suka kasance tare, dan sai tayi da gaske yake haɗa shimfiɗa da ita. Farin ciki kam babu tsakaninsu, dan ko murmushi sai dai taga yanayi amma ba ita ba har ALLAH ya ɗauke abinsa. Bayan barinsa duniya ta koma cikinsu Miran Arshaan a dalilin jin sirrinsu da tayi, a nan ne itama take sanar da su burinta na rama duk abinda Tajwar Haysam yay mata akan Tajwar Eshaan. Daga nanne kuma Miran Jasim ya koma nemanta, a ɓoye kuma tana tarayya da Miran Arshaan shima. Wannan kenan ALLAH yasa dai kun gane dan nidai na zayyano babu ruwana🥱). ★... MALIKAT BUSHIRAT ★.... Tunda ta shigo sashen nata ta zube tama kasa motsawa. Babu abinda ke mata zuwa da dawowa sai fuskar yarinyar da abinda ta gano a cikin idanunta. Tabbas anzo wajen, kuma lallai anzo gaɓar. Gaɓar da a farko ba ita tai hasashen zuwa ba. Wai ita, ita Malikat Bushirat, mahaifiyar Shahan-shan mai mulkin karagar ikon ƙasar ruman baki ɗaya, yarinya ƙarama, ƴar talakawa ta kalla tsabar idanunta, ta sanar mata _inma ta kasheta ta kashe maciji ne bata sare kansa ba, ko bata numfashi, ruhinta zai dawo bibiyar fansar ruhin ƴan uwanta_. Kai kai kai, wannan wace irin rana ce, wace rana ce haka tazo gareta? Itace fa, ita ɗin nan dai, tauraruwar taurari, farin wata fitilar samaniya, rana mai rabama kowa aiki, taiku mai ruwan ban mamaki, zakanyar da ba'ai mata wargi, buhun ƙayar da ba'ai masa danni, mace mai kamar maza kwarine babu. Bahun barkono ba'ai masa shiƙa. Kokino ba giyar yaro ba sai dai manya karami yasha ya kwana a jeji. Giwa taku da ga nesa isharar yara, ƙarfe baka karyuwa sai da wuta, MALIKAT matar Shahan-shan uwar Shahan-shan ƴar asali jinin asali. Takai zaune daɓas jin hajijiya na neman zubar da ita. A hankali ɗakin ya shiga juya mata, sai kawai ta lumshe idanun ko hakan zai bata salamar da take buƙata..... ★★.. SHAHAN-SHAN ★★... Bayan ta gama zayyane masa birkitattun zantukanta guduwa tai tabar ɗakin, har yayi yinƙurin bin bayanta ya fasa. Amma ko sau ɗaya bai rintsa ba, saboda yanda kalaman nata masu tsananin saka ruɗani ke masa kai kawo. Zai iya rantsuwar wani mahaluki bai taɓa bashi tsoro na gaskiya ba kamarta, tabbas yana buƙatar sake sanin ainahin wacece yarinyar nan bayan sanin da ta sanar masa a baya. A hankali tambarin nan ya sake masa flash a cikin idanunsa, tare da kalamanta akan bashi madara da cewar ita ke amfani da su ba sukeyi da ita ba, ita ta kawo kanta nan bashi ya kawota ba, sai kawai yaji zuciyarsa na wani irin rawa, ga kansa da ke masa sarawar ciwo tun a dare da ta barsa. Da ƙyar ya iya ajiye komai a gefe ya tashi zuwa bathroom, sai da ya fara wanka sannan ya fito yay nafila ya ƙarasa da shirin fita massalaci. ★.... Saɓanin shi kaɗan ita Iffah tana baro ɗakin zubewa tai a inda ta shigo sai barci, takai tsahon awa uku tana barcin kafin ta farka a firgice. Ta jiƙe sharkaf da zufa bata wasa ba, ga mummunan mafarkin da tai na mata matuƙar kai kawo, dole ta dangantashi da mummuna, dan yau ne karo na farko data farayinsa. Addu'a ta shigayi kamar yanda kaka ya gargaɗeta a duk sanda tai irin mafarkin, sai da ta samu ƴar nutsuwa sannan ta miƙe. Bathroom ta shiga ta wanke fuskarta, tsaye tai a gaban mirror tana kallon kanta, sai ta dinga hango kamar duhu-duhu ta bayanta, babu alamar zata tsorata, sai ma sake ƙurama mirror ɗin ido tayi, amma a ranta addu'oi take karantawa. Dishi-dishin ta cigaba da kallon abun, sai kuma ya shiga bajewa kamar wani hayaƙi ya fara ɓacewa. Juyowa tai a hankali, abin mamaki sai ko gashi a zahiri hayaƙin yana bajewa cikin ƴan sakkani ya ƙarasa ɓacewa ɓat. Ajiyar zuciya mai nauyi ta ja ta fesar, cikin halin ko'in kila kuma sai ta ɗage kafaɗa da sake juyawa ga mirror ɗin tana kai hanunta ta baya ta ɗan shafo gefen kafaɗarta ta dama, zuciyarta na raya mata ta ɗaga rigar ta gani, wata kuma na ture mata tunanin da cewar mafarki fa ba gaskiya bane. Rashin matsaya ya sata ajiye komai gefe ta ɗaura alwala ta fito. Nafila tayi kusan awa ɗaya harda karatun Alkur'ani duk da batai mai yawa ba ta koma gado ta kwanta. Maimakon barci sai abinda ya faru tsakaninta da Malikat Bushirat ɗazun ya shiga dawo mata a rai, tasan ta shaƙeta, bata tashi tsintar kanta ba sai a jikin Shahan-shan tana haɓo. Ya taimaketa ya tsaya har tai wanka ya bata kayansa ta saka ya bata shayi, da ga shan shayin ne bata tashi tsintar kantaba sai yanzu a ɗakin nan da ta farka da ga mummunan mafarkin nan. Ya akai ta shanye shayin daya bata da yanda tazo nan ɗakin bata sani ba..........✍️ _🚴Tofa wata jiƙaƙƙiya, Shahan-shan kayi takanka Iffah dai da alama ba.... (🥱Bara dai na gimtse bakina)_ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (36) .........Yana cikin Gym ɗinsa tun barowarsa masallaci sallar asuba yana motsa jiki amintaccensa ya isar da saƙon neman iso da ga Sayeed Fayzul-haq. Sayeed Fayzul-haq shima amintacce ne a garesa yanzu, dan haka ya bada izinin shigowar tasa. Kallo ɗaya Sayeed ya masa ya duƙar da kai, dan yau motsa jikin yake ko riga babu, dogon wando ne kawai bai sa rigar ba, sai ƙaramin towel dake saman kafaɗarsa ya taimaka wajen rufe jikin nasa. Batare da ya daina abinda yake ba balle kallon Sayeed ɗin cikin ƙasaitar nan tasa da zafin da Iffah ta haɗa masa a daren jiya muryar ta sake komawa ƙasa ya furta, “Akwai wata damuwa ne?”. Sayeed Fayzul-haq yay saurin sake risinawa cike da girmamawa yace, “Eh to badai mai yawa bace. Tun a daren jiya naso sanar da kai sai kuma na fasa dan nasan ka shiga barci. Akan Miran Jasim ne da iyalinsa......” nan ya zayyane masa komai a nutse. Ɗan murmushi yayi a karo na farko batare da ya ce komai ba har tsawon wani lokaci da Sayeed ya fidda ran cewar tasa ma. Machine ɗin da yake kai ya kashe, ya sakko yana jan towel dake a kafaɗarsa rataya ya shiga tsane wuyansa zuwa fuska. Zufa yake sosai kamar wanda yay wanka. Zama yay a kujera, da sauri Sayeed Fayzul-haq ya ɗan zuba ruwa a kofi ya miƙa masa. Baiyi musu ba ya amsa, sai dai kurɓa huɗu yay ya ajiye dan bai damu da shan ruwa ba idan ya gama motsa jiki, yafi son shan shayinsa na ƙa'ida. A fisge kamar an masa dole ya ce, “Mi Doctors ɗin sukace akan jikin nata?”. Yasan Matar Miran Jasim ɗin daya daka yake magana, “Ya shugaban sun tabbatar da taji ciwo musamman a ƙashin bayanta da ya taka. Wannan shine result ɗin binciken nasu.” ya faɗa yana miƙa masa takardun dake hannunsa. Amsa yay batare da ya duba ba ya ajiye gefensa. Hakan ya tabbatar ma da Sayeed ɗin yana buƙatar lokaci, dan shima tunda ya shigo ya fahimci yau ƴan miskilancin ne da mulki a kusa. Dan haka ya rissina ya masa sallama. “Afito lafiya”. Idanunsa kawai ya lumshe batare da ya tanka ba. Shiru yayi a gurin kamar mai nazari, idanunsa ƙyam akan file ɗin..... ★★.... Makarar da tai ya ja mata yin salla ba'a kan lokaci ba, ga jikinta na mata ciwo sosai tako ina har tana jin buƙatar ɗan motsashi ko zata samu sassauci. Gym ɗin da ta gono ranar a leƙe-leƙenta ta tuna. Yanda ya ƙayatu ya sake zaburar da ita ta miƙe tana murmushi. Fitowa tai da ga ɗakin data kwanan batare data damu da rashin ganin Tajwar Eshaan ɗin ba kasancewar tasan ɗakin barci dama ai sai wanda ya zaɓa. Ɗakin jiya ta koma, ta buɗe kayan da tai online shopping ɗin nan da har yanzu suna a jakar da aka kawosu. Pink kayan training ɗin nan na Company Adidas da suka ɗauka hankalinta tun a waccan ranar ta ciro ta fara kimtsawa. Tsaf ta fito cikinsu kamar wata babyn roba, bata damuba da yanda rigar ta tsaya mata iya kan ciki har ana ganin jikinta, hakama wandon ya matuƙar kama jikin nata. Kayan sun fidda mata ainahin shape ɗin ta masha ALLAH. Duk da tasan babu kowa da zai ganta sai da ta ɗaura after dress a sama. Cikin ranta take addu'ar ALLAH ya sa dai yana can sama yana motsa nasa jikin dan tasan dai da wahala ace ya fita iyanzu. Ganin hadiminsa a ƙofar Gym ɗin da yay saurin zubewa yana gaisheta bai sa takawo a ranta yana ciki ba, dan idanunta sun rufe da son zuwa ta ɗana machines ɗin nan masu ƙyau. Cikin sassanyar muryarta tai sallama tana shigowa kanta tsaye. Kamar wanda aka farkar da ga barci ya buɗe idanunsa da ke a lumshe. Sai dai kuma bai motsa ba ya kai dubansa ga ƙofar shigowar inda yaji muryar tata ta gefen ido. Mamaki ne ya kamashi dan baiyi zaton tama san da Gym ɗin ba, ganin kamar bata lura da shi ba ya sake lafewa yana kallon ikon ALLAH. Da ƙyar ya iya riƙe numfashinsa yana lumshe idanu da buɗewa lokacin data gama yaye after dress ɗin data ɗoro saman kayan training ɗin ta ajiye kan wani machine. Tun da ga saman gashin kanta dake ɗaure da ribbon a tsakkiya yana lilo har zuwa takalma ɗin ƙafarta yabi da kallon nan nasa na ƙasan ido. Idanun ya sake lumshewa yana ambaton sunan ALLAH, dan yau ne karan farko da ya taɓa ganinta a ainahinta kamar haka, dan kayan sun lafe mata da ƙyau da fidda ainahin surarta fiye da jiya da ya ganta da towel. Oho ita dai bata san yana yi ba, sai ma faman kokawar yanda zata kunna machine ɗin data hau take yi. Hararar Machine ɗin tayi tana ɗan diddira ƙafa na haushi. Ya ɗan murmusa yana kauda kansa. Kusan sakkani ashirin ya miƙe a hankali yana ajiye towel ɗin hannunsa. Tana ɗan duƙe da cigaba da ƙoƙarin son kunnawar taji ɗumin mutum a bayanta. A zabure ta ɗago gabanta na faɗuwa, jikinsa ta jingina kasancewar tsaye yake bayanta daf da ita sosai, shigewar idanunsu cikin na juna ya sake ruɗar da ita ta janye jikinta da sauri tai baya sai ta koma tana fuskantarsa. Kif-kif ta farayi da idanunta daka ganta kasan a ruɗe take, dan cikin sarƙewar harshe ta furta, “Good morning”. Ɗauke kansa yay cike da basarwa ya ɗan sake matsowa batare da ya amsa gaisuwar datai masan ba, idanunta ta rumtse da sauri ta sake juyawa a yanda take farko ta bashi baya. Kallon bayan nata ya sake ɗan yi ya kauda idanun, kaɗan ya motsa lips ɗinsa murya can ƙasan maƙoshi cikin kunnenta ya ce, “Bissmillah” yana kai hannu ya kunna mata tare da jan jikinsa baya duk a lokaci guda. Ji take inama ƙasa ta buɗe ta shige ciki kawai ta huta. Tayi dana sanin shigowa Gym ɗin nan a zuciyarta yafi sau dubu. Jin machine ɗin na neman zubar da ita ƙasa yasa dole ta fara ɗan yin gudun, sai kuma ta sauke nannauyar ajiyar zuciya hangosa ya juya mata baya ta cikin mirrorn da aka zagaye Gym ɗin gaba ɗaya. Yanzu kam ya saka riga, duk da haka ta kasa sakewa, kaɗan-kaɗan sai ta kai dubanta kansa da ga inda yaken gaban teburin wasan basket ball dan shima game ne mafi soyuwa a ransa bayan wasan polo da ƙwallon ƙafa. Duk abinda take yana hankalice da ita sarai, amma ya fuske domin bata damar motsa jikin yanda ya kamata. Cikar mintuna ashirin da hawanta machine ɗin ya ajiye ɗan abin 🎾 wasan basket ball ɗin ya nufeta. Ta gabanta ya zagayo, idanunta a rufe da alama hakan yafi mata daɗi ko ta rufene dan shi oho. Da haƙori ya danne lips ɗinsa yana kauda idanunsa da ga inda suka sauka, kashe machine ɗin ya sata buɗe ido da sauri, dan duk da taji ƙamshinsa ya sake kusanto ta batai zaton shi ɗin bane ba. Kamar zata fasa kuka ta duƙar da kanta da sauri tana tura baki gaba. Lips ɗin nata ya ɗan zubama idanu, sai kuma ya janye yana ƙoƙarin barin wajen da faɗin, “Next..” a hankali. Wani irin kwarjini da shakkarsa takeji, sai taji bazata iya masa musu ba sam. After dress ɗinta ta ɗauka tana maidawa jikinta tana nufarsa inda yake gaban wani machine ɗin. Komai baice mata ba akan after dress ɗin, ya nuna mata yanda zatai da hannu ya bar wajen. Yanzu ma tanayi tana satar kallonsa, ji take rigar na neman taɗeta amma ta fuske sai ɗan tattarota da tai a hannu ta cigaba da yi da sauri-sauri dan ya fara mata daɗi. Yanda ya basar da ita baya kallon ko inda take sai take jin ƙarin ƙaimi... “Wayyo ALLAH na!”. Siririyar muryarta ta ratsa kunensa a bazata, dan basket ball ɗin da yake ta fara janye hankalinsa shima ba kallonta ya ke ba. Tsabar ƙasaita ta zame masa jiki a hankali ya juyo duk da zuciyarsa na wani irin harbawa da sauri-sauri, ganinta a ƙasa wanwar ya sashi nufarta da ƴar sassarfar da bata canja komai a takun nutsuwarsa ba. Itako ganin yanda yake tafiya kamar ma bai ga faɗuwar da tai ba sai kawai ta fashe da kukan da ita kanta tasan na taɓara ne, dan koda ta faɗi ba wani ta bugu bane sai dai tanajin zafi a ƙafarta da ƙugunta sosai gaskiya. Kaifafan idanunsa ya sauke a kan hanunnta dake dafe da ƙugun nata, ɗayan kuma a agarar ƙafarta madaidaiciya fara sol. “What is Happening?”. Ya faɗa da ƙyar fuskar nan babu alamar fara'a tattare da shi balle nuna alhini, a can ƙasan ransa kam zafi yake ji a jikinsa shima kamar yanda ya fahimci tana ji. Wani kukan taɓara-taɓara ta sake fashe masa da shi tana nuna masa agarar ƙafarta da faɗin, “Shikenan ƙafana ya cire, ni dai ka kiramin Mamy da Jaddah wayyo ni Ummu, Iyyani ƙafana ya karye Hanash Akhi”. (Stubborn girl) ya faɗa a zuciyarsa idanunsa na wani shanyewa a kanta. A zahiri kam yi yay kamar zai share sai kuma ya kai duƙe gabanta a hankali. Maimakon duba ƙafar da take faman riƙewa cak ya ɗagata a wajen. Babu shiri tai saurin saƙalo hanunnta a wuyansa jin kamar zata faɗi tana waro manyan idanunta. Fahimtar magana zatai ya kauda idanunsa, a can ƙasan maƙoshi kamar an masa dole ya furta, “Ban son surutu..” Takaici kamar zai shaƙe Iffah ta cuna bakin nan gaba ta kauda kanta gefe itama lips dinta na motsawa da alama magana take wadda ba'aji. Ganin inda ya nufa da ita ta ɗan sauke ajiyar zuciya a ɓoye, yana sauketa a gadon ta yunƙura zata tashi, maidata yay ya kwantar yana watsa mata shegen kallon nan nasa na ƙasan ido da Iffah ta kasa gano fassararsa har yanzu, ba zato taji ya ture hanunta da ke dafe da ƙugunta dan anan tamafi jin zafin faɗuwar ya maye gurbinsa da nashi........✍️ _🥱To kuma dai, Ni na gaji da wagga lalata ta Iffah. Anya bazan koma team Shanshani ba😒😬🚴._ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (37) .........Da sauri ta sake maida natan kan nasa ta danne ta hanashi motsawa. Fuskar data kumbura yabi da kallo yana sake tsuke tashi, babu alamar wasa tattare da shi ya ce “Miye kuma?”. “Ni wlhy ba sai ka taɓa ba zan yi da kaina, kuma ai yama daina”. (Yarinyar nan zata kasheni wlhy) ya faɗa acan ƙasan ransa yana mai ture hannun nata ya matsa wajen. Zabura ɗaya tai ta kanannaɗe jikinsa tana fasa ƙara dan taji zafi na gaske. Yanda ta faɗo jikin nasa a bazata, ga hannunsa da yake ƙoƙarin toshe kunne saboda ƙarar da tai har cikin kansa. Baya sukai su duka, shi ya faɗa kan bayansa ita kuma tana a kansa. Bashi da zaɓin da ya wuce riƙota kawai. Wani irin dab-dab da juna fuskokinsu suka kasance, har hancinansu na gogar juna. Hakama idanunsu sun sarƙe cikin juna. Wani irin al'amari da ya sake rikita mata lissafin data manta da zafin ciwon da take ji ta gano cikin tsakkiyar ƙwayar idanunsa, da sauri ta kauda ƙwayoyin idanun nata a cikin nashi da son zame jikinta gaba ɗaya tsigar jikin nata na wani irin tashi, numfashinta kam fita yake da sassarfa. Hannunsa dake saman ƙugunta yasa ya sake maidota jikin nasa. Zafin da taji wajen bigewar ya sata matse fuska, sai kuma ta tura baki tana buɗe idanun nata kan ƙyaƙyƙyawar fuskarsa da gaba ɗaya kwarjininsa ya sa takeji ta kamar a wani kogon dutse suke a matse. Yanda taki yarda ta sake kallonsa ya sa yaji murmushi na zuwa masa. Amma tsabar iya miskilanci da jin kai sai ya haɗiye kayansa yana ɗan lumshe idanun da sake buɗewa kan ƙyaƙyƙyawar fuskarta da tai wani takwaf-takwaf kamar zata saki kuka. Cike da son ta magantu ya ɗaura hannunsa kan inda ta bugun da ƙyau, murya a shaƙe kamar mai raɗa ya ce, “A kira Doctor?”. Yanda yay maganar yana busa mata numfashinsa kan fuskarta ba ƙaramin yamutsawa tsigar jikinta tai ba. Cikin sauri ta jujjuya masa kanta tana ƙara ƙwaɓe fuska. Ita kanta bata sanin sanda take masa shagwaɓar nan, kawai samun kanta take a hakan. “Ni dai ya daina, ka barni na tashi ba ƙyau”. Kafeta yay da kaifafan idanun nasa da suka sake shanyewa can ƙasa, cikin wani irin salon ɗagesu ya furta, “Mike nan?”. A hakali saman lips. Idanunta a rufe ta nuna yanda suke tana kauda kai. Wani makirin murmushi ya suɓuce masa a karo na farko, a hankali ya juyata suka koma kwance a gadon su duka kan hannayensu suna fuskantar juna. Baya tai yunƙurin ja ya tareta da hannunsa ya sake maida fuskarsu daf da juna. “Nace na gama da ke ne?”. Iffah fa gaba ɗaya ji take ma bada Shahan-shan take tare ba wani aljanin ne yazo mata a siffarsa. To inba haka ba taya za'ace ma Shahan-shan ne wannan. Mutum data sani ko kallo mutane basu ishesa ba, gaskiya wannan aljani ne, aljanin da ta jima tana gani kafin shigowarta masarautar nan.... Iskar da ya busa mata kan fuska ya sata jan numfashi mai nauyi alamar dawowa hayyacinta. Ya ɗan yamutse fuskan ta sa dake tsuketa, sake maida idanunta tai ta rissinar. Shima sai ya lumshe nasan ya ɗan sake buɗewa kanta yana motsa lips ɗinsa a hankali kamar wanda akaima dole. “Shi kuma wanda ya biya sadakinsa fa?”. Idonta a rufen kanta tsaye, duk da muryarta a kasalance alamar ta fara laushi ta ce, “Kai dai ai baka biya ba, dan ta ƙarfi aka kawoni masarautar nan dan a lasheni kamar yanda aka lashemun yayu na”. Da ƙyar ya iya gimtse murmushin da ke son kufce masa ya sake tsuke fuska a zahiri duk da ita bama kallonsa take ba. Daɗin biye mata yake ji, dan haka cikin ƙara ƙasa da murya ya ce, “In ma ban biya ba ai lokaci ne zai nuna. Mun taɓa lasar wani ne a gabanki zaki mana sharri?”. “Babu wani sharri. So babu adadi ma”. “Sai ki faɗa dawa-dawa muka lasa a gaban naki?”. “Matarka da ta mutu mana. Kuma nima dan namana da ɗaci ne yasa kuka kasa, dan nifa nafi ƙarfin mayu, kaima nasan tsorona kakeji yanzu haka”. Ta faɗa da ƙarfin ikon son tabbatarwa tana wani ƙara tsuke fuska. (Bazaki kasheni ba yarinyar nan) ya faɗa a zuciyarsa yana danne dariyar dake taso masa. A zahiri kam hannunsa ya maida a ƙugunta dai-dai inda ta bugu yana wani lumshe idanu da buɗewa, a hankali yake murza mata wajen batare data farga ba duk da tana ɗan jin zafi kaɗan-kaɗan. “Yaushe kika fara gano inajin tsoron naki? Dan nima dai naga kamar tsoron naki nakeji da gaske. Da alama baki barni haka ba kema mayyar ce ko?”. Lips ɗinta tai wani irin turawa tana ƙwaɓe fuska, ita ala dole taji haushi yace mata mayya, “Ni ALLAH ya kiyaye na zama mayya. Tsorona kuwa tun randa ka fara ganina mana, kuma inba tsoro ba miya maidaka Ajmaal ka dinga naɗar min sirri...” Yanda ta ƙare maganar da yin takwaf-takwaf da fuska kamar zatai kuka ya sashi jan wata irin wawuyar ajiyar zuciya jin numfashisa na fisga, kansa har ya fara masa ciwo saboda ya gaji da surutun, itako oganniyar ya fahimci ko'a jikinta ma. Cikin nuna alamar gajiyawar har cikin harshensa ya ce, “Ashe dai ni kike jin tsoron, saboda na kasance Ajmaal duk wani sirrinki na sani?”. Idanunta da ke rufe ta buɗe fes a kansa, cikin son dakewa ta ce, “Hu'im lallai ma tsoro fa? To kaima ai naka sirrin na a tafin hannuna basai na faɗa ba”. “Ni ɗin?”. Ya faɗa a fisge yana waro duk girman idanunsa kanta. Jikinta tai ƙoƙarin janyewa da ga nasa dariya na taho mata ganin yanda ya waro idanun, a nata ganin ai ya tsorata ne. Sake riƙota yay suka koma daf-daf fiye ma da ɗazun, cikin wani salon da ke neman girmar kanta ya kai hancinsa kan wuyanta yana busa mata numfashinsa. Da wani irin karyayyar murya data sata zabura can ƙasan maƙoshi ya ce, “Faɗamin wane sirrina kika sani? Na yi alkawarin zan ƙara miki da wani ma yanzu duk ki haɗa”. Yanda yay maganar numfashinsa ma sauka saman wuyanta tare da murza hannunsa wajen ciwonta batare daya fargaba babu shiri ta zabura zatai magana, rufff ya rufe bakin da tausasan pink lips ɗinsa. Ɗifff komai na jikinta mai aiki da motsin ruhinta ya tsaya cak da aikin na wucin gadi kamar yanda nashi ya kasance. Idanunsa ya lumshe a hankali da sake buɗesu kan fuskarta, kafin ya kai hannunsa baya ta ƙeyarta ya tura yatsun kan tattausan gashinta, a hankali ya fara warwaro ribbon ɗin data ɗaure gashin a tsakkiya da juya lips ɗin nasa kan nata ya mirginata suka sake komawa kan hannayensu ta ɗaya ɓarin yanzu ma suna fuskantar juna. Wannan ne karo na farko da hakan ta faru a tsakaninsu, abune kuma da bai taɓa faruwar ba, hakan ya sata shiga cikin ɗimuwa da gigita, dan da wani irin salon dake neman ɗage numfashin nata da ga gangar jikinta yake juya lips ɗin nata cikin nashi tamkar ba Shahan-shan ɗin nan ba mai tsananin miskilanci da izza da ƙasaitar mulki, wanda hatta magana wahala take masa. Murmushinsa kam abune mafi tsada ga duk wanda ya sanshi. Gaba ɗaya duk sai ta daburce jikinta ya shiga rawa, ciwon ma da ƙafar ke mata da ƙugun ta nemesu ta rasa... (🤭Bily ki kiyayi kanki🏃) Da alama Shahan-shan Eshaan ya tafi, tafiya irin mai toshe kunne daga jin ko wane irin motsin sauti da ke a doron duniya, dan dukkanin takaicinsa akan waɗan nan lips ɗin masu masa tsiwa yau da alama sai ya hucesu. Ita kanta ɗalibar tasa tun zaburar farko da tai na dawowa hayyaci bata sake motsin kirki ba. Sai da taji hannunsa na ƙoƙarin shiga cikin ƙaramar rigarta ta sake zabura da ƙoƙarin dafe hannun nasa da nata tana son janye lips dinta da ya riƙe da nashi cikin kar-kar-war jiki. Babu alamar zai bata damar da take buƙatar, dan da gani dai yayi zurfi shi kam. Da sauri tasa dukan ɗan sauran ƙarfinta wajen jan jikinta baya, kamar zai riƙota sai kuma ya barta yana mai rumtse idanunsa da sukai wani irin mahaukacin kaɗawa jazur da ɗan ƙarfi. Baya ta juya masa tana mai dunƙule jikinta dake tsuma har yanzu waje ɗaya. Tunda Ummu ta haifeta tai hankali tai wayo babu wani da ya taɓa kai hannunsa inda Tajwar Eshaan ɗin ya kai yau a jikinta, kai itafa ko riga bata yarda ta saka gaban su Arfa ma dake yayunta tsabar yanda take jin kunya. Amma yau sai ga abinda batai zato ba, da ga mutumin da batai tsammani ba, wayyo ita Fhareedah ta ga takanta. Wani irin yarrrr yarrrrr take ji kamar har yanzu hannun nasa na'a jikin nata ne tsabar yanda ta firgita. Ɗaya da ga cikin filos ɗin da aka ƙawata gadon ta fisgo ta ƙanƙamesa a ƙirjinta dan ta kasa nutsarwa waje guda, da gaske ta tsorata tsoro irin wanda batajin ta taɓa shigarsa a rayuwarta, sai kawai wasu hawaye masu ɗumi da bata san na minene ba suka shiga rige-rigen sakko mata a kan fuskarta. Ajiyar zuciyar da take ja mai tafiya da kamar shashshekar kuka-kuka ta sakashi buɗe lumsassun idanunsa da sukai wani irin shanyewa sosai, akan bayanta data juya rigar ta ɗage sosai saboda tattareta da yayi ya sauke su. Ya ɗan rufe ya ƙara buɗewa yana mai ƙarema bayan nata fari sol kallo. Wani irin harbawa zuciyarsa ta sakeyi da ɗan ƙarfi lokacin da idanunsa ke sake sauka kan wannan dai tawadar ALLAHr babba da ke a ɗan sama-saman bayan nata ta gefen kafaɗar dama. Da sauri yake ɗan girgiza kansa alamar hakan bazai yuwuba kama ce kawai da ga ALLAH. Ta inama hakan zata faru? (Kai noo.. noo.. ba haka bane) ya faɗa a cikin ransa da kaushi sosai yana ɗauke idanun nasa da ga wajen. Sai ma ya miƙe a matuƙar kasalance, zama yay ya ɗan bata baya, cikin muryarsa dake a matuƙar sarƙe ya furta, “Ga wani sirrin nan nawa na baki ki haɗa ki adana min”. Batare da ya sake yarda ya kalleta ba ya nufi bathroom kawai yana mai sake ƙaryata zuciyarsa da taƙi amsar dagiyar tasa kan abinda idanunsa suka sake gani yau ma a jikintan........✍️ _Oh ohh girma ya daɗi🥱🚴🚴🚴🚴_ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (38) ........Da wani irin zazzaɓi mai masifar zafi da ƙullewar ciki ya fito da ga bayin, amma kasancewar sa jarumin jarumai ya shanye komai yana cigaba da ƙoƙarin shanye wanda ma ke taso masa sabo. Babu kowa a ɗakin da alama Iffah ta gudu, dan rigarta da ya cire ce kawai yashe a ƙasa, sai dai babu after dress ɗin da alama ita ta saka ta fice. Samun kansa yay da ɗan sakin wani miskilin murmushi yana cije lips ɗinsa da azabar ƙarfi. Duk yanda yake son dannewa hakan ya gagara, dan wannan shine karo na farko da ya iya nisan kiwo da mace kamar haka. Hakan na nufin ya tsokaloma kansa abinda ya fi ƙarfin jarumtarsa, dan yanda cikinsa ke cigaba da ƙullewa har numfashinsa ya ɗan fara fisga lokaci zuwa lokaci. Duk da sanyin da ya fara ji na ratsa shi bai iya ya canja bathrobe ɗin jikinsa ba ga sumarsa ma jiƙe take da ruwa ya kai kan gado da ƙyar ya zauna, zufa yake ga jikinsa na tsuma abun kamar wani tsafi. Addu'ar da duk tazo bakinsa ya fara ambato da damƙo fillon data runguma ɗazun ya matse cikin hannunsa da azabar ƙarfin da ke bayyana asalin gwarzantakarsa. Wannan ranar yake gudu, wannan ranar ya ɗauka tsahon shekaru yana kaucemawa. Amma duk da haka sai da ta zo masa a gaɓar da bai shirya amsarta ba. Gaɓar da bai shirya fuskantarta ba. Gaɓar da bai shirya komai na yanda zai fara gudanar da ita ba. “Ya arrahaman”. Ya furta a hankali komai na masa kaikawo cikin gizo. Ya tabbatar idan har aka cigaba a haka to tabbas yau aiki zai buɗe, dan babu shakka kwaɓarsace zatai ruwa. Da ƙyar ya iya miƙewa, maganin da ya jima da daina sha ya shiga nema a inda ya tabbatar ya killacesa, da ƙyar ya samosa dan yayi nisa kasancewar ya daɗe da kauda idanunsa a shansa saboda abinda ka iya zuwa ya dawo kamar yanda doctor ya sanar masa har yay sanadin ajiyewar. Kwalin ya buɗe ya ciro, sai dai a mamakinsa babu komai a ciki sai kwafsan ashe ya shanyesa ma a wancan lokacin, bashi da zaɓin daya wuce sakin kwalin a wajen ya kai kwance yana jan bargo jikinsa dan rawar sanyinsa ƙaruwa yake yi, ga wani irin sarawa da kansa kemasa. Da gaske abubuwa sun masa matuƙar yawa, har ma yakan rasa wane irin tunani zaiyi. Ammien sa da sharaɗinta? Ko Iffah da abubuwan ban tsoronta? Ko Uncle's na sa da son zuciyarsu? Ko matsalolin talakawarsa da dogaransu kan jiran adalcinsa a koda yaushe? Ko.... Ko.... Ko.... Ɗin sun masa yawa, yawan da matsalar dake tattare da shi a yanzu kamar tana son nuna fin ƙarfinsu. Dan ya jima da fahimtar kansa, amma ya zama mayaƙi na gaske akan kansa da kare mutuncinsa da ga taɓa ƴar kowa. Babban fatansa a koda yaushe ALLAH ya bashi ikon riƙe kansa har zuwa ga halalinsa da zai iya bama sirrinsa, sirrin da yake fata bayan matar aurensa kar wani mahaluki ya taɓa koda kwatanta sani insha ALLAH. yana ganin ko yaƙi ko yaso lokacin yayi, sai dai lokacin yazo da wasu abubuwa masu nauyin gaske. nauyin da ya rasa ma ina ya kamata ya fara kamawa...... ★A ɓangaren Iffah data sulale ta gudu tun bayan shigarsa bayi duk yanda tayi domin ganin ƙamshinsa ya bar jikinta hakan ya gagara. Tayi wanka, ta shafa nau'in turarruka daban-daban sai dai ƙamshin jikinsan na nan daram a cikin hancinta da yaƙi bata damar jin kowane ƙamshi bayan shi. Kamar wadda aka zarema lakar jiki tai sakwat a jikin bango tana lumshe idanu. Ita kanta bata san ainahin mima take ji a kansa ba, abinda kawai ta sani komai kawai ya ƙwace mata, bata da wani ƙarfi a zuciya da jikinta a halin yanzun, abinda ya farun kuma yay mata tsaiwar sojan badakare a ƙahon zuciya babu alamar zai motsa. Hanunnta ta kai ta shafi lips ɗinta, sai kuma tai saurin janye yatsun biyu tana mai girgiza kanta kamar wadda akema magana a kunne. Buɗe idanun nata tai cikin sauri ta sake nufar inda turarrukan suke, ɗaya bayan ɗaya ta dinga binsu tana shafama jikinta, ita dai a dole sai ta daina jin wancan ƙamshi. Abin dariya abin tausai harta gama ƙamshin na nan dai bata daina jinsa a cikin hancin nata ba duk da yanda ɗakin yay wani masifar haukacewa da ƙamshin data baza har ana jinsa waje. Miya rage kawai ta saki kuka ta huta, sai ko tai takwaf-takwaf da fuska kamar zata fashe... Haka taita kai kawonta a ɗakin har mai gyarawa yazo gyara da sanar mata an gama shirya break fast. Da gaske yunwar take ji, amma bazata fita su haɗu da shi ba, dan haka ta bada umarnin kawo mata nan tana mazurai a karo na farko. Cikin ƙanƙanin lokaci aka cika umarnin nata kuwa.... ★★.... ★.... A can fada tun kusan awa ɗaya baya ake tsammanin fitowarsa, amma shiru kakeji. Hakan abune da ba faruwa yake ba. Tajwar Eshaan mutum ne da baya saɓa alƙawari. In har yace zaiyi abu to zai yisan komai girman ƙalubale da zai iya fuskanta a yayin yinsa kuwa. Hakama in har yace bazai yiba tofa ko kai waye bazaiyi ɗin ba. Kaifi ɗaya ne shi, mai faɗa da cikawa. Mai gaskiya da son tabbatar da ita a mulkinsa, waɗan nan halayensa ne dake matuƙar sake ƙawatashi da kwarzantashi ga al'ummar sa a bayyane. “Anya kuwa lafiya yau?”. Miran Arshaan daya matsu da ganin fitowar Tajwar Eshaan ɗin ya taso zuwa inda Sayeed Fayzul-haq ke tsaye ya faɗa cike da nuna damuwa. Kai Sayeed Fayzul-haq ɗin ya jinjina masa shima da ƴar damuwar a fuskarsa. “Banajin matsala ce insha ALLAH. Dan ban daɗe da ganawa da shi ba, sai dai kasan mutum mai iyali...” ya ƙare maganar da wani ɗan murmushin su na manya. Kamar Miran Arshaan ya sokama Sayeed Fayzul-haq wuƙa a ƙirji yaji, dan haka kawai maganar iyalin na Tajwar Eshaan ta soki ransa, murmushi Sayeed Fayzul-haq ya ɗanyi yana kauda kai kamar bashi ya takalosa ba, dama kuma ya fadane da biyu.... ★★..... ★.... Shikam mai gayya da aikin har akai sallar azhar bai gama samun kansa yanda ya kamata ba, dan haka yay sallarsa a ɗaki cikin ƙarfin hali. Rashin fitowarsa salla ya sa su Sayeed Fayzul-haq suka tabbatar da akwai dalili mai ƙarfi daya hana shi fitowar kam tabbas. Ya cigaba da son ganin ya dawo normal, hakan bata samu ba sai kusan gab da la'asar da ya sake komawa Gym ya maida kansa busy, dan wani irin mahaukacin work out yayi, kafin ya fito sharɓan da zufa idanun nan babu alamar rahama yau kam an tsokalo maza. Tsaf yay shiri cikin ɗan sauran ƙarfin da ke jikinsa, dan gaba ɗaya jinsa yake sai a hankali. Haka dai ya daure ya fito domin zuwa massalaci. Iffah dake sharce ruwan alwala da tayo a fuskarta da wani irin sauri ta buɗe idanunta jin an buɗe ƙofar. Ido huɗu sukai da shi, da wani shegen sauri ta maida nata idanun ta rumtse da juyama ƙofar baya, cikin salon nasa na basarwa da shegen miskilanci da ƙasaitar nan tasa shima sai ya ɗauke kai tamkar bai ganta ba. Ta bayanta ya raɓa ya wuce, wasu takardu da ya ajiye ya ɗauka a kan study table ɗin ɗakin ya sake zuwa zai gittata. Tsaye take har yanzu idanunta a rufen ita a dole bata son su haɗa ido. Ƙirjin Iffah bugawa ya dingayi da sauri-sauri jinsa a kusa da ita, idanun ta buɗe kaɗan dan son tabbatarwa. Shi ɗinne dai a gabanta ya zuba mata idanunsa da ke cikin eyeglasses masu ɗan duhu. (Wayyo ni ALLAH) ta ambata a zuciyarta tana maida idanun ta rumtse a daburce ta ce “Barka da rana”. Idanunsa dake a wani irin yanayin da ya tilasta mishi saka gilashin ya ɗan lumshe yana sake buɗewa a kanta. Cikin dakewar muryarsa dake ɗan shaƙe fiye da koda yaushe data sani kamar wanda akaima tilas acan ƙasan maƙoshi ya furta, “After Isha ki sameni”. Idanunta ta buɗe a firgice, sai dai shi tuni ma har yayi gaba abinsa. Dai-dai yana ƙoƙarin ficewa taji kamar ta fasa kuka, amma sai ta haɗiyesa tana ƙoƙarin aro jarumta. A hankali ta furta, “Zanje na ga Ammie to kafin sannan Please”. Cak ya dakata sai dai bai juyo ba har na wasu sakkani. Kin san dai kina a ƙarƙashin umarnin shari'a ne ko?”. Kanta ta jinjina kamar yana kallonta, kafin ta ce, “Eh na sani, alfarma kawai nake nema. Jiya ranta ya ɓaci, matsayinta na mahaifiyata bai kamata na kwanta cikin nutsuwa ba tana fushi da ni. Ina son naje gareta domin neman afuwa”. Gaba ɗaya jijiyoyin jikinsa ne suka ƙarasa saki, wani sanyi na ratsa masa tun daga kan yatsun ƙafa har tsakkiyar kansa. A sannu ya waiwayo ya zuba mata idanunsa. Kallo yake mata irin na kin mamaye komai da komai ɗin nan, a zahiri kam baka isa tantance komai bai tattare da shi, dan fuskar na'a yanda taken nan tsuke tamau. “Ki jira ni”. Ya faɗa kai tsaye dai-dai yana ficewa. Numfashi ta sauke a hankali da yin ɗan baya kamar maijin jiri ta manne da bango, mamaki takeyi, mamakin kanta da komai ma, ta wani gefen kuma ta fara tsoron abubuwan da ke neman cigaba da wajabta kansu a ƙarƙashin mafarkinta, toso ture wannan amma zuciyarta nata ingizata akai, abu mafi ɗaure kai kamar yanda tai mafarkin ta tambayesa zuwan a mafarkin a zahirin amsar da ya bata acan ne anan ma, mi hakan ke nufi? Tayaya ma kanta zai cigaba da ɗauka, gaba ɗaya sai kewar iyayenta ta sake dawo mata sabuwa a zuciya, ta shiga jan ajiyar zuciya hawaye na ciko mata idanu. Iska ta ƙara fesarwa ta buɗe idanunta tana sakin murmushi, murmushi mai ciwo da ita kaɗai ta barma kanta sani sai ALLAH. Sai kuma ta taɓe baki kaɗan da tuno furucinsa. _Wai ta sameshi, to ta sameshi kamar ya? Itakam wace ƙaddara ce ma ta sata amincewa auren mutumin nan? Jibafa yanda yake wani ɗacin rai da ɗa duniya bashi ya gama murje mata lips da jikinta ɗazun ba, halan ma wai ya manta tsiyar da ya aikata ne. (Ko zaki tambayosa) zuciyarta ta ayyana mata. Zabura tai cikin masifa da tsiwa kamar zuciyar tata mutum ce, sai dai kuma batace komai ba aka dai cuna bakin gaba. (😂Gwara dai kiyi shirun ta gidana)........✍️ ______________ Sister's duk wacce batayi anfani da sabulun mg's ba ko kit dinsu inamai shaidamuku anbarku acan baya domin duk wnd yajaraba mg's sai sanbarka duk wani Mai tantama Akan kayan gyaranjiki toh tabbas yacire sabulun mg's domin yahadu bakarya zegyarajiki yafidda dattin fata Dama duk wani matsalan fata duk Wanda kefama da matsalan fata walau pimples ko spot, sunburn acne,stretch mark dama dukkan wani prblm yajaraba mg's bi'iznillah komai zaizama labari bayan jikinku yy fresh zaisa jikinku yy smooth yadinga glowing,gawanda basa San anfani da Mai zaku iya using mg's batare da kunbukaci wani Mai b🤗nd wnn new soap din💣ne,😯 bama cika Baki kujaraba kugane ma idanku domin ance gani yakoriji Kuma siyan nagari maida kudi gida You can check pic👇for the soap reviews🥰 Soap price:4k maiso yy mgn Whatsapp 08062991549 07046881166 07067210195 Call 08064532391 Instagram:glow_with_mgs Facebook: mg's skincare Masu bukatar cream Shima munadashi harda ma complete set nagyaranjiki sannan akwai na amare special Wanda inkinyi using baki Kuma bukatar kiyi Wani gyaranjiki domin keda kanki zaki shaida cewa fatar taki ta wanku tarwai😍08062991549 Munatura Kaya kowani gari dayardar Allah Amma delivery is not free Be part of the glow team😍karkubari abaku lbr👏 ____________________ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (39) .........Zuwa yanzu labarin abinda ke faruwa da iyalan Miran Jasim ya gama kewaye cikin masarautar. Hasalima babu wani ka-ce-na-ce dake kai kawo sama da zancen. Musamman da ya kasance Umm Husam na ƙarƙashin kulawar likitoci har yanzu, duk da dai Alhamdullah sun sami nasarar mata ɗorin karayar data samu a cinyarta. Amma taji mummunan ciwo a ƙashin bayanta da bama a saka ran zata iya ƙara cigaba da takawa da ƙafafunta. Malikat Haseenat ta fita dubasu a asibitin har shi Miran Jasim ɗin dan shima dai ya jigatu a hannun Husam ƙwarai da gaske. Lokacin da take fitowa bisa rakkiyar Daneen Ammarah da hadimanta amintattu irin su Banou tawagar Tajwar Eshaan ke gabato Clinic ɗin shima. Malikat Haseenat ta kafeshi da idanu na tsahon lokaci, yanda yake tafiya ɗaɗɗaya cike da ƙasaita da izza, ga wani mayataccen ƙamshinsa da tun kafin ya iso shi ya iso hancinansu. Sai dai fuskar ciɗin-ciɗin fiye da kullum alamar akwai ɓoyayyar damuwa tattare da shi. Idanu ta ɗan lumshe tana ɗan murmushi da jin tarin ƙaunarsa na sake mamaye zuciyarta. Tana ma jikan nan nata so mai ƙarfin gaske da itama bata san adadinsa ba. Zubewar Hadimanta bisa gwiwunsu ya fargar da ita isowarsa gab da su. Itama ƙasa tai da kanta alamar girmamawa garesa. Tun kusantowarsu wajen idanunsa shima na'a kanta, sai dai bashi da damar tsayawa gareta kasancewar a Shahan-shan ɗin sa ya fito ba jikanta ba. Har cikin ransa yana ƙaunar wannan baiwar, ƙauna irin wadda shi kaɗai ya barma zuciyarsa sani. Sai da suka shige sannan ta dubi Daneen Ammarah tana murmushi. Itama murmushin tai mata sai dai batace komai ba suka nufi motar da suka zo Clinic ɗin a ciki. Fuskar nan a matuƙar tsuke cike da barazanar da ke sake fidda ainahin kwarjininsa yake duban Miran Jasim da gaba ɗaya yake jin ya ruɗe bazai iya ma haɗa ko ido da shi ba. Gaba ɗaya yaron ya sake masa wani kwarjini mai ban mamaki fiye da da. Duk da ya tako zuwa Clinic ɗin ko uffan bai furta ba sai kaifafan idanunsa da ke sakaye a gilashin nan dan ɓoye yanayinsa da ya zuba masa. Sai su Sayeed Fayzul-haq ne ke tambayar lafiyar tasa da yawun Tajwar Eshaan ɗin. Shiko ko sau ɗaya ma bai motsa lips ɗinsa ba a wajen, hasalima shi hankalinsa kamar rabi da rabi ne a tare da su nan kawai. Basu wuce tsaiwar mintuna biyar ba suka nufi ɗakin da Umm Husam take itama. Itako ganin Tajwar Eshaan da kansa yazo dubata sai ta fashe da kuka. Idanunsa ya ɗan lumshe kawai, sai Sayeed Fayzul-haq ne ke bata haƙuri. Nan ɗin ma dai basu wuce mintuna biyar ɗin ba suka fice. Da ga shi sai Miran Arshaan da Sayeed Fayzul-haq suka koma sashensa, sai amintaccen hadiminsa da baya rabo da shi a koda yaushe, jami'an da ke bashi tsaro biye da su kowanne hannu ɗauke da mahaukaciyar bindiga. Tako ina hadimai zubewa suke, sai dai ransu fari tas da ganin sarkinsu duk da ba suna ganin fuskarsa bane. Amma suna jin alfaharin sun taɓa ganinsa, koba komai suna jin shauƙi da sanin fuskarsa sau ɗaya koda bazai sake buɗeta a gare su ba har abada. Shigarsu da ƴan mintuna shugaban jami'an tsaron ya nema iso. Kasancewar Sayeed Fayzul-haq ya san da zuwansa cike da girmamawa yake sanar da Shahan-shan tare da neman afuwar sanar masa a ƙurarran lokaci. Alama yayi ta abashi izinin shigowar kawai. Takaici ya sake kume Miran Arshaan da ke zaune shima. Ya ballama Sayeed Fayzul-haq hararar gefen ido yana ƙwafa a zuciyarsa. Cikin girmamawa shugaban jami'an tsaron ya miƙa gaisuwa, amintaccensa ya amsa a madadinsa. Zaune ya kai a inda Sayeed yay masa nuni, cikin sake risinar da kai na girmamawa ya miƙa files na hannunsa guda uku. “ALLAH ya ƙarama adalin shugabanmu lafiya da nisan kwana masu albarka. Alhamdullah mun kammala binciken da mukai alƙawarin yi yanda ya kamata, sai dai muna mai neman afuwar jinkirin da aka samu bisa wasu dalilai. Wannan files ɗin na cases ɗin ne duka uku. Alhamdullah mun sami nasarar gano hadimin da ya ɗakko Zawjata-almilk daga kurku ya jefata cikin swimming pool, a yanzu haka kuma yana hanunmu dan a daren ranar litinin muka cafkesa yana shirin guduwa da ga cikin masarautar nan. Mun gano shine ta hanyar zanen yatsun hanunsa da muka samu a jikin ƙofar kurkukun daya kasance ɗaya da ga cikin shaidun mu. Ya tabbatar mana da cewar sakashi akayi sai dai shima bai san wacece ba, amma ta jima tana sakashi ayyuka masu kamanceceniya da wannan tun ba yau ba. File na biyu akan kisan Sayeed Khairul-Bashar ne....” Wani irin bugawa mai azabar ƙarfi ƙirjin Miran Arshaan yayi kamar zuciyarsa zata faso ta faɗo. Shugaban jami'ai da bai san yanayi ba ya cigaba da faɗin, “......shima mun gano an kashesane ta hanyar kaisa ɗakin baya da ke a can wajen tsohon kurkukun can akai masa kisan gilla. A binciken da mukai cikin ɗakin ne muka gano zobensa da ɓalin gilashin jikin eyeglasses ɗin idonsa daya fita, tare da suffar hadimin da ya dinga azabartar da shi har ya mutu a gwajin ƙwayoyin idonsa da muka bibiya. Jinkirinmu ya samo asaline ma a dalilin binciko hadimin kasancewar yana rufe fuskarsa ne a lokacin aikata laifin. Shima dai kamar wancan ya tabbatar mana sakashi akayi, sai dai shi yanada matuƙar taurin kai dan yaƙi faɗar waɗan da suka sashi, da alama kuma shi ya sansu sani na zahiri saɓanin wancan.” Fitsari kawai ya ragema Miran Arshaan ya saki, amma illahirin jikinsa tsuma yake yana ƙoƙarin dannewa. Shugaban jami'ai ya cigaba da faɗin, “File na uku tushen samuwar madarar da aka kai sashen Zawjata-almilk ne.....” (Kun mutu Arshaan) zuciyar Miran Arshaan ta faɗa cikin matsanancin tashin hankali. Da ƙyar ya iya haɗiyar busashen yawu da fisgo numfashisa da ke neman suɓucewa da ga gangar jikinsa. Shugaban jami'ai ya cigaba da faɗin, “...madarar ta fito ne da ga sashen gidajen kuduncin wannan daula, dan an ɗauke ta daga can ne zuwa sashen uwar masu gida saboda yin ɓadda kama. Dan haka suspect ɗin mu dole zai kasance a ɗaya da ga waɗan can gidajen guda shida dake a cikin file ɗin. Domin a daren ranar ɗaya daga cikin jami'an mu ya ga wani a suffar ɓadda kama ya fito ta wata ɓarauniyar hanya da muma bamu san da ita ba a gidan nan. Munbi diddigin masu bin hanyar a tsahon kwanakin nan daya tilasta jinkirinmu, mun samu mutane huɗu sai dai har yanzu bamu tabbatar da fuskokinsu ba kasancewar a shirin ɓadda kama suke fitar. Amma hakan ba matsala bane saboda hanyar tabbatar da su ɗin su waye tana a hanunmu muna kan sake tabbatarwane gudun samun kuskure. Albishir dai da zamu bayar akan shi wannan case ɗin a yanzu haka wanda ya samar da dafin macizan yana hanunmu. An kamosa ne kuma a safiyar yau”. A karan farko Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed ya saki wani malalacin murmushi da ya nema sumar da Miran Arshaan da ke jin kamar ya rumtse ido ya gansa a sashen sa ko clinic wajen Miran Jasim ko ma wajen boka Barbushi shi ma bai san ina yafi so yaga kansa ɗin ba. Sayeed Fayzul-haq kam kansa kawai yake faman jinjinawa ransa na mamakin waɗan nan abubuwa abin kamar wani shirin film. Amintaccen hadimin Tajwar Eshaan kam abun ya masa daɗi, musamman ganin murmushi mafi tsadar gani a fuskar shugabansa adali, sannan koba komai a su kansu ma amintattun hadimansa suna fatan kowaye ɗin kodan wahalar da suka fuskanta ta kusan wata guda a kurkuku. Shi dama ya daɗe daji a ransa Zawjata-almilk bazata iya aikata abin nan ba sai da jagorancin wani sheɗanin da ya fi ƙarfinta. Dan haka kawai yake jin ƙaunarta matuƙa musamman da ya fahimci wani abu ɓoyayye da ke tare da shugabansa game da ita duk da yana ƙoƙarin ganin ya danne. Amma kuma shi a yanzu babu wanda ya kaisa sanin wanene Tajwar Eshaan, koba komai barci ne kawai ke rabasu sai ko idan ya shiga ciki ko ya yini bai fito a bedroom ba. Kuma ko'a hakan tabbas tabbas sai ya gansa a yinin sama da sau biyar. Zai iya cewar da ga matarsa a yanzu sai shi ko a mafi ƙololuwar ganin Tajwar Eshaan ɗin. Wani irin kirari ya shiga jeroma shugaban jami'ai, tare da jinjinar ban girma na ƙoƙarin sa da yawun Shahan-shan da bayan murmushi babu alamar zaice wani abu. Magana da ga bakin amintaccen Tajwar Eshaan tamkar kai tsaye ne da ga bakin sa, dan yana cewa ne da say ɗin sa bawai raɗin kansa ba. Sannan koba komai shima a idanunsa Tajwar Eshaan ɗin ya saki murmushin nan da zai iya rantsuwa bai fi a karo na ƙalilan kenan ya taɓa gani ba. Hakan na nufin da gaske Shahan-shan ɗin ya yaba da ƙwazon jami'an tsaron gidan koda bai furta ɗin ba. Jiƙewa iya jiƙewa jikin Miran Arshaan ya gama yi da zufa. Ga wani irin hajijiya da idanunsa suka fara gani. Kaɗan ya saci duban Tajwar Eshaan da babu alamar hankalinsa a kansa yake, hakama Sayeed Fayzul-haq. Yawu ya haɗe masu kaurin da har yanajin suna kamar ɗaɗa masa maƙoshi. Da ƙyar ya iya jarumtar cigaba da zama har shugaban jami'an tsaro ya gama ya fice. Babu alamar Tajwar Eshaan zai sake cewa wani abu akan batun, hakan yasa shima Sayeed Fayzul-haq haɗiyewa ya ɗakko zancen Miran Jasim da iyalansa, sai ɗansa dake a sashen Malikat Haseenat har yanzu. Ba ƙaramin dauriyar danne tashin hankalinsa yay wajen saka musu baki ba gudun kar Tajwar Eshaan ya harbo jirginsa. Dan ya mugu-mugun sanin hatsabibancin yaron nan, babu abinda ya baro a halin ubansa sai ma finsa taurin kai da yayi. Tattaunawar ta ɗan jasu wani lokaci dan har gab da magrib sannan suka tashi..........✍️ ______________ Sister's duk wacce batayi anfani da sabulun mg's ba ko kit dinsu inamai shaidamuku anbarku acan baya domin duk wnd yajaraba mg's sai sanbarka duk wani Mai tantama Akan kayan gyaranjiki toh tabbas yacire sabulun mg's domin yahadu bakarya zegyarajiki yafidda dattin fata Dama duk wani matsalan fata duk Wanda kefama da matsalan fata walau pimples ko spot, sunburn acne,stretch mark dama dukkan wani prblm yajaraba mg's bi'iznillah komai zaizama labari bayan jikinku yy fresh zaisa jikinku yy smooth yadinga glowing,gawanda basa San anfani da Mai zaku iya using mg's batare da kunbukaci wani Mai b🤗nd wnn new soap din💣ne,😯 bama cika Baki kujaraba kugane ma idanku domin ance gani yakoriji Kuma siyan nagari maida kudi gida You can check pic👇for the soap reviews🥰 Soap price:4k maiso yy mgn Whatsapp 08062991549 07046881166 07067210195 Call 08064532391 Instagram:glow_with_mgs Facebook: mg's skincare Masu bukatar cream Shima munadashi harda ma complete set nagyaranjiki sannan akwai na amare special Wanda inkinyi using baki Kuma bukatar kiyi Wani gyaranjiki domin keda kanki zaki shaida cewa fatar taki ta wanku tarwai😍08062991549 Munatura Kaya kowani gari dayardar Allah Amma delivery is not free Be part of the glow team😍karkubari abaku lbr👏 __________________ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (40) ______________ Lifestyle_Nig for everything that makes your lifestyle complete ..👌 Furnitures Decoration Kitchen items & Boutiques Quality is our watch word at lifestyle shop kano/kaduna Shop no 58 kabuga housing estate janblo kano on the road in between first gate and second gate near kashe magana suya spot Instagram Lifestyle_Nig Facebook Lifestyleng Tik tok Lifestyle_Nig Delivery nation wide 08036414048 Muna tura kaya ko ina cikin aminci da yardar Allah _______________ ..........A bala'i bala'in matsanancin tashin hankali Miran Arshaan ya nufi clinic, yaji daɗin samun Miran Jasim da ke tambayarsa lafiya ganinsa a firgice shi kaɗai. Maimakon amsa masa sai ca yay, “Kasa a sallameka da ga clinic ɗin nan a daren nan”. Cikin kallo mamaki Miran Jasim ya ce, “Kamar ya nasa a sallameni, kai bakaga yanda shegen yaron nan nawa ya fasan kai ba. Ga wuyana tsabar yanda ya nema karyashi sai da aka samun wannan abun”. Ya kare maganar da nuni da abin wuyansa. Tsaki Miran Arshaan yayi yana ji kamar ya sake shaƙesa shima. “Shaƙar da Husam ya maka ba komai bace akan wacce ke tunkaro rayuwarka”. Ya ɗan ƙara waw-wai-gawa alamar gudun kar wani ya jisu. Cikin sake ƙasa da murya ya cigaba da faɗin, “Idan ka bari ka sake awa biyu anan nadamace ta har abada zata zama abokiyar rayuwarka in har ma matsiyacin yaron nan ya Barka da ran naka kenan”. Yana ƙare faɗa ya ficewarsa da ƴar sassarfa dan dama yay amfani da lokacin shiga sallar magrib da akayi ne...... ★.... ★.... Bayan idar da sallar isha'i koda ya nufi sashensa maimakon ƙarasawa ciki sashen Malikat Haseenat ya nufa ta ɓoyayyar hanya. Tayi sallamar wutiri kawai sai ganinsa tayi. Ba yau ya saba mata irin wannan zuwan ba na sirri, sai dai yafi yinsa a bayan sallar asuba. A nutse take dubansa bayan shafa addu'ar data taƙaita cike da kulawa. Shima sai ya taso a hankali da ga zaman ƙasaitar da yay a bakin gadonta ya dawo inda take kan lallausan carpet ɗin dake fes babu datti sai ma tashin ƙamshi da yake da ɗaukar ido na sabunta. Ga taushi matuƙa da ko'a ido zaka iya fahimtar hakan. “Barka da dare Jadda-ti”. Ya faɗa a can ƙasan maƙoshi ya na kaiwa kwance bisa carpet ɗin ya ɗaura kansa kan cinyarta ya wani lumshe idanunsa da a kallo ɗaya ta fahimci damuwar dake tattare da shi a cikinsu tama ƙaru fiye da ɗazun. Murmushi ta saki mai sanyi a ranta tana faɗin, (Yau kuma ƴan shagwaɓan ne a kusa haka), a zahiri kam hanunnta kawai ta ɗaura kan ƙyaƙyƙyawar baƙar sumar sa siɗik ta fara ɗan tausa masa kan kaɗan-kaɗan. Idanun ya sake lumshewa da ƙyau har yanajin barci-barci na ɗibarsa. Tsahon mintuna kusan uku sannan ta magantu cike da kulawa. “Waya taɓamin kai Niger?”. Shiru bai motsa ba har wasu sakanni. Kafin ya buɗe idanunsa da suka ɗan fara shanyewar barci a hankali. Sai kuma ya ɗan ɓata fuska yana ƙoƙarin kaudawa gefe. Riƙo fuskar tai cikin tafukan hanunnta tana murmushi da faɗin, “Oh oh beautiful Hafidi na faɗamin kaji”. Idanunsa ya ɗan lumshe da jujjuya mata kansa kaɗan ya motsa lips ɗin da ƙyar da maganar nan nasa kamar ta dole, “Kawai ina son jin ɗuminki ne”. “Uhyim, ita kuma Hafida-ti na aka barta ita kaɗai”. Shiru yay kamar bazai tanka ba. Sai kuma ya yamutse fuskar daɗa duniya har cikin zuciyarsa ne ya wani kauda kai gefe, “Tanada hayaniya, gata da surutu”. Mi Malikat Haseenat zatai banda dariya. Cike da nutsuwarta da ƙasaita ta shiga yin abinta. Ta ce, “Wayyo ni kai kuma gashi baka son hayaniya da surutu. Nikam ai ta burgeni, gara ta koya maka hayaniyar tata da surutun ko zamu samu ka dinga amsa mana magana biyar cikin goma. Naji daɗin hakan, dan itace dai-dai da kai”. A yanda take maganar zaka san lallai tana matuƙar jin daɗin. Shima dai acan ƙasan ransa murmushi kawai yake, dan ya sake tabbatar da kakar tasa mafi soyuwa a ransa na matuƙar ƙaunar ƴar hayaniyarsa da gasken gaske. Dama shi baya shakku a kanta, dan duk abinda Malikat Haseenat ta so to da gaske tana sonshi ne har cikin rai, idan kuma ta nuna ƙi to da gaske take ƙin nasa. Kamar tasan abinda yake tattaunawa da zuciyarsa ta cigaba da shafa kansa har yanzu da sauran murmushin dariyar da tai akan fuskarta. “Eshaan da gaske ina son yarinyar nan har cikin raina batare dana san dalili ba nima. Halayyarta kuwa na tuna min wasu abubuwa masu yawa. Yarinyar nada shiga rai, sannan tana da ɓoyayyun abubuwan ban mamaki tattare da ita. Karo na uku kenan ina aikawa nemomin iyayenta batare da kowa ya sani ba amma ana tabbatar min wai basa gidansu, a binciken ƙarshe ne na samu cikakken bayanin dalilin barinsu gidan, nasaka an bibiyar min kakaninta a ƙauyensu da aka tabbatar min su suna nan amma sai suma aka taki rashin sa'a. Na fara jin tsoron kar wani a cikin masarautar nan ne ya shirya cutar da su, dan tabbas abinda ya faru tsakaninka da yarinyar nan aike ne.. Bazaka tabbatar da hakan ba sai ka kusanta kanka da ita, kusanci mafi girma da a yanzu shine babban mafarki na, ina fata kafin na bar duniya naga jininka, a koda yaushe kuma na ayyana hakan zuciyata hoton yarinyar nan take kawo min matsayin uwar ƴaƴanka” Yanda muryarta ke fita da sautin tabbatar da abinda ke zuciyarta ne ya saka shi ɗan buɗe idanu kaɗan yana kallonta, sai kuma ya tashi zaune shima a serious ɗin sa, shiru babu alamar zaice wani abu, ita har ta fidda rai ma da cewar tasa. Sai kuma a hankali taji sassanyar muryarsa ya ce, “Jaddah”. “Yes Niger” Ta amsa masa da kulawa. Kaifafan idanunsa masu nutsuwa da haske mai cika idanu da a yau launinsu ya ɗan surka ya zuba mata. Murya a can ƙasa maƙoshi da kamar an masa tilas ya jefa mata tambayar da ba ita tai tsammanin ji da ga garesa ba. “Tambarin baƙi mai kamar tawadar ALLAH duk wani zuri'ar gidan nan ke da shi ko wasu ne a ciki?”. Yanzu kam kallonsa take da mamaki matuƙa da ya gaza ɓoyuwa har a kan fuskarta. “Ban san miye dalilinka na wannan tambayar ba, ko kake son sani. Faɗamin miya faru?”. Kansa ya girgiza mata alamar babu komai, sai kuma a hankali ya ce, “Ina son sani ne”. Sam zuciyarta bata aminta da haka kawai bane, sai dai bazata matsa da son ji ba dan yana da hujjar ƙin faɗar, idan yaso wataran da kansa zai sanar mata. “In dai daga zuri'ar Aliy Qutb (mahaifin kakanka Abdull-Majeed) ka fito wannan tambarin shike tabbatar da kai. Sai dai bawai haka kawai ake gane kai ɗan zuri'ar bane da'an gansa. Akwai ajiyayyun hujjoji da ke tabbatarwar domin ana haihuwar jariri bayan yanke masa cibiya shine abu na biyu da ake duba masa. Yin wannan tambari a jikin duk wani jinin ahalinku ya samo asaline a dalilin kakanku na huɗu da yake da shi, mahaifin Aliy Qutb kenan, shi kuma Aliy sai yazam bashi da shi lokacin da aka haifesa amma sauran yan uwansa na baya duk sukazo da shi, maƙiya sai suka riƙe wannan hujjar a lokacin da za'a naɗashi sarki suka shigo da wata magana mai ban tashin hankali data girgiza masarautar nan baki ɗaya, har sai da ta kai anbi diddigin jinin Aliy da mahaifinsa. Wannan al'amari shi kuma sai ya riƙesa, bayan hawansa mulki duk wanda aka bincika bashi da tambarin sai an masa da wata alama da ke tabbatar da a cikin masarauta aka masa da hujjojin masu ƙarfi a rubuce. Idan aka haifi jariri kuma bayan yankan cibi shine abu na biyu da ake masa idan har babu shi...” Idanunsa da ya zuba mata tun fara maganar ya ɗan motsa kaɗan zuciyarsa na wani irin bugu da sauri-sauri. Amma a zahiri bazaka taɓa fahimtar a wane yanayi ya ke ba. Murya acan ƙasan maƙoshi ya sake furta, “An cigaba da samun masu tambarin da yawa ne? Ko wanda akai mawa ne suka fi rinjaye bayan farawar?”. Shiru na wasu sakkani Malikat Haseenat batace komai ba, sai kuma taja ajiyar zuciya. “I to ni dai a yanda na samu labari a ɗan binciken tarihi wani lokaci akan samu yawaytar masu shi, wani lokacin kuma sai kaga anata haihuwar marasa shi, al'amarin kamar yana tafiya a ƙarni-ƙarni ne, amma kaga tashi kaga”. Babu musu ya miƙe kamar yanda ta buƙata, da taimakonsa ta hau wheelchair ɗinta, kai tsaye inda ƙaton hoton kakansa Tajwar Abdul-majeed ke manne kamar ka masa magana ya amsa ta nufa. Yatsanta manuniya ta kai a saitin fuskar hoton ta shafa, zuuu ƙaton frame ɗin hoton ya shiga wani naɗe kansa kamar ana naɗe tabarma da ga sama yayo ƙasa. Ƙofa ce ta bayyana, bai wani nuna mamaki ba dan ya riga yasan da kofar nan tun ba yanzu ba, dan shi wannan sashe da Malikat Haseenat ke rayuwa yanzu a ciki asalinsa sashen kakansa ne Tajwar Abdul-majeed, shiyyasa akwai sorrika masu yawa a cikinsa da ita kaɗai tasan da su sai wanda kuma taso ya sani. Da taimakonshi ta shiga yana biye da ita a baya. Ɗakine madaidaici mai ɗauke da tarin littattafai kala-kala. Gurin yayi ƴar ƙura alamar bawani shigarsa ake akai-akai ba. Kekenta ta wulwula zuwa bangaren arewa tana bin jerin manya-manyan littattafan wajen da kallo, shi dai yana tsaye da ga tsakkiyar ɗakin yana binta da kallo a ƙasaitance. Juyowa tai ta yafitoshi da hannu, cikin takun nan nasa na izza da ƙasaita ya nufeta. Littatafai biyu masu girma da tudu sosai-sosai ta nuna masa. “Ciro min su”. Hannu ya kai a hankali yana ɗan yamutse fuska ya cirosu, duk sunyi ƙura, amsa sai ta shiga karkaɗesu, yanda ƙurar ke tashi sama ya sashi ja da baya har sai da ta kammala. Ƙara yafitosa tai da hannu ya sake dawowa gabanta, ta kamo tattausan hanunsa cikin nata ta ɗaura masa littattafan. “Wannan zasu taimaka maka samun duk amsar da kake nema, duk wanda ke cikin zuri'ar nan da aka haifa da tambarin ko akai masa akwai bayaninsa anan. Ka kula da ƙyau suna da muhimmancin da ba kowa yasan inda suke ba a cikin wannan masarautar”. Kai ya jinjina mata yana lumshe idanunsa da buɗewa a kanta...... ★★...... Taso share umarninsa na ta samesa bayan sallar isha'in amma zuciyarta taƙi bata haɗin kai. Sai ma ta samu kanta da yin sabon wanka da canja kayan jikinta zuwa wata ƙyaƙyƙyawar abaya mai laushi da santsi kalar fari da akaima adon manyan fulawa da golden mai ɗaukar idanu, ga stones taji farare da duk inda ta motsa sai sunyi ƙyalli kamar wani diamond. Samun kanta tai da nutsuwar naɗa veil ɗin ya zauna ɗam a kanta har wani ɗan gashi siriri data zubo ta gaban goshin na reto a fuskarta. Tayi ƙyau matuƙa, dan ko maƙiyinta sai yaji ta burgesa kasancewar Iffah yarinya ce mai shiga rai, ga ta ƙyaƙyƙyawa komai nata dai-dai da ita. Yau dai har an ɗauki turarurrukansa za'a bulbula sai kuma aka fasa. A cikin wanda tai shopping akai amfani da su, sai kuma aka koma dai aka saka nasan ƙaɗan. Yanda tayi haɗin sai ya bada wani irin ƙamshi mai sirrin da ko shi mai gayya mai aikin da wahala ya iya gane ainahin nasa ƙamshin. Taku take a nutsenta kamar wata ƴar wahainiya. Bedroom ɗin jiya ta nufa dan tafi tunanin samunsa a can duk da bata da tabbas.........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (41) _______________ Lifestyle_Nig for everything that makes your lifestyle complete ..👌 Furnitures Decoration Kitchen items & Boutiques Quality is our watch word at lifestyle shop kano/kaduna Shop no 58 kabuga housing estate janblo kano on the road in between first gate and second gate near kashe magana suya spot Instagram Lifestyle_Nig Facebook Lifestyleng Tik tok Lifestyle_Nig Delivery nation wide 08036414048 Muna tura kaya ko ina cikin aminci da yardar Allah ______________ .........Da ƙyar ta iya danne zuciyarta cikin rumtse idanu ta murɗa handle ɗin ƙofar ta shiga. Kamar jiya ɗakin diff babu yawaitar haske sai wani ni'imtaccen ƙamshi mai saka zuciya nutsuwa da sanyin ac. A hankali ta saki ajiyar zuciya tana mai bin ko'ina da kallo. Babu alamar akwai mutum a ciki kam duk da ita dai tana ji a jikinta yana nan. Tafiya ta cigaba da yi kamar wadda ta shigo sata da sanɗa tana ɗan lalleƙawa. “Bani shayi..” Cak ta tsaya ƙirjinta na wani irin dif-dif, sai kuma ta juyo da sauri domin tabbatarwa. Shi ɗin ne dai zaune cikin ƙyaƙyƙyawar kujerarsa mai ƙyawun gaske da laushi, a yanda yay zaman ƙafa harɗe bayansa kwance a kujerar sai ka ɗauka ma idanunsa a lumshe suke. Sanye yake da ga shi sai bathrobe da tausasan slippers alama wanka ya fito, cikin sauri ta sake juyawa tana rumtse idanu duk ta daburce. Sai da ta ɓata minti guda tsayen kafin tayi dauriyar jan ƙafa da ƙyar zuwa centre table na tsakkiyar kujerun da ke gefe kaɗan inda taga butar shayin. Mita take tayi a zuciyarta harta kammala zubawa ta zabga zuma a cikin ɗan kawai neman magana. Murmushi ta saki na mugunta ta ɗauka cup☕ ɗin da shayi keta turiri ta nufesa. Sai dai idanunta a rissine dan kunyar kallonsa take a haka duk da bawai jikinsa a buɗe bane. Tana ƙoƙarin ajiyewa a ɗan coffee table ɗin gabansa ya miƙa mata hannu alamar ta bashi. Miƙa masan tai har yanzu idanunta a ƙasa. “Thanks”. Ya faɗa a hankali yana kai kofin kan lips ɗinsa. Da sauri ya janye jin zaƙin zuman ya wani ratsa masa harshe zau-zau. Dai-dai kuwa da ɗaga ƙafar Iffah zata bar wajen. A hankali ya riƙo hanunta cikin nashi, ta rumtse ido da ƙarfi batare da ta juyo ba. Matsota yay jikinsa, a bazata ta jita zaune ɗare-ɗare a cinyarsa. Da sauri ta zabura zata miƙe ya maidata ya zaunar. (Ya ALLAHU wannan mutumin yana lafiya kuwa?) ta faɗa a ranta kamar zata saki kuka. “Haka ake haɗa shayi dama?”. Wani irin yamutsawa tsigar jikinta tayi saboda yanda yay maganar a saitin kunnenta da sassanyar muryar nan tasa da a yau gaba ɗaya yinin take jinta a shaƙe. Kasa cewa komai tayi, sai mutsu-mutsun son tashi shiko yaƙi yarda ya bata damar hakan. Sai ma hannunsa da ya saƙalo takan cikinta ya ɗaura kan nata da ke wajen tana ƙanƙame jiki. Tare da sake matsota jikinsa bayanta ya manne da ƙirjinsa. Ɗayan hannun kuwa shayin ya ɗauka ya kawosa bakinta. “Hhaah!”. Ya faɗa babu alamar wasa tattare da shi. A shagwaɓe ta ce, “Ni bance zan sha shayi ba fa”. “Ko?”. Ya faɗa cikin sigar tambaya yana ɗage gira sama. Sai kuma ya shiga yin sama da hannunsa zuwa saman jikinta, kansa kuwa na'a kan kafaɗarta yana wani irin kalan shinshinar ƙamshinta. Daburcewa tai duk da sautin fitar numfashinsa kawai take iya ji a kunnenta veil ɗin data naɗa ya lulluɓe wuyanta. Hannun tai saurin riƙowa ta damƙe, cike da in ina ta furta, “Za..zan sha kayi haƙuri”. Ɗan murmushi ya saki a karo na farko, batare da ya ce komai ba ya sake kai kofin bakinta. Ita kanta sai da ta ɗan rumtse ido jin yanda zaƙin ya ratsa mata harshe. Dan abu mai zaƙi bai cika damun Iffah ba. Baifi kurɓa uku ba tai ƙoƙarin kauda kanta gefe. Hannun ya sake ƙoƙarin kaiwa sama, da sauri ta riƙe kamar zata saki kuka ta ce, “Zan sha fa”. Nan ma ƙin tanka mata yay ya sake kai kofin lips ɗinta. Babu yanda ta iya dole sai da ta shanyeshi tas. “Ai na shanye”. Ta faɗa a marairaice tana ƙoƙarin janye hannunsa da ga jikinta. Amma sam yaƙi bata damar hakan. Sai ma kofin da ya ajiye ɗayan hannun ma ya kawo shi kan ƙugunta sai tin inda taji ciwon ya ɗan murza. Zabura tayi dan wajen har yanzu akwai zafi mai raɗaɗi saboda ya tsuma bata bari an murza ba. Sake maidata yay ya zaunar, yanda zafin ke ratsata sai batama san sanda ta maƙalƙalesa ba har ƙafafunta ta naɗe a jikinsa, hannayenta duka biyu kam ta saƙalosu a wuyansa tare da cusa kanta a ƙirjinsa da bathrobe ce kawai. “Karyani kike son yi ne?”. Yay maganar acan ƙasan maƙoshi kamar mai mura da son danne abinda ke ratsashi. Baki ta ɗan tura gaba tana ƙara cusa fuskarta ta gefen wuyansa, saukar numfashita a wajen gaba ɗaya ya ƙara hargitse masa lissafi har jikinsa na wani irin yamutsawa. Amma sai ya dake kamar yanda ya saba. Sai dai tambaya da ya sake jeho mata da muryarsa dake ƙara shaƙewa. “Kinyi salla?”. “Uhm”. Ta faɗa itama kamar wadda aka shaƙe. “Zaki tayani tawa?”. Ya sake faɗa shima a ƙasan maƙoshin yana ƙoƙarin dai-daita fuskarta da ke a kan kafaɗarsa da tashi. Bata da zaɓin da ya wuce ɗaga masa kai jikinta na tsumar da har yana ji. Tausayi da dariya take bashi, a ransa kam faɗi yake (Stubborn girl matsoraciya). A zahiri kam cak ya miƙe tsaye da ita a hannunsa, sake ɓoye fuskarta tai da cusa kai a ƙirjinsa jinta take kamar ta saki ihu dan kunya. Har cikin bayin ya kaita ya dire gaban tap, yana tsaye a bayanta ya kai hannu ya kunna mata..... Da kallo ya bita lokacin da suke fitowa ganin tana ɗan ɗingisa ƙafarta. Da alama dai faɗuwar da tai ɗin har yanzu na damunta. Baice komai ba kamar yanda itama taƙi yarda su haɗa ido. “Ina zuwa”. Ya faɗa ƙasa-ƙasa yana raɓata ya wuce, cikin closed room ɗin sa ya nufa, ta bisa da kallo ta gefen ido har sai da ya ɓacema ganinta ta saki ajiyar zuciya da kaiwa zaune a table ɗin gaban gadon mai laushin tsiya. Bata gama dai-daita ba ya sake fitowa cikin jallabiya kalar ash sai ɗaukar idanu take ga wani sirrintaccen ƙamshi. Shi da kansa ya shimfiɗa musu sallaya. “Mi zaki roƙa mana?”. Ya faɗa yana ɗan juyowa shanyayyun idanunsa a kanta. Fuska ta ɗan yamutse batare data kallesa ba kanta tsaye ta furta “Naga iyayena”. “Nifa?”. Ya sake tambaya har yanzu idanun dai na kanta. Sai da ta ɓata fuska da tura baki gaba sannan ta furta, “Kai mi kake buƙata kuma a duniya?”. (Tofa wata sabuwa) ya ayyana a zuciyarsa. A zahiri kam sai ya murmusa kaɗan da ɗan ƙara matsawa kusa da ita gab ya kai yatsunsa biyu kan haɓarta ya ɗago fuskarta da ƙyau. Lumshe idanunta tayi. Bai damu ba ya cigaba da kallonta sosai. “K! Mana”. Idanu ta waro waje da sauri. Sai ya waske, ya cigaba da faɗin, “K! Nake buƙata ki haifamin yara masu kama da ke?”. Baki ta laɓe da kauda kanta gefe ta ce, “Hu'um ALLAH ya kiyaye”. “Sai dai kuma na gaba”. Ya faɗa yana sakin mata fuska ya gyara tsaiwarsa. Itama gyarawar tai tana ƙara takwaf-takwaf da fuska, dan badan tana tsoron karya maimaita mata na jiya ba da tuni ta fece a binta. Sun gabatar da salla raka'a hudu da bibbiyu, ya kwararo addu'oin da suka sata jin nutsuwa a ranta harda ƴan ƙwallarta da bata san na minene ba. Bayan sun idar tana ƙoƙarin miƙewa ya riƙota. Bata da yanda zatai dole ta koma ta zauna a tunaninta wata maganar zai mata. Sai taga ya ɗaura farin hannunsa sol da ke ɗauke da dogayen farce ƙal-ƙal a saman ƙafarta, a hankali ya janyo ƙafar a saman tafin hannunsa ya ɗan riƙe yatsun, ɗayan kuma ya tallafo diddigen ya ɗagota gaba ɗaya ya ɗaura saman ƙafarsa da ya tanƙwashe. Kaɗan ya rage numfashin Iffah ya ɗauke dan mamakinsa, Shiko ko'a jikinsa ya shiga murza ƙafar a hankali cikin salon kulawa. Da sauri ta ɗan ɗaura hanunta a kan nasa tana narai-narai da fuska. “What?”. Ya faɗa yana tsareta da idanunsa da suka wani ƙanƙance sosai a kanta. Kamar zata saki kuka ta ce, “Zafi”. Komai bai sake ce mata ba ya ɗauke kansa cike da basarwa ya cigaba da murza mata ƙafar. Tsahon minti biyu kafin ya ajiye ƙafar ya miƙe. Itama miƙewar tai ƙoƙarin yi taji kawai anyi cak da ita an dire saman gado shima ya kai zaune gefenta. Man zafi ya ɗauka a side drawer ya sake kamo ƙafar ya shafa mata, ita dai tayi kurum yanzu sai binsa kawai take da kallo dan ƙafar ya fara sakin mata. Hannunsa ya janye yana ƙoƙarin rufe kwalban suka haɗa ido. Da sauri ta maida nata ta risinar da faɗin, “Thanks”. Yanzun ma komai baice ba ya miƙe, ita kuma ta zubama ƙafar ido tana sauke ajiyar zuciya. Bayan kamar minti biyu tana kan ƙulla shawarar barin ɗakin ya dawo inda ya tashi hannunsa ɗauke da lap-top da kofin shayi. Laptop ɗin ya ajiye a table ɗin gabansu tare da juya mata fuskanta batare da yace komai ba. Zamansa ya gyara cike da ƙasaita ƙafa ɗaya ƙan ɗaya ya ɗauka cup ɗin shayinsa ya kai baki yana wani ɗan lumshe idanunsa da ke mata kallon nan dai dake hanata sukuni... Itama ta gefen ido take kallonsa yanzu, a zahiri kam tayi wani irin gefe da fuska ita a dole ba kallonsa take ba... “Autah!”. Wata sassanyar murya da ko a cikin tsakkiyar barci ta jita a kunenta bazata taɓa manta mai ita ba. Ƙirjinta ne yay wata irin yankewa ya faɗi, sai kuma ta juyo da sauri jin an sake kiran sunan nata. Idanu huɗu sukai da Ummu, Babiy a gefen damarta, Hanash gefen haggunta. Kamar wadda ta firgita ta miƙe a zabure jikinta na rawa. Sai kuma ta dubi Tajwar Eshaan da ke zaunensa kamar baima san mike faruwa ba. Dan shayinsa yake sha a hankali cike da nutsuwa idanunsan nan a lumshe. Kai ta fara girgizawa, sai kuma ta dubi fuskar laptop ɗin. Still dai Ummu ɗin ta ce, da Hanash da Babiy data gama yarda ta rabu da su har abada. Sai Kaka da Iyyani da suka ƙaru. Sai kawai ta diro a gadon ta durƙushe gaban laptop ɗin ta fashe da kuka. “Dan ALLAH gaskiya ne ko mafarki nake? Gizo kuke mun ko video recording ne aka ɗauka?”. “Live ne auta. Video call ba mafarki kike ba”. Hanash ya faɗa fuskarsa shimfiɗe da murmushi. Yi tai kamar wadda tai suman wucin gadi, sai kuma ta dubi Tajwar Eshaan baki sake. Idonsa shima a kanta suke, ya sakar mata wani shegen murmushin da kanne mata ido ɗaya ya ɗauke kai..........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (42) _____________ Lifestyle_Nig for everything that makes your lifestyle complete ..👌 Furnitures Decoration Kitchen items & Boutiques Quality is our watch word at lifestyle shop kano/kaduna Shop no 58 kabuga housing estate janblo kano on the road in between first gate and second gate near kashe magana suya spot Instagram Lifestyle_Nig Facebook Lifestyleng Tik tok Lifestyle_Nig Delivery nation wide 08036414048 Muna tura kaya ko ina cikin aminci da yardar Allah ______________ .........Zubewa tai a ƙasan lallausan carpet ɗin wajen da ƙyau kamar wadda aka zarema dukkan kuzari. Duk da basu san mita kalla ba tai wannan irin zubewa zaune baki ɗaya duk sai suka saki dariya. Kaka yace “Rigimammiyar yarinya har yanzu ɗin baki yarda ba dai?”. Kuka ta sake fashewa da shi a karon na biyu kamar wadda kaka yay ma allura. Idonta kan Laptop ɗin ƙuri tace, “Kaka! Babiy! Iyyani! Ummu! Hanash Akhi. Dama duk kuna raye? Kuna raye kukai nesa da ni?. Kuna raye nake kuka babu dare babu rana ba mai share mun? Miyisa haka? Why! Why Iyayena? Miyasa akacemin kun mutu har yanda aka kasheku aka nuna min......” Wani irin kuka mai ratsa zuciya ya sake kufce mata. Idanunsa kawai ya lumshe yana ɗan matsesu da ƙarfi, dan har tsakkiyar zuciyarsa yake jin kukan. Ga wani abu na zaburo masa tun daga tsakkiyar kai har yatsan ƙafa. Jin zata ɓallo masa ruwa ya miƙe da ɗan sassarfa. A zahiri kam babu abinda mai kallo zai iya gani sai tarin nutsiwarsa da cikar kamala. Shiko shi kaɗai yasan sirrin dake tattare da baɗininsa. Sirrin da yake adanawa tsayin shekaru duk tsananin bamai iya ganosa akan fuskarsa. Da ga shi sai UBANGIJINSA. Sai amintaccen manomin ganyayyakin shayinsa da yake sha domin cigaba da binne raɗaɗin sirrin nasa. Jikin glass window ɗin ɗakin koma ace bango dan kamar da shi ne gaba ɗaya akai ginin sashen nasa ya ƙarasa. Huci yake faman firzarwa a jajjere, idanunsa da sukai wani irin kaɗawa launinsu ya canja nabin wajen masarautar dake ƙwanyar da haske tako ina da kallo. Babu yawan zirga-zirgan mutane, sai masu tsaro tako ina dake kaikawo kowanne da makami a hanunsa, dan tun abin nan na ƙarshe da ya ƙara faruwa da Iffah aka sake ninka tsaron gidan tako ina. A ɓangaren Iffah kam kalamanta sun matuƙar karya zukatan su babiy, tuni suma sun fara share hawaye musamman Ummu da Iyyani. Kaka dai murmushi kawai yake da bin ƴar jikallen tasa da yake matuƙar so da kallo kawai. Haka ma Babiy ya kafeta da idanu zuciyarsa cike da tausayinta da so. Iffah'r sa jaruma ce, amma kuma mai rauni ce. Kura ce, ga tsoro ga ban tsoro. Murmushi ya saki a karo na farko shima, kafin a hankali ya katse koke-koken nasu. “To ya isa haka ko? Wani ya akai? mi akayi? Duk ya wuce Fhareedah kinji, kiyi haƙuri bamuyi nesa da ke ba dan son zuciyarmu. A duk motsinmu kina ranmu. Ƙaddara ce ta rabamu dake badan mun so haka ba. Amma ki gafarcemu kinji autan Babiy. ALLAH yay miki albarka, ya cigaba da baki kariya”. Hawayenta ta shiga sharewa tana gyaɗa kai, haka take sam bata da gardama ko jayayya. Dan bata taso taga na sama da ita nayi ba. Sai da ta share hawayenta tas sannan ta sake kallonsu. Murmushi ta saki a yanzu kuma, cike da jin daɗin ganin sun canja mata gasu fas-fes da su. Gaishesu ta fara ɗaya bayan ɗaya, kowanne yana amsa mata cike da kulawa da ƙauna. Su kansu duk ta sauya musu, gani suke ta ƙara musu girma a ido, dan ma tasha wahala a kwanakin nan. Ga wani ƙyau na musamman ta ƙara da uban haske kamar mai yaron ciki. A ɗan marairaice ta ce, “Amma Kaka akace min duk an kashemin ku?”. Dariya ya ɗanyi cike da dattakonsa. “Uhm uhm Iffatu duk gudun son tabbatar da ƙaddarar wani ga masu buri ai dole suyi haƙuri hukuncin ALLAH da zartarwarsa. A tunaninsu kam mun mutum, sai da wani bawan ALLAH damu kammu har yanzu bamu san waye ba ya tallafi rayuwarmu ya ƙuɓutar da mu..” Da sauri Iffah ta kai dubanta inda Tajwar Eshaan ke tsaye har yanzu jikin window. Sai kuma ta sake maidowa ga su Kaka. “Har yanzu kuma baku san waye ba da gaske? To amma ya akai nake wannan video call ɗin da ku kuma?”. A yanzu kam Babiy ne ya bata amsa. “Har yanzu bayan Barrister Abdallah ba mu san takamaimai wanda ya jagoranci fiddomu zuwa wannan ƙasar ta Saudiya ba. Waya kuma ance mana kawai zamuyi magana da ke ne. Mu harma mun fara tunanin ko kece”. Idanunta ta waro da ƙyau, sai kuma ta sake kallon inda Tajwar Eshaan yake har yanzu, still dai yana tsayensa. “Ko kaɗan bani nace Babiy, hasalima ni an riga an sanarmin na rasaku. Shiyyasa a kullum nake cikin alhini da baƙin ciki.” Kallon juna suka shigayi da mamaki, sai dai Kaka mutum mai hangen nesa ya ce, “K waya haɗamu da k?”. Baki ta buɗe zata bashi amsa, sai kuma ta sake kallon wajen window ɗin. Cikin sa'a yanzu kam ya juyo, ya wani tsatstsareta da kaifafan idanunsa. Kansa ya girgiza mata, da mata alamar zip a baki da yatsunsa biyu cike da gargaɗi. Jiki a sanyaye ta maida dubanta gasu Babiy, kanta ta ɗan girgiza musu ta ce, “Wani bawan ALLAH ne, asirrance ya kawo min nima ban gama tantance ainahinsa ba”. Cike da gamsuwa suka shiga jinjina mata kawuna. Kaka kam dai murmushi kawai yayi ya basar. Da ga haka taci gaba da zaƙulo musu tambayoyi suna bata amsa ɗaya bayan ɗaya. Sun kwashe kusan awa biyu kamar ba kuɗi ake ci ba kafin yay mata nuni da sallama dan tuni ya baro window ɗin ya dawo inda ya tashi. Badan taso ba tai musu sallama. Suma ɗin dai da alama basu gaji da kasancewar da ita ba. Yanda take ta sakin murmushi ya sashi kasa daina kallonta. Sai dai murmushin nata mugu-mugun birkita masa lissafi yake. Jiki a saɓule ya miƙe da nufin barin wajen yana rumtse ido da cije lips, a bazata, bazatar data nema kifo zuciyarsa ƙasa kawai yaji ta rungumeshi ta baya. Cak numfashinsa da duk wani abu mai motsi a jikinsa yay tsaiwar mutuwar wucin gadi. Iffah da gaba ɗaya farin ciki ya lulluɓe mata idanu tama rasa mizata masa yasan tana cikin shauƙi ga neman abokin da zai tayata wannan farin ciki batare data kawo komai a ranta ba ta rungumesa dan yau kallon Hanash take masa ba Shahan-shan ɗin ƙasar ruman ba. Kanta ta sake kwantarwa a faffaɗan gadon bayansa da baifi iyakarta rabi da kwata ɗin tsahonsa ba ta sake matse hannayenta data sakalo ta saman shafaffen cikinsa waje guda tai masa ƙamƙam tana murmushi mai bayyana haƙwara. A hankali ta furta. “Jazakhallahu khairan Eshaan Akhi. Yanda ka faranta raina kaima ALLAH ya ninka maka farin cikinka na tsahon shekarun da zakai a duniya. ALLAH ya ƙara ɗaga darajarka ya baka kariya. ALLAH ya yafe maka kurakuranka ya baka ikon sauke nauyin daya ɗaura maka na jarabawar shugabanci. ALLAH ya jiƙan mahaifinka da kakaninka da duk wani makusancinka da baya numfashi. UBANGIJI ya biya maka buƙatinka harma wanda ka barma zuciyarka da wanda ma baka jisu a ranka ba har yanzu. ALLAH ya share maka hawayenka a duk lokacin da kaji son yinsu tun kafin su zubo....” Rawa jikinsa ya farayi, numfashinsa na fisgar fita da gudu-gudu. Dan gaba ɗaya Iffah ta hargitso duk wani rauninsa na baɗini da ya ɗauki tsahon shekaru yana adanawa. Hannayenta da ke akan cikinsa ya zare a hankali cikin son dai-daita kansa, janyota yay ta dawo ta gabansa, kafin ta iya cewa wani abu ko samun damar kallon fuskarsa a wani irin slowly ya rungumeta gaba ɗayanta cikin jikinsa da gaba ɗaya ƙofifin gashi suka buɗe. Ɓat ta ɓace cikin jikinsa tsabar yanda ya fita girma da tsayi, tsam-tsam yay mata har sai da ta saki ƴar siririyar ƙara da masa ƙaramin dundu (ƙulli inji Katsina wa😀) a baya. Ko gezau baiyi ba, sai numfashi da yake ta saki a sarƙe, itako da taji matsan yayi yawa sai ta shiga mutsu-mutsun son ya saketa. Yo ina dalili wannan matsar kamar za'a ɓalla mata ƙashi. Ganin fa zai ɓaɓɓalatanne a shagwaɓe kamar zata fasa kukan ta ce, “Wayyo Eshaan Akhiiiiii!!”. (Ya arrahaman) ya faɗa sauran notikan da suka rage suna aiki a jikinsa na ƙarasa kwancewa jin yanda ta fitar da kalmar Akhiiii ɗin. Ga wata irin hajijiya da ke juya masa ɗakin na neman zubar da shi ƙasa. Cak ya ɗagata da ga kan ƙasa. Da sauri ta ƙanƙamesa gabanta na faɗuwa jin yanda jikinsa ke wani irin tsuma kamar ba Shahan-shan da ta sani ba. “Am sorry” ya faɗa yana zubewa da su saman gadon da jawota jikinsa ya manne lips ɗinsu waje guda. Wani irin salo yake mata mai matuƙar birkita tunani da susuta rai. Kamar ba shi ba, kamar ba Shahan-shan ɗin nan ba mai tsananin miskilanci da ƙasaitar mulki. Idanunsa ya matuƙar rufewa, babu yaren da yake fahimta sai yaren isar da saƙonsa ga Iffah. Sai da ya tabbatar ya gama lausasata da dukkan iyawarsa da shi kansa bai san ya iya ɗin ba. Lips ɗinta kam har wani irin zafi-zafi radaɗi-raɗaɗi suke tsabar yanda suka sha wahala a hannunsa. Yana sakin mata su baya taja tana mai jujjuya masa kanta. Da matuƙar tashin hankali da tsoron da ke bayyane cikin idanunta ta. Har numfashinta sarƙewa yake tsabar yanda ta tsorata da yanayinsa wajen furta “Please Eshaan Akhiii Please”. “Bazan iya ba My Sohaa”. Ya faɗa cikin wata irin sarƙaƙaƙƙiyar murya da bata taɓa jinta tattare da shi ba. Ƙirjinta ne yay wata irin sake harbawa. Ta ɗan ƙara jan jikinta baya still tana jujjuya kanta. “Kai shugabane kamun adalci ban shirya hakan ba”. “Gareki ni bawa ne, ke kaɗaice sirrin Eshaan bin Haysam Abdul-majeed Aliy Qutb Fhareedah bint Zayyan”. A cikin matuƙar tashin hankali ta sake ja baya tana girgiza masa kai dan idanunsa basu taɓa firgita rayuwarta irin yau ba, yau ɗin ma yanzun nan. Wani irin murmushi da ya nema ɗauke numfashinta ya sakar mata, tare da ɗora hannunsa saman zip ɗin gabar rigarsa ya zugesa zuwa ƙasa, ya ɗaga rigar kawai ya zare baki ɗaya. Ai a wani irin mahaukacin gigice Iffah ta fasa ƙara jikinta na karkarwa ta tusa kanta cikin filos ɗin gadon ta cure gaba ɗaya jikinta waje guda........✍️ _😬🚴Lamarin ya girmi ƴan shekaruna bara nayi nan._ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (43) ........Murmushi ya saki yana mai lumshe rinannun idanunsa. Lumshesu yay a hankali yana cije lips ɗinsa, yayinda wani abu mai sanyi ke saukar masa tun daga saman kai har yatsar ƙafar sa. Tabbas shi yasan juriyarsa tazo maƙura, maƙurar da in har bai samarwa kansa abinda yake so ba akwai babbar matsala, matsala irin wadda doctor ɗinsa ya sanar masa a ƙasar Cuba shekaru huɗu kenan da suka shuɗe. A hankali ya buɗe fitinannun idanunsa a kanta ya sake lumshewa tare da kaiwa kwance kusa da ita shima. Idanun ya sake buɗewa tare da kamo hanunta cikin nasa, cirota yay daga cikin filos ɗin da take ƙara cusa kanta ya maidata jikinsa ya rungume ya na wani irin tsuma. Cikin disashiyar muryarsa da ke ƙara sarƙewa ya shiga faɗi a kunnenta “Kin yarda ke ce sirrin Eshaan bin Haysam Abdul-majeed Aliy Qutb? Tabbas kece, ki yarda kece Fhareedah bint Zayyan. Lokaci yayi da kowama zai yarda kece sirrin Eshaan, dole su tabbatar, dole ne na sakasu su tabbatar”. Ya ƙare maganar da ɗago fuskarta saitin tashi da tai jazur abinka da fari. Hawaye take sosai tana ƙara rumtse idanunta, itama tata fuskar duk ta birkice, jikinta kuwa rawa yake sosai har yana iya jin yanda bugun zuciyarta ke harbawa da azabar gudu. Dan yau tayi gamo, gamo mai tsananin saka ɗimuwa da tsayawar bugun zuciya musamman ga irinta. “Open your eyes my Sohaa. Please Open”. Ya faɗa cikin muryarsa da ke ƙara komawa can ƙasan maƙoshi yana ɗan bubbuga fuskarta. Maimakon buɗe idanun da ya buƙata sai kawai ta sakar masa kuka tana girgiza masa kai alamar bazata iya ba. Wani irin lallausan murmushi ya saki a wahalce da har take iya jin sautinsa cikin kunenta. Ya sake kusanta fuskokinsu dab-dab har hancinansu na gugar juna. A hankali ya sake matso da ita jikinsa yana shafa kanta da ɗan bubbuga bayanta yana hura mata iskar bakinsa cikin kunne alamar lallashi. Sannu-sannu ta fara sassauta rawar jikinta tana haɗiye hawayen da takeyi, sai kuma ta koma sauke ajiyar zuciya da sake yin luff a jikinsa kamar wata ƴar mage. Sai da ya tabbatar nutsuwar da yake buƙata gareta ta dawo jikinta sannan ya ɗan ɗago yana kallon fuskarta da tai shaɓe-shaɓe da hawaye. Dariya ta bashi ganin duk bakin tsiwar nan da baya mutuwa tun kan aje ko'ina har ya mutu yau murus. Cikin ƙoƙarin son danne dariyar ya furta, “Na ƙyale ki?” acan ƙasan maƙoshi. Da sauri ta ɗaga masa kai tana taɓe fuska zata sake sakin kuka. “No bana son kuka”. Saurin haɗiyewa tai tana jinjina masa kai. “Open your eyes muyi magana, in ba hakaba babu batun haƙuri”. Mar-mar ta farayi da idanun kamar zata buɗe amma kuma ta kasa, da ƙyar ta motsa lips ɗinta da ke rawa tana sake takwaf-takwaf da fuska. “Ka saka kaya to dan ALLAH”. Murmushi yayi, tare da riko hanunta ya ɗaura a saman lallausan duvet ɗin gadon ya ce. “Lulluɓeni to”. Da ƙyar ta iya riƙo bargon saboda yanda hanunta ke rawa, ganin yanda take yi ɗin ya taimaka mata suka janyo a tare. Cikin ƙara ƙasa da muryarsa ya ce, “Tom buɗe”. Ta jima tana kokawa da kanta kafin tai ƙundinbalar buɗewar ta saukesu kan ƙyaƙyƙyawar fuskarsa da gaba ɗaya ya canja mata kamanni kamar ba Shahan-shan ba. Da sauri tai ƙoƙarin sake maidasu zata rufe ya girgiza mata kansa. Bata rufe ba sai dai taƙi yarda ta sake kallonsa. Yatsun hanunsa ya saka cikin nata yana murmushin nan nasa na iya lips, yana shaƙar numfashinta da busa mata nasa tana shaƙa itama. “Miyasa baki so mu zama abu ɗaya?”. Kanta ta girgiza masa alamar bata sani ba. “Magana nake so”. “Ba komai”. Ta faɗa cikin muryarta da ke a matuƙar ɗashe dan gaba ɗaya wani irin kalar tsoronsa take ji. “Dole akwai dalili, gashi ni kuma na kai matsayar da bazan iya amsar uzirinki ba balle tunanin zan dakata. Sai dai zan miki alkawarin kasancewa da ke ina mai lallashinki daga nan har lokacin da hawayenki zasu daina kwaranya Niazmina. K ba MATATA bace kawai RAYUWATACE, ke RAYUWATA ce ki riƙe wannan ki faɗama duniya da ƙarfin iko”. Ya nisa a hankali yana ɗan kai hannu saman goshinsa ya murza alamar ya gaji da maganar dauriya kawai yake. “Bazan so tilastaki ba, ba kuma zan iya barinki ba. Am so sorry zan baki sirrina da ban taɓa koda kwatanta bama wata ba a duniya, sirrina da nake ɓoyewa a tsahon rayuwar hankalina gaba ɗaya, sirrina da nake faman adanawa domin ke dana ɗauka tsahon rayuwar hankalina ina addu'ar samuwarki da ƙyawawan suffofi matar ƙwarai. ALLAH ya tsare miki ni ne domin wannan ranar Fhareedah, kamar yanda kema nake ji a jikina ya killacemin ke domin ni kaɗai, mijinki bai taɓa koda kwatanta aikata Zina ba, wata mace daba muharramarsa ba bata taɓa raɓarsa ba, mijinki ya jure wahalar ƙishin yini da tsahon dare domin ya kasance naki ke kaɗai, ke kaɗai ɗin da nake fatan ki zama ke kaɗai har ƙarshen numfashina, ki yarda zan baki wannan sirrin domin *KECE SIRRINA* Fhareedah bint Zayyan...” Kalamansa masu tasiri ne ga rauninta, ita bamai jayayya bace mai saurin sallamawa ce. Ita bamai taurin kai bace mai saurin karɓa ce. Ita ba mai saurin ƙaryatawa bace tana da rinjayen gaskatawa musamman ga mutum mai daraja irinsa da ƙarfin iko. Bata da zaɓin da ya wuce shigewa cikin jikinsa ta sake masa siririn kuka mara sauti da tasirinsa yafi amsa kuwwar baradan mayaƙa dubu bisa dubu a katafaren filin gumurzin yaƙi na ƙarƙashin daular mulkinsa. “Karka cutar da ni”. Ta faɗa tana mai ƙara ƙanƙamesa cike da sallamawa baki ɗayanta. Hannu biyu ya amsheta cikin tsumar jiki ya ƙara matsota ya rungumeta jikinsa da ƙyau, “Eshaan ba mai cutarwa bane ga maƙiyansa ma balle ke da ke ce rayuwarsa my Farishta (My Angle)”. “Na baka amanar rayuwata, na baka tukuycin hidimata domin ALLAH da girman hidimtawarka gareni da zuri'ata”. “Ni shugabane, bama kowane rai kariya a cikin ƙasata dolene gareni balle zuri'arki Niger. Ba ahalinki kawai ba, ko ƙasar gidanku idan wani yace zai damƙa da cutarwa baza'a sake jin labarinsa ba a duniya sai dai wani ba shi ba”. Ya faɗa yana ƙoƙarin rabata da duk abinda yay masa shamaki da ainahinta. Tai ƙoƙarin kanƙamesa amma yaƙi bata damar hakan, ga lips ɗinta ya riƙe cikin nasa alamar baya buƙatar sake jin komai da ga gareta kuma. Daga haka dukkan labarin ya canja kansa. Canjawa mai girman da girmansa ya wuce fassara da baki ko rubutu. Abinda kawai na sani shine Iffah ta zama Eshaan, Eshaan ya zama Iffah a wata gaɓa mai wahalar hasashe ga duk masu iya zama ƙololuwa a hasashen. Da gaske itace ɗin sirrinsa, sirrinsa da ke matsayin sirri mafi girma a duk cikin zagayen sirrikansa.... ★★..... ★..... Duk yanda doctor ya so fahimtar da Miran Jasim da ya matsa a sallamesa ya ƙi saurarensa, akan dole ya sallamesa a daren. Motar asibiti ta kaisa har ƙofar sashensa. Duk ruɗewa matansa sukai da ganinsa, sai dai ko kallon inda suke baiyi ba ya shige ɗakin shi. A falonsa ya samu Miran Arshaan na faman kaiwa da komowa. Bai yi mamaki ba dan yasan shegen ruɗewa irin na Miran Arshaan ɗin, shi sam bai iya controlling tashin hankali ba ta siyasa a wani lokutan. caraf kawai yaji Miran Arshaan ɗin ya cafki hannunsa ya nufi bedroom ɗin sa da shi abinda bai taɓa faruwa ba. “Anya kana lafiya kuwa Arshaan?”. Ya tambaya yana dafe wuyansa da ke masa zafi ko magana yayi, cikin gatse Miran Arshaan ya ce, “Haukacewa nai”. Dai-dai da shigarsu ɗakin. Miran Jasim ya fisge hannunsa yana mai dalla masa harara, “Ai na fahimci hakan tun ɗazun, nikam ka ajiye wannan shirmen naka kamun bayanin da zan fahimceka kasan ban cika son hauka ba fa”. Wata irin shegiyar dariya Miran Arshaan ya kwashe da ita yana nuna Miran Jasim, “Idan hauka nake kaima wlhy yanzu zaka fara Jasim.......” tiryan-tiryan ya kwashe komai ya sanar masa. Ashe kam haukan Miran Arshaan ɗin ƙarami ne da gaske. Dan take Miran Jasim ya rikice yana rantsuwar lasar takobi akan sai ya datse numfashin Tajwar Eshaan da Iffah kafin su su tona musu asiri. “Wannan duk bashi ne mafitarmu ba in faɗa maka, neman barbushi a wannan daren shine. Sai dai kuma akwai matsala, dan a haƙe wancan matsiyacin yake da son ganin wanda zai fita a daren nan. Shawara ɗaya gareni muyi fitar rana kuma a daban-daban”. Miran Jasim ya gamsu da hakan, anan suka tsaida maganar Miran Arshaan ya wuce. Sai dai a wannan daren kam babu wanda ya rintsa a cikinsu. Dan hatta Jasrah kasa gane kan Miran Arshaan tayi gaba ɗaya..... ★★.. TA-KURYA ★.... A wani irin matsanancin firgici ta farka da ga mummunan mafarkin da ya nema zama sanadin bugawar zuciyarta cikin barcin jiran uwa da ya figeta. Sai kuma ta zabura dan farkawar tata dai-dai da dirowar UWA kamar wadda aka jeho. A gaban uwa ta zube babu alamar tana cikin hayyacinta, “Uwa ki tabbatar min mafarki nake, kice min ba Saiful-malik ɗina ba, kar kicemin tabbatacce al'amari na gani......” “Tabbatace ne, tabbas tabbatacce ne. Taci nasara, taci nasara ta-ƙurya taci nasara a kanki Ajlaan ya sallama mata. Ƴar shilar kanari ta zama mai nasara saman nasararki, ya bata sirrinsa fiye da girman kowane sirrinsa da wani ya sani a duniya, kin karya mana alƙawari da sakacinki. Dukkanin wahalarki ta baya ta rusa. Kina cikin matsala. Ke ce a matsala Ta-ƙurya, dan mu ba'a karya mana alƙawari ta-ƙurya, ba'a saɓa mana alƙawari, domin mu sharaɗinmu baya tashi hhahaha!!!!!.....”. Rawa jikin Malikat Bushirat yake kamar mazari, ga zufa tai mata wani irin mahaukacin sharkaf a jiki. Idanunta kam duhu-duhu take gani a cikinsu, tun tana iya jin furucin Uwa a kusa da ita har ya fara nesa-nesa, a cikin mintuna biyu tai rufff tare da yin baya yarafff ta zube alamar babu rai.......✍️ _Tofa abin na gaske ne. 😱🏃🏃🏇🏇🚴🚵🚲🛵🏍️🚙🚗🛻🚐🚚🚛🚜🏎️🚒🚑🚓🚕🛺🚌🚈🚝🚅🚄🚂🚃🚋🚎🚞🚊🚉🚍🚔🚘🚖🚆🚢🛳️🛥️🚤⛴️⛵🛶🚟🚠🚡🚁🛸🚀✈️🛫🛬🛩️Wanda duk wanda ya shirya yazo mu ware kawai😷😷🙆🙆_ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (44) ........Bai fahimci gagarumar ɓarnar da ya aikata ba sai da ya dawo jayyacinsa. Tun-tuni azaba tasa Iffah ta sume masa batare da ya farga ba. Ba ita da dama ya zama dole ta jigatun ba, hatta da shi kansa a jigacen yake kasancewar wannan shine lokaci na farko a tarihin rayuwarsa. A kallo ɗaya zaka fahimci tabbas maza sunyi laushi, laushi bana faɗuwa ko gazawa ba, laushi na jin-jina girman UBANGIJI da godiya a garesa dan shine mai azurta bawa da ni'imomin kala-kala iri-iri daban-daban da kai kanka baka fahimtar girman wannan ni'imar sai randa ta isa gareka. Babu ɗan gata a ma'aurata mace ko namiji sai mafi ƙololuwar iya riƙe kansa da nisanta kansa da ga ZINA har sai randa ALLAH ya azurtaka da halal ɗinka. Ya shaida yau kam ya shaida. Bayan uwa da uba da kakarsa bayajin ya taɓa jin ƙauna da soyayyar wani mai tsananin ƙarfi a zuciyarsa kamar yarinyar nan. Ƙololuwa yake jinta, ƙololuwar da in har akace yay fassara ba lallai masu jinsa su iya yarda ba ko zaman saurarensa har ya kai inda yake buƙatar gamsar da su. Badan kar ace ya bada maza ba da shimafa kukan zai fashe da shi kawai a wannan gaɓar. Da ƙyar ya iya ɗagota yana ɗan bubbuga fuskarta da kiran sunanta cikin sarƙaƙaƙƙiyar muryar sa. A baɗini a birkice yake, amma a zahiri da zaka iya ganinsa a nutse yake komai tamkar ma koman da mai kallo zai kalla komai bai zama komai ba. Iya jijjiga da kiran sunanta da yayi babu alamar rai tare da ita. Ya rumtse ido da ƙarfi tare da kai hannunsa saman goshinsa yana murzawa tsabar baima san miya kamata ace yayi ba. Shifa ɗan gata ne, ɗan hutu ne, ɗan lele ne, tunda ya tashi bai san komai ba sai ai masa cikin bada umarni, a inda ya rayu zagaye yake da masu hidima daban-daban da ko abinci inda zai yiwu tauna masa za'ai a zuba masa a cikinsa. Sai da yay matuƙar yaƙi da iyayensa kafin ya samu wasu damammaki na dogaro da kai dan shi yafi son tsayawa a kan ƙafafunsa koda ace shine mafi zama ƙololuwar gata a wannan rayuwar. Bai taɓa ƙyamatar rayuwar talakansa ba sai ma birgesa da basa tausayi yake. Shiyyasa ya zaɓi shiga cikinsu ta hanyar ɓadda kama, ya kuma ƙir ƙiri wasu hanyoyin tsaya musu a duk lokacin da ya fahimci ana zaluntar su. Bashi da zaɓin da ya wuce sake maidata a jikinsa kawai ya rungume tsam-tsam ya shiga bata wasu irin manya-manyan sumbata masu daraja da ba'aima macen data ɓarar da darajar a wajen marasa daraja. “Kiyi haƙuri, kiyi haƙuri na tuba my Ashna”. Ya faɗa cikin kunnenta yana ɗan hura mata isaka a sautin muryar nan tasa da ta sake disashewa matuƙa cikin maƙoshi kai kace zata iya jinsa. Kamar ko wani siddabaru sai kawai tai wani irin zaburowa da jan numfashi a fisge. Da sauri ya janye hannunsa da ke saman goshi ya dubeta, sai kuma ya sake riƙota da ƙyau cikin jikinsa da take neman kufcewa yana ambaton sunan ALLAH a daburce. Wani irin siririn kuka data sake birkita masa lissafinsa ta sake sakar masa tana ƙanƙamesa da jera masa magiyar roƙon ya barta, ya barta zata mutu, dan a rayuwar Iffah bata taɓa cin karo da azaba makamanciyar ta wannan gaɓa ba. “Am sorry relax, cool down babie” ya faɗa yana ƙara ƙanƙameta cikin jikinsa da tura yatsun hanunsa cikin birkitacciyar sumar kanta da ya gama harmutsawa. Har aka fara kiraye-kirayen sallar asubahi bai daina lallashin da bai san taya zai mata magana mai tsahon da zata fahimcesa ba. Shi gaba ɗaya ma ya wani mance kansa a matsayin Shahan-shan, duk ta gama harmutse masa ɗan sauran lissafin da ya rage masa da rikicinta. Yasan zai fiskanci ma fiye da haka in dai yarinyar nan ce, ba'ace mata kule ba ma tace cas inaga yau shi ya taro fitinarta da karan kansa, ai yasan a darunta ma bata fara komai ba kam dan har yanzu bata gama dawowa a hayyacinta ba ballema ta fara. A hankali yay ƙoƙarin kwantar da ita domin sauka ya samu mafita amma ta ƙanƙamesa ta na sake sakar masa wani sabon kukan da ko muryarta ma ba'a iya ji tsabar yanda ta gama galabaita. Ji yay kawai murmushi mai sanyi ya suɓuce masa, sake riƙota yay yasa a cikin jikinsa yana hura mata iska a kunne cike da soyayya da ƙaunarta da ke neman fallasa kansu a zahirinsa. Ajiyar zuciya ta cigaba da saukewa jikinta na saki kaɗan-kaɗan, da ga haka wani wahallen barci yay awon gaba da ita. Ɓoyayyar ajiyar zuciya ya sauke ya kwantar da ita a hankali sannan ya sauka a gadon. Cikin ƴar sassarfar da a zahiri bazaka taɓa gani ba, dan babu abinda ya canja a salon tafiyarsa ta ƙasaita ya nufi bathroom, ƙarƙashin shower kawai ya shiga, babbar gaba ɗaya ya kunna ma kansa tare da dafe bangon glass ɗin da aka zagaye wajen shower ɗin kamar wani ɗan ɗaki. Duk da sanyin da garin ya ɗauka na hadarin da aka haɗa ya ƙare da isaka da ɗan yayyafi ya baje dana ruwan baya jinsa ma. Cikin ƙanƙanin lokaci ruwan yay masa sharkaf, tattausan yalwataccen gashin kansa duk sun kwanta masa a goshi har wasu na ɗan taɓa saman idonsa saboda ɗan tsayin da suke da shi. (She's my everything. Ta daban acikin daban ƙololuwa!....) Kawai yake iya maimaitawa a zuciyarsa hakwaransa cije da lips ɗinsa kamar zai hudasu kawai ya huta. Sai da ya kwashe kusan mintuna bakwai a ƙarƙashin shower ɗin sannan yasa hannu ya danne makunar yana sauke numfashi a jajjere. Har lokacin hannunsa ɗaya dafe da bangon glass ɗin. Jin atshawa na taso masa sannan ya buɗe idanunsa da sukai wani irin jajir da ƙanƙancewa. Sanin in har ya fita da wannan sanyin a jiki zazzaɓi salamu alaikum ya sashi sake kunna shower ɗin, sai dai yanzu ruwan ɗumi ne saɓanin ɗazun. Sumar kansa ya shiga yamutsawa a kasalance ruwan ɗumin na ratsashi da ƙyau, da ace zai iya kuwwar tattaro hankalin mutanen duniya baki ɗaya zai faɗa musu itace komansa, idan yace komai, komai da komai yake nufi akan komai. Sake jin kiran salla ya sashi ƙarasa komai a gurguje ya fito.. Yana fitowa a kanta ya fara sauke birkitattun idanunsa da launinsu ya zama abin firgitarwa ga mai kallo. Tuni barcin da ya ɗauke ta ya ƙara nisa, barcin da shi a karan kansa yasan na wahala ne kawai. Janyewa yay ya cigaba da takowa cikin ɗakin sannu a hankali kamar mai sanɗa, dan gaba ɗaya jikinsa babu wani ƙarfi kona sisin kwabo. Sai dai jarumtarsa ta ɓoye komai bayan canjawar launin idanunsa baka isa fassara yanayinsa ba. A gurguje ya busar da kansa domin rage laimar cikinsa ya shirya cikin jallabiya mai taushi fara tas, ya ɗaura baƙar alƙyabba irin ta sarakunan Saudiya da mayafi a kansa tare da daɗaɗan ƙamshi kamar ba sallar asubahi zai fita ba. Gaban gadon ya tako a hankali, barcin kam da nauyi ya ɗauketa, sai dai a kallo ɗaya zaka fahimci a matuƙar wahalce takeyinsa, dan sai yamutsa fuskarta da yake ɗan gani a hasken ɗakin da yake dimmm take ga ajiyar zuciya da take ta faman saki a jajjere. Idanunsa ya ɗan lumshe ya sake buɗewa a kanta yana sakin guntun murmushi da jan jikinsa baya a hankali ya fice fara gabatar da salla kafin ya dawo su ɗora daga inda suka tsaya dan yasan sabon daru kam zai fuskanta. Shi kuma ko a yanzu badan yana jin tausayinta ba sake zuwa mata zai a yanda yake jin kansan nan. ★Ana idar da salla ya baro massalin, dan gaba ɗaya hankalinsa na gareta saboda yasan tana matuƙar buƙatarsa kusa da ita da taimakonsa a wannan gaɓar. Yanda ya barta haka ya dawo ya sameta. Yanzun ma baiyi wani motsin da zata farka ba har ya kammala zame kayan jikinsa ya canja da ƙananu. Bathroom ya nufa ya haɗa ruwa na musamman sannan ya dawo gareta. Kai tsaye ya kunna wutar ɗakin da ta haske ko'ina ko allura kuwa ka yarda kaga abunka. A hankali yake bin ɗakin da kallo tamkar yau ne karo na farko da ya fara kasancewa a cikinsa. Ya ɗan saki murmushi yana mai lumshe idanunsa da sake buɗewa. Shi kansa ɗakin ya ƙara zama mai wata irin daraja da kima ta musamman a garesa, dan ya zamar masa ɗaki mafi zama ƙololuwar sirri sama da duk sauran sirrikansa. Dubansa ya kai ga gadon inda Iffah ke ƙudindine sai faman sauke ajiyar zuciya take yi cikin barcin wahalar da take yi. Magiya roƙo neman agajin da ta dinga jera masa na dawo masa daki-daki, da'ace gilashin ɗakin nan ba mai hana fitar sauti bane babu abinda zai hana a daren na jiya gaba ɗaya daular ruman su jiye masa sirrinsa, dan bakinta bai mutu ba sai da ta sume masa. Ya ɗan sake murmusawa da takawa sannu-sannu kamar wanda baya so zuwa gaban gadon ya zauna gefenta. Fuskarta da tai luɓu-luɓu na kukan data sha ya shafa yana kaima lips ɗinta da sukai bushewar wahala sumbata. A firgice ta farka tamkar ɗazun, ta saki wani irin wahallen kuka da jujjuya kanta tana mai jero masa roƙon ya barta, dan ALLAH ya barta karya kasheta bazata iyaba. Yanda take yi ɗin dole ne ya baka tausayi, dan a kallo ɗaya zaka fahimci har yanzu bata cikin hayyacinta. Shi baima san ta ina zai fara ba duk da ya jima da shiryama irin wannan ranar ba tun yau ba, amma a yanda yaje mata shi kansa yasan ya jigata ta, irin jigatawar da da'ace wani ne ya aikata aka kawo masa ƙara sai ya hukunta mutum. Sai gashi shi da kansa ne, shi da kansa ya kasa control ɗin kansa yay ma ƙaramar yarinya kamarta zuwa har uku a dare ɗaya duk da ta kasance tamkar jaririya a hannun uwa garesa. “Shiiii!!” ya faɗa a hankali yatsansa kan lips ɗinta. Riƙeta yay da ƙyau tare da manna mata wata sumbar a goshi kafin ya miƙe cak ya ɗagata zuwa bathroom. Wata gigitacciyar ƙara ta saki jinta a ruwan zafi tana rirriƙesa azaba na ratsata, jikinta sai rawa yake shi kansa har abin ya bashi tsoro. Dole ya shiga cikin ruwan shima ya rungumeta a jikinsa. Kuka take matsananci da ƙoƙarin ganin tabar jikin nasa amma ya hanata damar hakan. Kansa ya dafe yana riƙota jikinsa da ƙyau cike da takaicin kansa, sai dai kuma shima ba laifinsa bane, gaba ɗaya idanunsa ne suka rufe, duk wani haƙurinsa da jarumtar da yake dannewa a tsahon shekaru sai da suka amayar da kansu. Tunfa yana da shekarun da basu haura ashirin ba yake dakon wannan matsalar, taya ma zai iya tuna abinda ya dace yayi a wannan gaɓar, ta yaya, ta yaya ake son ya tuna.......✍️ _🚴🚴🥱Bazaka tunaba kam mai Rumawa._ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (45) ........Sai da ya tabbatar ta samu isasshen gashi sannan ya taimaka mata tayi wanka, har lokacin bata daina hawaye ba. Idan kuma ya ɗan motsata da ƙarfi ko yaya ne sai ta saki siririyar ƙara da ƙara ƙarfin kukanta. Babu abinda ya ke iya jera mata sai kalmar “Sorry, I am sorry”. Bai san tunzura mata zuciya kalmar haƙurin nan take sake yi ba. Koda ya saka mata bathrobe shima sai da ya cire kayan jikinsa dan duk sun jiƙe. Yanzu ma cak ya ɗagota zuwa ɗaƙi, ganin lokacin salla ya ƙwace da yawa ya ɗakko mata rigar jallabiyarsa ya saka mata, veil ɗin ta na jiya ya naɗa mata sannan ya saka mata sallaya ya sake ɗakkota da ga kan sofar da take kwance ya ajiye kan sallayar. Ta kasa tsaiwa yanda ya kamata tsabar yanda ƙafafunta kansu sukai mata tsami, sai da ya dinga lallaɓata sannan tai dauriya da ƙyar, lokacin da take kaiwa ruku'u da sujida yana jin yanda kukanta ke ƙara ƙarfi alamar a wahalce take, zaman tahiya kam ta kasa zama da ƙyau. Duk sai hankalinsa ya ƙara tashi, dan ya fahimci lallai akwai matsala. Tana yin sallama ta zame kwance tana rusar kuka da kiran Ummu ta zo ta taimaketa. A gabanta yazo ya durƙuso tare da kamota jikinsa, yanda ya motsatan yasa ta ƙanƙamesa sosai. “Please stop crying babie”. Ya faɗa da wata irin murya mai tsananin sanyi da taushi yana rungumeta da ƙyau idanunsa a lumshe. Duk yanda taso tsaida kukan ta kasa, dan ciwo takeji sosai a jikinta. Ga kanta na mata wani irin ciwo mai azaba shima. Ga zazzaɓi mai zafi sosai. Gaba ɗaya ta birkice kamar ba Iffah'r Babiy mai shegen tsiwar nan da tsaurin ido ba. Dama irinsu bakin ne kawai ba iya jurar wahala sukai ba (lols😆). Bawan ALLAH Shahan-shan gaba ɗaya ta susutashi ya daina gane komai, yanda take kukan jinsa yake har tsakkiyar zuciyarsa dan shi mutum ne mai tausayi tun da can ma. Amma akan fuskar babu alamar wani abu kamancin hakan tattare da shi, yayi masifar dakewa kamar komai ma bai faru ba. Ɗagata yay daga wajen ya kaita saman kujera dan gadon gaba ɗaya ya ɓaci gashi farin bedsheet. Rirriƙesa tai da sauri alamar bazata iya zaman ba, dole ya ɗan kai gaban kujerar durƙushe yana riƙe da ita. “Faɗamin minene ke damunki?”. Yanda ya zuba mata fitinannun idanunsa ba shiri ta shiga ƙoƙarin ganin ta haɗiye kukan, da ƙyar ta iya furta, “Zafi yake wajen, zafi mai azaba kamar sanda k.......” sai kuma ta kasa ƙara sawa ta fashe da kuka. “Stop crying please, bara na duba naga ko kinji ciwo ne”. Da sauri-sauri ta shiga girgiza masa kai tana matse jikinta waje guda da faɗin, “Ni bazaka gammun ba, ka kiramin Ummuna”. Hannunsa ya ɗan kai bisa goshinsa ya murza. Sai kuma ya sake ɗago kan a hankali, har yanzu durƙushe yake gabanta tamkar ba Shahan-shan ba. Cikin ƙara tausasa murya da shima har yanzu bata gama dai-daita ba ya kai hannu saman fuskarta ya tallafo da duk hannayensa, babban yatsansa yasa yana share mata hawaye. “Kiyi haƙuri, ki zaɓi wanda zan kira miki bayan Ummu, dan ko tana a ƙasar nan bazan iya haka gareta ba, bazan so ta ganki a haka ba. Faɗamin wa kike so na kira miki bayan ita? Ammie, Jaddah, ko Mammy, ko Aunty Jasrah? Ko na baki wayar ki zaɓa wanda kike so yazo?”. Kanta ta ɗaga masa hawayen na cigaba da kwaranyowa. “Okay tom bar kukan, Ni bana son ganin hawaye nan suna sake raunani, rauni na kuma yana nufin sake maimaita abinda nai a daren jiya ko kina so a ƙara?..” Har zabura take tana girgiza masa kai wani sabon kuka na taso mata, amma sai tai saurin danne bakinta da hannayenta duka biyu tana ƙoƙarin haɗiyewa. Tausayi ta bashi da dariya, amma sai ya dake abinsa yana yi a cikin rai. Dan da gaske badan kar ya kashe musu yarinya ba babu abinda zai hanashi sake kai mata ziyara. Shi kaɗai yasan mi yake yaƙin dannewa da ga safiya zuwa yanzu, kawai dai abar kaza cikin gashinta. Ɗan kwantar da ita yay da ga zaman karkacewar da tayi, ya miƙe ya ɗauko ɗaya da ga cikin wayoyinsa. Gabanta ya sake zuwa ya dirƙusa ɗin dai maimakon zama da ya saba yi, ita inba a gaban UBANGIJINSA ba yayin bauta masa bata taɓa ganinsa durƙushe haka gaban wani ba. Duk da bawai yayi wani durƙuso bane na ƙasƙanci. Hasalima yanda yay ɗin sai ya ƙawatar irin masoyi a gaban masoyiyyarsa ɗin nan da suke cikin tsananin shauƙi ma juna. Contact ɗinsa ya shiga sannan ya miƙa mata wayar. Karɓa tai tana sake kumbura fuskar nan da tai jazur duk a suntume musamman idanunta. Kalmarsa ta zai ƙara ne ya sata danne hawayen tilas badan ta gaji da kukan ba. Number Mammy ta lalubo, taja wasu sakkani kamar mai tunani ko tsoron kiran sannan tai dialing. Bugu biyu zuwa na uku kuwa aka ɗaga. Da sauri ta rumtse idanunta hawayen da take riƙewa na ɓulɓulowa. Da ga can jin anyi shiru Malikat Haseenat da ta ɗauka wayar kasancewar Daneen Ammarah ta shiga wajenta sanar mata Malikat Bushirat babu lafiya tace ta haɗa mata ruwan wanka shine ta bar wayar gefenta, ita kuma ganin number Tajwar Eshaan yasa ta ɗauka da tunanin ko shima zancen Malikat Bushirat ɗin ne. Amma sai kuma taji anyi shiru ga kuma kamar ana jan ajiyar zuciyar kuka da ake ƙoƙarin dannewa yana son fita. “Assalamu alaikum”. Ta faɗa a nutse cike da dattakonta. Kamar an ƙwalama Iffah farantin silver saman kai da sauri ta ɗauke wayar a kunnenta ta miƙa masa kukan da take dannewa na kufce mata. Bashi da zaɓin amsar wayar shi ya kai nasa kunnen, tunda har aka riga aka ɗaga bashi da hurumin cewa zai yanke sai ya sakata a tashin hankali. Wayar ya kai kunnensa yana mikewa da yin sallama cikin sassanyar muryar nan tasa mai cike da nutsuwa da kame kai. Malikat Haseenat ta lumshe idanu da sakin ajiyar zuciya ta amsa masa. Cikin mamaki yace, “Jaddah ke ce? Ina Mammyn?”. “Tana haɗamin ruwan wanka ne. Ina fatan lafiya dai ko naji kamar ana kuka da farko?”. Ji yay duk yama kasa cewa komai, a karo na farko na rayuwarsa yaji yana jin nauyin kakar tasa. Amma sai ya daure da ƙyar acan ƙasan maƙoshi ya furta, “Fhareedah ce Jaddah. Dama muna buƙatar Mammyn ne anan”. Malikat Haseenat tsohuwar ƙwarai mai ran ƙarfe da cikar kamala. Sai kawai ta saki murmushi batare da ta nuna ma ta fahimcesa ba tace, “Oh to bara ta fito sai a sanar mata”. “Uhum”. Ya faɗa ciki-ciki. Bata sake cewa komai ba itama ta yanke wayar... Nannauyan numfashi ya sauke yana ɗan murza goshinsa. Sai kuma ya kalli Iffah da ta rufe idanu hawaye na cigaba da tsiyaya. Shi kam yama rasa gane kan wannan kuka, amma ya fahimci harda shagwaɓa da ragwantakar tsiya sai shegen tsiwa bakinta babu mai iya kadata a zance. Amma gashi a ɗan tabatan da yay da bai wuce ko ƙwayar zarra da ga abinda ke tattare da shi ba ya sauke take wannan rakin. Lallai ashe akwai aiki gabansa dan ba'a fara komai ba wannan sharar gona ce. (🚴🚴Taɓɗi). Tashi yay ya yaye bedsheet ɗin gadon dan yayi ma kansa alkawarin gyara sirrinsa da kansa. Gudun karma ya barsu a gani closed dinsa ya wuce da su ya adana. Sai kuma yama ga su bar ɗakin kawai, dan haka ya zo ya ɗauketa zuwa ɗakin kusa da wannan ɗin ya rufe wannan... Cikin abinda baifi mintuna goma ba sai ga kira da ga amintaccensa. Bayan gaisuwa da yay masa cike da tsantsar girmamawa ya nema wa su Daneen Ammarah iso. Duk da yaji mamakin jin kamar su biyu ake nufi kai tsaye ya bada umarnin ya shigo da su room 3. Karo na farko kenan bayan ita da ke matsayin matarsa da wani zai shigo jerin bedrooms ɗin sa na saman nan gaba ɗaya. Dan ko su matansa da duk aka kawo nan suka rasa ransu a hawa na huɗu ake ajiyesu. Iffah ce ta farko da ta taɓa hawowa hawan ƙarshen nan. Ba shi kawai ba, hatta da Iffah da tayo gayyar sai da ta daburce da jin sautin muryar Malikat Haseenat na sallama. Amma jarumin naku sai yay ɗam da fuska daɗa duniya bai aikata komai ba babu alamar ko gezau tattare da shi. Sai dai kasancewar sa mutum mai tsananin kunya sai ya kasa yarda ya haɗa ido da Malikat Haseenat ɗin. Dan ita kaɗai ta shigo Daneen Ammarah na falo ta kasa shigowa. Bata san dalili ba kawai taji bazata iya ba, dan zuwan ma sai da Mammah ta tilasta mata harma yanda ta nuna ya bama Malikat Haseenat ɗin mamaki matuƙa dan kunya ce a bayyane kamar wadda zatai gamo da surukinta. A hankali ta cigaba da gara kekenta cikin ɗakin idanunta na yawo kan Tajwar Eshaan da tun kallo guda da yay mata bai sake ba da Iffah da ke duƙunƙune a gado cikin bargon da ta sashi ya lulluɓa mata saboda rawar sanyi da takeyi. A gaban Iffahn ta dakata, a hankali cikin dattakonta da ƙasaita ta kira sunanta da kai hannu ta janye bargon data lulluɓe har kanta da shi. Ɗan zabura Iffah tayi, sai kuma tai saurin maida kanta tana hawaye. Tausayi yarinyar ta bata, dan duk wanda ya kalleta yasan tana cikin wani halli. Batace komai ba ta juya kallonta ga Tajwar Eshaan da ke ɗan satar kallonsu... “Barka da safiya Jaddah”. Ya faɗa a taƙaice yana wani ƙara fuskewa abinsa. Itama sai tai kamar bata fahimci komai ba ta ce, “Barkan ka dai. Mike damunta haka jikinta zafi zau ga fuska duk ta kumbura idanu sun ɗashe yarinya duk ta fita a hayyacinta”. Wayyo shikam ina ƙasa ya ɓuya ciki ko zai kuɓuta da ga bata amsar da bai ma san ta ina zai fara ba. Amma sai ya dake yana ƙara ɗan kauda kai gefe tsahon sakkani kamar bazaice komai ba. Sai kuma ya motsa lips a hankali a gaɓar da ma ta gama fidda rai da samun amsa. “Ta girma ne”. Kallonsa kawai Malikat Haseenat keyi, da jinjina murɗaɗɗen hali irin nashi mai cike da shegen miskilancin tsiya. Sai kuma ta janye a hankali ta maida kan Iffah dake raira kuka a hankali. “Niger (Sweetheart)” ta kirata a hankali. Da ƙyar Iffah ta iya amsa mata murya a ɗashe. “Daure ki tashi zaune muga”. Kwatanta tashin tai har sau biyu amma ta kasa, sai ma wani wahallen kuka da take saki saboda yanda zafi mai azaba ke ratsata. Ta shiga jujjuya kai da faɗin, “Jaddah bazan iya ba. Zafi kamar zan mutu”. Idanu ya lumshe a hankali. Ji yake kukanta na wani irin sukar masa zuciya. Itama kanta malikat Haseenat ɗin wani irin tausayin Iffah'r ne ke ratsata. Ita tasan ba lalaci bane ko raki kawai. Dan zuri'ar su Tajwar Eshaan ɗin fitinannun mutane ne da indai mace taje hannunsu basa iya mata ta sauƙi. Shiyyasa mafi yawansu basa iya zama da mace ɗaya, sannan suna aure da wuri gudun faɗawa halakar zina duk da akwai bijirarru a cikinsu da kan ringa aikatawar. Amma ita a karan kanta ta daɗe tana mamaki akan Tajwar Eshaan da ya nuna baya buƙatar aure tun a shekaru fara girmansa, hakama yanda ya kai har shekarun da aka masa auren fari na sata jin waswasin ko yana neman matan banza ne ko baida isasshen lafiya. Dan tasan duk wanda ya kasance jinin zuri'ar wannan daula baya iya kauda kai ga mace irin hakan da ya nuna shi.........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (46) .......Shiru Malikat Haseenat tai kawai tana kallon Iffah da ta koma ta kwanta, hanunta ta riƙo cike da lallashi ta ce, “To ya isa haka kukan kinji yarinyar albarka. ALLAH yay miki albarka. Ya jaddada rahama a gareki da yalwataccen farin ciki na har abada. ALLAH ya sa ki cigaba da zama haske mai haskaka wannan zuri'a”. A saman lips ya amsa da Amin. Yayinda Malikat Haseenat tai amfani da wayarta tai kiran Daneen Ammarah. Wani irin yamm ya dinga ji a jikinsa jin Mammah na bada umarnin Daneen Ammarah ta shigo. Sai yaji kamar kasancewar su a waje guda yau wani abu ne mai girman gaske. Da ƙyar ya iya dauriyar cigaba da tsaiwa a inda yake har ta shigo ɗakin. Itama yanda take yi ɗin kamar wadda ta daburce. Sam taƙi yarda ta dubi inda yake kamar yau ne rana na farko da suka kasance ƙarƙashin inuwa ɗaya. Koda ya gaisheta kamar yanda ya saba cike da jarumtar danne nasa yanayin shima a hankali ta amsa masa batare da ta dubesa ba. Ita dai Mammah hankalinta nakan Iffah ne bata san mima sukeyi ba. Sai da taji tsaiwar Daneen Ammarah kusa da ita ne ta ɗago. Daneen Ammarah da idanunta ke akan Iffah wani irin tashin hankaline ke ƙoƙarin mamaye fuskarta amma tana dannesa. Muryarta a ɗan sassauce ta furta, “Mike damunta haka?”. “Ɗanki ne”. Malikat Haseenat ta bata amsa a dunƙule. Ta fahimta dan haka bata sake magana ba sai da Malikat Haseenat ta ce, “Kamamun ita ta tashi zaune da ƙyau. Sai ki sake haɗamun ruwan ɗumi da waɗan nan turarrukan”. Kai kawai Daneen Ammarah ta jinjina ma Mammah, ta matsa ta kama Iffah ta tayar, kuka take sosai tana rirriƙeta amma Malikat Haseenat ta ce mata ta barta so take ta zauna ɗin sosai. Ba yanda zatai haka ta zaunar da ita ta zame jikinta batare da ta sake yarda ta kalla sashen da Tajwar Eshaan ya ke ba ta wuce bathroom abinta. Shima sai kawai yaji zaman ɗakin bazai yiwu masa ba. Dan haka ya fito abinsa yana mai satar kallon Iffah da ke kuka da mutsu-mutsun kasa zama da ƙyau. Kai tsaye Gym ɗinsa ya nufa. Jallabiyar jikinsa ya zame ya canja da sport wears ya shiga motsa jiki da zafi-zafi kamar wanda ake tunzurawa..... ★Da ƙyar Iffah ta iya kai kanta bayi da taimakon Daneen Ammarah. Ashe ɗazu ba ƙaramin taimako yake mata ba da yake ɗaukar ta a komai. Sosai hankalin Malikat Haseenat da ita kanta Daneen Ammarah ɗin ya sake tashi da yanda tafiya ma ta gagari Iffah. A bayin ma duk yanda taso ganin ta nutsu a cikin ruwan ta kasa zama. Sai faman rirriƙeta take da magiyar “Mamy dan ALLAH ki fiddani, wlhy da ciwo sosai”. Kwantar da kanta Mamy tai akan ƙafarta tana shafa kanta cike da lallashi dan tana zaune ne a bakin kwamin. “Yi haƙuri to ba'a magana a bayi zai daina”. “Mamy bazai daina ba ƙarawa yakeyi”. Dauriya kawai Daneen Ammarah keyi, amma ji take kamar tai kuka. Ta fahimci dole Iffah taji ciwo ne, ciwo kuma bawai ƙarami ba. Ita kam takan rasa miyasa maza basu da tausayine sam. A shekarun Iffah bai kamata namiji yay mata irin wannan zuwan na lokaci guda ba. Duk da tasan su waye mazan ahalin nan nasu akan mace, balle kuma shi da ya kasance tsahon shekaru ma babu macen, ko da ya samesu kuma ita dai Iffah'r ce ta farko dama take hasashen ya kusanta kenan ko yaya. Tunda kaf yaran randa aka kawosu garesa washe gari ake zuwa a ɗauki gawarsu sun rasa ransu. Ɗaga Iffah tai da ga ruwan, ta ɗaure fuska sosai babu alamar wasa tattare da ita, “Ki tsaya a duba ko kinji ciwo ne a wajen, dan wannan zafin da kike ta ambata dole zai kasance akwai damuwa Ibnati. Idan kuma aka bar mace da irin matsalar nan yana lalatata koma ya taɓa mata brain. Ko kina so ki samu matsala a brain ɗin ki?”. Da sauri Iffah ta jinjina mata kai alamar a'a tana hawaye. Daneen Ammarah ta haɗiye murmushin da ke taso mata dan ta mata hakane dan ta tsoratar da ita dama kawai. Ai ko sai gashi ta yarda ta duba cikin sauƙi amma fa ta ɓoye fuska cikin tafukan hanunnta, wani irin matsanancin kunyar Mamyn na ratsa ɓargo da jinin jikinta. Amma sai take jin inba itan ba bazata taɓa iya nunama wani ba sai ko Ummu ko su Arfa da suna raye. Rasama abin cewa Daneen Ammarah tayi, sai kawai ta miƙe jiki a saɓule cike da tausayin Iffah. Tabbas dolene ta dinga kuka, a hakan ma sai taga dauriyarta, dan in har watace tofa sai duk masarautar nan sun fahimci halin da ake ciki. Fitowa tai ta samu Malikat Haseenat da ke zaman jiran fitowarsu. “Mammah akwai matsala fa gaskiya, dole a nema likita dan yarinyar nan taji ciwo bana wasa ba”. Idanu Malikat Haseenat ta ɗan lumshe tare da buɗewa a lokaci guda. Dama ita ta fahimci hakan ai tun sanda tasa Iffah zama, ta kuma yi hakanne dama danta fahimta. Amma saboda ta sake tabbatarwar tasa Daneen Ammarah ɗin sake taimaka mata, turarrukan data bada a saka mata in har Iffahn taji ciwo mai yawa to bazata iya zama ba daman. “Ammarah wannan sirrine mai girma na shugaban daular ruman. Bazai yiwu ya fita ba kema kin san bama zai yarda ba. Dole ke zaki bata kulawar da ta dace”. “Hakane Mammah, amma ni na ɗauka shekaru rabona da yin wani abu a matsayin likita. Kar'a samu kuskure”. “Baza'a samu ba insha ALLAHU Ammarah. Na sanki akan komai shiyyasa nake alfahari da ke”. Da ƙyar Daneen Ammarah ta iya haɗiye kukan da ke taso mata. Dan in har aka tuna mata ita ɗin ƙwararriyar likitace a baya yakan sosa mata wani ɓangare na rayuwarta data shuɗe da bata son tinawa. Dan tamkar fami akan gyanbon da tasan har gaban abada bazai taɓa ya warke ba a zuciyarta ne. Muryarta na ɗan rawa ta ce, “Zanje clinic na samo kayan aiki”. Da ga haka ta fice. Da kallo Malikat Haseenat ta bita zuciyarta itama na raunana. Tana son Ammarah, matuƙar so da duk a cikin ƴaƴanta sai dai a biyo bayanta. Sai dai tana dannewa da nuna iya tausayinta kawai gudun karta raba kan zuri'arta da kanta.... ★.... Tsaf Daneen Ammarah taima Iffah da ke kuka na fitar hankali ɗinkin, wai dan ma ta mata allurar kashe raɗaɗi fa kafin ma ta taɓata. Ana kammalawa ta dinga rawar sanyi na zazzaɓi kanta kam ai kamar zai fashe da ciwo. Malikat Haseenat ta tafi domin basu waje, sai dai ta aiko da lafiyayyen farfesu na musamman da wani irin kunun madara mai zafi shima na musamman. Sai tarin wasu sirrika da Iffah zata dinga amfani da su yayin sit bath da zai taimaka mata warkewa da wuri da kuma wanda zata sha dan tasan in dai wannan yaƙinne kam Iffah yanzu ta farashi. Dan in ma fitinar ce shi kam kamar yacema kowa bai iyaba a ahalin nasa. Gashi yana ɗage-ɗagen waɗan nan shegunan ƙarafunan abu goma da goma. Daneen Ammarah sai da ta tabbatar ta gyara toilet ɗin ɗakin tsaf duk da bawani datti tunda ba'a nan suka kwana ba. Bata canja mata rigar Tajwar Eshaan ɗin da har yau take jikinta ba duk da ta mata girma da tsaho, dan ko'a wajen gashin dama sakata tai ta nannaɗe kawai. Zaunar da ita tai kan filos masu taushi amma ta kasa zama da ƙyau sai da ta karkace. Bata hanata ba ta zuba mata madarar da ke ta turiri tare da farfesun naman tsuntsayen da ke ta tashin kamshi. “Mamy na ƙoshi bakina ɗaci barci zanyi”. “A'a Ibnati daure kinji, idan kika sha madaran nan kikaci wannan naman sai na ƙarasa miki ɗayan alluran ki kwanta barci har sai sanda kukaso tashi kinji. Bakiji jikinki yayi zafi ba sosai. Haba ɗiyar albarka haihuwar alkairi”. Da wannan lallaɓawar Iffah ta fara shan madarar a hankali, Daneen Ammarah na bata farfesun da kanta cike da kulawa. A haka Tajwar Eshaan ya shigo ɗakin da sallama ya samesu. A cikin kwalliya ya ke tsaf ta alfarma ga uban ƙamshinsa da ya cika ko'ina na ɗakin, a taƙaice dai a Shahan-shan ɗin sa yake. Cikin dakewar nan tasa mai ɓoye duk wani sirrin zuciyarsa da ainahinsa yake. Idanunsa sakaye da eyeglasses. Ya wani ƙara ƙyau da cikar kamala ga wani kwarjini mai ƙara yalwata haibarsa ga mai kallo. Daka gansa kasan shi ɗinne dai ɗaya tilo Shahan-shan ɗin ƙasar ruman mai rumawa da ƙasar ruman. Sai wani shining yake da ke tabbatar da yau ɗin ranarsa ce ta musamman mai ɗunbin daraja da tarihin da bazai taɓa goguwa a garesa ba. Tun a kallo ɗaya da Iffah tai masa lokacin da yake sallamar shigowa ƙasa-ƙasa bata sake gigin hakan ba. Daneen Ammarah ma dai da ga kallo ɗaya bata sake wani ba, dan gaba ɗaya kwarjininsa ya cika ɗakin, ga wani kunyarsa da ke ɗawainiya da ita kamar itace ta aikata tsiyar ba shi ba. Koda yake shima ɗin dai ji yake Mamyn nasa a yau ta musamman ce a garesa, dan kasancewar ta a sashen nema ya sashi jin gara ya fita zuwa fada, sai kuma ga kira ya samu da ga Malikat Haseenat bayan fitowarsa Gym an wayi gari Ammien sa babu lafiya, yana shirin fitowar nan ma Jasrah tai kiran shi itama tana kuka dan tun ɗazun take kiransa ba'a ɗaga ba. Cike da dakewa ya sake gaida Daneen Ammarah idanunsa kan Iffah da ke kai kofin madara bakinta tana sha kaɗan-kaɗan. Miƙewa Daneen Ammarah tai cikin hikima ta ce ta cigaba da shan madarar da nama bara ta amso saƙon sauran magungunan ta data bada a siyo.... Shiru ɗakin ya ɗauka sai sassanyan ƙamshin da ya gaurayesa ke tashi. Taƙi yarda ta kallesa koda da kuskure duk da yanda take jin ɗakin yay mata tsukuku saboda kasancewar sa. Idanu ya ɗan lumshe da sake buɗewa a kanta sannan ya ɗan taka gaban gadon gab, zaune ya kai inda Daneen Ammarah ta tashi a gefen gadon kusa da ita sosai. Sai kuma ya kai hannu ya zare eyeglasses ɗin da ya sakaya launin idanunsa. “Good morning Mrs Eshaan Qutb”. Ya faɗa da wata irin shaƙaƙƙiyar murya mai sanyi matuƙa yana kai yatsunsa biyu kan haɓarta ya ɗago fuskarta da ƙyau. Har tsakkiyar kai muryar da yay amfani da itan ta ratsa Iffah, ga wata matsananciyar kunya da shakkarsa da ke ratsata. Idanun ta da hawaye ke cikosu ta lumshe da sauri. “Please open your eyes my life”. Ya faɗa fuskarsa gab-gab da ita batare data san lokacin da ya matsota haka ba.........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (47) ........Hawayen da take riƙewa ne suka ziraro, ta girgiza masa kai alamar bazata iya ba. Komai bai sake cewa ba, sai riƙo hanunta mai riƙe da kofin madarar yay cikin nasa tare da kofin, bakinsa ya kai ya sha madarar. Ta masa matuƙar daɗi fiye da duk madarar da yake sha. Still dai hanunsa nakan nata da kofin ya sake kaiwa ya sha. Sai da ya sha kusan sau biyar sannan ya kai bakinta itama. “Hhah”. Ya faɗa a narke yana wani irin busa mata iskar bakinsa kan idanunta da suke mar-mar, gaba ɗaya neman daburcewa take. “Kina so na buɗe da kaina?”. Da sauri ta girgiza kai da buɗe bakin kaɗan ya ɗaura mata kofin. Kaɗan tasha ta janye, sake ɗaura mata yay. Babu yanda ta iya dole ta cigaba da sha. Bai barta ba har sai da ta shanye duka sannan ya ajiye kofin. Naman ya ɗauka shima ya shiga bata yana ci har suka cinye tare da shanye romon ma duka a tare. “Sai mi kuma?”. Ya faɗa yana riƙo hanunta a nashi. Fuska a shagwaɓe ta ce, “Barci”. Murmushi yayi tausayinta da ƙaunarta na sake mamaye shi, sannu-sannu ya kai hanunta kan lips ɗinsa, babu zato taji saukar kiss a tsakkiyar tafin hannun. Idanunta ta rumtse da ƙarfi tana matse jikinta dan har cikin ɓargo sumbar ta shigeta. A tare suka sauke ajiyar zuciya, tai ƙoƙarin zamewa zata kwanta ya riƙota jikinsa. Tsam-tsam ya rungumeta yana shinshinar wuyanta da busa mata numfashinsa da ke saka tsigar jikinta yamutsawa. Luf tayi tana mai shaƙar daddaɗan kamshin turarensa mai saka zuciyar mai shaƙa nutsuwa, yanda yake hura mata iska a cikin kunne da murza yatsun hannunta dake cikin nashi tuni barcin da keta rinjayar idanunta ya fara tasiri kanta. Jin jikinta ya saki gaba ɗaya ya sashi ɗan sakin murmushin ta sake gyarata ta kwanta da ƙyau, cikin abinda bai wuce mintuna biyu ba numfashinta ya fara sauka a hankali alamar barcinta yay nisa. Numfashi ya ɗan furzar da gyara filos ɗin gadon ya kwantar da ita. Lumsassun idanunsa ya zuba mata batare da ya ɗago da ga ranƙwafawar da yay a kanta ba. Wasu kalamanta ne na jiya suka shiga dawo masa a rai, wani lallausan murmushi ne ya suɓuce masa ba shiri, ƙoƙarin haɗiye kayansa yay da sake matsawa da ƙyau jikinta ya sumbaci goshinta da hancinta da lips ɗin da sai da ya ɗan juya su a cikin nasa sannan ya saki. Bargo yaja ya lulluɓe ta da ƙyau ya miƙe... Koda ya fito falon bai saurari abincin breakfast da aka shirya masa ba. Hakama Daneen Ammarah bata falon, sai amintaccensa kawai da ke dakon fitowarsa. Gaisuwar amintaccen hadimin nasa ya ke amsawa yana nufar lift.. yayinda shima yake biye da shi da hanzarinsa. Fada ya fara nufa cikin takun nan nasa ɗaɗɗaya na izza da ƙasaita. Shigowarsa da aka sanar tun kafin ya iso ya sa duk wanda ke a wajen miƙewa kai a ƙasa har sai da ya kai zaune. Suma duk zaman sukai cike da girmamawa suka shiga miƙa gaisuwa suna satar kallonsa dan yay musu wani fayau da sake cikar kamala kamar wanda akaima wankan inji. Saɓanin ko yaushe kuma yau fuskar da ɗan sassauci duk da bawai dariya yake ba ko murmushi. Tana nan dai kadaran kadahan bata tsuke sosai ba bai kuma saketa ba. Kamar ko yaushe amintaccensa ne ya amsa da yawunsa. Da ga haka aka ɗanyi zaman fadanci masu ƙorafe-ƙorafe suka kawo yana saurarensu. Hakama masu shawara akan masarautar ko wani abu da ya faru harma da wajenta. Na masarautar dai duk sun samu rinjaye ne akan abinda ya faru tsakanin Miran Jasim da iyalansa. Komai baice akai ba, yana dai jinsu da kunne bisa ra'ayinsu har gardama ma ta ɗan nema sarƙewa sai da Sayeed Anwarus-sadat ya tsawatar. Baice komai game da rashin ganin Miran Arshaan ba, shima kuma Miran Jasim ɗin da aka sanar masa ya matsa an sallamesa tun a daren jiya baice komai ba a kai. Zaman gaba ɗaya bai wuce na awa biyu ba lokacin sallar zuhur yayi.... Bayan an idar da salla ya samu rakkiyar manyan masarautar duba mahaifiyarsa. Duk da amota suke duk inda motocin suka gitta hadimai ƙasa kawai suke zubewa kawuna a sunkuye har suka ƙarisa ƙofar sashen. Motar da yake ciki ma har cikin barandar gaban falonta ta tsaya. Amintaccensa da yay saurin fitowa da ga gaban motar ne ya buɗe masa. Shiru babu alamar zai motsa balle ya fito har sai da minti ɗaya da sakkani ya shuɗe. A hankali ya ziro ƙafarsa dake cikin takalman masu tsananin ƙyau da ɗaukar idon mai kallo farare tas heif cover, sai da ya sake jan wasu sakkanin kafin ya zuro ɗayar, nan ma ya sake jinkirtawa sannan ya fito gaba ɗayansa. Tuni mayataccen ƙamshinsa ya mamaye sashen tunkan ma ya shiga. Hadimai kam rige-rigen shigewa suke dan mai RUMAN ne fa da kansa ba aike ba. A waje kam jami'an tsaro sun zagaye sashen tamkar ba'a cikin gida ba. Ameera Danish-Ara da ke zaune a falon tare da Ameera Haifah da wasu a cikin matan masarautar masu faɗa aji da suka shigo duba Malikat Bushirat ɗin tuni sun miƙe kawunansu a ƙasa. Takun sawayensa kam tuni ya saka kowa nutsuwa kowa na satar kallon hanyar da zai shigo da kallo. Yayinda ƙafarsa ke taka cikin falon babu wanda bai ja numfashi ba, dan a wajen ado kam kowa shaidane Tajwar Eshaan ibn Haysam Abdul-majeed ɗawusu ne. Ƙamshi kam ba'a magana idan yana waje kowane turare disashewa yake duk ƙarfinsa. Ko sau ɗaya bai kalli kowa ba, takunsa yake a nutse cikin izza da ƙasaita da ka gansa kaga gwarzon gwaraza mai gwara kawunan gwarzo mai son nuna gwarzantaka. Gaisuwar da suke ta faman masa Sayeed Fayzul-haq ne dake take masa baya kawai ke amsawa. Dan sauran jama'ar da ke a tare da shi duk a farkon shigowa falon suka ja birki. Sayeed ɗin ma a ƙofar ɗaki ya dakata bayan ya buɗe masa ƙofar ɗakin da akai musu iso Malikat Bushirat na ciki. Isar ƙamshinsa ciki kafin shi ya saka Jasrah da ke kusa da ita tana bata shayi miƙewa da sauri. Malikat Bushirat kam idanunta dake matuƙar jazur ta zubawa ƙofar zuciyarta na wani irin bugawa da sauri-sauri. Tunda ya shigo shima kaifafan idanunsa dake sakeye cikin gilashi na kanta. Nata dake cikowa da hawaye ta rintse da sauri tana kauda kanta, wani irin zafi takeji, zafi mai amsa suna zafi na gaske a ƙirjinta har tana jin turirinsa a maƙoshi. A maimakon zama a kujerar da Jasrah ta gyara masa bakin gadon ya kai zaune. Hannun Ammien tasa ya kamo a hankali cikin nasa ya sumbata. Maimakon murmushi da take sakar masa a da idan yay mata hakan yanzu hawaye ne masu zafin gaske da ta kasa riƙewa suka ziraro da gudun tsiya kan ƙyaƙyƙyawar fuskarta da duk ta dame kamar ba Malikat Bushirat ɗin nan ba ƴar gaye, hamshaƙiya ƴar ƙwalisa. Idanunsa ya rumtse a hankali hawayen na ratsa har tsakkiyar zuciyarsa. Ya jima a haka kafin ya buɗesu ya sauke a kanta. Handkherciff ɗin jikinsa ya zaro ya miƙa mata, tare da motsa lips ɗinsa a hankali ya furta, *“لاَ بَأْسَ طَهُورٌ إِنْ شَاءَ اللهُ .* _La ba'asa tahoorun in sha'al-lah._ (Ba komai, tsarkaka ce in ALLAH ya yarda). أَسْأَلُ اللهَ الْعَظِيمُ، رَبَّ الْعَرْشِ الْعَظِيمِ أَنْ يَشْفِيكَ *.(سبع مرات)* _Asalul-lahal-'azeem rabbal-'arshil-'azeem an yashfeek._ (Ina rokon ALLAH mai girma, UBANGIJIN Al'arshi mai girma, ya warkar da kai)”. _(MANZON ALLAH, tsira da aminci su tabbata a gare shi, ya ce; “Babu wani bawa Musulmi da zai ziyarci mara lafiya wanda ajalinsa bai riga ya zo ba, sannan ya faɗi wannan (addu'a) sau bakwai face ya sami lafiya".)_ (ALLAH ya azurta marasa lafiyar mu da lafiya, ya basu ikon cinye jarabawa, yasa ta zama kaffara garesu. Masu ita ALLAH ya ƙara musu, ya karemu daga cutukan zamani masu haɗari da hana nutsuwar zukata😭🙏). Damƙe handkherciff ɗin kawai tai taƙi share hawayen da suka gagara tsayawa. Sai Jasrah ce ke faman amsa addu'oin sa da sannu. Cikin damuwa ya kalli Jasrahn batare da yace komai ba. Ta fahimcesa, dan haka ta fara bayani tana sharar hawaye itama. “Nima ban san ainahin abinda ke faruwa ba wlhy. Amma dama kwana biyun nan duk bata cikin walwala. Na kuma tambayeta amma tace min babu komai yanayine kawai, sai jiya dai da ƙyar ta ce min akan matarka ne, tace ka saketa amma ka share ko zancen baka sake tadawa ba, ta nema iso gareka ance ka shige ciki a jiya after isha'i. Ni dai na bata haƙuri da nuna mata abi komai dai a sannu kodan abubuwan da suka faru na rasa matanka da kai idan kuma akace ka saki wannan haka ɓakatatan ba'a kai ƙarshen case ɗin nan ba maimakon ita da bata da gaskiya sai a koma zarginka kai. Ta nuna kamar taji ma wuce, amma sai banyi barci cikin nutsuwa ba dan nasanta da saka abu a rai, shine ana idar da sallar asuba nazo dan gaisheta na sameta a ƙasa babu alamar rai tattare da ita. Na nemeka amma baka ɗaga ba, dole nai kiran amintacciyarta dan ta sanar da Mammah. Sai da ma sukazo ne muka iya ɗagata a ƙasan ni da Nina Ammarah da ƙyar, kafin a kira Doctors sukazo kanta har dai ALLAH yasa ta farfaɗo suka sake maidata barci dan tanata zabura kamar wadda ke a firgice. Sun tabbatar jininta ya hau ƙololuwa har yanama zuciyarta barazana ma. Amma dai yanzu data farka Alhamdullah Dr Aliyah tace jinin ya ɗan sauka bakamar ɗazun ba”. Idanu ya kafe Malikat Bushirat ɗin kawai da su na wani tsawon lokaci, kafin ya furzar da iska cikin damuwa ya furta, “Why Ammie? Why zaki jefa kanki irin wannan haɗarin saboda ni. Kina tunanin idan wani abu ya sameki zan iya yafema kaina? Haba Ammien na, ki tausaya mun karki maidani maraya gaba ɗayana babu uwa babu uba mana. Yayin da na rasa Abbie sai nake kallon fuskarsa tare da taki a waje ɗaya, hakanne ke samun nutsuwa na share hawayen da suka kwaranyo min kafin su zubo a kowane lokaci saboda kewarsa. Banƙi biyayya gareki ba, sai dai ina son kareki da ga abinda zai iya zuwa ya dawo game da umarninki gareni. Yarinyar nan tabbas mai laifi ce, laifin data ambata da bakinta ta aikata. Sai dai kuma ni shugaba ne, tanada hakkin da zan bata kariya a yayin da akai yunƙurin cutar da ita itama akan dalilai biyu. Ita ɗin MATATA ce....” wani irin rumtse idanu Malikat Bushirat tayi, kalmar matata ce ɗin na mata wani irin sukar mashi a ƙirji, ya cigaba da faɗin, “Akwai haƙƙoƙinta a kaina dolen dole. Sannan ni Shugaba ne, banda hurumin yanke hukunci cikin fushi ga talakawana har sai nayi bincike. Sannan ma abu na ƙarshe da kike zargin ta aikata ba'ita bace ba. Zaki tabbatar da hakan kuma a zaman shari'a na uku gobe insha ALLAHU. Nayi miki alƙawarin gaggauto da sake zaman shari'ar gobe kodan mukai inda kike buƙata. Fatana dai yanzu ki kwantar da hankalinki, ki sama ranki haƙuri Eshaan ɗin ki na tare da ke ɗari bisa ɗari, mai kuma bin umarninki ne a duk sanda kika bashi, bazan taɓa zama mai bijirewa ba in har ba'a taɓa hurumin UBANGIJINA ba”.........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 Book two(48) ....Sam kalamansa babu abinda suke kara mata sai suka a zuciya, Amma sai ta dake ta daga masa kai kawai tana dan murmushin karfin hali. Tare da kai hanunta saman fuskarsa ta shafa da fadin, "ALLAI yay maka albarka". A hankali. Murmushi ya mata shima a karo na biyu yana mai lumshe idanunsa da budewa lokaci guda ya ce, "Amin nagode Ammie, ALLAH ya kara miki lafiya da tsohon rai mai albarka" akan lips dinsa. Da ga haka ya dauka shayin da ya samu Jasrah a bata ya cigaba da bata da kanshi. Sha take tana kallonsa tare da kara tabbatar da zancen uwa. Dan kuwa babu abinda kake gani a tattare da shi sai nutsuwa da tarin cikar kamala. Fuskarsa kam sai shining take da daukar idon tabbatar da shi ango ga duk mai iya kallonsa. Ga wani kamshi da take i can kasa-kasa a cikin nasa da ke bata tabbacin na mace ne. Hawayen da ke sake taso mata take dannewa, dan yanzu kam tama fi bukatar kowa ya fice a barta ita daya saboda tana bukatar ganawa da wa. Dole ta samu mafia, dan bazata taba barin yaronta daya tilo ya sake kusantar mafi zama makivarta kololuwa ba. Ko zatai vawo tsirara sai taga bayan yarinyar nan, sai taga banda ya tsaya mata, sai taga yar ban wacece ita, mita taka ne haka da zata zamewa cikar burinta barazana, burin data dauka tsahon shekaru tana ginawa da kauda duk wanda ya nema shiga gabanta koda a kuskure ne. Itace fa ki gudu sa maze gudu TA-KURYA sa maza kurya. Wutar gobara kasheki koda taro sai an dace. Matar Shahan-shan din RUMAN war Shahan-shan. Never for ever ta fadi kasa a dalilin var cikinta da da'ace dan cikinta auren wuri yayi babu abinda zai hana ya haifeta". Ganin kamar ta dan saki jikinta har tasha magani bayan tea din da tasha Jasrah ta hada mata ruwan wanka sai kawai yay musu sallama dan sallar la'asar na gabatowa. A can kasan ransa kam hankalinsa ya rabu biyu ne. Wani na nan wani nakan Iftah da itama ya baro cikin halin da ya jefata. Sosai Jasrah taji dadin zamansa tare da su gain yanda yar war tata ta dan sake, hakama Malikat Bushirat din ta nuna jin dadinta a zahiri, amma ita kadai tasan kunci da dacin da ke zagaye da ruhinta... Barci tayi sosa dan har akai sallar azhar bata farka ba. Daneen Ammarah da ke a sashen zaune takan lekata lokaci zuwa lokaci. Sai kusan 3 ta farka. Yanda ta danvi dama-dama fuskar ta sabe sosai da kumburin ido ya sata in sanyi a zucivarta, Ga zazzabin ma ya sauka da ciwon kan. Ta rage rakin zafi-zafin sai dai idan ta motsa da dan karfi takan aije lips. Ruwa mai dumi sosai Daneen Ammarah ta hada mata. Da taimakonta ta kara sit bath sannan ta barta tai wanka da karasa kimtsa jikita. Kafin ta fito an sake gyara dakin da kunna masa turarruka komai ya dauki haramin kamshi. Kayan da aka kawo da ga sashen Malikat Haseenat masu kyau da daukar idanu ta alive mata ta fice da dan mata short not ta ajive. Cikin dabara ta fito tana cizar lips. Jinta take sakayau kamar iska zata iya daukarta. Ga bakinta daci sosai, Hatta tsamin da jikinta yay dazun yanzu duk ya saki sal can da idan ta motsa take in ciwon kadan-kadan. Yanzu ko data shiga ruwan zafi da sake gasa ikinta ma sai ta kara in dadi ko'ina ya mike mata. Ta dan ji dadin rashin gain Mammy, dan kunyarta take ji ALLAH dauriva kawai take vi. Da kanta ta dan daddogara ta shirya cikin kyakykyawar abayar baka da tasha adon duwatsu sai walkiya take. Harda b8p a cikin kayan. Salla ta fara gabatarwa a daddafe, tai achar tai la'asar da taga lokacinta vayi. Tana sallar Daneen Ammarah ta sake shigowa har sau biyu. Sai da ta idar ta lura da kyawawan kwanikan dake ajiye. Tana kan sellayar zahe Daneen Ammeran ta sake dawowa. Zama tai a kusa da ita tana tambayarta yaya ilkin. A shanwabe ta amsa mata cewar da sauki. Daneen Ammarah tai murmushi kawai batare data sake cewa komai ba. Sai ma abinci da tai kokarin zuba mata da talmakonta kuma ta dan ci dan girki ne na musamman da ga Mammah. Ta dadin vanda taga tari ganoshen naman da dan Rirk, ta bata magunguna sannan tai zaman busar mata gashi da dazum balar ba. Tsaf ta gyana mata shi ta daure sannan ta gyara mata fuska da kara saka mata was turarruka masu masifar kamshi da bata san da su ba. Ta kuma sakata yin tsugunno kan was turarrukan dai bavan wanda tai wanka da su a bavi lokacin da zatayi. Daneen Ammarah ta sauke duk wans neuvin da taken tai zaman ima Iffah nasiha da bata shawarwarin da Jaav taimaka mata a matsayin da take a yanzun mai banbanci da na baya. Sosai nasihar ke shigarta vanda ya kamata, da da karshe ta sanya mata albarka tari-tari sannan ta dore mata wayar Tajwar Eshaan da ta gani akan side drawer ta rike dan ta debe mata kewa kalm ya dalo, ta Kuma icunna mate television dir dakin ma ta aive mata remote kusa da ita da barpusm da Mammiali duk ta aiko mata elkin kavan abincin lunch. Ji Iffah tai kamar tai kuka, dan toro take ji a sake barinta da ga dasal shi a vanza. lla kadar lasan abinda ta fuskanta a daren jiya a hannun bawan. ALLAHn nan. Ita kanta Daneen Ammarah tausavin barin nata take. Amma yaya zatayi sai kawai ta zabi binta da addu'a dan bata so ya davo ya sake taddata a sashen.. Ajiyar zucia ta dan sauke da hadiye hawayen da suka ciko mata idanu, wani irin kewar yan uwanta take ji fiye da ko yaushe a yau din nan. Ganin zata saka kanta a damuwa tai musu addu'ar samun rahamar UBANGIJI ta dauka remote di da Mammy ta ajiye mata ta kunna tv. Searching channels ta faravi a hankali harta samu inda wani film mai kvau ya dauka hankalinta, sai dai film din akwai abun tsoro a ciki. A kan lips cikin disashiyar muryarta ta furta, "Bari muga kozan iva". Tana gara zamanta ta jingina da fuskar gadon tare da daukar popcorn din ta tasa a cinya tana kaiwa baki da daddaya.... Koda wasa bataji shigowarsa ba, dan hankalinta gaba daya ta maida shi ga kallon film dinne, duk da atsorace take kuma, wani gun ma har sai ta boye fuska an dan wuce take iva cigaba da kallon. Zamansa kusa da ita da saukar numfashinsa a gefen wuyanta ya sata yar zabura harda shirin fasa kara. Guntun murmushinsa din nan kamar na dole ya saki yana rikota. "Hy relax". Ya fada cikin rada kamar mai tsoron aji su. Idanunta ta rumtse da karfi ta sake budewa zuciyarta na wani irin gudu da sauri-sauri dan ta toratan fa da gaske. Cikin tura baki ta juya idanunta da har yanzu basu gama bajewa gaba daya ba tai masa yar hararar data nema tsarga masa zuciya. A hankali ta ce, "ALLAH kaban tsoro ka nema afuwa na". Yanzun ma murmushi ya sake yi, batare da yace komal ba ya gara zamansa yana daura kansa a kafadarta idanunsa akan television da take kallo. Cikin rada-dara da kamo hanunta da ke cikin popcorn din ya kai wanda ta dakko guda daya bakinsa yana fadin, "Babu tayi ne?" ya kare maganar da kallonta. Da sauri ta kauda idanunta da ga kallon da take masa ta maida ga tv cike da basarwa, a shagwabe ta ce, "Gashi kaci ba'a baka ba. Ina vini". Idanunsa va dan lumshe da budewa va tashi da kyau yana matsota jikinsa sosai kanta da bayanta suka koma saman kirjinsa, yayinda take a tsakkiyar kafafunsa. Ita duk jitai zaman ma ya bata kunya, amma ya ta iya dole ta dake dan Mamy ta mata nasiha sosai akan ta saki tiki da milinta karta bada wata kofa da zai y dana sani kan auranta ko tunanin mallakar wata mace saboda gazawarta. Kafarsa daya ya ajive a dan dogare yanda ta sake samun jin dadin zaman. Kusan mintuna biyar bai sake cewa komai ba itama bata sake ba idanunsu duk suna a tv. Yayinda yake kamo hanunta da take dibo popcorn din yana kaiwa bakinsa. Cikin maganar nan tasa kamar ta dole ya ce, "Kinci abinci?". Kanta ta daga masa tsigar jikinta na tashi saboda yanda yay maganar cikin kunnenta. Hannunsa na dama ya sakalo saman cikinta yana shinshinar wuyanta. "Ban yarda ba, mi kika ci?". Cikin yar in ina da son janye jikinta amma ya hana hakan ta ce, "Mammy ta bani gasashen jan nama da madara" "Uhm yar gatan Mammynta. Shine baki rage mun ba kuma? Gashi ina jin yunwa sosai banci komai ba tun wanda kika tsammin". Ita gaba daya jitake kamar an canja mata shi da wani ba Shahan-shan din nan miskili mai shariva da magana ma sai ya jinjina ta ba kafin yayi, duk da a yanzun ma daddaya yake yinta kamar abun dole. Kasa cemasa komai tai, dan gaba daya ita yamasa ta daina fahimtar film din ma. Shi kansa baima san mi yake ba, abinda kawai ya sani ta gama mamayesa da komansa. Tsananin begenta yake da jin kishin sake kasancewa da ita. Amma zai daure bazai aikata ba kodan tausayinta, ballema dinki da akai mala. Da. kyar ya dan dai-daita kansa, itama cikin dan rawar murya ta ajiye popcorn din zata mike. Riketa yay kamar mai tsoron ta gudar masa (g . A shagwabe tana narke fuska ta dubesa, sai kuma ta risinar da idanun da take kyakykyaftawa, "Zan samo ma abincin ne fa". A hankali ya saki hanun nata yana lunshe idanu da sake budewa a kanta gaba daya laurun idanuma ya canja Yanda take tafiya kaman a hahharde kuma a hankali yabi da kallo, tausayinta duk sai ya sake mamayesa. Yaso ya dakatar da ita, amma sai maganar kuma ta masa wahala dan yunwar kuma yakeji da gaske. Tan madarar da ya sha a wajenta da dan naman nan bai sake cin komai ba. Koda ya shigo bayan sallar la'asar kuwa baiko kalla dining room din ba ya shilge. Wanka kawai yay ya canja kayansa ya taho dubata tuna vasan a vanda ya barta sharban da safen nan.... DAUDAR GORA....!! Chapter: 49 Kyakykyawan bowl din data dauro saman tray mai kyau shima da tambulan din madara yabi da kallo. Ta ajiye a saman dan table din data janyo kusa da gadon kasancewar a baki- baki ya ke zaune shi ta daura. Bowl din ta bude tana dan kallonsa kasa-kasa kamar yanda yake binta da shegen kallon nan nasa. A saman lips ta furta "Kana son shi?". Gasashen naman da ke ta tashin kamshi mai tada kwadayi ya dan kalla. Batare da yace komai ba ya kamo hanunta da ke rike da murfin ya zaresa ya ajiye. Rikota yay ya zaunar a kusa da shi. "Sai dai in zaki bani da kanki. Hannuna ciwo suke min". Yanda yay maganar acan kasan makoshi matuka ya sata kallonsa da sauri, ido daya ya kashe mata da sakar mata wani lalataccen murmushi daya nema raba jikinta na numfashinta. Da sauri ta maida kan ta risinar zuciyarta na wani masifar harbawa da sauri-sauri. Hannunta ya riko cikin nasa ya dan murza yana kara narkar da idanunsa kan fuskarta Cikin sake tausasa harshe da cigaba da murza hannun ya ce, "A duk lokacin da kike tare da15:37 hannun ya ce, "A duk lokacin da kike tare da < an ki kallesa abokin ki, amininki, yaya A kal harma kaninki idan ya kama, sannan farin cikin ki. Ina son gidana da iyalina su kasance aljannar duniyata da duk inda naje na dawo da damuwa za'a goge min shi da farin ciki, duk sanda kaina ya dauka zafi za'a sanyaya min shi da nishadi. Duk sanda na shigo da farin ciki za'a tayani yi har ma a ninka min shi da wani da yafi wanda nake tare da shi. Anan Eshaan sunansa Eshaan Ion Haysam Abdul-majeed MIJIN Fhareedah (Iffah) bint Zayyan ba Tajwar Eshaan ko Shahan-shan ba. Ki raineni kamar jariri a fadarki, Ni kuma mai sallamawa ne gareki duk rintsi TAURARUWA TA". Wata irin nutsuwa ce ke ratsa mata zuciya, tabbas tana jin dadin kasancewa da shi, amma har yanzu bata san mi takeji game da shi ba. Ita dai kawai yana burgeta, a cikin ado ko sabanin hakan. Sannan duk da taji ciwo da a jikinta da jigatuwa a jiya batajin haushinsa ko jin bai kyauta ba, dan koba komai tayi ilimin addini, tasan hakkokin mace aka mijinta, tasan hakkokin miji akan matarsa, tasan muhimmancin aure da fa'idarsa. Ta kuma san Shahan-shan bazai taba sakinta ba koda ace zata bukaci haka. Mammy ta sake tisa mata fiye da abinda ta sani, har ma da wanda zatayi domin tabbatar da kanta a matsayin diya MACE a gabansa ko gaban wanin sa "Wayyo!". A ada yana matse ciki, da sauri ta kalles yamutse fuska kamar gaske shi adole yunwa yake ji. Cike da nuna damuwa ta ce, "Sorry". Sai kuma ta dakko tray din saman cinyarta. Cokali ta dauka zata diba naman ya rike hannun. Kallonsa ta sakeyi da mamaki. Cikin dan dage gira ya ce, "Nikam da hannu nake so". Komai batace ba ta ajiye cokalin kawai, tare da ajiye trayn ta mike, bai ta nufa bata wani jima ba ta dawo da alama hannu ta wanko. Tray din ta sake maidawa saman kafarta bayan ta koma inda ta tashi ta zauna ta debo naman ta kai bakinsa. Hannun ya riko da kyau ya karasa da naman bakinsa yana lumshe idanunsa, harda sakin siririyar ajiyar zuciya. Ita sai ma abin ya bata dariya harda murmusawa. Wani irin sanyi da nutsuwa yaji har cikin ranta ganin tayi murmushin. Dan gaba daya yau bakin ya mutu kamar ba ita ba, shi kuma yafi son yaga ta saki jiki da shi tana kiriniyarta da surutu kamar da. Sosai yaci naman har hakan ya bata mamaki, hakama madaran. A hankali ta rumtse idanunta sanda yake tsotse yatsun hannun abin kamar da gayya. Da gayyar kuwa yake yi, dan yana kallon yanda take faman matse ido yana murmushi a zuciyarsa Bai bar dakin ba sai da ana kiran sallar magariba < . Yace ta shirya kafin ya dawo zata rakasa wani waje. Da to ta amsa masa kanta a kasa, dan duk wannan abun da ake bata yarda su hada ido sai da kuskure. Bayan fitowarsa alwala a bathroom har ya wuceta ya dawo da baya, kama ta yay ya mikar tsaye da ga zaunen da take. Fuskarta ya dago dan taki yarda ta kallesa, shima bai matsa da sai ta kallesan ba ya manna ma goshinta sumba mai lafiyar da har sai da ta sanya jikinta motsawa. Idanunta a rufe har sai da ya fice sannan ta bude tana sauke nannauyar ajiyar zuciya, ita har yanzu ta kasa sabawa da salon nasa sam. Sai da ta dan kara gasa kanta kamar yanda Mammy tace ta dinga yi akai-akai sannan tayo alwala ta fito gabatar da sallar magriba. Bayan ta idar zama tai tunani mai zurfi akan Tajwar Eshaan, mutum nan nada abubuwan ban mamaki boyayyu, tabbas ta yarda hatsabibin kansa ne kamar yanda su Miran Arshaan ke fada. Gaskiya tana bukatar sanin yanda akai su Baby suka kasance a wata kasa bayan su Miran Jasim sun mata karyar ya kashesu. Kenan video din data gani jabu ne ko mi?. Rashin amsa da bukatar samunta ya sata mikewa ta gabatar da sallar isha'i da ake kira. Bayan ta idar ta shiga gyara jikinta dan haka kawai take dokin fitar duk da bata san ina suka nufa ba. Tsaf take cikin bakar doguwar rigar abayar datai mata kyau,sai Ver din nan da in aka nada yake yi kamar baoy hijab fari. Fitowa tai tsabar zumudin son fitar ta su. Dakin da suka kwana ta nufa duk da bata zaton ya isa dawowa salla. Kusan a tare suka aura hannayensu kan handle din kofar, ita ta tura shi kuma ya ja batare da kowanne yasan da dan uwansa ba. Cak ta tsaya kanta a kasa tana mai rumtse idanunta dan wata irin kunyarsa takeji har cikin kashinta. Ga kwarjini mai irin mamaye waje din nan da ya kara mata. Kusan minti daya suka kwashe a wajen ita bata tanka ba shima bai ce ba. Tasan in zasu kwana ma zai iya, dan haka ta dan saci kallonsa ta gefen ido. A hankali ta janye idanun nata gain yanda ya kafeta da shegen kallon nan nasa mai hanata sukuni. Sai ta samu kanta da in inar fadin, "Barka da dawowa". Karamar ajiyar zuciyar da bata ji ba ya yayi a ciki, batare da ya amsa gaisuwar tata ba ya karasa fitowa, fuskar babu fara'a sam kamar ko yau she, sai wani irin kwarjini mai cika idon mai kallo, a fisge ya furta, "Muje" yana rabata ya wuce cike da takun nan nasa daddaya. A hankali ta dan sauke numfashi dan jinta take kamar an daureta a wajen, sai kuma ta bisa da kallo kasa-kasa tana mai tsarkake sunan UBANGIJI mahaliccin wannan kyakykyawar halitta. (Kyau dai kam ALLAH ya bashi, sai dai miskilancin nan da jin nan da ke zagaye da shi) ta dan nal fuska kamar zatai magana, sai kuma ta fasa ranta fal tunanin ina ma zasu je a daren nan? rashin mai bata amsa ya sata dan zabura tabi bayansan. Ganin ya nufi lift.. taji duk ta tsure. Ita dai harga ALLAH abin nan baya wani birgeta. Dan indai ta shiga sai tayi hajijiya. Shiyyasa ya zamto sai ta rike wani dan batama taba gigin shiga ita kadai ba. Jiki a sabule ta shiga, jin kofar ta rufe kanta ta rumtse idanu da sauri, sai kuma ta bude akan yatsansa da ke kokarin danna inda yake bukatar suje. "ALLAH ina jin toro" ta fada kamar zatai kuka. Sarai ya jita, amma sai bai nuna yaji ba ya gyara tsaiwarsa bayan ya danna 2 floor. Iffah da ke jin kamar ta fasa kuka a hankali tai yunkurin zamewa dan gara ta zauna zai fi mata sauki. Babu zato taji an riko mata hannu, kafin ta iya ko bude idanunta tajita cikin jikinsa da ke fidda wani irin sirrintaccen kamshi mai ratsa zuciya da bargo da bazata taba iya mantawa ba. Da sauri ta bude idanunta sai ko cikin nasa da ke kallonta, dole ta maida nata ta rufe da sauri zuciyarta na wani irin bugawa da sauri-sauri, tabbas bazata mance wannan turaren ba, dan turarene da ta dinga fafitikar nema a washe grin da aka dakkota da ga sashenta cikin dare aka maidata nashi. Kenan da gaske shi dinne ya je ya dakkota kokuwa yaya akai? Dan wannan Kamshin dai shine. Tsaf ya fahimci inda ta nura, kuma a randa ta dinga neman turaren ya sani sarai, abinda bata sani ba ya ajiye abinsa ne kawai inda bataima zaton ganinsa ba o kawowa a ranta zai ajiye din. "Zamu kwana anan ne?". Ya fada a kasan makoshi yana kallon kyakykyawar fuskarta da ke kwance a kan kirjinsa. Idanun ta bude, sai kuma taja jikinta baya kunya na wani mamayeta. Dauke idanunsa yay da ga kallonta ya fice, itama sai ta bisa tana sauke ajiyar zuciya a jajere, sai kuma ta saki murmushi dan ita da kanta kunyar kanta taji. Wata hanyar da batama san da ita a wajen ba suka nufa, koda yake bawai ta taba shiga wani waje a floor 2 din nan bane bayan falo, shima a randa Malikat Haseenat ce ta kawota da suka biyo komai daki- daki ba kamar yanda yay ba yanzu Inda suka shigo dinne ya sakata tsayawa turus tana kallonsa. Sai kuma ta dan waiga ta kalli hanyar da suka fito, ita fa gaba daya notikan kanta sun kwace, ta ma rasa ta yanda zata misalta ta inda wannan hanyar take a zahirin cikin gidan, dan ita shaidace tsakanin sashensa da na Malikat Bushirat akwai nisa. Duk da sunyi yar tafiya suma amma sai gasu cikin sauki. Kallonsa tai fuska a marairaice kamar ba Iffah'r nan matsiwaciya ba da ya sani ta ce, "ALLAH toro nake ji". Kallonta yake da shanyayyun idanun nan nasa masu kaifi kamar bazaice komai ba, sai kuma jitai a hankali kamar mai rada ya furta, "Nima tsoron nake ji ai". Idanu ta dan waro alamar mamaki tace, "Kai din?". Kansa ya dan kada mata da lumshe idanunsa ya bude duk a lokaci daya. Sai kuma ya kai hannunsa kan nata ya matsota jikinsa. "Ki karamin karfi". Ya fada yana rungumeta cikin jikin nasa. Daburcewa tai ma ita gaba daya. Tai kokarin dagowa ya hana hakan. Dole ta hakura tai luff tana mai shakar kamshin da jikinsa ke fitarwa mai azabar dadi. Kusan minti biyu suka kwashe a wajen kafin ya dagota a hankali, kin yarda tai su hada ido sam, shima sai bai matsa ba ya ja hanunta kawai yana dan murmushin da iyakarsa makoshi suka shige. 15:39 DAUDAR GORA...II Chapter: 50 Zaune take kan gado tun bayan idar da sallar magrib da Jasrah ta taimaka mata tayi kafin ta wuce. Idanunta tsaye suke kyam a waje guda alamar tayi matukar zurfi a tunani, dan sam hankalinta ma baya a cikin duniyar mutane, ya tafi ga yanda zata shawo kan uwa ne kwai da kuma gusar da Iffah datai kane-kane a cikin rayuwar danta, dan tasan abinda uwa ta fada babu fashi bazasu taba canja sharadinsu ba inhar bata karasa cika alkawransu ba. Ita mai bada labari ce akan bijirewar da surikinsu (Tajwar Abdul-majeed) yay da abinda ya biyo bayan hakan, dan har yanzu hukuncin uwa na biye da su daki-daki wanda shine ma makasudin komai akan kanta yanzu haka da tushen faruwar komai akanta. Tun dazun gaba daya hankalinta a tashe yake. Tana ta kokarin kiranyen uwa amma babu alamar zata ziyarceta,wannan shine mafi zama kololuwar tashin hankalinta a yanzu. Motsi da kamshinsa ya sata dago manyan idanunta farare tas da a yanzu launinsu gaba daya ya koma jazur har baka iya gane bakin ma da kyau. Duk da fushin da take da shi bai hanata jin sanyi da ganinsa ba a cikin ranta, dan da gaske shine abu mafi kololuwar soyuwa a gareta a kaf abinda take ganin ta mallaka a diniva KAfesa tai dA kallo rike da so da kauna, sai dai tana kokarin dannewa a zahirance. Wani irin harbawa zuciyar Iffah da girarta ta dama sukayi a lokaci guda, tai saurin ja ta tsaya da kokarin son janye hannunta da ke a cikin nasa. Amma sai yaki sakinta har sai da suka isa gaban Malikat Bushirat da sai yanzu ta lura da Iffah da ke faman boyewa a bayansa Hannunta ya jawo a hankali ta dawo gabansa idanunsa akan Malikat din dake wani irin kallonsa. Sassanyan murmushi ya saki kadan dai-dai yana sakin hanun Iffah'r da kaiwa duke ya kamo na Malikat Bushirat ya saka na Iffah ciki sannan ya ja da baya zuwa bakin gado ya zauna abinsa tamkar baiga kallon da Ammien tasa ke masa ba. A wani zafi Malikat Bushirat ta yarfar da hannun Iffah'r tana watsa mata mummunan kallo. Iffah da kanta ke wani irin yamutsawa tun shigar hanunta cikin na Malikat Bushirat din ta bude idanunta da suka kada jajur. Amma sai taki kallon kowa a cikinsu tama risinar da kanta da fadin "Ammie ina yini?". "Mi wannan tazo yimun nan?". Ta fada ranta a matukar bace tana maida kallonta ga Tajwar Eshaan maimakon amsa war da Iffah tai mata. Shiru kamar ba Adi ba, ran Malikat Bushirat ya kara sos matuka, duk da sanin halinsa ne dama hakan. Sai da ya mula dan kansa sannan ya dubeta yana dan guntun murmushin daya sake harzuka Ammien tasa. A hankali ya motsa lips dinsa yana lumshe idanu da budewa. "Ammie! Munzo mu baki hakuri ne, ta kuma dubaki. "Hakuri? To nace mata ina bukatarsa ne.Saiful-malik ka fita idanafa ko. Ka fita idona karka bari akan yarinyar nan mu samu matsala da kai. Ita bata kai matsayin da zata zama kO abin kallona ma balle har a saurari wani abu daga bakinta. K! Tashi ki fitar min anan, karna sake ganinki a cikin idanuna, inba hakaba sai kinyi nadamar sake maimaita wanna kuskuren. "Ammie. Da sauri ta daga masa hannu, "Na fada maka bana bukatar jin komai daga gareka, kuma ina akan bakana na sai ka saketa. Inba haka ba Eshaan zan baka mamaki da ga nan zuwa safiyar gobe in har baka janye garkuwar daga bama yarinyar nan ba tare da takardar saki uku. Wani irin lallausan murmushi Iffah ta sakikamar ba'a kanta ake dambarwar ba. Ta dago a hankali ta dubi Malikat Bushirat, sai kuma ta maida kan Tajwar Eshaan. Hada ido sukai, ta sakar masa wani murmushin da yafi Nafarko neman wargaza masa lissafi. "Mutuwa da rayuwa gaskiya ne *_Sultan_*, kamar yanda kaddara da jarabawa suke abokan rayuwar kowane dan adam. Ammie tayi gaskiya, ban cancanci GARKUWA da ga gareka ba, sannan kuma igiyar aurenka bata dace da cigaba da zama kan mace irina ba. Nima a yau na fahimci komai, na gano komai, babu abinda ya rage kuma, tabbas babu. Ka bani dama zan bata hakuri da kaina, zan kuma fahimtar da ita yanda zata fahimci komai dan nasan yanzun ma bayin kanta bane masu zuga ne.Kallonta kawai yake a narke da jin kaunarta na kara ratsashi. Wayonta yana rinjayar duk wani karfin ikonsa a zahirance. Ya fahimci tana son ya basu wajene. Sai ko ya mike a hankali yana kai waya kunnensa kamar wanda ke shirin kiran wani. Wani irin shegen murmushi Iffah ta sake saki idanunta akan Malikat Bushirat da ke jin kamar ta hadiyi zuciya ta mutu. Itace wanna yarinyar zata nunama danta da ke matsayin Shahan-shan tacika mace a garesa. Iffah dake danne dariya ta wani kashe mata ido daya da kada mata yatsun hannunta biyu akan fuska. "Hy my Mather in-law ya da suman zaune haka tun ba'a fara wasan ba. Kin damu kanki da saki-saki kinmanta danki sarki ne, bai isa sakin n Ahaka kawai bai sai da hujja mai karfi? Oh!! Kina son a sakeni saboda na zame miki kadangaren bakin tulu ko? Ayya!! Ayya!! Mather in-law kinyi sakaci ai, kinyi sakaci tunda har kika bari Fhareedah bint Zayyan ta kasance daya da ga cikin Zawjata-almilk. Kinyi sakaci tunda har danki ya zama a tsakkiyar tafin hannuna. Kinyi sakaci tunda har kika yarda hanunki ya taba jikina a karo na farko yau ma karo na biyu kika sake. My Hamäh idon Iffah bude yake tun a randa ta shigo wannan masarautar, sannan biye nake da takun kowa hatta ke kanki. Dan haka nice zan baki mamaki kafin safiyar goben da kika shardanta masa idan baki bi a hankali ba ba kece zaki bada mamakin ba. Bara na bude miki zancen a bayyane, naba danki gubar dafin macizai a cikin madara badan ya mutu ba, sai dan na kusanta da shi. Dan wannan hanyar ce kawai zata bani damar zama a sashensa din-din, saboda na tabbatar duk wadda ta kasance tana aikata ko yana aikata barnar da kisan matansa da ma duk wani mugu mai boayyen nufi a kansa bazai barni ba zai yi yunkurin ganin ya kashe ni tun a cikin kurkukun, shiko bazai bari ba zai bani kariya dan dole-dole yana son sanin dawa mukai aikin ai. Kinji na farko kenan"ta kare maganar da dage mata gira. Sai kuma ta juya idanunta masu rikita lissafin Malikat Bushirat da har yanzu basu gama sabewa ba "'Na biyu tun a randa aka kawoni gidan nan wika zama suspect dina na farko. Dan nagano matsanancin tashin hankali a cikin idanunki lokacin da naki shan madarar da kika saka a bani. Kinji na biyu in-law. Na uku randa nake kwance asibiti dalilin rigar da aka sanya mun akwai kallon da kikai mun da ya saka na ajiyeshi a kyakykyawar ma'adana. Na hudu randa kuka zaunar dani akan kunaso na koa sashen Eshaan da zama danna gano muku wai shike kashe matansa ko wanine. kai jama'a" ta fada tana kyalkyalewa da siririyar dariya. "Wihy kinada basira in-law. Kin iya makirci da in har mutum bai san ainhinki ba sai ki gama halakashi bai sani ba. A ranar na fahimci abubuwa da yawa a cikin kalamanki, kawai kina boye kanki ne cikin rudanin bayin ALLAH. Uhhm kin dan birgeni fa. Randa Eshaan yasha gubar dana bashi shirunki ba yana nufin baki da abin fada bane, ni nasan kinfi kowa zama a kololuwar bala'i dan naga haka a cikin idanunki. Randa kika bashi umarnin ya sakeni na gano abinda ke bakiyi tunanin zan gano ba a cikin kwayoyin idanunki da taba jikina da hanunki yayi. Hhhhhh Iffahr nan da kike gani batta a inda kika ganta batta, tafi karfin zama yar wasan kura, ni din hazabibiya ce fiye da yanda kike tunani Mamana. A yau kuwa shigar hanuna cikin naki ya sake tabbatar min da ke ce, ke ce Malikat Bushirat da ke hallaka matan danki da kika haifa da cikinki. Mi kike bukata ne? Minene a rankine? Minene burinki ne? Mi kike son zama ne?Bayan duka ALLAH ya baki?. Ki fada min, nikuma na miki alkawarin taimakonki bazan kuma tona asirinki ba ko dan daraja da mutunci dakimar danki, dan bazan bar ZUCIYAR MIJINA ta buga ba a dalilin son zuciyarki. K uwa ce garesa,kuma ina kallonki da wannan kimar ne har yanzu saboda mutuncinsa Ammie. Sai dai bazan iya yafe miki jinin yan uwana guda biyu ba. Kar kiyi sakaci da wannan damar, in ba haka ba ki sani da ga yau wannan lokacin na yaki ne, tabbas na yakine. Tabbas Malikat Bushirat a sume take, sumar da kunne na ji ido na gani amma gangar jiki bata motsawa. Suma irin na mamaki da tsantsar tashin hankali. Dan babu abinda ake iya gani sai wutar masifar da ke ci a tsakkiyar idanunta dake kallon Iffah. Iffah da tuni ta fahimci haka murmushi ta sakar mata da buga hanunta na dama dake dunkule a tsakkiyar na haggu taialamar yanka wuya a saitin wuyanta tana kashe ido da cije lips. Wani irin mikewar zabura tayi kamar wadda aka dawoma da dukkan karfinta dai-dai da dawowar Tajwar Eshaan akin. Fashewa Iffah tai da kuka da durkushewa gaban Malikat Bushirat da ta mike tsaye a zafafe. Ta riko duka kafafunta tana kukan da fadin, "Ammie nasan zaki fadukkan bayani na, kuma zakimun adalci a cikin dukkan abinda ya farun nan. Nima ba laifina bane tirsasani sukayi da mun barazanar karar da ahalina dama ku musamman ke da kike mahaifiya ga adalin shugabanmu. Ni kuma a shirmena idan na bashin za'ai saurin kaisa ga likita kafin ma dafin macizan yay tasiri. Ki yafe min Ammie nayi kuskure da wauta ki yafe min… Gaba daya Malikat Bushirat sai ta sake mutuwar tsaye. Eh lallai yau taga masifa, anya yarinyar nan mutum ce kuwa? Shikam mai gayya da aikin yay wata irin tsaiwar da ko bai fito fili yace komai ba Malikat Bushirat da kanta ta hango abinda ta hango a cikin idanunsa da ke tsaye kyam akan Iffah da ke a gurfane gabanta.Tabbas idan tai wani abu a yanzu akwai matsala,zakuma tayi kuskuren da yafi na yarda da shigowar yarinyar nan masarautar nan. Hadiye abinda yay mata tsaye a makoshi tai da kyar, ta rankwafa ta kamo kafadun Iffah ta mikar da ita tsaye. (Ya ALLAH hawaye fa share-share a fuskar Iffah kamar gasket). Bata da zabin daya wuce rungumeta itama tana matsar kwallan karya ta shiga fadin. "Ban san haka bane Ibnati miyasa kika ki fahimtar da ni da ban miki irin wannan mummunan zaton ba ai. Kiyi hakuri ki gafarceni"……….✍️ _Wannan yarinya ta zama abin toro gaskiya 😂. Ahe haka take 🥱 🥱Ni wannan ya ta Babiy kodai sunada sarauta ne a kauyen Jumna bamu da labari. Wannan hayen izza na dauran kai gaskiya 😂 15:43 DAUDAR GORA… Chapter: 51 Sake kankameta Iffah tai, cikin diddishe dan ta fita tsayi ta kai bakinta saitin kunenta tana wani kuka kuka. "Hhhhh da dina dake akwai daukar haske Mather in-law. Why ki sallamemu mu tafi naje mijina ya rungumeni dan ban gama dawowa hayyacina da ga faffarkanin da yay ba". A zahiri kam raba jikinta tai dana Malikat din tana share hawaye da jera godiya. Sai kuma ta kashe mata ido dan ta fahimci yanzu ma fa ta sake kamewa ne ta juya ta kalli Tajwar Eshaan da ke kallonsu da alamar nuna jin dadin canjawar komai akan fuskarsa. "Ka tayani godiya *_My Asad_* (Zakina), Ammie ta fahimceni, na sanar mata komai kamar yanda na fada maka". A hankali ya wani lumshe idanu da takowa gabansu. Gaban Malikat Bushirat ya tsaya tare da kamo hannayenta cikin nasa. Firgigit ta dawo hankalinta kamar wadda aka kodama mari a cikin barci. Cikin kamewar nan tasa dake boye dukkan sirrikan fuskarsa yake dubanta a nutse. "Ammie nagode sosai, Nagode da kika fahimci abinda naketa son ki fahimta tun tuni.Fhareedah yarinyar kirki ce mai cike da tarin alkairai daban-daban, kuma nasan zaki sake tabbatar da hakan anan gaba. Na miki alkawarin aiki tare da ita har sai duk wani markiyinmu ya bayyana batare da shi kansa ye sani ba. Ki cigaba da mun addu'a ke dai,gaskiyar danki na gab da fitowa zahiri ga kowa.Dan yanzu haka dukkan wasu bincike akan cases din nan suna'a hannuna, hatta wanda yay tushen bada madaran, da wanda ya sakata a ruwa duk sunzo hanun hukuma. Kallonsa tai da wani irin sauri, sai kuma ta hadiye tana mai kankame hanunnsa a cikin nata. Idanunta ta lumshe hawaye sukai wani irin zubowa. "Ashe zanga wannan ranar, wanna ranar zatazo gareni haka Saiful-malik?". Ta fada cikin subutar baki. Ko kadan Tajwar Eshaan bai fahimci kalaman nata ba, ya fassarasu ne akan nuna farin cikinta na zataga wannan raar da za'ai walkiya halin wanda batai zato ba ya fito. Sai kawai ya saki murmushi da kai hannu yana share mata hawaye. "Zaki gani Ammie. Ai dama komai yay farko zakiga karshensa na zuwa. Ki cigaba da mun addu'a ke dai indai nasarorin ne yanzu kika fara gani. Sai kin zama mafi kololiwar uwa da zatai alfahari da haihuwar da daya tilo tamkar da dubu insha ALLAHU" "Na yarda da hakan Bin Haysam Abdul-majeed, tabbas na yarda, ALLAH ya makaalbarka kuje dare nayi ku huta ma karasa dasafe". 15:44 Godiya a sake mata da dan lallashi, hakama harda durkusawarta. Kafin ta wani kananna de ma Malikat Bushirat ido a kaikaice ta sakar mata gwalo. Tajwar Eshaan na juyiwa ta fuske kalar tausayi. Hannunta ya kama a hankali yana mai kallon fuskarta ya sakar mata murmushin nan nasa mai narke zuciyarta. Murtani ta maida masa da dan saka hannu ta kare fuskarta ita a dole taji kunya ne. Duk Malikat Bushirat na kallonsu. Suna ficewa ta zube kasa yarafff wani irin mahaukacin jiri na dibar idanunta. Sai kawai ta fashe da kuka tana kiran sunan Uwa. Tantabaru biyu iyayen soyayya da alkawarin kam suna fita ya duke kasa ya bata bayansa alamar ta hau. Idanu ta waro masa waje alamar mamaki. Ya dan juyo yana kada mata kai da lumshe idanu. Babu yanda ta iya ta tattare rigarta kadan ta hau tare da makalkale masa wuya dan sam bata iya gardama ba. Takun nan nasa yake a hankali cikin izza da kasaita har zuwa sashensa tana a bayansa kwance luff mamakinsa na neman kasheta, duk wanda yasanshi a Shahan-shan din sa bazai taba mafarkin abinda yake mata yanzu zai iya ba.Koda suka shiga elevator ma bai sauketa ba sai boye fuskarta da tai a wuyansa. Aiko gaba daya numfashin da take busa masa ya nema birkita masa lissafi.Maimakon ajiyeta a daki da ya shiga sai kawai ya wuce da ita bathroom ya direta ta bude idanunta. Da sauri ta kallesa a dan rude gain inda ya kawosu. Sai kawai yay wani luuu da idanunsa cike da basarwa ya danne makunnan shower ya sakar musu ruwa a kansu mai dumi. Babu shiri ta zabura ya rikota a hankali, jikinsa ya matsota ya rungume ruwan na cigaba da sauka a kansu. Kusan mintuna uku suna a hakan kafin ya bude idanunsa ya sauke a kanta yana mai kai hannunsa saman veil din ta ya shiga warwarewa a hankali. Tanaji tana gani ya raba jikinta da kayan da suka gama jikewa sharkaf shi ma ya cire nashi. Jikinsa ta fada kawai nata na rawa ga wata matsananciyar kunyarsa na ratsata. Sosai hakan da tai yay masa dadi, dan ya samu damar sake gain tawadan ALLAH din nan ta bayanta yanda ya kamata, yanda har sai da ya haddace ta. Ita kam har aka kammala wankan bata yarda ta bude idanunta da ta rufeba.. "Nagode" Ya fada a hankali lokacin da yake goge mata laimar ruwan fuskarta da towel zuwa wuya da bayan keyarta. Dan dago idanunta tai ta dubesa, itama a hankalin ta ce, "Akan mi?". “Ammie" Ya bata amsa a takaice. Baki ta dan tura masa tana narke fuska, a dan shagwabe ta ce, "Saboda Ammien ka ce kai daya?". Murmushi ya dan yi da lakace mata hanci. "K ta musamman ce". Baya ta juya masa tana murmushi, hannunta ya kamo ya sake juyo da ita. Ya dago fuskarta da kyau ta hanyar dago da habarta. "Baki yarda ke ta musamman ba ce?" Tana dan danne murmushin ta ta ce, "Ka dan dai", Yanda ta fada da yin kamar zata dan kashe ido daya sai kuma ta jujyasu wani luuuu hakan nan zuwa gefe ya sashi jin jikinsa duk ya saki,amma sai ya kanne yayi dan murmushi kawai da sake rankwafawa suka zama dai-dai tsaho. "Zan tabbatar miki k ta musamman ce Mrs Eshaan.Dan bazaki sake rayuwa babu Eshaan a gefenki ba har abada insha ALLAHU" Cikin dan waro idanunta kadan ta ce, "Har a kurkuku idan na koma". "'Koda a tandun mai ne Babie. Hukunci na gama yankuwa zamu tafi can abunmu muyi zamanmu har sai kin haihu". Takwaf-takwaf tayi da fuska kamar zata sakar masa kuka. "Wai da gaske kake sai ka maidani kurkukun?". *kyar ya iya danne dariyarsa, a zahiri ya dan Kara tsuke fuska da daga mata gira. "Way,miki ko Mrs Eshaan zata tsira da ga hukuncin Shahan-shan ne. Ai sai munje kurkuku dole, irin wanna laifi haka da muka rakitowa kammu". Baki ta bude a hankali zata sake magana ya manne lips dinsu waje guda, dole ta hadiye. Duk da a tsorace take da shi batai yunkurin hanashi ba, sai dai kuma bata bashi kowane irin gudunmawa ba har yay kidansa yay rawarsa ya barta. Da ga haka bakin ya mutu suka hau shirin barci, dama da biyu yay hakan dan ya gaji da maganar. Ya fara kula yarinyar nan so take tamaidashi parrot na karfi da yaji su Jaddah su sami abin masa gori. Wasu shegun kayan barci da bata san ina ya samo su ba ya dakko zai sakamata. Tako zaro ido zatai magana dan bakin faya fara dawowa (lols 😂)). Yatsansa ya daura saman bakinta ya ce, "Shill!!!". Dole ta hadiye abin cewar tanaji tana gani ya saka mata su. Ina kasa Iffah ta shige ta buya kota huta da kunyar da bawan ALLAHn nan ke dawainiyar jefata ciki itakam. Shiko gogan naku ko'a jikinsa. Sai ma nasa shirin da yay cikin pyjamas dinsa shima marasa nauyi ya jata suka fito. Zaunar da ita yaya daya daga kujerun dakin shima ya zauna kusa da ita. Idanunsa da basu ko kyaftawa a kanta ya motsa a kasalance. "Zaki sha madara?". Bawani tana jin yunwa bane, dan haka ta daga masa kai batare da ta yarda ta kallesa ba ita. Dan harga AllaH tsoron ma kallon jikin nan nasa take a tsaye, ga shi ya sa kaya marasa nauyi da gaba daya suka bayyana ainahinsa. Shi da kansa ya zuba madarar ya bata, ta amsa tana fadin, "Nagode". Shi dai nasa kawai kallonta. Yanda take shan tata a takure harya kammala ita bata gama ba, dan haka suka dan jima wajen a zaune har ta fara hammar barci. Koda suka kammala brush suka sake yowa ya ce mata ta kwanta dan ya fahimci barci takeji sosai. A darare ta kwanta har fuskarta na bayyana tsoronsa. Yi yay kamar bai lura da ita ba, yama koma cikin sofar da ya tashi ya zauna.Itako luff tai zuciyarta cike da toro da kuma mamakin abubuwan da tai yau a sashen Malikat Bushirat. Ta jima da sanin akwai wasu lokuta da take ganin abu baro-baro a zahiri bayan ta gansa a mafarkinta, amma fa yau ita kam kawai jitai tana zano zantuka ga Malikat Bushirat din wanda itafa kamar ana nuna mata su ne cikin idanunta a lokacin, sannan tana jin wani karfin iko da izzar fadar tasu babu o dar tattare da ita. Ta dafe kanta da ke dan mata ciwo kasa-kasa, ga wani barci da ke rinjayar idanunta mai nauyi. Dole ta tattara tunanin da tsoron ta hakura tai addu'a sai ko barci. Shima da ke zaman kallonta duk dahankalinsa nakan waya ne a zahiri sai ya shirya tattarawa ya bar dakin, dan ya tabbata idan fingilar rigar barcinta ya dagata sama kadan cikin sa'a ya iya ganin abinda yake son ga Hoton wajen ya dauka da waya ya maida mara rigar a yanda take ya mike yana sauke ajiyar zuciya. Dan ya tabbata ido biyu bazata yarda yay hakan ba cikin sauki, maybe ma tafassarashi da wani abu daban... Maimakon shiga wani dakin barcin ya kwanta karamin falonsa na hutawa dake rukunin dakun barcin ya shiga, agogo ya kalla, ganin sha biyu ta dan gota kadan ya dauke kai. Wayar dake gefensa ta landline ya dan daddana, batare daya dauka yakai kunne ba harta shiga ta yanke.Cikin abinda baifi mintuna biyar ba sai ga amintaccensa da butar shayi. A saman lips ya amsa sallamarsa batare daya dago ko motsa daga abinda yake ba. Koda ya gaisheshi ma bai ko amsa ba, ya dai daga masa hannu kawai, shiko bai damuba ya ajiye komai yanda ya dace ya zuba masa a karamin cup yasa yar zuma kadan dan yasan baima cika shan wannan shayin da komai a ciki ba. Bayan ya kammala cikin girmamawa kansa a risine ya ce, "Ko akwai abinda shugabana ke bukata?". Yaja kusan minti daya da rabi sannan ya daga masa hannu. Duk wani yaren jiki da Tajwar Eshaan zai yi magana da shi hadimin nan ya haddacesa, dan haka cikin risinar da kai ya furta, "A huta lafiya, ALLAH ya kareka da kariyarsa". Daga haka ya fice... DAUDAR GORA Book two ( 52) Duk da barcin dake cikin idanunsa tattaresa yay ya ajiye gefe guda ya tattara dukan hankalinsa kan littattafan da Malikat Haseenat tabashi. Inda zuciyarsa ke zallon zuwa kawai ya nufa bayan ya dan karanta tarihin mafarin komai. Babu bambanci da wanda Mammah ta bashi, dan haka ya ajiye gefe da burin sai ya nutsu zaiyi komai daki-daki. Bai san adadin shekarunta ba, amma sai ya kiyasta da adadin shekarun da yake kallonta da su. Yaci karo da kusan hudu da yay dai-dai da hasashensa, a ciki uku na mata daya na namiji, gefe ya maida na namijin, ya dauka wayarsa yana kallon natan da na sauran matan uku kozai dace da wanda zasuyi dai-dai. Wani irin masifar harbawa zuciyarsa tayi gain tambari na karshe bashi da banbanci da natan. Bayanin dake kasan tambarin na tabbatar da dashi aka haifeta, a duk ma wanda aka haifa a tsakanin lokacin ita kadaice wadda aka haifa da shi sauran duk yimusu shi akayi. An haifi mai tamarin a daren ranar juma'a 22 a shekarar 2003 uku ga wata.Sai dai ita kuma ta rasu ne bayan haihuwarta da kwana uku. Wani irin kai hannu yay saman kansa ya yamutsa sumarsa yana ambaton sunan ALLAH. Ya akai haka? Ta yaya ma? Idan har ya tabbata ita din ce ya akai take raye bayan ance kuma ta mutu? Idan kuma wadan can dinne Iyayenta tayaya suka bar masarautar ma?bata mutum ba suka boyeta sukace ta muturn? Kai ina akwai dai abinda ya kamata ya sani, farkoma shekarunta ita. Sannan sanin asalin iyayenta.Lokaci yayi da zaisa a maidosu kasar ruman. ** Kanta sara mata yake da cio mai azaba. Ga wani irin ja da idanunta sukai. Kofar da suka fita kawai ta tsurama ido tamkar suna a wajen har kusan awanni uku bayan fitarsu. Sosai take jin kuna mai radadi a zuciyarta. Har yanzu ta kasa yarda a ido biyu take, ta kasa yarda a zahiri komai ke faruwa, ta kasa yarda ita ta-kurya wata ta tsaya a gabanta tai mata wannan in kashir.Ta kasa yarda ita ta kurya yau wani ke tabbatar mata yasan itace silar mutuwar matan danta. Ta kasa yarda, ta kasa yarda da komai. "Ta-kurya!!". Muryar UWA ta shiga cikin kunnenta a bazata.Firgigit ta kai dubanta ga inda taji sautin kuryar.Ita dince kuwa, zaune cikin kujerar nan tata.Yanda fuskarta ke tsuke hancinta na fidda hucin bacin rai sai ta kara muni ga mai kallo. Idanunta jajurta kara budewa akan Malikat Bushirat itama kallonta kawai take babu alamar jikinta na aiki bayan fitar numfashi. "Kin bani kunya ta-kurya. Kin bani kunya da har kika kasance a haka kan wata karamar barazana da ga yar cikinki. Ashe bazaki iya yakin ba kika amsa takardar gayyata? Dama duk baki shirya zuwan irin wadan nan ranakun ba… "Uwa ya kike so nayi? Ya kike so na kasance?.Ni fa yarinyar nan ta kalla cikin idona ta fadamin abinda bayan ni da ke babu wanda ya sani a kaf duniya. Ni yarinyar nan ta shiryama makirci a gaban dana dana zama sanadin zuwansa duniya, wanda dukkan gwagwarmayata akansa ne da tabbatar da wanzuwarsa a matsayin da yake yanzu, wanda da shi take ado, da shi take takama da jin kanta ita har takai mace abar kallo. Uwa shiyyasa nace miki ki kasheta tun a farkon farawarta amma kik.... "Na fada miki na kara fada miki kashe wannan yarinyar kai tsaye ba abune mai sauki ba. Domin akwai wani boyayyen al'amari da yake zagaye a kanta. Tsaye nake kuma akan ganoshi dare da rana dan ba dake kawai ta shirya yakin ba har dani nan kaina. Sai dai abinda bata sani ba ni nafi karfin iyawarta, zan kuma tabbatar mata da hakan nan kusa. A cikin sharuddanmu kin tafka kurakurai da yawa ta-kurya, ciki harda kasa bamu alkyabba da ke a sashen mai babban daki. Tun a ranar farko kin kasa shayar da yarinyar nan madara, bayan gagara yimata wankan turare da saka mata alkyabbarmu. Kinyi yunkurin kasheta da hanunki bayan na sanar miki hakan babban kuskure ne amma kika ki jina. Kinyi kuskuren kasa saka ido har aka kaita sashen Ajlaan bada saninki ba. Kinyi kuskuren kasa hadiye abubuwa da dama dangane da ita.Wadan nan abubuwan dama wanda ban lissafaba sun taimaka mata wajen bude kofar samunki ta inda bakiyi zato ba. Babban na karshe daya bude komai kasancewarta da jininki matsayin abu guda, bayan kuma tun a farko mun sanar miki mune zamu bama Ajlaan matar aure mai kwaranye kishinsa... "Na amsa dukkan laifina gareki Uwa, ina kuma mai neman afuwa da agajinki karki barni na fadi kasa a gabar da makiya ke burin ganin bayana. Ki fadi mi kuke bukata na diyyar laifukana komai wahalarsa zan zama mai cikashi da gaggawa ni bazan kasance mai butulci irin wanda akai miki a baya ba. Ina son yarinyar nan tayi nadamar sanin kanta ma balle ni a karan kaina". "K mai kokarin cika sharudda ce ta-kurya shiyyasa bana iya dogon fushi da ke. Kije an miki, sai dai ki shirya dan shirinmu na yanzu zai zama a saman a bayane. Zaki biya diyyar kurakuranki da jinin bakaken shanu goma, na rakuma goma, na bakaken karnuka goma suma. Jariri sabuwar haihuwar kwana uku kamar yanda akai a wancan karon mai tambarin masarautar nan. Bayan sati guda zaki cika mana da jinin barin ciki na mata biyu masu sabon shigar ciki dan watanni hudu. Tare da namijin hadimi sabon aure shima da yay kwanciya da mace sau daya. Da ga yau madarar da Ajlaan zai koma sha zata dinga fita da ga hanunki ne, akwai shayi da yake sha a kullum kisa a nemo miki mai masa nomansa ya noma da wannan irin amaimakon wanda yake noma masa, dakin zai dawo tafin hanunki komai sai da umarninki zai aikata shi. Tana makirci da danki a tsakkiyarku,kenan sai kibi ta karfin ikon shi da ke a hanunki da ga yau. Zamu sama mata amintacciyar hadima, dan haka ta koma sashenta da zama.Muna akan bakanmu, waccan yarinyar zata shigo domin da ga gareta kawai muke bukatar magajin daular ruman kiyi gaggawar gain an kulla aurensu. Da ga shi har ita ki tabbatar sun sha wannan ruwan, shine zai hanasu sake kasancewa da juna har abada". Cike da farin ciki Malikat Bushirat ta amsa tana jera godiya ga uwa cikin gurfana. Ji take a daya duk wani bacin ranta da tashin hankali sun kwaranye kamar ma ba'ayi ba "Uwa sai dai akwai hadimin nan daya sakata a ruwa, Saiful-malik ya tabbatar min yana haninsu". "Wannan bashi da wani muhimmancin da zai dameki, dan baisa ke wacece ba ai". "Amma Uwa ita ai ta sani, baki ganin zata iya yin yanda kowa zai fahimci ni din ce?". "Bata isa sanarma kowa ba koda shi Ajlaan ne, dan akwai soyayyarki a zuciyarsa fiye da yanda duk wani mai hasashe ke zato". Nidai bilynku na ce, "humm" 🥱) * 大 Ta farka sau daya vin fitsari taga baya dakin,17:38 Ta tarka sau daya yin titsari taga baya dakin, sai hakan ya kara mata nutsuwa. Sai dai kuma Can tikin dare ko tace gabanin asuba taji a mata wata irin runguma data sakata farkawa a firgice. Gabanta faduwa yay lokacin data tabbatar da shine. Muryarta har kakkarwa take na son magana. Sai dai ma kafin ta furta ya ce mata "Shilli!!" dole ta hadiye tai luf. Yamutsata ya dingayi da jagwalgwalata yanda yake so, ta riga ta gama kaiwa makura a rudewa. Sai dai bai mata komai ba har aka kwala kiran salla ya mike a gadon ya nufi bathroom. Kusan mintuna goma tana nan kwance lamo da share hawayen da tasha na tsoro ya fito da alamar wanka ma yayi.Luff tai bata motsa ba har ya gama tsane gashin kansa ya wuce wajen canja kaya. Wuff tayi ta tashi zuwa bayi, lokacin da ya fito cikin shirin massalaci ya nufi gadon da shirin tadata ya samu wayam. Shi yama zata barin akin tai, sai kawai ya fice abinsa gudun kar ya makara kuma. Koda ya dawo da ga salla Gym ya wuce abinsa cike da kokarin danne abinda ke damun gangar jikinsa da ruhinsa. Wani irin mugun motsa jiki ya ringayi na tashin hankali duk dan ya samarwa kansa nutsuwar manta abinda ke bijiro masa. Sai dai maimakon samun nutsuwar da yake bukata hankalinsa ne make cigaba da tashi. Ya dauki tsawon awa biyu a Gym din kafin ya fito ,ya koyi zufa sharkaf kamar wanda iyo a cikin ruwa.Tana tsaye gaban gadon tana canja bedsheet ya shigo da sallamar nan tasa ciki-ciki. Dan juyowa tai kadan ta dubesa sai kumata dauke kanta. A can kasan makoshi ta ce, "Good morning". "Ya kike?". Ya fada a takaice yana cigaba da mata kallon mamaki. Kamar zai share dai ya kasa hakuri."Waya saki wannan aikin?". A dan shagwabe tace, "Ni na sa kaina, shike nan mutum bazai motsa jikinsa ba sai dai komai ai masa ni banaso". Takowa yay gabanta gab sosai, tare da riko hanunta da ke rike da filo.Dagowa tai ta kallesa.Zata maida ya girgiza mata kansa. Dole ta hakura, sai dai tai kasa-kasa da idanunta.Shikam dai idanunsa kyam kan kyakykyawar fuskarta da yau dai ta gama komawa normal kamar komai bai faru ba, ya dan matsa hannuna hankali yana dan huro iskar bakinsa kan fuskar tata. "Akwai muhimman ayyuka da yawa da zaki motsa jiki ai ba sai wannan ba Niger". Fuskarta a dan narke ta dago idanunta da kyau tana dubansa, "Wannan ma fa Mammy tace ni ya kamata na dingayi yanzu ba amintaccenka ba. Nima kuma kaga dai a gida Ummu ko mu bata yarda mu gyara cakin Babiy,ko Bata da lafiya sai tace bari ta danyi ko sama-sama". Gaba daya ta sake narkar da shi a halin da yake ciki, bai ma san sanda ya furta, "Kowane salonki kasheni yake autar mata". Yanda ya fada a narke da kai hannunsa ya shafo jikinta sai taji kunya. Da sauri ta juya masa baya tana rufe fuskarta da tafukan hanunta. Shima murmushin yayi ya ajiye filon yana nufar bathroom. Sai da taji shigewarsa sannan ta bude idanunta ta cigaba da aikinta. Haka kawai take jin kanta cikin wani irin nishadi yau. "Mammah wai yau ma zakije zaman kotun nan kema? Naga kamar kina jin kafar nan sosai fa?". Dan murmushin karfin hali Malikat Haseenat ta saki idonta akan Daneen Ammarah mai maganar. "Karki damu ai bawani ciwo take mai yawa ba. Ke dai yi sauri ki bani kunun nan nasha, kin sanshi dan ka'ida ne akan bin lokaci". Yar dariya Daneen Ammarah tayi kawai, Da ganta itama zaka fahimci tana cikin farin ciki. Daga ita har Malikat Haseenat din tun jiya fuskokinsu sun kasa daina murmushi, da dare kam zama sukai suka ding hirar Iffah. Su kansu sun kasa gane ta yanda akai yarinyar ta shiga ransu matuka har haka, kuma take ma kara shiga a kullum musamman ma ita Daneen Ammarah din da kwanakin nan taketa mafarkai da ta kasa gane kansu……………✍️ DAUDAR GORA Book two( 53) Wata shegiyar dariya ya saki idanunsa kan takardar da aka aiko masa ta sake zaman shari'ar yau. Ya kai hannu ya yarce ruwan wankan dake kan goshinsa zuwa fuska. Tun safiyar jiya basa gidan shi da Miran Jasim. Sai yau ne shi yake dawowa Miran Jasim kuma da daddare. Wayar landline dake gefe gadonsa ya dauka,yay yan danne-danne yana da ga tsayen da yake. Ana dauka ya kwashe da dariya, sai kuma ya kai zaune a bakin gado. "Yaya dai kawun mai sharia kaima an kawo maka takardar ne?". Wani irin shegen tsaki Miran Jasim yaja da ga can. Ya ce, "Bar wawa dan wahala mana. Shifa gani yake kamar ya wani kai anan. Muje zuwa idan ya isa sake zaman wata shari'ar da ga wannan. Zamuyi maganinsa ne shida shegiyar yarinyar nan mai bakin akkunaye". Sake kwashewa da dariya Miran Arshaan yayi, tare da fadin, "Ai boka dan gurguzu yayi,tunda muka fita muka dawo masarautar nan babu wani shege da yay magana shima bai isa yinta ba yau". Dariya suka kwashe da ita a tare kamar wasu mahaukata... _Tofa, mi Fir 'auna da hamana suka shiryo ne haka🥱😂🚴🚴🚴🚴 Yau kam a tare suka fito zuwa dining room. Amintaccensa ya zube kansa a kasa yana gaishesu cike da girmama. Iffah ce kawai ta amsa masa cikin kulawa. Gogan nata kam lips kawai ya motsa ya wuce abinsa. Da kansa ya ja mata kujera, itama sai ta ja masa tana kallonsa da murmushi. Shi dai bai murmushin ba, amma ya juya idanu cike da salon birgewa. Koda amintaccensa ya taso domin hada masa abinci kamar yanda ya saba dakatar da shi tai. Sai ma ta sallamesa akan yaje idan sun kammala sai ya dawo. Sai da ta gama bubbude duk kwanikan wajen sannan ta kallesa alamar mi yake so? Kaifafan idanun nan nasa ya zuba mata, sai kuma ya daga yatsarsa manuniya a hankali ya nuna ta.Baki ta tura gaba tana wani kyaf-kyaf da idanu."Ni abinci nace fa". Yanda tai din sai ya bashi dariya. Amma sai ya gimtse abarsa ya dauke kai Itama sai ta tabe baki ta dauke nata kan dan ta fahimci yau kuma yan mislinacin ne da mulki a kansa. Zabar abinda taji tana so a ranta tai kawai ta zuba musu ta ajiye komai gabansa da fadin bismillah. Abincin kawai ya zubama ido yana jinsa wani daban yau din. A da sai daiamintaccensa ya hada masa, yau kuma gashimatarsa ce, abinda ya jima yana mafarki. Rayuwa kenan mai farko da karshe. A nutse suka fara cin abincin, Iffah na satar kallonsa da jinjina mulki da kasaita. Yanda yake cin abincin ma kansa abin birgewa ne. Suna gab da kammalawa kanta yay wani irin sara mata. Da sauri ta kai hannu ta dafe tana ambaton sunan ALLAH. Kallonta yay shima da mamaki, sai kuma ya riko hanunta da ta dafe kan da shi. Dago idanunta da sukai wani irin jajaja cikin kankanin lokaci tai ta kallesa. Shi har sai da ma yaji tsigar jikinsa ya tashi, amma sai ya dake kasancewar shima akwai nasa abebadan a kansa. Da ido ya mata alamar minene? Dan da gaske yau miskilancin ne a kusa. Ji yake motsa lips din ma yay magana babban aiki ne. A hankali ta furta, "Kaina ke dan mun ciwo Tun yaushe?". Ya fada a fusge. "Da safen nan ne fa. Amma ba wani ya matsa bane karka damu. Dan ALLAH ka barni na fara tafiya kotun nan sai kai kuma ka taho da ga baya". Idanu kawai ya tsira mata. Ita kuma ta langabe kai gefe alamar roko. Dauke idonsa yay kawai da ga kanta batare da ya ce komai ba. Ya lima yana zargin akwai junnu a jikin yarinyar nan, yanzun ma kuma abinda yake zargin kenan. (Ya arrahaman, komai na yarinyar nan sake sakashi a rudani yake). Sai kuma maganar data fada masan yanzu ta shiga masa kaikawo a rai. Ya barta ta fara yin gaba kafin shi na nufin akwai wani abu kenan. Shikam yaga takansa da wadan nan ahali nashi. Wani abu kenan wani ya sake masa ko kuma dai aljanun nata ne ke neman raina masa hankali. Cikin rashin bama abin muhimmanci ya cigaba da cin abincinsa, sai dai kuma abinda ta fada kuma ya faru a wacan ranar na masa kaikawo. Iffah dake binsa da kallo kamar zatai magana sai kuma ta hadiye kayarta tana sakin nannauyar ajiyar zuciya da jan jikinta baya. Komai baice mata ba, sai da yaga ta mike. A can kasan makoshi ya furta "Ina zuwa?". Agogo ta nuna masa. Kallon agogon yay ya dauke ido. Batare da ya sake kallonta ba ya ce ,Kina bukatar masu rakkiya ne?". "A'a". Ta bashi amsa a takaice. '"Amma kin san bazai yuwu kije ke kadai ba. Kije akwai masu jiranki a can kasa". "Nagode". Da kallo kawai ya bita ganin yanda ta sauya lokaci guda. Ga fuska ta wani daure tamau babu alamar wasa. Shi sai ma ya fara jin ko dai itace aljanar da kanta. *Yau kam da alama shari'ar zatai zafi. Dan kotun tacika fie da zaton mai hasashe. Abinda Kuma zai birgeka duk ahalin masarautar ne.Cikin wani irin takun kasaita da izza da ya jawo hankalin duk wanda ke cikin kotun Iffah ta shigo da shi. Ga hadimai na take mata baya. Tayi matukar kyau cikin shigar jikinta, ga wani irin kyawu da fuskarta ta kara sai shining takeyi fiye da hasken tauraruwa zarah. A zahiri ita tafiyarta takeyi normal, amma ga masu kallonta babu abinda suke gani tattare da ita sai tsantsar izza mai ban mamaki. Wani abin birgewa da tai ya kayatar da was a wajen shine kai tsaye inda Malikat Haseenat take ta nufa. Takai kasa cike 17:42 yanzu bayan Tajwar Eshaan da Malikat haseenat sama da ita a duniya. Shigowar mai gayya mai aiki tasa tunaninsa katsewa…. a take kotun tai tsitt kowa ya mike domin girmamawa. Taku yake cikin tsantsar kasaita da izza data zame masa jinin jiki. Ga wani irin kamshinsa mai kada zuciyar mai shaka na tashi. Yammatan wajen da suka dade da folawa a sonsa tuni zukatansu suka shigar narkewa, duk da babu abinda ake gani bayyane a fuskarsa. Dan ya sakayata hatta da idanunsa saye suke cikin eyeglasses dake nuna blue daga waje. Addu'ar neman tsarin ALLAH da ga duk wani abin cutarwa ya karanto lokacin da yake kaiwa zaune a hadaddiyar kujerar da ke a mallakin zamansa. Ya dan saci kallon sashin da yake tunanin ganinta. Tana a wajen kuwa, sai dai abin mamaki ita sam bama shi din take kallo ba.Ajiyar zuciya ya dan sauke a hankali wadda ko amintaccensa da ke gefensa da masu tsaro guda hudu haggu da damansa basu isa ji ba. Bayan an tabbatar da kowa ya natsa Sayeed Hanifud-Din ya mike ya dubi jama'a. "Alhamdullahi muna godiya ga ALLAH da ya sake dawo damu zama na uku akan wannan shari'a. A zaman daya gabata wadda ake kara ta amsa laifinta, sai dai ta Bama wannan kotu mai adalci damar bincike mai zurfi akan tushen shugaba na wanna daula. Inda wannan kotu mai adalci ta amshi korafinta har ta bada dama ga masu bincike. Matsala ta ratsa ta yunkurin son halaka Zawjata-almilk da akai, inda dalilin haka aka samu tazarar daga wanna zama har sai da ta samu lafiya. To yanzu dai alhmallh, wanna zama a wanna gabar duka zai ta'allaka ne ga jin bayani da ga bakin shugaban jami'ai da aka danka wanna bincike garesa. Shugaban jami'ai bismillah". Sai da ya mika gaisuwa ga Shahan-shan cike da girmamawa kafin ya juya ga jama'a. "Assalamu alaikum kamar yanda aka bamu damar bincike a gaban wannan kotu mai adalci mun gudanar. Mun bibiyi tushen samuwar madara da kaita sashen Zawjata-almilk. Inda bincikenmu kuma ya kaimu har ga wanda ya shigo da wannan madara mai dauke da dafin macizai a ciki. Karna cikaku da surutu waka bakin mai ita tafi dadi. Ina rokon alfarmar wannan kotu da ta bani damar gabatar da Dafiq in Ghalib a gabanta". "An baka". Cewar Sayeed Hanifud-Din. Kallon juna Miran Arshaan da Miran Jasim sukai suka saki murmushi. Sai kuma sukai saurin duban wanda jami'ai ke kokarin shigowa dashi kirazansu na wani irin mummunan harbawa.Kokarin mikewa Miran Arshaan yay da sauri Miran Jasim ya danne masa hannu jikinsa na rawa. Iffah da ke kallonsu ta saki murmushi,cikin Sa'a kuwa suka hada do da Miran Jasim.Ido daya ta kashe masa da dauke kanta tana dan wani cizar lips cike da salo. Dattijo da jami 'ai suka shigo da shi bazai wuce shekaru hamsin da takwas a duniya ba. Cikin nutsuwa ya gurfana gaban Shahan-shan yay gaisuwa, bai o motsa ba da ga zaman kasaitarsa. Dattijo Dafiq in Ghalib ya gyara tsaiwarsa yana fuskantar kotu. Dubansa Sayeed Hanifud-Din yayi ya ce, "Dattijo waye kai?".Cikin dan rawar harshe ya ce, "Dafiq ibn Ghalib. Ni masanine akan macizai. Ina zaune a kauyen Bansh". "Miye alakarka da daular ruman?". "Alakata da Daula ruman alakace irin ta kowanne dan kasa. Wato fadan shugaban kasata adali". "Amma duk da haka ka iya bada dafin macizan da za'a cutar da shi?" "Ko kusa ba haka bane, ko wani naga zai cutar da hadimin wannan daula bama shugabana ba sai inda karfina ya kare ai. Ni dai a ranar daren wata laraba wani bawan ALLAH ya sameni akan shi din jami'in ne na hukumar bincike akan sanin nau'in dabbobi masu dafi.Yazo kuma wajena ne da bukatar samun kalolin dafin macizai zaiyi bincike a kansu. Da farko naso naki, dan nasan dan adam na wannan duniyar ba abin yarda bane. Amma sai ya nuna min katin shaidar aikinsa. Hakan yasa na yarda da shi na dauka na bashi"……….✍️ DAUDAR GORA Book2 (54) ......."Ko zaka iya gane mutum idan ka sakeganinsa". "Sosai ma kuwa. Dan akwai ma cctv footage na abinda duk ya faru a tsakaninmu batare da shi ya san inada camara a wajen ba." ya kare maganar yana duban shugaban jami'ai. Ya fahimci mi yake nufi, dan haka ya mike ya mikawa Sayeed Hanifud-Din flash da ke a hannunsa, anan take kuwa aka saka flash jikin lap-top aka kai gaban Tajwar Eshaan, sai ko ga duk abinda ya fada din dalla-dalla. An shigo da wanda ya amso dafin macizan, wanda ya kasance amintaccen hadimi ne ga Miran Jasim, kowa ya sani kuma a masarautar nan, dan tun yana a matashin saurayi ma yake tare da hadimin, shine ke masa duk wasu ayyuka na sirrinsa dama na mugunta. Ai Miran Jasim baima san yay wata iriyar zaburar tashin hankali ba jikinsa na kakkarwa. Yayinda gaba daya kotun ta dauka yan kananan magana har sai da aka tsawatar. Sayeed Hanifud-Din da shima dai gaba daya jikinsa yay sanyi da al'amarin ganin daga inda ya fito, dan koba'a fada ba komai a bayyane yake. Fuskantar hadimin da gaba daya ya fita hayyacinsa a hannun jami'ai yay. " "Bama bukatar wani kwana ja da ga gareka ko ja' in ja, fadar gaskiyarka na nufin zaka iya samun sassauci, zabar yin taurin kai kuwa ya rage naka. WANENE YA SAKA?". A hankali hadimin ya dago ya dan dubi inda su Miran Jasim suke, idanu suka hada da Miran Arshaan da yake masa kallon kasa-kasa yana wani dan motsa yatsunsa. Ajiyar zuciya ya ja a hankali, kafin ya maida dubansa ga Sayeed Hanifud-Din. Kai tsaye babu wata kwana-kwana ya ce, "Shugabana Miran Jasim ne ya sakani A take kotun ta dauki wani irin hun karajin Miran Jasim da ya zaburo kan hadimin nasa, sai da jami'ai suka rirrikesa. Yayinda jama'a suka hau salati suma har sai da aka tsawatar. Hadimin ya cigaba da fadin, "Sai dai ni ban san mizaiyi da ita ba, amma a gabana ya zubashi a cikin madara ya bani madarar yace na kai sashen Zawjata-almilk nace daga sashen uwar masu gida. Bani da ikon cemasa a'a, amma navi niyyar kin kaiwa sai dai nasan zai iya sawa a bibiyeni idan nai hakan zai halakani kuma, dan haka na cika umarninsa amma ni duk tunanina ma Zawjata-almilk din zai ba. A ranar nata kokarin ganin samun ganawa da ko amintaccen adalin shugabanmu ne amma hakan bai faruba,da ga karshe ma sai naji wai ashe shine za'a bama madarar ta hanyar Zawjata-almilk ba kamar yanda nai tunanin itace zai bamawa din ba. Kuma zan fadi gaskiya, ba laifin Zawjata-almilk bane ba asiri yay mata kan duk yanda yaso haka zaiyi da ita, daga baya itama zai kasheta. Duk yanda akaso samun nutsuwar kotun kam hakan ta gagara. Salati kawai kake ji da la'antar Miran Jasim da akeyi. Iffah ta saki wani irin shegen murmushi tana mai kallon Miran Jasim da yay sumar tsaye. Sai kuma ta maida kan Miran Arshaan da gaba daya yay sharkaf da zufa. Wata dariya ta kyalkyale da shi a zuciyarta tana fain (tun banzo kanka ba) a zahiri kam baka isa fassara yanayinta ba. A bangaren Miran Arshaan kam ya dauka makircinsa ne yay tasiri kan Miran Jasim. Dan kuwa hasalima shiya tura hadimin ya shiga jikinsa duk tsawon wanna shekarun da suke a tare, dan kawai ya san duk wani motsinsa Abinda bai sani ba a yanzu hadimin ba aikinsa yake ba aikin Iffah yake yi, ita kuma ta zabi tattara laifin ga Miran Jasim a karan kanta saboda haka ta tsara binsu daddaya, shi kuma zata cigaba da jansa a kasa har zuwa gabar da take so.. Wata irin daddagewa da fashewa da kuka da Miran Arshaan yay ne ya katse mata tunaninta. Ta zubama drama din tasa ido dan ya wani daddagene ya fashe da kuka yana duban Miran Jasim kai kace dada duniya har zuciyarsa ne. "Jasim! Jasim Akhi mu zakama haka? Kai da kanka zakaci amanar dan uwanmu ka zama jagoran shirya halakashi. Innalillahi wa'inna ilaihiraji'un.…. Mi kake bukata ne? Miye dan uwanmu bai mana na gata ba a wannan duniyar? Ya rikemu tamkar yanda Abie (Tajwar Abdul-majeed) zai rikemu, amma mu mu kasa rike jininsa daya tilo a duniya da bashi goyon bayan mulkin da ALLAH ya daura masa. Dama na jima ina zargin kana kwadayin mulkin nan ne,ban tabbatar da hakan ba sai randa aka samu kayan tsafin daka saka a kujerar da adalin shugabanmu yake zama, kaki zuwa kuma wajen meeting da ga karshe ma bakin cikin an ganoka ka nema halaka iyalinka" ya sake fashewa da kuka. Wata irin mahaukaciyar shaka Miran Jasim da jikinsa ya hau kakkarwa ya kaima Miran Arshaan da kyar kuwa aka bangaresa yana fadin sai ya kashe Miran Arshaan din. Duk da wannan dambarwa mai gayya mai aiki Shahan-shan na zaune ne yana binsu da kallo ta cikin gilashinsa. Shi kansa a wannan gabar sai ya shiga dan rudani, dan a iya bibiyar rayuwar uncle's din nasa da yake yi tun lokacin da ya fara zarginsu a tare suke aikata komai sai dai a sirrance ne kam. Kuma ita kanta Iffah ta sanar masa su biyu ne ai, amma yaya akai hakan ta kasance komai ya juye kan Miran Jasim shi kadai. Tamkar Sayeed Hanifud-Din kam yasan mike ransa ya ambato sunanta. "Ko Zawiata-almilk nada wani karin bayani akan alakarta da Miran Jasim da har hakan ta kasance tsakaninsu?". Shiru kamar Iffah bazata motsa ba, sai kuma ta yunkura da kyar fuskarta jage-jage da hawaye. Handkherciff din da Malikat Haseenat ke miko mata ta amsa ta goge fuskar sannan ta fuskanci kotu bayan ta saci kallon Tajwar Eshaan da takeji a jikinta kallonta yake, dan tun dazun takejin kaifafan idanunsa a kanta. Hakama Malikat Bushirat kallonta takeyi. A nutse cikin nuna rauni ta ce, "Ni ban san mizan ce ba, amma abinda na sani kawai bani da wata alaka da shi nikam, hasalima ban sanshi ba a zahirance sai a randa aka nunani gaban dai iyayen wanna gida mai albarka. Kuma ko'a ranar bazan iya cewa ga kamaninsa ba. Sai a randa Zawjata-almilk farko ta rasa ranta ne dai-dai da rasuwa sayeed Khairul-Bashar na nufi sashen mai girma Shahan-shan hankali tashe dan ina son tabbatar da abinda al'umma keta fade akan shine ke kashe matansa. Ina tsaka da dube-dubena akan gawar suka shigo tare da shugaban jami'ai, Ni kuma sai naji tsoro na buya, bayan an fita da gawar ashe shi ya ganni shine ya dawo da baya. Na tsorata amma sai ya ce na nutsu muyi magana, zai rufamin asiri amma yana so muyi aiki tare. Ya dan mun maganganu dai da yawa. A ranar ya kawo min maganganu masu rudarwa, mafi girma a cikinsu nunamin video cewar adalin shugabanmu ne ya halakamin iyayena da tsafin maciji kamar yanda naga alamar saran maciji a jikin Zawjata-almilk da ta rasu, ya kuma sanar min nima na tsira zanyi ba dan haka nima nayi takaina. Nazo mu hada hannu mu yakesa dan baza'a hukuntashi ba. Ni a lokacin maimakon cemasa wani abu ma rudani na shiga da tashin hankali akan iyayena,dan haka bamma gama saurarensa ba, ganin bana a hayyacina ya tashi ya fita. Sai kuma A ranar 9 ga watan 2 dai nanma na samu kiransa misalin karfe takwas a dare. Nayi matukar mamakin hakan, dan bai boyemun ba ya sanar min aiki fa yake son miyi tare kamar yanda ya a waccan ranar amma zai sanar min abu. Ban katsesa ba nace ina saurarensa.Yasanar min magana bazata yiwu ta wayar landline ba, amma ga number dinsa na kirashi direct video call. Har lokacin ban kawo komai a raina ba, duk da dai inajin toro ganin shiga uncle dinsa ne, idan na fadama wani bama za'a yarda dani ba. Dan haka nabi umarninsa na kira din dan bangama sanin yanda akeyi anan din ba. Tun daga wannan ranar ban sake fahimtar komai ba da ga yanda yake bibiyata sai da nakai madara ga adalin shugaban wannan kasa ya sha. Daga nan na fara fahimtar makirci ne musamman yanda ya dage akan sai an kaini kurkuku. Bayan an kainin kuma ya bini har can yana fadamin maganganun banza harda na rashin da'a". Ta fashe da kuka mai cin rai, wanda a yanzu kam da gaske kukan take, dan kalmar KARUWA da Miran Jasim ya ce zai maidata na mata radadi har yanzu a cikin rai. Dolene yanda Iffah ke bayanin yasa kaji hawaye yazo maka, kuma ko kai waye sai kaji ka yarda da ita. A nan din ma fa rudewa kotun ta sake yi, yayinda Miran Jasim ke hargowar sai ya batar da ita, sai ya shafe babin rayuwarta baki daya ita da Miran Arshaan da sukaci amanarsa. Babuma wanda ke saurarensa sai ALLAH wadai da ake jifansa da shi da tausayin Iffah da gaba daya yau kowa ya fahimci an mata makirçin ashe ,Dama can wasu da yawa tunma a ranar data aikata suke fadin bayin kanta bane, tayi kankanta da aikata laifin ita daya. To sai gashi yau kam komai ya fito filin ALLAH. Kotun tai bala'"in daukar turiri har sai da Tajwar Eshaan da kansa ya tsawatar. Dan danan kowa ya nutsu kotun tai tsitt. Ya dauka tsahon mintuna uku babu alamar zai ce wani abu, kafin ya nisa da kyar cikin maganar nan tasa a fuse kamar wanda akaima dole. Da kyar ya iya danne zafi da radadin da zuciyarsa ke masa kanjin wai uncle dinsa yama matarsa magana ta rashin da'a,amma ta boye masa. "Alamu da kalaman Jasim in Abdul-majeed Aliy Qutb sun tabbatar da duk abinda aka sanar anan game da shi ya aikata. Sai dai duk da haka wannan kotu mai adalci zata bashi damar sanar damu dalilinsa na aikata duk wannan a zama na gaba. Za'a tsaresa a kurkukun da Zawjata-almilk tai rayuwa har zuwa ranar da kotu zata sake bukatar ganinsa a gabanta. Wannan kotu kuma ta wanke Zawjata-almilk da ga zargi, tare da bada damar kawo bokan da yay sihirin gaban shari'a shima. Tanada damar shigar da kara itama a karan kanta game da amfani da ita da Jasim yayi. Daga karshe ni Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed Aliy Qutb ina shigar da kara nima bisa yunkurin kashe min MATA da akayi har karo biyu ta hanyar yimata allurar guda da jefata cikin ruwa..." da ga haka ya mike anutse cike da salon nan nasa yayinda ya bar jama'ar kotu gaba daya a yanayin mutuwar zuune da kalamansa na karshe. Malikat Haseenat kam murmushi ta saki mai sanyi da kayatarwa, hakama Daneen Ammarah. Yayinda zuciyar Malikat Bushirat ke bugawa da wani irin sauri-sauri a cikin kirjinta dake yin kamar zai bude. A bangaren Iffah kam idonta akan Miran Jasim ne, a cikin iska ta rubuta *_FINAL_* da yin alamar yanka wuya ta kashe masa ido daya…….✍️ _Mai RUMAN sai kayi takanka kaima to, dan da gaske Iffah kaza zata koma uwar tone-tone🥱_ 17:14 DAUDAR GORA.. Book2 (pg55) Il A ..Wani irin fadawa tai saman gado cike da farin ciki tana sakin siririyar dariya. Babu abinda take hangowa sai idanun Miran Jasim da na Malikat Bushirat harma da Miran Arshaan. Tai wani irin juya ta sake juyawa a gadon sai kace tarwada. "Kina lokacinki Fhareedah bint Zayyan". Ta fada a fili tana sake kyalkyalewa da dariyarta kai kace an mata albishir ne da dawowar su Baby kasar ruman. Yanda take ji kam kamar ta tashi tayita taka rawa. Daya da ga cikin burikanta ya cika, ya cika a gabar da ALLAH ya bata abinda baya cikin lissafinta. Tabbas zama mallakin Shahan-shan baya cikin lissafinta. Lissafinta na daukar fansa ne kawai,fansar jinin yan uwanta da bazata iya yafewa ba. Sai dai kuma dukkan labarin ya canja, ya canja da canjawar shigowar su Miran Jasim cikin tattakinta batare data tsaro da su ba. Shigowar Tajwar Eshaan in Haysam Abdul-majeed matsayin wani abu mai daraja a ciki labarinta batare da ta rubuto da hakan ba nan ma. "Ya rabba" ta fada a zahiri tana lumshe idanunta da sukai wani tar-tar na haske fuskarta na kara kawatuwa da murmushi mai kayatarwa. "Miyasa kika boye min?". Bata fahimci mi yake nufi ba, dan haka ta idanunta da jan cikinsu ke dan raguwa a hankali ta zuba masa. Bazata iya jurar kallonsa cikin ido ba dan haka ta dauke su ta maida gefe. "Ban san akan mi kake magana ba Sultan". Sai da ya dan furzar da hucin baci ran da yake ta dannewa, a dan fuse ya furta, "Jasim! Miyasa kika boyen ya sameki a kurkuku da maganar banza?" Shiru kamar bazatace komai ba, sai kuma ta motsa cikin sauke ajiyar zuciya ta ce, "Kayi hakuri, a lokacin ban san ta yanda zan tunkareka ba. Ban kuma san ta yanda zaka fahimceni ba. Kuma ai ALLAH ya kareni da ga sharrinsa tunda ga shi yau gaskiya tayi halinta". Shiru baice komai ba, dan zuciyarsa tafasar kishi take har yanzu akan wanna kalmar, tafi komai tsaya masa a zuciya fiye da abinda Miran Jasim din ya aikata masa dan ya jima da sanin dama suna farautar rayuwarsa. Sai maganar rashin fitowar sunan Miran Arshaan shima na masa kaikawo, kamar zai mata magana akan hakan sai kuma dai ya hadiye kayansa da tunanin ko Miran Jasim din ne kawai ya fiddo mata da nasa hali. Amma in bai manta ba ranar a kalamanta ta masa nuni ne da mutane biyu ko yace fiye da daya. Hakan na nufin bayan Jasim din akwai wani kenan. To miyasa ta boye? Bashi baice komal ba ya dal cigaba da kallonta. Kusan minti daya sannan ya motsa da cigaba da don takawa a hankali cike da kasaitar nan tasa. gabanta yaja ya tsaya, tare da zare hannunsa dake cikin aljihun wandon jeans dinsa ya mika mata. Idanunta ta dago ta kalli hannun da ke fari tas da shi, ga jini nata kaikawo a tafin kamar ba namiji ba. Idanunsa ya dan lumshe da budewa a lokaci guda yana gyada mata kai alamar ta daura nata. Kamar mai jin tsoron hakan ta dago natan ta dora a cikin nasan. Sake lumshe idanun yayi kamar wani wanda maganadisu ya taba,batare da ya bude ba ya dagota ta mike tsaye itama. Matsota yay kawai jikinsa ya rungumeta tsam-tsam. Sassanyar ajiyar zuciya ta saki nutsuwa na ratsata, sai kawai ta kankamesa itama tare da kwanciya luff a faffadan kirjinsa tana shakar daddadan kamshin turarensa mai saka zuciyar mai shaka nutsuwa _Oh oh su Iffah an waye an manta da mu dangi Mammah duniya abin tsoro ce why, duk da mun jima da sanin Jasim baya kaunar Abni sai yau din da komai ya fito fili ya bani mamaki. Har zuciyata iya abinda nake kallonsa da shi shine nuna adawa kawai ga mulkin tunda shine burinsa. Amma why ban taba kawo zai iya shirya halaka rayuwarsa ba haka. Wace irin rayuwa ce wannan wai dan uwanka jininka ya zabi cutar da kai akan abin duniya mai yankewa. Wai ina mahaifinmu da ya zama sanadin kawomu duniyar ma? A da shine a wannan kujerar, amma ya shude kamar ba'ayisa ba, aka daura dan uwanmu, shima ya shude kamar baiyi ba, idan sukai hakuri shima wataran bashi bane anan din. Bazan boye miki ba Mammah,zuciyata ta fara min sake-sake da kokwanto akan rasuwar Haysam Akhi, haka Zawjata-almilk da muka rasa, anya kuwa hakan baida alaka da su Jasim Akhi ya karba makamancin tayin da muka jima da tsigesa a cikin jininmu?. Dan zuciyata ta fara rabuwa biyu bayan zargin mushirakar can data dade da shudewa a tarihinmu kamar akwai wata mai irin al'amuranta a yau zagaye da wani namu". Malikat Haseenat da ke ta faman jinjina kai taja ajiyar zuciya mai karfi tare da fesar da iska zazzafa da ga bakinta. "Tabbas duniya ta cancanci zama abar toro kam Ammarah, nima kuma kamar ke zuciyata ta fara rawa, ta fara rawa da wannan gabar har inajin ni kaina ban yarda da kaina ba. Tabbas mushirikar can ta shude ita da tarihinta, amma sai zuciyata ta gagara nutsuwa da hakan duk da tsahon shekarun nan da suka shude da kasancewarta.Babu abinda Jasim bazai iya aikatawa ba,musamman idan na kalla irin mugun zaman da mukai da mahaifiyarsa a masarautar nan. Dan haka shima kam yanzu abin tuhuma ne. Sai dai akwai wani furuci da yarinyar nan tayi yafa tsaya mun a rai, tun dazun kuma yake mun kai kaWO…. "Wane furuci kenan Mammah?". "Furucin bibiyar gawar Zawjata-almilk ta karshe da muka rasa, inda ya zama sanadin haduwarta da Jasim. Lallai ina bukatar ganawa da Zawjata-almilk". Shiru Daneen Ammarah tai tana kallon Mammah, sai kuma ta nisa itama zuciyarta na mata kai kawo akan hakan. Eh tabbas wannan furuci abin a bibiya ne, dan sai a mahanga ya ke da nasaba da abu biyu. Shi kansa Jasim suspect ne a wannan case din shima. Duk da dai duk Zawjata-almilk na baya da suka rasa ransu suke fara zuwa su ganta kafin kowa. Firgigita ta daw hankalinta sakamakon tabatan dan Malikat Haseenat tayi, taja ajiyar zuciya mai nauyi da sauke numfashi. "Yi hakuri mammah, why na tafi wata duniyar tunan nima. Za'ai bincike ga Ibnati dinne? Ko kuwa ya kike nufi?". Kai Malikat Haseenat ta jinjina da fadin, "Fara nemo min ita a waya". *Har yanzu Iffah na kwance a kan gado cike da farin ciki da nishadi kira ya shigo a landline din dakin. Wayar ta kalla kamar bazata tashi ba. Sai kuma ta mike lokacin da take gab da yankewa ta daga. Kin yin magana tai, sai da Daneen Ammarah tai sallama sai kuma duk ta rude. "Lah Mamy kece, Barka da wannan lokaci a gafarceni". Murmushi Daneen Ammarah ta saki mai sanyi da ga can tamkar Iffah'r na gabanta, tana matukar kaunar yarinyar nan ta yanda ita kanta ma bata san adadi ba. A hankali ta nisa da sakin ajiyar zuciya ta ce, "Ba komai Ibnati, Mammah ce ke bukatar magana da ke daman". Tamkar Iffah na gaban Malikat Haseenat ne cike da girmamawa ta gaisheta duk da yanzun nan suke rabuwa da ga zaman kotu. Da ga can ta amsa mata cike da nutsuwa da dattakonta, kafin ta aura da fadin, "Mijinki ya shigo ne?". A hankali Iffah da kalmar ta bama kunya da yi mata nauyi ta ce, "A'a Mammah".Murmushi Mamma ta sakeyi da gyada kai da fadin, "Idan har bakya wani uziri bayan sallar isha'i ina son ganinki". Cike da girmamawa ta ce, "To Mammah insha ALLAHU". Shiru tai tana kallon wayar bayan ta yanke.Zuciyarta sai faman mata kaikawo take da tunani kala-kala. Sai kuma ta dage gira da dan tabe baki tana ajiye kan wayar ta mike. Ficewa tai da ga dakin ta nufi can saman ginin dan wajen na matukar kayatar da ita. Tana kaunarsa fiye da kowane waje a masarautar. "Abu Harith kana lafiya kuwa? Tunda muka baro kotu ka kasa zaune ka kasa tsaye. Duk da dai nasan abinda dan uwanka ya aikata ga wannan bawan ALLAH dole ya tabaka, amma sai nake ga damuwar taka da rudanin kamar sunma fi na kowa. Ka tuna nima fa dan yar uwata ce dat rikeni tamkar uwa, sannan shugabanmu baki daya. Mu dukanmu ya sakamu muka haukace akan baiwar ALLAHr yarinyar nan da bataji ba bata gani ba. Why har kunyar haduwa da ita nakeji yanzu. ALLAH sarki Mammah tai ta son nuna mana gaskiya muna bijirewa, duk da nuna mana gaskiya muna bijirewa, duk da ALLAH ne shaidata kai ne ka dinga kara tunzurani har idanuna sukai makancewar kasa hasashen komai gashi na kare da dana sani" Kallonta kawai yake tana zabga zance ko hadiyar yawu batayi, bata san jima yake tamkar ya shakota ba tsabar takaici da takura masa da tai. Shifa shi kadai yasan irin kalar tashin hankali da rudanin da yake ciki akan al'amurin nan. Da farko yayi zaton hadiminsa na aikine bisa aikinsa na tsawon shekaru da ya daurasa a kai akan bibiyar dan uwansa, sai dai kallon da yarinyar nan Iffah tai masa sanda suke fitowa daga kotun ya matukar saka zuciyarsa neman bugawa. Idan har ya canka dai-dai lokacin da take shigewa *_Next.…_* ta rubuta masa akan iska fa. Wannan kalmar itace ta tsaya masa a zuciya taki fadawa sai faman kaiwa da komowa take..... "Ya ilahi Abu Harith!!". Jasrah da ke hargowar kwala kiran sunansa ta katse masa tunani. Cikin bacin rai ya nuna mata kofa alamar ta fice masa. Rai bace take dubansa itama, har taji ta kasa hakuri ta ce,"Kamar ya na fita bayan kuma magana muke?Wai shin kodai kaima da naka kashin ne a jiki banda labari, dan wannan yanayin naka kam ya fara sakani a rudani.. "Jasrahhh!!!". Ya fada cikin karajin da ya sakata zabura. Cikin wata irin birkicewa da bata taba fuskanta da ga garesa ba ya sake nuna mata kofa. "Wihy idan baki fita min ba sai na kwashe fuskarki da maruka. Banza kawai kin dameni, ki barni naji da abinda ya isheni ban san wawanci". Ba karamin tsorata Jasrah tayi ba kam, dan wutar bala"i ta gano kuru-kuru cikin idanunsa da kan fuskarsa. Cike da sassarfa ta nufi hanyar fita ranta a bace da tsawar da yay mata.... Tana gama ficewa yaja wani shegen wawan tsaki da raka bayanta da harara ya ce, "Tinkiya kawai, ban san damuwa",. A wani irin zafafe ya koma jagwab cikin kujerar ya zauna yana dafe kansa da ke sara masa da karfin masifa. Dai-dai nan kira ya shigo wayarsa. Sharewa yay bai dauka ba har ta tsinke, sai kuma ga wani ya sake shigowa. Tsaki yaja da finciko wayar daga aljihu da niyar kashewa gaba daya yaci karo da sunan Ameera Haifah baro-baro. Kamar bazai daga ba nan ma sai kuma ya amsa a fusace da kaita kunnensa. "Ke kuma miye kike wani kirana a wannan lokacin bayan kin san mi ake ciki". Da ga can cikin muryar tashin hankali ta ce,"Dolene na kiraka Arshaan. Dan tabbas akwai matsala. Matsala babba why. Na kasa gane komai, ka saka zuciyata a rudani gaba daya game da abinda ka aikata a kotu. Shin mi hakan ke nufi? Taya komai da muka aikata mu ukkoma kansa shi kadai? Kai ne kai hakan kokuwa hatsabibin yaron can ne ya kulla mana gadar zare ta hanyar yar iskar yarinyar can. Wihy kaina ya kwance gaba daya, dan ALLAH ka zaba mana wajen haduwa yanzu da gaggawa kar zuciyata ta buga". "Da zata buga din ma da kowa ya huta.Please malama ki kyaleni bana bukatar magana da kowa okay". Kittt ya yanke wayar batare da jiran cewarta ba."Ashe zan kasheka na kashe banza idan kace zaka zamar min matsala Arshaannn!!!". Ta fada cikin karaji da cije lips dinta jikinta na rawa. Wayar ta cilla saman gadonta ta cigaba da kaikawon da take tun dazun a cikin dakin. Tunda ta baro kotu ta gagara zaune ta gagara tsaye.Tasan in har Miran Arshaan ne ya shirya komai ga Miran Jasim hakan na nufin itama bazata tsira ba dan tare sue kulla komai. Idan kuma Tajwar Eshaan ne ya ganosu kama Miran Jasim kawai ba komai bane garesu face talala. Don dole ma akwai wani abu da ya kamata ta sani, dole ta sanshi a yau din nan yanzun nan basai gobe ba. Idan Miran Arshaan ya cigaba da wofantar da tuhumar da take masa to lallai zai ganta yanzu a sashensa kuwa. Sai dai duk ma abinda matar tasa zata zarga ta zarga. Ko kuma in ma barewa zatai why sai dai ta bare da su su duka amma bazata taba barin Miran Arshaan ya sha ba shima ko ya kaita kasa kamar yanda ya kai Jasim. A fusace ta sake fisgar wayarta ta hau rubuta masa dogon text message jikinta sai tsuma yake. Ga uwar zufa ta mata sharban kamar wadda taci gudu a cikin dokar jejin da babu komai sai sahara mai zafi da ta dauki zafin rana. Yi take kamar zata tsumbula cikin wayarta dake a hanunta. Ihu kawai ya rage ta kurma akan kiran Daneen Waheeda da take faman yi tun bayan fitowarsu kotu amma bata daga ba.Ta bata lokaci da tunanin zatai kiranta in ta gani amma babu alamar hakan zata faru. Kuma asha ba shima ko ya kaita kasa kamar yanda ya kai jasim. A fusace ta sake fisgar wayarta hau rubuta masa dogon text message jikinta sai tsuma yake. Ga uwar zufa ta mata sharban kamar wadda taci gudu a cikin dokar jejin da babu komai sai sahara mai zafi da ta dauki zafin rana.. Yi take kamar zata tsumbula cikin wayarta dake a hanunta. Ihu kawai ya rage ta kurma akan kiran Daneen Waheeda da take faman yi tun bayan fitowarsu kotu amma bata daga ba.Ta bata lokaci da tunanin zatai kiranta in ta gani amma babu alamar hakan zata faru. Kuma a kalla kira na goma sha bakwai kenan take mata.Banda text message da zai iya zama biyar koma fiye da hakan. Kamar almara aka daga wayar, cikin rawa da kakkarwar jiki ta kaita kunnenta tana fadin. DAUDAR GORA Book 2 Chapter: 56 ."Haba Waheeda ina kika shiga kekuwa haka kinsa zuciyata na neman karasa harbawa a tsaye". Da yar raha-raha da ga can Daneen Waheeda ta ce, "Oh oh Kinga kwantar da hankalinki nabar wayar ne a daki why ina sashen surukinki. Halan wani masifar shegiyar can ta sake jangwalowa?". "Uhhm ai wannan karon ba ita ta jangwalo ba ita aka jangwalowa. Ni Ashwaq naga abinda zai kasheni a wannan masarautar yau da raina. Wai kin san kuwa madarar da aka shayar da dakinki wai Miran Jasim ne ya samar da ita". "What!" Daneen Waheeda ta fada cikin zabura da ga fasa zaman da tai niyyar yi da ga can. "Wait! Wait wait Ashwaq wai nikam mi kike son fada minne haka. Jasim Akhi namu kike nufi yake shirin kashe Eshaan din komi? Ni Wihy gaba daya ma kin rikitamin lissafi". "Bake lissafinki ke a rikice ba, ai kowa ma yau a masarautar nan lissafinsa a rikice yake wallahi. Tiryan-tiryan ta kwashe komai na zaman kotu a yau ta fada mata kamar yanda ta saba kai mata gulmar duk wani motsin yan masarautar musamman Malikat Bushirat. Wani irin irin tashin hankali Daneen Waheeda ta shiga tana zungura manya-manyan zagi dan ita dama can mace ce masifaffiya mai zafin tsiya. A wani lokutan akance tafi kowa gado mahaifinsu a kaf yayan Tajwar Abdul-majeed. Daga can ta ce, "Gobe ki tsumayi zuwana RUMAN yar uwa wannan dambarwar ba'ayita babu ni kusa ba. Amma karki fadama kosu Mammah. Shin yaya bakar dagarki tayi ne za'a kashe mata tilon dan gwal din ta da take hura muku hanci". "Uhm-iuhm ai labarin kam dai babu dadin ji, amma tunda kince kina tafe ke dai kwantar min da hankalinki sai kin iso kawai". "Okay bara kiga naje na fara shiri ma tun yanzu. Amma da mutuniyarki zan taho dan wannan karon kam inaga sai na nunama Eshaan kwanji akan Iftihal dan ko yaki ko yaso sai ya aureta tunda dai matan sun daina mutuwar". "Ina tare da ke dari bisa dari kuwa. ALLAH ya kawo ku lafiya". Da ga haka sukai sallama Malikat Ashwag na faman sakin murmushi, dan itafa ranta fari kal da abinda ya faru a yau din. (Ina fatan kun gane matsayin Daneen Waheeda dai. Itace kanwa ga Daneen Ammarah da Tajwar Haysam mahaifin Tajwar Eshaar ta uku ga Malikat Haseenat da mukace tana aure acan yankin larabawa. Kawace sosai ga Malikat Ashwaq, kuma yar uwa, dan kusan ma itace tai ruwa tai tsaki wajen gain Malikat Ashwag din ta auri Tajwar Haysam duk da shima dai ya sota a karan kansa. Tare sukai karatu dan haka akwai shakuwa mai karfi a tsakaninsu da har take tayata kishin Malikat Bushirat. A duk sanda ta sami wani sabon labari musamman akan koma bayan Malikat Bushirat sauri take taga ta sanar ma Daneen Waheeda. Shiyyasa a randa hadimanta sukazo mata da bayanin Malikat Bushirat taje wajen Malikat Haseenat akan kara auren Tajwar Eshaan tai azamar kiranta ta sanar mata dan tasan babban burin Daneen Waheeda din shine hada auren babbar diyarta da Tajwar Eshaan da suke kusan sa'anni. Ta matukar mutuwa a kansa amma shi ko kallo bata ishesa ba. Hakan yasa ita Daneen Waheeda din taso a hada auren amma Malikat Bushirat taki bada hadin kai. Dan ta fahimci so Daneen Waheeda keyi Tajwar Eshaan ya auri yarta su koma juya akalarsa data mulkin kasar ruman din. Ga kuma sharadin da UWA ta gindaya mata na karta yarda Tajwar Eshaan ya auri wata da ga cikin zuri'ar masarautar sam. Yin hakan gagarumin abune da zai rusa komai da yake komai a hanunsu. @) ALLAH yasa kun gane) Dan daburcewa uwa taso yi, dan bata so akazo wannan gabar da wuri haka batare data Karmala shirinta ba. Anya kuwa batayi babban sakaci akan ta-kurya ba. Itama fa itace tsanin cikar nata burin data dauki tsawon shekaru tana bi matakala-matalaka domin maida murtani ga ahalin wanna masarauta baki daya.…... Ganin irin kallon da ta-kurya ke mata ne ya sata hadiye komai ta dai-daita yanayinta. Fuskarta ta sake tsukewa da gyara zaman kasaitarta. "Ta-kurya ban boye miki domin wani dalili ba, sai dan kareki da ga shagala kan al'amarin sa, amma ki sani na jima biye da Jasim da hana makircinsa tasiri kan Ajlaan. Shin bakiyi mamaki ba ne yau? Bakiyi mamakin faruwar abinda ya faru din ba ne? To bari na kaiki inda baki sani ba. Nice nan da kaina na budewa Jasim aiki yau, kuma na fara ne tun a randa ya kai kayan asiri fadar Ajlaan. Ban miki maganar bane ba dan ina son sai an kai karshe. Kuma duk abinda ya farun yau a kotu nima ina tare da ku". Wata irin wawuyar ajiyar zuciya Malikat Bushirat ta sauke. Gaba daya sai taji abinda ya tsaya matan a makoshi ya fada a cikin cikinta.Dari bisa dari ta yarda da zancen uwa, dan bata taba mata karya ba (hummmm). Fuskarta dauke da murmushi ta sake gurfana a gabanta. "Yanzu kam na fahimta, na fahimci komai uwa. Dama ni nasan bazaki bari na fadì ba. Amma naso ace kin sanar min tuni, da sai na daidaita rayuwa jasim,sai na kafa tarihi akansa irin wanda harara wani bazai sake kwatantawa ga Saiful- malik dina ba a wanna masarautar" Wani irin shegen dariya uwa ta kwashe da shi."K yar halak ce ta-kurya, shiyyasa nake sonki fiye da duk wanda ya kasance a karkashin baiwata. Na miki alkawarin bazaki sake yin kuka ba, zan cigaba da tsaya miki fiye da tsayawar da nai miki a baya. Zan cigaba da kare Ajlaan fiye da kariyar da kike tunanin yana da (Wa"iyazubillah. Ya rabba ka tsaremu da aikata shirka koda a cikin duhun jahilci ne @ A). Zan baki mamaki, tabbas zan baki mamaki ta-kurya". "A kullum cikin bani mamaki kike ai uwa, shiyyasa bazan gaji da fada ba, bazan gaji da maimaitawa ba ke ta dabance a cikin daban". "Hhahahahahaha!!!!!!!". Uwa ta kyalkyale da wata irin mahaukaciyar dariya har ta-kuryar najin sautinta cikin iska, kai kace gaba daya masarautar koma kasar ruman dinne baki daya zasu jita. (Uhm uhm da alamafa akwai wani kulli tare da Uwa, ko minene shi@? Muje dai zuwa sannu sannu ai bata hana zuwan sai dai a dade ba'a je ba🏃‍♀️🥱) A wani bala' in firgice ta farka da ga barcin da ya figeta bayan idar da sallar azhar. Kanta dake wani irin sara mata ta dafe tana ambaton sunan ALLAH. Ta kai tsahon minti uku a haka kafin ta mike daga saman sallayar da anan barcin ya kwasheta. Gaba daya jikinta tsuma yake, yayinda zuciyarta ke mata tariyar mafarkin nata dalla-dalla. Jin jiri na neman zubdata kasa tai saurin zubewa bakin gado tana sake dafe kai. A hankali ta furta, "Uwa!! Wacece ita? Ta ina zan fara bincike saninta",. Kantane ya sake sara mata, tunda take mafarke-mafarkenta bata taba mai nauyi irin wannan ba. Duk da bataga fuskar wadda ke zaune a kujerar karfen nan ba zagaye da wasu irin munanan halittu taji a ranta dole ta kasance abar toro. Sai kuma gain Malikat Bushirat da tai a gabanta dirkushe, shin minene hadin Malikat din da wadan nan munanan hallitun? Tajwar Eshaan a gefe daddaure da wasu irin igiyoyi wuta, sai dai shima bata ganin fuskarsa amma tana iya jin yanda yake ambaton sunayen ALLAH radam. "What's wrong.. Dagowa tai da sauri dan sam bata san da shigowarsa cikin dakin ba, hasalima bata san ya dawo ba. Idanunta data kafeshi da su ta dan janye tana kara tsarkake sunan UBANGIJI mahaliccin wannan bawa. Komai nasa mai kyau ne da birgewa. Hatta kayan zaman gida dan ya saka badan kwalliya ba sai su fidda cikar kamalarsa da zati. "Kaina ke ciwo". Ta fada kanta a kasa dan kallon nan nasa na kasa-kasa da ke daburta mata lissafi bata son shi. (Aljanun sunzo kenan) ya fada a zuciyarsa yana wani dan yamutsa fuska. A zahiri kam baice komai ba ya dai cigaba da kallonta. Kusan minti daya sannan ya motsa da cigaba da takawa a hankali cike da kasaitar nan tasa. A gabanta yaja ya tsaya, tare da zare hannunsa dake cikin aljihun wandon jeans dinsa ya mika mata. Idanunta ta dago ta kalli hannun da ke fari tas da shi, ga jini nata kaikawo a tafin kamar ba namiji ba. Idanunsa ya dan lumshe da budewa a lokaci guda yana gyada mata kai alamar ta daura nata. Kamar mai jin tsoron hakan ta dago natan ta dora a cikin nasan. Sake lumshe idanun vavi kamar wani wanda maganadisu va taba. din akwai wani kenan. To miyasa ta boye? Bashi da mai basa amsa baya kuma bukatar sonji gareta yanzu dan ransa duk babu dadi yake ji. Itama da kanta ta fahimci hakan, dan fuskarsa a tsuke take fiye da sanda suka fita kotun. Sai duk take jin kuma babu dadi. Dan haka kawai take jin tausayinsa. Idan har zai shiga damuwa saboda halin wancan karen uncle din nasa, yaya zai kasance kuma a randa zai san mahaifiyarsada kanta ke halaka masa matan aurensa da duniya ke kallonsa a mai halakasu tsahon shekaru. Kai kai wannan al'amarin fa na taba mata zuciya why sosai matuka. Ajiyar zuciya ta dan sauke a hankali, sai kuma ta kai hanunta saman lallausan gashin sajen fuskarsa ta shafa. Murya can ciki ta ce, "Kayi hakuri? Ka amsa da hannu biyu jarabawace. Badan UBANGIJI baya sonka ba ya jarabeka da su. Shi kansa mulkin ma da kake kai ai jarabawa ce. Kai numfashinmu ma kansa jarabawace a garemu, dan UBANGIJI ya azurtamu da shine domin yaga zamu kasance masu bin dokokinsa ne ko kuwa masu bijire masa". Idanunsa da ke lumshe tun sanda ta daura hanunta saman fuskarsa ya bude a hankali,sunyi zajur fiye da yanda ya shigo da su a dan birkice. Hannun ya kamo yana kallonta, cikin tsananin kasala ya daura lips dinsa a tsakkiyar tafin ya sumbata. Sai da ta matse jikinta tsabar vanda lininta vAv wata irin vamuitsawa har cikin fara son kwatar kanta. Sai dai kuma babu hanyar samun wanna damar da ga jarum Shin yaya lafiyar giwa da ma. Balle kuma ita da kanta ta balle likin. Duk yanda taso tuna masa dinkin dake a tare da ita babu alamar yana ma iya jinta balle fahimta. Burinsa kawai yake kokarin cimmawa a cikin rufewar idanu.. (* Tsun-tsun da ya ja ruwa (?)) *** Da karfi, karfin karfi yake buga kansa a bangon dakin kurkukun mai tsananin duhu da ta iya karamin windown kawai ake iya gain dan ziririn haske. Gaba daya zuciyarsa ta bushe, zafi yakeji a cikinta mai tsananin tururi dake kona zuciya. Shi shi Jasim ibn Abdul-majeed Aliy Qutb ne wata karamar yar iskar yarinya yar cikin cikinsa tai sanadin kawowa cikin kurkuku. Shi Arshaan da ya koya sanin kansa a wajensa zai yima cin amana? Shi hadiminsa da ya dauka tsahon shekaru yana kyautatama zaici amanarsa a gaban makiyansa. Wace irin wannan, mai tsananin duhuwa da babu lissafinta a cikin duka lissafe-lissafensa. Ta yaya shi Jasim in Abdul-majeed Aliy Qutb zai yi irin wannan faduwar bakar tasan a gaban karfin ikon dan makiyansa kuma makiyinsa. Cigaba da buga kan yake da karfinsa yana ihu mai tsananin karaji da ya saka masu tsaron dakun kurkukun nasa da Tajwar Eshaan ya bada umarnin bama tsar mai tsananin tsauri tsora. Cikin karfin hali daya a cikinsu ya dan leko, ta dan hasken da ya hasko da ga karamin windown ya hango fuskar Miran Jasim da tai wani irin jage-jage da jini dan ya fasa goshinsa. A zabire yay baya yana zazzaro idanu. Yan uwansa ya sanarma, babu bata lokaci sukai kiran shugaban jami'ai suka sanar masa dai-dai da yanke jikin Miran Jasim da jini ke rinjayarsa va fadi kasa.... Rungumeta yay tsam-tsam a cikin jikinsa idanunsa a lumshe. Jin kukanta yake har tsakkiyar zuciyarsa. Dan kuka take sosai five a daren shekara jiya kasancewar yau fami yay akan ciwo. "Ni ka kaini wajensu Ummu". Ta fada cikin kuka. Yanda tai magana tana sake barke masa da kuka ga hawaye shabe-shabe harda su majina ya sa yaji dariya na yunkuro masa. Kamar ba yanzu ta gama iyayi a kotu ba,dan duk abinda ta dingama Miran Jasim akan idonsa ne tsaf. Amma jiba yanzu a dan abinda bai taka kara ya karya ba ta koma abin tausayi.Ya fahimci sai ya dage matukar dagewa akan dorata a irin layin da yake bukata ta hau inba hakaba ragguwa za'ai, bakinne kawai cike da zance da tsiwa. Bashi da burin sake wani auren bayan ita, dan haka dolene ta shirya karbarsa a duk sanda yazo. Murmushin da ke neman kufce masan ya hadiye da kyar da saka hannu yana goge mata fuskar data kwabe da hawaye. Cikin dadisashiyar muryarsa data kara komawa can kasan makoshi a fusge ya furta, "Am sorry bazan kara ba". "Why zaka kara, ranar ba sai da kace bazaka sake ba amma yau ka kara, ni bazan sake zama a sashen na a kasheni kwana na bai kare ba". Ta kara barke ma sa da kukan tabara. Yanzu kam kasa rike dariyar yayi, dole ya Murmusa har jerarrun fararen hakwaransa masu è da siririyar wushirya na bayyana Bashi da zabin da ya wuce sake rungumeta a jkinsa tsam-tsam yay murmushinsa iya san ransa. (Shi kam wannan Fitinanniyar yarinya ALLAH ya bashi, kuma yana so da kaunar abinsa fiye da zaton mai hasashe). A zuciyarsa yake maganar yana bata sumbata masu kyau a wuya. Kafin ya mike ya dagata cak zuwa bathroom. Idanunta ta rumtse sosai da kankamesa ita a dole karya gammata jiki kar kuma ta gansa itama. Gashi yay mata mai kyau bayan ya duba yau baiyi barna ba dan ciwukan wancan ranar ma sun warke sai abinda ba'a rasa ba, taimaka mata yay tai wanka, hawaye kuwa da ya ga ba dainawa zatai ba bai sake ce mata komai ba kansu. Da zasu fito cewa tai ita why bazata iya ba sai dai ya dauke ta. Baice komai ba, illa murmushi da yay a zuciyarsa ya dauke ta cak suka fito tana faman tura masa karamin bakinta.Ga idanu sunyi luhu-luhu na kukan da tasha. "Idan baki bar turamin bakin nan ba zan maimaita ni babu ruwana". Ya fada yana tsane mata laimar ruwan kanta da towel. Narai-narai tai da fuska zata sake masa kuka ya daura yatsansa saman bakinta ya ce, "Shilli!! Harda kuka ma". Babu shiri ta hadiye abunta da maida bakin da sauri.Murmushi ya saki ya cigaba,Da tsane mata mata gashin…. kiran da ya shigo ta sashi dakatawa su duka suka dubi wayar, kamar bazai daga ba dan har tana gab da tsinkewa sai kuma ya kai hannu ya dauka batare daya matsa da ga gabanta ba ko dauke towel din da ga kanta. Cikin girmamawa shugaban jami'ai ya shiga gaishesa da ga can, a takaice ya amsa masa murya a dake kamar bashine ke hidimtawa yar yarinya ba. Da ga can shugaban jami'ai ya kara nutsuwa sannan yay masa bayanin abinda ke faruwa. Shiru kamar bazaice komai ba kafin ya nisa a dan fisge da maganar nan tasa kasa-kasa ya ce, "Doctor Afif ya je ya dubasa a cikin kurkukun". Daga haka ya yanke kiran. Kallonsa Iffah tai da jajayen idanunta, gaba daya ya sauya kamar bashi ba ya koma mata Tajwar Eshaan ibn Haysam Abdul-majeed da ta fara gani a sashen Mammah. Muryarta a dashe saboda kukan da tasha ta ce, "Miya faru?".Kamar bazai kulata ba yana cigaba da goge mata kan tsahon minti biyu kafin ya motsa lips da kyar ya furta "Jasim"……………✍️ DAUDAR GORA Book 2 Chapter: 57 "Kinci abinci?". Kanta ta girgiza masa alamar a'a. "Mi yasa?". "Banajin yunwa ne". Shiru bai sake cewa komai ba har kusan minti daya. Hannunsa da ke kan bayanta ya dago ya daura saman goshinta data kwantar jikinsa, kan da zafi sosai har ma yana iya jinsa. "Na miki addu'a?". Nan ma kan ta daga masa. Komai bai sake cewa ba shima. Sai matsawa da su da yay zuwa gadon, tana a jikin nasa ya kai zaune itama ya zaunar da ita a cinyarsa. Addu'a ya fara mata a kan idanunta a lumshe, bayan ya kammala ta kwantar da kanta a kafadarsa tai luff tana sauke ajiyar zuciya a jajjere. Nan ma sun jima a zaman shiru kafin ya kirata muryarsa a can kasan makoshi. "Mrs Eshaan?". "Uhmyim". Ta amsa itama can kasa batare data dago kanta da ke a kafadarsa ba. "Miyasa kika boye min?". Bata fahimci mi yake nufi ba, dan haka ta dago idanunta da jan cikinsu ke dan raguwa a hankali ta zuba masa. Bazata iya jurar kallonsa cikin ido ba dan haka ta dauke su ta maida gefe. "Ban san akan mi kake magana ba Sultan". Sai da ya dan furzar da hucin baci ran da yake ta dannewa, a dan fuse ya furta, "Jasim! Miyasa kika boyen ya sameki a kurkuku da maganar banza?" Shiru kamar bazatace komai ba, sai kuma ta motsa cikin sauke ajiyar zuciya ta ce, "Kayi hakuri, a lokacin ban san ta yanda zan tunkareka ba. Ban kuma san ta yanda zaka fahimceni ba. Kuma ai ALLAH ya kareni da ga sharrinsa tunda ga shi yau gaskiya tayi halinta". Shiru baice komai ba, dan zuciyarsa tafasar kishi take har yanzu akan wanna kalmar, tafi komai tsaya masa a zuciya fiye da abinda Miran Jasim din ya aikata masa dan ya jima da sanin dama suna farautar rayuwarsa. Sai maganar rashin fitowar sunan Miran Arshaan shima na masa kaikawo, kamar zai mata magana akan hakan sai kuma dai ya hadiye kayansa da tunanin ko Miran Jasim din ne kawai ya fiddo mata da nasa hali. Amma in bai manta ba ranar a kalamanta ta masa nuni ne da mutane biyu ko yace fiye da daya. Hakan na nufin bayan Jasim din akwai wani kenan. To miyasa ta boye? Bashi da mai basa amsa baya kuma bukatar son ji da gareta yanzu dan ransa duk babu dadi yake ji.Itama da kanta ta fahimci hakan, dan fuskarsa a tsuke take fiye da sanda suka fita kotun. Sai duk take jin kuma babu dadi. Dan haka kawai take jin tausayinsa. Idan har zai shiga damuwa saboda halin wancan karen uncle din nasa, yaya zai kasance kuma a randa zai san mahaifiyarsa da kanta ke halaka masa matan aurensa da duniya ke kallonsa a mai halakasu tsahon shekaru. Kai kai wannan al'amarin fa na taba mata zuciya why sosai matuka. Ajiyar zuciya ta dan sauke a hankali, sai kuma ta kai hanunta saman lallausan gashin sajen fuskarsa ta shafa. Murya can ciki ta ce, "Kayi hakuri? Ka amsa da hannu biyu jarabawace. Badan UBANGIJI baya sonka ba ya jarabeka da su. Shi kansa mulkin ma da kake kai ai jarabawa ce. Kai numfashinmu ma kansa jarabawace a garemu, dan UBANGIJI ya azurtamu da shine domin yaga zamu kasance masu bin dokokinsa ne ko kuwa masu bijire masa". Idanunsa da ke lumshe tun sanda ta daura hanunta saman fuskarsa ya bude a hankali, sunyi zajur fiye da yanda ya shigo da su a dan birkice. Hannun ya kamo yana kallonta, cikin tsananin kasala ya daura lips dinsa a tsakkiyar tafin ya sumbata. Sai da ta matse jikinta tsabar la jininta yay wata irin yamutsawa har brain. Yunkurawa tai da nufin tashi a jikinsa ya hanata hakan, sai ma fuskarta da ya kamo cikin tafukan hannunsa ya manne lips dinsu waje guda. A tare suka saki ajiyar zuciya Iffah na rumtse idanu da karfi. A tsorace take matuka,amma ta danne ta karfin tsiya domin taimaka masa ya samu nutsuwar zuciya kamar yanda Mammy ta mata nasiha akan a duk sanda taga ya shigo da fushi tai kokarin gain ta cire masa wannan fushin da damuwar ta hanyar jansa jikinta da hira da raha ko nasiha. Idan kuma ya nuna bukatar wata hidimtawarta ko ita ta fahimci akwai abinda ke sakashi shagala ko kwaranyewar damuwarsa da wuri to tazama jaruma wajen aikatawa kota bashi hadin kai. Tunanin a iya abinda yake yi din baza'ai gaba ba ya sata sakar masa jiki harta fara bashi hadin kai. Gaba daya ta sake rikita masa lissafi, dan abune da bai zaton samu da ga gareta ba anan kusa haka. Tuni idanunsa sun rufe ya juyesu a gadon ya shiga yamutsata yanda yake so cikin nutsuwarsa, dan a rayuwa komai na Tajwar Eshaan babu gaggawa a ciki, koda kuwa yana a wani yanayi ne da zai iya canjawa sai kaga a zahirance babu wanna canjin a gaggawa garesa. Dan nutsuwa da kasaita a jinin jikinsa take yawo da harbawar bugun zuciyarsa. Jin al'amarin ya fara zarce karamin tunaninta tuni ta fara son kwatar kanta. Sai dai kuma babu hanyar samun wanna damar da ga jarumin ,Shin yaya lafiyar giwa da ma. Balle kuma ita da kanta ta balle likin. Duk yanda taso tuna masa dinkin dake a tare da ita babu alamar yana ma iya jinta balle fahimta. Burinsa kawai yake kokarin cimmawa a cikin rufewar idanu.. (* Tsun-tsun da ya ja ruwa (?)) *** Da karfi, karfin karfi yake buga kansa a bangon dakin kurkukun mai tsananin duhu da ta iya karamin windown kawai ake iya gain dan ziririn haske. Gaba daya zuciyarsa ta bushe, zafi yakeji a cikinta mai tsananin tururi dake kona zuciya. Shi shi Jasim ibn Abdul-majeed Aliy Qutb ne wata karamar yar iskar yarinya yar cikin cikinsa tai sanadin kawowa cikin kurkuku. Shi Arshaan da ya koya sanin kansa a wajensa zai yima cin amana? Shi hadiminsa da ya dauka tsahon shekaru yana kyautatama zai ci Amanarsa a gaban makiyansa. Wace irin wannan, mai tsananin duhuwa da babu lissafinta a cikin duka lissafe-lissafensa. Ta yaya shi Jasim in Abdul-majeed Aliy Qutb zai yi irin wannan faduwar bakar tasan a gaban karfin ikon dan makiyansa kuma makiyinsa. Cigaba da buga kan yake da karfinsa yana ihu mai tsananin karaji da ya saka masu tsaron dakun kurkukun nasa da Tajwar Eshaan ya bada umarnin bama tsar mai tsananin tsauri tsora.Cikin karfin hali daya a cikinsu ya dan leko, ta dan hasken da ya hasko da ga karamin windown ya hango fuskar Miran Jasim da tai wani irin jage-jage da jini dan ya fasa goshinsa.A zabire yay baya yana zazzaro idanu. Yan uwansa ya sanarma, babu bata lokaci sukai kiran shugaban jami'ai suka sanar masa dai-dai da yanke jikin Miran Jasim da jini ke rinjayarsa va fadi kasa.... Rungumeta yay tsam-tsam a cikin jikinsa idanunsa a lumshe. Jin kukanta yake har tsakkiyar zuciyarsa. Dan kuka take sosai fiye dana daren shekara jiya kasancewar yau fami yay akan ciwo. "Ni ka kaini wajensu Ummu". Ta fada cikin kuka. Yanda tai magana tana sake barke masa da kuka ga hawaye shabe-shabe harda su majina ya sa yaji dariya na yunkuro masa. Kamar ba yanzu ta gama iyayi a kotu ba,dan duk abinda ta dingama Miran Jasim akan idonsa ne tsaf. Amma jiba yanzu a dan abinda bai taka kara ya karya ba ta koma abin tausayi.Ya fahimci sai ya dage matukar dagewa akan dorata a irin layin da yake bukata ta hau inba hakaba ragguwa za'ai, bakinne kawai cike da zance da tsiwa. Bashi da burin sake wani auren bayan ita, dan haka dolene ta shirya karbarsa a duk sanda yazo. Murmushin da ke neman kufce masan ya hadiye da kyar da saka hannu yana goge mata fuskar data kwabe da hawaye. Cikin dadisashiyar muryarsa data kara komawa can kasan makoshi a fusge ya furta, "Am sorrybazan kara ba". "Wlhy zaka kara, ranar ba sai da kace bazaka sake ba amma yau ka kara, ni bazan sake zama a sashen na a kasheni kwana na bai kare ba". Ta kara barke ma sa da kukan tabara. Yanzu kam kasa rike dariyar yayi, dole ya Murmusa har jerarrun fararen hakwaransa masu da siririyar wushirya na bayyana a zahiri Bashi da zabin da ya wuce sake rungumeta a jkinsa tsam-tsam yay murmushinsa iya san ransa. (Shi kam wannan Fitinanniyar yarinya ALLAH ya bashi, kuma yana so da kaunar abinsa fiye da zaton mai hasashe). A zuciyarsa yake maganar yana bata sumbata masu kyau a wuya. Kafin ya mike ya dagata cak zuwa bathroom. Idanunta ta rumtse sosai da kankamesa ita a dole karya gammata jiki kar kuma ta gansa itama. Gashi yay mata mai kyau bayan ya duba yau baiyi barna ba dan ciwukan wancan ranar ma sun warke sai abinda ba'a rasa ba, taimaka mata yay tai wanka, hawaye kuwa da ya ga ba dainawa zatai ba bai sake ce mata komai ba kansu. Da zasu fito cewa tai ita why bazata iya ba sai dai ya dauke ta. Baice komai ba, illa murmushi da yay a zuciyarsa ya dauke ta cak suka fito tana faman tura masa karamin bakinta.Ga idanu sunyi luhu-luhu na kukan da tasha. "Idan baki bar turamin bakin nan ba zan maimaita ni babu ruwana". Ya fada yana tsane mata laimar ruwan kanta da towel. Narai-narai tai da fuska zata sake masa kuka ya daura yatsansa saman bakinta ya ce, "Shilli!! Harda kuka ma". Babu shiri ta hadiye abunta da maida bakin da sauri. Murmushi ya saki da cigaba da tsane mata gashin…. kiran da ya shigo ta sashi dakatawa su duka suka dubi wayar, kamar bazai daga ba dan har tana gab da tsinkewa sai kuma ya kai hannu ya dauka batare daya matsa da ga gabanta ba ko dauke towel din da ga kanta. Cikin girmamawa shugaban jami'ai ya shiga gaishesa da ga can, a takaice ya amsa masa murya a dake kamar bashine ke hidimtawa yar yarinya ba. Da ga can shugaban jami'ai ya kara nutsuwa sannan yay masa bayanin abinda ke faruwa. Shiru kamar bazaice komai ba kafin ya nisa a dan fisge da maganar nan tasa kasa-kasa ya ce, "Doctor Afif ya je ya dubasa a cikin kurkukun". Daga haka ya yanke kiran. Kallonsa Iffah tai da jajayen idanunta, gaba daya ya sauya kamar bashi ba ya koma mata Tajwar Eshaan ibn Haysam Abdul-majeed da ta fara gani a sashen Mammah. Muryarta a dashe saboda kukan da tasha ta ce, "Miya faru?".Kamar bazai kulata ba yana cigaba da goge mata kan tsahon minti biyu kafin ya motsa lips da kyar ya furta "Jasim"……….✍️ DAUDAR GORA Book 2 Chapter: 58 Bayan sallar isha'i cikin dauriya Iffah ta amsa kiran Malikat Haseenat. Tafiya take cikin dabara dan ko yau din ma dai tanajin zafin, ga zazzabi tun dazu yaki saukar mata. Ita bata san randa zatai sabo da wannan al'amari ba kamar yanda ya fada mata dazun. Ta dan yamutse fuska da cigaba da tafiyarta a hankali, dan ita kadai ta fito babu wani dan rakkiya, Tajwar Eshaan ma yana massalaci tunda ya tafi sallar magrib bai shigo ba. Kadan-kadan take dan cin karo da hadimai, duk da ko'ina na masarautar zagaye yake da haske ba ganeta suke ba, sai dai yanayin shigarta kansa su mata gaisuwar girmamawa kamar yanda suke ma duk wani ahalin masarautar babba ko yaro. Hannu ta dinga daga musu kawai dan batajin yin magana har takai sashen Malikat Haseenat din. Nan din ma bawani sun ganeta bane sosai, dan sanda take kokarin shiga falon Malikat Haseenat din da sauri Banou tai niyyar dakatar da ita. Sai dai mi, kallon ido cikin ido da sukai ma juna ya sa Hadima Banou din zubewa kasa cikin rawar jiki da tsananin kaduwa. Har taune harshe take wajen gaida Iffah da ke mata kallon tsaf kamar mai son gano ainahinta. Sai da ta mula dan kanta ta yamutsa fuska da watsa mata harara. "K! Har yanzu baki daina bibiyar mutane ba ko?Karki fasa ina tafe kanki ai". Ta fada tana wuceta batare data amsa gaisuwar tata ba. Jagwab Hadima Banou ta zube zaune a wajen zuciyarta na wani irin masifar harbawa. Sosai take tsoron wannan baiwar ALLAH, dan ita kadai tasan mi take ganowa tattare da ita. Ta jima a wajen kafin ta mike cikin rawar jiki ta fita. Can baya ta nufa cikin karamin garden din Malikat Haseenat da takan hutawa, da ga cikin wasu dunkulallun fulawoyi ta zaro yar tukunyar kasa da bakinta ke daure da kyalla an nannade da zare. Warware zaren tai har yanzu jikinta na rawa, abubuwane a daddaure ciki kamar tsokokin nama, haka ta shiga fiddosu tana ware wasu a kasa, sai da ta gama zabowa ta maida sauran ta sake daurewa ta ajiye. Wanda ta fiddo din kam ta kwance hudu ta sakesu, biyu da ga ciki tasa a baki ta cinye tana faman tande lips. Duk abinda take yi tanayi ne tana waige-waige, har dai ta kammala ta mike da sauri ta fito.. Tarba ta mutuntawa Iffah ta samu da ga Malikat Haseenat. Dan an shiryama zuwan nata da zuwa na musamman kamar yanda akan yima Tajwar Eshaan idan zai zo. Iffah har mamakin hakan tayi, dan bata taba tunani ko tsammanin tanada kimar da wani zai mata haka musamman idan akai dubi da shekarunta da kuma gidan data fito na talakawa. Malikat Haseenat dame binta da Kallo kuwa a kallo daya da taima takunta ta fahimci halin da Iffah take, idanu ta dan lumshe tana mai jin tausayinta, dama tasan bazai iya hakurin barinta ta warke yanda suke bukata ba ai, dole ne sai ta dage ma yarinyar da abubuwan da zasu taimaka mata batare data dinga jigata ba. A zahiri kam hannu ta ware mata alamar tazo gareta. Iffah da ke murmushi kanta a kasa ta karasa a nutse ta ko shige jikin nata. Wata irin tagwayen ajiyar zuciya ta dinga saukewa a jajjere haka itama Malikat Haseenat din. Kusan minti biyu suna a haka kafin ta zaunar da ita kusa da ita gab-gab dan har cikin rai take jin kaunar yarinyar nan. Duk yanda Iffah ta dinga nuna jin kunya Malikat Haseenat bata barta ba sai da sukaci suka sha a tare cike da farin ciki, suna tsaka da cin abinci ne ma Daneen Ammarah itama ta shigo. Cike da girmamawa Iffah ta gaisheta, ta amsa mata da kulawa cike da so da kauna. Bayan sun kammala hadimai suka gyara wajen, Malikat Haseenat kuma ta bama Iffah wata yar madara a kofi mai dadin tsiya data kasa gane ma wace irin madara ce, dan an mata wasu hadi ne na musamman. Dagawa daya ta shanye ta ajiye kofin, karamin bowl dake dauke da hadadden hadin zuma da dabino da kwa-kwa dama abubuwan da bata sani ba nan ma ta bata tare da karamin cokali a ciki da zata dinga diba kadan-kadan tana ci. "Hafidah!" Malikat Haseenat ta kirata a hankali. Amsawa Iffah tai kanta a kasa. Mammah bata damu ba ta cigaba da fadin, "Kin san miyasa nace kizo ki sameni?". Kai Iffah ta girgiza mata ta ce, "A'a Jaddah"., Malikat Haseenat ta kalla Daneen Ammarah suka dan sakarma juna murmushi kafin ta sake maidawa kan Iffah. "Magana nake so muyi mai muhimmanci dan nasan bazakimin karya ba". "Insha ALLAHU Jaddah". "'Dazun a zaman shari'ar can kinyi wata magana ce data kasa barin raina akan ganin gawar Zawjata-almilk da kikai. Shin ko akwai wasu alamomi da kika gani tattare da ita? Ko kuwa kisa ne kawai na kai tsaye da raunika?" Shiru Iffah tai da dan mamakin tambayar a ranta, ta kasa gane wann al'amarin, shi mai matan yace bai taba ganinsu ba, bayanan suke mutuwa, kuma ko gawarsu baya gani. Shin itama Jaddah din du matsayinta a masarautar bata taba gain gawarsu kenan amma har wadan can rubabbun su Jasim ke iya gani ko mi? ''Ibnati" Daneen Ammarah ta katse mata tunani. Firgigit ta kawo numfashi da kallonsu, sai kuma ta maida kanta ta risinar tana mai sauke ajiyar zuciya. "Jaddah zan fada miki duk abinda kike bukatar j, amma dan ALLAH ki gafarceni nima zanyi wat tambaya". "Bismillah". Malikat Haseenat ta fada kai tsaye cikin bata dama. Numfashi Iffah ta dan fesar ta nisa. Kafin tace, "Jaddah na kasa ganewa, shin duk matansa da suka rasu kuma baku taba ganin gawarsu ba kamar yanda shima yace bai taba gani ba kenan?". Daga Malikat Haseenat har Daneen Ammarah kallon Iffah suke mamaki fes a kan fuskokinsu. Daneen Ammarah ta ce, "Shi Abni din ya fada miki bai taba ganin gawar matansa ba?". "Har suna raye bai taba ganinsu ba ma yace". Kallon juna Daneen Ammarah da Mammah sukayi, sai kuma duk suka dubi Iffah da itama su take kallo ta gefen ido. "Tofa babbar magana".Cewar Malikat Haseenat. Daneen Ammarah ta ce, "Babbar magana kam, ta gaske ma Mammah. Ni kaina ma ya sake kullewa akan Al’amurin”. "Dole ne kam Ammarah. Amma Hafida-ti bara na baki amsar tambayarki, masarautar nan nada tsare-tsare irin nata da ka'idoji, a ciki harda zama iya huruminka, dan haka ni bana a cikin masu hurumin kan duk abinda ya shafi Zawjata- almilk na Hafidi, wannan hakkin mahaifinsa ce, ni kuma nawa hakkin a kansu yake tunda sune matan dana. Wannan ne dalilin da yasa ban taba gani ba. Kema da kike ganina tsaye a kanki saboda matsalolin da aka samu ne da har yasa ita Bushirat janyewa da ga al'amuran ki, ni kuma naga bazan iya yardawa ba na dauka na adana". Cike da gamsuwa Iffah ta jinjina kanta. Sai kuma ta cigaba da basu bayani akan abinda suke bukata. Riko hanunta Daneen Ammarah tai kamar a razane ta ce, , "Cizon maciji kuma?". Cike da mamakin yanda suka razana Iffah ta gyada mata kai. "Eh Mamy saran maciji. Sai dai da alama kafin ma hakan tayi yunkurin kare kanta da har ya zamto dakin ya kasance a harmutse". "Ya rabba! Uwa. Mammah tabbas wannan alama ne na UWA. Itace, itace azzalumar bata barmu ba. Bata barmuba Mammah, tana raye why tana raye". Daneen Ammarah ta fada tana rike kanta da ke mata wani irin sarawa ta fara layi kamar zata fadi. Da sauri Iffah ta mike ta riketa cikin tashin hankali. Hakam Malikat haseenat duk ta rikice, dan ta fahimci ma tsahon shekaru data shude ce da ga garesu ke neman dawowa ga Ammarah din kanta. Da kyar suka iya samu suka kwantar da ita, a tare suka dinga tofa mata addu'oi. sannu a hankali ta fara lafawa tana sauke ajiyar zuciya a jajjere sai kuma barci ya dauke ta mai nauyi.Ajiyar zuciya Malikat Haseenat ta shiga saukewa da sauri- sauri, yayinda Iffah sunan uwa da Daneen Ammarah ta ambata ke faman mata kaikawo kirjinta na wata irin bugawa.. "Jaddah waye UWA kuma?". Kalmar ta subuto da ga bakin Iffah batare da ta shirya hakan ba. Idanu kawai Malikat Haseenat ta zubama Iffah batare da tace komai ba. Har Iffah ma ta fidda rai da ga cewarta. Dan tsahon kusan mintuna biyar kafin Malikat Haseenat din ta nisa. "Uwa. Uwa.. uwa…. sanin wacece uwa na kunshe ne a cikin labarin masarautar nan Hafida-ti. Labarine mai tsaho da ya zama a cikin manyan labaran da suka kasance da ZUCIYAR ahalin Aliy Qutb gaba daya. Duk da ya shude, shudewa ta tsahon shekaru da muke tsammanin karnin ya shafe da fatan daina tunashi koda a cikin tarihinmu da alama hakan bamai yiwuwa bane." "Jaddah idan na dage akan son na sani ban shiga cikin hurumin daba nawa ba? Dan ina mutukar so da zumudin na sani din". Murmushi mai ciwo Malikat Haseenat ta yi, sai kuma ta zuba idanunta akan Iffah tana dan jinjina kai. "Baki tsallake huruminki ba Hafida-ti, tunda kin rigada kin zama mu mun zama ke. Sai dai dokar wanna zuri'a ta dade da shardanta goge wanna tarihin domin mantashi da daina tunashi garemu har abada..." taja nannauyan numfashi mai hade da ajiyar zuciya. "Da zan iya wofantar da bukatarki da nace karki sake tambaya. Amma inaji a raina bazan iya ba, dan inhar dai da gaske baya ce ke son dawowa ta maimaita kanta kamar yanda nake hasashe a kanki tun zuwanki masarautar nan dolene labari biyu ya dawo a lokaci guda domin kasancewarsu cikin juna duk da raina namin wasi-wasin taya hakan zata kasance bayan anyi ruwa ne an dauke kasa ta shanye kayanta?" Sam Iffah bata gane cudaddun kalaman karshe ba, dan haka ta tsurama Malikat Haseenat idanu kawai ko kyaftawa babu.Murmushi Malikat ta sakar mata tare da lumshe idanu ta bude a kanta lokaci guda. "Idan har zan samu warwarewar lissafina zan sanar miki abinda kike son sani Hafida-ti. Zan sanar miki tarihi da tushen kasancewar uwa a cikin tarihin wannan DAULA kamar yanda kike bukata". A hankali Iffah ta saki murmushi mai kayatarwa maimaita kanta kamar yanda nake hasashe a kankii tun zuwanki masarautar nan dolene dayan biyu ya dawo a lokaci guda domin kasancewarsu cikin juna duk da raina namin wasi-wasin taya hakan zata kasance bayan anyi ruwa ne an dauke kasa ta shanye kayanta?" A hankali Iffah ta saki murmushi mai kayatarwa da jinjina kanta. "Nagode sosai Jaddah, ALLAH ya kara girma da lafiya mai albarka da tsahon rai". "Amin". Malikat Haseenat ta amsa tana gyara zamanta cikin wheelchair dinta da fuskantar Iffah da kyau……….✍️ A muma to bara mu gyara zaman. @) 🥱😂 DAUDAR GORA Book 2 Chapter: 59 ."Labarin ya fara ne tun zamanin iyaye da kakanni da ya kasance akwai karancin ilimin addini. Ba a daular ruman kawai ba hatta da sauran dauloli da ma talakawan kasar RUMAN kowa yasan ani matukar imani da tsafe-tsafe a karnikan da suka shude. Zaki samu duk talaucin mutum duk yawan arzikinsa yanada wani boka da ke fada masa motsinsa ko wani abu dake tunkarosa, ko bashi Sa'a a abinda zai yi ko yake yi. A lokacin da addinin musulunci ya fara kutsowa cikin wanna kasa tamu idan akaji ka amsa sai an halaka ka, dan kuma kai shugaba ne to fa za'a tubeka a koreka kai da duk ahalinka. ALLAH sarki, masu shiga musulunci da masu hidimar gain an shiga sunsha matukar wahala a wancan karnin. Komai ya canja da cajawar labarin wanna kasa dalilin wani fari da akai na tashin hankali, ruwan dake zagaye da wannan tsuburi da kasar RUMAN take ya zagaye komai hadda gidaje da dukiyiyi har ma da rayuka. Ba kasar ruman ce kawai ta girgiza ba, Africa da ma duniya baki daya wannan al'amari ya matukar girgizasu, inda aka shiga kawo mana dauki ta kowane bangare. Wannan shine mafarin fara samun canji, domin a cikin wanna yanayin ne tarin bayin ALLAH mabiya addinai daban-daban suka fara yakin ganin sunja ra'ayoyin mutane da dukiyoyi da wasu abubuwan kyale-kyale na duniya, harda masu yimusu tayin binsu kasashensu suyi rayuwa. Babu mai son yabar kasarsa tushensa dan haka mutane suka fara bijirewa, sai ko wani bawan ALLAH ya basu goyon baya mai suna SHEHU UTHMAN DAN-FODIYO da ga kasar NIGERIA. shine ya tabbatar musu kasarsu itace yancinsu, itace gatansu, itace martabarsu, su tashi da karfin kwanji su gyarata yayi alkawarin tallafa musu da karfin jiki da ga tawagarsa. Zantukansa sun kayatar da kowa sun saka karsashi a jikin mutane, musamman yarima mai jiran gado Miran Aliy Qutb. Ganinfa Miran Aliy Qutb ya amshi wannan tunatarwa tun ya samu mabiya. Abu mafi daukar hankalin mutane SHEHU UTHMAN DAN-FODIYO ya kasance MUSULMI ne, hakama almajuransa da sukayi masa rakkiya, amma sai bai taba cema wani dole sai ya shiga addininsa ba ko masa tayi da wata dukiyar da zai shigan, ya dage dai tukuri da taimakonsu yana ibadarsa. Hakan sai ya shiga birge mutane tuni suka fara karbar musulinci. Sai kuma cikin kankanin lokaci kasashen musulunci manya irinsu Saudi Arabia suma suka fara yunkurowa, mabiya addinin islam suka hada karfi da karfe wajen hidimtawa wanna kasa ta RUMAN ta sake ginuwa ta komawa kan kafafunta. A cikin abinda bai wuce shekaru kalilan ba abubuwa suka cigaba da canjawa acewar munada tarin tattalin arziki ka davan-daban. An dauki babban mataki akar ruwan dake zagaye da mu, aka kuma kara fadada kasar ilimin addini ya yawaita, kafirci ya fara nisa a cikin al'ummar mu. Masu bautar gumaka da yin imani da bokaye duk suka fara janye jiki, wasu bokayen ma da kansu suka dinga ajiye kayan tsafe-tsafen suma suka koma ga ALLAH. Masu taurin kan cikinsu kuwa sai suka bijire da jan tunga, wasun su suka koma dazuka wasu kuma suka koma yi a boye." Ta dan ja ajiyar zuciya da daukar ruwa takai bakinta. Kafin ta cigaba da fadin, "Uwa diyar wata bokanya ce babba a wannan masarautar,bayan mahaifiyarta da ake kira bokanya Ta-bunu ta mutu itace ta gajeta. Shekaru masu yawan gaske da suka shude itake tafiya da jan zaren yi da hani na wannan gida harta mutu yarta ta gajetan (wato Uwa). Ta kuma gajeta ne ana gab da samun wannan iftila'i da ya faru,lokacin da abun ya faru tana farkon fara jin dadin kar fin ikonta dan tafi mahaifiyarta hatsabibanci. Domin kuwa komi za'ayi sai an sanar mata tace ayisa, idan ko ta hana akan dakata koda ana sonshi. Hatsabibiya ce matuka. Dan duk da mahaifin Miran Aliy ya yarda yan kasarsa suyi addinin da suke so shi ya kasa rabuwa da Uwa har ALLAH ya masa rasuwa Miran Aliy Qutb ya zama Shahan-shan. Shi dai men hirans da farbn amma hahmands yaso bijirewa da farko, amma babu wanda yasan miya faru hakan ta gagara ya cigaba mata biyayya akan abinda ta shardanta kota hana. Na takaice miki zance fa ikon Uwa sai da ya kasance itake kamar mulkar kasar ruman dan har shi Shahan-shan din sai da cewarta yake cewa ga talakawansa. Haka yay mulkinsa ya shude Miran Abdul-majeed dansa, mijina ya karbi kasar ruman. Muma mun cigaba da kasancewa a karkashin say na UWA, sai dai abun na matukar damuna kasancewar nayi ilimin addini mai zurfi. A lokuta da dama idan tace ai abu nakan kalubalanta har sai na fahimtar da Tajwar Abdul-majeed illarsa. Duk bayan wata uku takan saka ayi yanka na bakaken shanu da karnuka da rakuma wai tsarine na wannan daula. Takan tilasta daya daga cikin yayan Shahan-shan a aura mata wani talakan kasa ko bawa ta samu ciki ta hainu,da zaran ta samu cikin dole kuma ya saketa. Shi kuma abinda aka haifa zai cigaba da rayuwa a cikin masarautar bashi da wani karfin iko da shi. Sai dai kin san wani abun mamaki da ya fara jan ra'ayina harna bijirema wanna al'amarin?". Jiki a sanyaye Iffah ta girgiza mata kai. Nisawa Malikat Haseenat tayi da cigaba da fadin, "Duk wadan nan yaran da aka haifa ta wannan hanyar basa zarce shekaru bakwai a duniya suke rasa ransu. Na fahimci hakane ta hanyar bibiyar tarinhin wanna masarautar kasancewa mutum mai son sanin tarihi. Lokacin dana fara kalubalantar yankan da akeyi duk bayan wata uku na bakaken shanu da karnuka ne tasa Abdull-Majeed ya auro mahaifiyar su Jasim. Ban damuba dan wannan bashine gabana ba, ban kuma canja daga bijirewata ba da cigaba da nusar da su akan sanin ma'anar yankan nan.Alhamdullah naci nasara, naci nasarar dawowar hankalin wasu jikinsu akan hakan aka fara ja"injar a daina a canja da wani abu na sadaka bakwai sai yankan ba. Yayinda wasu kuma ke fadin ai yankan ma sadaka ne tunda raba naman ake wa talakawa da hadimai. A cikin tsaka da wannan dambarwa na haifi Haysam. Mahaifin mijinki kenan. Haysam yaci wahala sosai da cututtukan da aka gagara gane kansu, sai dai ALLAH ya kaddara kwanakinsa basu kare yana yaro ba. Bayansa na haifi Ammarah, Ammarah ta zo da wasu abubuwan ban mamaki a rayuwarta tun tanada karancin shekaru. Sai Waheeda, auta Nayyar, zuwa lokacin matan Abdul-majeed mu hudu ne, kowacce kuma ta haihu da shi, akwai maza kuma akwai mata. Bari na sake dawo miki akan yanka, bijirewata da mabiya dana samu yasa aka daina a zahirance,ashe a boye ana cigaba da yi batare da sanin Tajwar Abdul-majeed da ni ba. Sai da wata ranar juma'a da yamma fadan yara ya hada Jasim da Haysam shi da yan uwansa suka masa taron dangi Ammarah ta shiga dukan,mata kai da akai ta yanke jiki ta fadi ,abinka da yaro sai duk suka hadu kanta suna ihu ganin jini ta hancinta. An kinkimota an kawomin tana zubda wanna jini, cikin ikon ALLAH sai ban rude ba na fahimci habo ne. An bata taimakon gaggawa jini ya tsaya har tai barci, sai dai lokacin da take farkawa bayan sallar magriba sai ta tashi a firgice. Koda na tambayeta bayan na mata addu'a ta samu nutsuwa sai ta sanar min mafarki tayi ana yanka shanaye da yawa bakake da karnuka da rakuma. Ga mahaifinsu cikin bacin rai an dauresa da rufe masa baki. Da farko ban dauki wanna mafarki nata a komai ba, sai kawai nace tai addu'a mafarkine kawai. A'a bayan kwana biyu da hakan tai wata faduwa nan ma sai habo, akai mata magani dai ta kwanta sanda zata farka a firgice, nan mana tambaya ta maimaita min wancan dai mafarki da tayi. Abin ya dan fara damuna sai dai ban maida hankali ba. Da ga ranar kuma bata karayi ba har ta cika shekaru kusan goma sha biyar a duniya.Da ga lokacin kwanaki dai-dai ne bazaki samu Ammarah ta tashi a firgice a barci ba, idan ka tambayeta tace ba komai. Ban taba matsa mata ba duk da abun na dan damuna, sai dai ina binta da addu'oi akoda yaushe ita da sauran yan uwanta. Abu ya cigaba da faruwa daban-daban daga Ammarah naban mamaki, bamu fara sarguwa da ita ba sai a randa aka samu gawar Nayyar a cikin ruwa. Abubuwan data dingayi sai da ya tada hankalin duk wani mai numfashi a cikin masarautar nan, inda ta dinga ihu da jadada sai ta dauka fansar jinin dan uwanta. Anyi-anyi kuma ta fada miya faru take irin wannan magana taki cewa komai, harma abin ya ban haushi na tattarata na kyale, a kuma lokacinne ita kuma ta tattara ta tafi makarantar koyan aikin likitanci a kasar America, Sai lokaci-lokaci take zuwa mana hutu ta koma. Ta maida hankali sosai saboda tana so, gashi kuma makarantar da aka sakata makarantace ta musamman. A shekarar da take kammalawa a shekarar yayansu Haysam yay aure, hakama kanwarta Waheeda, anyi-anyi ta fidda miji itama tace a barta ba yanzu ba, ita akwai wanda take jira. Sam bamu takurata ba, dan tanada karamin jiki sosai, shekarun nata ma dai ba wasu bane masu yawa, in bama mun fada ba zaka dauka Waheeda ce babba gareta. Anyi bikin Haysam da Waheeda Ammarah ta cigaba da aikinta a cikin clinic din masarautar nan da kuma karatunsa a cikin wannan kasa ta ruman, a sati kuma takan zagaya jahohi biyu sau biyu domin bada gudunmawarta ita da wat kungiya da suka hada. Tsahon shekaru hudu babu haihuwa da ga matar Haysam, tadai samu ciki sau daya ya lalace bama ya haura wattani uku ba, harma Waheeda itama acan bata haihu ba. Nata bai damu kowa ba, amma na Haysam an fara kanan magana akan sai ya kara aure kasancewar shine Miran mai jiran gado. Bai son kara aure, amma mahaifinsa ya takura masa, ya nema damar a basa lokaci zai nemo da kansa. Anan kam sai ya bashi dama. Ba'a rufa watanni uku ba kuwa ya kawo sunan Bushirat, ta kasance kanwa ga wani abokinsa da sukai karatu, amma suma yan nan kasar ruman din ne, sannan kuma manyan mutanene dan mahaifinta babban malami ne masani sosai. Kyakykyawar nasabarta yasa bamu wani tsananta bincike ba akai biki. Sai dai me itama shiru, dan garama Ashwaq ta taba bari sau daya. Shekarar Bushirat biyu a masarautar nan itama babu labari sai ma Ashwag din ce dai ta kara bari, dan haka aka sashi ya kara auro Danish-Ara, cikin ikon ALLAH Danish-Ara bata rufa wata guda ba sai ga ciki da ga Bushirat. Kowa yayi farin ciki sosai musamman ma shi da ita da mu kammu, hakama Ammarah kai kacema ita keda cikin, dan gaba daya ta tattara ta koma sashen dan uwanta tana kula da Bushirat. Bamu hanata ba, duk da rashin aurenta na damunmu, sai dai mun fahimci akwai matsalar junnu tattare da ita, dan haka muka dage da addu'a gareta kawai"………..✍️ DAUDAR GORA Book 2 Chapter: 60 ."An haifi ciki lafiya, kuma da namiji sanbalele da yaci suna *_Eshaan_*, Eshaan kyakykyawan yaro mai lafiya da ban sha'awa ga kowa, ga shiga rai. Wata irin makauniyar soyayya Bushirat ke nuna masa har takai Ni kaina sai nayi da gaske nake ganinsa, hakan da take yasa Waheeda yimata tas kafin ta dan canja aka dinga kawomin shi nan. Ya taso yaro mai wayo, miskili da baka iya gane abinda yake so ko baya so sam. Shi ko irin abokan wasan nan na kuruciya Eshaan bayayi, yafi so ya zauna shi kadai shiru ko yayta karance-karancen abubuwa musamman a litattafan tarihin wannan daula da suka shude. Sai dai yana matukar son wasan doki da basket ball, da wasan takobi, idan kuma yana tare da Kakansa ko mahaifinsa zaki dingajin maganarsa ko babu yawa. Al'adar wannan masarauta da Miran mai jiran gado ya kai shekaru bakwai zuwa goma ake kaishi can wani boyayyen waje ya rayu har sai girmansa, ko kuma sarki ya zabi murabus kafin ya mutu shi ya daurasa, idan kuma bazaiyi murabus ba za'a dawo da shi cikin masarauta da iyalansa dan su basa wuce shekaru ashirin basuyi aure ba gaskiya. Shiyyasa sai kiga yaro ya taso mahaifinsa bai wani tsufa ba. Da farko Bushirat ta tsaya tsayin daka akan baza'a rabata da danta ba, nima kuma na bata goyon baya dan banji dadi ba sanda aka rabani da Haysam, sai dai was tsurface-tsurfacen tsafi da Uwa ta fara kawowa a kansa yasa nace a kaisan, ta nuna bakin cikinta sosai akan hakan da nayi, har tai gargadi mai girma akaina da cewarta ni na cika shiga mata hanci ni da zuri'ata. Sam wani kurarinta da tsubbace-tsubacenta basa bani toro, dan da UBANGIJI NAna dogara akoda yaushe. Dan haka na cigaba da dagewa har sai da Tajwar Abdul-majeed ya yarda aka kaisa kasar Cuba. Haukane kawai Uwa da Bushirat basuyi ba, sai dai kamar ALLAH ya saka tsorona ne a zukatansu ni ban sani ba. Dan duk hatsabibancin uwa iyakarta borenta a kaina a bayan idonane, taci alwashi sosai a kaina dalilin dauke Eshaan har ma abin ya dinga daure mun kai amma sai na daukesa aikin banza dan bata isa mun abinda bai kasance jarabawata ba. Komai ya lafa kowa ya cigaba da harkokinsa aka shiga watan azumin ramadan. Azumi nada kwanaki bakwai sai Tajwar Abdul-majeed ya sameni akan zan masa rakkiya ya duba Eshaan da ga can muje umrah da shi bayan salla sai mu maidasa Cuba mu dawo gida. Ban kawo komai a raina ba na shirya mukai wannan tafiya har da Haysam. Munyi-munyi Ammarah ta bimu taki, ashe lokacin ta samu wani saurayi ne ya kuma mata alkawarin dinga zuwa shan ruwa wajenta. Sai da na nuna bacin raina kan rashin son binmu 12:47 Sai da na nuna bacin raina kan rashin son binmu a zatona bata son taje ne su hadu da yar uwarta, sai da ta zauna ta fahimtar dani. Naji dadi sosai, dan tace tana son bashi damane ta karanci halayyarsa anay in bikin sallah ai aurensu kawai. Muni farin ciki da hakan, mun kuma mata fatan alkairi." Malikat Haseenat tai shiru tana jan ajiyar zuciya, yayinda Iffah kejin kaguwa matuka da son jin cigaba, sai dai batayi magana ba har sai da Mammah ta cigaba dan kanta bayan tasha ruwan zam-zam dake gabanta. "'Tafiyarmu itace mafarin kaddarar Ammarah,sannan itace mafarin yakice uwa da ga wannan zuri' ar, sannan itace mafarin yin kuka garemu dama duk al'ummar kasar ruman, sannan itace mafarin hawan Haysam karagar mulki matsayin madadi ga mahaifinsa. Bayan wucewarmu umarah, bisa yarjewar Jasim UWA ta sakasu yin yankan nan dai dana sa Tajwar Abdul-majeed bijire mata akansa, ta kuma basu umarnin daura auren daya daga cikin kannensu da wani bawa ko cikin talakawan gari. Son zuciya da sanin makomar dan da ake so a samar ko ya ta wannan hanyar suka aurar da Ammarah ga dan mai dinka kayan dokin masarautar, domin a ranar sunzo kawo kayan kwalliyar dokuna na bikin al'ada dake tunkarowa. Babu waya a lokacin balle ta sanar mana ko wani ya sanar mana,hasalima sunyi auren ne a sirrance sai ita da suka dauka suka kai wa yaron bisa tirsasashi Ya kusanceta in ba hakaba zasu kashe dukkan ahalinsa da shi kansa. Dolene ya tsorata ya aikata abinda suke bukata yana kuka itama tanayi. Shi UBANG|JI mai hikima ne, sun taya ya kuma isar musu bisa ikonsa, badan baya son Ammarah da wannan bawan ALLAH bane, ba kuma dan yana son nuna Uwa a saman kokarin mu bane. A'a wannan itace kaddararsu. Kuma ALLAH ya rubuta sai an samar da wannan abun haihuwar ta wannan hanyar. Sai dai alhmallh, ina godema ALLAH da sake gode masa, dan kuwa koba komai ta hanyar biyan sadaki da sheda aure abinda ya farun ya faru. Mun dawo muka tadda Ammarah a wani irin yanayi, dan kuwa ta birkice musu matuka, a lokacin kowa ya sake tabbatar da iska a tare da ita. Muni kuka ni da Mahaifinsu da dan uwanta sosai, mahaifinsu kuma ya fusata a wannan karon har ya kulle Jasim a kurkuku tare da duk wanda suka goya masa baya akan aikata aikin, yayi kiranyen uwa amma taki zuwa, an sa malamai domin mata kiranye nanma taki zuwa. Har takai an hada da bokaye irinta amma amsa daya suke bamu tafi karfinsu. Hankalinmu ya tashi matuka, musamman bayan wasu watanni da ciki ya bayyana ga Ammarah, gashi lafiya taki samuwa gareta, tama koma wata iri kamar mai ciwon hauka, ta daina magana da kowa, sai kuka,abinci ma sai an tsaya kanta take ci.ALLAH ne kawai ya zama kariya ga wannan ciki har zuwa ranar haihuwarsa. Tajwar Abdul-majeed ya sakka a nemo masa mijin da suka aura matan, sai dai anje ba'a dace da samunsu ba, wai sun bar asalin kauyensu a wani dare. Iya nema da bincike kuma ba'a dace ba dole aka hakura. A daren wata juma'a ALLAH ya sauki Ammarah lafiya, sai dai tasha matukar wahala kafin ALLAH ya kawo haihuwar. Ta haifo yarinyarta mace kyakykyawa, sai dai babu ta inda take kama da ita sai tambarin tabon tawadar ALLAH da zuri'ar wannan gida ke da ita, bamu san mahaifinta ba kuma balle musan ko da shi take kamar. Mun amsheta hannu biyu, sai dai zagaye take da addu'ar neman kariyar UBANGIJI da ga sharrin uwa. A randa aka haifi yarinyar a ranar ALLAH ya kawo wani mai magani. Malikat Haseenat ta saki murmushi mai ciwo.Tare da fadin "kin san wani abu?" kai Iffah da ke sharar hawaye ta girgiza mata. Malikat Haseenat ta sake sakin murmushi. "Mai maganin nan hatsabilin kansa ne, dan kira daya yayma uwa a randa ya cika kwana uku a masarautar nan a take ta bayyana gabansa gaban kowa wujiga-wujiga. Ya tabbatar mata shi ba azzalumi bane, da sai ya wahal da rayuwarta ta yanda bata isa sake numfashi a duniya ba, amma ko'a yanzu bazai kyaleta ba sai ya nakasa rayuwarta ta yanda bazata kara tunanin cutar da Wani ba. Ya sakata ta warware duka wani tsafi data aikata zagaye damu batare da mun sani ba, sannan ya bude dukkan surukanta a gabanmu yay mata korar wulakanci da gargadi mai tsaurin gaske. Sosai ta dinga kuka da neman gafara da tabbatar masa ta zubda makaman yakinta bazata sake ba a barta taci gaba da rayuwa damu amma yaki saurarenta. Majiya karfin hadimai aka saka suka kwasheta zuwa can tsakkiyar dokar jeji mai tsananin rintsi da hadari suka jefar da ita. Wannan shine mafarin barin uwa tare damu, sai dai kuma a wannan dare ALLAH yay ma jaririyar da Ammarah ta haifa rasuwa, washe gari shima Shahan-shan Abdul-majeed yabar duniya sakamakon bugawar zuciya da saran macijin da aka rasa tushensa, sai kuma ya kwana da tashin hankalin abubuwan da Uwa ta dinga sakasu sunayi na shirka da yanda bayan ya tsawatar wasu suka zagaye sunayi ciki harda dansa Jasim. Abdul-majeed ya rasu, uwa ta shude,jinjirar Ammarah ta koma. Haysam ya zama Shahan-shan. Bayan duk faruwar wadan nan abubuwa da shudewarsu zukata suka hakura abubuwa suka fara komawa dai-dai. Saurayin nan da Ammarah ta shirya gabatar mana matsayin miji ya dawo da burin aurenta duk da ba'a boye masa komai da take ciki ba. Yace yaji ya gani, dan ko a baya da ya janye jikinsaJasim a samesa da gargadin karya sake zuwa an mata aure. Bayan kuma yaji an saketa dan auren kwata-kwata na sati biyu ne ya sake dawowa amma aka hana mishi ganinta ma kwata-kwata. Ammarah taso bijirewa, dan har lokacin bata dawo dai-dai ba, amma naita lallabata da mata nasiha ni da yar uwarta hatta hakura aka daura aure. Sai dai sam auren bai wani je ko'inaba ta fito, sakamakon wata sabuwar kaddarar data afka mata, a duk sanda mijinta zaije gareta sai a sauya halittar matancinta ta koma ta namiji.Dole babu yanda zaiyi ya rabu da ita ta dawo gida, daga nan bata sake aure ba, daga nan bamu sake jin labarin uwa ba, daga nan bamu sake jin labarin bawan ALLAHn nan da ya taimake mu ba akan Uwa ba, daga nan Jasim ya nuna mana ya tuba, sha'anin mulkin Haysam ya cigaba da tafiya a tsaftace dan a masa gargadin nisantar duk wan mushiriki akan al'amurin mulkinsa.. Hawaye sosai Iffah takeyi na tausayin Daneen Ammarah, da tausayin su Malikat Haseenat dan labarin nan ya matukar girgizata, al'amari haka kamar a wasan kwaikwayo, wannan wace irin duniya ce mai cike da son zuciya. Kowa burinsa ya kasance a sama, mai nasara bisa nasarar dan uwansa, kai kai rayuwar gidan sarauta dabance, dabance a cikin duk wani rikicin gidaje da zuri'arsu. YaYanda Iffah ke kuka sai Malikat Haseenat ce ta koma lallashinta. Sai da ta tabbatar ta samu nutsuwa sannan ta mikar da ita. "Hafida-ti, kinga tashi ki tafi dare yayi maybe ma mijinki nacan na jiranki". Cikin share hawaye Iffah tace, "Ai bai san ma na taho nan ba". Idanu sosai Mammah ta waro da fadin "Ya ALLAH, aiko kinyi laifi, maza wanko fuskarki muje na miki rakkiya to". Bata musa ba taje ta wanko fuskar, Malikat Haseenat ta mika mata wata yar kyakykyawar jaka tana murmushi. "Kije da wannan, duk abinda ke ciki kiyi kokarin dinga amfani da shi kamar yanda na rubuta, ki yawaita shiga ruwan zafi har ki saba da daina jin ciwon". Kai Iffah ta sunkuyar cike da jin kunya, sambatai tunanin Mammah din zata gane ba yau, musamman yanda take dauriyar dai-daita tafiyarta duk da zafin da take ji……..✍️ Hummmm babu abin cewa kam yau 🥱🚴 DAUDAR GORA…..I Book 2 Chapter: 61 Tunda suka shigo idanunsa kyam a kansu, yana zaune a falo zama na kasaita da izza da jiran ta inda zata bullo. Tun bayan dawowarsa sallar isha'i ya duba bai ganta ba. Shegen miskilanci ya hanashi tambaya har sai bayan kusan awa daya sannan ya bincika ta cctv camaras. Anan yaga fitarta harma da nufar sashen Malikat Haseenat ita kadai ko tsoro babu tattare da ita duk da darene. Yayi tsammanin zuwan bamai jimawa bane, amma sai gashi har yay wanka yaci abincin dare yay yan ayyukansa babu labarinta, harya kwanta da tunanin zai iya shareta sai hakan ya gagara, gangar jikinsa da zuciyarsa suka tabbatar masa bafa zai iya rayuwa babu mahadinsa ba. Shine ya dawo falo yay zaman jiran ganin ta inda zata bullo kusan awa daya kenan. Gaba daya sai Iffah taji ta tsure da kallon nasa, dan haka ta koma da baya-baya ta labe a bayan Malikat Haseenat. Idanunsa ya dauke daga kanta ya maida ga Malikat Haseenat din shima. Cikin dan motsa lips dinsa ka dan ya furta, "Barka da dare Jaddah". Amsa masa tai cike da kulawa, tare da juyawa ta kamo hanun Iffah da ke labe a bayanta ta maidota gabanta. "Ga matarka nan tane tare dani tun dazun, ALLAH ya tashemu lafiya". Daga haka ta saki hannun Iffah ta gara kekenta ta nufi Elevator. '"ALLAH ya huta gajiya". Ya fada a hankali yana dan lumshe ido da risinar da kansa alamar girmamawa a gareta. Shiru falon bayan tafiyarta babu wanda ya sake kwakwkwaran motsi. Shi ya zuba mata idanun nan nasa masu kaifi, ita kuwa tana tsaye a inda Malikat Haseenat ta barta kanta a kasa tana wasa da yatsun hanunta, tsigar jikinta sai yamutsawa take dan har cikin jininta takejin tasirin kallonsa a kanta. Sun kwashi mintuna masu dan tsaho a haka kafin ya mike, gabanta yaje ya tsaya, ta rumtse idanu da karfi a tunaninta saukar mari ko wani abu dai mara kyau zata ji daga garesa. A mamakinta sai jin tattausan tafin hannunsa tai a saman nata ya zare jakkar hanunta, cikin takun nan nasa daddaya cike da izza ya rabata ya wuce.Numfashin da ta rike a kirji da makoshinta ta saki da karfi, sai kuma ta bude idanunta tabi bayansa da kallo har ya bace ma ganinta. Dan tarin dake neman rike makoshinta ta fara, dole ta nufi dining room ta samu ruwa ta sha. Daga haka takai zaune tana sauke numfashi. Sai da ta dan samu nutsuwa sannan ta tashi tabi bayansa tana addu'a a ranta. Bata da tabbacin a inda yake, dan haka kawai ta nufi inda zuciyarta ke raya mata da fatan ALLAH yasa ba'a nan din yake ba. Sai dai kuma da alama ta taki rashin sa'ar. Dan tana shiga taci karo da shi zaune a kan gado da lap-top kan cinyarsa. Dakin babu haske mai karfi, sai hasken screen din laptop dinne ya haske kyakykyawar fuskarsa ma'abociyar kamewa da kwarjini. Sum-sum ta wuce hanyar bathroom tana dan turo baki. Sai da ta gama tsaftace kanta ta fito cikin bathrobe, yana a yanda ta barsa, hakan sai ya bata damar tsayawa ta bayansa ta shirya cikin kayan barci masu dan kauri da turarruka. A take kamshin dakin ya sake karfi. Fahimtar kamar fushi yake ya sata takowa inda yake cikin sanda, zaune takai gefensa amma ya share abinsa bai ko nuna ya san da zamanta ba. Cikin dan bata fuska da jin haushi sharetan da yay ta zame ta kwanta tare da dan ture lap-top din tasa kadan ta daura kanta a cinyarsa ta kwanta. Da kyar ya iya cigaba da rike kansa yaki kulata. Ganin ya cigaba da aikin dai ya sata kurama fuskarsa idanu, sai kuma ta kai hanunta kan kwantaccen gashin kumatunsa ta fara masa tafiyar tsutsa. (@) Yarinyar nan da tsokale-tsokalan masifa kike * ). Yayi kokarin ganin ya danne ya cije amma aikin na neman gagararsa, baima san sanda ya cije lips dinsa da rumtse idanunsa da dan karfi ba. " ALLAH kayi hakuri bazan sake ba.ALLAH banyi zaton zan dade ba na samu Mammy batajin dadi ne fa". (Yarinyar nan sai ta kasheni zata huta) ya fada a zuciyarsa dake faman bugawa da sauri-sauri cikin kaikawo. A hankali ya janye hannayensa dake sarrafa lap-top din ya daura na damar kan nata dake cigaba da shafa fuskarsa. Rikesa yay yana kokarin son gain ya janye amma sai tai wani irin juyi ta maida fuskarta saitin cikinsa ta sakalo dayan hanun nata a bayansa ta kankamesa. '"Kasheni kawai ki huta" ya fada cikin subutar harshe jikinsa na saki gaba daya. Iffah da bata fahimci ita mima yake nufin ba ta kyalkyale da siririyar dariya har yana jin dumin numfashinta a kan Fatar cikinsa. Ita a nata shirmen kankamesan da tai ne yaji zafi. "dan na kasheka dawa zan zauna?". Ta fada cikin dariyar tana kara cusa kanta jikinsa. Dole ya ajiye lap- top din ya kai kwance tare da dagota gaba dayanta ta hau saman jikinsa. Fuskarsa take kallo cike da dakewa kamar yanda shima yake kallon tata idanunsa a shanye. "Miyasa baki son a zauna lafiya?". Ya fada a hankali yana sake kankance idanunsa cikin nata. Idanun ta juya tana shagwabe fuska da dan cuna masa lips dinta. "Toni mi nayi? In dai zuwa wajen Jaddah ne ai nace kayi hakuri". Dariya maganar ta bashi amma sai ya gimtse baiyi ba, ya dan tabe baki da tsatstsareta kaifafan idanunsa. Cikin dan dage gira "Har na kai ki?". "Hu'um, ni a suwa kuma, kana kallon kanka a mirror kuwa da kyau?. Badan kar ace nayi karya ba sai nace kafi kowa kyau a kasar ruman". Harga ALLAH ta bashi matukar dariya yanda ta fadi maganar cike da yarinta, yayinda zuciyar sa tai wani irin shiga farin ciki, domin kuwa bawai yafi kowa kyau din bane kamar yanda ta fada a zahirance, ya fahimci ta fara caukar karatunsa son sa ya fara shiga zuciyarta. Domin abinda kake so ne kawai kake ma kallon kasancewarsa a sama dana kowa. Shi kansa duk da yasan akwai kyawawan da suka fita ganinta yake samada kowa saboda kawai ita kadai yake so,kyawuntane kawai ke kayatar da shi. Bai fahimci murmushi yake ba sai da yaga yanda ta kura masa ido. Ya dan waro idanun waje alamar miye kuma, ita kuma sai ta girgiza masa kai tana murmushi da dan kauda idonta dake cikin nashi."Murmushi na maka kyau, gashi kuma baka son yi". Hannayensa duk biyu ya doro a saman bayanta ya sake matso da ita ta kwanto jikinsa sosai, fuskarsu ta koma gab-gab har hancinsu na gogar na juna. "A komai k ta dabbance my sohaa". "Kaima haka ai". Ta fada tana dan sumbatar lips dinsa, sai tai saurin jan jikinta zata sauka dan sai da tai babban kokari wajen masa kiss din, amma kunya take ji. A hankali ya rikota bayan ya fisgo numfashinsa da ya nema kufcewa da kyar.Mirginasu yay suka koma saman hannayensu suna fuskantar juna, batare da jiran wani abu ba ya manne lips dinsu waje guda.. 🥱🏃‍♀️Anfi karfin alkalamina anan. Babu alamar wasa tattare da shi, da ga tsayen da yake a kofa yana dubanta a yatsine ya ce,"Kifadi abinda zaki fada ina jinki, dan bazan wuce minti ashirin ba anan". Rai bace Ameera Haifah ke duba Miran Arshaan mai maganar, tai karamar kwafa da tabe baki," Arshaan kenan, idan kana ganin Kanada mafitar da zata iya kwabemin ne ma,dan har da kai sai dai ka shirya mu duka zata kwabe Dar harda kai, idan har ban tsira ba da ga yarda ka maida Jasim kaima zan bude maka aiki ne. Zan kuma tabbatar maka na fika iya makirci dan mace sunana idan ka manta". "hhhhahh! Ni kike tunanin zaki iya budema aiki Haifah? to ina baki shawarar fita a hanyata da ga yau, in ba hakaba why zan kasheki na binne gawarki a cikin masarautar nan kuma na kashe banza". "Oh really? To Dan ALLAH ko zaka gwada ne? Nace ko zaka gwada kashenin muga!!!". Tai maganar cikin tsananin hargowa tana wani hahhankada kirji a gabansa. Wani irin tafarfasa yaji zuciyarsa nayi, dama a wuya yake, a fusace ya kaima wuyanta wani irin shegen shaka na tashin hankali. Cikin kankanin lokaci manyan idanunta suka sake yowa waje ruku-ruku, ga kakarin mutuwa da ta fara da mutsu-mutsun ganin ta fisge hannunsa da ga kan wuyanta. Sai dai kuma hakan ya gagara, dan karfinsu ba daya ba. Tafiya ya dingayi da ita cikin rufewar ido har jikin bango, ya kara matse wuyan da karfi tare da wajigata ya buga kanta jikin bango. Wata irin wahalalliyar kara ta fasa da ta jawo hankalin Jasrah dake daki kwance ta farka tana nemansa, dan su suna'a falon baki ne kasancewar cikin shigar badda kama Ameera Haifah tazo a nufin bako tasa amintaccensa imata iso saboda baya daga mata waya yanzun. Sai da yazo yaga itace. Gaba daya idon Miran Arshaan da alama ya rufe, dan tuni ya sake jijigata ya buga a bango, jini ko ya samu hanya ya balle. lya karfi da budewar murya Jasrah ta daddage ta kwalla wata irin kara na firgita, dan ganin jini ya wanke fuskar Ameera Haifah ga Mijinta shake da wuyarta sai ta dauka ta mutu.Wani irin wancakalar da Haifah Miran Arshaan yayi yana duban Jasrah data yanke jiki ta fadi. Har rige-rigen shigowa hadiman masu tsaron sashin keyi, ganinfa abinda ke faruwa tuni wani ya firgita ya kyalla a guje ya sanarma jami' an tsaron gidan dan wannan faninsu ne...✍️ DAUDAR GORA Book 2 Chapter: 62 ...…….Tofa dan-dan-dan, da alama dama irin wannan damar Iffah ke jiran samu, dan cikin kankanin lokaci duk da darene masarautar ta dauki dumi, yayinda aka kwashi Ameera Haifah da Jasrah zuwa asibiti, Miran Arshaan kuwa da jikinsa ke tsumar toro gaba daya ya gama gigicewa, dan sai zuwa yanzu ya dawo a hayyacinsa. Tuni kuwa ya tsure da ganin abinda ya aikata, sai kawai ya bige da borin kunya. Sudai jami'an babu wanda yace da shi komai,sun tattara komai akan sai zuwa da safe za'a kai maganar ga Shahan-shan. Abu dai mafi daure kai shine miye tsakaninsa da Ameera Haifah din har haka a irin wannan tsohon daren, dan a kala fa karfe biyu na dare kenan. 大大 A lokacin da duk ake waccan dambarwar anan ta-kurya ce ke ganawa da manomin ganyayyakin shayin Shahan-shan. A cikin badda kamarta take, dan haka shi bai san wacece ba.Hasalima magana da Jazaa sukeyinta ita dai tana hakimce komai batace ba. Da farko yaso ya, amma ganin wata lukutiyar jakkal da zinare ga barazanar halaka zuri'arsa kunne tuni ya mika wuya akan an gama. Malikat Bushirat tai murmushin basawa ta dauke kanta.Kwalayen ganyen shayin da uwa ta kawo kan ya fara kaiwa sashen Shahan-shan din kafin wanda zasu noma ya tsiro nan ma Jazaa duk ta ajiye masa su har uku.. Hummm🥱🚴 ** Zaune take bayan idar da sallar asuba, yanda ta kurama waje daya ido zai baka tabbacin tunani take. Sai lokaci zuwa lokaci da takan saki murmushi, harda cusa kanta cikin kafafunta kamar mai jin kunyar wani da ke gabanta. Ta dan jima a hakan kafin ta mike kamar wadda aka tsikara idonta kan agogon dakin. Tasan yanzu kam yana Gym ne tunda har ya kai yanzu bai shigo ba. Itama tsaf ta shirya cikin kayan motsa jiki ta, sun mata matukar kyau da fidda ainahin surarta komai dam. Dan wani bana ta saka a kanta siriri kalar kayan sannan ta daura talda daura after dress saman sport wears din. Shiru tai tana bin Gym din data shigo da kallo, babu kowa komai ma a kashe yake, da alama banan yazo ba. Fuska ta dan bata da tura baki gaba, har zata koma sai kuma ta tuno randa ta samesa a can sama yana wasan takobi shi da Miran Arshaan. "Yes!" ta fada tana wani kashe ido daya da yin juyi sannan ta nufi can cikin takunta na nutsuwa Shelanta sunanta da na'urar kofar tayi kamar yanda ta saba duk wanda zai gitta ta cikinta ya sashi dakatawa da jujjuya takobin ya juyo a hankali. Tuni hadiman wajen sun jujjuya bayansu sukam. Yanda take takowa garesa kamar wata tarwada yasa shi gagara cigaba da abinda yake yi. "Good morning Ta fada cikin rashin tsoron nan nata na bayyane tana daura yatsanta saman tsintsiyar hannunsa ta zano a hankali ta dire kan kyakykyawar takobin da ya rike rikon kasaita da kwarewa. Da kallo kawai ya bita batare da ya amsata ba. Itama sai bata nuna tasan yana kallonta ba ta zare takobin a cikin hannun nasa fuskarta da murmushi. kin sakar mata yay, sai ma cike da salo yay wani irin juyata bata ankara ba ta dawo saman jikinsa takobin a wuyanta sai dai bai daura a kan fatar jikinta ba. Iffah jitai zatayi fitsari na neman kufce mata tsabar yanda ta tsorata har yana jin yanda jikinta ke tsuma. Dan dukowa yay kansa a kafadarta bakinsa saitin Kunnenta ya furta, "k takamarki tsokala ko?". Idanunta da ke kawo kwalla ta shiga kikkifatawa da girgiza masa kai a hankali. Cikin rawar harshe ta ce, "Eshaan Akhi na tuba". "Daga baya kenan". Ya fada yana kara matsar da takobin jikinta gaf.Sake tsurewa tai. Shiko sai faman danne dariya yake. "Ki fanshi kanki". Da sauri ta ce, "Da mi?". Dan lumshe idanunsa yay ya bude yana mai busa mata numfashinsa a wuyan. A dan salon tabe baki ya ce, "Komai ma". "Shike nan, shike nan naji na amince, amma dan ALLAH ka janye sau daya fa ake mutuwa, rai daya ne". Yanzu kam kasa daurewa yay sai da murmushi ya subuce masa. Ya janye tare da dauke hanunsa dake saman cikinta ya juyota suna fuskantar juna. Hawaye fa da gaske sun cika mata idanu. Da kyar ya iya gimtse dariyarsa. Idanunsa ya maida ga hadiman wajen da suka juya bayansu tun dazun, dasss daga yatsunsa sau biyu, cikin abinda bai sakkani ba sun bar wajen a ka barsu su biyu. Da baya-baya yaja zuwa table din gefensu kadan,wata takobin ya dakko a cikin kyakykyawan kufanta ya dawo gabanta, hanunta ya riko ya daura mata takobin sannan ya zare abayar ta ya ajiye tare da mata alamar bismillah. Kamar ba ita ta gama hadiyar hawayeba yanzu ta wani dubi takobin shima ta dubesa ta dan murguda baki. Kansa ya maida gefe yana murmushi, tare da ajiye tsinin tasa takobin bisa kasa ya fara zagayata. Yana a tsaye daga bayanta ya juya takobin cikin salon tsokanarta kawai a bazata yaji tama kanta garkuwa. Idanu ya dan waro waje, da bin takobin da kallo kawai ta zuke ta maida masa harin. Cikin zafin nama ya kare kansa shima mamakinta na nan kasheshi. "Dama kin iya wasan takobi?". Ya tambaya da mamaki idanunsa cikin nata Murmushi ta sakar masa da kara zukewa ta kai masa suka ta kasa. Nanma baya yay cikin zafin nama yay wata irin bahaguwar zukewa. Dariya tayi da dire takobinta ta fara zagayashi kamar yanda ya mata dazun, cikin salon dage gira da kashe masa ido daya ta ce, "Zaka cigaba da tsayawa tambayar a ina na iya ne na kaika kasa?". Tsaiwarsa ya gyara da kyau yana murmushi da kamo lips dinsa na kasa ya tura ( paki suka cigaba da zagaye juna. Sai kowa ya yinkuro cikin ragabza akai tsaiwar zakaru. Cikin kwarewa da nuna bajinta ga kowa suka cigaba da wasan mamaki na nan kashe Tajwar Eshaan a zuciya. Duk da ya fita kwarewa yanda ta iya din itama na bashi mamaki matuka.Sai dai ya bita da salon saffa-saffa yanda bazai cutar da ita ba dan karfinsu ba daya bane Tamkar wanda aka jeho kawai sukaji sallamarsa a kusan tsakkiyar wajen, dan kamar sai da ya matso gab da su ne ma yake sallamar.Da ga shi har Iffahn juyowa sukai, musamman Iffah da kamar wadda ta ma firgita, dan jikinta har rawa yake wajen neman abinda zata yafama jikinta, tsabar yanda ta rikice tama ki ganin after dress din nata. Bata san yanda akai ba, tayaya ma kawai jinta tai a jikinsa, jin kamshinsa ya sata kankamesa da sauri tana kokarin boye kanta. "Miya kawoka nan babu neman izini? Kabar wajen nan Aam!!" ya fada a matukar tsawace shima yana kankameta da juyawa da ita suka bama Miran Arshaan da yay mutuwar tsaye baya. "I say out!!!". Ya sake fada da wata irin mummunar tsawa mai karaji da har jikinsa na girgizawa, ga idanunsa sun yi wani irin kadawar masifa kamar wanda ake kadama gangi. Miran Arshaan har tuntube yake yi tsabar firgicewa da tsawar Tajwar Eshaan din. Bai taba sanin yaron nan dan bala'i bane irin yau. Next surar yarinyar nan ta matukar kidimashi, ashe abinda Jasim kenan ya gani kullum yake cikin sambatu da santin yarinyar, shi manemin matane tun yana da kananun shekaru, yayi mu'amula da mata kabila daban-daban a duniya da bai san adadi ba. A sanda yake ji da rashin ji har order din mata suke ta online, yaga matan ma da sukafi Iffah kira amma wannan jikin dabanne. Ji yake yama kasa cigaba da tafiyar yanda jikinsa ke bari, sai kawai ya samu bango ya manne yana sauke numfashi gudu-gudu. (Humm) Yanda Iffah taji zuciyarsa na bugawa da sauri- sauri kamar zata ballo kirjinsa ta fito ga tsawar da yayma uncle din nasa ya matukar sake rudar da ita fiye da tsoron ganinta a yanda take da tai gudu. Kanta ta shiga jujjuya masa da kankame hanunsa, sai kuma ta dan dago ta kalli fuskarsa. Ta wani irin kadawar masifa jazur hakama idanunsa gaba daya sun juye mata cikin canjawar kammani. Dole ta maida idanunta kasa jikinta na rawar toro da yanayin nasa. Jitai kawai ya wani irin fisgar hanunta zuwa hanyar kofar da ta shigo, bai tsaya da ita ko ina na bedroom. Yarfar da hannun yay yayi shigewarsa bathroom. Da kallo ta bisa hankalinta a tashe itama, dan ita kadai tasan kalar wutar masifar data gani a cikin idanunsan. Raya mata zuciyarta ta dingayi kawai tabar dakin nan karma ya fito ya sameta... Koda ya fito bayan tsahon lokaci da ya dauka a bayin bai nema Iffah ba dan yana bukatar kadaici saboda ya shiga bacin rai, shi mai kishi ne, tabbas yanada matukar kishin da yake ji akan yarinyar nan zai iya badda mutum. Wata irin tsanar Miran Jasim da Miran Arshaan yake ji irin wadda bai taba ji a kansu ba a dukkan abubuwan da suka aikata masa a baya, ga wani irin sara masa da kansa yake yi na ciwo. Jikin window ya karasa hannunsa goye a bayansa batare da ya cire ko bathrobe din jikinsa ba yana kallon sararin samaniya da ke hada was irin manyan bakaken giza-gizai na hadari, du da safiyar tayi sosai garin yaki washewa sai ma rinewa yake sake yi kamar za'ai wata sabuwar magriba. Kiran waya ne ya shigo, ya share kamar bai jiba, aka sake kira nan ma kamar zai share sai kuma ya nufi wayar a fusace ya daga. Sai dai yay shiru baice komai ba. Da ga can Sayeed Fayzul-haq ya gaishesa cike da girmamawa.Haushin kowa yake ji, duk da bashi yay lefin ba ya samu rabonsa. Dan maimakon amsa gaisuwa a dake ya ce, "Ya akai". Dan rikicewa Sayeed Fayzul-haq yayi, amma sai cikin dauriya da sake kankan da kai ya shiga masa bayanin abinda ke faruwa tsakanin Miran Arshaan da Ameera Haifah tun a daren jiya. A zafafe ya ce, "Kaima jami'ai magana su kamashi a hadashi da dayan sakaran, a saka na'urar daukar magana cikin akin kurkukun kuma.Itama Haifah din Doctors su sallameta idan babu wata matsalar data shafi lafiayarta jami'an tsaro su rufeta",. Daga haka ya ajiye kan wayar yana huci. Duk yanda yake kokarin rike kansa da bin komai a sannu ya fahimci ba haka makiyansa suke bukata. Fushinsa suke son gani, ainahinsa suke bukatar ya nuna musu. Ya barsu da yarinyar nan ne kawai domin shi din shugaba ne, shugaba kuma da hadiyewa aka sansa, amma tunda so suke shi ya fito musu a Eshaan In Haysam Abdul-majeed Aliy Qutb din sa to yanzu ne wasan zai fara.. 😆🥱TOFA ran yan maza ya baci, al'ummar kasar ruman kuyi takanku mai RUMAN dinne da kanshi 🚴🚴🚴🚴🚴🚴🚴🚴🚴🚴 DAUDAR GORA Book2 Chapter: 63 A bangaren Iffah kam itama dai wanka tai ta gyara jikinta, yunwa ta hanata cigaba da zaman dakin ta fito neman abinci. A irin wannan lokacin. Babu kowa a falon sai daddadan kamshi da sanyin ac mai ratsa bargon jiki, mamaki ya kamata, duk da dan sanyi-sany in garin na hadarin dake tasowa dan fitina sai an kunna na'urar sanyaya waje, baki ta tabe abinta ta nufi dining room din da glass ne kawai ya gitta tsakaninsa da falon dan komai a tsare yake. Shayi tai kokarin fara sha dan shi take bukata, wani irin masifar sarawa kanta yay lokacin da hanunta ke sauka kan abinda aka zuba shayin. Janye hannun tayi da sauri ta kurama flaks din shayin ido, sake kai hannu tai a karo na biyu, nan ma kanta ya kara sarawa al'amarin kamar wata almara. Sake janyewar dai tayi tana kaiwa zaune jagwab idonta akan flaks din dai. Ta kwashe mintuna uku tana kallon sa sannan ta sake daurawa a karo na uku, yanzu kam duk da abinda takeji a jikinta na azaba bata cireba tsahon wasu mintuna. Idanunta sunyi jazur cikin kankanin lokaci, gaba daya kamanninta sun canja kamar ba Iffah'r ba. A wani irin fusace ta mike dauke da tray din da flaks din ke kai zuwa kitchen. Taku take cikin nutsuwarta da kasaita ki tarwada ko budurwar hawainiya. Kwarjininta da cikar kamalarta kan shafe karancin shekarunta musamman dan tana a cikin irin wannan yanayin. Kasancewarta a kitchen ba karamin rudani bane ga ma'aikatan cikinsa. Hannu kawai take daga musu da ga gaisuwar da suke mikowa gwiyawunsu kan kasa. Kwalayen gayen shayi uku da daya daga cikinsu ke kokarin fitarwa ta zubama idanunta da sukai jazur. "Wannan fa?". Cikin sauri suka bata amsa da "Ganyen shayin shugabane". "Daga ina ya fito?". "Wanda ke kawowa a koda yaushe". '"Ina bukatar ganinsa daga nan zuwa awa biyu".Daga haka tai gaba tana kokarin hada sabon shayi da kanta. Sunyi kokarin ganin sun amsheta amma ta hana hakan, cikin kankanin lokaci ta kammala ta fice batare data sake bi takan kowa ba. Dai-dai kuma da fitowar Tajwar Eshaan cikin shiga mai sauki ta zaman gida alamar bazai fita ko'ina ba. Har yanzu fuskar cidin-cidin take babu alamar yasan minene murmushi. A sanyaye Iffah ta karasa cikin dining room din kamar yanda shima can din ya nufa kamar bai ganta ba.Kama kanta tai itama suka kai Zaune a tare tana dan satar kallonsa tai ta Kasan ido ganin ya kai hanunsa kan jug mar dauke da madara. Ta zubama madarar ido itama, wani irin kallo takema jug din na kurilla,sai kuma cikin dauke kai da cije lips muryarta a sanyaye da girmamawa ta ce, "Shi wannan madaran illane ga duk wanda ya sha shi, barinsa a inda aka gansa shi yafi alkairi". Shiru kamar bai jita ba, sai kuma ya waiwayo a hankali ya dubeta, fuska ta shagwabe tare da marairaiceta ta jinjina masa kai. "Dan ALLAH karka sha akwai matsala tare da madaran". (Ya arrahaman wai yarinyar nan mutum ce kuwa?) ya fada a zuciyarsa kaifafan idanunsa a kanta. A hankali ta daura hanunta kan nasa ta zare jug din madarar ta ajiye gefe. Shayin ta hada masa, tare da ajiyewa gabansa tana fadin "Zakaji dadin wanna shayin fiyema da madaran". Nan ma shiru babu alamar zaice wani abu, ya kumaki daukar shayin. Sai ma gani tai ya yunkura zai mike cike da izzar nan tasa ya taka zuwa kofar barin dining room din, Iffah ta bisa da kallo ta gefen ido zuciyarta na wata irin tafasa itama. Sai dai girmansa da kimarsa bazai barta ta nuna ba koda a fuska. Kanta kawai ta dukar, da karfi ta matse idanunta da cije lips dinta shima da karfi. Kadan ya dawo da jikinsa baya alamar dama bai fice daga dining room din ba ya kafeta da kallo.A karon farko ya saki kasaitaccen murmushin da ganinsa a fuskarsa ba karamin yaki bane. Dawo wa yay a hankali ya zauna ya dauka shayin ya fara sha. Sosai kam ya masa dadi, amma babu alamar hakan a fiskarsa. Itako ta dauke kanta gefe tama daina kallonsa. Cak taji anyi sama da ita batare da tasan sanda ya gama shan shayin ba ma.Wutsil-wutsil ta farayi da kafafu tana tura baki, bai kulata ba har sai da ya kaita bedroom ya dire a gado…. 😏 Yau dai bazan dauki rahoton ba. * * Cikin kankanin lokaci zartar da umarnin Tajwar Eshaan na rufe su Arshaan da Ameera Haifah ya zagaye masarautar. Nan fa aka fara yan kananun maganganu kamar yanda al'adar take.Yayinda kowa ke tambayar kansa mi yakai Haifah sashen Miran Arshaan din sanin babu wata alaka tsakaninsu ta zahiri face matar yayansa. Anya kuwa babu wani abu a kasa shr Tajwar Eshaan din ya shinshino dan kasancewar tasu tare kam dole akwai wani al'amari mai girma na boye. Wasu ma dai tuni suka fara fassara al'amarin da cewar akwai dai abinda suke aikatawa. In ba hakaba minene ya kaisu haduwa a irin tsohon daren nan ba mata ba, ba kanwa ba, ba uwa ba ko wata shakikiya, kuma har takaisa da neman kasheta irin haka. Labarin ya fara zama gaskiya lokacin da Jasrah ta farfado. Cikin kuka take sanarma Mammah da take dubata tare da Malikat Bushirat cewar dama ta taba zargin Haifah a wani lokaci da tai kiransa tsakar dare, ranar ta samu damar ganin kiranne dalilin manta wayarsa da yay ya fita wani kiran ujila da batasan wayayi masa ba. Tana dagawa Haifah ta yanke kiran, sai dai ta riga taji muryata, koda ta dauki number ta kira da wayarta ba'a daga ba, washe gari ta bada a mata bincike kan number din aka tabbatar mata bata akan waya. Taci gaba da saka masa ido akan hakan amma ba'a sake kuskuren kiran ba,sai dai a wasu lokuta takanji kamshin wani irin turare na mace wanda shine taji a daren jiya Haifah nayi. Ta rushe da kuka mai cin rai da zuciya. Babu abinda Malikat Bushirat keyi sai cika da batsewa, tana matukar son Jasrah a rayuwarta, sannan ga Haifah da ke matsayin kishiya da ma akwai burbushin wani abu a kasan rai na kishin zama da miji daya da sukai,duk da ita shaida ce mijinsu bai taba son Haifah k harva bata taba zama mai wata power a cikin masarautar ba shi yasa tuni bata a cikin jerin wanda suke a gabanta itama, duk da tayi aiki a kanta kamar su Malikat Ashwaq, dan acewar uwa ba'a sakaci da makiyi komai kankantarsa. Ta tabbata Jasim da Haifah neman juna suke a bakin kowa bisa zancen Jasrah, sai abinda Tajwar Eshaan din yayi yay matukar burge ahalin masarautar har wasu na saka masa albarka da rage jin zafinsa a zukatansu. Oho shi baima san duk anai ba, dan yana can tare da yar shilarsa suna hutawarsu. Shirunsa kuma na nufin bazai fitoba yau gaba daya kenan. **** Kamar yanda Iffah ta bada umarnin gain mai kawo kayan shayin Shahan-shan an isar da sakonta. Bayan sallar la'asar tana tsaka da nazarin littafi aka sanar mata zuwansa ta hanyar wayar landline. Bataso katsewar karatun nata ba, sai dai kuma haduwa da mutumin nada nada matukar amfani dan haka ta tashi ta kimts dazun ta riga ta gama tsara shirinta yanda ya dace, dan sun tattauna da Daneen Ammarah ta kuma bata shawara duk da a farkon bayanin Iffah din jimm tayi na rashin fahimtar manufar hakan. Sai da Iffah tai mata bayani dalla-dalla dai-dai da yanda ta tsara sannan ta gamsu ta Kuma bata goyon baya dari bisa dari. Hurumin duk wani bako a sashen Shahan-shan iyakarsa falon farko ne, wanda har va tsallake zuwa na biyu ya kai babban bako kam na musamman, balle na uku kuma da a tarihi ma bayan masu hidima Malikat Haseenat da Malikat Bushirat ne kawai suka taba iya tsallake wannan hurumin sai ko Daneen Ammarah da tai dalilin Iffah, dan Tajwar Eshaan fa bai zauna a sashen da mahaifinsa ya rayu ba. Shi da kansa mahaifin nasa yasa akai masa wannan ginin tunkan ya dawo kasar ruman. Hakan yasa har yanzu babu wani mahaluki daya san sirrikan tsarin wannan sashe sai mai shi din. A kowane falo Iffah na samun gaisuwar girmamawa, dan ta stairs ta biyo ko'a jikinta duk da wahalar hakan, yayinda amintattun Hadiman Tajwar Eshaan da'a ka'ida basa sakkowa ko falo na biyu sai da dalili ke biye da ita. Dattijon mutum da alamu suka nuna shima din dai wani babbane dan babu wata kazamar shiga tattare da shi vav saurin mikewa domin girmamawa ga zawjata-almilk din. Iffah takai zaune tana satar kallonsa ta gefen ido batare da kowa zal iya lura da hakan ba. Rissinawa yay domin gaisheta ta daga masa hannu kawai da masa nun da wajen zama. "Godiya nake ranki ya dade". Ya fada cikin kankan da kai yana kaiwa zaunen". Sai da taja kamar minti biyu falon shiru kafin ta nisa. "Na bukaci ganinka nan ne bisa wani dalili da bai gaza biyu ba. Na farko daga yau na dakatar da kawo duk wani ganyen shayi da sunan Maleek a gidan nan. Na biyu akwai aikin da zakamin". Hankali tashe ya dan dubeta sai kuma ya rissinar da kansa. "Ranki ya dade ki gafarceni, wani abu ya faru ne?". "Komai bai faru ba. An samu sauyin sabon tsarine kawai. Shin kozan iya sanin sunayen abubuwa da ake hada kayan shayin Maleek?" "Sosai kuwa ranki ya dade, mi kike bukatar sani?" "Komai" Ta bashi amsa a takaice. Da sauri ya bude jakkar gefensa ya zaro wani littafi. Da sauri daya daga cikin hadiman ta amso ta kawo mata bayan ta kai har kasa. A dake Iffah ta amsa babu alamar wani dar tattare da ita ta fara duba littafin Kavance dan babba. Duk da yasan babu wani abu na cutarwa a ciki tunda a sirrance kuma aka bashi ganyen shayin da ya aiko jiya da dare a tsorace yake, dan harga ALLAH gizagon wannan baiwa da kwarjininta ya cika masa ido matuka har yana jinsa a takure cikin falon ma. Da din dadawa kuma wannan shine karo na farko da akai masa irin wanna kiran ma sabanin da da sai ya hada wani samfur na sabon ganyen shayi yakan zo ya gabatar kozai birge Shahan-shan. Kusan mintuna biyar Iffah nabin littafin daki- daki har kusan tsakkiyar, dan gajerun bayanai ne akan yanda ake hada ganyayyakin da sunayensu. Rufewa tai tare da dan dagowa ta dubesa. "Uhm komai dake anan kam bashi da wani aibu, sai dai sabaninsa daga yanzu muna bukatar fresh ganyayyakin ne. Kuma za'a dinga noma su ne a cikin masarautar nan". "Yanda kike so haka za'ayi ranki ya dade". Ya fada cikin tashin hankali a bayyane. Iffah da tai kamar bata fahimcesa ba ta mike, "Ka hada duk abinda ya dace a turamin, idan na kammala da nawa shirin zan nemeka". "Godiya nake ya Zawjata-almilk. ALLAH ya kara miki lafiya da tsohon rai mai amfani". Hannu kawai ta daga mai tai wucewarta,hadiman da al'ajabi ya sandarar a tsaye suka take mata baya da sauri….✍️ (Wato wannan yarinyar ko? Humm 🥱😂 DAUDAR GORA Book 2 Chapter: 64 Tunda aka shigo da Arshaan dakin kurkukun da ke makwaftaka da juna da na Miran Jasim sukema juna kallon kallo, duk da dai shi Jasim bai ko motsa da ga zaman takurewa waje dayan da yay ba, su dukansu dakin babu yawaitar haske, sai dai ta dan hasken da ke lekowa sukan iya gain junansu. Sun kwashe awa guda a haka kafin Jasim ya mike cikin dan tangadi, dan baya cin abincin da ake bashi ga raunikan da ya jima kansa duk an masa tretiment dinsu. Jikin karfen da ya raba dakin nasu ya tsaya, sai kuma ya kece da wata irin dariya kamar wanda hauka ya kama. Cikin bacin rai da kunar zuciya Arshaan ke kallonsa, sai dai baice komai ba har yayi ya gama yay shiru dan kansa. "Oh!! Kai dama a tunaninka Jasim ne kawai ta karewa Arshaan? Lallai kai jaki ne bazan gaji da maimaita fada ba, why da ace uwarka na raye zuwa yanzu nayi imanin bakin cikin haihuwar wawa da tai irinka ne zai zama ajalinta. Kai anya ma kuwa bada cikinka ta shigo gidan nan namu b "Jasimmmmm!!!!!!!". Arshaan ya fada cikin karaji da wani irin girgiza karfen tsakanin nasu kamar zai babbagesa,amma da yake a gine yake cikin kasa ko gezau shegen baiyi ba. Ka dan Jasim yay baya yana dage hannaye sama kamar wanda yay surrunder, sai kuma ya sake kwashewa da dariya kamar zai fadi ya sake dafe karfen yana fadin, "Shegen kaya ashe kasan abinda kake. To to naji uwarka anan ta haifeka, sai dai wlhy bazan daina tantama ba nikan kodan kasancewarka kasurgumin annamimi, butulu,sannan rago mai labewa a bayan mace domin kubutar da kai. Shin nawa ta siyeka ne har haka?" "Yanda aka sayo uwarka a gidan karuwai. Why da ga yau idan ka sake kuskuren zagin uwata, sai na maka lahanin da sai ruhin uwarka ya dawo duniya yana mai cikin garari Jasim.Wawa jaki kawai maybe ma uwar takace ta shigo mana da cikinka da ga wajen dan tsautsayi kawai. Ko an fada maka bamusan tarihin tushenta bane a gidan. "Amma kasan zan iva kasheka na binne gawarka a cikin kurkukun nan ko? Idan ka manta bari na tuna maka wanene Jasim in Abdul- majeed Aliy Qutb, domin ni a gareka sai dai kallo sai kuma hange daga nesa koda bakin cikina zai ajalinka. Ko an fada maka ban san kulle-kullen da ka jima kanayi a kaina bane?, Kana goyamun baya domin in mun kauda shi nima ka kaudani, sai dai kuma kayi kuskure, domin kafin kaga biri shi birin ya ganka dan hau. Da ido daya Jasim ke barci,sannan a tafin hannuna kake, zakuma ka tabbatar da hakan nan gaba jadan". Ya kare maganar yana wata yar iskar dariya cikin rangaji harya koma wajen zamansa ya sake zama rigija yana dariyar har lokacin. Shiru Miran Arshaan baice komai ba, sai dai yana tsaye kamar gunkin da aka ajiye dan tarihi idanunsa nabin Jasim din da kallo, da alama dai tattaro abin fada yake, ko kuma maganar Jasim din ce dai ke masa kaikawo dan bai taba tunanin yasan da wannan burin tattare da shi ba. ** BAYAN KWANAKI BIYAR ** Kwanaki biyar kenan da mika su Arshaan suma a makargama, Jasim kuwa sati guda. Sai dai kuma Tajwar Eshaan bai sake cewa komai ba game da su, hasalima a yau da ake saran ganin watan azumin ramadana ya dauka hutun fitowa fada har sai bayan salla. Tare da daura Sayeed Fayzul-haq akan komai dan zaije Umrah shi da iyalinsa kamar yanda ya sanar.Tabbas a wannan karon babu wasa a cikin al'amarin Tajwar Eshaan din, dan haka kowa ya shiga taitayinsa har su manyan masarautar. Duk da akwai abubuwan fada a bakinsu har game da karasa zaman shari'ar da aka fara amma sun gagara cewa komai har ya gama jawabin fara azumi da gamashi lafiya yay musu bankwana. A lokacin da Tajwar Eshaan ke can yana bankwana da jama'ar fada anan Iffah ce cikin babban bitalmanin kasar ruman bisa jagorancin babban dan Sayeed Khairul-Bashar mai suna Abdul-Shakhur in Khairul-Bashar tana bada umarnin ware kayan masarufi nau'i-nau'i domin dorasa a jagorancin rabawa talakawan kasa. Sai matasan masarautar da ta saka shi Abdul- Shakhur din ya samo har su hamsin da zasu jagoranci sauran jihohi da wanda za'a kai wasu kasashen da yaki ya samarwa yan gudun hijira da ma iftila' in rayuwa na talauci. Wannan al'amari ya matukar jjiga kunnen duk wanda ya samu labari a cikin masarautar, dan abinda bai taba faruwa bane, duk da duk azumi akan fitar da kayan masarufi a dan kai jihohi suma kuma ana da kasune ga Tajwar na jihohi bawai a wakilta wasu suyi aikin ba a cikin masarautar. Sannan a duk shekara tun ba hawan Tajwar Eshaan din Malikat Bushirat ce ke da wanna karfin ikon matsayinta na mahaifiya ga Shahan-shan. Sai kuma a yau labarin ya canja akaga Zawjata-almilk kan komai cikin kuma sauyi. Kamar yanda labarin ya isa kunnen kowa kuwa yaje ga Malikat Bushirat din da take zaman tsara yanda zatai fitar da wanna abinci bisa tsarawar uwa kamar kowace shekara. Ba kuma a bada abincin ma sai bakwai da azumi, sai kuma gashi yau ana gobe saka ran daukar azumi za'a fara rabon. Kayan da aka fitar kuma sun ninka wanda ita take sakawa a fitar sau dari. Dan duk wani abinci dake shekara ta uku a cikin bital mali Iffah tasa an fito da shi ana da kasa a hannun wakilan. Su kuma kasancewar matasa masu zafin nama da son dama su nuna tasu baiwar amma basu da wanna damar sun bata goyon baya dari bisa dari, duk da kasancewarta karama a shekaru kuma sun bata girmanta matsayin Zawjata-almilk, to kwarjini da cikar kamalar ta da barazana ma bazai bari ko kaso kawo mata wargi ka iya aikata hakan ba. Tsaf numfashin Malikat Bushirat ya dauke na wucin gadi lokacin da Jazaa tazo mata da mummunan labari. Ta wani zuba idanunta kamar mai son gano gaskiyar maganar a jikinta. Kafin ta yunkura ta mike cikin wani irin zafin rai ta shiga bedroom din ta. Cikin kankanin lokaci ta canja shiri, tana kokarin fitowa Jasrah ta shigo dakin da sallama, dan tunda aka sallamota da ga asibiti nan sashen ta dawo take zaune, a kallo daya datai mata ta fahimci bacin rai dake tattare da ita. Itama yanzu take jin labarin komai a bakin hadiman sashin, dan haka ta biyota daki sanin yanzu yayar tata zata birkice. Ita mamaki take da yanda gaba daya yanzu wasu halayenta ke neman canjawa. Tunda ta dawo sashen kokarin ganin ta fahimtar da ita wacece Iffah take amma taki fahimtarta, gashi kuma yanzu Iffahn ta sake dangwalo wani al'amarin. "Akia Please kiyi hakuri, zuwanki wajen yarinyar nan a yanzu bashine mafita ba, sai dai maya zubar miki da mutuncinki. Ni a ganina nemanta ya kamata kiyi bayan tabar wajen sai muji dalilinta na zartar da hukuncin da kece ke zartar da shi, ko kuma ki tuntubi Abni kiji tunda dai bazatai komai bada saninsa ba". "Bani hanya Jasrah". Ta fada a zafafe kamar ma bataji mi Jasrahn ta fada ba. Cikin dakewa itama Jasrah tace,"Bazan barki ki fitaba gaskiya Akia, kiyi tunani abinda kike son aikatawa. Akia na miya canjaki haka? Bayan kuma a baya ba hakan kike ba. Karfa ki manta shekaru kusan hudu muna kuka akan matsalar dake zagaye da mu ta mutuwar matan Abni, amma a yanzu UBANGIJI ya kawo mana iyakar komai, a kanta komai ya canja har mutane suka fahimci makarkashiya ake masa sabanin da da shi kai tsaye kowa ke zargi. Kamata yay mu rungumi yarinyar nan muyi farin ciki da kasancewarta mata ga danmu bawai bore ga duk yunkurinta ba. Matsalarmu da ita dama can akan abinda muke zargin ta aikata ne, amma yanzu mun fahimci ba haka bane ba, to mizaisa bazamu manta komai ba mu maidata komai dinmu kodan farin cikin da yaronmu ke samu da ga gareta. Tassss! Kake jin saukar lafiyayyen mari a fuskar Jasrah, idanu kawai ta rumtse tana mai kauda kanta, yayinda Malikat Bushirat ke wani irin huci. Abune da bai taba faruwaba, dan ko sanda Jasrah a karama bata taba dukanta ba, shagwabata tai kamar yar data haifa ba kanwa ba, ta kyautata rayuwarta tai mata raino kamar Kwai a cikin cokali. Idanunta da sukai jazur ta bude, ta dan girgiza kai tana murmushi mai ciwo. "Zan iya amsar duk hukuncin da zakimun Akia dan ke uwa ce a gareni ba yar uwa kawai ba. Amma why bazan taba barinki ki zubar da mutuncinki ba". Tana gama fada ta zare key din kofar ta fice da sauri ta maida kofar ta kulle gaba daya. Duk kiran sunanta da Malikat Bushirat keyi cikin karaji batako kulata ba tai shigewarta dakin dake matsayin nata a yanzun tana hawaye. Ita kam ta fara shiga rudani akan canjin halayen yar uwar tata, ta sara mike damunta a yanzu. Anya ba masu son cutar da Eshaan bane suka dawo kanta suka saka kiyayya a tsakaninta da yarinyar nan. Ita kam yanzu ta fahimci Iffah, tanajin kaunar yarinyar a ranta kamar tun a da can farko, matsalar data biyo baya ma a dalilin abinda suke tunanin ita ta aikatane. Amma yanzu kunyar haduwarsuma take ji. Dan bata san da bakin da zata fara rokonta gafara ba. Amma koba komai ALLAH ya sakama yarinyar tun ba'aje ko'ina ba, tunda gashi wanda ta yarda da shi fiye da kowa da komai yau shine kecin amanarta da matar dan uwansa, wannan wace irin mummunar kaddara ce. Hawaye masu zafi suka silalo mata, dan abune dake mata matukar kuna da zafi a zuciya tunda ya faru, ga kunyar fitama da takeyi dan ko hadimai shune suke mata akaikaice matsayin matar mai neman tsohuwar matar Shahan-shan……..✍️ 14:23 DAUDAR GORA Book2 Chapter: 65 A gajiye tibis ta shigo sashen, yana zaune a falo harde kamshinsa ya karade falon. Da sauri amintaccensa da ke gefen kafafunsa zaune da ga kasa yana ware masa wasu takardu da suka barbaza ya sake kasa da kansa yana gaisheta.Da hannu ta amsa masa idonta akan zakinta da ke mata kallon kasan ido ta yanda ita kawai ke fahimtar hakan. A hankali ya motsa lips dinsa ya Bama amintaccensa umarnin tafiya. Zaram kuwa ya mike dan dama abinda yake jira kenan. Saboda a yanzu kam shigowarsa wannan falon sai da notis saboda yanda iyayen gidan nasa ke manne da juna akoda yaushe suna baje kolinsu yanda suka gadama. Shifa har mamaki yake da jin anya kuwa ba'a samu canji da ga Shahan- shan din nasu ba zuwa waninsa. Shifa yasan abinda yake gani kawai. A hankali ya bude mata hannayensa alamar tazo garesa idanunsa kyam akan kyakykyawar fuskar ta dake a shagwabe kamar zata saki kuka. Kafada tadan noke tana tura baki, sai kuma ta fara takawa a hankali zata wucesa, a hankali ya riko hanunta da dan murmushin iya lips din nan nasa. Gaba dayanta ya jawo ta fado jikinsa. Wani irin sakin ajiyar zuciya sukai a tare.Tare da rungume junansu tsam-tsam kamar masu tsoron a rabasu. K ta dabance". Ya fada a hankali cikin kunnenta yana sake kankamta. "Kai ne na daban a cikin daban ai Zakina". Ta fad itama tana sakar masa manya-manyan sumba a kan kirji. Sai kuma ta dago kanta suka zubama juna ido cike da kewar juna kamar ba da safe suka rabu ba. Cikin motsa lips dinsa da kyar ya ce" "Kin gaji ko?". Kanta ta jinjina masa tana marairaice fuska, sai kuma takai hanunta kan kyakykywar fuskarsa tana shafa kwantaccen gashin wajen dan tana matukar son sa. "Amma tunda aikin lada ne banajin gajiyar". Dan sumbatar lips dinta yay a fisge ya ce, "Da gaske?" "Yap". Ta fada cikin fari da kashe masa ido daya.Murmushi ya dan saki da lakace mata hanci, sai kuma ya maida bakin nasa kan nata ya shiga bata kyakykyawar sumba, ba' a barta a baya ba ta shiga taimaka masa cike da nuna kwarewar haddace dukkan karatunsa. Kafin akai wani dogon labari gaba daya yanayinsa ya canja. Dan shifa Tajwar Eshaan bai san wani yaren dandani haukaci ba. In har aka fara sai an kai karshe.Sannanake iya samun kansa dari bisa dari kuma dalibar tasa da alama dai irinsa ce, dan zuwa yanzu duk da ta kasa zama mai juriyar mika wuya yanda yake so saboda rashin sabo tana kokarta kamantawa musamman a bashi hadin kai a duk sanda yace kule takance cas. Da ga baya kuma ta dawo tana masa raki da shagwaba, Shiko yay ta mata murmushin miskilancin nan na.. Bayan sun samu daidaito ta lallabasa yay mata kiran su Babiy, sun jima suna hirarsu dan a yanzu kullum ne sai ta saka ya kira mata su, sai dai kuma duk sanda za'ai wayar yana dakin, bai kuma taba yarda shi sun gansa ba ko tayi wata magana a kansa, tayi-tayi ya barta suna gaisawarsu ita bazatace komai a kansa ba yaki bata damar hakan, ya dai yarda ya kira mata su su gaisa suma jima suna hira yana da ga gefenta yana saurare da jin komai. Bayan sallar magriba ta samu sakon kiran Malikat Bushirat da ga wajensa. Dama dai suna da shirin zuwa mata sallama, dan insha ALLAHU ana kai azumin farko a gobe zuwa dare jirginsu zai daga zuwa Saudiyya. Sanin abinda ta kullama ranta tace ya barta to ta fara vin gaba yazo da ga baya tunda zaije ya ma Malikat Haseenat ma sallamar, ita kuma da safe Insha ALLAHU sai tayoma su Malikat Haseenat din sallama. Bai wani kawo komai a ransa ba yace taje, dama yana bukatar yin magana mai muhimmanci da Mammah din kuma akantane baya kuma bukatar taji. Tunda ta fito a mota hadimai ke fama zubewa gaisheta. Kafin ma ta karasa ciki an kaima Malikat Bushirat labarin zuwan nata. A zahirance dai batace komai ba har Iffahn ma ta karaso. Gaba daya hadiman dake zagaye da ita ma wani irin zubewa sukai bisa gwiwunsu lokaci guda, dan wani irin kwarjini Iffah'r ta musu naban mamaki, sannan koba komai ita din dai Zawjata-almilk ce. Hannu kawai ta dan daga musu dai-dai tana kaiwa cikin kujera da wani irin salon zaman kasaita na kafa daya kan daya. A hadiman babu wanda bai girgiza da salon Iffah'r ba, dan kowa yasan duk da take matsayin Zawjata-almilk a gaban Malikat Bushirat dole ta risina kuma kasa ne wajen zamanta. Sunta satar kallon Malikat Rushirat din da tunanin ko zatace abu, amma sai sukaji shiru, hasalimal sau daya bata motsa da ga zamanta ba balle a karanci wani abu da ga gareta. Wani irin kallo Iffah ta watsa musu da masu alamar fita da yatsunta. Har ko rige-rigen fitar suke duk da sun so ganin yaya wasan zai kare. Falon ya dauki shiru na tsawon lokaci batare da wani cikinsu ya motsa ba, hasalima ita Iffah ta maida hankalintane ga wayar Tajwar Eshaan da ke a hannunta tsabar rainin hankali ma browsing abu takeyi hankalinta kwance kamar ta manta gaban wanda take. Malikat Bushirat ta dago idanunta da sukai wani irin kadawar bacin rai ta zuba mata, tsahon sakanni kafin ta nisa da kyar cike da zafin rai. "K har kina ganin kin kai wani matsayin da zaki iya jayayya da ni kenan?". Duk da sarai Iffah ta jita sai batako motsa ba tsahon wasu sakanni. Kafin ta motsa lips dinta batare da ta daina abinda take a wayar ba ta ce,"naga ai bakya bukatar amsa tunda har kin fahimci hakan Mother in-law. Kuma duk abinda kikaga Iffah tace zatayi sai ta yishi ki rubuta ki aje, dan hakan halitata ce bana manta gabar daukar fansa musamman akan jini na". "Humm ki taka a hankali, na fiki hatsabibancin yariya. Ki kama kanki kodan cigaba da rayuwar ahalinki a doron kasa". 14:24 cigaba da rayuwar ahalinki a doron kasa". *murmushi mai sanyi Iffah ta saki tare da dagowa ta dubeta ido cikin ido. "Barazana ne hakan in-law? To in barazana ce ki sanarma bokanyar taki bata iya aiki ba tunda har bata sanar miki ahalin Iffah sararin samaniya ne ba ganinsu sai da ga nesa akan yaro da babba. Ki fada min miyasa kika kirani da ina da yan ayyuka a gabana masu muhimmanci, idan kuma kin kirani din ne dan kawai ki jajjadamin karfin ikon naki da kasancewarki damisa da bata da banbanci da damisar takarda a wajena to". Ba karamin dukan zuciyar Malikat Bushirat kalmar (Bokanya) nan yay ba, dan maganganu ma da suka biyo baya sam bata jisu ba ko fahimtarsu, amma sai ta dake ta basar kamar shima bataji ba. Sai tama saki wani murmushin kasaita cike da izzarta tana ma Iffah'r kallon ke karamar kwaruwa. "Bazan hanaki wasa da Zakanya ba, koba komai zan ajiye darasin da zai zama izna ga yan baya gareki yarinya. Ina son sanin dalilinki na shiga hurumin da ba naki ba kan shiga bital mali ki fidda kayan azumi". Dan murmushi Iffah tayi yanzu ma, sai kuma ta ajiye wayar hannuta ta sauke numfashi mai nauyi. "Ammie na yarda ke Zakanya ce, sai dai ki sani duk karfin bajintarki da iya farauta a saman kowa watarana tsufa kan iya sa ki rissina ji inki ta zama sarauniya bisa karfin ikon Ni bance nafi karfin kaddara ba, sai dai ki sani a tafin hannunna kike ke da komanki. Bana son cigaba da jayya da ke ko nuna karfina akan karfin ikonki da har mutane zasu kalla gazawarki ko kaskancinki a cikin idanunsu saboda daraja. Eh tabbas daraja, darajar abinda kika haifa ya zama mai daraja a cikin al'umma badan yafi kowa ba a wajen ALLAH ko ke da kika haifesa kinfi wani. Ammie why inada abubuwan ban mamaki da daga labulen sirrinki sau daya kawai sai ya hana wannan idanun naki barci. Sai dai bazanyi hakan ba, bazanyi ba saboda mutunci da kimar danki har sai in kin bijirema hanyar da nake son ki dawo. Kwana biyar da suka wuce naci karo da bakon ganyen shayi mai hadari matsayin wanda Shahan-shan zai sha. Na kuma cin karo da madara itama, dana bincika sai na gane da ga sashenki madarar take, ba kuma na raba dayan biyu shima ganyen shayin naki ne. Na gagara fahimtarki ko inda kika dosa a zahirance. Kowa dai ya kalla fuskar Maleek da taki basai ya sake kallo ba yasan jininki ne shi,dan kamminku a bayyane suke ta abubuwa masu yawa. Kema a karan kanki kin fada kin kuma maimaita shi din danki ne. To wai nikam wane buri ne kike son cimmawa mai alaka da makiyi a tsakaninki da shi? Kin ko san da ace yasha ganyen shayin nan ko madarar nan illar da zatama rayuwarsa sai tafi wadda zatama tawa rayuwar? Sannan ke da kanki sai kin dawo kina kuka da dana sani. Idan ma wani ke baki wadan nan abubuwan matsayin wani kariya washi ko gurbata tawa rayuwar to tabbas ki farka. Ki farka why tunkan guri ya kure miki ki rasa kofofin fita a wannan masarautar. Na rasa mikike nema? Mikike bukata? Mi kekike son zama bayan abinda kike a yau dinki da har in kika rike zata jagoranceki zuwa gobanki cikin salama kamar yanda Jaddah take a yau ga kowa". Taja numfashi mai nauyi tare da dafe kai cikin kunar rai, sake dagowa tai tamkar bataga kallon wutar bala'i da tsanar da Malikat Bushirat din ke binta da shi ba ta cigaba da fadin………✍️ DAUDAR GORA Book 2 Chapter: 66 ."UBANGIJI ya halicceki mace bayan akwai maza da yawa dake kwaikwayo son zama macen amma basu isa komawa ba. Ya halicceki kyakykyawa, bayan awai wasu da yawa da kyawun da bai kai naki ba suke fafutukar nema ta hanyar sabama UBANGIJI suna amfani da abinda yace haramunne garesu. Ya baki lafiyar jiki babu ta inda kika nakasa. Bayan ga dubunki can su nakasar itace jarabawarsu. Ya baki lafiya matsayinki na yar adam. Bayan ga dubunki can kwance a asibitoci da gidaje basu da kudin shan magani, masu kudin ma basu isa iya sayawa kansu lafiya ba koda sun kai karuna dukiya. Ya azurtaki cikin nagartaccen addini, bayan ga dubunki can na bautar wanin ALLAH cikin batan da su a karan kansu basu san bata bane ba. Ya azurtaki da tarin dukiya. Bayan akwai dubunki da abincin yini daya ma gagararsu yake ci saboda basu da kwabo na saya. Ya azurtaki a cikin katon gidan aure dana haihuwa, karkashin kyakykyawar nasaba bayan akwai dubunki da a kan titi ko cikin bukka suke rayuwa badan kin fisu ba. Ya azurtaki da karfin iko na mulki, bayan akwai dubunki da su wanna matsayin naki suke kwadayon kaiwa, ke wasu ace ma su din hadimanki ne kawai farin ciki yake sanyasu. Ya azurtaki da ilimin addini dana zamani, bayan akwai dubunki da suke zagaye da jahilci, wasu ko suna son karatun rashin mai tallafa musu Yasa suka hakura suka zama masu aikata miyagun laifuka koda zukatansu basa so, sai dai basu iya banbance abinda ya dace da wanda zai dace da tasu rayuwar. Ya azurtaki da da daya tilo tamkar da dubu da nagartaccen mijin da duniya bazata taba mantawa da su ba, bayan akwai mata da yawa da su jarabawarsu mazajen aurensu ne da yayan da suka haifa. Duk da ya miki wadannan abubuwane badan kinfi sauran halittun duniya ba. Badan bazai dandana miki mutuwa ba. Badan bazai iya jaraftarki ki kasance su ba. Badan kinfi karfinsa ba. Sai dan kawai ya miki talala har zuwa ranar da zaki tabbatar ke din bakomai bace a cikin komai. Ke din yar adam ce, yar adam din nan da aka halitta da ga yunbun kasa, yar adam din nan mai rauni, mai barci, mai kashi, mai ciwo mai jiran kwanakin mutuwa. Badan kiyi alfahari da duk wadan nan abubuwan ba kuma ya halicceki, ya baki su ne domin jarabawaki itace su, kamar yanda ya bama wasu sabanin naki domin jarabawa suma. Dan ALLAH mi kike bukata a bayan duk wadannan? Minene burinki da fatanki da fafutukar ki da har halaka rayuwar yayan wasu ke sakaki a farin ciki amma baki son ko kuda ya rabu daya naki tilo da sunan cutarwa? Ke uwa ce, ya kamata kiyi hasashen zafi da ciwon da zaki iyaji dan akace babu wannan tilon dan naki kafin idonki ya rufe ki zama sanadin hana wasu. Ni Fhareedah bint Zayyan b yafe daukar fansa ki shaida haka, bakuma zan gajiya da fada miki na, amma ke uwa ce ina mutuntaki da wanna matsayin, dan ba'a bani tarbiyyar raina koda wanda ya girman da kwana daya ba a duniya balle ke da nasan zaki iya haihuwar wanda ya haifan musamman ace Maleek mace yazo ba namiji ba. Sannan koba komai kin haifamin gwarzo kuma barden miji da tun kan bakina ya tabbatar da alfahari da shi gabbaina isarwa suke. Shi mutum ne adali, mai addini, mai yawan bautar ALLAH da mika masa lamuransa. Baya jin wani alfahari da matsayin da ALLAH ya bashi kamar ke face takatsantsan dan yana kallonsa a matsayin jarabawarsa. Akwai tarin abubuwa masu dunbin yawa da nake bincikawa akanki da alakarki da halaka yaran mutane, idan kikace zaki cigaba da bina da izzarki why why Ammie baza'a ganeki ba. Ki bini a sannu-sannu ni zan kaiki inda kike son zuwa bake zaki kaini ba. Kamar yanda ni na kawo kaina masarautar nan bake kika kawoni ba. Kamar yanda ni nai amfani da Arshaan da Jasim da Haifah basu sukai amfani da ni ba, ke shaidace kuma ga irin makomar da suka kasance duk da somin tabi ne ma na fara musu.Kamar yanda ni na bama Shahan-shan din da kike takamar da shi garkuwa bashi ya bani ba har kike hakilo da hura hancin wai ya janyeta gareni.Kin san ALLAH kiyi maza ki dawo hayyacinki ina tsoratar miki shiga jerin mutanen da zan kwancema zani a bainar nasi cikin Masarautar nan dank kuma ya musu hukunci, kiyi azamar ajiyewa ki labe bayan mutuncin danki hukuncina ya kasance tsakanin ni da ke ne kawai. Dan saura kiris a fara bankada, idan kuma aka fara akwai gagarumar matsala, dan na fahimci ke kanki har yanzu baki gama sanin wanene danki ba da ainahinsa, kinama rogo kallon kitsene kawai, sannan kina kallon kasurgumin Zaki ne da fatar mage" ta saki murmushi tare da takawa gabanta a hankali. Hannunta ta kamo ta daura saman cikinta, "Ina tayaki murna da albishir din insha ALLAHU kafin mu dawo daga hutun in amarcinmu da iznin UBANGIJI zamu dawo da jikanki a wannan babbar garkuwar, dan haka kibar wahal da kanki akan sai Maleek ya auro wadda kike son ta haifa miki shi dole ko nisanta shakuwar iyayensa da zata zama sanadin samar da shi ta hanyar madara. Da ga kuma randa kika tabbatar da samuwarsa, ki fara irga kwanakin nadamarki da dana sani har zuwa ranar haihuwarsa. Hukunci da karfin ikon Iffah a saman naki, yanzun ne zai fara Mother in-law". Ta dan kyalkyale da dariya da sakin hannun, yako tafi yaraf alamar duk wata mahada mai motsi a jikin Malikat Bushirat din ba aiki take ba a yanzu. A hankali ta koma kasa kusa da kafafunta ta zauna, tare da hannu ta dago afar ta fara matsa mata. Zabura Malikat Bushirat tai kamar wadda aka kodama mari ko ta suma aka zubawa ruwan sanyi drum guda, sai hakan kuma yay dai-dai da shigowar Tajwar Eshaan ibn Haysam Abdul-majeed. Yar dariya Iffah tai kamar bata san da shigowarsa ba ta cubi Malikat Bushirat din. "Ammie irin wannan zabura haka na sake tabo wajen da yay dayin kenan?". Idanun Malikat Bushirat ne suka sauka akan Tajwar Eshaan din dake takowa a nutse idonsa a kansu fuskarsa da dan sakewa. Sai dai kafin ta iya cewa komai da ga daurin goro ko makircin Iffah zatace mane oho Tajwar Eshaan din ya karaso yana dan gyaran murya. Dagowa Iffah tai ta kallesa har yanzu fuskarta da murmushi. Cikin yar shagwaba ta ce, "Yauwa ai garama da kazo, Ammie na nan zata kasheni da dariya, tace fa na matsa mata kafarta ya mata dan nauyi saboda zaman waje daya amma da nayi- nayi sai ta fara fadin ya isa a bari ta huta". Wani dan moso yayi iya lips yana dauke idanunsa da ga kallon da yakema Iffah'r na kasa-kasa ya maida kam Malikat Bushirat da mamakin duniya a makircin matsiyaciyar yarinyar ke neman dauke numfashinta. A hankali cikin dan sanyin nan nasa da kamewa ya ce, Ammie shiyyasa nace ki dinga motsa jiki tun last year, wannan zaman waje dayan da kuke ai ba gata bane, gashi nan shi ya kashema Jaddah kafafu anata fama". Da kyar ta iya dannewa ta dan saki murmushin karfin hali da yafi kuka ciwo ta ce. "To ya za'ayi Saiful-malik, mizamuyi da wani motsa jiki a wannan shekarun namu?". Kafin ya bada amsa Iffah ta amshe da fadin, "Ai Ammie kike da motsa jiki kuwa, dan motsa jikin nada amfani sosai, kuma ya kamata ko dan cikin badda kama kuna fita kwamaga yanda talakawan kasa ke yan sabgoginsu, sannan koba komai ai hakama karin imani ne da lafiyar jikin harma da ta zuciya". Wani irin ji Malikat Bushirat tai kamar ta shako wuyan Iffah, dan ta fahimci maganace cikin ta jefa mata. Itakam ta farama tunanin anya yarinyar nan mutumce kuwa ba aljanaba a sufar mutane? Ya kamata a bincika mata kam dan al'amarin ya fara girman tunaninta. Amma a zahiri sai ta cije tai dan yake. Tajwar Eshaan da ke dan jinjina kai batare da ya fahimci komai ba shi kam a zancen idanunsa dake akan Iffah ya lumshe kadam da budewa lokaci guda. "Ammie shawaran nan nata mai kyau ne, ni kaina naso na miki tayin hakan tuni sabgogina basu barni na zauna ba. Amma Alhamdullah tunda gata yanzu bayan ni da Aunt kin sake samun diya daga ALLAH nasan zata kula mana da ke kamar mu din. Sannan kusantar al'ummar mu yanda ya kamata a zahirance zai kara saka mana son su da kaunar su a zukata kamar yanda ta fada. Zakiji dadin hakan, ki samu lokaci ki fara gwadawa koda tare da itane ni mai yarje muku ne". "Uhm kai dai. To ALLAH ya shige mana gaba kawai". Amin suka fada a tare shi da Iffah, sai dai a ransa yasan bata amshi lamarin ba. Dan haka ya basar da zance ya dakko mata na tafiyarsu.Cikin mamaki take kallonsa sai dai batace komai ba. A ranta kam wani irin zafi takeji mai kuna. Har itace sai yau Saiful-malik ke sanarma zaije Umrah, Umrah din ma na azumi baki daya. Kai anya bata fara rasa danta ba kuwa? Bata fara rasa danta daga jikinta ba kuwa? Jifa maganganun da yarinyar nan ta fada mata a yanzu, irin wanda ko mahaifiyarta sanda tana a raye bata jin ta taba fada mata su, amma shi ya hau ya zauna Kamar ma bai fahimci manufarsu ba. Tabbas akwai matsala, matsala babba da uwa sam bata lissafo ba a lissafinta. Yanda fa rawar take neman canjawa dole ne shima kidan ya canja inba hakaba zata kona Masarautar nan ne baki daya why, dan bazata dauki faduwa a saman nasararta ba. Never for ever……..✍️ DAUDAR GORA Book 2 67 …. Suna barin sashen cikin tashin hankali tashige ciki tai kiranye uwa. Cikin kankanin lokaci kuwa sai gata ta bayyana alamar dama a kusa take. Ido rufe Malikat Bushirat ta zayyanema uwa duk abinda ya faru tsakaninta da Iffah. Yanda uwa ke huci sai ya koma tsorata Malikat Bushirat din, tuni nata fushin da harzukar suka bace. Zabura tai gefe jin sautin kakkausar muryar uwa mai tsananin amo acikin kunnenta. "Wannan fadan ba naki bane damu takeyi!!! Lallai damu takeyi. Ita wacece? Yar wacece? Mitake takama da shi?! Zan tabbatar da ba uwarta kawai ba, hatta dukkan ahalinta sai sunyi nadama da dana sanin kasancewarta jininsu!!!!. Wanda suka fitama sunja bata kai musu ba balle ita haihuwar jiya-jiya.". Ta fada cikin wani irin karaji da dukan kasa da tafin hanunta, tare da rantsuwa da wani kasurgumin gunkin da take bautawa wanda sam Malikat Bushirat ita bama ta fahimta ba. Ji Malikat Bushirat din tai hatta dakin girgizawa yake, tamkar tashin guguwa uwa ta bace bat a dakin. Wani irin numfashi ta sauke mai nauyi, tare da zama jagwaf. Ta jima numfashinta na kai komo kafin ta samu daidatonsa, sai kuma ta saki murmushi mai matukar kayatarwa da dan tabe baki ta dage kamafada irin ko'a jikinta din nan,wanna kuma fadan yimata shi za'ai. Ni dai nace, "Humm" 🥱😂🚴 *. WASHE GARI*. Kasancewar ba' a ga wata a jyan ba basu wuce ba. Hakan sai ya saka Iffah yini a sashen Malikat Haseenat. Sai bayan sallar la'asar ta dawo. Lokacin su Tajwar Eshaan da was manyan masarautar na'a can saman ginin da agogon da duk ta inda ka bullo ta birnin Dahab City din zaka gansa da na'urorin ganin wata, Cikin amincewar UBANGIJI kuwa sai gashi an gansa, Dan danan kafofin yada labarai suka fara sanarwa da yawn Shahan-shan, dan shi da kansa yake duban wata tun hawansa mulki babu wani wakili. Alhamdullah washe gari an wayi gar da azumin watan Ramadan a bakunan mutane. Yayinda jirgin Tajwar Eshaan da Iffah sai hadimai hudu mata shida maza. A ciki akwai hadiman sashen Malikat Haseenat da Iffah ta roka ta bata su su biyu har da hadima Banou. Lokacin da akace mata zatabi Iffah rikicewa tai harda kukanta a boye. Sal Diwa amintacciyar hadimar Malikat Bushirat ta zahri, wadda itama dai Iffah!r ce ta nema ta bata a gaban Tajwar Eshaar babu yanda ta ya ta bata, sai hiyu da suka kasance daya a cikinsu hadimar da Uwa tace zasu batane samun wanna damar yasa suka cusata a ciki.Tafiyace ta sirri dan haka babu wanda yasan da ita a Kasar, ko'a cikin masarautar a ba kowa ya san da Shahan-shan din za'ai ba. Kowa ya dauka Iffah'r ce kawai zatai gaba kafin su Malikat Haseenat da ake hasashen kila sue su samesu acan tunda suma sukanje duk kusan bayan shekara uku, tun bayan hawan Tajwar Eshaan din kuma sau daya sukaje,shiko tunda ya hau mulkin ma bai taba ma zuwa ba sai yanzu. Lokacin da jirgi ke barin kasa wani irin kudindinewa Iffah tai a jikinsa na toro. Ta bashi dariya dan ya fahimci duk irin abubuwan nan tsoronsu takeji. Ga Elevator ma in zata shiga yanda take kasancewa balle kuma anan, tafa gwammace tabi stairs duk wahalarsa idan ita kadai ce. Rungure kayarsa yay dan su kadai ne, hadiman na nasu sashe daban. Koda jirgin ya gama dai-daita bata bar jikin nasa ba: sai ma barci da yay awan gaba da ita mai nauyi. Ajiyar zuciya ya saki yana mai sumbatar idanunta. Azuciyarsa ya ce, (Fitinanniyar yarinya nima nadan huta da surutunki) a zahiri kam sai ya gyara mata kwanciya nutsuwa na sake saukar masa. Shi kadai yasan kaunar da yakema yarinyar nan, ALLAH dai yasa karta zama ajalinsa. 😂Oh oh masoyan asali. 😉 *_SAUDI ARABIA_* Mamaki hade da al'ajabi ne ya mamaye Iffah lokacin da suke fita a cikin jirgin hannunta cikin nasa. Wasu zuka-zukan motocine na alfarma da tawagar masarautar Saudiya, yayinda Sultan a Saudiyya ne da kansa yazo tarbar Tajwar Eshaan ibn Haysam Abdul-majeed Ally Qutb ba sako ba. Cikin farin ciki sarakunan biyu masu karfin fada aji a duniyar musulinci suka tarbi juna. Sam Tajwar Eshaan bai saki hannun Iffah ba har suka rungume juna da Sultan din. Bayan sun saki junan ne ta dan rissinar da kanta alamar girmamawa ga Sultan din.Fuskarsa kawance da murmushi yay mata kallo daya da musulunci ya shardanta ya dauke kansa. Ya fai mata barka da zuwa DAULAR MUSULUNCI cike da mutuntawa a gareta duk da yasan zai iya haihuwarta. Dan manyan yaranta maza twins guda biyu suma bazasu wuce 20years ba karnar Iffah'r.. A hankali ta sauke ajiyar zuciya tana lumshe idanunta jin sanyin ac da kamshi mai shegen dadi ya ratsa hancinta lokacin da suke shiga daya daga cikin manyan motocin da sukazo tarbarsu. Dubanta Tajwar Eshaan yay tare da rungumota jikinsa da kyau. Tako late kamar yar mage tana shakar daddadan kamshinsa. Ashe Iffah ba komai ta gani a airport din nan ba. Sai da suka shiga babbar daular da lissafin dukiyar cikinta ma da kawatuwa bata lokacine. Tabbas tasan Daular ruman ta had, irin haduwar da babu wanda zai shiga bai yi santi ba. A tunaninta da anya akwai makamanciyar irin daularsu a duniya? Amma a yau ta tabbatar akwai, dan duk da daular Saudiyya bazatafi tasu ba, suma tasu bazata fita ba, dan nan clin ma dai badaga baya ba Dan in za'a baka zabima zaka ya kasa banbancewa ne tsabar shiga rudani. An musu tarba ta mutuntawa da tsantsar girmamawa, tare da masauki dan gaske da ko'a kasarsu iya abinda zasu iyama kansu kenan. Tattare suke da gajiya, musamman I/fah daba sabawa tai ba ga kuma azumi, saukin ma farkon farawa ne. Da kyar ya lallabata tal dan wanka ta kwanta. Kafin kace mi barci yay awan gaba da ita. Bata samu kanta ba sai la'asar, shima da kyar ya tadata sanda zai wuce massalaci. Bayan ya dawo yace ta shirya zasu wuce madina ne da ansha ruwa, da ga haka ya fice ita kuma wasu mata sukazo mata da kaya inji matar sultan. Sun jirata ta shirya sukai mata jagoranci zuwa sashen matar sultan din, inda ta samu tarba ta mutuntawa da har ta dinga jin kanta ya kara girma itama a yau. Dan duk da matar sultan din ta girmeta sosai janta ta dinga yi a jikinta cike da kulawa harda cewa itafa tana so ta saki likinta da ita ne dan sun zama kawaye. Murmushi kawai Iffah tayi mai sanyi. Ta wani nutsu kamar ba Iffah'r nan mai shegen surutu ba mai addabar Tajwar Eshaan. Magana ma an koma amsata ne dai-dai cikin nutsuwa da kamewa ita a dole ga matar Shahan-shan na kasar ruman (Ashe akwai a inda bakin Iffah zai mutu haka (😂). Suna a tare har aka sha ruwa, a tare suka gabatar da sallar magrib sannan suka fito kayataccen falo karami na musamman da aka shirya musu kayan alatu na shan ruwa. Daga ita sai uwargidan Sultan da Shahan-shan din ta. Sai wani irin binta da kallon nan nasa na kasan ido yake kamar zai hadiyeta dan ta masa matukar kyau cikin kykyawar bakar abayar data haske farar fatarta ga walwalin fararen duwatsu da akai mata ado dasu. Itama dai uwargidan Sultan irin kayanne a jikinta. Haka shima da Sultan din kayansu iri gudane. Lallausar farar jallabiya mai tsadar gaske an daura bakar alkyabba da akaima adon golden da mayafi fari tas a saman kawunansu. Kamshi dai nasa ne, dan daga su sai turarrukansu sukazo kasar. An sake gaisuwa irin ta manyan attajirai masu mulki da karfin iko, sannan a nutse sukai buda baki mai sauki (ba irin na su bily ba da sai anji ciki yay nak babugurin tura kosai 🥱), Karancin lokaci ya saka sarakunan biyu mikewa zuwa gabatar da sallar isha'i. Suma kuma su Iffah suka kora bedroom din uwarg/klan Sultah suka gabatar da tasu. Suna idarwa basu zauna ba, dan tafiya tsakanin nan da Madina akwai nisan gaske, dan ma lafiyayyun motocine. Sai lokacin Iffah ta san ashe tare da Sultan din da matar tasa ma zasu wuce. Tofa wayaga in da ranka kasha kallo, dan kuwa dal acikin zukekiyar motar da zasuyi tafiyarma dai an shirya musu abincine, ga an shiryar motar daga aiki kamar wani daki ha musamman. Iffah dai da al'amarin ya zame mata sabo ga kauyanci ga son nuna class t3, haka mutunivar tamu akaita basarwa kamar komai ba komai dai kun gane ai 😉(Kuka yarda naje gurin nan alkur'an sai na nuna hali, dan kowa sai yasan Bilyn Abdull daga 9ja nazo 🤣😆🚴). A yanzun kam sarakunan biyu sun baje filin hirarsu a nutse ga matansu a gefensu. Har takai ita dai Iffah ta fara ma hamma. Cikin mamaki Tajwar Eshaan yake mata kalion nan nasa na kasan ido, dan ya fara sakama yawn barcin nan nata alamar tambaya. Abu kadan ta fara hamma, yanzu zata tashi anjima kadan ta sake kwanci. Kuma bazaka taba ji tace barcin yaisheta ba. Anya kuwa? (Sa a bincika mana mai rumawaja🚴). * MADINA BABBAN BIRNI BURIN ZUWAN DUK WANI MUSULMIL* Duk da dare yayi kai tsaye massalacin MANZON ALLAH (S.A.W) suka wuce, inda nan ma suka samu tarbar da ga shugaban garin na Madina da tawagarsa cikin girmamawa ga Sultan din nasu a Saudiya gaba daya da kuma babban bakonsa shugaban kasar ruman. sai da suka gabatar da salla raka'a biyu sannan sukai zaman jira karasawar lokacin asubahi Basu bar mascalacin ba sal bayan sallar asuba. Yanzun ma dai wani katafaran gida aka kaisu. Gida daya amsa sunansa gida bawai muna gida ba. Gajiyar da ke tattare da kowa yasa ruwa kawai suka watsa kowa ya kwanta musamman ma Iffah dake jin kamar zatayi adungure tun a massalaci…..✍️ DAUDAR GORA Book 2 68 ...……….Lokacin da azhar ta gabato Tajwar Eshaan ya tashi yay wanka ya kimtsa babu alamar Iffah zata motsa, kwance take sharkaf tana kwasar barci kamar wadda ta mutu. Zama yay a bakin gadon ya zuba mata ido, tare da kai yatsunsa saman goshinta da wuyantan amma babu alamar wani zafi da ke nuna tana a cikin ciwo. Da kyar ya tadata tana faman tura baki gaba, ya kafeta da kaifafan idanunsan nan, sake tunzura bakin tai ta kauda kai. Sai shima ya dan girgiza kan a fusge ya furta, "Ki daina turamin wannan bakin na dinga kai azumina lafiya batare da ya raunana ba. A haka za'ai ibadan Nigar?". Kwalkwal tai da idanunta kamar zata saki kuka tace, "Nima zuwa fa barcin kawai yake, konace bazanyi ba sai na kasa". Shi dai kallonta kawai yake zuciyarsa na raya masa abubuwa masu yawa. Amma sai bai furtaba ya ce, "Okay tashi ki shirya muje massalaci ga su Sultan na jiranmu". Babu yanda ta ia dole ta tashi ya taimaka mata ta shirya din, dan a hakan ma sai faman lumshe masa idanun take da sakin hamma. Shi dai lallabata yay suka wuce dan ya fahimci abin bana lafiya bane. Kilama Aljanun nata ne ke sakata barcin dan kar tai ibadar.... (A gurguje Please munada sauran aiki, gashi nagaji walle. Gara muyi mu gama kowa ya huta 🏃‍♀️). Rayuwa a Saudiyya wani rubutaccen al'amari ne da Iffah bazata taba mantawa da shi ba a rayuwarta, dan rubutaccen labarine tsakaninta da Maleek dinta mai zaman kasan ga ma'abocin bibiyar labarinta, amma ta tattara ta killacema zuciyarta kawai kuma sai ku kiyasta da hasashenku. Duk da dai ta samu nakasun raunana a dalilin barcin da bata san kansa ba balle karshensa. Amma duk da haka tana matukar yaki da shi da ganin tayi cikakkiyar ibada. Dan abu mafi birgeta shine yanda Tajwar Eshaan ke tsaye akan kafafunsa koda yaushe babu wasa tattare da shi ko nuna gajiyawa a dare da rana. Gaba daya ya maida hankalinsa a bautar Sarkin sarakunan nan mahaliccin duniya da kayan cikinta, mai rahama da mukullin aljanna. Sarkin da babu kamarsa kai koda kwatankwacinsa ma babu. Gaba daya ya mika lamuransa garesa cikin kaskantar da kai da zubda gwiwunsa bisa kasa. A duk sanda yake addu'a zaka samesa da hawaye share-share da inba gaban UBANGIJINSA ba bazaka taba gani ba. Kullum cikin gayama ALLAH yake kan samun warwarar al'amuran da suka shige masa duhu musamman akan mutuwar yaran da basujiba basu gani ba a daliln aurensa. Duk da wannan jajircewar tasa kuma yana bata kulawa a dan kankanin lokacin da suka daukarma kansu na hutawa. Dan ko bayan kammala Umrah din su bai lamunce su zama a karkashin inuwar lalaci ba. A gefe kuwa wata Irin shakuwace ta shiga. tsakaninta da uwargidan Sultan. Mace hamshakiya ma'abociyar kyawawan halaye da nuna tsattattacen iko saman na kasa da ita. Nutsuwa sosai Iffah tai tana koyan abubuwa, yayinda itama bata tsaya boye-boye ba ta fito tana gyarama Iffah'r duk abinda zai bata martaba da kima a wajen mijinta da al'ummar da mijin nata ke shugabanta. Dan tayi dubi ne da karancin shekarun Iffah'r da ma labarin data bata na cewar ita iyayenta basu da alakan mulki. Ba halayyar Iffah da dabi'u ba hatta jikinta wani irin gyara yake samu na musamman ga uwargidan Sultan din. Hadimanta kam tunda sukazo bata gamsu sun ganta sau cikakken biyar ba. Hakama duk dokinta da tsammanin zal hadata da su Babiy tunkan su taho babu alamar zai yi hakan. Har magana ta masa cikin hikima amma sai baice mata komai akan hakan ba. Dole ta hadiye komai ta nuts bisa shawarar uwargidan Sultan din. Shanyewar tai kuwa, dan yanzu Iffah an koyi halin dattako da shanye abu a ral, sai dal fa à gaban Tajwar Eshaan bakin baya mutuwa, idan kin jita shiru barci take, a lokacine kawal zai huta da tsiwarta. Alhamdulillah yau an kai azumi na ashirin da shida, a yau ne kuma su Iffah sukayi ziyarar bankwana cikin dakin ka'aba ita da Tajwar Eshaan da Sultan na saudiya, da uwargidansa, sai wasu manyan masarautar tasu. Iffah tasha kuka lokacin da taganta cikin tsakkiyar dakin ka'aba, Abune da bata taba zaion kasancewarga ba koda a cikin matarkinta. Kal ita ketare kasar ruman ma bata taba zaton tana da rabon yi ba a rayuwarta. Amma yau sai gata da kwanaki ashirin da biyar cikin kasar Saudiyya, tare da mijin aurenta shugaban kasarta. Hannunta kawai ya rife cikin nasa alamar lallashi har suka fito, suna shige mota kuwa ta fada jikinsa ta kankamesa. Murmushi yay mai sanyi da dagota yana mata yan harara tare da lakace mata hanci. "So kike ki karyamun azumi ne?" Baki ta dan tura tana wan kikkitata Idanun dake cike da hawaye, a shagwabe tana war idanun da yanayin mamaki ta ce, "Dama maza azuminsu a karyewa ne?". Murmushi kawal yay ya dauke kansa, sai kuma ya sake juyowa a yanayin wanda ya tuna wani abu, kallonta yay da ga sama har kasa kafin ya jeho mata tambayar data daure kanta da bata yar kunya-kunya. "Mrs Eshaan kin sha wani magani ne dan kar kisha azumi?". Da kunya-kunya mamaki-mamaki ta dubesa, sai kuma ta girgiza kanta alamar a'a. Itama kuma sai kirjinta ya shiga harbawa da sauri-sauri. To al bama watan azumi kawal ba, idan bata manta ba rabonta da ganin proud din ta fa kamar tun wanda ta gama da kwanaki kadan ya ziyarceta bafa ta sake ba. Kai kodai ta sake ta manta, to idan ma ta sake din ai a watan nan ne na Ramadan ya kamata ta gani farkonsa, juya mata kanta ya fara yi saboda neman takurama kanta da tai na sai ta tunano. "Kinga relax karki takurama kanki"., Ya fada a hankali yana kwantar da ita a kujerar.Gaba daya jiyay yama kagara su koma cikin masarauta, suna isa kuwa masaukinsu aka zarce da su. Duk da an bude mata kamar yanda aka bude masa kofa shima sal ya fito da ita ta inda ya fita, basu fi zaman mintuna goma ba doctor din da ya bukaci gani ya iso tare da uwargidan Sultan da hankalinta ya tashi da tunanin ko kukan da Iffah tayi ne ya zame mata matsala, ita Iffah sai ma abin nasu ya bata mamaki da dariya,ta kal dubanta ga Tajwar Eshaan da yay zaman kasaitar nan tasa. Cikin langabe kai ta masa magana da ido alamar wai mike faruwa? Dauke kansa yay gefe a ransa shi kadal yasan miyake ji na farin ciki, ya kagara doctor din tace wani abu. Amma a zahiri baka isa fassara abinda ke ko"a kan fuskarsa ba balle zuciyarsa. Doctor da tai yan gwaje-gwajenta a gabansu abinka da gidan manya ta dago tana murmushi, cikin girmamawa ta fuskarci uwargidan Sultan ta mika takardar da tai yan rubuce-rubuce. "Ya ALLAH" Uwargidan Sultan ta fada fuskarta da kayataccen murmushi. Ta kai dubanta ga Tajwar Eshaan da ke jin kamar ya fisgo takardan hanuntan amma ya dake a zahiri. "Ina mai farin cikin kasancewa ta biyu bayan doctor akan sanar muku samun karuwa da mukai, ALLAH ya sauki Zawjata-almilk lafiya". Wani irin lumshe idanunsa yay da sauke sassanyar ajiyar zuciya kamar wanda aka zarema numfashi. Yayinda Iffah tai fakare tana kallonsu cikin rashin fahimta sam. Dan ita kanta ma sat ya toshe kawai a wanna gabar. Har suka gara bidironsu Uwargidan Sultan ta wuce bata iya tofa komai ba.. Wani irin dagata yay bayan ficewar kowa a falon ya shiga juyi da ita. Kawal ita sal abin ma ya bata dariya ta shiga kyalkyalawa. Bai hakura ya direta ba sai da yaga ta fara date kal alamar jujuyatan da yake akwai matsala. A tare suka dinga sauke numfashi, ya tsareta da idanun nan nasa masu kaifi ga kayataccen murmushi mai matukar tada da yakan dace baka gani a fuskarsa ba, Sal dal kuma a zahirance bakin ya gagara cewa komai. Sal da ya mula dan kansa a hankali ya furta "Mrs Eshaan kin mallakeni da komal na. Da gaske fa ni din bawanki ne". Da sauri tasa hannu ta rufe bakinsa tana zaro idanu da girgiza kanta. Cikin rawar murya kamar mai shirin sake masa kuka ta ce, "Please Sultan ka daina fadar haka karma yan kasar ruman suji sumin yankan rago. Kai fa shugabana ne, sannan ashekaru ka fini, gaka mijina,uban yayana", Hawayen suka silalo mata a hankali. Hannunsa ta kamo ta daura akan cikinta. "Nagodema ALLAH da ka kasance mahaifinsu badan ya baka daukakar mulki data dukiya ba. Domin su a duniya aka samar mana da su a cikinta kuma zamu tati mu bari wataran. Ina alfahari da kai ne matsayin uban yayana saboda nagartarka da adalcinka. Tsoron ALLAHn ka da kyakylyawar zuciyarka. Maleek kai na dabanne a cikin daban. Ba yan kasar ruman bane kawal suka dace a dalm shugaba ba. Daular musulunci ma kai abin alfaharinta ne. Sannan kuma nice kololuwar dacewa da ka kasance miji gareni, Nauyin mulki bai sa ka gaza bani farin ciki da sauke duk wasu hakkokina ba. Kana samar da nishadi a tsakaninmu ka manta da kai sarki ne mai jagorantar talakawan kasa bawai jaha ko wani dan yanki ba, Kwanciyar hankalin da nake samu da ga gareka bana jin wasu matan da mazansu basu da nauyin kowa na sarun makamancin sa. Maleek kai ne gwarzo na, kai ne Barde na, kuma kaine gagara badau dina". Idanunsa kawai ya lumshe a zahiri, maimakon ita da ke kuka a bayyane shi a zuciya yake yin nasan. Tabbas yaga ribar hakuri, kai shi baima san mizaice da UBANGIJI ba akan kyautar wanna yarinya da ya bashi. Ita din ta dabance. Tabbas itace komansa. Tsam-tsam ya rungumeta a jikinsa na tsawon lokaci, sal da ya ji tana sauke numfashi a hankali alamar barci ya dauketa sannan ya dagota. Kwantar da ita yay a hankali ya cigaba da kalionta hannunsa saman shafaffen cikinta da kamar babu komai a cikinsa abubuwa da yawa na masa kaikawo tun daga randa ya fara ganinta soyayyar farat daya ta shigesa har zuwa yau da ajiyar gudan jininsa ke à cikin jininta…..✍️ DAUDAR GORA Book2 69 .....WASHE GARI ta kasance ranar da zasu koma kasar ruman. Da safe bayan Tajwar Eshaan ya gama ganawa da Sultan na saudiya sunyi sallama amintaccensa da Sayeed Tasadduq-Husain da sai daga baya yazo ya samesu a saudiyyan da wasu mutane biyu suka samesa. Cikin girmamawa suka mika gaisuwa, kafin Sayeed Tasadduq-Husain ya mika ma Amintaccensa file din hannunsa. Amsa yay da sauri yaje gaban Tajwar Eshaan din shima ya ajiye. "Wannan shine result din binciken ALLAH ya kara ma adalin shugabanmu lafiya da nisan kwana. Sannan wadan nan sune sukai binciken. Sun kuma kasance kwararrun likitoci ta wanna fanin". Da sauri daya a cikinsu ya karbe zancen Sayeed Tasadduq-Husain din cikin harshen turanci, "Idan mukai bincike so daya ba'a samun kuskure, amma domin cire tantama sai da mukai wanna sau uku. Abu daya yake tabbatar mana shi namijin mahaifinta ne, mace kuma ba ita ta haifeta ba. Bayan muni sau uku mun sake bayarwa was asibitocin ga results din nan dai duk abu guda suke bayarwa". Baice komai ba, sai amintaccensa ne ya amsa da yawunsa. Da ga haka sukai masa sallama Sayeed Tasadduq-Husain yay musu rakkiya. Duk abinda akeyi Iffah na daga kofar falo na biyu ne tsaye zata fito zuwa sashen Uwargidan Sultan da zasuyi sallama. Duk da bata san manufar zancen ba sai duk taji ta tsargu, amma kasancewar yanzu an koyi wasu halaye musamman akan hadiye abu koda ta fito wucewarta kawai tavi tunda yasan da fitar tata.. Koda taje can kuma abun nata mata kaikawo har tana jin kwadayin son sanin abinda ke a tattare da file din da son sanin akan wama ake maganar da har sai anzo wata kasa za'ai binciken bayan kowa yasan kasar su suna daya a cikin masu kwararrun likitoci a duniya. Sai kuma a ka kara yin sa'a lokacin da take dawowa sashen ta samu Sayeed Tasaddug-Husain da Tajwar Eshaan din suna maganar again. Cikin kasaitar nan tasa da magana a fisge yake sanar masa. "Ayi musu komai da ya dace, nan da kwanaki biyar bayan anyi salla sai ku biyo bayanmu, dan ina son ku iso ne randa zamu koma zaman shari'ar". "Umarninka da cikawa shine abin jiranmu Insha ALLAHU" Iya abinda Iffah kenan ta iya ji ta shige. Lokacin da ya shigo dakin zai shirya tata fatan ya shigo da file din amma sai ya shigo babu komai. Kuma bai mata maganar ba. Amma koda suka kammala shirinsu suka fito Sultan da kansa yau ma da yayansa maza biyu da uwargidansa sukai musu rakkiya har airport Iffah harda kwallarta hakama Uwargidan Sultan abinka da sabon mata bayan shigarsu jirgi sun zauna tana a jikinsa yana lallashinta sai ga file din nan ajiye a gefensa. Ta danyi mamaki amma sai ta basar, sai dai zuciyarta na sake tabbatar mata da koma akan wa file din ya kunsa yanada matukar muhimmanci ga mijin nata. Jirginsu na dagawa babu dadewa barci ya kwasheta…... * KASAR RUMAN Duk da saukar dare sukai tako ina a airport din zagaye yake da matakan tsaro. Kai da gani kasan mai kasar ruman dinne da kansa zai sauka. Ta bangaren masu tarbarsu kuwa manyan masarautar ne masu fada aji. Ga wasu lafiyayyun motoci ababen birgewa ga mai kallo. Sosa barcine a idon Iffah dan yanzu kam bata da aikin da yafi wannan. Hakan yasa ta kasance a kusan rabin jikinsa lokacin da suke fitowa, Dole duk wanda ke wajen yay kasa da kansa cikin jin nauyi. Shika gogan nasu ko'a kwallar rigarsa rungume yake da ita hankali kwance yana daga musu hannu daya alamar amsa gaisuwarsu har zuwa motar da aka ajiye domin su kawai. Sai da suka shiga har aka rufe sannan hadiman da sukal masu rakkiya ke fitowa a jirgi suma. A wannan tawaga musamman ta matan Diwa ce kawai zuciyarta ke a tsarkakake game da nado labari, amma sauran duk yan daukar rahoto ne. Sai dai kuma basu samo yanda suke so ba sam kasancewar su/Iffah'r sun musu wahalar ma gani ba kamar yanda su Uwa sukai tunani ba. Tun daga airport har cikin masarauta jami'an tsaro ne, a cikin masarautar ma tarba suka samu da taima Iffah dadi, dan harda Malikat Haseenat da Daneen Ammarah da kanta. Sal wata da Iffahr bata sani ba amma suna kama da Daneen Ammarah sosai kuma tana kama da Jaddah. Haka kawai taji a ranta itace Daneen Waheeda da aketa fada. Lokacin da take dagowa da ga rungumar da taima Malikat Haseenat zata rungume Daneen Ammarah idanunta suka sauka kan wata kyakykyawar farar budurwa sol tana balla mata harara. Bata santa ba, dan haka ta dauke idanunta ta maida hankali ya Daneen Ammarah din cikin rashin damuwa. A hankali ta saketa ta nufi Daneen Waheeda da ke tsaye tana kallonsu kusa da Malikat Ashwaq fuskarta babu yabo babu fallasa. Gabanta ta rissina ta gaisheta tare da Malikat Ashwag din. Amsa mata tai da dan murmushin yake sakamakon kallon da Malikat Haseenat ta watso mata. Sai kuma ta nufi Malikat Bushirat ta rungume, itama dai gain kallon da ake musu ne yasata shafa kanta tana yake, Jasrah kam saita boye bayan Malikat Bushirat din dan da gaske kunyar Iffah take ji. Murmushi Iffah tai itama ta rungumeta, dan koba komai kafin faruwar hakan al ta nuna mata soyayya ta gaskiya.. Tuni shi Tajwar Eshaan ya shige ciki, dan haka itama Malikat Haseenat ta kama hanunta tana facin,"Kinga zomuje kema ki huta kunyi buda baki a jirgi babu nutsuwa". Da ga haka ta nufi ainahin sashenta da ita dan an sake masa gyara na musamman. Bayan wucewarsu abubuwa da yawa sun faru a cikin masarautar, ciki hard jajircewar Malikat Bushirat akan komawar Iffah sashenta. A zahirance dai babu wanda ya kawo komai a ransa game da hakan, sai Malikat Haseenat ce ma take gain Malikat Bushirat din na son hakanne da tunanin Iffah ta kanainaye mata Eshaan, ta kuma san sai dai Bushirat din tayi ta gama Iffah da Tajwar Eshaan sun riga sun gama zama abu daya. Ga tabbaci nan ma a yau ta sake gani, dan duk mai hankali da zai kalli Iffah'r a yau yasan tana tare da juna biyu. Komai nata ya canja, ga kyau data kara da budewa. Yanzun ma Malikat Bushirat na gain sun nufi can ta saki wani lafiyayyen murmushi tana fadin, (yes) a zuciyarta alamar akwai abinda suka kulla a sashen kenan. Ko dar Iffah bataji da komawarta sashenta ba. Sai ma farin ciki data tsinta kanta a ciki. Ga hadimanta duk an dawo mata da abinta, a ganinta ma ita wannan wata dama ce da zatai yakinta da kyau a yanzun. Wanka ta farayi bakinta dauke da addu'a, kasancewar duk tayi sallolinta tun a jirgi shirin kwanciya kawai tai ta haye gado abinta sai ko barci. Cikin barci take jin kamshinsa na sake shige mata hanci, a zatonta mafarki take, sai tai kokarin yin juyi abunta. Jinta jikin mutum a gaske ya sata bude idanunta da kyar. Akan kyakykyawar fuskarsa ta sauke idanun nata. Tashi tai a dan zabure ya rikota, maidata yay ya kwantar yana mai tura yatsunsa cikin gashin kanta, sai kuma ya matso da fuskarsa saitin tata ya daura goshinsa kan nata hancinsu na gogar juna. "Yaushe kazo?" Ta fada cikin muryar barci. Shiru kamar bazaice komai ba, sai da ya mula dan kansa sannan. "Dama zaki iya barci babu ni a tare da ke?". Kankamesa ta sakeyi tana sakin ajiyar zuciya, itama a hankalin ta furta, "Kawai dan banda yanda zanyi ne". "Toni gani nayi yanda zanyi ai". Ya bata amsa yana sake matseta cikin jikinsa kai kace amshe masa ita za'ai. Luf ta kwanta kuwa suna sauke ajiyar zuciya a tare. Sai kuma ya hade bakinsu a hankali. Da ga haka labarin ya sauya salo... Karfe uku nayi ya gudu, sai farkawa tai taga babu shi a dakin. Murmushi kawai tayi ta tashi zuwa bayi tai brush da tsaftace jininta ta fito. Madara mai dumi kawal tasha matsayin sahur. Duk da barcin dake cin idanun nata sai bata kwanta ba tayo alwala ta danyi nafilfili da karatun Alkur'ani. Bata tashi a wajen ba sai da tai sallar asuba, Tana idarwa kwanciyar ta sake yi, bata tashl ba sal azhar. Tayi mamakin barcin da tayi, amma kuma sanin yanayin da take ciki da rashin isasshen barcin da bata samu a Saudiya ba yasa ta fahirci akwai ramuwa dole dama. Tsaf tai shirinta cikin kyakykyawar abaya kamar ka sace ta ka gudu. Dama ga ko'ina ya sake fita da fitar kwarjini da kyawun haiba na ciki. Cike da girmamawa a gareta hadimanta ke zubewa Rasa gaisheta lokacin data fito. Nuni tai musu da su tashi, cikin sanyin da ciki ya haifar mata yanzu ta basu izinin mata rakkiya zuwa sashen Malikat Haseenat da ga nan su wuce na Malikat Bushirat. Da girmamawa suka arsa mata tai gaba suna take mata baya. Duk da akwal tazara a tsakaninsu bata shiga motar da aka ajiye domin ta ba tunda ta fito, A kafa ta taka hadimanta na take mata baya. Dolene ta birgeka, dan yanda ta fito da kafan ma sal ta kara kima a idanun hadiman. Ta ko'ina kuwa ta gitta hadiman ne ke zubewa mika gaisuwa, hannu kawal take daga musu fuskarta da dan murmushi dan sam bata daureta ba. Yayinda Amintacciyar hadimarta ke amsa musu da baki ita kuma. Tun kan shigowarta aka sanar da Malikat Haseenat da ke zaune Daneen Ammarah da Daneen Waheeda tare da ita. Sai Iftihal diyar Daneen Waheeda dake zaune a can gefe tana latse-latse a laptop. A nutse ta shigo bakinta dauke da sallama. Dan haka suka dago a tare. Sai dai kuma a hankali Iftihal taja sirrin tsaki da maida kanta ta cigaba da abinda take yi. Babu wanda ya jita, sai dai Iffah kam taga kallon da tai mata sarai. Amma tai kamar ma ita bata ganta ba ta nufi Malikat Haseenat da ta bude mata hannu fuska duke da murmushi alamar tazo gareta. Ita din ta nufa cike da kunya, ta durkusa a gabanta tana murmushi da gaisheta. Cikin murmushi Malikat Haseenat ta ce, "A'a kinga Hafidah tashi ki zauna keda ke fama da kanki, ALLAH dai ya raba lafiya". Sosai kirjin Daneen Waheeda ya buga, yayinda Daneen Ammarah ke murmushi kawai tana bin Iffah'r da kalion kasan ido, Bayan ta gaishe da su duk cikin girmamawa Daneen Ammarah ta nuna mata Daneen Waheeda. "Ga wata maman taki nan tazo kuna Saudiyya, nasan kin san dai sunanta da labarinta tun kafin yau". Fuskar Iffah cike da murmushi ta jinjina mata kai. Kafin ta kara gaishe da Daneen Waheeda din da zancen cikin nan va sata sumar zaune, cikin murmushin yake ta kai hanunta kan Iffah'r ta shafa. Daneen Ammarah ta sake waiwayawa ta nuna mata Iftihal da tai kamar ma bata san mi ake ba "Wannan yar uwarki ce ita kuma, sunanta Iftihal, itace first born a wajen mamanki. Tanada kanne maza har uku". Murmushi kawai Iffah tai sai dai batace komai ba kamar anda itama Iftihal din ko dagowa batai ba. Yanda tai din kuma sai ya zafi Daneen Ammarah. Ita kanta malikat Haseenat dai tayi shiru ne amma fuskarta ta nuna jin zafin abinda Iftihal din tayi. Ita kam Iffah ko'a kwalar rigarta, hankalinta kwance suka cigaba da hirarsu da Daneen Ammarah da Jaddah...✍️ DAUDAR GORA Book 2 70 ....Sai da tai sallar la'asar a sashen Malikat Haseenat sannan ta baro, fuskarta dauke da murmushin abinda take kullama Iftihal. Dan ta dau alwashin sai tayi dana sanin zamanta a masarautar nan duk da gidan kakanninta ne. Da ga nan sashen Malikat Bushirat ta nufa, sai dai ta samu wai bata nan tana a sashen Shahan-shan. Hakan bai bata mamaki ba, ba kuma ta nuna ya dameta ba ta koma sashenta ita da tawagarta. Sai kusan karfe biyar ta nufi sashen Tajwar Eshaan.. *** A lokacin da Iffah ke nufar sashensa a lokacin shi kuma yake fita ta kofar sirrinsa zuwa sashen Malikat Haseenat. Cikin sa'a kuwa ya sameta ita daya a dakin. Kyawawan idanunta na tsufa ta zuba masa har ya kammala sakama kofar key ya cigaba da takowa gareta a nutse. A hankali ya kai zaune gabanta ya tankwashe kafafunsa. "Barka da yamma Jaddah". Ya tada a kan lips a dan fisge kamar baya so.Murmushin ta sakar masa cikin yar tsokana ta amsa da "Barkan ka dai Abbien unborn". Idanunsa ya dan waro mata na alamar mamaki, sai dai kuma bai iya cewa komai ba dan yama rasa bin fadar. Dariya Malikat Haseenat tayi mai kayatarwa, tace, "Ni dai bana fata ko mace ko namiji da za'a haifa su gado min wanna miskilancin naka Hafidi. Ace magana a bakin mutum amma furta ta ta zama aiki", Kasa ya dan yi da kansa kawai yana murmushi. Kafin cikin son kauda maganar ya ce, "Amm Jaddah! Kamar yanda kika bada shawara nayi amfani da ita. Ani musu gwaji ta wasu abubuwan hallitar jikinsu kamar gashi da yawu jini batare ma da sun san duk muni hakan ba. Ita na bada nata, Sayeed Tasadduq-Husain kuma ya samomin na iyayen nata dan kamar yanda na fada miki dama tunda na saka a kaudasu a kasar shine yay aikin kuma shi kadai suka sani ya kuma san inda suke a yanzu haka ma". Cike da zumudi Mammah tace, "Ya ake ciki? Mi result din ya nuna kuma?" Sai da ya dan ja iska kusan minti daya kafin ya nisa. "Al'amarin gaskiya yazo da rudani zance ne koba haka ba oho. Result din sun nuna shi Mahaifinta ne,amma macen ba itace ta haifeta ba". "What! Kamar yaya kenan?". "Shine na kasa fahimta why Jaddah. Tun a Saudiyya a rikice lissafina yake. A daidaiton kwanakin watan haihuwarta da na yarinyar Mamy dake rubuce kwana uku ne, sannan tambarin da ke nan a ajiye iri dayane da na jikinta, ita waccan ta mutu a randa aka haifi ita Fhareedahn. Sai nake ji kamar akwai abinda ya kamata mu sani, amma idan na auna yiwuwarsa ni a karan kaina sai naji abin yazo ba daidai ba". "Kai mi kake tunani akan hakan?". Nan ma sai da yay jima kafin ya bata amsa. "Itama Mammy a mata gwajin halitta tare da ita. Kinga muma sai mu samu nutsuwar yarda ba ita bace, ko itance. To amma ya akai ta samu tambarin zuri'armu bayan mahaifinta bashi da alaka da wanna masarautar? Sosai nakejin kaina a rikice a duka abinda nake tunani da fatan ya tabbata". "Tabbas al'amarin akwai rudanin, rudanin kuma suna da yawa, dan inhar babu alaka tsakanin wannan yarinya da Arnmarah to tabbas tana da alaka da wani a wannan masarautar kuma dole ne mu sani. Sai dai dabi'un yarinyar na rikita mun lissafi Eshaan. Dan babu abinda ya banbanta da na Ammarah tana a irin shekarunta. Sai dai ni nasan diyar Ammarah ta rasu tunda da hannuna na mata wanka da hadata aka kuma kai ta aka bizne". "Kamar yanda na fada miki Jaddah akwai abinda ke boye. Dan da gaske yarinyar nan akwai aljanu a kanta wilhy. Naga alamominsu da yawa tattare da ita, dan a wan lokacin ita kanta aljanar ma nake kallonta". Dan murmushin karfin hali Malikat Haseenat tayi, amma a ranta fal yake da rudani... Sun cigaba da tattaunawa har zuwa gabanin magriba sannan ya baro sashen domin zuwa yay shirin massalaci….. A bangaren Iffah kam data nufi sashensa kai tsaye kitchen ta nufa, inda masu kula da abincinsa ke ta kaikawon lissafin abinda zasu shirya masa na buda baki. Tana shigowa duk suka zube kasa suna kwasar gaisuwa. Hannu kawai ta daga musu, kafin tai zaran bibiyar duk abinda suke shirin yin da kallo. Duk lissafinsu sal da ta wargaza ta shimfida nata, karshe ma ita ta koma shirya abincin da taimakonsu. Wannan al'amari ya matukar basu mamaki kam, dan ko'a tarihin masarautar basu taba jin a inda wata Zawjata- almilk ta shiga kitchen girka abinci ba koda na Shahan-shan ne kuwa. Sai gashi a yau Itfah ta ajye tarihin, A matukar gajiye suka kammala aikin, tayi tibis da ita saboda a yanayin da take, duk da dama cikin nata nada saukin laulayi da tsurfan abinci. Sannan ita dai bazatace ga wani waje na mata ciwo ba mai jigatarwa. A dining room din ma tana tsaye suka shirya komai, aka kara turaren wuta ko ina ya dauka harami. Bayan duk wucewarsu bedroom nashi ta nufa, ta dinga binsu daya bayan daya tana lekawa har sai da ta shiga a inda ya kwana. Kamar ko yanda tai hasashe ba'a gyarashi ba, tunda ita da kanta ta hutar da amintaccensa tun kan su wuce. Duk da yanda take jin kanta haka tai dauriyar gyarawa, sannan ta shiga toilet din tayo wanka shima bayan ta tsaftacesa Bata da matsalar kaya anan kam tunda tasan tabarsu tunkan su tafi ba, tako shirya cikin wandon jeans 3quater blue da karama roga mara nauyi fara tas, sai hoton heart da akayi babba a gaban rigar. Kayan sun mata kyau. Tana barbaza gashinta da haushi na rashin son a taba mata shi ya shigo dakin da sallama. Dan turus yayi yana kallonta irin na rashin tsammani. Dan a yanzu haka da yake shigowarnan da ita a ransa ya shigo, kewarta yake ji sosai, dan duk yau bai ganta ba, rabonsa da ita tun daren jiya da ya kai mata ziyarar sirri sashenta. A hankali ya cigaba da takawa cikin dakin yaje gabanta ya tsaya. Jitai kawai an tura mata yatsu cikin gashi. A firgice ta dago dan ko kadan bayaji motsin shigowar tasa ba. Cikin juna idanunsu suka shige, kowanne cike da kewar dan uwansa kamar sun hada watanni basu hadu ba. Itace ta fara janye nata a slowlv. kamar mai in kunvarsa ta maida kanta kasa ta dukar. Numfashi ya dan furzar kadan, tare da dukowa ya zare ribbon din hanunta ya saka cikin tsintsiyar nasa hannun kamar maisa bangles, sai kuma ya maida duk hannayen biyu saman kanta ya tattaro gashin a tsakkiya ya dare mata. "Thanks you". Ta fada cikin siririyar muryarta da ke ratsa masa jiki, yasan tsaiwarsa a wajen bazata hafar masa da da mai ido ba. Dan haka ya rabata ya wuce cikin tafiyar tasan nan daddaya dan azuminsa ya isa lafiya. Da kallo ta bisa har ya shige bayi, sai kuma ta saki sassanyar ajiyar zuciya ta mike. Closet dinsa ta nufa kasancewar akwai finger print dinta yanzu akai itama. Lallausar jallabiya kalar maroon ta zaba masa, tare da alkyabba irin ta sarakan saudiyya. Fitowarta dal-dai da tashi. Kallo daya ta masa ta dauke kai dan har yanzu ta kasa sakewa da kalion wanna jikin nasa. Kanta a kasa ta karaso gabansa, karamin towel da ke hannunsa ta amsa, babu musu ya sakar mata, sai da ta lumshe idanunta sannan ta fara tsane masa jikin. Dan garetan murmushi ya saki idanunsa kan kyakykyawar fuskarta harta kammala. Man da yake amfani da shi ta ajiye zata gudu ya rikota a slowly yaNmaidota baya. Sai da ya gama kare mata kallo da gaNsama har kasa sannan ya dire kan fuskarta da idanun ke lumshe. A can kasan makoshi ya furta, "Shi man wazai shafa?". Batare data bude idon ba ta ce, "Ka tayani". "Naki wayon". Ya bata amsa yana maidota gabansa da kyau. Dan murmushi tai zatai magana ya ce mata, "Shilli!!!" Shiru tai ta hadiye abunta. Shi kuma ya daura mata man a kan hannu. "Oya zan makara sallar magrib". Babu yanda ta iya dole ta shafa masa. Kirjinta sai bugawa yake da sauri-sauri dan da gaske jikin nan nasa toro yake bata. Ta rasa mike birge maza suke maida kansu haka ita kam. Rashin mafita ya sa dole har shiryawa sai da ta taimaka masa wajen yi. Tana kammala saka masa turare ya kamo fuskarta cikin tafukan hannunsa ya sumbaci goshinta da idanunta da karan hancinta, sai kan habarta. Sassanyar ajiyar zuciya ta dan saki. Bata ankara ba kawai ta gansa duke gabanta ya dan daga rigarta ya sumbaci cikinta. Da ga haka ya wuce abinsa cikin dakewa kamar bai aikata komai ba. Da kyar ta iya bude ido ta bisa da kallo, dai-dai zai fice ya dan tsaya a jikin kofar tare da juyowa suka hada ido. Kauda nata tai da sauri, shi kuma ya dan sakin murmushi a iya lips da fadin, "Idan kika bar sashen nan kafin na dawo sai na hukuntaki". Da ga haka ya fice ya barta da murmushi a fuska.. Bai shigo gida ba sai da aka idar da har sallar isha'in da asham, dan bayan idar da sallar magrib ya sha ruwa da dabino a can. Da ga haka yay zaman karatun Alkur'ani. Kowa yasan hakan yake yi a duk shekara, dan baya shigewa sai bayan an kammala salla baki daya kamar yanda yake yi idan ba'a azumi sai ani har sallar isha'i. Bisa rakkiyar su Sayeed Fayzul-haq ya dawo sashensa. Hadiminsa kam tun da yaji a bakin masu girki Zawjata-almilk tazo itamace taima Shahan-shan girki da kanta baiyi gigin biyosa har nan ba sai ya lake a 3 floor din. Babu kowa a faion sai sanyin ac da kamshi mai dad ba irin wanda ya bari ba. Bedroom ya nufa domin rage kaya, zuciyarsa na raya masa tama gudu kenan bataji gargadinsa ba. Sai dai yana murda handle din kofa itama tana budewa, kusan cin karo sukal da juna ALLAH dai ya kiyaye taja baya da sauri, sai kuma ta kusan faduwa sai da ya rikota jikinsa. A jiyar zuciya ta sauke cike da shagwaba ta ce, "Thanks you" Maimakon amsa. mata godiyar cak ya dagata bisa kasa suka koma dakin. Tana watsal-watsal da kafafu da rokon ya sauketa ita yunwa takejl bai ma saurareta ba sai da ya direta inda yake bukata ya rufe bakin tsiwar dan iya yaren da zuciyarsa da kwakwalwar ke bukata kenan kawai…….✍️ DAUDAR GORA Book2 71 _..Taji a jikinta kasancewar da gaske yunwar take ji,dan itama ruwan kawai tasha da dabino sai dan madara mai zafi da take matukar so a yanzu tunda akasha ruwan. Ta hakura ne tai salla dan tasan in har taci abu da yawa to tabbas bazatai sallar ba barci zatai. Duk yanda take wani tuttura masa baki na shagwaba bai kulata ba, da taimakonsa sukai wanka a tare sannan suka fito daning room din. Sai da ta tabbatar ta gam harare-hararen kwanikan abincin tsaf duk da tasan bayan sun ajiye babu mahalukin da ya sake shigowa nan sai shi bata aminta ba kai tsaye. Komai a tare ta hada musu, hatta shayi a kofi daya ta zuba duk da kasancewar dan mitsitsin nanne na larabawa. A haka suka dinga cin abincin kowa na ciyar da dan uwansa har sukaje iya inda suke bukata. Falo suka dawo, yana kokarin kuna Laptop din tasa ta fama ta je ta haye cinyarsa tana tura baki. "Wai nikam kodai computer din nan kishiyata ce?". A yanda tai maganar ma sai abin yaso bashi dariya. Amma dai ya gimtse bai yi ba ya dai tsareta da idanunsa kawai. Lumshewa yay ya dan bude tare da tallafo fuskarta cikin tafin hannunsa. A kasalance ya furta, "Ko dai ke ce ke kishi da ita". '"Ai dai banyi laifi ba". Murmushi kawai yay dan bashi da abin cewa kuma.Sai kawai ya dauka remote ya kunna musu television ya kamo babban gidan tvn kasar. Basu fara labarai ba, sai wani shiri mai suna * ZAUREN MUSULUNCI_*. sannin muhimmancin shirin yasa bai canja ba ya bar musu nan, itako harda gyara kwanciya a jikinsa ta lafe kamar wata mage. Shima sai ya gyara mata yanda zataji dadì sosai hannunsa saman cikinta da duk duniya a yanzu babu abinda yafi so da bukatar gani kamar girmansa da haihuwarsa. Koda wani takaici ya tuno a ransa daya tuna Iffah'r sa nada cikin gudan jininsa sai yaji nutsuwa ta saukar masa.. * -* Washe garin aka tashi da fatan gain watan salla,Iffah na zaune tana karatun Alkur'ani bayan idar da sallar asuba Tajwar Eshaan ya dawo da ga massalaci. Komawa yay ya dan kwanta dan barcine a idonsa sosai. Ta idar itama tana shirin hawowa gadon yake sanar mata sakonta ya iso yanzu Sayeed Fayzul-haq ke sanar masa. Fasa kwanciyar tai cike da doki ta mike ta hau shiri, shi dai kallonta kawai yake dan ya santa da barcin tsiya amma da ga cewa sakonta ya iso ta fasa yi. Ganin sauri-saurin nata yay yawa a hankali ya furta, "Madam a hankali karki jamin asara abuna baiyi kwari ba fa". Ita kunya ma maganar ta bata, dan haka ta juya masa baya tana rufe fuska. Shima sai ya dan murmusa kawai ya lumshe idanunsa. Kirtsawa ta karasa yi ta zo gaban gadon ta manna masa sumba a goshi. Hannu ya kai zai damkota ta zille. Murmushi yayi da kara gyara kwanciya yana fadin (Fitinanniyar yarinya) a zuciyarsa….. Duk da safiya ce sosai tuni kayan da aka shigo da su cikin manyan motoci kusan goma masarautar ta dauki dumi. Kowa jira yake ya ga da umarnin wa aka kawo kayan, dan abune dai sabo da ba'a san da shi ba, ga kuma wasu kayan da suka dan fitgito sun nuna suturu ne ma. Tuni fitowar Iffah da ga sashen Tajwar Eshaan Sayeed Fayzul-haq da amintaccensa biye da ita kallo ya koma sama, sal kuma ga tawagar matasan masarautar da ta saka suka mata aiki a wancan karon ma sun fito, a gabanta duk sukal rankwafawar gaisuwar girmamawa. Ta amsa musu itama da kulawa fuskarta da murmushi har da yar tsokanarsu wai kwanan nan zata fara saida form din aurar da samarin masarautar ta ga sun fara yawa. Dariya suka shigayi da barkwancin nata. Harda Sayeed Fayzul-haq da ke jin kaunar yarinyar, gata dai karama amma da halin manya, manyan ma sai an tona. Haka ma amintaccen hadimin Shahan-shan na jin kima da girmanta, dan yanda take kula da shugabansa kawai da sakasa farin ciki ma abin a jinjina mata ne. Shi baya ma ganin karancin shekarun sam sal wata kimarta da girma irin wadda yake kalion Shahan-shan da ita. Ta musu bayani akan kayan suma da za'a rabasu kamar yanda aka raba kayan abincin azumi ne. Akwai kuma kaji da shanu suma zuwa yammaci zasu isa. Sai dai su baza'a kawosu nan ba a kowace jaha aka samar da masu kiwonsu aka siya idan kowane wakili yaje inda zai raba kayan da aka bashi zai amsa. Sai kuma wanda za'a rabama hadiman masarautar suma da nasu daban, sukam harda kudi wanna kuma Sayeed Fayzul-haq ne zai bada su sakone da ga Shahan-shan da kansa Abdul-Shakhur in Khairul-Bashar shugaban tawagar ya share kwallar da suka ciko masa ido. Cike da girmamawa a gareta ya ce, "Lallai ke alheri ce garemu gimbiyarmu. Ke haske ce mai haskaka fararen fitulun da ke zagaye da daular ruman. Kasancewarki damu sake buda mana sanin wanene adalin shugabanmu yake da kyawawan halayensa a koda yaushe. ALLAH ya kara miki daraja, ya albarkaci rayuwarki data shugabanmu, ya zagayeku da kariyarsa da ni'imominsa. Yay riko da hannayenku ya baku ikon sauke nauyin al'umma da adalci. ALLAH ya bamu ikon muku biyayya ya karemu zaginku koda a bayan idanunku. ALLAH ya karya makiyanku koda jininmu ne ya azurtaku da zuri'a masu irin kyawawan halayarku da dabi'unku. ALLAH ya jika magabata, wanda suka rage ALLAH ya rabaku da su lafiya... Haka ya cigaba da jero addu'oi sauran a amsawa da Amin tare da hadiman da suka zagayesu cike da farin ciki. Iffah kam sai taji har hawaye na ciko mata idanu. Tabbas babu abinda ya kai kyautatawa dad da soyayyar mutane. Da ace dan adam ya gane da ya kasance mai kyautatama mutane sabanin munana masu. Kyautatawa na bada muhimman abubuwa uku a lokaci guda. *_DARAJA. SOYAYYAR MUTANE. SANNAN LADA A WAJEN UBANGIJI_* Cikin kankanin lokaci masarautar ta harmutse, bakin kowanne hadimi ka kalla a washe da farin ciki musamman idan ya kama yan kudadensa da kayan sakawa kusan kala biyar uku a hannu. Ga iyayen kaji da shanu an zube musu na girkin salla. Ga albishir na basu damar yin shagalin bikin sallarsu kamar yanda kowa keyi. Harda damar yin gyaran jikinsu matsayinsu na mata Iffah tabama matan, dama albishir din kawo masu gyaran jiki €ikin masarautar saboda hadimai matan kawai. Kai jama'a harda masu kuka, kaunar Iffah kam da Shahan-shan din kansa ba' magana a zukatansu. Sai sukejin kamar an yanta rayuwarsu ne da wani haske na musamman a yau din. Ba cikin masarautar ruman kawal ba. A cikin al'ummar. kasa ma duk wanda ALLAH ya tsaga da rabonsa a kayan' nan ya tsinta kansa a farin ciki mara musall. Badai ta wadata kowa da kowa ba. Amma ta ragema was radadin talaucin da suke ciki. Ta faranta ran marayu marasa iyaye. Duk da alkairi ne na sirrince da akaki bama yan jarida damar sani sai gashi ya fita karar wata amsa kuwwa a katafen yada labarai, Ya koma latest topic na wanna ranar harma da washe gari. Dan cikin aminci, UBANGIJI a ranar akaga watan salla washe gari aka tashi da farin cikin zagayowar wanna rana. Inda karfe tara dal-dai Shahan-shan da Kansa ya jagoranci sallar idi a massalacin Masarautar da mutane kasar suka ziyarta ta ko'ina a jar, harma abin ya bada mamaki, dan duk da ana cikashi dama duk shekara sai gashi a wannan shekarar ya ninka da ninki mai ban mamaki,. Talakawa da yawa sunzo cikin Dahab City yin salla domin kawai suga Shahan-shan.(Haka rayuwa take, duk kasancewarka mai mugun hali ko wanda za'a gogama bakin fenti da kayi alkairin da yay shura tsakaninka da ALLAH badan duniya ta gani ta fada ba ko a yaba maka sai kaga ALLAH ya saka soyayyarka a zukatan wadan nan mutanen dake aibantaka da kyararka a baya. Yan uwa mu dage da alkairi domin ALLAH, idan ka cire Naira dari a cikin dubu da ya baka sai ya sakama sauran albarka ya kuma daga darajarka. Dan shi alkairi da gaske danko ne baya faduwa kasa banza inji hausawa. Dan ko yayan cikinka kaima shi sake kaunarka suke, hakama iyayenka) Tajwar Eshaan yayi addu'oi masu ratsa zukatan bayan idar da salla. Hakama lokacin khuduba kalamansa masu ratsa zukata ne da hikima a cikinsu da mutare duk jikinsu yay sanyi da yanda suke kallonsa a baya. Bayan kuma kammala addu'oin yay wani dan gajeren nasiha da Fatan alheri ga kasarsa da ma al'ummar kasar da musulman duniya baki daya. Ya rufe da musu Barka da shan ruwa. Wannan jawabi a Tajwar Eshaan Ibn Haysarn Abdul-majeed Ally Qutb shine ya dinga amsa kuwwa a kafafen yada labarai, masu fashin baki nayl talakawan kasa da basu samu halarta ba nayin nasu suma, *Duk gayun da Iffah taci domin kayatar da zuciyar Maleek dinta bata samu ganinsa ba har sallar zuhur. Bataji haushi ba, sal dal ta kagu su hadun. Duk da itama da kanta tai masa shirin fita sallar. Yayi matukar kyau kamar wani dan saurayin dawusu (lols 😉😂)) harda fada masa ita why kamarma ya fasa kishin fitarsa a kalle mata shi takeyi haka. Amintaccensa da ke jinsu (okacin da take bashi shayi sai kasa ya karayi da kansa kawai yana murmushi. Bayan ta idar da sallar azhar ta fito domin zuwa gaida Jaddah da Malikat Bushirat da ya kasance dole tayi. Sai lokacin ta fahimci yanda masarautar ke cike. Ashe dole ne duk wani Tajwar a sauran jihohi sai yazo a yau din yayma Shahan-shan barka da shan ruwa, Hakama manyan attajirat da masu fada ajin kasar da dattijai. Zasuci abincin salla da Shahan-shan su kuma tattauna matsalolin kasa da shawarwarin magancewa. Gaba daya sai Iffah taji ta Kara tausaya masa. Dan lallai mulki ba wasa ba, yanda ta sanshi bal son hayaniyar nan yana can cikin takura ne. Sashen Mallkat Bushirat ta fara nufa yau tawagarta zagaye da ita. Kowa ya kalleta sai ya sake kallo dan kyawun da tai cikin walliyar sallar tata mai tsananin kayatarwa da daukar idanun mat kallo. Ga kyawu da cikin jikinta ya sake sakatayi kamar ka saceta ka gudu. Tako ina hadimar da jami'an tsaron masarautar gaisuwa kawai suke mikawa. Itako fuskarta kawace da murmushi mai sanyi da ke sake saka kaunarta a zukatan talakawan nata masu jin yanzu kam babu kamarta a cikin masarautar bayan Malikat Haseenat da itama ta kasance adalar shugaba…..✍️ DAUDAR GORA Book2 72 .....Cike Iffah ta samu sashen Malikat Bushirat da danginta da sukazo mata Barka da salla. Hakan ya mata dadi, dan duk wani wanda ke da alaka da Tajwar Eshaan a rayuwa tana ganinsa da kima da mutunci. Cikin mutuntawa suka tarbeta, dan sakonta da na Tajwar Eshaan yaje garesu har gida a jiya. Duk da suma sun kasance mafi yawansu basu nema komai na rayuwa sun rasaba. Amma alheri dadine da shi, musamman da ya kasance wani abu bai taba zuwa garesu ba ace daga dan yar war tasu kuma Shugabansu. Abinda ya basu mamaki da tabbatar da an samu sauyi yar uwar tasu ma sai da suka zo yanzu duk suke mata godiya har tasan Tajwar Eshaan din wai ya musu aike suma. Murmushin yake kawai ta musu, dan tun jiya dama a tunzure take da abinda Iffah'r tayi. Koda Iffah'r ma ta gaisheta cikin yake ta amsa gain yan uwanta duk sun zuba mata ido.Amma zuciyarta tafasa take da yanda suke ta sanya albarka da yaba abinda Iffah'r tayi, tare da tabbatar da shugabansu kuma dansu yayi dace da mace ta gari mai buda masa hanyar alkairi. Sukam suna farin cikin shigowarta cikin ahalinsu. Wasunsu harda kiranta gagara badau wadda tafi karfin duk wani shedanci a azzaluman masarautar. Iffah da mur mushi kawal ta dingayi kasa-kasa. Tayi zaman kamar awa guda sannan tai musu sallama akan zuwa anjima zata aiko azo da su su gashe da Shahan-shan. Wannan zance nata na karshe ta sakasu sake shiga jin dadi, dan a cikinsu ma akwai wanda rabonsu da Tajwar Eshaan din tun kan a bar kasar da shi, Kuma uwa daya uba daya suke da Malikat Bushirat din, Sun baje babin hira da sanya albarka ga Iffah Jasrah ha kara basu labarinta. Babbar yayar su Malikat, Bushirat din da suke kira Akia Badiha cikin nuna jin dad) ta furta, "Al ni babban abinda ma ya sakani farin ciki fiye da komai wannan cikin na jikinta, dan zamu samu tsatson alkairi a zuri'armu, ALLAH dai ya raba lafiya". Kusan a tare duk suka dubeta. Malikat Bushirat da ke kishingide tana shakar iska da fesarwa harda zabura. Jasrah ce tai karfin halin fadin, "Akia wal waye mai cikin? Kin samu a rudan!" Baki ta Kara washewa, cikin barkwanci ta ce, "Aw to tunda baku ramfo ba ku bada goron albishir tukkanna. Kudi sabbi kal-kal Jasrah ta sauke cikin tafin hannun Akia Badiha, cike da zumudi ta ce, "Muna saurarenki". "Uhm wadan nan din ma babu laifi, sai dai da kanku ma zaku karo idan kunji. Insha ALLAHU muna gab da samun Miran, ko Daneen a wannan masarautar. Dan da alama Zawjata-almilk tana tare da shigar ciki". "Whattt!!!!!!". Suka fada cikin hada baki da hun murna. ALLAH ma ya sosu hadimai yau an basu freedom din kansu sai dai-daiku dakan dan shigo dan an bukaci ganinsu. To su sunama a falon Malikat Bushirat din nacan ciki ne iya su dan yau ranar baje kolin hirar zuminci ce. Wani irin diff-diff kirjin Malikat Bushirat keyi, zuciyarta kamar zata faso ta fito. Ga kanta da yay wani irin azababben sarawa, sai ta fara ganin falon na juya mata da su da ke ciki. Tashi tai da sauri ta nufi daki ta kulle kanta. Tana gama sakama kotar key ta daura goshinta jikin kofar tai wani irin fashewa da kuka mai tahowa irin gaba dayan nan mutum yaji kamar numfashinsa zai bar gangar jikinsa.. Bama su fahimci halin da take cikiba su balle tashinta, sunata murnarsu, sai da mai bima Malikat Bushirat din ta juyo tana magana idonta ya sauka a wajen zamanta wayam. Bata kawo komai a ranta ba a tunaninta duk murnarce ta kebe yin abunta dan sun san yar war tasu da shegen kasaitar son mulki kamar itace Shahan-shan din ba matarsa ko uwa ba….. *A bangaren Iffah kam tana sashan Malikat Haseenat, taso ta samu Iftihal dan yau tayo mata tanaji sai dai aka samu rashin sa'a wai ta fita ita da Husam babban dan Miran Jasim. Anan ma Iffah ta jima sai bayan sallar la'asar ta baro, sunata shan hirarsu ita da Mammah da Mammy. Daneen Waheeda dai bata saka baki sai lokaci-lokaci... Tattauna zancen cikin Iffah ga zuri' ar Malikat Bushirat ya sa ya fito har ya fara yawo a cikin masarautar. Dan danan fa aka fara wani karamin bikin murna da sam Iffah da Tajwar Eshaan da sai da akai sallar la'asar ya samu kansa basu sani ba. Hasalima suna can manne da juna abinsu hankalinsu kwance da jin tamkar suma kadaine a cikin duniyar (Su bily duk an mutu ashe 😏🤔👹). A kankanin lokaci zancen ya cigaba da shiga lungu da sako. Da ga masu shiga farin ciki sai masu shiga rudani da tashin hankali dan abune da basuyi zato ba... "Aiko lokaci yayi da zaki bijiro da zancen auren nan Waheeda". Malikat Ashwag ta fada cikin tashin hankali bayan gama sauraren Daneen Waheeda. Daneen Waheeda da gaba daya ita tasan kunar da zuciyarta ke mata ga rikicin Iftihal taja numfashi mai matukar zafi. "Hakane Ashwaq, amma kin san kafiyar Mammah, ga shi Ammarah sam nunawa ma take tafi son yarinyar nan sama da Iftihal din, taya kike ganin hakan zai yiwu cikin sauki?". "Yuwuwarsa daya ce, mu nema su Sayeed Tasaddug-Husain da zancen shi da su Sayeed Hifzur-rahaman, da Sayeed Fayzul-haq tunda sune dai iyaye a gidan nan, duk da yake shugaba suma ai sama suke da shi, kuma dama a duk aure-auren nasa ai sune dai Mammah ke sakawa gaba ko da su Jasim". "Eh hakane, kema kin kawo shawara mai kyau.Yaushe kike gain zamu samesu?". "Ko zuwa anjima dan ba'a bori da sanyin jiki. Bara na kiga mu nema ganawar sirri da su, da ani ishan'i insha ALLAHU sai kawai mu zauna"... (To koyaya zata kasance,Iffah'r mu ga Abar nan na tunkaro ki ki hira 😝😢) Su Malikat Ashwaq sun gana dasu Sayeed Fayzul. haq, sun kuma tattauna sosai da sauraren abinda Daneen Waheeda tazo da shi, shi dai Sayeed Fayzul- haq ma baice komal ba. Garama Sayeed Hifzur- rahaman yace su basu lokaci zasuyi magana da Mammah a kuma jira Sayeed Tasaddug-Husain ya dawo daga Umrah gobe insha ALLAHU. Daga haka suka rabu. A lokacin da suke tasu tattaunawar Iffah na can taima yan wan Malikat Bushirat rakkiya ga Shahan- shan da ya sakko hawa na biyu. Ya nuna farin cikin ganinsu shima, dan bai taba zama irin wanna dasu ba tunda yasan kansa, ballema yanzu da yake a shugaba. Suma duk wanda ka kalla zaka fahimci tsantsar farin ciki a tare da shi. Sun kuma ji dadin yanda ya dan sake dasu yay hira duk da maganar daya biyu ce dai. Sai dai abu mafi kayatar da su yanda ya girmamasu ya mutunta su. Sai kuma komi yake idonsa aka matarsa Iffah. Kusan zaman awa daya da rabi sannan sukai masa sallama... Bikin sallah ya cigaba da gudana masu ziyara nata zuwa gaishe da Shahan-shan. Yayinda Malikat Bushirat ke a birkice, gaba daya Jasrah tama kasa gane kanta. Tayi kiranyen uwa har ta gaji amma taki zuwa. Sai taji komai ya karasa kwace mata. A kwana na uku da salla sai da doctor ya dubata. Jasrah dai tai shiru da bakinta babu wanda ya sani gudun kananun maganganu. A washe garin cikar sallar kwana hudu Maganar komawa zaman kotu taje kunnen kowa, dan haka wasu suka kasance cikin zullumi da tsoron karfa garin tone-tone ga su Miran Jasim suma tasu allurar ta tone galma.. * KOTU* A yanda zaman shari'ar ma ya cika yau sai ya baka maraki. Dan tarin matasan nan a yanzu da Iffah ta dunkule waje daya bisa jagorancin Sayeed Fayzul- haq kaf dinsu sai da sukazo. Abinda basu taba yi ba tunda ake zaman shari'ar. Hakama wasu a mata da mazan masarautar sun karu. Kotu dai ta cika tai hani'an masha ALLAH. Tsabar yau Iffah da jin kai ta shigo da yafi na kullum ma Shahan-shan ya rigata zuwa. Dan kusan itacema karshen shigowa da hadimanta. Nana kowa ya zuba mata ido harda uban gayyar ta cikin glasses din da ya boye idanunsa. A ransa kam kara jinjina fitinar yarinyar nan yake. Tafa rigashi kammala shiryawa amma tsabar taso neman magana sai ta gudu sashenta har sai da ya rigata zuwa kotun. Yau ma sai da taje ta gaida Malikat Haseenat da su Daneen Ammarah. Hakama Malikat Bushirat da tai wani irin ramar fita hayyaci da mai lurane kawai zai fahimta, dan abin dariya yau harda eyeglasses a idonta itama, da alama akwai abinda take boyewa. Hannu kawai ta dagama Iffah a maimakon amsa mata gaisuwa, ko a kwalar jikin Iffah tama mike abinta tana takun nan nata na neman magana. Bayan nutsuwa kotu yanda ya kamata aka shigo da su Miran Arshaan. Sunyi duhu sosai sun rame. Ba duka ba zagi babu harara zaman duhun nan kawai da suka saka Iffah ciki a wancan karon da bakin cikin kamar su a cikin kurkuku ya maida su haka. Yan kananan magana ne suka fara tashi a kotun har sai da aka tsawatar. Ameera Haifah dai sai faman rufe fuska take da mayafi, gashi yau kuma harda iyayenta itama a kotun dan habanta yazo akan maganarta tun washe garin rufesu amma bai samu gain Tajwar Eshaan ba. Bayan kotu ta sake nutsuwa Sayeed Hanifud-Din ya karanto karar haka. "Har yanzu dai muna kan zaman shari'a ne akan Miran Jasim da ya bada madara mai dafi ga Zawjata-almilk ta shayar da wanda suke son halakawa. A wancan zaman kotu ta bada damar kawo bokansu a zama na gaba, sai kuma aka samu wani al'amarin akan Miran Arshaan da Ameera Haitah, wanda yay dalilin kaisu kurkuku suma, zaman makwaftakar Miran Jasim da Miran Arshaan ta zakulo wasu sabbin abubuwa masu ban mamaki da ya karata ace an fara saurare a wannan shari'a kafin a cigaba da yinta. Idan adalin shugabanmu ya bada damar hakan to". Hannu Shahan-shan ya daga a hankali da yin alamar an baka dama. Godiya Sayeed Hanifud-Din yayi sannan ya kalla shugaban jami' an tsaron. Mikewa shugaban jami 'an tsaro yayi, yayinda Miran Arshaan da Miran Jasim ke kallon juna a rikice, dan sun dai san karn kalar tabargazar da sukaira juna da tone-tonen tsiyatakunsu a cikin kurkukun. A hankali Iffah ta saki wan irin sassanyan murmushi. Cikin Sa'a kuwa sai a idon su Miran Jasim din kamar an kirawosu su dubeta........✍️ 😂Gaskiya Iffah virus ce 😆🚴🚴🚴🚴 DAUDAR GORA....!! Book2 Chapter: 73 …...…..Kallon da Iffah ta musu shi ya kara girgiza zukatansu, sun kuma tabbatar akwai abinda shegiyar ke kullawa. Sannan recording din nan da akai musu batare da sanin su ba in fa har aka budeshi kowa yaji anan akwai matsala. Dan basa raba dayan biyu zama a iya kashesu a cikin kotun nan kuwa. Saboda basa tantamar duk abinda suka yi na tsiyatakunsu a cikin masarautar za'a samesa a ciki. Miran Jasim da yasan kwabarsa sai tafi ta kowa ruwa ya fashe da kuka yana girgiza kai. Ya fahimci idan har ya mika wuya da kansa zai iya samun tausayawar mutane ma. llai kuwa tsitt kotun tayi, yayinda Shahan-shan ya dan jin jinama Sayeed Hanifud-Din kai. Ya fahimci mi yake nufi, dan haka yay saurin dakatar da shugaban jami'ai da ke shirin playing recording din. Dakatawar kuwa yay cikin nuna girmamawa. Kotun tai shiru aka zubama Miran Jasim idanu. Shi kansa Miran Arshaan sakare yay kawai yana kallonsa dan ya kasa fahimtar ma'anar kukan. Iffah kam wani shegen murmushi ta saki da har sai da ya bayyana farare hakwaranta. Ganin kukan Miran Jasim bana karewa bane ga lokaci nata tafiya Sayeed Hanifud-Din ya gyara tsaiwarsa da fuskantarsa. "Shin ko Jasim na da wani abin cewa ne haka?". Kuka Miran Jasim ya sake fashewa da shi da fadin, "Tabbas nine mai abin cewa, na kumayi alkawarin fadin duk abinda ake bukatar jiNda ga gareni, domin nayi nadama, nayi nadama matuka akan biyema Arshaan da mahaifiyarsa da tawa, Dan komai ya faro asaline da ga su...." Ba Arshaan kawai ba, hatta Malikat Haseenat zura masa ido kawai tai, dan kowa yasan wacece mahaifiyar Arshaan. Mace ce mai kirki da kyawawan halaye. Haka kuma mahaifiyar shi Miran Jasim din. Mace ce mai mugun hali da son kanta, duk wanda ya kwana ya tashi a masarautar kuma ya san mahaifiyar Jasim din da ta Arshaan basa ma zama inuwa daya. Amma dai bara aji mi jasim din yazo da shi. Kuka ya cigaba da yi wiwi kafin ya nisa da cigaba da fadin, "Nasan a zahirance kowa zai ce iyayenmu mata basa shiri da juna ne, sai dai abin ba haka bane. A boye su din aminai ne matuka, dan mahaifiyar Arshaan ta shiga jikin Mammah (Malikat Haseenat) ne kawai danta dinga zakulo musu sirrikanta tana kawo musu. Burinsu shine muyi mulki, tare da mallake dukiyar Abbu (Tajwar Abdul-majeed) gaba daya, dan sun san Haysam ne zai gaje komai tunda shine babba. Sunta kulla-kullar gain mun halaka Haysam tun ma muna yara amma hakan bai kasance ba, dan haka suka yanke shawarar uwa ta kashe Abbu da Haysam tun a wancan lokacin. "Why karya kake matsiyaci makiri!!!". Miran Arshaan ya fada cikin karaji da fashewa da kuka yana kaima Miran Jasim duka. Dan fa shi duk lalacewarsa yana son uwarsa, kuma yasan sam bata taba saka kanta a cikin wanna al'amarin ba, koshi bai fito da maitarsa a fili ta son mulki ba sai bayan mutuwarta. Da kyar aka rabasu, har Miran Arshaan ya jima Miran Jasim ciwo da farce a fuska. Rumtse idoNkawai Shahan-shan yayi cikin kunar zuciya. Sai da kotun ta lafa da kananun magana da ta dauka sannan aka sake bama Miran Jasim damar ci gaba da magana. Kafin yace komai Miran Arshaan ya tare da fadin, "Ba gaskiya ya shirya fada ba, dan haka ni wihy zan fadi komai, na kuma bada damar bayan duk na gama fada a bibiyi recording din nan namu dan baiyi dai-dai da abinda zan fada ba amun duk hukuncin da ya dace. Dan da ya tozarta mahaifiyata da ke kwance a cikin kabari da mata kazafi akan abinda bata aikata ba gara na fadi gaskiya koda ace itace karshena. Abinda ya fara fada ya faru amma a iya shi da mahaifiyarsa ne banda Ummi na, shi da kansa ya bani wanna labarin a randa muka yarda zamu hade kai domin yakar dan uwanmu Haysam. Dunkulewar tamu kuma ta samo asaline kan ima diyar Hifzur-rahaman fade da mukai ta mutu, muka bizne gawarta a cikin masarautar nan batare da sanin kowa ba ranar bikin al'ada. Tabbas mune muka aikata ni da shi, kuma duk neman da akai taima yarinyar har zuwa wannan shekarun da kowa ke tunanin saceta akai ko bata tai a bikin al'ada ba haka bane ba. Bayan mun dunkule mun shiga yakin gain bayan Haysam tako ina amma bamuci nasara ba. Muna a cikin wannan yakinne kuma yazo mana da zancen yin murabus ya daura dansa. Hankalinmu ya tashi matuka, a lokacin muka bazama neman bokaye kwararru da suka iya aiki, har muka had da boka Barbushi. Boka Barbushi ya mana alkawarin taimaka mana, da kuma tabbatar mana kashe Haysam da dansa. Munji dadi matuka tare da kasancewa cikin farin ciki mara musaltuwa, dan haka muka ware akai bikin nadinsa kamar babu komai a ranmu. Sai dai kuma mi, a randa Barbushi ya bamu gubar da zamu zubama Haysam sai muka iske Haysam ba'a cikin hayyacinsa ba. Shi kadai a daki yana ta aman jini da kiran sunan Eshaan da Mammah. Ganinmu yasa ya fara kiranmu akan mu taimakesa mu kira masa su, amma sai mukai fitowarmu mamaki fal zukatanmu, duk da ta wani bangaren murna muke zai mutu. Mun garzaya wajen boka Barbushi muka sanar masa komai, nan fa take shima ya shiga mamaki jin bama mukai da basa tamu gubarba. Gubar ya amsa ya ce mana muje mu dawo washe gari zai bincika, dan tabbas bayan mu akwai mai farautar rayuwar Haysam din. Gabanin asubahi muka dawo cikin masarauta, sai muka iske ALLAH yay masa rasuwa ma. Muni farin ciki, sai dai zukatanmu sun karkata da son gano wanene keda irin burinmu, domin mu a ganinmu dole ne shima mu kaudashi dan karya zame mana matsala idan shima burinsa yin mulkinne. Abinda fa zai baku mamaki a duk hadin kan nan namu muma bawai muna kaunar juna bane. Mu dikanmu burinmu shine muga bayan juna idan mun kauda Haysam da dansa. Abinda ya kara rikita lissafinmu mutuwar matan Eshaan guda biyu a washe garin mutuwar Haysam, babufa shiri muka koma wajen Barbushi. Boka Barbushi ya tabbatar mana da lallai akwai matsala, sannan bayan mu akwai wasu masu kudirirrika sosai a cikin masarautar zagaye da rayuwar Eshaan. A yanzu hakama bayan wadan nan matan nasa biyu da suka rasu wasu zasu sake. mutuwa da shima bai san adadi ba. Sai dai akwai gabar da abubuwa zasu canja kansu dalilin auro wata yarinya da bata cika ashirin ba. Wannan yarinya akwai al'amari mai girman gaske tare da ita, sannan tana tare da manyan sirrika, a cikinsu ma harda babba daya kasance sirrin wanna masarauta. Idan kuma har ta shigo gidan burinmu bazai taba cika ba na mulkar kasar ruman. Mun tashi hankalinmu amma sai ya dakatar da mu da cewar mu kwantar da hankalinmu, munada hanya daya ta bullewa. Hanyar itace bibiyar duk matan da Eshaan zai aura, zamu gano wanna yarinya ne kawai ta hanyar auren yara biyu da ga gidansu itace cikon ta uku, biyun zasu mutu bayan suma sun shigo masarautar. Sai muyi kokarin shafe ahalin wanna yarinya gaba daya ita kuma muyi amfani da ita ta karasa halaka mana Eshaan shike nan zata kare rayuwarta a kurkuku koma a tsireta Jasim ya hau karagar mulki ni kuma na zama magajinsa batare da wancan sirrin ya bude ba. Komai ya mana, sai dai mu burinmu sanin wanene zai dinga kashe matan nasa? Ya sanar mana shima bai iya gano su wanene ba gaskiya. Amma sunada hadari sosai, kuma a cikin gidan nan suke suma, bai kuma kamata mu damu da abinda zasu aikata ba dan zasu mana aikinmu ne cikin sauki muma, Eshaan bazai samu soyayyar mutane ba a dalilin wanna kashe-kashen, dan kowa zai kallesa a mai kashe matansa. Shi kuma zai maida hankalinsa ne a neman wanda ke kashe masa mata mu kuma muna aikinmu a kansa cikin sauki, Mun gamsu mun kuma dawo gida cikin farin ciki. Tun daga nan abubuwa suka cigaba da gudana, muma muka dage, bama sanya waien kokarin shiga da fita da gain an aurama Eshaan mace bayan mutuwar wasu. Ga kuma abinda duk boka Barbushi ya fada yanata faruwa daki-daki, tako ina zaginsa ake da la'antar mulkinsa har mutane na kiransa da Fir'auna. Hakan a mana dad, shiyyasa ma muka baza yaranmu tako ina suna gano mana kyawawan matan da za'a aurama masa, da munzo muka kalame Mammah da zance musamman ni sai ta amine da fatan ALLAH yasa karshen al'amarin kenan. A haka har lissafinmu ya kai ga wasu yara da mahaifinsu ke kawo zuma masarautar nan. Wani kuma yaronmu dake mana aikine ya kawo mana zindensu ashe abokinsa ne. Mun tabbatar da auren ta farko kamar yanda aka saba itama ta mutu, kasancewar munga biyu bayanta muka sake shigewa gaba aka auro ta biyu. Itama dai ta rasun, dan haka muka dira akan ta uku. Shekarun yarinyar da wanda Barbushi ya fada ne ya samu farin cikin da fahimtar itace wadda muke nema, dan haka bayan an aurota muka fara shirya yanda zamu tarwatsa ahalinta. A wanna ranarce wanda yay mana hanyar sanin gidan yaji hirarmu (abokin nasa kenan), bamu nuna masa mun sani ba, sai muka bibiyi rayuwarsa ta hanyar matarsa. Kudi muka bata mai uban yawa da firgita mata rayuwa, harma Jasim yay amtan da ita sannan muka bata gubar data bama mijin nata sannan muka wuce. Washe gari bamu san miya faru ba ta kiramu a rikice wai mijinta ya tafi sanarma iyayen yarinyar nan komal amma ta bashi gubar da muka bata. Hankalinmu ya tashi, babu sanya muka samar da yan sanda suka je gareta da ga nan tai musu jagora zuwan gidan. Anan ne muka saka aka kama mai gidan da babban dansa. (Nasan dal baku manta kama babiy da Hanash ba?)". Arshaan yaja numfashi ya fesar cikin kunar zuciya, sai kuma ya cigaba da fadin, "Makwafcinsa da wani tsoho da akace mahaifin matarsa ne sun cigaba da fadi tashin gain sun san inda suke, sai dai hakan ya gagaresu, a da burinmu kawai mu kashesu a lokaci daya, sai dai yanda Barrister Abdallah Aas ya shiga zance sai mukai sha'awar cigaba da buga wasan. Dan haka muka cigaba da wasa da hankalinsu, mun shirya kawo karshen rayuwarsu a gabar da muka gama shirya kawo karshen rayuwar Eshaan. Sai dai su bamu maida hankali kansu ba sosai dan a ranar muka damka madara mai duke da gubar dafin macizai ga yarsu, dan haka tunaninmu ya karkata kan yarsu gaba daya da kuma aikin da muka sakata. Da ga baya aka sanar mana suma an kashe mana su.…..✍️ DAUDAR GORA Book 2 74 …...……….Komai ya zama an yanka ta tashi, kashe ahalinta ne kawai bata tashi mana ba, dan su kam an tabbatar mana sai dai was basu ba. Eshaan bai mutu ba, ita kuma ta samu nasarar barin kurkuku, sannan mun neman Barrister Akeem daya jagoranci kashe mana iyayenta mun rasa. Tun daga lokacin komai ya rikice mana, wasan ya fara sauya salo. Koda muka tunkari Barbushi sai ya kwantar mana hankali da cewar ya samo wata mafitar. Zai kauda mana yarinyar cikin sauki, zai kuma kwantar da Eshaan ciwo da komai sai dai a masa. Dolene a lokacin a yarda daya da ga cikinmu ya zama Shahan-shan. Wannan shine dalilin samun kaimi da ga kowannenmu na ganin ya kuma kada dan uwansa kasa. Yayinda muka cigaba da kulla makirce-makirce ga Eshaan ciki hard kashe Sayeed Khairul-Bashar da haddasa zanga-zangar mutanen kasa, da tada bomb a cikin motar Barrister Abdallah Aas, da hada videon yanda yake kashe mutane da tsafi muka Bama matarsa da tunanin zata yada duniya ta gani, amma sai duk batai haka ba... Wata irin hayaniya ta tashin hankali ce ta tashi a kotun, musamman iyalan Sayeed Khairul-Bashar. Babban dansa yay wani irin daka tsalle sai gashi a gaban su Miran Arshaan din. Shaka ya hadasu ya kai musu, take yan uwansa suma suka iso. Da kyar aka kwaci Miran Arshaan da Miran Jasim a hannun yayan Sayeed Khairul-Bashar, dan sai da Shahan-shan ya tsawatar da kansa. Sai dai shima karfin hali kawai yake, duk da kuwa yasan abubuwa da yawa da Miran Arshaan din ya fada a yanzu ta dalilin bibiyarsu da ya rinkayi, akan su Bably kuwa randa Iffah tai masa rakon nan na ya binciko mata iyayenta a matsayin Ajmaal a ranar ya fara bibiyarsu har ya gano sune, shine kuma ya kubutar da Barrister Abdallah as da ga tashin waccan nakiyar da har yanzu mutane da yawa suke dauka ya mutu. Kisan Sayeed Khairul- Bashar ne kawai bai gama tabbatar da wanda yayisa ba sam sai yanzu da suka fada. Bayan kotun ta natsa da kyar, masu kuka nayi, masu tsine musu nayi Sayeed Hanifud-Din da gaba daya jikinsa yay sanyi ya dubi Miran Arshaan din da fadin, "Ita kuma Ameera Haifah minene alakarku kenan?" Kallonta Miran Arshaan yay, ganin yanda ta kakkafesa da idanunta ya sashi sakin murmushi. "Duk abinda na lissafa maka anan harda ita a ciki, alakarmu ta fara kasancewa a tare ne bayan mutuwar Haysarn Akhi. Sai dai ita da Jasim tun kafin shigowarta masarautar nan suke tare. Dan ta kasance ma tarkar matarsa ce a yanda yake tarayya da ita a duk sanda ya yaso… *Tsinanne kaima ai naga kana tarayyar da ita, kuma garama ni kafin tai aure ne, kaiko a cikin gidan nan tana matsayin matar Haysam din kake tarraya da it... "Karya kake gatalalle, ban taba kusantar Haifah ba sai da Haysam ya rasu, ita kuma ta kawo min kanta da kanta bani a gayyato ta ba. Idan karya na mata gata nan ta misalta mana....... Wani irin mahaukacin buga guduma Tajwar Eshaan yayi, sai da kowa ya zabura a cikin kotun har Miran Arshaan din da ya karbe Miran Jasim a fusace. Tabbas da ace idanunsa ba cikin gilashi suke ba babu abinda zai hana juyewarsu firgita kowa da ke a wajen. Sai dai fuskarsa fa tayi masifar sake tsukewa, Sayeed Hanifud-Din da ya fahimci maganar ce baya bukatar a cigaba da yi, ya ce, "Kowa ya fahimta. Sai dai akwai abubuwan da bamuji da ga gareka ba,wanda kuma kowa yake ji a jikinsa kune kuka aikata din. Na farko ima Zawjata-almilk allura lokacin da take a kurkuku, sannan jefata a cikin ruwan shima". "Tabbas allura mune, sai dai Bama allurar komai bace face ta sihiri da Barbushi ya bamu domin kame mata jiki ta kasa tsinana komai, dan haka mukai amfani da rigar da ke jikin Eshaan a randa ta bashi madara dan ta dauka shine, Haifah ce kuma tare da ni muka je mukai mata allurar a ranar. Amma jefata cikin ruwa wlhy bamu bane ba...." "Karya kake kune Jasim, dan duk wanda ya aikata wadan can ayyukan to shine ya aikata wannan, kana son ka boyene domin kuwa al'amarin yayi iri daya da saka Miran Nayyar ruwa da akai shekarun da suka shude…. "Gaskiya ya fada basu bane ba!!". Kusan a tare duk wanda ke'a cikin kotun ya dubi wanda yay maganar, yayinda Iffah ta mike a zabure dan wanna muryar ko'a mafarki bazata taba layance mata ba. Kaka kenan, dattijo ko muce tsoho mai ran karfe. Ya kara wani fes abinsa saboda canjin rayuwa da ya samu duk da jikin tsufarsa na nan tare da shi. A hankalin Tajwar Eshaan ya lumshe idanunsa da ke a cikin glasses, duk da shima dai abinda kakan ya fada ya girgiza mamakinsa, ga zuciyarsa dama a takure take da zancen su Miran Jasim na tabbatar da basu ke kashe masa mata ba kamar yanda Iffah ta taba fada masa..... Sayeed Hanifud-Din ne ya katse shirun idanunsa a kan Kaka ya furta,"Taya akai ka sani bawan ALLAH? Idan kuma har basu bane wanene?". Kaka da ke fitowa da ga wajen zamansa ya tsaya gaban kotu yana mai sake jinjina kansa. "Tabbas kamar yanda na fada basu bane. Abinda kuma ya fada sun aikata iya shi din suka aikata sai wanda ALLAH ya barma kansa sani da su da suka aikata abinsu. Amma tabbas kamar yanda basu da alaka da kashe duk Zawjata-almilk da suka rasu, haka basu da alaka da kashe Miran Nayyar, itama kuma Zawjata- almilk Fhareedah basu ne suka sakata a cikin ruwa ba". "To wanene?". Murmushi kawai kaka yayi sai dai baice komai ba. Yayinda kowa ya zuba masa ido a cikin kotun. Malikat Haseenat son tuno inda tasan fuskar take. Malikat Bushirat kam zuciyarta wani irin mugu mugun harbawa take da masifar karfi kamar zata fito ta bakinta saboda abinda kakan ke fada. Sai dai zuciyarta kwantar mata da hankali take akan ta nutsu ko shi hadimin da ya aikata aikin bai isa ganita ba balle wannan shashashan tsohon da ke jiran ranar mutuwa….. Shirun kaka yasa Sayeed Hanifud-Din sake maimaita masa tambayar. Yanzu ma kaka murmushin ya saki mai sanyi sannan ya dago ya duba kowa da ke cikin kotun, idanunsa ne suka tsaya akan Iffah dake kallonsa tana jin kamar ta taso ta rungumesa. Murmushin ya sake sakar mata ya dauke idanunsa "Ina rokon afuwa ga wanna kotu mai adalci akan kartsalandan da mai mata. Ban kasance anan dan sanar da wanda ya aikata abinda ake son ji ba, domin kowanene a wanna gidan yake kuma yana a cikin wannan waje sannan da kansa zai fallasa kansa a gabar da ya dace kowa ya sansa..." "Tofa babbar magana, kotu zata so sanin miya kawoka baba?". Sayeed Hanifud-Din ya fada saboda inkiyar da Sayeed Tasadduq-Husain ya masa. Gyara tsaiwa kaka yay da kyau, sannan ya ce, "Kamar yanda na fada a farko basu bane, tabbas basu din bane. Su kawai ALLAH ya jarbcesu ne ta hanyar bibiyar wata tushiya da suka zama sanadin samar da tsirranta a shekarun baya batare da sun sani ba. Ta tafi ta sanadin su, sannan ta dawo ta sanadin su, duk da asali basu bane mafarin komai, dan suma a karan kansu suna aiki ne akan aikin daba nasu ba". "Baba ka sake sanyani a rudani, ko zaka bayyana mana komai a bude dai-dai da fahimtar mu?". "Mizai hana in har kotu ta bani dama?". "Kotu ta baka dama, domin kana akan abinda take bukatar sani ne dan zartar da hukunci ga masu laifi, da yin adalci ga masu gaskiya". "To Alhamdullah ". Kaka ya fada yana murmushi. Sai kuma ya maida dubansa ga su Miran Jasim da suke a rudanin son tuna inda suka san fuskar, dauke kai yay kamar bai gansu ba ya sake maidawa ga Sayeed Hanifud-Din. "Mune ahalin Zawjata-almilk Fhareedah. Mune kuma suka bada kwangilar halakawa, sai dai ALLAH ya kubutar damu tare da Barrister Abdallah Aas da ya dinga fafitikar taimkonmu tun sanda suka fara bibiyar mu". Ya karen maganar da nuna inda ya taso can karshen kotun. A kusan tare Miran Arshaan da Miran Jasim suka zabura na tsabar kaduwa da gain Barrister Abdallah Aas da su Baby. Dai-dai kuma da zaburar Daneen Ammarah da idanunta suka sauka kan Babiy. Ba shekara ashirin ba, koda shekara dubu ashirin ce bata jin zata manta da wanna fuskar duk da ganin kwanaki goma sha uku kawai ta taba masa. An musu auren zalunci a wancan lokacin bada san ransu ba bada amincewarsu ba. Amma sun hade kai sunyi kuka tare, sunyi murmushin kuma a tare, sun kuma shaku a tare, sun kumaji radadin rabuwa da juna a tare, yayinda sukai kewar rashin juna a tare, Hankalin duk mutanen da ke a cikin kotun ya rarrabu, wasu akan Daneen Ammarah da ke nuna Baby cikin rawar lips alamar tana son magana ta kasa. Wasu akan su Miran dasim da suka rikice. Was akan su Ummu da ke fitowa: "Zayyan!! Tabbas kai ne! Kai ne Zayyan ko bayan shekara ashirin sau ashirin ne bazan taba mantawa da kai ba!!!". Wadan nan zantuka na Daneen Ammarah ne suka zaburar da kowa da kowa ido ya koma kanta har Babiy da kansa ke a duke bai san anai ba, sai dai zuciyarsa wani irin harbawa take da sauri-sauri tunda ya shigo cikin masarautar dama a yau. Shima dai a karo na farko idanun nasa suka sauka akan Daneen Ammarah din, tsaf numfashinsa ya dauke, yay taga- taga zai fadi sai da Barrister Abdallah as da Hanash suka tarosa. Yan kananun magana ne suka fara tashi a kotun, yayinda Tajwar Eshaan ya kafe Iffah da idanu ta cikin eyeglasses dinsa, sosai jikinta ke tsuma itama kamar wadda take a rudani. Sai yaji ta bashi tausayi, wai a hakama bata san tushen al'amarin ba kenan. Ji yake kamar ya rufe ido ya gansa da ga shi sai ita kawal ya rungumeta dan sarar mata nutsuwa shima ko zai samu da ga radadin da zuciyarsa ke masa. Badan karya raba kan mutane ba da zai dage shari' ar nan ne har sai gobe idan ALLAH ya kaimu. Amma sai ya hadiye komai kamar yanda ya saba dan shi a karan kansa so yake yaji ta inda aka fadi a ragaya, tunda dai gashi gwajinsu ya tabbatar da Daneen Ammarah matsayin mahaifiyar Iffah'r itama. Sannan yanayin Babiy da Mammyn mana yanzu ya sake bude komai a bayyane….✍️ DAUDAR GORA... Book2 Chapter: 75 Da kyar da kyar aka samu kotun ta lafa, yayinda kalaman Daneen Ammarah dake kuka sukai matukar daukar hankalin kowa. Fadi take, "Wlhy Mammah shine, shine wanda suka cutar da mu a tare. Bazan taba yafe musu ba, wlhy bazan yafe musu ba, sun haddasa bakin ciki mai ciwo a zuciyata. Sun nisanta ni da shi bayan sun alakanta mu". Sosai hankalin Malikat Haseenat dama duk wanda ke'a kotun ya tashi, dan yanda take kuka haka Babiy make kuka sai dai shi kansa duke yake a kasa. Ummu ma dai tasan komai da ya faru, dan a lokacin bai boye mata ba. Hakama lyyani. Iffah nason tashi taje garesu amma babu dama, dan ita Zawjata-almilk komai nata nada ka'ida da son nutsuwa. Dole ta hakura ta zuba musu ido kawai musamman Babiy da Ummu da Daneen Ammarah. Tajwar Eshaan ya nisa tare da motsa lips dinsa a hankali, "Wannan kotu na bukatar Daneen Ammarah a gabanta, da son jin fassarar kalamanta". Sayeed Hanifud-Din ne ya maimaita abinda Tajwar Eshaan din ya fada, dan haka Daneen Ammarah ta fito da taimakon Daneen Waheada,dan da alama abubuwan kanta ma neman sukeyi, idanunta har sun kada. "Ko zamu iya sanin abinda kike nufi da kalamanki Daneen Ammarah. Sannan ko kinada alaka ne da wanna shari'ar?" "Bani da alaka da wannan shari'ar face a farkon ta mai bada kariya ga Zawjata-almilk. Sai dai inada alaka shudaddiya da wannan bawan ALLAHn". Ta nuna Babiy. '"'Ko zamu iya sanin alakar taku?" "Mun taba kasancewa mata da miji kusan shekaru ashirin da daya da suka shude". Ba Iffah kawai ba, mafi yawan wanda ke'a cikin kotun sai da suka waro idanu saboda razana. Sayeed Hanifud-Din ya ce, "Ta yaya?". Shiru kamar batace komai ba, sai kuma ta nisa da share hawayenta. "Komai ya faru ne a cikin littafin kaddara ta. Na san duk wanda yake anan in har ya kai shekara talatin da biyar zuwa sama yason tabon da ke a jikin bangon littafin labarina da duka shafukan cikinsa. Bazan kirasa abin kaico ba, amma zan kirasa zalunci mai ciwo a gareni dama duk wanda yake cikin wannan masarautar. Faruwarsa kuma ta fara ne a bisa son zuciyar dan uwana Jasim dake a gaban shari’a a yanzu. Sun kulla min aure da wan nan bawan ALLAH bisa umarnin wata mushirika da ta shude ita da labarinta a wannan masarauta. Sai dai aure ne na kwanaki goma sha uku kacal suka saka ya sakeni. Bisa kudirar UBANGIJI kuma ya samar da haihu a tsakaninmu batare da shi ya sani ba ma, dan ban sake ganinsa ba tun wannan ranar sai a yau, sai dai ALLAH yayma yarinyar rasuwa a kwana uku da haihuwarta... "BATA MUTU BA!!". Kalmomi uku masu razanarwa da ga bakin kaka. Wani irin zabura Babiy da Daneen Ammarah, da Malikat Haseenat, da Iffah, da Ummu, da Daneen Waheeda, da Malikat Bushirat, da Miran Jasim sukai a lokaci guda kuma a tare kamar wanda aka saita da camara.Su dukansu kuma suka zubama Kaka da yay maganar idanu kowanne da irin kalar luguden dakan da zuciyarsa ke masa a zahirance da badini. Cikin karfin hali Malikat Haseenat ta furta, "Taya wadda naima wanka, na shirya a cikin likafani, aka sallaceta a gaban kowa, aka gina kabari aka sakata za'ace bata mutu ba. Kai wanene? Ya akai kuma kasan hakan?". "ALLAH ya kara miki lafiya da tsohon rai mai albarka. Nine mutumin da ya kora waccan bokanyar mushirikar a waccan raar dai da nasan bazaki manta ba". Ya arrahaman! Bawan ALLAH dama kana raye? Amma ka sakani a rudani. "Nasan zan saka kowama a rudani, sai dai wannan ranar ita naita rokon UBANGIJI zuwanta gareni kafin ya dauki rayuwata dan na cika wasiyyar mahaifina. Duk da burina ya cika na dawowar Fhareedah cikin zuri'ar mahaifiyarta a dalilin aure". Kowa zubama Iffah idanu yayi, kamar yanda itama take kallon Kaka jikinta na dan rawa. Malikat Bushirat ma wani irin bugawa kirjinta keyi, hakama Daneen Ammarah da Babiy. Cikin rawar baki data harshe Babiy ya ce, "Baba na kasa fahimtar komai". "Yanzu zan fahimtar da kai dama duk wanda ke anan. Kamar yanda Daneen Ammarah ta fada an aura mata miji kuma an saka ya saketa a sati biyu bisa umarnin mushirikar dake katantanwa da ikon wanna gida. Ba kowa bane wanda aka aura matan nan face Zayyan in Abbas. Zayyan dai da ne ga wani aminina da zan iya cewa ma ya zama jinina. Dan tunda muka taso babu abinda ke rabani da Abbas. Hatta aure an mana a rana guda ne, hakama haihuwar yaranmu tana zuwane a kusa da kusa. Sai dai shi nashi basa zama sai akan Zayyan. Sana'ar gidan su Abbas dinka kayan doki ne, dan haka ita ya gada ita kuma yake yi tunda yasan kansa, wannan dalilinne ya sani koyo a wajensa, danni gidanmu abinda na tashi naga anayi bana ra'ayinsa. Mahaifina babban mutumne mai bada magani sannan yana cire kowadanne irin aljanu a jikin mutum duk taurarin kansu. Ni kuma sai nake ganin kamar wani abun akwai kauce hanya, dan haka naki yarda na dingayi duk da tunda na taso yanayi a gabana na kuma san magunguna da sirrika kala-kala. Mukan dinka kayan doki ni da Abbas mu kawosu cikin Dahab City, anan ne muka hadu da wani bawan ALLAH da yay sanadin fara kawo wadan nan kaya namu cikin masarautar nan. A duk sanda muka kawo akan bamu kudinmu ne gaba daya, sai ma yazamindai mun dinka din nan kawai muke kawowa. A haka muka cigaba da rayuwa har shekarun yayanmu suka kawo girma, iyayrnmu suka bamu shawarar hada yaranmu aure. Munko yi farin ciki da shawarar, babu bata lokaci aka sha bikin Jumayma da Zayyan. ALLAH ya azurtasu da haihuwar fari da wuri, ta biyu ma haka, hakama ta uku. Zuwa sannan idan mun dinka kayan doki duk wanda zai o kawowa yakan taho ne da Zayyan da shine kadai keda sha'awar irin sana'ar tamu. Sauran yarana biyu maza kuwa suna nasu aikinne da sukafi so suma. A wata rana data kasance nine zan kawokayan da muka dinka masarautar a cikin azi sai na tashi da ciwo na zazzabi, dan haka Abbas ya amsa suka tafi kaiwa tare da Zayyan. Basufi awa takwas da tafiya ba sai gashi ya dawo min yana kuka. Hankalina tashe na tarbesa da tambayar lafiya. Bai boyen komai ba ya sanar min wai amma Zayyan aure da diyar Shahan- shan, cikin mamaki nace aure kuma? Wane irin aurene haka kamar auren kaza? Kuma da yar Shahan-shan guda anya kuwa?. Ya tabbatar min hakane, amma yanaji a jikinsa akwai dalili mai karfi nayin hakan dan yaji wasu yan samari da basu wuce sa'an Zayyan din ba na labari. Nan ya zayyane min komai dake faruwa ni da baba. Na lallashesa da kwantar masa da hankali na shirya a boye naje masarautar bisa umarnin mahaifina. Anan nake jiyo komai dama asalin dalilin hadin auren. Hankalina ya tashi dan na fahimci babban al'amari ne kam gashi ance Shahan-shan ma baya kasar shi da uwargidansa da Miran mai jiran gado. Kannensa ne da wannan aika-aikar. Na koma gida cikin damuwa mukai zaman jiran tsammani, tun muna irga kwanaki harya koma sati har sati biyu. anar kwatsam sai ga Zayyan ya dawo mana. Duk mun tarbesa da tambayoyin yaya akai ya kubuta. A take ya zayyane mana komai yana hawaye. Murmushi mahaifina dake kwance yana jiyya yayi, sai dai baice komai ba, sai daga baya 22:58 ¡kirani yake sanarmin ya fahimci Zayyan ya kamu da soyayyar matar aurensa ta sati biyu dan haka a karo na farko yana son nayi wani abu, ya kuma tabbatar min ba shirka bace kamar yanda nake dauka dan shi ba mushiriki bane. Komai sai da ya zayyane mun, dan haka na dauka alwashin bibiyar al'amarinta har sanda zata haihu kamar yanda mahaifina ya bani umarni. Shi kuma ya sakashi baro cikin Jumna dan yace ya tabbata za'a iva zuwa nemansa, za kuma a nemesa a ko'ina dan haka yace yaje cikin Dahab City din inda bazasu taba tsammanin zasu samesa a kusa da su din ba, wannan ne dalilin dawowar Zayyan wanna gari, su kuma su Abbas ya sakasu dawowa cikin gidanmu yanda mutane zasuyi tunanin suma sun gudu. Haka kuwa akayi, bayan tafiyarsa da kwana biyu shi da matarsa da yaransu uku sai gashi anzo nemansa. Sai dai iya bulayi basu samesan ba, da ga baya dole suka hakura. A wannan dan tsakanin Abbas ya kamu da rashin lafiya ta kwana hudu kacal ALLAH yay masa rasuwa. Wannan mutuwa ta gigitamu matuka,hakama matarsa da Zayyan. A wajen zaman gaisuwar Abbas da Zayyan ke zuwa a sirrance ya hadu da Abu Musa, wanda shine silar masa hanyar kai zuma cikin masarauta dama abokinsa ne na yarinta. A tsorace yazo ya sanarma mahaifina abinda Abu Musa yazo masa da shi. Sai yay murmushi tare da kwantar masa da hankali tare da bashi kwarin gwiwa saboda wani hasashe da yace yayi akan hikimar cigaba da zuwan nasa masarautar. Duk da shima yana da mai kawomasa duk wani rahoton da yake so na cikin masarautar, a haka nema muka san samuwar cikin Fhareedatu, wanda kuma yay dai-dai da samuwar ciki na hudu ga diyata matar Zayyan itama. Abubuwa sun cigaba da kai da kawo har zuwa ranar haihuwa, a lokacinne kuma mahaifina yasa na shirya yin abinda ban taba yi ba. Wato aiki da kayansa. Alhamdullah sai kafin ma nai wani yunkuri sai ga kiran mahaifina da ga masarauta wai zasuyi aiki. Da farko banyi niyyar zuwa ba dan shi mahaifina bazai iyaba saboda ciwo, amma sai ya zaunar dani yay min bayanin komai dama ban hasaso ba. Tunda dama ni nayi shirin shiga masarautar ne kawai na dakko abinda za'a haifa na fito kamar yanda ya sani sai a yanzu kuma labari ya canja. Bani da ikon bijirema umarninsa, kamar yanda shima bashi da ikon bijirema kiran masarauta dan haka na shirya zuwa kamar yanda ya umarceni tunda a duk abinda ya sanin banga shirka ko wani tsafi a ciki ba. Ina cikin shirin tafiya masarautar a dai-dai lokacin sai ga labarin haihuwar Fhareedatu da ga bakin amintaccen mahaifina. Wannan shine ya zaburar dani zuwa a gaggauce. Lokacin dana iso bokanyar ta riga ta gama shirya komai da su basuyi zato da tsammani ba ma, amma duk da haka nai iya kokarin da zan iya na mata kiranye da hadata ita da yan kayanta na Koreta a cikin masarautar kamar yanda mahaifina duk yace nayi. Ni nasan a korar da mahaifina yasa nai mata bazata iya ta dawo ba, amma kuma sai zuciyata keta faman mini kikawo. Idan uwar masu gida bata mantaba, nine na fadi cewar yarinyar ta rasu a lokacin da nasa a kawota gareni na dubata". "Tabbas anyi haka". Cewar Malikat Haseenat. Murmushin Kaka yayi, da cigaba da fadin a lokacin amintaccen mahaifina ya bani gawar wata jaririyar dana canji jaririyar da ita ya fito da wadda aka haifa. Bakowa bane kuma sai wanda a yanzu kuke kira da Baba mai magani a gonar yaro, shugaban masu magajin gargajiya na wanna masarautar, saboda shi din yaron mahaifina ne"…..✍️ DAUDAR GORA Book2 Chapter: 76 .....…."Na iso gida da farin cikin wasan ya kare, sai dai ina danka jinjirar a hannun mahaifina ya kalleta da juya bayanta ya tsirama tambarin tawadar ALLAH dake a bayan nata idanun, sai cewa dani yay (A sanadin ta kullika da yawa zasu bude. Harma da wanda ba'ai zato da tsammani ba. Zata zama tauraruwa mai hasken gaske a cikin taurari, zata kuma zama shahararriya a duniya bama a kasar ruman kawai ba. Zata auri mutum mai daraja da cikar kamala, amma sai kunyi hakurin jure rasawa kafin ita ta samu. Sai kun boye komai kafin komai ya bayyana. Hatta da mahaifinta zai raineta ne batare da yasan ita bace) ban fahimci mi yake nufi ba, Ni damuwarta ma a lokacin yanda zamuyi da yarinyar nan. Kamar da ga sama sai ga Zayyan, baba ya sani na boye jinjirar sannan aka bashi izinin shiga. Bayan ya gaishemu yake sanar mana Jumayma na nakuda ne, yazo amsar mata magani ne a wajen kaka kamar yanda ya saba basu. Babu musu mahaifina ya hada masa komai ya basa, tare da sanar masa ya gaggauta komawa a bata tasha. Bayan wucewarsa da kadan mahaifina ya ce nai haramar daukar jinjirar nan nabi bayansa, dan Jumayma zata haihu yarta babu rai, na dakko waccan na alive musu wannan din. Da mamaki na tambayesa yanda akai yasan haka, danni dai dama wadan nan abubuwan nasa yasa nake kyamatar harkokinsan. Dan murmushi kawai yay, da fadin kusan wata guda kenan Jumayma a sanarmin batajin cikinta na motsi, a ranar karshe da tazo kuma na fahimci yaron cikinta ya mutu mata a ciki ne, shiyyasa ma nace matarka taje ta zauna da ita a can ita da Maman Zayyan. Nan ma a tsorace nace to kace baka son kowa ya sani, amma taya zan canja yarinyar bayan su zasu amshi haihuwar? Nan ma sai da yay yar dariya sannan yace karka damu jeka kai dai ka basu. Kaina a daure da wannan lamari nasa na tafi, na sake dawo da jinjira cikin Daular ruman. Ban yarda na shiga gidan ba, na saka aka kiramun matata (lyyani) a sirrance, a mamakina koda ta fito na bata jaririyar bata nunamin damuwar komai ba face rungumeta da tai da sumbatarta ta shige abunta. Ashe ni ban fahimci yanda al'amarin yake ba sai da na dawo gida yake sanarmin ba lyyanin bace, suffarta kawai aka shiga. Nasan zaiyi fiye da hakan ma, sai bance komai ba dan banda abin fadar. A takaice dai yarinya taci suna Fhareedatu, amma iyayenta na mata alkunya da Iffah, da gani sai babana muka san ba yarinyar da Jumayma (Ummu) ta haita bace. Sun cigaba da rainonta cikin yanayin ciwuka daban-daban, dan tanata laulayi har sat da takai Jumayma ta dawo da zama Jumna tare damu. A lokacin jikin baba yayi tsanani, amma haka ya dinga fadamin abubuwan maganinta, dan ya tabbatar min abinda sukai niyyar yi da itane ya tabata tun tana a ciki, ALLAH ya bata kariyane baiyi tasiri ba, sannan iskokin da ke akan mahaifiyarta ma masu karfine, a yanzu haka ma sun dawo jikinta itama. Kwanan Jumayma bakwai da zuwa gida ALLAH yay ma mahaifina rasuwa shima, inda ya barni da wasiyya mai girma akan Iffah. Ya tabbatar min hatsabibiyar bokanyar nan zata dawo, zata dawo cikin wanna masarautar dan akwai wanda ke tare da ita da jimawa, zata dawo ta jikinsu kuma zata cigaba da illar daukar fansa. Dan tun fil'azal tanada burine darna akan karagar mulkin Shahan-shan. Ya umarcenta karna sake zuwa cikin masarautar, amma Zayyan ya cigaba da kai zumarsa babu wanda ya isa ya ganeshi, hatta ita mahaifiyar yarinyar ma bazasu tapa hada koda hanya ba sat bayan komawar iffah cikin masarautar matsayin matar aure. Hankalina ya tashi, na tambayesa ta yaya kuma zata koma. Ya cemin la kudirar UBANGIJI, amma st kansa bai sani ba. Abinda kawai zanyi shine a duk lokacin da hakan yazo duk abinda na gani a mafarkina har sau uku yana maimaita kansa to na aiwatar. Cikin damuwa na sanar masa ni bana son al'amuran nan nasa. Yay murmushi idanunsa a kaina. Kafin ya kira sunana da fadin, (Baka isa canja abinda ALLAH ya rubuta ba daga kaddararka, tabbas al'amarin dake zagaye damu baiwace da ga ALLAH, sai dai wasunmu na kaucewa wajen tafiyar da ita har su hada da shirka ko saka wasu a shirka. Why why Ban taba aikata shirka da wannan baiwar tawa ba, sai dai ina bada maganin da ALLAH ya sanar dani akan duk wani shaidani da cututtuka. Kai jinina ne, a kuma dade da tabbatar da abinda yake tare da ni kaima yana a tare da kai, sai dai bazan tilastaka yin abinda ni nayi ba, zan dai rokeka tsayawa a bayan yarinyar nan da izinin UBANGIJIN har ranar da makiyanta zasuyi kuka. In ba hakaba ba iya ita ba, kasar ruman gaba dayanta na cikin garari inhar waccan mushirikar ta samu cikar burinta a kanku. Domin burinta shine mulkar kasar ruman ne, ta taka wasu tsanikan nasararta kuma a dalilin son zuciyar wasu dake cikin masarautar da karancin toro da dogaro ga ALLAH. ALLAH ne ya daura maka wannan nauyin bani ba, dan haka jeka, jeka maza da iznininsa ka magance matsalar). Wanna wasiyyar ta mahaifina sune sanadin komai, sune suka cigaba da jagorantata har zuwa yau. Fhareedatu ta tashi yarinya mai shiga rai, kyakykyawar gaske da akoda yaushe mukanta mamakin wama ta biyo a kammani, dan duk da tana kama da yan uwanta idan ka nutsu zaka fahimci kamanin nata sunada sirrika masu yawa kuma duk ta fisu kyawu. Kamar yanda mahaifina ya fada nakanyi mafarki akan abubuwa da yawa da suka shafeta, wani lokacinma akan min abu kamar wanda aka budema idanu, duk yanda nake gudun bada magani ko taimako akan masu hatsabiban iskoki wani lokacin saina tsinta kaina nayi, amma dai ina iya bakin kokarina na ganin na kaucema hakan. Dan da gaske abubuwa da yawa basa kwanta min a rai, duk da Alhamdullah ni dai wani aljani bai taba sakani yin yanka na zubda jini ba ko shardantamin wasu abubuwa. Kawai nakan samu kaina da yin abunne.Komai ya fara fitowa ga Fhareedatu a lokacin data fara mafarkai akan abubuwa, duk mafarkin da tayi nima sai nayisa cikin amincewar UBANGIJI. A lokacin na fahimci komai yana tunkarowa kenan, ban fahimci kalaman baba ba na sai muni hakuri mun rasa kafin ta samu sai lokacin da Arfa ta rasa ranta, aka kuma na Fariha itama. A jiyyar da Fhareedah tayi na kusan wata bakwai kamar wadda ta fita a hayyacinta ne na fahimci komai da ga wasiyyar mahaifina, da ga lokacin ne kuma abubuwa suka fara daki-daki har zuwa yau. Hatta bibiyarmu da suka saka anayi na barsune kawai, hatta kubutar damu da akayi da ga shirinsu nasan wanda yayi. Duk kanin kalubalen da Fhareedah ke fuskanta a gidan nan nasani duk. Sai dai abinda masu hakilon basu sani ba tana zagaye ne da kariyar UBANGIJI, ya saka wasu halittu gadinta domin masu talala da ita da ruguza ayyukansu badan ta banbanta da sauran mutane ba ko zama ta daban. Kawai dai UBANGIJI idan yaso karya azzalumi sai yay masa talala da abinda ya raina. To hakance akan Fhareedah da mushirikar bokanya da ma duk mabiyanta dan sun san kansu". Kotu fa tayi matukar yamutsewa, yamutsewa ta tsananin tashin hankali da al'ajabin wanna labari mai rudarwa. Rudarwar da ke neman hargitsowa da zukatan wasu. Wasun da har shi kansa Shahan-shan din a wannan gabar ya matukar girgiza. Tabbas yasan labarin Bokanya uwa da aka kora a masarautar, sai dai lokacin baya kasar. Ya kuma san Aunt dinsa Daneen Ammarah tayi aure ta haihu yar ta mutu amma bai san tushen auren ba tunda a lokacin duk baya nan,sanda zai dawo kuma an binne labarin da binnewar dokar mahaifinsa. Idanunsa da ke cikin eyeglasses ya sauke akan Iffah da tun dazun kanta ke a duke, yana bukatar sanin halin da take ciki a yanzu fiye da komai. Dan hatta da tunani akan wanda ke tare da bokanyar ya kasa nutsuwar yi so yake ya fara sanin halin da take ciki. Yanda aketa kokarin son ganin kotun ta nutsu amma hakan ya gagara dole aka dage zaman har sai zuwa washe gari domin yankema su Miran Jasim hukunci dai-dai da laifinsu, sannan a dora sabuwar sharia da bincike akan wanda ya saka Iffah a cikin ruwa saboda alakarsa da uwa.... * SASHEN MALIKAT HASEENAT* Rungume Iffah take a jikin Ummu da Daneen Ammarah da suka sakata a tsakkiya suna kuka, kuka mai ban tausayi da taba zukata. Hakama Babiy da Hanash da lyyani nasu sukeyi. Duk taurin zuciyar Daneen Waheeda kukan takeyi, Kaka da Malikat Haseenat ne kawai zaune shiru sai dai kowa yasan suma kukan zuci sukeyi. Yar gyaran murya kaka yay da gyara zamansa. Hakan yasa duk suka dubesa. "Inaga kuka bashi bane mafita ayi hakuri hakanan.Abinda ya faru ya riga ya faru. Komai daya faru hikimar UBANGIJI ce da ga cikin hikimominsa da rahamarsa. Ya boye komai a inda kuke batare da saninku ba. Ina naman afuwarku na boye komai da mukai ni da mahaifina. Bamuyi hakan domin son zuciya ba. Sai dai kawai dan hakan itace kaddararmu mu duka dake anan din. Mu talakawanku ne, amma a sai UBANGIJI ya fidda tsiro a tsakaninmu domin nuna ikonsa akan shi fa talaka da mai arziki da mai mulki duk daya suke a garesa, wanda yafi waninsa shine wanda yafi tsoronsa kawai. Dan haka ya rinjayar da Fhareedatu garemu matsayin iyaye maza ku kuma mata, shiyyasa ta dawo ta rayu a hanunmu duk da a zahiri bamu da wannan karfin sam. Sannan ya kaddara Jumayma itace zata shayar da ita da rainonta matsayin uwa batare da ta taba farga da ba'ita ta haifeta ba. Wannan na nuna mana cewar da na kowa ne, hakama uwa ta kowane da ne. Ka haifa bashi ke nufin naka bane kai kadai, baka haifaba bashi ke nufin bazaka samu daga samuwar wasu ba. lyaye dake kallon yayan da suka haifa ne kawai yaya masu daraja da soyayya a zukatansu sai su canja. Kima dan wani kyakykywar addu'a yayinda kika gansa a wata hanya kema sai mala'iku su amsa da fadin(Amin!! Tare Da naki) wasu mutanen kuma su masa batare da kin sani ba. Ki tausayama maraya da dan daya tashi a yanayin wahalar talauci na iyayensa ko tsintar kansa a wani yanayi kema sai ALLAH ya tausayama naki da hadashi da masu tausaya masa, dan dole kema akwai abinda rayuwarku take bukata. Ki kyautatama dan wani ALLAH zai kyautatama naki koda bakya a raye a duniya. Kar kiga gazawar yaye akan kaddarar yayansu tayasu masa aadu'a da musu fatan alkair ALLAH zai katange naki, Hikimar UBANGIJI babu ta inda baya zartar da ita ga bawansa"….✍️ DAUDAR GORA Book2 Chapter 77 ....………"' Tabbas hakane, yau kuma na kara tabbatarwa. Auran Ammarah da Zayyan abunne da bamu shirya masa ba, hakama samuwar wannan yarinya da rasata duk cikin tsarin UBANGIJN talikai ne. Baku aikata laifin komai a garemu ba face taimako. ALLAH kuma ya kaddara Zayyan matsayin miji ga Ammarah dan ya sanar damu abinda bamu da ilimin saninsa. Lallai jini ba karya bane ba. Dan tun a randa na fara ganin Fhareedah naji kaunarta mai karfi a raina, hakama mahaifiyarta. Komin kankantar al'amarin da ya shafeta Ammarah bata wasa da shi. Zuciyata ta fara rawa a kanta a lokacin da was al'amura nata ke kamanceceniya da Ammarah. Sai dai ban san ta ina zan kamo al'amarin ba balle na bashi fassarar da ya dace da shi. Dan ko'a randa mijinta yazomin da batun tambarin tawadar ALLAH dake jikinta irin na wannan zuri'a al'amarin ya jima yana mun kai kawo da kasa banbance makamar rikewa. Hakan yasa a cikin watan azumin nan dukkan addu'oina suka karkata ga al'amarinta. Sai gashi ya sake zuwa min da batun gwaji, yau kuma gashi kun tabbatar mana da komai ALLAH ya saka muku da alkairinsa, ya baku kariya fiye da wadda kuka zama sanadin bama wanna yarinya da ahalinmu bisa zartarwar UBANGIJINMU da ya sakaku zama sanadi. Yanda UBANGIJI ya hada jininmu a duniya, muna fatan ya hadamu a aljannarsa.Ina farin ciki matuka da kasancewar Fhareedah a cikin jikokina jinina, dan ita abar so ce ga kowa". A tare duk aka amsa da Amin kowa na sharar kwalla. Kafin kuma rikici ya balle tsakanin Ummu da Mammy (Daneen Ammarah) akan Iffah. Ummu ta tabbatar har yanzu Iffah bata sauya ba kuma bazata taba sauyata matsayin wadda ta haifaba a zuciyarta ba. Tana mata kauna irin wadda takema su Hanash, dan haka bafa zata barma Daneen Ammarah ba. Itako ta marairaice mata akan tunda ta dana na shekara goma sha tara itama ta barta tai goma sha tara sai a koma yar sati-sati. (Iffah mai iyaye da yawa😂) Dariya Kaka da Mammah da lyyani da Hanash, Daneen Waheeda suka dinga yi musu. Shi dai Babiy kansa a kasa yana murmushi kawai, lokaci-lokaci yakan saci kallon Mammy din kamar yanda itama take satar kallonsa. Ummu duk tana lure da su, amma sai bataji komai na jin zafi a ranta ba sai ma tausayi da suke bata. Hakama Malikat Haseenat tana lure da su. Sallar la'asar ce ta tada zaman. Fuskar Iffah murmushi da hawaye sun kasa tsayawa. Ana dawowa da ga salla sashen Tajwar Eshaan suka nufa gaba dayansu bisa umarninsa. Kallon Iffah da duk tayi wani sukuku yake ta kasa ido zuciyarsa cike da tausayinta. Tun dazu hankalinsa na kanta, ko abinci bai iya ci ba sai madara kawai da ya dan sha kadan, yata tsammanin shigowarta amma shiru, dan haka ma yama Malikat Haseenat aiken son ganinsu gaba daya. Yau dai kam gasu Baby ga Shahan-shan a zahirancensa dan ko eyeglasses babu a idanunsa ma. Sun mika gaisuwar girmamawa a garesa yayinda shi kuma ya amsa musu da mutuntawa. Sun kara tattaunawa sosai inda shi babu wata kwana-kwana ya bukaci jin ta bakin Babiy da Mamy (Daneen Ammarah) akan maida musu aurensu. Diri-diri sukai su dukansu kamar wanda suka shiga rudani da maganar. Yayinda Kaka da Malikat Haseenat ke murmushi, hakama Hanash da Iffah kallon juna sukai sai kuma suka saki murmushi. Jin kowa ya kasa cewa komai Ummu da tai shiru kanta a kasa ta dago fuskarta da murmushi. Cike da nutsuwarta ta ce, "ALLAH ya karama adalin shugabanmu lafiya da tsohon rai mai albarka. Idan akai hakan tabbas zamu kasance a cikin farin ciki, dan an mutuntamu da karamci mafi girma da ba'a tabama wani a wannan kasa ta ruman ba. Nima zanso kasancewa da yar uwata kodan karta kwacemin yarinyata, why zan shiga wani hali". Ta juya ta kama hannun Baby dana Daneen Ammarah cikin roko tace, "Dan ALLAH karku bani kunya ku amince mu sake zama abu daya. Karan farko Tajwar Eshaan ya saki wani dan murmushi mai ban mamaki, ji yake wata irin kimar Ummu da darajarta ta karu a ransa. Murmushinsa ya matukar birgesu, ya kuma sake sanyasu a farin ciki, sai dai kuma bai sake cewa komai ba..... • MALIKAT BUSHIRAT* Daga kotu da kyar ta iya fitowa zuwa mota, suna isa sashenta dakinta ta shige ta kulle kanta. Jiri take ji da wani irin mahaukacin ciwon kai ga bugun zuciyarta kara hauhawa yake. Shin mike shirin faruwa da ita ne haka, mike tunkaro rayuwarta. Danta Eshaan, Eshaan dai data sha wahala kafin samunsa ne yake auren yar Daneen Ammarah. Mai tambarin tawadar ALLAH a jiki, yarinyar da ke cikin lissafin ayyukansu. Mai tambari dai irin wanda Uwa ta shardanta mata a cikin sharudanta. Mike faruwa haka? Ta yaya hakan zai kasance? _(Ina tayaki murna da albishir din insha ALLAHU kafin mu dawo daga hutun in amarcinmu da iznin UBANGIJI zamu dawo da jikanki a wannan babbar garkuwar, dan haka kibar wahal da kanki akan sai Maleek ya auro wadda kike son ta haifa miki shi dole ko nisanta shakuwar iyayensa da zata zama sanadin samar da shi ta hanyar madara. Da ga kuma randa kika tabbatar da samuwarsa, ki fara irga kwanakin nadamarki da dana sani har zuwa ranar haihuwarsa. Hukunci da karfin ikon Iffah a saman naki, yanzun ne zai fara Mother in-law)_ kalaman Iffah suka shiga mata kaikawo da amsa kuwwa a cikin kunne kamar yanzu ne take fada mata su. _(Ammie na yarda ke Zakanya ce, sai dai ki sani duk karfin bajintarki da iya farauta a saman kowa watarana tsufa kan ¡ya sa ki rissina jikar bayanki ta zama sarauniya bisa karfin ikon naki, Ni bance nafi karfin kaddara ba, sai dai ki sani a tafin hannunna kike ke da komanki....)_. Kuka ta fashe da shi, cikin karaji ta furta "Bazai yiwu ba, bazan dauki faduwaba, wihy Uwa bazan dauka ba sai dai duk mu fadi tare, sai dai ai mutuwar kasko mu dukanmu baki daya" wani irin kuka ya sarketa, wasu kalaman Iffar ne suka sake shiga dawo mata…. _(Ammie wihy inada abubuwan ban mamaki da daga labulen sirrinki sau daya kawai sai ya hana wannan idanun naki barci.....)_ wani irin naushi ta kaina mirror din akin da sake kwala kiran sunan uwa_(…..……To wai nikam wane buri ne kike son cimmawa mai alaka da makiyi a tsakaninki da shi? Kin ko san da ace yasha ganyen shayin nan ko madarar nan illar da zatama rayuwarsa sai tafi wadda zatama tawa rayuwar? Sannan ke da kanki sai kin dawo kina kuka da dana sani. Idan ma wani ke baki wadan nan abubuwan matsayin wani kariya washi ko gurbata tawa rayuwar to tabbas ki farka. Ki farka why tunkan guri ya kure miki ki rasa kofofin fita a wannan masarautar.…)_ "Har abada! Har abadan abada bazan taba faduwa kasa ba, bazan rasa komai ba a lokacin da komai ya zama nawa ba.... "Dole ki rasa! Dole kirasa!! Dole kirasa ta-kurya!!Hahahahaha!!!!". Uwa ta fada cikin karaji da amsa kuwwar mummunar muryarta alokacin da take bayyana. A kallo daya zaka fahimci itama a birkice take. Dan idanun nata sun sake jajur, fuskarta ta sake muni matuka. Da wani irin karsashin wutar bala'i Malikat Bushirat ta fiskanceta, a yau babu wani tsoro ko shakku tare da ita balle girmamawar da ta saba ga uwar. Gabanta taje ta tsaya tana mai nuna ta da yatsa. "Sai dai mu rasa gaba dayanmu, amma ba Malikat Bushirat kawai ba. Miyasa kika yaudareni?.. "Ke kika yaudari kanki, domin a yarjejeniyar mu akwai sharadin kin auren yarinyar data fito a wannan zuri'ar musamman mai tambarin na hakika". "Amma da umarninki ta zama matar Saiful-malik, shin bokancin naki ya fara raunine ko dama ke din mayaudariyace kamar yanda yarinyar ta fada?!!!". "Ki iya bakinki ta-kurya!!!". *Bazan iyaba, nace bazan iyaba uwa. Wihy why, kinji na rantse, bazanyi asarar wahalata ba. Sai dai ni da ke duk muyi mutuwar kasko". "Kece da danki zakuyi mutuwar kasko, kuma dole ki bamu jinin Ajlaan madadin sauran ayyukanmu da baki cika ba!!". "Har abada, har gaban abada jinin Saiful-malik yafi karfinki azzalumar mushirika. Nima da kike gani hatsabibiyar kainace uwa, dan tun kafin ke gwanace a iyawata!!" "Kin san da iyawar taki miya hanaki iyama kanki sai da taimakona. Butulu ke wacece, har wacece ke nace ta-kurya? Har mi kike takama da shi? In ce dai Ajlaan ne ko? Kuma mune muka samar miki da shi a lokacin da kike neman samuwarsa do rufe (Wa'alaikissalam 😭ALLAH ne kadai ke badawa da hanawa a lokacin da yaso, ga kuma wanda yaso. To ki rubuta ki ajiye mune zamu shafe babinsa da tarihinsa, kamar yanda muka shafe na ubansa da kakansa a doron duniya.Idan kin isa, Kin cika sunanki tsagera mu zuba!!!!" Bat uwa ta bace a akin kamar tashin guguwa. Wani irin fashewa da kuka Malikat Bushirat tai cikin ihu da fisgo duk abinda ya tare mata gaba ta dinga ratsawa da kasa. Jikinta want rin jiljigar rawa yake na masifa, da ga karshe ma kawai sai ta yanke jiki ta fadi dan jini ya balle mata sosai saboda raunikan da ta jima kanta a dalilin fashe-fashe.….✍️ 🥱 Tofa anzo wajen kenan, wannan da alama fadan cikin gidane fa. Akwai kuma babban kulli akan haihuwar Tajwar Eshaan ma kansa 🤔. 🚴 Bari dai mu cigaba da bin uwa da diyarta muga yaya wasan zai kaya ne. DAUDAR GORA Book2 Chapter 78 .....…..Bayan idar da sallar magrib dunbin al'ummar dake cikin masarautar ruman suka shaida daurin auren Zayyan ibn Abbas Jumna. Da amaryarsa Ammarah bint Abdul-majeed Aliy Qutb, akan sadaki mai darajar gaske, inda Kaka ya zama waliyyin ango, Tajwar Eshaan ibn Haysam Abdul-majeed Aliy Qutb ya zama waliyyin amarya. Ba mutanen daular ruman bane kawai suka girgiza, masarautar ce gaba dayanta ta girgiza da wanna al'amari na bazata. Duk da ana cikin dunbin jimami na abubuwan da suka faru a kotu yau, babu wanda yay zato ko tsammanin faruwar abinda ya farun kamar haka ba. A take sabon topic ya sake barkewa a saman wanda dama aka yini anayi har a cikin hadimai… ** Tun bayan sallar la'asar da suka shigo da su Kaka bata koma ba tana a sashen nasa. Dan sanda zasu fita domin gabatar da sallar magrib har zata bisu itama Malikat Haseenat ta dakatar da ita. Kasancewar sallar magrib da ake kira ita da shi babu wanda yacema dan uwansa komai. Ajiyar zuciya mai nauyi ta sauke a bayan fitarsa sallar, sai kuma ta shiga wanka dan a karo na farko tun bayan samuwar cikinta yau ne take jin zazzabi a jikinta. Doguwar riga mara nauyi kawai ta saka ta tada salla, bayan ta idar ta zauna komai na dawo mata daki-daki kamar wani shirin film. Kuka sosai tayi fiye da wanda tayi a dazun, a haka kunnenta ya tsinkayi shelanta sake aura auren mahaifanta guda biyu da kaddara ta hada. Kuka ta sake rushewa da shi har kanta na mata ciwo batare da tasan dalilinsa ba. Shin farin ciki ne ko sabon rudani, da kyar tai sallar isha'"i ta zame akan abin sallar ta kwanta..... Tana kwance a wajen cikin yar takurewar sanyin zazzabin da take ji ya shigo dakin da sallamar nan tasa ciki-ciki. Bata motsa ba har ya karaso gabanta, jin tsaiwarsa a kusa da ita ya sata bude idanun a hankali ta sauke kansa. Kallon juna suke kamar yau suka fara ganin kansu, kafin itama ta fara janye nata idanun ta mike a hankali. Ganin yanda take dan layi na wandda jiri ke kwasa ya sashi mika mata lallausan farin hannunsa sol mai dauke da dogayen farata. Nata ta daura a hankali cikin nasa, ya dagata gaba dayanta ta mike tsaye a gabansa. Yanda yake binta da kallo kamar sabuwar halitta ya sake raunana mata zuciya, sai kawai ta sakar masa wani shagwabebben kuka da fadawa jikinsa ta kankamesa. Bashi da zabin da ya wuce amsarta hannu biyu shima ya kara matseta a jikin nasa yana mai lumshe idanunsa dake cike da so da kaunarta. Kuka take sosai dake sake sukar zuciyarsa, sai dai baice mata uffan ba har kusan tsahon mintuna uku suna tsayen. Sai da yaji ya daina jin dumin hawayenta dake sauka masa a kan kirji ta koma sauke ajiyar zuciya sannan ya dagota. Mayafin da tai rolling ya warware, yaja hanunta a hankali ya zauna a bakin gado ita kuma ya daurata a saman cinyarsa. "Shi kukan baya isa ne". Ya fada a fisge fuskarta a cikin tafukan hannunsa. Fuskar ta sake kwabewa zata saki wani sabon kukan ya girgiza mata kai da fadin, "Please bana son gani kuma, kin cika shagwaba fa". Shaaa hawayen suka zubo dan ta kasa rikesu, sai kuma ta turo masa baki gaba. Murmushi yayi a zuciyarsa, tare da matso fuskarta dab da tashi ya tura yatsunsa cikin gashin kanta ya zare ribbon din data dauke gashin a tsakkiya ya shiga yamutsa mata shi yana goga mata hancinsa kan nata, lips din ta sake dan turowa, shiko ya samu damar hadesa da nashi kirif. Iya kokari yayi na ganin ya tsaya iya hakan, sai dai zuciyarsa gaba daya taki bashi hadin kai. Sai kawai ya zarce da abinda gangar jikinsa ke tsananin bukata da kwadayi, da ga haka labarin ya canja da salo mai matukar nauyi dake kara tabbatar musu yanda suka narke a so da kaunar juna mai tsananin gaske. Dakin yay shiru sai fitar sanyin na'ura tana lafe a jikinsa cikin muryarta da ta disashe take fadin, "Komai kamar a mafarki ko? Ji nake kamar idan na farka zanga ba haka bane ba Maleek. Har yanzu gaba dayan zuciyata taki yarda da komai dari bisa dari". Murmushi yayi mai sanyi da sake gyara mata kwanciya a jikin nasa, hannunsa kam na'a kan cikinta. Lumsassun idanunsa ya bude a kan kyakykyawar fuskarta da hatta dan kumbura saboda kukan da ta sha a yinin yau. Motsa lips dinsa yay a hankali ya furta "Rayuwar ma gaba dayanta tamkar mafarkice Niger. Yanda muke kwantawa mu tashi da wucewar gobenmu haka kwanakin kaddarar rayuwarmu ke shudewa da abubuwan da suka gabacemu. A duk abinda kikaga ya far a yau tabbataccene da tabbatar rubutun alkalamin kaddara. Wata hikimace kuma da ga hikimomin UBANGIJI. a randa na fara hacuwa dake komai ya cigaba da maimaitamn kansa tamkar mafarkina. Da ga cikin duk abinda ya faru har kina tunanin akwai abinda zai iya gagara da ga tarkar UBANGIJI? "Murmushi ta danyi mai sanyi a karo na farko tare da dagowa tana kallon kyakykyawar fuskarsa. "UBANGIJI gagara misalin masu misali ne ai, duk abinda ya zartar haka yake babu kokwanto ko shamaki a cikinsa. Kai dabanne a cikin daban MIJINA RAYUWATA" tai maganar da dan ja masa hanci. Murmushi yayi mai Kayatarwa da dungure mata kai. Ya ce, "Ai kin fini zama daban. Mai mama biyu, yayu biyu, kakanni biyu, gida biyu, kefa hatta duniyarki biyu ce My sohaa". Dariya ta kyalkyale da shi kamar ba yanzu ta gama rusar kuka ba. Ta kankamesa da fadin, "Idan na hada da taka duniyar ma uku garan FARIN CIKINA". "Oh oh, yarinyar nan fa naga alamar kin fetsare". Yay maganar yana dagota. Gashin da ke a gemunsa ta kamo da yatsunta tana wasa da shi, cikin shagwabe fuska ta ce, "To ai duk karatunka ne, su Ummu ma shaidane ba haka suka baka ni ba, ni da ko kallon mutane bana iyayi cikin ido..." "K din dai dana sani?". Ya fada cikin katseta da dan waro idanunsa waje. Fari ta masa tana murmushi cikin dage gira sama da fadin, "Kaima ai shaidane, saliha dani aka kawo maka ga hakuri ga shiru-shiru"., Mizai yi inba dariya ba, sai da yay mai isarsa tana kallonsa cike da jin dadi sannan ya dungure mata kai. "Wai ke din nan ce mai shiru-shiru, bayan randa na fara ganinki da rashin kunyarki nai karin kummalo. Lallai an cuci masu shiru-shiru kuwa indai aka sakaku. Ke Fitinanniyar nan. Ranar fa harda fadin wai ko Shahan-shan ne sai kin sashi ya tsaya dole. Kai yarinyar nan ke abar toro ce". Dariya ta kyakykyale da shi, sai kuma ta shiga boye fuskarta dan sai yanzu abinda tai din yake bata kunaya ma. Kanta a boyen ta ce, "Wai dan ALLAH ranar bakaji kamar kasa a tsireni ba?". "Ke dai kika tsiremun zuciya ban shirya ba. Danni kadai nasan dauriyar da nayi ban fallasa abinda ke a raina ba tun a wajen". Dariyarta mai tada masa tsigar jiki tayi da fadin, "Nima fa kadan birgeni a ranar, dan kamshinka ya tafi dani matuka da wadan nan fararen idanun masu kyalli kamar madara. Kawai dai ranar haushin kowa nakeji ne sai na samu na sauke akan yaranka. Wai kuwa suna ina ma?". Murmushi kawai yayi baice komai ba, sai da ya mula da kansa sannan ya magantu. "Uhm ashe nayi babban kamu tun a ranar faro amma aka tsiwaceni tas. Ke ta dabbance yar kanwata. Su Azaan suna nan abinsu, ma'aikata ne a gidan jaridata ta AFRICAN EYE. Inda kika so zuwa ki tone mun asiri da min zigidir a bainar nasi ALLAH ya taimakeni". "Shine ka tareni ko? Ashe dai kanajin tsorona?". "Kai sosai ma kuwa. Mra Eshaan ko bakin nan naki da baya gajiya da magana ai yasa aji tsoronki." Harara ta dan masa tana tura bakin, sai kuma kamar wadda aka tunatar ta ce, "Wai dama dan ALLAH gidan jaridar Africa eye naka ne?". Kai ya gyada mata idanunsa a lumshe ya ce, "Shine burina na farko dana cika bayan kammala karatuna". "Uhm Masha ALLAH, shiyyasa akema manyan duniya tone-tone ba ragi babu ragowa kuma komai bai faru ba. Amma gaskiya kayi kokari. Nima wannan shine burina" "Ki dauka kin cikashi insha ALLAHU My Sohaa, Kina haifomin babyna makaranta zaki koma, insha ALLAHU arena bazai tauye miki cikar duka burikanki ba. Zan tsaya miki da tsayawar UBANGIJI har sai kin cika duk burin da ALLAH ya rubuto a cikin kaddarar rayuwarki na alkairi". Wani irin rungumesa tai da fashewa da kuka. Hannu biyu ya amsheta yana murmushi. Gain kukan na gaske ne aka sauya masa salon lallashi kamar ba yanzu aka fito a komar ba. Da alama dai Iffah'r mu ta haddace karatun gwarzon nata har sun zama dai-dai,🚴 Hankalin Jasrah ba karamin tashi yay ba da yanayin data samu yar uwarta. Rasama abinda ya dace tayi tai, a rikice tai kiran number likitan Malikat Bushirat din. Cikin kankanin lokaci kuwa sai gashi. Shima hankalinsa ya tashi, dan shi abinda ma zuciyarsa ke raya masa da ban da wanda ke a hakika. Zai zauna bin ba'asi Jasrah ta katsesa da fadin, "Yanzu ba lokacin sanin miya faru bane. Ceto rayuwarta shine mafita first". "Hakane" Ya fada cikin gamsuwa. Da taimakonsa suka maidata saman gado, babu bata lokaci ya shiga aikinsa, ya samu nasarar tsaida jinin, tare da ceto numfashinta da tuni yabar gangar jikinta. A tare suka saki ajiyar zuciya bayan daidaiton komai. Jasrah ta dubesa cikin roko ta ce, "Doctor Please wanna al'amarin ya tsaya da ga ni sai kai dan ALLAH. Dan yana da kyau mu fara sanin abinda ya faru da ga bakinta karmu tashi hankalin mutane. Musamman ma Shahan-shan abubuwan zasu masa yawa. Ga wanna rikicin da yake ciki ga kuma wannan. Shima mutum ne kamar kowa yana bukatar sassauci". "Gaskiya ne ranki ya dade. Insha ALLAHU baki da matsala. Dan aikina ne wannan. Ki dai kasance a kusa da ita dan zata iya farkawa a firgice kasancewar daga suma muka maidata barci, Sannan gaskiya ya kamata kusan abinda ke damunta Kinga wanna fa shine karo na biyu, zata iya samun matsala idan haka ya cigaba da faruwa. Dan yanzu haka da kyar na samu bugun zuciyarta ya daidaita, ga jininta ya hau matuka sai tana samun kulawa lafiyarta zai samu daidaiton da muke bukata". "Insha ALLAHU Doctor za'a kiyaye". "ALLAH ya tabbatar, zuwa safiya zan kawo magunguna ko kuma zuwa anjima kadan" "Okay inaga ka kawo anjima din zai fi". "Shike nan bara naje sai na dawo"….✍️ 5:21 m DAUDAR GORA Book2 79 …..Bayan wucewar Doctor jagwaf Jasrah takai zaune idonta akan yar uwar tata. Abubuwane da yawa ke mata kaikawo, ga dunbin mamakinta da al'ajabin wai mike faruwa haka? Ko ita dake a cikin halin tashin hankalin hallayar mijinta batajin tana a rabin wannan yanayin. Amma ita da bata nema komai na rayuwa ta rasa ba tarasa mike faruwa da ita. A kwanakin nan fa har rama tayi, sannan zaka ganta jigum kamar mai tunani duk ta hargitse. Gaskiya ta fara ji a ranta lamarin ya fara zarce na kiyayyar Iffah kawai. Akwai dai abinda take boye musu da ya kamata ace sun sani, dan al'amarin ma kamar gaba- gaba yake. Jiba dai yanda ta hargitsa dakin yau gaba daya, ta fasa abubuwa masu daraja da tasan ko sanda suna yara bata bari su taba mata. Tashi tai da kanta ta gyara komai, dan kiran wata hadima ta gyara kamar yana nufin fitar zancen ne, dan hadimai da yawa dake akowane sashe zaka samu an leken asirin wasu ne. Musamman ma ita da girman ikonta yasa kowa kunnensa bude yake da son jin labarin wani al'amari ya bullo da ga gareta makamancin haka. Tana cikin gyarawar doctor ya kirata ya dawo, ajiye aikin tai taje ta amso magungunan ta daw sannan ta karasa gyara komai ya koma need. Gabannin asuba ta farka a wani irin firgicen da yafi wanda ma Doctor ya ce zata iya tsintar kanta a ciki. Yanda jikinta ke rawa haka gadon ke rawa, ta fasa wata irin gigitacciyar kara ganin halittun da suka firgitata a cikin barcinta zahiri muraran a cikin dakin. Gaba daya sunma gadon zobe ga wani kalar kuka da sukeyi mara dadin saurare a cikin kunne., Sotake ta ambaci sunan ALLAH koda sau daya ne amma bakinta ya gagara furtawa, sai rawar da lips dinta keyi kamar yanda jikin nata ke rawa. Duk da sanyin ac dake dakin ita a jike take sharkaf da zufa kai kace wanka tayi. "Hahahaha!!!!" Uwa ta bayyana cikin mummunar dariyarta. Kamar koda yaushe a kan kujerar tata take cikin jajayen kayan nan. Mummunar fuskarta ta tsufa ta sake munancewa tsabar itama bata a cikin hayyacinta.Dariyar ta sake kyakyalewa da shi da fadin, "Kikace zaki ¡ya hahaha! Dama na fada miki ke karamar mara kunyace Bushirat, k! Karamar tsagerace!! Hahaha!!!!! Daga yanzu zuwa ranar cikar burina saina dandana miki azaba, kisa a ranki yanzune wasan zai fara na gaskiya. Kuma dole ne ki biya diyyar da jinin dan da mune mukai sanadin samuwarki garesa (Wa'iyazubillah🙏) da ga karshe zan tona miki asiri ta yanda jama'arki su zasu idasamin rayuwarki karamar yar iska kawai butulu. Hahahaha!!! Kuje gareta, ku sauyamun kamaninta". Ta fada cikin bada umarni ga munanan halittun nan ita kuma tana bacewa. Wata irin zabura sukai kanta, hakan yay dai-dai da bude kofar da Jasrah tayi a rikice, dan ta farka saboda kiran sallar asuba kawai ta dinga jin kamar dokuna na sukuwa a cikin masarautar, shine ta fito a zabure, amma maimakon jin da take duka masarautar ne sai taji kamar a dakin Malikat Bushirat din ne kawai, shine ta nufo nan a rikice. A take duk suka bace batare da taga komai ba, sai Malikat Bushirat da gaba daya ta gama fita a hayyacinta. Sallallami ta dauka tare da haurawa gadon a rikice, bata kawo komai a ranta ba face maganar doctor da yace dama zata iya farkawa a rude, ita kuma ta koma daki ne dan taji yace zata iya kaiwa ma safiyar gobe bata farkaba saboda nauyin allurar da yay mata. Rikota tai ta rungume a jikinta hawaye na ciko mata idanu na tausayin yar uwar tata. Zuciyarta ta fara bata kodai asiri akai mata ne wai.... **.. Itama a gabanin asubar ta farka a razanen da ta saba a duk sanda tai mafarki mai nauyi irin haka. Ta dafe kanta dake sara mata tana mai karanto addu'a. Taja kusan minti biyar a haka kafin nutsuwa ta dan dawo jikinta. Hannunta ta janye da ga saman kanta tare da kai dubanta ga Tajwar Eshaan da ke getenta yana barcinsa hankali kwance. Fuskarsa ta tsurama ido kamar mai son karanto komai data gani a cikin mafarkinta kan fuskar. Ta jima batai mafarki mai sakata a rudani irin wannan ba. Itakam wadan nan abubuwa sun fara damunta, Shikenan da ga wannan sai wannan kullum babu hutu, da anyi maganin wannan sai was su sake ballowa wace irin rayuwace wannan. "Ya rabba ka kawo mana iyakar wadan nan musibu". Ta fada a hankali tana sauke ajiyar zuciya. Yunkurawa tai zata sauka a gadon taji an rikota. Juyowa tai ta dubesa dan sam batai tunanin ya farka ba. Maidota yay ta hawo saman jikinsa, cikin yanayin muryar wanda ya tashi a barci ya kai hannu saman wuyanta da fadin,"Zazzabin ne?". Kai ta girgiza masa a hankali. Cikin yar damuwar mafarkinta da bai gama sakinta ba ta ce, "A'a na farka ne kawai asubama yay". Ajiyar zuciya kawai ya dan sauke batare da ya sake cewa komai ba. Itama sai ta sake yunkurawa ta mike.... Tana idar da sallar asuba ta fito a dan harzance, dan so take taje ta dawo kafin ya dawo da ga massalaci. Sashen Malikat Bushirat ta nufa a yanayin badda kamar data fito. Kasancewar da dan sauran duhun asuba duk da ko'ina zagaye yake da haske babu wanda ya fahimci wanene a cikin tsirarun hadiman da suka fara ayyukansu. Koda ta shiga sashen ma tsirarune a hadiman suka fito fara shara. Cikin dabara ta dinga wucesu batare data yarda kowa ya ganta ba. Koda ta iso kofar dakin da zuciyarta yafi karkata da samunta sal data dan nutsu a kofar domin tabbatar da babu motsin komai sannan ta murda handle din a hankali ta shiga. A hankali ta sauke ajiyar zuciya tana bin dakin da kallo, babu kowa a ciki sai Malikat Bushirat din da ke zaune jingine da gado tana sallah a haka. Da alama bazata iya yi a tsaye ba. Key ta murzama kofar sannan ta karasa shigowa cikin dakin, dai-dai da ta idar. A dan yatsine Iffah ke mata kallon mamakin gain yanda tai wani irin zuru-zuru, duk rashin gane abubuwan mutum idan ya kalleta yasan akwai matsala a tattare da ita.... "Miya kawoki nan?". Ta fada muryarta a shake sai dai cikin bacin rai. Baki Iffah ta labe itarna cikin tunzura ta bata amsa. "Kin san abinda ya kawo ni ai. Wai ke dan ALLAH bazaki dawo cikin hayyacinki ba. Inata nuna miki hanya, inata miki kanta farga amma kin kasa fahimta saboda son zuciya ya toshe tunaninki. Wai shin dole ne sai kin saka rayukan masoyanki cikin kunci da bakin ciki ne. Wlhy ki fadama bokanyarki ta fita a hanyata, danni nafi karfin ta da izinin UBANGIJI, hakama shi wanda kuke fadan a kansa yanzu duk da dank ne. Ta shiga hankalinta ta tsaya a iya kanki ke da kika gayyaceta a rayuwarki. Why duk randa ta sake gigin zuwa sashenmu sai kunyi nadama da ga ke har ita. Ni babu abinda ya shafeni da abinda zata miki matsalarkice wannan, tunda na nuna miki qujema irin wanna ranar tun kan tazo amma kika nun ban kai ba. Idan kuma ta cika cikakkiya dan ALLAH ta zo gareni a zahiri taga ikon ALLAH, wlhy sai na sauya mata kamannin halitta da tambarin da harta mutu bazai gogu a jikinta ba". Tana gama fada ta juya tal tafiyarta fuuuu ta fice tana bugo kofar. Da kallo kawai Malikat Bushirat ta iya binta, zuciyarta na.raya mata anya kuwa (wannan yarinyar mutum ce? Koma dai wanda aka kira uban nata bashi bane Aljanun Ammarah din ne suka mata cikinta).…... Fitowar Jasrah da ga bayi ya katse mata zancen zucin. Sai kuma yanda Jasrahn ke mata kallon tuhuma da rudani ya sata shan jinin jikinta, ita sai yanzu ne ma hankalinta ya dawo jikinta. Duk da abinda yarinyar nan ta fada kenan Jasrahn ta jisu tunda tana a cikin bathroom... "Akia!". Jasrah ta katse mata tunanin. Dan firgigit tai ta dubeta. Sai dai ta kasa amsa mata. Babu alamar wasa tattare da Jasrahn ta sake fadin, "Akia kamarfa maganar Zawjata-almilk naji, shin wane maganganu take fada miki haka masu rudarwa? Mike faruwa ne?". Dauke idanunta tai da ga kan Jasrahn zuciyarta na wani irin gudu a kirjinta...... "Hakan na nufin hasashena nakan gaskiya kenan,Akia akwai abinda kike boye mana tsakaninki da yarinyar nan? Taya kamarki da ke matsayin mahaifiyar mijinta, shugabanta amma tazo tana datsa miki irin mijinta, shugabanta amma tazo tana datsa miki irin wadan nan maganganun cikin kaushin harshe amma ko tari bakiyi ba. Anya kuwa Akia..... "Jasrah!!" Ta fada a zafafe cikin dakatar da ita, muryarta adan kausashe da bata fita. Shiru Jasrahn tayi sai dai ta kasa dauke idanunta da ga kanta. Babu abinda ke mata kai da kawo a zuciya sai kausasan kalaman Iffah masu nuni da akwai wata jikakkiya a kasa tsakaninsu. Sannan kalmar bokanyar nan ya matukar tsaya mata a kahon zuciya ya kasa fadawa... **. Koda ta koma ta iske ya dawo sai dai ya wuce Gym.Ajiyar zuciya ta dan sauke ta canja kayan jikinta ta nufi kitchen. Yau ma da kanta ta hada masa abincin breakfast din, suko masu girkin duk sun tsargu duk da tare da su take yi. Sai dai aikinsu kawai bani kaza yankamin kaza wanke mun kaza. Amma komai ita da kanta ta hada abunta. Ta kuma tsaya a kansu har sai da aka kawo komai dining room din. Ya fito da ga wanka kenan ta shigo da sallama hanunta dauke da tray mai dauke da kofin shayi da keta faman turiri. Ido ya dan tsira mata har ta iso gabansa ta ajiye. "Good morning ". Ta fada tana zuba zuma kadan a shayin. Cikin dan lumshe ido da budewa ya amsa mata da "How Are you". "Alhamdullah". Ta amsa masa itama tana mika masa kofin shayin.Amsa yay dan dama shi yake jira. ya ce, "Thanks". Kai kawai ta dan jinjina masa tana murmushi. Da ga haka ta wuce bathroom dan yin wanka. Kallo ya bita da shi kasa-kasa zuciyarsa na masa kaikawo. Lokacin da take fitowa har ya kammala shiryawa,dan haka ya taimaka mata itama ta shirya cike da tattali da kulawa. A tare suka fito cin abincin gwanin sha'awa. Duk abinda take kallonta kawai yake cike da so da kauna harta kammala hada musu komai. Bismillah ta masa tana masa nuni da abincin da ido ya make kafadarsa yana kauda kai gefe. Hannu ta kai ta dan ja masa kunne tana murmushi, sai hakan yay dai- dai da fitowar amintaccensa da basu san da shi ba da ga cikin karamin falonsa ya gyaro. Da wani masifar sauri ya juya har yana cin ban tuntube dan idonsa ras akan hanun Iffah da ta ja kunnen Shahan-shan din nasu. Itama idanu ta waro da sauri ta mike da sauri ta rungumesa. Dan harga ALLAH bata san bayan su akwai wani a wajen ba. Da kyar ya danne dariyar dake taso masa ya danna mata mintsini a gefen ciki shima, tako zabura gaba dayanta ta haye saman cinyarsa……✍️ DAUDAR GORA Book2 80 ……..• KOTU * Yau din ma kotun ta cika sosai,harma wanda basu halarta a jiya ba yau kam sunzo, Sai dai babu Malikat Bushirat. Dan tana can wani irin zazzabi mai masifar zafi da ciwon kai sun lullubeta har sai da Jasrah ta sake kiran likita ya dubata. Ta gama shirya ana gama zaman kotun nan gida zataje, dan ita kam har yanzu a cikin rudani take. Zataje ta sanar da babban yayansu da a yanzu shine kamar uba a wajensu komai tunda ita taki fada mata. Maybe su sai suzo su binciki wane irin TAKUN SAKA ne tsakaninta da surukar tata da har irin wadan nan maganganu ke shiga tsakaninsu. Yanke wannan hukuncin ya sata nufo kotun kamar yanda kowa ya hallara. Iffah tare da su Daneen Ammarah da su Ummu yau ta shigo. Dan suna kammala breakfast sashen Malikat Bushirat taje ta gaishesu kasancewar lyyani da Ummu a can suka kwana. Barrister Abdallah Aas da Abu Zainab kuwa tun a jiyan suka wuce gidajensu da iyalansu. Kaka ma kin kwana yay, sai suka wuce gida shi da Babiy da Hanash akan yau sa dawo. Ya kumayi hakane dan yana so suje su tattauna inda za'a nemawa Daneen Ammarah (Mammy) wajen zama itama. Saboda Tajwar Eshaan ya sanar musu ana yanke hukuncin nan zuwa jibi insha ALLAHU Mammyn (Daneen Ammarah) zata tare gidanta. Shine karshen shigowa. A take kotun ta sake nustuwa kayin kowa a kasa har sai da ya kai zaune.Kamar ko yaushe Sayeed Hanifud-Din ya fito hannunsa rike da takardu. Bayan yay gaisuwar girmamawa da Shahan-shan aka fara gabatar da Shariar. "Bayan jiya kotu ta gama sauraren bayani da ga bakin Arshaan wata shari'ar mai alaka da juna ta sake shigowa a cikin zaman. Inda muka saurari babban al'ararin da ya rikita kowa har sai da aka yanke wannan zama da alkawarin yau za'a kawo karshen komai. To Alhamdullah domin tabbatar da abinda muka ji a bakin Arshaan. Da wanda muka ji a bakin dattijon nan gamu yau rike da hujjoji. Hujja ta farko zamu saurari recording din da aka shirya saurara a tun farkon shari'ar ta jiya hakan bai faru ba. To a yanzu zamu ji domin sake tabbatarwa. Sannan zamu gabatar da hadiman da sukai aikin kisan gilla ga Sayeed Khairul-Bashar bisa sawar su Jasim, da kuma bokansu mai suna Barbushi dorin jin karin bayani da ga garesu. Hakama bayanan wanna dattijo duk da a jiya Daneen Ammarah ta tabbatar mana da abinda mukaji itama wanna kotu mai adalci ta saka anvi gwaje-gwaje da zasu sake tabbatar mana da komai., Shugaban jami'ai bismillah" Bayan shugaban jami' ai yay gaisuwa ga Shahan- shan shima ya cika umarnin kotu na saka recording din da aka nada a zaman su Miran Jasim cikin kurkuku batare da sun sani ba. Kotu tai tsit kowa na sauraren kasancewar an saka speaker mai karfi a kowacce kusurwa kowa radam yake ji. Rikicin Miran Jasim da Miran Arshaan tun da ga ranar farkon kasancewar tare a cikin kurkuku daki-daki suna fallashe kansu da zagin juna da tsinema juna har zuwa jiya da safe. Tiryan-tiryan sai ga abinda Arshaan ya fada na fitowa harma da wanda bai fada ba. Jikin kowa da ke kotun duk sai ya kara sanyi. Yayinda aketa la'antarsu da ALLAH wadi da mummunar hallayar tasu duk da fa suma yan zaman kotun akwai masu wasu boyayyun al'amuran a cikinsu suma. Sai dai tunda tasu bata fitoba mai sauki ce. An fito da boka Barbushi shima da tunda aka kawosa masarautar aka rabashi da duk kayan tsafinsa aka aske masa kai da basa kaya bayan an sashi wanka. Gaba daya sai kamanin nasa suka canja kamar bashi ba. Sai faman sinne kai yake kuwa da satar kallon su Miran Jasim kamar yanda suma suke masa kallon mamaki. Shima yay gaisuwa ga Shahan-shan sannan Sayeed Hanifud-Din ya fara jefa masa tambayoyi. "Kane mushirikin da ke basu tsubbun da zasu cutar da mutane ko?". "Ina neman afuwa kuskurene ranka ya dade". "Tun yaushe kake tare da su?". "Mun kai shekara goma sha takwas". "Kace ka dade kana basu lakanin kashe mutane da musu illa?" Shiru ya kasa cewa komai, Sayeed Hanifud-Din ya cigaba da fadin, "Kotu na bukatar jin duk tsiyatakun daka jagorancesu aikatawa". Cikin rawar murya data baki ya shiga zayyane komai. Da ga karshe ya dora da fadin, "Naki fada musu gaskiya ne tun farko saboda karsu daina bani kudin da suke bani. Amma ni nasan anfi karfinsu a duk inda suke kai hari. Bakuma zasu samu cikar burinsu ba har abada". Ba wanda suke a kotun ba hatta Miran Jasim da Miran Arshaan wan irin kallo suke masa mai ban mamaki, sai dai ko sau daya yaki yarda ya dubesu shikam, Bayan shi an fiddo hadiman da suka kashe Sayeed Khairul-Bashar. Inda suka zayyane komai har yanda Miran Jasim ya sakasu aikin, da yanda suka sacesa lokacin da yake fitowa da ga sashensa zaije sallar asuba. Sun azabtar da shi matuka, dan azabtarwarce ma ta kaisa ga rasa rayuwarsa. Sosai wasu ke kuka, iyalansa kam su kadai suka san irin zafin da sukeji a zukatansu. Babu abu mafi ciwo sai gain amintaccen hadiminsa a cikin wadanda suka halakashi. Sayeed Hanifud-Din ya ja numfashi da fesarwa yana mai sake fuskantar kotu. "To Alhamdullah wanna kenan. Sai kuma gwajin kwayoyin halittar da wanna kotu ta bada akai mata tsakanin Zawjata-almilk da mahaifanta guda uku, inda gwajin ya tabbatar da Zayyan ibn Abbas da Ammarah bint Abdul-majeed Ally Qutb matsayin mahaifanta na gaskiya. Wadan nan sune gwaje-gwajen, gashi za'a jaranto.", tiryan-tiryan ya karanto komai, a take matasan nan da Iffah yanzu ta jawo jikinta suka cika kotun da kabbara. Da kyar aka tsawatar suka lafa.Miran Jasim kam sai kawai yaji ya fashe da kuka tsabar yanda zuciyarsa tai wani irin kunci da takurewa waje daya a kirjinsa, Bayan shirun da kotun ta dauka kowa ya zuba ido da baza kunne na jiran yanke hukunci ga Shahan- shan da kuma makarrabansa da ke zaune yau a kusa da shi domin yanke hukuncin. Yaja tsahon mintuna hudu shiru kafin yaja numfashi mai sanyi, cike da nutsuwar nan tasa da kamewa ya motsa tausasan lips dinsa idanunsa kyam akan Iffah ta cikin bakin gilashin daya sakaya su. Tana kwance ne a jikin kafadar Malikat Haseenat idanunta a lumshe da alamar har yanzu batajin dadin. Janyewa yay a hankali ya maida ga takardun gabansa ya sake motsa lips dinsa. "A bisa hujjoji da kwararan shaidu da ji da ga bakin masu laifin wannan kotu mai adalci tayi dubi da nauyin laifukansu da hukunce-hukuncensu masu nauyi daya dace ta musu. Domin saukaka wahalarwa ga kotun ta yankema Miran Jasim da Miran Arshaan hukunci ta hanyar rataya a tsakkiyar al'ummar wanna kasa a dunkule bisa laifukansu..... A take kotun ta dauki kabbara cikin motsuwar zukata da tsananin rudani musamman ga Miran Jasim da Miran Arshaan da sukai wata irin zabura. Da kyar aka samu aka lafa ya cigaba da fadin. "Za'a yanke musu hukuncinne a ranar bikin al'ada dake hada kowa da kowa da za'a iya bukata da fatan su shaida Kafin hakan zasu cigaba da zama a cikin kurkuku, zakuma su bayyana dukkan laifukansu a gaban yan jarida. Bama bukatar wata kungiya a duniya wajen mana katsalandan akan hakan, zakuma su biya diyyar ran yarinyar Sayeed Hifzur-rahaman da ta Sayeed Khairul-Bashar ga iyalansa. Hakama zasu biya kudade masu nauyi ga ahalin Fhareedah bint Zayyan da suka wahalar bisa son zuciya. Bokansu an bashi damar zaman kurkuku na daurin rai da rai idan yana da rabon shiriya ALLAH ya shiryar da shi. Hakama hadiman da sukai musu ayyukansu an yanke musu hukuncin daurin rai da rai suma. Wannan kotu ta sallami wanda ya samar musu da dafin macizai abisa gargadin kiyayewa. Idan ya sake sakaci makamancin wanda yay zai yabama aya zakinta. Haifah za'ai mata hukuncin bulalar aikata Zina tare da zaman kurkuku na shekara goma bisa yunkurinta da hadin bakin son yin kisa. ALLAH yasa mufi karfin zukatanmu, ya yafe mana kurakuranmu mu da zuri'armu da al'ummar mu baki daya". Da ga haka ya mike. Babu wanda ya iya motsawa har sai da ya fice. Kotun tai wani irin harmutsewa kowa na ALLAH wadai da halayyar su Miran Jasim da kuna da tashin hankalin karshen su Miran Jasim da kuna da tashin hankalin karshen su yama hanasu iya duban kowa. Arshaan sarkin rudiya ma kuka yakeyi, dan yayi nadamar biyema Jasim a rayuwarsa duk da shima da nasa kudirin. Amma bai taba samun kwarin gwiwar aikatawa ba sai da suka dunkule. Haka aka wuce da su da kyar da ga cikin kotun aka maidasu kurkukun... Gaba daya Iffah bawani son hayaniyar take ba yau, dan batajin dadi gaba daya saboda gumurzu sosai tasha da uwa a cikin mafarkinta na daren jiya. Ga yanayin da take ciki na laulayi duk da bata jin wani ciwo kafin jiya da rana. Ta riga su Malikat Haseenat baro kotun ma ita, kai tsaye kuma sashenta ta nufa dan kwanciya kawai take bukata da kadaici, Hannu kawai ta iya dagama hadimanta, kafin a takaice ta shige ta bada umarnin a kawo mata dafaffen madara. Cikin sauri kuwa Amintacciyar hadimarta ta amsa. Ita kuma ta shige cikin takun nan nata sai dai yau tattare yake da kasala. Da sallama ta shigo dakin da ya sha gyara sai tashin kamshi masu dadi yake. Ta maida kofar ta rufe. Juyowar da zatai gaba dayanta idanunta suka sauka akan Uwa da ke zaune zama irin na izza da kasaita cikin kujerar ta ta gado ko nace ta tsafi tana wani irin cika da batsewa katon hancin nan nata ya sake budewa….✍️ DAUDAR GORA Book2 81 ...._..Wani irin wawan tsaki Iffah taja mai masifar karfi ta dauke kanta. Babu alamar ko dar tattare da ita ta cigaba da shigowa cikin dakin, kai tsaye gaban mirror din ta ta nufa, dai-dai tana cire bangles din hannunta batare data sake duban inda Uwa ke zaune a harzuke ba ta furta, "A haduwa daya kawai harkin tsorata kin bayyana kanki karamar agwagwa mai wanka da ruwan dagwalon gulbin wasu. Ai nazata karfin ikon naki zaisa ki cigaba da kawomin harin a cikin barci?". "Idan tunaninki ke kin iya to da sauranki". Uwa ta fada cikin tsananin kaushin murya mai fita da dacin da ke har a kasan ranta. Wata yar dariyar rainin hankali Iffah tai tare da juyowa, ta dan jingina da mirror hannayenta harde a kirjinta. gaba da idanunta sun canja kamanni mai firgitarwa. Sama da kasa take kallon uwa da itama nata idanun ke jazur kamar garwashin wuta."Tsohuwa iyawa ba yawan shekaru bane ko kwarewa a mishirikanci. Karkiyi wasa da wannan dagwalon tabon dan shi zameki zaiyi ya kaiki kasa wanwar. Da ace iyawar taki ta cika iyawa, da kin iya a gabar da Iffah bata san komai ba sai UBANGIJIN da ya halliceta. Indai har wannan jinjirar yar kwanaki uku da haihuwa zata bacema ganinki da jinki, basirarki ta toshe a gabar da kike gab da isa ga nasararki ki sake dawo da ita a inda karfin ikonta ke a saman naki to ki sake tabbatar da k ba komai bace face batacciya mai jahilin tunani. Ni wlhy da ga lokacin dana san kana gaba daya sai kika kara komawa kasa wanwar a karkashin kasan tsinin takalmana. Ashema ke karamar kwaruwa ce tunda har sai kin jinginu jikin raunin wasu a fagen cimma burinki. Ashe ke ba komai bace face makaskanciya da dan yanzu UBANGIJI yace mutu dole ki amsa kira a shafe babinki kamar yanda aka shafe na uwar data haifeki harta nuna miki wanna hanyar shiga wutar. To wai ni banda ke din jahilar dabba ce a cikin kaskantattun dabbobi a wannan shekarun naki kike tunanin mulkar kasa irin ruman wai harma da duniya. Oh oh lallai kin cika babbar aladiya wih... "K! Karamar halittar da muka samar da samarwarmu!!… "K! Babbar dakikiyar da ALLAH ya halitta domin zama makamashin wutar jahannama in har bata tuba ba!!!!'". Iffah ta katseta a tsananin tsawacen da har sai da ta zabura acikin kujerar tsafin nata. Cikin rufewar ido da nunata da dan yatsa ta cigaba da fadin "La'ananniya gatalalliya butulu. K! Har wacece da kika isa samar da koda halittar kwarkwata tsinanniya mai kwana da tashi da tsinuwar UBANGIJI tattare da ita.Why wihy ina miki gargadi na karshe, da ga yau idan kafarki ko wanna kujerar tsafin naki ta sake rabar inda nake sai na sabauta miki rayuwa. Sai na miki kisan gilla irin wanda ya kamata ama mushirikai batattu irinki a doron kasa". Ta wani irin rarumi wani dunkulallen abun fulawa na tangaran irin mai tsananin kaurin nan bakinta da bismillah ta wulwula sai gashi ya tarwatse a saman fuskar Uwa. Yanda kasan ta jefa wuka mai kaifin masifa ko mayen karfe sai ga hancin uwa a kasa ya gundulo gaba daya namansa. Dama gashi katon gaske mara fasali. Wata irin gigitacciyar kara uwa ta fasa jikinta ya hau kakkarwa ta dafe fuskar da tai faca-faca da jini da duka hannayenta biyu. Wani Iffah ta sake rarumowa, tana ambatar bismillah kafin ta wulwula uwa ta bace kamar walkiya, sai hancinta da digo-digon jininta da ya faffalatsa kasan harma da bango. Bata fasa wulwulawa ta jefa ba sai ko a keyar uwa da ke kokarin ficewa ta jikin bango ta salon tsafinta. "Karamar yanyan ki tsaya mana, ki tsaya kiga yanda ake jifan shedan a zahirin rayuwa",. Ta kyalkyale da dariya kamar ba ita ke kumbura da cika da batsewa ba da. Sai da tayi mai isarta harda fadawa gado. Sai kuma ta dan dafe kanta dake mata ciwo har yanzu. Dai-dai nan akai knocking kofar, damar shigowa ta bada dan tasan hadimarta ce. Ita dince kuwa dauke da madaran da ta saka a dafa mata. Cikin girmamawa ta ajiye a inda ta nuna mata. Kafin ta bata umarnin gyara wajen da jinin uwa ya faffalatsa, sai dai abun mamaki yanzu babu bantalen hancin uwar da alama dai ifiritan aljanunta sunzo sun dauke.. **.... Kamar wadda aka wurwuro kwallo da ga nesa haka ta fado da ga ita har kujerar tsafin nata a tsakkiyar wasu irin bakaken bukkokin bamboo da ke a jajejin. Firgitaccen ihunta da gumzar azabar da take yasa dajin amsawa, kamar busa kaho wasu irin mutane marasa kyawun gani da mummunar suffa irrin tata suka fara tururuwar fitowa. Duk dinsu babu mai kaya a cikinsu, tsirara suke yara da manya maza da mata, sai dan ganyen da suke rufe iya al'aurarsu kawai. Matan ko da ga samansu ma duk a bude yake tun daga yammata har tsoffi. Cikin kankanin lokaci duk suka zagayeta, yayinda wasu tsoffi da bazasu kaita shekaru ba suka rufu a kanta su kusan biyar maza biyu mata uku. Dagata sukai gaba dayanta ita da kujerar, daya da ga ciki kuma yay saurin yafa mata jan kyalle a saman fuskar datai kaca-kaca da jini. Daya da ga cikin dakunan Bamboo din suka shiga da ita, shikam da yar sabuntarsa kuma babba ne, sai dai cike yake da da was irin tarkacen bakaken gumaka da akaima ado da ja. Kujerar suka ajiye tare da fara zagayata suna was irin surutai da dukawa da tashi kamar wanda zasuyi ruku'u. Tuni nacan waje ma sun tattaru a kofar dakin yara da manya a layi, idan wadan can suka fadi surkullen sai su kuma su amsa musu da ga waje suma suna dukawa da mikewa. Gaba daya jajejin babu wani sauti da kakeji sai wanna surkullen nasu. Haka suka dingayi tsahon lokaci kafin a ciki su fara dibo was ruwa dake a manya-manyan randunan kasa na cikin akin suna zubama Uwa da cigaba da zagayeta cikin surkullen. A haka suka wanke mata jinin fuskarta tsaf, hancin dai ya fita babu kyawun gani sai fuskar ta kara munancewa fiye da da can. Amma jinin ya tsaya. Magunguna suka sassaka mata a ciwukan dan duk ta yayyanke dan ba hancin kawai ba. Bayan sun nutsa itama ta daina mummunan nishin da takeyi sai dai har lokacin a wajige take. Cikin mummunar muryar nan tata ta shiga kwala kiran wasu irin sunaye, jif!! jif!! jif!!! Kakejin abubuwa na fadowa cikin dakin, babu alamar toro a tattare da su, sai dai duk suna gabanta a tsaye kawunansu a kasa alamar girmamawa a gareta, Da wani irin zafin rai ta shiga nuni da bakaken hallitun dake ta fadowa. Ta nuna na farko cikin karaji da fadin, "Keje jajjal, da ga yau na baka umarnin, karka sake barin ta-kurya barci lafiya, a zagaye jikinta da kuraje masu warin da babu wanda zai iya rabarta koda danta ne, a dinga firgitata a ido biyu da cikin barcinta". "Fadi naki, cikawa tawa Uwa magajiyar Uwa". Ya fada yana mai zabura a guje kamar iska ya bace bat. Na kusa da shi ta nuna, shima cikin bada umarnin, "Zurnini kaje ga dan da muka samar mata(Shahan-shan 😱), da ga yau karya sake tunani irin na mutane, a maidashi majanuni, yayta dariya da soshe-soshe. Ya tsani shegiyar matarnan tasa fiye da komai a duniya, nanda kwanaki kadan jininsa halattacene garemu". "Fadi naki, cikawa tawa Uwa magajiyar Uwa". Shima ya fada yana bacewa. Ta sake nuna na kusa da shi shima "Rudde! Kaje ga tsohuwar can (Malikat Haseenat 52 ), ka taya Banou aikinta, da ga nan zuwa kwana uku jininta halattacce ne agaremu". "Fadi naki, cikawa tawa Uwa magajiyar Uwa". "Zambo kaje ga karsugumar shegiyar yarinyar can,ka zukemin gudan jinin da ke jikinta, ka ringa firgitamin ita da wajiga rayuwarta, har saita san wacece Uwa kafin masana nayi gareta". "Fadi naki, Cikawa tawa Uwa magajiyar Uwa". "Gamberu! Ina bukatar jinin shegun iyayen da suka haifi yarinyar nan da umarnin mu (Wa'iyazubillah)". "Fad naki, cikawa tawa Uwa magajiyar Uwa". Wani irin mahaukaciyar dariya ta shiga babbagawa da fadin, "Sai na ga bayansu, sai na haukata rayuwarsu, saina gigitasu. Yanda suka hanamu zama cikin alkaryar kasarmu suma basu isa su rayuwuba. Sai na mulki ruman, sai na mulki duniya, zan zama mafi girma a karfin iko. Matsiyacin tsoho (Kaka) gani nan gareka, nice da kaina zan tsireka a tsakkiyar kasar ruman. Hahahahaha! Gaba daya na wajen suma suka dauki dariya. Dandanan dajin ya dauki amsa kuwwa. Tako ina dariyarsu amsawa take a cikin dajin.. ***** "Akia, an taba ciwo babu cin abinci, ki daure ko kadan kisha madarar nan sai kisha magani". Jasrah da dawowarta kenan da ga gidansu tun bayan tashi a kotu data tafi sai yanzu take dawowa, ta sanar ma babban yayansu komai yay mata alkawarin zuwa kuma duk da dama Shahan-shan ya tura masa sako, dan yana daya daga cikin mashawartansa ma akan yankema su Miran Jasim hukunci, kasancewarsa babban malami masani. Kai tsaye dakin Malikat Bushirat ta nufi, shine ta iske ta farka. Ganin jikin nata duk babu karfi tai zaman fara bata madara mai dumi akan tasha kafin ta watsa ruwa sai tai sallolin azhar da la'asar da suka wuceta. Amma Malikat Bushirat din taki amsa sam, gaba daya ta gama fita a hayyacinta. Lallashinta Jasrah ta cigaba da yi har ta samu ta dan sha madarar kadan. Magungunan ma da kyar tasha. Mikewa tai zuwa bayi ta hada mata ruwan wanka sannan tazo ta kamata ta kaita. Fitowa tai ta barta da rokon tayi wanka koda ruwanne kawai ta zubama jikinta kozai danyi karfi. Kamar jira ake Jasrah ta fita aka fara kyalkyala dariya. A firgice ta fara waige-waige sai dai bataga komai ba. Kuka aka fashe dashi kuma. Nama duk ta kidime tuni ta mike zumbur kamar ba itace aka kawo bayin da kyar ba. Sake kwashewa akai da dariya. Sosai jikinta ke wani irin rawar mazari kamar zata amayo zuciyarta ta baki. Tako ina waigawa take amma babu komai sai ita kadai a bayin. Da mugun sassarfa ta nufi kofa da nufin ficewa. Amma ina kofar ta rufe gam-gam babu alamar zata bude, Tanata kiciniyar budewa akai mata wani irin harrrrr!!! Daga jikin kofar sal ga mummunar suffa ta bayyana, baya taja a razane ta kwalla wata irin kara mai tsananin firgitarwa data saka Jasrah dake gyara mata gadon kafin ta fito zabura itama tayo bathroom din a razane….✍️ DAUDAR GORA....!! Book 2 Chapter: 82 ..A guje Jasrah ta fado toilet din da tunanin ko faduwa tayine tunda taga jikinta babu kwari. Wanwar ta sameta a tsakkiyar bayi sume harta farke hannu da wani dan karfe da akaima bayin ado da shi. Ai batama san ta fasa razananninayar kara ba tai kanta itama a kidime. Jijjigata ta shigayi amma babu alamar rai tare da ita. Sai kawai ta sake fashewa da kuka, dan a rayuwa tana matukar kaunar yar uwar tata, itace ta zame mata uwa a lokacin da suka rasa mahaifiya. Ta mata gata irin na Va da uwa bata taba banbantata da dan data haifa ba. Zama ta iya cewa ta fishi samun gata dan shi an dauke sa a gabanta.Itako tunda tasan kanta a gabanta take,duk abinda tace tana so shi take yimata.Idan tashin hankali yay tashin hankali baka tuna-mai ma ya dace kayi, kuka kawai take faman rusawa tama manta a bayi suke. Diwa da ke tsaye a bakin kofar dauke da kayan lunch da ta kawo ma Malikat Bushirat din ce ALLAH ya jiyar kukan Jasrahn. Dama kuma itace tace ta hado abinci mara nauyi ta biyota da shi. Bata da hurumin shiga dakin sai da izini, ga kuma kukan tashin hankalin da takeji Jasrah nayi. Tray din ta ajiye cikin dan rawar jiki ta fice zuwa sashen Malikat Haseenat. Suna zaune a falo Daneen Ammarah na faman lallaba Ummu ta sake kwana itako ta ce yau sai gida zataje suyi shirin tarbar amarya gobe insha ALLAHU sai ga Diwa ta shigo a firgice. Kallon mamaki gaba daya suka bita dashi, Daneen Waheeda Sarkin masifa ta daka mata tsawa dan abinda Diwar tayi babban tsaurin ido ne. Malikat Haseenat ce ta katseta da fadin, "'a Waheeda wannan ba dai lafiya ba bita a hankali. K! Miya faru ne?". Kuka Diwa ta fashe da shi tana nuna bayanta bayan ta zube a kasa. "Ku gafarceni ranki ya dade, babu lafiya ne gaskiya. Ga Aunty Jasrah can nata kuka a dakin Malikat, da alama akwai matsala ne why, tabbas akwai matsala, dan dama likita nata zaryar dubata tsakanin jiya da yau" Babu wanda gabansa bai fadiba a cikinsu, dan dama basu jima dayin maganar rashin ganinta a kotu ba. Daneen Waheeda ce make cewa kila bata da ra'ayin zuwan ne yau tunda sun san halinta. Gudun kar maganar tai tsaho ga Ummu da take bakuwa a tare da su yasa Daneen Ammarah kauda zancen ta dako wani. Gaba dayansu suka kunduma sashen Malikat Bushirat, Ummu kawai aka bari. A gaban idon Banou da ke tsaye da wata bakuwar fuska a jikin fulawoyi suka wuce.Da wani mummunan kallo suka bisu, sai dai babu wanda yace komai. Su Malikat Haseenat da basu san sunayi ba ko mota suka shiga zuwa sashen Malikat Bushirat din. Sun sami Hadiman sashen Jigum-jigum, dan zuwa yanzu kusan duk sunji irin kukan da Jasrahn keyi. Babu wanda ya saurari gaisuwar hadiman sukai ciki da hanzari, dan suma dai suna shigowa da kukan Jasrahn suka fara cin karo. A bathroom din suka sameta har yanzu, da kyar Daneen Ammarah ta dagata, rungumeta tai cikin jikinta dan ta sami nutsuwa, Malikat Haseenat kuwa inda Malikat Bushirat ke kwance wanwar ta nufa, tattabata ta shigayi. Daneen Waheeda dai na tsaye babu alamar damuwa tattare da ita. Sai ma bin toilet din take da kallo baki a labe. Da kyar Daneen Ammarah ta lallashi Jasrah har ta dan musu bayani a takaice. Dole aka kara kiran Doctor sannan aka saka hadimai shigowa suka kakkamata aka fiddota aka kwantar saman gado. Zuwan doctor ya tabbatar musu ba mutuwa tai ba, ta dai suma ne. Ajiyar zuciya suka dinga saukewa, shi kuma ya shiga kokarin ganin ta farfado, yayinda Malikat Haseenat ke faman tofa mata addu'oi. Wani irin numfashi ta kawo tare da zabura mai karfi, wadda har doctor dole ya kai hannu a kanta domin maidata amma ya gagara shi kadai. Dole Jasrah da Daneen Ammarah suka matso domin taimaka masa. Amma fa sun kasa dan wani karfi na masifa ta musu, ga fisge-fisge tanayi na tashin hankali. (Tofa al'amarin fa babbane) cewar Daneen Waheeda a cikin zuciya tana dan tabe baki. Suko da basu san tanayi ba sunata kici-kicin son gain ta lafa, Malikat Haseenat kuma na tofa mata addu'a. Da kyar suka iya tankwarata, har sun hada zufa sharban kamar yanda itama tayi.Numfashi suka shiga saukewa na jigata. Doctor kuma ya shiga aikinsa. ya sake maidata barci sai dai fa barcin yaki yiwuwa. Dan da ya dan figeta sai ta zabura sai sun sake dannata ta koma kwance. Al'amari fa tun anayi da marmari harya fara gundurar kowa aka karo doctors da was alluran masu karfi sosai da sukafi na farko da akai mata.. Cikin kankanin lokaci zancen rashin lafiyar ya zagaye masarautar. Masu tausaya mata nayi masu farin ciki nayi. Masu kuma fassara al'amarin da wani abu daban nayi. Dan danan labarin ciwon nata ya zama latest topic à cikin masarautar. Dama ga nã hukuncin su Miran Jasim da bai gama disashewa ba. *** Duk wanna al'amarin Iffah nacan kwance tana shan barcinta bata san bikin da ake ba. Dan sai la'asar ta tashi. Wanka tai tayi salla. Bayan ta kammala kimtsawa ta fito neman abinci dan yunwa takeji. Hadimanta da ke dan kus-kus din su suma akan al'amurin Malikat Bushirat din sukai saurin mikewa. Kallo daya ta musu ta dauke kanta, dan har yanzu zuciyarta babu dadi. Zama tai tare da bada umarnin a kawo mata abinci anan. Cikin ko kankanin lokaci amintacciyarta ta jere komai. Ta bude zata zuba mata ta dakatar da ita idanunta kur akan abincin. "Waya dafa wannan abincin?"Ta fada tana kallonsu. Cikin rawar jiki amintacciyar tata ta sanar mata itace da mai girki. Ta nuna mai abincin. Shiru Iffah tana duban wadda aka nuna matan sai faman sinkuy da kai take. Ai bama tasan ta daka mata tsawa ba tace ta dago. Ba ita da taima tsawar ba hatta sauran hadiman sun matukar razana. Dan abu ne da bata taba musu ba. Wani irin kallo Iffah take ma matar rai bace. Jikinta har tsuma yake ga idanunta sunyi jazur na tashin hankali. Duk wanda ya dubeta sai ya razana, idan ma irin su Bily ne fitsari zamu saki a zani😝Dan gaba daya ta juye tabbacin ba Iffah bace. Wani irin shakota Iffahir tayi ta dauke ta da bahagon marin da ya idasa tsurar da sauran hadiman jikunansu suka fara rawar mazari. Marin matar nan Iffah take tamkar ALLAH ya aikota. Gashi ta shaketa da iya karfi. "Ubanwa ya aikoki nan?". Ta fada da wata irin gigitacciyar murya mai matukar razanarwa da amsa kuwwa. Cikin kakarin azaba matar da gaba daya ta gama jiyo kamshin mutuwa da kyar ta ce, "Uwa." "Uwa. uwa. Iffah ta fada kamar mai bitar sunan, sai kuma ta kyalkyale da dariya ta kuma hade fuska. Cikin dage gira da zuba jajayen idanunta a tsakiyar na matar da ke a shake har yanzu a hanunta ta ce, "Ohhhyyyyo ita bata gane karatun kurma kenan. Bakuma ta gane gargadin makawo sai ya doka sandarsa. Shin wai dolene sai ta fusatani ne?!!!!!. Nace sai ta ga ainahina sannan zata tabbatar nafi Karfinta?!!". Ta sake fada cikin karaji tana gwara kan matar da centre table. Wata iriyar wahalalliyar kara ta sake illahirin jikinta na rawa dan fa ta bugu matuka duk da katako ne. Tuni hadiman sun fara sakin fitsari a wandunansu. Yayinda Iffah da bata san sunayi ba tana cigaba da maka kan matar nan jikin centre table. Sai da tai mata ligi-ligi har numfashinta na fita da kyar ga jini yay mata faca-faca sannan ta dagata tsaye, cikin daka tsawa ta dubi amintacciyarta tace a kira mata Ghazi guda biyu. Cikin kankanin lokaci suka iso kuwa. Jefa musu matar tayi taki zube yaraf a gabansu. Rai bace ta ce, "Ku dauketa, a dauremin ita a tsakkiyar masarautar nan". Cikin rawar jiki suka amsa mata da "Umarninki shine abin jiranmu ranki ya dade". Kota kansu batabi ba ta nufi dining, wajen wanke hannu ta nufa ta wanke hanunta da jini ya dan bata, har yanzu a birkicenta take. Bedroom dinta ta koma, babu jimawa ta sake fitowa cikin sabuwar shiga. Har yanzu hadimanta na lafe jikin bango a tsorace. "Ku biyoni da wannan abincin". A zabure duk suka mike, Itako tuni ta ma fice abinta. Kamar yanda ta saba tafiya duk inda take so a kafa yanzun ma hakane. Sai dai yau ko sau daya bata kula gaisuwar kowanne hadimi ba. Koma kallo basu isheta ba har ta isa sashen Malikat Haseenat. Anan din ma babu hadimin data kula Sai dai tana binsu da kallo daya bayan daya. Ganin babu wadda take nema cikin wata irin razananninayar murya ta kwala kiran sunan "Banouuuu!!!" Ba Banou din da taima kiran mafarautan ba, hatta Ummu da Iftihal a dari suka fito, hakama duk wani hadimi dake sashen dama wanda basu san da zuwanta ba har tuntube suke wajen fitowa. Banou da jikinta ke wani kakkarwa ta zube a gabanta, wani irin mari ta kai mata itama tare da shakota ta mikar da ita tsaye. Cikin murya mai razanarwa ta furta, "Ina bakuwar takini?!!!!" Ba Banou din kawai ba, kowa ma a wajen jikinsa rawa yake yi, hatta Ummu data raineta yau ji tai Iffahn na bata toro. Iftihal kam ai tuni ta jike dogon wandon jeans din jikinta da fitsari, jikinta ko tsabar rawa da yake tuni har wayarta taje kasa bata sani ba Banou dake watsal-watsal din kakarin mutuwa ta nuna matar da suke tare dazun lokacin da su Malikat Haseenat ke fita zuwa sashen Malikat Bushirat. Sakin Banou din tai, sai gata a kasa rikica. Tako kwalla karar azaba. Da hannu taima waccan nuni da tazo. Zatai mata wani noke-noke tai wani irin fisgota ta buga da bango. Gaba daya falon ya sake ridewa, Iftihal ta shige jikin Ummu ta fashe da kuka. Cikin karaji Iffah ta ce, "Ku nawa ne?!!". Jikin matar na rawa ta ce, "Karki kasheni, nayi alkawarin zan fada miki duk abinda kike bukata, na rokeki. '"'Na ce dan uban ubanka ku nawa ne?!!". "Mummu biyar ne?" "Kai mi aka aikoka yi? Da har ka koma suffar mata?" "'Z.z zan taimakawa Banou ne mu karasa uwar masu gida, d. d. Dan ta dade anan din tare da ita…✍️ DAUDAR GORA....!! Book2 Chapter: 83 …Babu wanda bai zaro ido ba a falon. Cikin bacin rai Iffah ta ce, "Na fika sanin wannan"Jikin matar na rawa ta cigaba da zayyano mata sauran. Yayinda tuni Ummu dake rude Iftihal mamuke da ita ta yunkura da niyyar zuwa ta nemi Kaka a waya, dan dazun da sukazo sun kawo mata wayarta shima Babiy yana amfani da nashi. Kin sakinta Iftihal tayi, dole sai tare suka tafi. Iffah kam juyawa tai ta dubi hadimanta da ke dauke da abincin data bada umarnin a biyota da shi, ta nuna na hannun amintacciyarta. "Ajiye musu shi suci" Da ga Banou har abokiyar aikin nata kuka suka sanya, dan su suka san abinda suka gani a abincin. Ko kallo basu ishi Iffar ba, tana tsaye a kansu fuskarta kawai abar firgitarwa ce. Haka suka fara cin suna kuka da rokon tayi hakuri, a haka su Malikat Haseenat da akeje aka sanarmawa suka shigo hankali tashe. Dan can sun samu Malikat Bushirat tayi barcin da kyar bayan an rufu kanta da addu'oi. Kallon Iffah da su Banou din kawai suka tsaya yi cirko-cirko. Daneen Waheeda kam tuni ta koma bayan Mammah ta makale, yayinda Daneen Ammarah itama nata kamanin suka fara canjawa dan idanunta sun kada sunyi jazur. Ture abincin Iffah tai da ga gabansu, ta wani irin hankada Banou gaban Malikat Haseenat. "Jeki sakar mata kafafu!!". Cikin madaukakin mamaki Malikat Haseenat ke duban Banou da Iffah. Sai dai razananniyar tsawar da Iffahr taima Banou din ita kanta sai da zuciyarta ta shiga tsitstsinkewa. Banou dake kuka cikin rawar jiki ta kama kafafun Malikat Haseenat, wani fushin kumburi da kafafun sukai tsahon shekaru an kasa gane kansa sai gashi yau yana bajewa, Kusan minti biyu tace mata ta mike, mikewar tai jikinta sai kakkarwa yake, du da girman jikin nan nata ga tsaho amma Iffah dake yar digila gabanta ta zame mata dodo. "Na baki minti hudu, ki dakko tukunyar da kika ajiye a cikin flowers". "Umarninki shine abin jirana ranki ya dade". Banou din ta fada cikin sake gurfana. Suna tsaitsaye har yanzu babu wanda ya iya cewa komai sai ga Banou ta dawo da tukunyarta, A gaban Iffah ta zube, ta bude tukunyar ta shiga fiddo abubuwan da ke ciki. Abinne kamar tsokar nama, duk ta daure. Kwancewa ta shigayi tana sakinsu, firrrr suke tashi kamar tsuntsaye, wasu ko da kyar zakiga sun tashin saboda ta jima tana wahalar da su. Cikin bada umarni ta dubi sauran hadiman ta ce, "Aje a duba duk wanda yake a halin ciwo ya mike a yanzu a kaimun shi tsakkiyar masarautar nan. Ina bukatar Ghazi guda biyu anan". Cikin kankanin lokaci Ghazin data bukata suka shigo, su tasa suka tasa mata keyar su Banou. *Tun fito da Hadimar da ta jibga a sashenta al'amarin ya fara zagaye masarautar. Abin mamaki sanda take fitowa su Malikat Haseenat biye da ita masarautar ta gama cika. Dan sashe-sashe an fito kamar busar kaho. Cikin kankanin lokaci duk wani mara lafiya dake gidan aka fito da shi, harma wanda ba Banou din ce ta tabasu ba. Tana kuka da faman rufe fuska ta tsatstsallakasu. Tana gamawa suma sawa tai aka daure mata su tare data farkon. Dai-dai nan su Baby suke isowa cikin masarautar. Hakama Tajwar Eshaan a rikice Malikat Haseenat tai kiransa ta sanar masa babufa lafiya a gidan da ya kamata ya fito. Dama shirin fitowa yake, dan amintaccensa yazo masa a kidime babu dadewar nan, hakama Sayeed Fayzul-haq ya kirasa shima. Lokaci daya wajen ya dauki shiru sakamakon fitowar tasa, dan abunne da babu wanda yay zato. Kowa a wajen sai da yay kasa da kansa har Iffah, dan a zahirinsa yake kyakykyawar fuskar nan a bayyane, sai dai fa cinkus take babu alamar wasa ko sassauci. Amintaccensa ya ajiye wata yar kujera mai kyau dake a ninke aka budeta. Sai kuma katuwar umbrella da aka bude masa duk da bawani ranar nada zafi bane dan ta la'asar ce ma dake neman faduwa. Sai dai kuma a mamakin kowa ma bai zauna ba. Sai duban Iffah da yay na kusan mintuna biyu. A hankali ya furta, "Mike faruwa". Cike da irin girmamawar dake nuni da ba ita bace ba ta kai kasa gurfane gabansa. Gaisuwa ta fara mikawa,kafin dukkan abinda ke faruwa ta zayyane masa. Idanu ya dan lumshe da sake budewa. Kamar bazaice komai ba sai kuma yay mata nuni da ta tashi, tare da fadin,"Duk da ba itace a tare da gangar jikinta ba kuskurene kai Zawjata-almilk kuma * Malikat * kasa a kowane irin yanayi a gaban al'ummar kasar ta" Wanna furici nasa ne yasa kowa fahimtar ba ainahin Iffah'r bace iskokinta ne yau suka bayyana kansu abinda basu taba yi ba, sannan kuma maganar cikin jikinta tabbataccene tunda har shi da kansa ya kirata (MALIKAT). Neman afuwa suka shiga yi, da tsayawa tsaye akan kafafun Iffah'r. Alokacinne Sayeed Fayzul-haq ya yafito Kaka dake tsaye kawai yana murmushi. Sai da ya fara mika qaisuwa ga Shahan-shan shima sannan ya duba Iffah, kamar yanda sukaima Tajwar Eshaan bayani haka shima kakan sukai masa. Kansa kawai ya jinjina da cire jakar hannunsa ya ajiye. Ruwa ya bukata, cikin kankanin lokaci aka kawo masa. Magunguna ya fiddo da yawa ya shiga zubawa a ruwan nan. Wani irin ihu su Banou suka dingayi da rokon yayi hakuri, bama su ishesa kallo ba ya fara dibar ruwan maganin yana watsa musu. Ihu na gaske suka dinga kwallawa da surutai suna girgiza da gunji. Sai da yay musu ligif sannan ya basu umarnin bayani da bakunansu. Biyun sun tabbatar da su ba mutane bane sun rikidane kawai. Kuma a yau din nan suka shigo cikin masarautar bisa umarnin uwa da Iffah ta raunata a dazun. Banou kam mutum ce ita, sai dai akwai aljanun maita tare da ita, irin kusan duk zuri'arsu ke da shi, dan itama cikin zuri'ar uwa take. Cikin galabaita ta shiga fadin tun sanda take tare da su. "Ni shekarata goma sha tara anan, tun bayan korar uwa da akayi da ga wannan masarauta. Ina daya daga cikin zuriarta da aka kora shekaru masu yawa da ga cikin wannan alkaryar, a da kakanninmu wannan filin masarautar shine garinsu. Amma sanda za'a kafata sai aka tashesu aka canja musu waje. Ransu ya baci matuka da wannan al'amari, dan tunda suka taso anan suka samu iyayensu da kakanni suma, nan kadai suka sani matsayin kasarsu kuma gari, ga abubuwan bautarsu masu tsahon tarihi tsahon shekaru duk an ruguza musu. Dan haka sukaji zafin tashinsu da akai da bata musu wajen bauta da abubuwan bautarsu saboda gina masarauta bayan akwai filaye da yawa da babu kowa a cikinsu miyasa baza ai acan ba. Wannan haushin yasa sukaki zama inda aka basu sukai hijira zuwa cikin jeji. A haka suka cigaba da sabuwar rayuwarsu wadda da kyar suka saba da wajen, sai ya zam duk wanda aka haifa a cikin zuri'ar mu wannan shine labarin da za'a raineka a kansa, da kuma kiyayyar wannan gida. A haka duk muka rayu da burin daukar fansa. Mun dade da shiga jikinku muna muku illa da suffar bokanci, hatta lokacin da kuka samu ambaliyar ruwa a kusan kasar baki daya zuri 'armu ne suka balle wani yanki na kogin da ke zagaye da ku. Mu bamu taba jingina da ku domin mu taimakeku ba sai dan mu ruguzaku, a haka iyayenmu da kakanninmu suka dinga shudewa. Uwa ta kasance mafi girman hatsabibanci da yin tasiri a al'amuranku a cikin duk wanda suka zo da nufin masu taimako a gareku a cikinmu. Duk da dai akaf zuri'armu daga maye sai matsafi, kuma kowannenmu nada abinda yake yi domin ku. Jajircewar uwa da zamowarta mafi iyawa a kan iyawar kowa cikinmu yasa ta zama shugaba a garemu, kuma ita muke fata da gain ta kusa karbo mana wanna masarauta data kasance tushenmu ta koma tamu. Amma sai abubuwa suka fara canja salo a dalilin tsohuwar can (ta nuna Malikat Haseenat) ta kanainaye komai tana faman rushe duk wahalhalinmu da muke gain saura kiris komai ya kare. Dan haka mukaita kawo mata hare-hare amma bam samu nasara a kanta ba. Ana cikin hakan rana tsaka ma sai ga Uwa mun tsinta a yashe cikin mawuyacin hali anci zarafinta a dalilin wanna mutumin da mahaifinsa (ta nuna kaka). Hakan ya mana ciwo matuka, ga uwa nakan gangarar mutuwa, a take muka tattara duka karfinmu wajen cetonta, dan duk karfin dake tare da ita na tsafinmu na gado da ma wanda ta samarwa kanta wannan mutumin ya lalatashi. An bada umarnin wasunmu su sake dawowa cikin masarautar nan, duk da zuwane na kasada ni a kasance a daya da ga cikinsu. Kuma nice nan a kashe Shahan-shan Abdull-Majeed a cikin suffar maciji, dan inada maita mai karfin gaske fiye data kowa a cikin zuri'armu. Bayan mutuwarsa na cigaba da bibiyar rayuwar war masu gida, sai dai na kasa kaita kasa saboda abubuwan kanta, nadai samu nasarar nakasar mata kafafu ta hanyar ciyar da ita abubuwa a cikin abincinta. Amma tun randa na had da Zawjata-almilk abubuwa da yawa suka lalace min, dan tanada iskoki masu karfin gaske, itace ta dakusheni akan abubuwa masu yawa. Ta kuma min daurin da bazan iya barin wannan gidan ba duk da naso yin hakan tun a ranar farko dana hadu da itan. Uwa tayi iya kokarinta itama na son ganin ta fiddani amma ta gagara". Ajiyar zuciya kawai kakeji na sauka da al'ajabin wadan nan abubuwa wai kamar wata almara. Banou da kowa ya sani mafi zama kololiwar amintacciya ga Malikat Haseenat dai, wadda inba abincin data girka mata ba batacin abincin kowa sai Daneen Ammarah. Kai to ai yanzu kowama ba abin a yarda da shi bane hatta hadiman nasu. Kaka ya jefama Banou tambayar, "Mutane nawa kika cutar a shekarun zaman nan naki?" "Ni ban san adadi ba. Amma na halakasu da yawa, dan akwai ayyukan da na dinga ma uwa da yarjewar wata babba a gidan nan. Sannan akwai wadanda na kashe dan radin kaina da wanda na dinga cinyewa cikinsu. Na karshen nan dana cinye shine na Jasrah a randa Zawjata-almilk bata da lafiya…..✍️ DAUDAR GORA Book2 84 ..Salati wajen ya dauka da sallami, kowa na tsinema wa da banou. Cikin girmamawa Kaka ya dubi Shahan-shan da shi gaba daya ma komai ya tsaya masa cak. "ALLAH ya karama adalin shugabanmu lafiya da tsohon rai mai amfani, a ganina barin wadan nan bashi da wani amfani, a samu dutsina a juye musu ruwan maganin nan kawai a musu rajamu anan, dan wadan nan mutane nada karfin tsafin da rufesu ko musu hukuncin zaman kurkuku bazai taba iya magance matsalarsu ba. ALLAH yasa ban shiga hurumin da ba nawa ba". Shiru baice komai ba. Kusan minti uku sannan ya dubi Sayeed Fayzul-haq. Da ga haka ya taka a hankali gaban Iffah. "A gusa daga jikinta",. Iya abinda ya fada kenan. A take kuwa tai hamma jikinta ya saki gaba daya. Rikota yay cikin jikinsa ya rungume. A take kowa da kowa na wajen yay saurin yin kasa da kansa cikin hanzari. Shiko ko'a jikinsa ya dagata cak dagakasa kamar ya manta ma da wasu halittu a wajen yay wucewarsa. 🥱Wannan fa shine ga abin fada babu damar magana 😝 Kamar yanda kaka ya fada kuwa haka akai, tuni hadimai suka cika wajen da duwatsu, kaka ya yayyafesu da ruwan magani, Kamar jira suka shiga diba ana ambaton sunan ALLAH ana jifan su Banou.Ihu suke mai tsananin kururuwar sauti. Amma mutanen nan ko'a kwalar rigarsu. Dama wasu harda fushin Banou tai musu sanadin yaya wasu iyaye, wasu maza, wasu matansu. Dan a cikin wanda ta halakar mafi rinjaye hadimai ne. Babu wanda ya tausaya musu a haka aka jefesu har sai da suka daina numfashi. Kakane ya ce abar gawawwakin a wajen masu su zasu aiko a debe su, dan sune aiken farko da zasu turama kabilarsu. Haka kuwa akayi, sai dai dan daukar da was samari da yammatan gidan sukayi a wayoyi suka saka a social media cikin kankanin lokaci al'amarin yay amsa kuwa. Wasu kungiyoyin kare hakkin dan adam suka shiga caccakar al'amarin a bayyane ta kafafen ya da labari, kafin wasu awanni labarin ya shiga zagaye duniya, ya zama video mafi rinjaye da ke yawo kuma ake kallo..... ** Sun iso gareta a whale, wahalar da duk wanda ke cikin wanna zuri'a sai da ya girgiza. Hakan yasa su yin cirko-cirko da zaman sauraren abinda sukazo da shi. Ita ko tana zaune a cikin kujerar tsafinta hancinta da Iffah ta gundile ya kara saka fuskar munana matuka. Hakama sauran raunikan da taji sun kumbura fuskar ta kara zama humm. Cikin gurfana da garshekar hakin rudani daya da ga cikinsu ya shiga zayyane mata abinda ke bakinsa, "Shugaba wannan aikin yafi karfinmu, ba namu bane ba sai dai ke. Sun halaka Rudde da Zambo da Banou Sun halakasu har lahira uwarmu mai share kukanmu". Yanda take huci har Kirjinta na dagawa sama zai baka tabbacin tafa kai kololuwar hasala. Cikin wata irin mummunar tsawa ta nuna su da yatsanta mai dauke da zurkeken farce. "Ni uwa nizan sakaku aiki ku dawo kuce anfi karfinku. Idan kun gujema mutuwarku acan anan ma ita kuka tarar. Ahamanu a daure min su, a aka angulu ta dakkomin gawawwakin su Banou!!" "Fadi naki cikawa tawa, uwa magajiyar uwa". Wanda aka kira da Ahamanu ya fada cike da girmamawa a gareta. Cikin abinda bai wuce awa daya ba angulu ta dawo da gawawwakin su Banou, ta jima tana kallon gawarwakin guda uku da ke jina-jina da raunikan jifa,hakama sauran mutanen garin tsaitsaye suke yara da manya maza da mata. Sirkullensu a tsafi ta fara sauran suka dauka da amshi kowa ka gani ransa a jagule da bakin ciki. Bayan sun dauka lokaci sunayi ta bada umarnin daukar gawar Banou zuwa dakin gumaka. kasancewar sauran su aljanu ne dama wani ruwa kawai ta yarfa musu namansu suka shiga zaganyewa, a hankali a hankali suka bace bat. "Lokacin da zamu shirya akin gaba-da-gaba yayi, Jajjal ne kawai ya jurema umarninmu har yanzu bai dawo ba. Na sani shi dama mai jajircewa ne da naci akan komai. Kuma duk wani dan da ya cika dan halak a zuri'armu irinsa ya kamata ace ya zama. Kuje maza kuje ku shirya yaki. Sai mun sabauta gaba daya al'ummar kasar ruman. Sai mun sake dawo musu da tarihi irin na baya koma mafiyinsa. Kuje maza kuje!!!!!" Wani irin hun fusata suka fasa a tare ikkunansu na jujjiga irin an kada musu gangin nan. A take kowa ya nufi dakinsa na Bamboo suna kwada kiran sunan babban gunkinsu suka shiga shirin yaki. Ba wai wuka ko bindugu suke tanada ba. A tsafinsu suka shiga sake tsimawa. Shiri suke karshen shiri dan gaske. Maza da mata, yara kuwa anata faman tsumasu da abubuwa.…. Babu wanda ya sake fitowa sai cikin dare, inda aka dakko gawar Banou dake tire jikin wani katon mashi aka kafe musu a tsakkiya. An yanke wasu sassan jikinta da ke matsayin hakkin uwa, su kuma suka rufu akan gawar suka dinga yagar namanta sunaci da ihu kamar wasu kiyashi sun samu nama, suna kwala kiran sunayen gumakansu da dodanni Jejin har wani girgiza yake saboda tashin sautin muryiyinsu….. (😱😱🏃‍♀️🏃‍♀️🏃‍♀️) Washe gari an tashi masarautar a rincabe da tashin hankali kala-kala matuka. Dan haka kawai aka samu gawawwakin hadimai da Ghazi da jami'an taro sama da hamsin an musu kisan gilla a daren jiya. Ga Iffah tun fitar aljanun nan jiya da ga jikinta barci kawai take, lokacin salla ne kawai idan yayi take tashi da kyar tayita. Tana idarwa kuma zata sake komawa ta kwanta kamar wadda tasha wani abu ko batun abinci ma ba'ayi. Tashin duniya Tajwar Eshaan yayi amma taki tashi in har ba lokacin salla ne yayi ba. Ga a jiya da dare yaje ya duba Malikat Bushirat dake ta faman zabura da ihu sam batai barci ba itama jikin ya sake rikicewa. Hakama duk wanda ke zagaye da ita bai barci ba. Safiyar yau kuma kawai ta tashi da wasu irin manya-manyan kuraje masu radadin azabar zafi dana kaikayi. Kuka kawai take tana rokon a cire mata. Ga sunayen Zawjata-almilk da suka rasu sai lissafowa take daki-daki wai sunzo zasu kasheta, sun zo daukar fansa. Gaba daya kowa ya kasa fahimtar komai da ga zantukanta, sai dai duk mai imani ya ganta sai ya ji tsoron ALLAH ya sake kamashi. Kusan a tare babban yayansu da Kaka da akaima kiran gaggawa cikin masarautar suka iso. An fara taruwa an ma gawawwakin wadanda aka rasa salla harda Tajwar Eshaan, bayan an kammala biznesu ne kuma aka rufu kan Malikat Bushirat da zuwa yanzu kurajen duk sun rure da ruwa. Duk wanda yay mata kaikayi ta sosa kuma azabace mai zaman kanta. Shiru kawai kaka yay yana kallonta, yayinda duk wanda ke cikin dakin dan yan uwanta duk sunzo kuka suke sosai. Babban yayansu da shima ke kallonta ya juyo yana duban kaka. Cike da girmamawar kasancewar ya fisa shekaru ya ce, "Baba wannan aikin jinnu ne kam tabbas. Amma miya hada Jinnu da Bushirat duk da dal an sanar min da dambarwar da ake fama da ita a gidan. Ajiyar zuciya kawai kaka yayi kamar bazaice komai ba. Sai kuma ya nisa a hankali da fadin, "Wannan al'amari ne kam da ya kamata muji a bakinta, dan babu rami babu abinda zai kawo rami kam. Ambaton sunayen wadanda suka mutu da fadin karsu kasheta da take babbar ayar tambayece a gareta Abni". Babu wanda bai gamsu da zancen kaka ba a wajen, sai dai kuma hankalinsu ya tashi da jin abinda ya fada din. Dai-dai yana fiddo wani magani Tajwar Eshaan ya shigo dakin rike da hanun Iffah da farkawar ta kenan ta zabura. Riketa yay amma ta rokesa ya barta sashen Ammie zataje. Shima bai jima da baro sashen ba, dan tafiyarsa babu jimawa su kaka suka shiga. Zaunar da ita yayi sannan shima ya kai zaune, take aka shiga mata sannu sai dai babu wanda ta amsawa. Kaka da babban wan su Malikat Bushirat din suka sake mika gaisuwa ga Shahan-shan dan sun gaisa tun shigowarsu masarautar. Da ga haka Kaka ya bada maganin da ya fiddo yace amata hayaki da shi. Cikin sauri suka amsa aka zuba a burner da aketa bulama turaren wuta saboda kurajen Malikat Bushirat din duk wanda ya fashe wari yake yi kamar an tono rubabben nama a cikin kasa. Wani irin fisge-fisge ta dingayi da hun da ya saka Tajwar Eshaan lumshe idanu kawai idanunsa sun kada jazur abin tausayi, shi Iffah ta tsurama ido, ji take da'ace tanada damar sashi ya bar masarautar nan a yau data sakashi, dan sam bata son ai wannan tone-tonen a gabansa. Amma yaya ta iya, bazai yuwu ace a wannan dambarwar babu shugaban wanna kasar gaba daya a cikinta ba. Malikat Bushirat ta jima tana fisge-fisge gashi babu damar taba ta saboda kurajen jikinta itama in ta taba radadi take ji, dan kanta ta lafa bayan ta gama jigata. Yanda ta nutsu yasa kowa tunanin ma Kota mutu ne. A razane Jasrah ta shiga kiran sunanta tana kuka, sai da Kaka yace ta kwantar da hankalinta tanada ranta, turaren zai rage mata radadin kurajenne matuka. llai kuwa sai gashi ta bude ido. Gaba dayansu tabi da kallo daki-daki, yayinda wasu keta tofa mata addu'oi kamar yanda yayanta ya basu umarni tun dazun. Wasu. hawayene masu radadi suka shiga zaryar zubo mata lokacin da idanunta ke sauka akan Tajwar Eshaan da Iffah. Ta jima tana kallon su, sai kuma ta sake fashewa da kuka. Yayanta ne ya katseta da fadin, "Sai hakuri Bushirat, kuka baya daya da ga cikin mafita, ki daure ki sanar mana abinda ke faruwa domin musan makamar rikewa wajen yimiki magani. Shin garin aya wadan nan abubuwan masu alaka da aljanu ke zagaye da ke? Minene kuka sani ke da Zawjata-almilk da mu bamu sani ba? Mi kuke boye mana da Jasrah har taji kuna sa'insa a shekaran jiya?". Idanu Tajwar Eshaan ya bude da sauri ya zubama Iffah idanunsa da suka kada jazur, amma ita sam taki kallonsa ga fuskarta kicin-kicin kamar yanda tashin take, Malikat Bushirat kam kuka ta sake fashewa da shi. Kafin a hankali ta motsa lips dinta wajen fadin, "Ni na jama kaina Akhi. Ni na siyama kaina komai. Komai kuma ya farane a dalilin HAIHUWA. a dalilin neman haihuwa da tsananin bukatar samuwarta. Buri da kwadayin gani da son haihuwar magaji shine silar labarin zamana a wanna masarautar da ma duk abinda na aikata a tsahon shekaru arba'in da a yau nake girbar abinda na shuka tun daga nan duniya........ 🤔Tofa UBANGIJI gagara misali, Nama rasa abin cewa. DAUDAR GORA Book2 85 ."Duk wanda ya sanni tun a kuruciya yasan ni yarinya ce mai yawn kirinki, nayi rashinji matuka, dan a fada biyar da za'ai dani cikin yara to da wahala ka samu daya a ciki da nake da gaskiya. Tun ina karamata na kasance mutum mai son gain kowa ya zama a karkashin ikona. Hakan yasa ban yarda da abota da wanda muke shekaru daya ba ko ko sukafi gidanmu arziki. Duk kawayena na girmesu, na kuma fisu wayo, gidanmu kuma yafi nasu komai. Hakan yasa dole sukemun biyayya da bin abinda nake so koda ace su basa son sa. Mahaifiyarmu na yawan mun fada akan wannan halayyar, hakama mahaifinmu. Nakan nuna naji na dan wani lokaci amma da kura ta lafa sai na koma gidan jiya. A haka na taso da wannan rayuwar har girma. Kowa yasan Bushirat boss ce a cikin kawaye, idan kuma kana son ka zauna lafiya tilas ne kamun biyayya. Gidanmu gidane na manyan mutane, masu ilimi kuma Alhamdullah munada dukiya. Ina alfahari da hakan, amma kuma inada buri na kai da kai. Kasancewata kyakykyawa nayi samari kala-kala, duk da dokar mahaifinmu shike zabama kowace yarinya a gidan mu miji, a nawa bangaren babu wannan ra'ayin. Sai dai na shanye ban taba sanarma kowa ba. Duk wanda zai zo gurina sai nayi duk yanda zanyi na bibiyi nasabarsa da nauyin aljihunsa, idan ka kasance baka da ko sisi zan tattaraka na watsar, tare da kashedi mai girma na ka fita a hanyata. Wasu sukan barni cikin sauki, wasu ko saina yi jan ido kona hada musu tuggu a wajen yayuna sun kore su. A haka na kammala karatuna na boko, wanda na taso naga anayi a gidanmu kam shima na samu gwargwadon iko wat ilimin addini. Sai dai sam bana maida hankali garesa, dan ni salla ma sai mahifiyarmu tamun jan ido. Da girmana da hankalina nasha daukar azumi na karya batare da an sani ba, kawai dan inajin wata kaina sama can. A haka wata rana naji Akhi kazo ma da baba batun wai Miran Haysam mai jiran gadon karagar mulkin Shahan-shan ya baka zabin nema masa matar aure. Kai kuma kayi tunanin dubawa a cikin yarn gidanmu amma har yanzu baka gama yanke hukunci tsakanin ni da Hubba ba. Abinda ya girgizani shine, jin Abie kai tsaye ya furta ("Uhm-uhm Muhammad, ajiye maganar Bushirat gefe, bata jin magana, sakata a babban gida irin wannan zai iya zubar mana da kimar mu da nuna gazawar tarbiyyar da muka baku. Yarinyace mai kaudi da hange, ina tsoron al'amarinta. Akance a cikin yaya an fidda maka zakka, to tabbas Bushirat ni itace zakkata. Ka bashi Hubba kawai zamuyi alfaharin da ita") wannan bayani na Abbie ya tayarmu da hankali matuka. Dan ga koshi ga kwanan yunwa ne. Zama nai naita nazarin mafita, dan har wata zuciyar na bani shawarar kashe Hubba dan itace kawai matsalata.Naki karbar wannan shawarar, dan ko yaya ina matukar kaunar yan uwana, Haka na cigaba da saka ido a duk motsinka da na Abbie, sai dai shiru bakayi maganar ga Hubba ba balle iyayenmu mata. Dan duk da mahaifiyarmu ta rasu wajen haihuwar Jasrah bamu taba kukan rashin uwa ba ga matan babanmu, sun rikemu hannu biyu tamkar sune suka haifemu. A cikin dogon nazari dana bama kaina kwana biyu a samo mafita. Ranar na yini cikin farin ciki sosai dan inaji a raina na gama zama matar Shahan-shan. ALLAH kuwa ya yarjemin, dan a randa na gama yanke wanna shawara a bibiyar Akhi da nakeyi da Abbie na samu jin Akhi zai tura sako ga Miran Haysam ibn Abdul-majeed Aliy Qutb na zabin matar da ya nema.Tuni na garzaya na rubuta wasuka mai nutsuwa tare da saka hotunana a ciki da dama na tanada. Dakin Akhi na lallaba batare da sanin kowa ba, nai sa'a kuwa yana wajen karatu dan haka a shiga bincike dakinsa. Na samu nasarar gain hotunan Hubba da ya shirya tura masa cikin jin dadì na kwashesu na ajiye nawa da wasikar nan na sake sabon manne envelope din. Gudun a yanka ta tashi na kone hotunan Hubba a cikin toilet batare da sanin kowa ba…. Kamar yanda Akhi ya fada ya aika sakon Miran Haysam batare da sanin na canja hotuna ba. Kwana biyar tsakani sai ga masu neman aure sunzo. Hankalina ya tashi naita kaikawo da neman hanyar da zanji yaya akai amma ban samu ba. Dole na hakura har bakin suka tafi Abbie da Akhi suka shigo gidan. Cikin muryar damuwa najiyo Abbie na sanarma Ummu cewar maganar da sukayice ta taso, sai dai sabanin Hubba da su suka zaba shi yanzu ya aiko cewar Bushirat, harma sun rasa a ina ya sanni. Kokwanton da suka shiga yasa Akhi tashi da kansa zuwa masarauta dan tabbatar wa. Amma magana daya ce dai Bushirat ya zaba. Babu alamar damuwa akan fuskar Ummu tace ai duk kai da kaya mallakar wuyane ALLAH yasa haka shine mafi alkairi, dan itama dai batai magana bane kawai amma abin na damunta. Kar ace dan Hubba yarta ce aka tsallakeni aka bata alhalin nice babba. Oho ko dar banji da kalamanta ba, ni dai tunda burina ya cika damuwa ta kare. An shiga shirye-shiryen biki, yayinda niko keta nokewa kamar bana so dan harda kukana. Sai gashi su Abbie sun zubda makaman su sun koma lallashina. Da wanna salon nai amfani na cinye wasan akan bikina cikin kwanciyar hankali kowa na lallabani. An kawoni masarautar ruman masarauta mai abubuwan kawa da na birgewa. Duk da na tashi a gidanmu akwai kudi sai naga ashe muma yayan malam Shehu ne dukiya na'a inda take. Abu na farko da bai munba shine dole na zauna a kasan ikon Malikat Haseenat mai amsa sunan mahaifiya ga mijina, sai dai kuma babu yanda zanyi dan ta hakanne kawai zan samu yanda nake so. Na hakura na mika wuya anan dan koba komai tana nunamin kauna babu bambanci da yayanta. Abu na biyu shine Ashwaq a matsayin uwargidana wadda kowa ke jingina zamanta Malikat. Na shiga damuwa matuka a kanta tare da neman hanyoyin dakile al'amarin ta. Ban gama da itab ba aka auro Danish-Ara. Wannan shine mataki na farko da ya hada alakata da UWA. Dan tun sanda naji labarinta da dambarwar dake faruwa tsakaninta da Mammah a daura dammarar neman kusanci da ita. Nako sami nasara ta hanyar amintaccen hadimin Haysam, bayan na shaka masa makudan kudade amma ya nunamin har abada bazai ci amanar shugabansa ba, raina ya baci dan haka na koma barazana akan iyalansa, harma na aikata masa a aikace ta hanyar sakawa matarsa ta kawo min diyarsu daya da suka haifa sashena. Na tabbatar masa zan kasheta wanna shine dalilin amincemin badan yaso ba ya hadani da uwa. Na razana a ganin farko dana mata, dan mutumce mummunar gaske, da zaka iya rantsewa badaga yankin wanna kasa ta fito ba koma na dake zuciyata. A ranar batako kulani ba, hasalima korani tai wai ban shirya ba. Naji zafi amma na daure harda dukawa kasa ina bata hakuri akan laifin da ban san nayi ba. Bata dai kulanin ba haka na taso na taho. Na shiga damuwa dan tun daga wanna ranar bata sake yarda mun haduba har tsawon wata uku. A haduwa ta biyu ma dai bata kulanin ba sai da ta mula dan kanta sannan ta dubeni a kaskance da fadin, "Kije ki daina sallar la'asar dan kin shirya kasancewa da Uwa mai share kukan masu kuka". Na mata godiya na taso. Banyi wani tunani ba na fara bin dokarta har tsawon watanni uku. Kawai wata rana sai gata da dare ayam ta bullomin ta bango. Hankalina ya tashi na tsorata amma tsawar data mun ta sani nutsuwa. Cikin jan tsaki ta furta a haka zaki iya zama tare da uwa kina matsoraciya, Sosai na dake zuciyata wajen bata amsar ni ba matsoraciya bace. Ta sake maimaita min nima na maimaita mata nawa. Munyi haka har sau uku kafin ta kyalkyale da dariya da fadin, (Ke abokiyar tafiya ce. Mike tafe dake wajen uwa?). Cikin matukar farin ciki na qyara zama, na shiga zayyano mata haihuwa nake so, dan ina son zama Malikat bawai Zawjata-almilk ko Ameera kawai ba. Ni wannan matsayin duk yamin kankanta. dariya sosai ta shiga babbagawa har sai da na koa dan haushi amma dai na hakura na shanye. (Lallai ke abokiyar tafiya ce). Ta fada tana nunani har lokacin fuskarta da sauran daiyar. Murmushi nai mata cike da jin dad. Ta cigaba da fadin, (Nice da kaina na hana Haysam haihuwa saboda abinda uwarsa ke mun, idan tana takama ita Malikat ce dan ta haifi Miran mai jiran gado na shirya tabbatar mata komai a gidan nan sai da karfin ikona yake tabbata). Hakuri na dinga bata nidai, dan babban burina kawai bukatata ta biya nidai. Cikin tabe baki ta furta, (Ai kin wanke komai yar gari, indai zaki iya bin sharadinmu ki dauka kece Malikat a wannan karnin). Babu wani tunani nace na amince da duk wani sharadin ta tunma kan ta fada min su. Nan ma dariya tayi sosai kafin ta ajiye min wata takarda da koko mai dauke da jini wai a saka hannu da wannan jinin, itama zata saka wannan itace yarjejeniyar mu ta farko, Banji ko wani dar ba na saka ta saka. Ta bani daya ta dauki daya tana fadin, (Daga yau sunanki a wajenmu shine *_Ta-kurya_" ta kurya sa maza kurya kenan). Yar dariya nai ta farin ciki itama tana tayani. Ta wuce a ranar batace dani komai ba acewarta sai zama na biyu. Na matukar nustuwa a sati na uku da babu ita babu labarinta, dan haka na shiga bulayin nema. Harma a fiddla rai ranar kawai sai gata ayam ta kawo min ziyarar dare kamar wancan lokacin. Kafin nace komai ta tabbatar min doka ta biyu bayan suna dolene a duk sanda ta bayyana a gareni zansa gwiwuna kasa dan girmamawa a gareta, sunan da zan dinga kiranta da shi shine uwa. Nan ma babu musu na amince mata. Nanma dariya tayi kafin ta ajiye min kullin garin magani guda biyu. (Wannan sune maganin matsalarki Ta-kurya, daya zaki sha daya ki shayar da Miran Haysam. Ina mai tabbatar miki kafin watan ya mutu zaki samu ciki) na matukar kasancewa a farin ciki, sai kuma nai sansarakwai da ga baya na jeho mata tambayar to amma idan ya kasance wata a cikinsu nada ciki fa ko kuma muka samu cikin tare na haifi mace ita namiji?…✍️ DAUDAR GORA Book2 86 -."Anan ma dai tayi dariya da fadin (Ke ta dabance ta-kurya, sannan kanki na kawo wuta fiye da yanda nake bukata). Naji dadin yabonta harda godiya ta. Wasu magungunan ta sake bani, ta tabbatar min nai duk kokarin da ya dace na shayar da Ashwaq da Danish-Ara. Na mata godiya nan ma ta sake bace mun. Na shayar dasu maganin su duka uku nima kuma na sha wanda ta umarceni, sai dai kuma washe garin da Ashwaq tasha nata akawayi gari tayi barin cikin da ni ban taba sanin da shi ba. Ranar nayi farin ciki sosai, a wani gefen kuma ina mamakin toda miye na boyewar da tayi? A nufinta da karmu taba sani sai ranar haihuwa kenan? Lallai kasancewata da uwa alkairine. Abu mafi kara sakankancewa da uwa shine bayyanar ciki a jikina kafin cikar wata gudan data fada. Nayi farin ciki nayi farin ciki, duk wani masoyina ma yayi farin ciki. Itama kanta uwa tazo ta tayani farin ciki tare da sake kawo min wasu magungunan dazan na amfani da su har na haihu. Tace kariyane ga abun cikina dani kaina. Dan suma su Ashwaq zasu iya kawoma cikin nawa hari. Na yarda da ita fiye da kowa da komai a duniya zuwa yanzu, dan haka babu wani dar a tare dani na amsa. Haka na cigaba da rainon ciki, tare da soyayyar da ban taba zato da tsammani da ga Haysam ba. Ashe haka yake tsananin so da kaunar haihuwa. Hakama mahaifiyarsa da yan uwansa su Ammarah kowa tattalin rayuwata yake yi, Masarautar ma gaba daya wani irin girmamawa akemun data kara sakamun kaina fadì da jin babu kamar uwa a tare dani a wannan duniyar. A haka watan haihuwa ya kama mun, kowa fatansa ALLAH ya saukeni lafiya, ni kuma babban fatana na haifi da namiji, dan inata fargabar tambayar uwa hakan, kar tacemun bata da tabbaci. A haka dai na wayi gari wata safiyar laraba ina nakuda a tsaitsaye, uwa ta gargadeni fadama kowa, dan haka naita dauriya sai Jasrah dake nane dani, idan taga ina murkususu taita kuka, idan ya lafamun ta sani gaba da tambaya naita dai lallabata. Har safiyar Alhamis babu haihuwa babu alamarta, ranar mana cinye wannan yinin a wannan wahalar babu wanda ya farga har dare, dan ko Ammarah dake tare dani naki barin ta sani. Sai zuwa dare da ya ke tafiya daren juma'a kenan ina tsaka da shan murkususu na sai ga uwa. Naji dadin zuwanta, dan koba komai ina saka ran taimakonta. Tako zomin da taimakon sai dai ta hanani, acewarta yau ne ranar da zata sanarmin sharudanta, idan na amince zata bani maganin da zan haihu lafiya kuma da namiji da zai zama magajin kujerar Shahan-shan, idan kuma na bijire zata barni tai tafiyarta babu kuma tabbacin zan rayu balle dan, idan kuma na rayu na haifi mace ta warware abinda taima su Ashwaq su sami ciki wata a cikinsu ta sami da namiji, dan dama dai tun farko ita ta hana Haysam haihuwa saboda abinda Mammah take mata. Cikin riko da magiya nace mata dan ALLAH ta bani, indai nice na amince, koma mi tazo da shi zan amsa. Sai da ta jadadada min sau uku nima na amsa mata sau uku. Maganin ta bani nasha kadan ta karbe abunta sai ko na samu lafawar ciwon, harna samu damar zaman saurarenta. Ta ce da ni (Bushirat ke ce kika kawo kanki gareni ban gayyatoki ba, kika kuma zo min da bukatarki ta magance miki ita?) Kai na daga mata alamar hakane, taci gaba da fadin (Gadai abinda kike nema nan kin samu, da ga yau zuwa gobe sunanki ya koma *_MALIKAT BUSHIRAT ne, zaki samu girmamawa da ga kowa. Ada nayi alkawarin hana Haysam gadar sarautar kujerar Shahan-shan, dan in har bashi da magaji ko ubansu mutuwa yay bai isa hawa ba. Amma a yanzu saboda ke na janye komai, Zan hukunta Abdul-majeed da Haseena akan laifukansu su da zuri'arsu, amma ke kam kin tsira keda danki, zan baku gata zan maidaku yan lele) godiya na mata cike da jin dadi. Cigaba tai da fadin, (Sharadina na farko bayan kin haihu zan dauke mahaifarki gaba daya, dan wanna dan kwara daya ya isheki yakar kowa a masarautar nan, sannan haihuwarsa shi kadai a nufin shine kawai magajin wanna masarauta) na amince Uwa. Na bata amsa babu wani tunani ko kyakykyawan nazari. Murmushi tayi tamun jin jina. Ta cigaba da fadin, (Sharadi na biyu bayan haihuwarsa zakiyi yankan bakaken shanu guda goma, rakuma mata da basu wuce shekara uku da haihuwa ba suma goma zaki soke. Sai bakaken karnuka) anan ne na dani diri-diri da jin karnuka, amma sai tai saurin fadin (Karki damu su wannan karnuna zaki yankasu domin kariyar duk wani cutarwa da wani zai kawoma danki ne, dan kina haihuwar magaji tofa babu mai zama haka kuma bayanki za'aita yunkurin gani ke da dan) hakane kuma uwa. Na gane mi kike nufi na amince. Na bata amsa cike da gamsuwa da bayanin ta. Nan ma tayi murmushi da cigaba da fadin (Zaki cigaba da wannan yanka ne duk bayan watanni shida, sannan zaki sadaukar da jinin macen hadima mai dauke da ciki karami bayan ya cika wata uku, idan ya kara wata wata ukun zaki sadaukar da hadimi mai sabon aure da basu wuce wata daya ba shima) nan ma nadan shiga rudani amma ta nunamin idan bana bukata zatai gaba, ai duniya babu abinda ake iya samu cikin sauki. Sannan kuma bawai tace na kashesu bane da kaina, nawa kawai shine bata sunansu, sauran aikin nata ne) nifa matsalata kawai shine a haifi magaji, na zama abar kwatance akan karfin iko fiye dana Malikat Haseenat dan haka na amince. Ta cigaba da fadin (Saradi na biyu lokacin da yake cika shekaru goma sha biyu a duniya zakiyi kokarin a hada aure tsakanin wani makaskancin talaka da wadda kukafi shakuwa a kannen Haysam idan an samu ciki aka samu kuma mai tambarin zuri'arsu a gado bayan kwana uku zamu amshe yarinyar, inma babu tambarin ma dai ahakan zamuyi, za kuma mu kauda Abdul-majeed a doron duniya Haysam ya gajesa. Haysam zaiyi mulki na tsahon shekarun girman danki, yana cika shekarun gadar mulki zaiyi murabus ya daurasa. A ranar nadin zamowarsa Shahan-shan za'a aura masa mata hudu, matan nan dukansu zasu zama sadaukarwarmu tare da Haysam, dan in har yana raye tofa zaki cigaba da zama yar kallo ne sai abinda Haseenat tace danki ma yayi zai yi.…..) Da sauri nace na amince, dan bazan taba iya cigaba da zama karkashin ikon wata ba bayan kuma dana ke mulki. Tayi murmushi a lokacin da fadin (Shiyyasa nake jinki kamar yar dana haifa a cikina ta-kurya. Zan saki ki zama mai nasara kuwa bisa nasarar kowa. Wannan yaro da zaki haifa zai cigaba da aure muna kauda matan har sai sun cika adadin da zasu zama ginshikin rike karagar mulkinsa. Da ga karshe zamu kawo masa matar aurensa da zata zama duk wani motsinta sai da umarninki ne, koda ta haifa masa magaji kece zaki cigaba da amsa suna MALIKAT. Dan hatta shi a karan kansa ko hukunci bazai iya zartarwa ga wani ba sai da umarninki. Ki kula ki nutsu kisa hankali a jikinki a duk aure-auren sa kada ya auri wata mai alaka da zuri'arsa, idan kuma har kikai hakan to komai ya lalace kenan, duk wahalarki ta tashi a banza, mu kuma bazamu taba amsar kuskure ba, in har kika gagara cika wadan nan sharucidan namu zaki bamu madadinsu ne da jinin abinda zaki haifa, dan shine diyyar kuskurenki. Kuma shine hukuncinki) hankalina ya matukar tashi dan duk duniya a yanzu babu abinda nafi so kamar abinda ke cikina din, a shiga rokonta da magagiya. Ta tabbatar min itafa saina kuskure mata ne zata aikata hakan, dan bijirewar Abdul- majeed ga ayyukanta bisa shishshigin matarsa yasa zatai masa hukunci da mutuwa da mutuwar dansa (Haysam) da ya fi so, zakuma ta tabbatarma Mammah ita ba komai bace a wanna masarautar shiyyasa ta hanyar yayan da take takama da su, dan haka Ammarah ce zata zama wadda za'"aima auren sati biyu ta haifi yar da muke bukata, dama ta kashe Miran Nayyar a cikin ruwan swimming pool na gidan, Waheeda kuwa dama bawani tanada zuciya mai kyau bane kanta kawal ta sani dan haka bata gabanta, Jin wanna kashe-kashen hukunci da zatai ga zuri'ar Mammah saboda abinda Sukai mata a bijirewa yasa na karajin tsoronta, dan haka na amince ga dukkanin shardanta. Ta bani magani nasha, tare da tabbatar min zata kaworin hadimar da zata kasance amintacciyata wajen gudanar da ayyukana. Dan dolene zan boye kaina tsahon rai batare da kowa yama taba kawowa kansa nice ta-kurya ba. Koda kuwa a cikin hadiran da zasu dingamun aiki ne matsayin ta-kurya, Bayan tafiyarta haihuwa ta tashi gadan-gadan, Alhamdullah na haifo yarona namiji mai kamanina dana Haysam. A hankali, abinda duk ta fada ya cigaba da tabbata, babu wata matar Haysam da ta kara koda kwatanta samun ciki, dan haka na kara sakankancewa da ita, duk kan umarninta na fara cikasu kamar yanda ta bada, kuma komai na tafiyamun babu wata damuwa har zuwa lokacin da aka dauke Eshaan daga gabana. Ta nuna bacin ranta, kamar yanda na nuna damuwata, sai dai duk wani kokarin mu babu wanda ya saurareni, da Mammah ce ma, itama daga baya ta bada goyon bayan dauke san. Duk da tafiyace ta wani shekaru naji zafinta, sai dai bana iya cika wata guda banje na dubeshi ba. Yawan zuwana yasa Abbu (Tajwar Abdul-majeed) yayi magana a lokacin, aka kuma sakamun dokar sai bayan shekara-shekara. Naci kuka a ranar amma uwa ta kwantar min da hankali akan daukar mataki da tabbatar min ba sai yana raye dokar zatai aiki ba.Lokaci yayi da Ammarah zatai aure. Da taimakon su Miran Jasim aka cika wanna aikin, bayan wucewar su Mammah Umrah. Anyi auren Ammarah an kuma samu cikar burin samun ciki. Bayan dawowarsu an kwashi rikicin da har yay sanadin kai Jasim kurkuku. Da ga baya dai komai ya lafa Ammarah ta haihu. Bayan haihuwarta abubuwa suka nema cabewa dalilin samo wani hatsabibin mutumn, sai dai duk da haka muni nasarar mallakar abinda ta haifa da kuma kauda Abbi (Shahan-shan Abdul-majeed) nafi kowa jin ciwo da shiga tashin hankalin abinda akaima Uwa a masarautar nan dan ranar ni nasan irin kukan da naci na tashin hankali. Kwatsam bayan na gama fidda rai da rasa uwa a wata raar da Haysam ke cika shekara uku da hawa karagar mulki sai ga uwa ta bayyana.Farin cikine ma da bazan iya musaltashi ba, itama har taitamun dariya, ta kuma nuna jin dadinta da yanda na damu da rashin ta, ashe tanada y an leken asiri da ke kai mata rahoton komai a shekarun nan da bata nan…✍️ DAUDAR GORA Book2 87 …..……….Bayan dawowar uwa al'amuran mu sun cigaba da tafiya, dukan shardanta a cigaba da cikasu, dan dama ko bayan batanan ban fasa ba, dan ina tsoron abinda ta fada akan Saiful-malik ya tabbata. Dan wannan tsoron da son cimma buri ne suka jagoranceni har zuwa wannan lokaci. Ni naita zungurar Haysam akan yin murabus lokacin da Saiful- malik ke cika shekara talatin da uku a duniya, nayi hakanne kuma bisa umarnin uwa. A duk sanda nai maganar yakan yi murmushi ne kawai, amma baya cewa dani komai, Sai hakan ke cimun rai da tunanin baya son ya sauka ya daura Eshaan din ne. Ni kuma abinda nake hange adadin shekarun da Uwa ta tabbatar min zai rasa ransa a dalilin shayin da nake shayar da shi gabatowa suke, ta kuma tabbatar min infa ya mutu ba'a daura Saiful-malik a karagar mulki ba akwai rikici sosai, domin Haysam nada kanne, shekarunsu kuma sunfi zama shekarun hankali da yan kasa zasuyi jayayya da samun rabuwar kai akan magajinsa Eshaan. Na sake takura masa da tada hankalina akan hakan har takai wata rana ya furta min abinda ya girgizani. Ya ce (Bushirat basai kinyi gaggawa akan mutuwata ko rayuwata ba. Idan kaddarar mulkar kasar ruman na rubuce a littafin kaddarar Eshaan sai yayi ko ina raye ko bana raye, abinda na sani kawai ina matukar tausaya masa, ina tausaya masa yaki na cikin gida da waje. Yakin da zai masa matukar wahala musamman kasancewarki ke wa mahaifiya da kika zamto a cikin manyan makiyansa) rai bace nace ban gane ina cikin manyan makiyansa ba? Bai sake cemin komi ba, illa murmushi kawai da ya saba mun. Maganar ta zauna min a rai matuka, har ta kaini da fadama uwa. Itama naga alamar ta girgiza, dan haka take anan ta tabbatar min dole muyi motsin da Haysam fa zai bada mulkin nan sannan mu kaudashi, dan alamominsa na nuni da akwai abinda ya sani game da ni, idan kuma har mukai sakaci wahalarmu ta baya zata zama a banza. Babu wani damuwa a raina na bata goyon baya, dan saima tashin hankali da nakeji akan cewar Haysam yasan wani abu game da ni din, ina tsoron ya fadama mahaifinmu, dan wilhy zai iya tsireni ne kawai kasancewarsa mutum mai zafi da bin dokar addini. Haka akai, ta kawo abinda naita saka masa a madara yana sha har tunaninsa ya karkata a yin murabus, babu zato babu tsammani kawai ya dawo da Eshaan gida, ya kuma tabbatar da zai yi murabus ya daurasa a karagar mulkin Shahan-shan. Kalubalen dana so fuskanta shine Eshaan da kansa, dan yaso bijirewa da cewar shifa baya son mulkin nan, bai taba ma birgesa ba, yafi son rayuwar yanci, yayi abinda yake so a lokacin da yake so, a cikin tarin burukan rayuwarsa ma babu maganar mulki a ciki. Na tashi hankalina Uwa tace na kwantar, ta bani wani turare tace na basa kyauta, in har yay amfani da shi na kwana uku sai ya amince. Hakan ce kuwa ta kasance. dan satin bai shigeba sai gashi da cewar ya amince. Uwa ta kara shiga raina da jin bani da kamarta duk duniya, zata kuma iya sakani komai nayi amma banda sadaukar mata da Eshaan, dan shine abinda nafiso fiye da komai a duniya. Anyi nadin sabon Shahan- shan tare da shagalin bikin aurensa na mata hudu, ko sau daya bai tanka akan auren ba, baice bai son su ba bai kuma ce yana so ba. Ni kuma bam ma damu da tambayarsa ba tunda nasan makomarsu. Kamar yanda uwa ta fada Haysam ya shude, matan Eshaan ma daya bayan daya sun zama labari, an cigaba da auro masa was suma tarihinsu na shudewa, a haka har nazo gab da cikar burina na gama wannan sharadin. Rana tsaka, ina gab da cimma abinda na faro kwatsam yarinyar ta shigo rayuwata. Ba kai tsaye ta shigoba, dan bana jin ma ta sanni ita. Yaki ta shirya, ya ki domin yakar Eshaan saboda rasa yayunta biyu da suka shigo cikin aikina. Itama tanada tunani ne irin na sauran mutanen kasar ruman akan Saiful-malik ne ke halaka matansa. Wanna itace mafarin matsala, dan tunkan ta shigo ita nacema uwa ta kauda min ita, dan ina a gabar da zuciyata ta gama dakewa da bushewa zuwa yanzu, hatta hadiman dake mun ayyuka da sunyi kuskure mafita daya nake hangoma kaina shine kawai na kaudasu, idan na kaudasu matsalata ta kare kenan. Da nayi din sai inga ta kare kuma, dan haka nake kallon kashe duk wanda ya shiga gabana akan cikar burina kawai na kauda san Uwa ta tabbatar min babu kaddarar mutuwar yarinyar a wannan tsakanin, sai dai mu nemo wata hanyar, a cikin neman mafitar ne muka yanke zamowarta a daya da ga cikin matansa, domin a ganinmu idan ta matso gab da mu sai munfi cin nasara a kanta. Sai dai kuma al'amarin bai kasance yanda mukai hangesa ba, dan tunda ta shigo rayuwar gidan komai ya daina yiwuwa a cin sauki. Labarin farko ya canja zuwa wanda bashi muka tsara ba. Dan hatta madarar farko da nake shayar da duk Zawjata-almilk ita kin sha tai, alkyabba da turaren da nake badawa a musu wanka da shi a sako musu tun daga gidansu shima basu akai mata ba, ban hakuraba na bibiyeta da su nan ma taki yarda tai amfani da shi, duk ta inda muka bullo sai ta waske, da ga karshe ma wata rigar da mu bamu san ta ina ta fitoba ce ta sanya, daga haka ta koma sashen Mammah da zama, ita kuma ta kaita sashen Saiful-malik batare da shawarar mu ba bayan mun yanke a yanda zamu mata rakkiya zuwa can. Dan saboda na rabota da sashen Mamma da uwa bata iya zuwa yasa na bada shawarar maidata sashen Saiful-malik ta mana bincike, amma sai Mammah ta canja shirin namu gaba daya. Wannan abu ya konamin rai matuka, ya kuma zafi zuciyata na kasance a bakin ciki. Mairakon nasara komai sai sake tabarbarewa yake, da kyar muka samu cikon ayyukan mu akan Zawjata-almilk data tarar, Itako dai ta kasa tabuwa a garemu a duk ta inda muka bullo. Tun ana yakin sunkuru har komai ya fito fili da fitar da ban san mafari ba da ga gareta, yakin ya koma na kasanni na sanka......" ta rushe da kuka mai karfi. Sai da tayi mai isarta babu wanda yace mata ko kanzil sannan ta cigaba da fadin, "Babban tashin hankali na a yanzu da jagorantar dukkan karfin halin iya maida martanina ga uwa a wannan gabar da komai na tabbatar da ya lalace shine rasa Saiful-malik, ta sake tabbatar min sai sun amshi jininsa matsayin diyyar kin cika shardansu, bana son na rasashi, shine kadai ya kuka ya sarketa ta kasa cigaba. Jasrah ma kuka take iya iyawa, sauran yan uwanta kam tagumi duk sukayi kawai. Hankalin Iffah gaba daya akan Tajwar Eshaan yake, dan tunda ya dukar da kansa da kamo hanunta ya rumtse a cikin nasa har yanzu bai ko yi wani motsin kirki ba, hannun nata kuma na rumtse a nasan duk da azabar da takeji saboda yanda yake matse a cikin nasan haka ta cigaba da daurewa tana mai ambaton addu'oi da duk sukazo bakinta. Fatanta ALLAH ya saukaka masa zuciyarsa, ya bashi juriyar dauka. Gyaran muryar kaka ne ya katse tunanin kowa. Ya nisa a hankali tare da gyara zamansa. "Lallai kinyi kuskure, kin kuma shiga rigar yaudara irin ta wadda bokaye kanyima bayin ALLAH saboda son zukatanmu da burin gina DUNIYA mai yankewa. Wannan mushirika tai tasiri da tasirin gurbataccen burinki ne da niyyarki ta shigowa wannan gida. Amma karya take bata da alaka da samuwar cikin Shugabamu da kikayi, dan dama sanda ta baki maganin kina tare da shigar cikinsa….... Babu wanda bai zabura ba, hatta da Malikat Bushirat din kanta. Tajwar Eshaan kam sake kankame hanun Iffah yay cikin nasa tsam-tsam fiye da farko. Kai Kaka ya jinjina musu, "Wanna maganar da nake fada muku haka take, dama akwai cikin. Koda ace babu shi ta bada taimakon magani shi wannan maganin sai dai ya magance matsalar wani ciwo da ya zama sanadin jinkirta samuwar haihuwar bawai ya samar da dan ba. To sai a wannan labarin ma akwai samuwar cikin ma kafin ta shigo cikinsa. Rashin samuwar haihuwa jarabawace ga duk wanda baiyiba, jarabawa kuma mai ciwon gaske da radadi a zuciya, bazaka fahimci haka ba sai in ka kasance daya daga ciki. Ya halatta ka nema magani da ga kowace irin cuta a rayuwa. Sai dai fa akwai matakan da ya kamata mumini yabi wajen neman magani kowane irine balle ma akan neman haihuwa. A duk lokacin da muka rasa haihuwa idanunmu kan rufe da fadi tashin neman mafita ta kowanne yanayi. Burinmu shine kawai mu haihun. Sam babu tunanin maybe ita haihuwar ba alkairi bace a tare damu, a ganinmu kawai mun rasa shine mu nemota ta kowace irin hanya. Duk da abinda UBANGIJI ya baka ya fika sanin dalilin baka shi, idan kuma ya hanaka ya fika sanin dalilin hanaka da yayi. A rayuwa babu abinda yafi karfin addu'a, sadaka, yarda da kaddara mai kyau ko sabaninta. Idan kuma har ta kama saika nema maganin ka zama sani ba a wata gabar. A neman haihuwa wajen bokaye da malaman tsibbu zakaci karo da abu hudu in har ka samu daya da kaje nema. Na farko rasa imaninka da cire yardarka ga UBANGIJI mai badawa da hanawa, dan zaka cigaba da ji a ranka shifa wanna din nan ne ya baka wannan haihuwar (Wa'iyazubillah). Na biyu zata iya yiwuwa dan aljani ma aka samar a cikin naka batare da kasan hakan ba kai tunda kai a kai kanka ai. Na uku wasu matan ko da saninsu, ko bada saninsu ba zata iya yuwuwa bokan yay mata cikin a zahirance ko kuma ta hanyar tsafe-tsafen sa batare da ita tasan hakan ta kasance ba domin shi tsafi gaskiyar mai shine. Idan kuma ALLAH yasa dama ana a kan gabar da ALLAH ya iyakance ne dama haihuwar tata ta kusanto gareta batare data sani ba sai a samu dai-daito da bada maganin nasa haihuwar ta samu amma zuciyarta na tabbatar mata ta sametane daga wannan bokan ko malamin tsubbun……..✍️ Mu hadu in ALLAH ya kaimu Please🚴🚴🚴🚴🚴🚴🚴 hannuna ya gaji😂 DAUDAR GORA Book2 88 ."Kamar dai yanda ta kasance a gareki. Ita tana da buri akan wannan masarautar, sai akai sa'a ke ma kinada naki burin da kika kai kanki gareta. Ita kuma sai tai amfani da haka kika zame mata yar aiken isar da sakonta ta yanda babu wanda zai fahimci ruhinta ya sake dawowa wanna masarauta balle ma a zargeta akan dukkan abubuwan da suka faru har a maida hankali. Wanna labarin naki yasa na fahimci maganar mahaifina da ya ce, duk saninka kankanuwar samarwace da ga taskar ALLAH da bata yankewa. Sannan haihuwar ita Fhareedah wani mashine da ga UBANGIJI da zai zama sanadin tarwatsa al'amuranku batare da kun fargaba, shiyyasa ya boyeta a cikin sirrinsa har zuwa ranar da zata dawo gareku cikin karfin ikonsa da zai tabbatar muku babu wani karfi da ke saman nashi. Shirka babbar faduwa ce, ginshikine na gina kaskanci a duniyar bawa dama lahirarsa. A duk lokacin da ka dauki cewar wanin ALLAH a iya baka koda kariyane da ga wani abin tsoratarwa to akwai babbar matsala,dan kuwa shi wanna mushirikin zai bika mataki-mataki ne wajen kaika fie da inda bakai hange ko tsammanin zuwa ba. Kamar dai ke din nan. A matakin farko bukatar haihuwa kikaje mata da shi, sai ta ce miki kada kiyi sallar la'asar. Tayi hakane saboda kasancewarki mai bautar ALLAH, sannan kina jingine da wasu muminai da zasu iya saurin fargar dake kuskurenki kuma ki gyara. Amma data kafa miki wannan tarkon sai ta busar miki da zuciya ta yanda duk yanda za'a kiraki bazakiji wannan kiran ba, ba kuma zaki saurari mai kiran ba koda ace kin jisa. Hanaki bautama UBANGIJI itace allurar farko mai tsananin dafin data sakaki shagaltuwar da bijire mata zai miki wahala koda ace kina so. Shiyyasa maganin ayima kar a fara, tun farko ma yi kokarin yin addu'a da yakar kanka daga son zuciya ko tunanin nema daga wanin ALLAH. Miyasa musulunci ya mana gatan cewa mu tashi mu nemu na kammu? Saboda kare kammu da ga biyayya ga abinda zai iya cutar damu. Dan a mafi yawa ko nace rinjayen dan adam yana son a duk sanda ka nema daga garesa duk sanda wani abu ya taso da zaka iya masa to ya tuna maka wannan taimakon da yay maka wanda zai iya sakaka jin kunyar yimasa abun nan koda ace bai dace ba. Kamar dai cin hanci da rashawa. A duk lokacin da mai bada cin hanci ya mika ga mai karba zai iya aikata aiki komai muninsa koda ace zai iya cutarwa ga rayuwar mal karbar shi kansa ne ma. Dan haka maganin data baki a tun farko ma bashi da alaka da abinda kikaje neman. Ta baki shine domin cutar da abinda ke cikin ki data riga ta tabbatar da akwai. Sai dai ALLAH ya riga ya kaddara babu abinda zata iya yi sai ya zo duniya, dan haka ta tafi mataki na biyu wajen rabaki da mahaifarki gaba daya. Mataki na uku ta rabaki da mijinki, mataki na hudu tai amfani dake wajen gogama rayuwar danki bakin fentin da zai bakantashi ga al'ummar kasar sa da mulkinsa. Lokacin da ake ihun yay murabus badan Iffah ta shayar da shi wannan madarar mai dafin macizai ba da burinta a tsigesan, hakan yana cikin plans dinta da idan wanna baiyi tasiri ba zata tsallaka na gabansa. Da ace taci nasarar kun hada auren wadda taso ta haifi magajinsa da taci nasarar duka wasan. Dan sam wadda take burin ya aura bama mutum bace cikakkiya yar zuri'arsu ce aka raina a anan duk saboda zuwan wannan lokacin. Daga kuma sanda ta samu ciki burinta shine ta kasheki, shima ta kasheshi wanna jinjirin ya amsa suna magaji, da ga haka ta karbe mulkin ta karfin tuwo da ga wanna ahalin. UBANGIJI bai gitta rayuwar Iffah a cikin al'amurran ki da rayuwar danki ba sai dan shi tsarkakakkene mai tarin tsoron ALLAH da kiyaye dokokinsa. Ya gadar da shine da ga kyawawan halayyar mahaifinsa sabanin naki dabi' un. Addu'oin da al'umma ke masa na tasiri a tare da shi tare da yin dubi da tsarkakakkiyar zuciyar kakarsa da tai yaki da yakar mushirikai. Mutuwar mahaifinsa da kakansa tazo ne akan gaba bawai bisa karfin ikonta ba. Da ace ma tayi hakuri zasu musu, tabbas zasu mutu a dai-dai wanna gabar har su matan nasa. Amma a yanzu hakkin ruhinsu duk ya rataya a gareku ke da ita domin harda amincewarki akai komai ba tilastaki tai ba a aikace.Kaiconmu da irin wannan burin duniya, kaiconmu da irin wannan hangen da babu hango iyakar karewarsa, kaiconmu da zuciyar da ke jin hakkin wani ba komai bane komai Kankantarsa komai rashin muhimmancinsa, Wlhy duk abinda akace maka ba naka bane sunansa ba nakan ba. Idan kuma harka taba da son zuciya ko izgili sai ka biyashi a ranar da babu kudi irin madadin a duniya. A ranar da cuniya ce zata taru, a ranar da ake biyan hakki da lada ko zunubi. Dan duk hakkin wanda ka taba zaka biyashi da ladanka, idan baka da lada za'a dibo zunubinsa a lafta maka. Shiyyasa mutane da yawa zasuje lahira da tarin lada a taskokinsu, amma yayin kammala musu hisabi sai su koma basu da korai sai tarin zunubai dan an biya duk wanda suka cima hakki da wanna ladan nasu. Haba yan uwa har wane aiki muka tara da har mukejin cin hakkin wani zai isa mu biyasa har mu sami rarar shigar aljanna da sauran. Wani ma har kaji yana izgilin shi hakkin wani ko ALLAH ya isa bata masa komal a jiki, why da tabon da zatai maka a rayuwarka gara ace a jikinka take tsirowa maybe kaji tsoron ALLAH da wuri ka sauke hakkin. Shi kuma wanda ma ya hadiye bai ce dakai komai ba yafi ban tashin hankali fiye da wanda zai furta maka maybe ka razana ka sauke. Wai miyasa bama tunanin cewar wanda muka cima hakkinsu sune masu nasara akan mu ne? Tabbas masu nasara a kammu, dan sun kasance masu ajiyewa a dauka a kuma biyasu a ranada ake farautar ayyukan cika mizani. Kawai akan son farantama was mu mu tauye kammu mu daga nasarar wasu. Wai a hakan dan wawanci murna mukeyi, farin ciki mukeyi mun karya wane, mun kaskantar da wane, mun maida wane baya, waya fada maka dariya ya kamata kayi ko kiyi?Wlhy kuka, kuka ya kamata ki fara tun kafin ganin anar nasarar mai wanna hakkin da taki faduwar,Wadan nan hakkokin da muke rainawa suke hauhawa su gawurta su zama manyan abubuwan ruguza ayyukanmu. Kamar dai ita, ta fara ne tun a kuruciya, zalinci wancan, tirsasa wancan ana gain yarintace hakan ba komai bane amma sai abin ya cigaba da tasiri a rayuwarta har yay gawurtar da ayanzu ta fado kasan-kasan kafafun wadan da take gain ba komai ba, wanda take ganin murjesu ta taka ko cin hakkokinsu ba komai ba. Gadai shi taji dadin, tayi farin cikin, ta dauki kanta a mai nasarar, amma a karshe itace ta zama mara nasarar, mafi kaskanci.Mafiya masu cin hakki da ruguza rayuwar wasu zamu samu matasane masu tasowa, maybe batai aure ba ko baiyi aure ba, kokuma bata jima da yin auren ba,dan duk wanda, ko wanda ya kai shekaru arba'in a duniya ya zabi take hakkin wani babu babban wawa sama da shi. Amma su wadan nan masu tasowar gani suke abinda sukeyi ba korai bane, yanzu ma aka fara rayuwar. Waya gaya miki koya gaya maka ba komai bane ba. To ko kasa mutum ya gino ya tara kikazo wucewa ko kazo wucewa ka barbaza masa ai hakkine balle abinda ya killace koya nunama duniya abun nan mai muhimmanci ne a garesa koda ace kai baka ganin muhimmancin nasa. Kanada kananan shekaru kana ta daukar hakkin mutane da kake gain bamai muhimmanci ba kana tarawa yana hauhawa a mizanin aikinka yana rusaka, yana rusa rayuwar yayanka masu tasowa, yana rusa cigabanka na duniya dana lahira kai kana shirmen kana nasara akan mai hakkin. Kajifa toshewar basira, shi kana kara masa nasara ne fa, tunda dole-dole ka biyashi a inda babu kudi sai aiki inhar baka biyasa da kudin daya shardanta akan kayan nasa ba. Kamar dai ita a yau, komai yazo mata a gabar da bata da damar neman gafarar wadanda ta zalunta ta cutarma da rayuwa saboda nasararta da neman cikar burinta. Ta rasa a lokacin da su kuma suka samu, wata tayi amfani da ita dornin nasararta ta barta da katon nauyi bisa kai. Kaicon rayuwar da ba'a tuna mutuwa a cikinta. Kaicon rayuwar da ake ginata kamar bazata yanke ba. Kaicon rayuwar da ake daukar hakkin wani kamar ba hakki ba. Kaicon rayuwar da cikar buri ke jagorantar imani da tsoron ALLAH a zuciyar mai shi. Kaicon zuciyar dake bushewa da jin komai tayi dai-daine. Ya ALLAH ka karemu, ka kara tsaremu, ka tsarkake mu, ka kiyaye mu. Ka killace mu, ka karfafa mu, ka jagorance mu bisa tsoronka da tsoron shirka, da tsoron cin hakkin wani komai kankantarsa, ka kyautata neman mu da ga halak, ka karfafa ayyukanmu bisa umarninka da kiyaye saba maka badan halinmu ba. ALLAH ka shiryar da wanda suka kauce, idan ba masu shiryuwa bane UBANGIJINMU mun barka da su kafimu sanin miya dace da su. ALLAH ka rabamu da ruin duniya da kyale-kyalen cikinta. Ya rabbi ka saka DUNIYA a tafukan hannayenmu ka nisantata zama a cikin zukatanmu. Ya rabbi ka wajabta mana tsoronka, ka karfafa imaninmu. Ka yafe mana kura kuranmu, ka bamu ikon kyautatama duk wanda ka hada kaddarar zaman mu a tare ko mu'amularmu, Ya rabbi ka hana mugayen halayenmu cin nasara a kammu, kasa muci nasara akan mugayen halayenrnu da ayyukanmu". A tare suka dinga amsawa da Amin kowa na sharar hawaye, yayinda Malikat Bushirat ke kuka mai tsananin gunji. Matuka takejin radadi a zuciyarta da azaba a cikin jikinta, So take ta kara cewa wani abu koda ga tilon danta ne da har yanzu bai dago kai a dubi kowa ba balle ita amma ta kasa hakan. Da ga karshema mikewa yay a hankali cikin tangacfin juwa hannunsa cikin na Iffah har yanzu batare daya kalla kowa ba balle cewa wani abu ya jata suka fice. Ta hanyar sirrin da suka fito ta can suka koma hankalin Iffah a tashe da yanda yake tangadì mai bada tabbacin akwai matsala….✍️ DAUDAR GORA Book2 89 ...... Suna shiga bedroom din sa ya wani irin rungumeta tsam-tsam a jikinta tamkar zai maidasu su zama abu guda. Yanda Iffah kejin gudun zuciyarsa da bugawarta hankalinta ya tashi matuka. Tayi yunkurin dagowa ta kallesa amma yaki bata koda kankanuwar dama. Sosai numfashinsa ya fara fisga, gashi ya ki sakinta balle ta bashi wani taimako, mutsu-mutsun kwatar kanta take amma ta kasa. Sai kawai ta fashe masa da kuka. Sakinta yay da sauri, sai dai bai yarda sun hada ido ba ya rabata ya wuce. Gaban window yaje ya tsaya kawai ya tsirama harabar masarautar ido. A gurin Iffah ta durkushe ta cigaba da kukanta. Tsahon mintuna goma suna a haka sautin kukanta kawai ke ratsa dakin, shiko yana a inda yake tsayen kamar gunkin da aka dasa domin tarihi. Mikewa tai itama jin jiri ya fara dibar idanunta, dan akwai yunwa tare da ita, rabonta da abinci tun jiya. A bakin gadon ta zauna jagwaf, ta dafe kanta tsahon minti daya kafin ta janye. Ciwo hannayenta ke mata sosai saboda matsar da suka sha a wajensa, har sun dan kumbura dan matsar bata wasa bace. Jin sun mata tsami babu dadi ta shiga murzasu a hankali ko zataji sassauci. Bata san sanda ya baro wajen window din ba, ganinsa kawai tai durkushe gabanta ya kamo hannun nata a cikin nashi. Kallo daya taima fuskarsa tai saurin dukar da kanta, dan idanunsa sun yi masifar firgitata. Sun yi wani irin kadawa jazur irin wanda bata taba gani ba,hakama fuskarsa gaba daya tayi jazur kuma babu alamar yayi kuka, kawai tsabar tashin hankaline ta sauya masa kamanni. Hannayen ya shiga murza mata a hankali, kafin tsahon lokaci kamar wanda aka fisgo furucin da ga halshensa ya ce, "I am sorry". Da sauri ya dago ta dubesa, ganin yanda ya tsurama tafin hanunta idanunsa masu ban tsoro yasata jin hawaye sun sake cika mata ido. Dayan hanunta ta daura akan habarsa mai cike da lallausan bakin gashi ta dago, cikin dauriya da dakiya ta saka idanunta cikin nasa, muryarta na karkarwa ta furta, "Dan ALLAH kayi kuka koda kadanne Zakina. Kayi kuka! kayi kuka!! kayi kuka!! Zan shanye hawayen a cikina na adanasu cikin manyan SIRRIKANKA da ka bani ajiy....." Kafin tama kai karshe sai ga hawaye sharrrrr da ga idanunsa kamar an bude fanfo, wani irin murmushi mai tsananin ciwo da kuna ya sakar mata hawayen na kara gudu. Da sauri ta tara hannayenta suka sauka a ciki, kallon tafin hannun nata da hawayen nasa ke sauka yayi, sai ya sake fashewa da kukan, hawayen na cigaba da sauka a cikin tafin hannun nata. Sai da suka taru sosai sannan tasa harshenta ta shiga lashe hawayen tana hadiye tare da fashewa da sabon kukan itama. Kansa ya daura a saman cinyarta yana zaune da ga kasan lallausan carpet din gaban gadon itako tana daga zaune a kan gadon, itama sai ta daura kan nata a kan nasa suka cigaba da kukan a haka zabban tausayi… Bayan sallar azhar da ya kasa fita saboda zazzabin da ya rufesa mai zafin gaske itama ciwon ciki ya takurama Iffah na jin yunwa, abinka da ba ita kadai ba. Haka ya tashi cikin kakkarwar sanyi ya bata madara ta sha, tana sha ta amayar da ita, a hakan dai ya taimaka mata cikin karfin hali ta gyara jikinta, sake bata madarar yay tasha kadan, shima sai ta takura masa wai sai ya sha dan rabonsa da abincin kirki tun jiya. Kin sha yay ta sanya masa kuka, dole yasha rabin kofi ya kauda kansa, da ga haka suka dunkule waje daya kwance zafin jikinsa na matukar ratsata. Ganin zazzabin baida alamar sauka sai ma karuwar da yake yi yasa Iffah kiran Sayeed Fayzul-haq. Babu bata lokaci suka iso da Doctor Afif da ke matsayin amintaccen likitansa. Doctor Afif din kansa sai da hankalinsa ya tashi gain yanda jinin Shahan-shan din yay wata irin kololuwar hawa, ga bugun zuciyarsa har ya canja. Cikin sauri ya danna masa allurar barci mai matukar karfi dan in har aka cigaba da zama a hakan akwai babbar matsala kam. Da farko kin yarda ma yay ayi allurar sai da Iffah ta sanya masa kuka sannan ya kauda kansa kawai baice komai ba. Sai Sayeed Fayzul-haq ne yay ma Doctor din nuni da yayi aikinsa dan kauda kan nasa a nufin amincewa, Iffah dai na zaune ne kansa a saman cinyarta tanata faman sharar hawaye. Duk da karfin allurar ya jima baiyi barcin ba, dan sai da Iffahr ta hada da tofa masa addu'oi sannan aka dace barcin ya daukesa. Haka ta cigaba da zama kansa a saman cinyarta har aka kira sallar magrib, kafafunta duk sunyi tsami,da kyar ta gyara masa kansa ya koma kan fillo, sannan ta mike ta gabatar da sallar magrib din. Alkur'ani ta dauka ta shiga raira karatu a nutse tana hawaye, bata ajiye ba har aka kira sallar isha'i nan ma ta gabatar. Ta jima tana addu'oi akan wadan nan al'amura da suka cure musu, tashinta babu jimawa Malikat Haseenat da Daneen Ammarah da Daneen Waheeda da Iftihal sukazo dubashi. Basu shigo ciki ba iyakarsu falo, Iftihal nata yan kalle-kalle dan wanna shine karo a farko a rayuwarta ma data shigo sashen nasa. Iffah na fitowa ta wani dukar da kai dan ita kam tsoranta takeji matuka yanzu. Cike da kauna da tausayi Malikat Haseenat ta rungumeta, kafin ta dagota da fadin, "Hafida-ti kema ai ba lafiyarce da ke ba ma, dan zazzabin ne a jikinki. Kin ma ci abinci. Idanun Iffah cike da hawaye ta girgiza kai da fadin, "Na koshi Jaddah". "Bazai yiwu ba dan bake kadai bace. K Iftihal hadomin abinci mai sauki acan. Cikin rawar jiki Iftihal ta nufi dining room, har yanda tai din ya bama Daneen Waheeda haushi sai dai babu damar magana. Babu jimawa ta kawo abinci, Malikat Haseenat ta amsa da kanta ta na bama Iffah'r. Da kyar take amsa da taunawa kamar magani, batafi cokali hudu ba tace ta koshi. Lallabata Malikat Haseenat da Daneen Ammarah suka shiga yi, da kyar ta kara biyu, daga haka suka shiga lallashinta da nasihar ta kwantar da hankalinta, dan saita kwantar da hankalin natane shima zata taimaka masa ya kwantar da nasa. Ta gamsu da nasihar tasu, anan ma takejin Ummu sun wuce, Malikat Bushirat ma jikin nata ya sake rikicewa yanzu haka ga likitoci can sun kasa shiga su dubata dan kurajen jikinta nata cigaba da fashewa warin na kara karuwa. Batace komai ba illa hawaye da suka zubo mata sharr. Wanna ranar ita take guje mata, gashi tun kan aje ko' ina kuwa har tazo din. Basu wani jima a sashen ba suka tafi, haka ta koma dakin ta zauna ta saka Tajwar Eshaan gaba tana tofa masa addu'oi da fatan ALLAH ya sanya masa nutsuwa da Karfin zuciya akan al'amarin. Haka dai ta kasance bata wani samu isasshen barci ba, koda ya farka cikin dare da taimakonta ya samu yay salloli, ta debo masa abinci amma yaki ya ci, sai da ta fara masa kuka ya danci spoon biyu shima dole ta hakura ta kyalesa dan barcine bai gama sakinsa ba.Dan haka ya koma ya sake kwanciya…… Gabanin asuba wan irin ihuface-iface na tashin hankali ya farkar da ita, zumbur ta mike kamar wadda aka tsungula. hun yayi yawa matuka dan haka ta fita a razane, ALLAH ma yaso doguwar riga ce ta abaya a jikinta. Hadiman sashen Shahan-shan din duk wasu sunyi barci ma, sai jami'an tsaro dake kai kawo a ta waje da Ghazi. Sai dai duk an firgitasu ashe sune keta hun, Wani irin sarawa kan Iffah yayi, a take ta birkice alamar mutanen sun zo. Wani irin jan takobin dake a hannun masu tsaron kofar shiga falon farko na kasa Iffah tai da ga cikin kubenta ji kake wani zuuuuuu!! Sharbebiyar takobi ce mai tsananin walkiya da tada tsigar jiki, tuni tayi tsakkiyar masarautar ta wani irin karta takobin bisa kasa. Kamar yanda mafi yawan mutanen masarautar sukaji wanna tashin hankali haka sukaji karta takobin da Iffah tayi akan kasa da yin wani irin kara ji ta ce. Duk wanda ya shirya idan ya isa yazo gabanta. Saiko ga kusan mutum hudu sun bayyana gaban nata tsirara sai dan ganye a gaba suna wani irin huci da bulbulo da wutar tsafi ta baki, Juyi ta sake. yI, da wulwula takobin ta cake akan kasa, kafin tai wani irin zarota tai juyi bakinta na ambaton sunan ALLAH tamkar kyattawar ido sai ga kawunan shegun a kasa hudu reras. Zo kaga ihu, ga hadiman da duk suka farka saboda tsabar tashin hankalin firgitasu da wadan nan mutane sukayi, wanda sune a daren jiya suka shigo sukai musu kisan gilla dama. Ba kowa bane kuwa face a cikin zuri 'ar su uwa. Tuni fa masarautar ta kara rikicewa, wanda ma bai farka ba sunata farkawa. Can sai ga Jasrah ta fito cikin kuka da kururuwar an dauke Malikat Bushirat. Ba kowa yasan mike faruwa akan Malikat Bushirat din ba sai su shakikanta, duk da dai dazun anga duk ahalinta sunzo gidan, sannan Malikat Haseenat ta fito ranta a bace da sashen ita da Daneen Ammarah. Dama Daneen Waheeda bataje ba dazun din dan haka maganar dai har yanzu bata fita akan tsiyatakun da Malikat Bushirat din ta fada ta aikata da bakinta ba. Kowa dai nata hasashe da son bin kwakwkwafin al'amarin. Masarautar ta rude gaba daya, ALLAH dai yasa itama Daneen Ammarah da nata kwankwaman a ka da kyar ta rike Iffah. Barci dai a wannan dare yara kanana ne da basu san komai ba a wannan masarauta suka yisa. Dan tuni shima Tajwar Eshaan ya farka. Tun a daren Iffah tai kiran kaka a waya, asubar fari kam a cikin masarautar ta masa. Ana idar da sallar asuba aka shiga meeting na gaggawa. Kaka, Iffah, sai manyan masu fada ajin masarautar irin su Sayeed Fayzul-haq da sauransu........✍️ DAUDAR GORA Book2 90 .....Kaka ne ya fara magana rai bace. "Wadan nan mutanen yaki suka shirya dan gaske bawai wasan yara ba. Daren shekaran jiya sun zo sunyi kisan gilla jiya ma sun dawo harda daukar Malikat. Wadan nan da Fhareedatu ta sarema kawuna jiya bawai su kadai bane, guduwa sauran sukayi. Dolene a nemo mafita dan a dawowa ta uku zasu sake sabon shiri ne. Shakaran jiya sun kashe kusan mutane hamsin, yau ga kusan mutum tara fa, dan ma yau ALLAH ya fargar da da sai sun gama illarsu sun tafi kamar ta shekaran jiyan sannan za'a sani". Sayeed Hifzur-rahaman ya ce, "Tabbas akwai matsala kam, dan da gaske suke ba wasa ba. Sai dai fa matsalar idan munce wani yunkuri zamuyi ta ina zamu kama ne?. Ku dubesu kamar ba daga jinsin mutane suke ba, ko kyawun kallo basu da. Ga su da karfin tsafin mai ban tashin hankali..... '"Babu wanda yafi karfin UBANGIJI ai. Dan haka zamu tunkaresu gaba-da-gaba". Iffah ta fada cikin bacin rai. Duk kallon toro sukai mata, sai dai kafin wani yace komai da ga bayansu aka amsa da "Tabbas mune zamu tunkaresu kamar yanda ta fada". A razane duk suka juya suna kallonsa. Shi din ne dai ba wani ba. Shahan-shan Eshaan Ibn Haysam Abdul- majeed Aliy Qutb. A kallo daya idan kai masa bazaka sake marmarin karawa ba dan firgicin a yanda yake yau. Cikakken GWARZON BARDE abin tsoratarwa ga duk wanda zai iya kallonsa. Karasa takowa yay cikin takun nan nasa daddaya da yau ya kara zama cikin izzar damuwa da bacin rai. Ga ido ya toshe da bakin gilashi alamar yau babu koda digon sassauci. Dole kowa ya mike cike da girmamawa a garesa.Maimakon zama tsaye yay kikam idonsa akan Iffah, cikin bada umarni ya ce, "Cigaba da bayanin ki". Kai ta jinjina masa cikin girmamawa sannan ta dubi kaka. Shima kai ya jinjina mata dan haka ta sake fuskantarsu. "Tunkararsu itace babbar mafitarmu kamar yanda Kaka ya fada, dan tsafinsu da wani karfin maita babu abinda zai mana da karfin tasirin UBANGIJI. Dan dole ne mu shafe babinsu gaba daya in har muna son cigaba da rayuwa cikin salama.Mataki na farko a yanzu shine Taswirar jejin da ake saka ran samunsu, sannan hada manyan baradan mayaka da ga yanzu zuwa awa biyar kacal da muke da ita…. '"Amma ranki ya dade ai bamu san jejin da za' a iya riskarsu ba. "Sayeed Aashiq-Muhammad ya fada cike da girmamawa ga Iffah'r". Kaka ne ya amshe da fadin, "Wannan bazai zama mai wahalarwa ba, dan dukkanin abinda ke zagaye da wanna kasa muna dasu a rubuce a kundin litattafan tarihinmu. Za'a iya bincikawa tunda kabilar tasau dadaddiyar kabila ce". Itama Iffah kanta ta jinjina da fadin hakanne kam, dan nima a karance-karancen tarihi da nai a kwanaki akwai wani littafi daya tabo makamancin dabi unsu. Dan haka muna bukatar Sayeed Aynul-Hassan shima anan". Ba'a wani bata lokaci ba wajen kiransa, sai ko gashi da tarin littafai da wasu manyan takardun taswura da ke kunshe da gaba daya kasar ta ruman da dazukanta. Kaka ya bada umarnin tattara mayakan da ake da kyakykyawan zato a kansu, dan haka Sayeed Tasadduq-Husain ya fice domin yin wanna aiki. Sayeed Aynul-Hassan mai alhakin kula da da books room na masarautar, wanda kuma yayi rubuce- rubuce da yawa hakama mahaifinsa da kakansa a take ya bada littafin da ake kyautata zaton sune a wannan tarihin, dan bayan su din akwai dazukan da wasu mutanen daba su din ba ke zama sai dai su sun banbanta da su. An aika amintaccen Tajwar Eshaan wajen Malikat Haseenat domin amso wasu taswuriri nan ma da ke a daki littatafan sirri dake ainahin dakin karatun Tajwar Abdul-majeed. Nan take su Iffah suka shiga bincike aka kuma baje manyan taswuririn a bangwayen babban dakin meeting din. Annan ne fa Tajwar Eshaan ya bama kowa mamaki, dan ashe masanin taswurane matuka. Komai da shi akayi, kusan shine ma gaba wajen bada sirrikan dazukan, kaka da Iffah na bada shawarar yanda ya kamata a shigesu a kankanin lokacin da ake da shi suma. Suma dai sauran kowanne da irin rawar da yake takawa. Da ga can cikin masarautar Kuwa kowa ka gani hankalinsa a tashe yake, dan hadimai masu karfin hali ne kawai suka iya gudanar da ayyukansu. Wanda aka kashe kuma anata kokarin musu sutura amma na iya cikin masarautar. Wadan da Iffah ta fillema kawuna ko ace aljanunta kam suna a nan tsakkiyar masarautar rufe yara da mata dama wasu a mazan sun zagayesu sunata kallo. Yan uwan Malikat Bushirat tuni sun iso masarautar suma hankali tashe da jin cewar wai Uwa ta dauke ta. Duk da tsiyatakun data aikata, da kuma ciwon da ke jikinta sai ya zam maganar nan ta malam ba haushe da kan ce *_DAUDAR GORA CIKI KA SHATA_* Hankali iyaye musamman mata na masarautar bai kara tashi ba sai da suka ga ana tattara matasan masarautar ga dokuna majiya karfi ana fiddowa, Sayeed Tasadduq-Husain nata waya da shugaban sojoji na kasa ana shirya motsocin yaki da jirage uku da ya bada umarni. Hakan na nufin mataki na karshe ake shirin tunkara wato yakin gaba-da gaba da matsafan mutane irin su uwa, kafirai da basa gane komai da ga tsoron ALLAH. Wasu tuni suka fara nuna basu yarda yaransu suje ba. Amma matasan samarin nan da Iffah ta dunkule akan sakasu aikin raba abubuwan azumi dana salla sun hade kawuna akan sufa babu gudu babu ja da baya zasu kare martabar masarautarsu da sarkinsu da kasarsu ne. Duk da basu san wahala ba, bama su taba gain yaki na zahiri ba. Gain fa abinda matasan nan sukai yay matukar burge was hadiman suma suka fito da shirinsu na kasancewa a cikinsu.. Ga al'ummar gari ma ba'a barsu a baya ba. Dan tun zuwan labarin abinda ke faruwa ta hanyar matasan nan da suka yada a social media sai ga mutane nata yo gangami musamman matasa da dama jirafa suke ace kule suce cas, Dan shi matashi a duk inda ake dan shirin a mutu ko ai rai ne, shiyyasa a mafi yawan gaba ta rayuwa inhar wani rikici ya tashi sai ka samu matasa ne sukafi zama gaba-gaba akan al'amarin. **. Da sauri Iffah tabi bayan Tajwar Eshaan da ya fice da ga dakin meeting din, Shigowarta dai-dai da fitowarsa da ga closet dinsa rike da sulken yaki da bata taba sanin da su ba ma a masarautar. Da ga shi har kayan takema kallon mamaki. Shiko ya dauke kai kamar bai fahimci abinda take kalion ba ya hau shirinsa. Dammarar da yake kokarin daurawa ta rike jikinta na rawa. "Maleek mi kake shirin yi ne haka?!". "Fita bama kasata kariya mana da al'ummar cikinta, ko kina nufin zan bar yayan mutane su tunkari wannan hadarin su kadai Sohaa". '"Ba haka nake nufi ba, sai dai ka tuna mutanen nan kai ne fa abin harinsu kai tsaye a wanna gabar shiyyasa ma suka dauki Ammie, fitarka wannan yakin akwai damuwa. Kayi hakuri ka barmu mu muje". Ido ya tsira mata na wasu mintuna, sai kuma ya saki murmushi ya cigaba da daura dammararsa. "Ai ke badake ma za'aje din ba..." "Saboda mi?". Ta fada cikin tsananin damuwa. Nan ma shiru kamar bazai amsa mata ba, sai da ya mula dan kansa a fisge yace, "Saboda matata kwai ce a a hannuna, tattalinta shine abu mafi girma a gareni, kuma kin manta kinada karamin ciki ne." "Amma.. "Shini!!!!" Yay saurin katseta ta hanyar aura yatsarsa akan bakinta idanunsa da har yanzu suke jazur a cikin nata. Kif-kif ta farayi da nata sai ga hawaye sharrr. A hankali ta daura hanunta saman nashi da ke a bakinta ta janye, hannunta biyu ta saka ta rike hannun har yanzu idanunta dake cikin nasa na zubda hawaye. "Bazan Iya barinka ka tafi kai kadai ba". Murmushi ya sake sakar mata yana lumshe idanunsa A hankali ya ce, "Sohaa idan mun tafi gaba daya waye zai rike al'ummar kasar? Dole kece madadina anan, roko daya zan miki koda a rasa rayuwata a wanna gabar ki zama shugaba adala, karkiyi sakaci da hakkin, al'ummar wanna kasa. Kiyi gaskiya da adalci akan masu gaskiya, ki hukunta duk wanda yay kuskure akan kuskurensa. Ki zama uwa ta gari da zata bama ya ko dan da zaki haifa mana, ki tsaya akanta ko a kansa da ilimin addini dana zamani, ki cusa masa muhimmanci tsoron ALLAH da gaskiya a zuciya..... Kuka ta wani irin fashewa da shi ta fada jikinsa.Rungumeta yay tsam-tsam shima yana sauke ajiyar zuciya. Gangi da aka fara bugawa na umarnin fitowar mayaka ya sashi janyeta a jikinsa a hankali, shirinsa ya karasa sai gashi ya fito a cikakken gwarzon barden sa. Bai bata wata damar cewa wani abu ba ya kama hanunta kawai suka fito. Tsitt kakeji masarautar tayi da mamakin ganin har da shi za'ai fitar, sai kuma hankalin iyaye da yawa ya dan kwanta, al'amarin kuma ya kayatar da kowa. Sai da ya gama kallonsu daya bayan daya duk kawunansu a kasa sannan ya nisa yana lumshe ido da budewa. A hankali ya furta,"Kuyi hakuri! Kuyi hakuri!. Kuyi hakuri da gazawata a matsayin shugaba gareku. Ina jin ciwo fiye da irin ciwon da kuke ji, duk abinda zan iya fada muku a yanzu kun riga kun sanshi. Wanda zan maimaita kawai shine koda na rasa raina a wannan yakin MATATA itace mai gadon shugabancin da ALLAH ya daura min, inada yakimin zata samar muku fiye da abinda ni na samar muku. Idan kuma inada rabon dawowa gareku akwai abubuwan fada a bakina sosai zan kuma isar da su gareku. Duk wanda nama ba dai-dai ba a wannan hukunci ya gafarceni, ina hango muku abinda ba lallai ku hangoma kanku ba. Nagode da tarin kaunar da kuka nunamin a tsahon shekarun dana dauka matsayin shugabanku". Hawaye kowa keyi a wajen. Ya dan murmusa yana hadiye abu mai ciwo da ya tsaya masa a makoshi. Hannun Iffah kawai ya kama ya nufi fada, gaba daya aka take musu baya, sai dai manyan ne kawai suka shiga. Can ya dagata ya ajiye akan kujerar karagar mulkin Shahan-shan. Wani irin kabbara aka dauka Iffah kuma ta fashe da kuka. Murmushi yayi tare da kaiwa gabanta ya ajiye guywarsa kasa ya tokare kafa daya kamar wanda ke shirin saka mata zoben baiko. Hanunnta ya kamo cikin nasa ya rike tare da kaiwa saitin bakinshi ya sumbata. Cikin wata irin murya mai sanyi da nutsuwar ya ce, "Kin tuna ranar da kika sanar da Ajmaal burinki na hawa wannan kujerar? To ki dauka yau ALLAH ya cika miki, ALLAH ya baki ikon sauke nauyin hakkin al'umma My Sohaa". Gaba dayanta ta zubo kasa ta fada jikinsa suka kankame juna. Dole gaba daya kowa ya fice kawuna a kasa… Bayan minti kamar biyar suka fito hanunsu cikin na juna, a gaban barden dokinsa dan amana suka tsaya, kamar yanda ya saba yay haniniya tare da kwafutar kasa yay wata irin girgiza. Murmushi yayi a hankali tare da daura hannunsu dake cikin a juna akan fuskar dokin. Sai ko dokin ya kara girgiza da matsawa gaban Iffah sosai. Murmushi Iffah dake hawaye tayi, ya kalleta shima murmushin har yanzu akan fuskarsa. Dayan hamunsa yasa ya goge mata hawayen sannan yay wani irin salon tsalle na bajinta ya haye saman dokin. Take suma sauran suka haye nasu dokunan aka cigaba da buga gangi. Iffah ta kallesa ta kalli Babiy ta kalla kaka ta kalli Hanash da duk suna a cikin wanna tafiya sai kawai ta fashe da kuka.......... 🚴🚴🚴🚴Basai munga yakin ba kawai a tsallake ALLAH na gaji 😫 DAUDAR GORA Book2 91 ....Sun hadu ne a mahadar shiga jejin su da sojojin kasar da suka rigasu isowa kasancewar su a dokuna ne. Shine ya fara dirgowa da ga dokin nasa. A tare sojojin suka mika gaisuwar girmamawa ga Shahan. shan din nasu. Ya amsa musu da kulawa, tare da basu umarnin mikewa. Duk mikewar sukai, sannan shugaban sojojin ya iso garesa tab…. a hannunsa ya mikama Sayeed Tasadduq-Husain dake a gefensa. Amsa Sayeed Tasadduq-Husain yayi tare da matsawa kusa da Tajwar Eshaan, shi din masanine na gaske akan ilimin sanin taswura da bibiyar waje, dan haka cike da kwarewa ya fara sarrafa tablet din cikin bibiya ya saita abinda suke bukata. Tab.. din a maidama Sayeed Tasaddug-Husain yana mai dubansu gaba daya. Kowa sake nutsuwa yayi akan kafafunsa har shugaban sojojin. Taku daya biyu yay sai kuma ya tsaya cak hannayensa goye a bayansa. "Bazai yuwu ace mun fito wannan yakin batare da an rasa ran wani ba a cikinmu, ina fatan koza'a rasa din to ya kasance ni ne!?.……." babu wanda maganarsa bata razanar ba a cikinsu. Dan sai da duk suka zabura suka kallesa.Basarwa yay tamkar bai fahimta ba ya cigaba da fadin, "Kowanne shugaba yakanyi yaki ne domin kare al'ummarsa da kasarsa. Haka ma kowace al'umma kanyi yaki ne domin kare shugabansu da kasarsu. To a wannan gabar ina son kuyi yakine domin kare kasarmu da kayinku. Karku damu da bada kariyarku gareni zan kasance a karkashin kariyar UBANGIJINA.Mutanen da zamu tunkara duk nan mun san mutane ne masu hadari, wanda kuma bai sani ba ya sani anan sunada hadari, sannan an raini zukatansu ne da daukar fansa tamkar yanda uwa ke rainon yaronta da abincin jikinta. A mu duka da muke nan akwai masu mata da iyaye da yaya, akwai masu yaya da mata kawai, akwai masu yaya kawai, akwai masu iyayen ma kawai. Mu duka mun barsu ne suna kuka, kuka, mai ciwon shiga kila wa kala a saran dawowarmu ko mun rabu kenan. Ya zama dole musa a ranmu mun barsu da wannan tabon, musa a ramu koda bazamu dawo ba to mu kasance su mun karesu da ga sharrin wadan nan mutanen ta hanyar shafe babinsu a doron kasa na har abadan abada. Dukanmu bamu taba yaki ba a zahirance, amma sanin kowane dan kasar ruman iyayensa kan horesa da iya wasan takobi tun yana kankaninsa musamman mu maza. Wanna yasa bana jin ko dar da ga gareku jarumaina. Zamu tunkaresu da karfin ikon ALLAH, da karfin zukatanmu, da karfin kwanjinmu, da karfin horaswarmu, da karfin kare kasarmu, da karfin kare al'ummar mu da addininmu. Ka tuna a ranka mafifici a halitta ya yaki kafirai ne da duk wadan nan karfin ikon domin mu kasance a yau din mu cikin bautar UBANGIJI babu wani mai kuntatamu. Sai dai idan har mune muka wofantar da darajar daya sama mana tun a wancan lokacin sai mu rayu a karkashin mulkin mallakar kaskastattun kafirai. Bana fatan mu kasance hakan da karfin ikon ALLAH " A tare sukace insha ALLAHU. Murmushi yay a karo na farko tare da duban kaka da shugaban sojoji. "Mu ukun nan mune kwamandojin wannan yakin, kar'a taba kananan yara, dan zamu iya zama jagororin canja musu alkibla bayan sun dawo hanunmu. Daga basu ba kowa abin harinmu ne. A lokacin da kuke shagalta da yakarsu, ni zan tunkari shugabar tasu ne.. Duk sun amsa da girmamawa. Daga haka aka fara nufar abin hawa. Wasu a cikin sojoji sun shiga jirage, inda aka bukaci Tajwar Eshaan shiga daya da aka kawo domin shi amma ya ce shi akan doki zaije. A dai duk cikin matasan idan da mai sha'awar haka ko rashin jimirin tafiya a doki ya kasance a cikin sojojin.Wasu sunyi hakan, wasu ko suna tare da shi a dokunansu. Bayan anyi doguwar addu'a masu bibiyar hanya ta na'urori suka fara aikinsu. Masu dokuna ne a gaba, motocin yaki na sojoji a biye da su, ta sama jiragen yaki da suka rarrabu a jejin domin sanar musu motsin komai da zai iya tunkarosu a tafiyarsu su da suke kasa musamman ma nakan dokuna. Kamar yanda Tajwar Eshaan ya bada shawara kowannensu bakinsa dauke da addu'oi.. Anan ma cikin kasa da kewaye tuni an dukufa addu'oin musamman ma cikin masarautar ruman.Yara da manya kowa ya nutsu gayama UBANGIJI da fatan kariya ga wadan nan bayin ALLAH da suke tunkaran hadarin rayuwa ko mutuwa. manyan malamai da al'ummomin yankunan su an dukufa gayama ALLAH.Yayinda mutane suka dinga cincirindon taruwa a kofar jejin ta kowacce kusurwa zaman jiran tsammani.. ** Sun nausa matuka cikin jejin da bakajin motsin halitta irin ta mutane sai tsuntsaye nau'i-nau'i,yayinda a farko-farko suka dinga wuce kauyuka. Duk kauyen da suka gifta aka sanar da Shahan-shan ne da kasan sai kaga matasan kauyen sun daura dammarar bin bayansu suma. Dan sunfi kowa sanin dazukan wajen da abinda ya kunsa. Ga sojoji ta sama suna isar da sakon duk inda suke tunkara. Tafiyar awanni biyu cur ta iso da su gab da bataliyar sansanin da su uwa suka kafa gari. Anan suka taka birki bisa umarnin Shahan-shan aka gabatar da sallar la' asar, yayinda jiragen sojoji keta kai kawo da sake bincike jejin ta yanda su Uwa bai zama lallai su fahimta ba a tunaninsu. Sai dai kuma abinda basu sani ba su Uwa nada yan leken asiri a wasu kauyuka, hakama sunada na hatsabibanci tsaface-tsafacensu da suka kafa domin shirin kota kwana a irin wanna yanayin. A yanzu haka ma yan leken asirinsu sun isar musu da sakon shigowar su Shahan-shan din. Jin harda Tajwar Eshaan wata irin kyalkyalewa da mahaukaciyar dariya uwa ta shiga babbakawa da dukanin budaddiyar muryarta, sautin yay wani irin karade dajin. Sai da tayi mai isarta sannan ta bada umarnin kowa ya kasance cikin shirinsa. Dandanan suka fara shiryawa mazansu da matansu, masu hayewa kan bishiyu nayi, masu hawa kan dunitsina nayi, yaran aka tattaresu cikin wani kogon dutse gaba dayansu dake nan jikin kauyen. Dai-dai nan jiragen sojoji suka mamaye garin ta sama. Dabbobin da su uwa ke kiwo kawai suka iya gani, dan haka suka sanarma da Tajwar Eshaan akwai matsala fa. Dan kauyen babu kowa cikinsa sai dabbobi. Da mamaki yace, "Kamar ya babu kowa?". Shugaban sojoji ya ce, "Wlhy babu kowa sai dabbobi”. Yanke wayar Tajwar Eshaan yayi, kaka dake kusa da shi duk yaji komai, murmushi kawai yayi, kansa a kasa batare da ya kallesa ba ya furta,"Babu inda sukaje ranka ya dade, hakan na nufin sun san da zuwanmu zuwa yanzu. A sanar musu kar jirgi ko daya ya sauka kasa har sai mun fara shiga". Sayeed Tasadduq-Husain Tajwar Eshaan ya mikama wayar, dan haka shi yay kiransu ya sanar musu.Shugaban sojoji zaiyi gardama Tajwar Eshaan ya sake amsar wayar, babu alamar wasa tattare da shi ya furta, "Kuyi yanda akace". Cikin girmamawa yay saurin amsawa. Daga haka suma suka hau dokunansu, kaka ya juya yana kallonsu, "Kowa ya kasance bakinsa da addu'a, duk abin tsoron kuma da za'a iya bude maka do da shi karka razana. Kar kuma mu yarda addu'a tabar bakinmu dan itace babban makamin da zai iya rusa wadan nan mutanen bakwai makaman hannunmu ba". Duk sun amsa da girmamawa garesa, da ga haka Tajwar Eshaan ya yunkura. Shi da Kaka sune a gaban,sai tawagar masu dokunan biye da su, sai motoci sojoji da duk wanda bazal iya tafiyar kan doki ba. Har suka iso tsakkiyar garin suma basuga komai ba sai farin dabbobi. Shiru sukai tsaiwar shirin kota kwana suma da baza idon son gain ta inda wani zai fara bullowa. Mintuna uku shiru sunata ambaton ALLAH sudai, sai jirage da ke ta kai kawo ta sama. "Kodai zamu sauka mu bincika ne?". Daya da ga cikin samarin ya fada. Alamar yay shiru kaka yay masa. Kai ya jinjina masa. Cikar minti daya da hakan bai karasa ba dajin ya dauki wani irin sautin kuka mara dadin ji. Hatta wanda ke cikin jiragen sal da zukatansu suka shiga bugawa da sauri-sauri. Sai dai kowa yayi tsam bakinsa da addu'a. Kukan sake cika musu kunnuwa yake da tunkarosu, hakan yasa kowa sake shiri. Wasu inn halittune masu ban tsoro da rashin dadin kallo suka zagayesu. Cikin dakiyar zuciya Kaka ya furta. "Kar wanda ya firgita". A zahiri dai kowa ya amsa masa da to, amma a zukatansu wasu dai kam sun razana. Amma sai ambaton ALLAH da sukeyi ya saka musu wata jarumta da jin karfi, kafin ma halittun sun yunkura su sun yunkura a dokunan batare da jin zasu gagaresu ba duk da yawansu. Na cikin motoci ma duk sun fito, haka ma wanda ke cikin jirage, jirgin na daga sama suka dinga silalowa ta sama sai ya zamto sunma halittun kawanya. Su Tajwar Eshaan a tsakkiya, sai halittun,sojoji a karshe. Cike da jin karfin zuciya Tajwar Eshaan ya fara ketawa cikin halittun sai ga kawunansu yana saukewa da takobin hanunsa shi da kaka. Gain hakan yasa a cikin samarin ma wasu suka afka sura. Tuni halittun suma sun fara tsalle a kawunansu, sai kusan uku su taru a kan mutum daya, cikin dai amincewar UBANGIJI suka gama kaudasu a abinda bai wuce mintuna ashirin ba. Da yawansu sun jijii musu ciwuka da farautansu. Ganin haka su Uwa suka sake turo wasu. A yanzu kam kaka ne yay wani irin dirowa daga saman dokinsa. A kausashe ya dubi halittun da suka sake zagayesu da fadin, "Ku kananun hatsabibai, idan har baku kasance matsoratan kafurai ba ku bayyana kayinku mana mushirikai. Ko kun tsorata ne? Nace ko kun tsoratane Uwar gijiyar taku ta reneku da tsafine kawai amma babu karfin zukata da jarumta!!!". Tabbas wadan nan kausasan maganganu na kaka sun matukar musu dacin, dan kuwa jikin uwa da ke a dakin gumakansu ga Malikat Bushirat shimfide sun zagayeta cikin wata kaya da kayan tsafi rawa ya kamayi, cikin wani irin kara ji da mummunan sauti ta ce, "Ku fito ina bukatar kan shugaban nasu a gabana. Kuma ina bukatar karagar mulkin ruman a gabana a yanzun itama tare da kan tsohon nam dana matar shugaban nasu da ya bari gadin gida"….✍️ DAUDAR GORA Book2 92 -.Maganarta ta zama tamkar busa musu kaho da kada musu gangi ne. Dan saukar kibau kawai su ka fara ji shuuuuuu daga sama. Da sauri Sayeed Tasadduq-Husain yace,"Garkuwa sojoji masu karfi da karfafawar ALLAH!!". A take suka dunkule waje daya suka zagaye Tajwar Eshaan ya koma tsakkiya tare dama kansu garkuwa kibiyiyin suka dinga sauka akan saman garkuwar karfen hannayen nasu. Da wanna damar yan kabilar su uwa da ke saman bishiyu da duwatsu fara dirgowa kasa suka zagayesu. Sanda suke janye garkuwar bayan gama saukar kibau din sun gama zagayesu. Ko kadan hakan bai razanasu ba, dan kowa a fusace yake da jin tsanar wadan nan kafirai. Sannan sunyi alkawari duk rintsi bazasu bari a taba musu Shahan-shan din su ba. Tuni sukai wata irin rabewar da kaka duk ya tsara musu. Su kuma gain hakan sai sukai tunanin tsorata sukayi ne suka afka kai tsaye da tunanin korar su. Wannan itace damar farko data basu nasara akan wadan nan mutane, cikin kankanin lokaci kura ta tashi waje ya hargitse. Kabilar uwa sunyi shiri ne irin shirin da wuka ko bindiga bazata ratsasu ba. Yayinda Kaka ya bada shawarar fara tunkararsu da wuka sai sunzo hannu ai amfani da maganin daya tanada wajen karyasu su da karfin yakin nasu. Gurin na cakudewa kam wadanda zasuyi feshin maganin ta sama da ga cikin jirgin sojoji suka fara. Tun anan fa ihu-da-ihu ya hargitse, suka fara kaiwa kasa samarin nan a gille kawunansu. Yayinda kabbara ke tashi da amsa kuwwa a cikin jejin. Cikin abinda bai wuce awa uku ba an gama da kaso biyu da rabi bisa uku a cikinsu. Zuwa yanzu fa hankalin uwa da ke kwasar dariya ya fara tashi. A take ta bada umarni ga wadanda ke zagaye da ita fara aiwatar da shirinsu akan Malikat Bushirat. Dan hakanne plan c dinsu, plan b shine wasu kason mutanensu da ke can masarauta dakko karagar mulkin Shahan-shan.. ** MASARAUTA ** Kukan da taci ya haifar mata da matsanancin ciwon kai, duk yanda taso kin kwanciya sai da Malikat Haseenat ta takura mata. Kwanciyar tayi, sai dai bata rufa mintuna ashirin cikakke ba ta tashi a matukar firgice. Hankali tashe Malikat Haseenat da Daneen Ammarah sukai yunkurin riketa amma ta girgiza musu kai. Sun fahimci tabbas akwai matsala, dan haka Daneen Ammarah ta ce, "Mammah barta. Barta kawai akwai matsala ne". Hankalin Malikat Haseenat tashi ya karayi, dan tuni itama Daneen Ammarah din ta birkice a cikin kankanin lokaci. Dai-dai nan ko Amintacciyar hadimar Malikat Haseenat ta shigo hankali tashe, cikin hakki take sanar musu babu lafiya, ga was irin mutane nan da ba'asan ta inda suka shigo masarautar ba sun zagaye ko ina. Wasu a cikin jami' ai sun fara harbinsu amma ko gezau da alama ma bindigar bata kamasu. Wasu kaso a cikinsu kuma sun nufi fada ne inga karagar mulki take. Kafin ma takai karshe Iffah ta fice, Daneen Ammarah biye da ita. Gaba daya masarautar ta gama harmutsewa. Tuni kowa ya fara gudun ceton rai.Yayinda jami'an masu karfin hali da Ghazi da wasu a cikin hadimai da samari da aka bari sunata kokarin kai musu hari amma mutanen nan babu alamar razani a tare da su, saima wani irin dariya sukeyi cike da karfin iko na ko gezau. Ai babu wanda yasan ta yaya, ta ina ma, kawai saukar kawunansu aka fara gani bisa kasa. Hankalin Ghazi ya tashi, ganin SARAUNIYA Iffah ce da kanta ba sako ba. Tare da Daneen Ammarah da a yau kowa ya shaida eh lallai ba ita kadai bace itama da nata ifiritan aljanun bisa kai. Duk wanda ya tunkari Iffah kai kawai take sauke masa ta matukar fita a hayyacinta da canjawar kamanni. Suko hatsabiban wani irin bulbulo wuta suke ta bakunansu suna kokarin tunkarar fada da tuni aka rufo ruf. Masarautar tayi masifar rikicewa, mata da yara kuka kawai suke. Hakama wasu a cikin mazan tuni sun nema wajen buya. Hatta su Miran Jasim da ke a cikin kurkuku sun tabbatar yau gidan babu lafiya kam...... ** * Su uwa na tsaka da zagaye Malikat Bushirat da aka gama jikewa da ruwan tsaffi a tsakkiyar gumaka Tajwar Eshaan ya fado musu. Da wani irin jarumta dokinsa yay haniniya mai razanarwa kawai yay kansu.Daga dokin har shi Tajwar Eshaan din gani sukai sun koma musu wata halitta daban. Yau sai ga uwa tsaye akan kafafunta ta mike da ga kujerar tsafinta cikin matsanancin tashin hankalin gain dokin nan fa babban gunkinsu ya nufa. Kafin tai wani yunkuri yay ma butum-butumin gunkin wani irin duka da dukan karfin kwanjinsa shi da dokinsa sai gashi tarwatse a kasa. Ai ko kashin hannunsa yay wata irin karar masifa da ke tabbatar da yaji ciwo a cikin kashi. Hannun yay kokarin rikowa da dayan Hannunsa dake rike da linzamin dokinsa yaji saukar kakkaifar wuka a cikin damtsen hannun. "Ya Arrahaman!!" Ya ambata da dukkan karfin murya dana jiki da ya masa saura. Dan wata irin azabar zafi ce ta ratsasa har cikin kwakwalwa, Dai-dai juyowarsa kan wanda ya sokesa da wukar a dartsen hannun ya sauka kasa. Babiy ne da ya biyo bayansa, dan tun barowar Shahan-shan din a cikinsu ya farga yay azabar biyo bayansa. Bummm!!!! Shima Baby uwa ta sauke masa wani mulmulen ice saman kai, kara ya saki shima cikin ambaton ALLAH ya dafe kansa da jini ya balle, luuuu ya tafi kan dokinsa zai zubo cikin karfin hali Tajwar Eshaan yay wani irin juyi ya tallafosa. Gaba dayansa ya dago ya ajiye saman dokinsa. Kafin ya fisgo sarkar da suka shirya rataye Malikat Bushirat a ciki ya watsata, cikin amincin UBANGIJI ya samu nasarar sarko wuyan uwa da ke kokarin zare wata takobin tsafi da ga jikin wani gunki. Razananninayar karar data fargar da wanda ke waje ta saki, dan sarkar ta tsafi ce, amma cikin amincewar UBANGIJI shi Tajwar Eshaan din sai bata masa komai ba. Duk da da yawansu an musu jina-jina haka suka dinga dannowa dakin dan zuwa yanzu suma sun gama da wanda suke wajen, wadan da suka rage kuma an kamesu an daure bisa umarnin kaka. Cikin tashin hankali suka nufi Shahan-shan, amma sai ya girgiza musu kai alamar su barsa. Da kansa ya dirgo kasa, su kuma suka kama Baby da babu numfashi tare da shi suka sauke aka fita da dokin Shahan-shan. Shi da kansa ya daure uwa da sarkar nan tare da bama matasan sa umarnin rushe gumakan: a gabanta, rushewar kam suka farayi itako tana kukan bakin ciki da wata irin jijiga a cikin sarkar da ya dauretan. Shi kam takawa tay a hankali gaban Malikat Bushirat. Hannu ya kai ya yaye jan mayafin da suka. lulluba mata, dai-dai nan ta bude idanunta sai ko a cikin nasa, kallon juna sukai na kusan sakkani goma. Shi ya fara janye nashi da sukai wani irin jazur cikin lumshesu da budewa. Batare da ya yaye farin mayafin dake a kasan jan ba yasa hannayensa biyu ya dauketa duk da yanda hannunsa a haggu da yaji ciwo ga wuka a ciki jini na zuba ke masa azaba da rawa. Wasu irin hawaye ne masu zafi suka shiga rige-rigen sakko mata, dan su kadaine ke aiki a jikin ta, amma su Uwa sun sandarar mata da jiki gaba daya babu abinda ke aiki tare da ita sai kanta da idanun.Duk yanda ta kuresa da ido shi yaki yarda ya kalletan.Cikin sauri masu bada taimakon gaggawa da aka taho dasu cikin sojojin suka nufosa da gadon daukar marasa lafiya. Amma bai daurata ba har sai da yaje ga jirginsu na sojoji da suka sauka. A hankali ya shimfidar da ita, sai da ya tabbatar ya gyara mata mayafin da take ciki dan tsirara take sannan ya dubi matukin jirgin yana lunshe ido. Ya fahimci abinda yake nufi, dan haka ya kame jikinsa tare da salute nashi. A gaban su kaka ya tsaya ya wani rumtse danunsa da daura hannunsa saman wukar nan dake kafe a jikinsa zai fincike kaka yay saurin dakatar da shi. "A'a ranka ya dade, hakan da zakai matsalane, dan wukar ba wuka bace takai tsaye kamar saura akwai dafi tare da ita. Kawai ka shiga jirgi dan bai kamata ka koma damu ba a doki". Bai cire din ba, sai dai ya bama kaka amsa da cewar"Tare da ku zan koma Jaddi". Murmushi kawai kaka yayi shi da Sayeed Tasadduq- Husain, dan yau ne karo na farko da Tajwar Eshaan din ya kira shi da kaka. A dai-dai nan aka fito da Uwar dake daddaure cikin sarka. An tsareta da tambayar ina yaran garin suke amma taki fada, sai ma dariya data sanya musu da cewar, "Bazan fada ba, bazan taba fada muku ba. Dan ku tabbatar karar da mu iyayensu kamar kashe maciji ne baku sare kansa ba hahahahaha!!!!!". Babu wanda ace da ita komai saboda isowar jiragen sojoji da shugaban sojoji ya bada umarnin a karo, dan yanda suka jigata din nan babu mai karfin iya komawa ta mota ko doki. Ga wasu shimfide babu alamar rai ma tare da su. Wasu kuma sun jigata matuka da ko yatsansu basa iya dagawa ma. Kin fadar inda yaran suke yasa sukai tunanin ko sun dauke su ma daga jejin ne gaba daya yasa shugaban sojoji bada umarnin ana gama kwashe su a sakama garin wuta kawai. Uwa bataji wannan furuci ba, kasancewar an tisa keyarta ita da sauran mutanensu ashirin da daya daba'a kashe ba cikin motar yaki.Hakama sauran mayakan duk an sakasu a jirage su, marasa lafiya sune farkon wucewa domin zuwa a basu taimakon gaggawa. Kaka da Tajwar Eshaan da Sayeed Tasaddug-Husain da shugaban sojoji sune karshe, za'a warema Tajwar Eshaan jirgi ya dakatar dasu. Tuni sauran sojojin da aka bari suka sakama garin wuta gaba dayansa bayan an tabbatar da babu wani kauye a kusa da su da wutar zata iya shafa. Dan su tsabar bakin hali ma basu yarda yin makwaftaka kota kusa da wasu kauyukan ba. Wannan wuta itace ta dinga wasar kogon dutsen da suka boye aransu zafin ya dinga ashes batare da an san anan din suka boyesu ba. * Abinda ya far a cikin masarautar ya sasu iske cikin Dahab City a hargitse. Dan jiragen a inda suka dauke su farkon jejin dole anan suka dakata aka dinga kwasarsu a motoci. Nan din ma cike suka samesa da jama'ar gari ga yan jarida. Jinin da Tajwar Eshaan ya rasa sakamakon sukar wukar da aka masa mai dafi a hannu dama ga kananun raunuka yasa idanunsa har sun fara rinjaya, dan sal da taimakon shugaba sojoji da kaka aka fito da shi aka daura a gadon marasa lafiya zuwa mota Hankalin mutane ya tashi matuka dan sun fahimci Shahan-shan dinsu kenan gariin yanda sojoji suka zagaye gadon, hakama da aka saka shi a motar an zagaye motar da uban tsaron da korna miye ya gitta zal iya zama gawa ne….✍️ DAUDAR GORA Book2 93 ……..Cikin masarautar ma a hargitse suka sameta,dan tuni an is da Malikat Bushirat da aka fara tahowa da ita. Ga Iffah da jini ya balle mawa ta yanke jiki ta fadi itama aka shiga da ita ciki har yanzu likitocin da ke kanta basu fito ba. Tashin hankalin hakan yasa ko wanda suka sarewa kawuna ita da Daneen Ammarah bama a janye ba. Ba'a bari kowa ya ga halin da Tajwar Eshaan ke ciki ba aka shige da shi sashensa. Hakama sauran mayakan da sukaji munanan raunika aketa nufar cikin clinic da su duk da kukan da iyayensu keyi ba'a bar kowa matsowa kusa da su ba, wanda sukaji kananan raunuka ne dai aka zube a harabar masarautar suma ana basu taimakon gaggawa na ruwa da magani. Ga magrib ta gabato. Amma burin kowa dai yaji yaya Tajwar Eshaan ibn Haysam Abdul-majeed Aliy Qutb yake. Yanda suka tada hankalinsu yasa dole sai da Sayeed Fayzul-haq ya fito yay magana da yan jarida akan kowa ya kwantar da hankalinsa Shahan-shan na nan raye, sai dai yana bukatar addu'oin Su... *WASHE GARI* Alhamdullah an wayi gari da dadin rai, dan su Babiy duk sun farfado. Hakama Tajwar Eshaan kaka ya saka masa magani an kuma masa na asibiti da dorin karayar sai dai ace Alhamdullah. Itama dai Iffah an samu nasarar tsayar da jinin kuma cikin da aketama damuwar zai iya lalacewar dai yana nan. Malikat Bushirat ce dai idanun nan da kai kawai ke aiki, sai dai duk abinda za' a fada tana ji. ALLAH sarki Jasrah bata gazaba a yi mata hidima. Jama'"ar gari dama na masarautar da basu san komai akan al'amarin nata ba sunata tausayinta da gain Uwa ta tsafeta ne saboda cikar burinta. Was har addu'a suke mata na samun lafiya. Gawarawakin dangin uwa an tattaresu anyi rami acan daji an biznesu, wanda kuma suka rage tare da uwa an zubasu a kurkuku har sai ALLAH ya bama Tajwar Eshaan lafiya. Tako ina labaran abinda ya faru a kasar ruman dinne ke yawo a duniya, wasu na caccakar Shahan- shan akan abinda akai bai dace ba suma mutanen nada yancin kansu, wasu ko na ganin hakan da akai shine dai-dai. To koma dai yaya ne yan kasar ruman sudai hakan da akai yayi musu. Dan babu wata kasa da zata so rayuwa da masu bakin kafirci irinsu uwa.Masu ganin ba'a musu dai-dai ba ma son zuciya ne kawal. Lokacin da Iffah ta tartado taci karo da Tajwar Eshaan jikinsa ta fada kawal ta fashe da kuka. Ya rungume kayarsa yana murmushi shima idanun nasa dai sun kada. Sai da tayi mal isarta sannan ta dago, babu zato kawai yaji ta manne lips dinsu a waje guda. Idanu ya zaro itama sai ta zaro nata tare da janyewa tana dariya. Da sauri ya rikota da hanunsa mai lafiyar ya maidota jikinsa yana murmushi. "Wannan ai mugunta ce a lasama mutum zuma a baki a gudu". Ya fada cikin rada a kunnenta. Dariya ta shigayi a hankali tana boye kanta a cikin jikinsa, da ga haka ya canja wasan a yanda yake bukatar kasancewarsa, duk da kuwa komai da yake na karfin hali ne kawai, dan sam zuciyarsa babu dadi, shi kadai yasan halin da yake ciki akan mahaifiyarsa. Amma yanata kokarin dannewa da gayama ALLAH kukansa. Lokacin sallar azhar domin sake Kwantan da hankalin mutane ya fita sallar cikin karfin hali duk da hanun nasa an masa dorin karaya ne. Ga yankan wukar nan da yay matukar shiga jikinsa sosai, saukin ma dal anyi maganin dafin. Bayan anyi salla an fito ya dan gana da manema labarai da yasa a tara masa. A nan yay ma al'ummar kasarsa godiva da fatan alkairi bisa kokarinsu da addu'oinsu. Ya kuma sake jaddada Iffah matsayin SARAUNIYARSU har yanzu dan bazai amshi mulki ba sai ya samu lafiya. Babu wanda yay jayayya da wannan al'amari. Sai ma Tajwar na jihohi da manyan kasar dake ta layin zuwa dubashi tako ina, tare da sauran mutanen da suka fita wannan gumurzu. Musamman yan kauyukan nan da Hadimai da wasu a jama'ar gari da suka taimaka musu anhadasu da manyan kyautuka, hakama itama SARAUNIYA Iffah ta bisu su dukansu da manyan kyaututtuka da ya sakasu a farin ciki, dan ita dukansu ta hada har matasanta. Lokacin da don Malikat Bushirat ke gain bayanin Shahan-shan akan Iffah zata cigaba da rike matsayinsa har sai ya samu lafiya, da lokacin da ake nuna Iffah'r akan karagar mulkin Shahan-shan din randa take zartar da hukuncin kyautukan da ta bama wanda sukaje yakin a matsayin Sarauniya kuka ta dingayi, kuka mai zafi da tsananin kona zuciya. Sosai takejin radadi matuka a cikin kirjinta, ji take inama kafin zuwan wanna ranar ta mutu ta huta. Bayan tasha kukanta ta godema ALLAH ta cema Jasrah a cire mata tvn daga dakin. Jasrah har ta amsa da to Malikat Haseenat ta ce kar a cire. Dan tsaf ta fahimci manufar Malikat Bushirat din. Tana ammakin taurin zuciyar matar nan, ace duk wadan nan abubuwan daka gani basu isheka izna ta saraya ba. Ko dan data haifa ta kasa neman gafararsa ma balle su. Kai ALLAH ya rabamu da irin wanna mummunar zuciyar ta kafuran farko, Kullum sai Tajwar Eshaan yabi ta barauniyar hanyarsa dubota. Zasuje da safe shi da Iffah da an idar da sallar asuba. Zakuma suje bayan sallar isha' i. Da ga gaisuwa da tambayarta yaya jiki bai iya kara sake cewa komai. Sai ma ita Iffah'r ce kan dan mata addu'a ta tofa mata, duk da dai kaka nata kokarin bada magani ana mata ko za'a dace. Haka zatayi ta kallon Tajwar Eshaan tana hawaye, amma shi daga kallo daya na gaisheta baya sake yarda ya kalleta har yabar dakin kansa a kasa yake. **. Bayan kwanaki bakwai abubuwa da yawa sun dai-data, musamman masu kananun raunuka sunji sauki sosai, sai wanda suka jigata ne sosa ke cigaba da karbar magani. Baby ma dai da yake buguwace Alhamdullah jikinsa da sauki, dan haka Tajwar Eshaan yace kawai Daneen Ammarah ta tare haka nan. Duk yanda taso zamewa sai da aka shirya wani dan kwarya-kwaryar walima data kayatar. Dan anyita ne irin ta manyan mata masu aji da ilimi. Zuwa dare aka shirya mika amarya dakinta, Iffah kuwa ta dage sai taje. Sai da aka tuna mata itafa SARAUNIYA ce a yanzu, babu yanda ta iya dole ta hakura, amma tanata ima Mamyn (Daneen Ammarah) tabarar wai shikenan ita haka kowa zai tafi ya barta. Ita an kawota gidansu ita kuma za'a maidata gidansu. Itakam data san hakane kawai kowa yay zamansa gidansu. Dariya sosai Malikat Haseenat da Daneen Waheeda keyi da drama din tasu. Dan wata shakuwace ta musamman ta sake shiga tsakanin Iffah da Mamyn (Daneen Ammarah) taja yarta jikinta sosai da sake tabbatar mata da kaunar da take mata dabance a rayuwa. Haka itama Iffah'r tana kaunar mahaifiyar tata matuka duk da bata rayu da ita ba. Sannan tana kaunar Ummu dinta da Baby. Hanash Akhi kam ai shi na musamman ne gareta da Kakanta abin alfaharinta. Kullum cikin lallabasa take shi da lyyani su dawo cikin masarautar da zama ko zata dan ji saukin kewarsu da tayi. Shi dai ya nuna bazai dawo ba. Amma Tajwar Eshaan ya ce ta kawantar da hankalinta zai dawo mata dasu, Ba karamin farin ciki tayi da hakan ba.Dan shima Babiy an gyara masa gidansu sosai dan bazai iya barinsa ba saboda gidan gonarsa. Lokacin da za'a wuce da Daneen Ammarah sai gashi tana kuka, ta rungume Malikat Haseenat da Iffah sunata kuka. Da kyar Daneen Waheeda da Malikat Ashwaq suka rabasu aka fita da ita. Yau kuma sai dakin mijinta ban yarta. Tarbace ta mutuntawa suka samu da ga su Ummu, kowa halayen Ummu na birgesa, dan mace ce data amsa sunanta cikakkiyar mace jaruma abin koyi da nunawa a duniya ga kowa, Yan kawo amarya basu wani jima ba suka wuce abinsu. Lokacin da ango zai shigo Ummu da kanta tayo masa rakkiya cakin amaryarsa. Zata gudu Daneen Ammarah tace saifa ta zauna sunyi hira. Babu yanda Ummu ta iya dole ta zauna. Sai dai hirar ma dai duk akan rayuwarsu ta bayace data shude. Kuruciyar Iffah da su Arfa Daneen Ammarah har kuka tayi, ta jinjinama hakuri irin na Ummu. Ta kumayi alkawarin kyautata zamansu tamkar yan wan juna har abada. Zasu zama aminan juna bawai kishiyoyi ba. Ganin dare yaja da wayo Ummu ta tattare kwanikan da sukaci abinci ta gudu. Dama shi Hanash Akhi yana can masarauta Iffah ta rikesa wai shine amintaccenta, nan ko duk wayone dan taita gain dan uwanta ne. Dan babu wani abu da yake yi sai idan sun dan shiga fada zatai wani zama mai muhimmanci da manyan masarautar ya kasance a gefenta. Hakan sai ya saka mata zaman lafiya da Tajwar Eshaan sarkin kishi, dan tana ambata maganar Hanash Akhi dinne zai kasance amintaccenta harda kyauta sumba aka bata. Wai hakan shine dai-dai. Ummu na fita Babiy sauka yay kasa gaban Daneen Ammarah ya zabga tagumi ya wani zuba mata idanu. Murmushi tayi da jan mayafin jikinta ta rute fuska cike dajin kunyarsa. Ya lumahe idanu da budewa yana murmushin shima, Kafin ya mike tsaye ya yaye mayafin gaba daya ya kama kafadunta ya mikar da ita ya rungume abinsa. A tare suka dinga sauke ajiyar zuciya, sai kuma hawaye na tsananin kewa da tuna baya. "ALLAH na gode maka daka maimaitamin wannan rana a rayuwata. Ka gamamin komai UBANGIJINA daka bani mafi tsadar nan a cikin mata matsayin matata" "Ni zan godema ALLAH da samunka matsayin miji kuma uban yayana Zayyan. Tare da yar uwa jaruma Saliha irin Jumaymah. Yanda kuka sharemin hawayena, da zama silar canja labarin da ban taba tunanin zai canju daga kaddarata ba kuma ALLAH ya share naku hawayen. ALLAH ka hana shaidan shiga tsakaninmu. Nayi alkawarin in har inada rabon sake haihuwa a duniya zan malakama Jumaymah (Ummu) yayan nan har abada". Cikin rada-rada a kunenta ya furta, "Insha ALLAHU a yau din nan zan dasa kwam Arfa da Fariha gimbiyata." cike da jin kunyar furicin nasa ta wani kankamesa da boye kanta a jikinsa. Wani irin rungumeta tsam-tsam Baby ya sakeyi shima yana dariya, tare da bata sumbata tako ina a jikinta harya sauke akan lips dinta, Jin tsaiwar na neman gagararsu ya dauke abarsa tsamm suka shige daga ciki, dama dai ga Daneen Ammarah yar dum-dum kai kace bata wuce talatin a duniya ba. Jin an rufo kofa harda murza key nayi baya dan wanna fagen na manya-manya ne ba gain kanana irimmu ba 🥱😉😂🚴 * BAYAN WATANNI SHIDA DA FARUWAR YAKI TSAKANIN SU SHAHAN-SHAN DA SU UWA Kai kawo yaketa famanyi a cikin bedroom din nashi bakinsa dauke da addu'a. Duk ko yanda waya ta motsa sai ya daga da tsammanin su Malikat Haseenat ne. Babu abinda yafi burin ji a wannan gabar kamar ace ALLAH ya sauki Sohaa dinsa dake nakuda tun a daren jiya lafiya. Duk yanda yake da tarin ayyuka a fada ya kasa fita. Su Sayeed Fayzul-haq ma sun hakura da fitowar tasa yau tun sanda labarin nakudar Iffah'r daya iso kunensu. Sai kowa ya koma fatan saukarta lafiya. Daga wayar da tai dai-dal da bugawar agogo karfe sha biyu dai-dai na raar litinin din ya wani irin sauke ajiyar zuciya da zama cikin kujerarsa a hankali. Murmushi ne mai sanyi ya subuce ma kyakykyawar fuskarsa. A hankali ya motsa lips dinsa ya ambaci "Alhmdullah"., Sai kuma hawaye suka dan ciko idanunsa. Shi Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed Aliy Qutb ne yau ALLAH ya azurta da kyautar yayan har guda biyu mace da namiji daga jikin yar uwarsa kuma matarsa, farin cikinsa Fhareedah bint Zayyan. A take bakin ciki da kuncin dake tare da zuciyarsa a cikin watanni shidan nan yaji ya wani fada masa daga makoshi zuwa cikin ciki. Babban yatsarsa ya kai a idanun nasa a hankali ya dauke hawayen da sake furta. "Abbie an haifo maka jikoki har guda biyu a rana daya, lokaci daya da ga tilon danka. Insha ALLAHU za'a sake haifo maka wasu biyun kamar haka har sau hudu Abbie na. ALLAH ya gafarta maka, ALLAH ya yafe maka kurakuranka kai da Jaddi da ma duk zuri'ata data musulmi baki daya. Kai da Jaddi da Jaddah ne abin AL'FAHARINA ABBIE NA"……✍️ 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (94) *_MAAB LUXURY HOME._* _Duniyar kayan Kitchen da decoration din gida na keta raini. Ina uwar gida da Amarya, Ku ziyarci shagon mu dake No 22 Ahmadu Bello Way, Kano state. Ko kuyi order daga shafin mu na Instagram @maabluxuryhome. Ko Facebook @maabluxuryhome. Ko Ku nememu a lambar waya *08034631010*._ _____________________ .........Cikin ƙanƙanin lokaci zancen haihuwar Iffah ya karaɗe ƙasar ruman baki ɗaya. Tuni farin cikin kowa ya bayyana, tare da addu'oi ga waɗan nan jinjiraye da ga bakin al'umma. Yayinda Tajwar Eshaan daya matsa a kai masa su ke can rungume da kayansa tsam-tsam a jiki. Jinsa yake a yau ɗin kamar wani sabon mutum, final shima dai ya zama Abbie. Ga yaran sun ɗakko kamanninsa sosai musamman ma mace kamar an tsaga kara an karya da shi, gara namijin yafi rinjaya da Iffah shi kuma. Da kansa ya tauna dabino ya basu tare da musu huɗuba. Duk yanda yaso ganin Sohaa ɗin sa hakan bata yuwuba sai bayan la'asar tai barcinta ta huta sannan. Murmushi ta dingayi kanta a sinne saboda irin kallon nan na ƙasa-ƙasa da yake faman binta da shi. Duk sai taji kunya ta lulluɓeta. Har ya ƙaraso gaban gadon bata yarda ta ɗago ɗin ba sai da ya zauna a kusa da ita ya ɗago fuskar tata da kansa. Bai tsaya wata wata ba kawai ya manne lips ɗinsu waje guda. Sai da yayi yanda yake so da ita ya barta dan kansa sannan ya rungumeta yana jero mata daɗaɗan kalamai masu sanyi da ratsa zuciya da bata san yayi nisa a sani ba har irin haka. Jitai kawai idanunta sun cika da ƙwalla. Dan ita kanta bata san adadin ƙaunar da takema wannan bawan ALLAH ba zuwa yanzun. Tana jinsa daban a cikin daban a duniyarta. Shi ɗin na musamman ne a gareta fiye da yanda yake jinsa na musamman... Lokacin da aka kaima Malikat Bushirat da har yanzu ake nan yanda ake babu abinda ke motsi sai kai da ido Jasrah baiwar ALLAH nata wahala da ita kuka sosai ta fashe da shi. Suko yara kamar sun san inda aka kawosu suka wani dage da tsanyara kuka tsiyau-tsiyau kamar ƴaƴan magena da yau mukasha bikin sunansu (Na manta ban faɗa muku ba magena ta haihu ƴaƴa hudu kowa sai ya kawo kayan barka haihuwar fari ce babu ɗaga ƙafa😂🚴🥱) kuka sosai suka dingayi har abin ya bama kowa mamaki, ana fita da su sukai shiru kuma kamar basu ba. Koda aka maidasu anan bama Malikat Haseenat da Iffah labari murmushi kawai Iffah tai batace komai ba. Garama Malikat Haseenat tsohuwar ƙwarai ta tofa kaɗan. A can ko jikin Malikat Bushirat rikicewa yay sosai. Dan har sai da takai an kira Shahan-shan da Malikat Haseenat. Al'amarin kam yau dai bana wasa bane. Dan doctors da suka rufu a kanta ma dai sunyi iya ƙoƙarinsu amma bata bar jijjigar da ta dingayi ba, daga baya ma sai ga aman jini. Hankalin kowa ya tashi musamman Tajwar Eshaan, dan da kansa ya hau gadon ya rungumeta jikinsa ta dinga bulesa da aman jinin nan. Addu'a ya dinga tofa mata, ganin fa tafiyar mai tsaho ce Malikat Haseenat ta fara maimaita kalmar shahada ko za'a dace Malikat Bushirat ɗin ta karɓa. Hakan yasa suma sauran jama'ar dake a ɗakin suka dinga maimaitawa, Jasrah dai kuka take kamar ranta zai fita. Sai dai kuma ita rayuwa duk yanda kaso, bai zama lallai abinda kaso ɗin ya kasance a yanda kaso shi ba. Dan kuwa dai Malikat Bushirat ta koma ga UBANGIJI batare da ta iya neman gafarar koda ɗan cikinta tilo data jefa kanta a halaka domin haihuwarsa ba. Tayi mutuwa mai ban tsoro da tashin hankali, dan kuwa maimakon kalmar shahada da suka so ji daga bakinta sunan UWA ne ƙarshen ambaton ta cikin wani irin gurnani mai ƙarajin gaske daban tashin hankali. Wannan al'amari ya matuƙar kiɗima Shahan-shan. Dan jikinta na gama saki shima ya kife kansa akan fuskarta. Tsahon lokaci bai ɗago ba har sai da kowa ya fita a ɗakin Malikat Haseenat tazo tana lallashinsa. Sannan aka samu ya ɗago idanun nan nasa jazur matuƙa abin tausayi, sai dai baiyi kuka ba, ya jima yana kallon fuskar mahaifiyar tasa abubuwan data lissafa ta aikata na dawo masa tiryan-tiryan kamar yanzu take yinsu.... Masarautar gaba ɗaya ta gama rikicewa. Dan mutuwar nan kam ta daki kowa musamman da Malikat Bushirat ta zama tamkar wata tauraruwa a zamaninta a cikin gidan. Sai dai yanda mutuwarta tayi dai-dai da mutuwar kaf mutanen nan ƴan ƙabilar uwa abin ya bama kowa mamaki. Dan kamar waɗanda aka shayar guba kawai aka samesu duk a mace su kusan goma sha uku. Dama wasu sun ɗan mummutu ɗaɗɗaya. A yanzu dai kam Uwa kawai ta rage a raye. Itama ɗin dai sai a hankali dan duk ta ƙara wani irin yamushewa na tashin hankalin faɗuwa ƙasa da tai. Wai yau itace mai zaman kurkuku a cikin masarautar ruman kuma da ranta da lafiyarta tsahon watanni shida. Ai ko'a iya haka aka tsaya ta gama kunyata a wannan duniya. Jasrah ce ta mata wanka tana kuka abin tausayi ita da yayarsu Badiha. Bayan an mata sutura aka fiddota Tajwar Eshaan ya jagoranci sallatarta tare da miƙata gidanta na gaskiya aka barta da halinta kuma. Dan ya rage ita da UBANGIJINTA. A yanzu kam. Wannan itace ranar da ya kama kowa ya kasance yana gudu a rayuwarsa. Dan ko kaƙi ko kaso sai tazo. Ko kai mutumin kirki ne kona banza ne ma dai sai tazo. Ko shekara dubu bisa dubu zakayi a duniyar sai tazo. Koka shirya ko baka shirya ba sai tazo. Yau dai gashi Malikat Bushirat ta tafi tafiya ta har abada. An shafeta an shafe babinta dama iyakarta kenan akan duk wani abin kirki ko ɓarna da zaka shuka a duniyar.... Tajwar Eshaan bai samu hawayen dake riƙe da maƙoshinsa sun zubo ba sai da yaje ya rungumi ƴaƴansa da matarsa sannan. Kuka yayi sosai Iffah na tayasa. Sai da sukayi mai isarsu abin tausayi. Ranar ma har zazzaɓi yayi dole Iffah ta kwana tare da shi da ƴan yaransu da sukaci sunan Ajwaad da Ajwaa (Dan su bawani al'adar suna a sati ɗaya suke ba ba irin ƴan 9ja bane😝). An dai yankama yara raguna da shanu akai sadaka a washe gari tunda ranar mutuwar Malikat Bushirat ta hana. Gida kam ya cika maƙil, ƴan gaisuwa da taya murnar haihuwa ta ko ina ketowa suke. Su Mamy (Daneen Ammarah) sun zo suka kwana itama da cikinta ɗan watanni biyar da wasu kwanaki. Da alama dai zancen Babiy ya tabbata. Ita da Ummu idan ka gansu abin sha'awa kamar yaya da ƙanwa. Sai ma shirye-shiryen bikin Hanash da sukeyi dan shikam ya koma ɗan ɗakin Mamy, Iffah dai na nan ƴar gaban goshin Ummun ta kuma autarta. Dan duk ƙurarta idan ta yaya Ummu dai, itace abokiyar shawararta itace abokiyar sirrinta. Sai an gama Mammy kanji da Babiy. Iyakarsu dariya idan na dariyane. Idan na fatan alkaicine kuma suyi addu'a. Iyyani da kaka kuwa ai dama tuni sun dawo cikin masarautar. Ko yaushe zaka sami Iyyani tare da Malikat Haseenat ne da ƙanwarta Yamma. Tsaffin sun matuƙar haɗe kansu sun zama iyayen kowa. Hakama Kaka da su Sayeed Fayzul-haq sun zama aminan juna dattijan ƙwarai kuma a masarautar kuma iyayen kowa har shi kansa Shahan-shan ɗin.... *_BAYAN WATTANI UKU DA HAIHUWAR IFFAH DA MUTUWAR MALIKAT BUSHIRAT (BIKIN AL'ADA)_* Kamar kowacce shekara a wannan karon ma tarin al'ummar ƙasar ruman da kewaye sun cika birnin Dahab da akafi sani da DAULAR RUMAN tako ina domin gudanar da bikin wasan al'ada. Kowa ka kalla a wannan karon yasan wasan na musamman ne sannan ana gudanar da shine cikin tsafta da nutsuwa. Duk wani wasan ganganci da za'a iya rasa rayuka an kafa masa doka, hakama matakan tsaro tako ina an baza domin kare kowa da kowa. Duk wani boka ko ɗan bori ko malamin tsubbun an hanasu yin kowane motsi a yanzu. Dama yanzu kam dokane, in har aka kamaka to hukuncin kisa kawai ake yanke maka. A yau kam Iffah taga mutane da yawa da suka kawoma Shahan-shan gaisuwa. Ciki harda Sir Fawzan da tuni yay aurensa. Tare da yaran Shahan-shan su Azaan da a yau kam sukaita faman sinne kai na kunyar abinda ya faru tsakaninsu da ita a shekarun baya. Ita dai murmushi ma ta dingayi, shi kansa uban gayyar Shahan-shan murmushin yaƙe yi dan kawai ba'a ganin fuskarsa ne. Su Ajwaa da Ajwaad sunsha addu'oi yau a wajen mutane. Duk da ma bawai kowa ake bamasu ba. Yaran sunyi ɓul-ɓul abinsu gwanin sha'awa. To mi yafi ransu suna samun kulawa da tattali da soyayyar iyayensu. Dan zuwa yanzu ma dai kam Iffah ta tattara inata-inata ta koma sashen Shahan-shan ɗin gaba ɗaya ita da yaranta. Dan yace shikam babu wani sashen matarsa da ban nasa daban. Idan ka ganta a sashenta sai in tayi baƙine ko yin wani abun dai tunda babu mai hurumin zuwa sashen Shahan-shan ɗin sai ita. Hatta da amintaccensa ma zuwa yanzu iyakarsa hawa na na uku ne kawai, idan ka gansa a hawan ƙarshen sai ƙwaƙwƙwaran dalili..... ★Alƙawarin ALLAH ya cika akan zartar da hukuncin su Miran Jasim da Miran Arshaan a yau. Dan kuwa wanda ya kashe dole ne a kasheshi. Hatta da malikat Bushirat Tajwar Eshaan ya gama yanke hukunci a yau ɗin zai zartar da hukunci a kanta irin hakan sai ALLAH kuma ya ɗauki ranta kafin zuwan yau ɗin. Sosai al'amarin ya girgiza kowa matuƙa, musamman ganin iyalan Miran Jasim ƙalilan ne a cikinsu suka koka saboda wahalar daya basu a rayuwa. Shi dama Arshaan ba'a ajiye kowa ba. Amma duk da haka Jasrah mai karyayyar zuciya sai da tai kuka. Al'ummar ƙasa sun taru wajen nema musu afuwar ƙarƙashin cigaba da zama a cikin kurkuku tsahon rayuwa. Hakan yasa duk sai jikin Tajwar Eshaan ɗin yay sanyi, dan shima yanajin ɗaci fiye da irin ɗacin da kowa ke ji kasancewar su kaɗai ne Uncle's nasa makusanta da mahaifinsa da suka rage a duniya sai mata. Ganin dai jama'a sun dage ɗin kuma harda iyalan Sayeed Khairul-Bashar da kansu dana Sayeed Hifzur-rahaman ɗin suma yasa aka maidasu cikin kurkukun a bisa sassaucin ɗaurin rai da rai. To saima dai ta ALLAH dan shi Miran Jasim ma bawani cikakkiyar lafiya ce da shi ba. Hatta Miran Arshaan ɗin kansa kawai dai a rufe rufau ne. Uwa kam da aka fiddo cikin sarƙa cike da ƙarfin iko kowa ke shelanta a kasheta!! A kasheta!!! A kasheta!!!. Kallonsu kawai take tana kuka da dariya da kiran sunayen gumakansu duk a lokaci ɗaya. A haka aka ɗaureta jikin ƙarfen. Mutane zasu fara jifanta da dutsina aka dakatar da su. Dan wannan aikin ba nasu bane na mai gayya da aikine da kansa tare da matarsa. Bayan lafawar kowa fiye da yanda ake buƙata Shahan-shan ya fito hannunsa na dama riƙe da na Iffah, na haggun rungume da Ajwaa da aka canjama gayu ita da Ajwaad. Da shi kuma ke a hannun Iffah. Masha ALLAH aka shiga ambata, dan a zahirinsa ya fito ga mutanensa babu wani shamaki yana son su gansa ya gansu. Haka itama Iffah duk jikinta a rufe amma fuskarta a bayyane ga al'ummar ƙasarta. Bayan sunyi gaisuwa ga al'ummar ƙasar su da fatan alkairi aka kawo kwari da baka na tsire Uwa da zasuyi. Iyyanni da Malikat Haseenat ne da ke tare da su suka amshi twins, yayinda Tajwar Eshaan ya kamo hanun Iffah a hankali cikin nasa yana kallonta ƙasa-ƙasan nan nashi ya tsayar da ita gabansa. Matsawa yay ya jingina jikinsa a nata tare da kamo duka hannayen nata biyu cikin nashi ya saka mata kwarin tare da ɗaga hannayen nasu a tare ya daidaita su sannan ya daidai mashin da zasuyi amfani da shi cikin bakar saitin manya-manyan idanun nan na uwa da ke kwasar dariya da kuka kamar sabon kamu...........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (95 END) ______________ *_MAAB LUXURY HOME._* _Duniyar kayan Kitchen da decoration din gida na keta raini. Ina uwar gida da Amarya, Ku ziyarci shagon mu dake No 22 Ahmadu Bello Way, Kano state. Ko kuyi order daga shafin mu na Instagram @maabluxuryhome. Ko Facebook @maabluxuryhome. Ko Ku nememu a lambar waya *08034631010*_. __________________ ..........Wata irin mahaukaciyar razananniyar ƙara ta saki lokacin da kibiyar mashin ke sauka a cikin idonta ɗaya. Kafin ta gama dawowa cikin hayyacin azabar data shigeta suka sake soke ɗayan ma. Tuni jikinta ya shiga matsanancin karkarwa ta cigaba da ihun ambaton gumakansu. Na uku kama sai da suka saita maƙogwaronta sannan suka sakeshi. Kakari ta shigayi irin na mai fitar rai. Yayinda al'umma ke ta faman kabbara. Gaba ɗaya Iffah ta juya ta rungume Shahan-shan tsam-tsam ta fashe da kuka. Hannu biyu ya amshi abarsa ya rungume ko tuna ɗunbin mutanen dake a zagaye da su ma bayayi. Ai tuni jami'an tsaro da Ghazi dake zagaye dasu suka musu zobe, yayinda ƙatuwar umbrella ta musu runfa daga sama. Ganin wannan damar ta samu Shahan-shan ya ɗago fuskar sohaa ɗinsa ya manne lips ɗin sa a kan nata cike da ɗunbin so da ƙauna. Murmushi mai sanyi da ƙayatarwa kawai Malikat Haseenat tayi ita da Iyyani.... Shike nan kuma an shafe da babin Uwar mushirikai itama. Wanda mutuwarta itama kuma yay dai-dai da haihuwar Daneen Ammarah ta samɓalo ƙyaƙyƙyawar ƴarta mace mai kama da babiy. Ai sai bikin al'ada ya cigaba dana murnar haihuwa, yarinya taci suna Arfah. Zo kaga farin ciki wajen Iffah Nina Arfa ɗin ta ta sake dawowa. Daneen Ammarah kuma ta cika alkawari, dan a ranar a gaban kowa ta damƙa Arfa ga Ummu. Ummu tasha kuka matuƙa Mamy na tayata. Daga ƙarshe ta dawo mata da Arfa akan ta bata shawayarwata har yaye. Babiy da Kaka dai nasu murmushi ne hakama Hanash da shima matarsa ɗauke take da ƙaramin cikin itama dan tanata fama ma da laulayi..... *_BAYAN WASU SHEKARU_* Abubuwa da yawa sun faru, wasu masu daɗi wasu marasa daɗi. Wasu a tuna wasu baza'a ma iya tunawar ba. Haka rayuwa ta gada dama. Zuwa yanzu kam zamu iya cewa hankalin Iffah da Tajwar Eshaan ɗinta ya kwanta sosai, dan manyan matsaloli dai sun ɗan ragu musu musamman wanda suka shafi tsafe-tsafe da sauransu. Amma na maƙiya kam har goben-gobe a kwaisu. Dan duk inda bawa yake, komai ƙyautatawarsa ya sani akwai wanda su burinsu kawai cin dunduniyarsa. Ƴar uwa karki damu, kamar yanda Bily bata damuwa. Dammu masoyanmu sun wadatar damu😘. Haka dama rayuwar take dole ka kasance a zagayen abu biyu, (Masoya da maƙiya) idan ka kwantar da hankalinka duka sai su amfanar da kai. Idan har MANZON ALLAH da yafi kowa a halitta, ɗan gatan ALLAH zai fuskanci ƙalubale na maƙiya, masu hassada da kushen abinda yazo da shi daga umarnin UBANGIJI kai waye da bazaka samu kanka da irin waɗan nan mutanen zagaye da kai ba. Kai dai kawai yi abinda zaka iya, kuma ƙyautatama duk wanda ke tare da kai maƙiyi ko masoyi duk zakai alfahari da hakan wataran. Wannan shine abinda su Iffah da Tajwar Eshaan suka haƙƙaƙewa rayuwarsu da zukatansu suka zauna lafiya. Sun ajiye komai, basa ganin komai sai kansu da masoyansu. Sun fi kallon masoyansu fiye da tuna maƙiyansu, suna shimfiɗa mulki a tare cikin gaskiya da riƙon amana, randa suka sami saɓani kuma sukan binne a tsakaninsu suyi haƙuri dan yau da gobe sai ALLAH. Duk inda zo mu zauna take sai ka samu zomu saɓa. Iffah ta ƙara haihuwar ƴarta mace taci suna *_Bilqeesa_* (Dan bazanyi a banza ba sai na ma kaina takwara a ƙasar ruman ehe🥱😂). Ajwaa da Ajwaad sun girma abinsu masha ALLAH. Yara ƙyawawa da ke samun soyayya ga mutane, wasu ko basu da wanda suka tsana kamar su a yanzu musamman ma Miran Ajwaad da kowa kema kallon magajin mahaifinsa. Sai dai kuma babu abinda suka isa yi dan tun ran gini tun ran zane. Burin Iffah ya cika akan karatu, inda a yanzu haka ta zama cikakkiyar ƴar jarida koma muce shugabar gidan jaridar nan na *African eye* da mijinta ya kafa. A zahirance dai kamar yanda yake ɓoye kansa a baya itama haka take ɓoye kanta a yanzu. Sai dai rubuce-rubucenta da zaƙule-zaƙulen sirrikan munafukai na matuƙar tada hankalin wasu. Dan a duk lokacin da tai wani rubutu game da wata ɓarnar da akeyi koma ta fitar da muryar wasu da abin ya shafa kusan duniya ɗauka take aita cecekuce musamman da ya kasance bayan kafofin yaɗa labarai a yanzu social media ma na taka rawar gani akan yaɗa abu cikin sauri. Sai ta gama zaƙulowa da tallace mutum mijinta kuma gwarzonta ya zama gaba-gaba wajen hukunta mai laifin idan a ƙasar sa ne. Idan ba ƙasarsa bane zai yi duk yanda zai yi ga shugaban da ke shugabanta ƙasar da mai laifin ya fito dan ganin an hukuntashi, cikin ƙananan lokaci sunan da take amfani da shi yay wata irin amsa kuwa, mutane har zalamar jiran fitar wani abu da ga African eye sukeyi, dan sun san mai amfani ne kuma na gaskiya ne. Takanyi ayyukanta a gida, idan kuma fitar sirri ta kama sukanyi ita da Mijinta harma subar ƙasar batare da wani ya sani ba koda a masarautar ne kuwa. ★★... Ƙoƙarin kamota yake tana zillewa, ya kwaɓe fuska da ɓata rai kamar gaske. Gwalo ta masa da ga inda take tana cigaba da dariyarta mai narkar da shi. A hankali ya furta, “ALLAH Sohaa karki bari na kamaki, kizo nan na yarda zamu raba 50-50”. Kafaɗa ta maƙe masa tana mar-mar da idanu da tura baki gaba. Fuskarta a shagwaɓe ta ce, “Naƙi wayon sai dai na baka 30 na ɗauka 70”. “Tunda na fara jin tsoronki ko?”. Ya faɗa cikin ɗage gira sama. Baki ta ɗan murguɗa masa itama. “To dama ai tun tuni tsorona kake ji”. Murmushi ne ya suɓuce masa, shi baima san yanda zaiyi da tsiwar yarinyar nan ba. Fitinanniyar yarinya ce ta bugawa a jarida, yara uku har yanzu bata san ta girma ba. Hannayensa ya tura cikin aljihunsa wandonsa har yanzu fuskar tasa da murmushi ya nufeta. “Okay shikenan na yarda 30-70 ɗin, sai dai yanzu yarana najin yunwa zo muje a fara cin abinci amma da sharaɗi”. “Nami?”. Ta tambaya tana matsawa da baya-baya. Tana ganin ya kusa isa inda take tai yunƙurin sake zurawa da gudu. Wani ɗan tsalle yayi ya cafkota, bai saurari ɗan ihun da take masa na taɓara ba ya murɗe hannun ya amshe ɗan box ɗin dake cikin hannun nata. Cak ya ɗagata ta shiga watsal-watsal da ƙafa. Dariya ya shigayi ganin yanda take kukan taɓara da faɗin ita sai ya bata abunta. Sai da ya zauna akan kujera ya ɗaurata a kan cinyarsa sannan ya dungure mata kai da faɗin, “K yarinyar nan rigimarki tayi yawa, wai nida abuna”. Da sauri tace, “Nawa dai, dan 30 ne naka a ciki”. “Tun kan kiji sharaɗin nawa ma kin yanke hukunci”. “Ka faɗi sharaɗin mana banga wanda bazan iya ba”. “Okay haka kika ce?”. “Eh”. Ta faɗa cike da ƙarfin gwiwa. Murmushi yayi ya ce, “Okay muje a fara cin abinci mu dawo zamu gani ai”. ★Kamar ko yanda ya faɗa yaransu na zaune a falo zaman jiran fitowarsu. Balqeesa dake tsalle-tsallenta ita kaɗai da gudu ta nufesu, a hankali ya kai duƙe fuskarsa da ƙayataccen murmushi dan a rayuwarsa yana matuƙar ƙaunar yaransa, bai haɗa su da komai ba. Hakan kuma bai hanashi tsayawa akan tarbiyyarsu ba. Mulkin al'umma kuma bai hanashi shaƙuwa da su ba, rungumeta yayi tare da miƙewa da ita a hannunsa duk da kuwa takai shekaru shida a duniya. Cikin ƴar muryarta ta ce, “Abbie ina sonka kai da Ammie”. Idanunsa ya lumshe fuskarsa ɗauke da murmushi ya ce, “Muma muna sonku mai gadon zinari na”. Sosai yarinyar ta ƙanƙamesa tana dariyar jin daɗi. Kallon juna sukai shi da Iffah suna murmushi. Dai-dai nan Ajwaa da Ajwaad suka iso garesu suma. Yara masu nutsuwa da shiru-shiru kamar mahaifinsu. Suma hannu ya miƙa musu alamar suzo garesa. Fuskokinsu ɗauke da murmushi suka rungumesa. Baki Iffah ta zumɓira ita a dole taji haushi. Murmushi yayi itama ya mata alamar tazo. A hankali ta matso jikinsu tana murmushi ya haɗesu gaba ɗaya ya rungume........✍️ *_🥱To nima dai na haɗaku gaba ɗaya na rungume masoyan albarka ababen alfahari. Alkairin ALLAH da rahamarsa da ni'imarsa sukai gareku ku da zuri'armu baki ɗaya._* *ALHAMDULILLAHI🙏* _Ya rabba na gode daka kawoni wannan rana badan iyawata ba ko dabaruna. Ina roƙonka ka yafemin kurakuraina, abinda ya kasance dai-dai a cikin wannan ɗan littafi ya rabbi ka haɗamu a ladan. ALLAH ka amfanar damu amfanin cikinsa, wanda ya kasance mai cutarwa ALLAH ka hanashi tasiri a zukatanmu.🙏_ Bazan gaji da faɗa ba. Rubutun nan nishaɗine. Fadakarwa ce. Wani lokacin ma harda ban haushi. Wasu abubuwan akan saka ne kawai domin ayi nishaɗi. Ina roƙonku yin watsi da duk abinda bamai amfani ba a ciki. _Mungode! Mungode!! Mungode masoyan Zafafa. Alkairin ALLAH ya kai gareku, yanda kuka kasance damu kuma ALLAH ya kasance daku cikin rahama da amincinsa. Yanda kuka somu domin ALLAH kuma ALLAH ya soku haka❤️❤️🙏_ *_Yanda muka fara lafiya muka kammala lafiya ALLAH ya haɗamu ana gaba cikin lafiya da nutsuwar zukata. Wanda duk naima kuskure ko ba daidai ba dan ALLAH ya yafemin a yayin wannan rubutun ajizanci ne banda burin ƙuntata kowa koda da magana ne🙏. Ngd Ngd sosai masoya ƴan DAUƊAR GORA CONVERSATION, ku ɗin na dabanne a cikin daban gareni. Alkairin ALLAH ya kasance daku a duk inda kuke. Ku na dabanne a zuciyar Bilyn Abdull 😘😘Nikam kune Sohaas ɗina TAURARINA⭐._* *Bilyn Abdull ce 😘😘🙏* *_ƙaunarku nake irin trillions ɗin nan🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰😘😍😘😘_* _🙈🙈Yau sunan magena har yanzu banga kun fara kawo kayan Barka ba 😂😂 fa. Bye bye idan na mutu da ga nan kowa ya yafe min🙋🏻‍♀️🙋🏻‍♀️🙋🏻‍♀️😭🙏🏻_ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*