𝑃𝑒𝑟𝑓𝑒𝑐𝑡𝑙𝑦 𝑝𝑒𝑛'𝑠..... ✍💫 🎀 _*🔥🔥SHIRYAYYIYAR ƘADDARA 🔥🔥💫*_ _*Season one*_ _*FREE*_❤️🔥 𝑄𝑢𝑒𝑒𝑛 𝐾𝑎𝑖𝑛𝑒𝑟𝑡..... ✍💫 𝑇ℎ𝑒 𝑤𝑟𝑖𝑡𝑒𝑟 𝑜𝑓 𝐷𝑜𝑐𝑡𝑜𝑟 𝑆ℎ𝑎𝑧𝑖𝑚 𝑎𝑛𝑑 𝑛𝑜𝑤 𝑠ℎ𝑖𝑟𝑦𝑎𝑦𝑦𝑎𝑟 𝑘𝑎𝑑𝑑𝑎𝑟𝑎 _*Episode 1_2*_ _*Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah ma ɗaukakin sarki mai kowa mai komi da ya bani ikwan rubuta wannan littafi.*_ _*Ya ubangiji al'arshe kabani ikwan rubuta abin da zai amfani muslinci da muslmai, ka bani ikwan rubuta abun da zai amfaneni duniya da lahira 🙏*_ ❌❌❌❌❌❌❌ _*Ban amince wani ko wata ya yi amfani da wani sashe na littafin nan ba ta kowace hanya ba tare da an nemi izni a wurina ba.*_ _*idan kunne ya ji jiki ya tsira, ko da Allah na bar mutun zai bi min haƙƙina!*_ _*Wannan labari ƙagegen ne ,sannan ban rubuta shi ba da niyyar muzanta wani ko cin zarafin wani ba, duk wanda ya ga wani abu yayi shige da halayyar shi to arashi ne ba da nufi ba*_. *A big big hug to Khadija Sabi'u yahaya A.k.a Nainarh kd Nkds* *special thanks to Ameenatu Muhammad Yakasai A.k.a oum Yasmeen the writer of Binta ƴar jagaliya* _*Dedicated to my family*_ *@Kainaat1733* *Wattpad* _بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ_ 1:30 am *Sydney,Australia* *Bound by fate,freed by love, A romantic Odyssey*❤💘💘 ______________________________ Can cikin bacci taji ana nocking window ɗakin da su ke,a hankali ta buɗe idanuwanta da su kayi mata nauyi. sake nocking ɗin window a kayi, gabanta ne ya ɗan faɗi dan duk a tunanin ta a mafarki ne taji nocking ɗin ba gaske ba. jin an dage da nocking ɗin ne yasa tayi saurin kallon gefanta, baccin shi yake shara abun shi hankali kwance, magidanci ne da a ƙalla zai kai kimanin shekaru 60 a duniya,baƙi ne kyakyawan gaske matar dake gefan shi itama zata kai kima nin shekaru 46 zuwa da 8 a duniya. fara ce kyakyawa ajin farko, kai tsaye idan ka kalleta ba zaka ce zata kai kimanin wannan shekarun ba. ɗan bubbuga pillow da yake kwance ta shiga yi tana kiran sunan shi cikin muryar raɗa “ranka ya daɗe! ranka ya daɗe!!” a ƙalla sai da ta kira sunan shi kusan sau uku ba tare da ya farka ba still ba'a fasa nocking ɗin da ake yi ba. ƙara sautin kiran sunan shi tayi cikin harshen hausa take faɗin“dan Allah ka tashi, inajin fa babu lafiya yau a ɗakin nan” ko gezau baiyi ba gashi wanda yake nocking yanzu ƙoƙarin buɗe window yake ta ƙarfin tsiya ya shigo. cikin muryar kuka ta fara haɗa shi da Allah akan ya tashi “dan Allah yallaɓai ka tashi , babu lafiya” can cikin baccin shi yaji shashekar kukan ta, firgigit ya faraka, jin dai da gaske kukan take ne yasa shi tashi da sauri yana faɗin“lafiya mi yasa ki ku ka??” window ta nuna mashi cikin yin ƙasa da murya tace“wani ke ƙoƙarin shigowa ta window” duban shi ya kai ga sliding door dake ɗakin,wacce mutum idan yaje gabanta ko ya buɗe zai iya hangen cikin garin sydney da harabar hotel ɗin. zuro ƙafar shi yayi daga kan bed ɗin ya sauko wurin window ya nufa, ɗan saurarawa yayi,bugun windowa yaji anyi da ƙarfin gaske can yaji sautin kukan mace cikin harshen turanci tana faɗin“please open the door, help please!” ɗan ja da baya yayi yana mamakin wacece kuma mi ya kawo ta window ɗakin su duk yawan ɗakunan dake cikin hotel ɗin tarasa in da zata zo sai na su, banda zare ido babu abunda matar dake zaune kan bed take. ƙara ƙarfin kukan tayi da dukan window tana cigaba da faɗin“please help me,open the door please” shahada kawai yayi ya nufi window, hannu yasa ya yaye curtain ɗin dake jikin window,matashiyar baturiya ce ya gani tsaye da uban ciki haihuwa yanzu ko anjima,da ƴar madaidaiciyar jaka rataye a kafaɗar ta, a ƙalla zata kai kima nin shekaru 25 a duniya. fuskar ta sharkaf da hawaye idanunta sunyi jawur hakama hancinta da kumatunta, kyakyawa ce ajin farko tana da manyan idanuwa da tsayayyen hanci har baka sai ɗan ƙaramin baki mai ɗauke da red lips tana da tsayi dai dai misali. baƙar duguwar riga ce a jikinta, har ƙasa rigar ta kai mata, ta rufe kanta da mayafin rigar. ganin yayi shiru ya zuba mata idano ne yasa ta sake fashewa da wani kukan tana sake roƙon shi da ya taimake ta. tasowa matar dake zaune kan bed tayi ta nufo bakin window, kallon baturiyar dake tsaye tayi daga sama har ƙasa. “yallaɓai mu taimake ta” ta faɗa tana kallon mijin nata dake tsaye. hannu yasa ya buɗe door, kamar jira take ya buɗe da mugun sauri ta shigo cikin ɗakin kamar zata faɗin,sakin jakar dake rataye a kafaɗar ta tayi, da sauri matar ta taro ta tana faɗin ki kula cikin harshen turanci. kamata tayi har zuwa cikin ɗakin, jakar data yarda mutumin ya ɗauka yana bin bayan su,sofa da ke ɗakin su ka nufa, zaunar da ita tayi, a gefanta ya ajiye mata jakar, nufar wani ɗan table dake ɗauke da robar ruwa da cup matar tayi, ɗaukowa tayi ta dawo wurin sofar. tsiyaya mata ruwan tayi a cup ta miƙa mata, hannunta har rawa yake wurin amsar cup ɗin, kallon mijinta dake tsaye matar tayi wani irin tausayin baturiya ne ya kamasu daga gani ba ƙaramar wahala tasha ba. da sauri ta dafe ƙaton cikinta tana ɗan rintse ido da fatin “Auch, oh my god” ƙoƙarin miƙewa take saboda wani ciwan mara daya taso mata lokaci guda, da sauri matar ta ajiye cup ɗin hannunta sannu ta shiga yi mata tana sa hannu ta taro ta. ƙara baturiya ta fasa tana faɗin matar ta kaita toilet,matar kamar zata fashe da ku ka ta kalli mijinta tana faɗin“haihuwa ce za tayi”ɗan zaro ido yayi “ya za muyi kenan?” “nima ban sani ba, da ace a gida muke ina da komai da zamu buƙata” “haka ne, yanzu babu wani taimako da za ki iya yi mata?” “akwai sai dai su kasan basa son haihuwa a gida sai a hospital” “yanzu tana a wannan halin ina ruwanta da inda zata haihu, tunda dai Allah yasa ke dr ce kawai kiyi mata abun da ya dace” “shikenan”matar ta faɗa,barin wurin mijin matar yayi ya koma can nesa da su sosai. tai makon gaggawa matar ta shiga bata, banda kuka da kiran sunan mahaifiyar ta babu abun da baturiyar nan ke yi. sannu matar ke mata tana bata haƙuri, ba ƙaramar azaba baturiyar ke sha ba matar na iya bakin ƙoƙarin ta ganin ta taimake ta. mijinta ma dake can nesa da su adu'a yake tayi Allah ya sauƙeta lafiya. wahala sosai take sha gashi har yanzu haihuwar sai a hankali, barin wurinta matar tayi ta nufi mijinta fuskarta duk tayi jagajaga da hawaye “yallaɓai ina tunanin dole fa sai mun kaita hospital” “saboda mi?” “nayi iya yanda zanyi amma haihuwar sai tazo sai ta koma” “dr yanzu ya zamuyi?, kinga nan ba ƙasarmu bace fita da ita daga cikin hotel ɗin nan haɗari ne, gashi daga gani yana yin data shigo wani ne ya biyota, kuma na san wanda ke binta duk in da yake yana nan cikin hotel ɗin” “to yanzu ya za'ayi kenan?” “shine nima ban sani ba” “ko zaka nemi alfarma wurin dr mark sai yazo da nurses su dubata” “anya dr kina ganin barin wani ya san halin da ake ciki ba zai jaza matsala ba kinga nan ba ƙasar mu bace kada daga timako mu jefa rayuwar mu cikin haɗari” “to yallaɓai ya ka ke so muyi?” ko rufe baki matar ba tayiba kukan jariri ya cika ɗakin da mugun sauri ta juya ta koma can cikin ɗakin, a durƙushe ta samu baturiyar nan riƙe da jaririya a hannu ga wata sabuwar naƙuda da ta taso mata. da sauri matar ta nufeta tana amsar jaririyar dake hannunta, towel ta ɗauka ta lulluɓe jikin jaririyar ta kwantar da ita saman sofa a hankali,gaban baturiyar ta dawo tana mata sannu haɗi da bata taimakon daya dace,ko minti ɗaya ba'ayi ba ta sake santolo wata jaririyar fara ƙar da ita kyakyawar gaske kamar wacce ta fara haihuwa sai dai wannan bata numfashi kwata kwata babu alamun rai a tattare da ita. da sauri matar ta karɓi yarinyar ta shiga jujjuyata,kusa da ƴar uwarta daketa tsala kuka ta matsa ta kwantar da ita,ɗaukar mai ran tayi ta shiga goge mata jikinta bayan ta gama ta gogema ɗayar jikin itama,baturiyar tana daga in da take durƙushe ta kafe kyawawan yaran nata da kallo fahimtar ɗaya bata numfashi ne yasa ta tashi a hankali ta nufi jariran,shafa fuskar yaran ta shigayi can kuma ta fashe da kuka tana tambayar matar bata da rai ne. jinjina mata kai matar tayi hawaye na bin kumatunta dan ba ƙaramin tausayi baturiyar ta bata ba,kuka sosai baturiyar ta fashe dashi matar na lallashinta har ta samu tayi shiru. ɗaya bayan ɗaya matar ta shiga da yaran toilet ta wanke su a cikin jakar da mahaifiyar tasu data shigo da ita kayan jarirai ne harda su teddys,wasu riga da wando na saƙa farare ta sama yarinyar,gawar kuwa lulluɓeta tayi da farin towel ta kwantar saman sofa kusa da ƴar uwarta,taimaka ma mahaifiyar tasu tayi zuwa toilet danta gyara jikinta,ruwa ta haɗa mata da duk wani abu da zata buƙata tukun ta fice daga toilet ɗin ta bata wuri,cikin ɗakin ta dawo ta gyara wurin kamar wani abu bai faru ba sannan ta nufi wurin jariran,ɗaukar jaririyar daketa faman kuka tayi ta nufi mijinta ta miƙa mashi, hannun biyu yasa ya amshi jaririyar “masha Allah, Allah ya rayata” ya faɗa “Ameen,ƴaƴa biyu ne sai dai ɗayar ba ta zo da rai ba” “Allahu Akbar, Allah ya raya mata wannan ɗin” “Ameen” “mahaifiyar ta su fa?” “Alhmdllh ta haihu,tana toilet ma yanzu haka”ta bashi amsa “masha Allah, amma ya ki ke ganin za muyi da ita duba da yanda ta shigo gashi kuma time ɗin tafiyar mu na ƙurewa?” “yanzu dai mu bari ta fito na sake duba lafiyarta sannan sai mu tambayeta daga ina take” “shikenan ba damuwa” amsar jaririyar tayi daga hannunshi Zama su kayi kan sofar dake kusa da su “yallaɓai yarinyar kyakyawa ce ina ma ace ni na haifeta” murmushi yayi yana kallon fuskar matar ta shi“da kuwa munyi farin cikin da bamu taɓa irin sa a ruyuwar mu ba” “da sai mun tara shagali irin wanda ba'a taɓayi ba a duniya ko da a finafinai da littafi”matar ta faɗa tana sakin murmushi da shafa kumatun jaririyar, shima mijin shafa kumatun yarinyar yayi da fara'a a fuskar shi. “yallaɓai dan ma ba kaga ɗayar ba,kyakyawa ce itama ta ƙarshe da ka ganta kaga ƴar uwarta sai dai tafi kama da mahaifiyar su kamar an tsaga kara” “zan so kuwa na ganta” sun jima a nan zaune suna jiran fitowar mahaifiyar jaririyan daga toilet amma su kaji shiru har lokacin bata fito ba “yallaɓai anya lafiya?, naji shirun nata yayi yawa” “haka ne gashi time na ƙure ma na, ko za kije ki dubata?” tashi matar tayi ta miƙa masa jaririyar da tayi shiru tayi lamo a hannunta. tun kafin ta ƙarasa bakin ƙofar toilet ɗin gabanta yayi wani mugun faɗi, fara fahimtar a kwai abun da ke shirin faruwa ko ma ya faru tayi, ba ta sake tabbatar da hakan ba sai da taga babu gawar jaririyar data bari,da ƙarfi ta ƙwala ma mijinta kira “yallaɓai!yallaɓai!!” ta kira sunan shi har sau biyu, a hanzarce ya iso in da take , sofa ta nuna mashi da sauri ya kai dubansa zuwaga sofa amma sai yaga ba komai “mi ya faru ne?” “babu gawar jaririyar” ta faɗa cikin rawar murya tana zare ido “to ina mahaifiyar tasu?” “tana toilet” “to kila ita ta ɗauketa” “anya kuwa?” ta faɗa tana zaro ido “fara dubata ki gani tukun” a hankali tayi nocking ƙofar toilet ɗin shiru taji, sake nocking tayi nan ma shiru taji babu almun mutum,deciding tayi ta tura ƙofar toilet ɗin ta shiga kawai, tura ƙofar tayi ta shiga wayam taga toilet ɗin ba kowa kamar ma ba'ayi amfani da shi ba, gabanta ne yayi wani mummunan faɗuwa da sauri ta fice tana ambaton Innalillahi wa inna ilaihi raji'un. “lafiya?” mijin ya tambaya da alum ruɗu “ba kowa,bata ciki” ta bashi amsa bakinta na rawa “ya salam, to ina ta tafi?” “nima ban sani ba” dube dube su ka shiga yi cikin ɗakin wai ko ta shiga wani wuri har bakin window data shigo mijin matar ya nufa yana leƙa wajen ko ta nan ta fita amma bai ga alamun ta nan ta fita ba, hankali su ne yayi ƙololuwar tashi. “yallaɓai anya matar nan ba aljana bace?” “wane irin aljana ana zaman lafiya” “idan ba aljana ba, taya za ace ta fita bamu sani ba kuma da yarinya a hannunta” “koma dai minene zama nan bai kama mu ba,mu haɗa kayan mu kawai mu tafi Airport dama lokacin tafiyar ya gabato dan hankalina bai kwanta da wannan lamarin ba” mijin ya faɗa yana kwantar da jaririyar dake hannun shi saman sofa sai a sannan ya lura da ƴar guntuwar takarda da wani ɗan madaidaicin teddy bear a jikinshi an rubuta mommy a kan sofa. da sauri ya ɗauki takardar ya duba rubutu ne a jikin takardar cikin harshen turanci, fara karantawa yayi da sauri matar ta nufo shi ganin pepar a hannunshi kusan a tare su ka gama karanta abun da ke cikin takardar, da sauri su ka kalli juna “anya yallaɓai wannan lamarin akwai tsoratar wa, taya uwa za tayi kyauta da ƴarta daga haihuwarta ba tare da ta ko san wanda ta ba” “gaskiya abun akwai ban tsoro sai dai yanzu abun da za'ayi kawai mu tafi Airport ɗin idan ya so ma kirata tunda ga number waya nan ta rubuta” “to shikenan” matar ta faɗa tana cigaba da haɗa masu kayan su cikin ɗan madaidaicin trolly, tana gama haɗa kayan ta ɗauki teddy ta saka cikin bag ɗinta sannan ta ɗauko mayafi mai ɗan girma cikin kayanta ta lulluɓe jaririyar a kafaɗa ta saɓa jaririyar mijinta kuma yaja trollyn su ka fice daga ɗakin.... *Abuja_Nigeria* _*COURT*_ Mutanene ta ko ina a harabar court ɗin ƴan jaridu ne ƴan gidan radio da television , ƴan social media gasu nan birjik a harabar kowa burinshi ace shine na farko wurin ɗaukar rahoton yanda shari'ar zata kaya. mutane dake kai kawo a harabar da wanda suke zaune sai faɗin albarkacin bakin su suke wasu na iƙirarin idan har hukuncin koto baiyi masu yanda suke so ba to babu abun da zai hanasu ɗaukar doka a hannun su sai dai duk abun da zai biyo baya ya biyo. mutanen dake bakin gate security sun hanasu shigowa kansu abun kallon ne wasu galan galan na fetur ne a hannun su yayin da wasu tayoyi ne a hannun su duk yan ɗaukar doka ne a hannu idan court batayi masu adalci ba. Wasu danƙara daƙaran motacine na gidan television suka dunfaro court ɗin tun kafin su ƙaraso police ɗin dake wurin suka shiga kora mutane gefe dan su basu hanya. A ƙalla motocin gidan tv zasu kai guda biyar huɗu baƙaƙe ne ƙirar reng rover yayin da suka sako tv broadcasting van car white color a tsakiyar su da gudun gaske suka nufo court ɗin,ganin irin gudun da suke ne yasa mutane darewa suka basu hanya, tuni security's sun buɗe masu gate suna ƙarasowa ciki suka shige , sai da suka gama dai daita parking tukun suka shiga fitowa kowanen su sanye yake da journalist jacket black color a gaban rigar anyi rubutu da farin paint inda aka rubuta press da mayan haruffa. ba ɓata lokacin suka shiga fito da kayan aikin su cameras ne yan uban su dan duk yan jaridar dake wurin babu masu nagartatun kayan aiki masu tsada kamar na su. cikin ƙanƙanin lokaci suka gama dai daita kayan aikin su bayan sun gama daidaitawa ne aka buɗe back seat na motar dake gaban tv broadcasting van car, wata matashiyar budurwa ce tafito sanye take da pant suit white color tayi roling da black ɗin veil,high hills ne a ƙafarta black color,fara ce kyakyawar gaske wurin cameras ɗin ta nufo cikin takun ƙasaita. Kallo fa ya koma sama gaba ɗaya hankalin mutane ya dawo kan su sai ƙus ƙus ke tashi a wurin. wannan matashiyar budurwar ce ta fara gabatar da shirin nasu cikin harshen hausa amma saboda zaƙin muryar ta kamar bada hausa take magana ba “masu kallon mu barkan mu da sake saduwa acikin shirin mu mai farin jini GANI YA KORI JI, a inda muke kawo maku shari'ar hajiya Asma'u wacce ake zargin dasa hannunta a kisan mijinta wato CP ( commissioner of police ) na wannan jaha ,masu kallon mu idan baku manta ba a wancan lokacin koto ta ɗaga sharia'ar zuwa goma ga wanta febrairun shekarar da muke ciki bisa ga wasu dalilai, a yaune adadin kwanakin da koto ta yanke dan zartar da hukunci suka cika , ku biyo mu dan jin yanda shari'ar zata kaya” tana gama faɗa ma'aikatan suka kashe kemarorin, wani daga cikin ma'aikanta ne yace “good job BALQIS babu wanda zaice ba LAATIFA ba ce” ɗan ya mutse fuska tayi tana faɗin “thanks” tana komawa back seat ɗin motar data fito, jinjina kai kawai yayi,yana sakin murmushi tana shiga cikin motar wayarta dake ringing ta ɗauka picking call ɗin tayi haɗi da kara wayar a kunnenta, muryar mai kiranta ne ya daki dodon kunnan ta “ hello balƙis ya aikin yake tafiya?” ya mutse fuska tayi tana faɗin “wallahi bawani abun duk wahala ne, kuma ni banga amfanin bin wannan shari'ar ba” “haba balqis miye abun wahalar aciki, na kalli live kuma naga kinyi ƙoƙari, ke da yake ba yar jarida bace shiyyasa zaki ce haka” taɓe baki tayi tana faɗin “ni dai wallahi kin haɗani da Aiki Aunty laatifa” “kai balƙis miyasa za kice haka bana jin daɗi kina faɗin haka sai naga kamar na takura maki ne ba da son ranki ki kayi ba” jin abun da laatifa tace yasa balqis cewa “ni baki takura man ba, dan nayi niyya ne yasa na zo” “shikenan sai kin dawo amma dan Allah kar kice ma dady ni na nace kizo please” “zance mashi ni nayi niyya ba ke ki ka sani ba,amma kin tabbata zaki cika man alƙawari na?” “nagode ƙanwata sai kin dawo karki damu” “ok sai na dawo” balƙis ɗin ta faɗa tana rejecting kiran iska ta fesar daga bakinta,wayarta ta shiga shafawa tana kallon wallpaper wayar tana sakin murmushi,sai sakin murmushi take tana aikin shafa wayar, matso da wayar tayi zuwa fuskarta kissing screen ɗin wayar tayi tana faɗin “am eager to see u my hero,i miss u” tana cikin wannan shauƙin taji hayaniya tayi yawa ga kuma jiniyar motocin security Army's da yake glass ɗin motar da take ciki na gaba a buɗe yake,tsaki taja tana faɗin “i hate this sound gaskiya Aunty latifa baki kyauta man ba” ta faɗa tana ɗan jan tsaki, nocking ɗin ƙofar motar taji anyi da sauri ta juya tana kallon mai yin nocking ɗin ranta a haɗe tace “what?” “sorry dama cewa zanyi ki fito ga BARRISTER ZULAIHAT nan ta ƙaraso” ya mutsa fuska tayi tana faɗin ok fitowa tayi daga motar sai wani sa hannu take tana kare fuskanta saboda zafin rana. wasu jibga jibgan motacin sojoji ne ke shigowa cikin court ɗin gaba ɗaya sun cika court ɗin da ƙarar jiniyar su yayin da tsakiyar su wasu expensive bullet proof latest car ne masu nufashi guda biyu fara da baƙa. Anan compound ɗin court ɗin su kayi parking,security Army's ne suka fara fitowa daga cikin motacin su hannuwan su riƙe da manyan bindigu ga wasu soke a ƙugun su. farar motar su ka nufa, wani jibgegen security guard ne ya buɗe back seat ɗin motar. wata kyakyawar baturiyar mata ce ta fito daga back seat ɗin a ƙalla zata kai kimanin shekara 50 a duniya, kyakyawa ce ajin farko ƴar gayu kai tsaye idan ka kalleta ba zaka ce tayi waɗannan shekarun ba a duniya,sanye take da fararen flat pant suit a jikinta ta yafa farin mayafi a kanta,tana da dara daran idanu farare wanda cikin su ya kasacen Ash ne a manne su ke da farin medical glasse,fuskarta ɗauke take da ni'imceccen murmushi. 𝑏𝑎𝑟𝑟𝑖𝑠𝑡𝑒𝑟 𝑧𝑢𝑙𝑎𝑖ℎ𝑎𝑡 𝑘𝑒𝑛𝑎𝑛 𝑓𝑖𝑟𝑠𝑡 𝑤𝑖𝑓𝑒 𝑜𝑓 𝑡ℎ𝑒 𝑓𝑜𝑟𝑚𝑒𝑟 𝑝𝑟𝑒𝑠𝑖𝑑𝑒𝑛𝑡 𝑜𝑓 𝑛𝑖𝑔𝑒𝑟𝑖𝑎,𝑤𝑎𝑐𝑐𝑒 𝑚𝑢𝑡𝑎𝑛𝑒 𝑘𝑒𝑚𝑎 𝑙𝑎𝑘𝑎𝑏𝑖 𝑑𝑎 𝑙𝑎𝑢𝑦𝑎𝑟 𝑎𝑙'𝑢𝑚𝑚𝑎ℎ. daga front seat na motar security guard ce ta fito hannunta riƙe da black coat da white hand bag sai briefcase rataye a ƙafaɗar ta wanda nake kyautata zaton na barrister ne. wani daga cikin security guard ɗin ne ya buɗe back seat ɗin baƙar motar dake bayan wacce barrister zulaihat ta fito,ƴan mata ne guda biyu su ka fito, dukan su baƙar abayace a jikinsu anyi mata aiki da golding stones sai sheƙi da ɗaukar ido su ke, sunyi roling da glenta,fuskar ɗaya sanye take da niƙab,ɗayar kuwa sunglasses ne manne a fuskarta dake ɗauke da fara'a,hannunta riƙe da ƴar madaidaiciyar bag ta company Gucci golding color,tana matuƙar kama da barrister zulaihat kamar an tsaga kara. cikin tafiyar ƙasaita balqis ta ƙaraso wurin su tana sakin murmushi,tana isowa hugging ɗin barrister tayi tana faɗin “good morning mom” raba jikin su barrister tayi fuskarta ɗauke da murmushi tace “morning balqis, yau kece da kanki?” murmushi balqis tayi tana faɗin “ayyuka ne su ka yima Aunty laatifa yawa shine tace nazo nayi attending wannan shari'ar dan bata so tayi missing” “good,laatifa ba dai aiki ba” barrister ta faɗa,ƴan matan nan ne suka ƙaraso wurin su, mai niƙab ɗin ce ta gaishe da balqis yi tayi kamar bata san da ita take ba,saima kyauda kai da tayi tana kallon gefe, yamutse fuska mai kama da barrister tayi tana faɗin “Abun ma yar haka ce ko Aunty balqis” murmushi balqis tayi kamar ba ita ba tana faɗin “miye kuma yumnah shagwaɓa” bubbuga ƙafa wacce aka kira da yumnah ta shiga yi tana turo baki da faɗin “mom kina jin Aunty balqis ko, ba zata daina ce man haka ba” “bana cike da wannan shiritar taki yumnah,balqis nayi ciki” barrister ta faɗa tana yin gaba, bin bayanta yumnah da wannan budurwar dake sanye da niƙab su kayi yummah na cigaba da shagwaɓarta security guard ɗin na biye da su. murmushi kawai balqis tayi tana komawa wurin aikinta. Yan jarida na ta so suyi magana da barrister amma security guard ɗin ta sun ƙi ba su dama,amma saboda ƙwaƙwa irinta ƴan jarida ana ture su amma suna jefoma barrister tambayoyi. A bakin ƙofar office ɗinta security su ka tsaya macen dake ɗuke da jakarta da rigarta ce ka ɗai ta shiga ciki sauran securitys ɗin kuma su ka zagaye office ɗin yanda ko ƙuda bai isa ya gitta ba tare da sun ƙwamushe shi ba. Wani irin haɗaɗen office ne naji da faɗa, yasha expensive desk da leather chair's masu shegen kyau ,barrister zulaihat kujerarta ta nufa ta zauna,akan desk ɗinta securityn ta ajiye mata hand bag ɗinta sannan ta rataya mata coat ɗinta jikin office suit hanger,wasu files ta ciro daga cikin briefcase ɗinta ta shiga dubasu tana ƙarasa haɗa hujjojine kafin lokacin shiga court ɗin yayi. saman sofa dake cikin office ɗin yumnah su ka nufa su ka zauna sai a lokacin ne ɗayar ta yaye niƙab ɗin dake fuskar ta, masha Allah na furta da ganin kyakyawar fuskar matashiyar budurwar wacce a shekaru bazata wuce sha tara ko ashirin ba kusan sa'anni ne da yumnah. damuwace ƙarara akan fuskarta, murmushi yumnah tayi tana faɗin “yanzu dan Allah da ki ka cire wannan abun ba kiji daɗi ba?” kallon yumnah kawai matashiyar tayi ba tare da tace komai ba “zaki fara wannan shirun naki ko, mom kiyi mata magana mana ta saki jiki da ni ko dan taga na damu da ita” yumnah ta faɗa tana wani ɓata fuska, girgiza kai kawai barrister tayi tana cigaba da aikin dake gabanta ba tare da tace ma yumnah komai ba. “mom kema shirun zaki man?” ta faɗa tana turo baki kamar zata fashe da kuka “yumnah wai miyasa ke baki san lokacin da mutum ke son magana da lokacin da bai so ba, baki san halin da take ciki bane zaki dameta?” a hankali ta kama kunnenta tana faɗin “sorry mom, zama da damuwa bashi ke maganin matsala ba, that's why nake son ta ɗan saki jikinta” kallon matashiyar tayi tace “sorry NAINARH idan na takura maki, inaso ki saki jiki ne kawai” murmushi wacce aka kira da nainarh ta saki “karki damu baki takura man ba, nagode da kulawar ki a gare ni” martanin murmushi yumnah ta mayar mata tana buɗe hand bag ɗin data shigo da ita, ciro wayarta ƙirar iPhone 14 pro max tayi dialing wata number,waya ta shiga yi cike da shagwaɓa. miƙewa barrister tayi da sauri security ta matso tana harharɗa files ɗin dake kan desk ɗin tana maidawa cikin briefcase, ganin haka ne yasa su yumnah miƙewa da sauri nainarh na maida niƙab ɗinta tana ɗaurawa, kallon su barrister tayi tace “ina zaku?” yumnah tace “mom ba time yayi ba” “eh, ku zauna anan duk yanda shari'ar tayi za kuji” duƙar da kai nainarh tayi alamar ba haka taso ba matsowa barrister tayi ta dafa kafaɗar “sorry nainarh ba dan wani abu yasa nace ku zauna nan ba sai dan tsoron abun da zai biyo baya acikin court, nan sai kin fi samun tsaro” “shikenan mom,amma ba za'a neme ni ba?” nainarh ta faɗa “babu mai neman ki, idan yiwuwar hakan ma ta taso za'a zo a tafi dake ne, fatana dai ki kwantar da hankalin ki” gyaɗa mata kai kawai tayi. Komawa su kayi su ka zauna barrister kuma su ka fice,security tunda su ka ji alamun buɗe ƙofar office ɗin su ka gyara tsayuwar su tana fitowa su ka nufi cikin court ɗin har lokacin yan jarida basu daina binta da jefo mata tambayoyi. ciki su ka ƙarasa security guard biyu ne suka shiga cikin court room haɗi da macen sauran su ka tsaya a waje, lokacin da su ka shiga court room ɗin a cike take,duk wani mai ruwa tsaki ya hallara suna zaune a mazaunin su yan jarida sun saita kamarorin su jiran a fara kawai su ke, balqis na daga zaune saman chair daga can baya,Attorney tables da aka tanada domin su ta nufa zama tayi security na ajiye mata briefcase ɗinta daga gefenta su ka tsaya,gaishe da ita attorneys ɗin su ka shigayi tana amsa masu cikin kulawa , mutum biyu ne a cikin su ko kallon in da take ba suyi ba,wata macece da wani namiji,fuskar ko wanen su a haɗe take kamar an aiko masu da saƙon mutuwa, namijin ya jingina da head board ɗin chair ɗin da yake zaune hannunshi riƙe da ƙwallon wasan chess yana wasa da ita saman desk,murmushi saki tana faɗin “good morning BARRISTER HASHIM” sai a time ɗin ya juyo masha Allah na faɗa kyakyawa ne na gaske fatar jikinshi chocolate color ce, kallonta yayi da wasu lumsassun idanuwanshi, kallo ɗaya yayi mata ya ɗauke kai yana faɗin “morning” kamar irin anyi mashi dolen nan,girgiza kai kawai tayi tana buɗe briefcase ɗinta ta fito da files da laptop ɗinta dake ciki...... _*Episode 3_4*_ *Bound by fate,freed by love, A romantic Odyssey*❤💘💘 _________________________ Prison officers ne su ka shigo su biyu sai mata guda biyu ma'aikatan prison sun sako wata mata a tsakiyar su yayinda police maza gudu biyar ke a bayan su kowanen su riƙe yake da bindigar sa,uniform ɗin prison ne a jikin matar inda a gaban rigarta aka rubuta number 106 da farin fenti’ black ɗin hulace a kanta,hannunta a sanye yake da handcuff, kanta a duƙe yake har su ka ƙarasa cikin court ɗin, kusa da brisster zulaihat matar ta zauna yayin da police ɗin su ka tsaya a bayan su. ƙus ƙus ne ya fara tashi a cikin court room ɗin wasu na tausaya ma matar yayin da wasu ke kiranta da munafuka in sha Allah asirinta sai ya tonu. shiru su kayi sun kafe juna da ido kowa na so yayi ma ɗan uwansa magana amma ya kasa daga brisster har mata,ƙwalla ne ya taru idon matar da sauri brisster ta miƙa mata handkerchief tana faɗin “karki kiyi kuka, in sha Allah yau gaskiya za tayi halinta” jinjina mata kai matar tayi tana goge hawayen dake zuba a idonta, brisster ma dauriya kawai take amma itama kukan take son yi kawai ta daure ne dan karta ƙara karyama matar zuciya. A hankali matar tace “ina nainarh?” “suna office ɗina ita da yumnah, na hanata shigowa nan ne dan ban san wani abu ya faru da ita” jinjina kai kawai matar tayi da ka ganta ka san tana cikin matsananciyar damuwa. ɗaya daga cikin prison offices ɗin ne yace “hajiya za mu iya tafiya?” miƙewa matar tayi su ka nufi in da aka tanada domin zaman su,zama tayi matan su ka sata a tsakiya. miƙewa su kayi gaba ɗayan su saboda shigowar alƙali,saida alƙali ya zauna tukun suma suka zauna,bayan koto tayi tsit, miƙewa judicial Assister yayi ya gabatar da ƙara bayan ya kammala ne alƙali ya buƙaci da lawyer masu ƙara ya fito. Cikin ƙwarewar aiki clerk yake typing duk wani abu da ake furtawa a cikin court kama daga sunaye mutane har zuwa yanda shari'ar ke tafiya ga DAR (digital Audio recording ) box a gefenshi tana ɗaukar komai. miƙewa tsaye brisster hashim yayi wasu files dake gabanshi ya ɗauka yana ajiye chess ball ɗin dake hannunshi, fitowa yayi daga inda yake zaune yana wani gyara zaman coat ɗin dake jikinshi,papers ɗin dake hannunshi ya miƙama judicial Assister, juyawa yayi ya miƙama alƙali. “my lord wannan rahoton gawar marigayi ne wanda ƙwararon likitoci su ka gudanar tare da horoton cctv camera dake gidan shi, sai bincike da ƴan sanda su ka gudanar akan shatin hannun hajiya Asma'u da aka samu a jikin bindigar da aka kashe marigayi da duk wasu wayoyi daya amsa kafin faruwar abun,sai sunayen witness” yana gama faɗa ya koma mazauninshi ya zauna yana ɗaukar ball ɗin shi ya cigaba da juyata saman table. miƙewa mom tayi cikin taƙon kamala ta fito tsakiyar court,ɗan rissinar da kai tayi tana kallon alƙali alamar girmamawa, jinjina mata kai alƙalin yayi,takardar dake hannunta ta miƙama judicial Assister tana faɗin "my lord wannan sune jadawalin shedo da nayi ma court alƙawarin kawowa" tashi judicial Assister ɗin yayi ya miƙama alƙali takardar, amsa alƙalin yayi yana ɗaukar glass ɗin shi ya manna a ido, ya ɗan ɗauki tsawan lokaci yana duba duka takardun harda wanda brisster hashim ya bada kafin yace“zaki iya tafiya” godiya tayi mashi tana komawa ta zauna. “idan malam Aisha tana kusa ta matso gaban koto” Alƙali ya faɗa, a hankali matar ta miƙe daga cikin mutanen dake zaune saman chair, jikinta sai rawa yake daga ganin yana yinta bata cikin natsuwarta,ƙarasowa tayi ta tsaya a cikin witness stand, tashi mom tayi ta nufi in da matar ta tsaya. ƴan jarida nan su ka fara ɗaukar komai, tasowa balqis tayi ta dawo inda mutane su ke hannunta riƙe da abun magana,juyawa tayi saitin da attorney su ke karab idanunta su ka haɗu da na brisster hashim wani ɗan iskan kallo ya watsa mata wanda yasa ƴan hanjin cikinta kaɗawa ita kaɗai ta san ma'anar wannan kallon daya watsa mata , da sauri ta duƙar da kai tana juyawa ta bar wurin da sauri, gyaɗa kai yayi yana maida hankalinshi ga Alƙali. Rantsuwa Alƙali ya fara sa Aisha tayi akan zata faɗin gaskiya, kafin ya ɗaura da cewa “court na san sanin cikaken tarihin ki?” kasa magana tayi saboda wani irin rawa da jikinta yake har sai da Alƙali ya sake magana “kina ɓata ma koto lokaci" da ido mom tayi mata alama data kwantar da hankalin ta, magana ta fara cikin rawa rawar murya dake nuna rashin natsuwarta “suna na Aisha Usman shekaruna 42 ni ƴar asalin garin faskari ce dake jahara katsina,nazo Abuja ne ta dalilin wata ƙanwar mahaifiyata itace sanadiyyar fara aikina a gidan marigayi” “malama Aisha tsawan wane lokaci ki ka san marigayi da matar shi hajiya Asma'u?” “tsawan shekara goma sha biyar” “ko zaki iya faɗa ma court yanda zamantakewar gidan take tsakaninki da masu gidan?” “mutanene masu karamci da san al'ummah ko da kuwa ya kasance na ƙasa da su ne, duk tsawan shekarun dana ɗauka tare da su basu taɓa nuna man cewa wai ni ƙasa nake da su ba, hajiya Asma'u ta ɗauke ni tamkar ƙawarta kuma ƴar uwarta,haka marigayi tamkar ƴar uwarshi ta jini haka ya ɗauke ni” ƴan rubuce rubuce Alƙali yayi kafin ya ɗago yana faɗin “ko zaki iya bama court labarin yanda kisan marigayi ya....” tun kafin Alƙali ya ƙarasa magana tayi saurin ƙatse shi jikinta na rawa tace “wallahi ni ban san komai a game da kisan marigayi....” desk Alƙali ya buga yana faɗin “nan court ce, ki san yanda zaki riƙa magana, laifi ne Alƙali na magana ka tari numfashin shi, ki kiyaye” “tuba nake” ta faɗa tunda Alƙali ya fara magana gaban matar nan ke faɗuwa, tama kasa ɗagowa ta kalli Alƙalin ko mutanen dake cikin court ɗin,brisster hashim kuwa da wannan matar tunda Alƙali ya fara gabatar da ƙara ya mida hankalin shi kan Alƙali ko motsin kirki ba yayi ƙwallon chess ɗin dake hannunshi ma ajiyeta yayi. tambayar Alƙali ya sake jefa mata, kawai sai gani a kayi tafashe da kuka abun yayi matuƙar ɗaurema brisster kai hajiya Asma'u kuwa jikinta sanyi yayi zuciyarta ta karaya, ta san da wahala ta ƙubuta, Aisha ka ɗaice shedar da take ganin zata iya taimakawa wajen faɗar gaskiya. wicked side smile brisster hashim ya saki, yana kallon macen dake kusa da shi su ka kashe ma juna ido, da yawan brisster's ɗin dake wurin sun jin daɗin yanda abun ke tafiya ƙalilan ne abun ya taɓa zuciyar su. sai da ta gama kukan mai isarta tukun Alƙali yace“koto na saurarenki” “wallahi ni ban san komai ba, hasalima bana garin abun ya far.....” da sauri brisster zulaihat ta tari numfashin matar tana faɗin “my lord!, shaidata ta shiga halin ruɗani, tana tsoron magana a gaban court sabo....” da sauri matar tace “babu ruɗanin da na shiga, kuma ba wai ina jin tsoro ba ne , gaskiya ce nake faɗa, bana nan abun ya faru” matar ta faɗa with full confidence,mamaki kamar ya kashe mom, saboda Aisha tana Abuja komai ya faru amma a gaban koto tace bata nan, brisster hashim har ƙara gyara zama yake abun yana tafiya yanda yake so. “laifi ne katse shaida yayin bada amsar da Alƙali ya tambaye shi, brisster ki kiye” “tuba nake” ta faɗa “ina ki ka je a lokacin da abun ya faru?” Alƙali ya jefa mata tambaya “naje garin mu domin duba jikin ɗana da ke fama da ciwan daji ( cancer ), kuma hajiya Asma'u da kanta ta bani izinin tafiya ita da mijinta” “ A ranar yaushe ki kayi tafiyar?” “na tafi garin mu ranar laraba a washe garin ranar Alhamis nake samun labarin abun da ya faru” “mi yasa baki dawo ba da ki ka samun labarin abun da ya faru da ubangidan na ki?” “saboda lalurar ɗana, jikinshi ne yayi tsanani shiyyasa ban samu damar zuwa ba” ƴan rubuce rubuce Alƙali yayi kafin yace “zaki iya komawa ki zauna, kotu za tayi bincike akan bayanan da ki ka bata, lawyer masu ƙara ko kana da tambayoyin da za kayi ma malam Aisha” miƙewa brisster hashim yayi yana gyara zaman coat ɗin shi, cikin takun ƙasaita ya nufi tsakiyar koton, cikin maganar ƙasaita yake faɗin “my lord, ina so zanyi ma shaida wasu ƴan tambayoyi” izini Alƙali ya bashi “godiya nake” ya faɗa yana matsawa in da Aisha take tsaye “malam Aisha ina so zanyi maki wasu ƴan tambayoyi,ya zamantakewar iyayen gidan naki take, shin kafin mutuwar cp ko a kwai wani saɓani da ya taɓa shiga tsakaninshi da uwar ɗakin ki, ko akwai rashin jituwa tsakaninsu, wasu dai Abubuwa maka mantan haka???” “babu yallaɓai,a kwai fahimta a tsakaninsu, marigayi yana matuƙar kyautata ma matar shi hatta mu ƴan aiki ya ɗauke mu da matuƙar daraja” jinjina kai brisster hashim yayi yana faɗin “ita fa uwar ɗakin taki, ya nata halayen su ke, bata da wasu ɗabiu marasa kyau wanda baku jin daɗin su???” ran brisster zulaihat ne ya fara ɓaci da irin tambayoyin da brisster hashim kema Aisha “gaskiya babu” “koda a ɓoye bata da su?” ya sake mata tambayar, miƙewa brisster zulaihat tayi rai a ɓace “objection my lord” “sustained”Alƙali ya faɗa yana bata izini “lawyer masu ƙara kamar yana son tursasa witness ɗina akan dole sai ta faɗi abun da bashi ba” “brisster hashim ka kiyaye” jinjina kai brisster hashim yayi “malam Aisha a ra'ayin ki ne ki ka tafi gida ko kuwa uwar ɗakin kice ta nuna dacewar tafiyar ki a wannan lokacin?” “Itace tace ya kamata na tafi na duba jikin shi , da tace man haka sai nace mata zan shirya ranar juma'a ko asabar naje amma sai tace na shirya gobe na tafi da farko naƙi amincewa da tafiyar a washe garin nace kawai zan tura masu kuɗin su fara amfani dashi kafin zuwa ranar juma'ar na tafi, amma sai ta zaunar dani ta nuna man dacewar na tafi a goben shine na amince” “da tace ki tafi a lokacin ba kiyi wani tunani ba ko akwai dalilin da yasa tace kije?” Miƙewa brisster tayi tana ɗan dukan table ɗin dake gabanta “objection my lord” “Overruled”Alƙali ya faɗa komawa tayi ta zauna tana cizon yatsa na rashin bata dama da Alƙali yayi, side smile brisster hashim ya saki amsar tambayar da brisster hashim yayi mata ta bashi “banyi tunanin komai ba, saboda idan ahalina suna cikin matsala ta kan fini shiga damuwa akan halin da nake ciki,shiyyasa banyi zargin komai ba” jinjina kai brisster yayi “mudi mai gadi ya sanar da koto cewa akwai wani matashin saurayi dake yawan zuwa wurin uwar ɗakin na ki, baki taɓa tunanin mike kawoshi wajenta ba , ko miye alaƙarta da shi ???" “sunan sa Abid, ɗan ƙanwarta ne dake zaune a ƙasar waje, yana yawan zuwa wurinta duk lokacin da yazo suna samu saɓani da marigayi saboda kwata kwata jinin marigayi bai haɗu dana Abid ba, saboda Abid yaro ne mara tarbiya baya girmama na gaba da shi , gashi duk lokacin da yazo sai ya takura ma yarinyar su , hakan yasa marigayi baya son yana zuwa gidan, ita hajiya sai ta nuna ba taji daɗi ba kan nuna kyara da tsangwama da yake akan yaron, a ranar da mu kayi magana kan tafiyata ya zo gidan har saɓani ya shiga tsakanin shi da marigayi ya dake shi, abun yayi matuƙar ɓata ran hajiya har su ka samu saɓani da marigayi, bayan mungama magana da ita naje ɗakina na wanke kayan da zan tafi da su na zagaya baya zanyi shanya na hangesu ita da Abid suna tattauna wasu maganganu wanda ban san mi su ke tattaunawa ba, nayi ƙoƙarin naji abun da su ke faɗa amma abun ya gagara saboda tazara dake tsakanin mu,bayan na koma ɗakina cikin dare naji Abid ɗin yana waya a bayan ɗakina kamar yana faɗama wanda suke waya saɓanin da su ka samu da marigayi bana jin mi na ciki wayar ke faɗa masa na dai ji yana faɗin a cikin satinnan ya kamata suyi aiki a kanshi ko zai daina mashi shiga hanci da ƙudindine, na tsorata da jin abun daya faɗa har na kasa bacci , washe gari tunda safe na samu hajiya da maganar amma sai ta nuna kar na damu da abokan kasuwancin shi yake waya” tunda Aisha ta fara jera wannan jawabin gaban hajiya Asma'u ke faɗuwa bata taɓa sanin komai dake faruwa a gidan Aisha na sane ba sai yanzu. “abokan ka suwanci, ko kin san wane irin ka suwanci yake?, sannan wane saɓani ya shiga tsakanin shi da marigayi?” “gaskiya ban san kasuwanci da yake ba, amma na taɓa jin labari a wurin mai gadi cewa yaron yana harkar kayan maye , kuma dukiyar da yake juyawa ta hajiya Asma'un ce ” jinjina kai brisster yayi “wane saɓani ne ya shiga tsakanin shi da marigayi?” ya sake maimaita mata tambayar “gaskiya ban sani ba” juyawa brisster hashim yayi ya kalli Alƙali “my lord , tun ranar da mai gadin gidan ya ba police duk wasu bayanai akan yaro suka tsaurara bincike sai dai kash bayan kwana biyu da fara binciken na su aka samu gawar shi yaron a cikin gidan shi anyi mashi kisa makamancin na marigayi,hakan na nufin hajiya Asma'u ta tura Aisha gida ne dan ta samu damar aiwatar da shirinta ba tare da wani ya ganota ba,sannan ta sallami ma'aikatan gidan dan kar su ga abunda zai faru,Abid ya ƙi bata haɗin kai ne shiyyasa ta tura makasan da su ka kashe cp su ka kashe shi dan kar ya zame mata matsala” “Objection my lord” jinjina mata kai Alƙali yayi alamar amincewa “my lord lawyer masu ƙara na son tabbatar da laifi akan wacce nake karewa ba tare da ƙwararan hujjoji ba” “brisster hashim ka kiyaye” “tuba nake” jinjina kai Alƙali yayi kafin ya ɗauki pen ɗin shi yayi ƴan rubuce rubuce “lawyer masu ƙara ko kana da sauran wasu tambayoyi da za kayi ma malam Aisha” “su kenan tambayoyin da nake son yi mata” brisster hashim ya faɗa, tsaki brisster taja a zuciyarta tana faɗin “ko ina amfanin wannan tambayoyin” “lauyan wanda ake ƙara ko kina da wasu tambayoyi da za kiyi ma malam Aisha?” miƙewa brisster tayi “eh my lord” dama Alƙali ya bata, fitowa tayi brisster hashim kuma ya koma mazauninshi. “malam Aisha a bayanan da hajiya Asma'u ta bada da kuma binciken da muka gudanar ya tabbatar mana da cewa kina a gidan a ranar da abun ya faru , hasalima kece ki ka fara sanar da su zuwa mugayen mutanen da su ka shigo gidan” “wallahi brisster bana garin ita da kanta tace naje, munyi maganar da ita yau washe gari tunda safe na tafi” murmushi gefen fuska brisster ta saki tana faɗin “ƴan uwan naki su su ka bada shedar cewa a ranar ba kije garin naku ba sai a washe garin ranar da abun ya faru” shiru Aisha tayi ba tare da tace komai ba “malama Aisha ke koto ke saurare?” “ranar na tafi sai dai ban samu isa garin ba sai cikin dare,hakan yasa basu san da zuwa na ba sai washe gari”jinjina kai brisster tayi tana juyawa ta kalli Alƙali “my lord malama Aisha ta sanar da koto cewa bata nan abun ya faru, a binciken dana gudanar ya tabbatar man da tana a cikin komai ya faru” “binciken koto zai tabbatar da hakan, kina da sauran wasu tambayoyi da za kiyi mata” “babu sauran wasu tambayoyi da zanyi mata” “malam Aisha zaki iya komawa mazauninki kafin binciken koto ya kammala” “godiya nake” ta faɗa tana ɗan rissinar da kai,barin witness stand ɗin tayi ta koma mazauninta ba tare da ta bari sun haɗa ido da brisster ba ko hajiya Asma'u. brisster wurin zamanta ta koma itama,haka shari'ar ta cigaba da tafiya duk wasu jadawalin sunayen witness ( sheda) sai da Alƙali ya kira su gaban koto yana masu tambayoyi bayan ya kammala masu ya ba brisster's dama suma suyi masu nasu tambayoyi, ko wane sheda da kalar amsar da yake ba dawa a kan kisan marigayi CP,hajiya Asma'u tun tana sa ran kuɓuta har ta sadaƙata tasan bazata taɓa kuɓuta ba daga yanayin amsoshin da shedun ke ba court,brisster ma gwiwowinta sun sage bata taɓa shari'a irin wannan ba tana shari'a akan kisa amma kuma bata taɓa rashin nasara ba amma wannan shari'ar na neman tafi ƙarfinta , shedun da take taƙama dasu gaba ɗaya sun juya mata baya,duk wanda aka kira a cikin su abu ɗaya su ke faɗi hajiya Asma'u ta kashe mijinta kuma suna bada ƙwararan hujjoji wanda dole koto ta yarda . brisster hashim kamar ya zuba ruwa a ƙasa yasha yasan zaiyi wuya yau bai yi nasara akan brisster zulaihat ba abun da ya daɗe yana jira kenan tsawan shekaru. Magana Alƙali ya fara, tsit kotun tayi kowa na sauraron hukuncin da court zata yanke “binciken kotu ya tabbar da malam Aisha bata nan a ranar ashirin da ɗaya ga watan biyar” Ajiyar zuciya Aisha ta sauke tana dafe saitin zuciyarta, brisster wani mugun faɗuwa gabanta yayi hajiya Asma'u kuwa tuni hawaye sun taru a cikin idanunta “bayan kammala haɗa duk wasu hujjoji da binciken koto dana likitocin dake kula da gawar marigayi CP ya tabbatar da hajiya Asma'u itce ta kashe CP” tunda Alƙali ya fara magana brisster hashim ke sakin murmushi, brisster zulaihat kuwa banda faɗuwa babu abun da gabanta ke yi. “kotu ta yanke ma hajiya Asma'u hukuncin kisa ta hanyar rataya tare da biyan tara ta naira milayan hamsin” Wani irin murmushin farin ciki barisster Hashim ya saki yana kallon ƴan uwan shi wanda hukuncin yayi masu dai dai,a ɗayan ɓangaren kuwa barisster Zulaihart wani irin tashin hankali mara misaltuwa ta tsinci kanta, da dama mutanen dake Court ɗin abun yayi masu daɗi yayin da wasu ke tausaya ma Hajiya Asma'un. ana cikin jimamin hukuncin da court ɗin ta yanke sai ga saƙo daga fadar shugaban ƙasa na nemama Hajiya Asma'u sassaucin kotu daga rataya zuwa ɗaurin rai da rai tare da biyan tara ta nera miliyan ɗari saɓanin hamshin. Ran barisster hashim idan yayi dubu ya ɓaci ba haka yaso ba yaso hukuncin kisa aka yanke mata ta hanyar rataya bai so ɗaurin rai da rai ba amma idan ya tuna ba wai zata fito bane sai hankalishi ya kwanta, mom ta ɗan ji sassauci da ba kisa bane ɗaurin rai da rai ne sai dai idan ta tuna halin da hajiya Asma'u da nainarh za su shiga hankalinta na tashi. wasu daga cikin mutane kwata kwata ba su so haka ba gani suke kamar wata maƙarƙashiya ce ake ƙullawa. Miƙewa Alƙali yayi gaba ɗaya su ka miƙe,ƙofar office ɗin shi ya nufa kamar jira a ke Alƙali ya fita koto ta ɗauki haya niya kowa da abunda ke fitowa daga bakin shi,can compound ɗin curt ɗin kamar zai fashe saboda haya niyar mutane, mom tunda Alƙali ya fita ta kifa kanta saman desk ko motsin kirki ta kasa yi,matsowa wannan security guard ɗin tayi tana bata haƙuri, miƙewa brisster hashim yayi yana wani gyara zaman rigar shi fuskarshi ɗauke da murmushin mugunta, ɗaya bayan ɗaya mutane su ka fara fita daga cikin kotun suna tofa albarkacin su. hanyar fita prison officers suka nufa da hajiya Asma'u, da ƙyar take taka ƙafafuwanta suna zuwa tsakiyar court ɗin ta yanke jiki ta faɗi a sume, salati mutanen da su ka rage a ciki su ka rabka da sauri mom ta miƙe kusan a tare su ka isa inda hajiya Asma'u ke yashe a ƙasa ita da wasu mata guda biyu, amma kafin su ƙaraso ma'aikatan gidan yarin sunyi mata rumfa mom ka ɗai su ka bari ta ƙarasa in da take, jijjigata ta shiga yi tana kiran sunanta amma ko gezau ba tayi ba, ɗaya daga cikin prison officers ne ya miƙoma mom ruwa,a hannu ta zuba ruwan ta shafa mata a fuska, tayi hakan kusan sau ba adadi amma bata farfaɗo ba mom bata san lokacin da ta fashe da wani matsanancin kuka ba,doctors ɗin gidan yari ɗaya daga cikin jami'an gidan yarin ya kira, ba'ayi five minutes ba sai gasu sun ƙaraso, nurses huɗu mata ne su ka kamata su ka ɗaura saman stretcher,ficewa su kayi da ita daga cikin court ɗin bayan su mom tabi tana goge hawayen dake zarya saman kumatunta, a hanzarce security guard ɗinta tabi bayan ta har zuwa in da su kayi parking Ambulance,ganin fitowar mom ne yasa sauran security guard ɗin nufota da sauri saboda mutane da ƴan jarida da suka fara jefa mata tambayoyi harda na hauka, wasu ma a fakaice magana su ke gaya mata,buɗe Ambulance ɗin ɗaya daga cikin officers ɗin yayi ciki su ka saka hajiya Asma'u,maganganu mutane ke jifa ma mom,tana jinsu amma tayi kamar bata jin mi suke cewa tana nan tsaye har sai da taga ficewar Ambulance ɗin daga cikin court ɗin tukun ta juya da nufin ta koma office ɗinta, juwar da za tayi taga brisster hashim tsaye ya harɗe hannuwa saman chest ɗin shi, wani ɗan iskan murmushi ya sakar mata yana tunkaro in da take tsaye, bashi hanya security guard ɗinta su kayi da alama dai shima ba ƙaramin mutum bane. zuba mashi ido tayi har ya ƙaraso inda take, murmushi ya saki cikin wata irin murya kalar ta ƴan duniya yace “ya dai lawyer Al'ummah?, yau ina goyan bayan Al'ummar taki yake?” ɗauke kai mom tayi wani ƙululun baƙin ciki na tokare mata maƙoshi, dariya brisster hashim ya saki “see u next time” ya faɗa yana kashe mata ido ɗaya, barin wurin mom tayi securitys ɗinta su ka bi bayanta, da kallo brisster hashim ya bita har ta ƙarasa inda su kayi parking motocin su,duk Abun da ke faruwa balqis na tsaye tana kallo,hawaye ne su ka taru a idonta ta rasa dalili rashin jituwar brisster hashim da mom, juyawa tayi ta nufi motocinsu ta shiga barin court ɗin su kayi baki ɗaya. wannan lawyer ce ta nufo brisster hashim dake tsaye “brisster na lura so ka ke baƙin ciki ya kashe brisster zulaihat a yau ” ta faɗa tana sakin murmushi, martanin murmushi ya sakar mata yana faɗin “yanzu ta fara gani in dai ni ne” “Allah ya shirya ka, gaskiya baka kyautawa matar yayan ka ce fa” “na tsaneta bana son ganinta” ya faɗa yana barin wajen, bin bayan shi lawyer tayi. waya brisster ta ɗauka tayi dialing number yumnah bugu ɗaya tayi picking “ku fito ina parking space ku same ni” tana gama faɗa tayi rejecting ba tare da ta tsaya jin mi yumnah za tace. miƙewa yumnah tayi tana kallon nainarh data zuba uban tagumi, girgiza kai tayi tana nufar ta, dafa kafaɗar tayi firgigit nainarh tayi ta miƙe a tsorace har sai da gaban yumnah ya faɗin “yumnah an gama shari'ar ne?” nainarh tajefa mata tambaya “ban sani ba, amma dai mom tace mu sameta waje ban sani ba ko an gam....” tun kafin ta ƙarasa nainarh ta nufi hanyar fita da sauri, bin bayanta yumnah tayi. tana fitowa ƴan jarida su ka yo mata caaa, sai jefa mata tambayoyi su ke marasa kan gado, ruɗewa tayi ta rasa in da zata dosa hawaye har sun fara zuba daga idanuwanta,ganin halin da take ciki ne yasa securitys ɗin nufarta, zagayeta su kayi suna tutture ƴan jaridar, in da mom ke tsaye tana jiran su suka nufa,maganganun mutane ne su ka fara ɗaukar hankalinta da irin kallon da suke binta da shi “itace ɗiyarta ko kunya ba tajiba ta kashe ma yarinya ubanta saboda neman duniya kawai” “ai hukuncin da kotu ta yanke mata bashi ya kamata da ita ba hukuncin kisa ne dai dai da ita” “saboda brisster zulaihat yasa ba'a yanke mata hukuncin kisa ba, kasan suke da ƙasar sai yanda su kayi da talaka” maganganun dake fitowa daga bakin mutane kenan, tunda ta fara sauraronsu gabanta ke faɗuwa. bayan su yumnah ta biyo sai turo baki take kamar zata fashe da kuka,da sauri nainarh ta nufi mom hawaye na fita daga idanunta “mom ina ummah?” shine tambayar data jefa ma brisster, juyawa mom tayi ta shige motar ta ba tare da tace mata komai ba, motar da ke bayan wacce brisster ta shiga security guard ɗin ya buɗe ma nainarh da nufin ta shiga, a masifance ta maida marfin ƙofar ta rufe tana juyawa zata nufi cikin court ɗin, da sauri brisster ta fito tana faɗin “kar ku barta ta wuce” umarnin mom su ka bi, duk yanda nainarh ta so shiga cikin court room ɗin hanata security su kayi ƙarshe data gaji zubewa tayi ƙasa tana fashewa da wani matsanancin kuka,kamata mom tayi ta miƙar da ita tana lallashinta su ka nufi mota, itama daurewa kawai take yumanh da yake saurin kuka ne gareta har ta fara matse ƙwalla abun tausayi, motar da su ka zo ita da nainarh ta shiga nainarh kuma a tare su ka shiga da brisster, kuka take kamar ranta zai fita tun brisster na daurewa har itama ta kaida zubar da ƙwalla, a tamanin security guard ɗin su ka shiga motocin su, da gudun gaske su ka fice daga court ɗin. tun daga farkon shigowa anguwar zaka tabbatar da anguwa ce ta manyan mutane masu faɗa aji a cikin ƙasa,manyan gine gine ne ta ko ina,tun daga nesa ƙarar jiniyar motocin su ka cika anguwar,da wani irin matsiyacin gudu su ka shigo anguwar, miƙe titin su kayi shantal sai da su ka kusa kai ƙarshen shi tukun suka karya kwana,tun daga farkon street ɗin da su ka shigo check point ne na sojoji,kowanen su ƙatuwar bindigace a hannunshi yayin da wasu ke soke a ƙugunansu, tun kafin motocin su ƙaraso sojojin dake zaune bakin ɗan gate ɗin da su ke sawa su ka buɗe masu, suna isowa babu jira suka wuce,tafiyar kusan minti goma sha biyar su kayi a ƙalla sun wuce check point na sojoji da ƴan sanda kusan guda goma kafin su ka kawo bakin wani ƙatafaran gate,ba sojojin dake gadin gate ɗin ba shi kanshi gate ɗin abun kallo ne, wani irin zungureren gate ne ƙaton gaske. ga wasu irin manya manyan sojoji dake gadin shi, kwata kwata babu ɗigon imani a fuskar su,sojojin dake zaune saman bench ne suka miƙe da sauri lokacin da motocin su ka ƙaraso bakin gate ɗin,wani mahaukacin horn akayi da motar dake gaba da sauri wani soja ya danna wani abu dake hannunshi mai kama da remote nan take gate ɗin ya shiga zugewa zuwa gefe ɗaya,da gudun gaske suka danna kan hancin motocin zuwa ciki, masha Allah na furta a yayin da nayi arɓa da ƙaton Castle ɗin da su ka shigo,gidajene a cikin shi na alfarma hagu da dama aƙalla za su kai kimanin guda hamsin kusan a jere suke sai dai akwai tazara mai ɗan yawa a tsakanin ko wane gida, security guard ne ke yawo a cikin Castle ɗin ta ko ina,babu abun da babu a ciki kama daga clinic ne sport center, garden babu abun da babu a ciki, duk wani abu na more rayuwa a kwaishi a cikin estate ɗin. a ƙalla sunyi tafiyar kusan minti biyar kafin su ka kawo bakin wani ƙaton luxury Villa wanda yafi ko wane gida dake cikin estate ɗin girma haɗuwa da tsaruwa, yana yin shi ma da ban yake da gidajen dake ciki shi ba'a jere yake da sauran gidajen ba yana a tsakiyar su yana fuskantar gate ɗin estate ɗin, water falls ne masu matuƙar kyau da ban shawa'a a bakin villa ɗin da a ƙalla ya kai hawa biyar, parking motocin su kayi... _*Episode 5_6*_ *Bound by fate,freed by love, A romantic Odyssey*❤💘💘 ___________________________ A zaune take saman royal sofa mai mazaunin mutum uku dake a katafaren main parlorn dake villa ɗin,faɗa maku tsaruwa da haɗuwar parlorn ɓata lokaci ne,royal sofas ne a cikin shi set uku, komai na cikin parlorn white and golding color ne,wani irin daddaɗan ƙamshi ne ke tashi a cikin parlorn haɗe da sanyi AC,parlorn iya haɗuwa ya haɗu. duguwar rigar lace ce a jikinta ɗinkin bubu,wuyanta yasha adon sarƙar gold hakama hannuwanta da ƴan yatsunta da suka sha ƙunshin jan lalle sunsha zobunan gold masu tsadar gaske, fara ce mata ƴar duma duma ba laifi kyakyawa ce,gashin attachment ne a kanta ya zubo har gadon bayanta,wani daddaɗan ƙamshine ke fita daga jikinta wanda ya haɗe da na fresheners ɗin dake parlorn ya bada wani ni'imtaccen sanyin ƙamshi. tsadaddiyar wayarta ƙirar company Samsung ce kare a kunenta da alama waya take,cikin maganarta ta ƙasaita da isa take faɗin “nayi matuƙar jin daɗin wannan daddaɗan labarin daga gareka” bana iya jin mi na cikin wayar ke faɗa, murmushi ta saki tana cigaba da faɗin “kar ka damu in dai nice zaka samu harda gyara ma, fatana dai sirrin mu ya cigaba da ɓoyiwa” jin jina kai tayi har ta buɗe baki za tayi magana ƙarar dirar motocin su ya katse ta, da sauri ta miƙe daga saman sofa ta nufi bakin window cikin taƙun izza da ƙasaita, yaye curtains ɗin dake jikin window tayi,a hankali ta sauke idanunta a compound ɗin gidan,kusan a tare aka buɗe motacin dake tsakiyya, brisster zulaihat ce ta fito ɗayan ɓangaren kuma nainarh ce ta fito dafe da kai yayin da yumnah ta fito daga bayan motar dake bayan ta su,daga ganin yanayin fuskarta ba ƙaramin ku ka tasha ba. main entrance ɗin gidan su ka nufo wannan security guard ɗin ce ta shiga gaban su yayin da mazan su ka rufa masu baya har bakin entrance ɗin villa ɗin,wani ɗan card security guard ɗin ta ciro daga aljihun wandonta ta zura a jikin wata ƴar na'ura dake jikin ƙofar , cikin ƙanƙanin lokaci ƙofar ta shiga zugewa,zare card ɗin tayi, kama Nainarh mom tayi, ciki su ka kunna kai ban da security guard ɗin maza, juyawa su kayi su ka koma in da su ke zama. Taɓe baki matar tayi tana sakin curtain ɗin ta juya zuwa cikin parlorn, ya mutse fuska tayi “sorry kaji ni shiru, dangin yahudawan ce ta dawo, matar nan akwai ɗan banzan taurin kan tsiya,babu abun da ta rasa a rayuwa amma saboda tsabar zubar ma da kai aji ina ita ina aikin lawyer dukiya mulki babu wanda Allah bai bata ba, daga gidan mijin har gidan iyaye da ƴaƴa amma ta zaɓi wannan aikin wahalar” jinjina kai tayi can ta kwashe da dariya tana faɗin “no ba haka nake nufi ba, kaima ai kafi ƙarfin shi kawai ra'ayi ne irin naku kai da ita” dariya ta sake saki tana faɗin “ok bye bye, take care of ur self for me sai na sake jinka” tana gama faɗa ta janye wayar daga kunnenta, mazauninta ta koma ta zauna tana ɗaura ƙafa ɗaya kan ɗaya tana wani jijjiga ƙafarta dake manne da chain na gold, ƙafar sai sheƙin ƙunshin jan lalle take. tana a nan zaune su ka shigo parlorn bakin su ɗauke da sallama, daga yanyin da su kayi sallamar zaka tabbatar da rashin natsuwar da su ke a ciki, yumnah har time ɗin kuka take,miƙewa matar tayi tana nufar su fuskarta ɗauke da wani shu'umin murmushi, tana ƙarasowa gabansu tace “Ashe haka shari'a ta kasan ce?” banza mom tayi da ita kamar bada ita take ba “dama duk wanda yace tukunyar wani bazata tafasa ba to tabbas tashi ko zafi ba za tayi ba,to Allah dai ya kyauta na gaba” ta faɗa tana sakin murmushi,wucewa mom tayi ba tare da ta tanka mata ba ta nufi elevator,bin bayan ta su yumnah su kayi. dariya matar ta saki tana faɗin “ita ƙarya dama ai fure take bata ƴaƴa,salihan bayi kullum a cikin nasara suke, tsinanne kuwa baya taɓa nasara akan masu daraja” mom na jinta amma tayi kamar bata san tana yi ba, wasu madannai ta dannan a jikin elevator, buɗewa ƙofar tayi su ka shige ciki,wata ƴar iskar dariya mata ta sake saki “Allah ya la'anci yahudawa da nasarawa, duk wanda ya kasance cikin wa ƴannan da Allah ya la'anta yayi asara, Allah mungode maka da kayo mu cikin jinsi mafi daraja da ɗaukaka kayo mu a muslmai ba sabon tuba ba” dariya ta saki tana bin su mom da kallo har suka yi sama. juyawa tayi da nufin komawa mazauninta,wata kyakyawar budurwace tsaye a bayanta fara ce sai dai ba irin sosai ɗinnan ba,gown ce a jikinta white color ta ɗan wuce gwiwarta yayinda kanta ke sanye da hular saƙa baƙa,manya idanunta farare ƙar ta zubama matar, tsuke fuskarta matar tayi tana wani yamutse fuska tace “miye ki ka wani tsare ni da idanu uwata?” girgiza kai tayi cikin ƙunar rai da takaici tace “MAMY gaskiya abun da ki ke baki kyautawa, miyasa kullum ki ke son zubarma kanki da mutunci ne?, yanzu dan Allah abun da ki ka yima mom kin kyauta?, gaskiya mamy ki dai na wannan ba hali bane mai kyau,kina jawo ma kanki abun kunya damu kan mu” “ehyye!,sannu uwata, nace sannu uwata faɗa za kiyi man?” ta faɗa kamar zata rufeta da duka “mamy ba faɗa zanyi maki ba, ina faɗa maki gaskiya ne a matsayina na ƴar ki, hakan bai dace ba” “to bana so” mamy ta faɗa “mamy dole na faɗa maki gaskiya,idan har DADY ya san baki daina wannan ɗabiun ba bazai taɓa raga maki ba kin dai san halin shi, a kullum mom tana son ku zauna lafiya amma ke baki son haka, kullum burinki ki tada fitina, kuma mamy da ki ke mata gori kema fa ba rawa ki kayi Allah ya hallice ki muslmar ba sai kiga tafiki dacewa ita data shiga muslincin daga baya sama dake da aka haifa a cikin s...” bata ƙarasa ba mamy ta daka mata tsawa tana faɗin “FA'IZA! ni ki ke faɗama wannan kalaman dan uwarki?” “kiyi haƙuri mamy gaskiya ce” riƙe haɓa tayi “ah gaba gaba duka zaki fara kaiman idan banyi wasa ba” “Allah ya tsare ni da kai maki duka mamy, amma ki sani wallahi sai na sanar da DADY baki dai na cin mutuncin mom ba, kuma ma ai ya hanaki zama main parlor,kin dai san sauran idan har yazo ya sameki” tana faɗar haka ta nufi elevator da su mom su ka hau da sauri dan ta san zamanta a wurin bazai haifar da ɗa mai ido ba, madannan dake jiki ta danna. “ina zaki uwar iyayi?” mamy ta faɗa tana ɗan ɗaga murya “zanje na lallashi mom ne” baki mamy ta saki har fa'iza ta ɓace ma ganinta, jinjina kai tayi tana faɗin “zan kama ki ne dan ubanki, sai naji uban dake zugaki kina faɗa man magana san ranki” ta faɗa tana nufar elevator dake ɗayan ɓangaren parlorn ta shiga, dan ta san muddin dady ya shigo ya sameta a main parlorn ranta idan yayi dubu to sai ya ɓaci. ƙofar elevator ne ya buɗe, zuro ƙafarta tayi ta nufi wani ɗan corridor,wata ƙofa ta shiga,wani haɗaɗen parlor ne ta shigo,ya fi na ƙasan da su ka baro kyau da tsaruwa, komai na cikin shi ya kasance gloding color ne,set ɗin sofa biyu a cikin shi. Wata ƙofa ta nufa wacce nake kyautata zaton kitchen ne,tura ƙofar tayi ta shiga makeken kitchen ne gari guda babu wani da babu a ciki,ma'aikata ne su shidda gaba ɗayan su mata ne, kowaccen su na sanye da uniform ɗinta riga da wando, rigar fara ce yayin da wandon ya kasance baƙi, kowannen su aikin gaban shi yake, bakinta ɗauke da sallama ta shiga, gaba ɗaya su ka ɗago suna kallonta, amsa mata sallamar su kayi suna ɗan rissinawa su ka gaishe ta, cikin kulawa ta amsa masu tana ƙarasawa cikin kitchen ɗin, ɗaya daga cikin su ce tace “Aunty Fa'iza mi ki ke buƙata, ai da kin kira waya ba sai kin zo da kanki ba?” dish rag ta nufa tana faɗin “karki damu ISHRAT zan ɗauka da kaina, kawai dai ina so ku haɗa ma su mom lafiyayyan abinci mai rai da lafiya” “in sha Allah yanzu za'a kammla” jinjina kai tayi tana ɗaukar plate mai ɗan girma ta nufi fridge,kayan ci da sha ne shaƙe a cikin shi, duk wannan kayan ƙwalam da maƙulashe dake ciki ruwa da lemu kawai ta ɗauka ta ɗaura saman plate ɗin,ƙofar fita ta nufa ɗan dakatawa tayi. “kina buƙatar wani abun ne?” ishrat ta faɗa “A'a, wai yaushe ummah za ta dawo ne?” “tace man yau ko gobe amma ba tabbas” ishrat ɗin ta faɗa, jinjina kai fa'iza tayi tana ficewa daga kitchen ɗin. parlorn data shigo ta koma wata ƙofa ta nufa nan ma wani madaidaicin parlor ne, anan ta samu yumnah da nainarh,nainarh har lokacin kuka take yumnah kuwa ta dafe kanta da hannunta ɗaya yayin da idanunta ke a lumshe hawaye na fita,wannan security na zaune gefen nainarh tana lallashinta “Assalamu Alaikum” ta faɗa tana ƙarasawa cikin parlorn, “good morning ma” security guard ɗin ta faɗa “morning”fa'iza ta faɗa tana nufar in da suke ,trayn dake hannunta ta ajiye saman table, zama tayi kusa da nainarh, dafa ƙafaɗarta tayi “ba kuka ya kamata kiyi ba Nainarh, Adu'a ya kamata kiyi in sha Allah komai yayi farko zaiyi ƙarshe, in sha Allah babu abun da zai faru da momyn ki,zata dawo gareki in sha Allah” lallashinta fa'iza ta shigayi tana faɗa mata kalamai masu daɗi, shiru nainarh tayi tana sauke ajiyar zuciya, kallon yumnah fa'iza tayi “Autar dady da mom kukan ya isa haka sai kisa zuciyarta ta karaya, ki daina kinji” jin jina mata kai kawai yumnah tayi “ku shiga ɗaki sai ku kwanata ku huta kunji, ga breakfast can nasa su ishrat su haɗa maku” da to su ka amsa mata, suna tashi itama miƙewa tayi tana faɗin “mom na ciki ne?” da eh yumnah ta bata amsa. trayn ta ɗauka,ƙofar dake kallon dama ta nufa, a hankali ta tura ƙofar bakinta ɗauke da sallama,masha Allah na furta a yayin da nayi arba da katafaren bedroom ɗin data shigo,expensive furniture's ne a cikin shi na alfarma,royal bed ɗin dake ciki kawai abun kallo ne,yasha blanket da bedsheet masu tsadar gaske, bed ɗin a cike yake da pillows, bedroom ɗin ba wani cike yake da kaya ba, bed ne kawai sai nightstand dake ɗauke da bedside lamps sai dressing mirror,sai sofas guda biyu dake can bakin sliding window sai ɗan round table dake tsakiyar su. Cikin ɗakin ta ƙarasa yayin da take yin sallama, a tsaye ta hango brisster zulaihat bakin window hannunta riƙe da curtains,girgiza kai fa'iza tayi cike da tausayawa ta nufi in da brisster take, sallama ta sake yi dan a tunaninta bata jita ba,kafe garden ɗin dake bayan villa ɗin tayi da ido yayin da hawaye ke sauka daga idanunta, a zahiri kallon shuke shuke dake cikin garden ɗin masu ɗaukar hankali take amma a zahirin gaskiya hankalinta kwata kwata ba'a kan su yake ba,babban tashin hankalin ta a wane hali yanzu aminiyarta take ciki sannan ya rayuwar nainarh zata kasance ba tare da mahaifiyarta ba, da sauri ta juyo jin an dafa kafaɗar ta. kallon fa'iza dake tsaye a bayanta tayi “Fa'iza yaushe ki ka shigo?” “mom yanzu na shigo ina ta ƙwala sallama ba kijini ba, mom dan Allah ki daina sa damuwa a ranki kar wani abun ya same ki, in sha Allah momy zata fito” ajiyar zuciya ta sauke,hannu fa'iza tasa ta shiga guge mata hawayen dake zuba daga idonta tana sake bata haƙuri, jan hannunta tayi su ka nufi sofas ɗin dake wurin. Zama su kayi suna fuskantar juna “mom in sha Allah zata fito, mom kinfi kowa sanin yanke mata hukuncin ɗaurin rai da rai ba shike nuna gaskiya baza tayi halinta ba,ba kuma shi ke nuna ba zata iya fitowa wata rana ba, dan Allah ki kwantar da hankalin ki” “Nagode fa'iza” shine kawai abun da brisster tace “mom kinfi ƙarfin haka a waje na fatana dai ki rage damuwar a zuciyar ki, sannan nayi maki Alƙawari mom zan tayaki da Adu'a Allah ya bayyanar da gaskiya” “Ameen fa'iza” “sannan mom ina mai baki haƙuri akan abun da mamy tayi maki, bata kyauta ba dan Allah kiyi haƙuri” murmushi brisster ta saki yarinyar akwai shiga rai ta na matuƙar burgeta “fa'iza kenan idan da sabo ai yaci ace na saba da hakin mamyn ku, karki damu abun da tayi man kwata kwata bai ɓata man rai ba” “shikenan mom amma duk da haka ina mai baki haƙuri a madadinta” murmushi brisster ta saki trayn data shigo ta nufa, ruwa ta tsiyaya mata a cup “mom gashi kisha, na sa chefs su haɗa maku breakfast dan na san haka ku ka fita bakuci komai ba” ”nagode fa'iza Allah ya biyaki da mafificin Alkairi” “mom dan Allah ki daina gode man” “ya zama dole ne fa'iza” “ni dai dan Allah ki daina gode man, nifa ƴarki ce kuma mom kin san cewa babu godiya tsakanin iyaye da ƴaƴansu” murmushi brisster ta sake saki tana zubama fai'za ido, fa'iza badai iya tsara kalamai masu daɗi ba. Turo ƙofar bedroom ɗin a kayi, da sauri su ka kai duban su ga ƙofar a tsaye ya ke ya harɗe hannuwan shi a ƙirji,Army green ɗin shirt ce a jikinshi haɗe da Army trouser wanda ya tsaya mashi iya gwiwa , babban mutum ne da a ƙalla zai kai kimanin shekaru 56 zuwa da 8 a duniya, dogo ne sosai yana da jiki, ƙaƙƙarfa ne na gaske kamar ba dattijo ba, a ido idan ka kalleshi baza kace shi ke da waɗannan shekarun ba,fari ne kyakyawa kallo ɗaya za kayi mashi ka hango kamaninshi da fa'iza da yumnah,da gudu fa'iza ta nufe shi, faɗawa tayi jikinshi “good morning dady” murmushi ya saki yana jan kumatunta “har yanzu baki san kin girma ba ko fa'iza?, kina abu sai kace yumnah” ɓata fuska tayi kamar ƙaramar yarinya “dady nice ma yumnah” zuba masu ido brisster tayi tana kallon su baƙaramin birgeta suka yi ba, raba jikin su yayi yana faɗin “ƙwarai ma kuwa” cikin ɗakin ya ƙarasa, ƙofar fita fa'iza ta nufa tana faɗin “mom sai na dawo, dady ka barta ta kwanta ta huta ta gaji” ta faɗa tana jan handle ɗin ƙofa “na lura fa'iza kin raina ni da yawa” dariya tayi tana jan ƙofar ta fice, murmushi kawai mom tayi tana girgiza kai. bakin bed dady ya nufa,zama yayi yana zuba ma barrister ido, ɓata fuska tayi kamar zata fashe da kuka ta nufeshi, tana ƙarasowa gabanshi faɗawa tayi jikinshi tayi hugging ɗin shi,hannu biyu yasa ya zagaye bayanta,shafa doguwar sumar kanta ya shiga yi “Barrister lafiya?” saukar hawayenta yaji a saman chest ɗin shi, da sauri ya ɗago da fuskar ta yana kallo,hawaye ya gani suna zarya a kumatun ta. hannu yasa ya shiga share mata su “gaskiya ƙarshen wannan aikin naki ya zo,bazaiyu a riƙa sa man mata kuka ba, dole ki ajiye wannan aikin dama ba so nake ba saboda kin dage kina so ne kawai yasa na barki” “sir kar kace haka,wannan aikin da nake ban san iya adadin ladar da nake samu ba, zaka so ka zama sanadiyyar yankewar wannan ladar?” “amma kullum sai su riƙa sa man ke kuka, bana jin daɗin hakan?” “ba laifin su bane kukan ne dole nayi, ina ji ina gani na kasa taimakon Aminiyata kotu ta yanke mata hukunci ba tare da ta aikata laifin ba” “karki damu,in sha Allah komai zai daidaita yanke mata hukuncin ai ba yana nufin shikenan ba,ki dai na kuka kinji bana so” wasu hawayen ne su ka sake zubuwa, ɗan bubbuga bayanta ya shigayi “ya isa haka, idan ba nima nawa hawayen ki ke son gani ba” hannu tasa tana share hawayen “na daina” “yawwa ko ke fa,ina ita yarinya Asma'un?” “dama ina so na nemi wata Alfarma a wurin ka” “Alfarma kuma?” “Eh,dangin mahaifiyarta sun so tafiya da ita amma nace A'a saboda karatunta zata zauna anan in yaso sai su riƙa tafiya tare da yumnah,kuma dai gaskiya ina son ta zauna a tare da ni sai tafi samun kulawa sama da can, zata iya zama nan ba matsala?” jinjina kai yayi “dama makarantar su ɗaya da yumnah ne?” “eh school ɗin su ɗaya” “shikenan ba damuwa, zata iya zama a nan ɗin ai kema tamkar mahaifiya ki ke a gareta” “haka ne, nagode sosai Allah yasa da Alkairi” ɗan ɗaure fuska yayi “ni ki ke ma godiya zulaihat?” “eh mana, idan an kyautata maka sai ka gode ai ba wani abu bane” “to bana so, nan ɗin gidan ki ne kina da ikon ajiye duk wanda ki ke so, idan kuma ki ka sake godeman to ni da ke ne” murmushi tayi tana kwantar da kanta saman shoulder ɗin shi “zuwa anjima ina so zanje prison dan na duba jikinta,his excellency yanke jiki fa tayi ta faɗi na shiga tashin hankali matuƙa a lokacin” “Allah ya kaimu anjimar sai mu tafi tare, Allah ya bata lafiya” “Ameen ya Allah” 𝑄𝑢𝑒𝑒𝑛 𝐾𝑎𝑖𝑛𝑒𝑟𝑡..... ✍💫 Baƙar motar ce ƙirar benz ta tukaro gate ɗin estate ɗin,sanin halin mamallakiyar motar ne yasa tun kafin motar ta ƙaraso sojojin dake gadin gate ɗin su kayi hanzarin buɗe mata ƙofa,babu ɓata lokaci ta danna kan hancin motar zuwa ciki,ɗaya daga cikin gidajen motar ta nufa,a parking space ɗin duplex ɗin data nufa tayi parking,dai daita parking tayi, kafin aka buɗe motar ƙafarta ta zuro kafin ta fito gaba ɗayanta,iska ta shaƙa ta fesar, hannu ta zura ta ɗauko hand bag ɗinta, main entrance ɗin duplex ɗin ta nufa bayan ta rufe motar, sai ya mutse fuska take alamar ta gaji. Wani madanni ta danna jikin ƙofar, nan take ƙofar ta buɗe, ciki ta kunna kai,mash Allah na furta a yayin da nayi arba da haɗaɗɗen parlorn data shigo, komai na cikin shi ya kasance light brown, faɗa maku haɗuwa da tsaruwar parlorn ɓata lokaci ne,babu kowa a parlorn sai mai aiki dake ƴan goge goge,jin ƙarar buɗe ƙofa ne yasa mai aikin ɗagowa, ganin wacce ta shigo ne yasa ta nufota da sauri,hannu ta miƙa da nufin amsar jakar dake hannunta tana faɗin “good Afternoon ma” wani ɗan iskan kallo mai haɗe da harara ta watsa ma mai aikin, saurin sadda kai ƙasa mai aikin tayi tana ja da baya,tsaki taja tana nufar stairs case dake parlorn. da kallo kawai mai aikin ta bita har ta ɓacce ma ganin ta,taɓe baki tayi tana komawa kan aikin dake gabanta, a bakin ƙofar wani ɗaki ta tsaya, tura ƙofar tayi ta shiga,wani haɗaɗeb bedroom ne ta shigo komai na cikin shi ɗan dai dai babu haya niya, ciki ta ƙarasa tana kiran sunan “Aunty laatifa! am home where are u” matashirya mata ta hango zaune kan study chair yayin da laptop ke a saman desk tana operating. “Aunty nah sarkin aiki,a gidan ma baki huta ba, gaskiya mijinki ya shiga shiga uku na san a daren ku ma nafarko kwana za kiyi kina aiki, shiyyasa momy ke ce maki agogo sarkin aiki” juyowa tayi masha Allah na faɗa da ganin wannan madarar kyan, laatifa kyakyawa ce ajin farko,riga da wando ne a jikinta masu taushi, kanta babu ɗan kwali tayi parking gashinta a tsakiyar kai, medical glass ɗin dake idonta ta cire. “ƙanwata idan ban yi aiki ba mi ki ke so nayi?” “gaskiya kina aje wa kina hutawa” “shikenan, ya gajiyar aiki?” ya mutse fuska tayi yayin da take samun wuri bakin bed ta zauna “aiki babu daɗi” murmushi laatifa ta saki wanda ya ƙarama kyakyawar fuskarta kyau “gaskiya Balqis kin cika raki, miye abun gajiya a wannan aikin ke da kina bayan mota kina shan iskar Ac” “haka za kice mana tunda ke kin saba, duk ranar dana sha a court za kice haka” “ba wai zan ce ba haka ne ma, kawai dai kin cika raki” “shikenan naji ina alƙawari na?” “yanzun nan na gama tura mashi saƙo ta email kin san baya ɗaukar kira ba tare da ka fara tura mashi saƙo ba” “haka ne, amma ai ke naga kuna waya” “wannan ai shi ke kirana, amma duk lokacin da ni nake son magana da shi sai na fara tura mashi saƙo tukun” taɓe baki Balqis tayi “shi dai komai nashi na daban ne” “classic boy ake faɗa maki dole komai nashi ya kasance unique,ke dai kawai ki dage da Adu'a dan akwai aiki a gabanki” “ni kaina na sani Aunty laatifa abun har tsoro yake bani” “karki damu nima zan tayaki da adu'a ” “in sha Allah, bari na tafi ɗakin momy bata san na dawo ba, nan na fara shigowa” “ok anjima zaki bani labarin yanda ƙarar ta kasance” “kin ma tuna man, wallahi dady ya ganni ba kiga harar da ya watsa man ba kamar ƴan hanjin ciki na su faɗo” dafe ƙirji laatifa tayi “nashiga uku!! dan Allah da gaske ki ke”laatifa ta faɗa da tsantsar tashin hankali “wallahi kuwa na san dole yaji ba'asin abun da ya kaini, amma zanyi duk yanda zanyi ganin bai gane ke ki ka tura ni ba” “yawwa dan Allah kice ra'ayi ki ka yi ba ni nace kije ba” “in sha Allah karki damu” “yawwa na gode” ƙofar fita Balqis ɗin ta nufa tana ƙara jaddadamata karta damu. zama tayi bakin bed dafe kanta“ya Allah” ta furta,da alama hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba jin dadyn su yaga Balqis. Balqis tana fita daga ɗakin wani ɗan corridor ta nufa, wani ɗan madaidaicin parlor ta shiga,a zaune take saman sofa mai mazaunin mutum biyu les ne a jikinta ɗinkin half bubu da zani, hannunta da wuyanta sun sha adon zinari, wayace kare a kunenta da alama waya take “lamari ai baiyi daɗi ba, in sha Allah anjima idan Barrister ya dawo zan tambaye shi naje nayi mata jaje ai abun ayi jaje ne” murmushi Balqis ta saki tana ƙarasawa cikin parlor. faɗawa tayi saman jikinta“momy na dawo” da sauri ta janye wayar daga kunenta “ja'irar banza kin girma amma baki san kin girma ba, ba ki gani waya nake, karya ni ki ke son yi?” tashi tayi zaune tana turo baki“momy daga nayi kewarki zaki rufe ni da faɗa” “an rufeki da faɗa, dan gidan ku haka ake kewa kina shirin karya ni” “ke momy haka ki ke daga abun arziƙi sai ki rufe mutum da faɗa na san da dady ne bazai ce man komai ba” "ai shi ki ka ce ƙashin shi ƙwari ne gare shi” ficewa Balqis ɗin tayi daga parlorn tana gungunai. Mai da wayar tayi a kunne “kina jina da wannan ja'irar yarinyar tana neman karya ni”bana jin mi na cikin wayar ke faɗa “to shikenan idan Allah yasa mun haɗu anjimar to shikenan, idan kuma bamu haɗu ba sai ranar friday kenan idan mun haɗu a part ɗin Abbah” jinjina kai tayi kafin daga bisa ni su kayi sallama. *UNITED STATE* _*Las Vegas (Nevada)*_ _*Nailarh Racing Track (N.R.T)*_ Ƙaton track ne gari guda wanda girmanshi zai kai girman wani babban ƙauyen,kallo ɗaya zaka ma wurin ka hango tsirarar dukiyar da aka kashe wajen gina shi, ta ko ina ka duba mutane ne zazzaune a saman chairs gaba ɗaya hankalin su naga wasan da ake gabatarwa,kowa burinshi nashi yayi nasara,duka mutanen dake wurin suna sanye ne da polo shirt white color wacce a gabanta a kayi rubutu da ɓakin fenti in da aka rubuta QUEEN da manya haruffa daga saman shirt ɗin logo ne na sunan center ɗin ( N R T) sai p_cap da hat wanda suma aka rubuta QUEEN a jikinsu kamar na shirt ɗin,maza ke sanye da p_cap yayin da mata ke sanye da hat wacce aka yi mata kwalliya da gashin tsintsaye a samanta, Al'adar wurin wasan ce duk wanda zai shiga sai an bashi wannan shirt da cap ya sa wanda kyauta ce daga mamallakiyar wurin wasan. dawakai ne kyawawan gaske ke gudu a tsakiyar filin,yayin da mamallakansu ke saman su jikin su sai salƙi yake yana ɗaukar ido,color uku ne dawakan wasu brown yayin da wasu su ka kasance baƙaƙe doki ɗaya ne a wurin ya kasance white color,daga yanayin tsarin dokin zaka san na musamman ne, a jere su ka fara gudun,cikin ƙwarewa da karsashi dawakan ke gudun abun gwanin ban sha'awa,abun dai sai wanda ya gani,rabuwa su ka fara yi da junan su, dawakai uku ne su kayi gaba yayin da su ka bar sauran a baya harda wannan farin dokin yama fisu yin baya sosai sama da sauran dawa kan,sosai su ke gudu dan kaiwa ga matsaya,miƙewa tsaye mutane su ka fara yi da alama dawakan nan gudu uku na daban ne, mutane na da buri a kan su. Wasa fa ya fara ɗaukar zafi dawakan kansu su ukun sun rabu da juna yanzu biyu ne a gaba ɗayan a baya. “da alama dai yau tarihin N R T zai canza, ban taɓa ganin wasa irin wannan ba” cewar wani bature dake zaune cikin ƴan kallo, murmushi gefen baki mace dake gefen shi ta saki tana faɗin “ba abu bane mai yuwuwa canza tarihin N R T cikin sauƙi, a ko wane lokaci da sabon salo take zuwa, kana tunanin wannan baya bayan da tayi babu wata a ƙasa?” taɓe baki yayi yana ɗaga kafaɗa “i don think,tazarar tayi yawa duba kiga in da su Ryder su ke kalli in da king yake”murmushi matar ta saki “dear sai kace yau ka fara zuwa kallon wasan N R T” “ba yau na fara zuwa ba, but wasan yau ne ban taɓa ganin irinshi ba” “to ka zuba ido za kace na faɗa maka” “okay” ya faɗa yana mai da glass ɗin shi daya cire. ran wani magidanci ne daga cikin ƴan kallo ya fara ɓaci,sign matar wannan baturen tayi mashi, duban shi ya kai ga mata da majin “bazan taɓa ƙyale Anthony ba idan har kuɗina su ka lalace” ya faɗa da alamar ranshi ya ɓaci“but why?” matar shi ta tambaya “babu alamun zanyi nasara,kin kuma san dama ba da san raina na zuba kuɗi na a wasan nan ba, idan har kuɗina su ka salwanta bazan ƙyale shi ba” “just bcox of five hundred thousand dollars kake wannan maganar akan brother nah?” kallonta yayi da mamaki“its not a money?” “no it's money, but ai kafi ƙarfin su, kuma banyi tunanin zaka iya furta wannan maganar akan Anthony ba” “it's not my concern,kuɗina kawai na sani” “sai ka bari idan kaga ba kayi nasara ba sai ka faɗi duk abun da zaka faɗa,ai har yanzu wasan ake” murmushi takaici mutumin ya saki “oh wai kina nufin har yanzu kuna da sa rai a wannan wasan,ƙazamin tunani kawai” ya faɗa yana kauda kanshi gefe, haɗa ido su kayi da wannan matar da mijinta, a tare su ka sakar mashi murmushi suna ɗaga mashi hannu, shima hannun ya ɗaga masu yana maida kanshi ga wasan. Murmushi matar tayi“mi na faɗa maka kowa ya san cewa canza tarihin N R T ba abau bane mai sauƙi, ka dai ji wance magidanci ya saduda ta ƴan kuɗaɗen shi kawai yake” ta faɗa tana sakin murmushi, murmushi shima mijin nata yayi yana jinjina kai da faɗin“na tabbata... _*Episode 7_8*_ *Bound by fate,freed by love, A romantic Odyssey*❤💘💘 _____________________________ Murmushi matar tayi“mi na faɗa maka kowa ya san cewa canza tarihin N R T ba abau bane mai sauƙi, ka dai ji wance magidanci ya saduda ta ƴan kuɗaɗen shi kawai yake” ta faɗa tana sakin murmushi, murmushi shima mijin nata yayi yana jinjina kai da faɗin“na tabbata” mai da hankalin su su kayi akan wasan,wasan ne ya fara canza salo kamar walƙiya sai ga dokin dake baya sama da ko wane doki ya zama shine a tsakiyar dawakai biyun dake gaba, kamar a mafarki masu kallon wasan ke kallon ikon Allah,tashi wannan magidanci yayi yana jan tsaki ya kalli matar shi “kin dai ji abun dana faɗa maki sisi na ban yarda tayi ciwo ba” yana gama faɗa ya bar wurin gaba ɗaya, taɓe baki matar tayi ita har a lokacin ba taga wani alamar rashin nasara ba tunda dai ba'a gama wasan ba. fita dokin yayi daga cikin jerin dawakai biyun daya shiga ya zama shine ke biye da dokin dake gaba sai dai akwai ƴar tazara a tsakaninsu,sosai dawakan ke gudu cike da karsashi suna tunkarar matsayar wasan in da ya kasance nan ne ƙarshe duk wanda ya riga isa shine ya lashe gasara. hankalin mutane dake sa ran cin gasar ne yayi matuƙar tashi, tuni zufa ta shiga wanke wasu daga cikin su saboda maƙudan kuɗin da su ka zuba wanda suke ganin suna gab da yin asara,seconds Biyar ya rage a kammala wasan,bai wuci taku kaɗan ya ragema dokin dake gaba ya isa matsayar wasan, kamar walƙiya wannan farin dokin ya gita ta gabanshi ya riga shi isa matsayar, da sauri ma hayin dokin yaci birki rai a ɓace ga ci yana gani amma ya rasa. Ihu da sowa ne ya fara tashi a wurin wasan haɗe da kiɗe kiɗe, a fusace ɗai ɗai kun mutane su ka fara tashi suna barin wurin wasan,birki dokin yaci cike da kuzari mamallakin dokin ya sauko, da sauri wasu matasan ƴan mata su biyar suna sanye da riga da skirt iya gwiwar su, rigar white color yayin da skirt ɗin ya kasance black color aƙalla kowace a cikin su zata kai kimanin shekara 28 zuwa 30,cikin filed ɗin su ka nufa a gaban wannan dokin su ka tsaya ɗaya na riƙe da water bottle yayin da wata ke riƙe da ɗan ƙaramin towel wacce tafi kowa girma a cikin su ce take goye da backpack sauran biyu babu komai a hannun su sai sakin murmushi su ke, wani matashi sauarayi ne ya amshi dokin, helmet ɗin dake kanta wacce aka rubuta Queen a jikinta ta zame tabarakallahu ahsanul kaliƙin na furta da ganin wannan maƙurara kyan. fara ce tas doguwa kyakyawar gaske wacce idan akace kyau to fa anazuwa kanta an rufe babin kyau,tana da idanuwa masu matuƙar jan hankali launin Acme white grey sai sheƙi su ke ga zira ziran eye lashes ɗinta da su ka ƙara ƙawata su,tana da siraran laɓɓa launin light pink masu matuƙar taushi tana da ɗan tsayin fuska hancinta a tsaye yake kem,tana da cikar gashin gira sai dai ba sosai ba,kanta ta ɗan girgiza yayin da take zame ɗan ƙaramin ribbon ɗin data ɗaure gashin kanta nan take wavy hair ɗinta launin light golding brown ta tarwatse a gadon bayanta ,tana da shape mai matuƙar ɗaukar hankali skin ɗinta sai sheƙi take tana salƙi kamar hasken rana bai taɓa raɓarta ba. kissing neck ɗin dokin tayi tana ɗan sakin murmushin gefen baki har sai da dimples ɗinta su ka lotsa sosai murmushin ya ƙarama kyakyawar fuskarta kyau “madam water”ɗaya daga cikin matan ta faɗa tana miƙa mata water bottle ɗin dake hanunta mai kyan gaske wacce a jikinta aka rubuta Queen, ya mutse fuska tayi ba tare da ta ko kalli in da matar take ba,wacce ke riƙe da towel a hanunta ce ta matsa kusa da ita daddaɗan ƙamshin turaren ta ne ya daki hancin matar har sai da ta lumshe ido duk da zufar da tayi haka bai hana dawwamamman ƙamshinta fita ba, a hankali ta shiga goge mata zufar da tayi,jefi jefi mutane su ka shiga ƙarasowa cikin field ɗin suna mata congrat yayin da take ya mutse masu fuska ba tare da ta amsa masu ba hakan bai dame su ba saboda sanin halinta sunma samu sa'a yau da har ta tsaya harma take yamutse masu fuska. barin wurin matashi yayi da dokin, ɗaga ma dokin hannu ta shiga yi tana faɗin“ i miss u” murmushi matan su ka saki,fly kiss ta ma dokin tana sakin murmushi,bata bar wurin ba har sai da ta daina ganin dokin tukun ta bar wurin yayin da matan ke biye da ita har gaban wasu motoci guda bakwai,guda shidda rang robbers ne yayinda su ka saka wata farar Rolls Royce tsakiyar su sai ɗaukar ido take,body guards ne tsaye a bakin motocin Aƙalla za su kai su biyar ban da drivers ɗin da da su kayo driving motocin,cikin girmama su ka shiga gaishe da ita suna tayata murnar lashe wasan, babu wanda ya samu arziƙin data amsa mashi sai ma nufar wannan fara rolls royce ɗin dake tsakiyar motocin tayi, da sauri ɗaya daga cikin su ya buɗe mata back seat ta shiga,komawa su kayi cikin motocin harda wannan matan,a jere su ka hau wani dogon titi a cikin wurin wasan. A kishingiɗe take a cikin motar ta lumshe idanunta yayin da sanyin Ac ke ratsata, tafiya mai ɗan nisa su kayi kafin su ka nufo wani katafaren gate ga wasu irin jibga jibgan security guard a bakin shi, horn driver dake gaba yayi, babu ɓata lokaci security guard ɗin su ka buɗe masu gate,da gudu motocin su ka kunna kai ciki security guard ne ke kai kawo ta ko ina na wurin, titi ne su ka sake miƙewa shantal, wani ɗan ƙaramin gate na ɓakin ƙarfe wanda ya kasance shara shara kana iya hange ciki su ka nufo, wani remote driver dake gaba ya danna nan take gate ɗin ya buɗe ciki su ka kutsa kai ciki. masha Allah na furta da ganin irin haɗuwar wurin ,ƙatafaren luxury skyscraper ne iya ganinka, ta ko ina ka kallah a jikin ginin gilasai ne masu matuƙar ɗaukar ido A ƙalla yana da sassa guda shidda,harabar gidan kanta abun kallo ce lion water fall ne a tsakiyar gidan yayin da yake fitar da ruwa da styel daban daban, security guard ne ke kai kawo a ko ina na harabar gidan. A bakin skyscraper ɗin su kayi parking da sauri ɗaya daga cikin security guard ɗin ya fito ya buɗe mata car door,ɗaya bayan ɗaya su ka shiga fitowa,gaba ɗaya matan gaban motar da take ciki su ka zo su ka tsaya, a hankali ta zuro ƙarta kafin ta fito gaba ɗaya, security guard ɗin dake kai kawo ne su ka shiga rissinawa suna gaishe da ita, hannu kawai ta ɗaga masu kafin a hanzarce ta nufi gidan matan nan na take mata baya,a bakin main entrance ɗin gidan suka tsaya,wata irin haɗaɗiyar ƙoface ta glass,sai ta fuskarta tayi a jikin wata na'ura dake manne jikin ƙofar wacce nake kyautata zaton face ID ne magana na'urar ta fara cikin harshen turanci “welcome back home miss NAILARH” zugewa ƙofar ta shigayi, kutsa kai su kayi ciki, wani katafaren parlorn ne su ka shigo,painting cikin shi sliver glod ne, an ƙawatashi da manya manyan sofas jigunannun gaske masu matuƙar taushi da daɗin zama set huɗu sai throw pillows dake kan ko wace sofa, daga tsakiyar parlorn round glass table ne an jera flower vase masu matuƙar kyau, daga saman ceiling ɗin ginin crystal chandeliers ne golding color masu girman gaske an ƙawata su da kwalliya, sai faskekiyar flat creen tv mai matuƙar girma ta mamaye kusan rabin bangon da take sai kayan sauti dake gefe da gefen tv, sparkling floor lamps ne ajiye a ƙasa suna bada haske mai launika daban daban, ga dogayen curtains wanda aka ƙawata da zanen furanni kewaye da parlorn an zuge su,idan ka kalli ƙasan parlorn wanda ya kasance na glass wasu irin kifaye ne masu launika a jikin su suke shawagi. komai na cikin parlorn golding color ne hatta stairs case ɗin dake ciki,A ƙalla floor ɗin na ɗauke da parlor biyar harda wannan wanda ya kasance shine babba a cikin su kuma yake a tsakiyar su, daga cikin parlorn zaka iya hangen sauran falukan dake floor ɗin,masu karatu ba ƙaramar dukiya aka kashe a wajen haɗa wannan parlorn ba idan nace sai na fayyace maku komai dake cikin shi to tabbas anan book one zai ƙare,kawai ku ida ƙissma sauran a zuciyar ku. ma'aikata ne ke kai komo a cikin parlorn, zubewa su ka shigayi akan gwiwowunsu suna kai gaisuwa gareta, ko kallon in da suke ba tayi ba. glass elevator su ka nufa,ɗan yatsanta tasa a jikin na'ura dake jikin ƙofar elevator nan take ƙofar ta buɗe, ciki ta shiga tana lumshe idanunta alamar gajiya,mara mata baya ma'aikatan su kayi,ɗaya daga cikin ma'aikatan ce ta danna wasu madanni dake ɗauke da nombobi a jikin su,ƙofarce ta shiga zuge, sama elevator tayi da su, daga ta ciki zaka iya hangen manya manyan parlor kan da suke wuce masu matuƙar kyau wanda tsayawa fayyace su har littafin ya ƙare ba'a gama faɗar kyawu da haɗuwar su ba, tsayawa elevator yayi da alama sun kawo in da za su tsaya, ƙofar ce ta shiga zugewa,sai data gama zugewa tas tukun tasa kai ta fice ma'aikatan na biye da ita kamar wasu jela. nan ma wani katafaren parlorn ne su ka shigo wanda yafi na farkon haɗuwa sai dai bai kaishi girma ba,ma'aikatan ne nan ma ke kai kawo, take su ka shiga zubewa ƙasa suna gaishe da ita, hannu kawai ta ɗaga masu yayin da take yin gaba, a bakin wata katafariyar ƙofa su ka dakata, ɗaya daga cikin matan ce tayi saurin miƙa mata wayarta dake hannunta, amsa tayi yayin da take ɗaura tafin hanunta saman na'urar dake jikin ƙofar, zanen hannunta ne ya fito a jikin na'urar ,scanning hannunta na'urar ta shigayi na tsawan secon biyar kafin na'urar ta fara magana kamar ta ƙofar da su ka fara shigowa yayin da ƙofar ke zugewa. sai da ƙofar ta gama zugewa tas tukun ta kunna kai zuwa ciki yayin da matan guda biyu ke biye da ita sauran su ka kama gaban su, wacce ke ɗauke da backpack ce ta bi bayanta sai ɗaya wacce take riƙe da towel ɗin data goge mata jiki. wani irin katafaren bedroom su ka shigo a ƙalla girman shi ya isa ayi ɗan ƙaramin plat house saboda girma da faɗin shi, bedroom ɗin yana ɗauke da king size bed light golding, gadon na shimfiɗe da tattausan bedsheet da ƙaton blanket mai azabebben taushi ga jerin pillows wanda su ka kusa cinye kwata gadon, gefe da gefen gadon nightstand ne mai ɗauke bed sides lamps daga gaban gadon ottoman table ne mai ɗauke da drawer chest a jikin shi daga saman shi anyi mashi kwalliya da wasu stones masu sheƙi an mamman a jikin shi. daga ƙasan gadon wani haɗaɗɗe rug ne mai gashi gashi a jikin shi tsabar taushin shi har bacci mutum zai iya a kanshi ba tare da ya fahimci ba'a katifa yake ba,idan ka kalli saman ɗakin wani irin ƙaton chandeliers ne,daga hannun dama na ɗakin glass sliding door ce wanda nan ma wani bedroom ɗin ne sai dai komai na cikin shi white color ne, daga ɗayan ɓangaren kuma wani haɗaɗen stairs case ne can ma saman wani bedroom ɗin ne sai dai bai kai wannan dana kusa da shi girma ba, daga ɓangaren haggun ɗakin wasu ƙofofi ne guda uku a jere ɗaya bathroom sai spa and saloon wanda yake haɗe massege spa sai ɗaya ƙofar dressing room ne wanda idan ka shiga cikin shi zaka ɗauka boutique ne. wacce ke goye da back pack ɗin ce ta nufi laundry room,ɗurƙusawa ɗayar tayi a gabanta takalamin ƙafarta ta shiga cire mata, zama tayi saman ɗan stool hakan ya bata dama wurin cire mata takalmin, bayan data gama cire takalmin,sama nailarh ta ɗaga hannunta hakan yaba matar damar cire mata rigar dake jikinta tayi ta barta daga ita sai bra ta ajiye gefe kafin ta koma kan wandon, wandon shima zame mata shi tayi shantala shantalan cinyoyinta ne su ka bayyana farare tas da su sai sheƙi su ke kai kace haske rana bai taɓa ratsasu ba,kwashe kayan matar tayi ta nufi laundry room da su,a tare su ka fito daga laundry room ɗin ita da wacce ta fara shiga sallama su kayi mata su ka fice daga ɗakin. A kasalance ta shiga taka ƙafafunta tana nufar ƙofar toilet, tafiya take kamar bata son gaka ƙasa tana tafiya ko ina na jikinta na juyawa musamman ƙugunta da zanen rose flower na tattoo ya ƙarama fatar bayanta kyau,tun kafin ta ƙaraso bakin ƙofar ta shiga zugewa kutsa kai tayi ciki,wani irin bathroom mai girman gaske komai na cikin shi expensive ne,harda silver bed mai ɗauke da rober mattress mai haɗe da pillow sai daga jikin bangon toilet ɗin glass drawer ce mai girman gaske an rarrabata gida gida wanda bakomai ne a cikinta ba sai tarin shower gels,soaps,shampoos, towels, bathrobes,sponges da flip flops. ƙofa biyu ce a toilet ɗin da wadda ta shigo sai wata dake can ɗayan ɓan garen , silver bed ɗin ta nufa kwanciya tayi rub da ciki tana sauke ajiyar zuciya,wasu irin abubuwa ne a jikin ɗayar ƙofar masu kama da bulbs haske su ka shiga kawowa suna fitar da wani irin sauti can kuma su ka daina suna sanar da isowar lolah da larah,a hankali ta furta open ba tare da ta ɗago ba, zugewa ƙofar ta shiga yi, wasu matan turawa ne su ka shigo manya da su kamar ƴan wrestling,baƙin mini skirt ne a jikin su tare da farar shirt ajikin rigunan su an rubata sunayen su da wani irin style, haka shigar ma'aikatan gidan take. in da take su ka ƙaraso gaishe da ita su kayi suna ɗan rissinawa,bata amsa masu ba hakan bai dame su ba idan da sabo sun saba da halin uwar gidan ta su,lolah ce ta nufi glass drawer ɗin nan, buɗewa tayi ta ɗauko shower gel tare da soap da shampoo da sponge,a saman wani ɗan table mai ƙafafu ta ɗaura, maida ƙofar drawer tayi ta rufe turo table ɗin tayi zuwa gaban bed ɗin, ɗaukar shampoo larah tayi, buɗe marfin tayi ta shiga tsiyayama Nailarh shi a kai, bayan data gama ne tashiga cuɗa mata kan sai data tabbatar ya wanku tukun ta jawo hand shower ta shiga wanke mata kan, bayan data gama ne ta ɗauki shower gel ta shiga zubawa a ko ina na jikin Nailarh,sponge sock lolah ta saka a hannun ta larah na gama zuba shower gel ɗin ta shiga mulka mata mashi a ko ina na jikinta, ko motsi Nailarh ba tayi kamar matatta su ke juyata yanda su ke so dan su wanko ko ina na jikinta. sangarta da gata ne yasa Nailarh ko wanka bata ma kanta ba wai dan bata iya ba isa ce kawai da lalacewa tasa bata iya yi da kanta musammusam ta ajiye lolah da larah dan su riƙa yi mata wanka wanda aikin su ke nan a gidan, daga wankan ta da yi mata massege sai gyaran jiki babu abun da su ke iya aikin su kenan. ta ɗauki tsawan lokaci tana cuɗa mata jikinta sai data tabbatar ko ina na jikinta ya wanku tukun larah ta jawo hand shower ta shiga wanke mata jikin bayan data gama ne ta ɗauko hairdryer ta shiga busar mata da gashin kanta bayan data kammala busar mata da kan ta nufi glass drawer ɗin nan ta ɗauko bathrobe da flip flops ta dawo a bakin bed ɗin ta ajiye mata, a kasalance Nailarh ta sauko daga saman bed ɗin,flip flops ɗin ta zura a ƙafarta, miƙa mata bathrobe ɗin tayi , ƙarɓa tayi da kanta ta zura kafin ta cire hook ɗin bra ɗin dake jikinta ta ciro a ƙasa ta yarda ita kafin ta warware igiyar pant ɗin shima nan ƙasa ta sake shi, igiyar bathrobe ɗin ta ɗaure ƙofar fita ta nufa ba tare da ta ko kalli ɗaya daga cikin su ba. bra da pant ɗin lolah ta kwashe ta nufi dustbin ta saka Nailarh tana da wata ɗabi'a ta rashin maimaita sutura idan har kaga ta maimaita sutura to ba ƙaramin sonta take ba bra da pant dama su daga idan ta cire su to sun zama wasted bata ƙara amfani da su,gyra toilet ɗin su kayi su ka maida komai mazaunin shi sannan su ka wanke toilet ɗin duk da ba datti yayi ba bayan da su ka gama ƙofar da su ka shigo su ka nufa tun kafin su isa ƙofar ta buɗe alamar an basu izinin fita, ficewa su kayi. Nailarh tana fita daga toilet ɗin wannan sliding glass door ɗin ta nufa tana isowa ƙofar na buɗewa, ciki ta kutsa kai sai wani lumshe ido take, nan ma bedroom ne komai na cikin shi white color ne , babu wata hayaniya a cikin shi bed ne sai nightstand dake ɗauke da bedside lamps sai rug mai taushi dake shimfiɗe a ƙasa sai chaise lounge chair dake bakin wata ƙatuwar glass sliding door wacce da an buɗeta zata sadaka da ƙyataccen swimming pool wand kusan haɗe yake da ɗakin ƙofar ce kawai ta raba su sai ruwan da suke a kewaye daga bakin swimming pool ɗin lounger chairs ne guda biyu suna fuskantar juna sai daga can ɗan nesa da su ball chair ce daga gabanta ɗan madaidaicin glass table ne. nightstand ɗin ta nufa ear phone ɗin dake ajiye ta ɗauka tare da eye mask,bed ɗin ta dawo a kune ta sa ear phone ɗin kafin ta rufe idonta da mask ɗin, faɗawa tayi saman bed ɗin ta ɗaura kanta saman pillow tana saka ɗaya tsakankanin cinyoyinta yayin da ta rungume ɗaya a haka bacci yayi awan gaba da ita yayin da waƙar data kunna a ear phone take ratsa ƙwaƙwalwarta, Al'adarta ce bacci tana sauraron sauti. _*ABUJA . NIGERIA*_ _*G J I ESTATE*_ momy da laatifa ne zaune saman sofa da alama fita za su yi,momy ta ɗau wankan swiss lace maroon color ta yafa mayafi saman kanta, wayace kare a kunenta da alama waya take laatifa na daga gefenta zaune saman sofa mai mazaunin mutum ɗaya ta ɗau wankan black abaya tayi rolling da gyalenta simple make_up ne a fuskarta sai medical glass ɗinta dake ƙarama kyakyawar fuskarta kyau,wayar tace riƙe a hanunta tana aikin latsawa, janye wayar momy tayi daga kunenta tana ɗan jan tsaki “du kace zaka fita tare da Balqis sai ta ɓata maka lokaci,gaskiya tafiya zanyi na barku ni driver ya kaini idan ta gama shiriritar kun ta ho” momy ta faɗa tana miƙewa tsaye ta ɗauki hand bag ɗinta, tashi laatifa tayi itama tana ɗaukar hand bag ɗin ta “baza ki tafi ki barni ba momy, tare zamu tafi ita driver ya kaita “gani nan bama sai an tafi an barni ba” Balqis ta faɗa yayin da take taka stairs case tana nufo parlorn, Abaya ce a jikinta tayi rolling gyalen kamar yanda laatifa tayi tana riƙe da hand bag a hannunta fuskarta tasha uban make_up ba ƙaramin kyau tayi ba. harara momy ta watsa mata tana nufar ƙofar fita daga parlorn, murmushi Balqis ta saki yayin da ta ƙarasowa cikin parlorn, bin bayan momy su kayi,a parking space su ka sameta har ta buɗe back seat na wata ɓakar Acura ta shiga,ƙarasowa su kayi laatifa ta shiga driver seat yayin da Balqis ta buɗe front seat kusa da laatifa ta shiga, babu ɓata lokaci laatifa tayi ma motar key haɗi da reverse, cikin Estate ɗin su ka nufa tafiya su kayi mai ɗan nisa, parking space ɗin gidan dady su ka nufa, parking laatifa tayi haɗi da kashe motar, momy ta fara fitowa sannan sai Balqis, momy bata tsaya jiran su ba ta nufi main entrance ɗin villa ɗin,fitowa laatifa tayi a tare su ka jera zuwa entrance ɗin a lokacin da su ka ƙaraso har ƙofar ta buɗe alamar an basu izinin shiga. a tare su ka kutsa kai, babu kowa a parlorn sai jefi jefin ma'aikata dake kai kawo, gaishe da su su ka shiga yi cikin kulawa momy da laatifa su ka shiga amasawa yayin da Balqis ko kallon banza ba su isheta ba, glass elevator dake parlorn ta ɓangaren mom su ka nufa,laatifa ta danna nombobin dake jikin elevator ɗin,zugewa ƙofar tayi, momy ta fara shiga kafin su ka bi bayanta rufewa ƙofar tayi elevator tayi sama da su. ba su samu kowa a main parlorn mom ba hakan yasa su ka nufi ɗayan parlorn,yumnah da fa'iza su ka samu zaune a parlorn kowacce ta tasa waya a gaba sai aikin latsawa take ba su jima da dawowa daga prison ba duba jikin mahaifiyar nainarh, bakin su ɗauke da sallama su ka ƙarasa ciki, ɗagowa su kayi suna amsa masu sallamar da gudu yumnah ta taso ta nufi momy faɗawa tayi jikinta tana faɗin oyoyo, murmushi momy ta saki tana shafa bayanta. “sannu da zuwa momy, ina wuni , yanzu mom ta shiga ciki” “lafiya lau Alhmdllh ya hutu” da Alhmdllh yumnah ta amsa yayin da take raba jikin su gaishe da momy fa'iza tayi cikin kulawa momy ta amasa mata tana faɗin “yan hutu, shine har yau banga ƙafarku ba ko” sunnar dai fa'iza tayi tana sakin murmushi yumnah da sauri ta nufi laatifa buɗe mata hannuwa laatifa tayi tana sakar mata murmushi da sauri ta ƙarasa gabanta faɗawa tayi jikinta tana faɗin “nayi missing ɗinki sosai Aunty laatifa” murmushi laatifa tayi tana shafa bayanta “nima nayi missing ɗinki, ya hutu” “hutu ya kusa ƙarewa” yumnah ta faɗa yayin da suke raba jikin su, taɓe fuska Balqis tayi tana nufar ƙofar bedroom ɗin mom yayin da take faɗin “ni bari nayi ciki tunda babu wanda yayi missing ɗin na dama banyi na mutum ba” dariya gaba ɗayan su ka saki saboda sun san bakomai yasa Balqis faɗin haka sai tsabar kishi saboda babu wanda yayi mata oyoyo “Aunty Balqis ai ni mun haɗu a court shiyyasa ban yi maki oyoyo ba” yumnah ta faɗa, murmushi fa'iza ta tayi tana faɗin “ke nan dai wannan faɗan dani ake, to Allah ya huci zuciyarki ƴar uwa nayi kewarki ya ki ke” ya mutse fuska Balqis tayi tana faɗin “lafiya” dariya gaba ɗayan su suka saki ganin yanda ta amsa bayan abun da take so kenan, girgiza kai momy tayi tana nufar sofa ta zauna, ƙofar bedroom ɗin mom Balqis ta buɗe ta shiga,zama laatifa da Yumnah su kayi fa'iza itama zama tayi yayin da take gaishe da laatifa, cikin kulawa ta amsa mata, fira su ka shiga taɓawa. Mom ce ta fito hannunta riƙe dana Balqis dake sakin murmushi, da sauri laatifa ta miƙe sakin hannun Balqis mom tayi tana buɗe ma laatifa hannuwanta alamar ta zo gareta, laatifa ba tayi ƙasa a gwiwa ba ta ƙarasa ga mom ɗin, hugging ɗinta tayi fukarta ɗauke da murmushi “mom ina wuni, mun same ku lafiya” “lafiya lau agogo sarkin aiki” mom ta faɗa yayin da take raba jikin su, ɓata fuska laatifa tayi tana faɗin “mom kema haka za ki ce” dariya Balqis tayi tana faɗin “wallahi mom gaskiya ki ka faɗa Aunty laatifa bata saurarama aiki” momy na daga zaune,murmushi ta saki a ranta tana faɗin sarakai za ku fara “ai ba sai kin faɗa ba Balqis na santa ne” mom ta faɗa “shikenan mom tunda kema haka za kice” laatifa ta faɗa tana komawa mazauninta “wasa nake maki laatifa ai aiki abu ne mai kyau” murmushi laatifa ta saki jin mom wasa take mata itafa babu abun da ta tsana sama da ace mata ta cika nacema aiki. sofa da momy take zaune mom ta nufa, tashi momy tayi su kayi hugging ɗin juna kafin su ka raba jikin su fuskokin su ɗauke da murmushi, gaishe da juna su ka shiga yi cikin kulawa yayin da suke samun wurin zama su ka zauna,masu aiki fa'iza ta kira dan su kawo ma su momy abun sha ta hanyar landline ɗin kitchen. fira sosai su ka shiga yi a tsakaninsu momy na jajanta ma mom abun da ya faru da aminiyarta hajiya Asma'u,tambayar mom momy tayi ina ɗiyar hajiya Asma'u take “tunda mu ka dawo daga prison wajen mahaifiyarta ta shige ciki bata jin daɗi,yumnah je ki kira man ita” mom ta faɗa, har yumnah ta miƙe fa'iza tayi saurin tashin tana faɗin “bari na kira ta”ta faɗa tana nufar corridor da zai sada ka da bedroom ɗin yumnah, tura ƙofar bedroom ɗin tayi ta shiga bakinta ɗauke da sallama. bedroom ɗin yana da girma sosai, king size bed ne a cikin shi mai matuƙar kyau gefe da gefen shi nightstand ne mai ɗauke da bedside lamps,daga saman headboard ɗin bed ɗin ƴar rumfa ce mai haɗe da sparkling bulbs,sai ƙaton dressing mirror an cika gaban shi da body lotion da perfume masu dadda ɗan ƙamshi da tsadar gaske, tsakar ɗakin shimfiɗe yake rug carpet. daga bakin sliding door glass balls chairs ne guda biyu suna kallon juna, daga wajen door ɗin ƴar baranda ce mai ɗauke da chairs guda biyu tsakiyar su round table ne daga nan kana iya hangen cikin estate ɗin da swimming pool dake cikin garden ɗin gidan. A kwance fa'iza ta hangota saman makeken gadon ta rufe jikinta da duvet, bakin bed ɗin fa'iza ta ƙarasa pillow da take kwance ta ɗan bubbuga tana kiran sunanta, a hankali ta shiga buɗe idanuwanta da su kayi mata ɗauyi ga wani irin azabebben ciwo da kanta yake yi mata “ki tashi mom na parlor tana kiran ki”pro khaki eyes ɗinta ta sauke akan fuskar fa'iza da tayi maganar,eyes ɗin sun ɗanyi jajja jajja saboda baccin data fara ga ciwan kai. A hankali ta tashi zaune hanunta dafe da kanta, matsawa fa'iza tayi tana bata hanya dan ta samu damar saukowa, a hankali ta zuro da fararen ƙafafunta ƙasa,rober gown ce a jikinta ,rigar ta kamata ta bayyanar da surar jikinta,kanta babu ɗan kwali, water wave hair ɗinta har gadon bayanta ya sauka, gashin duk ya ɗan yamutse saboda bai samu gyara kwana biyu ba,sannu fa'iza ta shiga yi ma mata yayin da take binta da kallon ba ƙaramin tafiya da ita kyan nainarh yayi ba yarinyar ce Allah ya zuba mata kyau ko mace ƴar uwarta ta kalleta sai ta sake kallon, hijab ɗin ta dake kan bed ɗin ta ɗauka ta zura a jikinta. “muje”fa'iza ta faɗa, gaba nainarh tayi fa'iza na biye da ita, a hankali take taka ƙasa kamar zata faɗi saboda rashin ƙwarin jikinta,tunda su ka shigo parlor momy da laatifa ke bin nainarh da kallo har su ka ƙaraso ciki, wurin mom nainarh ta nufa tana faɗin mom gani, momy ta nuna mata tana faɗin “ga momyn su laatifa nan kun gaisa” sai a sannan nainarh ta kai dubanta ga momy. gaishe da ita tayi cikin kulawa momy ta amsa mata tana faɗin“ ya jikin ki naji ance ba ki jin daɗi” “da sauki Alhmdllh” ta faɗa, gaishe da laatifa tayi cikin kulawa laatifa ta amsa mata Balqis tunda su ka shigo parlorn kallo ɗaya tayi ma nainarh ta ɗauke kai “amma kin sha magani kuwa?” laatifa ta faɗa cikin nuna kulawa “A'a” nainarh ta faɗa tana nufar rug carpet zata zauna saboda wani jiri da take ji, da sauri momy ta nuna mata kusa da ita tace ta zauna. sannu su ka shiga jera mata mom na faɗin“bari idan IRFAN ya shigo ya duba ki, yumnah kira man shi a waya kice nace idan ya taso daga aiki ina son ganin shi” da to yumnah ta amsa tana ɗaukar wayar ta ta shiga contact, number Irfan ta shiga nema, dialing number tayi ringing ta shiga yi har ta katse bai ɗaga ba, sake kira tayi sai da ta kusa katsewa ta samu sa'a yayi picking,sallama tayi tana gaishe da shi babu wanda ya amsa mata daga ciki sai cewa yayi“ lafiya ki ke man irin wannan kiran?” shagwaɓe fuska yumnah tayi kamar tana a gaban shi “dama mom ce tace idan ka ta so daga aiki ka shigo gida tana son ganinka” rejecting kiran yayi kawai ba tare da yace komai ba, taɓe baki yumnah tayi. masu aiki ne su ka shigo hannun su ɗauke wooden tray, soft drinks ne da ruwa masu sanyi haɗe da glass cups, cikin parlorn su ka ƙaraso bakin su ɗuke da sallama, amsa masu sallama su kayi,ajiye tryas ɗin su kayi saman glass round table ɗin dake parlorn, ficewa su kayi, fa'iza ce ta shiga zuba masu ruwan da lemu ta miƙa masu. masu aikin suna fita daga parlorn ɗaya kitchen ta nufa yayin da ɗaya ta nufi elevator, da sauri ƴar uwarta tace“munirat ina za kije?” “part ɗin mamy ”wacce aka kira da munirat ta faɗa, girgiza kai wacce ta kira munirat ɗin tayi tana faɗin “munirat ina rabaki da kiwan kyalla kina akuya ta haihu, wallahi ki daina shishige ma mamy, dan wallahi za kiyi da kin sani dan ita ba'a mata gwaninta ina guje maki ranar da zata shuka maki rashin mutunci” “banji bakin ki ba, kuma ni bani ke shishige mata ba itace ke jana a jiki” “na dai faɗa maki dan idan baki san abun da ya faru da baaba jummai ba gara tun wuri ki sani” “ni dai naji,yanzu zan dawo” ta faɗa tana daddana madannan dake jikin elevator, girgiza kai kawai ƴar uwar tata tayi tana nufar kitchen... _*Episode 9_10*_ *Bound by fate,freed by love, A romantic Odyssey*❤💘💘 ______________________________ A kishingiɗe take saman makeken king size bed ɗinta ta ɗauki wankan rantsatsiyar shadda white color anyi mata aiki da red color ɗin zare, fuskarta tasha make_up a ko wane lokaci zaka samu hannuwanta da wuyanta da ƙafarta cikin adon gold ko zinari, kanta babu ɗan kwali gashin Attachment ɗin dake kanta ya sauka har gadon bayanta,wayarta ce a hannunta tana aikin daddanawa. Nocking ƙofar bedroom ɗin a kayi,yamutse fuska tayi cike da izza tace “waye?” ɗan ɗaga murya munirat dake tsaye bakin ƙofar tayi “munirat ce mamy” “ke da waye ne?” mamy ta faɗa “ba kowa ni kaɗai ce” “ok shigo”mamyn ta faɗa. a hankali munirat ta turo ƙofar ta shigo bakinta ɗauke da sallama,ƙaremata kallon mamy ta shiga yi tun daga sama har ƙasa, a bakin bed ɗin ta tsaya,cike da girmamawa ta durƙusa har ƙasa ta gaishe da mamy. ƙin amsa mata mamy tayi sai ma cewa tayi “ina sauraronki mi ya kawoki ɗakina?”ta faɗa tana wani yamutse fuska. “dama zuwa nayi na sanar dake hajiya maimunatu matar yallaɓai hashim ta zo ita da ƴaƴanta suna part ɗin madam zulaihart” “mi su ka zo yi”mamy ta faɗa tana wani tsuke fuska “nima ban sani ba amma ina tunanin sun zo yima madam jaje ne” jinjina kai mamy tayi“naji daɗin jin wannan labari da ki ka zo man dashi, abunda nake so dake ki sa man ido akan kowa dake part ɗin komai ki ka gani ki sanar dani, komai ƙanƙantar abu ki sanar da ni” “in sha Allah madam” jinjina kai mamy tayi“yawwa haka nake son ji, tashi ki tafi bana son janar ya shigo ya sameki, zan tura maki saƙon ki ta waya” miƙewa munirat ɗin tayi “nagode sosai Allah ya ƙara girma”ta faɗa tana nufar ƙofar fita ta fice. tsaki mamy taja tana faɗin“munafuncin banza ko miye abun zuwa jaje in ba tsabar tsugudidi ba” mamyn ta faɗa tana sake jan wani tsakin. wayarta ta ɗauka tayi dialing wata number, bugu biyu a ka yi picking, murmushi ta saki yayin da take kara wayar a kunenta. “Allah ya taimaki first lady,hutawar ki lafiya hajiyar yallaɓi Ahmad”mamy ta faɗa ta na sakin dariya,on the other hand ta cikin wayar itama dariya ta saki. “kullum da kalar tsokanar da ki ke zuwa MABARUKA, yau kuma ni ki ke ma wannan kirarin?” “ai kin can canta ne, ya ki ke ya kwana biyu?” “Alhmdllh, fatan kema kina lafiya, ina madam ɗinki take?” taɓe baki mamy tayi “tana nan kamar yanda ki ka santa,ban ma baki labari ba” “ina jinki mi ya faru?” “uhmm ina wannan shari'ar da suke akan ƙawarta wannan munafukar hajiya Asma'un?” “eh na gane ,ɗazu naji WASEEF na mata jaje wai an yankema hajiya Asma'u hukuncin ɗaurin rai da rai” “eh ashe kinji?” “naji waseef na mata jaje kin san ni ba ma'abociyar bibiyar labarai bace” “ai kuwa kamar yanda ki ka ji an yanke mata hukuncin ɗaurin rai da rai” “tab! Allah ya kyauta gaba,ki ce yau ku baku ba walwala” “bata ba walwala dai, kema kin san babu abun da zai hanani walwala dama abun da na daɗe ina jira kenan dan wallahi ba ƙaramin jin haushin Asma'un nan nake ba” dariya mai ɗan sauti ta cikin wayar ta saki “duk da haka da kinyi mata kara ai zaman tare baice haka ba” “wa ni? Allah ya ki ya ye dama ta dawo magana na samu na nannausa mata na san sai ta da ɗe tana damunta” dariya ta cikin wayar ta sake saki “gaskiya mabaruka baki da kir ki, mai makon ki taya ta ja je shine zaki ɓige da gaya mata magana” “Allah ya ki ya ye ai ga abokan cin mushenta can ɗayar har ta zo wai ja je ɗayar munafukar ma na san tana nan zuwa anjima” “baki da dama mabaruka, nima anjima ko gobe zan shigo nayi mata ja jen” taɓe baki mamy tayi“ai da yake ke akwai kara a tsakanin ku” “to ya zanyi tunda Allah ya haɗa Auratayya a tsakanin ƴaƴan mu dole ne zumunci ko bama so” “Allah ya kawo ki lafiya” da Ameen ta cikin wayar ta amsa, sallama su kayi. wata number mamy ta sake dialing, ringing wayar ta shiga yi, sai da kiran ya kusa katsewa sanann a kayi picking, murmushi mamy ta saki tana faɗin “kaga abun gidan janar, halama bacci ki ke nake kira ba'a picking in time” on the other hand ta cikin wayar tace “ina fa na shiga kitchen ne wurin masu aiki, kin san idan baka sa masu ido sai suyi maka shirme” murmushi mamy ta saki“ kice kina can kina gasa masu aya a tafin hannu dan na san halinki ba sauƙi ne dake ba” “duk rashin sauƙina na kai ki ne?” “ai wallahi masu aikin ne sai da jan ido, idan kayi sanya sai su kawo maka raini” “haka ne kam,to ya gidan, ya kwana biyu fatan kina lafiya??” “lafiya lau Alhmdllh, ya naki gidan” taɓe baki mamy tayi“ yana nan yanda ki ka san shi sai ma abunda ya ci gaba” murmushi ta cikin wayar ta saki “ki ce kina nan kin hana dangin nasara masu jan kunne sakat” “mi za'a fasa, ai in dai ina raye ta shiga uku” “Allah ya shirya man ke ƙawata, ki zo ki samu mata a har gidan mijinta ki hanata rawar gaban hantsi” “tama isa, wanda yace tayi sakacin da mijinta yayi mata kishiya” “kina sha'aninki ta wajena, wai ni kam ɗazu nake gani a TV an yanke ma ƙawarta hukuncin ɗaurin rai da rai” “eh Allah yayi maganin ɗayar munafukar saura manyan, kin san kuwa ɗayar harta kwaso ƙafa ta zo jaje??” “wa ki ke nufi?” “wacece kuwa ban da uwar ƴan tausayi maimunatu” tsaki ta cikin wayar taja “munafukan banza kawai, na san ɗayar munafukar ma tana nan zuwa” “wannan a rubuce take sai ta zo” “wallahi haushi hajiya maryam ke bani, sai girman kan masifa” “ai wallahi bake kaɗai take ba haushi ba, wani lokacin idan tana hura hanci tanama mutane kallon banza ji nake kamar na rufeta da duka” “ke dai ki bari mai abun duniyar ma batayi ji da kai ba sai ita” “za ki shigo anjima?” mamy ta faɗa “mi zan zo nayi” “ai nayi tunanin ko zaki zo mata ja je” “wa ni? Allah ya ki ya ye, lokacin da hajiya Asma'un zata kashe mijinta shawara tayi dani da zan zo mata ja je, ai in kin ganni lahira to kaini a kayi” dariya mamy ta saki “shiyyasa nake sonki ƙawata, yanzu na gama waya da hajiya SALIMA ta ce zata zo” “ita ki ka ce ji tayi zata iya” “ai kin san so akwai alaƙa mai ƙarfi a tsakanin su” “wace alaƙa?, daga ɗanta na Auren ɗiyarta shikenan ko dan IRFAN na hannun mijinta, ni ba NAEEM bane ke Auren NAFISAT, ke ni bazan iya ba alaƙar Aure ma dake tsakanin nafisat da naeem dan bani da yanda zanyi ne amma wallahi da ba'ayi Auren ba” “nima dai haka na gani” “rabu da ita kawai sai mun haɗu ranar juma'a a part ɗin Abba” “ok Allah ya kaimu” da Ameen matar ta amsa sallama su kayi. 𝑸𝒖𝒆𝒆𝒏 𝑲𝒂𝒊𝒏𝒂𝒓𝒕💫 Mom da momy ne kawai babu a parlorn, Yumah na kusa da laatifa sai zuba mata zance take yayin da balqis da fa'iza ke zaune saman sofa suna firar yaushe gamo. tashi Nainarh tayi ta nufi bedroom ɗin Yumnah,da sannu su laatifa su ka bita balqis kuwa banda binta da kallon tsana babu abunda take, haka nan taji bata son Nainarh ita kanta bata san dalili ba amma taji ta tsaneta. Sallama su ka ji daga bayan su da sauri su ka kai duban su ga matar dake shigowa, ta ɗau wanka baƙar Abaya tayi rolling da gyalenta,da gudu Yumnah ta nufeta hugging ɗinta tayi tana faɗin“momy kema ashe kina hanya” murmushi matar ta saki tana raba jikin su “wani ya zo kenan da har ki ke tunanin nima ina hanya” murmushi Yumah ta saki “momy ma ta zo tare da su Aunty laatifa” ta faɗa yayin da su ke ƙarasowa cikin parlorn, cike da girmamawa su laatifa su ka shiga gaishe da matar tana amsa masu cikin kulawa yayinda take hugging ɗin su ɗaya bayan ɗaya. “su mom na garden ita da momy” Yumnah ta faɗa “ok bari na ƙarasa wajen su” ta faɗa yayinda take nufar sliding door dake parlor wacce daga nan kana iya hangen cikin garden ɗin da kusan zagaye yake da gidan. shuke shuke ne a cikin a garden ɗin masu matuƙar ɗaukar hankali da ban sha'awa,ga grass carpet dake malale a cikin garden ɗin,ƙaton swimming pool ne a cikin garden yayinda aka ƙawata gafe da gefenshi da lounger chairs da deck chair masu kyan gashe domin zama,ducks ne ke shawagi a cikin swimming pool ɗin farare tas da su,daga can gefen swimming pool ɗin wasu rukunin bishiyu ne masu matuƙar ɗaukar hankali sunyi rukuni,peacocks ne masu kyan gaske ke yawo tsakanin bishiyun,babu kalar tsuntsun da babu a cikin garden ɗin. A tsakiyar bishiyun mom Maryam ta hango mom da momy kishingiɗe saman rug sun yi matashi da tum tum yayin da aka cika masu gaban su da fresh fruit cikin kwandon kaba haɗe da snacks da soft drinks masu sanyi. Momy ka ɗaice ta ɗan gatsi Apply yayin da mom ta zuba ma ducks ɗin dake shawagi cikin ruwa ido,damuwar halinda Aminyarta take ciki ce duk ta isheta ,bata so duniya ta juya mata baya lokaci guda ba. “ki kwantar da hankalin ki barisster in sha Allah babu abun da zai faru da Asma'u,ina sha Allah zata kuɓuta su kuma wanda su kayi silar jefata cikin wannan halin da izinin Allah asirin su zai tonu” Ajiyar zuciya mom tayi “babu abunda yafi ɗaga man hankali sama da yanda jami'an tsaro da mutanen gidan su ka kafe akan ita ta kashe shi, ni na san wacece Asma'u ko dabba bazata iya kashewa ba bare ɗan Adam” “nima a iya sani na da ita bazata iya aikata wannan babban laifin ba amma in Sha Allah gaskiya za tayi halinta” “ina fatan haka” fuskarta ɗauke da murmushi ta ƙaraso in da suke, sallamarta su ka ji daga bayan su ,da sauri su ka kai duban su gareta, murmushi su ka sakar ma juna yayinda su ka miƙewa, hugging ɗin juna su ka shiga yi cike da kulawa suke gaishe da junan su,kalar ta su gaisuwar kenan a duk lokacin da su ka haɗu da juna. saman rug ɗin su ka koma su ka zauna,sake gaisawa su kayi “ya kuma mu ka ji da abun da ya faru da Asma'u” mom Maryam ta faɗa “sai godiyar Ubangiji” momy ta faɗa “Allah ya kuɓutar da ita” “Ameen ya Allah” mom ta faɗa yayin da take ɗaukar sherry glass cup ta zuba ma mom maryam drink mai sanyi, miƙa mata tayi , murmushi mom Maryam ta saki ya yinda take amsar cup ɗin. shiru ne ya gitta a tsakanin su,kowa da abunda yake saƙawa a ranshi ba kamar mom da kwata kwata bata cikin walwala,mom maryam ce ta katse shirun na su. “amma barisster kin ɗauki wani mataki a kan shari'ar nan?” ta faɗa ya yinda take ajiye cup ɗin dake hannunta. “ban fahimci ya ki ke nufi ba ,wane mataki zan ɗauka??” mom ta faɗa cikin rashin fahimtar Abun da mom maryam ɗin take nufi. “ai nayi tunanin zaki sa ayi maki bincike na daban akan case ɗin,idan Allah yasa aka dace kinga ba sai a tada shari'ar ba tunda hukuncin ɗaurin rai da rai ne” “wane bincike zan sa ayi bayan wanda barisster Hashim yayi” yana yin fuskar mom maryam me ya canza “uhmm barisster hashim fa ki ka ce?” “eh shine lawyer dangin marigayi ,duk wani bincike da ya kamata ayi yayi” “kenan kin yarda ita ta kashe mijinata?” “A'a sai dai na san barisster ba zai faɗi abunda ba shikenan ba, kuma bana zargin zai haɗa kai da kowa dan kawai yayi nasara a kaina” girgiza kai mom maryam tayi,mom Maimunatu na kallon su ƙala ba tace ba “am sorry hajiya Maimunatu ba wai ina zargin barisster ba ne” murmushi kawai mom Maimunatu tayi ko zargin barisster su ke ya za tayi halin mijin nata ne dole a zargeshi. “mu duka mun san cewa barisster baya ƙaunar zulaihart tun fil'azal, ni bana zargin zai iya haɗa kai da wasu dan dai kawai ya cika burin shi akan barisster,amma ƙara binciken da za kiyi yanada matuƙar amfani ni a nawa tunanin amma ya ku ka gani” shiru mom tayi tana tsunduma duniyar tunani ta wani ɓan garen hajiya maryam na da gaskiya sai dai bata son ta binciko ma kanta abunda zai hanata zaman lafiya duk da har zuciyarta bata zargin Aminyarta zata aikata laifi makamancin haka. “maganarki gaskiya ce hajiya maryam,ƙara binciken yanada amfani,sai dai waye zaiyi binciken?” mom Maimunatu ta faɗa “haka ne ƙara binciken yanada amfani, Allah yasa ya zama sanadiyyar tonuwar asirin duk wanda ke da sa hannu,sai dai ta maganar Maimunatu wa zan sa yayi man binciken?” mom ta faɗa “yawwa burina dama ku fahimce ni, maganar kuma wanda zaiyi binciken ba matsala bace karku manta gidan nan cike yake da jami'an tsaro kala kala samun wanda zaiyi bincike ba abun bane mai wahala NAEEM ma zai iya tunda dama aikin shi ne” jinjina kai su kayi da alama sun aminta da maganar mom maryam “shikenan zan samu lokaci mu zauna da shi,zanyi mashi bayanin yanda case ɗin yake” mom ta faɗa “yawwa hakan yayi ,sai dai fa ya zamana cikin sirri zaiyi shi, kuma kar ya sanar a wajen aikin su yayi shi parsonal,duk da na san aikin su dama na sirri ne sai dai wannan ya ɗauke shi a matsayin na gida bana aiki ba” mom maryam ta faɗa “in dai wannan ne ba matsala”a cewar mom , murmushi mom Maimunatu ta saki “shiyyasa nake sonki hajiya maryam akwai kawo shawara mai ɓullewa” murmushi su ka saki gaba ɗayan su “abun ne wallahi ya taɓa zuciyata,baiwar Allah nan babu ruwanta amma ace lokaci guda wani ya dabaibayeta da sharri,su barta mana taji da zaluncin kashe mata miji da su kayi mana ba sai sun manna mata kisan a kanta ba” “gaskiya ko waye ba ƙaramin cutar da ita yayi ba” firar su suka shigayi suna alhinin abunda ya faru da ƙawar mom. 𝑸𝒖𝒆𝒆𝒏 𝑲𝒂𝒊𝒏𝒂𝒓𝒕💫 A tsaye take a gaba motar ta ƙirar honda Black color, blue black ɗin Abaya ce a jikinta ta yafa gyalen saman kanta,hand bag ɗinta ce riƙe a hannunta,cikin faɗa faɗa take faɗin “Enaaya wai zaki fito ne ko sai nayi tafiyata?” daga cikin motar naji Muryar yar ƙaramar yarinya tana faɗin “momy gani nan fitowa hand bag ɗina zan ɗauka” tsaki matar taja “ko uwar mi za kiyi da hand bag,ni kinga tafiyata idan kin gama kilibibin naki kya shigo” matar ta faɗa tana nufar entrance ɗin gidan. da sauri wata ƴar ƙaramar yarinyar ta fito, Black ɗin abaya ce a jikinta tayi rolling da gyalen, simple make_up ne a fuskarta yayin da kyawawan idanunta ke manne da ɗan sunglasses dai dai idonta mai butterfly,ƴar hand bag ɗinta ce riƙe a hannunta,highills ne a ƙafarta ba ƙaramin kyau tayi ba. bayan mahaifiyarta ta tabi tana wani tako ɗai ɗai kamar wata uwar mata,a main parlor part ɗin ta samu mahaifiyarta tana jiranta,glass elevator dake part ɗin mom yarinyar ta nufa da sauri mahaifiyarta ta tace. “ENAAYA ina kuma za kije?” ya mutse fuska yarinyar tayi tana faɗin “part ɗin mom mana”ta faɗa cike da yanga “muje mu fara gaishe da mamy tukun” mahaifiyar ta faɗa tana nufar part ɗin mamy,juyawa yarinyar tayi tana faɗin “ni gaskiya bazanje part ɗin mamy ba,haka nan kawai ta rufe mutum da faɗa ba abunda yayi mata,kuma Ni dady nake son nunama wannan kwalliyar dan karma sister ta rigani,sai kin dawo kawai momy ” yarinyar ta faɗa tana nufar elevator part ɗin mom. girgiza kai kawai mahaifiyarta ta tayi tana faɗin “Allah ya shirya ki Enaaya” A parlor ta samu mamy zaune saman sofa kayan ɗazu ne a jikinta,bakinta ɗauke da sallama ta ƙarasa ciki. fuskar mamy da fara'a ta amsa mata sallamar tana sannu da zuwa,wuri ta samu saman sofa ta zauna. “in wuni mamy, ya gida” “lafiya lau NADIYA, ya gida?” “lafiya lau” “masha Allah,Ina uwayen sanabe ko ana islamiyya?” murmushi nadiya ta saki tana faɗin“A'a ta shiga part ɗin mom ne” jinjina kai mamy tayi tana maimaita kalmar part ɗin mom. “watau ni tafi ƙarfin ta zo ta gaishe ni,shine ta wuce wajen ƙanwar uwarta, tunda ban haifi mahaifinta ba ai ba tazo ta gaishe ni ba,zata zo ta sameni ne” murmushi kawai Aunty nadiya tayi dafa gaskiyar enaaya mamy ba dai faɗa ba. “tana nan zata shigo,na san duk saurin ta haɗu da dady ne” “A'a tayi zamanta kawai ba sai ta zo ba” “kiyi haƙuri mamy idan ranki ya ɓaci” uhmm kawai mamy tace mata ba tare da ta sake cewa komai ba. sallama su ka ji daga bayan su ,Aunty nadiya ce kawai ta kai dubanta ga mai shigowa,riga da skirt na atamafa ne a jikinta ta yafa mayafi tun daga kanta fuskarta tasha make_up,manyan idanunta sun sha eyelashes na company, hand bag ɗinta ce riƙe a hannunta yayinda yaranta ke biye a bayanta mace da namiji ,namijin ya ɗau wankan jeans and t_shirt,hannuwan shi zube su ke cikin aljihun wandon shi kamar wani babban mutum, fuskar nan tashi a ɗaure take, ƴar macen ce ke sanye da Pakistan dress riga da wando ta yafa mayafin kayan saman kafaɗar ta, anyi mata parking gashinta a tsakiyar kai,light make_up ne a fuskarta,ƙafarta sanye take cikin wedge shoe masu kyan gaske, itama sunglasses ne a fuskarta mai butterfly kamar Enaaya. da sauri Aunty nadiya ta miƙe fuskarta ɗauke da murmushi ta nufi matar dake shigowa, hugging ɗin juna su kayi,gaba ɗayan su suna sakin murmushi. “sister NAFISAT shine baki faɗa man kuna tafe ba ai dana jira ku” Aunty nadiya ta faɗa yayinda su ke raba jikinsu daga na juna. “uhmm ki bari kawai nima ban san da fitar ba, ina zaune ya NAEEM yace wai mu zo,Ni ban ma san mi ke faruwa ba” ta faɗa tana ɗan ya mutse fuska. “tare ku ke dashi ne?” “eh ajiye mu yayi yaje ya dawo” zuba masu ido mamy dake zaune tayi tana kallon su,wurin mamy Aunty nafisat ta nufa, gaishe da ita tayi cikin girmamawa,mamy da fara'ar ta ta amsa mata,suma yaran gaishe da mamy da Aunty nadiya su kayi,taɓe baki mamy tayi “miskili kafi mahaukaci ban haushi,yau kuma aljanun sun bari a zo a gaishe ni kenan?” ɗan taɓe baki Aunty nafisat tayi tana dallama yaron harara da duk ya wani ɓata fuska shi dole an sa shi abunda baiyi niyya ba,da sauri ya kalli gefe ganin kallon da mahaifiyar tashi tayi mashi,tsaki taja. “momy nadiya wai ina Enaaya ne?” ƴar macen ta faɗa “tana part ɗin mom” ko gama faɗa nadiya ba tayi ba ta juya da sauri ta nufi ƙofar fita,bin bayanta namijin yayi, da sauri Aunty nafisat ta daka mashi tsawa “ina za ka ,ko kaima Enaayar ƙawarka ce?” “ai wajen Aunty Yumnah zan je” ya faɗa yana ficewa daga parlor ba tare da ya tsaya jin mi Aunty nafisat ɗin za tace,jinjina kai Aunty nafisat tayi. “wai shi mi a kayi mashi yake wannan kumbura fuskar?” mamy ta tambaya “saboda nace sai mun fara shigowa nan shi baiyi niyyaba shine yake wannan cin ɗacin” “kaga ƴan bantan uban yara sun raina ni,sai kace wata uwar nake masu da ba sa son zuwa in da nake” “iskanci ne kawai irin na su” a cewar Aunty nadiya “zanyi maganin su ɗaya bayan ɗaya ne”mamy ta faɗa. canza fira su kayi,su Aunty nafisat Nama mamy jajen abunda ya faru da mom,taɓe baki kawai mamy tayi ba tare da ta ce masu komai ba. 𝑸𝒖𝒆𝒆𝒏 𝑲𝒂𝒊𝒏𝒂𝒓𝒕💫 ƙarar takun takalminta ne ya cika masu kunne,da sauri su ka kai duban su gaba bakin ƙofa,mamaki ne gaba ɗaya ya cika su,dariya fa'iza ta saki tana faɗin “ƙamshi duk ya cika mana hanci kace uwayen mata ne a hanya” tsayawa Enaaya tayi tana wani tsuke baki “kar wanda yasa ran zanyi mashi oyoyo,saboda wannan kwalliyar ta dady ce” ta faɗa tana wani yi masu fari da ido ta cikin glass, murmushi su saki “yanzu baby Enaaya ko ni baza kiyi ma oyoyo ba” Yumnah ta faɗa tana wani marairaice fuska. “gaskiya yau sai dai kiyi haƙuri Aunty Yumnah kwalliyar nan ta dady ce,ki bari idan na dawo daga wurin shi nayi maki oyoyo” tsuke fuska yumnah tayi tana riƙe ƙugu“ai kuwa bana so” “shikenan tunda so ki ke su Aunty balqis suyi mana dariya” Enaaya ta faɗa tana nufar stairs case dake hannun daman parlor,tana tafiya tana wani jujjuya jiki. murmushi kawai balqis tayi tana faɗin “manyan mata sun hallara kowa yayi ta kansa” dariya su ka kwashe gaba ɗayan su. *KITCHEN* Gaba ɗaya masu aikin gidan suna kitchen domin lokacin fara aikin dinner yayi,a hankali take tafiya dan karma taji ƙarar takalminta alama tayi ma masu aikin dake ciki da kar suyi magana,da gudu ta nufi Eishrat dake tsaye gaban fridge tana jera drinks,kamar daga sama taji mutum ya faɗa saman bayanta, ƙara ta saki tana jefar da lemun dake hannunta,dariya ta fashe da ita. “gaskiya chef Ishrat kin cika tsoro” ajiyar zuciya Ishrat ta sauke dan ba ƙaramin tsorata tayi ba saboda bata san da shigowar ta ba sai dai kawai tajita a jikinta. tsuke fuska Eishrat tayi tana “amma baby Aneesah kin raina ni da yawa” dariya Aneesah ta kwashe da ita “ba wani kin dai cika tsoro ne” “to naji,saukar yaushe?” yamutse fuska Aneesah tayi “yanzu muka zo da momy fatan kin ajiye man Alƙawari na?” yana yin fuskar Eishrat ne ya sauya “Ayyah! baby Aneesah ban san za kizo yau ba” ɓata fuska Aneesah tayi “chef Eishrat na fa sanar dake jiya, ko kin manta na kiraki da landline ɗin kitchen?” Aneesah ta faɗa tana tsuke baki “sorry baby Aneesah mantawa na yi,amma yanzu zan haɗa maki” ɓata fuska Aneesah tayi “har dady ya fita baki kammala haɗa man ba” murmushi Ishrat ta saki “wasa nake maki baby, tunda ki ka sanar da ni zuwan ku na haɗa maki” da sauri Aneesah ta dafe saitin zuciyarta tana wani lumshe ido “wai Allah! har kin sa hankali na ya kwanta,da yau kin sa sister Enaaya tayi man dariya, duk wannan saurin da nake dan kar ta rigani ba dady wani abu” “Ayyah sorry,na san ta rigaki dan tun ɗazu tana part ɗin shi” yamutse fuska Aneesah tayi “ita komai nata cikin sauri take yin shi,ai na san duk abun da zata bashi bazai kai wanda zan kai mashi ba” “nima ina fatan haka, bari na shirya maki komai” Ishrat ta faɗa. ƙaton wooden tray Ishrat ta ɗauka, fridge ta buɗe fruit salad ta ɗauko a cikin bowl sannan ta ɗauko yogurt daga gani haɗin gida ne mara zaƙi da lemun wanda shima haɗashi tayi da kanta sai chocolate cake. Murmushi Aneesah ta saki ganin abun da tafi buƙata,dish rag ta nufa cups ta ɗauko da fork guda biyu ta ɗaura saman tray,ficewa su kayi daga KITCHEN ɗin Aneesah na gaba yayin da Ishrat ɗin ke biye da ita. bakin su ɗauke da sallama su ka shiga cikin parlor,su Yumnah na nan zaune kamar yanda Enaaya ta barsu,Jamal na kwance saman sofa yayi pillow da laps ɗin Yumnah. murmushi su ka saki yayin da su ke amsa sallamar da su kayi,sama Aneesah ta nufa ba tare da tace ma kowa ƙala ba suma binta su kayi da ido dan sun san ba lallai ta tanka masu ba tana sauri taje wurin dady. bin bayanta Ishrat tayi ,dariya fa'iza ta saki tana faɗin “yan bantan uban yara kowa zai haƙura ya barma wani dadyn a cikin su?” “rabu da ƴan ƙwal uba sun gama iskancin su su barma su mom majin su,yara sai kilibibin masifa” a cewar Balqis, murmushi laatifa ta saki “kar kuga laifin su,kuma da kune a matsayin su na san sai kunyi abun da yafi nasu” “haba Aunty laatifa mu mi yasa ba mu yima Abbah haka” “babu face ne shiyyasa” murmushi kawai su kayi ba tare da sun ce komai ba. A kishingiɗe yake saman rug carpet dake katafaren parlon shi, ya ɗaura kanshi saman tum tum yayin da Enaaya ke gefenshi ,cike da salo da kisisina take bashi labarin school ɗin su,ya ƙafeta da ido sai sakin murmushi yake. sallamar Aneesah da Ishrat ce ta katse masu firar da su ke, waro ido waje Enaaya tayi yayinda take miƙewa tsaye “wayyo Allah nah!, sister Aneesah dama za ki zo” Enaaya ta faɗa tana yarfe hannu murmushi Aneesah ta saki tana ƙarasowa ciki, da sauri Enaaya ta nufeta, hugging ɗin juna su kayi sai sakin murmushi su ke,raba jikin su su kayi. gaishe da junansu su ka shiga yi kamar wasu manyan mutane, Ishrat da dady ban da sakin murmushi babu abun da su ke. cikin parlor Ishrat ta ƙarasa a gaban dady ta ajiye tray “barka da hutawa dady” murmushi dadyn ya saki “lafiya lau Ishrat,sannu da ƙoƙari” murmushi kawai Ishrat ɗin ta saki tana nufar ƙofar fita “thank u” Aneesah ta faɗa, alamar jinjina Ishrat ɗin tayi mata tana ficewa daga parlorn. wurin dady Aneesah ta ƙaraso tana sakar mashi murmushi haɗi da fari da idanu, murmushi kawai dadyn ya saki yana girgiza kai lamarin su Aneesah na matuƙar bashi mamaki. a saman rug ɗin su ka zauna, gaishe da dady Aneesah tayi yayinda take zuba mashi lemu a cup,cikin kulawa dady ya amsa gaisuwar yayin da yake ƙarɓar cup ɗin lemun da take miƙa mashi. a tare su ka shiga cin chocolate cake ɗin banda dady saboda ciwan sugar fira su ka shiga zuba mashi yan sauraron su. Aunty nafisat sun jima a part ɗin mamy kafin su ka shigo part ɗin mom lokacin har su mom Maryam sun tafi ya rage saura fa'iza da Yumnah kawai, nainarh har time ɗin tana kwance a bedroom ɗin Yumnah. bedroom ɗin mom su ka shiga a zaune su ka sameta bakin bed ɗinta tunda su mom Maryam su ka tafi take a nan zaune. cike da girmamawa su ka shiga gaishe da ita tana amsa masu cikin kulawa,sosai su ka nuna alhinin su kan abunda ya faru da ƙawar mom ɗin. tambayar su Aneesah mom tayi dan tun ɗazu suna part ɗin dady ba su fito ba, murmushi kawai tayi ko da su ka sanar da ita suna can. fira su ka shiga taɓawa sama sama har aka fara kiran sallar magrib, bedroom ɗin Yumnah su ka nufa domin yin sallah,sunyi mamakin ganin nainarh dan basu san da zamanta a gidan ba,kasa haƙuri Aunty nafisat tayi har sai da ta tambayi Yumnah wacece,faɗa mata ko wacece Yumnah tayi. taɓe baki kawai Aunty nafisat ɗin tayi Aunty Nadiya kuwa ko kallon in da su ke ba tayi ba tana sallame sallah ta fice daga ɗakin zuwa na mom, anan ta samu Aneesah da Enaaya sai zubama mom fira su ke Jamal na gafen su zaune. Aunty nafisat ma data gama sallah bedroom ɗin mom ta koma,ko da lokacin sallar isha yayi a nan su kayi ta,suna zaune saman carpet sallame sallar su kenan a kayi nocking ƙofar bedroom ɗin. da sauri Enaaya taje ta buɗe, a tsaye suke su biyu ɗaya suit ne a jikinshi yayin da ɗayan ke sanye da Army trouser da white ɗin shirt. Kamannin fuskar su ka ɗai zai tabbatar maka da su ɗin jinin dady da mom ne ba kamar mai Army trouser ɗin. Da gudu Enaaya ta faɗa saman jikin mai Army trouser ɗin wando tana faɗin “oyoyo dady NAEEM ashe da rabon mu gana yau” dariya su ka saki gaba ɗayan su “ai kuwa da rabon mu gana, ya school?” ya faɗa yayinda yake raba jikinsu “Alhmdllh dady NAEEM,wai ina ka shige kwana biyu bana ganin ka?” “aiki ne ya yi man yawa baby Enaaya,kuma ma ai idan kina son gani na kin san in da zaki same ni” ɗan zaro ido tayi tana kallon wanda ke kusa dashi “wannan maganar tafi karfina dady NAEEM,ga dady nah nan ka tambaye shi” ta faɗa tana komawa cikin ɗakin da gudu. murmushi kawai su ka saki ya NAEEM na faɗin “kenan dai ADNAN kai ke hanata zuwa gida na?” ya faɗa yana ɗan tsuke fuska. “haba SECOND FATHER sai ka ce baka san sharrin Enaaya ba,ni ƙarya take man” cikin ɗakin su ka ƙarasa ya NAEEM na faɗin “yanzu dai maganar wa zan kama tsakanin ku?” “tawa mana dady NAEEM” Enaaya ta faɗa tana wani marmar da ido. da sauri ya NAEEM yasa hannu yana toshe bakin shi haɗi da ɗan zaro ido kamar yanda Enaaya tayi ɗazu, girgiza mashi kai ta shiga yi alamar kar ya faɗa tana zare ido. dariya gaba ɗayan su suka sa dan sun san saboda mi ya NAEEM yayi mata haka watau dadyn ta ƙarya yake. da gudu Aneesah ta faɗa jikin ya ADNAN tana mashi oyoyo, Jamal ma nufo su yayi,Barka da zuwa yayi masu yana koma bakin bed daya ta so. gaishe da ya NAEEM Aunty Nadiya tayi tanama ya ADNAN sannu da dawowa,hakama Aunty nafisat gaishe da su tayi. ta shi su kayi su ka fice daga ɗakin ya zama daga mom sai su ya NAEEM ɗin,a gabanta su ka zo su ka zauna ƙasa suna tanƙwashe gwiwowin su kamar masu neman gafara. cikin girmamawa su ka shiga gaishe da ita tana amsa masu cike da kulawa. “ya aiki” ta tambaye su da Alhmdllh su ka amsa mata haɗi da jajanta mata abun da ya faru. “in sha Allah gaskiya za tayi halinta” ya Adnan ya faɗa, da Ameen su ka amsa. sun ɗan jima suna fira kafin su ka tashi zuwa part ɗin dady dan su gaishe da shi,har sun kai bakin ƙofa mom tace ma ya NAEEM tana son magana dashi gobe idan ya dawo aiki ya zo ya sameta,da to ya amsa mata, ficewa su kayi zuwa part ɗin dady. su Aunty Nadiya na zaune parlorn Ishrat ta shigo ta sanar da su an kammala dinner. “sannunki da ƙoƙari Ishrat” fa'iza ta faɗa, murmushi Ishrat ɗin ta saki tana barin parlorn. a dinning room su ka hallara saman makeken dinning table mai mazaunin mutum shabiyu, Aneesah da Enaaya sun sa dady a tsakiya, Nainarh ka ɗaice babu, itama ba bu yanda Yumnah ba tayi da ita ba a kan ta fito suyi dinner amma taƙi sai dai aka kai mata nata can,tsit ka ke ji sai ƙarar spoon da plate dake tashi kowa na ba ciki haƙƙin sa. hakan ya ba dady damar kafe su da ido yana kallon su cike da Alfaharin yanzu duk shi ke da wannan danma wasu basa nan,yana yin fuskarshi ne ya canza da alama ya tuna da wani abun,hawaye ne su ka taru a idanuwan shi saurin goge su yayi yana kawar da tunanin a ranshi. sai wurin ƙarfe goma na dare su ya NAEEM su ka bar gidan,har part ɗin mamy Aunty Nadiya da Aunty nafisat su ka shiga yi mata bankwana harda su ya NAEEM amma ban da su Enaaya dan cewa su kayi basa zuwa da iyayen su ka matsa masu sai ficewa su kayi daga gidan da gudu. murmushi kawai fa'iza da Yumnah su ka saki suna bin bayan su Aneesarh. cikin girmamawa su ya NAEEM su ka gaishe da ita amma sai ta amsa masu tana wani ya mutse fuska,hakan bai dame su ba idan da sabo ai sun saba. ba su zauna ba su ka fice a parking space su ka samu su Enaaya tare da su fa'iza,sallama su kayi ma junan su su ka nufi motocin su yayin da fa'iza da yumnah su ka koma ciki, barin gidan su kayi zuwa na su gidajen dake cikin Estate ɗin... _*Ep11_12*_ *Bound by fate,freed by love, A romantic Odyssey*❤💘💘 _____________________________ A main parlor fa'iza da Yumnah su kayi sallama fa'iza ta nufi part ɗin mamy yayin da Yumnah ta nufi na su part ɗin. direct ɗakinta ta nufa, a hankali ta tura ƙofar bakinta ɗauke da sallama, a tsaye ta hango Nainarh bakin sliding door ɗin dake cikin ɗakin ta zubama cikin estate ɗin da yake ƙwanyar da haske kamar rana ido, jefi jefi take hange motoci na kai kawo a cikin Estate ɗin. A zahiri kallon cikin Estate ɗin take a ɓaɗi kuwa hankalinta na can prison wajen mahaifiyarta, ko a wane hali take, wasu irin zafafan hawayen su ka wanke fuskarta lokacin data tuna irin kisan wulaƙancin da a kayi ma mahaifinta. Sosai take zubar da ƙwalla kwata kwata ko sallamar Yumnah ba taji ba, bakin door ɗin Yumnah ta ƙaraso, a hankali ta kira sunan Nainarh amma bata amsa mata ba saboda hankalinta da baya tare da ita, dafa kafaɗarta Yumnah tayi, da sauri ta kai dubanta ga Yumnah. “nainarh dan Allah ki daina sa damuwa a ranki, komai zai wuce” da sauri Nainarh ta faɗa jikin Yumnah tana sakin kuka mai sauti,jikin Yumnah ne yayi sanyi, wani irin tausayin Nainarh ne ya rufeta musamman yanda taji jikin Nainarh ya ɗauki zafi. ɗan bubbuga bayanta ta shiga yi tana lallashin ta. “nainarh dan Allah ki daina sa damuwa a ranki, komai zai wuce, ki daina kuka dan Allah,naji ma jikin naki ya ɗau zafi gashi ya Irfan ɗin baizo ba,amma bari naje medical room na samo maki maganin zazzaɓi kafin zuwa gobe” Yumnah ta faɗa yayin da take raba jikin su,jan hannun Nainarh tayi zuwa ottoman chair dake bakin bed. “ki zauna bari na kawo maki magani, naga ma ko dinner ɗinki ba ki ci ba” Yumnah ta faɗa tana kallon dinner ɗin da Ishrat ta kawo mata. cikin dasashiyar muryarta tace “bana jin yunwa ne” girgiza kai Yumnah tayi “bazai yuwu ba, idan baki son wannan ne na kawo maki wani, amma zama da yunwa ba masalaha bace” “na ƙoshi ne Yumnah, bazan iya cin komai ba” “dole kisa wani abu a cikin ki” Yumnah ta faɗa tana kwashe kayan abincin da aka kawo mata tana nufar ƙofar fita ta fice daga ɗakin, kitchen ta fara nufa ta ajiye trayn kafin ta fice. Ƙaton medical room ɗin su ta shiga babu abun da babu a cikin shi,komai da mara lafiya zai buƙata a kwashi a ciki,girmanshi zai kai clinic. glass drawer dake ɗauke da nau'in magunguna ta nufa,side ɗin da magungunan zazzaɓi dana ciwan kai ta buɗi maganin zazzaɓi dana ciwan kai ta ɗauko mata, mai da ƙofar tayi ta rufe, ƙofar fita ta nufa light ɗin ɗakin ta kashe haɗi da ficewa. da mom taci karo zata part ɗin dady hannunta riƙe da tea cup wanda ta haɗa ma dady herbal tea. “ke kuma daga ina?” mom ta faɗa, in da take ta ƙaraso. “magani na ɗauko ma Nainarh” “ya Allah!, kinga shaf namanta IRFAN ɗin bai zo ba, gashi yanzu dare yayi da na sa dr lelah ya dubata, jikin nata yayi zafi ne sosai?” “A'a da sauƙi, damuwace tayi mata yawa” “dole damuwa tayi mata yawa, yanzu tafi da maganin ki bata” mom ta faɗa tana nufar part ɗin dady. Kitchen Yumnah ta nufa,hot milk da coffee ta haɗa mata,saman ɗan madaidaicin tray ta ɗaura da maganin,ruwa ta ɗauko mata cikin fridge, ɗaukar trayn tayi ta ficewa zuwa bedroom ɗinta. kamar yanda ta barta haka ta same ta zaune,ku sa da ita ta zo ta ajiye mata tryan, ɗaya daga cikin chairs ɗin dake ajiye bakin sliding door dake ɗakin ta jawo,zama tayi tana tasa Nainarh gaba. “gashinan ki sha ko ɗaya daga cikin su ne sai kisha magani”ruwa ta ɗauka da nufin su zata sha,da sauri Yumnah ta girgiza mata kai. “kar muyi haka dake Nainarh,ki daure kisha hot milk ɗin nan ko da baki sha coffee ba” jinjina mata kai tayi tana ajiye ruwan data ɗauka ta ɗauki milk ɗin ta kafa a baki,da kyar tasha rabin cup ɗin shima Nainarh ta tursasata har ta sha kamar haka. yumnah da kanta ta shiga miƙa mata maganin tana sha,bayan data kammala tashi tayi ta kai kayan kitchen. Toilet Nainarh ta shiga,ruwa ta watsa dan taji daɗin jikinta,tana fitowa Yumnah na shiga,wata ƙofa ta nufa,tanƙamemiyar glass drawer ce gari guda,daga waje kana hangen cikinta shaƙe take da sutura kala kala,kowace sutura wajenta daban. ɓangaren pajamas ta buɗe tsaye tayi tana kallon kayan har Yumnah ta shigo, girgiza kai tayi yayinda take ƙarasowa ciki. “please Nainarh ki riƙa abu da hanzari,yanzu ɗauko kayan ne ki ka ɗauki lokaci haka” da kallo kawai Nainarh ta bita har ta ɗauko ma su kayan da zasu sa,riga da wando na saƙa farare ta miƙa mata saboda zazzaɓin da take ne yasa ta ɗauko mata su. fita Nainarh tayi daga ɗakin,ƴar gown ɗin data ɗauko ta zura a jikinta,baby bant tasa ta ɗauke kanta,ficewa tayi daga ɗakin,samun Nainarh tayi har ta kwanta,itama bed ɗin ta nufa, laptop ɗinta dake ajiye saman night stand ta ɗauka,opreting ɗinta ta shiga yi, video call ne ya shigo ta laptop ɗin. murmushi ta saki tana faɗin “yanzu nake shirin kiran ka saiga kiran naka” picking call ɗin tayi, a shagwaɓe tace “hey” tana yarfa yatsun hannunta irin na gayu. Yana daga zaune saman Leather chair,da alama a office yake, Army shirt ce a jikinshi haɗe da trouser ɗinta,sosai rigar tabi shape ɗin broad chest ɗinsa ta bayyanar da strong arms ɗinsa,kallo ɗaya za kayi mashi ka tabbatar da jinshi turawa ne,kyakkyawa ne na gaske,hancinshi a tsaye yake ƙem, blue eyes ɗin shi sai ɗaukar ido su ke, kwantaccen sajenshi baƙi wul sai sheƙi yake,sumar kanshi ta sauka har saman neck ɗinshi,daga yanayin zanen tattoo ɗin dake saman neck ɗin shi da ear ring mai alamar Cross ɗin dake a ƙunnanshi zai tabbatar maka da Addinin shi. ƙayataccen murmushi ya sakar mata wanda ya ƙara bayyanar da kyawun fuskarshi yana maida mata martanin sallamar da tayi mashi, a shagwaɓe cikin harshen nasara tace “mi yasa baka kirani ba duk yau?” in a cool voice yace“Am sorry, yayan ki ne yau duk yabi ya takura man” murmushi ta saki “ko dai ka takura mashi,kai ma fa na san..” murmushi ta saki ba tare data ƙarasa ba,wani irin killer smile ya sakar mata,shagwaɓe mashi fuska tayi kamar za tayi kuka. cikin shauƙin soyayya su ke waya Nainarh na daga kwance tana sauraronta sama sama kafin bacci yayi awan gaba da ita. Yumnah ba itace ta gama waya ba sai wajen ƙarfe uku na dare, kusan kullum haka take ɓata lokaci suna waya saboda shi lokacin ne ya ke samun sararin kiranta saboda banbancin lokaci dake tsakanin ƙasashen guda biyu. *WASHE GARI* Alhmdllh jikin Nainarh zazzaɓin ya sauka sai ciwan kai da take fama dashi har lokacin gashi har time ɗin Irfan bai zo ba. kwance take saman bed ita ka ɗai a ɗakin,babu yanda Yumnah ba tayi da ita ba ta zo su fita tayi breakfast tare da su amma taƙi sai dai a kawo mata a ɗaki. turo ƙofar ɗakin a kayi aka shigo, Yumnah ce ta shigo jikinta sanye da riga da wando masu taushi peach color ta yafa farin mayafin a saman kanta. cikin ɗakin ta ƙaraso “ki tashi ki shirya mom tace mu tafi hospital Dr Faawar ya dubaki tunda ya Irfan bai zo ba” yumnah ta faɗa yayinda take nufar toilet,tashi Nainarh tayi tana bin bayanta da ido,bata motsa daga inda take ba har Yumnah ta fito sanye da bathrobe. “tashi ki shiga” Yumnah ta faɗa,sauka Nainarh tayi daga saman bed ɗin toilet ɗin ta nufa “ki fa yi sauri kar mom tace tare da wani za ku tafi ko ya Irfan ya shigo” Dressing room ta nufa,shaf shaf ta shiga shiryawa duk tana wannan saurin ne dan kar wani abu yasa a fasa fitar ko Irfan ɗin ya shigo dan da ƙyar ta samu mom ta amince akan za su je hospital ɗin dan cewa tayi kawai su tafi clinic ɗin dake cikin Estate ɗin ko ta kira dr Faawar ɗin ya zo har gida ya duba Nainarh. Nocking taji anyi,da sauri ta ƙarasa zura rigar data fara sawa,ficewa tayi zuwa cikin bedroom ɗin har time ɗin Nainarh bata fito ba,ƙofar ta nufa tana faɗin waye. shiru taji wanda ke Nocking bai Bata amsa ba ba'a kuma fasa Nocking ɗin ba,buɗe ƙofar tayi da ɗan faɗa faɗa tace “wai waye ke neman fasa ma mutane kunne da noc.......” bata ƙarasa ba ganin wanda ke tsaye,wani kyakkyawan matashi saurayi ne tsaye yana sanye da wandon suit a jikinshi tare da shirt long sleeve mai maɓallai gaba,hannunshi riƙe da briefcase ɗin shi tare da rigar suit ɗin da bai sa ba. tun daga ƙafafunshi dake sanye cikin leather shoes masu masifar kyau ta shiga kallo ,dogo ne ɗan dai dai fatar jikinshi fara ce tas,yanada broad chest Dan tana iya hangen six pack ɗin shi saboda maɓallan rigar da bai sa duka ba ,hancinshi a tsaye yake ƙem ga wasu idanuwa masu matuƙar jan hankali farare tas da su,launin ƙwayar idonshi ash color ce, pink lips ɗin shi ba ƙaramin ɗaukar ido su ke ba,yanada tsayin fuska ga wani kalar kwantaccen saje sai sheƙi yake,kwantacciyar sumar kanshi har saman neck ɗin shi ta sauka, fuskar shi a ɗaure take kamar wanda aka aiko ma saƙon mutuwa. Tsuke fuska ya sake yi ganin irin kallon da take binshi da shi “ya Irfan kai ne!!?” Yumnah ta faɗa “ban sani ba,zaki ban hanya na wuce ko sai kin gama kallon nawa?” da sauri ta matsa mashi,wani wawan tsaki yaja yana kunna kai zuwa ciki. A tsakiyar ɗakin ya tsaya “ina yarinyar take?” “tana toilet” ta bashi amsa,tsaki yaja yana juyawa ya nufi ƙofa “idan ta fito ina parlorn mom ku same ni a can” har ya kai bakin ƙofa Nainarh ta turo ƙofar toilet ɗin ta fito ɗaure da towel iya gwiwarta ta saki sumar kanta har gadon bayanta. “yawwa gata nan ma ta fito” Yumnah ta faɗa,sai a lokacin Nainarh ta lura da mutum a tsaye,juyowa yayi karab idanunsu suka shiga cikin na juna,tun daga kan santala santalan cinyoyinta farare ya fara kallo har izuwa kan pro khaki eyes ɗinta,kafe juna da ido su kayi kamar sun samu TV Yumnah na daga tsaye tana kallon ikon Allah. Nainarh ce ta fara janye ido ta gabanta na wani irin faɗuwa,ƙaton namiji a gabanta gashi daga ita sai towel,da sauri ta nufi dressing room ɗin har tana tuntuɓe,da kallo kawai ya bita har ta shige cikin ɗakin,wani irin yanayi yake ji a tattare da shi wanda bai san minene ba. Tsaki yaja,duk sai yaji haushin kanshi ya rufeshi ko miye a jikin yarinyar da ya tsaya yana kallo shi da kullum cikin ganin ƴan mata yake daban daban wanda su ka fita komai nesa ba kusa ba,duk sai yaji ya tsani kanshi,a zafafe ya juya ya fice yana sake jan wani tsaki. da kallon mamaki Yumnah ta bishi har ya ɓace ma ganinta, dariya ta kwashe da ita tana nufar dressing room ɗin da sauri, a tsaye ta samu Nainarh gaban clothset ta kasa taɓuka komai jikinta har wani rawa rawa yake. “wai da baki sa kayan ba,ya Irfan fa baya son jira yana iya tafiyar shi” shiru Nainarh tayi, girgiza kai Yumnah tayi “na lura ba ƙaramar wahala zan sha ba wajen dawo dake dai dai” Yumnah ta ɗauko mata kayan da zata sa,ficewa tayi ta bata wuri,shaf shaf ta shirya ta fito,ficewa su kayi daga ɗakin. parlorn mom su ka je,wayam su ka samu parlorn ba kowa,hakan yasa su ka ƙarasa bedroom ɗin mom ita ka ɗai su ka samu. “mom ina ya Irfan ɗin?” “ya fice,ga magani nan ya bata,zo Nainarh,ya jikin naki?” ƙarasawa tayi gaban mom ɗin “da sauƙi” “Allah ya ƙara sauki,mi Irfan ɗin yace yana damunki?” “mom ya Irfan fa bai dubata ba cewa yayi mu same shi a parlorn ki” “amma yace ya dubata,ɗauko mata ruwa tasha maganin to” da to Yumnah ta amsa tana ficewa daga ɗakin,dawowa tayi hannunta riƙe da glass cup na ruwa, Nainarh ta miƙamawa,mom ta Bata maganin tasha. “kwanta ki huta kinji” mom ta faɗa, a saman bed ɗinta Nainarh ta kwanta Yumnah sai complain take ma mom akan Nainarh ta cika sa damuwa a ranta. *UNITED STATE* _*Las Vegas (Nevada)*_ *10:00 pm* A hankali ta zuro ƙafarta dake sanye da flip-flops masu gashi gashi, bathrobe ce a jikinta yayin da kanta ke naɗe cikin short towel da alama daga wanka take. masu aikinta ne su ka shigo su biyu,juyawa tayi ta nufi ƙofar HOME BEAUTY bin bayanta masu aikin su kayi. Ɗakin ya haɗu sosai,yana da girma ba laifi,komai na cikin shi unique ne,beauty shelf ne manne jikin bangon ɗakin an jera kayan gyaran jiki kala kala dana gyaran gashi harda foot care product da skin care product masu tsadar gaske,ga wani faskeken mirror a jikin bango tun daga sama har ƙasa ,daga gabanshi tulip chairs ne guda biyu, daga can ɓangaren da skin and foot product su ke lounger chair ce. nufar lounger chair tayi ta zauna miƙar da ƙafafuwanta tayi tana kwantar da kanta saman head ɗin chair ɗin haɗe da lumshe ido. ɗaya daga cikin matan ce ta matso ɓangaren skin product ta buɗe, mayuka masu matuƙar tsada ta shiga fito da su,gyaran jiki ta shiga yi mata,cikin ƙanƙanin lokaci fatar jikinta ta riƙa wani glowing tana fitar da wani daddaɗan ƙamshi. A hankali ta buɗe idon ta,sauka tayi daga saman kujerar ta nufi mirror dake ɗakin,ƙarema kanta kallo ta shiga,ta ɗan ɗauki tsawan mintoci tana kallon kanta a mirror kafin ta nufi ɗaya daga cikin kujerun dake gaban mirror ta zauna. ɗayar matarce ta nufo inda take,warware mata short towel ɗin dake saman kanta tayi ,nan take sumar kanta ta zubo har saman bayanta,hairdryer ta jawo, busar mata da kan ta shiga yi,bayan data kammala ne ta ɗauko smoothing serum haɗe wide tooth comb,shafa mata ta shigayi tana taje mata kan,saidata tabbatar ya shartu tukun ta shiga kwarara mata hair oils masu daɗin ƙamshi tana cuɗa kan yanda oil ɗin zai shiga ko ina. Nan take color ɗin kanta light gloden brown ya ciza sai ƙyalli yake da ɗaukar ido ga wani daddaɗan ƙamshi dake fita daga cikin shi. Straightener ta ɗauka ta shiga miƙar mata da gashi,bayan data ta gama miƙar da gashin,half up half down style tayi mata a kan, ba ita da ake yima gyaran ba hatta su kansu masu gyaran ba ƙaramin tafiya da su kan yayi ba. Kallon kanta tayi a mirror,ita kanta ta san baƙaramin kyau tayi ba,side smile ta saki, simple make_up su kayi mata,baƙaramin kyau tayi ba. miƙewa tayi ta nufi wata ƙofa a cikin ɗakin wacce za ta sadaka da dressing room ɗin ta. Masha Allah na furta a yayin da nayi arba da dressing room ɗin wanda idan ba an faɗa maka a gida ne ba zaka yi tunanin boutique ne,duk wani nau'i na sutura a kwaishi a cikin, hatta jakunkuna da takalma babu abun da babu. Ƙatuwar wall drawer ce mai ɗauke da sliding door zagaye da ɗakin,daga waje kana iya hangen tarin suturun dake ciki,ɓangaren pajamas da ban,ɓangaren gwon da ban skirts, shorts, underwears, trousers,shirt, sweaters komai da ku ka sani nadaga ɓangaren sutura an ware mashi wajen shi,idan muka koma ɓangaren takalma da jakunkuna abun sai ya baka tsoro,takalma ne da jakunkuna iri iri ga su na. daga tsakiyar ɗakin half drawer ce ajiye ƙasa doguwa wacce itama marfinta ya kasance na glass, tsawanta ya kusa tsawan ɗakin ta kwance,an kakkasata kashi kashi wanda bakomai ne a cikinta ba sai gold jeweleries,wristwatch, watch chain, watch glass, sunglasses,links,neak chain,rings,babu abun da babu na adon ƴa mace,komai na ciki daga gold sai zinari. bango ɗaya na ɗakin mirror ne,daga gaban shi stool ne guda biyu masu kyan gaske,zama tayi kan ɗaya daga cikin stool ɗin,masu aikin ne su ka shiga zaɓo mata kayan da za su dace da fitar da za tayi,sun jima wajen ganin sun ɗauko mata kayan da su ka dace,kafin su ka dawo in da take zaune hannunsu riƙe da sexy summer bodycon dress masu matuƙar jan hankali. gwada kayan su ka shiga yi a jikinta,duk wacce su ka ɗaura saita girgiza kai alamar ba tayi mata ba,haka su ka shiga gwada kayan,aƙalla sun gwada yafi kala ashirin har sun fara gajiya da gwada mata kayan sai da ƙyar su kaci sa'a ta zaɓi wata White color mai one shoulder tana da baza daga ƙasa,bazar taji adon sparkling stones masu matuƙar ɗaukar ido. A jiyar zuciya su ka sauke ganin sunyi nasarar samarta wacce ta dace don baƙaramar wahala su ka sha ba wajen ɗaukowa da maidawa, ɓangare takalma su ka koma nan ma jido mata su suka shiga yi,duk wanda su ka nuna sai ta nuna baiyi mata ba sai da ƙyar su ka samu ta ɗauki wani high hill Pump black color masu shegen tsini. Ɓangaren da jeweleries su ke su ka nufa,basu sha wata wahala ba wajen zaɓo mata ɗan kunne da sarƙa sai Agogo da chain ɗin ƙafa. Turo ƙofar ɗakin a kayi aka shigo tun kafin ta ƙaraso ta san ko wacece ita ka ɗai ce a cikin ma'aikatan gidan ke da lasisin shigowa part ɗin ta ba tare da ta nemi izinin ba, su kansu na'urorin dake sarrafa part ɗin sun san da zamanta. kyakkyawar matashiyar dattijiwa ce ta shigo,baturiya ce, sai dai duk da manyantar ta hakan bai nuna a fatarta ba,fatarta kamar ba ta tsohuwa ba, kyakkyawa ce ajin farko ,hancinta tsaye yake babu lanƙawasa bakinta ɗan dai dai, launin idonta sak irin na Nailar Acme white grey. long sleeve shirt ce a jikinta tare da A_line skirt wanda ya wuce gwiwarta,sumar kanta dake da jefi jefi na furfura sai sheƙi take tana ɗaukar ido, simple make_up ne a fuskarta ba ƙaramin kyau yayi mata ba jikinta sai fitar da wani ni'imtaccen ƙamshi yake. Aunty Sophia kenan ƴar ƙwalisar tsuhuwa ko budurwa bazata gwada mata iya ɗaukar wanka ba wasu abubuwan duk a wurinta masu Aikin Nailar ke koya,ta san ta kan fashion. In da Nailar take ta ƙarasa fuskarta ɗauke da murmushi wanda yaba dimples ɗin ta damar lotsawa,ta cikin mirror Nailar ke kallonta, Murmushi itama ta sakar mata. cikin girmamawa masu Aikin su ka shiga gaishe da Aunty Sophia,harara ta ɗan watsa masu da sauri su ka sadda kai saboda sanin laifin su na ƙin faɗa mata Nailar zata fita, hugging ɗin ta tayi ta baya. “i miss U so much Aunty sopi,jiya shi ne kwata kwata baki neme ni ba ko?” Nailar ta faɗa a shagwaɓe kamar ba ita ba, murmushi Aunty Sophia tayi tana miƙewa tsaye haɗi da juyo da stool ɗin da Nailar ke zaune. “my baby na shigo fa kina bacci,bana son na takuraki ne shiyyasa na fice” ɓata fuska Nailar tayi “dama na san babu wanda zai kashe man ear phone sai ke” “nayi laifi kenan?” taɓe baki Nailar tayi“ dan kin san baki laifi a wajena shiyyasa ki ke yanda ki ka ga dama” ƴar dariya Aunty Sophia ta saki wacce ta bayyanar da kyawawan haƙoranta. juya mata baya Nailar tayi tana turo baki,kallon masu Aikin tayi da ido tayi masu alamar su fice,kayan dake hannunsu su ka ajiye saman table su ka fice. cikin ɗakin Aunty Sophia ta nufa, ɓangaren underwears ta nufa,bandeau style top ta ɗauko mata haɗe boyshorts masu matuƙar jan hankali white color. dawowa tayi wurin Nailar,miƙa mata tayi “am sorry idan na ɓata ran Queen,ga wannan kisa sai na idasa shirya gimbiyar tawa da kaina” turo baki Nailar tayi “ni bazan iya sawa ba” ɗan zaro ido Aunty Sophia tayi “ƴata fa yanzu budurwa ce dole ta koyi wasu abubuwan da kanta,ba sai masu aiki sunyi mata ba” tashi Nailar tayi sai ɓata fuska take ta amshi kayan dake hannun Aunty Sophia, murmushi Aunty Sophia ta saki,cikin ɗakin ta nufa sai turo baki take. saman ɗaya daga cikin stool ɗin Aunty Sophia ta zauna tana sakin murmushi ita ka ɗai ke kema Nailar haka a zauna lafiya,tana da matuƙar ƙima a idanun Nailar,a kwai soyayya da shaƙuwa mai ƙarfi a tsakanin su, Nailar ta ɗauketa tamkar mahaifiyarta tun tana ƴar ƙaramarta Aunty Sophia ke kula da ita,Nanny ɗinta ce hakan yasa su ka shaƙu,wani lokacin har cewa masu Aikin gidan keyi suna kama. Dawowa Nailar tayi in da Aunty Sophia take ta cire bathrobe ɗin pant da bra ɗin ne kawai a jikinta, a gaban Aunty Sophia tazo ta tsaya,da sauri Aunty Sophia tasa hannu ta rufe fuskanta hakan da tayi ba ƙaramin dariya yaba Nailar ba. “baby ya kamata ki riƙa jin kunya ta fa, yanzu ke ko a jikinki ki tsaya haka a gabana” “dan me zanji kunyarki,ni bana jin kunyar kowa” “dama taya za kiji kunya bayan wannan tsinannun na maki wanka har yanzu” ta faɗa yayin da take zame hannunta daga saman idanunta ƴar dariya Nailar ta saki “Aunty sopi wai har yanzu baki daina jin haushin Lara da Lolah ba” “taya zan daina jin haushin su,wasu ƙatti da su kamar ƴan dambe kullum suna gane man jikin baby” ta faɗa tana tsuke fuska tsawan shekaru abun na cimata tuwo a ƙwarya dan dai kawai bata da yanda za tayi,da tana iya hana Nailar wankan da aike mata da tuni ta hana hatta masu aikinta haushin yanda Nailar ta sakar masu komai na rayuwarta take ji ,ace comon sutura su za su cire su sa mata. “zaki fara ƴan tunane tunanen naki ko,su fa basa da laifi,nice mai laifi sai dai idan ni zaki hukunta” “zan hukuntaki ne mana idan har baki daina wannan san jikin banza ba” “shikenan yanzu tunda kin korar mansu sai ki ƙarasa aikin na su” dungure mata kai Aunty Sophia tayi tana ɗaukar rigar da zata sa,ɗan sosa in da ta dungureta tayi “ karfa garin wannan fushin naki ki ɓata man gyaran gashi na” zura mata rigar Aunty Sophia tayi,ta zuge mata zip,kallon yanda rigar tayi mata tayi a mirror “yanzu haka zaki je maza suyi ta kallon jikin ki” “iya kar su kallon,kuma ma Ni da nake zaune a office ina ruwana da su” “kafin ki shiga office ɗin maza nawa zasu kalle ki musamman wannan ƴan iskan security guard ɗin naki masu fuskar shaiɗanu” “to yanzu wane kaya ki ke so na sa?” Na jikinta ta nuna mata dariya Nailar ta saki “ kina so ajina ya zuba ko,ace na zama tsohuwa” “zaki zama tsohuwar ne mara kunya” murmushi kawai Nailar ta saki,idan har kaji dariyar Nailar to tana tare da Aunty Sophia ko momyn ta,Aunty Sophia baturiya ce amma ɗabi'unta sun banbanta dana turawa. sun ɗan ɗauki tsawan lokacin wajen shiryawa,ba ƙaramin kyau Nailar tayi ba kamar ka saceta ka guda,sosai rigar tabi shape ɗin jikinta,ƴar pose Aunty Sophia ta ɗauko mata tare da sunglasses mai shegen kyau pose ɗin taji adon stones multicolors sai ɗaukar ido take,wata ƴar locker Nailar ta nufa,ɗan duƙawa tayi saitin wata ƴar na'ura dake jikin locker ɗin,idanunta ta saita a jikin na'urar da alama Eye ID ne a jikin ƙofar,nan take ƙofar ta buɗe,ƙananan guns ne a ciki nau'i daban daban tare da bullet ɗin su,watama idan ka ganta zaka ɗauka lipstick ne,ɗaya daga cikin su ta ciro. bullet ta ɗauka guda biyar ta zuba a ciki kafin ta ɗaga rigar dake jikinta,wani ɗan belt dake jikin boyshorts ɗin dake jikinta ta saka bindigar da alama anyi shi ne saboda haka. maida locker tayi ta rufe,juyowa tayi tana kallon Aunty Sophia da tunda ta buɗe locker ta kauda kai,bata ma san ganin abunda ke ciki, murmushi Nailar ta saki tana ƙarasowa inda take. A tare su ka fice daga ɗakin Aunty Sophia na faɗin ji take kamar kar Nailar ta fita Ita kuwa sai sakar mata murmushi take. A parlor su ka samu masu aikinta su biyu na jiran su kowacce su ta ɗauki wankan suit black color,tunda su ka fito Aunty Sophia ke banka masu harara sai kace sune za fita da Nailar ba ita bace zata fita da su ba. Elevator su ka shiga ta kai su a salin main parlor gidan wanda in ka shigo dashi zaka fara cin karo. main entrance ɗin gidan su ka nufa,yanzu ma sai da ƙofar tayi scanning fuskar Nailar kafin su ka fice harda Aunty Sophia. Harabar gidan ƙwanyar take da haske kamar da rana,motocin ne guda biyar a bakin ƙofar fitowa,huɗu baƙaƙe ne ƙirar HYUNDAI yayin da ɗayar ta kasance fara ƙirar Mercedes benz s class a tsakiyar su. rissinawa security guard da masu aikin dake yawo jefi jefi su kayi suna gaishe da Nailar da Aunty Sophia,cikin kulawa Aunty Sophia ke amsa masu. har gaban Mercedes benz ɗin Aunty Sophia ta raka Nailar,da kanta ta buɗe mata door ɗin ta shiga tana mata fatan dawowa lafiya,kissing hannunta Nailar tayi tana faɗin saina dawo,a dawo lafiya Aunty Sophia ta faɗa tana rufe mata marfin motar. Motocin security guard ɗin su ka shiga tare da masu Aikin Nailar,Aunty Sophia na nan tsaye har su ka nufi gate ɗin gidan,sai da taga bata ganinsu tukunna ta koma ciki,ranta duk a jagule, ji take inama zata iya hana Nailar fita. _*HEART OF VEGAS CLUB AND CASINO*_ Tun daga nesa zaka fara hangen hasken sparkling bulbs na haska saman building ɗin in da aka rubuta _* heart of Vegas club and casino*_ da wani irin style. Tsarin ginin building ɗin ma kawai abun kallo ne, A katafaren parking lot na club ɗin da ke cike da tarin rides masu shegen kyau da tsada su kayi parking a wajen parking ɗin motocinta wanda ya kasance nata ne ita kaɗai. Dai dai ta parking ɗin su su kayi, security guard ɗinta ne su ka fara fitowa tare da masu aikinta,ɗaya daga cikin su ne yazo ya buɗe mata marfin motar. A hankali ta zuro ƙafafunta,kafin ta ƙarasa fitowa,gaba tayi suna biye da ita a baya,da wasu jibga jibgan security guard dake sanye cikin baƙaƙen kaya ƙugunsu soke da bindigu su ka ci karo a bakin entrance ɗin shiga,tun kafin ta ƙaraso su ka bata hanya suna ɗan rissanar da kansu Alamar gaisuwa,ko kallon in da suke ba tayi ba ta nufi security door ɗin shiga. Wata irin katafariyar ƙofa ce wacce kai daga ganinta kasan ba ƙaramin waje bane,ƙofarce ta fara magana cikin harshen turanci “welcome to Heart of Vegas,ur Access card please” da sauri ɗaya daga cikin masu aikin ta ciro wani ɗan card a pose ɗin Nailar dake hannunta ta mannashi a jikin ƙofar. dan da nan ƙofar tayi acknowledging card ɗin tana faɗin“welcome miss Nailar” nan take ƙofar ta shiga zugewa,ciki ta kunna kai suna biye da ita. wani irin katafaren club ne su ka shigo,yaji kayan alatu kamar baza'a mutu ba,yana yin tsarinshi yasha ban ban dana sauran clubs. mata ne a tsaye a stage strippers cikin wata irin shaiɗaniyar sutura suna poll dance sauti na tashi,ga mata ga maza wasu a zaune wasu a tsaye suna taka rawa ana spraying dollars,wasu na shan giya,wasu na shaƙar cocaine,ga customize azul na yawo ta ko ina suna kaima waɗanda suka yi order, gawasu designs na shisha wanda a irin waɗan nan clubs ɗin kawai ake samun su, ga vape anasha suma,idan kashigo club din kai kanka kasan ana barin kuɗi, ga wasu irin security guards dake a different corner tsaitsaye da communicative devices a kunnensu kai kace gumaka ne yanda suka tsaya kiƙam ko alamar fitar da breath ba su yi. Kiɗan dake tashi ne ya tsaya,Dj ne ya shiga sanar da zuwan Nailar hakan yasa mutanen dake ciki kai duban su gareta,ihu da sowa ne ya fara tashi wasu na ambatar Queen wasu President,ƙayataccen murmushi ta saki tana ɗaga masu hannu,gungun wasu maza ne su ka nufo in da take sai tangaɗi suke alamar sun sha sun sha sunyi tatul,da sauri security guard ɗinta su ka dakatar da su, murmushi gefen fuska ta saki tana yarfa masu ƴan yatsunta haɗi da ɗan cizon ƙasan lips ɗinta so sexy,ba ƙaramin jan hankalin mazan dake wurin tayi ba harda ma mata,ca su ka yi mata da idanu kamar tsaffin mayu ga nama suna kallo amma ba halin tunkara. fly kiss ta sakar masu tana nufar glass elevator dake cikin wurin, security guard ɗin ta na biye da ita. Wani irin ƙato casino su ka shigo,yaji kayan alatu, uwar dukiya a ka narkar wajen gidanasa ba kaɗan ba ,da kaɗan ne bai ƙarasa girman club ɗin da su ka fara shigowa ba. Wani irin casino Aesthetic ne mai matuƙar ɗaukar ido,ga wasu matsiyatan poker tables and gaming table haɗe da chairs ɗin su,casino cards ne a kowane table,a ƙalla ko wane table na ɗauke da chairs guda biyar. Mata da maza ne zazzaune saman chairs ɗin, casino cards ne a gabansu suna buga caca ga tarin dollers da kowane a cikin ya ajiye a matsayin kuɗin wasan shi, nau'in beers ne masu tsadar gaske haɗe cigarettes wanda tsadar su ta kai mutum ya sayi gida da mota na mutunci ajiye a gaban su,wasu na shan giya wasu na zuƙar taba ana buga wasa kiɗa na tashi ƙasa ƙasa. nan ma security guard ne a kowane corner tsaye ƙiƙam. murmushi Nailar ta saki ganin yanda ake buga wasan,fito tayi wanda ya jawo hankalin mutanen dake wurin,ihu mazan dake wurin su ka saka suna faɗin QUEEN!!!! dariya Nailar ta saki tana ɗaga masu hannu,wani ɗan corridor ta nufa,shuffle machines ne haɗe da slot machines, video poker and video lottery terminals a wajen, ma'aikata ne zaune saman poker chairs suna opreting ɗin su. cikin girmamawa su ka shiga gaishe da ita kamar za su russuna mata,jin jina masu kai ta shiga yi, office ɗin ta ta nufa dake can floor ɗin ƙarshe,a bakin ƙofar shiga office ɗin security guard ɗinta suka tsaya masu aikin su ka bi bayanta. wasu numbobi ta danna a jikin ƙofar nan take ƙofar ta buɗe,kutsa kai tayi ciki jelarta na biye da ita,wani irin katafaren office su ka shigo kamar na shugaban ƙasa,ga sanyin AC dake busowa kamar ƙanƙara,ƙaton transparent glass office table ne a ciki haɗe leather chair mai shegen kyau,laptop ce ajiye saman table ɗin haɗe office lamp,daga gefe 50gm ne na cocaine anyi packaging ɗin su sai Cuba Aliados cigarettes dake a cikin ƙana nan kwalayenta itama anyi packaging ɗinta sai kwalaben shisha nau'i daban daban masu tsadar gaske,ga ɗan madaidaicin bottle keeper wanda aka jera kwalabanan beers kala daban daban. daga can gefe poker table ne wanda ke ɗauke da casino cards,sai faskekiyar glass computer dake ajiye anyi connecting ɗin ta da gaba ɗaya CCTV CAMERAS dake heart of Vegas. Cikin office ɗin su ka ƙarasa,chair ɗinta ta nufa ta zauna yayin da masu aikin suka nufi wasu sofas guda biyu su ka zauna, laptop ɗin dake ajiye saman table ɗin ta buɗe,opreting ɗinta ta shiga yi a hankali. Muryar na'urace ta karaɗe office ɗin tana sanar da zuwan MDs na gaba ɗaya club da casino ɗin, izinin shigowa ta ba da ta hanyar danna wani maddani a jikin table ɗin,a hankali ƙofar ta shiga zugewa,wasu murɗa murɗan ƙatti ne majiya ƙarfi su ka shigo cikin shigar baƙaƙen suit,gaban table ɗin Nailar su ka ƙara so. gaishe da ita su kayi suna russunawa,amsa masu tayi tana nuna masu kujerun dake facing ɗinta,zama su kayi saman kujerun. “is there any problem?” “no ma,but kayan da Boss ta turo suna hanya,muna sa ran isowar su next tommorow around 2:00Am” jinjina kai Nailair tayi“good,bayan nan babu komai?” “yes” “ok,take this” ta faɗa tana nuna masu packeg ɗin cocaine da cigarettes,miƙewa tsaye su kayi,ɗaukar kayan su kayi suna mata sallama haɗi da ficewa. tura kujeran da take zaune tayi,ƙafafunta ta ɗaura saman table ɗin tana jinginar da kanta saman head ɗin kujerar,ɗaya daga cikin masu aikin ce ta miƙe,can cikin office ɗin ta nufa,bata jima a sai gata ta fito hannunta ɗauke da ƙatuwar kwalbar champagne haɗe da champagne tulip glass sai ice a cikin bowl,har gaban table ɗin Nailar ta ƙaraso,ajiyewa tayi,ice ɗin ta fara zubawa a cikin cup kafin ta buɗe kwalbar, tsiyaya mata tayi cikin cup ɗin ta miƙa mata,amsa tayi tana wani lumshe ido. barin wajen tayi,komawa tayi ta ɗauko masu milkshakes guda biyu,duk yanda su ke son shan kayan shaye shaye Nailar ta hana sai dai su sha lemu ko milkshake. wayarta ce ta fara ringing,kallon screen ɗin tayi love shine sunan daya bayyana, murmushi ne ya bayyana a fuskarta, picking call ɗin tayi tana kara wayar a kunne. “sweetheart” shine sunan da Nailar ta furta,on the other hand murmushi ta cikin wayar ta saki “baby nah ya ki ke,ya gidan” ɓata fuska Nailar tayi “babu daɗi,yaushe zaki dawo?" “kinyi kewata ne?” “i really miss u, please come back home” Nailar ta faɗa kamar zata sa kuka murmushi ta saki “i think next week,fatan kina office?” “momy mai makon ki tambayi lafiyata amma ta office ki ke,wai tsaya dani da wannan business ɗin ma wa ki ka fi so ne?” “nafi sonki sama da komai, sorry fatan kina lafiya” “lafiya lau,fatan kema haka” “ina lafiya kamar yanda ki ke,kina office ɗin?” ɓata fuska Nailar tayi “yes,su Joseph sun sanar dani kayan da ki kayi order suna hanya?” “yes, Please my baby ki kasance a wurin lokacin da shipment ɗin zai ƙaraso bana son any problem ya faru, kaya ne masu tsadar gaske, munada tarin customers a ƙasa wanda zuwan kayan kawai su ke jira” “please momy,su Joseph za su iya ji da komai ba sai naje ba” “no kije dai zaifi,zan turo maki komai ta email,ki tabbatar ba wani kuskure” turo baki Nailar tayi ba tare da tace komai ba da alama ba taji daɗi ba,sallama su kayi, ajiye wayar tayi saman desk tana lumshe ido haɗe da sakin ɗan ƙaramin tsaki. Sai Around 5:00Am ta koma gida a gajiye,ko kayan dake jikinta bata cire ba ta faɗa saman bed,ficewa masu aikin su kayi bayan sun ajiye mata bag ɗin ta haɗe da wayarta. Aunty Sophia da saurinta ta zo amma sai ta tarar tana bacci, murmushi kawai tayi taja mata blanket,kissing forehead ɗinta tayi ta fice daga ɗakin... _Ep 13_14_ *Bound by fate,freed by love, A romantic Odyssey*❤💘💘 ______________________________ *ABUJA NIGERIA* Turus ta tsaya ganin ko kallon dinner ɗin da aka kawo mata ba tayi ba, kallonta ta kai zuwa bed ɗin dake ɗakin, a zaune take ta jingina da head bord ɗin gadon,photon mahaifiyarta tare da mahaifinta ne riƙe a hannunta sai aikin shafawa take yayin da hawaye ke sintiri a fuskarta. girgiza kai Yumnah tayi yayin da take ƙarasawa bakin bed ɗin, zama tayi kusa da ita tana dafa kafaɗarta,cikin sigar lallashi ta fara magana. “sister Nainarh na san abun da ciwo, nasan zai ɗauki lokaci kafin zuciyarki ta dake, sai dai ki sani yawan ku ka da sa damuwa a rai bashi ke maganin matsala ba Adu'a itace maganin duk wata matsala, a halin yanzu Adu'arki su ke buƙata sama da komai, in sha Allah komai daran daɗewa gaskiya za tayi halinta, in dai da rai wata rana a gabanki duk wani mai sa hannu a al'amarin zai zo a ƙasƙance dan neman yafiyarki,dan haka ina so ki daina yawan kukan nan da sa damuwa a ranki” shiru Nainarh tayi tana sauraron Yumnah, hannu Yumnah tasa ta shiga goge mata hawayen dake zuba daga fuskarta tana sake kwantar mata da zuciya. “kiyi haƙuri kinji,komai zai wuce in sha Allah” “na kasa mantawa da irin kisan wulaƙancin da a kayi ma mahaifana,a gaban na su ka kashe shi amma Court ta ɗaura laifin a kan mahaifiyata ba tare da tausayin halin rasa mijinta da take ciki ba” “Allah ya fisu Nainarh,duk wani mai sa hannu asirin shi zai tonu,ki kwantar da hankalinki komai zai wuce mahaifiyarki zata dawo gare da izinin Ubangiji,ki daina kuka kinji” jinjina mata kai Nainarh tayi,sosai Yumnah ta shiga kwantar mata da hankali,har ta samu ta ɗan saki jikinta. *ASO VILLA* Kyakkyawar matashiyar matace kwance saman makeken gadon ta,daga yanayin yanda numfashinta ke fita zaka fahimci ba ta cikin kwanciyar hankali. Wani mahaukacin Nocking a kayi ma ƙofar ɗakin wanda yayi sanadiyyar farkawar ta,a firgice ta farka tana ambaton Innalillahi wa Inna Ilaihi rajiun,sake nocking ɗin a kayi kamar za'a ɓalla ƙofar. Waro kyawawan idonta tayi tana kallon ƙofar gabanta na wani irin lugudan duka, Adu'a ta shiga yi Allah yasa ba shi bane duk da ta san babu wanda zaiyi mata wannan Nocking ɗin a irin wannan lokacin bayan shi. Wata irin kakkausar murya wacce kenuna mamallakinta a buge yake taji daga bakin ƙofar ɗakin “KAINART wai uwar mi kike a ciki ne da bazaki zo ki buɗe man ba, wallahi ki ka bari na shigo da kaina sai kin yaba ma aya zaƙinta” ya faɗa yana sake kaima ƙofar wani mahaukacin duka. hawaye ne su ka wanke fuskarta dama ta san zaiyi wuya ace ba shi bane,ita kam yau ta shiga uku dan daga yanayin muryar shi baya a cikin hayyacinshi,banko ƙofar yayi kamar zai karyata, da gudu ta duro daga saman gado jiki na rawa ta kama handle ɗin ƙofar ta buɗe mashi. matashin magidanci da aƙalla zai kai kimanin shekaru 32 zuwa da 3 a duniya,baƙaƙen suit ne a jikinshi yayinda hannunshi ke riƙe da ƙatuwar Whiskey , kyakyawane sai dai munanan ɗabi'un shi sun boye kyawun fuskarshi. cikin ɗakin ya ƙaraso yana huci kamar wani mawuyacin zaki, jifa yayi da kwalbar dake hannunshi ƙasa ta tarwatse sauran ruwan dake ciki ya malale a ƙasa,ja da baya tayi ganin irin kallon ƙasƙancin da yake mata, cikin rawa murya tace “dan Allah ya Zaabith kayi....” bata ƙarasa ba ya wanketa da lafiyayyun maruka har sau biyu,dan da nan jinta da ganinta su ka ɗauke na wucin gadi taurari ta fara gani suna mata shawagi a cikin idanunta, bata dawo daga hutun marin da yayi mata ba taji saukar belt, dukanta ya shiga yi kamar ya samu jaka. kuka take tana ambaton “dan Allah ya zaabith kayi haƙuri, na tuba bazan sake ba” ko saurarenta baya yi dukanta kawai yake kamar an aiko shi,bai ƙyaleta ba sai da ya tabbar ya sauya mata kammani tukun ya jefar da belta ɗin ƙasa,wuyan rigarta ya cakumo yana manne bakinshi da nata,kamar zai cire mata baki haka ya shiga kissing ɗinta,cikin rashin imani ya shiga yayyaga suturar dake jikinta, doguwar sumar kanta ya jawo kamar zai cire mata ita yayi jefa da ita saman gadon babu tausayi ko imani ya shiga biyan buƙatar shi da ita, sai da ya tabbar ya kusa kasheta tukun ya ƙyaleta ya miƙe,yana tangaɗi ya nufi wata ƙofa wacce nake kyautata zaton toilet ne. wani sabon kuka ta saki ta rasa wannan wace irin rayuwa take, ko baiwar da aka siyo ba'a wulaƙantata kamar yanda Zaabith ke mata kuma a haka wai ita ɗin matarshi ce ta sunnah wacce su kayi Auren soyayya bana ƙiyayya ba,wasu zafafan hawayen ne suka sake wanke mata fuska. da jan jiki ta sauko daga saman bed ɗin,blanket ɗin dake shimfiɗe taja ta rufe jikinta,a daddafe ta nufi ƙofar fita, ficewa tayi daga ɗakin, a hankali take tafiya tana ƴan waige waige gudun karta haɗu da wani ko masu aikin gidan su ganta a irin wannan yanayin, Allah ya taimaketa har ta kawo bakin ƙofar wani ɗaki bata haɗu da kowa a hanyar ba, tura ƙofar ɗakin tayi ta shige,mai da ƙofar tayi ta rufe da key,a jikin ƙofar tabar key ɗin,yara ne ƴan maza guda biyu kwance saman makeken bed ɗin dake ɗakin cikin shigar PJ white color, sai sharar baccin su suke hankali kwance. Ƙofar toilet ta nufa, tsarkake jikinta tayi,sannan ta gasa jikinta da yayi mata tsami, bathrobe ta zura a jikinta ta fito,zuwa tayi tsakiyar yaran ta kwanta bayan ta kashe light ɗin ɗakin,hugging ɗin yaran tayi ajikinta yayinda hawaye ke sintiri zuba daga idanunta, tsawan shekara goma kenan da yin Auren su,shekara ɗaya kawai su kayi suna shan soyayya amma tun daga nan komai ya lalace kullum cikin fuskantar azaba take daga Zaabith duk wasu munanan halayenshi babu wanda bai nuna mata ba, ya fita gida sai sanda yaga dama zai dawo,idan ya koma wajen Aiki Lagos sai yayi wata da watanni bai dawo ba duk ranar da zai dawo a buge yake dawo mata kuma a ranar ta shiga uku, iyayenshi sunyi faɗa sunyi faɗan sunyin jan hankalin amma a banza,duk da fara tara iyali da su kayi bai sa ya canza halayen shi ba. tayi tunanin zaman su a gidan gomnati zai sa ya canza ɗabi'un shi kodan gudun zubar mutuncin mahaifin shi da siyasarshi a idon duniya,amma a banza saima abun da yaci gaba gashi duk wannan uƙubar da take ciki ta kasa sanar da iyayenta duk dan gudun lalacewar zumunci dake tsakanin su saboda mahaifin Zaabith yaya ne ga mahaifinta uban su ɗaya. ta jima tana saƙawa da kwancewa har baccin wahala yayi awan gaba da ita rungume da ƴaƴanta, lokacin da ya fito daga toilet ɗin ƙugunshi ɗure da towel, kallon gadon daya barta a kwance yayi, ganin wayam bata nan me yasa shi jan wani mahaukacin tsaki yana faɗin “zan kamaki ne yarinya”. ƙofar fita shima ya nufa, ficewa yayi daga ɗakin zuwa master bedroom ɗin shi, yana shiga ɗakin a saman gadon shi ya faɗa rub da ciki babu Adu'a babu komai,cikin ƙanƙanin lokaci bacci yayi awan gaba dashi. *WASHE GARI* Tunda Asussu ba ta koma ɗakinta ta gyara gudun masu aiki su ganshi haka bata son su zargi wani Abu,duk da irin azabar da take sha a wajen shi har kawo wannan lokaci tana son shi tana kuma yi mashi kallon uban ƴaƴanta, Adu'arta a kullum Allah yasa ya gane kuskuren da yake aikatawa. shaf shaf ta gama kauda komai,toilet ta shiga wanka tayi haɗe da Alwala,fitowa tayi ta nufi cloth set ɗin ta,doguwar rigar Abaya ta ɗauko ta zura a jikinta,da ƙyar ta zura rigar a jikinta saboda ciwukan da taji a dalilin dukan da yayi mata duk ya faffasa mata baya,sawun duka har saman wuyanta ga marin da yayi mata, ta san dole sawun hannunshi ya fito. a saman kai ta ɗaura mayafin Abayar tukun ta ɗauko hijab,ficewa tayi daga ɗakin dan ta san a kowane lokaci zai iya dawowa. Bedroom ɗin yaranta ta koma,a kwance ta same su kamar yanda ta barsu, tashin su ta shiga yi domin lokacin sallah yayi,ɗaya bayan ɗaya su ka shiga toilet su ka ɗauro Alwala,jallabiya ta ɗauko masu cikin kayan su, cire PJ ɗin dake jikin su suka yi suka zura jallabiya. “momy Dady ya dawo ko??”faɗuwa gabanta yayi dalilin tambayar da yaron yayi mata. “Eh ya dawo tare ma za ku tafi masallaci,yana ɗakin shi kuje ku same shi” “momy shine ya dake ki ko” faɗuwa gabanta ya sake yi “shine ko momy??” yaran su ka sake jefa mata tambayar saurin ƙaƙalo murmushi tayi tana girgiza masu kai alamar A'a “shi ne mana momy,ga sawun duka nan a fuskar ki” “faɗuwa nayi Ammar ba duka bane” “duka ne mana,gashi nan sawun hannunshi ne a saman fuskar ki” “momy mun gaji da dukan ki da dady yake,sai mun rama maki dukan da yake maki yaji shima idan da daɗi,kuma sai mun sanar da grandfa har yanzu bai daina dukanki ba” duk yanda take daurewa kasawa tayi hawaye ne su ka wanke fuskarta,tun tana ɓoye masu yanzu yaran babu abunda ba su sani ba game da irin zaman iyayen na su. hanyar fita su ka nufa suna sai sun faɗama grandfa Aman har ya fara zubar da hawaye,da sauri tabi bayan su,jawo su tayi zuwa jikinta, hugging ɗin su tayi. “kuyi haƙuri Aman kar ku sanar da dady Ahmad,dadyn ku bada gangan ya mareni ba ya bani haƙuri bazai sake ba” “momy kullum haka yake faɗa,amma har yau bai daina ba,kinga da gangan yake dukan ki” “duk da haka Ammar shi ɗin fa mahaifin ku ne,idan baku rufa mashi asiri ba waye zai rufa mashi,kuyi haƙuri kunji ko,ku yafe mashi nima na yafe mashi” sake shigewa su kayi jikinta suna sakin kuka,wasu hawaye ne itama su ka wanke fuskarta,ɗan bubbuga bayan su ta shiga yi “ya isa haka ku daina kuka kun ji,zai daina wata rana” raba jikin su ta yi,hannu tasa ta shiga goge masu hawayen fuskar su. “kuje yana ɗaki ku same shi” maƙe mata kafaɗa su kayi “mu dai tare da grandfa zamu tafi da su uncle Waseef” “ki bar mu kawai momy muje tare da grandfa” “shikenan sai kun dawo,Allah yayi maku Albarka” da Ameen su ka amsa suna nufar ƙofar fita,turo ƙofar ɗakin da a kayi ne ya dakatar da su,gaba ɗayan su suka kai dubansu gare shi. farar jallabiya ce a jikinshi,jikin shi da alamar danshin ruwan da yayi alwala,cikin ɗakin ya ƙaraso,hannuwan shi biyu ya buɗe ma yaran alamar su zo gareshi fuskar shi a sake. tsuke fuska su kayi suna bin shi da wani irin kallon tsana,lamarin yayi matuƙar ɗaure mashi,da sauri ya kai duban shi ga kainart dake tsaye tana kallon su,saurin kauda kai tayi kamar ma bata ga abun da su Ammar ɗin su kayi mashi ba. ta gefen shi su ka zo za su wuce,saurin kamo hannun su yayi,wayancewa yayi irin kamar ma bai fahimci mi yaran su ke nufi ba “ fushi ku ke da dady saboda bai dawo da wuri ba,kuyi.....” bai ƙarasa ba saboda fisgewa da su kayi daga riƙon da yayi masu,ƙofar fita su ka nufa ba tare da ko sun kalli inda yake ba,baki ya saki kamar saka rai wai yau shine su Aman su kayi ma haka,mi hakan ke nufi mahaifiyar su ta fara hure masu kunne ke nan. yana nan tsaye har su ka ɓacce ma ganin shi,jinjina kai yayi yana nufo in da take,da sauri ta ɗauki hijab ɗin ta zata zura a jikinta,a zafafe ya fisge hijab ɗin yayi jifa da ita,damƙara sumar kanta yayi,rintse ido tayi saboda zafin daya ziyarci kanta. “wato raini ya fara shiga tsakanin mu ko,har kin fara tara yara kina gaya masu ina dukan ki ko,a tunaninki dan kin sanar da su hakan zai canza wani Abu ne,ki sani a duk faɗin duniyar nan babu wani wanda ya isa ya hanani abun da nayi niyya ko da kuwa mahaifina ne,dan na san shi ki ke tunanin zai iya hanani??” cikin ƙunar rai tace “a tunanin ka ya Zaabith su Ammar ba su san abun da ka ke aikatawa ba ne?,ko a tunaninka ba su da wayan sanin abun da kake aikatawa ,karka manta kasha dukana a gaban su dan mi baza su ji haushin ka ba,nifa mahaifiyar su ce” fisgar kanta yayi kamar zai cire shi gaba ɗaya “to sai mi dan sun sani,ke baki isa ki shiga tsakani na da su ba saboda ni ɗin mahaifin su ne ko suna so ko basa so” fashewa tayi da kuka “kaji tsoron Allah ya Zaabith,ka sani alhakin mu bazai barka ba,Allah zai saka m...” tsawa ya daka mata “ya isa haka” ya faɗa yana sakin gashin kanta,idan da abun da ke tada hankalinshi ta furta Allah zai saka mata baya son tana barin shi da Allah, yana tsoron ranar da Allah zai tashi saka mata. ƙofar fita ya nufa,da kallo ta bishi har ya fice hawaye sai sintiri suke a fuskarta. hijab ɗinta ta zura, prayer mat ta shinfiɗa,gabatar da sallah ta shiga yi,ta jima zaune tana kai ku kanta ga Ubangiji sammai da ƙassai. Tana a nan kwance a kayi Nocking ɗin ɗakin, tambayar waye tayi ba tare da ta tashi ba. “saraj ce dama madam Salima ce tace ki fito time ɗin breakfast yayi,takuma ce anjima za ku je can family house ɗin ku” “bana jin daɗi sarah,ki kawo man nawa breakfast ɗin nan kawai” “to shikenan,ya zance ma Madam ɗin?” “ki faɗa mata bana lafiya” “to shikenan” mai aikin ta faɗa tana barin wajen,bayan kamar minti biyar mai aikin ta dawo. iznin shiga Kainart ɗin ta bata,a hankali ta turo ƙofar ɗakin ta shigo hannunta ɗauke da tryan data haɗa mata breakfast ,saman ɗan table ɗin dake ɗakin ta ajiye mata. “sannu madam,Allah ya baki lafiya” “Ameen sarah,su Ammar na wajen dady ne?” “eh suna can harda yallaɓai Zaabith” “ok shikenan zaki iya tafiya” “ok Allah ya ƙaro sauƙi” da Ameen kainart ɗin ta amsa,ficewa mai aikin tayi. * Big Daddy's house* Mom da ya Naeem ne zaune a saman gondola chairs dake cikin garden ɗin gidan,ɗan madaidaicin glass table ne a gaban su an cika masu shi da fresh fruit haɗe da snacks, yayin da mom ke riƙe da wasu takardu a hannunta sai jujjuyasu take, kallonta ya Naeem yayi “mom kinyi shiru ba kice komai ba?” ɗan sauke ajiyar zuciya tayi tana kallon ya naeem ɗin daya kafeta da idanu,takardun dake hannunta ta miƙa mashi “ban san ta in da zan fara maka bayani ba ne naeem” “koma ta yayane ki fara mom Zan fahimce ki in sha Allah” jinjina kai mom tayi “wani taimako nake so kayi mana game da case ɗin Asma'u” “umarni za kice mom,Dan kinfi ƙarfin neman taimako a gare mu,mi kike buƙata nayi maki a kan case ɗin?” “yawwa,ina so ka sake wani sabon bincike a kan case ɗin bayan wanda jami'an tsaro su kayi” “amma mom saboda mi?” “naeem zuciyata ta kasa yarda cewa Aminiyata zata iya aikata wannan laifin ,duk da ɗan Adam yana canzawa akan yanda ka san shi amma ita ina kyautata mata zato” “shikenan mom in Sha Allah zanyi yanda ki ke so ,amma dole sai na samu wasu ƙarin bayanan sama da wannan da ki ka bani” “wanann ba damuwa bace,ko a wajen yarinyar ta zaka iya samun wasu baya nan,sannan akwai masu aikin gidan da masu gadi duk da sun bada bayanan su a court da wurin ƴan sanda sai dai bayanan na su ban gamsu da su ba, ina ji a raina kamar sun ɓoye wani ko wanda su ke da alhaki a kan kisan su suka hansu faɗar gaskiya” “shikenan ba damuwa mom ko da sun ɓoye wani Abu nayi maki alƙawarin sai sun magantu dole za su faɗi gaskiya” “yawwa haka nake son ji,amma ina so ya zama sirri kai ka ɗai nake so kayi aikin sai wanda ka yarda da dashi daga cikin yaran ka wanda kasan bazai yaudareka ba” “karki damu da wannan mom,komai zai tafi yanda ki ke so in sha Allah” jinjina kai mom ɗin tayi “bayanan komai yana a cikin takardun nan” “zaka samu komai a ciki,tun daga tarihin rayuwar su, sunayen mutanen da suke mu'amula da CP lokacin da yana raye da ita kanta Asma'u da duk wani ma'aikacin su,hatta ƙasashen da su ke yawan zuwa da garuruwa da wurare da su ka fi yawan zuwa a faɗin ƙasar nan zaka samu, Naeem kar kayi sakace da su duk da na san ba halinka bane amma ka kula da su sosai akwai baya nan da ko Court bata san da zaman su ba naƙi bayyanar da su ne a gabanta saboda wasu dalilai nawa, dan Allah ka maida hankali a kan su Naeem” ɗan dariya ya Naeem yayi “dama na daɗe ina zargin tsakanin ke da dady wa SAM ya gado naci da bin ƙwaƙwafi case Ashe ke ce?” murmushi mom ta saki “bana son shashanci Naeem,wannan case ɗin karka manta Aminiyata ce a ciki kaga kuwa dole na nace akan shi” “haka ne in sha zan baje gaba ɗaya ilimina akan wannan case ɗin,zanyi ƙoƙarin ganin munyi nasarar fitar da momy in sha Allah” “haka nake son ji,ka ko yi waya da SAM?” “A'a,mun kwana biyu ba muyi waya ba,kin san ɗan naki sarki ne sai ya sha iska yake neman mutane gashi ko ka kira shi a banza idan ba yana free ba shine zai ɗaga ko idan yaga missed call ya kira” “nima kwana biyu bai kirani ba,amma Alyar da James sun kira ni kuma sun shaida man yana lafiya,aiki ne yayi mashi yawa” “nima Alyar ya kirani harma ya ke sanar dani suna nan zuwa ƙarshen shekarar nan shi da James,na dai ce su lallaɓa SAM ɗin nima zan gwada sa'ata ko za'a samu wannan karan ya biyo su” “duk lokacin da mu kayi waya dashi sai na roƙi Alfarmar ya taimaka ko kiran dadyn ku ne yayi a waya ko ya tura mashi message ko da bai zo ba amma ina,baƙar zuciyar dana rasa awajen wa ya gadota taƙi barinshi,harda momy da Uncle Jonas nasha haɗashi saboda yafi jin maganar su sama da tawa amma a banza sunyi sunyi yaƙi, ko da picking call ɗin dadyn ku ne yayi idan ya kirashi amma ina” “in sha Allah mom wata rana da ƙafarshi zai tako ya zo har ƙasar nan saboda dady,komai zai wuce” “bana tunanin SAM zai yafe ma dadyn ku,ya riƙeshi sosai a zuciyar shi,tsawan shekara 18 fa kenan” “mom ki daina wannan tunanin in sha Allah zai yafe mashi wata rana,koda shekara 50 ne,ke da ma yayi ma laifin ki ka yi haƙuri bare shi SAM ɗin,zai dawo da kanshi saboda dadyn in sha Allah” “Allah yasa haka Naeem” “in sha Allah mom,wata rana komai zai wuce har jikokin SAM ɗinki za ki gani a gabanki dan na san burinku kenan ke da Dady” murmushi ta saki “Allah yasa haka,da kuwa nayi farin ciki mara misaltuwa” “Ameen mom,ni zan wuce gida” “ok muje nima zan koma ciki” tashi su kayi, jerawa su kayi a tare su ka nufi ƙofar cikin gidan. part ɗin dady su ka nufa,a kishingiɗe su ka same shi saman rug carpet yana duba wani littafin addini,bakin su ɗauke da sallama su ka ƙara da ciki,ɗagowa dady yayi yana amsa masu sallamar. kusa da shi ya Naeem ya zauna mom kuma ta zauna saman kujera kallon su dady yayi fuskarshi a sake yace “uwa da ɗa daga ina haka,wani abun daɗin ya faru ne” murmushi ya Naeem yayi “barka da hutawa dady” “barka dai Naeem,ya Aiki yau ba ku shigo tare da Adnan ɗin ba?” “Eh kila sai anjima zai shigo” “Allah ya kaimu anjimar lafiya,na shiga wurin Abbah ɗazu yace kwana biyu bai saka a idon ba ina fatan dai lafiya?” “Ayyuka ne su ka ɗan yi man yawa kwana biyu shiyyasa ban shiga ba na bari sai ranar juma'a” “duk da haka Naeem tunda har kana samun lokacin shigowa nan ai ka ɗan leƙa ku gaisha ko da da dare ne” “in sha Allah daga nan zan shiga” “yawwa hakan yayi,Allah yayi maku Albarka” “Ameen dady” ya Naeem ɗin ya faɗa yana miƙewa,sallama yayi masu ya fice. *Main Parlor* da sauri yaja baya saboda karon da yayi da mutum,duban shi ya kai ga matashin saurayin dake tsaye a gaban shi sai layi yake kamar zai faɗon mashi,da tsantsar mamaki yake bin saurayin dake neman ya raɓa ta gefenshi ya wuce,a wani zafafe ya fisgoshi baya,saukar maruka matashin saurayin yaji a saman fuskar shi wanda su kayi sanadiyyar dawowar shi cikin hayyacin shi,da sauri yasa hannuwanshi ya dafe kumatunshi. ɗan uwan shi dake bayan shi ganin irin marin da ya Naeem ya sauke ma ɗan uwan nashi ne yasa shi komawa baya cikin sanɗa ya koma parking space ya shige motar da su ka zo,mai da ƙofar yayi ya rufe a hankali,shiru yayi yana baza ido a hanya ko zaiga wucewar ya naeem. tun daga kan crazy short ɗin dake jikin shi da ƴar iskar shirt ɗin dake jikinshi mai kama da rariya zuwa ɗan iskan askin dake kanshi ya Naeem ke kallo,ga wani chain dake manne a wuyan shi kunnenshi ɗaya a huje yake ya saka ear ring. wani marin ya Naeem ya sake kifa mashi,dafe kuncinshi yayi sai ga hawaye shar da alama marin ya shige shi sosai “dan Allah second father kayi haƙuri,wallahi bangaka bane shiyyasa na bigeka” saurayin ya faɗa yana watso ido kamar tsohun kwarto a kan ya Naeem. “daga gidan ubanwa kake haka?” ya naeem ya faɗa yana cakumo wuyan rigar shi cikin rawar murya yace “wallahi daga islamiyya muke Ni da YAZDAN,yazdan dan Allah ba daga can muke ba” ya faɗa yana waigawa bayan shi wayam ya gani babu yazdan “wallahi daga can muke” ya sake faɗa yana kallon ya naeem,dariya ma maganar tashi ta so ba ya naeem in ba ya ɗauke shi ɗan iska kamar shi ba taya zaice mashi daga islamiyya yake da irin wannan shigar ya yarda,ta ina ma yayi kama da mai zuwa islamiyya. “saboda ka ɗauke ni shashasha kamar kai ko” “wallahi ka tambayi yazdan daga can muke mun shiga gida ne muka canza kaya” “in tambayi abokin cin mushenka ko,zan kamashi ne shima” “Allah ba ƙarya muke ba” “to naji, karanta man abun da aka koya maku yau ko ka kwana kana frog jump” da ƙyar ya haɗe yawu jin abunda ya naeem ɗin yace,raba ido ya shiga yi kamar wanda yayi ma sarki ƙarya “oya kai nake saurare” ya naeem ɗin ya faɗa fuska a tsuke yana harɗe hannuwanshi a ƙirji nan fa ido ya raina fata,ƴan kame kame ya fara,ran ya naeem ne ya fara ɓaci,cakumo kwalar rigar shi yayi yaja shi ƙiiii zuwa waje,yazdan na ganin haka yayi saurin kwanciya cikin motar sai zare ido yake. ɗaya daga cikin sojojin dake shawagi cikin Estate ɗin ya Naeem ya kira,da sauri sojan ya ƙaraso,ƙato ne bana wasa ba,daga bakin parking space zuwa bakin main entrance ɗin shiga gidan ya Naeem ya nuna ma sojan “ka sashi frog jump ko sau ɗaya ya tsaya ka kirani” “ok sir” sojan ya faɗan yana sakin murmushi dama rana irin wanann yake jira saboda yaron ya raina su kwata kwata baya ganin su da ƙima ya raina su. barin wurin ya Naeem yayi ya nufi motar shi,shiga yayi,key yayi ma motar ya bar wurin. “amma wallahi second father ya gama dakai FA'IZ,ya rasa wa zai sa ya hukunta ka sai waɗannan ƴan iskan sojojin, tir wallahi” yazdan ya faɗa yana buɗe marfin motar ya fito “oya start,ko yanzu na kira shi” sojan ya faɗa yana kallon Fa'iz ɗin dake tsaye yana binshi da kallon ƙasƙanci “an gaya maka tsoron shi nake ji ne?” “wannan kuma matsalar kace,zaka fara ko sai na kira shi?” sojan ya faɗa yana zaro wayar shi daga Aljihu “kai dallah malam dakata,ce maka a kayi bazan yi ba ne?” “to fara idan ba so kake na kira shi ba” tsaye Fa'iz yayi sai ƴan kalle kalle yake,yana tsoron ya Naeem amma bai son ajinshi ya zuba a gaban securitys ɗin gidan. yazdan ne ya ƙaraso wajen shima sai layi yake kamar zai faɗi ƙasa,kayan jikinshi iri ɗaya ne dana Fa'iz sai dai shi kanshi kitso ne saɓanin Fa'iz dake da aski “malam ai sai ka tafi ko” yazdan ɗin ya faɗa yana ma sojan kallon rainin wayau. “na tafi saboda kai ka sani ko?”sojan ya faɗa ,kallon fa'iz yazdan yayi su ka kwashe da wata ƴar iskar dariya “cewa za kayi na shan fura kake so,ai da kayi magana” Fa'iz ne ya zura hannu cikin Aljihu ya ciro bandir ɗin dollers ya watsama sojan yana jan hannun yazdan “zo mu tafi kaji” ran sojan ne yayi matuƙar ɓaci hakan yasa ya fisgo rigar Fa'iz ɗin “kai har ni zaka wulaƙanta?” sojan ya faɗa “an wulaƙanta ka,dama can kai ba wulaƙantaccen bane,maza ka sauke hannunka saman jiki na ko ranka yayi mummunan ɓaci yanzu” Fa'iz ya faɗa dai dai jiniyar motocin sojoji na tunkaro gidan,da sauri Yazdan ya duƙa ya kwashe kuɗin. mota biyu ce ta security guard ta nufo parking space ɗin yayin da su ka sako wata baƙar Nissan a tsakiyar su, parking motocin su kayi,da gudu security guard ɗin su ka shiga fitowa suna nufar baƙar Nissan ɗin dake tsakiyar su, ɓack seat ɗin motar ɗaya daga cikin security ya buɗe. Wata kaykyawar mata ce ta fito cikin shigar lafaya fara mai adon flowers ja,tasha adon zobba da sarƙa na gold, high hills ne a ƙafarta,cikin takun izza ta nufo in da su Fa'iz ɗin su ke ,sojan na ganinta ya saki Fa'iz ɗin yana ɗan rissanawa ya gaisheta,taɓe baki Fa'iz yayi yana faɗin matsiyaci kawai. murmushi su saki shida yazdan suna ƙarasawa in da matar take, hugging ɗin su tayi itama fuskarta ɗauke da murmushi,raba jikinta tayi da nasu tana faɗin “ 5 and 6 lafiya na ganku tsaye nan,mike faruwa??” kallon sojan dake tsaye yazdan yayi “wannan matsiycin ne ya Naeem wai yasa yasa Fa'iz tsallan kwaɗo” kallon sojan matar tayi “wai haka ne?” “eh ranki ya daɗe” sojan ya bata amsa,dubanta ta kai ga Fa'iz “laifin mi kayi mashi yasa a hukuntaka?” “momy babu abunda nayi mashi,kawai kin san ya tsaneni ne” girgiza kai matar tayi “babu yanda za'ayi Naeem yasa a hukuntaka haka nan Fa'iz dole a kwai abun da kayi mashi,jeka kawai wajen aikin ka” ta faɗa tana kallon sojan “to ranki ya daɗe” sojan ya faɗa yana barin wajen,bai so Hajiya ta zo ba yaso yau ya koyama Fa'iz hankali amma idan ba yau ai akwai gobe. cikin gidan su ka nufa ita da su Fa'iz ɗin securitys ɗin ta da PA ɗin ta har sun biyo su ta dakatar dasu,ciki su ka shiga su yazdan sai zuba mata ƙarya su ke wai sunyi broke gashi kwana biyu dady bai basu ko sisi ga motar su babu mai a ƙasa suke takawa zuwa school,murmushi kawai tayi tana girgiza kai ta san ƙarya su ke mata,hannu ta zura a jakar ta ciro bandir ɗin ƴan dubu dubu har guda shidda ta basu kowa uku uku,godiya su ka shiga zuba mata kamar tsaffin maroƙa. A main Parlor su ka rabu ta nufi part ɗin mom su kuma su ka nufi part ɗin mamy. tun daga first parlorn mamy Fa'iz ya shiga ƙwala mata kira “mamy! mamy!! mamy!!!,wai ba kowa ne a gidan nake magana anyi man banza??” masu aikin gidan najin maganar shi su ka nemi wajen ɓuya dan sun san muddin ya gansu sun shiga uku baijin kunyar taɓa jikin su a gaban kowa ko da kuwa mahaifiyar shi ce . kitchen ɗin part ɗin ya fara leƙawa ganin babu kowa ne yasa shi jinjina kai yana faɗin “ƙana nan ƴan iska basa nan kenan” ya faɗa yana nufar ƙofar bedroom ɗin mamy. A bakin ƙofa yaci karo da mamy doguwar rigar less ce a jikinta kanta babu ɗan kwali gashin Attachment ɗin ta har gadon bayanta kamar dai kullum,daga sama har ƙasa ta shiga ƙare mashi kallon kafin ta sauke idonta kan fuskarshi da sawun hannun ya Naeem ya fito raɗau. “mamy wai ina ki ka shige ne sai ƙwala maki kira nake?” ya faɗa yana layi kamar zai faɗo mata,saboda tsaɓar shaye shaye ko bai sha komai ba baya iya tsayuwa dai dai sai ka ganshi yana layi “kai Ni da Allah karka faɗo man a ka,daga ina kake haka?” “daga yawo”ya bata amsa a gadarance “yawon iskanci ko, a can ma ka samu wani ya ɗauke ka da mari ko?,wallahi Fa'iz ka shiga hankalinka dani,kai kullum burinka kaja man abun zagi ko dan ubanka” shafa kumatun shi yayi “nifa ba abun zagin da nake ja maki,kuma wannan sawun marin da ki ka gani Naeem ne ya mare ni dan kawai na bigeshi ban gani ba” “mari fa kace, wai tsayama wane Naeem ɗin??” “akwai wani Naeem ɗin ne banda wanda ki ka sani” “ya mareka dan kawai ka buge shi?” “eh” ya bata amsa “yana cikin gidan ko ya fita” “ya fita” ya bata amsa “idan ya fita ai uwar shi na nan” mamy ta faɗa tana damƙar hannun Fa'iz ɗin ta ja shi zuwa part ɗin mom,dan suyi saurin isa ta corridor da zai sadaka da duk wani part dake second floor tabi,cikin ƙan ƙanin lokaci su ka iso part ɗin mom Fa'iz sai faɗi yake ta sake shi amma ina... _*Ep 15_16*_ *Bound by fate,freed by love, A romantic Odyssey*❤💘💘 ______________________________ A saman sofa suka samu mom da matar data shigo,fizge hannunshi Fa'iz yayi, babu sallama babu Nocking mamy ta hau surfa masifa “wallahi bazata saɓu ba bindiga a ruwa,bazai yiwu ko wane ɗan iska yariƙa dakar man yaro ba ehe” kusan a tare mom da matar data shigo su ka kai duban su ga mamy dake fama sirfa masifa, Yumnah da gudu ta fito daga ɗakin mom. “naga dai iskanci babu wanda baiyin shi,Allah na tuba akwai wanda akafi sani da iskanci sama da soja,wane irin iskanci ne nasu Bama gani a gidanan, ko kuwa wanda ke matse ƴaƴan mutane a office da sunan aiki ne ba ɗan iska ba, ko wanda ya haiƙe ma tsarar haihuwar shi da ƙananun shekaru ya kuma wanke ƙafa ya koma can cikin nasara masu jan kunne dangi sheɗan ne ba ɗan iska ba, ko mai yawan mashaya duk daren Allah ne ba ɗan iska ba!!???” daga mom har matar data shigo zuba mata ido su kayi kawai suna kallonta kamar wata mai taɓin hankali. “to wallahi bazan yarda ba tunda ba wani yasha man wahalar haihuwa ba ehe” clapping hand taji anyi daga bayanta. Da sauri gaba ɗayan su ka kai duban su ga dady dake tsaye can sama tun ɗazu ya dafa handrail,tunda mamy ta shigo yake tsaye yana kallonta,wani irin mummunan faɗuwa gaban mamy ya shiga yi duk a tunaninta baya gidan. parlorn dady ya nufo yana faɗin “da kyau uwar ɗa,da kyau wacce ta iya haihuwar ɗan kirki” ya faɗa yana ƙarasowa in da suke. Fa'iz shan jinin jikinshi yayi ganin irin kallon da dady ke mashi,yana ƙarasowa in da yake ya ɗauke shi da lafiyayyun maruka har sau biyu,da sauri ya dafe kuncin shi. Mamy gabanta ne ya faɗi,nan ta shiga ƴan kame kame da nufin ba dadyn haƙuri,wata mahaukaciyar tsawa ya daka mata wacce ba ita da yayi mawa ba hatta su mom sai da ƴan hanjin cikin su suka kaɗa “yanzu ni na mareshi ko zaki rama mashi??” Ya faɗa yana sake saukema Fa'iz ɗin wani lafiyayyan marin “haba janar taya za kaita dukan yaron haka,ba fa shi yayi maka laifi ba” “na sake marin shi dan na gwada maki iskancin soja kamar yanda ki ka faɗa” dadyn ya faɗa a karo na uku yana sake ɗauke fa'iz ɗin da wani marin har sai da ya saki fitsari a wando, yumnah bata san sanda ta fashe da dariya ba, da sauri tasa hannu ta toshe bakinta gudun kar wani yajita. “dan Allah janar kayi haƙuri, wallahi ba haka nake nufi ba” “haka ki ke nufi mana,ai gwara na gwada maki iskancin sojan” “dan Allah dady kayi haƙuri ba dan ni ba” fa'iz ɗin ya faɗa hawaye na zobo mashi shar “yiman shiru ko nayi ƙasa ƙasa da kai a wurin nan shashasha” da sauri fa'iz ɗin yasa hannu yan kama bakin shi, kallo mamy dady yayi “Mabaruka!!!” dady ya kira sunanta da kakkausar murya,jiki na ɓari tace “Na'am” “wannan ya zama na farko kuma na ƙarshe da ƙafarki zata sake takowa zuwa ɓangaren zulaihart da sunan tujara ko rashin mutunci, Naeem yaya yake ga Fa'iz ya isa ya hukuntashi akan kowane laifi da yayi,daga yau idan ki ka sake tada jijiyoyin wuya akan Naeem ko wani a cikin ƴaƴana ya hukunta ɗanki, ina mai tabbatar maki zaki gamu da fushina wanda hakan bazai taɓa maki daɗi ba kinji na faɗa maki” “naji in sha Allah hakan bazata sake faruwa ba” mamy ta faɗa kamar da gaske,hanyar fita dady ya nuna mata ita da Fa'iz ɗin “maza kija ɗanki ki ba mutane wuri” kama hannun fa'iz ɗin tayi sumi sumi su ka fice kallon dady matar data shigo tayi “ina wuni ya Tahir, na sameku lafiya?” “lafiya lau Salima ya mutanen gidan, ina ki ka baro man ƙanina” murmushi matar ta saki tana faɗin “ yana can yana fama da jama'a” “ai dole ne, Allah dai yasa a gama lafiya” dady ya faɗa “Ameen ya Allah” “ki gaishe man da shi” dadyn ya faɗa yana nufar part ɗinshi “zaiji in sha Allah” matar ta faɗa tana kai dubanta ga mom “ba mu gisaba, na same ku lafiya?” “lafiya lau hajiya salima, ya kuma fama da jama'a” “lafiya lau Alhmdllh,ashe kuma abunda ya faru da Asma'u kenan, to Allah ya kyauta gaba” “Ameen ya Allah” mom ta faɗa “da tare zamu zo da Kainart bata jin daɗi ne shiyyasa bamu zo tare ba amma tana maki jaje” “Ayya Allah sarki, ina amsawa Allah ya bata lafiya” “Ameen summa Ameen” ƙarasowa yumnah tayi cikin parlor “momy shine baki zo man da su Ammar ba?” “suna school ne yumnah” “ke ki ka ma biye mata idan tana son ganin su ai ta san in da zata same su” “ai kuwa dai, dan tunda yallaɓai yaci zaɓe ina jin zuwan yumnah Villa sau ɗaya shima bata wani jimaba ta dawo” ɓata fuska yumnah tayi “school bata bari na saketa, kuma dokokin gidan gwamnatin ne momy sunyi yawa” “kaji ja'ira banza lokacin da ku kuna gidan gwamnatin ai ba suyi maki yawa dokokin ba sai yanzu ko, kawai baki son zumunci” “ba haka bane momy” “to yaya ne?” “ina nan zan zo kafin muyi resuming school” “ina nan ina saurare Allah ya kawo ki lafiya” “Ameen” tashi matar tayi tana faɗin “bari na shiga ɓangaren mabaruka mu gaisa” “to nagode Allah ya bar zumunci, a gaishe man da Kainart ɗin” “za taji in sha Allah” “momy sai na zo” yumnah ta faɗa “Allah ya kawo ki lafiya” da Ameen ta amsa, har main parlor mom ta rakata, part ɗin mamy hajiya salima ta nufa. Mamy a lokacin da su ka fito daga part ɗin mom, fiszge hannunshi yayi daga riƙon da tayi mashi “mamy ai ga irinta nan sai da nace ki ƙyale ni gashi nan yanzu kin ja man shan maruka, na san yanzu hankalin ki ya kwanta?” “wallahi Allah ne ya ceceta da ace janar baya gida yau data gane kurenta” taɓe fa'iz yayi “ kullum haka ki ke cewa,kin taɓa ɗaukar mataki a kan mom ɗin ne ko da sau ɗaya, wallahi mamy ina guje maki randa dady zai shuka maki rashin mutunci saboda matarshi” “wane shi, ya dai shuka mata rashin mutunci” “ai yanzu naga faɗan da yayi maki ita yayi mawa,wallahi mamy ki rage shige mata wallahi ko ƴaƴanta ba raga maki za suyi ba, ki bar ganin kowa ya zuba maki ido a gidanan kamar ana tsoronki, wallahi lokacin biye maki ne basu dashi amma duk randa ki ka kaisu bango abun bazaiyi kyauba” “faɗa mata gaskiya fa'iz kullum abunda nake so ta gane kenan amma taƙi, wallahi mamy wannan abun da ki ke ida sirema dady ki ke, dan zubarma kanki da mutunci ki ke a gaban kowa muma kina ja mana” Fa'iza ta faɗa wacce fitowarta kenan daga bedroom ɗin ta baki mamy ta saki ta rasa har yaushe tayi lalacewar da Fa'iz da Fa'iza su ka rainata irin haka “ni ku ke faɗa ma haka dan uwarku?” “gaskiya ce kuma daga ƙinta sai ɓata, kai yazdan zo mu tafi muje kawai restaurant muci abincin a can” Fa'iz ya faɗa yana jan hannun yazdan su ka fice, Fa'iza ma shigewa tayi ɗakin ta da kallo kawai mamy ta bisu. duk wannan hargagin da take tana yi ne saboda su amma basa gani “Allah ya wadaran naka ya lalace” ta faɗa tana nufar ɗaya daga cikin sofas ɗin parlorn ta zauna, masu Aiki dake laɓe suna sauraron abun da ke faruwa ban da Allah ya ƙara babu abun da su ke. hajiya salima ta shigo parlorn bakinta ɗuke da sallama, da sauri mamy ta kai dubanta gareta,tashi tayi ta nufeta fuskarta ɗauke da murmushi, hugging ɗin juna su kayi. “saukar yushe?” mamy ta faɗa tana jan hannunta su ka nufi sofa su ka zauna “dama yaushe zaki ganni kinje kina tsula tsiyarki” mom salima ta faɗa “wai da ke ce a parlorn, ni inama na lura da wacece ido a rufe suke ne raina ya ɓaci” “ai naga alama, wai dama mabaruka har yanzu baki daina hargagi da zulaihart irin wannan ba?” “yaushe kuwa zan daina, ai idan kinga na daina to na sake sender ta ƙasar su kamar shekarun baya” kallon baki da hankali matar ta shiga binta dashi. “ke har yanzu kina tunanin zaki iya raba Tahir da zulaihart ne, to wallahi idan ma bacci ki ke tun wuri ki farka kar kije garin tsige igiyar Aurenta ke ki tsige taki a banza” “ban gane ba, mi kike nufi” “ko wannan matakin daya ɗauka yau akan fa'iz a gabanki saboda zagin ƴaƴanta da ki ka yi ya isa yasa kiyi hankali kisan cewa da da yanzu ba ɗaya bane” “ni wallahi Hajiya salima kin barni a cikin duhu,dan ban gane inda maganar ki ta dosa ba” “ kin manta bala'in da ki ka shiga lokacin baya?, da ba dan mama Ameena ba da yanzu kina wani gidan ba wannan ba, idan zaki canza salon kishin ki ki canza idan kuma haka ki ke ganin ya fiye maki tam, shi dai yaƙi ɗan zamba ne” jinjina kai mamy ta shiga yi alamar gamsuwa da maganar hajiya salima “shikenan naji zanyi ƙoƙarin ganin na sauya” “hakan dai shi ya fi, ni na shigo ko gaisawa ba muyi ba,kin wuni lafiya?” “lafiya lau, ya yau ban ganki da tawagarki ba?” “ki bari kawai ni na hana su biyo ni nace suyi zaman su jaje zanje ba ɗabbaka siyasa ba, ko security cewa nayi su jira ni a waje” “kina sha'aninki ta wajen Ahmad, ai wallahi ni lokacin da janar na kan kujerar shugaban ƙasa duk in da zani da tawagata nake zuwa ai shine girman” “ban manta ba” matar ta faɗa, mai aiki mamy ta ƙwalama kira dan ta kawo ma hajiya salima ruwa da lemu. “ai barshi kawai mabaruka nasha a part ɗin zulaihart tafiya ma zanyi” “nifa kinga abun da ke haɗani dake kenan,dan mi zaki sha ruwa a wajenta” “ni dai yanzu idan na sake dawowa na sha, amma yanzu kam gaba nayi” “shikenan Allah ya nu na man lokacin da zaki sake dawowar” da Ameen hajiya salima ta amsa, a tare su ka miƙe ita da mamy. har parking space mamy ta rakata, sai da taga tashin motocin ta tukun ta koma ciki. *ASO VILLA* Kusan a tare motocinta da motar da aka ɗauko su Ammar daga school ta shigo. A bakin main entrance ɗin shiga part ɗin su motocin su kayi parking, drivern da yayi driving ɗin su ne ya fito ya buɗe masu,da gudu su ka fito suna nufar motar kakar tasu,suna isowa security na buɗe mata ƙofa ta fito. da gudu suka faɗa jikinta “oyoyo granny,shine ki ka fita bama nan ko” murmushi ta saki tana shafa fuskokin su “ayi man afuwa gidan big daddy naje” shagwaɓe fuska su kayi “amma granny kin san cewa muma muna son zuwa shine ki ka tafi bama nan” “ayi man Afuwa,ai gobe za ku haɗu dashi a gidan Abbah” ta faɗa tana jan hannunsu suka nufi cikin gidan “ai gidan Abbah ba gidan shi bane,mu gidan shi muke son zuwa” “karku damu idan kuna son zuwa sai nasa dadyn ku ya kaiku gobe da kun dawo daga school,kunga sai kuyi ma Aunty Yumnah weekend ko” tsallan murna su kayi “yeee har gidan papa ma sai muje” “na san Aunty Yumnah zata kai ku ko ina,amma fa sai dady da momynku sun amince” ɓata fuska su kayi “dady bazai amince ba mu dai kawai kice ya kaimu” “to naji muje na duba jikin momyn ku” ɗan zaro ido su kayi suna kallonta “mi ya samu momy?” “bata jin daɗi ne” Hajiya Salima ta faɗa dai dai tana tura ƙofar ɗakin kainart ɗin,wayam su ka gani bata ciki har ƙofar toilet sai da Aman yayi nocking amma bata ciki, Ammar ne yace kila tana bedroom ɗin su ,ficewa su kayi zuwa bedroom ɗin na su. A kwance su ka sameta saman bed ɗin su Aman, idanunta a rufe kamar mai bacci,gaba ɗaya ta rasa mike mata daɗi a duniyar nan,har ta ƙagara ya tattara kayan shi ya koma Lagos. da gudu su ka ƙarasa in da take,faɗawa su kayi saman jikinta “momy mun dawo” a firgice ta miƙe zaune dan ba ƙaramin tsoro su ka bata ba, ajiyar zuciya ta sauke ganin su. “amma yaran nan anyi ja'iran yara,ba kuga bata jin daɗi ba shine zaku faɗa mata haka” Hajiya Salima ta faɗa yayin da ta ƙarasowa bakin bed ɗin. da sauri kainart ɗin taja gyalen abayarta ta rufe gefe da gafen fuskarta tana kai dubanta ga Hajiya Salima “momy har kin dawo?” “na dawo kainart,ya jikin naki?” “Alhmdllh,ya su mom ɗin?” “suna lafiya,tana ma gaishe dake” “ina amsawa” “mi Dr yace yana damunki?” “zazzaɓi ne kawai” “to Allah ya sawaƙa” da Ameen kainart ɗin ta amsa,tashi hajiya Salima tayi “ku kuzo ko muje can sarah ta shirya ku,kunga momy ba lafiya” da gudu su ka sauka daga saman bed ɗin suna nufar ƙofar fita,bin bayan su hajiya salima tayi tana sakin murmushi, murmushi itama kainart ɗin ke saki har su ka fice daga ɗakin. *Uncle Hashim's House*😡 A zaune su ke saman dinning chairs a katafaren dinning room ɗin gidan,baka jin ƙarar komai sai na spoon da plate ɗin da su ke cin abincin. gaba ɗaya a takure take saboda kafetan da ido da dadynta yayi,hakan ya hanata sukuni,momy da balqis sai cin abincin su suke hankali kwance dan basu san abun da ke faruwa ba. a hankali ta ajiye spoon ɗin hannunta tana miƙewa da nufin barin wajen,table ɗin ya buga da ƙarfi wanda yayi sanadiyar dawo da hankalin momy da balqis kan su. “koma ki zauna” ya faɗa da kakkausar murya yana nuna mata chair ɗin data tashi,da ɗan rawa rawar jiki ta nufi chair ɗin ta zauna,duƙar da kanta tayi ƙasa gabanta na faɗuwa. “barrister lafiya?” momy ta faɗa tana ajiye spoon ɗin dake hannunta,maida kanshi yayi kan abincin da yake ci ba tare da ya tanka mata ba kamar ma ba dashi take magana ba. sanin bazai tanka mata bane ya sata kallon laatifa,da ido tayi mata alama da lafiya, girgiza mata kai laatifa tayi alamar itama bata sani ba hawaye na taruwa a idonta. “Allah ya kyauta” shine kawai abun da momy tace tana cigaba da cin abincinta,sun kai tsawan 20 mins kafin kamar daga sama su kaji ya kira suna balqis murya a kausashe. da sauri balqis ɗin ta ajiye spoon ɗin dake hannunta “na'am dady” “last day mi ya kai ki court??” ya faɗa babu alamun wasa a fuskar shi,kamar saukar ardu haka laatifa taji tambayar duk da ba ita yayi mawa ba,tayi tunanin ya bar maganar tun lokacin ashe ba haka ba. gabanta na faɗuwa ta kai dubanta ga balqis tana mata alama da ido data rufa mata asiri. “naje saboda Aunty laatifa ne” wani mugun kallo yayima laatifa “saboda mi?” “bata jin daɗi ne shine nace ta zauna gida ni na wakilceta” jinjina kai barrister yayi. “mi na faɗa maki laatifa??” ya faɗa yana tsareta da idanu “dady ba fa ita ta tura ni ba, da kaina nace zanje” “tambayar ki nayi?” girgiza mashi kai balqis tayi “dan Allah kayi haƙuri dady wallahi bani nace taje ba”laatifa ta faɗa a hankali “laatifa kin raina maganata ko,bance maki idan za kiyi yawan iskancinki ki daina sa ƴata a ciki ba” kamar zata fashe da kuka tace “kace dady” “wato saboda ban isa ba shine ki ka turata cikin ƙattin da ki ka saba yawo da su ko?” “kayi haƙuri dady bazan sake ba” rai a ɓace momy tace“wai lafiyar ka kuwa barrister,itama ba ƴar ka bace ,mi yasa k..?” bata ƙarasa ba yayi saurin daka mata tsawa yana ɗaga mata hannu,hakan yasa tayi shiru tana kallon shi cike da mamaki. “wannan ya zama rana ta ƙarshe da zan sake maki warning akan ƴata,duk yawan banzan da za kiyi kiyishi ke kaɗai amma banda ƴata kinji na faɗa maki” “in sha Allah hakan bazata sake faruwa” laatifa ta faɗa hawayen da su ka taru a idonta na zubowa. tashi yayi ya nufi bedroom ɗin shi,da wani kallo momy ta rakashi,tashi laatifa tayi ta nufi bedroom ɗinta yayin da take fashewa da wani matsanancin kuka, balqis ma kuka ta fashe da shi sun rasa yaushe dadyn su zai rage wannan ƙiyayyar da yake ma laatifa. bayan laatifa momy tabi hakama balqis,a kwance su ka sameta ta kifa kanta saman matress tana fitar da wani kalar kuka mai ban tausayi,zama momy tayi kusa da ita hannunta ta ɗaura saman bayan laatifa,a hankali take shafa bayanta. “momy wai mi yasa dady ya tsaneni,mi yasa baya sona kamar yanda yake son balqis, nima ba ƴarshi bace ko ina da wani uban wanda ni ban san shi,momy dan Allah idan ba shine mahaifina ba ki faɗa man???” saurin toshe mata baki momy tayi da tafin hannunta “kul laatifa kar na sake jin bakin ki ya furta wannan kalaman,ki daina tunanin baya sonki ne, mahaifinki na sonki fiye ma da yanda yake son balqis,yana yi maki haka ne saboda ya kasa mantawa da abun da ya faru shekarun baya,ki dage da Adu'a wata rana sai labari” “momy mi yasa dady har yanzu ya kasa gane cewa ba abun da yake zargi ba ne,momy har sau nawa zan faɗa mashi babu abunda ya faru dani kawai taimako na SAM yayi” “saboda shi mahaifinki ne abun na damun shi shiyyasa ya kasa mantawa,kiyi haƙuri kinji in sha Allah wata rana gaskiya za tayi halin ta dadyn ki zai gane baki da laifi” “momy amma ke mi yasa ki ka fahimce ni,dady baya sona ne kawai” ta kai ƙarshen maganar tana sake fashewa da wani matsanancin kukan. momy bata san lokacin da itama hawaye su ka wanke fuskarta ba, balqis ma ƙarfin kukan da take ne ya ƙaru,gaba ɗayan su rasa me lallashin wani a kayi,sai da su kayi mai isar su tukun momy ta shiga lallashin su,da ƙyar ta samu su kayi shiru,tashi laatifa tayi ta nufi toilet. tashi momy tayi ta fice zuwa ɗakin barrister, a tsaye ta sameshi gaban wardrobe ɗin shi fitowarshi kenan daga wanka ƙugunshi ɗaure da towel. “kaji tsoron Allah barrister,ka sani wannan aibatatan da kake ba shine mafita ba,itama ƴace a wurin ka kamar balqis,kuma ka sani ɗan Adam bai isa ya tsallake jarabawar da Allah yayi mashi ba,ko da ace abunda kake zargi gaskiya ne, kai ba mahaifinta bane dan mi bazaka ɗauki ƙaddararta hannu bibbiyu ba,amma ace tsawan shekaru ka kasa mantawa da abu,kullum cikin aibatata da nuna mata tsana kake, Allah ma munayi mashi laifi ya haƙura sai kai ne bazaka yafe ma ƴarka ba kan laifin da zargi kawai kake baka da tabbaci, haba barrister ka zama mahaifin ƙwarai mana” “kin gama?” shine kawai abun da yace,wani ƙululun baƙi ciki ne ya tokare mata maƙoshi wato ma ta gama “get out from my room” ya faɗa yana nuna mata hanyar fita,rai a ɓace ta juya ta nufi ƙofar fita har ta kama handle ɗin ƙofar sai kuma ta tsaya,rai a ɓace ta juyo tana kallonshi. “ka sani balqis da laatifa Amana ce Allah ya baka,kuma zai tambayeka akan yanda ka tafiyar da rayuwar su,ka sani muddin baka gyara alaƙarka da ƴarka ba za kayi daka sani ne mara amfani” tana gama faɗa haka ta fice daga ɗakin baki ɗaya,tsaki yaja kawai yana cigaba da abunda ke gaban sa. shaf shaf ya shirya cikin pajamas ɗin shi white color masu fatsi fatsin baƙi,feshe jikin shi yayi da perfume ɗin shi masu ƙamshi,bed ɗin shi ya haye yayi kwanciyar shi bayan ya kashe light ɗin ɗakin. wayar dake kan nightstand ya ɗauka,dialing wata number yayi,bugu biyu a kayi picking call ɗin,kara wayar yayi a kunne,in low voice yake waya yanda ko kusa dashi ka tsaya bazaka iya jin abunda yake cewa ba,idan ka shigo ɗakin sai ka rantse da Allah bacci yake. barrister kenan ko matashin saurayi bazai gwada mashi iya kashe murya idan yana waya ba. *Big daddy's House* “ko fa mi za kice sai dai kice amma yau sai kin fita dinning kinyin dinner tare da kowa na gidan nan,na gaji da wanna ƙunshi kan naki da ki ke” “please Yumnah ki fahimta mana,bana jin yunwa ne ba wai ban son fita ba” “to naji,muje ni ki raka ni koda ba kici komai ba ai za ki gaisa da mom da dady,kuma zaki rage wanann yawan tunane tunanen da kike” duk yanda ta so zille ma Yumnah akan ta ƙyaleta Yumnah taƙi bata dama dan dole ta miƙe,hijab ɗinta dake saman bed ɗin ta ɗauka,zurawa tayi a jikinta “muje to” ta faɗa tana kallon Yumnah “ko ke fa,amma wannan hijab ɗin da ki ka sa saikace wacce zataje gaban sirikai, dinning fa zamu je ba wani waje ba” “ni dai haka zanje” “ai saiki ta tafiya haka”yumnah ta faɗa tana jan hannunta su ka fice. Mom da dady ka ɗai su ka samu a dinning ɗin, Ishrat na daga tsaye tana serving ɗin su,bakin su ɗauke da sallama su ka ƙarasa cikin dinning room ɗin,zama su kayi saman chairs yayinda su ke gaishe da dady da mom. murmushi dady yayi yana kai duban shi ga Nainarh,cikin kulawa su ka amsa masu gaisuwar da su kayi dady na faɗin “ɗiyata kinyi wuyar gani,tun ranar da muka dawo daga wajen mahaifiyar ki ban sake saki a idona ba,ina fatan dai lafiya?” “lafiya lau dady” Nainarh ta faɗa tana duƙar da kanta ƙasa “yanzu ma fa da ƙyar na samu ta fito,kullum tana ɗaki daga kuka sai tunani” Yumnah ta faɗa tana kallon Nainarh data sadda kai ƙasa. “wai haka ɗiyata?” shiru Nainarh tayi tana wasa da gefen hijab ɗinta “ki dai na sa damuwa a ranki kinji, mahaifiyar ki zata dawo gareki,in sha Allah asirin wanda su ka kashe mahaifinki zai tonu” “in sha Allah” Nainarh ta faɗa “bana son kina sa damuwa a ranki kinji ko,ke da ma ki ke da wata mahaifiyar a kusa dake miye na sa damuwa a ranki” dady ya faɗa yana nuna mom da tunda su ka shigo dinning ɗin ta kafe Nainarh da ido ko ƙyaftawa ba tayi dan duk maganar da dady ke yi bata sani ba hankalin ta baya wajen. “zulaihart!” dady ya kira sunanta,ɗan saurin kallon dadyn tayi “lafiya ki ka kafe ƴar taki da kallo” murmushi mom ta saki “wani lokaci sai nake ganin tana man kama da ƴar uwata,sai dai ita bata kai ta kazar kazar ba Nainarh ta cika sanyi” mom ta faɗa tana sake kai dubanta ga Nainarh data sadda kai ta sauraron su. “nima na jima ina ganin kamaninta da Carol, da ace ban san mahaifiyar ta ba kuma a ce Carol ta taɓa Aure da babu abunda zai hana nace ƴarta ce” murmushi mom ta saki “nima ina yawan faɗama mahaifiyar ta haka,wani lokacin idan nace haka sai tace dan kawai ina son Nainarh ne yasa nake ganin kamanin su” “ta iya yiwuwa” dadyn ya faɗa, Yumnah da Nainarh dai na jin su,fa'iza ce ta shigo dinning room ɗin,tsaye tayi tana riƙe ƙugu fuskarta a turɓune “shine yau aka rasa wanda zai kirani ko?” ta faɗa tana sake tsuke fuska. “sorry Aunty Fa'iza nayi tunanin a part ɗin mamy za kiyi dinner shiyyasa ban kira ki ba” Yumnah ta faɗa tana ɗan kama kunnenta alamar sorry “nima ayi man Afuwa na rashin faɗa maki da banyi ba” Ishrat ta faɗa wacce ke serving ɗin Yumnah da Nainarh,ɗaya daga cikin kujerun Fa'iza ta nufa ta zauna. “ni dama na san ai kun rigada kun gama rainani gidan nan” murmushi kawai dady da mom su ka saki. gaishe da su dady fa'iza tayi, murmushi dady yayi yana faɗin “ai da nayi tunanin baki gannu ba” ɗan murmushi tayi tana sosa ƙeyar ta. serving ɗin ta itama Ishrat tayi kafin ta bar dinning ɗin,tsit wurin yayi ba wanda ya sake magana. mom ta fara tashi kafin dady ya miƙe yana kallon Yumnah yace “Autar mom ina fatan baki manta gobe juma'a ba?” “ban manta da gyaran part ɗin shalelen dady ba,gobe tunda safe zansa a gyara shi” “good,haka ne son ji,sai da safe ku” har haɗa baki suke wajen furta good night,jinjina masu kai dadyn yayi yana fice daga dinning room ɗin. suma basu wani jimaba su ka tashi, Ishrat ta zo tare da su munirat su ka kwashe kayan da su kaci abinci su ka gyara wajen tsaf. part ɗin mamy Fa'iza ta nufa sai da safe Yumnah da Nainarh su kayi mata suma suna nufar bedroom ɗin su. Toilet Nainarh ta shiga tayi brush haɗe da alwala,kusan kullum za tayi bacci sai tayi Alwala abun ya zame mata jiki. tana fitowa Yumnah na shiga,wanka tayi haɗe da Alwala kafin tayi brush,lokacin data fito har Nainarh ta kwanta, dressing room ɗin ta ta nufa, pajamas ta zura a jikinta kafin ta dawo bedroom ɗin. kashe light ɗin ɗakin tayi,kwanciya tayi tana jan duvet ta rufe jikinta. “yau ba wayar kenan?” Nainarh ta faɗa “tun ɗazu mu kayi waya sai gobe kuma” “Allah ya nuna mana goben lafiya” da Ameen Yumnah ta amsa. ɗan shiru su kayi kafin Nainarh ta juyo tana fuskantar Yumnah “wai wacece Carol da naji mom na faɗin muna kama?” “ƙanwar mom ce” Yumnah ta bata amsa,gyaɗa kai kawai Nainarh tayi tana juya mata baya... _*Ep 17_18*_ *Bound by fate,freed by love, A romantic Odyssey*❤💘💘 ______________________________ *Washe Gari* A zaune suke saman sallaya da alama basu jima da kammala sallah ba,tashi Nainarh tayi,hijab ɗin dake jikinta ta cire ta linke ta nufi bed,kwanciya tayi tana ɗan jan blanket ta rufe rabin jikinta. yumnah na daga zaune har gari ya ɗan fara haske,tashi tayi itama ta cire hijab ɗin dake jikinta, toilet ta shiga,bata fi five minutes ba ta fito, dressing room ɗinta ta nufa,kayan jikinta ta canza zuwa gwon mai hannun armless,low bun tayi ma kanta da ƙaramin ribbon,mayafi ta ɗauka ta yafa saman kanta sannan ta fice daga ɗakin ta koma bedroom ɗin, Nainarh na nan kwance kamar yanda ta barta. wayarta dake ajiye saman nightstand ta ɗauka ƙofar fita ta nufa,tashi Nainarh tayi zaune “sister Yumnah sai ina haka da safe?” juyowa Yumnah tayi “wai da ba bacci ki ke ba?” “kwance kawai nake,baccin ne yaƙi zuwa” “ok part ɗin dady zanje na ɗauko key,za ayi gyaran part ɗin shalelen dady ne,tunda kin tashi sai ki zo muje” “A'a sai kin dawo” “wannan ne kuma baki isa ba,ki tashi kawai mu tafi abunda yasa ban tasheki ba nayi tunanin bacci kike,ta so mu tafi gari na waye wa bana son mu makara zuwa gidan Abbah” saukowa Nainarh tayi daga saman bed ɗin,hijab ɗinta ta ɗauka,ficewa su kayi daga ɗakin. direct sama su ka nufa zuwa part ɗin dady,a Parlor su ka same shi zaune saman sofa da Qur'an a hannunshi yana karatu,ciki suka ƙarasa suna mashi sallama ɗagowa kawai yayi ya kalle su ba tare da ya katse karatun da yake ba, bedroom ɗin shi Yumnah ta nufa Nainarh kuma ta zauna kan ɗaya daga cikin sofas ɗin,shiru tayi tana sauraran yanda dady ke furta ko wane harafi cikin ilimi,sai da ya kai aya tukun ya kai dubanshi gareta. fuskar shi ɗauke da murmushi yace “ɗiyata yau kece a part ɗin na” murmushi Nainarh tayi tana ɗan rissinar da kai tace “ina kwana dady,an tashi lafiya” “lafiya lau Alhmdllh,fatan kema kina tashi lafiya” “lafiya lau” ta bashi amsa “masha Allah, Yumnah ta hanaki bacci ko?” murmushi tayi tana faɗin “A'a dady da kaina na tashi” “ai nayi tunanin ita ta taso ki” girgiza kai Nainarh tayi fuskarta ɗauke da murmushi,fitowa Yumnah tayi hannunta riƙe da key's,wurin su ta ƙaraso. “dady ka tashi lafiya?” ta faɗa yayinda take ƙarasowa inda yake side hug tayi mashi, kissing forehead ɗinta yayi fuskarshi ɗauke da murmushi “lafiya lau,fatan kema kina tashi lafiya?” “lafiya lau dady, key's ɗin part ɗin Autan ka na ɗauko za'aje a gyara” murmushi dady yayi yana dungure mata kai “zaki sani idan yaji ki ne” murmushi Yumnah tayi “taya zai sani,shida yana can” “ai zai dawo kuma zan faɗa mashi ne” “Allah ya Amince,nima nayi kewarsa na ƙosa naga ya zo” “in sha Allah,yana nan zuwa” “Allah ya kawo shi lafiya” da Ameen dadyn ya amsa,tashi Yumnah tayi tana kallon Nainarh “muje,dady sai mungama” “yawwa Nainarh harda sabon part ɗin yau ku shiga ku gyara shi” “dama yau ko bakace a gyara ba sai na shiga naga abun da ka zubama shalelen naka bayan wanda kayi mashi” “zaki kuwa gani,amma fa karki ta kallo dayawa bana son a cinye mashi kyau tun mai shi bai gani ba” “karka damu dady,amma fa idan yafi nawa kyau tam” ta faɗa tana jinjina mashi kai murmushi dadyn ya saki yana faɗin“dan Allah kisa su gyara da kyau kin ji” “in sha Allah”ta faɗa suna ficewa daga part ɗin. staircase ɗin dake can ɗan gefe da part ɗin dady su ka nufa,hawa su kayi zuwa can floor ɗin ƙarshe. “ina so su kammala gyarannan da wuri dan mu samu zuwa part ɗin Abbah a kan lokaci” Yumnah ta faɗa dai dai time ɗin da su ke kawo bakin wata ƴar madaidaiciyar ƙofa ta glass. wasu madannai Yumnah ta danna a jikin ƙofar “ina tajin ana faɗin Abbah da part ɗin shi,yayan dady ne?” “granfa ɗin mu ne, mahaifin su dady,duk ranar Friday gaba ɗaya family ɗin mu a can muke wuni,tundaga safe har dare a can muke lunch da dinner” jinjina kai Nainarh tayi a lokacin da ƙofar ke buɗewa, wani irin katafaren parlorn ne su ka shigo,launikan dake cikin parlorn Royal blue, light brown and white color ne, an ƙawatashi da manya manyan sofas set biyu na gani na faɗa masu matuƙar taushi da daɗin zama,sai throw pillows dake kan ko wace sofa, daga tsakiyar parlorn round glass table ne an jera flower vase masu matuƙar kyau, daga saman ceiling ɗin wasu irin crystal chandeliers ne masu girman gaske , sai faskekiyar flat creen tv mai matuƙar girma sai kayan sauti dake gefe da gefen tv, sparkling floor lamps ne ajiye a ƙasa suna bada haske mai launika daban daban, ga dogayen curtains zagaye da parlorn an zuge su,daga can bakin glass wall wanda daga nan kana iya hangen main entrance ɗin shigowa part ɗin daga compound ɗin gidan,armchairs ne guda biyu ajiye daga tsakiyar su ɗan madaidaicin glass table ne,idan ka kalli ƙasan parlorn zaka ɗauka mirror ne yanda yake ɗaukar ido dan kana iya kallon kanka tsab. Daga cikin parlorn kana iya hangen katafaren dinning room, wanda aka ƙawatashi da haɗaɗen dinning table,ƙyataccen glass table ne mai mazaunin mutum shidda,wasu haɗaɗun chairs ne kewaye da table ɗin,daga saman ceilling ɗin dinning room ɗin ƙaton bulb ne ya haskaka ko ina na dinning room ɗin,ga wata irin zungureriyar floor lamp. cikin parlorn su ka ƙarasa Yumnah na gaba yayinda Nainarh ke biye da ita tana ƙarema parlorn kallo,tayi mamakin wannan part ɗin wanene dan yafi ko wane part dake gidan haɗuwa da tsaruwa duk da ba ko ina na gidan ta sani ba,wayar landline dake ajiye cikin parlorn Yumnah ta nufa, number kitchen ta kira,daga can ɗaya ɓangaren a kayi picking call ɗin. “na buɗe part ɗin ku nake jira” Yumnah ta faɗa tana rejecting ba tare da ta tsaya jin amsar da za'a bata ba,wata ƙofa Yumnah ta nufa ganin haka ne yasa Nainarh binta a baya,nan ma wani parlorn ne su ka shigo wanda yafi na farkon haɗuwa,komai na cikin shi blue White and gold color ne,glass door ne guda biyu a jere sai wasu corridor guda biyu dake hannu dama da hagu can ɗan nesa da ƙofafin,wanda na hannun hagu ya kasance gym room ne ɗayan kuma wani part ne mai zaman kanshi. ɗaya daga cikin ƙofofin dake jere Yumnah ta nufa tun kafin ta ƙarasa ƙofar ta shiga zugewa da kanta,cikin ɗakin ta kunna kai Nainarh na biye da ita a baya,wani irin haɗaɗen bedroom ne su ka shigo komai na cikin shi black,white and gold color ne, bedroom ɗin yana ɗauke da Royal bed mai matuƙar ɗaukar hankali,bed ɗin a shimfiɗe yake da tausassan bedsheet ga ƙaton blanket mai gashi gashi a jikin shi,gefe da gefen gadon nightstand ne mai ɗauke da bedside lamp,daga gaban gadon Ottoman table ne color ɗaya da bed ɗin,ƙasan ɗakin shimfiɗe yake da rug carpet mai taushi,wani irin ƙayataccen dressing mirror ne a cikin ɗakin daga gaban shi stool ne mai taushin gaske. cikin ɗakin su ka ƙarasa,dogayen curtains ɗin dake a sake Yumnah ta shiga zugewa,kafin ta nufi wata ƙofa wacce nake kyautata zaton dressing room ne mai haɗe da bathroom, buɗe ƙofar tayi,shiga ciki tayi ta bar Nainarh nan tsaye tana ƙarema bedroom ɗin kallo baƙaramin tafiya yayi da ita ba duk da babu wasu kaya a cikin shi. fitowa Yumnah tayi “gyaran ma bazai ɗauki wani lokaci ba saboda babu datti da yawa” jinjina kai Nainarh tayi “eh gaskiya babu wani datti sosai” “haka ne muje na duba sauran ɗakunan kafin su Ishrat ɗin su ƙaraso” da to Nainarh ta amsa mata,ficewa su kayi daga ɗakin,ƙofar dake kusa da wacce su ka fito su ka nufa itama ta glass ce kamar wacce su ka fito. Nan ma wani bedroom ɗin ne su ka shigo kusan duk abun da ke cikin wacan a kwaishe a nan banbancin color ne kawai shi wannan red and white color ne saɓanin wacan,mamaki gaba ɗaya ya kashe Nainarh yanzu duk mutum ɗaya keda wanann part ɗin kuma ba zaune yake a ciki ba, zata so ganin wannan shalelen dady. curtains ɗin shi kawai Yumnah ta zuge ta duba dressing room da toilet Kamar dai yanda tayi a wacan bedroom ɗin kafin su ka fice, corridor ɗin dake hannun damanƙofofin su ka nufa,ƙofofi ne guda biyu a wurin na glass daga in da su ke tsaye suna iya hangen komai dake ciki. tura ƙofar su kayi su ka shiga ciki,wani irin azabebben parlorn ne su ka shigo wanda ya doke gaba ɗaya falukan dake part ɗin,yafi su komai nesa ba kusa furniture's ɗin dake ciki ma kwata kwata ba irin tsarin su ɗaya da waɗancan ba,komi na cikin parlorn white color ne da ratsin gold,daga cikin parlorn kana iya hangen bedroom da swimming pool ɗin dake part ɗin ta hanyar glass wall dake mamaye da part ɗin gaba ɗaya. bedroom ɗin Yumnah ta nufa tana faɗin “gaskiya na fara kishi da shalelen dady” murmushin Nainarh ta saki tana biye da ita ba tare da tace mata ƙalla ba sai raba ido take a parlorn kamar ba'a niger ba,kusan suman tsaye Nainarh da Yumnah su kayi a yayin da su kayi arba da makeken bedroom ɗin da su ka shigo,riƙe ƙugu Yumnah tayi tana jinjina kai alamar mamaki tunda aka gina wannan sabon bata taɓa shigowa ba sai yau da dadyn yace su shiga a gyara,gaba ɗaya bedroom ɗin a mamaye yake da glass wall. bedroom ɗin yana da girma sosai dan tsab za'a iya gidan parlorn, bedroom, kitchen da toilet wadatattu a cikin shi, wani irin makeken king size bed ne daga can ɗan saman stape,a shimfiɗe yake da bedsheet mai taushi gaske da blanket kafi mage taushi,gefe da gefen shi nightstand ne,bed ɗin kusan rabi da kwatar shi a cike yake da pillows ƙasan bed ɗin na fitar da wani kalar haske,daga can gefen bed ɗin sofa ce mai masifar kyau color ɗaya da gadon itama ƙasanta na fitar da haske kalar na bed ɗin. daga cikin ɗakin kana iya hangen haɗaɗen gym room dake can ɓangaren hagu na ɗakin,wasu irin expensive machines ne a cikin shi kamar a gym center,sai toilet da shima kana hangen komai dake cikin sa. daga ɓangaren dama sliding door ne wacce idan aka buɗe ta ƴar baranda ce,cuddler chairs ne guda biyu ajiye a wurin daga tsakiyar su round glass table ne ajiye. jinjina kai Yumnah ta shiga yi tsarin part ɗin ba ƙaramin tafiya yayi da ita ba,wayar dake hannunta ta dannan, video ta shiga ɗaukar part ɗin,tundaga parlor har zuwa wannan yar barandar,babu in da bata ɗauka ba har toilet tukun su ka fice daga part ɗin su ka koma parlorn na biyu da su ka shigo. tsaf tsaf yake part ɗin saboda yawan gyarawa da ake duk da ba mai zama,ɗaya daga cikin sofas ɗin su ka nufa su ka zauna,daga cikin parlorn suna hange parlorn da su ka fara shigowa ta hanyar glass wall dake mamaye da parlorn. basu jima da zama ba Ishrat ta shigo tare da wasu masu aiki su biyar haɗi da ita su shidda kenan hannunsu ɗauke da mop da tsintsiya da detergent,in da su Nainarh su ke suka ƙaraso,cikin girmamawa su ka gaishe da su,amsa masu su kayi Yumnah na faɗin “yawwa Ishrat sai kun mai da hankali,ki fara nuna masu in da za'a fara gyarawa,yau har sabon part ɗin dady yace a gyara” gyaɗa mata kai Ishrat ɗin tayi,kasa masu aikin tayi gida biyu,biyu tace su gyara bedrooms da gym room,biyu kuma su gyara parlors ɗin da dinning room da kitchens,ita da ɗayar kuma su ka nufi part ɗin da su Yumnah su ka fito. babu ɓata lokaci masu aikin su ka shiga gyaran ko ina a cikin gidan,main parlorn part ɗin Yumnah da Nainarh su ka nufa, sliding door dake wurin su ka buɗe suka fita ƴar barandar dake wajen,a saman chairs ɗin dake wurin su ka zauna,daga nan in da su ke suna hangen main entrance ɗin shigowa part ɗin da compound ɗin gidan,suna iya hangen katafaren parking space dake wajen,rides ne da yawa a ciki an lulluɓe su da alama an ajiye su ne kawai. Kasa haƙuri Nainarh tayi har sai da ta tambayi Yumnah “wai nan part ɗin waye?,naji kina faɗin shalelen dady dama ba ke bace Auta ba,dady na da wani ƙaramin ɗa bayan ke?” kallon Nainarh da tayi maganar Yumnah tayi tana sakin dariya “wai dan kinji ina faɗin shalelen dady?,dady baya da wani ƙaramin ɗa ko ƴa bayan ni,ni ce Autar sa” “ok,amma nan part ɗin waye,mi yasa ki ke ce masa shalelen dady??” “part ɗin ya SAM ne shi ne yaron dady na uku,daga ya Naeem sai ya Adnan sai ya SAM sai ya Irfan sai Aunty Fa'iza sai ya Fa'iz sai Yumnah Auta” yumnah ta faɗa tana sakin murmushi, murmushi itama Nainarh tayi tana faɗin “masha Allah,Allah ya Albarkace ku ya rayama dady ku” da Ameen Yumnah ta amsa tana faɗin “tsawan shekara 18 kenan ya SAM baya ƙasar,tun ina ƴar shekara 2 da haihuwa ya koma US wajen granny da zama” “ikon Allah,yanzu zuwa zaiyi ne yasa dady yace a gyara part ɗin?” girgiza mata kai Yumnah tayi “babu wanda ya san ranar da zai zo,tunda ya tafi bai sake dawowa ba,kawai dai dady yana sa a gyara part ɗin ne duk ranar friday” “sorry kar kice na cika shiga abun da ba ruwana,amma miyasa ya tafi tsawan wannan shekarun bai dawo ba??” murmushi Yumnah ta saki “nima ban sani ba,kawai dai na taso naga baya gidan kuma bai taɓa zuwa ba” jinjina kai kawai Nainarh tayi ba tare da ta sake cewa komai na,amma lamarin ya bata mamaki wane irin ɗa ne zaiyi nesa da iyayen shi tsawan waɗannan shekaru ba tare da ya waiwaye su ba,haka nan taji tana son sanin dalilin barin shi gida da rashin waiwayar iyayen shi tsawan wanann shekarun,wani ɓangare na zuciyarta na gargaɗarta da shiga abun da babu ruwanta, Yumnah ce ta katse mata tunanin da take ta hanyar faɗin “next week fa muke komawa school,ni wallahi duk na ƙagara next week ɗin tayi dan na gaji da zaman gida” yanayin fuskar Nainarh ne ya canza da alama ba tayi farin cikin da labarin komawar ta su makaranta ba “ya dai,baki son komawa ne?” Yumnah ta faɗa tana tsareta da idanu, girgiza mata kai kawai Nainarh tayi ba tare da tace ƙala ba,itama Yumnah bata sake cemata komai ba dan ta san dalilinta naƙi son a koma,amma ya za tayi dole tayi haƙuri ta koma komi ƴan school ɗin su za su ce. *ASO VILLA* Gaba ɗaya a halin gidan sun hallara a katafaren dinning room dake villa ɗin domin breakfast, Zaabith na zaune saman chair dake kallon wacce su Ammar ke zaune,sai Irfan da Waseef dake zaune kusa da juna,sun duƙar da kai,magana su ke ƙasa ƙasa idan ba kana kusa da su sosai ba ba zaka iya jin mi su ke cewa ba. kallo Zaabith dake cikin abinci hankali kwance hajiya salima tayi “lafiya ka fito kai kaɗai,ina kainart ɗin take,ko har yanzu jikin ne??” da sauri ya ɗago yana kallon mahaifiyar tashi da tayi magana. “zata fito,ta tsaya wani abun ne ciki” Zaabith ɗin ya faɗa yan maida kanshi ga abincin da yake ci,wani ɗan iskan kallo Ammar da Aman su ka watsa mashi ba tare da wani ya lura da su ba. jinjina kai hajiya salima tayi tana kai dubanta ga sarah dake tsaye “maza ki kira man ita sarah” da to sarah ta amsa tana juyawa tabar wajen zuwa part ɗin Zaabith. bayan kamar minti biyar sarah ta dawo “lafiya, tana ina??” hajiya salima ta faɗa tana kallon bayan sarah ganinta ita kaɗai “gata nan fitowa ranki ya daɗe”jinjina kai hajiya salima tayi tunda ta tunkaro dinning room ɗin ya kafeta da ido,da yake chair ɗin da yake zaune tana fuskantar ƙofar shigowa dinning room ɗin,baƙar jallabiya ce a jikinta ta lulluɓa mayafinta ta rufe rabin fuskarta da har yanzu sawun hannunshi na nan raɗau kamar yanzu ne ya mareta. wani irin kallo ya shiga jifanta dashi wanda ita kaɗai ta san ma'anar shi,saurin kauda kai tayi kamar bata ganshi ba, murmushi hajiya salima ta saki lokacin da kainart ɗin ta ƙaraso ciki. da sauri Zaabith ɗin ya miƙe yana ja mata kujerar dake kusa da shi,alama yayi mata data zauna yana sakar mata wani soft smile,ɗauke kai tayi kamar bata ga abun da yake nufi ba ta nufi inda su Ammar suke,tashi Aman yayi ya koma kujerar dake kusa da wacce ya tashi,murmushi ta saki tana shafa kanshi,zama tayi a tsakiyar su. “ina kwana momy,kin tashi lafiya” “lafiya lau Alhmdllh, kainart ya ƙarin ƙarfin jikin” da Alhmdllh ta amsa mata,da sauri sarah ta ƙaraso in da kainart ɗin take tayi serving ɗinta. har time Zaabith na tsaye mamaki ne duk ya cika shi,kallon shi momy tayi “kai kuma lafiya kayi ma mutane tsaye a ka??” “bakomai” shine kawai abun da yace ya koma mazaunin shi ya zauna. “ashe baki jin daɗi Aunty kainart?” waseef ya faɗa yana kai duban shi gareta “naji sauƙi waseef” “Allah ya ƙara sauƙi,amma shine baki ce na zo na dubaki ba” Irfan ya faɗa yana wani ya mutse fuska. ɗan zaro ido tayi “irfan nace ka dubani,rufa man asiri in ka ganni lahira kaini a kayi” dariya Irfan ɗin ya saki kamar ba shi ba “nafa manta tsoron Allura ki ke” dariya waseef ya kwashe da ita har da su Ammar “gaskiya Aunty ya kamata ki rage wannan tsoron,akwai fa su Ammar a gabanki,amma kiyita abu sai kace farar kura” a cewar waseef. jifar shi tayi da spoon ɗin dake hannunta saurin duƙewa waseef yayi,hakan da yayi ba ƙaramin dariya ya ba su,zuba masu ido kawai Zaabith yayi yana kallon su. gyaran murya su kaji daga bakin ƙofar shigowa dinning ɗin saurin kai duban su ga magidancin dake tsaye cikin shigar Jogging suit launin blue black,a tsarin hallita dogo ne,launin fatar jikinshi fara ce ba irin sosai ɗin nan ba,sumar kanshi da gemun shi farare ne tas da alama rina launinsu yayi ba dan ya kai shekarun da za su koma haka ba,kunnen shi a manne yake da ear phone haka kyakkyawar fuskar shi a manne take baƙin glass. Uncle Ahmad kenan, mahaifin Zaabith,Aunty Nadiya da Waseef,daga dady sai shi,shine President ɗin Nigeria na wannan lokaci. da gudu Ammar da Aman su ka nufe shi saurin zame glass ɗin dake fuskar shi yayi ya tura shi a aljihun wando shi,faɗawa jikin shi su kayi suna mashi oyoyo, murmushi ya saki yana shafa sumar kansu,hannun su ya kama su ka ƙarasa cikin dinning room ɗin “granfa shine yau ka fita ba tare da mu ba?” a cewar Aman “bacci ku ke ne time ɗin,amma gobe idan zan fita tare da ku zan fita” “gobe ai muna gidan big daddy tare da shi zamu fita” “au haka ne?” eh su ka bashi amsa,jinjina kai grandfa ɗin yayi “shikenan idan kun dawo sai mu fita tare” ihun murna su ka saki suna koma mazaunin su. gaishe dashi su Zaabith su ka shiga yi yana amsa masu cikin kulawa,sarah dake tsaye ma gaishe dashi tayi yayin da take matsowa domin tayi serving ɗin shi,da katar da ita hajiya salima tayi ,da kanta ta shiga serving ɗin shi. “good morning” ta furta dai dai kunnen shi,kashe mata ido ɗaya yayi yana sakar mata murmushi, mazaunin ta dake kusa da nashi ta koma ta zauna tana sakin murmushi. kallon Zaabith dady yayi “zaabith ka kuwa haɗu da Muhsin??” “A'a dady,ya dai kirani jiya yace yau su ke sa ran isowar su Mubarak” “kai yaushe za ka tafi can kenan?” “ƙarfe ɗaya su ke sa ran isowa,sai na tafi after Isha” wani irin sanyi ne ya ratsa zuciyar kainart jin yau zai koma “good” kawai dadyn yace ba tare da ya sake cewa komai ba,kallon Zaabith momy tayi “yau zaka koma ne?” “A'a,sai next week” ya bata amsa, kainart ba hakan ta so ba ta so ace tafiya zaiyi ko ta samu ta huta da uƙubar shi. Dady da Zaabith ɗin su ka fara tashi sai Irfan da Waseef,tashi kainart tayi itama ta fice aka bar momy da su Ammar. *Big Daddy's house* wajen awa biyu su ka ɓata wurin gyaran part ɗin, gyara su kayi mashi na musamman ko ina ka shiga sai tashin ƙamshi yake haɗe da sanyin AC. “sannunku da ƙoƙari Ishrat,wannan idan dady ya gani dole ya baku tukwici” murmushi kawai Ishrat ɗin ta saki “ai ina jin ku saki curtains ɗin kawai a kashe bulbs,tunda an kammal” da to su ka amsa mata suna nufar bedrooms da falukan dan ciki umarninta,duk wani kayan wuta da su ka san sun kunna sai da su ka kashe shi hatta AC ba su bari a kunne ba,kayan da su kayi amfani da su suka kwashe,ficewa su kayi daga part ɗin bayan sun kammala. ƙofofin bedrooms ɗin Yumnah ta rufe tukun suma su ka fice, direct part ɗin dady ta nufa Nainarh kuma ta nufi bedroom ɗin su,bata samu dady a part ɗin ba har ya fice,key's ɗin kawai ta ajiye ta fice. A zaune ta samu Nainarh bakin bed,da kallon mamaki ta bita “yanzu Nainarh maimakon ki shiga kiyi wanka sai ki zauna,ni ban san mi yasa ki ke haka ba komai sai nace kiyi sai kace wata ƙaramar yarinya?” “ba haka bane,naga ke sauri ki ke saboda fitar da za kuyi ,shine na bari idan kin fito sai na shiga” wani ɗan iskan kallo Yumnah ta watsa mata “mi ki ke nufi da fitar da za muyi,kina nufin ban da ke??” “haɗuwa fa za kuyi da family ku ni miye nawa na zuwa” “gaskiya Nainarh bana jin daɗin irin wanann abun,ni kawai ki tashi ki shiga wanka karma su mom su shirya su fara jiran mu” “yumnah gaskiya ni bazan je ba,taro ne na familyn ku, taya za ayi naje” “wallahi sai kin shirya mun tafi kin ma ji na rantse,kullum naita fama dake kamar wata yarinyar goye” Yumnah ta faɗa tana nufar dressing room ɗin ta. tashi Nainarh tayi ta shiga wanka ta so Yumnah ta ƙyaleta dan bata san wane irin kallo family ɗin su za suyi mata ba ganin ta shigo cikin su,ba lallai suyi maraba da ita ba. bata jima da shiga wanka ba Yumnah ta dawo bedroom ɗin jikinta ɗaure da towel,zama tayi gefen bed ɗin, Nainarh na fitowa ta tashi ta nufi toilet ɗin har ta kai bakin ƙofa ta tsaya “kayan da zamu sa na nan na fito mana da su” gyaɗa mata kai Nainarh tayi ƙofar bedroom ɗin ta buɗe ta shiga, dressing room Nainarh ta nufa, dressing mirror ta nufa,zama tayi saman stool, expensive body lotion ɗin dake jere saman dressing mirror ta ɗauka,shafama jikinta ta shiga yi, simple make up tayima fuskarta Masha Allah tayi kyau abunta. tashi tayi ta nufi kayan da Yumnah ta ɗauko masu, expensive egyptian abayas ne Black color anyi masu ado da royal blue ɗin yadi a hannun,sunji adon stones a jikin su sai sheƙi suke. ɗaya daga cikin rigunan ta ɗauka ta zura a jikinta ba ƙaramin kyau tayi ba kamar wata balarabiya,kallon kanta tayi a gaban mirror ita kanta ta yaba da kyawun rigar a jikinta,baby ribbon ta ɗauka ta ɗaure gashin kanta,mayafin rigar ta ɗauka tayi rolling, masha Allah kawai zamu ce Nainarh Allah yayi mata wani irin sanyi kyau,ba ƙaramin haska farar fatar ta rigar tayi ba,shagala tayi da kallon kanta a mirror. “wayyo Allah na sister Nainarh ke ce haka?,kai masha Allah kinga yanda rigar nan tayi maki kyau kuwa?, wallahi kamar mutum ya saceki ya gudu,karfa ki rikita mana samarin family a kasa gane kan su” dariya Nainarh ta fashe da ita jin irin sambatun da Yumnah ke mata,sosai Yumnah ta shiga zuzuta kyan da Nainarh tayi,ita kuwa ban da dariya babu abun da take. “bari nayi sauri na shirya ko na samu nayi maki pics kar wannan wankan ya tafi haka nan” ta faɗa tana nufar dressing mirror. shaf shaf tashiga shiryawa,itama simple makeup tayima fuskarta,rigarta ta ɗauka ta zura Nainarh na daga tsaye sai Binta da ido take harta kammala shiryawa,itama ba ƙaramin kyau tayi ba abunka ga farar fata sai rigar ta sake fito da haskenta. jinjina kai Nainarh tayi tana faɗin “masha Allah kema ba ƙaramin kyau ki ka yi ba” “ban kai ki ba” Yumnah ta faɗa tana ɗaukar wayarta, hand bag ta ɗauko masu mai shegen kyau tare da sunglasses mai ɗaukar ido. bedroom su ka nufa Nainarh ta ɗauki wayarta dake saman nightstand ajiye,ficewa su kayi daga ɗakin zuwa parlor,anan su ka ɓaje kolin ɗaukar photo, photo Yumnah ta shiga ɗaukar Nainarh ba ƙaƙƙautawa,bayan nan ta kira Ishrat tayi masu a tare. A tare su ka shigo parlorn,a bakin ƙofar su kaci burki cikin shigar shadda gezna fara ƙal sai ɗaukar ido take,kan su a sanye yake da hula, kwantacciyar sumar kan su sai sheƙi take. fuskar shi a tsuke take kamar ko da yaushe saɓanin ta ɗan uwan shi dake ɗauke da murmushi yana kallon Nainarh da Yumnah da su ka juya ma ƙofa baya, kallo ɗaya yayi masu ya ɗauke kai yana kai dubanshi ga Ishrat dake ɗaukar su photo,wani ɗan iskan kallo ya watsa mata wanda yayi sanadiyar hautsinawar ƴan hanjin cikinta. saurin sauke wayar tayi ƙasa har tana sake ɗaukar su wani pic ɗin ba tare da saninta ba,da mamaki Yumnah ke kallonta “Ishrat wai lafiya ki ka tsaya sauri muke,ƙara mana ɗaya kafin mom ta fito” Yumnah ta faɗa tana kallonta cikin rawar murya Ishrat ta furta “barkan ku da zuwa ,ina wuni” ta furta da sauri Yumnah takai dubanta ga... _*Ep 19_20*_ *Bound by fate,freed by love, A romantic Odyssey*❤💘💘 ______________________________ da sauri Yumnah takai dubanta ga Irfan da Waseef dake tsaye a bayan su, murmushi ta saki “laa ya Irfan ya waseef ku ne?” yumnah ta faɗa cikin nuna jin daɗin ganin su, wani irin faɗuwa gaban nainarh yayi jin sunan da yumnah ta ambata, idan bata manta ba shine mutumin daya shigo ɗakin su ya sameta daga ita sai towel. wani irin takaici da kunya ne su ke rufeta ji tayi ina ma ƙasa zata tsage ta shiga,ko ƙwaƙwaran motsi kasawa tayi. da sauri yumnah ta nufe su “kun zo a dai dai, Ishrat yi mana photo” nainarh ta faɗa tana shiga tsakiyar su, saurin kallon Irfan da yayi kicin kicin da fuska Ishrat tayi,kasa ɗaukar photon tayi saboda hararar daya watsa mata, ƙofar parlorn mom ya nufa ba tare da ya tsaya photon ba, da kallo kawai yumnah da Waseef su ka bishi, Nainarh kuwa tsananta faɗuwa gabanta yayi lokacin da taga giftawarshi ta idonta. taɓe baki yumnah tayi tana kallon Waseef “ya Waseef wai mike damun ya Irfan ne?” “ban sani ba yumnah, kin san halinshi sometimes ba iya mashi ake ba” “Allah ya kyauta,Ishrat yi mana kinji” yumnah ta faɗa, saurin dakatar da Ishrat ɗin waseef yayi yana nuna Nainarh data juya masu baya. “wacece wannan ita bazata zo muyi photon ba” “laa sister Nainarh zo muyi photo tare da ya Waseef” yumnah ta faɗa tana nufar Nainarh ta kamo hannunta zuwa in da Waseef ɗin yake tsaye. “sannu pretty, muyi photo ko?” Waseef ya faɗa yana sakar mata murmushi, murmushi itama ta sakar mashi tana gaishe da shi, cikin kulawa ya amsa mata, tsakiyar su ya shiga, photon Ishrat ta shiga ɗaukar su a nan Fa'iza ta same su itama ta ɗau wankan Abaya simple makeup ne a fuskarta ba ƙaramin kyau tayi ba. shiga itama tayi a kayi photon da ita,photona sosai su ka ɗauka Waseef sai da yasa Yumnah tayi masu su biyu shida Nainarh,Fa'iza ma sai da a kayi mata da Nainarh, sai da su kayi mai isar su tukun su ka bari a nan parlor su ka zauna suna kallon photunan. mom ce ta fito Irfan na biye da ita, ta ɗau wankan Arabiyan Embellished open Abaya launin Royal blue tayi rolling da Veil ,babu makeup a fuskarta amma ba ƙaramin kyau tayi ba, cikin parlorn ta ƙaraso Irfan na riƙe da hand bag ɗinta. “mom kinyi kyau sosai, dan Allah muyi photo dake kema” yumnah ta faɗa tana nufo mom ɗin “lokaci ya ƙure Yumnah,na san mu kaɗai ne bamu je ba, ki bari sai wani lokaci” ɓata fuska yumnah tayi ba haka ta so ba. ficewa su kayi daga parlorn gaba ɗayan su Ishrat na masu a dawo lafiya, parking space su ka nufa, motar Irfan mom da Waseef suka shiga yayin da Yumnah da Nainarh su ka shiga motar Fa'iza,key su kayi ma motocin su ka fice daga gidan zuwa gidan Abbah dake cikin Estate ɗin. Tafiya su ka yi mai ɗan nisa kafin su ka iso gidan Abbah, katafaren luxury Villa ne na gani na faɗa,yaji kayan alatu kamar baza'a mutu ba,a katafaren parking space ɗin gidan su kayi parking Wanda yake cike da expensive rides masu matuƙar kyau. fitowa su ka shiga yi ɗaya bayan ɗaya,a tare su ka nufi entrance ɗin shiga gidan mom da su Irfan na gaba yayin da Yumnah da su Nainarh ke bayan su, yanzu ma hand bag ɗin mom ce a hannun Irfan, bakin su ɗauke da sallama suka shiga katafaren parlorn gidan wanda aka ƙawatashi da manya manyan sofas masu matuƙar kyau da tsada. matasan ƴan mata ne zaune saman sofa kowacen su ta ɗauka wanda Egyptian Abaya ɗaya tayi rolling da veil ɗin yayinda ɗaya kanta yake a buɗe,zallar gashin kanta ne kawai, gaba ɗaya wayoyinsu ne a hannunsu sun tasa gaba sai aikin latsawa su ke. Kairiyyah da Noor kenan, Kairiyyah ta kasance ɗiya ga Aunty Adama Noor kuma ɗaya ce ga Uncle mutallaf. sake ƙwaɗa sallama Yumnah tayi yayin da Irfan da Waseef su ka nufi glass elevator dake cikin parlorn. saurin ɗago kai su kayi,riƙe ƙugu Yumnah tayi tana jijjiga jiki haɗi da kauda kai gefe,da sauri ƴan matan su ka nufo mom. hugging ɗin ta su kayi cikin girmamawa wacce tayi rolling veil ta gaishe da mom, da fara'a mom ta amsa mata. “lafiya lau Kairiyyah,ya school?” “lafiya lau Alhmdllh mom”mom ta faɗa “momy ina wuni” ɗayar ta gaishe da mom ɗin “lafiya lau Alhmdllh,Noor zuwan yaushe?” “jiya cikin dare mu ka zo” “masha Allah harda dadyn ku kuka zo ne?” Eh taba mom ɗin amsa, elevator mom ta nufa tana faɗin “bari na shiga wajen Abbah” da to su amsa mata, hugging ɗin Fa'iza su kayi cikin kulawa su ka gaishe da ita,kishi duk yabi ya cika Yumnah ganin sun ƙi kulata,kama hannun Nainarh tayi. “mu tafi kinji sister” da sauri Noor tabi bayan su, hugging ɗin Yumnah tayi ta baya “haba sister ba dai fushi ki ka yi damu ba?” fisgewa Yumnah tayi “ni ki ƙyale ni” “bazan ƙyale ki ba,sai kinyi haƙuri” murmushi Fa'iza tayi tana nufar su ita da Kairiyyah, Nainarh bin su kawai take da ido. “sister sannu” Kairiyya ta faɗa tana kallon Nainarh, murmushi Nainarh ta sakar mata tana amsa mata sannu da tayi mata. lallashin Yumnah Noor ta shiga yi da ƙyar su ka samu ta saki fuska,part ɗin Abbah su ka nufa gaba ɗayan su. *MOM*💫 a second floor elevator ta sauketa, corridor da zai sadata da part ɗin Abbah ta nufa,tunda ta tunkaro ƙofar shiga part ɗin take jin muryoyin su suna fira cikin nishaɗin, a bakin ƙofar shiga ta tsaya,a hankali ta tura ƙofar ta shiga. Masha Allah katafaren parlorn ne da yaji kayan more rayuwa, manya manyan sofas ne set uku masu matuƙar kyau da tsada ga taushi kamar audiga,haɗaɗiyar rug carpet ce shinfiɗe a ƙasa, kyakkyawan Dattijo ne mai cikar kamala cikin shigar farar Alkyabba a kishingiɗe saman rug carpet yayi matashi da tumtum yayin da ƴaƴan shi ke kewaye dashi sun saka shi tsakkiya,fira suke cike da nishaɗin. su goma ne ƴaƴan Abbah dady shine babba daga shi sai uncle Ahmad daga su sai uncle Mustafa da uncle Ubaid daga su sai uncle mutallaf daga shi ne sai barrister Hashim da Aunty mariya daga su sai Aunty Safeenah da uncle Khamis daga su sai Aunty Adama ita ce Autar Abbah. gaba ɗayan su ne a parlorn uncle Khamis ne kawai babu shima baya ƙasar ne tsawan shekara 19 kenan rabon shi da ƙasar,shi ka ɗai ne a cikin su baya da Aure. Dady na daga hannun daman shi yayin da dady Ahmad ( mr president ) ke kusa da shi sai Uncle Mustafa, Uncle ubaid da uncle Hashim, ɓangaren hagu kuma Aunty mariya,Aunty safeenah da Aunty Adama ne sai uncle mutallaf dake tsakiyar su,Irfan da Waseef na daga saitin kan Abbah zaune,gaba ɗaya hankali su na kan Abbah dake basu labarin yarintar su dady cike da nishaɗi. sallamar mom ce ta katse masu firar da suke,gaba ɗayan su suka kai duban su gareta, murmushi ne ya bayyana akan fuskar Abbah da alama yaji daɗin zuwanta,kaf cikin surikan sa babu wacce yafi so sama da mom,tamkar ɗiya haka ya ɗauketa,idan ka cire barrister Hashim da Aunty Safeenah babu wanda baiyi farin ciki da zuwanta ba,da sauri Aunty Adama ta tashi fuskatar ɗauke da murmushi ta nufo mom. hugging ɗin juna su kayi hakan ba ƙaramin ɓata ran Aunty Safeenah yayi ba,kauda kai tayi gefe tana jan tsaki, cike da kewar juna suka gaishe da juna,cikin parlorn su ka ƙarasa,wurin Abbah mom ta nufa fuskarta ɗauke da murmushi. zama tayi kusa dashi “in wuni Abbah,mun sameku lafiya?” “lafiya lau Alhmdllh,ya gidan ya kuma aiki” “lafiya lau” Masha Allah Abbah ya furta,duban ta ta kai ga dady Ahmad cike da girmamawa ta gaishe da shi,cikin kulawa ya amsa mata yana tambayar Yumnah. ɗaya bayan ɗayan tabisu tana gaishe da su,cike da kulawa su ke amasa mata in ka cire barrister da Aunty Safeenah da su kayi kamar ba su san da su take ba,hakan kwata kwata bai dameta ba dan idan da sabo ta saba da halin su,dady baiji daɗin hakan ba ya rasa miye matsalar ƴan uwanshi da matar shi. “Ashe abun da ya faru da Asma'u kenan?, ubangiji Allah yayi mata mafita,Allah ya kuɓutar da ita,su kuma wanda su ka da baibaye ta da sharrin Allah yayi gaggawar tona masu Asiri” Abbah ya faɗa da Ameen ya Allah Abbah su ka amsa banda uncle Hashim da yayi tsit kamar baya parlorn “Allah ya kuɓutar da ita ya kyauta gaba” a cewar uncle Ahmad da Ameen su ka amsa suma,ɗaya bayan ɗaya su ka shiga yi mata jaje in ka cire Aunty Safeenah data miƙe ta nufi ƙofar fita, barrister Hashim kuwa lumshe idonshi yayi kamar mai bacci . “saffenah!!” Abbah ya kira sunanta,dakatawa tayi da tafiya ta juyo tana fuskantar shi “ina zaki kowa na nan?” “zan shiga wajen mama ne,naga an gama firar zumunci tunda har bare sun fara zuwa shiy...” bata ƙarasa ba sakamakon tsawar da dady ya daka mata “Abbahn ki ke faɗama haka?,maza ki dawo ki zauna kafin ranki ya ɓaci” murmushi kawai mom tayi bata so dady yasa baki ba. rai a ɓace ta nufi wajen zamanta zata zauna “jeki kawai” Abban ya faɗa,babu ko kunya ta juya ta fice,kauda kai kawai dady yayi da alama baiji daɗi ba,kallonshi Abbah yayi yana sakin murmushi haɗi da girgiza kai. A bakin ƙofa Aunty Safeenah taci karo da su Yumnah, fuskar su ɗauke da murmushi su ka gaishe ta,ta amsa ma kowa amma banda Yumnah da Nainarh da tabi da wani irin kallo mai wuyar fassarawa. hankali Nainarh ba ƙaramin tashi yayi ba da irin kallon da Aunty Safeenah tayi mata,duk sai taji wani iri dama ba tayi niyyar zuwa ba Yumnah ta jawota tasan dama ba dole bane dangin Yumnah su sota ba. ganin yanayin data shiga ne yasa Fa'iza kamo hannunta cikin nata,da murmushi akan fuskarta tace “muje ko” tura ƙofar parlorn tayi su ka shiga bakin su ɗauke da sallama,gaba ɗaya parlorn su ka kai duban su gare su. Amsa masu sallamar su kayi in ka cire uncle mutallaf daya kafe Nainarh da ido ko ƙyaftawa baya yi uncle Ahmad ma kallon sani yake mata,har suka ƙaraso cikin parlorn uncle mutallaf bai janye idanunshi daga kanta ba har sai da Abbah yayi mashi gyaran murya tukun yayi sauri kauda idoshi daga kanta ya kalli Abban,hararar wasa Abbah ya watsa mashi. saurin duƙar da kai yayi duk sai yaji kunyar kamashin da Abbah yayi yana kallonta yasan Abbah zaiyi tunanin wani abu shi kuwa har ga Allah kama tayi mashi da wacce ya sani. zama su kayi kan rug carpet ɗin cikin kulawa su ka gaishe da su suna amsa masu,nuna Nainarh Abbah yayi da hannu “in ku ka samu wannan mai kama da mariyata?” gaba ɗayan su suka kai duban su ga Nainarh sai da Abbah ya faɗa su kaga kamaninta da Aunty mariya in ka cire mom da dady dan su sunfi ganin kamaninta da Carol ƙanwar mom,sai yanzu uncle mutallaf ya fahimci da wacce take mashi kama. kallo ɗaya Irfan da barrister suka yi mata suka kauda kai “ƴan mata yaya sunan ki?” Aunty mariya ta faɗa tana kallon Nainarh “NAINARH” ta bata amsa,jinjina kai Aunty mariya tayi “masha Allah, Nainarh suna mai daɗi” Aunty mariya ta faɗa, murmushi Nainarh ta saki a hankali ta furta “nagode” juyawa Aunty mariya tayi ta kalli mom,fahimtar abunda Aunty mariya ke nufi ne yasa mom faɗin “ɗiyar Asma'u ce” “Allah sarki” Abbah ya faɗa cike da jin tausayin Nainarh,babu wanda baiji tausayinta ba jin itace ɗiyar Hajiya Asma'u, barrister Hashim kuwa ko a jikinshi. “sannu kinji Nainarh Allah ya kuɓutar da mahaifiyar ki” a cewar Abbah ,gaba ɗaya parlorn su ka amsa da “Ameen ya Allah” fira suka shiga yi cikin kwanciyar hankali. Noor tunda su ka shigo Irfan ke Binta da wani irin narkaken kallo,itama tunda ta zauna hankalin ta na kanshi,wasu alamomi yake mata da ido wanda daga ita sai shi su ka san ma'anar su,sosai su ka shagala da kallon juna ƙarshe da su ka gaji tashi Irfan ɗin yayi ya nufi ƙofar fita shida Waseef ,zambur ta miƙe tabi bayan su babu wanda ya lura da ita sai Yumnah da Kairiyyah dake kusa da ita. A parlor Waseef ya tsaya Irfan kuma ya nufi back yard,wassef na zaune sai ga Noor,nufoshi tayi cikin takun sauri “ya Waseef yana ina?” “back yard” ya bata amsa,da sauri ta nufi ƙofar da zata sadata da back yard ɗin gidan, gyara zaman shi yayi kan sofa yana ciro wayar shi daga Aljihu. tun daga nesa ta hango shi ya jingina da wall gaba ɗaya hannuwanshi na cikin Aljihun wandon shaddarshi, idanunshi a lumshe suke kamar mai bacci,a hanzarce ta ƙarasa in da yake tun kafin tayi magana ƙamshin turarenta ya sanar da shi isowar ta,a hankali ya buɗe idanunshi a kanta. wani irin kallo ya shiga binta da shi yayin da ita kuma ta marairaice mashi fuska kamar zata sa mashi kuka. “shine daka shigo kayi kamar baka ganni ba ko?” ta faɗa a shagwaɓe,buɗe mata hannuwanshi yayi alamar ta zo gare shi, ba tayi musu ba ta nufe shi,faɗawa tayi jikin shi, hugging ɗin juna su kayi tightly kamar za su koma abu ɗaya. matso da baƙin shi yayi saitin kunnenta,magana ya fara yi mata kamar mai raɗa “duk laifinki ne miyasa kin san tare za ku zo da dady baki faɗa man ba,kin san yanda nayi kewarki kuwa?” “ina so nayi surprising ɗin ka ne shiyyasa”ta faɗa a shagwaɓe “kinyi missing ɗin na?” “sosai ma,har gani nake kamar bama sauri da muna tafiya” “amma shine baki nemi ni ba ki ka zo part ɗin Abbah?” “saboda na san anan zan same ka” “da ban zo ba fa?” “nama san bazaka ƙi zuwa ba” raba jikin su yayi yana jan hannunta su ka nufi wasu haɗaɗun chairs dake back yard ɗin,zama yayi saman ɗaya daga cikin kujerun yana nuna mata ta kusa da shi,maƙe mashi kafaɗa tayi alamar bazata zauna ba,hannunshi ya miƙa mata babu musu ta kama jawota yayi zuwa jikinshi yayi mata mazauni akan laps ɗin shi, murmushi ta saki tana lafewa a jikin shi. shafa doguwar sumar kanta dake a buɗe ya shigayi yayin da ita kuma tayi lamo har wani lumshe ido take. *😳 Irfan⁉️* idan mu ka koma parlorn Abbah,sun jima suna fira sai da lokacin zuwa masallaci yayi tukun su ka tashi,ficewa mom tayi tare da su Aunty Mariya da su Yumnah, wani ɗan corridor dake kallon parlorn Abbah su ka nufa. wani irin hamshaƙin parlorn ne su ka shigo,yaji kayan alatu kamar a gidan sarakai,ga wasu jigunannun sofas masu rai da lafiya har set biyu. Aunty Safeenah ce zaune saman sofa mai mazaunin mutum uku yayin da mamy ke hakimce kusa da ita ta ɗau wankan less ɗinkin riga da zani kamar ko wane lokaci zaka samu fuskarta da makeup,sofa dake kusa da su Hajiya fatilah ce matar uncle mutallaf tare da Hajiya Halima matar Uncle Ubaid sun ɗau wankan tsadadden less mai shegen kyau,fuskarnan ta su tasha makeup hannuwan su a cike su ka da ƴan hannu da zobba na zallar zinari. Mama Ameena ce hakimce saman sofa mai mazaunin mutum biyu dake kallon ƙofar shigowa parlorn,super atamface a jikinta anyi mata ɗinkin riga da zani kalar na su na tsaffi,ta dafka uban ɗaurin ɗankwalinta kamar koda yaushe. cikin parlorn su mom su ka nufo bakin su ɗauke da sallama,tsuke fuska mama tayi lokacin da idanunta su ka sauka kan mom,taɓe baki mamy tayi tana kauda kai. Amsa masu sallamar su kayi in ka cire mamy dake cin ɗaci sai wani buɗar hanci take, har gaban sofar da mama take zaune mom ta ƙara so,cikin girmamawa ta gaishe da ita,cike da izza tana wani yamutse fuska ta amsa mata a taƙaice,lamarin yaba Nainarh mamaki ita da abun ya zama sabo a idonta amma duk wanda ke parlorn yasan cewa babu jituwa tsakanin mama Ameenah da mom kwata kwata bata sonta. Mama Ameenah matace ga Abbah,ita ta haifi Aunty Adama,ita ka ɗai ta rage a matan Abbah,kwata kwata bata ƙaunar mom. “mun same ku lafiya?” “ga zahiri kuwa kin gani” mama Ameenah ta faɗa tana nuna kanta da hannu, murmushi ne ya bayyana akan fuskar mamy da su Hajiya fatilah da alama abun yayi masu daɗi. shiru mom tayi ba ta sake cewa komai ba,gaishe da mama su Yumnah su kayi, a taƙaice ta amsa masu tana sauke idonta kan Nainarh da duk tasha jinin jikinta. “ita kuma wannan ina aka sameta?” mama Ameenah ta faɗa tana nuna Nainarh da hannu,faɗuwa gaban Nainarh yayi,gaba ɗaya parlorn duban su suka kai ga Nainarh. “ɗiyar Aminiyata ce Hajiya Asma'u” mom ta faɗa,jinjina kai mama tayi “ziyara ta zo maki ko mi?” “A'a wani iftila'i ne ya faɗama mahaifiyar ta,to shine na daw...” bata ƙarasa ba mama tayi saurin dakatar da ita “to sai aka yi yaya,zama mi take cikin zuri'ata,ita mahaifiyar ta ta bata da dangi ne da bazaki barta a hannunsu ba,?” “ba haka bane mama,zaman...” “dan Allah dakata mana Zulaihart, wai sau nawa zance karki sake kirana da mama,banda jaza masifa ina ni ina haihuwar dangin sheɗan wanda Allah ya tsinemawa,ko nayi maki kama wannan tsohuwar banzar mai yawo ƙwauri waje??” ƴar dariya mamy tayi tana kallon su Hajiya gaje “Allah ya huci zuciyarki” mom ta faɗa tana tashi, ta nufi ƙofar fita daga parlorn, Yumnah idanunta har sun cika da hawaye bakomai yasa bata son zuwa part ɗin Abbah ba idan ba ranar Friday ba sai dan saboda wannan cin mutuncin da mama kema mom,tashi tayi tana kama hannun Nainarh da duk jikinta yayi sanyi. Fa'iza ma ranta ba ƙaramin ɓaci yayi ba,tashi itama tayi ta bi bayan su da kallon mamaki mamy tabita har ta fice daga parlorn. rai a ɓace Aunty Adama ta kalli mama Ameenah “gaskiya wannan abun mama da ki ke a gaban ƴaƴa da jikokin ki bai dace ba,haba dan Allah da shekarunki zaki zauna yara na zugaki kina abu irin haka” “kamarya yara na zugata, mi kike nufi Adama?”mamy ta faɗa rai a ɓace “da mahaifiyata nake magana ba dake ba,karki ƙara sa man baki,kuma duk abunda take akwai mai zugata sama da ku ne?” tsantsar mamaki ne ya bayyana a kana fuskar mamy wai yau ita Adama ke faɗama haka “lallai Adama Ni kike faɗa ma haka saboda Zulaihart?” “fiye da haka ma sai ta faɗa maki mabaruka,gaba ɗaya ku babu mai hankalin data san abun da ya kamata,mama shekarunta sun ja tunaninta baya yake komawa,maimakon ku zama masu bata shawara idan kunga za tayi abun da ba dai dai ba amma saboda son zuciya kullum cikin birkita mata tunani kuke,babu wanda yafi bani haushi a cikin kuka sama da ke Safeenah” Aunty Mariya ta faɗa rai a ɓace tana kallon Aunty Safeenah “ni mi nayi Aunty mariya,babu ruwana fa a cikin wannan abun?” “dama zaki ce haka mana,akwai wanda ya ɗaure masu gindin yin abunda su ka ga dama sama dake,kina ƙanwar mazajensu ko kunya bakiji” “da Allah ya isa haka mariya,ni ya kamata Ku rufe da faɗa ba su ba,kune za ace ma ko kunya ba kuji,kun fifita bare sama da ƴan uwanku musulmai,ko da yake ke barewa ai baza tayi gudu ɗanta yayi rarrafe ba” “ko mi zaki ce mama a shekarunki wanan abun da ki ke bai dace ba” Aunty Mariya ta faɗa tana nufar wata ƙofa,da harara mamy ta bita har ta shige ɗakin,tsaki Aunty Adama taja tana bin bayan su mom. “aikin banza dana wofi, kullum da an taɓa wannan dangin sheɗan ɗin sai su rufe mutane da faɗa kamar wasu ƴaƴan cikin su” Hajiya Gaje ta faɗa tana sake jan wani tsaki “gaba ɗaya zanyi maganin su ne daga su har ita” a cewar mama Ameenah “wallahi mama karki bari yarinyar nan ta zauna,ta maidata can dangin uwarta,haka kawai zata jajubo ma mutane gayyar tsiya inji ba uwarta bace ta kashe mahaifinta ba” Aunty Safeenah ta faɗa sai wani huci take. “rabu da ita ai Tahir ɗin zai zo ya same ni,zanji idan shi ya bata damar ajiye wanann annobar a gidan shi” mamy ranta fes kamar ta zuba ruwa a ƙasa tasha,dama ta san muddin mama Ameenah taga Nainarh sai tasa an koreta daga Estate ɗin gaba ɗaya. first floor mom ta koma, bedrooms ɗin dake floor ɗin ta nufa, toilet ta shiga yayin da Yumnah da Nainarh su ka zauna saman arm chairs ɗin dake bedroom ɗin, Nainarh hankalinta duk a tashe yake da abunda ya faru a part ɗin mama Ameenah,tunaninta yanzu wace irin rayuwa za tayi idan ta koma hannun dangin mahaifinta,kwata kwata basa sonta musamman yanzu da suke zargin mahaifiyarta da kashe mahaifinta,bare ace dangin mahaifiyar ta da ba nan suke ba,yanzu ita ya za tayi kenan...⁉️ _*Ep 21_22*_ *Bound by fate,freed by love, A romantic Odyssey*❤💘💘 ______________________________ sosai tayi nisa a duniyar tunani har mom ta fito daga toilet yumnah ta shiga bata sani ba,prayer mat Fa'iza ta shimfiɗa ma mom ɗin, wurin da Nainarh take ta nufo. dafa kafaɗarta Fa'iza tayi, saurin kallon fa'izar tayi,murmushi Fa'iza ta sakar mata “ ina ta magana kinyi nisa a tunani baki ji,karki damu da maganar mama Ameenah babu in da za kije kina nan a tare da mu, ki kwantar da hankalin ki kinji” murmushi kawai Nainarh ta sakar mata ba tare da tace komai ba, turo ƙofar ɗakin Aunty Adama tayi ta shigo,duban su suka kai gareta, cikin ɗakin ta ƙaraso, zama tayi kan chair ɗin da yumnah ta tashi tana fuskantar Nainarh, fuskarta ɗauke da murmushi tace “kiyi haƙuri da halin kakar taku wasa take babu in da za kije, kina nan tare da mu har Allah ya kubutar da mahaifiyarki kinji” murmushi Nainarh ta sakar mata “nagode sosai Aunty, Allah ya bar zumunci” “kar ki damu,ai yanzu munzama ɗaya, zansa yumnah ma ta kawoki gida ki zo man ziyara, ai zaki zo ko” “Eh in sha Allah, nagode sosai Aunty” “shikenan, tashi ki shiga toilet ki ɗauro Alwala ki zo kiyi sallah” da to ta amsa mata, tashi tayi ta nufi toilet ɗin, kusa da Yumnah ta zo ta kabbar sallah, bayan fitowar Nainarh Fa'iza ta shiga,ɗaya bayan ɗaya su ka shiga gabatar da sallar zuhur, bayan da su ka kammala ne su Yumnah su ka fice aka bar mom da Aunty Adama a ɗakin. main parlorn su ka nufa,a zaune su ka samu kairiyyah da Noor,ƙarasawa su kayi cikin parlorn, kusa da kairiyya yumnah da Nainarh su ka zauna. suna a nan zaune parlorn Aunty Nafeesa da Aunty Nadiya su ka shigo,sun ɗau wanka Abaya maroon color yayinda Enaaya da Aneesarh su kayi ankon Pakistan dress riga da wando white color ,rigar da wandon sun sha adon sparkling stones,sunyi rolling Veil ɗin kayan a kan su,simple makeup ne a fuskarsu, kamar ko da yaushe eyes ɗinsu manne suke da sunglasses mai shegen kyau. basu jima da shigowa ba Laatifa da Balqis su ka shigo tare da mom maryam da mom maimunatu, suma ankon Abaya su kayi yayinda mom maryam da mom maimunatu suka ɗau wankan tsadadden Swiss less naji da faɗa. mom maimunatu ta so su shiga part ɗin mama Ameenah Amma mom maryam tace babu inda za ta sai dai mom maimunatu taje ita ka ɗai,duk yanda mom maimunatu ta so su shiga su gaishe da mamah ƙin zuwa mom maryam tayi sai ma tashi da tayi ta nufi bedroom ɗin da su mom su kayi sallah, itama sallah tayi. *Queen Kainart💫* A jere danƙara danƙaran motocinsu su ka shigo cikin estate ɗin yayinda motocin securitys Armys ɗin su suka sako su a tsakiya,katafaren parking space ɗin dake part ɗin Abbah suka nufa, daidaita parking ɗin su kayi, durowa security Armys ɗin su ka shiga yi daga motocin su,cikin girmamawa su ka shiga buɗe masu car doors, motar farko Abbah ne ya fitowa hannunshi riƙe da sandarshi mai shegen kyau sai ɗayan ɓagaren dady ya fito, motar bayan su dady Ahmad ne da dady mustafa su ka fito bayan ta su sai tasu Uncle ubaid da Uncle mutallaf su ka fito daga nan sai Uncle hashim. bayan motocin su sai na jikokin Abbah,a mota ɗaya ya Naeem da zaabith su ka fito motar bayan su ya Adnan da ya usman, ya Ahmer ne su ka fito bayan tasu ne sai ta su Irfan da Waseef su ka fito waseef riƙe da hannun Jamal a front seat na motar da su ka fito Aman da Ammar su ka fito su ukku sun sha ankon white jallabiya harda Arb turban a kansu ba ƙaramin kyau su kayi ba kamar ka sace su ka gudu, motar bayan su Fa'iz da Yazdan ne su ka fito sun ɗauki wankan farar shadda kamar sauran, kawunan su a sanye su ke da huluna hakan ya ɓoye tarin sumar dake kansu. gama fitowar su kenan daga motocin su motocin her excellency salima suka kunno kai cikin estate ɗin,da katawa su kayi har motocin su ka ƙaraso parking space ɗin, sai bayan da su ka gama daidaita parking ɗin tunkun ɗaya daga cikin securitys ɗin ya buɗe mata car door ta fito,masha Allah na furta a sanye take da lafaya white color ta yafa gyale saman kanta, fuskarta ɗauke take da simple makeup kyawawan eyes ɗinta a manne su ke da farin shade mai shegen kyau. wurin Abbah ta nufo cikin takun ƙasaita yayinda PA ɗinta ke take mata baya, cikin girmamawa ta gaishe da Abbah, da kulawa ya amsa mata “ina ki ka baro man Amaryata na ganki ke ka ɗai?” “ bata jin daɗi ne” “subhanallah, mike damunta?” “ta dai ceman zazzaɓi na damunta, da tare zamu zo to sai da muka shirya kuma taji bata iya zuwa jikin ya ɗanyi zafi” “ya salam, to Allah ya bata lafiya, Allah yasa kaffarane” gaba ɗayan su da Ameen su ka amsa “dr ya dubata kuwa?” uncle Mustafa ya faɗa “eh dr James ya dubata” “mike damunta yace?” “zazzaɓin ne kawai” mom salima ta faɗa “zazzaɓi kawai ne a wajenki?,ni dama na san Zaabith bazai iya kula man da ƴata ba,idan baza ku iya kula da ita ba ku dawo man da ita zan sa ƙwararren likita ya duba man lafiyar ɗiyata” ya faɗa yana zaro wayar shi daga Aljihun wandon shaddar shi. Uncle Ahmad har ya buɗe baki zaiyi magana Abbah yayi saurin dakatar da shi dan ranshi ya ɓaci ya rasa miyasa Almustafa yake mashi haka, kullum gazawar su yake gani a wajen kula da ƴarsa,gaba ɗaya zuba mashi ido su kayi suna kallon ikon Allah, Zaabith duk yasha jinin jikinshi yasa bazai wuce rashin mutuncin da yayi mata bane ya haddasa mata zazzaɓi. dialing number dr fawar yayi, bugu biyu yayi picking “hello fawar kana hospital ne?” on the other handa dr fawar ya amsa mashi da “Eh sir, kana buƙatar wani Abu ne?” “kainart ce ba lafiya nake son kaje ka duba man ita” “ok sir” “thank u” ya faɗa yana rejecting call ɗin. “amma kasan cewa gidan gomnati ba wurin shigar kowa bane haka kawai ?” Uncle Ahmad ya faɗa yana kallon Uncle Mustafa da yayi kicin kicin da fuska “Irfan kaje kayi mashi rakiya zuwa Villa ɗin,idan kun isa ka kira ni ina son na san mike damunta da gaggawa” “in sha Allah Uncle” Irfan ya faɗa yana nufar ɗaya daga cikin motocin da suka dawo,driver seat ya shiga, suna anan tsaye yayima motar key ya nufi main gate ɗin estate ɗin. babu wanda Uncle Mustafa ya kalla a cikin su ya nufi ƙofar shiga katafaren garden ɗin gidan, murmushi kawai hajiya salima ta saki,Uncle Mustafa yanda mataƙar tsaurin akan ƴaƴan sa, bai haɗa soyayyar da yake masu da komai ba, zai iya ɓatawa da kai saboda ƴaƴan shi shikuma tashi ƙaddarar kenan son ƴaƴa,shiyyasa Kainart ke mugun tsoron ya san irin zaman da suke da Zaabith dan ta san muddin ya sani abun bazai yi kyau ba. “bari na shiga ciki Abbah” “to salima” Abbah ya faɗa, enterence ɗin shiga part ɗin Abbah ta nufa “muje ko Abbah”dady ya faɗa “kuje gani nan zuwa” da to suka amsa mashi,ƙofar shiga garden ɗin su ka nufa, dakatar da Uncle Ahmad Abbah yayi. “zo Ahmad” dawowa yayi in da Abbah yake tsaye, kamo hannunshi Abbah yayi cikin nashi, wata ƙofar shiga garden ɗin su ka nufa daban da wacce su dady su kashiga,wasu irin shuke shuke ne a wajen masu matuƙar kyau da ɗaukar hankali,ga wasu tsuntsaye masu ban sha'awa dake kai komo a cikin garden ɗin. wasu ƙayatattun benchs dake ƙarƙashin wasu rukunin bishiyu su ka nufa,zama su kayi suna fuskantar wasu killatattun ruwa,kai tsaye baza'a kira su da swimming pool ba ga wasu tsuntsaye dake shawagi saman ruwan abun gwanin ban sha'awa. “na san ba kaji abunda ɗan uwanka yayi maka ba,amma ina so kayi haƙuri kayi mashi uzuri” Abbah ya faɗa “Abbah amma mi yasa kullum Al'mustafah yake ganin gazawata akan ƴar sa,ina iya bakin ƙoƙarina wajen ganin wani abu bai faru da ita ba” “haka ne Ahmad,amma kafi kowa sanin halinshi,yanada saurin fushi ga zuciya musamman akan ƴaƴanshi shi kalar tashi ƙaddarar kenan shiyyasa nake son kuriƙa yi mashi uzuri idan yayi wasu abubuwan,yanzu na san yana can hankalinshi duk ba'a kwance ba saboda rashin lafiyar ɗiyarshi,da ƙyar yau yayi bacci mai daɗin,kayi haƙuri da ƙaddarar ɗan uwanka” “shikenan Abbah komai ya wuce a wajena, Allah ya bashi ikon cinye ƙaddarar shi” “Ameen ya Allah,ya fama da mutane,ina fata komai yana tafiya daidai??” “Alhmdllh Abbah komai yana tafiya yanda ya kamata” “masha Allah,labari yana samuna har gida daga mutane daban daban,suna kawo man labarin yanda komai ke tafiya,kuma Alhmdllh naji daɗin yanda kowa daya buɗe baki yake faɗin Alkairi a kanka,Na yarda da tarbiyyar ka da gaskiyar ka da riƙon amanarka,nasan yanda kake da tausayin talaka ina so Ahmad ka ƙara fiye da haka, kazama adalin shugaba kamar ɗan uwanka,ina fatan yanda ɗan uwanka yayi ya gama lafiya har yau ƙasar nan bata manta da ayyukan Alkairin sa ba,ina so kaima kowa ya buɗe baki ya faɗi Alkairin ka ko bayan saukar ka” “in sha Allah Abbah zaka sameni fiye da yanda kake tunani” “haka nake son ji,Allah yayi jagora” “Ameen ya Allah” fira su ka shiga yi Abbah na ƙarfafa mashi gwiwa akan mulkinshi da bashi shawarwari. Idan muka koma ɓan garen su dady wani ƙaton dinner hall su ka nufa dake cikin garden ɗin,gaba ɗaya zagaye yake da glass daga waje kana iya hangen abunda ke ciki,wasu irin zungura zunguran luxury dinner tables ne guda biyu masu ɗauke da chairs guda ashirin akan kowane table,daga saman floor ɗin wasu irin manyan crystal chandelier ne masu shegen kyau dogayen da su kamar za su sauko ƙasa,gaba ɗaya hall ɗin a zagaye yake da manyan curtains masu matuƙar kyau an zuge su. hall ɗin an ƙawatashi da wasu tukwanan ƙasa dake ɗauke da furanni masu matuƙar jan hankali,chefs ne maza da mata da a ƙalla zasu kai su goma sai aikin jera warmers suke a saman tables ɗin,cikin hall ɗin dady su ka shigo bakin su ɗauke da sallama. da sauri chefs ɗin su ka dakata da abunda su ke,cikin girmamawa su ka shiga gaishe su,da kulawa suke amsa masu,tunda su ka shigo suka sauke idon su a kan uncle Mustafa dake can zaune saman ɗaya daga cikin kujerun dinner table ɗin,ya ɗaura ƙafa ɗaya kan ɗaya sai aikin jijjigata yake,bini bini yake kallon wayar shi haɗi da jan tsaki. dinner table ɗin su ka nufa kwanansu kujera yaja ya zauna dady ne kawai bai zauna ba ya nufi uncle Mustafa,kujerar dake kusa da wacce ya zauna yaja ya zauna,dafa kafaɗarshi yayi,saurin kallonshi uncle Mustafa da baisan da zuwanshi wajen yayi ba. “yanzu Mustafa duk dan saboda ƴarka ka shiga wannan yanayin?, rashin lafiya ne ba wani abu ba amma duk kabi ka tada hankalin ka?” “bazaka gane bane ya Tahir,ni ka ɗai na san yanda nake ji” “taya zan gane tunda ni ban haifa ba, Al'mustafa ka rage wannan mugun son ƴaƴan da kake,duk kabi ka ɗaurawa kanka damuwa saboda ƴaƴa sai kace kai kaɗai Allah yaba ƴaƴa,akan ƴaƴanka ba kaji baka gani,haba!?” ɗan dakatawa dady yayi yana kallonshi kafin ya ɗaura da cewa “yanzu abunda kayi ma matar Ahmad kana ganin ka kyauta kenan,karka manta yanzu kainart ta tashi daga ƙarƙashin kulawarka ta koma hannunsu,sun fika iko da ita,sannan ina so ka sani ko babu Aure a tsakanin su Ahmad mai iya riƙe kainart ne haka Zaabith,ka zamo mai kawaici a kan ƴaƴanka” tunda dady ya fara magana ƙala Uncle Mustafa bai ce ba sai yanzu “kayi haƙuri ya Tahir in sha Allah hakan bazai sake faruwa ba,hankalina ne ya tashi ban san wane irin ciwo take na” “koma wane irin ciwo take Adu'a ya kamata kayi mata ba abunda kayi ba” “in sha Allah zan kiyaye,kayi haƙuri” “shi zaka ba haƙuri ba ni ba” Dady ya faɗa,waige waige uncle Mustafa ya shiga yi ko zaiga Uncle Ahmad “yana waje tare da Abbah,kaje ka bashi haƙuri” “to” uncle Mustafa ya faɗa yana miƙewa ya fice daga hall ɗin. tun suna ƙananansu suna matuƙar girmama umarnin dady har kawo yau da su ka mallaki hankalin su kuwa. tashi dady yayi ya nufi in da su uncle Ubaid su ke ya zauna,matan ne su ka fara shigowa hall ɗin,Mama Ameenah ce a gaba yayinda su mamy ke biye da ita a baya,sai da su ka gama shigowa mom da mom maryam da mom Maimunatu su ka shigo bayan sun shigo ne yaran su ka fara shigowa. Su Yumnah ne su ka shigo hannunta riƙe da hannun Ammar da Aman yayinda da Jamal ya maƙalƙale hannun Nainarh sai turo baki yake shi adole fushi yake yumnah bata riƙe hannunshi ba. ɗaya bayan ɗaya su ka shiga shigowa, kowannan su ya shigo wajen zama yake nema ya zauna, table ɗin da su dady ke zaune su mom su ka zauna, kowaccen su na fuskantar mijinta yayinda mamy da su hajiya fatilah su ka cure waje ɗaya su da Mama Ameenah bako ta mazajen na su suke ba, sai hura hanci su ke sunama mutane kallon tara saura kwata. ɗayan Table ɗin su Yumnah su ka zauna da sauran jikokin Abbah, a tare Abbah da Uncle Ahmad da Uncle Mustafa su ka shigo, suma wajen zama su ka nema su ka zauna,saida kowa ya gama samun wurin zama ya zauna tukun chefs su ka shiga serving ɗin su, cika masu gaban su su kayi da Abinci kala kala na Alfarma. tunda su ka shigo Aunty Safeenah ta kafe mom Maryam da kallo,wani irin kallon mamaki take binta dashi,tsaki taja tana kallon mama Ameenah “dan Allah mama dubeta,sai wani hura hanci take kamar wani ta fi,mai Abun duniyar ma ba tayi ƙafafa ba sai ita” “ai ni wallahi lamarin Maryam mamaki yake bani,wai ni baku lura da ita ba yanzu tafi ƙarfin zuwa ta gaishe da mama bare mu data gama rainawa mu samu arziƙin da za tayi mana magana” A cewar hajiya halima “rabu da ita kawai zanyi maganinta ne”acewar mama Ameenah firarsu su ka shigayi wacce banda zagin su mom ba abunda su ke, Hajiya Salima na cikin su amma kwata kwata bata saka masu baki ba haka mamy ma tunda ta zauna hankalinta na can wani waje daban,bamata san akan mi su ke magana ba,ta ƙurama waje ɗaya ido,suma da su ka gaji shiru su kayi hall ɗin yayi tsit banda ƙarar spoon da plate baka jin komai. Noor tunda ta zauna dinning ɗin Banda juya spoon babu abunda take gaba ɗaya ta kasa cin abincin saboda rashin shi a kusa da ita duk tabi ta damu,kallonta laatifa dake kusa da ita tayi. “lafiya dai ko Noor?” murmushin yaƙe ta sakar mata tana faɗin lafiya. “mi yasa baki cin abincin,ko dai wannan baiyi maki ba chefs su canza maki wani??” girgiza mata kai Noor ɗin tayi “A'a, bana jin daɗi ne ” “Ayyah!,sannu mike damunki?” “jikina nake ji babu daɗi” ta bata amsa, murmushi Kairiyyah ta saki dan ta san ba komai yasa noor faɗin haka ba sai dan saboda Irfan. Ringing ɗin wayar laatifa ne yaja hankalin mutane da dama dake hall ɗin har da dadyn ta,wani kallo ya shiga watsa mata,kwata kwata bata lura da irin kallon da yake mata ba, ganin sunan mai kiranta nata ne ya sata saurin miƙewa daga saman chair ɗin da take zaune,ƙofar fita daga hall ɗin ta nufa yayinda take picking call ɗin. a bakin ƙofar shiga hall ta tsaya tana amsa wayar “hello sister,kamar kin san duk ina nan na damu da rashin zuwanki” laatifa ta faɗa,on the other hand ta cikin wayar tace “bana jin daɗi ne ƴar uwa shiyyasa ban zo ba” “subhanallah! mike damunki naji ma muryarki wani iri, fatan dai ba wani abun ba ne ya sake faruwa ba dan naga ya Zaabith na gari” “please sister ki zo idan babu abun da ki ke” “wai mike faruwa ne,duk kin sa hankalina ya tashi” “babu komai ki zo dai Please” “ok gani nan zuwa” “sai kinzo” rejecting call ɗin tayi,hanyar fita daga garden ɗin ta nufa ba tare da ta koma cikin hall ɗin ba,daga inda dadynta yake cikin hall ɗin yana hangen ficewar ta. miƙewa yayi ya fito daga hall ɗin,bayanta yabi, parking space ɗin gidan ya nufa,yana isa motar ta na ficewa daga parking space ɗin,wayar shi ya zaro daga cikin Aljihu yayi dialing wata number, bugu biyu a kayi picking. “gata nan ta fito ina son kutabbatar da in da taje” on the other hand wata irin kakkausar Muryar ce mara daɗin jin ta daki dodon kunnenshi “angama ranka ya daɗe” rejecting call ɗin yayi ba tare da yace komai ba. yana a nan tsaye kamar daga sama yaji anyi hugging ɗin shi ta baya tightly, murmushi gefen fuska ya saki ba tare da ya juya ba dan ya san bazai wuce ita ba ce dan babu mai mashi irin wannan rungumar idan ba ita ba. “ai nayi tunanin sai na kira ki zaki fito?” ya faɗa cikin wani irin yanayi kamar ba barisster ba “ni na isa, kawai jiran damar da zan fice nake ba tare da wani ya lura da ni ba” taɓe baki yayi yana faɗin “fushi nake dake,yau wajen kwana nawa da alƙawarina amma baki ciki ba” “kafi kowa sanin halin yayanka kwata kwata baya bani damar da zan matsa daga gidan,yanzu ina sa ƙafa na fita zaisa abi masa diddiƙin in da na tafi,kuma nasha faɗa maka ka riƙa zuwa gidan babu mahaluƙi da ya isa ya zargeka akan zuwa gidan yayanka,kuma har ka gama abun da ya kawoka ka fice ba tare da ya san ka zo ba. hannunshi yasa ya jawo hannunta ta dawo gaban shi, ƙare mata kallo ya shiga yi tun daga sama har ƙasa kafin ya tsaida lumsassun idanunshi a kanta, wani irin shaiɗanin kallo ya shiga binta da shi,ba ita da yakema kallon ba hatta ni dake laɓe sai da naji kunyar irin kallon da yake mata. kasa jure kallon da yake mata tayi,tafin hannunta tasa ta rufe idanuwan shi “barisster irin wannan kallo haka, sai ka sa gaban ya faɗi” murmushi ya saki yana janye hannunta daga idanunshi,baki ta buɗe da nufin yin magana amma yayi saurin manne bakinshi da nata. *Tashin sense Barisster Hashim,mamy 😳😳😳😳* Zagayo da hannayenshi yayi ya riƙe ƙigunta,itama ƙanƙameshi tayi kamar za su koma abu guda,a ƙalla sun shafe tsawan five minutes a haka kafin ya raba jikin su,jan hannunta yayi su ka nufi ɗaya daga cikin motocin dake parking space ɗin,front seat ya buɗe mata ta shiga,zagayawa yayi ya shiga driver seate,Key yayi ma motar su ka nufi cikin estate ɗin. *ASO VILLA* Bata sha wata wahala ba wajen shiga, saboda ita ɗin sannance a idanun securitys ɗin kuma bayan haka sun san alaƙarta da mazauna gidan. A katafaren parking space ɗin Villa ɗin tayi parking, kusan a tare su ka fito da wani matashin ba indiye dake zaune a cikin motar shi,bai jima da parking ba tayi parking. in da take ya nufo hannunshi ɗauke da briefcase, fuskarshi ɗauke da fara'a ya ƙaraso,murmushi itama ta sakar mashi. “Dr fawar dama kana ƙasar?” ta faɗa da almun mamakin ganinshi, murmushi ya sakar mata cikin hausar shi da bata gama daidaita ba yace “ina za ni, Ina nan hajiya laatifa, dama yaran irin mu na ganin ku?” dariya ta fashe da ita wacce ta ƙara fito da ainihin kyawun fuskarta “daɗina da kai zolaya fawar, in da ka so gani na ai ka san in da zaka same ni” “kina son dadyn ki yayi ƙarata kenan?” ya faɗa,dariya kawai laatifa tayi ba tare da tace komai ba. juyawa su kayi da nufin barin wajen zuwa ciki, horn ɗin da a kayi a bayan su ne ya dakatar da su,parking space ɗin matuƙin motar ya nufo, parking yayi, zuba ma motar ido su kayi dan ganin wanda zai fito. Irfan ya fito,da sauri ya nufo su yana faɗin “sorry Dr, na san na ɓata maka lokaci” ɗan hararar shi dr fawar ɗin yayi “haba Irfan ka san yanda tsarin gidan nan naku yake amma ka barni a tsaye a bakin gate da ba dan nayi hausar kiran Zaabith ba da tuni ina can rana na duka na” “sorry na tsaya amsar wani saƙo ne, muje ko, Aunty Laatifa ina wuni” “lafiya lau Irfan, kwana biyu” da Alhmdllh ya amsa mata yayinda su ke shiga cikin gidan,babu kowa sai masu aiki dake kai komo, direct part ɗin Zaabith su ka nufa, parlorn su tsit yake babu kowa sai masu aiki dake ƴan hidindimun su, gaishe da su masu aikin su kayi, a saman sofa fawar da Irfan su ka zauna yayinda laatifa ta nufi bedroom ɗin Kainart. bakinta ɗauke da sallama ta tura ƙofar ta shiga tana ambaton “my own sis gani na ƙa...” dakatawa tayi da maganar ganinta a kwance saman bed harda su rufa,ƙarasawa tayi bakin bed ɗin. “Kainart lafiya?” ta faɗa tana ɗan yaye blanket ɗin data rufa,tashi tayi zaune ta jingina da head board ɗin gadon. wani irin mummunan faɗuwa gaban laatifa yayi ganin sawun duka a saman neck ɗinta gana mari da har yayi baƙi saboda hasken fatar ta. “kainart mi ya same ki haka, kardai kice har yanzu ya Zaabith bai daina dukanki ba??” Laatifa ta faɗa da tsantsar damuwa “har yau Laatifa ya Zaabith yaƙi ya canza halinshi” “kainart idan har da laifin ya Zaabith naki yafi yawa, ni banga amfanin zaman nan da kike da shi ba, mutuminnan baya sonki amma ke har yau kin kasa ganewa, so ki ke ki salwantar da rayuwarki a banza?” Laatifa ta faɗa ranta a ɓace. “bazaki gane bane Laatifa” “dama taya zan gane tunda soyayya ta rufe maki ido har kina shirin salwantar da rayuwarki a banza, wallahi Kainart ko ni da nake fuskantar tsangwama daga dady gara ni dake, duk ranar da Allah ya bani miji mai sona nayi Aure shikenan, amma ke fa?, karki manta zaman Aure ba zama ne na ɗan lokaci ba zama ne na har abada, kuma tuda har ya Zaabith bai sonki ko kun ɗau tsawan shekaru tare ba ganin mutuncinki zaiyi ba, gara tun wuri kisan Abun da ya dace??” “ina sonshi ne Laatifa shima yana sona bazaki gane ba, kuma idan na barshi ya ki ke so nayi da su Ammar?” “matsalar ki kenan soyayya,wlh ya Zaabith baya sonki da yana sonki bazai riƙa wulaƙantaki ba, sannan su Ammar da ki ke magana, karki manta ko babu Aure tsakaninki da ya Zaabith zai iya riƙe abun da ki ka haife barema ƴaƴan sa ne, kuma kin san cewa duk tashin hankalin da za'ayi dady bazai taɓa bari a rabaki da su ba hakama Abbah, ki nemama kanki mafita Kainart,ba kiga yanda ki ka koma ba kamar ba ke ba duk kinbi kin lalace” “wace mafita zan nema Laatifa?” ta faɗa da alamun son ƙarin bayani daga Laatifa “na san zaki ce bazaki iya rabuwa da shi ba, amma ya zama dole dady ya san irin zaman da kike a gidanan” girgiza mata kai tayi “gaskiya Laatifa bazan iya sanar da dady ba kin san halinshi, muddin ya sani ya Zaabith ya shiga uku” “to ya shiga ukun mana ina ruwan wani, ke sau nawa yana saki a ukun” Laatifa ta faɗa a hassale da alama dai ranta ba ƙaramin ɓaci yayi ba “bazan iya ba, ina tausayin hukuncin da dady zai yanke mashi,zanta kai kukana wajen ubangiji, in sha Allah wata rana zai daina” “ai shikenan sai ki tashi dr fawar na nan dady ya turoshi ya dubaki” wani irin faɗuwa gabanta yayi, saurin dafe saitin zuciyarta tayi “na shiga uku! waya faɗa mashi bana da lafiya?” “kema kin san dole yaji ba'asin abunda ya hanaki zuwa gidan Abbah,may be mom salima ce ta faɗa mashi baki da lafiya, kin san kuma komi a kayi maku idan ba shi yayi ba baya ganin daidain shi, ki tashi kawai kije” “amma bata faɗa mashi dr James ya dubani ba?” “kinfi kowa sanin waye dady, kawai ki wuce kije” hijab ta ɗauka ta zura a jikinta, ficewa tayi zuwa parlorn, gefen bed ɗin Laatifa ta zauna. A zaune ta same su saman sofa kamar yanda laatifa ta barsu masu aikin sun kawo ma Dr fawar abun motsa baki. cikin girmamawa su ka gaishe da juna ita da Dr fawar,bayan da su ka gaisa ne ya shiga yi mata ƴan tambayoyi tana bashi amsa. duk wani abun da ya kamata yayi mata yayi mata,baisha wahala ba saboda duk wani da zai buƙata wajen duba patient ya zo da shi,sallama yayi mata akan idan ya kammala binciken zai ba Irfan sakamakon ya kawo mata,godiya tayi mashi sosai. sallama yayi mata su ka fice shida Irfan,a parking space yana shirin shiga motar shi uncle Mustafa ya kira dan yaji mike damunta,sanar da shi yayi zazzaɓi ne dai yanzu sai sakamakon test ɗin da yayi mata ya fito sannan ya san taƙamaimai abunda ke damunta. godiya sosai uncle Mustafa yayi mashi kafin su kayi sallama,ficewa su kayi daga Villa ɗin motar Irfan na gaba yayinda ta Dr fawar ke bayan shi. Estate Irfan ya koma lokacin har sun kammala lunch suna part ɗin Abbah,Noor tayi fushin tayi fushin har ta gaji,sai da ƙyar ya samu ya shawo kanta. Barisster Hashim da mamy da su ka fita ba sune su ka dawo ba sai da yamma liƙis ana gab da kiran magrib,sai ma da suka dawo sannan wasu su ka fahimci ba sa nan. Bayan sallar isha su kayi dinner kowa ya kama shirin tafiya gida,Ammar tunda lokacin tafiya suka fara murnar yau a gidan big daddy za su kwana Jamal ma rigima yasa shima dole ya bisu,wayau Aunty Nafisat ta so yi mashi kan ya bari idan sun koma gida dadyn shi zai kawo shi amma fir ya tubure shi dole yanzu yake son bin su duk yanda ta so ya bari sai wani week ƙin amincewa yayi dole tasa su ka haƙura. motar su na bayan ta Irfan daya ɗauko mom,Yumnah na back seat tare da yaran yayin da Nainarh ke front seat kusa da Fa'iza dake driving. Yumnah tun kafin su ƙarasa ta kira Ishrat ta sanar da ita zuwan su Ammar saboda su gyara masu bedroom ɗin dake kusa da na Yumnah,sosai Ishrat tayi murna da zuwan su Ammar yaran na matuƙar burgeta. A tare motocinsu su kayi parking,a tare su ka shiga fitowa daga motocin,cikin gidan su ka nufa su Ammar na riƙe da hannun Yumnah, Jamal ma Nainarh ya maƙalemawa tunda Aunty Yumnah ta yadashi,ɗaya daga cikin security ɗin gidan ne ya shigo da kayan su Ammar. Irfan har bedroom ya raka mom da jakatar a hannunshi mom har mamaki take miye alaƙar Irfan da son riƙe jaka,duk za su fita tare baya barinta riƙe jaka ko kau ina za su je haka zai riƙe jakarta,Fa'iza har iya shage take mashi saboda riƙe jakar mom. Basu wani jima su ka fice shida Waseef da alama sauri suke zuwa wani waje, bedroom da Yumnah tasa aka gyara masu ta nufa da su Ammar, bedroom ɗin yana da girma sosai dan yafi na Yumnah girma ƙaton king size bed ne a cikin shi. ruwa Yumnah tasa su ka watsa su ka shirya cikin pajamas ɗin su,a nan ɗakin su kwana harda Nainarh dan rigima su ka masu akan sai sun kwana tare da su... _*HEART OF VEGAS CLUB AND CASINO*_ *12:00 AM* _*HEART OF VEGAS CLUB AND CASINO*_ Ƙarfe shabiyu na dare daidai motar su tayi parking a ƙaton parking space ɗin dake club ɗin, maƙil yake da motoci kasancewar yau Friday duk wani mashahurin da yake ganin ya shahara ayawan club zaka same shi a nan. Kamar yanda sunan ya kasance iri ɗaya haka tsarin ginin ma iri ɗaya ne,banbanci kawai wacan yafi girma sai dai ba wani sosai ba,gaba ɗaya photocopy wacan ne. Kusan a tare su ka fito,jeans da T_shirt ne a jikin Waseef yayinda Irfan ke sanye da shirt haɗe da short iya gwiwarshi,kanshi a sanye yake da Ivy Cap idanunshi a manne su ke da baƙin shade mai shegen kyau. Entrance ɗin shiga club ɗin su ka nufa,wasu irin jibga jibgan security guard a gaban katafariyar ƙofar shiga club,tun kafin su ka ƙaraso securitys ɗin su ka rissinar da kai alamar girmamawa a gare su,kallon in da su ke babu wanda yayi tsakanin Irfan da Waseef,bakin ƙofar su ka ƙarasa, Waseef ne ya ciro card ɗin shi daga cikin aljihu,a jikin na'urar dake jikin ƙofar ya zura card ɗin,zugewa ƙofar ta shiga yi bayan na'urar ta kammala acknowledging card ɗin. ciki su ka kunna kai Irfan na baya yayin da Waseef ke bayan shi,tsarin club ɗin ɗaya ne dana US duk abunda ke a wancan a kwaishi a wannan banbanci abubuwa kaɗan ne, mata da maza ne ta ko ina kowa na harkar gaban shi, wasu na rawa wasu na shaye shaye,babu wanda ya lura da shigowar su har su ka isa bakin galss elevator dake club,maddanan dake jiki Waseef ya danna nan take ƙofar ta buɗe,ciki su ka shiga,sama elevator tayi da su zuwa floor ɗin ƙarshe. fitowa su kayi bayan ƙofar ta zuge,a bakin wani office su ka tsaya,wasu nombobi dake a jikin na'urar dake jikin ƙofar ya danna,nan take ƙofar ta buɗe,ciki su ka shiga, katafaren office ne kamar ba'a niger ba komai na cikin shi extraordinary ne, Executive chair ɗin dake gaban haɗaɗɗen glass desk Irfan ya nufa,zama yayi yayin da Waseef ke jan ɗaya daga cikin chair ɗin dake gaban desk ya zauna. mac book ɗin dake ajiye saman desk ɗin ya buɗe,babu ɓata lokaci ya shiga operating ɗin ta. “wai yaushe Muhsin yace maka Boss zai dawo ne,akwai kayan da babu ga tarin customers da muke da su?”Irfan ya faɗa ba tare da ya ɗago daga abunda yake ba “kasan ba kowa ke sanin lokacin tafiyar shi ba haka lokacin dawowarsa” jinjina kai Irfan ɗin yayi “gashi Muhsin ɗin bai shigo ba,amma bari na kira wayar shi naji” ya faɗa yana zaro wayarshi daga aljihu,number Muhsin ya shiga dialing, ringing wayar ta shiga yi har kiran ya katse ba'ayi picking ba, Yana ƙoƙarin sake kira aka turo ƙofar office ɗin. “ina jin gashi nan” Waseef ya faɗa yana kai dubanshi ga ƙofar dan ya san idan ba Muhsin ɗin ba to Boss ne su kaɗai keda lasisin shigowa ba tare da na'ura ta dakatar da su ba. Wani matashin saurayi ne ya shigo cikin shigar ƙananan kaya,ƙaƙƙarfa ne na gaske,cikin office ɗin ya nufa, kujerar dake kusa da wacce Waseef ke zaune yaja ya zauna,hannu ya miƙa masu su kayi musabaha “kamar kuwa kasan nemanka nake”irfan ya faɗa “shigowata kenan naga kiranka,neman mi kake man fatan dai lafiya?” “dama tambayarka zanyi yaushe boss zai dawo, akwai tarin customers a gaban mu” “ka san halin yaya idan zai tafiya baya faɗa, nama yi tunanin ko kai ya faɗa maka” “ya dai faɗa man zaiyi tafiya amma bai sanar dani time ɗin da zai dawo ba” “ok abunda ya kamata kawai ka kirashi kaji yaushe zai dawo dan akwai tarin schedules na meeting wanda dole ya halarce su” “ok bari na kira naji” Irfan ya faɗa yana ɗaukar wayar shi yayi dialing number boss, ringing wayar tashiga yi har sun fitar da ran za'a ɗauka akayi picking,wata irin buɗaɗiyar murya ce ta daki dodon kunnenshi. “hello Irfan,fatan lafiya ka kira ni?” na cikin wayar ya faɗa “lafiya lau,dama cewa nayi yaushe ne zaka dawo,kaya da yawa fa sun ƙare gashi yau muna da guest da yawa?” “ sai next week nake sa ran dawowa ina las Vegas ne,akwai key a hannun Muhsin ku duba store na san baza'a rasa wa su a ciki ba” “amma meeting ɗin ka fa,kasan fa dis week kayi masu alƙawari” “haka ne,ina sane,kai nake so kayi Attending ɗin su” “nikuma boss?” Irfan ya faɗa da alamar ruɗu “eh,na san ai zaka iya dan ya kamata ka fara wasu abubuwan da kanka ba dole sai da ni ba” “amma Boss kasan bana da gogewa a abun, infact ma ban taɓa Attending meeting irin wannan ba” “karka damu idan zaka je za muyi amfani da communicative devices,zan dunga sanar da kai abunda ya kamata ka faɗa” “ok Boss,sai ka dawo” “thanks” Boss ɗin ya faɗa yana rejecting call ɗin. saurin tambayar shi su kayi dan jin yaushe yace zai dawo “sai next week” ya basu amsa “kayan fa?” Muhsin ya faɗa “yace akwai key a hannunka mu duba store baza'a rasa ba” “ok,bari muje tare da Waseef,amma meeting ɗin fa?” “ni yace nayi Attending ɗin su” Ok kawai Muhsin ɗin yace,tashi su kayi su ka fice daga office ɗin zuwa store,maida kanshi yayi a kan mac book ɗin dake gaban shi. *ASO VILLA* A kwance take saman makeken gadonta ta rufe jikinta da duvet,tunda laatifa ta tafi take a kwance sallah kawai ke tashin ta. Turo ƙofar ɗakin yayi ya shigo,Black suit ne a jikinshi looking smart,cikin ɗakin ya ƙaraso,a bakin bed ɗin ya zauna,hannu yasa ya yaye duvet ɗin da tayi rufa in a low voice ya kira sunanta “kainart!” tsit tayi kamar batajishi ba,sake kiran sunanta yayi still bata amsa mashi ba fuskarta ya leƙa dan yaga bacci take ko kuwa,motsi ya ga tana yi da idanunta alamar idonta biyu. shafa fuskarta yayi da tafin hannunshi “ya jikin naki?” ya faɗa cike da kulawa,banza tayi da shi kamar bata san da ita yake ba “kainart na san kina jina,fushi kike dani ne?” nan ma ƙin tanka mashi tayi a ranta tana faɗin “watau ma bai damu da abunda yayi mata ba har yake tambayar fushi take. tashi yayi ganin da gaske ba kulashi za tayi ba,ƙofar fita ya nufa ɗan buɗe idonta tayi a hankali ta saci kallonshi,har ya kama handle ƙofa zai fice sai kuma ya dakata yana juyowa ya fuskance ta,saurin rufe idonta tayi. “zan fita akwai yiwuwar sai gobe zan dawo ki kulaman da kanki” yana gama faɗa ya fice haɗi da jan ƙofar ya rufe. a hankali ta buɗe idonta tana bin ƙofar da kallo,gaba ɗaya takaice ne ya cikata ko ina zaije da wannan tsohon daren kuma har yake faɗa mata wai sai gobe ma zai dawo,baƙin cikinta da takaicinta idan ya tashi dawowa abuge zai dawo mata ya shuka mata rashin mutunci, shikenan ita a haka rayuwarta zata ƙare. idan tana tuna lokacin baya kafin suyi Aure sai taga kamar ba Zaabith ɗinta ba wanda kwata kwata baya son ganin ɓacin ranta,inda wani yace mata zai sauya mata bayan sunyi Aure bazata taɓa yarda ba saboda irin soyayyar da yake mata amma lokacin guda komai ya canza. siraren hawayen da su ka zubo mata tasa hannu ta share,sauka tayi daga saman bed ɗin ta nufi toilet,alawa ta ɗauro ta zo ta kabbar sallah, nafilfilu ta shiga jerowa tana kai kukunta ga Ubangijin sammai,ta jima sosai tana Adu'a akan Allah ya shirya mata mijinta. *UNITED STATE* _*Las Vegas (Nevada)*_ *6:30 PM* A kwance take saman leg press machine dake gym room ɗinta tana pressing leg ɗin ta up to down, active wears ne a jikinta vest da short Black color ta ɗaure sumar kanta da ribbon,kunnenta a manne yake da earphone tana sauraren sauti,sosai take press leg ɗinta ta haɗa uban gumi. masu aikinta na zaune saman wasu benchs,hannun su riƙe da dumbbells,Gym room ɗin yana da girma sosai kamar gym center,babu kalar nau'in machine ɗin da babu a ciki gasu nan kala kala su exercise ball, punching bag, dumbbells,ellptical cross trainer, treadmill,bench press,step machine, trampoline, fitness cycle da dai sauran su. Turo ƙofar Gym room ɗin a kayi,Aunty Sophia ce ta shigo cikin shigar shirt da dogon wando Black color ta ɗaure sumar kanta da ribbon black color, hannunta ɗauke jug Wanda ba komai bane a ciki sai tacaccen ruwan lemu na musamman wanda ta haɗa domin babynta, murmushi ta saki ganin yanda Nailarh ta dage bataji bata gani. cikin Gym room ɗin ta ƙaraso,jug ɗin dake hannunta ta ajiye saman wani ɗan round table dake kusa da Nailar kafin ta nufi treadmill tahau,kunnawa tayi a hankali ta shiga running. Nailar ta kai tsawan 30 minutes kafin ta dakata,dubanta ta kai ga Aunty Sophia, murmushi ta saki tana zame earphone ɗin dake kunnenta,alama jinjina tayi ma Aunty sophia, murmushi Aunty Sophia tayi tana maida mata martanin alamar da tayi mata. Tashi tayi daga saman machine ɗin ɗaukar jug ɗin tayi ta nufi bench press,zama tayi,a hankali ta shiga shan lemun da Aunty Sophia ta haɗa mata, sai da tasha kusan rabin jug ɗin kafin ta ajiye,zufa har rige rigen fitowa take daga ƙofofin gashin jikinta,ɗaya daga cikin masu aikin ce ta nufo inda take da ɗan madaidaicin towel a hannunta. goge mata gumin da tayi ta shiga yi,sai data tabbatar ta goge mata kafin ta koma mazauninsu,tashi Nailarh tayi ta nufi punching bag,boxing gloves dake ajiye saman wani table ta ɗauka ta zura a hannunta,a hankali ta fara kaima bag ɗin bugu kafin ta shiga kaimata duka da sauri sauri. Wayarta dake hannun masu aiki ce ta fara ringing hakan ya dakatar mata da jin sautin da take da sauri mai aikin ta nufo ta,da katawa tayi, boxing gloves ɗin dake hannunta ta shiga zamewa,karɓar wayar tayi lokacin data gama zame hand glove ɗin, picking call ɗin tayi bayan ta duba sunan mai kiranta. picking call ɗin tayi haɗi da kara wayar a kunne ba tare da tace ƙala ba,daga cikin wayar mahaifiyarta ce tace “hello baby” shiru tayi tana turo baki kamar bada ita take magana ba, sake magana tayi tana faɗin “baby fushi ki ke da momynki?” still shiru tayi bata tanka mata ba, Aunty sophia dakatawa tayi da abunda take, in da nailarh take ta nufo, alama tayi mata da waye, turo baki nailarh tayi ba tare da ta bata amsar tambayar da tayi mata ba. “please baby kiyi man magana mana, momynki ce fa?” mahaifiyar tata ta faɗa kamar zata sa mata kuka “momy yaushe zaki dawo?” shine kawai abunda Nailarh tace mata,daga cikin wayar tana jiyo yanda mahaifiyar tata ta sauke ajiyar zuciya “kina so na dawo ne?” “eh,gidan duk yayi baƙi saboda babuke a ciki, jina nake kamar ba ni ba saboda rashinki a kusa dani please momy ki dawo na gaji” ta faɗa kamar zata fashe mata da kuka, Aunty sophia na daga gefe tana kallonta, masu Aikin ma zuba mata ido sukai suna kallonta “nima duk a daddafe nake saboda rashinki a tare da ni,amma ba sophia na nan ba?” “tana nan mana, amma kin san matsayin kowa a cikinku daban a zuciyata, momy gaskiya ki dawo idan ba haka ba bazan sake zuwa Empire ba” “baby kin cika rigima,nafa ce maki sai upper week zan dawo” “ni dai na riga na faɗa maki bazan sake zuwa ko inaba muddin baki dawo ba” “sorry zan dawo shikenan” “yaushe?”ta jefa mata tambayar da son jin yaushe za tace “yaushe ki ke son na dawo?” “dis week”ta faɗa a shagwaɓe “dis week yayi kusa Nailarh, ban kammala abunda nake ba fa” “to zan biyoki” “A'a ki bari zanyi ƙoƙarin squeezing schedules ɗina na dawo next week,hakan yayi maki?” “Eh” ta bata amsa a shagwaɓe. murmushi mahaifiyar ta saki tana faɗin “rigimammiyar yarinya kawai ina fatan baki manta da shipment ɗin mu ba?” “ban manta ba” “yawwa haka nake son ji, kiyi ƙoƙari ku isa port ɗin da wuri” “please momy su Joseph suje port ɗin ni sai na same su a Orphanage ɗin” “baby mi yasa ki ke son maida magana baya, na faɗa maki ke nake son kije,so nake ki koma ke ke kula da komai ba tare da wani ba” “shikenan momy sai kin dawo” “ok bye take care” “bye” ta faɗa tana rejecting kiran, dubanta ta kai ga Aunty sophia data tsareta da idanu. shafa fuskarta Nailarh tayi tana faɗin “lafiya ki ke mana wannan kallon?” girgiza mata kai tayi “ina za kije?” “port” ta bata amsa tana nufar plyometric box ta zauna “amma miza kiyi a can?” “yau shipment ɗin mu zai ƙaraso” “na sani, amma su Joseph ke zuwa ba ke ba,mi za kiyi a can??” “su ke zuwa amma wannan time ɗin ni zanje” in da take Aunty sophia ta ƙaraso kamo hannunta tayi cikin nata “please Nailarh ki bari su suje,a kwai haɗari a irin wannan wurin kuma kinga dare ne” “momy tace ni zanje, kuma Aunty sophi kin manta wacece ni,Nailarh ce fa, Queen, ni da nake kula da heart of vegas amsar kaya ne zai gagare ni” “ba haka bane Nailarh, bana son wani abu ya sameki” “ki kwantar da hankalinki babu abunda zai same ni” “duk da haka Nailarh ko heart vegas da ki ke zuwa hankalina kullum a tashe yake, please ki bari suje da kansu” Aunty sophia ta faɗa da tsantsar damuwa tana matuƙar son Nailarh shiyyasa take tsoron wani abu ya sameta. “nafa ce maki babu abunda zai same ni,ki kwantar da hankalin ki” “shikenan” Aunty sophia ta faɗa ba dan ta so ba, murmushi Nailarh ta saki tana shafa gefen fuskarta “na lura tunda ki ka ƙara tsufa tsoronki yayi yawa a kaina” bige hannunta Aunty sophia tayi “bana son shirme, kije kiyi wanka time ɗin dinner ɗinki yayi” “ok muje yau kiyi man wanka da kanki” Nailarh ta faɗa tana miƙewa haɗi jan hannun Aunty sophia, saurin fisge hannunta tayi “nailarh waike baki da kunya ne?” ɗaga mata gira tayi haɗi da faɗin “eh” ta bata amsa a gadarance haɗi da kashe mata ido ɗaya, girgiza kai Aunty Sophia tayi “idan ke baki da kunya ni inada ita”ta faɗa tana nufar ƙofar ficewa daga Gym room ɗin,bin bayanta Nailarh tayi tana sakin murmushi. Part ɗin ta ta nufa,tana shiga direct toilet ta nufa anan ta samu Lara da Lolah da tun kafin ta shiga su ka san da zuwanta,babu ɓata lokaci su ka shiga abun da ya kawo su,ba su wani jimaba su ka kammala mata wankan ficewa tayi daga toilet ɗin ta nufi home of beauty ɗinta. Aunty Sophia tana ficewa daga Gym room ɗin katafaren kitchen ɗin gidan ta nufa,tun daga waje ƙamshi abinci ya daki hancinta har sai da ta lumshe idonta,ciki ta ƙarasa,chafs ne maza da mata kowannan su ya duƙufa akan aikin haɗa dinner da su ke. cikin girmamawa su ka shiga gaishe da ita,cike da kulawa take amsa masu tana nufar dinner table ɗin da su ka jera wermers,bubbuɗe wermers ɗin ta shiga yi tana ganin abunda su ka girka,jinjina kai ta shiga yi da alama ta yaba da aikin su. “wannan girki haka sai kusa kunnen mutum ya tsinke tun kafin yaje bakin sa saboda daɗi,sannun ku da ƙoƙari” washe mata baki su kayi suna faɗin “Thanks” jin jina kai tayi “yanzu ba jimawa Nailarh zata sauko,ya kamata ku shirya dinning” da ok su ka amsa mata. ficewa tayi daga kitchen ɗin,maza biyu daga cikin su suka shiga jidar wermers ɗin suna nufar ƙayataccen dinning room ɗin gidan,cikin ƙan ƙanin lokaci su ka kammala shirya dinning room ɗin. Bedroom ɗin Nailarh ta nufa,direct home of beauty ɗinta ta nufa ta san bata wuce nan,tura ƙofar tayi ta shiga, a zaune ta hangota kan stool daga ita sai bathrobe Luna da Mary masu aikinta na gyara mata jiki. cikin ɗakin Aunty Sophia ta ƙarasa,wuri ta samun saman ɗaya daga cikin chairs ɗin dake ɗakin ta zauna. “baby an kammala haɗa dinner” “thanks U Aunty sophi”ta faɗa tana miƙa mata hannunta,kama hannunta Aunty Sophia tayi. har aka kammala mata gyaran jiki dana gashi hannunsu na a cikin na juna,a tare su ka fice daga ɗakin zuwa dinning room Aunty sophia taso ta fara shiryawa amma ta nuna ba haka ba tafi son ta kammala dinner tukun. A jere su ka isa katafaren dinning room ɗin,a zagaye yake da glass wall wanda ke waje zai iya hangen abunda ke ciki,daga sama ƙatuwar crystal Chandelier ce ta sauko ƙasa yayinda take bada wani irin haske mai ƙyatarwa, zungureren dinning table ne mai kyan gaske aƙalla yana ɗauje da 20 chairs,komai na cikin sa golding color ne table ɗin a shaƙe yake da wasu irin warmers masu matuƙar kyau da ɗaukar hankali, kai tsaye zaka iya cewa da kumfar zinari aka yi su, sai ƙyalli su ke da ɗaukar ido. chefs ne a tsaitsaye cikin dinning room ɗin, ciki su ka ƙarasa,cike da girmamawa chefs ɗin su ka shiga rissinawa suna gaishe da uwar ɗakin na su,ciki ta ƙarasa ba tare da ta amsa masu gaisuwar da su ke mata ba, cikin kulawa Aunty sophia tayi masu alamar jinjina,murmushi ne ya bayyana a fuskarsu. kujerar dake gaban table wacce ke facing gaba ɗaya kujerun dinning ɗin Aunty sophia taja mata ta zauna,gaban table ɗin chefs ɗin su ka ƙaraso, ɗaya bayan ɗaya su ka shiga buɗe warmers, wani irin daddaɗan ƙamshi ne ya daki hancinta har sai dai ta lumshe ido. madaidaicin plate ɗaya daga cikin chefs ɗin ya ɗauka haɗe da serving spoon, abunda ya girka ya ɗiba ya zuba a plete ɗin,a gabanta ya ajiye mata, jinjina kai tayi tana kama hannun Aunty sophia dake tsaye kamar sauran masu chefs. “please ki zauna mana” ta faɗa fuska a marairaice, girgiza mata kai Aunty sophia tayi “kiyi sauri kici time na tafiya” ƙwaɓe mata fuska tayi “kin san bana iya cin abinci ni kaɗai” ta faɗa a shagwaɓe “baby kina da rigima” “ni dai naji, idan kuma baza ki bani ba na tashi” “kema kin san bazan so ki zauna da yunwa, kwantar da hankalinki” Aunty sophia ta faɗa tana jan chair ɗin dake kusa da wacce take zaune ta zauna, spoon ɗin dake cikin abincin ta ɗauka, a hankali ta shiga ɗibar abincin tana bata,har wani lumshe ido take da alama ya mata daɗi, ba ƙaramin farin ciki chef ɗin yayi ba ganin yanda take lumshe ido. spoon biyu zuwa uku ta amsa ta kauda kai, fahimtar abunda take nufi ne yasa wani chef ɗin saurin matsowa, shima ɗibar wanda ya girka yayi kamar na farkon ya miƙama Aunty sophia, amsa tayi tana ture wacan gefe, shima spoon biyu zuwa uku tayi ta kauda, ɗaya bayan ɗaya masu aikin su ka shiga zuba na su suna ba Aunty sophia,abun gwanin ban sha'awa chefs ɗin ke kallon su kamar uwa da ƴa,a ƙalla taci kusan kala shidda kafin ta buƙaci da Aunty sophia ta bata lemu. ɗaya daga cikin chefs ɗin ne ya tsiyaya mata lemu a wani haɗaɗɗen cognac balloon glass ya miƙama Aunty sophia, amsa tayi tana nufar bakin Nailarh da cup ɗin,sai da tasha kusan rabi tukun ta janye bakinta,tashi tayi ta nufi ƙofar fita daga dinning room ɗin, ajiye cup ɗin Aunty sophia tayi tabi bayanta. gyaran dinning room ɗin chefs ɗin su ka shigayi da kansu, su Luna na ganin ta nufi bedroom ɗinta su kayi saurin bin bayanta, dakatar da su Aunty sophia tayi, badan sun so ba su ka dakata, kwata kwata basa jin daɗin yanda Aunty sophia ke hanasu Aikin su wani lokacin, shiyyasa su ka fi son madam na gidan ita bata shiga hurumin Aikin su duk da kuwa itace mahaifiyar Nailarh. A tsakiyar bedroom ɗinta ta sameta “muje ko baby” Aunty Sophia ta faɗa tana kama hannunta cikin nata, dressing room ɗin ta su ka nufa “yau ke zaki shirya ni ne?” ɗaga mata kai Aunty Sophia tayi dai dai lokacin da take tura ƙofar dressing room ɗin. faskeken mirror dake ɗakin Nailarh ta nufa zama tayi kan ɗaya daga cikin chairs ɗin Aunty Sophia kuma ciki ta ƙarasa. ɓangaren haɗaɗɗun suit ɗinta Aunty Sophia ta nufa,bata wani tsaya ruwan ido ba ta ɗauki mata wasu Black color,wurin underwears ɗinta ta nufa plunge and high waist bikini ta ɗauko mata suma Black color. mirror ta nufa hannunta ɗauke da kayan “tashi kisa” Aunty Sophia ta faɗa tana miƙa mata kayan dake hannunta,kallon kayan tayi haɗi da kallon Aunty Sophia “kin san bazan iya sa kayan nan ba” ɗan hararar ta Aunty Sophia tayi “saboda baki da hannu ko mi?” “amma ai kin san bani ke sawa da kaina ba,kuma ki ka hana masu saman shigowa,tunda har ki ka hana su shigowa dole ki saman da kanki” cikin muryar lallashi Aunty Sophia tace “my baby mi yasa kullum ki ke son maida kanki baya ne,ya kamata ace yanzu da kanki ki ke wasu abubuwan ko dan saboda gaba,ko so ki ke kiyi Aure a haka komai sai anyi maki,ki sani ba kowane namiji bane zai lamunci wannan sangartar taki ba” “wa yace maki ni zanyi Aure?” Nailarh ta faɗa tana tsare Aunty Sophia da idanu,yanayin fuskar Aunty Sophia ne ya canza ta rasa mike damun Brain ɗin Nailarh kwata kwata bata tunani irin na mutane. “kina nufin haka zaki tabbata?” “ƙwarai ma kuwa,ni Aure baya ɗaya daga cikin tsari na,a taƙaice ma na tsani maganar shi” ta faɗa tana wani ya mutse fuska. girgiza kai Aunty Sophia tayi “please ko dan saboda ni ki daure kina wasu abubuwan da kanki” “bazan iya ba!” ta bata amsa a taƙaice, marairaice fuska Aunty Sophia tayi “please Nailarh Aunty Sophian ki fa?” “sorry Aunty Sophi bazan iya ba ne” “shikenan,yanzu karɓi ki sa” “bazan iya ba” ta sake faɗa,lallashinta Aunty Sophia ta shigayi Dan ta samu ta sa kayan da kanta amma fir taƙi amincewa,dan dole Aunty Sophia ta shiryata da kanta. sosai kayan su kayi mata kyau abunka da farar fata sai ta fito a ainihin baturiyar ta, high hills masu shegen tsini Aunty Sophia ta ɗauko mata tare da wristwatch haɗe da earrings,da kanta ta saka mata wristwatch da earrings ɗin bayan ta ajiye mata hills ɗin a ƙasa,zura ƙafarta tayi a takalmin. “baby kin yi kyau sosai” Aunty Sophia ta faɗa, murmushi Nailarh ta saki “thanks” locker ta ta nufa,ƙofar fita Aunty Sophia ta nufa tana faɗin “baby zan jiraki a parlor” Bata tsaya jin mi Nailarh za tace ba ta fice. murmushi Nailarh ta saki ta rasa miye matsalar Aunty Sophi da gun kwata kwata bata son kallon locker ta bare akai da abunda ke cikin ta,buɗe locker tayi ta ɗauki pistol,a ƙugunta ta soke ta tukun ta rufe locker. jerin shades ɗinta ta nufa,Black color ta ɗauka ta zura a idonta,ficewa tayi daga dressing room ɗin, wayarta dake ajiye saman makeken gadonta ta ɗauka. a parlor ta samu Aunty Sophia na jiranta,tunda suka shigo main parlor gidan masu aiki ke bin Nailarh da kallo baƙaramin tafiya da su wankan nata yayi ba. russunawa suka shiga yi suna gaishe da ita,hannun kawai ta ɗaga masu,a jere su ka samu motocin da zata fita da su a compound, jiki na rawa security guard ɗinta suka shiga gaishe da ita,suma hannu kawai su ka samu ta ɗaga masu,har gaban motar da zata shiga ƙirar ACURA RDX black color Aunty Sophia ta rakata,da kanta ta buɗe mata back seat ɗin motar ta shiga ta rufe,ɗaga mata hannu tayi tana juyawa ta koma ciki. A jere motocin su ka fice daga gidan,babban titin da zai fitar da su gaba ɗaya street ɗin su ka hau,suna karya wata kwana motocin su Joseph suka kunno kai,haɗewa su kayi da nata motocin su ka ɗauki babbar hanyar da zata sada su da ƙaton PORT dake RENO. Tafiya su kayi mai ɗan nisa tukun su ka iso PORT,ƙaton port ne iya ganinka,ga manya manyan truck dake kai kawo ɗauke da containers,a parking lot ɗin dake port ɗin su kayi parking. kusan a tare su ka buɗe cars door ɗin su ka fito,motar Nailarh securitys ɗin su ka nufa tare da Joseph,car door su ka buɗe mata ta fito,ya mutse fuska tayi tana kallon port ɗin kafin ta kai dubanta ga Joseph. “ina containers ɗin su ke ne?” ta faɗa ganin tarin containers dake wurin ga wanda trucks ke ɗawainiyar ɗauka. “sai mun fara zuwa office ɗin C G tukun” “ok mi kake jira” “sorry boss” ya faɗa yana ɗan rissinar da kai haɗi da nufar office ɗin CG ɗin dake cikin port ɗin,tsaki taja tana komawa cikin motar ta zauna,bata rufe door ɗin ba ƙafarta ɗaya a ciki ɗaya a waje. Bayan kamar 5 minutes Joseph ya dawo tare da wani mutumin dake sanye da uniform white color hannunshi ɗauke da wasu takardu, bayansu matasan samari ne har su shidda suna sanye da overall orange color. har gaban motar su ka ƙaraso, ƙarasawa Joseph yayi bakin door ɗin motar “boss ga CBP nan,shine in charge na cargos ɗin” zame shade ɗin dake fuskarta tayi tana kallon mutumin da tunda Joseph yayi magana yake washe baki “ƙarasa” Joseph ya faɗa yana nuna mashi bakin door ɗin motar,ƙarasawa mutumin yayi,fuskarshi ɗauke da fara'a ya gaishe da ita cikin girmamawa. glass ɗinta dake hannunta ta ɗaga mashi alamar amsawa, murmushi ya saki yana jin jina kai, takardun dake hannunshi haɗe pen ya miƙa mata “CG ya sa hannu sai naki kawai ya rage” yamutse fuska tayi tana karɓar takardun da yake miƙo mata, sign ta shiga yi a takardun ba tare da ta ko karanta abun da su ka ƙunsa ba. miƙa mashi tayi tana faɗin “what next?” “za muje ne kiga kayan” “ba sai naje ba kawai su ɗauko” ta faɗa “please madam ganin yanada amfani,kuma zaki shaida adadin containers nawa ne su ka iso” yamutse fuska tayi tana zuro ƙafarta da nufin fitowa ringing ɗin wayarta ne ya dakatar da ita,jawo wayar tayi tana duba sunan mai kiran nata Sweetheart shine sunan daya bayyana a screen ɗin. picking call ɗin tayi haɗi da kara wayar a kunnenta,fitowa ta yi su ka nufi cikin inda containers su ke,cike da shagwaɓa take waya da mahaifiyar ta ta data kira dan taji ya abun yake tafiya. a gaban wani ƙaton container ship dake bakin ruwa, trucks na jidar containers su ka tsaya, Nailarh na can bayan su tana waya,nuna ma Joseph containers ɗin su da trucks su ka ɗauka har guda biyar yayi. jinjina kai Joseph ɗin yayi “aikin ka yayi kyau,fatan kayi waya da Madam?” “eh tun kafin ma ku ƙaraso ta kira ni” “ok good,muje ko” Joseph ya faɗa yana nufar Nailarh harta kammala wayar. Juyawa tayi ta koma inda su kayi parking,motar ta shiga security daya buɗe mata ya rufe door ɗin,sallama Joseph yayi ma in charge ɗin ya shige motar shi, a jere su ka fice daga port ɗin trucks ɗin containers ɗin su na biye da su... A jere su ka fice daga port ɗin trucks ɗin containers ɗin su na biye da su, wata hanya su ka ɗauka daban, tafiya su kayi mai ɗan nisa kafin su ka iso wani ƙaton orphanage, daga yana yin ginin zaka san cewa bana ƙana nan mutane bane,yanada girma sosai. horn su kayi a bakin gate ɗin, can cikin bacci masu gadin orphanage ɗin su ka ji ƙarar horn ɗin, ba suyi mamakin jin horn da tsohun dare nan ba saboda mamallakan orphanage ɗin sun saba yi masu shigar dare irin haka. ɗaya daga cikin securitys ɗin ne ya leƙo ta ƴar ƙofar dake jikin gate ɗin,kallo ɗaya yayi ma motocin ya fahimci ko su waye, a hanzarce ya koma ciki, gate ɗin ne ya shiga zugewa zuwa gefe guda, da gudu motocin su ka danna kai zuwa cikin orphanage ɗin,da sauri securitys ɗin su ka shiga motocin dake bakin gate ɗin su ka bi bayan motocin. wasu irin gine gine na zamani su ka shiga wucewa ba laifi Orphanage ɗin yanada girma sosai, a bakin wasu manya manyan store har guda biyar su ka yi parking,fitowa su ka shiga yi daga cikin motocin su, wani matashin saurayi ne ya fito daga motar Joseph tun ɗazu sai yanzu ya fito,black American ne, neck ɗin shi yasha zanen tattoo kallo ɗaya zaka mashi ka gane riƙaƙen ɗan duniya ne. motar da Nailarh ke ciki Joseph ya nufo, back seat ya buɗe mata, fitowa tayi a dai dai lokacin da securitys ɗin ke ƙarasowa, da sauri su ka nufeta, gaishe da ita su ka shigayi cikin girmamawa, ko arziƙin kallo basu samu daga gareta ba, trucks ɗin ta nufa umarnin a buɗe su ta bada,fitowa drivers ɗin su ka shigayi,kowace truk mutum uku ne su ka fito daga cikinta, babu ɓata lokaci su ka shiga buɗe bayan truck ɗin, wasu irin tarin kwalaye ne a bayan truck ɗin, da hannu tayima Joseph alama da ya zo, da sauri ya nufo in da take, wayarta ta miƙa mashi,da sauri yasa hannu ya amsa,video ya shiga ɗaukar kayan. truck ɗayace ba'a buɗe ba kallon drivers ɗin tayi “wannan fa?” ta tambaya tana nuna masu truck ɗin, Joseph ne yayi saurin faɗin “ina tunanin itace wacce madam tace kar a shiga da ita” cike da bada umarni ta furta “ku buɗeta” da sauri Joseph yace “ba kuji ana magana” a hanzarce su ka shiga buɗe truck ɗin, wani irin mummunan faɗuwa gabanta yayi a lokacin da tayi arba da abunda batayi tunanin gani ba, da tsantsar mamaki take kallon matasan ƴan mata da samari dake bayan truck ɗin an rufe masu bakunansu yayinda hannayen su ke a ɗaure. da sauri Joseph ya sauke wayar ƙasa, da mugum mamaki tashiga kallon drivers ɗin kafinta sauke idanunta akan Joseph, cike da tuhuma ta furta“miye wannan?”babu wanda ya iya buɗe baki a cikin su ya bata amsa, suma sun shiga ruɗan, sunyi matuƙar mamakin ganin yaran, wata irin gigitacciyar tsawa ta daka masu kamar ba Nailarh ba. “tambayar ku nake miye wannan, ina aka samu wannan yaran??” ɗaya daga cikin drivers ɗin ne yayi ƙarfin halin bata amsa “mu ma bamu sani ba kawai dai mun samu truk ɗin a cikin jadawalin da miss m...“ kasa ƙarasawa yayi saboda tsawar data daka mashi, bashi da tayima tsawar ba hatta Joseph sai da ƴan hanjin cikinsa su ka kaɗa. gaba ɗaya fuskarta ta rikiɗe da tsantsar ɓacin rai, a fusace ta buɗe baki da nufin magana amma sai ringing ɗin wayarta ya dakatar da ita, da saurin Joseph ya miƙa mata wayar, picking call ɗin tayi ba tare da ta ko duba sunan mai kiran nata ba. muryar mahaifiyarta ce ta daki dodon kunnenta daga cikin wayar “hello baby har kun kammala” saurin maida kiran tayi zuwa video call, back camera ta kunna ta saita wayar dai dai inda truck ɗin take. “momy wannan container ta waye?” ta faɗa ranta a matuƙar ɓace, a kwance take saman hammock chair a bakin beach daga Ita sai bra da wani matsiyacin pant mai igiya gefe da gefe kusan rabin mazaunanta a waje,ta rufe idonta da baƙin shade hannunta a riƙe da coconut drink tana sha. cike da bariki irin bata fahimci mi Nailarh take nufi ba tace “wace container baby?” “wacce idanunki su ka nuna maki” ta bata amsa dai dai da tambayarta dan ba ƙaramin ɓaci ranta yayi da ganin yaran ba. “sorry baby na manta banyi maki bayani ba,marayu ne basu da gata, gashi suna fama da wata lalura na turo su nan ne saboda suna buƙatar emergency treatment” maida front camera tayi tana jifar mahaifiyarta ta da wani kallon rainin wayao “amma momy kwata kwata yaran nan basuyi kama da patient ba kama suke da wanda a kayi kidnapping, momy ina ki ka samo yaran nan?” ta kai ƙarshen maganar babu alamun wasa “baby kin fi kowa sanin mahaifiyarki ko dabba bazata iya sacewa ba bare mutum, ki yarda da ni yaran nan taimakonsu kawai nake son yi” “idan taimakonsu ki ke son yi mi yasa baki turosu a Flight ba amma ki ka turo su a container bakunan su a rufe,mi hakan yake nufi?” “ki yarda da ni baby taimakonsu nayi” ta faɗa cike da shagwaɓa kamar bada ƴarta take magana ba “gaskiya banji daɗin yanda ki ka sa aka ɗaure su ba,kamar wasu dabbobi” “sorry baby na amshi laifin hakan bazai sake faruwa ba, sorry” ta faɗa tana ɗan kama kunnenta, tsaki Nailarh taja tana rejecting kiran. umarni ta bada akan su fito da yaran bayan ta tura securitys ɗin orphanage ɗin sun kira doctors ɗin dake hospital ɗin orphanage ɗin, ɗaya bayan ɗaya su ka shiga fito da yaran sai layi su ke kamar za su kifa ƙasa da alama wani abun aka basu wanda ya gusar masu da hankalin su. doctors da nurses dake ɗauke da stretcher ( gadon ɗaukar marasa lafiya) su ka ƙaraso wasu sun su sai hamma suke da alama daga bacci su ke, cike da girmamawa su ka shiga gaishe da Nailarh bata wani amsa masu ba ta bada umarnin a ɗauki yaran, babu ɓata lokaci su ka shiga ɗaukar yaran a gadon ɗaukar marasa lafiya suna nufar hospital ɗin, bayan su Nailarh tabi, ganin haka ne yasa Joseph bin bayan su. cikin gaggawa likitocin su ka shiga ba yaran emergency treatment dan ganin sun dawo cikin hayyacin su, sun shafe awanni da yawa suna abu ɗaya sai da ƙyar su ka samu yaran suka farfaɗo amma sun gagara gane taƙamaimai abunda ke damun yaran. kallon Nailar dake zaune saman waiting chair Joseph yayi, idanunta a lumshe bacci ne sosai a idonta amma saboda san ta san mike damun yaran taƙi tafiya gida, cike da tausasa murya joseph yace “boss ya kamata ki tafi gida ki huta” “bazan tafi ba sai na san abunda ke damun yaran nan” “am sorry boss, da dai kin tafi har yanzu bincike doctors ke yi kuma na san idan suka gama bincike har gida za su kawo maki result ɗin” “kana ba kanka wahala Joseph babu in da zan tafi bansan abunda ke damunsu ba” lallashinta ya shiga yi shida securitys ɗin amma babu wanda ta saurara a cikin su sai ma cewa tayi idan ba so suke suyi ta aikin su ba to karsu sake mata magana. ganin dai da gaske ba amincewa za tayi ba ne yasa Joseph yanke shawarar kiran mahaifiyarta, number mahaifiyarta ya shiga dannanama kira amma ba tayi picking ba, canza akalar kiran yayi ga Aunty sophia, baiwar Allah tunda Nailarh ta fita bata rintsa ba, ta kasa zaune ta kasa tsaye hankalinta duk a tashe yake saboda inda Nailarh ta tafi, kiran Joseph na shiga wayarta har sai da gabanta ya faɗin, jiki na rawa tayi picking ko da ya sanar da ita dalilin kira ba ƙaramin kwanciya hankalin ta yayi ba. “please bata wayar” ta faɗa, da sauri ya miƙa mata wayar“boss miss sophia na son magana dake” a hankali ta buɗe ido tana jifanshi da harara, saurin sadda kanshi yayi ƙasa, kauda fuska tayi gefe ba tare da ta amshi wayar ba, kara wayar yayi a kunnenshi “taƙi karɓar wayar” ya faɗa “sata a speaker” shine kawai abunda Aunty sophia ta faɗa,ok ya furta yana sa wayar a speaker “hello baby kina jina?” Aunty sophia ta faɗa da wata kalar kasalalliyar muryar ta wanda bacci ke neman fin ƙarfinshi ta furata “Aunty sopei ” “baby mi yasa baki son ki dawo gidan, kin san yanda hankali na ya tashi da fitar da ki ka yi, tunda ki ka fita ko bacci na kasa yi please ki dawo gida” “zan dawo Aunty sopei kawai ina son na san abunda ke damun yaran” “karki damu har gida doctor zai kawo maki result ɗin su kuma nayi maki alƙawarin tare da ni zamu zo duba su idan doctors sun kallama bin cike amma yanzu ki dawo gida” “shikenan sai na dawo” “yawwa ko ke fa keda na sanki babu ruwanki da shiga abunda bai shafeki ba?” “ke ki ka fara koyaman damuwa da damuwar mutane” murmushi Aunty sophia ta saki da alama taji daɗin maganar Nailarh. “sai kin dawo” da ok ta amsa mata, rejecting kiran Joseph yayi yana sauke ajiyar zuciya, harara Nailarh ta watsa mashi murmushi kawai ya saki, tashi tayi ta leƙa ɗakin da yaran suke kafin ta nufi ƙofar fita,har inda motocin su suke doctors ɗin suka rakata kafin sukayi mata sallama. a guje motocin su ka fice daga orphanage ɗin, tun a hanya su ka rabu da su Joseph su kuma suka kama hanyar gida, Nailarh bata san sun iso gida ba saboda tun a moto bacci yayi awana gaba da ita, sai da Aunty sophia tasheta tukun ta san sun ƙaraso,fitowa tayi su ka nufi cikin gidan, direct bedroom ɗinta Aunty sophia ta nufa da ita, suna shiga ta faɗa kan bed ko takalman dake ƙafarta bata cire ba. murmushi kawai Aunty sophia ta saki, da kanta ta shiga rage mata kayana jikinta, rigar suit ɗinta ta zame mata haɗe da earring ɗinta da wristwatch tukun ta zame mata takalman ƙafarta, idanunta ta sauke akan gun ɗin dake suke a ƙugunta har zata wuce sai kuma tasa gefen suit ɗinta ta zame gun ɗin, a cikin rigar ta naɗeta,dressing room ɗinta ta nufa, maida komai tayi a mazauninshi, a saman locker ta ajiye mata gun ɗin saboda bata san password ɗin locker ba kuma Nailar tafi amfani da eye I D, ficewa tayi daga dressing room ɗin ta koma bedroom ɗin, gyara mata kwanciya tayi kafin ta fice daga ɗaki baki ɗaya. *ABUJA NIGERIA* Nainarh da yumnah ne suka fito daga bedroom ɗin mom,less ne a jikin yumnah ɗinkin bubu ta yafa mayafi saman kanta yayinda Nainarh ke sanye da riga da skirt na atamfa hijab ne a jikinta saɓanin yumnah dake da gyale, hannunsu riƙe da na su Ammar, Aman da jamala da alama fita za suyi. Part ɗin dady su ka nufa,da sallama a bakin suka shiga a parlor su ka sameshi shida mamy,ciki suka ƙarasa, kallo ɗaya mamy tayi masu ta ɗauke kai dady kuwa da fara'a sa yake kallon su, a saman rug carpet su ka zauna cike da girmamawa su ka gaishe da su dady kawai ya amsa masu amma mamy yi tayi kamar ma bata san da zaman su a parlorn ba. “my friends sai ina haka?” dady ya faɗa yana kallon su Ammar, Aman ne ya bashi amsa da “gidan papah” ɗaure fuska dady yayi “shine za ku fita ba tare da ni ba, kodai mun dai abotar ne ban sani ba?” jamal ne yayi saurin cewa “A'a ka tambayi Aunty Nainarh idan tace aje da kai shikenan” gaba ɗayan su suka kai duban su ga Nainarh da kwata kwata hankalinta baya kansu tunda su ka shigo idanunta suka sauka akan wani ƙaton photo dake manne a bango,sosai ta shagala da kallon photon, tayi mamakin ranar da su ka shigo bata ganshi ba tunanin ta fara yi to kodai ba'a jima da sashi ba. ɗan taɓo ta yumnah tayi “dady na magana” da sauri ta kai dubanta ga dady “Aunty Nainarh jamal yace sai kin amince za'a tafi dani, za kuje dani kuwa?” saurin sadda kai ƙasa tayi tana sakin murmushi, murmushi shima dadyn ya saki yana leƙa fuskarta “idan na fahimta wannan shirun alamace ta ba'a zuwa dani” da sauri ta ɗago tana faɗin “A'a dady zamuje da kai” “wasa nake maku sai kun dawo ina gaishe da mutanen gidan” tashi yumnah tayi tana kama hannun Nainarh “za su ji in sha Allah, ku tashi mu tafi”sallama su kayi masu suka fice, taɓe baki mamy tayi tana kallon dady “wai ni kam Janar da sanenka wannan yarinyar take zaune a gidan nan?” “wace yarinya kenan” dady ya faɗa yana kai duban shi gareta dan bai fahimci akan wa take magana ba “wacce su ka fita yanzu da yumnah” “wai kina magana ne akan Nainarh” “ni ban ma san sunanta ba amma ita nake nufi” “da sani na take zaune gidan akwai matsala ne?” “ni gaskiya bana son zamanta a gidan nan” “miye matsalar ki da zamanta a gidan yarinyar da ba'a kanki take ba” “kamarya miye matsalata, gidan mijina ne fa,kawai sai mu zuba ma zulaihart ido tayi ta yin abunda taga dama, hakanan zata kwaso mana yarinya idan ta cutar damu fa??” tunda ta fara magana dady ya kafeta da ido tsantsar mamaki ne akan fuskarshi ko miye abun masifa kamar wacce ke jiran mutane “ni gaskiya bana son zamanta gidan” “ta kawo duk wanda zata kawo gidan mijinta ne kuma gidan ƴaƴan tanada ƴancin ajiye duk wanda ta so” “haba Janar wai miyasa kullum kake fifita zulaihart a kaina ne, komai tayi dai dai ne a wajenka amma ni kuskure ɗaya zanyi ka ɗau mataki a kaina” ta faɗa rai a ɓace,mamaki yaƙi ɗaukewa akan fuskar dady lamarin mamy har tsoro yake bashi “ni gaskiya bana son zamanta a gidan” “to sai mi dan baki son zamanta a gidan, naga ba'a kanki take ba kuma gida gidana ne kuma ni na amince da zamanta dan haka bana son na sake jin kinyi tari akan Nainarh, idan ba haka ba ranki ne zai ɓaci” “hakama za kace,kenan Zulaihart tafini?” rai a ɓace dady yace “Zulaihart tafiki komai mabaruka, ko ƙafarta baki kama ba, dan Zulaihart ban taɓa bata umarni ta saɓa man ba, Zulaihart bata man rashin kunya kamar yanda ki ke man,Zulaihart bata sa'insa dani,nayi mata cin mutuncin mafi muni a rayuwa amma haka nan tayi haƙuri dani take zaune da ni har kawo yanzu duk da a ƙasarta da Al'adarta bata saba ganin irin haka ba sannan ki sani Zulaihart ta fiki haƙuri mabaruka” wani irin ƙululun baƙin ciki ne ya tokare zuciyar mamy, idan da abunda ta tsana a rayuwa taji ana yabo mom musamman dady abun na ɓata mata rai, rai a ɓace ta fice daga part ɗin gaba ɗaya, da kallo kawai dady ya bita. Su Yumnah suna fita daga part ɗin dady ficewa su kayi daga gidan baki ɗaya,suna fitowa motar ya Naeem na kunno kai cikin parking space ɗin, ɗan dakatawa su kayi, daidaita parking ya Naeem yayi, kusan a tare aka buɗe car doors ɗin su fito,ya Naeem ne ya fito daga driver seat yayinda ya Adanan ya fito daga front seat. Uniform ne a jikin ya Naeem yayinda ya Adnan ke sanye da suit back color, da gudu su Ammar su ka nufe su, hugging ɗin ya Naeem su kayi ɓata fuska ya Adnan yayi kamar ƙaramin yaro yana faɗin “abun ƴar haka ce ya Naeem kawai ku ka sani, shikenan nima ai ga Autar dady nan” ya faɗa yana buɗema Yumnah hannayen shi, da sauri ta nufeshi tana sakin dariya, faɗawa tayi jikinshi tana hugging ɗin shi. murmushi Nainarh dake tsaye ta saki, yaran mom na matuƙar burgeta Irfan ne kawai take ganinshi daban a cikin su kamar ya banbanta da su. “dady mun fara gaishe da second father ne fa”Aman ya faɗa yana turo baki “ba wani nan, bana dai yi daku, da Autar dady nake yi” “ku rabu dashi kishi ne kawai” ya Naeem ya faɗa yana basu hannunshi suka tafa “sai ina haka?” Ya Adnan ya faɗa lokacin da yake raba jikinsu “gidan uncle Mustafa” yumnah ta bashi amsa “a dawo lafiya muna gaishe da mutanen gidan” “za suji in sha Allah” kama hannun ya Adnan ya Naeem yayi yana faɗin “sai kun dawo” da sauri Nainarh ta gaishe da su ganin za su bar wajen,duban suka kai gareta Murmushi ya Naeem ya saki “lafiya lau Nainarh, ya gidan” da Alhmdllh ta amsa mashi, ya Adnan tunda ya kafeta da idanu ƙala baice ba, duk tsawan wannan lokacin da Nainarh ta ɗauka bai taɓa ganinta ba in fact ma baisan wacece ba, ɗan taɓoshi ya Naeem yayi “baka ji ana gaishe ka” washe mata baki yayi yana faɗin “lafiya” murmushi ta sakar mashi “muje ko, Yumnah sai kun dawo” ya Naeem ya faɗa yana nufar ƙofar shiga gidan, ya Adnan kasa ɗauke idonshi yayi a kan Nainarh har su ka nufi motar Yumnah su ka shiga, yumnah har ta buɗe driver seat zata shiga yayi saurin jawo Arm ɗinta, bayan motar yajata. da tsantsar mamaki take binshi da kallo, hannu yasa ya kauda fuskarta gefe “kin wani tsare ni da ido, tambayarki zanyi wacece waccan?” ya faɗa yana nuna cikin motar “wai Nainarh?” “sunanta kenan?” “eh sunanta kenan, ɗiyar fa mom Asma'u ce” ɗan zaro ido waje ya Adnan yayi “amma ya akayi ban santa ba?” “may be baka zuwa gidan ne” “eh gaskiya bana zuwa, wajen mom ta zo?” “ai ka san abunda ya faru da mom Asma'u to shine mom ta dawo da ita nan gidan” “ok na tuna”murmushi Yumnah ta saki tana kallon fuskarshi “na tafi?” “idan kin tsaya wani abun za kiyi man ne?” “ok sai mun dawo” ta faɗa zata bar wajen,muryar Noor ce ta dakatar da ita, da sauri su ka kai duban su ga Noor dake fitowa daga cikin mota,palazzo trouser ne a jikinta haɗe da shirt open shoulder,daga sama rigar ta kama jikinta sosai kusan rabin brest ɗinta a waje,ga wasu irin high hills masu shegen tsini tasa, ɗan siririn mayafi ne a saman kanta. fuskarta da fara'a ta nufo su, tana ƙarasowa tayi hugging ɗin ya Adnan, saurin tureta yayi daga jikinshi rai a ɓace yace“wai Noor har sau nawa zance maki kidaina hugging ɗina, wai ke baki san cewa ni ba muharraminki bane akwai fa Aure a tsakanin mu” ɓata fuska tayi kamar zata fashe da kuka “ya Adnan daga kawai nayi murnar ganinka”harara ya watsa mata yana kallonta tundaga sama har ƙasa “yanzu dan Allah miye amfanin wannan suturar dake jikinki, yanzu mom Fatilah na kallonki ki ka fito a haka?” cike da shagwaɓa tace “miye aibun kayan dake jikina ya Adnan?” “ban sani ba” ya faɗa haɗi da jan tsaki, bari wurin yayi gaba ɗaya ya nufi cikin gidan. taɓe baki tayi tana kallon Yumnah “ina zaki na zo wajen ki?” “kin dai zo wajen ya Irfan kuma duk yau baizo gidanan ba” “ke fa banza ce wa yace maki wajen shi nazo, na zo gaishe da Mom ne” “a haka?” Yumnah ta faɗa tana kallon kayan jikinta, ɓata fuska Noor tayi “wai miye matsalar kayan jikina ne?” “ok bama kiga matsalar su ba, na so ace second father ki kayi hugging ba ya Adnan ba,da kuwa kin san matsalar kayan jikin ki” “shikenan ni dai naji, ina zaki?” “gidan Uncle Mustafa” “kai Yumnah yanzu sai ki tafi duk da na zo?” “eh mana saboda na san ba wajena ki ka zo ba, idan kuma kina zuwa to?” “kin san halin mom Maryam ina zuwa zata rufeni da mashifa ita komai nayi rashin kunya ne” “da gaskiyarta Noor kuma tana yi maki haka ne dan ki gyaru, ki zo muje kawai” gyaɗa kai Noor ɗin tayi, motar Yumnah su ka nufa, back seat ta buɗe kusa da su Ammar tashiga Yumnah kuma ta buɗe driver seat, key Yumnah tayi ma motar “sorry kinjini shiru ko,ga sister Noor nan ku gaisa” ta faɗa tana kallon Nainarh. Juyowa Nainarh tayi “sannu, ya gida” da lafiya lau Noor ta amsa mata, gaishe da Noor ɗin su Ammar su kayi da fara'arta ta amsa masu tana tambayar “wane ɗan kasadar ne ya baku wayarshi?” ta faɗa tana kallon wayar dake hannunsu suna buga game Aman ne ya bata amsa da “ta Aunty Nainarh ce” taɓe baki tayi tana kai dubanta ga Yumnah “sister Yumnah wai da gaske ya Irfan baizo ba, daga Villa nake fa can ma baya nan kuma sai kiran wayarshi nake bana samu” “ni dama na san ba wajen mom ki ka zo ba” “ni dai naji, dan Allah yana ina?” “wallahi rabona da ganin ya Irfan tun jiya da muka dawo daga gidan Abbah, amma yau da safe naji sunyi waya da mom, ki gwada kiran ya Waseef na san dole suna tare” “kin kawo shawara” ta faɗa tana zaro wayarta daga cikin Aljihun wandonta, Number Waseef tayi dialing, bugu biyu ya ɗaga “hello Noor, ya ki ke ya gida?” “lafiya lau ya Waseef, wai ina ka kaiman ya Irfan ne tun jiya nake faman neman number shi baya picking??” “amma kin raina man wayo Noor wato nima na kai Irfan ɗin wani waje ko” “eh mana” ta faɗa a shagwaɓe. shiru taji baice komai ba, jin Waseef yayi shirune yasata faɗin “dan Allah yana ina?” muryar Irfan taji daga cikin wayar “hello beb” “haba ya Irfan ka san kuwa halin daka jefani ciki kuwa, sai kiraka nake bana samu dama jiya ka bani haushi shine ma ka kashe wayarka ko nayi duk abunda zanyi?” “sorry Noor ba haka bane, kina a raina wani uzuri ne ya sani kashe wayata amma kiyi haƙuri, kina ina ne yanzu?” “gajiya nayi da nemanka na zo gidan big dady ko zan sameka” “ok kina can yanzu?” “A'a mun fita tare da su Yumnah zuwa gidan Uncle Mustafa” “sorry gani nan zuwa kinji” “zan jiraka fa karka shanya ni?” “karki damu zan zo kinji” “ok sai ka zo” “ok bye” ya faɗa yana rejecting kiran, ajiyar zuciya ta sauke tana turu wayar cikin Aljihun wandonta. murmushi yumnah ta saki “gaskiya na kusa tona maku asiri keda ya Irfan kowa ya san abun da ke tsakanin ku” saurin kallonta Noor tayi “ban gane abunda ke tsakanin mu ba?” “zan fallasaku kowa ya san soyayya ku ke” ajiyar zuciya Noor ta sauke tana dafe saitin zuciyarta da “da kuwa kin kyauta min Yumnah dan na gaji da hiding ɗin da ya Irfan ke yi” dariya Yumnah tayi “da ɗina dake fa Noor rashin kunya, yanzu ya Irfan na hiding amma ke so ki ke a faɗa ko, idan basu amince ba fa??” “wallahi har poising zan iya sha idan har su kace za su rabani dashi” da wani mugun sauri Nainarh ta juyo tana kallonta dan kalamanta sunyi matuƙar bata mamaki. murmushi ta sakar mata tana kashe mata ido ɗaya, saurin juyawa Nainarh tayi tana girgiza kai. murmushi Yumnah ta saki “za ki iya fiye da haka,dan na lura baki da hankali a kan ya Irfan” “duk ma wanda yace maki inda hankali akan ya Irfan yayi maki ƙarya” “Allah ya shirye ki” shine kawai abunda Yumnah ta ce yayinda take shiga compound ɗin gidan Uncle Mustafa, parking tayi “Ameen idan da gaske ki ke” Noor ta faɗa tana fitowa daga cikin motar, girgiza kai kawai Yumnah tayi. A tare Yumnah su ka fito ita da Nainarh, back seat Yumnah ta nufa tana buɗema su Ammar. sojoji ne ta ko ina a harbar gidan, da gudu su Ammar su ka nufi ƙofar shiga gidan. mom maryam na zaune a katafaren mai parlorn gidan su ka shigo da gudu su ka faɗa samanta har sai da ta ɗan tsorata “wane mai son gamawa da duniya lafiya ne ya kawo man ku?” dariya su kayi suna faɗin “su Aunty Yumnah ne” da sauri ta kai dubanta ga ƙofar shigowa saboda sallamar su Yumnah da taji. zambur ta miƙe tsaye tana rabka salati “innalillahi wa Innah ilaihi raji'un” wani irin mummunan faɗuwa gaban su Nainarh yayi da sauri su ka juya... Da sauri su ka juya suna kallon bayan su dan duk a tunanin su wani abu ta gani a bayan su. “amma Allah wadaran naka ya lalace, yanzu ke Noor fatilah na kallonki ki ka fito haka ƙirji a waje, ubanwa zaki nunama ƙirji da ki ka fito haka” gaba ɗayansu su ka sauke ajiyar zuciya dan ba ƙaramin tsoro ta basu ba. turo baki Noor tayi gaba“ni dama shiyyasa bana son zuwa gidan nan idan muzo” “dama yaushe zaki so zuwa gidanan tantiriyar banza, wallahi Noor kiyi ma kanki faɗa kwata kwata wannan ba ɗabi'a bace mai kyau, kina zubar ma kanki da mutunci ne” “haba Momy yanzu dan Allah miye laifin kayan jikina?” baki mom maryam ta saki “shaiɗaniyar banza tambayata ma kike, kin wuce kinje ɗakin Kainart kin nemi kaya na mutuncin kin sa ko kuwa” baki Noor ta turo gaba“ni gaskiya bazan sa wasu k...” bata ƙarasa ba saboda yo kanta da mom maryam tayi,ai kuwa babu arziƙi ta kwasa da gudu zuwa cikin gidan. “mara kunyar banza ai dakin tsaya” ta faɗa tana nufar sofa data tashi ta zauna,dariya Yumnah da Nainarh su kayi suma suna samun wajen zama su ka zauna, cike da girmamawa su ka gaishe da ita, da fara'arta ta amsa masu tana tambayar mutanen gidan. “suna nan lafiya sun ma ce mu gaishe ku” “muna amsawa,wallahi ku riƙa yima yarinyar can faɗa tunda uwarta ta kawo ido ta sa mata, kwata kwata shigar da take bata dace ba, da wanan shigar sai ta rasa mijin Aure dan duk wanda ya san kanshi baizai kwashi wannan tarkacen ba, dan ni wallahi AHMER ya kwaso man mace irin wannan da sunan zai Aure sai nace ubanshi daga shi har ita” dariya Yumnah ta kwashe da ita“mom itafa Noor zaman waje ne ya maida haka” “ke ni dallah rabani,ku da kuke da alaƙa ta jini da turawa mi yasa baki shiga irin haka ƙarshen dai rashin kunya kenan ko, mi yasa Zulaihart bata zuba maki ido kina shigar da ki kaga dama ba,saboda ta san ciwan kanta” murmushi kawai Yumnah tayi ta san da ace mom maryam ta san Irfan ke son Noor da ya shiga uku dan saita rabasu may be shima dalilin da yasa kenan yaƙi bari kowa ya sani. “ku riƙa yi mata nasiha” “insha Allah mom zamu riƙa yi mata” “hakan shi yafi” “mom ina papah?” a cewar su Ammar “papah na wajen aikin, sai anjima zai dawo” “Allah ya dawo dashi lafiya” da Amee su duka su ka amsa. Noor koda ta shiga bedroom ɗin kwanciyart tayi saman bed ɗin ɗakin, wayarta tashi latsawa. *Uncle Hashim's House* Zaune suke a parlorn Uncle hashim Laatifa ce kawai babu, mom maimunatu na daga zaune saman sofa mai mazaunin mutum uku Balqis na kwance tayi pillow da laps ɗinta yayinda Uncle Hashim ke zaune saman rocking chair hannunshi riƙe da jarida yana dubawa. juyowa Balqis tayi tana fuskantar shi da ƴar shagwaɓa tace “dady wai har yanzu shiru maganar fara aiki na?” “ayyah sorry my daughter, shaf na manta na faɗa maki munyi magana da ya mutallaf harma na bashi takardunki” “na gaji da zaman gida ne” “karki damu zuwa next week za kuyi interview” “thanks u dady, momy nima na kusa fara fita aiki kamar Aunty Laatifa” murmushi mom maimunatu ta sakar mata tana shafa gefen fuskarta. “amma dady a wane hospital ya samar man aiki?” “muna da wani hospital ne bayan namu?” ya faɗa ba tare da ya kalleta ba “eh mana dady akwai S J Hospital, ni nafi son can” “wane hospital ne S J” “SAM Internati...” kasa ƙarasawa tayi saboda wani kallo da barrister ya watsa mata, dan dole ta shanye sauran maganar,maida hankalinshi yayi kan jaridar da yake dubawa yana jan tsaki. taɓe baki mom maimunatu tayi “ni da wannan sama mata aikin da miji kasa su ka fitar ita da ƴar uwarta kayi masu Aure in yaso sunyi Aikin a ɗakin mazajensu” “idan kin tashi Aurar da ƴarki babu wanda zai hanaki amma ni ƴata ba yanzu za tayi Aure ba” “ban gane idan na tashi Aurar da ƴata ba, wai kai barrister har yanzu bazaka sauko daga dokin zuciyar daka hau ba ka yafe ma ƴarka?” “bayan Balqis bana da wata ƴa a duniya, karki sake dangantani da ƴarki dan ranki ne zai ɓaci” tashi yayi yana kwashe Jaridar shi, juyawar da zaiyi yaga laatifa a tsaye bakin ƙofa kaf maganganunsu a kunenta, ɗauke kai yayi kamar ma bai gantaba ya nufi bedroom ɗinshi. juyawa tayi da nufin barin wajen, da sauri Balqis tace“laa Aunty Laatifa yaushe ki ka dawo?” juyowa mom maimunatu tayi tana kallonta “dawowata kenan ƙanwata, ya kike ya gida?” ta faɗa tana nufo cikin parlorn “lafiya lau Aunty Laatifa” murmushi kawai Laatifa tayi mata tana nufar mom “momy barka da rana ya gida?” “lafiya lau Laatifa, harkin dawo?” “eh mom,bari na shiga ciki na watsa ruwa duk a gajiye nake” ta faɗa yayinda take juyawa ta nufi bedroom ɗinta, da kallo kawai mom maimunatu ta bita fatan dai Allah yasa ba taji abunda Dadynta yace ba, Laatifa na matuƙar bata tausayi ta rasa miye matsalar barrister da bazai yafe mata ba. bin bayanta Balqis tayi, lokacin da ta shiga ɗakin Laatifa har ta shige toilet mayafinta da briefcase ɗinta kawai ta samu a kan bed, wuri ta samu saman bed ɗin ta zauna. tana shiga toilet ɗin tap ta kunna ta barshi hakanan kawai yana zuba a ƙasa,bakin bathtub ta nufa ta zauna,fashewa tayi da wani kuka mai ban tausayi, ta rasa wace irin zuciya dadynta gareshi da bazai iya yafe mata tsawan shekaru, tunani ta fara yi anya mahaifinta ne dan ta san babu wani uba da zai ƙyamaci ƴarsa kan laifi da baya da tabbaci,tasan da ace shiɗin mahaifinta ne bazai ƙyamaceta ba ko da kuwa abunda yake zargi gaskiya ne,shawara ta yanke anya baza tayi nesa dashi ba ko hakan zai sa ya yafe mata, sosai tayi nisa a duniyar tunani. maganar Balqis ce ta dawo da ita cikin hayyacinta “Aunty Laatifa lafiya dai, tun ɗazu nake jiranki fatan dai lafiya” da sauri tayi mata gyran murya, jinjina kai Balqis ɗin tayi tana komawa mazauninta ta zauna,shaf shaf Laatifa ta watsa ruwa ta fito ɗaure da towel, murmushi Balqis ɗin ta sakar mata “inata jiranki” “gani ai na fito, akwai labari ne?” Laatifa ta faɗa tana nufar dressing mirrow. yanyin fuskar Balqis ne ya canza zuwa damuwa “dady ne wai dole sai a G J I hospital zai sama man aiki ni kuma na fi son S J I” “to ni yanzu mi ki ke so nace, kawai kiyi haƙuri da in da yake son kiyi” “haba Aunty Laatifa nazo wajenki dan ki bani shawara amma shine za kice haka?” “to Balqis ya ki ke so nace kin dai san yanda nake da dady bare naje na roƙar maki shi, kawai kiyi haƙuri kiyi mashi biyayya” “na san da haka,amma ai sai ki bani shawara” “to wace shawara zan baki bayan wacce na baki?” Laatifa ta faɗa lokacin da take neman wurin zama kusa da Balqis ɗin ta zauna harta shirya cikin doguwar riga mai hannun Armless. gyara zama Balqis ɗin tayi “kina ganin idan na sanar da big dady bazai sa dady ya amince ba?” “too! ki gwada ki gani wataƙil ya amince” “ni bana so naga baki bani ƙwarin gwiwa, so nake naji kince zai amince” “to shikenan zai amince” dariya Balqis ɗin ta saki “yawwa haka nake son naji kince” murmushi Laatifa ta sakar mata. “yawwa Aunty Laatifa dama ina ta so na...” ringing ɗin tab ɗin Laatifa ne ya dakatar da ita, da sauri ta buɗe briefcase ɗin Laatifa ta ta ciro tab ɗin, jiki na rawa ta miƙa mata, amsa Laatifa tayi, murmushi ne ya bayyana akan fuskarta lokacin da tayi arba da sunan mai kiran nata, da sauri Balqis ta matso tana leƙen wayar,da tsantsar mamaki ta kalli Laatifa, ɗan tahalikin da kullum sai tayi maganar shi, yanzu haka maganar shi take shirin yima Laatifa sai ga kiran shi. Wani irin annurin farin ciki ne ya bayya akan fuskar Balqis yau dai ga abunda ta daɗe tana jira picking call ɗin Laatifa tayi, sai da tayi picking call ɗin tukun ta fahimci video call ne, amma tayi mamakin ganin duhu babu haske,ƴan dube dube ta shiga yi a wayar tana faɗin “Balqis bani glass ɗina” da sauri Balqis ta buɗe briefcase ɗin tana miƙo mata glass ɗin,gyaran murya a kayi mata daga cikin wayar, da sauri takai dubanta ga wayar still duhu ta gani,wata irin zazzaƙar muryar ce ta daki dodon kunan su, in low voice aka furta “LAATIFA” da sauri Balqis ta leƙa wayar amma sai taga babu kowa, murmushi Laatifa ta saki “yau kuma ni ka ke ɓoye ma fuskarka SAM” “ya ki ke?”shine kawai abunda aka furta mata maimakon bata amsar tambayar da tayi “ina lafiya SAM, kwana biyu bana jinka, har saƙo na tura maka namayi tunanin baka gani ba?” “i saw it already,ayyuka ne su kayi man yawa” Balqis sai sakin murmushi take, tama rasa inda zata sa kanta dan daɗi. “ayyah,ya aikin?” “Alhmdllh” ya faɗa “masha Allah,ya su Uncle da su ALYAR?” “suna lafiya” shiru ne ya gitta tsakanin su, gyaran murya yayi mata “lafiya ki ke dai,yana yinki kamar baki cikin walwala” murmushi ta saki tana faɗin “lafiya lau nake” “ban yarda ba Laatifa, yanayin fuskarki ya nuna kamar kina cikin damuwa, tell me who touch u?” ya faɗa cike da tsantsar kulawa, wani irin sanyi taji a ranta tana matuƙar son yanda SAM ke nuna mata kulawa duk da basa tare,Balqis wani daɗi ne ya rufeta duk da ba ita ya nunama kulawa ba tana dai fatan ta samu kulawarshi fiye da yayarta. “kinyi shiru, mike damunki?” saurin sakar mashi murmushi tayi “babu komai SAM lafiya lau nake,ban jima da dawowa daga wurin aiki bane,duk a gajiye nake” “ok, idan ma akwai abunda ke damunki kiyi gaggawar sanar dani” “in sha Allah, nagode sosai da kulawarka a gare ni” shiru taji bai tanka mata ba dama ta san ba tanka mata zaiyi ba. SAM na matuƙar kula da ita, a duniya babu wanda take samun kwanciyar hankali da natsuwa gareshi irin SAM,duk damuwar da take ciki data sanar dashi zaiyi mata maganinta,ko momy bata bata irin kulawar da SAM ke bata duk da suna jimawa ba suyi waya ba,amma kullum ne akwai masu sanar dashi halin da take ciki musamman yasa masu bibiyar mashi rayuwarta, akwai kyakyawar alƙa a tsakanin su, tun suna yara Allah ya haɗa jininsu kaf yaran family babu wacce yake kulawa kamar Laatifa in fact ma ita kaɗai yake kulawa tana da wani matsayi a zuciyar shi,wani ɓangare na zuciyarta tunzurata take akan ta sanar dashi abunda ke faruwa tsakaninta da dady ta san zai sama mata mafita. ganin tayi shiru ne yasashi yi mata gyran murya, da sauri ta kalli wayar “lafiya?” ya faɗa “lafiya lau” ta faɗa tana karkata wayar zuwa fuskar Balqis dake wani noƙewa a bayanta,fuskarta ɗauke da murmushi tace “SAM ka gane wacece wannan?” saurin sadda kai ƙasa Balqis tayi, wata irin kunyarshi take ji duk da bawai ganinshi za tayi ba, a hankali ta gaishe shi “who is she” shine kawai abuda yace,yanayin fuskar Balqis ne ya canza tuni hawaye sun cika idanunta, yanzu duk yanda take dakon sonshi amma tashi ɗaya yace bai ganeta ba. “Balqis ce fa ƙanwata, kana nufin ka mantata?” Laatifa ta faɗa “i don know her,bye take care” yana faɗa yayi rejecting kiran, da sauri Balqis ta kifa kanta saman mattress, murmushi Laatifa ta saki tana dafa bayanta, kamar jira take Laatifa ta taɓata ta fashe da kuka, hankali a tashe Laatifa ta ɗago da ita “Balqis lafiya ki ke kuka?” kuka sosai take kamar ƙaramar yarinya, lallashinta Laatifa ta shiga yi harta samu tayi shiru “haba Balqis miye abun kuka a nan?” “dole nayi kuka Aunty Laatifa, yanzu duk tsawan shekarun dana ɗauka ina sonshi amma yace bai sanni ba, taya ma zaice bai sanni ba bayan ni shaidace akan ya sanni”ta faɗa cike da takaici “kiyi haƙuri abun babu daɗi,amma ta yiwu ya mantaki ne shiyyasa ya faɗi haka” “amma Aunty Laatifa ya tsaya kiyi mashi bayani mana, amma kawai yayi rejecting saboda ko kallona baya sonyi” “ba haka bane Balqis, kiyi mashi uzuri tsawan shekara nawa baya ƙasar ya isa ya manta da kowa tunda ba waya yake da ku ba,dan yayi rejecting ba wai dan saboda ke bane haka yake baya da son yawan magana ne, ko ni idan muna waya ya gaji da magana rejecting yake,kiyi haƙuri kinji” lallashinta sosai Laatifa tayi har ta samu ta kwantar da hankalinta. *Queen Kainart💫* Noor tunda ta shige bedroom ɗin Kainart bata sake fitowa har yamma tayi gashi har lokacin Irfan bai zo ba baikuma kirata ba. Su Yumnah na parlorn tare da mom maryam fira su ke hankali kwance, mom maryam ba ƙaramin nishaɗi tasa su ba. Uncle Mustafa ne ya shigo,Army trouser ne a jikinshi tare da farar shirt, da gudu su Ammar su ka nufe shi, saurin buɗe masu hannayen shi yayi yana sakin murmushi, ai kuwa gaba ɗayan su suka faɗa jikinshi,hugging ɗin su yayi cike da farin cikin ganinsu. raba jikinsu yayi yana faɗin “yaushe ku ka zo gidan?” “tun ɗazu, har munata jiranka” ɗan zaro ido yayi “amma shine ba'a faɗa man ba, da na san zaku zo ai da ban fita ba” ya faɗa yana jan hannusu zuwa cikin parlorn. “sai da nace Aunty Yumnah ta kiraka amma taƙi” “kai Jamal bana son sharri yaushe ku ka ce na kira maku shi iye??” da sauri jamal ya ɓoye bayan uncle Mustafa,dariya su ka saki gaba ɗaya parlorn ganin yanda Yumnah ta haƙiƙance da kuma Jamal ɗin daya ɓoye bayan Uncle Mustafa. “Aunty Yumnah kinyi laifi kuma dole na hukuntaki” “wallahi ƙarya yake man dady, ni baice na kira ka ba” ta faɗa kamar zata fashe da kuka,murmushi mom maryam tayi “rabu da su kinji kowa ya san ƙarya suke” “sai na hukuntata dole” Uncle Mustafa ya faɗa,turo baki Yumnah tayi tana dallama su Ammar harara “in wuni dady” Nainarh ta gaishe dashi cike da girmamawa “lafiya lau, ya gida” “Alhmdllh” gaishe dashi Yumnah tayi, cike da kulawa ya amsa mata. up stairs ya nufa bin bayan shi mom maryam tayi,da gudu su Ammar su ka bi bayansu dan sun san sai Yumnah taci mutuncin su saboda sharrin da Jamal yayi mata. sun jima zaune a parlorn su kaɗai, tunda su mom maryam suka nufi sama ba su sake saukowa ba,fara kiran sallar magrib da akayi ne ya sa su ka tashi su ka nufi bedroom ɗin Kainart, a kwance su ka samu Noor har bacci yayi awan gaba da ita. tashinta Yumnah tayi akan tayi sallah amma fir taƙi tashi da Yumnah ta dameta ma rufeta tayi da masifa akan ta ƙyaleta ita ba yanzu za tayi ba “ke ki ka sani sai kita kwanciya idan Alkairi ce” bathroom ɗin ɗakin su ka shiga su kayi alwala,Yumnah ta ɗauko masu carpet haɗe da hijab cikin wardrobe. shimfiɗa masu tayi su kayi sallah, basu tashi kan sallayar ba sai da su kayi harda isha tukun, har time ɗin Noor bata tashi ba, babu ma alamun zata tashin. duka Yumnah ta kaimata a bayanta “yanzu ai sai ki tashi mu tafi gida, idan kuma anan zaki kwana naji, wallahi kin dai san halin Mom maryam” tashi tayi tana wani hararar Yumnah,murmushi Yumnah ta sakar mata “ai da kin kwanta” tsaki taja tana nufar ƙofar fita “uncle dai na nan idan kuma haka zaki fita tom” dawowa tayi ta buɗe wardrobe ɗin hijab ta ɗauka har ƙasa tukun su ka fice. A parlor su ka samu Uncle Mustafa tareda su Aman sai zuba mashi surutu su ke,gaishe da shi Noor tayi da kulawa ya amsa mata, bedroom ɗin mom maryam su ka nufa zaune su ka sameta saman sallaya tana lazimi. “ban gane ba, na ganku tsaye?” “tafiya za muyi mom dare yayi” “sai ku jira kuyi dinner tukun” “A'a mom idan muje gida za muyi” “ke zanci mutuncinki Yumnah, sai kace wasu baƙi, ku wuce gani nan zuwa” ba dan sun so ba suka koma parlorn. sai bayanda su ka yi dinner tukun su kayi masu sallama, har parking space mom da Uncle Mustafa suka rakasu. “yaushe ni zaku zo man weekend kenan” a cewar Uncle Mustafa, Aman ne ya bashi amsa da “sai next weekend” “Allah ya kaimu, zan jiraci zuwanku kuwa” haɗa baki su kayi wajen furta sai munzo, murmushi su ka saki, ƴar madaidaiciyar jaka mom maryam ta miƙama Yumnah. “sai da safenku, ku gaishe mana da mutanen gidan” “za suji in sha Allah mom” ba su koma ciki ba har saida su kaga tafiyar su tukun. Yumnah harta kama hanyar gidan Uncle mutallaf Noor tayi saurin cemata gidan big dady zata kwana, hakan yasa Yumnah kama hanyar gidan su, tun a mota Noor ta kira momynta ta sanar da ita nan zata kwana, babu yanda mom fatilah ba tayi ba ta dawo gida amma taƙi bakomai yasa bata son Noor ta kwana gidan ba sai dan saboda ta san part ɗin Mom zata kwana gashi kwata kwata basu jituwa da Mom. Motar Yumnah na shiga harabar gidan Motar fa'iz na shigowa, kusan a tare su kayi parking,yazdan ne ya fara fitowa sai Fa'iz, jeans da t_shirt ne a jikinsu, yau babu laifi anyi shigar kirki saidai a buge su ke kamar koda yaushe,har wani gaba suke suna baya kamar zasu kifa ƙasa. tunda suka fito su ka kafe motar Yumnah da ido har suka fito, tsaki Yazdan yaja yana faɗin “ca nake baƙi akayi ashe wannan tsamayen ne” harara Noor ta watsa masu haɗi da murguɗa masu baki “kaiii ashe yau zan daka wata yarinya, ke dama kin rainani ko?” A cewar Yazdan yana yo kan Noor ɗin kamar zai faɗi dama sun saba kusan kullum ne sai mom Fatilah ta rabasu, muddin su ka zo ƙasar basu barinta sakat kamar mage da ɓera haka su ke, sauƙi ma ɗaya Yazdan baya binsu shi yana Nigeria. riƙo hannunshi Fa'iz yayi “ kai dalla rabu da ita, daga ina kuke haka?” Yumnah ta bashi amsa da “daga gidan Uncle Mustafa” “soja marmari daga nesa ba” Yazdan ya faɗa yana saluting Fa'iz,kwashewa su kayi da dariya kamar wasu taɓaɓɓu. su Jamal tunda su ka fito daga mota su kaga su Fa'iz su kayi saurin ɓoyewa bayan Nainarh, bala'in tsoron Fa'iz da Yazdan su ke,Nainarh itama hankalinta a tashe yake dan bata san haka su ke ba ko jiya a gidan Abbah lafiya lau ta gansu. “kaiii wa kuke ɓoyemawa” Yazdan ya faɗa yana leƙen su Ammar daketa faman zare ido, yana layi ya nufo inda Nainarh take, wani irin duka gaban Nainarh yayi su Jamal kuwa yana ƙarasowa su ka fashe da kuka suna barin bayan Nainarh su ka nufi main entrance ɗin shiga gidan da gudu. “kaga ƴan iskan yara” Yazdan ya faɗa yana riƙe baki,da sauri Fa'iz ya nufo inda suke, wani ɗan iskan kallon ya shiga watsama Nainarh,kamar za su faɗo mata shida Yazdan aikuwa jikinta ya hau rawa ga hawaye da su ka cika idonta “mutum ko Aljana?” Fa'iz ya faɗa yana nunata da yatsa, Yumnah ce tayi saurin ce mashi “ƙawata fa ce ya Fa'iz” “ƙawarki, ina ki ka samu wannan kayan??” rai a ɓace Noor tace “haba dan Allah ya Fa'iz, duk kunbi kun tsoratata,ƙawar Yumnah ce fa” ta faɗa tana jan hannun Nainarh “yi haƙuri kinj, muje ko” da sauri Yazdan yabi bayan su “ke kin raina mutane ko?” saurin riƙo hannunshi Fa'iz yayi, tsaki taja tana jan hannun Nainarh suka shige gidan. jakar da Mom maryam ta basu Yumnah ta ɗauka, bayan su tabi, part ɗin dady ta fara shiga ta sanar dashi sun dawo tukun ta fice, a bedroom ɗin mom ta samu su Noor su Jamal sun lafe a jikin mom,jakar dake hannunta ta ajiye haɗe da mayafinta. “mom maryam na gaishe da ke” “ina amsawa, kun barosu lafiya?” “lafiya lau” Yumnah ta faɗa tana buɗe jakar data shigo da ita, chocolate ne kala kala haɗe da wasu expensive perfume masu daɗin ƙamshi, da sauri su Aman su ka nufota, saurin rufe jakar tayi. “kun tsaya na baku ko” turo baki su kayi “to ba namu bane?” “ko naku ne kunsan dai bazan tasa maku su gaba ba ku shanye su yanzu” ɓata fuska su kayi kamar za suyi kuka. ɗiba tayi ta basu sannan ta rufe jakar “wannan sai gobe” ta faɗa tana ɗaukar mayafinta da jakar “kuzo muje ayi shirin bacci, mom sai da safe” “a tashi lafiya” mom ta faɗa, ficewa su kayi daga ɗakin su duka, bedroom ɗin da suka koma tunda su Ammar su ka zo su ka nufa Noor kuma ta nufi na Yumnah. tana shiga bedroom ɗin kayan jikinta ta rage ta faɗa toilet,bayan kamar 10 minute ta fito ɗaure da towel, dressing room ɗin Yumnah ta nufa, body lotion ta shafama jikinta haɗe da perfume, wardrobe ta nufa, ɓangaren PJ ɗinta ta buɗe,ƴar baby doll ta ɗauka sabuwa pink color mai haɗe da top. rigar ta zura haɗe da top ɗin sai dai bata ɗaure igiyoyin ba, gaban rigar net ne sharara ana hangen jikinta,ribbon tasa ta ɗaure gashinta perfume ta sake fesama jikinta kafin ta fice, bedroom ɗin ta koma, kwanciyarta tayi ba tare da ta kashe bulbs ɗin ɗakin ba. Parking Motar su suka yi a parking space ɗin gidan big dady, Waseef ne ya fito sanye da cargo pant haɗe da shirt yasa p_cap haɗe shade, Irfan ne ya fito daga driver seat,suit ne a jikinshi black color idanunshi a manne da baƙin shade. ciki gidan su ka nufa, part ɗin dady su ka nufa, a bedroom ɗin shi suka sameshi har yayi shirin kwanciya mamy na daga gefen bed ɗinshi zaune har ta gama fushin, PJ ne a jikinta riga da wando,cikin girmamawa su ka gaishe da su, da kulawa su ka amsa masu har mamy na tambayar ya mutanen gidan, da lafiya lau su ka amsa mata. “daga ina kuke a cikin daren nan” dady ya faɗa, Waseef ne ya bashi amsa da “dinner bikin abokin mu” “dinner yanzu?” “eh dady” “shikenan sai kun dawo, amma dan Allah ku kula kundaiga yanzu yanda zamani ya canza da mata da samari sun haɗu sai shashanci, dan Allah ku kula” “In sha Allah dady, sai da safe” “dare naƙarayi ku dawo, dan ma kun shirya ne yasa zan barku ku tafi” “in sha Allah dady bazamu jimaba” “shikenan sai kun dawo” sallama su ka yi mashi su ka fice. bedroom ɗin mom su ka nufa harta kwanta,faɗa sosai tayi masu kamar wasu ƙananun yara kan mi za su fita yanzu cikin dare, haƙuri kawai su ka bata su ka fice,a bakin ƙofar bedroom ɗinta su ka rabu Irfan ya nufi ɗakin Yumnah saboda Noor tace mashi tana nan,parking space Waseef ya koma “kayi sauri fa kaga dare nayi” ok kawai Irfan ɗin yace mashi. bakin ƙofar bedroom ɗin ya tsaya yana nocking amma shiru ba'a amsa mashi ba, gajiya yayi da nocking ɗin ya tura ƙofar ɗakin ya shiga, a kwance ya hangota saman bed ɗin idanunta a rufe tana jan numfashi a hankali alamar bacci. ƙarasawa yayi bakin bed ɗin,kallon fuskarta yayi, baccinta take hankali kwance, murmushi ya saki yana shafa gefen fuskarta, motsi tayi kamar zata farka hankan da tayi ba ƙaramin tafiya yayi dashi ba, ya san da idonta biyu daya bani da ƙorafi. a hankali ya duƙa yayi kissing forehead ɗinta ai kuwa ta buɗe ido dama idonta biyu kawai tayi kamar tana bacci ne ko nocking ɗin da yayi tana ji, sauri tashi yayi tsaye “dama ba bacci ki ke ba?” “eh, ya Irfan wai mi nayi maka ka ke gudu na wannan time ɗin, ko dai bakayi farincikin zuwana bane??” ta faɗa a shagwaɓe “nayi farincikin zuwanki mana” “to mi yasa kake guduna” ta faɗa tana sauka daga saman bed ɗin ta nufo in da yake,faɗawa tayi jikinshi tayi hugging ɗin shi “ko nayi maka wani laifi ne?” shafa bayanta ya shiga yi a hankali “ba kiyi man laifin komai ba Noor, kawai wani uzuri ne ya riƙe ni” “amma ai ba haka kake man ba duk muka zo, kofa zaman one hour ba muyi ba, a da da kake ɓata kowane lokacinka a tare da ni” tana a kwance saman ƙirjinshi take faɗar haka,cike da salon bariki take manna mashi ƙirjinta a nashi,hakan da take mashi ba ƙaramin jefashi a yanyi take ba,ɗago da kanta yayi yana kallon kyakyawar fuskarta,turo baki tayi kamar zata fashe mashi da kuka. “kasan yanda nake ji kuwa saboda guduna da kake?” bai bata amsar tambayar da tayi mashi ba sai manne bakinsu da yayi waje ɗaya, ai kuwa da sauri ta kama tongue ɗinsa tana kissing dama abunda take so kenan,wasu irin hot kisses su ka shiga bama juna kamar za su haɗiye juna, cikin ƙanƙanin lokaci suka fita a hayycin su suna a wannan yanayin ne Nainarh ta faɗo ɗakin, Yumnah tace ta zo nan su kwanta kar a bar Noor ita ka ɗai. wani irin mummunan faɗuwa gabanta yayi da sauri ta juya masu baya gabanta na wani irin duka kamar zai faɗo ƙasa, da sauri Noor ta tureshi tana faɗin Nainarh! , saurin kai duban shi yayi gareta,da gudu ta fice daga ɗakin... ______________________________ wani irin mummunan faɗuwa gabanta yayi da sauri ta juya masu baya gabanta na wani irin duka kamar zai faɗo ƙasa, da sauri Noor ta tureshi tana faɗin Nainarh! , saurin kai duban shi yayi gareta,da gudu ta fice daga ɗakin. A jiyar zuciya suka shiga saukewa kamar wanda su kayi tseren gudu “amma ba kince man ke kaɗai bace?” Irfan ya faɗa “eh, ban san ya a kayi ta zo ba” juyawa yayi ya nufi ƙofar fita,saurin kamo Arm ɗinshi tayi “when zaka dawo,saboda kaifa zan kwana?” “zuwa safe” ya bata amsa yana wani lumshe ido,gaba ɗaya jinshi yake a wani irin yanayi na daban ƙafarshi ma da ƙyar yake ɗagata “shikenan saika dawo ka kula man da kanka” jinjina mata kai yayi ya fice daga ɗakin. Ajiyar zuciya ta sauke tana kama igiyoyin rigarta ta ɗaure,switch ɗin ɗakin ta nufa ta kashe bulbs ɗin bedside lamps su ka kawo, kwanciya tayi saman bed ɗin,lumshe idanunta tayi tana jan iska haɗe da fesarwa,wani irin yanayi take ji a jikinta, kwata kwata ba taji kunyar ganinsu da Nainarh tayi ba sai ma haushin katse masu jindaɗi da tayi, tsaki taja tana gyara kwanciyarta. Nainarh tana fita daga ɗakin da gudu parlor ta nufa tasan muddin ta koma bedroom ɗin da Yumnah take dole taji ba'asin abunda ya dawo da ita koma ta nufi ɗakin dan ganema idonta, a jikin pillar ta samu ta ɓuya, ajiyar zuciya ta sauke tunda take a rayuwarta bata taɓa jin haushin wani ɗan Adam ba kamar yanda take jin haushin Irfan da Noor a yanzu, ko wace irin taɓewace ta samesu haka,idan sun san suna son junansu danmi bazasu sanar da iyayen su suyi masu Aure ba amma zasu ɓige da neman juna ta ƙazamar hanya, ko basu san hakan babban zunibi bane, duk da take kallonshi daban da ƴaƴan mom batayi tunanin haka halayenshi su ke ba,a ido kamar mutumin kirki ko kunya basa ji yanzu da Yumnah ce ta shigo ta samesu da wane ido su ke tunanin zata kallesu. wani irin tausayin mom da dady ne ya rufeta,mutanen kirki amma ƴaƴansu ke aikata laifuka irin haka,dady yafi bata tausayi ga Irfan ga Fa'iz mutumin ƙwarai mai riƙo da addini Allah ya jarabceshi da ƴaƴa haka, dama Allah baya barin bawansa haka ba tare da ya jarabashi ba ta hanya daban daban , ita kaɗai take sambatunta babu mai bata amsa. tana a nan tsaye Irfan ɗin ya fito sai ƴan waige waige yake, harara ta watsa mashi kamar idanunta zasu faɗo ƙasa wani irin tsanarshi take ji a ranta,saida taga ficewarshi daga gidan tukun ta nufi bedroom ɗin ko ta kan Noor dake kwance bata biba ta juya mata baya itama Noor ɗin yi tayi kamar tana bacci. A cikin mota ya samu Waseef har ya gaji da zaman jiranshi, yana isowa driver seat ya buɗe ya shiga kifa kanshi yayi, tunda yake a rayuwa bai taɓa jin kunyar dayaji ba yau, bai taɓa tunanin ko Yumnah ce ta ganshi zaiji irin wannan kunyar da yaji dalili ganin da Nainarh tayi masu, yayi fatan ace bata shigo ɗakin ba,damuwarshi yanzu da abun zata riƙa kallonshi za tayi mashi kallon mara kamun kai koma ta sanar da wani mussaman Yumnah. dafa kafaɗarshi Waseef yayi “lafiya dai?” ya tambaya “babu komai” shine kawai abun da Irfan ɗin yace mashi “Irfan indai irin wannan haɗuwar da kuke zata zama matsala mi yasa bazaka sanar da dady ba kana sonta,sai suyi maku Aure,bana son ku ƙetara in da bai kamataba, dan muddin ku ka cigaba a haka wata rana sai kunyi dakun sani mara amfani” “bazan iya sanarda dady ba Waseef” Irfan ɗin ya faɗa ba tare da ya ɗago da kanshi ba “bangane bazaka iya faɗa mashi ba, kana nufin ba sonta kake ba??” “ina sonta mana Waseef, kawai dai bazan iya sanar da dady ba, lokuta da dama ko nayi niyyar sanar da wani a cikin su kasawa nake sai duk na rasa ƙwarin gwiwata” “na fahimci sanar dasu ke baka wahala, ni ka bani dama na sanar da dady ko big dady nasan za suyi farin ciki da hakan” “karka sanar da su nafi son suji a baki na” “tayaya kenan?” “zan sanar da su in sha Allah” “shikenan, amma dai karka ja jiki” jin jina mashi kai Irfan ɗin yayi “please kayi driving ɗin mu” Irfan ɗin ya faɗa yana ficewa daga motar, driver seat Waseef ya dawo shi kuma ya koma mazaunin shi dan a yarda yake jinshi zai iya watsar da su a titi, ba Noor bace damuwarshi Nainarh ce damuwarshi bai taɓa jin kunyar wani a rayuwarshi ba kamar yanda yake jin ta Nainarh yanzu,key Waseef yayi ma motar su ka fice daga estate ɗin baki ɗaya. Heart of vegas su ka nufa saɓanin wurin dinner da su ka cema dady za su sun faɗin haka ne kawai dan su kare kansu,parking Waseef yayi,kusan a tare su ka fito shida Irfan ɗin su ka shiga ciki , a cike yake kamar kullum,third floor na club ɗin su ka nufa, wani irin ƙaton meeting room dake kusa da office ɗin Irfan su ka shiga,zungureren table ne mai ɗauke da chairs,manyan mutane ne su shidda a zaune a saman chairs ɗin zaman jiran Irfan ɗin kawai su ke, an cika masu gabansu da kayan sha kalar nasu na club, chair dake kallon duka chairs ɗin Irfan ya nufa ya zauna, Waseef ya zauna ata kusa dashi, system ɗin dake ajiye kan table ɗin ya buɗe haɗe da ɗaukar communicative device, yasa a kunnenshi. gabatar da meeting suka shiga,cike da natsuwa Irfan yake gudanar da komai duk da baya da gogewa akan abun sai dai mubarak na taimaka mashi ta hanyar Bluetooth,sun shafe kusan Awa biyu a ɗakin meeting ɗin kafin su ka kammala around 2am *WASHE GARI* Ana kiran sallar farko ta farka hakan al'adarta ce tun tana gidan su, kallon Noor dake kusa da ita tayi, baccinta take hankali kwance, sauka tayi daga saman bed ɗin ta nufi bathroom, Alwala ta ɗauro, bakin bed ɗin ta dawo tashin Noor ta shiga yi, nauyin bacci gareta da ƙyar ta samu ta farka. “ki tashi lokacin sallah yayi” ya mutse fuska Noor ɗin tayi tana juya kwanciyarta “ki sani wannan baccin bashi da amfani,idan kin kammala sallah kina iya dawowa ki cigaba da baccinki” “kiyi taki kawai zanyi” Noor ɗin ta faɗa, gyaɗa kai kawai Nainarh tayi, dressing room ɗin Yumnah ta nufa, kayan jikinta ta canza zuwa doguwar riga,bedroom ɗin ta dawo hannunta ɗauke da hijab da carpet, shimfiɗa carpet ɗin tayi, hijab ta zura a jikinta ta kabbar sallah, harta kammala raka'atanil fijir tayi sallah ta zauna tana azkar Noor bata tashi ba, mamakin momy Noor ne ya kamata, wace irin uwace ita da har ƴarta ke wasa da Sallah irin haka bata tsawatar mata ba, ta san da ace mahaifiyarta na kula da tarbiyarta da duk hakan bai faru ba a ganinta sakacin mahaifiyarta ne ba laifin Noor ɗin, Allah sarki ita lokacin da tana tare da iyayenta kullum mahaifinta sai ya tabbatar da ta tashi domin yin sallah yake nufar masallaci hakama mahaifiyarta bata yin sallah sai ta tabbatar da taga tashinta tayi Alwala tukun take komawa nata ɗakin tayi sallah. wata irin kewar iyayenta ce ta kamata musamman mahaifinta a irin wannan lokacin tana part ɗin shi yana ɗora mata karatu, duk asubar duniya sai ya zaunar da ita ya bibiyi karatunta na islamiya ya koya mata abunda bata gane ba, rayuwa kenan yanzu bata da wanda zaiyi mata hakan kowane farin ciki na rayuwarta ya tarwatse. saurin ɗago da kanta tayi dalilin dafa kafaɗarta da aka yi, Yumnah ta gani tsaye a gefenta “lafiya ki ka zuba uban tagumi da asubar fari?” ƙaƙalo murmushi tayi “ba komai” gyaɗa kai Yumnah tayi tana nufar dressing room ɗinta “sister Yumnah ina ta so na tambaye ki?” Nainarh ta faɗa, juyowa Yumnah tayi tana fuskantar ta “ina jinki?” “wai babu islamiya ne a Estate ɗin nan?” “akwai mana,kina so ne?” “eh, amma mi yasa ke baki zuwa” ɗan ya mutse fuska yumnah tayi “da ina zuwa na bari” “saboda mi?” “haka nan kawai” “ya kamata ace kina zuwa, shifa karatun addini ba'a gamashi” “zan koma amma sai idan da ke” “karki damu,da zan samu ma wanda zai koyaman harda asuba ina so” “in dai kina so zanyi ma dady magana, da yana koyaman na bar zuwa” “ina so kuwa” “shikenan idan munje gaishe shi sai nayi mashi magana” “nagode sosai” murmushi Yumnah tayi mata tana shigewa dressing room ɗin. Sai da gari yayi haske sosai tukun su ka nufi part ɗin dady a zaune su ka same shi a parlor saman rug carpet,hannunshi riƙe da Qur'an yana karatu kamar kullum, zama su kayi har ya kammala, gaishe da shi su ka yi cike da kulawa ya amsa masu. “dady dama Nainarh ke son zaka riƙa biya mata karatu da asuba” Yumnah ta faɗa, kallon Nainarh dady yayi fuskar shi a ɗan ɗaure “shine ba zaki iya tambayata ba har sai kin sa Yumnah?” duk sai taji kunya “A'a dady, kayi haƙuri” “gaskiya banji daɗi ba nima mahaifinki ne zaki iya tambayata duk abunda ki ke so” “kayi haƙuri” “karki damu,duk lokacin da ki ka kammala sallah ki zo zan koya maki gwargwadon abunda na sani” “in sha Allah dady, nagode” kallon Yumnah yayi “Auta yanzu ko kunya ba kiji ba?” saurin sadda kai ƙasa tayi tana susar kai “ai harda ni ba ita kaɗai ba” girgiza kai kawai dady yayi, sallama su ka yi mashi su ka fice. tunda su Nainarh su ka shigo Mamy take laɓe tana sauraronsu,wani irin haushin Nainarh ne ya sake kamata,ji tayi kamar ta fito ta shaƙi wuyanta gani take kamar neman samun gindin zama ne da neman shiga wurin dadyn yasa ta ƙirƙiro da wai tana son dady ya koya mata karatu. tsaki taja tana fitowa parlorn, ko kallon in da dady yake ba tayi ba ta fice. *A fter some days* Nainarh tun ranar da su ka yima dady magana kullum da asuba sai sunje ya ƙara masu karatu ita da Yumnah,islamiya ce kawai basu fara zuwaba sun bari sai wani weekend ɗin saboda school,Noor da su Ammar tun washe garin ranar su ka koma gida,Nainarh da Yumnah ne su ka maida su Ammar gida harda Jamal. *UNITED STATE* _*Las Vegas (Nevada)*_ A zaune suke a saman wasu haɗaɗɗun chairs dake katafaren garden ɗin gidan,Nailarh ta miƙe ƙafafunta saman ɗan madaidaicin table yayinda system ɗinta ke ajiye saman laps ɗinta tana operating fuskarta ɗauke da murmushi,hot pant ne a jikinta haɗe da ƴar shirt da bata wuce cibiyarta ba, Aunty sophia na daga gefenta zaune hannunta riƙe da mug ɗin coffee. kallon fuskar Nailarh dake ɗauke da murmushi Aunty sophia tayi da alama ba ƙaramin nishaɗi take samu a tattare da system ɗin ba “da alama yau kina cikin farin ciki,ko zan iya sanin abunda yayi dalilin sa wannan kyakyawar fuskar taki farin ciki?” Aunty sophia ta faɗa ƴar dariya ta saki tana ɗaukar mug ɗin coffee dake ajiye kan table ɗin,sai data ɗan kurɓa tukun takai dubanta ga Aunty sophia “ba komai yayi silar shigata wannnan farin cikin ba sai wasan da zamu gabatar a N R T ranar sunday, na samu ƙarin ƴan wasa daga California,abunda yayi matuƙar burgeni da ƴan wasan, details ɗin dawakan su da su ka turo, ji da kansu yayi matuƙar ƙyatar dani, a tunanin su canza tarihin N R T abu ne mai sauƙi sai dai basu san samun dokin da zaifi KING zimma da karsashi abu ne mai matuƙar wahala” ta faɗa cike da alfahari Murmushi Aunty sophia ta saki tana ajiye mug ɗin coffee dake hannunta “baby na lura kina matuƙar ji da kanki kema,karki manta ba kullum mutum ke nasara ba,anyi gwaraza tun talataini kuma sun shuɗe,duk yanda ki ke ji da kanki akwai wanda ya fiki kuma dole a samu wani wanda zai karya tarihin N R T, kullum ke ke hawa akan mutane kema dole a samu wani wanda zai zama sama da ke” wani irin kallo Nailarh ta jefa mata “Aunty sophia mi yasa ki ke faɗa man haka,kina baƙin ciki da nasarar da nake samu ne?” saurin girgiza mata kai Aunty sophia tayi “ba haka bane baby,kawai ina son kisan cewa a rayuwa ba kullum mutum ke samun abunda yake so ba” “please ki daina faɗa man haka raina ɓaci zaiyi” “sorry ban faɗa maki haka dan ranki ya ɓaci ba,ina maki fatan nasara kamar ko da yaushe” murmushi Nailarh ta saki “ko ke fa,da za ki ɓata man farin cikin da nake ciki,a round 5 pm jirgin momy zaiyi landing a airport” yanayi fuskar Aunty sophia ne ya canza zuwa tsantsar damuwa,ba dawowar mahaifiyarta ta bane bata so ba, yana yin da take jefa Nailarh ne bata so “ya dai Aunty sophia” Nailarh ta faɗa ganin yanyin da Aunty sophia ta shiga “ban manta ba,yanzu nake shirin tashi na duba chefs, kema ya kamata ki ajiye aikin nan ki shirya dan kije airport ɗaukota” “yanzu zan kammala” “ok,bari na shiga ciki” Aunty sophia ta faɗa tana ɗaukar mug ɗin coffee da take sha ta nufi cikin gidan,direct kitchen ta nufa chefs ɗin ta fara dubawa har sun kusa kammala aikin dinner da suke,ficewa tayi daga kitchen ɗin ta nufi part ɗinta dake kusa dana ma'aikatan gidan,a corridor ta tsaya,wayarta ta zaro daga cikin Aljihun rigar dake jikinta. dialing wata number tayi,kiran har ya katse ba'ayi picking ba,maida wayar tayi cikin Aljihun rigarta ta koma kitchen. Nailarh tana kammala aikin da take part ɗinta ta nufa shaf shaf masu aikinta su ka shiga shiryata ko sanda Aunty sophia ta shigo ɗakin har ta kammala shirinta wani kallo Nailarh tayima Aunty sophia “dama ba tare dake zamu je ba?” “eh Nailarh sai kun dawo” taɓe baki Nailarh tayi tana ɗaga kafaɗarta, ficewa su kayi daga ɗakin har compound Aunty sophia ta rakata sai da taga ficewarsu daga gidan tukun ta koma ciki. Masu aikin ta fara dubawa saida ta tabbatar komai na tafiya yanda ya kamata kafin ta wuce part ɗinta, a bakin corridorn ɗazu ta tsaya number ɗazu ta sake dialing yanzu ma har kiran ya katse ba'ayi picking ba yanke shawarar turama number saƙo tayi, a hanzarce ta shiga typing message, da harshen Spanish take rubutun hakan yasa ban san abunda take rubutawa ba,tana tura message ɗin tayi saurin maida wayar Aljihun jin alamar kamar mutum a bayanta, saurin kai dubanta tayi bayanta. ganin ba kowa ne yasata sauke ajiyar zuciya ƙofar part ɗinta ta buɗe ta shiga ina saurin na shiga dan na gane mana nida ku masu karatu amma tayi saurin murza key dan dole na tsaya a bakin ƙofa. A round 5 pm agogon U S jirgin su yayi landing a katafaren Airport dake garin,Nailarh a zaune take ita da maƙarabanta saman waiting chairs. Passengers ne su ka ɓullowa ta ƙofar da aka tanada domin su, momy Nailarh ce ta ɓillo a sanye take da suit black color sun bi shape ɗin jikinta, tana da diri sosai kamar matashiyar budurwa,ta rufe kanta da scarf idanunta a manne da baƙin glass,hannunta a riƙe da trolleynta, da gudu Nailarh ta nufeta securitys ɗinta na biye da ita a baya, sakin trolley dake hannunta tayi tana buɗe mata hannayenta, Nailarh na ƙarasowa ta faɗa jikinta, hugging ɗinta tayi tightly, murmushi securitys ɗin su ka saki ba Nailarh ba kawai suma sunyi matuƙar farin cikin dawowar miss MALIKA,raba jikin su tayi,kissing lips ɗin Nailarh tayi hakan ba ƙaramin ƙyatar da securitys ɗin da mutanen dake wurin tayi ba. wani irin narkakken murmushi su ka sakar ma junansu wanda ke nuna tsantsar kewar juna da su kayi, hannun Nailarh taja da sauri securitys suka shiga rissinawa suna gaishe da ita,cike da kulawa ta amsa masu,trolley ta su ka ɗauka, in da su ka yi parking motocin su suka nufa Nailarh da miss Malika na gaba yayin da securitys ɗin ke take masu baya,Nailarh sai wani narke mata take a jiki tana zuba mata shagwaɓa kamar ba ita ba. back seat ɗin motar da za su shiga securitys ɗin su ka buɗe masu,sai da Nailarh ta shiga tukun ta zagaya ɗayan side ɗin ta shiga,rufe ƙofar securitys ɗin su kayi,motocin su ma su ka shiga haɗi da yi masu key su ka fice daga airport ɗin. matsowa tayi kusa da ita, kwantar da kanta tayi saman shoulder ɗinta a hankali ta furta “well come back home” ƙyataccen murmushi miss Malika ta saki tana shafa gefen fuskarta “thanks u baby” kafe juna da ido su kayi kamar za su haɗiye juna, ta cikin mirror drivern dake driving ɗin su ke satar kallon su ba ƙaramin birge shi su kayi ba, suna matuƙar mamakin wace irin soyayyace a tsakanin uwannan da ƴarta, nima dai abun ya fara ɗaure man kai. ⁉ sosai su ka shagala da kallon juna har su ka ƙaraso gida ba tare da sanin su ba,buɗe masu car doors ɗin securitys ɗin su kayi,ficewa su kayi da sauri securitys ɗin dake compound su ka shiga gaishe da ita cike da girmamawa, fuskarta da fara'a take amsa masu,cikin gidan su ka nufa a main parlor su ka samu gaba ɗaya maids ɗin gidan harda Aunty sophia, sun ja layi kamar masu jiran umarni. cike da girmamawa su ka shiga gaishe da ita suna mata barka da dawowa,cike da tsantsar kulawa take amsa masu, ba ƙaramin farin ciki tayi ba na ganin ma'aikatanta cikin ƙoshin lafiya, murmushi tayi tana kallon Aunty sophia “na sameki lafiya, fatan babynah bata baki ciwan kai” murmushi kawai Aunty sophia ta yi ba tare da tace komai ba, murmushi itama kawai ta sakar mata. part ɗin dake kusa da na Nailarh su ka nufa,a bakin ƙofar shiga ɗakin su ka dakata suna sake mata bangajiya ko wacce ta kama gabanta,ciki su ka ƙarasa ita da Nailarh da maid ɗin data ɗauko trolleyn ta,part ɗin ya haɗu iya haɗuwa kusan komai dake part ɗin Nailarh akwaishi a nan, a katafaren bedroom ɗinta suka yada zango,dressing room ɗinta maid ɗin ta kai mata trolley tukun ta fice. “ki zauna mana baby” ta faɗa tana kallon Nailarh dake tsaye ta riƙe ƙugu, fuska a ya mutse Nailarh tace “zanje bedroom ɗin na,kina buƙatar hutu” “please baby ki tsaya tare dani” “zan dawo” ta faɗa tana nufar ƙofar fita ba tare da ta jira amsarta ba, girgiza kai kawai miss Malika tayi tana sakin murmushi. Nailarh na ficewa daga bedroom ɗin part ɗinta ta shiga, Aunty sophia na daga dinning room ta hangi wucewarta, tana shiga bedroom ɗinta kayan jikinta ta rage da kanta,toilet ta nufa, bayan kamar five minute ta fito sanye da bathrobe, bedroom ɗinta dake can kusa da swimming pool ta nufa, a saman bed ɗinta ta kwanta, lumshe idanunta tayi kamar mai bacci. can cikin baccin daya fara fisgarta taji kamar ana shafa jikinta, ya mutse fuska tayi ba tare da ta buɗe idonta ba ta san bazai wuce ita ba ce, dama da wuya ta iya kwanciya ba tare da ta biyota ba. “why baki kwanta kin huta ba?” ta faɗa yayinda take buɗe idanunta da suka fara canza launi saboda baccin daya fara fisgarta, a kan miss Malika ta sauke idanunta, ƴar baby doll ce a jikinta, iya karta gwiwarta,shara shara rigar take ana hangen komai na jikinta muraran. “baby kema kinsan bazan iya kwanciya ba tare da ke a kusa da ni ba” “please ki tafi,ai nace maki zan dawo” “baby ai Baki dawo ba hasalima kwanciya ki ka yi,fushi ki ke dani ne har yanxu?” “mom..” Bata ƙarasa ba tayi saurin rufe mata Baki da tafin hannunta “dont call me momy,call me sweetheart” ta faɗa tana wani marairaice mata fuska ɗan rintse Ido Nailarh tayi haɗi da zuƙar iska ta fesar “ki tashi ki tafi ɗakin ki zan zo na same ki” “baby please ki barni a nan,ko na minti ɗaya bana so nayi nesa dake,wai ke ko ba kiyi kewata bane??” ta faɗa kamar zata sa mata kuka. “nayi kewarki,amma ki tafi zan zo” “wai saboda mi ki ke korata ne,idan saboda yaran nan ne please kiyi haƙuri bazan sake maimaita kuskure irin wannan ba” “nace maki bana fushi dake kuma nayi kewarki kawai I need space” fashe mata da kukan shagwaɓa tayi kamar wata yarinya “baby ba bu in da zanje,ina nan a tare da ke,kawai dan kin ga na damu dake shine za kiyi man haka” ta faɗa yayinda take sa hannu ta shiga warware igiyar bathrobe ɗin dake jikin Nailarh,zuba mata Ido Nailarh tayi tana kallonta,kashe mata Ido ɗaya tayi yayinda ta gama warware igiyar,manne bakinta tayi Dana Nailarh. Hot kisses ta shiga bata a gaba ɗaya ilahirin jikinta,tun Nailarh bata biye mata har abun yayi tasiri a jikinta,dama tana da matsananciyar sha'awa wanda idan abun ya motsa mata komawa take kamar mahaukaciya musamman idan Bata samu abunda take so ba,idan tana a cikin irin wannan yanayin hatta ma'aikatan gidan tsoron tunkararta su ke dan kowa tana iya kai mashi farmaki a wannan yanayin. Cikin ƙanƙanin lokaci su ka fita hayyacin su,baka jin komai sai sautin breath ɗin su dake tashi sama sama,murzar juna su ke basa ji basa gani,gaba ɗaya sun fice a hayyacin su. *Queen Kainart💫* Gajiya tayi da zaman jiran fitowar su, ganin lokacin yin dinner ɗin su na neman wucewa ne yasa ta shiryama miss Malika nata taba Luna ta kai mata ɗakinta,ita kuma ta shiryama Nailarh nata,ganin taga wucewarta part ɗinta ne yasa bata haɗe masu waje ɗaya da Malika ba. A faffaɗan tray ta shiryamata harda banana ice cream ta haɗa mata sanin tana matuƙar sonshi,a bakin ƙofar bedroom ɗin Nailarh ta dakata,madannan dake jikin ƙofar ta Danna,nan take ƙofar ta buɗe,kutsa kai tayi ciki,ta ɗan yi mamakin ganin Nailarh bata bedroom ɗin amma sai tayi tunanin ko tana ɗaya daga cikin bedrooms ɗin nata ko bathroom. Table ɗin dake tsakiyyar Arm chairs ɗin dake ɗakin ta nufa,sautin breathing ɗin mutanan da taji ne yasata dakatawa,saurin kai dubanta tayi ga glass door ɗin bedroom ɗin,dan daga nan take jin sautin,wani irin mummunan faɗuwa gabanta yayi, a lokacin da idanunta su ka nuna mata Nailarh da miss Malika Babu mai sutura a jikin shi,idanunsu sun rufe basa ji basa gani, sakin tray dake hannunta tayi ba tare da saninta ba gaba ɗaya dinner data haɗa mata ya zube a ƙasa glass cup ɗin dake kai ya fashe. A buɗe miss Malika ta bar ƙofar lokacin data shiga hakan ne ya bata damar jin sautin su,saurin kauda idonta tayi jikinta na wani irin kakkarwa kamar wacce sanyi yayi ma mugun kamu,ko ƙarar faɗin tray da fashewar glass cup ɗin basu jiba saboda basa cikin hayyacin su. jiki na rawa ta duƙa ta shiga kwashe abincin da ya zube da cup ɗin daya fashe tana zubawa a tray,garin sauri har yankarta glass yayi amma Bata damuba saboda hankalinta a tashe yake,ba yau ta saba ganin su ba amma yau abun yayi matuƙar ɗaga hankalinta data San Malika na ɗakin da Babu abunda zai shigo da ita kwata kwata bataga lokacin data wuce zuwa part ɗin ba. da sauri ta fice daga ɗakin har tana haɗa hanya, kitchen ta nufa da dishes ɗin,da mamaki chefs ɗin ke kallonta ganin kayan dake hannunta a fashe ga jikinta dake kakkarwa. “lafiya miss Sophia?” ɗaya daga cikin chefs ɗin ya tambaya,cikin rawar murya tace masu bata jin daɗi ne,kanta ke mata ciwo sannu su ka shiga yi mata,ajiye trayn tayi ta fice da sauri, da kallo kawai su ka bita har ta ɓacema ganin su. a corridor part ɗinta ta tsaya,fashewa tayi da kuka mai ban tayi tausayi,bata taɓajin tausayi Nailarh irin na yau ba, tayi fatan ace ita ta haifeta ba Malika,kwata kwata Nailarh ba tayi dace Uwa ba, ta gurɓata rayuwarta gaba ɗaya. Nailarh tunda ta kai kimanin shekaru 14 a duniya mahaifiyarta ke nemanta,tana amfani da pills wajen ganin ta gusar mata da hankali dan ta biya buƙatar ta da ita, tun Nailarh na gudun abunda take mata har ta koma tana jin daɗin abun,yanzu abun har ya zame ma Nailarh lalura idan abun ya motsa mata fita hayyacinta take idan ba ta samu abunda take so ba,a lokacin da Aunty Sophia ta gane ta tausaya ma Nailarh matuƙa takuma yi ƙoƙarin ganin ta ganar da miss Malika illar dake cikin hakan amma sai ta nuna mata ƴarta ce ba abun da ya shafeta bane, tana kai shekara 18 ta fara koya mata kula da club da Casino da su Joseph ke kula da su amma sai ta maida Nailarh,tunda ya koma ita ke kula dasu sai su Joseph su ka koma masu taimaka mata, a lokacin ran Aunty sophia yakai ƙololuwar ɓaci harta kasa haƙuri ta samu Malika a karo na biyu ta sake nuna mata illar sa rayuwar Nailarh a wannan tsarin kawai zata kashe mata rayuwar ne, a lokacin cin mutuncin na gidan duniya babu wanda Malika bata yima sophia ba amma hakan baisa ta daina faɗa mata gaskiya ba daga ita har Nailarh, ganin ta dage ne yasa Malika yima sophia barazanar korarta daga aiki ,da farko Aunty sophia bataƙi tabar aikin ba saida tayi tunanin taga idan kuma ta bar gidan wa zai faɗa mata gaskiya wa zai taimaki rayuwar Nailar, tana matuƙar son Nailarh da tausayinta hakan yasa tayi haƙuri ta fasa tafiya,taja bakinta tayi shiru amma abun na damunta kullum cikin yima Nailarh adu'a neman kuɓuta daga sharrin mahaifiyarta take. ta jima a tsaye a nan, idanunta har sun kumbura saboda kukan data sha,ƙofar part ɗinta ta buɗe ta shiga. A wannan yanayin bacci yayi awanta gaba da su, sun shigema juma kamar za su koma abu ɗaya. sai around 11 pm su ka farka, miss Malika ta fara farkawa dalilin baƙar yunwar data addabeta tun a cikin bacci, kallon Nailarh dake kwance saman jikinta tayi, ta shige jikinta sosai ta kanainayeta kamar wani yace zai ƙwace mata ita. A hankali ta shafa gefen fuskarta tana kiran sunanta,instead of ta tashi sai ma shake shigewa jikinta da tayi “please baby ki tashi muyi dinner 11 tayi, idan mun kammala sai ki koma ki cigaba” maƙe mata kafaɗa Nailarh tayi “ban jin yunwa” lallashinta ta shiga yi da ƙyar ta samu ta tashi, toilet ta nufa da kallon Malika ta bita tana wani langwaɓar da kai, sai da ta shigewar Nailarh toilet tukun ta tashi ta fice bayan ta ɗauki rigarta ta maida. Part ɗinta ta nufa itama wanka tayi ta shirya cikin PJ riga da wando, part ɗin Nailarh ta koma bayan ta gama shiryawa,a zaune ta samu Nailarh bakin bed bathrobe ce a jikin yanzu ma, tayi shiru kamar mai nazarin wani abu. Zama Malika tayi kusa da ita “baby lafiya?” ta faɗa tana ɗaura hannunta saman bayan Nailarh, ajiyar zuciya ta sauke “ba komai” “ok tashi muje muyi dinner” ta faɗa tana tashi haɗi da jan hannun Nailarh su ka fice zuwa dinning room. duk da kasancewar dare ne sosai chefs ɗin nan ba su tafi makwacinsu ba saboda rashin fitowar su yin dinner. kujera tajama Nailarh ta zaune tukun itama ta zauna kusa da ita, babu ɓata lokaci chefs ɗin su ka shiga serving ɗin su,kallon chefs ɗin Nailar tayi “ina Aunty sophi?” ɗaya daga cikin su ne ya bata amsa “ta tafi part ɗinta bata jin daɗi ne” “mike damunta” “bamu sani ba gaskiya, amma dai tace kanta ke mata ciwo” yanyin fuskarta ne ya canza duk sai taji wani irin jin Aunty sophia ba lafiya, ta damu da ita sosai. fatan samun lafiyar sophia Miss Malika tayima masu aikin,da kanta ta shiga ba Nailarh abincin a baki har su ka kammala,tattara dinning room ɗin chefs ɗin su ka shiga yi, Nailarh ta so zuwa part ɗin sophia ta dubata amma miss Malika tace ta bari sai da safe. Part ɗin Nailarh su ka koma a nan su ka kwanta. *WASHE GARI* A hakimce take saman sofa mai mazaunin mutum uku a katafaren main parlor gidan, PJ ne a jikinta, laptop ɗinta na ajiye saman table ɗin dake gaban sofa, a hankali take Operating ɗinta,Joseph na zaune saman sofa mai mazaunin mutum ɗaya, ya ɗau wankan black suit,rigar suit ɗin na ajiye saman hannun sofa da yake zaune, hannushi riƙe da fils. daga gefe chief security ɗin gidan ne sai masu kula da C C TV sai drivers ɗin Nailarh da su Luna sai chefs,gaba ɗayan maids ɗin ne Aunty sophia ce kawai babu. Aikin ko wane ta ke bincika dan sanin abun da ya faru bayan bata nan duk da suna sanar da ita abunda ke faruwa lokacin da bata nan, drivers ɗin Nailarh ta fara tsarewa da tambayar da bata nan ina da ina su ka kai Nailarh. Alex ne ya shiga zayyana mata inda Nailarh taje bayan bata nan,shi ke driving motar Nailarh duk za su fita kuma shine shugaban drivers ɗin gidan baki ɗaya, jinjina kai ta shiga yi har ya kammala sanar da ita, maida hankalinta tayi kan su Luna suma dai magana ɗaya ce da Alex, sallamar su tayi su koma bakin aikin su. Masu kula da C C TV gidan ne su ka fara kora mata bayanin kaf abunda ya faru,babban cikin su ne ya sanar da ita “ma'am still Sophia's CCTV doesn't work” jin jina kai tayi tana ɗan dakatawa da aikin da take “duk gyaran da a ka yi?” “yes ma'am” da kamar za tayi magana sai kuma ta fasa “u can go” ta faɗa, gabanta ɗaya daga cikin su ya zo flash ya miƙa mata kafin ya fice. tana cikin magana da Chefs Aunty sophia ta zo,kallo ɗaya za kayi mata ka hango tsantsar damuwar dake kwance a fuskarta,gaishe da miss Malika tayi da kulawa ta amsa mata “chefs sun ce baki lafiya,how do u feel now?” “am feeling much better” “I'm points hope quick recovery dear” “thank U ma'am” Nailarh ce ta fito daga bedroom ɗinta shirt da short ne a jikinta ta ɗaure gashin kanta da ribbon, ciki parlorn ta nufo, tunda ta fito su ka kafeta da ido musamman Joseph har wani ɗaga kai yake dan ya kalleta da kyau. tana ƙarasowa tayi hugging ɗin Aunty sophia ta baya “good morning” “morning baby, kin tashi lafiya” “lafiya lau” Nailarh ta faɗa tana raba jikin su “mi ya samu hannunki?” ta faɗa yayinda take riƙo hannun Aunty sophia “yankewa nayi da glass” “Ayyah, sorry chefs sun ce man baki da lafiya, mike damunki” “it was a headache,but i got better now” “is this tumor the cause you of the headache?” ta faɗa da tsantsar kulawa girgiza mata kai Aunty sophia tayi “bashi bane” “sorry” Nailarh ta faɗa kamar ƙaramar yarinya jin jina mata kai Aunty sophia tayi. mahaifiyarta dake zaune kan sofa ta nufa, ɗan rissinawa tayi ta sumbacin lips ɗinta, saurin rintse ido Aunty sophia tayi tana jin wani irin ɗaci a ranta. “good morning” Nailarh ta faɗa “morning beb” malika ta faɗa tana kashe mata ido ɗaya, kusa da ita ta zauna tana ɗaura ƙafa ɗaya kan ɗaya. “good morning boss” Joseph ne ya faɗa, amsa mashi tayi tana ɗaga mashi hannu, gaishe da ita chefs ɗin dake tsaye su ka shiga yi da kulawa take amsa masu. sallamar chefs ɗin miss Malika tayi bayan sun gama bata amsoshin tambayar da tayi masu, sofa dake kusa da wacce Joseph ke zaune miss malika ta nuna ma Aunty sophia, zama tayi tana fuskantar ta. Ta sowa Joseph yayi daga mazauninshi files ɗin dake hannunshi ya miƙama miss Malika, amsa tayi tana jinjina mashi kai “zaka iya tafiya,idan na kammala dubawa zan tura maka replys ta email” “ok ma'am, have a nice day” rigar suit ɗinshi dake ajiye kan hannun sofa ya nufa,ɗaukar rigar yayi haɗe da briefcase ɗin shi dake gefe “bye” ya faɗa yana ɗaga masu hannu, jinjina mashi kai miss Malika tayi, ficewa yayi daga parlorn. ɗaya daga cikin chefs ne ya shigo hannunshi ɗauke da madaidaicin tray wanda ya shirya masu coffee, Nailarh ya nufa ya fara miƙa mata ta ɗauka kafin miss Malika da Aunty sophia, barin parlorn yayi ya koma kitchen. “Sophia!” miss Malika ta kira sunanta, ɗagowa Aunty sophia tayi ta fuskanceta da kyau “William ya sanar dani har yanzu C C TV part ɗinki bata aiki, what is the problem?” ta faɗa tana kafeta da ido “nothing, but naga is not good ace har a bedroom da bathroom an sa mana camera ba, a barshi a iya parlor kawai,bedroom and bathroom is our part of secret” tunda ta fara magana Malika ta kafeta da ido “but if that offends u, am very sorry” “saboda bai dace ba yasa ki ka lalata na part ɗinki?” cike da tuhuma miss Malika ta faɗa “please momy Aunty sophia ce fa, mi kike son sani a game da rayuwarta da har sai kin sa mata C C TV, gaskiya i'm really not happy” Nailarh ta faɗa da alamar rashin jin daɗin abunda momy tata tayi “shikenan nima ba dan komai yasa nake sawa ba sai dan na riƙa sanin halin da ku ke ciki,taking care of ur health is my responsibility” “hakan yana da da kyau,we thank u for ur care for us” Aunty sophia ta faɗa, jin jina kai kawai Malika tayi, tashi Aunty sophia tayi ta nufi kitchen dan ta duba chefs, da kallo Malika ta bita har ta ɓacce ma ganinta. “honestly momy baki kyauta ba, how many years Aunty sophia ke tare dake dan mi zaki sa mata C C TV a part,wannan old women ɗin mi kike tunanin zata iya aikatawa, ban da kula dani babu abunda take a gidan nan, that's why I love her,babu ruwanta” wani kallon banza Malika tayi mata“u love her, ban gane ba?” “yeah, ina jinta tamkar mahaifiyata wacce ta haife ni” harara Malika ta watsa mata “ni fa?” “u are special,ur position is different sweetheart” murmushi Malika ta saki. ❤💫❤💫❤💫❤💫❤💫❤ Tun da malika ta dawo Aunty sophia ta ƙauracema Nailarh ko part ɗin ta ta daina zuwa, iya karta ta duba masu aiki ta koma part ɗinta,duk wata hanya data san zata haɗata da malika tare da Nailarh tayi blocking ɗinta. Yanzu ma tana kitchen ne tare da chefs tana sanar da su abubuwan da ya kamata su yi saboda celebration ɗin da za suyi bayan kammala wasan da Nailarh zata gabatar a yau, dama al'adarta ne duk ƙareshen shekara suna gabatar da wasa wanda ya fi kowane a N R T. Duk wanda yake ji da kanshi a wasan doki zaka sameshi a ranar gasar, ƙwararrune daga yanki daban daban na ƙasar dama wasu ƙasashen ke halartar wasan, tsawan shekara biyar kenan suna gabatar da wasan har yau ba'a samu wani wanda yayi zarrar da zai zo na ɗaya a gasar wasan ko wane lokaci Nailarh dai. A hankali ta lallaɓo masu aiki na kallonta amma ba halin suyi magana saboda gargaɗin da tayi masu,hannuwanta tasa tana rufe mata eyes ɗinta ta baya. Murmushi Aunty sophia ta saki ta san babu wanda zaiyi mata hakan face ita, hannunta dake kan idanunta ta kama “baby” ta kira sunanta, sakin idanunta Nailarh tayi tana ɓata fuska “u are too quick to recognize ” ta faɗa tana turo baki, murmushi chefs ɗin suka saki “banda abunki Nailarh waye zai yiman haka bayan ke,how was ur night,I hope u slept well?” “fine,na biyoki har nan ne dan naji laifin me na maki ki ke avoiding ɗina tow days?” gaishe da ita chefs ɗin su ka shiga yi,jinjina masu kai kawai tayi, shafa fuskarta Aunty sophia tayi “baki man laifin komai ba, na barki ki samu enough time with ur momy” taɓe baki Nailarh tayi “amma ai kin zo har ɗaki kiyi wishing ɗi na ko?” “kema kin san zan zo, ina duba chefs ne” “baby!” aka faɗa daga bayan su, saurin kai dubansu su ka yi ga Miss Malika dake tsaye, PJ ne a jikinta da alama daga bacci take. Cike da girmamawa suka shiga gaishe da ita, da kulawa ta amsa masu tana nufar cikin kitchen ɗin , kama hannun Nailarh tayi “ashe kina nan ki ka bar ni sai wahalar nemanki nake” “nazo wajen Aunty sophia ne” “ok muje” jan hannunta tayi “Aunty sophia sai kin zo” jinjina mata kai tayi, ficewa su kayi daga kitchen ɗin. *ABUJA NIGERIA💫* Shigowar su kenan daga school duk a gajiye su ke,Yumnah tun a parlor ta cire mayafin dake kanta, a saman bed ɗinta su ka yada zango. “wallahi sis am very tired har ƙosawa nayi a kammala lectures” Yumnah ta faɗa tana ya mutse fuska “me too, yanzu bani da wani buri da wuce na watsa ruwa na kwanta na huta before magrib” Nainarh ta faɗa tana nufar dressing room. kwanciya saman bed ɗin Yumnah tayi “ni gaskiya sai na tashi daga baccin tukun zan yi wanka” Nainarh na shiga dressing room ɗin jakarta ta a jiye tukun ta cire kayan jikinta ta ɗaura towel, bedroom ɗin ta koma, Yumnah na nan kwance har bacci ya fara ɗaukarta. toilet ta nufa ta watsa ruwa kafin ta fito, dressing room ta koma,gown ta saka mara nauyi kafin ta dawo bedroom ɗin kwanciya tayi kusa da Yumnah. Duk yanda take jin bacci kafin ta kwanta, tana kwanciya taji kwata kwata baccin ya ƙaurace ma idonta,juyi ta shiga yi a bed ɗin Yumnah kuwa baccinta take hankali kwance. shiru tayi tana ƙurama sailing ido, ba komai ya faɗo mata a rai ba sai photon da ta gani a part ɗin Abbah, bata san waye a photon ba amma haka nan ta kwaɗaitu da san sanin waye shi, kullum tana son tambayar Yumnah amma sai ta manta. kallon fuskar Yumnah tayi kafin ta maida idonta akan teddy bears ɗinta dake ajiye saman head board ɗin bed ɗin. ƙaramin tun bata da wayau mahaifiyarta ta bata shi, babban kuwa mahaifinta ya bata shi a matsayi kyautar ƙarin shekara lokacin data kai kimanin shekara goma. Murmushi ta saki lokacin data tuna shirmenta na yarinta, haka zata tasa teddys ɗin a gaba tana faɗin ga momy ga dady,haka iyayenta za su tasata gaba suna dariya, duk tana tuna rayuwarta da iyayenta abun ba ƙaramin nishaɗi yake bata ba,amma lokaci ɗaya komai ya rushe, duk ta tuna kisan wulaƙantaki da aka yima mahaifinta da sharrin da aka da bai baye mahaifiyarta dashi sai taji wani ƙunci ya mamaye zuciyarta, ta rasa laifin mi su ka aikatama wanda yayi masu haka. Adu'arta a kullum Allah ya toni asirin wanda yayi silar rushewar farin cikin su, shima Allah ya rusa nashi farin cikin, ya tozarta rayuwarshi kamar yanda ya tozarta ta su, sosai tayi nisa a duniyar tunani ringing ɗin wayar Yumnah ne ya dawo da ita hayyacinta, a jiyar zuciya ta sauke tana jawo jakar, wayar ta ciro, duba sunan mai kira tayi,ya Naeem ta gani. da sauri ta ɗan bubbuga kafaɗar Yumnah “ki tashi ya Naeem na kira” juya kwanciya Yumnah tayi “please ki ɗaga kice mashi bacci nake” picking call ɗin tayi tana kara wayar a kunenta “Assalamu Alaikum” ta faɗa, on the other hand ya Naeem ya amsa mata sallamar “ya Naeem ina wuni” “lafiya lau Yumnah, kun dawo ne ko har yanzu kuna school?” “ba ita bace, Nainarh ce” Nainarh ta bashi amsa “yawwa Nainarh dama ke nake nema, kun dawo daga school ɗin?” “eh” ta bashi amsa “ok,meet me in the garden now” a sakale ta amsa mashi,mamaki ne ya cikata, neman mi yake mata “right now” ya sake jaddada mata haɗi da rejecting ɗin call ɗin “ni kuma, neman mi yake man” ta faɗa da tsantsar mamaki, ajiye wayar tayi ta nufi toilet, bata wani jimaba ta fito, dressing room ta nufa, hijab ta ɗauko,ficewa tayi daga ɗakin. bata samu kowa a parlorn ba, tun daga nesa ta hango su saman chairs shi da ya Adnan a garden ɗin, waya ce kare a kunen ya Naeem ɗin da alama waya yake, tunda ta tunkaro su ya Adnan ya kafeta da ido yana kallota harta ƙaraso in da su ke, sallama tayi masu ya Adnan ne ya amsa mata ya Naeem kuwa hannu kawai ya ɗaga mata. Cike da ladabi tana ɗan rissinawa ta gaishe da Ya Adnan ɗin, da kulawa ya amsa mata yana sakar mata murmushi ya nuna mata chair dake fuskantar wacce su ke zaune dan ta zauna, murmushi ta saki “nagode” ta faɗa tana zama. “ya school,fatan kun dawo lafiya?” “lafiya lau Alhmdllh” masha Allah ya faɗa, hankalin su ne ya koma kan ya Naeem dake waya “it's a favor i'm asking for, please ka taimaka ranar birthday ɗinka ka zo,ya ɗauki ranar birthday ɗinka rana mai daraja da mahimmaci, ka daure a wannan karon ka tabbatar mashi da darajar ranar,the anger u have with him is enough, dan Allah ka kawo ƙarshen wannan guje mashin da ka ke” ɗan dakatawa yayi da magana ya can ya cigaba “kayi shiru ba kace komai ba, ka sa ni yanda ya ke sonka ko mu dake tare dashi baya mana son da yake maka, baka tare dashi amma duk wani abu daya shafeka baya wasa dashi,ka sani duk abunda zaiyi mana a rayuwa sai yayi maka,more than u think,wasu har gani suke kamar ya samu taɓin hankali a kan ka saboda wasu abun da yake hankali ma bazai ɗauka, please yaci albarkacin wannan ƙaunar da yake maka kayi haƙuri ka daina wannan fushin da shi” sosai ya Naeem ya kwantar da murya yana bashi haƙuri duk dan ya sauko. zuba mashi ido Nainarh da ya Adnan su kayi, lamarin yayi matuƙar ɗaure mata kai waye wannan ake haɗashi da Allah irin haka amma yaƙi yayi abunda ake so. “shikenan kayi duk abunda ka ke ganin shine dai dai, amma ka sani haƙƙin baƙin cikin da kake cusa mashi bazai barka ba, he's ur father, ko wane irin laifi zaiyi maka aduniya he didn't not deserve to be anger with him” yana gama faɗar haka yayi rejecting call ɗin. haka nan Nainarh ta tsinci kanta da rashin jin daɗin abun, bata san ko waye ba amma bai kyauta ba mahaifa ba abun wasa ba ne. “in wuni ya Naeem” “lafiya lau Nainarh, ya school” da Alhmdllh ta amsa ma shi “dama akwai wasu maganganu da nake son zamu tattauna game da abunda ya faru da dadynki” tunda ya faɗi haka yanayin fuskarta ya canza, fahimtar hakan ne yasa shi cewa “karki damu ba wani abu bane kawai ƴan tambayoyi ne zanyi maki,in dai ki ka bani haɗin kai in sha Allah za muyi nasarar gano wanda su ka kashe shi” “in sha Allah zan baka haɗin kai, duk wani abu dana sani zanyi ƙoƙarin sanar da kai” “yawwa haka nake son ji, da na so muyi maganar yanzu,but bana da time, zuwa ranar Saturday za muyi magana ko kuje can gida keda Yumnah ku same ni” “to shikenan, Allah ya kaimu” “Ameen ya Allah, za ki iya tafiya kawai” to tace ta na tashi daga chair, sallama tayi masu ta koma cikin gidan, ranshi ya rigada ya gama ɓaci bayajin zai iya maganar da za suyi shiyyasa kawai ya sallameta. tunda Nainarh ta fito daga gidan ta nufo garden yake tsaye bayan pillar da waya a hannunshi, da alama video yake ɗaukar su, baƙaƙen kaya ne a jikinshi ya rufe ko ina na jikinshi banda idanun shi babu wani abu da ake iya gani daga jikinshi. Nainarh na tunkaro ƙofar shiga gidan yayi saurin ɓoyewa yana zura wayar Aljihun wandon jikinshi, kowaye da alama leƙen asiri yake masu. ɗan dukan kafaɗar ya Adnan ya Naeem yayi ganin ya bi Nainarh da ido “ya dai,lafiya ka kafe yar mutane da ido ka ke binta da wannan kallon ƙurillar?” kauda kai gefe ya Adnan ɗin yayi yana sakin murmushi “ba komai, kawai dai tana burgeni ne she's so innocent” murmushi ya Naeem yayi “ka tsaya dai iya haka” dariya ya Adnan ɗin yayi yana girgiza kai “ya ku ka yi da SAM ɗin ya amince kuwa?” ya Adnan ya faɗa yana kallon fuskar ya Naeem, tsaki ya Naeem yaja “ka kyale SAM kawai Adnan,na rasa gane wane irin bauɗaɗɗan mutum ne shi, Allah ma muna mashi laifi ya yafe mana sai shi ne bazai yafe ba, na rasa a wajen ubanwa ya gaji wannan baƙar zuciyar da idan ya juyama abu baya ya juya mashi kenan?” “uncle Mustafa shi ka manta tashi kalar zuciyar ne?” “uhmmm Allah gara uncle Mustafa dashi, tsawan shekara nawa kenan ana fama dashi amma ya maida mutane shashashu, ka du ba fa ka ga irin haukan da dady keyi a kan shi wannan bai isa ba ace ya yi haƙuri,bawan Allah nan sau nawa yana taka ƙafa ya bishi amma haka zai ƙaraci zamanshi ya dawo bazai taɓa ganinshi ba haba” ya ƙare maganar cikin fushi “Allah ya kyauta, amma SAM lamarin shi sai shi, ni kaina sai na kusa haɗa shekara banji muryarshi ba” ya Adnan ya faɗa “wallahi zanyi mashi maganin abun da ke damunshi ne” murmushi ya Adnan ya saki “ai da yake kunfi kusa, dama da kai yake uban ba da dady ba” tsaki kawai ya Naeem yaja. *Queen Kainart💫* tafe take kwata kwata bata lura da mutum dake tahowa ba duk da ƙofar ta glass ce,shima hankali shi baya gaban shi yana a kan wayarshi da yake latsawa. saurin ja da baya tayi dalilin karon da su ka yi,wayar dake hannunshi ta faɗi ƙasa, dafe goshinta da ya bigi broad chest ɗin shi tayi,wani irin zafi ne ya ziyarci kwakwalwarta, a masifance ta ɗago tana kallonshi ido cikin ido “dallah malam baka gani ne or are u blind da ka ke tafiya baka kallon gabanka??” ta faɗa tana wani zazzare mashi ido, wani irin haushin shi da tsanar shi take ji a ranta. kasa magana yayi saboda mamaki daya rufe shi, ta bugeshi har ta yar mashi da waya ƙasa amma ta rufeshi da faɗa kamar wani sa'anta,mamakinshi ma a ina ta samu confidence ɗin yi mashi rashin kunya. harara ta sake watsa mashi haɗi da jan tsaki,raɓawa tayi ta gefenshi zata wuce, rai a ɓace ya fisgo Arm ɗinta, gaba ɗaya ta tafi taga taga zata faɗin, riƙota yayi sosai, idan da abunda ya tsana a rayuwarshi tsaki, ya tsani tsaki musamman ace mace ce tayi mashi shi. Raba idanu ta shiga yi a fuskarshi, ba ƙaramin tsorata tayi da yana yin shi ba,cike da mugunta ya sake matse hannunta,saurin rintse ido tayi saboda wani zafi daya shigeta. Murya a kausashe yace “wa ki ke ma tsaki?” banza tayi da shi ƙoƙarin ƙwace kanta kawai take daga riƙon da yayi mata, tsawa ya daka mata “tambayarki nake wa ki ke ma tsaki??” ya faɗa yayin da yake murɗe hannunta fashewa tayi da kukan azaba, murya na rawa tace “ai ba da kai nake ba” “dawa ki ke” ya faɗa fuska a ɗaure “dan Allah kayi haƙuri” “tsaran wasanki ne ni?” girgiza mashi kai tayi hawaye na bin cheek. “bani wayata” ya faɗa yana nuna mata wayarshi dake yashe a ƙasa “ka sakar man hannu to” sakin hannunta yayi, duƙawa ƙasa tayi ta ɗauko mashi wayar “gashi” ta faɗa tana turo mashi baki. amsar wayar yayi yana sake riƙe hannunta “this should be the first and last time da za kiyi gigin yiman rashin kunya if not, sai na ɓaɓɓalaki a gidan nan useless” “IRFAN” su ka ji an faɗa a bayan su. saurin sakin hannunta yayi yana juyawa bayanshi,dady ne da uncle hashim,tun lokacin da su ka yi karo su ke tsaye suna kallon su. hannunta da Irfan ɗin ya riƙe ta shiga murzawa saboda zafin da yake mata “Irfan mi ya haɗaka da ita?” dady ya faɗa “babu komai, ina wuni Uncle” “lafiya lau” uncle hashim ya faɗa, saurin barin wajen Irfan yayi ya nufi garden wajen su ya Naeem. “zo nan Nainarh”dady ya faɗa yana mata alama data zo, nufo su tayi har time ɗin hawaye na bin kumatunta, hannu dady yasa ya shiga share mata hawayen “kukan ya isa haka, mi yasa ki ka yi mashi rashin kunya?” “babu komai” “he's ur elder brother, kar na sake gani,kina jina ko” “eh dady in sha Allah bazan sake ba” “haka nake son ji, ga Uncle ɗin ku nan ku gaisa” ya faɗa yana nuna mata Uncle hashim dake tsaye yana kallonsu “in wuni Uncle” “lafiya lau, ya ki ke, ya school??” “lafiya lau Alhmdllh” “masha Allah, Allah ya taimaka” da Ameen ta amsa tana barin wurin ta nufi bedroom ɗin su. tana shiga bedroom ɗin saurin zame hijab ɗin jikinta tayi tana kallon hannunta da Irfan ɗin ya riƙe wurin har yayi ja. wasu hawaye ne su sake taruwa a idonta “mugu kawai” ta faɗa tana turo baki. *Queen Kainart*💫 “muje ko” ya dady ya faɗa yana kallon Uncle hashim “gida zan tafi” “tafiya dai hashim, ai ka shiga ku gaisa da Zulaihart ko?” “A'a yaya tafiya zanyi, idan na sake dawowa mun gaisa” dady ya faɗi haka ne kawai amma dama ya san uncle hashim bazai tsaya ba in dai dan su gaisa da mom ne “shikenan ka gaishe da mutanen gidan” “za su ji, sai anjima” jin jina mashi kai dady yayi yana nufar sama zuwa part ɗin shi. ficewa uncle hashim ɗin yayi amma instead of ya fice daga gidan baki ɗaya sai ya nufi part ɗin Mamy, bai samu kowa a falonta ba, masu aiki na part ɗin su Fa'iza na gidan shi wurin Balqis. direct bedroom ɗinta ya nufa, bai sameta a ciki ba sai ƙarar ruwa da yaji a cikin toilet alamar tana ciki. bed ɗinta ya nufa, zama yayi yana kwantar da kanshi jikin head board, wayarta dake ajiye kan nightstand ya ɗauka, babu password a wayar hakan ya bashi damar shiga contact da messages ɗinta. turo ƙofar toilet ɗin tayi ta fito tana yarfe hannunta da alama alwala tayi, da mamaki take kallonshi bata san yaushe ya shigo ba, mamakin ganinshi a irin wannan lokacin ne ya hanata ƙarasawa gare shi. wayarta dake hannunshi ya ajiye yana zuba mata mayatattun idanunshi “ƙaraso mana ki ka tsaya nan” ya faɗa ganin tayi tsaye kamar an dasata. cikin ɗakin ta nufo kamar yanda ya umarta “yaushe ka shigo, baka tsoron wani ya ganka a irin wannan lokacin??” jin jina mata kai yayi alamar eh “eh fa kace, baka gudun yayanka ya shigo gidan?” “tare mu ka shigo da shi, yana part ɗin shi” “amma shine ka shigo part ɗin, baka tsoron ya shigo part ɗina??” “wait mabaruka kinyi farin cikin gani na ko na tashi na kama gabana?” ya faɗa yana ɗan tsuke fuska alamar rashin jin daɗin tambayoyinta “kaima ka san am really happy to see u but kawai dai bana son abunda zai jawo mana matsala” sauka yayi daga saman bed ɗin ya nufo inda take, kama hannunwanta yayi ciki nashi “naga hankalinki bai kwanta da zuwana ba,lee me go” ya faɗa yana sakin hannunta, saurin kamo hannunshi tayi “tunda har kai hankalinka a kwance yake bana da wata matsala” “are u sure?” “really sure, kai da kazo ma baka damu ba sai ni daka iske” a jiyar zuciya ya sauke yana wani lumshe ido “why did u not pick my call yesterday?” “am with u brother, ka san jiya a wajena yake” “mi yarinyar can take har yanzu bata bar gidan nan ba?” tsaki taja “hmmm ka bari kawai u know ur brother yanda yake da matarshi komai tayi dai dai ne a wajansa, duk wata hanya na bi dan ganin ta bar gidan nan har mama Ameenah na sanar mawa tace za tayi mashi magana amma shiru, dama nayi mashi maganar sai shata man layi yayi akan yarinyar, wani mugun sonta yake ga yarinyar da ɗan banza kilibibi, duk wata hanya data san zata bi danta samu shiga a wurinshi sai da tayi” “alright, amma dole yarinyar nan ta bar gidan nan kema kin san da haka?” “i know, in sha Allah zanyi iya bakin ƙoƙari na ganin tabar gidan nan” jawota yayi zuwa jikinshi, cikin wata irin shu'umar murya yace “alright, yaushe zaki bar ya Tahir ki dawo gare ni, na gaji da wannan raba dai dan da nake dashi” ya faɗa yana wani lumshe ido “ko a yanzu a shirye nake, umarninka kawai nake jira” sake matso da ita yayi jikinshi, hannunshi ya zura bayanta, zip ɗin rigarta ya shiga zugewa, a hankali ya furta “har yanzu burinmu bai cika ba mabaruka” “don't worry about that, nan da wani lokacin komai zai zo ƙarshe” “are u sure?” “am sure, Fa'iz da Fa'iza ne kawai nake ganin za suyi man cikas” “karki damu da wannan sun riga da sun girma, kuma ko baki nan Zulaihart zata kula da su kamar yaranta, kuma da sunyi Aure ai shikenan” “haka ne, amma maimunatu fa kasanfa bana son zama dakai tare da kowa?” “maimunatu is not ur problem ni na san yanda zanyi da ita” ya faɗa yana wani kashe mata ido ɗaya, murmushi ta saki itama tana maida mashi martani. saurin manne bakinshi yayi da nata, a zafafe ya shiga kissing ɗinta ba ƙaƙautawa,sun jima a haka har ƙafafunsu suka fara gajiya, ganin tsayuwar baza tayi masu bane yasa shi sakin bakinta,ida unzipping rigartar daya fara yayi, he slipping her all and throw it away, sake manne bakinsu yayi yana ɗaukarta,a haka ya nufi bed da ita. *UNITED STATE❤* _*Las Vegas (Nevada)*_ *THE PRESENT DAY* Aunty sophia da Chefs ne a kitchen suna shiri akan celebrating dinner da za suyi zuwa anjima,suke aikin tana kula da su,tunda miss Malika ta dawo ta koma kitchen duk da ba girki take ba. “i hope Miss Nailarh enjoyed this Burger more than the previous one” ɗaya daga cikin chefs ɗin ya faɗa,riƙe ƙugu wanda ke gaban oven yayi “i also wish this cake is better than the last celebration” murmushin Aunty Sophia ta saki tana jin kowa da abunda yake buri “ni dai ba komai ke burgeni ba except how we can relax today,har Adu'a nake shekara ta zagayo because of this celebration,i like how Nailarh allow us to do what we want on this day” ɗaya daga cikin chefs ɗin ta faɗa tana sakin murmushi. Aunty Sophia na sauraron kowa sai faɗar albarkacin bakinsa yake ƙala bata ce masu ba,amma tana jin daɗin yanda su ke yabon Nailarh. maida hankalinsu su ka yi kan aikin da suke,ƙarar fashewar wani abu su ka ji daga waje “ba ku jin wata ƙara kamar fashewar nockout?” ɗaya daga cikin chefs ɗin ya faɗa “ko dai sun dawo ne ,naji kamar hayaniya ƙasa ƙasa?” wani ya sake faɗa daga cikin chefs ɗin,tashi Aunty Sophia tayi daga saman chair ɗin da take zaune “ku ci gaba da aiki,lee me check” Aunty Sophia ta faɗa tana nufar ƙofar fita. sauran ƙiris suyi karo da luna ta shigo kitchen ɗin da gudu,da sauri Aunty Sophia taja baya tana kallonta ganin yanda ta shigo kitchen ɗin kamar wacce aka koro “lafiya!?” Aunty Sophia ta faɗa tana leƙen bayanta ko za taga abunda ya biyota. da mamaki Aunty Sophia ta dawo da dubanta gareta dan ba taga komai ba “are u okay?” ƙofar fita ta shiga nuna mata tana sauke numfashi da sauri sauri alamar na wanda yayi gudu ko yaga wani abun tsoro. “minene wai,i don't see anything?” da ƙyar luna ta fisgo kalma daga bakinta tace “Na..i..larh” zaro ido Aunty Sophia tayi,da sauri ɗaya daga cikin chefs ɗin ya miƙa mata ruwa,hannunta har rawa yake wajen amsar ruwan,kafa kai tayi ,tas ta shanye ruwan tana maida numfashi “Miss Nailarh shot Alex with a gun!” wani mummuna faɗuwa gaban su yayi,gaba ɗaya su ka zaro ido suna kallon luna da tayi maganar,Aunty Sophia bata tsaya jin abun da luna zata sake cewa ba ta fice daga kitchen ɗin da sauri ta nufi main parlor,tana shiga parlorn Nailarh na Kunno Kai da gun a hannunta yayin da miss Malika ke biye da ita kamar mahaukaciya tana mata magiya akan ta ajiye gun ɗin. cikin parlorn security ɗin su ka shigo da Alex hannunshi sai jini yake,ba ƙaramin tashi hankalin Aunty Sophia yayi ba,da sauri tasha gaban Nailarh “baby are u out of mind,what are u planning to do like this?” ɗago idanunta tayi ta kalle Aunty Sophia,da sauri ta kauda kanta gefe ganin yanda idanun Nailarh su ka yi jawur wutar ɓacin rai ce kawai ke ci a cikin su, fuskarta tayi jawur musamman cheek ɗin ta. “if u dont move of on my way,I will kill u!” Kamar saukar aradu haka Aunty Sophia taji maganarta “Nailarh are you saying that you will kill me?” tsawa Nailarh ta dakata mata tana zaro mata ido “i said move or I will shoot u!” gaba ɗaya parlorn babu wanda hankalinshi bai tashi ba yau Nailarh kema Aunty Sophia tsawa har take faɗin zata kashe ta lallai ba ƙaramin ɓaci ranta yayi ba. wasu irin hawaye ne su ka wanke fuskar Aunty Sophia cikin ƙunar rai tace“bazan matsa ko ina ba kill me Nailarh” “sophia are out of mind or u forgot who's Nailarh when she's angry?”miss Malika ta faɗa tana zazzare ido “babu inda zan matsa taje ta illata kanta,Nailarh just kill me if that can calm u're mind”Aunty Sophia ta faɗa babu alamar tsoro,nuna ta Nailarh tayi da gun ɗin,rintse ido Aunty Sophia tayi,wani irin wahalallan yawu miss Malika ta haɗe kamar ita aka nuna da gun ɗin. magiya parlorn su ka shiga yima Aunty Sophia kan ta matsa amma ko gezau ba tayi ba. hawayen da suka taru idonta tun ɗazu sai yanzu su ka samu damar zubo,wani irin Shaking jikinta ya shiga yi,canza direction ɗin gun ɗin tayi zuwa sama, crystal Chandelier ɗin dake ceilling tayi shooting,gaba ɗaya ya ruguzo ya faɗa kan center table dake parlorn,toshe kunnuwansu su ka yi in ka cire Aunty Sophia data kafe Nailarh da idanu hawaye na zuba. hawaye ne su ka shiga sintiri a fuskar Nailarh,ita kuka Aunty Sophia kuka ga wani irin rawa da jikinta ke yi,jifa tayi da gun ɗin da gudu ta raɓa ta gefen Aunty Sophia ta nufi sama. zubewa Aunty Sophia tayi kan gwiwoyinta,bin bayan Nailarh miss Malika da sauran masu aikin su ka yi,kallo su Alex Aunty Sophia tayi tace su tafi hospital,ficewa su ka yi dashi har time ɗin jini ke zuba. tashi tayi tabi bayan su jiki a sanyaye dan taga halin da Nailarh take ciki,daga nesa ta hange su a home bar kasancewar glass wall ne a wurin,da sauri ta ƙarasa a tsaye ta same su sunyi cirko cirko idanunsu a kan Nailarh dake tsaye ta ɗaga kwalbar wine tana ɗurama cikinta. da mugun sauri Aunty Sophia ta faɗa ɗakin har tana bangaje wanda ke bakin ƙofa,a zafafe ta fisge kwalbar daga hannun Nailarh tayi jifa da ita nan take kwalbar ta fashe. “mi yasa ki ka yi haka sophia?,atlest idan tasha zata samu relief” Malika ta faɗa, ko kallon inda take Sophia bata yi ba kamar ma bata san tana magana ba,cikin raunannar murya tace “Nailarh idan rai ya ɓaci hankali baya gushewa,wannan abun da ki ke is not a solution,ko kin manta alƙawarin da ki ka yi man,mi yasa ki ke son maida hannun agogo baya,tell me mi ke damunki sai muyi solving matsalar tare???” cike da kulawa Aunty Sophia ta faɗa. hannu biyu Nailarh tasa ta kama kwalar rigar Aunty Sophia,zaro ido su kayi gaba ɗayan su da mamaki su ke kallon Nailarh,Aunty Sophia ma da tsantsan mamaki take kallon Nailarh. jijjigata Nailarh tayi cike da karaji tace “who is he,kalamanki na ranar da momy zata dawo sun tabbatar man dasa hannunki,tell me who's he??” ta ƙarashe maganar tana daka mata tsawa. wani irin mugun tashi hankalin Aunty Sophia yayi dan kwata kwata bata fahimci inda zancen Nailarh ya dosa ba “baby what are u talking about, please kiyi man bayani?” “i said who is he answer me” Nailarh ta faɗa tana wani zare mata ido, hawaye ne suka wanke fuskar Aunty Sophia,girgiza mata kai ta shiga yi “believe me Nailarh ban san akan mi kike magana ba” gani tayi ɗakin na juya mata ga wani irin ciwo da zuciyarta ke mata,dafe saitin zuciyarta dake barazanar faso ƙirjinta ta fito tayi tana faɗin “my chest”gaba ɗaya ta tafi zata faɗi da sauri Aunty Sophia ta riƙota jikinta,gaba ɗaya ta faɗa jikinta “please Aunty Sophia waye shi” Nailarh ta faɗa a hankali daga haka kuma bata sake cewa komai ba, jikinta ya saki alamar suma tayi. fashewa Aunty Sophia tayi da kuka kamar ƙaramar yarinya.. *Ya Allah mike shirin faruwa dake Nailarh,mi ya faru a N R T* *Back to N R T Dan muji abunda ya faru* Track ɗin a cike yake maƙil ,ta ko ina ka duba mutane ne zazzaune a mazauninsu da aka tanada,Track ɗin ya cika Masha Allah,mutane ne daban daban daga garuruwa daban daban wasu ma ba daga ƙasar su ke ba. kamar ko wane lokaci suna sanye da shirt da cap na track ɗin kamar yanda ya kasance al'adar wajen. daga gefe manyan baƙi ne da, wasu daga cikin ƙasar su ke wasu kuma daga wajen ƙasar,suna zaune a mazauninsu na musamman wanda akatanadar masu,miss Malika na cikin manyan baƙi ta ɗau wankan Sheath gown kamar wata yarinya kanta sanye da haɗaɗirya hat mai net daga gabanta anyi mata ado da bird feather,su luna na daga gefenta tsaye,kiɗa da bushe bushe ne ke tashi a cikin Field ɗin. dawaki ne aƙalla guda ashirin a cikin field ɗin,suna a killace cikin ɗan cage ɗin su a tsaye,kowa wane doki akwai mutum a saman shi,a shirye su ke umarnin fara gudu kawai su ke jira, Nailarh na daga tsakiyar dawakan saman dokinta. wani baƙin doki ne a hannun damanta sai sheƙi yake yana ɗaukar ido,kallon wanda ke kan dokin tayi,daga yanayin shigarshi ta fahimci sabon ɗan wasa ne dan komai nasa daban yake da nasu hatta suturar dake jikinshi da helmet ɗin dake kansa,sosai ta zuba mashi ido tana kallo, banda idanunshi bata iya hangen komai daga fuskarshi,saurin kauda kai tayi ganin yana ƙoƙarin juyowa alamar ya fahimci ana kallonshi,kallon inda Nailarh take yayi,kallon ƴan seconds yayi mata ya ɗauke idonshi. lokaci na cika aka basu damanr far gudu ta hanyar hura whistle,cike da karsashi dawakan su ka shiga gudu a cikin babban field ɗin, a tare su ka fara gudu abun gwanin ban sha'awa,sosai suke gudu kowa burin shi ya kai ga matsaya. rarrabuwa dawakan su ka yi,shidda su ka yi gaba yayinda aka bar sha huɗu a baya,dawaki biyu ne cikin shidda su ka yi baya a dalilin karon da su ka yi da juna,hakan yasa suka koma bayan huɗu yayinda sha huɗu ke biye da su,sosai Dawakai biyu dake cikin sha huɗun su ka dage har sai da su ka cimma biyun dake gaban su suka zama su huɗu, huɗu na gaba huɗu na tsakkiya sha biyu a baya. A wannan karan Nailarh ba tayi baya ba kamar na last wasan da su ka yi,tana cikin huɗu dake gaba,sosai ta dage dan ganin tayi nasara a wannan karon kamar ko yaushe. Mutane kowa sai baza ido yake dan ganin yanda wasan zai kwashe,da yawan mutane na fatan Nailarh tayi nasara kamar ko wane lokaci yayinda wasu ba haka bane a zuciyar su burin su ta faɗi ko za su rage raɗaɗin kuɗaɗen su da suke asara a wajen wasan, murmushi kawai miss Malika ke saki cike da ƙwarin gwiwa take kallon wasan ta san cin galaba akan babyn tata abune mai wahalar gaske. sosai su ka dage da gudun gashi har sun kusa isar ma matsaya amma dawakan nan uku na tare dana Nailarh, hankalin ta ne ya fara tashi ganin duk iya bakin ƙoƙarin da take dan ganin tayi masu zarra abun yaci tura, data ta samu ta kere masu sai su sake cimma mata. duka ta kaima king dan a ganinta sakacinshi ne yasa har ta kasa tsere masu,ganin dai idan ba tayi wani abu ba komai zai iya faruwa ne yasa cike da dabara yanda alƙalan wasan bazasu lura da abunda take ba ta matsa kusa da dokin dake kusa dashi,cike da mugunta taja igiyar dake jikin dokin ta tarɗe ƙafar dokin,mahayin dokin baiyi auneba ba sai jinshi yayi ya tafi ƙasa har ya shafi dokin dake kusa da shi,gaba ɗaya su ka kifa ƙasa daga su har dawakan nasu,nan su ka shiga birgima a ƙasa,hankali tashe mutane su ka shiga miƙewa ganin abunda ya faru. da gudu emergency officers suka shigo cikin Field ɗin ɗauke da stretcher,ɗaukar wanda su ka samu rauni su ka yi suka ɗaura a stretcher su ka fice da su,juyawa Nailarh tayi tana sakin wani wicked smile ko a jikinta,yanzu ya rage saura su biyu daga ita sai wannan baƙin dokin,tunda yaga abunda tayi ya kafeta da ido yana kallon ta cikin helmet ɗin dake kanshi, fingers biyu yasa yayi saluting ɗinta,tsuke fuska tayi tana kauda kai. haka aka cigaba da gabatar da wasan duk yanda Nailarh ta so yima wannan mai baƙin dokin mugunta kamar yanda tayi wacan abun ya faskara, ƙoƙarin kereta ma yake hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba gashi sun kusa isa Wining line,hankalin wasu daga cikin ƴan kallo ne ya fara tashi yayinda wasu ke fatan a karya tarihin N R T,ƙus ƙus ne ya fara tashi wasu na son sanin waye wannan dake neman yima Nailarh zarra dan da yawan mutane basu san shi ba. hankali Nailarh sosai ya ƙara tashi, zufa duk ta wanke jikinta,tun tana ganin abun kamar wasa sai ga dokin nan ya ƙetare Wining line kamar a mafarki,wani irin mummunan faɗuwa gabanta yayi ba shiri taci birki tana haki,abunda bata taɓa kawo ma ranta ba ya faru da ita,miss Malika ma zabura tayi daga inda take zaune tana kallon field ɗin. Ihu da sowa ne ya fara tashi a filin wasan, mutane da dama hakan yayi masu,da gudu securitys ɗin wajen suka shigo cikin field ɗin, tai maka ma duk mahayan dawakan su ka yi su ka sauko daga kan dawakan,tsaye Nailarh tayi a wurin kamar idol, ta kasa motsawa in a shock take kallon field ɗin dan har yanzu ta kasa yarda da hakan gaskiya ne. Murna wajen mutanen da su ka daɗe suna jin haushin Nailarh ba'a magana, dama da yawan su irin wannan ranar su ke fata gashi kuwa ta riske su. cikin field ɗin mutane su ka fara shigowa suna nufar wannan mutumin da har yanzu yaƙi cire helmet ɗin dake kanshi haka ma Nailarh,hannu mutane su ka shiga bashi suna taya shi murna wasu kuma na hugging ɗin shi. tunda ya sauka kan dokin idanunshi ke kan Nailarh ko ƙiftawa bayayi ganin mood ɗinta, walking majestically ya nufo inda Nailarh take still he's eyes on her kuma har time ɗin bai zame helmet ɗin dake kanshi ba,tunda ya tunkarota take kallon shi, yana da tsayi sosai dan ya kereta sosai duk da tana da tsayi, ƙaƙƙarfa ne na gaske yanada broad chest dan tana iya hangen shatin six pack ɗin shi ta jikin polo shirt ɗin dake jikin shi, ga wasu strong arms dake a murɗe, kallo ɗaya za kayi mashi ka gane gym product ne, bazaka iya tantance kalar fatar jikinshi saboda jikinshi dake a rufe. saurin ɗauke idonta tayi daga kallonshi tana tsuke fuska, har inda take ya ƙaraso, ɗan rissinawa yayi dai dai saitin kunnenta ya kai bakinshi, whisper ya shiga yi mata, bazaka iya jin mi yake cewa ba, a hankali yake magana kamar baya son buɗe bakinshi,wani irin kishi ne ya turniƙe miss malika ta tsani taga wani ya raɓi Nailarh, wani irin kallon wulaƙancin ta shiga binsu dashi zuciyarta na wani irin tafarfasa. sun kai five minute a haka kafin ya janye bakinshi daga kunnenta, saurin kallonshi Nailarh tayi, from head to toe yake kallonta ta cikin helmet ɗin kafin yayi saluting ɗinta a hankali yace “nice to meet u cutie,see u next time, have a nice day” ya faɗa yana ɗaga mata hannu,barin wurin yayi wani irin ƙara ɓaci ran Nailarh yayi. da sauri Luna da sauran maids suka nufota Miss Malika na bayan su, hannu luna ta kai da nufin cirema Nailarh helmet ɗin kanta, saukar wani irin azabebben mari taji,saurin dafe cheek ɗinta tayi tana kallon Nailarh data mareta,a masifance ta zame helmet ɗin kanta tayi jifa dashi, jiki na ɓari malika ta nufota, kafin ta ƙaraso Nailarh har ta bar wurin ta nufi motocin su maganganunshi na yawo a brain ɗinta. da sauri Alex ya buɗe mata back seat ko jiran su malika ba tayi ba tace ya kaita gida,Malika suna isowa suma motocin su suka shiga, da mugun sauri su ka bi bayan su Nailarh, a kusan tare su ka yi parking,ko gama daidaita parking driver baiyi ba Malika ta fito ta nufi Nailarh, tana isowa Nailarh na fitowa da gun a hannunta, hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba, saita kanta Nailarh tayi da gun ɗin da nufin shooting kanta. hakan ba ƙaramin sake ɗaga hankalin Malika yayi ba,umarni taba securitys da drivers ɗin dake wurin da su amshe gun ɗin, garin su amshe ne Nailarh ta harbi Alex. *back to story* Jijjigata Aunty sophia ta shiga yi tana kiran sunanta,miss Malika ma kamar za tayi hauka wajen kiran sunan Nailarh, ɗaya daga cikin chefs ne ya nufosu da ruwa, da sauri Aunty sophia ta amsa tana yayyafama Nailarh amma ko gezau ba tayi ba, tayi hakan kusan sau huɗu amma Nailarh bata farfaɗo ba,wani mummunan faɗuwa gaban Aunty sophia yayi haka ma miss Malika, tsoron kar ace ciwan Nailarh ne ya tashi ne ya mamaye zukatansu yaushe rabon da Nailarh ta samu Attack, dan suna kula da duk wani abun da zai ɓata ranta, komai ta buƙata yi mata su ke. *Nailarh tunda aka haifeta take fama da haert Attack infact ma dashi aka haifeta, shiyyasa duk wani abu da zai faranta ranta miss malika na ƙoƙarin yi mata shi,haka Aunty Sophia bata wasa da lafiyar Nailarh duk wani abu da zai faranta mata tana ƙoƙarin yi mata tana kumakiyaye abunda zai ɓata ranta bare harya kai da ciwonta ya tashisai ta yi mi bata samu Attack ba dan duk abunda take so a rayuwa shi take samu* hawaye su ka wanke fuskar Miss Malika, maids ɗin dake wurin wasu har sun fara zubar da ƙwalla Jijjigata miss Malika ta shiga yi tana faɗin “please Nailarh wake up, I promised u to punish this man and sai ya girbi abunda ya shuka,sai yayi daya sanin shigar shi gasar nan, please wake up dear” kamar mahaukaciya haka take jijjiga Nailarh tana roƙonta akan ta tashi,Aunty Sophia banda hawaye babu abunda take. “Please Nailarh, don't leave me, please wake up, I promised you, I promised u sai yayi daya sani,nayi maki alƙawarin zanyi mashi hukunci mai tsanani, don't leave me please wake up” Sosai take sambatu tana roƙon Nailarh,wani tausayin miss Malika ne ya rufe maids ɗin dan daga yanayin da take magana kamar bata cikin hayyacinta,da ƙar Aunty Sophia tayi ƙarfin halin faɗin “Ma'am,I think she's on attack” Aunty Sophia ta faɗa tana share ƙwalla ƙara rikicewa miss Malika tayi jin abunda Aunty Sophia ta faɗa. zabura tayi da nufin ɗaukar Nailarh “please tell Alex to bring the car, Sophia let's go to the hospital, I don't want to lose Nailarh” magana take tana ƙoƙarin ɗaukar Nailarh amma ta kasa,gaba ɗaya a gigice take har ta manta da abunda ya faru da Alex,da sauri luna ta fice dan sanar da NOAH saƙon miss malika,shima ɗaya daga cikin drivers ɗin gidan ne. da sauri William ya ƙaraso cikin ɗakin,hannu biyu yasa ya ɗauki Nailarh,a shoulder ɗin shi ya ɗaurata,gaba ɗaya jikinta ya saki kamar mattaciya,ficewa su kayi daga cikin ɗakin baki ɗaya,miss Malika kamar zata tashi sama,Aunty Sophia kuwa sai sharar hawaye take. NOAH har ya shiga Mota yayi mata key,jiran fitowar su kawai yake,back seat ɗin motar William ya saka Nailarh Aunty Sophia ta shiga kusa da ita yayin da miss malika ta shiga front seat,reverse yayi suka nufi main gate ɗin gidan, securitys ɗin ma shiga motocin su su ka yi harda su luna su biyu,bin bayan motar su miss malika su ka yi. komawa bakin aikinsu suka yi sauran securits ɗin da aka bari,cikin gida chefs ɗin su ka koma wasu na jimami yayinda wasu ke sharar ƙwallar tausayin halin da Nailarh take ciki. *Get well soon Nailarh,to be honest wannan bawan Allah baka kyauta ba😢* *ABUJA NIGERIA* *UNCLE MUTALLAF'S HOUSE* saukowa yake daga saman stairs, walking gently yake taka stairs case ɗin,white suit ne a jikinshi,waya ce kare a kunnenshi. “gaskiya I'm really happy yaya da wannan maganar,amma nayi mamaki da ban taɓa fahimtar hakan ba” saurin ɗaga kai mom fatilah dake zaune a parlor ita da Noor tayi tana kallon uncle mutallaf,kallo ɗaya za kayi mashi ka hango tsantsar farin cikin da yake ciki. cikin parlorn ya ƙaraso,ɗaya daga cikin sofas ya nufa ya zauna “wallah da gaske nake yaya ban taɓa lura da hakan ba,kuma kasan duk rashin kunyar Noor Bata taɓa faɗa man ba” da sauri Noor ta tashi ta nufi dadynta jin abunda yace,saurin kai kunnenta tayi jikin wayar wai ko za taji dawa dadynta ke waya. ture kanta yayi yana sakin dariya “kaji ja'iri wato shi mai kunya shine sai ya aiko maka abokinsa” ƴar dariya yayi yana gyara zaman shi “to shikenan in sha Allah zuwa goben sai muyi magana,amma gaskiya nayi farin ciki da hakan Allah yasa ayi muna da rai,amma Abbah da yayan sun sani kuwa?” ɗan jim yayi yana sauraron na cikin wayar can yace “ok to shikenan Allah ya kaimu sai na shigo goben in sha Allah” sallama yayi da wanda yake wayar “dady kai da waye ka ke waya?” Noor ta faɗa cike da shagawaɓa “kawunki ne, maza je part ɗina ki ɗauko man glass ɗina yana Nan kan nightstand” “to dady,amma maganar mi kuke kai dashi?” “idan kin dawo zan faɗa maki” saurin tashi tayi ta nufi stairs case da sauri, girgiza kai kawai mom Fatilah tayi. iska uncle mutallaf ya shaƙa tukun ya fisar,yayi ɗan shiru yana nazarin wani abu “lafiya dai Dr?” mom fatilah ta faɗa tana leƙen fuskar shi, ajiyar zuciya uncle ya sauke kafin ya kalleta “ya Ahmad ne ya kirani,kin san cewa Noor da Irfan soyayya su ke?” yana yin fuskar mom fatilah ne ya canza,tsuke fuska tayi “mi ya faru,kiran mi yake maka to?” “ya kirani ne ya sanar dani har ma sun tattauna maganar shi da su ya Ubaid, Abbah da ya Tahir ɗin ne kawai ya rage basu sanarmawa ba,amma yace zuwa gobe zai sanar da su dan a san yaushe ya kamata a sa bikin na su,amma fa nayi mamakin da ban taɓa lura da suna soyayya ba duk abun Noor ma bata taɓa sanar dani ba” tunda ya fara magana mom fatilah ta shiga binshi da wani kallon rainin wayau,Noor saukowarta kenan taji abun da dadyn nata ke furtawa,da gudu ta nufi ɗakinta ba tare da ta ko kawo masa glass ɗin da yace ta ɗauko mashi ba. “gaskiya naji daɗin haka,kinga kafin mu tafi sai a tsaida ranar Auren na su zuwa bayan sallah sai ayi bikin,yara nata ƙara mana daƙon zumunci,saura Yazdan fatana shima ya daina wannan shashanci ya zama mutumin ƙwarai kinga sai mu haɗa su shi da Yumnah” kallon mom fatilah yayi jin tunda ya fara magana ƙalla ba tace ba “naji kinyi shiru ba kice komai ba,magana nake kana Auren Noor f...” saurin katse shi mom fatilah tayi “dan Allah dakata Dr,wallahi sam ba zai yiwu ba” da mamaki yake kallonta bai taɓa tunanin wannan ce kalmar zata fito daga bakinta ba. “fatila kin san mi ki ke faɗa kuwa?” “na san mi nake faɗa kuma ina cikin hankalina,wannan haɗin sam bazai yiwu ba ni ba hajiya halima bace ko salima da ku ka nunama fin ƙarfi akan ƴaƴan su,ku ka nuna basu da right ɗin zaɓarma ƴaƴan su abokan zama,ni sam bazan ƴarda da wannan ba,babu ƴaƴana babu ƴaƴan Zulaihart period” kallonta kawai uncle mutallaf keyi cike da mamaki,ko a mafarki bai taɓa tunanin wannan amsar daga gareta ba,yayi matuƙar mamakin ta duk da ya san ba su jituwa da matar yayan nashi. “wallahi babu ƴaƴana babu ƴaƴan Zulaihart,haka kawai kuyita kwasar mana ƴaƴa kuna ba ƴaƴan Zulaihart sai kace ita kaɗai ke da ƴaƴa, gaskiya ni ban amince ba” “amma nayi mamakin jin haka daga gareki,banyi tunanin za ki yi haka ba,miye laifin Zulaihart ne da zaki ƙi son haɗa alaƙa da ita,ai ko dan ya Tahir da farin cikin ƴarki kin amince” tashi tayi daga inda take zaune cikin ɗaga murya tace “wallahi bazan amince ba,haɗa dangantaka da Zulaihart wallahi bazan yi ba,ai da Noor ke faɗa man na ɗauka shashancinta ne ai ban san abun da gaske bane da wallahi tuni nayi ma tufkar hanci,haka kawai kuyi ta haɗa mu da dangin yahudawa, wallahi tun wuri kace ma ƴan uwanka baka amince ba dan Noor bazata Auri Irfan ba” ta kai ƙarshen maganar tana huci “kin gama” uncle Mutallaf ya faɗa yana tsareta da idanu “ban gane na gama ba,haka kawai sai inƙi faɗin ra'ayina,kowace yarinya sai ku ɗauka kuba ƴaƴan Zulaihart haka akeyi,idan su hajiya halima sun amince saboda kwaɗayin abun duniya ni wallahi bazan amince ba” “Fatilah ina so ki san wani abu Noor da Irfan are my kids, ke baki isa ki sa na fasa abunda nayi niyya ba,Aure tsakanin Noor da Irfan Kamar anyi an gama ne in dai ni ne ubanta ba wani daban ba” ya faɗa a kausashe “lallai Dr zaka tafka babban kuskure in dai kace sai ta Auri Irfan” “kwarai kuwa,kije kiyi duk abunda ki ke ganin zaki iya amma Aure tsakanin Noor da Irfan Kamar anyi shi angama,ke baki isa kisa na zuba ma ƴan uwana ƙasa a ido ba,yanda aka yi na Naeem da Adnan lafiya haka za'ayi na Noor da Irfan sai dai kiyi duk abunda za kiyi” Kwashewa tayi da wata irin dariya“haka dai kace ko,za kuwa kaga abunda zan aikata” sosai saɓani ya shiga tsakaninsu akan wannan maganar. Noor lokacin data nufi bedroom ɗin ta,wayarta ta ɗauka tayi dialing number Irfan,har Kiran ya katse baiyi picking ba, sake kira tayi sai a na biyun ne yayi picking “hey beb, what's up?” ya faɗa daga cikin wayar “am really happy dear,yau dai ka cika alƙawari, i really really love u irin billions ɗin nan,i wish kana kusa da na baka warm hug of happiness”ta faɗa tana sakin dariya daga cikin wayar tana jin yanda ya sauke ajiyar zuciya “I would like that baby,but wait farin cikin mi kike?” “ban gane farin cikin mi nake ba,kana nufin baka sani ba?” “am serious dear ban sani ba” ɓata fuska tayi tana turo baki “bana son wannan wasan yaya” “am serious Qanwata ban sani ba” “yaya yanzu maganar Auren namuce baka sani ba” ta faɗa tana wani murguɗa mashi baki kamar irin yana kusa da ita ɗin nan “maganar Auren fa,a ina ki ka ji?” “yanzu naji dady na waya da Uncle Ahmad yana sanar dashi” ajiyar zuciya taji ya sauke “Alhmdllh, gaskiya naji daɗin jin haka,am really happy dear” dariya ta saki “wai da gaske ba kai ka faɗa mashi ba” “da gaske nake,i think Waseef ne ya sanar dashi” “amma naji daɗi ya Waseef ya faranta man shima Allah ya faranta mashi” “Ameen,yanzu shikenan beb mun kusa zama husband and wife” “yeah very soon we became husband and wifeee” ta faɗa tana jan wife ɗin,dariya su ka yi gaba ɗayan su, faɗawa tayi saman bed ɗin ta “gaskiya dole nayi ma ya Waseef kyauta yayi abunda ka kasa tsawan shekaru” a shagwaɓe yace “beb Ni fa kyautar” “taka special ce husband to be” “beb,Ina so mu haɗu Please” ya faɗa yana wani shagwaɓe murya kamar ƙaramin yaro “ka zo gida mana” “No beby kunyar uncle nake ji,kina so yace daga faɗa mashi har na fara mashi Zarya a gida” “kunya fa yaya,shi fa dady ba ruwanshi” “ni dai bazan iya zuwa ba beb,kawai ki nema mana inda zamu haɗu” “please Ni dai ka zo, ko a compound ne sai ka tsaya ba saika shigo ciki ba” “ok let me see idan zan iya zuwa” “zaka iya dear” cike da farin ciki su ka cigaba da waya,daga yanayin yanda su ke wayar zaka tabbatar suna cikin farin ciki,hayaniyar da taji ne yasa tayi saurin ce mashi tana zuwa, rejecting call ɗin tayi,da sauri ta sauka daga saman bed ɗin ta nufi ƙofar fita zuwa parlor,anan ta samu dadynta da momynta suna saɓani saboda Auren su. cikin parlorn ta ƙarasa,fashewa tayi da kuka “momy mi yasa za kice haka akan ya Irfan,gaskiya ki daina man wannan wasan” “sai na mareki idan ba kiyi man shiru anan ba shashasha”turo baki Noor ɗin tayi hawaye na bin cheek ɗinta “kowa na farin ciki sai ke ce zaki tsiro da haka,ni gaskiya ya Irfan nake so kuma shi zan Aura,haka kwai burinda na daɗe ina jira zaki wani ɓ...” bata ƙarasa ba saboda saukar marin da taji,da gudu ta nufi dadynta tana fashewa da kuka. “shashashar banza wacce bata san inda ke mata ciwo ba,ai da duk a zatona kina da hankali ashe sakaryace ke ban sani ba” “dady dan Allah karka bari ta rabani da ya Irfan” ta faɗa tana kuka “yi shiru Noor,karki wani tashi hankalinki ni ne dai dadynki ba wani ba,babu wanda ya isa rabaki da Irfan sai Allah,Irfan shine zaɓi na” tsaki mom fatilah taja “zaku sha mamakina daga kai har ita” tana faɗar haka ta nufi sama,hannu yasa ya shiga goge mata hawayen dake zuba. “yi haƙuri kukan ya isa haka,where is my glasses?” bedroom ɗinta ta nufa da sauri, glass ɗin ta ɗauko mashi,amsa yayi yana ɗan shafa kanta “karki damu kinji” gyaɗa mashi kai tayi,ficewa yayi daga parlorn ita kuma ta koma bedroom ɗinta ranta duk a jagule bata taɓa zaton haka daga momynta ba... *Uhmmm mom fatilah yada haka* *UNITED STATE❤* _*Las Vegas (Nevada)*_ Suna isa hospital ɗin nurses na turo stretcher,tun a hanya Mrs malika ta sanar da zuwan su,da sauri Noah ya buɗe masu back seat ɗin,kama Nailarh su ka yi su ka ɗaura a gadon,a gaggauce su ka nufi cikin hospital ɗin da ita,bin bayan su su Mrs malika su ka yi. Hospital ɗin yanda girma sosai,komai na cikin shi are expensive and extraordinary, parking lot ɗin su da reception ma kanshi abun kallo,sai ka kai wani kake iya jinya a hospital ɗin,manyan mutane ne ke Zarya a cikin shi. suna shiga reception nurses ɗin dake wurin su ka shiga gaishe da Mrs malika,da yawansu sun santa wa su kuma Nailarh su ka sani,ko kallon inda su ke ba tayi ba,kwata kwata hankalinta baya jikinta,Aunty Sophia nose mask ta amsa ta sa,har bakin emergency ward su ka bi nurses ɗin amma basu basu damar shiga ba,suna kallo aka shiga da Nailarh. doctors biyu ne su ka nufo Emegency ward ɗin,da sauri Mrs Malika ta nufe su,hannu kawai su ka ɗaga mata suna nufar Emegency ɗin a hanzarce. mazauninta ta koma tana dafe kanta dake mata barazanar fashewa,Aunty Sophia tunda ta zauna motsi ma na kirki ta kasa,sai dai time to time take goge hawayen da su ka ƙi tsaya mata,itama Mrs malika hawayen ne ke zarya a fuskarta,su luna ma banda hawayen babu abunda su ke. har 30 minutes su ka wuce babu wanda ya fito a cikin doctors ɗin sai ma wasu da suka sake shiga,hankalin Mrs malika da Aunty Sophia ba ƙaramin tashi yayi ba,after a hour su ka fito gaba ɗayan su,da sauri Mrs malika ta nufoso amma har sun bar wurin a hanzarce, ficewa su kayi zuwa compound ɗin asibitin,suna shiga compound wasu expensive rides guda uku na kunno kai cikin hospital ɗin. da sauri su ka nufi ride ɗin dake tsakiyar su, parking motocin su ka yi,motar dake gaba aka fara buɗewa wasu irin securitys Army's ne jibga jibgan dasu su ka fito kowanen su da gun a hannunshi ga wasu a soke a ƙugunsu haka motar dake baya,motar dake tsakiya su suka nufa,ɗaya daga cikin securitys ɗin ne ya buɗe back seat ɗin motar,a hankali ya zuro ƙafarshi dake sanye cikin leather shoes masu shegen kyau kafin ya fito gaba ɗayan shi,sanye yake cikin suit one of the world most expensive suit brand black color,sosai suit ɗin yabi shape ɗin jikinshi,he has a gym product body, fuskarshi a sanye take da face mask,sumar kanshi har saman neack ɗin shi yayi parking ɗin ta da baby ribbon black color. da sauri Drs ɗin su ka nufe shi,cike da girmamawa su ka shiga gaishe da shi,hannu kawai ya ɗaga masu yana nufar cikin hospital ɗin,da sauri nureses ɗin dake reception su ka miƙe,with full respect su ka shiga gaishe da su,babu wanda ya samu damar amsamawa sai dai ɗaga masu hannu da yayi,hannu ya sa ya shiga zame rigar suit ɗin dake jikinshi. Amsar rigar Suit ɗin Dr Daniel yayi,naɗe hannun longsleev shirt ɗin dake jikinshi yayi,da sauri Mrs Malika ta miƙe lokacin da su ka ƙaraso,ciki ya nufa tare da drs guda biyu,Dr Daniel ya nufi Mrs Malika. “Dr Daniel What's her condition now, has she recovered??” girgiza mata kai yayi “please ma'am garin ya haka ta faru,you know her problem more than anyone,duk wani emergency treatment mun bata but her body fought to accept it,her heart became very weak she's stop beating, I don't know why you are so careless that her heart is weak like that,I don't want to use a defibrillator because of her myocardial, but it is necessary” wasu hawaye ne su ka zubo daga idanun Mrs malika jin abunda Dr yace. “It's not my fault Dr,u know she's presenting a game at her Center,You know how she always wants to see her win in the game,here the problem happened,someone who we don't know where he is from, won her in the competition, shikenan ranta ya ɓaci har ya kaiga ta zamu Attack” ajiyar zuciya ya sauke “I didn't think that what happened will throw her into such a problem like that, but don't worry our Dr has arrived,she will get better, don't worry Nailarh will recover soon” da sauri Aunty Sophia ta miƙe tana nufar ƙofar Emergency ward ɗin,daga sama door ɗin ƴar madaidaiciyar glass window ce,tana iya hangen abunda ke ciki,sauke idanunta tayi akan Nailarh dake kwance saman Electrical bed,blue gown ce a jikinta sai ƴar cap dake saman kanta,hancinta a manne yake da oxygen. da sauri takai dubanta kan Dr dake tsaye gaban Ventilator machine,Dr daya shigo yanzu ne har ya ɗaura surgical gown akan kayan jikinshi hannunshi sanye da robber glove,inda Nailarh take ya nufo,oxgyen ɗin dake hancinta ya zare,defibrillator dake ajiye ya ɗauka,a saman ƙirjinta ya ɗaura,ɗaga defibrillator ɗin yayi gaba ɗaya Nailarh ta biyo abun,da sauri Aunty Sophia ta rintse idonta,sake ɗaura defibrillator yayi a ƙirjinta,gaba ɗaya bayanta ya rabu da bed ɗin,kasa jurar ganin halinda Nailarh take ciki tayi,da sauri tayi baya wani irin jiri ne ya kwasheta,daga haka bata sake sanin halin da take ciki ba sai farkawa tayi ta ganta a wani ward da drip a hannunta,kallon Nures ɗin dake zaune saman chair tayi,da sauri nurse ɗin ta nufota tana mata sannu,turo ƙofar ward ɗin akayi aka shigo,Dr Daniel ne da Mrs malika su ka shigo,da sauri Miss malika ta nufota. “sophia how do u feel now” da kallo kawai Aunty Sophia ta bita without saying anything to her,wani irin tausayinta ne ya rufe Mrs Malika ta san ita kaɗai ta san yanda take ji a zuciyarta,tana matuƙar son Nailarh ko ita da take mahaifiyarta bata mata kalar son da Aunty Sophia take mata. “sorry Sophia don't worry Nailarh will recover soon” kwantar mata da hankali Mrs malika ta shiga,amma um Aunty Sophia batace ba sai bin Mrs malika da take da ido,ita kanta malika daurewa take amma da tuni ta kai ƙasa. Ficewa su ka yi daga ward ɗin, da kallo kawai Aunty sophia ta bisu kafin ta maida dubanta ga nurse ɗin dake kula da ita “Nailarh,where is she?” ta furta a hankali, murmushi nurse ɗin ta sakar mata “let the drip end and I will take you to her” hawaye ne su ka zubo daga idanunta “please take me now, i need to see her” “I'm sorry, let it end,our Dr is around and ya hana a shiga wajenta yanzu, but we'll go later, I'm sorry” kwantar mata da hankali nurse ɗin ta shiga yi harta samu ta haƙura. Mrs Malika ce zaune a office ɗin Dr Daniel yana sanar da ita umarnin Dr da dalilin da yasa ya hana kowa ya shiga inda Nailarh take “But Dr.how I will not be able to see her until the next two days” “am sorry it's not my fault, it's our Dr's order” “amma da ai ina shiga, ko last zuwanmu da tayi one week a ICU ai na shiga, Why are you stopping me now?” “haka ne, time ɗin he's not around,but now babu tayanda zan kai ki wajenta,be patient na san data farka ke zata fara nema” “I'm really not happy. If you don't let me to see her, I'll take her to orphanage even if u don't discharge her.” “I'm sorry ma'am, he did that because of her health” “miye haɗinshi da ita da har zai hana mu relatives nata kula da ita” “nothing, he's just so kind,as long as he is in the hospital duk wani patient dake buƙatar special care shike kula dashi ko nurses baya bari” “wai miye alaƙarshi da Hospital ɗin ne ma” ɗan zaro ido dr daniel yayi yana kallonta “he's our CEO and he's the CMO of the entire USA,it's his hospital” jin jina kai kawai tayi tana lumshe ido without saying anything “ma'am u need to have some rest, ki tafi gida zuwa anjima sai ki dawo ko gobe,na san zuwa lokacin ta farka” “no bazan iya tafiya na bar Sophia ba, please ko ita ku bari taga Nailarh kunga halinda ta shiga saboda ita” “i will do something, but kina buƙatar hutu, dan da yiwuwar saina auna BP ɗinki dan zaiyi wuya ace jininki bai hau ba” “no need Dr,bari na koma wajen sophia” gyaɗa mata kai kawai yayi, ficewa tayi daga ɗakin zuwa ward ɗin da Aunty sophia take ciki, samunta tayi harta koma bacci, gefen bed ɗin ta nufa ta zauna,sannu Nurse ɗin dake wurin tayi mata, jinjina mata kai kawai tayi. Su luna ne su ka shigo su biyu hannunsu ɗauke da madaidaitan basket, tunda aka fito da Nailarh daga Emergency ward su ka koma gida tunda an hana kowa shiga inda take, besket ɗin hannunsu su ka ajiye, sannu su ka yima Mrs Malika,jinjina masu kai kawai tayi, sofa dake cikin ɗakin su ka nufa su ka zauna, jugum su ka yi kamar masu zaman makoki. *ABUJA NIGERIA* Magana yake amma taƙi ɗaga ido ta kalleshi balle yasa ran zata tanka mashi akan maganar da yake, shiru yayi yana kallonta,mug ɗin tea data haɗa mashi ta miƙa mashi,ƙin amsar mug ɗin yayi yana bin fuskarta da ido,kallonshi tayi,ajiyar zuciya ya sauke yana amsar mug ɗin ya ajiyeshi saman Table ɗin dake kusa dashi, kamo hannunta yayi cikin nashi “mi yasa nake magana ki ka yi shiru?” “mi ka ke so nace, hukunci ne da ku ka yanke kaida ƴan uwanka ni kuma miye nawa a ciki” “akan Auren ɗannaki ki ke faɗin haka?” “to ƴallaɓai mi zance, kun riga da kun gama yanke hukunci” “sai kisa mashi albarka kamar yanda ki ka yima sauran ƴan uwanshi” ajiyar zuciya ta sauke tana kallonshi “I won't hide it from you but honestly speaking I am not happy with this relationship hasalima ɗiyata nake mashi sha'awar Aure ba Noor ba” “nima nayi wannan tunanin barrister, amma da wanan maganar ta zo sai na barshi a haka Allah ya ƙaddara,haƙuri kawai za muyi” “gaskiya banyi farin cikin da haɗin nan ba, da da yanda za ai a fasa shi gaskiya dana so” murza hannunta dake cikin nashi yayi “mi yasa zaki ce haka barrister, ki sa mashi Albarka kamar yanda ki ka sa ma ƴan uawanshi, karki zamo uwa mai tauye farin cikin ƴaƴanta” “bazaka gane bane yallaɓai, kasan cewa fatilah ba ƙaunata take ba, she hates me completely,a gaskiya a wannan yanayin banason abunda zai tada man hankali,ka fi kowa sanin yanda akayi bikin Naeem, wane irin tashin hanlali ne ban fuskanta ba daga wajen hajiya Halima?, har yau na kasa manta cin mutuncin da tayi man, kawai na amince da Auren ne saboda Abbah, dan Allah kafin maganar nan ta kai gareshi ku dakatar da ita” tuni hawaye sun cika idonta duk wani abu da zai haɗata da su mamy a yanzu ba ƙaunar shi take ba “c'mom Zulaihart mi yasa za kiyi wannan tunanin, karki manta ba ita keda alhakin bada Auren Noor ba,ko ubanta bai isa ya hana wannan haɗin ba, Mustafa keda alhakin bada Aurenta kin kuwa san bazai taɓa hana Irfan ba” fashewa tayi da kuka “haba yallaɓai ka gane mana, mutanen nan fa ba sona su ke ba, miyasa kullum ku ke son haɗa alaƙa tsakanina da su” jawota yayi zuwa jikinshi, zaunar da ita yayi kan laps ɗin shi “ya isa haka miye na ku ka to,adu'a za kiyi mashi kisa mashi Albarka in sha Allah babu abunda zai faru sai Alkairi” “haka kawai yara suyita ja man abun magana, dan mi zasu maƙale sai ƴaƴan su, su ka ɗai ne ƴaƴa da bazasu nemi wasu ba” hannu yasa ya shiga goge mata hawayen dake zuba “ba nace ya isa haka ba, kiyi haƙuri in sha Allah babu abunda zai faru sai Alkairi, kuma yaran nan danƙon zumunci su ke ƙara mana,Don't forget that they are also my kids,my brothers kids, kuma idan dan saboda ƴarki ne bazaki amince ba karki manta ba shi kaɗai bane ɗanki, sai kiba yayansa” saurin kallonshi tayi “wa kenan ka ke nufi?” “ɗana mana ko bazaki bashi ba?” “tab ni gaskiya bazan ba SAM ba, yaronda ko mu ba mutuncin mu yake gani ba shi zanba ƴata, gaskiya A'a, to in bashi ma tayaya yaronda ma baya tare dani” “he will come back ai” “ni gaskiya bazan bashi ba koda yana so” “to shikenan sai kiba Naeem ko Adnan” “Allah ya kiyaye ƴata ta Auri mai mata” dady baisan lokacin da ya saki dariya ba jin furicin mom “ke nan bazaki iya ba mai mata ƴarki ba?” “ko da kuwa yana so, haka kawai da ƙananun shekarunta a hana mata zaman lafiya” “to ai shikenan, yanzu dai kin haƙura da maganar Auren Irfan ɗin ko?” turo baki tayi kamar ƙaramar yarinya “idan hakan Alkairi ne Allah ya tabbatar, idan kuma akasin haka ne shima ina fatan ya kasance Alkairi” dariya dady ya saki yan jan dogon hancinta “That's why I'm proud of u because of ur patience, i love u my baby katte” “ni karka sake kirana da wannan sunan” zaro ido dady yayi yana riƙe baki “ki rufa mana asiri idan ba so ki ke momy tace rashin kunyata ta kai har na canza maki sunan data sa maki ba, ko so ki ke tace na dawo mata da ƴarta?” dariya su ka saki gaba ɗayan su “momy, i luv her” dady ya faɗa, murmushi mom ta saki, wayar dady ce ta fara ringing tashi mom tayi ta miƙo mashi ita, duba sunan mai kiran nashi yayi, saurin nuna mata screen ɗin yayi, my friend ta gani,zaro ido tayi, murmushi dady ya saki yana picking call ɗin “hello, how are u” on the other hand na cikin wayar yace “am fine my friend,long time,how is ur family?” “they are fine,guess what?” dady ya faɗa yana kallon mom “what?” na cikin wayar ya faɗa, murmushi dady ya saki “I'm with ur daughter” “really, please give her the phone” murmushi ya sake saki yana miƙa ma mom wayar “hello uncle” “hi katte,how are u, where's my children??” “they fine,how was mom Natasha and james?” “their all fine” kallon dady tayi tana canza harshe zuwa Spanish,yanyin fuskarta ne ya canza zuwa tsantsar damuwa “El tío SAM todavía no cree que volverá?, su padre estaba muy preocupado” _Uncle har yanzu SAM bai amince zai dawo ba, mahaifin shi ya damu sosai_ ajiyar zuciya ya sauke “Él todavía no está de acuerdo, pero intentaré que venga a su fiesta de cumpleaños” _Har yanzu bai amince ba, amma zan yi kokarin sa shi ya zo da birthday ɗin shi_ “okay,El tío Irfan se casará” _shikenan,uncle Irfan zaiyi Aure_ “cuando! pero por qué no me lo dijiste?” _yaushe,amma miyasa baki sanar dani ba?_ “Ahora he's padre que me lo dice,but uncle, no me gusta la chica con la que se va a casar, pero él no me entiende” _yanzu dadyn shi ke sanar dani,amma uncle bana son yarinyar da zai Aura,amma yaƙi ya fahimce ni_ “Por qué no la amas?Quién se casará?” _mi yasa baki sonta, wacece zai Aura_ “tío es hija de su hermano menor, sabes que no todas las esposas de su hermano menor me aman, ella mother no me ama.” _Uncle ‘yar kaninsa ce, ka sani ba duka matan kanensa ke so na ba, mahaifiyarta ba ta so na._ “Irfan la ama y ella lo ama?” _irfan ɗin yana sonta,itama tana sonshi?_ “si se aman, solo que a su madre no le agradamos” _eh suna son juna, mahaifiyarta ce kawai bata sona ni da Irfan_ murmushi Uncle ya saki “No es nada, es la boda de Naeem y dices que su madre no te ama, y ​​se casaron y viven felices, no te preocupes, esto también estará bien” _karki damu,lokacin Auren Naeem ma haka ki ka ce mahaifiyarta bata sonki,kuma sunyi Auren suna zaune lafiya,karki damu shima wannan lafiya za'ayi_ turo baki tayi jin abunda uncle ɗin nata yace “uncle por qué siempre apoyas a Tahir?” _uncle mi yasa ko wane time ka ke goyan bayan Tahir ne?_ kallonta dady yayi jin ta ambaci sunanshi “No lo apoyo, cálmate y todo irá bien” _ba goyan bayansa nake ba,ki kwantar da hankalin ki komai zai tafi dai dai_ ƴar dariya yayi cikin hausar sa da sai a hankali yace “ke da nake so ki samar ma SAM mata anan” turo baki kawai tayi tana kallon dady without saying anything,zuba mata ido dady yayi har su ka kammala wayar, sallama tayi mashi tana miƙama dady wayar, kara wayar yayi a kunnenshi cike da zolaya yace “wato abun ƴar wariyar launin fata ce, shi ne za ku canza man yare dan kar naji abunda ku ke faɗa ko??” dariya Uncle Jonas ya saki, cikin hausarshi da bata gama daidaita ba yace “baruwana laifin matarka ne ita ta fara”dariya dadyn ya saki, sun ɗan jima suna waya kafin su ka yi sallama, kallon mom dady yayi “maganar mi ki ka yi mashi?” “i talk to him about SAM and Irfan's marriage” “shine sai kin canza harshe dan kar naji” “ai kaine ka ƙi ka koyi spanish” “it's too hard, that's why” murmushi kawai mom ɗin tayi. *UNITED STATE❤* _*Las Vegas (Nevada)*_ Around 10pm Miss Malika ta koma gida, saboda jikinta daya rikice dan sosai jininta hau,Dr Daniel ya so ya bata gado amma tace A'a, magunguna kawai ya bata,da baza ta tafin ba ma sai dai dan ganin har time ɗin Nailarh bata farka ba ne yasa ta tafi, Aunty sophia ma har time ɗin bacci take. bayan tafiyar Miss Malika da 30 Minutes Aunty sophia ta farka,luna na kan sofa tana bacci,da sauri Nures ɗin dake kula da ita ta nufo bed ɗin ganin tana shirin sauka “sorry,how do u feel now?”kallonta Aunty Sophia tayi “Nailarh,Please take me to her place,I want to see her” ajiyar zuciya nurse ɗin ta sauke kafin tace ok,ficewa tayi daga ward ɗin,bayan kamar five minutes sai gata ta dawo. kallon Aunty Sophia tayi “we can go” kamar jira take tace haka,da sauri ta shiga ƙoƙarin sauka daga saman bed ɗin, taimaka mata tayi ta sauko,slippers ɗin dake bakin bed ta zura a ƙafarta,ficewa su ka yi daga ward ɗin, direct office ɗin doctor Daniel su ka nufa. A bakin ƙofa su ka tsaya,nocking nurse ɗin tayi kafin aka basu iznin shiga,tura ƙofar tayi ta shiga Aunty Sophia na biye da ita,a zaune su ka samu Dr Daniel yana duba wasu files dake gabanshi,cikin office ɗin su ka ƙarasa,sallamar nurse ɗin yayi,ficewa tayi daga office ɗin,kallon Aunty Sophia yayi da tsantsar kulawa yace “how do u feel now?” “am feeling better, please Dr I need to see her” jinjina mata kai yayi kafin,ya ɗauki landline ɗin dake ajiye kan table ɗin shi,wasu numbobi yayi dialing,kara wayar yayi a kunne bayan anyi picking,alfarma ya shiga nema kan a bar ta taga Nailarh,Aunty Sophia dai na kallonshi,can ya katse wayar,miƙewa yayi yana faɗin“we can go” Ficewa su ka yi daga office ɗin zuwa ward ɗin da Nailarh take,Ward ɗin tsit yake baka ganin gifcin kowa sai na nurses jefi jefi,da kallo kawai Aunty Sophia ke bin wurin,a bakin ƙofar wani ɗaki su ka tsaya, nocking Dr yayi kafin aka bashi iznin,ƙofar ya nuna ma Aunty Sophia yana barin wajen. tsaye tayi ta kasa shiga sai kallon ƙofar take,rabinta glass ne kana iya hangen cikin ɗakin,ɗan leƙa cikin tayi,ba komai yasa ta kasa shiga ba sai fargabar halin da za ta ga Nailarh,a hankali ta shiga bin ɗakin da kallon kafin ta sauke idonta a kan Nailarh dake kwace,yana daga tsaye bakin bed ɗin ya ɗan rissinar da kanshi saitin fuskarta,still face mask ne a fuskarshi,sosai ya zuba mata ido kafin ya ɗan lumshe idonshi yana motsi da bakinshi kamar mai shirin furta wani abu,can ya buɗe idonshi,tafukan hannayenshi ya kai saitin baƙin shi,da alama Adu'a yayi mata kafin ya shafa mata a fuska,still da oxgyen a hancinta,Aunty Sophia dai na tsaye da tsantsar mamaki take kallonshi,to miye hakan yake ma Nailarh. a hankali ya ɗago da kanshi yana kallon ƙofar jin anyi nocking kuma ba'a shigo ba,da sauri Aunty Sophia ta turo ƙofar ta shigo,tashi yayi daga bakin bed ɗin ya nufi Ventilator machine,cikin ɗakin ta ƙarasa,a bakin bed ɗin Nailarh ta tsaya,wani irin tausayin Nailarh ne ya rufeta,tuni hawaye sun cika idonta,saurin kamo hannun Nailarh tayi cikin nata,hannunta ɗaya ta kai ta shafa fuskar Nailarh, muryar shi ta tsinkaya a cikin kunnenta“how was ur body,I hope u feel better now??” ya furta without looking at her dubanta ta kai gareshi,haka nan muryarshi tayi mata kama da wacce ta sani,a hankali tace “am feel better”jin jina kanshi yayi,kafin ya ɗauki wa su pepars ya fice daga ɗakin baki ɗaya,da kallo kawai Aunty Sophia ta bishi har ya fice,dubanta ta kai ga Nailarh dake fitar da numfashi a hankali,kwantar da kanta tayi saitin kanta tana jin wani iri a zuciyarta,ji take inama zata iya yaye mata ciwan,cike da tausayi take kallon Nailarh har bacci ya sake ɗaukarta ba tare da ta sani ba. Miss malika lokacin data koma gida,wanka ta samu tayi da ƙyar chefs su ka samu tasa ma cikinta wani abu kafin tasha magani,kwanciya tayi duk da ta san da wuya bacci ya ɗauketa,hakanan dai ta kwanta ta lumshe idonta,wani iri take ji a zuciyarta ga tsanar wannan bawan Allah da tayi mata kane kane a ƙahon zuciya,tun tana hospital ta bada umarnin a kawo mata shi ko a ina yake ,har yanzu ba taji feedback daga gare su ba,ta ɗau alwashin sai tayi mashi azaba mai raɗaɗi saboda halin da ya jefa Nailarh a ciki,sosai ta lula duniyar tunani, ringing ɗin wayarta ne ya dawo da ita daga duniyar tunani, ajiyar zuciya ta sauke tana ɗan jan tsaki dan a yanda take bata jin zata iya waya da kowa,jawo wajar tayi da nufin rejecting amma ganin sunan mai kiran nata ne yasa ta fasa, picking call ɗin tayi tana ɗan tsuke fuska,kara wayar tayi a kunne ba tare da tace ƙomai ba,on the other hand na cikin wayar yace “hello wife” ɗaure fuska tayi“don't ever call me with that name again” ajiyar zuciya ya sauke “i know u are angry with me,am so sorry,where is my baby?” rai ɓace tace “which baby,dama kana da baby ban sani ba?” “u know who I mean,where is Nailarh” tsaki taja “Nailarh da baka damu da ita ba ko wa?” “am sorry Malika,U know I love her and I care for her” “a yaushe ka ke son nata,tunda kayi ma US ƙaura ka taɓa kira dai dai da rana ɗaya kace naba Nailarh ko ka tambayi lafiyarta?” “am sorry Malika,kinfi kowa sanin yanda Nailarh ke treating ɗina, Nailarh Bata so na Bata san gani na a tare dake,Ni kuma da shekaruna da matsayina bazan zauna yarinya ƙarama ƴar cikina na treating ɗina like that ba” “Nailarh yarinya ce danmi zaka biyeta?” “to ai kema harda laifinki,kema nunawa ki ke tafini a wajenki,kulawar da ki ke bata tafi ƙarfin ta uwa da ƴa” “kaima ai kanada wanda ka nuna sunfini mahimmanci a rayuwarka,tunda na bar Australia baka sake ɗaga waya ka kirani ba almost 5 days kenan,kana can wurin matarka wacce duniya ta shida Aure tsakanin ku” “ba haka bane Malika,ni ban fifita kowa sama dake ba” “haka ne mana,ko dan babu ƴaƴa tsakanin mu yasa baka ɗauke ni da mahimmanci ba” “ko ɗaya Malika,kiyi haƙuri na san nayi kuskure amma na maki alƙawari hakan bazata sake faruwa ba,yanzu ina Nailarh ina son magana da ita” “she in serious sick, she had an attack” “what,attack” ya faɗa cikin tsantsar tashi hankalinki,ɗaga mashi kai tayi kamar yana a gabanta“amma taya hakan ta faru?” kaf ta kwashe abunda ya faru a N R T da yanke jikin da Nailarh tayi ta faɗi ta faɗa mashi “zan shigo US ɗin next week,Ina mata fatan samun lafiya” “mi yasa sai next week,kai da nayi tunanin zaka ce gobe” “akwai wani ɗan issue ne nan da ya riƙe ni,kiyi haƙuri zan shigo next week ɗin” “shikenan” “yanzu a wane hali Nailarh take ciki?” “har yanzu bata farka ba” “ok idan ta farka let me know” “ok I will let u know” sun ɗan jima suna waya kafin su ka yi sallama. Aunty Sophia sosai bacci ya ɗauketa a ward ɗin da Nailarh take,nurse ɗin dake kula da ita ne ta shigo ward tashinta tayi daga bacci ta sanar da ita Dr yace a bar Nailarh haka ta koma ɗakinta,ba dan ta so ba ta tashi, kissing forehead ɗin Nailarh tayi kafin su ka fice. *ABUJA NIGERIA* “amma gaskiya abun nan ya bani mamaki da haushi,Irfan ya rasa wa zai so sai Noor Fisabilillahi,to wai ma mi ya gani a jikinta da har yayi sha'awar Aurenta,yarinyar da kwata kwata bata da tarbiyya” mom Maryam ta faɗa rai a ɓace, ajiyar zuciya mom ta sauke “ni ba ma duk wannan ba,Hajiya Fatilah kin san halinta,kwata kwata bata da mutunci,ina tsoron duk wani abu da zai hanani zaman lafiya,anyi na Naeem ya wuce gaskiya yanzu bazan iya ɗaukar tashin hankalin dana ɗauka lokacin Auren Naeem ba” “ni wallahi da ki ka kira kina faɗaman ban ɗau maganar mai mahimmanci ba sai da yallaɓai ya dawo yake faɗa man,haba dan Allah sai kace Idanun Irfan ɗin rufewa su ka yi ,ga ƴaƴan arziƙi ya rasa wacce zai so sai Noor” “dama ya san bazan amince ba bai taɓa faɗa man ba,sai dai ya samu iyayenshi ya faɗa masu” “ya san zaki hanashi ne,amma duk da haka ya kamata ayima tufkar hanci tun kafin maganar ta kai ga Abbah dan Noor ba mace da zai sha'awar zaman Aure da ita ba ne” “babu yanda ban nunama janar ba amma yaƙi fahimtata,saima gani yake saboda ƴata yasa naƙi amincewa” “shi dama bazai ƙi amincewa ba saboda ƴar ɗan uwan shi ce,kuma duk abunda za kice gani zaiyi kin ƙi ƴan uwanshi,amma maganar gaskiya Irfan bai yima kanshi zaɓi na gari ba” “ni yanzu tashin hankalina abunda zai biyo baya idan fatilah ta sani” “karki wani tashi hankalinki, mata ta hana maki zaman lafiya,in sha Allah ma wannan Auren bazai yiwu ba,zan ga Irfan ɗin ne” *Tashin sense Irfan da Noor wane irin rayuwa ne wannan kowa baya farin ciki da Auren ku?* A kishingiɗe take saman rug carpet da ke katafaren parlorn ta,shigar alfarma ce a jikinta kamar koda yaushe, fuskarta tasha makeup kamar wata amarya,hannunta riƙe da fork tana shan fruit salad,time to time take sakin murmushi kamar wata zautatta,bakomai ke sata nishaɗin nan ba sai time ɗin da su ka ɓata ita da barrister hashim, wani irin shauƙi take ji, ji take inama ace sun dawwama a lokacin,ta ƙosa komai yazo ƙarshe su kasance a inuwa ɗaya,tundaga main parlor ɗinta taji ana kwaɗa sallama kamar tashin hankali. zambur ta miƙe tana dafe saitin zuciyarta dan baƙaramin tashi hankalinta yayi ba, mom Fatilah ce tare da mom halima da ƙanwar mom Fatilah hajiya zainab su ka faɗo parlorn kamar an jehosu, da sauri mamy taja baya tana faɗin “innahu min sulemanu wanna innahu bismillahi, ku kuma daga Ina haka abu kamar tashin duniya?” “wallahi yau tashin duniyar ne ma za'ayi” hajiya zainab ta faɗa, gwalo ido mamy tayi waje jin furucin hajiya zainab “Auzubillahi, mi yafaru?” “miyema bai faru ba, zuwa za kiyi muje part ɗin waccan dangin sheɗan ɗin, yau wallahi sai mun nuna mata tantagaryar rashin mutunci” a cewar mom halima “yo ni naga jaraba,shegun ƴaƴanta kowane mai tashen balaga daya ta so sai ya liƙe ma ƴaƴan mu dan mi baza taje can danginta ta nema masu Aure ba sai ƴaƴan mu saboda son zuciya” a cewar mom Fatilah “to fa mi zulaihart ɗin tayi ne wai?” mamy ta faɗa “ok bama ki san mi tayi ba”a cewar hajiya zainab “A'a ban sani ba” “idan munje can za kiji”mom halima ta faɗa, da sauri mamy ta nufi mayafinta dake kan sofa ta rufe gashin attachment ɗin dake kanta tana faɗin “ai ko dan naga yanda fuskar ƴar banza zatayi naje, muje mutanena ku nuna mata bakin rijiya ba wajen wasan makahu bane” “wallahi yau sai ta yaba ma aya zaƙinta” hajiya zainab ta faɗa, ficewa su ka yi daga part ɗin kamar za su tashi sama... *A dai yi a sannu mamy* “please sister Yumnah ki faɗa man, wallahi ina so na sani ne amma ba dan wani abu ba” Nainarh ta faɗa tana kallon Yumnah dake mata dariya “saifa kin faɗaman dalili,sannan zan faɗa maki” “kawai dan kinga na damu da na sani ne ki ke jaman aji tun jiya”tun jiya take fama da ita ta faɗa mata waye amma sai ja mata aji take wai ta gano da kanta yar dariya Yumnah tayi “na tambayeki miye dalilin da yasa ki ke son ki sani kinƙi faɗaman gaskiya” “haba Yumnah kema kin san babu wani dalili dayasa nake son sanin waye” “ban yarda ba dan ina lure dake” “shikenan tunda haka za kice,banama son ki faɗa man,zan tambayi dady shi na san bazai ƙi faɗa man ba,ke kuma kar Allah yasa ki faɗa man”ta faɗa yayinda take sauka daga saman bed ɗin “yanzu ke sai ki tambayi dady?” “sosaima kuwa” Nainarh ta faɗa tana murguɗa mata baki “lallai abun naki azimun ne” juya mata ido Nainarh tayi tana nufar dressing room ɗin su,da sauri Yumnah ta jawo hannunta “sorry,kema kin san zan faɗa maki,kawai ina son ganin react ɗinki ne,ai ban san haka ki ka damu ba”fisge hannunta tayi “ni sakar man hannu,banaso ki riƙe kayanki” da sauri Yumnah ta sauka daga saman bed ɗin tana kamo hannunta “sorry zan faɗa maki ba sai kin tambayi dady ba”tsuke fuska Nainarh tayi “nace maki bana so” “ke wallahi sai kin saurareni,dallah can kawai” Yumnah ta faɗa tana murguɗa mata baki, murmushi Nainarh ta saki ganin yanda Yumnah ta murguɗa mata baki,jan hannunta Yumnah tayi,cikin ɗakin su ka nufa,zama Nainarh tayi kan bed, laptop ɗinta dake ajiye saman Nightstand dake chaji ta jawo,kunnata tayi,zubama laptop ɗin ido su ka yi harta gama searching, murmushi Yumnah ta saki lokacin da tayi ido biyu da photonshi dake wallpaper system ɗin,hannu tasa tana shafa kyakkyawar fuskarshi,kissing hannuta tayi tana shafa lips ɗinshi,da mamaki Nainarh ke kallonta ta rasa mike damun Yumnah duk ta buɗe system ɗinta sai tayi haka,ita dai in ba idanunta ne basa gani sosai ba kamar ba musulmi ba,shiru dai tayi ba tace komai ba tana kallon Yumnah,gallery ɗinta ta shiga,turama Nainarh system ɗin tayi yayin da ta shiga wata folder,zuba ma system ɗin ido tayi har ya gama loading,fotunanshi ta gani kamar an jehosu harda na part ɗin dady dama wasu daban,saurin kallon Yumnah tayi, murmushi ta sakar mata tana ɗage mata gira ɗaya “kin san waye?”girgiza mata kai tayi alamar bata sani ba,yar dariya Yumnah tayi “to wannan ba kowa bane face shalelen dady ya SAM kenan” bata yi mamakin jin cewa SAM ne,dan tunda taga photo a part ɗin dady da yanda Yumnah ke ja mata aji ta fara zargin shine,sai gashi zarginta ya tabbata “ya SAM” ta furta a hankali,jinjina mata kai Yumnah tayi,wani irin ƙayataccen murmushi ne ya bayyana a fuskarta ba tare da ta shiryama hakan ba,kallonta kawai Yumnah take ba tun yau ba take zargin akwai wani abu a zuciyar Nainarh game da yayan nata dan kusan kullum ne sai tayi mata maganar shi,maida dubanta tayi kan system ɗin,a hankali ta ɗaura hannunta kan keyboard ɗin kamar mai tsoron taɓawa,cikin photo ɗaya ta shiga,ɗaya bayan ɗaya ta shiga kallon pics ɗin,zuba mata ido Yumnah tayi tana sakin murmushi,sosai ta shagala da kallon pics ɗin wasu a cikin mota aka ɗaukeshi,wasu yana a cikin jirgi wasu a gym room ne,mafi yawan photo an ɗauke su ne ba tare da sanin shi ba,duk kyan photon babu wanda aka ɗauka yana dariya,fuskarshi a ɗaure take sai dai hakan bai ɓoye kyawun fuskarshi ba. saurin janye system ɗin Yumnah tayi tana faɗin “kallon ya isa haka baby,karki cinyeshi mu shige su” da sauri ta kalli Yumnah can kuma ta saki murmushi tana kifa kanta saman pillow,dariya Yumnah ta saki tana leƙa fuskar Nainarh “wai kunya ki ka ji”sake ɓoye fuskarta tayi da pillown,hakan da tayi ba ƙaramin sa Yumnah nishaɗi tayi ba,dan sosai take mata dariya tana ƙoƙarin zame pillown data cusa fuskarta,dariya take itama Nainarh tana sake ɓoye fuskarta a jikin pillown. hayaniya su kaji sama sama da yake ƙofar bedroom ɗin a buɗe take,da sauri Nainarh ta ɗago tana kallon Yumnah,sauka Yumnah tayi daga saman bed ɗin tana nufar ƙofar fita,da sauri itama Nainarh ta sauka daga saman bed ɗin tana bin bayanta,turus su ka tsaya a parlorn mom suna kallon su mom fatilah daketa fama ɗura ashar kamar wasu maguzawa,mom da mom Maryam na tsaye bakin ƙofar bedroom ɗin mom su na kallon su “ehe warning nake bige maki,tun wuri Irfan ya fita harkar ƴata, idan har ta hanyar halak ki ka haifesa ba shege ne shi ba daga yau ya rabu da ƴata,inba ma jaraba ba ko wane shege daya ta so bashi wacce zai maƙalemawa sai ƴaƴan mu,idan abun arziƙi ne dan mi bazasu nemi danginki ba sai ƴaƴan mu,to wallahi tun wuri ya fita safgar ƴata dan ban haifama wani ƙaton banza dangin nasara masu jan kunne dangin sheɗan ƴata ba ehe,ƴata tsarkakakkiya ce gaba da baya,babu ta idan take da abun faɗe,jinin musulunci ce gaba da baya ba sabbin tuba ba”tunda mom fatilah ta fara zazzaga rashin mutuncinta babu wanda yace mata ƙala daga mom har mom Maryam da mamaki ya gama kasheta,jikin Nainarh duk ya yayi sanyi,wani irin tausayin mom ne ya rufeta, Yumnah tuni ƙwalla sun cika idanunta dama ta san dole hakan ta faru muddin mom fatilah ta san da maganar soyayyar Irfan da Noor “idan ba so ake mu shuka rashin mutuncin da har a koma ma Allah ba'a manta damu ba to tun wuri yaje can ya nemi wata,amma ba ƴar mu ba”hijaya Zainab ta faɗa tana wani jijjiga jiki “wallahi har gobe takaicin haɗa zuri'a nake da wannan dangin sheɗan ɗin,dan da yanda zanyi da wallahi ba'ayi Auren Nafisat da Naeem ba,har gobe Adu'ar abunda zai tsige wannan tsinanniyar igiyar Auren nake” mom Halima ta faɗa cike da takaici “wallahi ke ki ka so,Ni ba'ayi ɗan iskan da zaiyi man wannan ba,dan wallahi ko ubanta bai isa ba bare wani can ƙanin ubanta da ko kallon banza bai ishe ni ba” a cewar mom fatilah, kwashewa mamy tayi da wata ƴar iskar dariya tana guɗa kamar zata fasa parlorn “musluncin rahama ne”ta faɗa tana wani rausaya kai “duk kun gama ƴaƴan malamai jikokin malamai,mahaddata Alqur'ani,masu tafiya harrufa na zuba?” mom Maryam ta faɗa,kyaɓe baki MOM halima tayi“A'a uwar mu ke muke jira” Hajiya Zainab ta faɗa,tsawa mom maryam ta daka mata rai a ɓace “kee dakata tsaya matsayinki da yayarki nake dan ke baki isa nayin dake,dan ko kallon banza baki ishe ni ba” shewa su ka yi kamar wasu karuwai suna tafa hannu, girgiza kai Nainarh tayi a ranta tana faɗin “tayama Noor za tayi tarbiyya bayan mahaifiyarta ma ba ita gareta ba,sai yanzu ta fahimci ta inda rayuwar Noor ɗin ta samu matsala,tausayi ma uncle mutallaf da Ubaid su ka bata dan ance mace ta gari jarice amma su kam ba suyi dace ba” “da ku ka zo kuna cika ma mutane kunne da hayaniya sai kace wasu ƴan dandi, a haka Musluncin da ku ke iƙarari yake?,inji dai duk wannan hauragiyar da haukan kuna yi ne akan Noor,to me Noor ɗin take dashi da har namijin arziƙi zaiyi fatan kasancewarta uwar ƴaƴanshi,mi Noor ɗin take dashi banda tsagwaron rashin tarbiyya da jahilinci???”mom Maryam ta faɗa tana bin su da idanu “ke Hajiya Maryam tsaya matsayinki,ba dake muke magana ba da ita muke,kuma da ki ke magana,idan har bata da tarbiyya mi yasa ɗan naku ya maƙale mata,yaje ya nemi mai tarbiyya mana” a cewar mom Halima, murmushi mom Maryam ta saki tana girgiza kanta “bari ku ji na faɗa maku,babu wacce a cikin ku ta kai matsayin da Zulaihart za tayi musayar baki da ita,Aure tsakanin Noor da Irfan tun kafin zuciyarki ta raya maki kizo kiyi rashin mutunci ki sake tabbatar ma da Uwarshi ba'a baki tarbiyya a gida ba bare har kiba taki ƴar tayi ma tufkar hanci,ki sani tasan darajar ɗanta baza ta so abunda zai ruguzar rayuwar shi ba,Noor ba Macen arziƙi bace da za'a so haɗa alaƙa da ita,dan haka ku tattara ƙafafuwan ku kufuce ku ba mutane wuri” “kan bala'i lallai Hajiya Maryam,ke har kin isa ki faɗama mana haka,idan ba macen arziƙi bace uban mi yasa ɗan nata ya maƙale mata,wato an baki kin tada kai har kinyi ƙwarin shiga gaba, wallahi kinji kunya” a cewar mom Halima “wannan ku ta shafa,mara tarbiyyar ƴar ku dai bata gurbi anan sai ku ƙara gaba,gayyar tsiya” carb Mamy tace “shishshigi shiga dangin miji da gana masgo,shi ɗan naku da ku ke cika baki tarbiyyar gareshi,yaron da duk daran Allah yana yawan mashaya,kullum idon shi akan tsiranci yake,ko da yake ba baƙon abu bane a wajen Uwarshi bare shi”tunda mamy ta fara magana gaban mom ya faɗi ta rasa miyasa duk wani abu ya haɗasu saita danganta Irfan da yawan mashaya abun yana ɗaga mata hankali,juyawa Yumnah tayi da gudu tana fashewa da wani sabon kuka “ko kwana yake a cikin kwalbar giya ba mashaya ba,ƴarku dai nan ƙwalelenta,tai makon da aka yi ma na baya bazata samu ba” mom Maryam ta faɗa,wani irin mugun ɓaci ran mom Halima yayi wato da ƴaƴan su take Sosai su ka shiga musayar baki kamar zasu kaima juna duka, maganganu su mom Fatilah ke faɗa ma mom amma ƙala batace masu ba mom maryam ke aikin maida masu da maratani, Nainarh tausayi ma su ka bata su duka,kowa na ƙoƙarin ganin ya kare nashi, kowa iƙirarin nasha nada tarbiyya yake, to ita dai a iya fahimtarta da Noor da Irfan ɗin bataga wani wanda yafi wani tarbiyya ba amma suna cecekuce da junansu, a ganinta barinsu su Aure juna kamar rufin asirinsu ne baki ɗaya dan tayi imani kaf a cikin iyayen su babuwanda yasan kalar soyayya da su ke. “da ki ke tada jijiyoyin wuya mi yasa ke baki haifa mata mai tarbiyyar ba, kinga ai da sai ki bashi ƙarewa shigema uwarshi faɗa”mom fatila ta faɗa tana kallon mom Maryam, ƴar dariya mom Maryam tayi “mai tarbiyya dai sai mai tarbiyya, dan haka kija gayyar tsiyar ki ku ba mutane wuri ko wallahi nasa ayi waje da ku”mom maryam ta faɗa “ke har kin isa kisa a fitar damu, karki manta yanda yake gidan mijinta haka yake gidan mijina, ke kinyi kaɗa kisa a fitar damu wallahi” mamy ta faɗa tana huci “dallah jacan kilaki kawai” mom Maryam ta faɗa tana aikama mamy da harara,da mugun gudu mamy tayo kanta dan ranta ba ƙaramin ɓaci yayi da kalaman mom Maryam ba,bata ƙarasa gareta ba a dalilin muguwar tsawar da aka daka masu,babu ƴan hanjin cikin wanda basu kaɗa ba a cikin su dan Nainarh barin wajen tayi ta nufi wurin Yumnah,gaba ɗaya su ka kai dubansu ga dady, uncle Mustafa, uncle hashim,ya Naeem da ya Adnan da sun ɗan jima da shigowa parlorn,kusan rabi da kwatar faɗan a kunen su,kallo ɗaya mom tayima dady ya kafeta da idanu ta nufi bedroom ɗinta,juyawa mom Maryam tayi zata bita,wata irin gigitacer tsayawa wacce tafi ta ɗazu uncle Mustafa ya dakata mata “zo ki wuce kafin ranki ya ɓaci” “zan ɗau jakana ne” tsawa ya sake daka “i said get out” ƙofar fita kawai ta nufa ba tare da ta ɗauko jakar ba. murmushin mugunta su mamy su ka saki dan hakan da Uncle Mustafa yayi ba ƙaramin daɗi su kaji ba,tsuke fuska yayi fiye da ɗazu yana kallon su mamy “U,what are u waiting for,get out before i deal with you” da sauri sumi sumi su ka nufi ƙofar fita dan ba ƙaramin shakkarshi su ke ba ko mom fatilah dake cika bakin ko uban Noor bai isaba bare wani can ƙanin ubanta ta faɗa ne kawai dan ba'a gabanshi bane ba,yanzun ma Adu'a take Allah yasa baiji lokacin da tace hakan ba dan ba su kaɗai ba hatta ƴan uwanshi shakkarshi su ke,kallon dady yayi, tsantsan ɓacin rai ne kwance a fuskarshi,haka su ya Naeem babu wanda ranshi bai ɓaci da wannan abun da su mamy su ka yi ba,kallon ya Adnan uncle Mustafa yayi yace ya ɗauko mashi jakan mom Maryam dake ɗakin mom,da to ya amsa mashi yana nufar bedroom ɗin mom,fitowa yayi da jakan a hannu,amsa uncle Mustafa yayi,ficewa kawai yayi without saying anything,dan rashin a ɓace yake,a parking space ya samu mom Maryam jingine jikin motarshi sai wani cika take tana batsewa,tun daga nesa ya shiga aika mata harara,yana isowa driver seat ya buɗe ya shige without looking at her,jefa jakatar dake hannunshi back seat yayi,front seat mom Maryam ta zo buɗe saiƙara ɗaure fuska take ganin ko kallon inda take baiyi ba,key yayi ma motar su ka fice daga gidan,tsit motan tayi can dai yayi breakin silet ɗin “dama abunda ke kawo ki gidan ya Tahir kenan ko?” wani kallo tayi mashi da kamar baza tace komai ba sai kuma tace “shine zaka wulaƙantani gaban wann...” “abunda na tambayeki kenan?” ya faɗa babu alamun wasa “to dan mi suna ci mata matuncin naƙi shigar mata,dan kawai sunga bata da son fitina” kallonta uncle Mustafa yayi “ke me son fita ko?” murmushi ta sakar mashi “ni bazan iya zuba ido a wulaƙanta ta a idona ba” “da kyau,idan na riƙa ki zaki san bazaki zuba ido a wulaƙanta ta ba” ƴar dariya kawai tayi without saying anything to him. uncle Hashim ma sallama yayi ma dady,motarshi dake parking space ya shiga,shima ficewa yayi daga gidan zuwa nashi,tun a main parlorn gidan ya shiga kiran sunan Balqis da ƙarfi, har amsawa parlorn sai da yayi,da gudu balqis ɗin ta fito tare da mom maimunatu da Laatifa,da sauri balqis ta nufeshi ai kuwa Unexpected taji saukar mari a cheek ɗinta,da mugun sauri ta dafe cheek ɗin ta tana kallonshi cike da mamaki “barrister lafiya?” a cewar mom Maimunatu,nuna balqis yayi “wannan yarinyar har ni zata kai ƙara wajen ya Tahir,tasa su tasani gaba shida ya Mustafa suna man faɗa kamar wani ɗan cikin su” “wane irin ƙara kuma,ke balqis lafiyar ki kuwa??” kuka balqis ta fashe da shi “momy Ni nace mashi hospital ɗin yaya SAM nake so ba nasu ba,amma yace s...” ai bata ƙarasa ba ganin ya yo kanta,da gudu tayi bayan momy ta ɓoye “kina tunanin dan kin kai ƙarata wajen ya Tahir shine zai sa na haƙura,wallihi kinji na rantse babu ke babu hospital ɗin wacan yaron” wani kallo mom Maimunatu ta shiga yi mashi “wai kai barrister miye matsalarka da SAM ne,dan mi bazaka barta ba,sai kace SAM ɗin ma yana nan ne” “ina ruwanki da ƴata nake magana,aiki ne dai wacan hospital ɗin baza tayi ba” fashewa balqis ta sake yi da wani sabon kuka “dan Allah dady kayi haƙuri,momy d...” bata ƙarasa ba saboda tsawar da momy ta daka mata “kar bakin ki ya sake kiran sunana,if not saina tsintsinka maki mari” tana faɗin haka ta tureta daga jikinta, kitchen ta nufa laatifa na bin bayanta,da kallo kawai uncle hashim ya bita dan baƙarim haushi yaji ba data bangaje balqis,yasan ba komai yasa tayi haka ba sai dan yace ba ruwanta,to ai shi ba wai yana nufin karta sa masu baki ba ne. kuka sosai balqis ɗin take,har cikin ranshi yake jin kukanta,kwata kwata baya son abunda zai ɓata ranta amma bazai iya amincemata tayi aiki a hospital ɗin SAM ba,kallo ɗaya yayi mata ya nufi part ɗin shi. hawaye ne ke zuba idon mom lallashinta dady yake kan abunda su mamy su ka yi mata amma kamar ba da ita yake ba,kuka kawai take taƙima ta saurareshi “haba Zulaihart dan Allah kiyi haƙuri kibar kukan nan,su basu isa su tada maki hankali ba,dan Allah kiyi haƙuri” “yallaɓai yanzu inace kaga abunda nake gudu ko,ina zaman zamana mata ta tada man hankali haka kawai,dama dan saboda su ci man mutunci yasa ku ka dage akan dole sai kun haɗa alaƙa tsakanina da su” “kinfi kowa sanin bana son ganin ɓacin ranki,wallahi na amince ne saboda ƙara danƙon zumunci tsakanina da ƴan uwana” “a rayuwata ban san miyi matsala ba ko na nemi abu na rasa,amma mi yasa tunda na Aure ka nake fuskantar matsaloli,laifi ne dan na cika burin soyayya ta,ko laifi ne dan nabi addinin mijina??” “ko ɗaya ba laifi ki ka yi ba,basu san ciwan kansu bane shiyyasa su ke maki hakan,amma kiyi haƙuri” hawayen dake zuba daga idanunta ta share “i want to go US tomorrow”da sauri dady ya kalleta jin abunda tace“why Zulaihart,saboda wannan ɗan saɓanin zaki tafi?”fashe mashi da sabon kuka tayi kamar ƙaramar yarinya mom tana da raunin zuciya abu kaɗan ke ɗaga mata hankali “i said I want to go,I want to see my mom” “please Zulaihart karki man abunda baki taɓa ba a zaman mu” “I need my mother's shoulder to cry on, I want to hug her and tell her all my problems” kusa da ita ya matsa, jawota yayi zuwa jikinshi “as long as that will make your mind calm,cry on my shoulder” zame hannunta tayi daga cikin nashi “mamana nake son gani, Please ka barni na tafi gobe” “haba Zulaihart miyasa za ki man haka,at ur age kin wuce zuwa gida da sunan wai ranki ya ɓaci a gidan mijin ki,duk abubuwan da ki ka fuskanta a baya baisa kinje ba sai yanzu,kinfi kowa sanin momy bawai tana son Auren mu ba ne,miyasa zaki man haka,ko kin gaji da zama da ni ne??” ɗan dakatawa yayi kafin ya kwantar da murya yana sake kama hannunta “Please kiyi haƙuri komai zai wuce,in dai son ganin momy ki ke nayi maki alƙawarin zamuje tare lokacin birthday ɗin SAM,sai kar muyi celebration a nan sai muje can, Please kiyi haƙuri kinji”lallashinta ya shiga yi dan ta bari sai lokacin birthday SAM su je,amma kamar ƙaramar yarinya taƙi saurarenshi ta kafe akan dole itafa sai taga momynta har cewa dady ta kirata video call amma fir tace itafa ganinta take son yi a zahiri,kallonta kawai yayi,shi kanshi yasanta tanada matuƙar haƙuri yanzunma kasa jurewa tayi ne,dan abunda ake mata a familyn shi da watace da tuni ta rabu dashi,amma tayi haƙuri tsawan shekaru,sosai ya sake kwantar da murya yana bata haƙuri “please i want to see my mom” iska dady ya fesar,ganin dai ba daina maganar tafiyar za tayi ba ne yasa shi tashi ya fice ya barta,a parlorn ya samu su ya Naeem in da ya barsu zaune,kallo ɗaya yayi masu ya wuce sama, bedroom ɗin momy su ka nufa,suma kwantar mata da hankali su ka shiga yi,su ka yi mata alƙawarin tunda har bata son Auren dole shima Irfan ya haƙura,ta ɗanji sassauci da kalaman su amma bata fasa maganar tafiya gobe ba,suna nan dady ya shigo da waya kare a kunnenshi,miƙa mom yayi,amsa tayi takai wayar kunenta tana kallon shi, Muryar uncle Jonahs ce daki dodon kunnenta “katte mi yasa za kiyi haka da girma ki,ur not a kid fa,dan mi zaki tada hankali shi,idan kin zo taya zaiyi solving matsalar??” “momy nake son gani Uncle” “yace nan za kuyi celebration birthday SAM why baza kiyi haƙuri ba,kefa ba yarinya bace ko Carol da ace tana nan baza tayi abunda ki ke ba,yara nawa ne a tsakanin ku?” ɗan kallon dady tayi kafin tace “five” “five kids amma ki ke wannan abu like Yumnah,you should be patient, everything will be fine” “thank u uncle” “bey take care of ur self” jinjina mashi kai tayi,miƙama dady wayar tayi bayan tayi rejecting amsa kawai yayi ya fice. *UNITED STATE❤* _*Las Vegas (Nevada)*_ A round 1:30Am ta shiga buɗe idanunta da su ka yi mata nauyi sosai,ta jima da farkawa ta kasa buɗe idanun ne saboda nauyin da su ka yi mata,a hankali ta sauke idanunta kan ceilling,kallon ɗakin ta shiga yi,biji biji take gani,buɗe idanunta ta ɗanyi sosai tana son tuna abunda ya faru da ita da kuma ina ne nan ,idanunta ne suka sauka akan mutum dake zaune saman sofa, scrub suit ne a jikinshi,ya ɗan jinginar da kanshi jikin head ɗin sofa, fuskarshi har time ɗin da facemask,idanunshi ne kaɗai a waje,ɗan lumshe idanunta tayi kafin ta sake buɗe su akanshi,wayace kare a kunnen shi yayinda hannunshi ke riƙe da wani littafi,zuba ma littafin dake hannunshi ido tayi kamar Bible sai dai kuma rubutun dake jikin littafin sun banbanta dana Bible,saurin kallon fuskarshi dake manne da facemask tayi,idanunshi a lumshe su ke kamar mai bacci,kauda kanta tayi zuwa Ventilator machine da drip ɗin dake hannunta,sai a time ɗin hankalinta ya kai ga oxgyen ɗin dake hancinta,fahimtar a hospital take ko medical room ɗin su ne yasa ta fara tuna abunda ya faru,a hankali ta lumshe idanunta zuciyarta na mata wani irin zafi “she wakeup now I will call you later” ya faɗa yana rejecting call ɗin,bed ɗin da take ya nufa yana ajiye book ɗin hannunshi da waya saman Centre table dake gaban sofa,ventilator machine ɗin ya fara kashewa kafin a hankali yasa hannunshi ya zame mata oxgyen ɗin dake hancinta,da sauri ta buɗe idanunta ta sauke su akan fuskarshi,tana iya hangen murmushin shi ta cikin mask,zuba mashi ido tayi tana kallo shima kallonta yake,dafa bed ɗin yayi yana duƙo da kanshi saitin fuskarta a hankali ya furta “wellcome back, how do u feel now?” raba idanu ta shiga yi a fuskarshi without saying anything to him,gabanta na wani irin faɗuwa,sake duƙo da fuskarshi yayi saitin tata breath ɗinta na sauka a face nashi “how do u feel now?” ya faɗa a hankali,faɗuwar gabanta ne ya tsananta dan mi muryar shi ke mata kama da wacce ta sani ko ta taɓa ji,a hankali ta motsa bakinta magana take amma baya iya jin mi take faɗa,kunnenshi ya kai saitin bakinta,a hankali yaji ta furta “who are u, where's my Mom??” ɗago da kanshi yayi yana kallon kyakkyawar fuskarta,tayi fayau har wata ƴar rama tayi,lips ɗinta sun ciza launinsu,she look so pretty a hakan, ɗan lumshe idanunshi yayi yana buɗewa a hankali ya furta “ur destiny” ya furta yana tsareta da idanu,wani kallon rainin wayau tayi mashi,ɗan murmushi ya saki yasan yau da lafiyarta lau daya sha masifa na wannan kalmar daya faɗa “i said who are u” ta sake faɗa ɗan lumshe ido yayi kafin a hankali yace “I'm the doctor who's taking care of u” kallonshi tayi,ɗaga mata gira ɗaya yayi yana faɗin “what?” lumshe idanunta tayi kafin hankali ta furta “I want to see Aunty Sophia and my mommy” a hankali shima ya furta “are u tired of seeing me?” lumshe ido tayi kawai without saying anything to him,wallahi dan tana jinta sai a hankali amma yau da ya shiga uku,ya taki sa'a da sai taji miye matsalar shi da ita da zai dameta haka,tashi yayi daga bakin bed ɗin ya nufi landline ɗin dake ward ɗin, dialing wasu numbers yayi,an picking ya bada umarnin akawo mata coffee,ajiye wayar yayi ya nufi ɗan ƙaramin table ɗin dake haɗe da bed ɗin,magungunanta dake wurin ya shiga dubawa,injection ya ɗauka yana dubawa,nocking ƙofar ward ɗin akayi,umarnin shigowa ya bada,turo ƙofar ward ɗin akayi da sauri Nailarh ta kai dubanta ga ƙofar shigowa,wata nurse ce ta shigo ɗauke da ɗan madaidaicin tray,mug ɗin coffee ne guda biyu sai gorar ruwa,ɗauke kai Nailarh tayi,cikin ɗakin ta nufo,har gaban bed ɗin ta ƙaraso,ajiye tray tayi saman table ɗin dake ɗakin,cike da girmamawa tace “good evening sir” jinjina mata kai yayi, dubanta ta kai ga Nailarh “how's u body?” lumshe ido Nailarh tayi without answering her “wish u quick recovery” nurse ɗin ta faɗa,ficewa tayi,trayn ya nufa,mug ɗin coffee ɗin guda ɗaya ya ɗauka,bakin bed ɗin ya nufo,ajiye mug ɗin yayi kan table ɗin dake jikin bed ɗin,wani ɗan button ya danna a jikin bed ɗin,ɗan bending bed ɗin yayi yanda za taji daɗin shan coffeen,saurin buɗe idonta tayi tana kallonshi,mug ɗin coffeen ya miƙa mata,kallonshi kawai tayi ba tare da ta amshi mug ɗin “do u want me to gave u?”saurin kallonshi tayi,gira ɗaya ya ɗaga mata,sauke idanunta tayi daga kallonshi,zama yayi gefen bed ɗin,mug ɗin coffeen ya kai bakinta,bata yi musu ba ta amsa,bata coffeen ya shiga yi har sai da tasha kusan rabi tukun ta kauda kai,ajiye mug ɗin yayi,magungunanta ya shiga bata,da ƙyar ya samu tasha. “whare's Aunty Sophia and my mom,I want to see them” Allurar dake cikin magungunan ya shiga haɗawa kafin a hankali yace “not now,u need to have some rest”ɗan zame hannun rigar dake jikinta yayi,saurin kallonshi tayi,rintse ido tayi lokacin da ya tsira mata alurar,siraren hawaye ne su ka shiga zubowa daga idanunta,zame allurar yayi bayan ya kammala mata,maida mata hannun rigar yayi “i'm sorry” ya faɗa “please I want to see them” ta faɗa kamar za tayi ku ka,lallai Nailarh ba kanta “I'm sorry ,u need to have some rest now,u can see them later,okay” ya faɗa yayinda yake goge mata hawayen da su ka zubo daga idonta,sofa ya nufa,da kallo kawai ta bishi,wani iri take ji a ranta,ga zuciyarta dake mata zafi,gashi yaƙi bari ta gansu ko za taji sauƙin abunda take ji,mug ɗin coffeen taga ya ɗauka,zama yayi kan sofa yana ɗaukar wayar shi dake ajiye kan Centre table,unexpected taji bacci na neman ɗaukarta,lumshe ido tayi ko two minutes bata ƙaraba bacci yayi awan gaba da ita,bata sake farkawa ba sai a round 8:30Am,baccin awa bakwai tayi saboda magani da alluran da yayi mata,a hankali ta sauke idanunta akan jikinta ganinta lulluɓe da duvet ga drip ɗin da aka sa mata ancire,ɗan lumshe ido tayi ta buɗe,a hankali ta kai hannunta da nufin zame duvet ɗin dake jikinta,idanunta ne su ka sauka akan tafin hannunta,ganin kamar alamar note ne yasa tayi saurin buɗe tafin hannun tana,yes note ne da mamaki ta shiga karanta note ɗin _I'm so proud of myself for taking care of u_ _do u know how pretty u are when u are sleeping?_ _like an innocent baby, that's how u look when u are sleep_ _Good morning baby_ ɗan zaro ido tayi kaɗan tana sake maimaita abunda aka rubuta,saurin kallon sofa dake ɗakin tayi amma wayam ta gani ba kowa,hatta book ɗin data gani hannunshi jiya da mug ɗin coffeen da yasa aka kawo mata babu, saurin kallon ɗayan side ɗin tayi,idanunta ne su sauka akan bunch of tulip flower mai matuƙar kyau da ɗaukar hankali dake ajiye saman table,daga ƙasan bunch ɗin a ɗaureshi anyi mashi style kamar ribbon,ɗan card ta gani a jikin flower,lumshe idanunta tayi tana sake buɗe su akan flower,ba ƙaramin kyau flower tayi mata ba,tunani ta fara ko dai momynta sun zo ne,zame duvet ɗin jikinta tayi,hannu ta zura ta ciro card ɗin,note ne a jikin card ɗin anyi rubutu with style,karanta note ɗin ta shiga yi _whether it's a royal blue satin gown or ordinary blue hospital pajamas u look pretty as always. Nothing would make me happier an more relaxed than seeing u again in good health! Hope u feel better soon._ _get well soon cutie._ iska ta furzar daga bakinta, lallai mutumin nan bai san wace ita ba shiyyasa yake gigin shige mata,ko dan ya ganta a kwance a hospital yake tunanin bazata iya yi mashi komai ba ne,to yaushe ma duk yayi wannan abun,jin an turo ƙofar ɗakin ne yasa tayi saurin kai dubanta ga ƙofar. Aunty Sophia ce ta shigo,da sauri ta rufe idonta tana tura hannunta cikin duvet,wani iri Aunty Sophia taji dan duk a kan idonta Nailarh tayi haka,ta san dama dole tayi fushi da ita,cikin ɗakin ta ƙara so,zama tayi gefen bed ɗin,a hankali ta kai hannunta saman fuskar Nailarh,saurin juya mata baya tayi tana ture hannunta dake kan fuskarta “baby har yanzu fushi ki ke da Aunty Sophi ki?” Aunty Sophia ta faɗa a hankali,banza Nailarh tayi da ita without saying anything ta her “I'm very sorry Nailarh,ki fahimce ni bana da sa hannu akan wannan abun daya faru, Please I'm very sorry” hannunta dake cikin duvet ta kama da sauri Nailarh ta fisge hannunta duk da ba wani ƙarfi ne da ita ba. “baby dama zaki iya juya man baya saboda wani dalili?,kinfi kowa sanin a duniya bana da wani buri wanda ya wuce naganki cikin farin ciki,you know better than anyone that I can't do anything to hurt you, please be patient and understand me” still ba tace mata komai ba,tashi Aunty Sophia tayi ta koma ɗayan side ɗin “please Nailarh kiyi haƙuri,baki san halin dana shiga saboda wannan rashin lafiyar taki ba, Please kar ki sa zuciyata ta buga dan bazan juri ganin kina fushi da Ni ba,kiyi haƙuri ki yafe ma Aunty Sophin ki” magiya Aunty Sophia ta shiga yi mata tana bata haƙuri amma ko kallon inda take Nailarh ba tayi ba,saukar ruwan hawayen Aunty Sophia taji saman hannunta,ɗan rintse ido tayi,duk yanda ta ɓata mata rai baza ta so ganinta cikin damuwa ba,kawai tayi mata hakan ne dan ta fahimce irin yanda taji saboda kalamanta,dan tayi imani Aunty Sophia baza ta taɓa yin abunda zai cutar da ita ba,a hankali ta buɗe idon,juyowa tayi tana fuskantar Aunty Sophia data kifa kanta saman mattress,kuka take amma ba mai sauti ba,wani irin tausayinta ne ya rufe Nailarh ita kanta sheda ne akan halin da Aunty Sophia ke shiga idan wani abu ya sameta,to taya ma za tayi tunanin zata iya cutar da ita,kawai dai kalamanta ne idan ta tuna su ranta yake ɓaci,a hankali ta ɗaura hannunta on his head “Aunty Sophi!” ta kira sunanta ,da saurin Aunty Sophia ta ɗago,fuskarta duk tayi sharkaf da hawaye,hannunta dake saman kanta ta riƙe “Nailarh” ta kira sunanta yayinda wasu hawaye ke zuba daga idanunta, girgiza mata kai tayi tana sa ɗayan hannunta ta shiga goge mata hawayen “stop crying, you know that I can never be angry with you,kawai banji daɗin kalaman ki ba” “I promised you that you will not hear another unpleasant word from my mouth again,I'm sorry dear. “please to ki bar kukan haka” da sauri Aunty Sophia ta kai hannunta saman fuskar Nailarh,shafa fuskarta ta tayi “shikenan bazan sake ba,ya jikin naki?”da sauri Nailarh ta kamo hannunta ganin kanula “what's happening with u?” “saboda ke ne,amma ba wani abu mai mahimmanci bane na samu sauƙi” “lafiyarki ce ba abu mai mahimmanci ba?” girgiza mata Aunty Sophia tayi “karki wani damu,ya jikin naki,fatan da sauƙi?” “na samu sauƙi sosai Aunty Sophi” “thank God,haka nake son ji,fata samun lafiya maiɗorewa” jin jina mata kai Nailarh tayi turo ƙofar ɗakin a kayi,da sauri su ka kalli ƙofar,miss malika ce ta shigo,tana sanye da Suit white color,hannunta riƙe da bunch ɗin rose flower mai matuƙar kyau,daga bayanta su luna ne ɗauke da basket,da sauri ta ƙarasa bakin bed ɗin Nailarh,a saman table ta ajiye flower tashi Aunty Sophia tayi ta bata wuri,da sauri ta zauna in da Aunty Sophia ta tashi,kamo hannun Nailarh tayi cike da tsantsar kulawa “baby!” ta kira sunanta,hannu Nailarh ta kai a fuskarta,shafa fuskarta tayi “sweetheart!”ta kira sunanta a hankali,da sauri miss Malika ta goge hawayen dake idonta “Baby, how is your body?” “I felt relieved”Nailarh ta faɗa “I miss you so much baby” “me too sweetheart” murmushi Malika ta sakar mata,da sauri su luna su ka shiga gaishe da Nailarh da yi mata ya jiki,ɗan murmushi kawai ta sakar masu, flower data shigo da ita ta ɗauko, fuskarta da murmushi ta ɗaura mata ita saman jikinta “this for u my baby”murmushi ta sakar mata tana kai flower hancinta,daddaɗin ƙamashin da flower ke fitarwa ta shaƙa,zuba mata ido su ka yi suna kallon yanda ta lumshe ido tana shaƙar ƙamshi flower,wani irin daɗi ne ya rufe Mrs Malika,janye flower tayi tana kallon Momyn ta ta, murmushi ta sakar mata “thank U” ta faɗa, murmushi Mrs Malika ta sakar mata tana kashe mata ido ɗaya,card ɗin dake jikin flower ta ciro tana karanta rubutun dake ciki _u always told me my hugs are always warm and comfy. I really want to hug u all day to keep warm. I know your fever will go away!_ _get well soon my baby_ da sauri Nailarh ta kai dubanta ga Mrs Malika, murmushi ta sakar mata tana kashe mata ido ɗaya,buɗe mata hannayenta tayi alamar tazo gareta,ba musu kuwa ta ajiye flower gefenta,hugging ɗin juna su ka yi,Sofa dake ɗakin Aunty Sophia ta nufa ta zauna,sun kusan five minutes a haka,idanunsu a lumshe,Mrs Malika ta fara bude ido,a kan wannan tulip flower idanunta su ka sauka,saurin raba jikinta tayi daga na Nailarh,kallon fuskarta tayi “baby wacen flower fa,ko dai Sophia ce ta kawo maki?” mrs Malika ta faɗa tana kallon Aunty Sophia,girgiza mata kai aunty sophia tayi alamar ba ita bace, kallon Nailarh tayi “I think doctor brought it to me” Nailarh ta faɗa “dr! Which doctor?, Dr Daniel?” Mrs Malika ta faɗa “I don't even know it it's dr daniel,but wanan dai dr dake kula dani” “dr dake kula dake?” Mrs Malika ta faɗa yanayin fuskarta na canzawa zuwa tsantsar ɓacin rai “yes” Nailarh ta bata amsa, iska ta fesar mai huci “baby dole yau mu bar hospital ɗin nan ko da ba suyi discharge ɗin mu ba, ni dama kwata kwata ban yarda da wannan hospital ɗin nan ba da dokokin wannan CEO ɗin na su na banza,kawai mu tafi gida sai sophia ta cigaba da kula dake ko dr Mark” “yes, sweetheart, I'm tired too, let's just go home” “ma'am bai kamata mu tafi ba ba tare da anyi discharge nata ba, please mu bari suyi discharge namu, zata fi samun kulawar data dace a hospital, bata jima da farfaɗowa ba fa” Aunty sophia ta faɗa “gaskiya sai mun tafi, in ya so sai mu koma orphanage can ma akwai professional drs to take care of her” “please ma'am kiyi haƙuri,tunda har nan muka fara zuwa muyi haƙuri ta ƙarasa samun sauƙi su sallame mu” “to dan mi za su wani kafa mana doka, ya hana mu shigo inda take, sannan yanzu miye alƙarshi da ita da zai wani kawo mata flower sai kace ce mashi akai bata da wanda za su kawo mata” “na fahimci damuwarki, amma duk da haka kiyi haƙuri suyi discharge ɗinta, kuma dan ya yi wish ɗinta dan ta samu lafiya ai ba laifi bane, drs da dama suna haka ga patient ɗin su, kiyi haƙuri” shiru kawai miss malika tayi ba tare da tace mata komai ba amma har cikin ranta bata san zaman hospital dan gani take kamar akwai wani abu da yasa dr nan yake shige ma Nailarh, amma dai ko miye za ta zuba ido sosai akanshi kafin su bar hospital ɗin. “baby mi za kice na zuba maki?” Aunty sophia ta faɗa “I'm not hungry” Nailarh ta faɗa “please,na haɗa maki koda tea ne mana” turo baki kawai Nailarh tayi, basket ɗin da su luna su ka shigo da shi Aunty sophia ta nufa, tea and fried ege ta haɗan mata,tashi miss Malika tayi ta koma kan sofa,inda miss malika ta tashi ta zo ta zauna, cup ɗin tea ta kai bakin Nailarh,kurɓa daya tayi mashi ta kauda kai “please baby ki sha mana” ta faɗa tana marairaice mata fuska “coffee nake so” Nailarh ta faɗa,ok kawai Aunty sophia ta ce tana tashi ta nufi basket ɗin, turo ƙofar ward ɗin aka yi,Nurse ce ta shigo tana turo food trolley,da mugun sauri su ka kai duban su gareta har ta ƙaraso gaban bed ɗin Nailarh “hi Miss Nailarh,how was ur body,hope u feel better now” ta faɗa cike da kulawa tana sakar ma Nailarh murmushi,jin jina mata kai Nailarh kawai tayi,kallon Mrs Malika da Aunty Sophia tayi “good morning” da ƴar fara'a Aunty Sophia ta amsa mata,Mrs Malika kuwa ko kallon inda take ba ta yi ba,dan yanzu gaba ɗaya haushin su take ji, warmers ɗin dake kan trolley ta shiga buɗewa,Wheat Bread,Greek Yogurt,cup of milk,fresh fruit,Chicken and etc. wani kallo Mrs Malika ta watsama nurse ɗin ganin tana shirin sarving Nailarh tace “hi! wait,We also brought food for her,so take yours and go out”ɗan murmushi Nurse ɗin tayi “sorry ma'am na sani,amma wannan shi ne ya dace ta ce saboda lafiyarta” “mu ma wanda mu ka zo dashi zai taimaka ma lafiyar ta,kawai ki kwashe kayan ki” “I'm sorry ma'am hakan bazai yiwuba” “saboda mi” “umarnin CEO ne wannan shine abincin da za taci” “u and your CEO idiot” murmushi kawai nurse ɗin tayi tana maida hankalinta kan abunda take “She won't eat this food” Mrs Malika ta faɗa tana nufo bakin bed ɗin,da sauri Aunty Sophia tace “please ma'am kiyi haƙuri,sun fi mu sanin mi ya dace da Nailarh Please” “baza taci wannan abincin ba Sophia” tsayawa Nurse tayi tana kallon Mrs Malika cike da mamaki tunani ma ta fara anya lafiya take,dan duk wanda ke zuwa hospital ɗin nan ya san cewa su ke ba patient abinci to miye matsalar wannan matar “sophia haɗa mata coffee ki Bata,ke fita da kayan ki” “mom please enough” Nailarh ta faɗa da ɗan tsawa duk da rashin ƙarfin jikinta,da sauri ta nufi Nailarh“am very sorry,kawai bana son abunda zai cut...” Bata ƙarasa ba Nailarh ta ɗaga mata hannu “bana son jin wata hayaniya,be quite” saurin kama bakin Mrs Malika tayi tana faɗin “okay ok ” kallon Nurse ɗin Nailarh tayi a hankali ta furta “sarv me” murmushi Nurse ɗin ta sakar mata, sarving ɗinta ta shiga, milk ta fara haɗa mata kafin ta ɗaura mata two sliced of Wheat Bread a saman plate sai Greek Yogurt with berries sai boiled chicken drumsticks,bayan data kammala haɗa mata,tai maka mata tayi zuwa toilet dan ta wanke bakinta,a hankali take taka ƙafarta har zuwa toilet ɗin,sai da tayi brush ɗin tukun su ka dawo ɗakin,kan bed ɗin Nailarh ta koma yayinda Nurse ɗin ke nufar food trolley ɗin,cup of milk ta fara miƙa mata “thank u” ta faɗa tana amsa,wani banzan kallo Mrs Malika ta watsama nurse ɗin tana kauda kai gefe,sai data sha ɗan rabin cup tukun ta janye baki “I'm sorry duka zaki shanye” Nurse ɗin ta faɗa kallonta Nailarh tayi “it's CEO'S odar” murmushi Aunty Sophia ta saki ganin yanda Nailarh ta wani juya ido alamar an dameta fa,tsaki kawai Mrs Malika ta saki tana kallon gefe itafa ba komai ke damunta ba sai kishin Nailarh,ta tsani taga wani na raɓarta,tas ta shanye milk ɗin kamar yanda Nurse ɗin ta faɗa mata, Wheat bread ta nuna mata,sliced ɗin ta ɗauka ta ci,bowl ɗin farfesun kaza ta miƙa mata,Aunty Sophia ta miƙama bowl ɗin,amsa Aunty Sophia tayi,a hankali ta shiga bata,tas ta shanye shi dama dai dai wanda zata iya shanyewa ne,robar greek Yogurt ɗin ta miƙa mata,Aunty Sophia ta buɗe roɓar haɗe yake da fresh barriers,Aunty Sophia ta shiga bata sai ɓata fuska take saboda ba zaƙi unsweetend ne,murmushi kawai Aunty Sophia ke saki,wayar Miss Malika ce ta fara ringing, da sauri marry ta miƙo mata wayar data ciro daga cikin jakan Mrs Malika,amsar wayar tayi tana duba sunan mai kiran nata,ɗan murmushi ta saki tana picking call ɗin,can cikin ɗakin ta nufa dan amsa wayar,sosai ta sha Yogurt ɗin duk da bawai yayi mata daɗi bane sai takura matan da Aunty Sophia tayi,sai da tasha da yawa tukun Nurse ɗin ta shiga bata magungunan ta, injection ɗin dake ciki kuma sai anjima idan Dr ya zo,wurin Mrs Malika ta nufo da waya a hannunta,miƙama Nailarh wayan tayi “baby dady na magan” saurin kallonta Nailarh tayi,hakama Aunty Sophia “amsa mana, yana so ya ji ya jikin ki” kauda Nailarh tayi yanayin fuskarta na canzawa zuwa tsantsar ɓacin rai “please baby ki amsa mana” Mrs Malika ta sake faɗa, ko kallon in da take Nailarh ba tayi ba,wayar tasa a speaker daga cikin wayar Muryar mutumin ta bayyana “hello Nailarh” wani ɗan iskan kallo Nailarh ta watsama wayar without answering him “baby are you hear me” ya sake faɗa,banza Nailarh tayi da shi,ajiyar zuciya ya sauke, a hankali yace “ya jikin naki,fatan da sauƙi,ina nan shigowa next week na dubaki” wani ɗan iskan tsaki taja tana ƙoƙarin sauka daga saman bed ɗin,saurin riƙeta Aunty Sophia tayi tana girgiza mata kai,ran Mrs Malika ba ƙaramin ɓaci yayi ba ta tsani wannan wulaƙancin da Nailarh ke mashi “baby are u Angry with your dady?” ya faɗa cikin kwantar da murya,hararar wayar tayi “who are you to said that,you will never be my father forever” saurin cire wayar Mrs Malika tayi a speaker tana kara ta a kunenta “I'm sorry I will call u later” Bata jira jin mi zaice ba tayi rejecting call ɗin,rai a ɓaci ta kalli Nailarh “baby mi yasa ki ke haka,ya damu da ya san halin da ki ke ciki shine zaki mashi haka??” ko kallonta Nailarh ba ta yi ba “mi yasa ko wane lokaci ki ke son wulaƙantashi,shifa Kamar mahifinki ne” sai a sannan Nailarh ta kalleta “he's not my father,I hate him”rai a ɓace Mrs Malika ta buɗe baki da nufin magana Nurse ɗin tayi saurin cewa “Be patient Ma'am, this may affect her health, I'm sorry” sai da nurse ɗin tayi magana tukun ta tuna da condition ɗin Nailarh,iska mai zafi ta furzar daga bakinta,har ta nufi sofa sai kuma ta juya ta fice daga ɗakin rai a ɓace,ko kallonta Nailarh ba tayi ba,kwantar da kanta tayi jikin pillow haɗi da lumshe idanunta,Aunty Sophia just looked at her without saying anything,hannunta ta kama,note ɗin dake jikin hannunta Aunty Sophia ta zubama ido,buɗe ido Nailarh tayi tana kallonta,rufe mata hannun kawai Aunty tayi ba tare da tace mata komai ba itama Nailarh ɗauke idonta tayi, ficewa Nurse ɗin tayi,bayan kamar 2 minutes da fitarta wata Nurse ta shigo ɗauke da gown da body lotion cikin ɗakin ta nufo,gaishe da Aunty Sophia tayi kafin ta kalli Nailarh,ya jiki ta fara tambayarta kafin tace “It's time to take a bath ma'am” Nailarh looked at her before she looked away, da sauri Aunty Sophia tace “ok, bring the gown and I will help her to take a bath, thank you” ba tayi musu ba ta bata gown ɗin,zama tayi kan chair dake gaban bed ɗin, taimaka ma Nailarh Aunty Sophia tayi zuwa toilet,Sosai toilet ɗin ya haɗu kamar a gida,duk wani abu da za su buƙata akwai a ciki,ruwa Aunty Sophia ta haɗa mata,sanin halin Nailarh da koda tana lafiya ba wanka take da kanta bane yasa Aunty Sophia ta taimaka mata tayi,wani iri Aunty Sophia taji wannan shine the first time tayi ma Nailarh wanka bayan ta girma,hawaye ne su ka taru a idanunts lokacin da ta tuna yarintar Nailarh,da sauri tasa hannu ta goge kafin Nailarh ta gani,shaf shaf ta taimaka mata tayi wanka har ta canza mata rigar jikinta ta shafa mata lotion,ficewa su ka yi zuwa ɗakin,Nurse ɗin kaɗai su ka samu su luna sun fice da alama wajen Mrs Malika su ka nufa, taimaka mata tayi ta koma saman bed,kwanciya tayi,duvet Aunty Sophia ta ja mata ta rufe mata rabin jikinta,lumshe ido tayi kamar mai bacci,gown ɗin Nailarh ta cire Nurse ɗin ta kwashe ta fice. *ABUJA NIGERIA* gaba ɗayan su ne a bedroom ɗin mom ya Naeem,ya Adnan sai Irfan,mom na daga zaune gefen bed ɗin ta yayin da ya Adnan ke zaune saman stool a gaban mirror sai ya Naeem dake zaune kan sofa shida Irfan,tunda su ka fara magana kan Auren shi da Noor ƙala baice masu ba kanshi na ƙasa,ɗaya bayan ɗaya yake sauraren su “idan har ba so ka ke kaga ɓacin raina ba,ka ƙyale masu ƴarsu kawai kaje ka nemi wata,Allah zai baka wacce ta fi ta” mom ta faɗa tana kallon Irfan ɗin “akwai ƙanwar Usman abokin aikina yarinyar tana da hankali ga tarbiyya,Ni zan mashi magana sai kaje ka ganta idan tayi maka shikenan a gidan shi take zaune” ya Naeem ya faɗa yana kallon Irfan ɗin “idan ba tai maka ba ma ga Kairiyyah nan ɗiyar Aunty Adama sai ka nemeta,tama fi Noor natsuwa da komai,kuma Mahaifinta bazai hanaka ba ko ita Aunty Adama” a cewar ya Adnan “gaskiya bazan iya da tashi hankalin mama Ameenah ba,kawai ni nayi mashi alƙawarin ƴata indai har yana so,dama tuna farko ita nake da burin ya Aura ba Noor ba” sai a lokacin Irfan ɗin ya ɗago ido ya kalli mom,gaba ɗaya su ka zuba ma mom da tai magana ido,ya Adnan ne yace “dama kina da wata ƴar ne bayan Yumnah bamu sani ba?” “NAINARH nayi mashi alƙawarin ta muddin yana so” tunda mom ta fara magana gaban Irfan ya faɗi,wani irin mugun ɓacin rai ne ya rufeshi, mom tama rasa wa za tace ya Aura sai wannan yarinyar,ya Adnan da ƙyar ya haɗiye wani abu daya tsaya mashi a maƙoshi,kwata kwata baiyi tunanin mom za tace haka ba,ajiyar zuciya ya Naeem ya sauke yana faɗin “gaskiya tana da hankali da natsuwa uwa uba tarbiyya da Ilmi, gaskiya naji daɗin jin haka mom,wlh ni ban ma yi wannan tunanin ba saboda ganin halin da take ciki,kinga idan ya Aureta hakan zai rage mata raɗaɗin rashin iyayenta,amma mom dangin Mahaifinta kina ganin za su Amince?” “wannan ba matsala bace Naeem,tunda mahaifinta ya rasu su ka datse duk wata alaƙa dake tsakanin su da ita” “duk da haka mom,dole su sani” “zan sanar da su amma sai in ya Amince itama ta aminta da shi tukun,idan duk sun amince sai na sanar da su yanda idan ba su amince ba ina da right ɗin da zan maka su a Court” kallon Irfan ɗin ya Naeem yayi “kaji abunda tace,minene ra'ayinka akan hakan,kana sonta ko dai mu bari kayi tunani” “yaya mi yasa baza ku fahimce ni ba, ni gaskiya bazan iya son wata ba bayan Noor” da mugun sauri su ka shiga kallonshi, wato duk bayanin da suke da bashi haƙuri ba fahimtar su yake ba “dan mom fatilah Bata son Auren ai ba ita zata ban Aurenta ba kuma ba da ita zan zauna ba ni gaskiya Noor nake so,dukan ku ba wanda hakan bata faru ba lokacin Auren shi kuma ai kuna zaune lafiya,sai ni za a hana ni,ni gaski...” bai ƙarasa ba ta dalilin marin da ya Naeem ya ɗauke shi da shi,dafe cheek ɗin shi yayi yana kallon ya Naeem da kallo ɗaya zaka mashi ka hango tsantsar ɓacin da ranshi yayi,tashi Irfan ɗin yayi rai a ɓace ya nufi ƙofa,kuka mom ta fashe dashi,da sauri ya Adnan ya nufo inda take,hannunta ya kama cikin nashi “dan Allah mom Kar wannan abun da yayi ya ɓata ranki,wallahi ko yana so ko bai so bazai Aureta ba” tashi ya Naeem yayi ya nufi Irfan ɗin dake bakin ƙofa “wannan yanayin ka ke son gani a tare da ita,to bari kaji na faɗa maka, kai baka isa ta dalilinka ka hana mata zaman lafiya ba,dan mun zauna muna baka haƙuri it doesn't mean cewa bazamu iya tursasamaka ba,wllh kaji na rantse baka ba wannan yarinyar” “haba second father dukan ku kun Auri muradin ranaku sai ni ne zaku hana” “ka dai ji abunda na faɗa maka,idan kuma ban isa ba to”yana faɗa hakan ya bar wurin ya nufi mom,ya Naeem yana da saurin fushi amma yana da saurin sauka.                         *Ep 41_42* ____________________________ Ficewa Irfan ɗin yayi rai a ɓace,karo su ka yi da juna,gaba ɗaya mug ɗin Coffeen dake hannunta ya zube mata a jiki,sakin trayn tayi tana fasa wata irin gigitaciyar ƙara saboda azabebben zafin daya ziyarci ganganr jikinta,gaba ɗaya coffeen ya wanke gaban rigarta da hannunta da ƙafarshi,kuka take sosai tana yarfe hannu,kallo ɗaya yayi mata ya bar wurin,A 360 mom ya Naeem, ya Adnan da  dady wanda kusan akan idonshi komai ya faru su ka faɗo parlorn, dan ƙarar da Nainarh tayi har cikin ƙwaƙwalen su, gaba ɗaya kanta su ka yi,a ruɗe ya Adnan yake tambayar mi ya sameta,daƙyar ta iya faɗa masu abunda ya faru da ita, sannu su ka shiga jera mata, ya Adnan ji yake kamar ya cire mata azaban da take ji, kamata yayi zuwa sofa, bin bayansu su ka yi zuwa cikin parlorn, kuka take sosai har ga Allah ba ƙaramin zafi take ji ba “sannu kinji kukan ya isa haka muga hannun”dady ya faɗa, mayafin dake kanta daya rufe hannun mom ta janye tana kallon  inda ta ƙone,wurin yayi ja sosai, da sauri ya Adnan ya miƙe ya nufi kitchen, da gudu Yumnah ta faɗo parlorn ita da Fa'iza, wurin Nainarh su ka nufa hankali a tashe “sister mi ya sameki?” Yumnah ta faɗa kamar itama za tayi kukan “mom mi ya sameta?”a cewar Fa'iza “ƙonewa tayi” mom ta bata amsa, zaro ido Yumnah tayi tana yarfe hannu “wayyo Allah nah, garin yaya ki ka ƙone!?” a hanzarce ya Adnan ya dawo parlorn ɗauke da ɗan madaidaicin silver bucket mai ɗauke da ƙanƙara, da sauri yumnah ta tashi daga gaban Nainarh, hannun Nainarh data ƙone ya kama yasa a cikin ƙanƙarar,sake fashewa da kuka tayi tana faɗin “wayyo hannuna, mom zafi” “sannu kinji, zai daina in sha Allah” a cewar dady “yumnah bani towel” ya Adnan ya faɗa, da gudu ta tashi ta nufi bedroom ɗin mom sai gata ta dawo riƙe da ɗan madaidaicin towel, miƙa mashi tayi da sauri ya amsa yana sakashi cikin bucket ɗin,sai da yayi kamar five seconds tukun ya ciro shi, ɗan ruwan dake jiki ya matse, gaban rigar Nainarh ya nufa, da sauri mom ta amshi towel ɗin ganin abunda yake shirin yi “ya isa haka”  ta faɗa wallahi gaba ɗaya a ruɗe yake shi kanshi bai san mi yake shirin yi ba burinshi kawai ta samu sauƙi, har cikin zuciyarshi yake jin kukanta, gyalen dake saman kanta mom ta zame, ɗan zaro ido tayi ganin wurin yayi ja sosai fatar wurin har ta ɗan taso, da sauri ta ajiye towel ɗin, kama hannun Nainarh tayi tana faɗin “tashi muje hospital kawai,Yumnah ɗauko mana hijab, Adnan muje hospital kawai”  da sauri su ka miƙe gaba ɗayan su, bedroom ɗin su Yumnah ta nufa a hanzarce “lafiya dai ko barrister?” “to ƙone ne sosai, wurin har ya tashi” “mom to ki bari a kira dr fawwar sai yazo ya dubata” acewar ya Naeem, da sauri ya Adnan yace “ko kafin ya iso wutan ya gama shiga jikinta, mu tafi kawai” a hanzarce Yumnah ta dawo riƙe da hijab ɗin Nainarh har ta zura nata a jiki, da sauri mom ta amsa ta sa ma Nainarh,bedroom ɗinta Yumnah ta nufa hijab ta ɗauko mata, Nainarh banda hawayen azaba babu abunda take har cikin cikinta take jin zafin, mug uku ne ya zube mata a jiki, dama da suka shigo ya Adnan ya ce ta kawo mashi coffee, ganin suna tare da ya Naeem da mom ne yasa ta haɗo da su dan bata ma san Irfan na gidan ba, coffeen da zafinshi yana turiri, shiyyasa take jin zafi sosai ga fatarta bawai ta saba da wahala bane,amsar hijab ɗin mom tayi ta zura a jikinta,Fa'iza gyara zaman mayafin dake jikinta tayi su ka fice dady kawai su ka bari,Ishrat yayi ma magana ta zo ta gyara wurin kafin ya wuce sama. Motar ya Adnan su ka shiga, ya Naeem na kusa dashi yayinda yake zaune a mazaunin driver mom da Nainarh na baya, Yumnah kuwa motar Fa'iza su ka shiga, ficewa su ka yi daga estate ɗin, motocin securitys ɗin su na gaba wasu na baya,time to time yake leƙo back seat yana ma Nainarh sannnu ya Naeem sai kallonshi kawai yake. Irfan yana ficewa daga parlorn motar shi dake parking space ya nufa, rai a ɓace ya buɗe marfin motar ya shiga,a tsiyace ya rufe motar kamar zai balla marfin,kifa kanshi yayi saman Steering wheel wani irin tafarfasa zuciyarsa ke mashi,sai a time ɗin ma ya ji zafin ƙonewar da yayi,kallo ƙafar yayi yana jan wani mugun tsaki,key yayima motar ya fice daga Estate ɗin,direct S I hospital ya nufa,wani mahaukacin horn ya buga lokacin da ya isa bakin gate din hospital ɗin,da mugun sauri securitys su ka buɗe mashi, a 80 ya shiga ciki kaɗan ya rage bai ture ɗaya daga cikin securitys ɗin ba,da ido su ka bishi, parking space ɗin da aka tanada domin su Dr's ya nufa, parking yayi,fitowa yayi bayan ya gama daidaita parking a zafafe ya maida marfin motar ya rufe,da ido ɗai ɗai kun mutanen dake kai kawo cikin hospital ɗin su ka bishi,yana da girma sosai hospital ɗin, abun kamar ba'a 9ja ba,ginin skyscraper ne hawa huɗu,ta ko ina ƙyallin glasses ne masu ɗaukar ido,cikin hospital ɗin ya nufa,yana shiga reception nureses ɗin dake wurin su ka shiga russunawa suna gaishe dashi,ko kallon inda su ke baiyi ba bare su sa ran zai amsa masu,da kallo kawai su ka bishi har ya shige elevator,da yawan ƴan matan dake wurin ji su kayi kamar su bishi suji mike damunshi,da yawansu dakwan wata irin azababbiyar soyayyar shi su ke amma ko kallon banza babu wacce ta ishe shi a cikin su. katafaren office ɗin shi dake can 3rd floor na hospital ɗin ya nufa,a bakin ƙofar office ɗin ya tsaya,key yasa ya buɗe ƙofar office ɗin ya shiga,sanyayyan ƙamshin dake tashi a office ɗin ne ya daki hancinshi,dum light ne a office ɗin, switch ya nufa ya kunna,haske ne ya gauraye office ɗin, office ɗin yana da girma sosai ga wasu expensive office desk black color,ga book shelf mai matuƙar kyau,sai fridge, cikin office ɗin ya nufa,executive chair dake gaban desk ya nufa ya zauna,kifa kanshi yayi saman desk,wani iri yake ji a zuciyarshi kamar zata kama da wuta tsabar ɓacin rai, bakomai ke ƙara ɓata mashi rai ba face marin da ya Naeem yayi mashi da kafewa da su ka yi akan bazai Auri Noor ba,kawai dan yana masu biyayya it doesn't mean cewa zasu tauye mashi hakki yayi shiru,su lokacin Auren su wa yayi masu hakan,sun Auri maradan ransu sai shi za su nunama fin ƙarfi,abun takaici ma su rasa wa zasu ce ya Aura sai wannan yarinyar,wani wawan tsaki yaja yana tashi daga saman chair ya nufi fridge,buɗe fridge ɗin yayi kwalaben Alcoholic wine dana whiskey, tequila,Vodka and orange juice ne sai container ice cube, kwalbar red wine ya ɗauka tare da cup sai ice cube daya zuba cikin bowl,komawa yayi ya zauna ba tare da ya rufe fridge ɗin ba,buɗe kwalar wine ɗin yayi ya zuba a cikin cup tare da ice cube,rai a ɓace ya shiga shan wine yana fitar da wani irin hucin ɓacin rai,tas ya shanye ya sake zubawa, sai da yasha 3 cups kafin ya ajiye yana fitar da wani irin huci mai zafi,idanunshi sun ƙaɗa jawur har wasu ruwa ruwa ke kwanciya a cikin su, locker dake jikin desk ɗin ya buɗe, Cuba Aliados cigar ne a cikin locker,ɗaya ya ɗauka tare da lighter,a baki yasa yana kunna lighter,zuƙar cigar ɗin ya shiga yi a zafafe,yana fitar da hayaƙi ta baki da hanci,sake tsiyaya wine ɗin yayi a cup,yana sha yana zuƙar cigar,turo ƙofar office ɗin akayi,da yake a buɗe ya bar ƙofar,idanunshi da suka kaɗa jawur ya sauke akan Dr fawar dake shigowa office ɗin,da tsantsar mamaki yake kallon Irfan ɗin,rabon da ƙafarshi ta taka hospital ɗin kusan one month da wani abu kenan,yanzu ma wata Nurse ce ke sanar dashi Irfan ɗin ya zo,maida ƙofar Dr fawar yayi ya rufe,cikin office ɗin ya ƙaraso,kallo ɗaya Irfan yayi mashi ya ɗauke ido “Irfan dama kana nan?” Dr fawar ya jefa mashi tambaya,ko kallon arziƙi Irfan bai mashi ba, girgiza kai Dr fawar yayi “yanzu da hankalinka kake aikata haka a office ɗinka,baka jin kunyar wani cikin familynka ya zo ya sameka haka??” “how many time nake warning naka akan sa man ido,get out from my office kafin nayi maka abunda zanyi regretting daga baya” Irfan ya faɗa murya a kausashe, girgiza kai Dr fawar yayi yasan dama zai iya faɗa mashi fiye da haka ma dan daga gani ya fara fita hayyacinshi “miyasa baka zuwa aiki,kasan cewa yayanka zai turo da supervisors dis week?” “ban sani ba bana kuma son na sani, Please kafice ka bani wuri” “Irfan ka kuwa san abunda ka ke, baka son zuwa Aiki idan ma kazo ba aiki ka ke ba,kafi kowa sanin halin yayanka,mi kake tunanin idan ya fahimci abunda ka ke??” “sai dai idan kai zaka sanar dashi,ɗan sa ido kawai” rai a ɓace Dr fawar yace “dole na sa maka ido,amanar ka yayan ka ya bani dole kuwa na sa maka ido” wata irin iska mai zafi Irfan ɗin ya fisar,cike da tsawa yace “i said get out,if not...” ya faɗa yana nuna mashi ƙofa ba tare da ya ƙarasa faɗar abunda zai faɗa ba,juyawa kawai Dr fawar yayi ya fice yana girgiza kai,a shekaru ya girmi Irfan nesa ba kusa ba,kuma yana bashi girmanshi amma daga inda ya faɗa mashi gaskiya ajiye girmanshi da yake gani yake ya faɗa mashi magana san ranshi. tashi yayi daga saman chair ya nufo ƙofa da cup ɗin wane da cigar yana ɗan layi kaɗan, alcoholic wine ɗin ta fara kai mashi karo,ƙofar office ɗin ya maida ya rufe harda key,a jikin ƙofar ya bar key ɗin,anan bakin ya zube. ya Adnan lokacin da su ka iso hospital sun ga motar Irfan amma babu wanda yabi ta kanshi su ka nufo cikin hospital,da Dr fawar su ka ci karo a reception saukowarshi kenan daga office ɗin Irfan,da sauri ya nufesu, fuskarshi da ɗan fara'a,gaishe da su nurses ɗin dake wurin su ka shiga yi,da kulawa su ke amsa masu “good evining mom,ai da kin kirani ba sai kinzo da kanki ba?” cewar Dr fawar “ba damuwa fawar, patient gare ni,ƙonewa tayi” “ayyah sorry” ya faɗa yana kallon Nainarh “muje ko” ya faɗa yana kiran wasu nurses guda biyu,bin bayanshi su kayi ɗaya na kama Nainarh,su mom kuwa office ɗinsa yace wata Nurse ta kaisu,a bakin office ɗin shi suka tsaya, Nurse ɗin na ƙoƙarin buɗe masu ƙofa ya Adnan ya juya da nufin nufar sama,da sauri ya Naeem ya riƙo hannun shi dan duk tunanin shi Emergency ward din zaibi su Dr fawar “ina zaka?” “office ɗin wancan mara mutumcin,ya ƙone ɗiyar mutane amma ko a jikinshi” ya faɗa cikin tsantsar ɓacin rai “calm down Adnan,ba sai kaje ba rabu dashi kawai,ai zai dawo gidan ya same mu” “wallahi ka kyaleni na koya mashi hankali tunda shi bashi da hankali” girgiza mashi kai ya Naeem yayi “nace ka rabu dashi ko,zai dawo gida ne ya same mu” iska mai zafi ya Adnan ya fesar,cikin office ɗin su ka shiga dan mom da su Yumnah tuni sun shige sun barsu. suna a nan zaune office ɗin sunyi shiru kowa da abunda yake saƙawa a ranshi,Dr fawar ne ya shigo da sauri ya Adnan ya miƙe yana tambayarshi wutar dai da sauƙi bata shiga cikinta ba,cikin office ɗin ya ƙaraso “ku kwantar da hankali,ba wani sosai ne ta ƙone ba,kuma Alhmdllh zafin coffeen baikai har ya shiga cikinta ba,kawai dai fatan ta bata son zafi ne sosai,amma Alhmdllh da sauƙi,magunguna ne kawai zata sha sai cream da zata dinga shafawa a wurin” tunda ya fara jawabin nan hankalin su ya kwanta,dama damuwarsu kar ace wutan ya ƙonata sosai “na bar Nurse Fatima ta shafa mata cream,data shafa mata zaku iya tafiya,Allah ya bata lafiya” da Ameen duka su ka amsa,ba'a wani jimaba Nainarh su ka shigo tare da Nurse ɗin dake riƙe ledar maganinta, Yumnah ta amshi ledar tana ma Nainarh sannu,sannu su ka shiga yi mata,sallama su ka yima dr fawar ɗin su ka fice,lokacin da su dawo gida,bedroom ɗin su Nainarh ta nufa ita da Yumnah da Fa'iza, ya Naeem tun a parking space yayi masu sallama ya wuce gida. *UNITED STATE❤* _*Las Vegas (Nevada)*_ daga ita sai Aunty Sophia ne a ward ɗin,miss Malika tunda ta fita bata sake dawowa ba,fira suke ba wani sosai ba Nailarh na bata labarin yanda taji lokacin da wannan mutumin yayi wining wasan,tana faɗa mata irin yanda zuciyarta tayi mata,lallashinta Aunty take tana bata ƙwarin gwiwa da kuma yi mata alƙawarin sai sun hukunta shi akan abunda yayi mata “but Aunty ina zargin Dr dake kula dani kamar shine,abunda yasa ban faɗama mom ba na san data sani zata haɗashi da su Noah ne,na fi son saina tabbatar da zargina lokacin na warke,nafi son na hukuntashi da hannuna” “nima bazan sanar da ita ba,zan so ki hukuntashi da kanki,duk ta yanda za muyi yayi daya sani za muyi,karki damu kinji” jinjina mata kai tayi “sai ya san wacece ni,sai yayi daya sanin sa kanshi a hanyata” Nailarh ta faɗa “dole ya san wacece ke,nima dole yaga ɓacin raina saboda wahalar man da princess da yayi” marairaice fuska Nailarh tayi “Aunty Sophi ba kiji zafin dana ji ba,gaba ɗaya naji duniyar ta yiman zafi,lokacin dana shaƙi wuyan rigar ki ji nake kamar zan mutu a lokacin” saurin girgiza mata kai Aunty Sophia tayi tana kama hannunta “kwantar da hankalinki kinji,dole ya gane kuskuren abun da ya aikata”gyaɗa mata kai Nailarh tayi, nocking ƙofar ɗakin akayi, izinin shiga Aunty Sophia ta bada,Nurse ɗin ɗazu ce ta shigo da food trolley,har bakin bed ɗin ta ƙaraso,gaishe da Aunty Sophia tayi kafin ta kalli Nailarh“good afternoon ma'am, it's time for lunch” kauda kai gefe Nailarh tayi,itafa idan zasu cigaba da bata wannan Yogurt ɗin zata daina cin abincin su, warmers ɗin dake saman trolley Nurse ta buɗe,sarving Nailarh ta shiga yi,lafiyayyan sandwich ta bata tare da gasashshen kifi. Aunty Sophia ta shiga bata, Nurse ɗin na daga kan robber chair tana kallon su,turo ƙofar mrs Malika tayi ta shigo tare da su luna,kallonta Nurse ɗin da Aunty Sophia su ka yi amma Nailarh ko kallon inda take ba tayi ba,harta canza kayan jikinta da alama gida su ka koma dan harda basket ɗin abincin a hannun su luna,gaishe da ita Aunty Sophia da Nures ɗin su ka yi,amsa masu tayi yayin da idanunta ke kan Nailarh kamar zata haɗiyeta,tashi Aunty Sophia tayi daga inda take zaune lokacin data kammala ba Nailarh abinci, magungunan ta Nures ɗin ta bata kafin ta fice,bakin bed ɗin Mrs Malika ta zo ta zauna,hannun Nailarh ta riƙo a cikin nata ba tare da tace komai ba, Nailarh bata kulata ba, around 6 ɗaya daga cikin nurses ɗin ta shigo ta sanar dasu time ɗin da zasu bar Nailarh ita kaɗai yayi dama aroud six su ke rufe visiting,babu musu ko wani abu mrs Malika tace ok,kallon su Aunty Sophia tayi ta ce su tafi kawai,shirin tafiya su ka shiga yi,su luna su ka ɗauki basket ɗin da su ka zo dashi Aunty Sophia ma kaɗai taci abincin,kissing forehead ɗin Nailarh Aunty Sophia tayi haɗi da yi mata sallama su ka fice,mrs Malika ma kissing forehead ɗinta tayi without saying anything to her,fushi take da ita saboda abunda tayi ma mijinta,tun fil'azal Nailarh bata shiri da mijin Mrs Malika tunda ta fahimci ba shi bane Mahaifinta ba ta ɗauki karan tsana ta ɗora mashi,ga haushi da kishin kusantar Malika da yake da take ji,duk da itama ba wai ta damu da abunda ke tsakanin su can sosai dan bata da ra'ayi da ƙarfin tsiya ta hanyar alura Malika tasa abun yayi tasiri a gareta har ya zame mata jiki, har ya kai take kishin Malika,saboda ita yasa basa zaune waje ɗaya da Malika sai dai idan ta bar ƙasar ya bita inda ta tafi,sometimes saboda shi take barin US ta tafi wata ƙasar badan business ba saidai dan kawai su haɗu. saurin kamo hannunta tayi,kallonta Malika tayi fuskarta a ɗaure,side smile Nailarh ta sakar mata “are you angry with me because of your that black husband?” Kallonta Malika kawai tayi,dan ajiyar zuciya Nailarh ta sauke,sake riƙo hannunta tayi tana faɗin “If u continue to be with him, I will break the promise I made to you, I will also get married,I promise u” Nailarh ta faɗa babu alamun wasa akan fuskarta,wani irin kallon Mrs Malika ta shiga binta dashi “you're going to do what!?” “I know you heard me well” zame hannunta tayi daga na Nailarh,zama tayi kan chair dake gaban gadon “baby kin fi kowa sanin cewa duk dukiyar da muke takama da ita akwai tasa a ciki,Duk wani kasuwancinmu yana da jari a ciki,shine silar arziƙina” “i don't care, I told you If you want me to fulfill promise i made u,just break this useless marriage” wani irin wahalalliyar yawu Mrs Malika ta haɗiye,bata taɓa expecting jin haka daga gareta ba “please Nailarh ki gane mana,rabuwa da shi tamkar na rabu da kaina ne,shine komai nawa fa” “alright,but I want u to know that there is no any promise between us,I will marry,ko da baki so hakan ba” ta faɗa tana tsare Malika da ido,kamo hannunta Malika tayi “kiyi haƙuri kinji,kin san ina sonki fiye da kowa a duniyar nan,karki fasa Alƙawarin da ki ka man Please Nailarh,bazan juri ganinki tare da wani ba,kina so nima heart Attack ya kamani??” “zanfi kowa farin ciki idan ya kama ki”Nailarh ta faɗa ba tare da nuna wata damuwa ba,kallonta Malika ta shiga yi,mi yasa sai da komai ya kusa zuwa ƙarshe Nailarh zata ɓullo mata da wannan tsarin,kenan abunda take zargi zai zama gaskiya “baby that doctor ne ya ce kice man haka,dama that the reason yasa ya kawo maki flower,dama wannan shine dalilin da yasa yake wanan abubuwan akan ki,sonki yake kema kina sonshi ko?” “wannan kuma matsalar ki ce,idan ma sona yake I will marry him” wata irin gigitaciyar tsawa Malika ta daka mata “idan har ki ka cigaba da faɗin haka i promise u I will kill him,I sewer” kallonta Nailarh tayi tana sakin wani malalacin murmushi “ if u kill him I promise u I will kill your husband” iska Malika ta furzar mai zafi,dan mi Nailarh zata mata haka sai da ta gama preparing komai zata ɓullo mata da hakan,nannauyar ajiyar zuciya ta sauke,in a cool voice tace “please Nailarh ki daina faɗa man haka,nifa momynki ce,kuma kin san ina sonki,saboda ke ne kawai bazan iya rabuwa da shi ba,amma ke nake so ba wani ba, Please ki fahimceni” “kin dai ji abunda nace maki idan kina son zaman mu tare to ki rabu dashi” “please Baby,don't do this to your momy, please baby,mi ki ke so a tare da wani namiji wanda bazan iya yi maki shi ba,mi zai burgeki a tare da wannan doctor da ki ke magana” “abunda yake burgeki a tare da wannan mijin naki” wani kallon Malika tayi mata,ganin fa da gaske Nailarh take idan har bata yi wani abu ba,plan ɗinta na tsawan shekaru Nailarh zata rusa,wanda bazata so hakan ba “shinenan I will think about that,I promise u zanyi abunda ki ke so just give me a time” lallashinta sosai ta shiga yi har ta ɗan samu Nailarh ta sauko “da gaske baby sai ki iya Aure that doctor” “yes idan har ba kiyi abunda nace ba” “zanyi,nayi maki alƙawari,but please ki dai na maganar doctor nan” jin jina mata kai kawai Nailarh ta yi,turo ƙofar ɗakin a kayi, Nures ɗin dake kula da Nailarh ce ta shigo “time is over madam” ta faɗa tana kallon Mrs Malika,okhy tace,kafin ta miƙe sallama tayima Nailarh ta fice,a zaune ta samu su Aunty Sophia har sun gaji da zaman jiranta,ficewa su ka yi zuwa motocin su dake parking lot. rufe ido tayi kamar mai bacci,maganganunta da mahaifiyarta na mata yawo a kai,ita kanta ta san she can't survive without her mother,ta riga tayi mata sabon da bazata iya rabuwa da ita ba ,kawai tace mata haka ne dan ta rabu da wannan mutum amma ba wai dan zata iya aikata abunda tace bane. Around 10pm ceo ya shigo domin dubata,har bacci ya soma ɗaukarta,motsinshi a cikin ɗakin ne ya tasheta,a hankali ta buɗe idonta ta sauke su a kanshi,yana daga tsaye gaban gadon ya ɗan juya mata baya hannunshi riƙe da file ɗinta yana dubawa,from head to toe ta shiga kallonshi cargo pant ne a jikinshi haɗe da shirt mai gajeren hannun,breton cap ce a kanshi hakan ya ɓoye sumar kanshi,ɗan lumshe ido tayi kafin ta buɗe, a hankali ta furta “who Are You?” har cikin tsakiyar kanshi yaji maganarta...   *Ep 43_44* ____________________________ A hankali ta furta “who Are You?” har cikin tsakiyar kanshi yaji maganarta bai yi tunanin ba bacci take ba,juyowa yayi yana fuskantar ta,kamar ko da yaushe fuskarshi a rufe take da mask,bed ɗin ya nufo,zama yayi saman chair “good Nailarh,I think we discharge u tomorrow” “why are u pretend,i'm asking u who are you” “i told you since,I'm your destiny” wani matsiyacin kallo ta watsa mashi “who do you think you are,do I look like idiot to you?” girgiza kai kawai yayi ba tare da yace mata komai ba “ko dan ka ganni kwance a nan yasa har ka samu damar shige man,do you know who I am” girgiza mata kai yayi “i don't Know who u are Nailarh” “that's why ka ke man shiga hanci da ƙudundune kenan,amma I will teach you a lesson,I will show you who I am,you regret all abubuwan da kayi man” “idan zaki sa nayi regretting ki sassuta man kinji baby” wani banzan kallo ta watsa mashi,kamo hannunta yayi cikin nashi “Nailarh!” ya kira sunanta in a serious tolk,cikin murya mai daɗi da tausasawa ya fara magana “am sorry about what happen in N R T,am sorry Nailarh I don't mean to hurt you,bansan hakan zai jefaki a matsala ba,abunda ki ka yima wannan mutunanen ne yasa har nayi ƙoƙarin ganin nayi nasara a kanki amma ba da nufin hakan na zo ba,I just came to see you amma ba da nufin yin nasara akan ki ba,I am deeply sorry for hurting u, please forgive me” “tsoro kaji ne ka ke bani haƙuri?” girgiza mata kai yayi “i hate my self because I hurt you,duk hukuncin da zaki man i deserve it” kallon shi ta shiga yi “Ohk but why Are You hiding your face?” murmushi yayi “bana son na tsoratar dake da munin fuskata ne” dariya ta saki ba tare da ta shiryama hakan ba “Who told you I'm scare?” “ba kowa,but nayi expecting hakan ne” “bana jin tsoro,na saba ganin fuskoki mabanbanta,taka bata isa ta bani tsoro ba” “I will show you in a rightiouse time but not now” “why not now” “this is not the right time” wani kallo ta mashi ba tare da tace komai ba,tashi yayi daga saman chair ya nufi drugs ɗinta, injection ɗin dake ciki ya shiga haɗawa,ita dai binshi kawai take da ido ba tare da tace ƙala ba,inda take ya nufo bayan ya kammala haɗa Allurar “give me your hand” kallonshi kawai tayi ba tare da tayi abunda yace ba,ganin haka ne yasa da kanshi ya kama right hand ɗin ta ya mata Allurar,kafeshi da ido tayi kamar mai son ganin wani abu a fuskanshi,bata da wani buri bayan ta ɗau fansar abunda yayi mata,yanzu burinta ta ga fuskarshi,kwata kwata idonshi baya kanta Allurar da yake mata yake kallon harya kammala ya zare Allurar,unexpected yaji hannunta a saman mask ɗin dake fuskarshi tana ƙoƙarin zame mashi shi,saurin riƙe hannunta yayi,cire hannun yayi daga saman fuskarshi,kallonta ya shiga da tsantsar mamaki,sakin hannunta yayi haɗi da barin wurin batare da yace mata komai ba,ko fiv e minute ba tayi ba bacci yayi awan gaba da ita. Kamar yanda yace washe gari a kayi discharge ɗinta,gagarumin party Malika ta shirya mata,sosai Nailarh tayi farin ciki ganin yanda maids ɗin gidan su ka damu da ita,hakan yasa ta sake jin wani kwanciyar hankali duk wata damuwarta akan abunda ya faru ta ragu,har dare shagali su ke gidan duk dan saboda Nailarh. *ABUJA NIGERIA* Alhmdllh jikin Nainarh kamar yanda Dr fawar yace ba wani ƙonewa tayi ba fatanta ce bata son zafi,kulawa sosai mom ke bata duk bayan ƴan lokuta sai ta leƙo ɗakin ta dubata,haka Fa'iza a ɗakin nasu ta wuni tunda su ka dawo daga hospital ɗin,Yumnah ma Ba'a barta a baya ba dan duk tafi kowa shiga damuwa,ya Adnan ma sai da dare yayi sosai tukun ya tafi gida,Irfan tunda ya fice daga gidan bai sake dawowa ba,Nainarh ta ji haushin rashin nuna damuwarsa akan abunda yayi mata,wani sabon tsanarshi ne ya rufeta,saƙe saƙen ta yanda zatai taking revenge dan shima yaji zafin da taji. Yanzu ma zaune take gaban door glass ita kaɗai a ɗakin,skert ne a jikinta haɗe da riga mai hannu ɗaya saboda ciwan dake chest ɗinta, sai mayafi dake saman kanta,ta yaye curtains ɗin dake jikin door ɗin,zuba ma cikin Estate ɗin ido tayi tana kallon securitys ɗin dake kai kawo,turo ƙofar ɗakin da aka yi ne yasa tayi saurin kai dubanta ga ƙofar,Enaaya ce ta shigo da gudu tana buɗema Nainarh hannu,riga da wando ne a jikinta,kanta babu scaf anyi mata space buns,ga wasu baby ribbons da aka sa mata masu kyau, kamar ko da yaushe fuskarta na manne da glasses, murmushi Nainarh ta saki har ta ƙaraso inda take,side hug tayi mata saboda ciwan jikinta “sannu Aunty Nainarh,ya jikin?” Enaaya ta faɗa da tsantsar kulawa tana kallon ciwan dake jikin Nainarh “naji sauƙi Enaaya,ke da momy ku ka zo?” “A'a,momy na gida,dady ne ya kawo ni na gaishe dake” murmushi ta saki tana shafa fuskarta “nagode sosai,ya ki ka baro momy?” “tana lafiya,ki zo muke parlor dady na can” “no ba sai naje ba Enaaya” “please ki dai zo muje,sai ku gaisa ya sake maki ya jiki” Enaaya ta faɗa tana marairaice fuska,gyaɗa mata kai Nainarh tayi,tashi tayi daga saman chair,ƙofar fita daga ɗakin su ka nufa Enaaya na riƙe da hannunta,suna isa bakin ƙofar ana buɗe ƙofar,sauri dakatawa su ka yi,ya Adnan ne ya turo ƙofar, blue Black ɗin yadi ne a jikinshi mai taushi,kanshi sanye da hula,sai ƙamshi yake kamar wanda zaije zance,da sauri Nainarh taja mayafin dake kanta ta rufe jikinta,saurin sakin hannunta Enaaya tayi tana bi ta gefan dadyn nata ta fice daga ɗakin,ɗan sadda kai tayi tana gaishe shi da kulawa ya amsa mata “lafiya lau Nainarh,ya jikin na ki,hope dai da sauƙi?” “da sauƙi Alhmdllh” “Allah ya ƙara afuwa,fatan dai babu inda ke maki ciwo, sannan wurin ya daina zafi” “Eh ya daina,babu in da ke man ciwo” “masha Allah haka ake so,Allah ya ƙara lafiya” “Ameen,ya Aunty Nadiya?” “tana lafiya” “ina gishe da ita” gyaɗa mata kai yayi,shiru su ka yi babu wanda ya sake cewa komai, Nainarh jira take yace mata sai anjima,shima jira yake tace mashi,ɗan ɗago da kai tayi kalleshi ganin ita yake kallo ne yasa tace “yaya ko akwai wani abu” saurin girgiza mata kai yayi “ba komai Nainarh, Allah ya ƙara afuwa sai anjima,ki kula da kanki” “in sha Allah,Nagode” gyaɗa mata kai kawai yayi ya juya ya bar bakin ƙofar,maida ƙofar tayi ta rufe ta koma cikin ɗakin,bayan tafiyar ya Adnan da kamar five minutes Yumnah ta shigo ɗakin hannunta riƙe da ƙatuwar ledar Eatery Enaaya na bayanta riƙe da wata ledan,da mamaki take kallonsu har su ka ƙaraso in da take,saman table ɗin dake gabanta Yumnah ta ajiye ledan “gashi inji ya Adnan” Yumnah ta faɗa,Enaaya ma ajiye ledan dake hannunta tayi tana juyawa da sauri tace “Allah ya ƙara sauƙi Aunty Nainarh,sai da safe” da kallo kawai Nainarh ta bita har ta fice daga ɗakin,maida dubanta tayi ga Yumnah, murmushi ta sakar mata “gashi nan get well soon ne ya kawo maki” kallon Yumnah tayi kawai without saying anything,she's just surprised about ya Adnan “Nainarh!,ba kice kin gode ba” Yumnah ta faɗa, murmushi ta sakar mata “ke zan ma godiyar ne,ko ke ki ka kawo man?” ɗan zaro ido Yumnah tayi “oh na manta,ashe fa ba ni na saya maki ba” ta faɗa tana juyawa zata bar wurin,riƙo hannunta Nainarh tayi “dallah can wasa nake maki,nagode ki bani number sa nayi mashi godiya” taɓe Yumnah tayi tana zama saman Arm chair dake kallon wacce Nainarh ke zaune,ledan ta jawo tana buɗewa dan ganin miye a ciki,lafiyyan kebab ne with vegetables sai ƙamshi yake,ga beef shawarma,ɗan kallon Nainarh Yumnah tayi tana murmushi dan da ga kallon kebab har wani motsi kunnenta yake,ɗayan ledan ta buɗe kwalin pizza ne sai ƙatuwar robar Ice cream,ledar da Enaaya ta ajiye Yumnah ta jawo,fresh fruit ne “wow gaskiya ya Adnan na ji dake,wallahi ba kiji yanda yawuna ya tsinke ba” Yumnah ta faɗa tana sake buɗe ledan kebab ɗin,ɗaya ta ɗauka ta kai baki,lumshe ido tayi tana wani gyaɗa kai irin na daɗin nan,murmushi Nainarh ta saki tana girgiza kai kawai,sake ɗaukar wani tayi ta kai baki,saurin janye ledan Nainarh tayi “ki bari a kaima mom da Aunty Fa'iza mana” murmushi Yumnah ta saki “wallahi ba ki ji daɗin sa ba ne, kamar kunen mutum zai tsinke” “yanzu dai fara kai masu tukun kafin kunen naki ya tsinke” dariya Yumnah ta yi,ledan pizza ta buɗe ciro kwalin da robar Ice cream ɗin tayi,a cikin ledan ta zuba ma mom da Fa'iza, ice cream ne kawai bata ɗaukar masu ba tunda ɗaya ne,ficewa tayi tana cema Nainarh yanzu zata dawo, kitchen ta nufa direct,a plate ta zuba ma mom fa'iza kuma ta bar mata a leda, bedroom ɗin mom ta nufa ta kaimata nata kafin nan ta nufi part ɗin mamy bata samu kowa masu aikinta na part ɗin su mamy kuma na part ɗin dady, bedroom ɗin fa'iza ta shiga har tayi shirin kwanciya,tana bata ta fice ta koma part ɗin su. *Uncle Hashim's house 😡* Laatifa na daga kan chair zaune gaban table ɗinta tana opreting system ɗinta yayinda balqis ke zaune tsakiyar bed ɗinta,dukan su PJ's ne a jikinsu,ɓata fuska balqis tayi tana turo baki “wai Aunty laatifa magana fa nake kinyi shiru,mi yasa wai duk ku ka share ni ne keda momy,ni fa ba laifina bane laifin dady ne” still laatifa bata ce mata ƙala ba aikin gabanta kawai take “dan Allah mi yasa za ku man haka idan da sabo ai yaci ace kun saba da halin dady,haba Aunty Laatifa idan ku ka haɗe man kai ke da momy ya ku ke so nayi,please Aunty nah” iska laatifa ta ɗan furzar,juyowa tayi tana fuskantar balqis ɗin, murmushi balqis ɗin ta sakar mata “Balqis ban san mi yasa baki jin magana ba,mi zai sa ki nace dole sai kinyi aiki a hospital ɗin nan,kuma da ki ke magana mun haɗe maki kai ba dole mu haɗe maki kai ba ince a gabanki mahaifinki yayi ma momy iya dake bareni da ba komai bace a cikin gidan nan,kiyi haƙuri kawai ki janye wannan burin naki,kiyi haƙuri kiyi aiki a in da yake so” tunda Laatifa ta fara magana yanayin fuskar Balqis ya sauya zuwa tsantsar damuwa,a halin nan na yanzu bata jin zata iya haƙura da Aiki a hospital ɗin nan “sannan shawarar da zan baki wallahi wannan soyayyar ta SAM dake zuciyarki kiyi gaggawar kasheta,da ina ganin dady zai sauka ya amince amma yanzu na fahimci babu wannan,kiyi haƙuri Allah ya baki mai sonki wanda mahaifinki ke so amma ba SAM ba” wasu irin hawaye ne su ka taru a idon balqis dama tun da daɗewa zuciyarta ke raya mata ba lallai ta samu SAM ba duba da shaƙuwar dake tsakaninshi da yayarta sai take ganin kamar soyayyace tsakanin su kawai ta ɓoye mata ne shiyyasa kullum ta ke nuna mata illar dake cikin dagewar da take akan tana son SAM ɗin “kiyi haƙuri duk da ba haka na so ba, amma ya zama dole, nayi maki sha'awar Auren SAM amma mahaifinki bazai Amince ba,shi kanshi SAM kafin ki samu soyayyar shi ba ƙaramin aiki bane balle a zo ga dadyn ki ya amince,kiyi haƙuri kawai in sha Allah zan tayaki da Adu'a Allah ya baki miji mai sonki fiye da yanda ki ke son SAM” “mi yasa ki ke faɗin mahaifina ke ba mahaifinki bane?” Balqis ta faɗa hawaye na bin cheek ɗinta, murmushin takaici Laatifa tayi tana faɗin “Balqis da nake ganin dady a matsayin mahaifina amma yanzu na tabbatar da ba mahaifina bane,ina zaune gidan nan ne saboda mahaifiyata amma ba dan kowa ba” jan hanci balqis tayi har time ɗin hawaye na zuba daga idanunta,laatifa ce ƙwarin gwiwarta amma yau ta nuna mata itama ta gaji “Aunty laatifa dan Allah karki ce na haƙura da ya SAM wallahi ina son shi,son da nake jin bazan iya rayuwa babu shi ba” wani kallo laatifa tayi mata,fashewa tayi kuka tana faɗin “idan ki ka ce na haƙura dashi ya ki ke so nayi, wallahi bazan iya rayuwa ba tare da ya SAM ba” ɗan rintse ido laatifa tayi ta buɗe tana girgiza kai irin ya zanyi maki ki fahimta ɗin nan,tasowa tayi daga kan chair da take zaune ta nufo balqis ɗin,zama tayi kusa da ita,hannu tasa ta shiga goge mata hawayen dake bin cheek ɗinta “kiyi haƙuri Balqis duk wasu qualities da ki ke ganin SAM yana da su a irin mijin da ki ke so, ki sani akwai maza bila'adadin a duniya masu irin wannan qualities ɗin dama wanda su ka fishi,in Sha Allah zaki samu miji wanda yafi SAM,kiyi haƙuri kinji” wani irin kallon Balqis ɗin tayi mata kafin ta sauke ajiyar zuciya a hankali ta ce “Aunty laatifa kina son ya SAM ne!?” ta faɗa tana tsareta da idanu,kamar saukar aradu haka laatifa taji tambayar balqis a kunnenta,saurin zame hannunta dake kan fuskar Balqis ɗin tayi tana Binta da wani irin kallon “Aunty laatifa tuntuni ina lure dake kamar kina ɓoye man wani abu a game da alƙarki da ya SAM,a lokacin dana nuna ina son ya shi da kin faɗa man soyayya ku ke wallahi da ban wahalar da kaina ba,amma miyasa sai da nayi nisa a soyayyar shi zak...” bata ƙarasa ba a dalilin tsawar da Laatifa ta daka mata,kuka Balqis ɗin ta fashi dashi mai tsuma zuciya tana faɗin“mi yasa sai da ki ka bari soyayyar shi tayi man mugun kamu za kice na rabu da shi” “zan mareki balqis idan bakin ki bai dai furta wannan maganar ba,dama kallon da ki ke man ke nan,ke ko wani yace maki zan iya soyayya da SAM ke sai ki yarda,kin bani mamaki Balqis,saboda na zauna ina baki shawara shine zaki kalli tsabar idona ki faɗa man wannan maganar,SAM he's just my favorite brother daga haka bashi da wani matsayi a zuciyata,kinfi kowa sanin bazan taɓa iya yima SAM son Aure ba,bari na tuna maki idan kin manta SAM he's my younger brother not my boyfriend” cikin muryar ku ka Balqis tace “idan ke baki sonshi shi yana sonki ai” girgiza kai Laatifa tayi, cikin ɗan ɗaga murya tace “balqis wai kin rasa tunaninki ne,mi ke damun brain ɗinki ne,kamar yanda yake favorite brother a wajena haka nake favorite sister a wajenshi, ke kin san da ace yana sona bazamu kai tsawan wannan shekarun ba tare da ya furta man ba,SAM bazai taɓa sona da sunan Aure ba idan ma wani abu ke maki yawo a kai ya daina” “idan har ba sonki yake ba, mi yasa ya ware ki a cikin mu ke kaɗai yake kulawa, ke kaɗai yake saurare, ke ka ɗai ya ɗauka a matsayin ƴar uwarshi, saboda ke ya kawo S N J T Nigeria, yanda yake baki kulawa ko mom baya ba kulawa haka” wani kallo laatifa ta shiga bin Balqis da shi she's be came speechless akan maganganun Balqis “how many times yake faɗin ki bar Nigeria ki dawo gareshi, idan har ba sonki yake ba bazai yi maki hakan ba” tashi Laatifa tayi daga saman bed ɗin rai ɓace,dan muddin ta cigaba da zama kusa da Balqis tana iya ɗauketa da mari saboda wannan kalaman da take faɗa,da wani yace mata Balqis zata mata wannan zargin bazata taɓa yarda ba amma sai gashi da bakinta take faɗa mata wannan kalaman, Balqis ba komai ya sata faɗar hakan ba sai yanda Laatifa ke faɗin ta haƙura da SAM, a rayuwa idan da abunda ta tsana to ace ta haƙura da SAM, wayarta dake ajiye saman Nightstand Laatifa ta ɗauka, number SAM ta shiga sa mata a wayar da yake ta haddace, tana gama rubuta number tayi mata saving da red heart ɗin emoji, in da Balqis take ta dawo “karɓi ga number sa nan na sa maki kina iya kiranshi ki faɗa mashi duk abunda ke ranki, idan ma binsa za kiyi har can Ni mai iya yi maki booking flight ne kije har can ki sameshi ki faɗa mashi kina son shi,sannan ina so ki sani wannan ya zama last time da zaki sake man maganar SAM, duk wani abu da ki ka san ya shafi soyayyarki karki ƙara tunkarata dan wallahi ranki ne zai ɓaci” kallon wayar kawai Balqis take tana sauraronta ba tare da ta amsa ba,ƴar tsawa Laatifa ta mata “zaki amsa ko sai ranki ya ɓaci” amsar wayar Balqis tayi, duk sai taji ba taji ba daɗi ganin yanda ran Laatifa ya ɓaci, ta san Laatifa na matuƙar ƙoƙari a kanta,bata da wani zaɓi ne bayan hakan. “tashi ki fice man daga ɗaki” Laatifa ta faɗa babu alamun wasa tana nuna ma Balqis ɗin ƙofar fita, kallonta kawai Balqis ɗin tayi ba tare da motsa ba, bata taɓa ganin tsantsar ɓacin rai a idanun yayar tata ba irin na yau, juyawa Laatifa tayi ta nufi hanyar toilet tana faɗin “karki bari na fito na sameki a ɗakin nan” da sauri Balqis ɗin ta miƙe ta nufi Laatifa, hugging ɗinta tayi ta baya tana fashewa da wani kuka mai ban tausayi,ɓan ɓareta Laatifa ta shiga yi daga jikinta,ƙanƙameta Balqis ɗin tayi tana kuka “am deeply sorry about kalamai na,please Aunty Laatifa kiyi haƙuri, wallahi bazan sake furta irin wannan kalaman ba, kiyi haƙuri” kuka take sosai tana bata haƙuri,jin yanda take ku ka ne ya karya zuciyar Laatifa har cikin ranta take jin kukan Balqis ɗin “kiyi haƙuri Aunty laatifa bazan sake furta irin wannan kalaman ba,nayi kuskure kiyi haƙuri kar kiyi fushi dani” ajiyar Laatifa ta sauke ba tare da ta raba jikinsu ba tace“ki dunga sarrafa fushinki a yayinda ranki ya ɓaci,saam banji daɗin kalamanki ba,daga yau ki dunga sanin kalaman da zaki faɗa ma mutum idan ranki ya ɓaci,ba komai ya zo bakinki zaki faɗa ba” “to in sha Allah bazan sake ba Aunty laatifa,ki yafe man” ta faɗa kamar zata sake fashewa da wani kukan “shikenan ya isa haka,komai ya wuce,ni mai iya sadaukar maki da komai nawa ne,ki kwantar da hankalinki babu wani abu dake tsakanina da SAM,bana burin SAM ya Auri ko wace ƴa mace sama dake” ta faɗa still ba tare da ta raba jikinsu ba “na sani Aunty laatifa bazan sake maimaita wannan kuskuren ba” Jinjina mata kai laatifa tayi “yanzu ga number sa nan na sa maki kina iya kiranshi,ki daure ki sanar dashi duk wani abu dake zuciyarki” a ɗan shagwaɓe balqis tace “abuda ko na kirashi bazai ɗauka ba,please ke dai ki kira manshi” “A'a gaskiya bazan kira maki shi ba,ki kirashi kawai na san in sha Allah yaga number Nigeria ce zaiyi picking” “please Aunty nah” “bafa zan kira maki shi ba kiyi fighting soyayyarki da kanki, ki daure kawai ki kira sa in sha Allah zan cigaba da tayaki Adu'a,Allah ya karkato da tunanin sa gareki yaji duk duniya babu wacce yake so sai wannan kyakkyawar ƙanwar tawa” wani irin murmushin jin daɗi balqis ɗin ta saki “shikenan Aunty laatifa zan kirasa Please ki tayani da Adu'a Allah yasa dady ya Amince” “in sha Al...” bata ƙarasa ba ta dalilin jin balqis ɗin ta fita daga jikinta da mugun sauri,juyowa laatifa tayi da sauri,wani irin mummunan faɗuwa gabanta yayi ganin wanda ke tsaye zufa ce ta shiga keto mata,har tsawan wane lokaci ya ɗauka a ɗakin,kuka balqis ta fashe dashi saboda azabebben zafin daya ziyarci ƙwaƙwalwar ta a dalilin mugun riƙon da yayi ma hannunta, laatifa kamar zuciyarta zata fasa ƙirjinta ta fito,wani irin kallon yake binta da shi,kallon da yake mata ne ya ƙara rikitar da ita,rawa bakinta yake magana take son furtawa amma ta kasa tsoron abunda zai biyo baya ne ya mamayeta,fisgar balqis yayi ya fita da ita daga ɗakin,da sauri tabi bayan su “dan Allah d...”tun kafin ta furta abunda ke bakinta ya juyo da mugun sauri,ji ka ke tasssss ya saukemata lafiyayyun maruka har sau biyu...    *Ep 43_44* ____________________________ ji ka ke tasssss ya saukemata lafiyayyun maruka har sau biyu,sakin hannun balqis yayi,cikin wata kalar murya wacce bata san shi da ita ba yace “who do you think you are da ki ke ƙoƙarin lalata man yarinya,saboda na barki a cikin gida na yasa ki ke ƙoƙarin lalata man tarbiyyar ƴa,tunda ya gama lalataki har yau kin rasa mai kallonki yace yana soki, shi ne ki ke ƙoƙarin ganin itama ya lalata ko,zaki yi mata booking flight taje ta sameshi ko,this should be the last time da zan ganki tare da ƴata, albarkacinta kawai ki ke ci yasa har yanzu muke tare da ke,daga yau baki ba ƴata nayi maki iyaka da ita,stay away from my Daughter if not wallahi wallahi wallahi rantsuwa uku nayi ko?...” nuna ta da index finger ɗin shi yayi yana girgiza kai irin kinsan mi zai biyo baya ɗin nan,wasu irin zafafan hawaye ne su ka wanke fuskar laatifa haka ma Balqis,fisgar hannun balqis yayi da nufin fita daga ɗakin,momy su ka gani tsaye fuskarta a ɗaure kamar wacce aka aiko ma saƙon mutuwa,raɓawa yayi ta gefenta ya fice daga ɗakin riƙe da hannun balqis dake kuka,a fusace momy ta juya tabi bayan su, a parlorn ya tsaya da Balqis,kunnenta ya riƙe gam,cikin kausasheshiyar murya ya fara magana “me na faɗa maki game da waccan yarinya?” rintse ido Balqis tayi saboda zafin da taji a kunnenta,sake murɗe kunen yayi,ƴar ƙara ta saki hawaye na bin cheek ɗinta “dan Allah dady kayi haƙuri,wallahi ba laifin Aunty laatifa bane,laifina ne dan Allah kayi haƙuri” tsawa ya daka mata “yi man shiru ko nayi ƙasa ƙasa dake a wajenan shashashar banza,wallahi daga yau ko hanya na sake ganin ta haɗaki da ita sai ranki yayi mummunan ɓaci,kina jina” ya faɗa yana daka mata tsawa “naji dady,dan Allah kayi haƙuri karka rabani da Aunty laatifa” ɗayan hannunsa yasa ya bige bakinta “na sake jin ko sunanta bakin ki ya furta sai naci mutuncinki,baki ba ita nayi maki iyaka da ita,idan kuma har ban isa ba to” kuka balqis ta fashe dashi fiye da wanda take jin furucin dadyn nata akan ƴar uwarta, girgiza mashi kai ta shiga yi tama kasa magana sai hawaye dake zarya a cheek ɗinta “get out from my side useless kawai” ya faɗa yana sakin kunenta,da gudu ta nufi bedroom ɗinta tana kuka, Ajiyar zuciya ya sauke yana huro iska mai zafi daga bakinshi,juyawa yayi da nufin zuwa bedroom ɗin shi,momy ya gani sanye da hijab tana aikin tura box,da tsantsar mamaki yake binta da ido harta ƙaraso tsakiyar parlorn, trolley ta saki ta juya zuwa ɗakin Laatifa,da mugun sauri ya riƙo hannunta,a masifance ta fisge hannunta daga nashi,idanunta sun ƙaɗa jawur hawaye ne kwance a cikin su “how dare you to touch me,don't eve touch me again our marriage is over” juyawa tayi ta nufi bedroom ɗin Laatifa,sake riƙo hannunta yayi,yanzu riƙo yayi mata ba na wasa ba,fisgarta yayi zuwa cikin parlorn a saman sofa ya zaunar da ita “baki da hankali ne maimunatu,ina ki ke tunanin zaki a wannan lokacin,ko baki san ƙarfe nawa ba ne??” ya faɗa yana nuna mata agogo dake manne jikin bango “is not your business,ko ina zani bai shafeka ba” “calm down,idan saboda abunda nayi mata ne ki ke shirin aikata haka,samunta nayi tana ƙoƙarin cusama Balqis wannan yaron har faɗi take zata mata booking flight taje ta sameshi a can” “bai shafe ni ba,ka sani babu sauran wani Aure tsakanina da kai,yau bazan kwana gidan nan ba,ka biyoni da takardata har gidan iyaye na” “kina hauka ne saboda wannan abun ki ke faɗin our marriage is over,zaki tafi gidan ku,ko dai kin fara shan wani abu ne ban sani ba” “abunda ka ke sha shi nasha,wallahi sai na tafi,kuma bani ba kai,yanda ka tsani ƴata haka ni ma na tsaneka” kuka ta fashe dashi mai ban tausayi “kai azzalumin uba ne Hashim kuma azzalumin miji,wallahi haƙi na dana laatifa sai ya ga bayanka,macuci kawai wanda bai san haƙƙin dake kanshi ba,mai nuna wariya a tsakanin ƴaƴanshi,wallahi nayi dana sanin Aurenka a rayuwata,ka sake ni wallahi bazan cigaba da zama da...” tsawa ya daka mata wacce tasa dole tayi shiru,Laatifa na daga bakin ƙofar ɗakinta duk abunda ke faruwa akan kunenta,kuka take sosai bata taɓa jin muguwar tsanar Mahaifinta ba irin yau, tayi baƙin cikin kasancewar shi mahaifinta, tayi fatan ace ta mutu tun da daɗewa bata riski irin wannan baƙin cikin ba “ni ki ke furta ma waɗan nan kalaman?” ya faɗa cikin ɗaga murya yana nuna kanshi “na faɗa maka haka, fiye ma da haka za kaji daga bakina, wallahi nayi dana sanin Auren ka,ka sawaƙe man” ɗan rintse ido yayi yana girgiza kai,duk fa abunda yake aikatawa da alƙarshi da mamy yana son mom maimunatu kuma baya son rabuwa da ita,tashi tayi daga saman sofa tana goge hawayen dake fuskarta, bedroom ɗin Laatifa ta nufa “yau ba sai gobe ba zamu bar maka gidanka kai da ƴarka” da mugun zafin nama ya nufeta,fisgota yayi zuwa jikinshi,kuka ta fashe da shi tana ƙoƙarin ɓanɓare kanta daga jikinshi,janta yayi ta ƙarfi zuwa bedroom ɗin shi,ture shi take tana faɗin “ka rabu dani hashim,bazan cigaba da zama da kai ba” zaunar da ita yayi saman makeken bed ɗin shi,cikin kwantar da murya yace “ki tsaya ki fahimce ni munarh,ba wai bana son Laatifa ba ne,ina mata hak...” tsawa ta daka mashi “karka kawo man maganar banza,ka sani babu abunda zaka yi da zaisa na haƙura,baka son laatifa kowa ya shaida haka” “wallahi ina son Laatifa,ki tsaya ki fahimce abunda nake son na faɗamaki” “hashim ka riga ka makaro,gida dai sai mun bar maka yau ba sai gobe ba” girgiza kai yayi ya lura ba sauraren shi za tayi ba. kuka sosai take kamar ranta zai fita bata taɓa tunanin tsanar da dadynta ke mata har ta kai yayi mata iyaka da ƴar uwarta ba,ta jima sosai a bakin ƙofar ɗakin sai da kanta ya fara mata ciwo tukun ta sassauta ma kanta,wayarta dake ajiye saman dressing mirror ta ɗauka,missed call ɗin SAM ta gani har biyu,hawayen dake fuskarta ta share,kusan duk time da zata shiga cikin wani hali sai aci sa'a ya kirata kamar yana jin duk wani abu dake faruwa da ita,bin bayan kiran tayi amma har kiran ya katse baiyi picking ba, sake kira tayi karo na biyu still baiyi picking ba, ajiye wayar tayi ta nufi bathroom. Uncle hashim kusan kwana su kayi zaune yana lallashin mom maimunatu amma kwata kwata taƙi ta saurareshi saima kuka data sa mashi ganin zai dameta, babu yanda ya iya dan dole ya kawo ido ya zuba mata. Zukatan nan huɗu yanda su ka ga rana haka su ka ga dare har shi kanshi Uncle hashim da shi ne musabbabin komai. zazzaɓi mai zafi ne ya rufe Balqis ga matsanancin ciwan kai saboda kukan data sha. *Second father's house* zaune yake saman chair,yayinda system ɗin shi ke ajiye saman desk yana opreting,shirt ce mai gajeran hannu a jikinshi haɗe da short, idanunshi a manne suke da glass ya zuba su akan system  ɗin shi da yake aiki, Aunty Nafisat na daga kwance saman bed ta baje sai kwasar baccinta take,ƴar baby doll ce a jikinta pink color yayinda kanta ke sanye da black ɗin hula,baccinta take peacefully. mug ɗin coffeen dake ajiye gefe ya ɗauka ya kai bakinshi,yayinda yake tsayar da idanunshi akan system ɗin, ya shafe kusan awa biyu yana aikin kafin ya kashe system ɗin,saurin ɗaukar wayarshi dake gefe yayi a dalilin ƙarar da tayi na alamar shigowar message,buɗe message ɗin yayi, karanta abunda ya ƙunsa ya shiga yi har ya kammala,ƙyataccen murmushi ya saki yana girgiza kai, yana shirin tashi daga saman chair sai ga kira ya shigo wayar daga Uncle Ubaid wato sirikinshi mahaifin Aunty Nafisat,kallon kiran yake cike da mamakin ko lafiya yake kiranshi a irin wannan lokacin duk da kasancewar shi shugabanshi a wurin aiki,har kiran ya katse baiyi picking ba, ya Naeem yanda wata ɗabi'a muddin na gaba dashi ya kirashi baya taɓa picking har sai kiran ya katse tukun ya kira da kanshi, kiran na katsewa yayi dialing number, ringing biyu Uncle Ubaid yayi picking,cike da ladabi ya gaishe dashi bayan ya amsa sallamar da yayi mashi,da kulawa ya amsa mashi yana faɗin “Afuwan na tashe ka daga bacci” murmushi ya Naeem yayi yana faɗin “babu komai dady aiki ma nake ban kai da kwanciyar ba” “ok dama akwai wani case da nake son ka yi aiki a kanshi, shaf mantawa nayi ɗazu a office ban baka ba, yanzu ma gudun karna manta ne yasa na kira ka a wannan lokacin” “ba damuwa,akan miye case ɗin?” “case ɗin about kidnapping ne,wasu yara ne aka yi kidnapping tsawan wata biyu kenan, kasan mutanen mu yanda su ke musamman ace marasa ƙarfi ne,sai abu ya lalace tukun za suyi involving force,amma zan tura maka da C D,gobe idan kazo office ka same ni zan baka files ɗin case,sai na maka ƙarin bayani akan case ɗin, Please Naeem na san ka da hazaƙa da maida hankali akan aiki,ba na da shayi ko ɗar akan ka please kayi aikin yanda ya kamata,aiki ne mai matuƙar mahimmanci da haɗari,saika maida hankali sosai” “in sha Allah dady,zai tafi yanda ka ke so” “yawwa haka nake son ji,gobe sai ka same ni a office” “to Allah ya kaimu goben lafiya” “Ameen,mu kwana lafiya” da Ameen ya Naeem ya amsa, rejecting Kiran uncle Ubaid yayi,ɗan shiru ya Naeem yayi yana tunanin wani abu, message ɗin da aka turo mashi ya sake dubawa kafin ya tashi, switch ɗin ɗakin ya nufa ya kashe hasken ɗakin tukun ya nufi bed,ajiye wayarshi yayi haɗi da cire glasses ɗin dake idonshi tukun ya kunna bedside lamp,kwanciya yayi bayan ya karanta Adu'a kwanciya bacci ya shafe jikinshi da na Aunty Nafisat, murmushi yayi yana jawota jikinshi haɗi da ja masu duvet. *UNITED STATE❤* _*Las Vegas (Nevada)*_ tunda su ka dawo daga hospital bayan sun gama shagalin su take zaune a ɗaki ita kaɗai Aunty Sophia ma data shigo fita tayi domin haɗa mata dinner dai dai da lafiyarta,mrs Malika kuwa tunda su ka dawo bata tako zuwa ɗakinta ba har yanzu fushi take da ita kan abunda tayi ma mijinta ga wani sabon tsari data ɓullo mata na sai ta rabu da shi. zaune take tsakiyar bed ɗinta ta jingina da head board ɗin bed ɗin,idanunta a lumshe kamar mai bacci,PJ ne a jikinta riga da wando masu taushi white color. wayarta dake ajiye saman Nightstand ce tayi ƙara alamar shigowar message,ɗan kallon wayar kawai tayi da kamar bazata ɗauka ba sai kuma ta zura hannu ta jawo wayar. shiga cikin message ɗin tayi, scrolling message ɗin ta shiga yi,jifa tayi da wayar saman bed bayan ta kammala karanta message ɗin,tsaki taja tarasa miye matsalar wannan ɗan tahalinkin da ya damu rayuwarta ko dan kawai yaga ta zuba mashi ido ne yasa yake mata wannan shiga hancin ne,wannan kusan message na uku ke nan daya tura mata a yau,sake jan wani tsakin tayi. A hankali ta turo ƙofar ɗakin ta shigo hannunta riƙe da wasu papers, da ido Nailarh ta bita har ta ƙaraso gaban bed ɗin,zama tayi tana faɗin “baby ya jikin naki” ta faɗa idanunta na kan pepars ɗin data shigo da su without looking her position,kallonta kawai tayi without answering her,bata damu da ƙin amsa mata da ba tayi ba, pepars ɗin ta miƙa mata “gashi yanzu Joseph ya kawo man,na cike Form ɗin nayi signing zuwa gobe zan aika mashi da nashi saboda ya shigo U S jiya,kome ke nan idan ya dawo da nashi Form ɗin zan kawo maki ki gani,fatan kinyi farin ciki yanzu?” still she's not looking at her,ɗan ajiyar zuciya Nailarh ta saki “saboda haka ne yasa duk ki ka shiga damuwa haka?” banza Malika tayi da ita,matsowa Nailarh tayi kusa da ita,kwantar da kanta tayi saman shoulder ɗin ta a hankali tace “sweetheart idan baki son rabuwa dashi karki cutar da kanki,ki ƙyale ni nayi abunda nake so kema ki zauna da mijinki” wani kallo Malika tayi mata ba tare da tace mata ƙala ba,kallonta itama Nailarh tayi,turo ƙofar ɗakin Aunty Sophia tayi ta shigo hannunta ɗauke da tryan data haɗa ma Nailarh dinner,sadda kanta tayi ƙasa harta ƙaraso cikin ɗakin,a saman table ta ajiye dinner,kallon Malika tayi “ma'am dinner is ready” jin jina mata kai Malika tayi “thanks U Sophia” gyaɗa kai Aunty Sophia tayi tana kallon Nailarh “gud Night baby” tana faɗa haka ta fice daga ɗakin,trayn Malika ta ɗauko,a saman bed ɗin ta ajiye,da kanta ta shiga ba Nailarh,kallonta kawai Nailarh take tana ganin yanda gaba ɗaya mood ɗin ta ya canza saboda kawai zata rabu da wannan mijin nata,ɗaukar trayn tayi ta fice bayan ta kammala bata,da ido kawai Nailarh ta bita,bata sake dawowa ɗakin ba har Nailarh tayi bacci. *ABUJA NIGERIA* washe gari tunda asubar fari mom maimunatu ta fice daga ɗakin dady,da zai fita sallah ya manta ya bar ƙofar a buɗe hakan ne ya bata damar ficewa daga ɗakin,direct ɗakin Laatifa ta nufa box ɗinta na nan parlor Kamar yanda su ka barshi jiya ,turus ta tsaya gabanta na wani irin faɗuwa ganin yanda ɗakin Laatifa ya koma,sakin ƙofar tayi ta nufi cikin ɗakin tana bin ko ina na ɗakin da kallo, duk wani abu mai amfani na laatifa babu shi a ɗakin,hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba lokacin da idanunta su ka sauka akan box ɗin Laatifa da babu guda biyu. da mugun sauri ta nufi bakin ƙofar bathroom, nocking ta shiga yi tana kiran sunan laatifa amma taji tsit,sai da ma ta saurara da kyau tukun ta fahimci babu kowa a ciki,tura ƙofar toilet ɗin tayi ta shiga,wayam ta gani kamar ma anyi kwanaki ba'ayi amfani da shi ba,bugun zuciyarta ne ya tsananta,hankali a tashe ta fice daga toilet ɗin kamar mahaukaciya,tun a cikin ɗakin ta shiga ƙwala kiran sunan laatifa kamar maƙoshinta zai tsage,room by room na gidan ta shiga bincikawa tana kiran sunan Laatifa kamar zata fashe da kuka,hankali a tashe laure ta fito dan duk wanda ke gidan yaji yanda momy ke kiran sunan laatifa,tun kafin laure ta ƙaraso momy ta shiga tambayar ta ko ta ga inda laatifa ta shiga,idanunta da bacci bai gama isarsu ba ta shiga murzawa tana faɗin “cikin dare bayan hatsaniyar data faru na fito na kashe bulbs sannan na ɗauki ruwa a kitchen” saurin dakatar da ita momy tayi “ba dogon labari na tambayeki ba,ina Laatifa kin ga inda ta tafi??” “ai shine zan faɗa maki, tun cikin daren ta fice da da akwatunanta guda biyu” saurin dafe saitin zuciyarta momy tayi “ina tace maki za taje” ta faɗa tana ɗan ɗaga murya “ceman tayi wani waje mai nisa zata ,harma ta nemi yafiyata tace man ba lallai mu sake haɗuwa ba,tac..” ai tun kafin ta ƙarasa momy ta ɗauketa da mari mai rai da lafiya dai dai nan Balqis da uncle hashim da dawowarshi kenan daga masjid su ka faɗo parlorn,dafe cheek laure tayi tana kallon momy “saboda kina shashasha ki ka kasa sanar da wani a cikin mu” laure na kuka tace “wallahi hanani tayi ita tace karna sanar da kowa” cikin parlorn balqis da uncle hashim su ka ƙaraso,zubewa momy tayi saman sofa tana dafe kanta “na shiga uku ni maimunah,mi yasa laatifa zaki man haka,mi yasa, wannan wace irin rayuwace” ta faɗa tana fashewa da ku ka mai ban tausayi “kiyi haƙuri momy” laure ta faɗa,da sauri Balqis ta nufi ɗakin yayar tata,kusa da momy uncle hashim ya ƙaraso, kneeling yayi a gabanta yana kamo hannunta cikin kwantar da murya yace “kiyi haƙuri maimunatu” bai kaida ƙarasa faɗar abunda zai faɗa ba ta fisge hannunta daga nashi tana rufeshi da masifa “dama dole kace nayi haƙuri tunda ka riga ka cuceni,yanzu ai sai hankalinka ya kwanta laatifa ta bar maka gidanka sai ka zuba ruwa ƙasa kasha,amma ka sani tunda har kayi sanadin da laatifa tabar gidan nan nima na barshi har abada kuwa” “dan Allah kiyi haƙuri,kusan kwana nayi fa ina lallashinki nayi maki alƙawarin hakan bazata sake faruwa ba,kuma laatifa babu inda taje tana cikin Estate ɗin nan,Dan Allah kiyi haƙuri” balqis ce ta fito daga ɗakin Laatifa riƙe da pepar tana kuka,tun kafin ta ƙaraso cikin parlorn take faɗin “momy Aunty laatifa” sai kawai ta fashe da kuka ba tare da ta ƙarasa faɗar abunda zata faɗa ba,da sauri momy ta nufota, pepar dake hannun balqis ɗin ta amsa,karanta note dake jiki ta shiga yi kamar haka _na san ban kyauta maki ba momy,kiyi haƙuri ya zama dole ne na tafi,bana son Aurenki ya samu matsala a saboda ni,dady bazai taɓa yafe man ba,yayi man iyaka da ƴar uwata a yau,bazan iya cigaba da ganin tsanar da yayi man a idanunsa ba, shiyyasa kawai na yanke shawarar nayi nesa dashi ko hakan zai sa ya yafe man,ki yafe man momy idan da rabon mu sake haɗuwa zan dawo gareki,ki kula man da kanki_ _*Ina sonki uwa ta gari,zanyi kewarki sosai*_ jefama uncle Hashim paper tayi lokacin data gama karanta abunda paper ta ƙunsa,fashewa tayi da kuka tana faɗin “yanzu sai hankalinka ya sake kwanciya Laatifa ta tafi kamar yanda kaso,wallahi Allah sai ya saka mana,ka cuci ƴarka ka cuci kanka” tana kaiwa nan ta nufi ɗakinta tana kuka, Balqis kuka laure kuka kamar ransu zai fita,jiri Balqis ta fara ji ga wani mahaukacin zazzaɓi da ya sake rufeta,kanta kamar zai fashe,sofa ta nufa zata zauna tunkafin ta ƙarasa ga sofa ta yanke jiki ta faɗi,da gudu laure da uncle hashim su ka yi kanta,kiran sunanta ya shiga yi yana jijjigata,laure sai kuka take tana kiran sunan Balqis ɗin itama,suna a haka mom maimunatu ta shigo parlor da wani box a hannunta,ko kallon inda su ke ba tayi ba ta ɗauki wayarta haɗi da jan box ɗinta wanda ta bari tun jiya ta fice daga parlorn duk da tana jin yanda su ke kiran sunan Balqis. hakan da tayi ba ƙaramin taɓa zuciyar uncle Hashim yayi ba,hannu yasa ya ɗauki balqis ɗin a kafaɗar shi,ficewa yayi da ita a hanzarce,yana isa parking space motar momy na ficewa daga gidan,a mota yasa Balqis ɗin,key yayima motar ya fice zuwa hospital. Mom fitowarta kenan daga part ɗin dady bayan gama ta ƙaddamar su akan Auren Irfan ɗin da har yanzu dady yaƙi haƙura,sanye take da hijab har ƙasa hannunta riƙe da tasbaha, bedroom ɗinta ta nufa kwata kwata bata lura da mutum dake kwance kan sofa ba harta kai bakin ƙofa,hannunta ta ɗaura kan handle ɗin ƙofa jin an kira sunanta ne yasa ta dakata,ƙarasowa su ka yi har inda take,cike da girmamawa su ka shiga gaisheta “good morning mom” murmushi ta sakar masu tana amsa masu gaisuwar “morning,how was your night,I hope you slept well?” “Alhmdllh” su ka faɗa a tare, murmushi ta sake sakar masu tana shafa fuskar Nainarh “how was your body,I hope u feel better now” “Alhmdllh mom,I feel much better now” “Alhmdllh,Allah ya ƙara lafiya,ya tsare gaba” da Ameen su ka amsa,jinjina masu kai tayi “kuje ku gaishe da dadyn ku” To su ka ce,barin bakin ƙofar su ka yi,idanun Yumnah ne su ka sauka akan mutum dake kwance saman sofa,ƙara ta saki dan tashin farko tsorata tayi,saurin riƙeta Nainarh tayi tana tambayar lafiya,da sauri mom ta nufo cikin parlorn dan bata kai da ƙarasawa ciki ba Yumnah tayi ƙara “lafiya Yumnah ki ke wannan ƙarar haka mai makon kiyi salati,kwata kwata wanan ba ɗabi'a bace ta gari” sofa ta nuna masu “mutum ne a kwance”saurin kallon sofa su ka yi, ɗan zaro ido mom tayi,bulbs ɗin parlorn a kashe su ke sai ɗan hasken bulbs ɗin kitchen daya hasko parlorn hakan yasa basu gane waye ba. har gaban sofa mom ta ƙarasa yumnah tunda ta maƙalƙale jikin Nainarh ko motsi ba ta yi sai zare ido take kamar wacce aka kama tana satar naman miya. mayafin dake saman fuskarta mom ta yaye zaro ido tayi tana ambatar sunanta “LAATIFA!” jin sunan data furta ne yasa yumnah sakin Nainarh ta nufo sofa,bayanta Nainarh ta biyo,ɗan bubbuga hannun sofa mom tayi tana kiran sunanta,a tsorace ta farka tana faɗin innalillahi wa Inna ilaihi raji'un,saurin riƙo hannunta mom tayi “laatifa lafiya ki ke, What's wrong with u, why are u slept here??” mom ta shiga jera mata tambayoyi,iya jiya kawai har wata irin rama tayi ga jirwayen hawaye nan a cheek ɗinta bakinta ya bushe sosai,kallon mom ɗin tayi ba tare da tace komai ba “Aunty laatifa kiyi magana mana” yumnah ta faɗa kamar za tayi ku ka,sadda kai tayi ƙasa hawaye na bin cheek ɗinta ɗan ajiyar zuciya mom ta sauke,kama hannunta tayi “tashi muje kiyi sallah kinji” bin mom ɗin tayi har bedroom ɗin ta, bayan su su Nainarh su ka bi amma mom tace su wuce kawai wajen dady,juyawa su ka yi zuwa part ɗin dady,sun ɗan jima a part ɗin dady kafin su ka fito duk da ba karatu yayi masu ba,tun da Nainarh ta ƙone ba suyi karatu ba yaune ma taje part ɗin dady dan ta gaishe da shi. Laatifa bayan da ta gama sallah asuba,kwanciya mom tace tayi ta hutu ita kuma ta fice zuwa part ɗin dady,a zaune ta sameshi kamar yanda ta barshi,ƙarasawa tayi har gaban shi,zama tayi kamar mai ɗaukar karatu, littafin dake hannunshi ya ajiye yana kallonta “lafiya dai ko katte?” ɗan ajiyar zuciya ta sauke tana bashi labarin ganin laatifa da yanayin da su ka ganta “da alama anan ta kwanta,na tambayeta amma bata bani amsa ba,kasan halin hashim yanzu haka wani abu ya haɗa shi da ita har yayi mata abunda yasa ta bar gidan cikin dare” tunda mom ta fara magana dady ke Binta da ido ƙala baice ba,amma kallo ɗaya zaka mashi ka hango tsantsar ɓacin da ranshi yayi “ban san wane irin uba bane ba hashim,kwata kwata bai san role ɗin shi ba a matsayin shi na mahaifi,ya ɗauki karan tsana ya ɗaura ma yarinya saboda Sam,in banda abun shi yaushe rabun Sam ma da ƙasar da zai zauna yana gallaza ma yar sa saboda shi,wallahi har ga Allah bazan iya yafe ma wanda yayi ma Sam wannan ƙazafin ba,sun hana ni zama da ɗana, duk sun ɗauki karan tsana sun ɗaura mashi” ta faɗa kamar zata sa kuka, da alama abun ya daɗe yana damunta “waye ya ce maki ya tsani Sam?,shifa tamkar ɗan su ne taya za su tsane sa?” “basa son shi mana,duk kai ka basu ƙwarin gwiwa,da baka wulaƙanta ɗan naka a gaban su ba,ka ƙi tsayawa ka fahimce shi a lokacin da yake buƙatar taimakon ka da duk hakan bata faru,da kaima yanzu haka kana tare da shi,ban san mi yasa kun cika son kanku da yawa ba,ya kamata ku riƙa bincike kafin ku yanke hukunci” nannauyar ajiyar zuciya dady ya sauke “ya isa haka Zulaihart,bana son kina tada abunda ya wuce,komai daya faru kuskure ne,na riga da nayi kuskure,kuma dan kinga Laatifa baki da tabbacin saboda hakan ne yasa ta fito gida” girgiza kai mom tayi “wallahi ni na san baƙin halin hashim,babu abunda tayi mashi bayan wannan” “ya isa haka dan Allah,yanzu ina Laatifa take?” “na barta a ɗaki tana bacci” “to shikenan,zan kira Hashim ɗin,zanji mike faruwa” taɓe baki mom ɗin tayi ba tare da tace ƙala ba,wayarshi dake ajiye saman sofa ya ɗauka, Number uncle Hashim ya shiga dialing harta katse baiyi picking ba sake kira yayi still bai ɗauka ba. tashi mom tayi ta fice daga ɗakin,bedroom ɗinta ta koma,with full of surprise mom ke kallon Laatifa dake yafa mayafin abayar dake jikinta,sakin ƙofar tayi ta ƙarasa cikin ɗakin “lafiya dai ko Laatifa,ina ki ke shirin zuwa haka?” saurin kallon mom tayi sai kuma ta sadda kanta ƙasa,har in da take tsaye mom ɗin ta ƙaraso,hannunta ta kama zuwa bakin bed,zaunar da ita tayi itama ta zauna “lafiya laatifa,mi ya sa ki ka bar gida cikin dare,ina kuma ki ke shirin zuwa yanzu??” mom ta jera mata tambayoyin tana kafeta da ido cike da son jin amsa daga gareta,duƙar da kai laatifa tayi a hankali tace “mom mun samu saɓani ne da dady”kaf abunda ya faru bata ɓoye ma mom ba,ba ta yi mamakin jin abunda uncle Hashim ɗin yayi mata ba dama ta san zai iya fiye ma da hakan,kamo hannunta tayi cikin nata “amma ai Laatifa da baki fito a wannan lokacin ba ko dan saboda mahaifiyarki” “mom bana da wani zaɓi ne,bazan iya jurar ganin saɓani a tsakanin su ba saboda ni” “haka ne amma kinga dare ne,ke macece bai kamata ki fito a wannan lokacin ba” shiru kawai Laatifa tayi ba tare da tace komai,ɗan ajiyar zuciya mom ta sauke “yanzu ina ki ke shirin zuwa dana ga kina yafa mayafi” shiru laatifa tayi tana wasa da gefen mayafinta without answering her “baza ki faɗa man ba” ɗan ɗagowa tayi ta kalli mom ɗin sai kuma ta maida kanta ƙasa“California” ta faɗa a hankali, mom was surprise da magananta “mi za kiyi a can?” mom ta jefa mata tambaya tana tsareta da ido “wajen Sam zan je” wani kallo mom ta jefe mata,tama rasa mi za ta ce mata,ɗan ɗagowa tayi ta saci kallon mom ɗin,kauda kai gefe mom tayi “shi yace maki ki zo,ko kawai ke ki ka yi deciding ki je?”mom ta jefa mata tambaya “shi yace na zo” ta bata amsa “kunyi waya da shi kenan?” “eh tun jiya munyi waya” ɗan ajiyar zuciya mom ta sauke “Laatifa!” ta kira sunanta in a serious tolk,ɗaga kai tayi ta kalli mom ɗin ba tare da tace komai ba “laatifa a matsayinki na mace wacce ba muharramarshi ba bai dace ace kije wurin sa ba,ko kin manta shine dalilin wannan matsalar da ki ke samu da dadyn ki??” “mom dady bazai yafe man ba,kuma zan koma S N J T ne na cigaba da aiki a can” “a ina zaki zauna kenan?” “gidan ma'aikata” “look laatifa maganar zuwanki California wurin sam ma bata ta so ba,ki yi zamanki anan har Allah yasa mahaifinki ya sauko” “amma mom...” da katar da ita mom tayi “karki ce komai,kiyi haƙuri dadynku zai yi magana da dadynki, idan ma bai sauka ya yafe maki ba,kiyi zaman ki anan a tare dani har lokacin da Allah kema zai baki miji kiyi Aure,amma maganar zuwa wurin sam ki barta” “ya riga yayi man booking flight tun jiyan” “karki damu zanyi magana dashi,ki kwantar da hankalinki kinji” “to Nagode mom” “yawwa ki kwantar da hankalinki ni ma momynki ce,zan zauna dake har Aurenki laatifa,nan ma fa gidan mahaifinki ne kuma darajarar ƴa mace gidan mijinta idan ba tayi Aure ba gidan mahaifinta,ki kwantar da hankalinki kinji” “momy bata san ina nan ba” “karki damu zan kirata yanzu,bari nasa Ishrat ta kawo maki breakfast” gyaɗa kai tayi a hankali,ficewa mom tayi daga bedroom ɗin,da kallo laatifa ta bita. komawa tayi ta kwanta,lumshe ido tayi kamar mai bacci. *Wai waye* Bayan ta ajiye wayar ta shiga toilet,ta shafe kusan 10 minutes a toilet ba tare da tana wani uzuri ba,tunanin yanda zata samu mafita daga wannan tashin hankalin kawai take,saƙe saƙe take kan yanda zata samu mafitar abun,zuciya bata da ƙashi babu irin tunanin da bai zo mata ba amma data tuna illar dake cikin hakan sai ta ture shi gefe. ganin ɓatama kanta lokaci kawai take kowace mafita zata zo mata da illa a cikin ta,haƙura tayi ta fito tana share hawayen ta,gaban dressing mirror ɗinta ta nufa,zama tayi saman stool ɗin dake wurin tana kifa kanta saman mirror table ɗin, ringing ɗin wayarta ne yasa ta ɗan ɗagowa,ɗaukar wayar tayi ganin mai kiran nata ne yasa tayi saurin picking call tana ƙara wayar a kunne,cikin muryarta da tayi laushe saboda kukan data sha tayi mashi sallama,cike da kulawa ya amsa “how are u,I hope u are fine” a hankali tace mashi “am fine” “what are doing in this time da ba kiyi bacci ba?” ya tambaya,shiru tayi ba ta bashi amsa ba “laatifa!” ya kira sunanta a hankali,lokaci ɗaya taji wani kuka ya zo mata wanda ta kasa controling,kawai ta fashe mashi da kuka,ajiyar zuciya ya sauke “dama naji a jikina akwai abunda ke faruwa dake a cikin daren nan that's why I call u, please stop cry and tell me what happens to u kinji” kuka kawai take tama kasa buɗe baki ta sanar dashi abunda ke damunta, ajiyar zuciya ya sauke in a cool voice yace “stop cry please,it's paining me” jin abunda yace ne yasa ta sassauta kukan da take tana sauke ajiyar zuciya “ke da dadynki ne?” ya jefa mata tambaya,gyaɗa mashi kai tayi kamar tana a gabanshi “ya yi man iyaka da ƙanwata” kaf abunda ya faru ta sanar da shi sai dai bata sanar dashi a game da soyayya Balqis ba. “i told u in several times Laatifa,that guy u think is your father baya sonki ki bar masa gidan sa but kin ƙi fahimta” “sam saboda momy nake zaune” “but hakan ya hana tsanar da yayi maki ne?” “A'a,amma...” da katar da ita yayi “wait,give me a tow minutes I will call” ok tace mashi, rejecting kiran yayi,tagumi tayi tana zuba ma wayar ido,bayan kamar five minutes sai ga kiranshi ya shigo wayar, picking tayi ta kai wayar a kunne “nayi maki booking flight At eight o'clock in the morning zai tashi,ki bar masa gidansa,kije wajen mom ki kwana in the morning sai ki tafi airport ɗin,I will send the ticket for u” bata da wani zaɓi bayan tayi nesa da dadyn nata ko hakan zai sa ya yafe mata “ok, thank u Sam” “u have a special place in my heart,see u California soon,make sure u live that house,take care,bye” yana gama faɗa yayi rejecting kiran,zubama wayar ido tayi kamar zata ganshi,ta gumi ta zuba ba komai take ji ba face momyn ta,tasan ba za ta juri rashinta a kusa da ita ba amma bata da wata mafita bayan tayi nesa da dadyn ta ko hakan zai sama mata salama a rayuwarta da shi kanshi dadyn nata,ta ɗan jima tana a haka kafin ta miƙa ta shiga haɗa duk wani abunta mai mahimmanci,box biyu tayi na kayanta,kafin ta ɗauki passport ɗinta,bayan data kammala haɗa kayanta,ta ɗan jima tana kallon ɗakin kafin ta fice,a parlor ta ci karo da laure kamar yanda lauren ta sanar ma momy,bayan ta yi bankwana ta roƙeta da kar ta sanar da kowa ta fice daga gidan baki ɗaya,a motar ta ta tafi gidan big dady, Estate tsit kamar babu kowa a cikinta sai yan tsirarun securitys dake kai kawo,lokacin data shiga gidan bata haɗu da kowa,da tayi deciding zuwa ɗakin Yumnah amma sai ta fasa kawai tayi zamanta a parlorn tunda zuwa safe zata wuce ko boxs ɗin ta a booth ta barsu. *Back to story* “look Sam,wai kai baka san matsalar dake cikin zuwanta nan ba ne?,karka manta har yanzu Uncles ɗinka da wannan tabon su ke kallon ka,kai ko dan saboda hakan baza ka ƙyale masu ƴar su ba” “mom i don't care about yanda su ke kallona,ni wannan bai shafe Ni ba,saboda babu wani wanda yake da wani mahimmanci a rayuwata, Please ki bar Laatifa ta zo,zata cigaba da aikinta ne a nan” “wai mi yasa ka kasa understanding abunda nake son ka gane ne,zuwanta zai ƙara masu tabbaci akan zargin da su ke maka,mi yasa ba zaka gane ba ne,Sam bana son abunda zaiyi affecting mutuncinka,kai wai ba ka jin komai ne da ka yi nesa dani??” “mom ina ji mana,ke ki ka zaɓi mijinki sama dani” “sam ina son mahaifinku dole na dawo gare shi” ɗan ajiyar zuciya ya sauke yana faɗin “love birds,soyayyan da bata maki amfani ba” “wait idan kana da matsala dashi ni bana da matsala dashi,mahaifinku is a kindnesses parson,har yau ka kasa fahimta hakan ka daina wannan fushin mara amfani da shi,ba dan yana so ba yayi maka haka,sai dan ƙin magana da kayi da kowa,kaƙi faɗan gaskiyar abunda ya faru Sam,har yau kaƙi magana da kowa sai fushi ka ke,baka san halin da ka ke jefa mahaifinka akan wannan fushin da ka ke da shi ba,kana son Allah ya yi fushi da kai saboda wannan halin?” dakatawa tayi tana sauraran ma zai ce,ɗan ajiyar zuciya ya sauke ba tare da yace komai ba, girgiza kai kawai mom tayi “kasan haƙƙin iyaye akan yaran su Sam amma mi yasa ka ke haka,mahaifinka yana matuƙar sonka fiye da sauran ƴan uwanka,har yau ya kasa yafe ma kanshi akan abunda yayi maka,kullum cikin azabtuwa yake da soyayyarka,Sam baka san ya muke ji a zukatan mu ba saboda nesan da kayi da mu,please ka daina wannan fushin kaji,ka dawo gare mu, jin mu muke uncompleted saboda rashin ka” “shikenan mom,yanzu ya maganan zuwan Laatifa” ya faɗa hakan ne kawai dan ya kauda zancen “na riga na gama magana,baza ta zo ba” mom ta faɗa rai a ɓace “ok,zan kwanta bacci sai anjima” “baka bani amsa tambayata ba” “mom bacci fa nace maki ina ji,yanzu fa 1:00 Am ne, mom I will call u” yana faɗa yayi rejecting kiran, girgiza kai kawai mom tayi ta san maganar ce kawai baya so. tashi tayi daga parlorn ta nufi bedroom ɗinta,a kwance ta samu Laatifa bacci ya ɗauketa bayan ta kammala breakfast,wayanta ta ajiye saman Nightstand ta nufi toilet. Nainarh zaune take saman bed kusa da Yumnah tunda ɗazu take tashinta saboda gyaran part ɗin sam da za suyi kasancewar yau Friday,tashinta take amma ko motsi Yumnah ta ƙi yi “please Dan Allah ki tashi muje time fa na ƙurewa” ta faɗa tana kallon fuskar yumnah da ko motsi taƙi,ɗan bubbuga kafaɗarta tayi “na san fa kina jina,dan Allah yumnah ki tashi” ya mutse fuska tayi tana juya mata baya “ki bari sai 10:30 tayi Please” wani kallo Nainarh ta mata ita tunda su ka yi sallah bata koma bacci ba saboda ƙwallafa rai da tayi na zuwa part ɗin amma yumnah na wani ja mata rai. “wai minene haka ne Yumnah” “bacci fa nake Nainarh,dan Allah ki ƙyale ni ki tafi wajen dady ki amshi key ɗin mana ni ba yanzu zan zo ba” hararar ta Nainarh tayi,wata dabara ce ta faɗo mata,da sauri ta kai bakinta saitin kunnen yumnah ƙara tayi wacce tasa yumnah tashi a firgice,fashewa da dariya Nainarh tayi,ɓata fuska yumnah tayi “gaskiya baki kyauta man ba,ji fa yanda ki ka tsorata ni” “ai maganinki kenan sai magana nake kinyi banza dani” “to ba sai kije wajen dady ki amshi key ɗin ba” “ai ba ni ke amsa ba” harararta yumnah tayi “Allah sai nayi maganinki akan ya Sam,kin fa soma takura man akan shi” “oho dai,ni dai yanzu tashi muje” tsaki yumnah taja,ba dan ta so ba ta tashi,hijab ta zura a jikinta,ficewa su kayi zuwa part ɗin dady,sai da yayi ma yumnah faɗa kan sun ja time,dariya Nainarh tayi mata. lokacin da su ka isa part ɗin a bakin ƙofa su ka samu su Ishrat su kawai su ke jira,buɗe masu part ɗin tayi, Nainarh da su Ishrat kawai su ka shiga amma ita kitchen ta nufa wai zata sha coffee,part ɗin ta dawo bayan ta kammala haɗa coffeen,samun Nainarh tayi ta zage tare da ita ake aikin, murmushi yumnah tayi ta rasa wane irin ji Nainarh ke yima yayan nata. jawo hannunta tayi “madam irin wannan haƙilo haka,sai anyi magana kice ke ba haka ba” “yumnah bana son wulaƙanci,kawai aikin nake so ba wai dan wani abu ba” “oh ni zaki maida bican ko” “ke wallahi kin cika matsala,ni dai yanzu ki ƙyale ni” “yanzu dai ajiye aikin soyayyar ga coffee ki sha” yumnah ta faɗa tana miƙa mata mug ɗin coffee dake hannunta, hararar ta Nainarh tayi tana amsar coffeen,zama su ka yi anan parlon su Ishrat kuma na ciki suna aikin. nainarh jujjuya mug ɗin dake hannunta ta shiga yi ba tare da ta sha ba,kallonta yumnah tayi tana faɗin' “ya dai mrs Samad, ko coffeen bai maki ba a canzo maki wani?” harara Nainarh ta watsa mata “wai mi yasa kin cika wasa ne yumnah?” Nainarh ta faɗa babu alamun wasa, ƴar dariya yumnah tayi “kema mi yasa kin cika rainin hankali?” tsaki kawai Nainarh tayi mata “Nainarh!” yumnah ta kira sunanta, kallon yumnah tayi ba tare da ta amsa kiran ba “ina so na tambaye ki please yanzu ki faɗa man gaskiya” stuke fuska Nainarh tayi tun kafin taji ma mi yumnah zata faɗa “maganar hankali ce za muyi naga kin wani ɓata rai, da gaske ne ba son ya Sam ke ki ba kamar yanda ki ka faɗa man ko dai kawai baki son sanar da ni ne??” yumnah ta faɗa tana wani tsareta da ido,mug ɗin da tun ɗazu bata sha ba ta kai bakinta tana kauda ma yumnah fuska,murmushi yumnah tayi tana ajiye mug ɗin dake hannunta saman table, amshe na hannun Nainarh tayi ta ajiye, da mamaki kawai Nainarh ke kallonta. kamo hannunta tayi cikin nata “please Nainarh ki faɗa man, ki ka sani ko da akwai wani abu da zan taimaka maki dashi” yar ajiyar zuciya Nainarh ta sauke “yumnah idan nace maki bana son ya Sam nayi maki ƙarya, amma yumnah ke kanki kin san bazan samu soyayyar shi ba, wahalar da kaina kawai zanyi shiyyasa duk time ɗin da ki ka man magana nake kauda zancen” “saboda mi ki ka ce baza ki samu soyayyar shi ba?” “da bakin ki fa ki ka faɗa man shekarun da ya ɗauka rabonshi da ƙasar nan, kuma ni ko waya banga anyi da shi ba, sau ɗaya naji ya Naeem na waya da shi, a haka taya ki ke tunanin zan samu soyayyar shi?” “ki ka sani ko Allah ya dubi zuciyarki wata rana kawai ya wanko ƙafa ya zo” murmushi kawai Nainarh ta saki tana girgiza kai “kina ganin wasa ko?” “babu wasa a cikin lamarin ubangiji, idan hakan ta kasance zanfi kowa farin cikin” “in sha Allah wata rana zaki tuna wannan maganan dana faɗa maki” “Allah ya Amince” “Ameen,yanzu ki tashi muje mu shirya na san zuwa lokacin da zamu gama sun kammala gyaran” “amma tun yanzu zamu tafi” “eh akwai family meeting ne, shiyyasa zamu tafi da wuri” “family meeting!,anya yumnah baza ku tafi ku barni ba,ni kawai prison zanje wajen momy” “gobe fa mu ka yi dake zamu je,dan Allah karki man gardama ki zo kawai muje” tashi tayi su ka fice ba tare da ta sake cewa komai ba,sai da yumnah ta fara ajiye mugs ɗin da su ka sha coffee tukun. shiryawa su ka yi, kamar yanda yumnah ta faɗa lokacin da su ka koma su Ishrat har sun kammala gyaran,rufe part ɗin kawai tayi ta maida key ɗin part ɗin dady da har ya fice daga gidan,bedroom ɗin mom su ka nufa, harta kammala nata shirin itama,Laatifa ce kawai ta so gardama ba zata ba amma ganin mom ta dage ne yasa ta shirya,a parlor su ka ci karo da Fa'iza itama ta shirya “mom Irfan bai shigo ba ne?” fa'iza ta tambaya sanin duk za su tafi tare su ke tafiya “bai shigo ba,ku mu tafi kawai” mom ta faɗa,tun ranar da ya ƙone Nainarh yake fushi da su bai sake dawowa gidan ba. ficewa su ka yi daga gidan,motar yumnah Fa'iza da Nainarh su ka shiga mom da laatifa kuma su ka shiga motar mom da driver zaiyi driving ɗin su,motar su mom na gaba ta su yumnah na baya su ka fice daga gidan zuwa gidan Abbah. *UNITED STATE❤* _*Las Vegas (Nevada)*_ tsit gidan yake baka jin motsin komai kasancewar dare ne sosai,duhu ne ya mamaye ko ina sai ɗan hasken bulbs ɗin dake compound da ya haska gidan kamar rana,ɗai ɗai kun securitys ne ke kai kawo a compound ɗin. A tsaye take cikin garden ɗin da haske kaɗan ne a ciki,riga da wando ne haɗe da mayafi a jikinta masu santsi,ta rufe rabin fuskarta da mayafin,hannun ta riƙe da ƴar madaidaiciyar leda,ta kai tsawan minti 30 a cikin garden sai safa da marwa take da alama akwai wanda take jira,time to time take duba wristwatch ɗin dake hannuta haɗe da kallon ƙofar shigowa garden ɗin. ganin har 2:45Am tayi yasa kawai ta yanke shawarar bazai zo ba,harta juya da nufin barin garden ɗin ta hangoshi yana shigowa. ɗaya daga cikin securitys ɗin gidan ne,baƙaƙen kaya ne a jikinshi yayinda ya rufe fuskarshi da face mask,ko Ina na jikinshi a rufe,nannauyar ajiyar ta sauke,ƙarasowa yayi har in da take. “am sorry ma'am” “wannan wane irin shirme ne baka san ina jiran ka bane?” ta faɗa rai a ɓace “tun around 1:30 am nake nan jiranka amma har tsawan 45 minutes baka zo ba” “am very sorry ma'am,na tsaya ne dan na tabbatar babu wanda yaga shigowata nan ne,am sorry” tsaki kawai taja,leda dake hannuta ta miƙa mashi,amsa yayi yana zuba mata ido dan jin ƙarin bayani “please ka tabbatar ka bata zuwa gobe,I hope baka manta yanda plan ɗin yake ba” “yeah ban manta ba” “okay,Ina wanda ya kawo shi?” “yana bedroom” “ohk kana iya tafiya kar su fahimci baka nan” ok ya ce yana zura leda cikin aljihun rigar dake jikinshi,ta hanyar da ya shigo ya bi ya fice,har sai da taga ficewarsa tukun itama ta bi ta wata ƙofar ta fice,cikin gidan ta nufa ta ƙofar wacce zata sadata da ɗakinta,a hankali take tafiya har ta kawo bakin ƙofar ɗakinta ba taci karo da kowa ba,kama handle ɗin ƙofar ɗakin tayi “Mrs Sophia!” kamar daga sama taji an ambaci sunanta,wani irin mummunan faɗuwa gabanta yayi,a hankali ta sakin handle ɗin ƙofar,juyowa tayi tana kallon luna data ambacin sunanta,a tsaye take hannunta riƙe da bottle water “daga Ina ki ke haka a wannan lokacin?” luna ta faɗa tana tsareta da ido “na duba jikin Nailarh ne” ta faɗa tana juya,saurin buɗe ɗakinta tayi ta shiga,barin wurin itama luna tayi ta nufi ɗakin su. *Washe gari* A zaune su ke saman dinning chairs a katafaren dinning room ɗin gidan,Aunty Sophia na kusa da Nailarh tana bata abinci,kwata kwata hankalinta baya kan abincin yana kana momynta da har yanzu take fushi da ita,ko kallon in da take bata son yi. Tissue ta yaga ta goge bakinta “sophia”ta kira sunanta,kallon malika tayi tana ba Nailarh abinci “i will travel tomorrow please take care of her” “ok ma'am safe trave” jinjina mata kai Malika tayi,Nailarh kasa haɗiye bread ɗin dake bakinta tayi jin abun da Momyn tata tace,fushin da take da ita har ya kai ta tafi ta barta, tissue hannunta ta ajiye haɗi da ficewa daga dinning room ɗin,miƙewa itama Nailarh tayi tabi bayanta,a bedroom ɗinta ta sameta, saurin juyowa tayi jin an buɗe ƙofar ɗakin,idanunta ne suka sauka akan Nailarh dake binta da wani kallo,juya mata baya tayi tana nufar bakin window ɗakin. A hankali ta taka har izuwa inda take,hugging ɗinta tayi ta baya tana zagayo da hannunta saman flat tummy ɗinta “am sorry momy” Nailarh ta faɗa tana langwaɓar da kanta saman shoulder malika “sorry mom” ta sake faɗa, ajiyar zuciya Malika ta sauke,zame hannun Nailarh dake kana tummy ɗinta tayi,juyo da ita tayi suna facing juna,zuba mata ido tayi tana kallo itama Nailarh kallonta take “momy I'm sorry if I hurt u” kamo hannun Nailarh tayi “sorry for what?” Malika ta faɗa “na san kina fushi dani saboda rabuwa da mijinki da na saki” “I'm not angry with you” “idan har baki fushi da ni mi yasa za ki yi tafiya bayan kin sa I'm not completely healed?” “important issue ne that's why” “please ki sa su Joseph su yi reflecting naki mana” “dole da kaina zanje” kallonta Nailarh tayi kamar za tayi kuka “please momy ki zauna a tare dani” “bazai yiwu ba baby,dole na tafi,but if you follow me then” Malika ta faɗa tana kallonta duk da ta san da wahala ne Nailarh ta amince zata bita, duk da itama ta fi son hakan tana so ta bata space ne ko hakan zai sa taji sauƙin abunda ke damunta “zan biki” Nailarh ta faɗa,kallonta Malika tayi da mamaki “are u sure?” “yeah am sure,zan tafi tare da ke” murmushin Malika tayi mata,saurin shigewa tayi jikinta tana sake hugging ɗinta,a hankali ta ɗaura hannunta saman head ɗinta,shafa sumar kanta ta shiga yi “baby wane lokaci ki ke ganin ya kamata muyi Aure?” “you said next year” “na canza ra'ayi yanzu kuma,da mun dawo daga wannan tafiyar kawai tunda kin sa na rabu da mijina” “am sorry” Nailarh ta faɗa “alright” nocking ƙofar ɗakin aka yi “who there?” Malika ta faɗa “ma'am its me,Noah” sakin Nailarh tayi ta nufi bakin ƙofar,buɗe ƙofar tayi “is they anything?” ta faɗa tana kallonshi,ledan dake hannunshi ya miƙa mata “saƙo ne daga Dr Daniel, injection ɗin Madam Nailarh ce ya aiko da ita” amsar leda Malika tayi tana duba kwalin alluran dake ciki “thank You” ta faɗa tana maida ƙofar ɗakin ta rufe,in da Nailarh take ta nufa “i think tafiyar mu tare bazata yiwuba” “why” Nailarh ta faɗa tana kallonta,leda dake hannunta ta nuna mata “allurace Daniel ya aiko da ita yanzu” “ni fa am fine yanzu,babu wata allaura da za'a man” “no Nailarh tunda ki ka ga ya aiko da ita tana da mahimmanci ne a gareki,kiyi haƙuri kawai ai ba jimawa zanyi ba zan dawo,karki manta we will get married soon” turo baki Nailarh tayi “kiyi haƙuri kinji,zan ba Sophia sai ta dinga yi maki naga kamar towce ne far day, morning and evening” “mu tafi tare da ita mana sai ta dinga man acan” zama malika tayi tana kama hannunta “please Nailarh ki bari na tafi,time ɗin da zan dawo kinga kin ƙara samun sauƙi” lallashin Malika tayi har ta samu ta haƙura da tafiya. Aunty Sophia Malika taba injection ɗin kamar yanda tace. Aunty a salinta kafin ta zama nanny Nailarh a orpernage take aiki a matsayin Nurse anan Malika ta ganta har ta ɗauketa aikin nanny lokacin Nailarh na da shekara 3 a duniya,tunda ta dawo gidan Malika dan kula da Nailarh ta ajiye aikinta na Nurse,sai ta jima ba tayi allura ba ko wani abu daya shafi aikinta. *ABUJA NIGERIA💋* After Asr prayer gaba ɗayan su su ka hallara a katafaren meeting room ɗin gidan dake part ɗin Abbah. Abbah na daga kan royel sofa a zaune yayin da gaba ɗayansu suke zaune a ƙasa saman rug carpet sun harɗe ƙafafunsu kamar ma su ɗaukar karatu,Nainarh na daga zaune kusa da Aunty Mariya da tunda ta zo gidan take maƙele da ita,har da ɗan faɗa ta mata saboda rashin zuwa gidanta da bata sake yi ba,mom a zaune take kusa da dady idanunta ta sauke akan Irfan da kwana biyu kenan rabon data sa shi a idonta,yana na daga zaune gefen ƙafanfun Abbah,kanshi a ƙasa,ƙallo ɗaya zaka mashi ka hango tsantsar damuwar da yake ciki,kwana biyu kacal amma duk yabi ya rame kamar ba shi ba,wani irin tausayin shi ne ya rufeta,amma ya za tayi,rabashi da Noor shi yafi Alkairi a gare shi,kallon ɗin Noor dake kwance saman jikin momynta tayi,itama duk ta fita hayyacinta,itama ba ƙaramar rama tayi ba abunka da mara jiki duk sai ta koma wani iri,har wani haske ta ƙara,sauke idanunta tayi ƙasa tana jin wani iri a zuciyarta. Mama Ameenah tunda ta zauna wajen idanunta ke kan mom tana Binta da wani kallo mai cike da tsana,gaba ɗaya kallon da tayi ma Irfan da Noor akan idonta. Laatifa suna wuri ɗaya zaune ita da su Aunty Nafisat,Aunty Nadeya da Aunty kainart sai Noha matar ya Usman ɗiyar Aunty Safeenah, baiwar Allah tunda su ka shigo parlorn idanunta ke kan dadynta da yayi kamar bai san da zamanta ba ko kallon inda take baiyi ba,idan ka cire su mamy da mom data san abunda ke faruwa,ba bu wanda bai tambayi ina mom maimunatu da Balqis ba, amma sai uncle Hashim yace ma su Balqis ce ba lafiya shiyyasa ba su samu zuwa ba. Laatifa sosai hankalinta ya tashi jin ƴar uwarta ba lafiya,ta kira wayar su ya fi a ƙirga amma bata samu ba,wayar balqis na ringing amma ba tayi picking ba,mom maimunatu kuma tata a kashe,hakan ba ƙaramin ɗaga hankalinta ya yi ba. Gyaran murya Abbah yayi gaba ɗayan su su ka kai dubansu gare shi,ya Naeem dake ɗayan gefenshi ya kalla yace ya buɗe masu taro da Adu'a,tashi yayi kamar yanda Abbah ya umarta,tsit parlorn yayi har ya kammala Adu'a ya koma mazaunin sa, gyara zama Abbah yayi cike da Dattaku da kamala ya fara magana “Alhmdllh gaba ɗayan ku ina maku Barka da juma'a,da yawan ku nan sun san maƙasudin wannan zaman ɗai ɗai kun cikin ku ne ba su sani ba” tsit parlorn ya sake yi kamar mutuwa ta gitta “na tara ku nan ne saboda abun farin cikin daya same mu wanda nake fatan ɗorewar sa har bayan raina” tunda Abbah ya fara magana mom fatilah ta haɗe girar sama da ƙasa irin ba mutuncin nan “shekarun baya da su ka wuce munyi ire ire wannan taron wanda da yawan ku sun hallara ƙalilan daga cikin ku ne basa nan,to kamar dai shekarun baya yau ma cike da farin ciki da fatan ɗorewar irin wannan taro nake sanar daku maganar Auren ƴan uwanku Irfan da Nurjahan . wanda za'ayi nan da wata uku idan Allah ya sa muna da rai da lafiya sai Waseef da Kairiyyah” Abbah na kaiwa nan yayi shiru, murmushi farin ciki ne ya bayyana akan fuskokin su dady,babu wanda a cikin su baiyi farin ciki da wannan haɗin ba,Irfan da Noor bugun zuciyarsu ne ya tsananta,abunda zai biyo baya daga iyayensu mata kawai su ke tsoro,ɗaga ido ya Naeem yayi yana kallon mom da kallo ɗaya zaka mata ka hango tsantsar damuwar da take ciki,mom fatilah tunda Abbah yayi shiru ta shiga aikama Irfan harara Kamar zata tashi ta rufe shi da duka. “kamar ko wane lokaci bazan hana ku iyayen yara faɗar ra'ayin ku ba,ranar da aka tsaida tayi maku ko da mai abun cewa a cikin ku?” Abbah ya faɗa yana bin su da ido. dady Ahmad da dady Mustafa wanda sune wakilan Irfan da Noor su ka yi saurin cewa “babu wata matsala Abbah,duk lokacin da aka tsaida rana hakan yayi,Allah ya nuna mana lokacin bikin lafiya” da Ameen su dady su ka amsa,mom fatilah sai wani cika take tana batsewa,ji take kamar ta shaƙi wuyan uncle Mustafa da yayi maganar. kallon dady da uncle mutallaf Abbah yayi “ku fa hakan yayi maku?” dady ya bashi amsa da “ai ƴaƴan su ne Abbah,duk hukuncin da suka yanke yayi” “to Masha Allah hakan yayi, shi kuma Waseef sai munji daga dangin mahaifin Kairiyyah,muji su kuma yaushe ne za su sa ta su ranar,sai ku iyayen su mata idan da mai abun cewa to” Abbah ya faɗa, tunda Abbah ya faɗi haka uncle mutallaf ke jefa ma mom fatilah wani irin kallo mai cike da gargaɗi amma sai ta kauda kamar ma bata san yana yi ba,tsit parlorn yayi babu wani wanda yayi making any move har Abbah ya fara tunanin ko ba mai abun cewa ne a cikin su,mom fatilah tana son magana amma uncle mutallab yaƙi bata space ga Noor daketa faman haɗata da Allah kan karta hanata farin cikinta “kamar yanda muka haɗu haka Allah ya nuna mana ranar Auren lafiya” Abbah ya faɗa da Ameen duka su ka amsa. kallon ya Naeem Abbah ya yi yace ya rufe masu taro da Adu'a,miƙewa yayi Naeem yayi “Abbah ina ne Alfarma kafin a rufe taro” mom ta faɗa kanta a ƙasa,gaba ɗaya parlorn su ka kai dubansu gareta,wani irin mummunan faɗuwa gaban Irfan yayi haka ma Noor dady kuwa zuba mata ido kawai yayi “muna jinki Zulaihart, wace irin alfarma ki ke nema,faɗi muna saurarenki” dady sai kallonta yake burin shi ta ɗago ta kalle shi ko ya hanata abun da take shirin yi amma taƙi bashi Accesse ɗin da zai yi hakan “ina mai baku haƙuri gaba ɗayan ku,Alfarmar da nake nema ba lallai taima wasu daga cikin ku daɗi,amma ina fatan ku fahimce ni ku kuma yi man uzuri” “ba komai Zulaihart muna sauraren ki” kallon su uncle Ahmad tayi “a karo na biyu ina mai sake baku haƙuri,ban so a wannan karan nayi jayayya akan wannan hukunci da ku ka yanke ba amma ya zama dole,Irfan ɗanku ne kun isa ku yanke ko wane irin hukunci akansa,amma a matsayina na mahaifiyar shi ina neman alfarma maganar Auren shi da Noor a barta” dady ne yayi saurin cewa “amma Abbah tana so...” saurin dakatar da shi Abbah yayi “barta tayi magana” shiru dady yayi,yana jin wani iri a ranshi bai taɓa tunanin haka daga gareta ba,Abbah dama tunda ta shigo part ɗin ya fahimci kamar akwai abunda yake damunta,sai yanzu ya fahimci mike damunta,tunda ya ke da ita wannan ne karan farko data nuna hukuncin da ya yanke bai mata ba,har ta kasa haƙuri ta iya faɗa da bakinta,ko bikin su ya Naeem bata so ba amma tayi haƙuri,a wannan karan ya kamata suyi mata uzuri kamar yanda ta buƙata “ba'a san raina naƙi amincewa da umarnin ku ba sai dai bani da wani zaɓi ne,ni kaina zan so zumuncina da mutallab ya ƙara ƙarfi sai dai haƙura da Auren shi ne mafi Alkairi sama da ɗaura shi,nayi haƙuri na jure komai da Auren Naeem sai dai a wannan karon nakasa wannan haƙurin da juriyar,ku gafarce ni idan har alfarmar dana nema batai maku daɗi ba,ina mai baku haƙuri,banyi hakan da nufin wani abu ba” “babu komai Zulaihart ai ɗanki ne,babu wanda zai mashi Auren da baki amince da shi ba,babu damuwa Allah yasa hakan shi ya fi zama Alkairi” Irfan tunda Abbah ya faɗi haka wata irin zufar tashin hankali ta rufe shi,gaba ɗaya ji yayi duniyar ta daina mashi daɗi,Noor ma maƙale momynta ta yi jikinta na wani irin shaking kamar wacce fever ta kama,su uncle Mustafa babu wanda maganar mom tayi ma daɗi,amma duba da abunda ya faru rannan a gaban su sai su ka yi mata uzuri,wannan ne karan farko data taɓa nuna ƙin amincewarta akan wani abu. mom fatilah har wani sauke Ajiyar zuciya take tana sakin murmushi,su mamy babu wanda fasa Auren bai ma daɗi ba,kallon juna su ka yi ita da mom halima suna sakin murmushi,ba ƙaramin daɗi suka ji ba. tashi ya Naeem yayi ya rufe masu taron da Adu'a kamar yanda Abbah ya bashi umarni,yana kammalawa matan su ka fara tashi suna fita. kama hannun Noor mom fatilah tayi amma taƙi tashi, duƙawa tayi tana kallonta “Noor lafiya, tashi mu tafi mana” kallon Momyn ta ta tayi numfashinta na sama da ƙasa “Noor lafiya?” ta faɗa tana jijjigata ganin yanda ta fara gasping Kamar breath ɗinta zai ɗauke she's asthmatic since she was a child kamota tayi ta ɗago da ita amma kwata kwata jikinta ba ƙwari gaba ɗaya ta koma ƙasa gasping ɗin da take na tsananta,dafe chest ɗinta tayi,hankalin mom Fatilah ba ƙaramin tashi yayi ba,hankali a tashe ta shiga kiran sunanta gaba ɗaya su dady su ka yo kansu su mom har sun fice ba su san ma mike faruwa ba, hankali a tashe uncle Mustafa ya shiga yi mata fifita da gefen rigarsa,ƙirjinta sai sama yake yana ƙasa,Irfan kasa motsi yayi daga in da yake zaune,shi kanshi bazai iya cewa ga taƙamaimai yanda yake ji. ruwa uncle mutallaf ya shiga bata amma ina numfashinta neman ɗaukewa yake,hannu biyu uncle Mustafa yasa ya ɗauketa,ficewa yayi da ita daga parlorn gaba ɗaya su ka bi bayan shi Irfan da Waseef kawai aka bari,magana yake ma Irfan ɗin amma kamar baya hayyacin sa,kama hannunshi yayi su ka fice daga parlorn,lokacin da su ka zo parking space da yawan su sun tafi gida mom ma sun tafi ita da su Aunty laatifa da Aunty Kainart da za taje gidan saboda Laatifa,gaba ɗaya ta sanar da ita abunda ya faru bata ɓoye mata ba,su dady kuma hospital su ka nufa tare da Noor, Nainarh da yumnah da Fa'iza kuma sun wuce gidan ya Naeem wanda shi yace Nainarh ta sameshi su ka rakata. ♠♣♠♣♠♣♠♣♣ “haba laatifa mi yasa zaki man haka,kin tada man hankali sosai”mom maimunatu ta faɗa wacce a gidan su ka sameta tunda taga text ɗin da mom ta tura mata kancewa laatifa na nan ta wanko ƙafa ta zo. “kiyi haƙuri mom ba ni da wanni zaɓin ne bayan nayi nesa da ku, bazan juri ganin tsanar da mahaifina yayi man ba” “amma ai Laatifa sai ki duba halin da ni zan shiga idan babu ke” “yanzu kiyi haƙuri maimunatu tunda har Allah ya sa su ka yi shawarar cewa ta zo nan ta kwana,kiyi haƙuri ba inda Laatifa zata tafi ta barki” mom ta faɗa “hakane mom, ba tayi shawara da kowa ba ne shiyyasa amma da ba zamu bari har Sam yayi mata booking flight ba” kainart ta faɗa tana sake kwantar ma mom maimunatu da hankali “yanzu ya jikin balqis ɗin naji barrister yace bata jin daɗi” mom ta faɗa “wacece kuma Balqis,ni ban sani ba,na bar masa gidansa da yarsa tun jiyan” gaba ɗaya su ka kalleta jin abunda tace “amma munarh saboda me,bai kamata ace kin bar gidan saboda haka ba” mom ta faɗa cike da nuna rashin jin daɗinta akan abun “zulaihart ba za ki gane ba,Hashim ya wuce inda ki ke tunani shiyyasa kawai na yanke shawarar rabuwa da shi” “kul karki faɗi haka dan Allah,ko dan saboda ƴaƴanki ai kya zauna,duba fa ki ga shekarunki,dan Allah dai kiyi haƙuri” “duka yaran nawa ne, Laatifa ce kuma laatifa ba yarinya bace,Ni gaskiya na gama zama da hashim har abada” “dan Allah momy kiyi haƙuri,bazan ji daɗi ki kashe Aurenki saboda ni ba,dan Allah kiyi haƙuri ki koma” “eh momy dan Allah haƙuri za kiyi”Kainart ta faɗa “shikenan naji amma ba yanzu ba sai nayi shawara” “mom...” saurin dakatar da Laatifa dake shirin magana tayi “ba yanzu ba,faƙat na gama magana” ta faɗa tana ɗaure fuska da ido mom tayi mata alama data ba su waje,tashi su ka yi ita da kainart su ka fice daga ɗakin zuwa main parlor. wayar kainart ce ta fara ringing,da sauri ta zura hannu cikin jakar ta fito da wayar,duba sunan mai kira tayi,Dr fawar shine sunan daya bayyana a gaban screen ɗin, picking call ɗin tayi tana kara wayar a kunne. amsa sallamar da fawar ɗin yayi mata ta yi kafin tace “ok ka iso?” on the other side fawar yace mata eh “ok kana iya shigowa” da ok ya amsa mata yana rejecting kiran. “wai mi fawar ɗin zai maki ne,ko baki da lafiya ne?” Laatifa ta faɗa tana kallon kainart ɗin “for now lafiyata lau, result ɗin gwajin da yayi man zai kawo man” “ai nayi tunanin an wuce wurin tun time ɗin daya baki magani?” “nima nayi tunanin haka,to sai daga baya ya kirani yace man wai ya gano wani abu amma ni kaɗai yake son faɗamawa,wallahi shiyyasa duk nabi na damu Allah yasa ba wata mummunar cutar ba ce ta kamani ba” “in sha Allah babu wani abu sai Alkairi” “Allah ya sa” kainart ɗin ta faɗa,da sauri su ka kalli ƙofar shigowa adalilin sallamar da suka ji anyi, Dr fawar ne ya shigo cikin shigar pathani Suit golding yellow haɗe da White trouser,kanshi yasha gyara sumar sai wani sheƙi take,ga wani haɗaɗɗen jutti dake sanye a ƙafarshi kalar rigar,sosai ya fito a ba indiyen shi sak, sallamar da yayi su ka amsa,cikin parlorn ya ƙaraso fuskar shi ɗauke da murmushi,hannunshi ya haɗa waje ɗaya yana faɗin 🙏 “Namaste” murmushi su kayi gaba ɗayan su Laatifa na faɗin “namaste too” kwashewa kainart tayi da dariya,zaro ido fawar yayi yana kallon laatifa,dan da ya shigo sam bai lura da ita ba “vaah lateefa tum bahut sundar lag rahee ho” ya faɗa yana haɗe fingers ɗin shi biyu👌,saurin kallon jikinta tayi sai kuma ta kalleshi tana faɗin “ni kar ka zageni fawar” dan bata fahimci mi yace ba,fashewa yayi da dariya kainart ma dariyar take,cikin parlorn ya ƙaraso,zama yayi saman sofa yana faɗin “ni na isa nayi insulting naki,kawai u look beautiful” girgiza kai tayi tana faɗin “ban yarda da kai ba, kai dai kawai ka zage ni dan ka san ba gane abunda ka ke faɗa nake ba” murmushi kawai yayi without saying anything to her “good evening fawar” kainart ta faɗa murmushi ya saki “evening,how are you” “Alhmdllh” ta faɗa,gaisawa su ka yi da laatifa,wayar landline dake parlorn ta ɗauka, dialing number kitchen tayi ta bada umarnin a kawo mashi ruwa da lemu. “sorry fa na shiga lokacinki” ya faɗa yana kallon kainart “ba komai fawar,Allah dai yasa lafiya?” “lafiya lau” ya faɗa yana zaro wata envelope daga cikin aljihun shi,miƙa mata yayi,amsa tayi tana kallonshi “za ki iya buɗewa” ya faɗa,buɗe envelope ɗin tayi pepar dake ciki ta ciro,buɗe takardar tayi abunda ke ciki ta shiga karantarwa,da sauri ta ɗago tana kallon Dr fawar ɗin bayan ta kammala karantawa, murmushi ya sakar mata yana faɗin “congratulations mrs Zaabith” murmushi ta saki a lokaci ɗaya hawaye na zuba daga idanunta, bata taɓa expecting wannan ne dalilin kiran nata da yayi ba “thank you so much fawar, amma mi yasa baka sanar da ni tun tuni ba?” “because Ina so na amshi tukwici na da kaina ne” murmushi ta saki “karka da mu gaskiya am really happy, thank you” “don't mind mrs zaabith,but sai dai ban sanar da sir ba” “hakan yayi, thank you” murmushi ya sakar mata,bin su da ido kawai laatifa take ba tare da tasa masu baki ba,ɗaya daga cikin chefs ɗin gidan ce ta shigo hannunta ɗauke da tray data ɗauko ma fawar ruwa da lemu sai cup cake, cikin parlorn ta ƙaraso cike da girmamawa ta gaishe da shi kafin ta fice,Laatifa ta zuba mashi lemu a cup ta miƙa mashi, murmushi ya saki yana faɗin “thank you Jaan” murmushi kawai ta saki tana girgiza mashi kai, ta rasa mi yasa fawar yake mata haka shi bilhaƙƙi sonta ya ke,ita kuma bazata iya soyayya da age mate ɗinta ba dan idan bata girmeshi ba za su yi sa'anin juna. ya jima sosai a gidan banda tsokanar Laatifa babu abunda ya ke Kainart kuwa kallo ɗaya zaka mata ka hango tsantsar farin cikin da take ciki, sai da yamma tayi sosai tukun ya tafi, har parking space Laatifa ta rakashi sai da taga tafiyar shi tukun ta dawo. zama ta yi kusa da Kainart ɗin tana faɗin “da alama abun farin ciki ne ya faru ba kamar yanda mu kayi tunani ba?” murmushi Kainart ɗin ta saki tana miƙa mata envelope ɗin tana faɗin “laatifa am pregnant, four months pregnant” with a shock laatifa ke kallonta ba tare ma data buɗe envelope ɗin ba “am really happy, na san wannan news ɗin zai tashi kan ya Zaabith,am eager to tell him this news” wani kallo Laatifa ta shiga binta da shi kafin ta ce “ke yanzu har farin ciki ki ke zaki sake haihuwa da ya zaabith?” “ban gane ba, da baƙin ciki ki ke so nayi?” girgiza mata kai Laatifa tayi ganin kamar ranta ya ɓaci kuma ta san komai zata faɗa mata ba wai zata fahimta bane,ta riga ta gama mutuwa akan ya Zaabith “congratulations,Allah ya kawo mana shi ko ita duniya lafiya” Laatifa ta faɗa “Ameen my best” Kainart ɗin ta faɗa tana sakin murmushi. *second father's house* Tunda su ka shigo gidan a zaune suke a parlor,Aunty Nafisat kusan a tare su ka shigo da ita tunda ta haura sama bata sake fitowa ba Jamal da Aneeserh ne kawai su ke zaune kusa da yumnah yayinda Fa'iza ke can ɗan nesa da su tana amsa waya, za su yi 30 minutes da zuwa gidan amma har time ya Naeem bai shigo ba. Nainarh tunda su ka shigo ta nemi wuri ta zauna tayi shiru,bakomai ke yawo a kanta ba face message ɗin da aka turo mata jiya,abun ya tsaya mata a zuciya,miye manufar message ɗin waye ke mata barazana dan kai tsaye baza ta kira shi da kashedi ba, suna a haka ya Naeem ɗin ya shigo tare da ya Adnan. “afuwan na barku kuna jirana” ya faɗa yayinda yake nufa wani corridor,ya Adnan kuma ya ƙaraso cikin parlorn zama yayi a saman sofa dake facing wacce Nainarh ke zaune. gaishe da shi su ka shiga yi yana amsa masu cikin kulawa “ya jikin ki Nainarh?” ya faɗa “naji sauƙi” “Allah ya ƙara afuwa” da Ameen ta amsa mashi,wayar shi ya Naeem ya kira kan ya tura mashi Nainarh, da kanshi ya rakata har baki ƙofar ɗakin da ya Naeem ɗin yake ciki tukun ya koma parlor. a hankali ta tura ƙofar ɗakin bakinta ɗauke da sallama ta shiga. ɗan madaidaicin ɗaki ne mai ɗauke da desk da chair kamar investigation room,a tsaye ta hango ya Naeem ɗin a gaban wata ƴar book shelv mai ɗauke da tarin books da files. wani files ya ɗauko,chair dake gaban table ɗin ya nufa ya zauna yana nuna mata wacce ke kallon wacce yake zaune,zama tayi sai satar kallon ɗakin take, gyaran murya yayi mata hakan yasa ta maida hankalinta gare shi. “Nainarh!” ya kira sunanta “ba komai ya sa nace ki zo gida ki same ni ba sai wasu ƴan tambayoyi da nake son yi maki,kuma ina fatan zaki bani haɗin kai kamar yanda ki ka faɗa a baya?” “in sha Allah nayi alƙawari” “masha Allah,kafin na maki ƴan tambayoyi zaki iya shaida waɗannan fuskokin?” ya faɗa yana zaro wasu photona guda uku daga cikin file ɗin dake gaban shi,tura mata su yayi a gabanta. da sauri ta kai hannu ta ɗauki ɗaya daga cikin hotunan,wani magidanci ne da aƙalla zai kai kimanin shekaru 57 zuwa 60 a duniya yana sanye da police uniform,dan da nan hawaye ya kawo idonta,kallon hoton ta shiga yi bata ko ƙiftawa,hawayen da su ka taru a idonta ne su ka shiga zubowa, gyaran murya ya Naeem ɗin yayi mata,ɗago idanunta tayi ta kalleshi “zaki iya faɗa man ko waye shi” da sauri ta sa hannu ta goge hawayen dake zuba daga idonta “ko zanyi shekara 100 banga mahaifina ba duk ranar dana ganshi zan iya gane shi” jinjina kai ya Naeem “masha Allah” ya faɗa yana ɗaukar ɗayan hoton yace “wannan fa,zaki iya shaida wanene” “uncle Abdulrashid ne,shine A C P daddy,sati biyu da mutawarshi su ka zo har gida su ka kashe daddy” “good,miye alaƙarshi da dadynki bayan ta aiki?” “tamkar ɗan uwa haka yake a wurin dady” ta kai ƙarshen maganar hawaye na zuba daga idanunta,tissue ya bata ta goge fuskarta “sorry about that” ya faɗa yana ɗauko mata wani hoton “sunan sa Inspector Hussain, wurin aikin su ɗaya da dady” “akwai wata alaƙa tsakanin su kamar A C P?” “babu wata alaƙa tsakaninsu bayanta uban gida da yaronshi” jinjina kai ya Naeem yayi,duk wani abu da take faɗa yana recording a wayarsa dake ajiye saman table ɗin “akwai wani saurayi da akace yana yawan zuwa gidan ku,kuma ance basa ga maciji da dadynki,ko zaki iya faɗaman miye alƙarshi da mahaifinki?” hannu tasa ta goge hawayen da su ka kasa tsaya mata mutuwar mahaifinta abu ne wanda ta kasa mantawa da shi duk ta tuna sai ta zubar da ƙwallah “ina jinki miye sunansa sannan miye alƙarshi da dadynki??” “cousin ɗina ne,ɗan yayar momy ne,sunansa Abid,babu wata alaƙa tsakanin shi da dady kawai basa jituwa ne saboda dady baya son halayen ya Abid” “good,miye gaskiyar kasuwancin da aka ce momynki da Abid ɗin suna yi” “iya abunda na sani momy suna business ita da Aunty Fatima mahaifiyar ya Abid wanda shi yake kula masu da shi” “wane irin business ne?” “gaskiya ban sani ba” jinjina kai ya Naeem yayi “a binciken Court an tabbatar da Abid yana smuggle drugs Wanda akwai sa hannun mahaifiyarki a ciki!” ya faɗa yana tsareta da ido. wani irin mummunan faɗuwa gabanta yayi jin abunda ya Naeem ya faɗa, sosai hankalinta ya tashi tunda take bata taɓa jin wannan mummunan furucin akan momynta ba dan duk abunda ya faru a Court ba wai ta sani ba ne. ganin yanda yanayinta ya canza ne da shirun data yi yasa ya Naeem cewa “karki manta kinyi man alƙawarin zaki faɗi gaskiya kuma faɗar gaskiyar ita zata tona asirin wanda su ka kashe dadynki da A C P Abdulrashid” “wallahi ban san komai game da business ɗin su ba,hasali ma babu wanda ya taɓa faɗa man kalar business ɗin da su ke” kallonta ya Naeem yake kamar mai observing wani abu a fuskarta ko kalamanta “kar ki ɓoye man komai Nainarh,ki sani mahaifinki mutumin kirki ne bai kamata ki rufa ma wani asiri a kisan shi ba” fashewa tayi da ku ka, cikin muryar ku ka take faɗin “ba bu abunda na ɓoye maka, wallahi iya abunda na sani kenan” ta faɗa tana sake rushewa da wani kukan, ba komai ya sata ku ka ba sai jin wani sabon sharrin da ake bin mahaifiyarta da yayanta da shi. tashi yayi daga mazaunin shi ya nufi ɗan madaidaicin fridge ɗin dake room ɗin, water bottle ya ɗauko mata tare da cup, dawowa yayi ya zauna,zuba mata ruwan yayi ya miƙa mata. amsar ruwan tayi ta sha duk da haka bata fasa kukan ba, tissue ya sake miƙa mata yana faɗin “sorry kukan ya isa haka” lallashinta ya shiga yi har tayi shiru tana sauke ajiyar zuciya “ko zaki iya sanar da ni abunda ya faru a ranar da dadynki ya rasu” muryarta gaba ɗaya tayi laushe irin ta wanda yasha ku ka sosai “ina sauraronki mi ya faru a ranar??” jan hanci tayi kafin tace “ba komai na sani a game da abunda ya faru ba” “ba damuwa faɗa man iya abunda ki ka sani” gyaɗa kai tayi tana goge hawayen fuskarta “a ranar da misalin ƙarfe biyu na dare,ina tsaka da bacci aka banko ƙofar ɗaki na,a firgice na farka saboda ƙarar dukan ƙofan,wasu irin jibga jibgan maza ne su huɗu na gani a cikin ɗakina,ɗaya daga cikin su ne ya daka man tsawa yace na sauko daga saman bed,a gigice na sauko jikina na' ɓari,mutum biyu su ka tasani har main parlor biyu kuma suka shiga bincike ɗakin,a main parlor na samu momy da dady wanda wasu maza guda biyu su ka rirriƙe,momy kuma wani na tsaye a kanta da gun yayinda wani ke zaune saman sofa ya ɗaura ƙafa ɗaya kan ɗaya hannunshi riƙe da gun ga wasu maza majiya ƙarfi dake tsaye dama da hagunshi dukkansu gun's ne a hannunsu,da gudu na nufi dady ina kuka ina tambayarshi mi ke faruwa, murmushi dady yayi man yana faɗin na kwantar da hankalina ba bu komai,tsawa wanda yake zaune saman sofa ya daka mana,da sauri na ɓoye bayan dady saboda na tsorata sosai,in da muke ya nufo ko ina na jikinshi na motsi,ƙato ne sosai dan duk yafi mazan dake wurin girma,duƙawa yayi a gaban mu yana kallona sai kuma ya kalli dady yana sakin wata irin dariya mara daɗin jin yace wato dady ya zaɓi ya turashi inda ya tura A C P Abdulrasheed sama da ya faɗa masu gaskiya, murmushi dady yayi mashi yana faɗin in dai akan rayukan bayin Allah ne da ba suji ba basu gani ba barazanar su baza ta taɓa tsoratar da shi,wannan furuci na dady yayi matuƙar ɓata ranshi hakan yasa yasa yaranshi su ka rufe dady da duka,Ni da momy kuka muke muna roƙonsu amma babu wanda ya saurare mu,sai da su ka yima dady dukan mutuwa,duk sai da su ka sauya mashi kamanni amma hakan bai sa dady ya miƙa wuya yayi masu abunda su ke so ba,roƙon dady muka shiga yi ni da momy kan ya basu abunda su ke so amma yace muyi haƙuri basu isa suyi mashi abunda Allah bai nufa ba,muna a haka sai ga mazan dake can sama sun shigo da laptop ɗin mu duka da duk wani flash da su ka samu a gidan da wasu files wanda daga ɗakin dady su ka ɗauko su,Boss ɗin su da ya koma kan sofa su ka nufa,ɗaya bayan ɗaya su ka shiga bincike laptop ɗin mu bayan sun sa mun cire masu password duk da dady sai da ƙyar su ka samu ya cire nashi password ɗin,jifa yayi da laptop ɗina data momy bayan ya tabbatar da babu wani abu da zai amfane shi a ciki,wani Flash ya ciro daga cikin aljihun rigar sa yasa a system ɗin dady,yaran shi ya ba system ɗin su ka fice da ita bayan ya gama ɗaukar duk wani abu da zai ɗauka,files ɗin da su ka ɗauko daga ɗakin dady ya shiga dubawa,sai da ya du basu tas tukun yasa masu wuta ya ƙone su duka,dady harda ƙwallarshi saboda mahimmancin files ɗin da su ka ƙona,tasowa yayi ya dawo in da dady yake,ɗago da kanshi yayi yana kallonshi fuskar shi a ɗaure,ba muyi aune ba muka ji ya sauke ma dady lafiyayyun maruka har biyu ya kuma rufe shi da duka,da gudu na nufi dady ina kuka ina haɗa mutumin da Allah kan ya ƙyale dady,fisgo gashin kaina yayi ban san lokacin dana fasa ƙara ba saboda azaba,yaran shi dake wurin yace...” Kasa ƙarasawa tayi saboda shaking ɗin da muryarta ta fara kuka na neman yaci ƙarfinta “He said they should rape me a nan tunda dady yaƙi ya basu abun da su ke so” ta kai ƙarshen maganar tana fashewa da kuka,wani irin mummunan faɗuwa gaban ya Naeem yayi da sauri ya daki desk ɗin dake gabanshi saboda tsabar shock... wani irin ɓacin rai ne ya rufe shi idanunshi su ka kaɗa jawur,kallon Nainarh dake ku ka yayi, lokaci ɗaya tsoron ƙarshen labarin ya mamayeshi,da ƙyar yai getting courage ɗin faɗin “ina fatan babu abunda su ka maki?” ya faɗa cike da tsoron amsar da zata bashi, girgiza mashi kai tayi tana goge hawayen dake zarya a fuskarta “ fashewa nayi da kuka lokacin da naji furucin Boss ɗin na su,haka ma dady da momy kuka su ke muna roƙon su amma ba su saurare mu ba,fisgata su ka yi zuwa tsakiyar parlorn,unclothing PJ dake jikina su ka fara,ganin da gaske su ke ne yasa dady ya shiga ƙoƙarin ƙwace kanshi daga riƙon da su ka yi mashi dan ya kawo man ɗauki,dame su ka shiga da shi yana son zuwa inda nake suna riƙeshi har Allah ya bashi sa'ar kaima ɗaya daga cikin su duka a ido hakan yasa su ka sake shi,da gudu ya nufo inda nake,kokawa ya shiga yi da wanda ke kaina,a haka ba muyi aune ba sai jin karar gun muka yi a falon tsoro da firgici ne yasa na suma nan take,ban sake sanin inda kaina yake ba sai farkawa nayi na ganni a hospital tare da mom,a nan nake samun labarin sun kashe dady momy kuma na station ana zarginta da kashe...” kasa karasawa tayi saboda kukan da yaci karfinta a lokacin,ya Naeem ba ƙaramin karaya zuciyarshi tayi ba,lokaci ɗaya wani mugun tausayin ta ya rufe shi,fatan shi dai ya zama gaskiya ba abin da suka mata recording din da yake ya kashe, tashi yayi daga mazaunin shi ya nufo inda take zaune,kamo hannunta yayi ya miƙar da ita,tissue ya ɗauka,hawayen dake zuba daga idanunta ya shiga goge mata,amma kamar yana tunzurata ne,ɗan jawota yayi closer to him,faɗawa tayi jikin shi tana sake fashewa da wani kukan. A hankali ya kai hannunshi bayanta,hitting bayanta ya shiga yi yana lallashinta,turo ƙofar ɗakin aka yi da sauri ya juya yana kallon ƙofar amma baiga kowa ba wanda ya turo ƙofar har yayi saurin maidata ya rufe, lallashinta ya shiga yi sosai,har sai da tayi shiru tukun ya rabata da jikin shi,da hannu ya shiga goge mata hawayen da su ka kasa tsaya mata “daina ku ka kinji,nayi maki alƙawarin duk wani mai sa hannu a wannan al'amarin bazan barsa ba ko waye shi, don't bother your self kinji” a hankali cikin muryar ku ka tace “ya Naeem momy fa, wallahi bata da sa hannu” “kar ki damu bincike ne zai tabbatar da hakan, muddin bata da sa hannu zata fita ba bu abun da zai sameta, kar ki damu kin ji” taji sanyi sosai da kalamanshi,hakan ya ɗan kwantar mata da hankali “Erm.. Erm...” kame kame ya shiga yin gaba ɗaya shakkar amsar da zata bashi yake, daga ƙarshe dai yayi getting courege ɗin cewa “ Are u sure ko bayan da ki ka suma ba bu abunda su ka maki,Erm ina nufin ba suyi raping ɗinki ba kamar yanda Boss ɗin su yace??” “A'a ba suyi man komai ba” tana jin yanda ya sauke ajiyar zuciya “Alhmdllh,in Sha Allah asirin su zai tonu soon” jin jina mashi kai kawai tayi “ina wayarki?” “tana hannun yumnah” ta bashi amsa “ok muje ki amso man akwai abun da zan duba” ok tace, a tare su ka fice daga ɗakin bayan ya ɗauki wayarshi dake ajiye saman desk. A parlor su ka samu su yumnah har sun soma gajiya da zaman jiran Nainarh,suna ƙarasawa parlorn Aunty Nafisat na fitowa ɗaga kitchen,kallo ɗaya ta masu ta ɗauke kai tana nufar bedroom ɗin ta,tashi ya Adnan yayi ya nufo su, wayarta dake hannun yumnah ta amsa ta miƙa ma ya Naeem ɗin, amsar wayar yayi,ƴan danne danne yayi na tsawan minti ɗaya kafin ya miƙa mata wayar,amsar wayar tayi ya Adnan kallonta yake ganin yanda hancinta da cheek ɗin ta su ka yi ja alamar tayi kuka ga idanunta da su ka ɗan kumbura. tashi yumnah da fa'iza su ka yi,saurin kallon su ya Naeem yayi “second father za mu tafi” yumnah ta faɗa “Auta tun yanzu,baza ku bari kuyi dinner ba?” “A'a yaya idan mun dawo next sai mu yi” Fa'iza ta faɗa “ok to shikenan bari nayi ma mom Jamal magana, ko kunyi sallama?” “A'a” su ka bashi amsa “ok bari nayi mata magana” ya faɗa yana haurawa sama zuwa bedroom ɗin nata. da sauri Jamal ya riƙe yumnah yana faɗin “please Aunty yumnah zan biki” da sauri ita ma Aneesah tace zata bi ta “ba ruwan,ku je ku tambayi iyayenku to” da gudu su ka ruga zuwa ɗakin Momyn ta su. ya Naeem yana shiga ɗakin tsaye ya sameta gaban clothset ɗin ta, wayace kare a kunnenta da alama waya take amma yana turo ƙofar tayi saurin zame wayar daga kunnenta,cikin ɗakin ya ƙaraso “ki fito ku yi sallama za su tafi” ko kallon in da yake ba tayi ba ta shiga latsar wayar dake hannunta “nafeesah magana fa nake, ki zo ku yi sallama za su tafi” “Allah ya raka taki gona” shi ne kawai abunda tace without looking at him, with a surprise yake kallonta he never expect to hear that from her,har ya buɗe baki zai yi magana su Jamal su ka faɗo ɗakin,da gudu su ka nufeta suna faɗin “momy dan Allah mu bi su Aunty gidan big daddy??” “A'a gobe akwai islamiyya” “please momy sai muje daga can” “na ce baza ku je ba” ta faɗa cikin faɗa faɗa,kallonta kawai ya Naeem dake tsaye yake “dan Allah mom...” ko ƙaraswa ba su yi ba ta daka masu tsawa dole su ka ja baki su ka yi shiru “ku wuce kuje ku yi alwala lokacin sallah ya kusa,yara sai shegen son yawon tsiya” ficewa su ka yi daga ɗakin kamar za su sa ku ka,juyawa ya Naeem yayi shima ya fice. tsaki taja tana faɗin aikin banza,wayarta ce tayi ƙara,da sauri tayi picking call ɗin dama bata gama wayar da take ba “sorry muna tsaka da waya kinji nayi rejecting,shigowa yayi shiyyasa” on the other side Aunty Nadeeya ta ce “mi kuma ya zo ya ce maki?” “zuwa yayi wai za su tafi na fito muyi sallama” “sai ki ka je?” tsaki ta ja “Allah ya kiyaye,ce mashi nayi Allah ya raka taki gona” “haka shine dai dai wallahi,Gara da ki ka ce mashi haka” “baza ki gane ba ne Nadeeya na tsani yarinyar nan kamar me,duk abunda ki ke faɗa akanta ban taɓa jin muguwar tsanarta ba irin yau,rungume da juna fa na gansu” “ai nace maki yarinyar nan zubin karuwai gareta,na fa faɗa maki dadyn Enaaya ba kiga yanda ya ruɗe ba lokacin da bata da lafiya, har da wani ɗaukar Enaaya wai taje yi mata ya jiki” “ki bar shegiya kawai zata san da mu take magana,wallahi sai tayi data sanin shigowarta Estate ɗin nan” “lallai dole mu ɗau mataki dan irin su tsoro su ke bani,ki gansu sumi sumi kullum cikin hijabi kamar na Allah” “karki damu,wallahi sai taci ubanta” Ya Naeem yana fita daga bedroom ɗin parlorn ya koma, a tsaye ya same su kamar yanda ya barsu “sorry kuna jiran mu ko,na shiga ma naga mom Jamal ɗin ta shiga toilet,sai da safe kawai ku gaishe da su mom” to kawai su ka ce suka yi mashi sallama suna nufar ƙofar fita. Ya Adnan ma sallama yayi mashi,har bakin ƙofa ya raka su, su yumnah na fita yayi saurin kamo hannun ya Adnan,ɗan ƙasa da murya yayi “tana buƙatar wanda zai bata kulawa ta musamman, please take care of her,kasan irin wannan abun daga lokacin da aka tuna ma mutum shi sai a hankali” “karka damu in Sha Allah, Thank you” “ok good night” “good night” ya faɗa yana ficewa,a parking space ya same su suna ƙoƙarin shiga motar yumnah da su ka zo,amma sai yace yumnah su tafi da Fa'iza Nainarh kuma ta shiga tashi shima gidan zashi zaije ya gaishe da mom,da to su ka amsa mashi suna shiga motar,yumnah tayi mata key su ka fice daga gidan,da kallo Nainarh ta bi motar yumnah harta ɓace ma ganinta. front seat ya buɗe mata yana faɗin “let's go home” jiki a sanyaye ta nufo motar ta shiga, maida marfin ya yi ya rufe,driver seat ya shiga,key yayi ma motar su ka fice daga gidan, tsit motar tayi,tunda ta shiga ta kwantar da kanta jikin head rest,gaba ɗaya she was just moody,ɗan farin cikin data samu few days a go ya gushe tas ƙuncin data shiga kwanakin baya ya dawo mata sabo,ji take kamar yanzu ne komai ya faru,abunda ya ƙara jefata cikin ƙunci da damuwa yanzu jin kuma wani sabon sharrin da ake bin mahaifiyarta da yayanta dake kwance cikin kabarin sa da shi. gyaran murya ya yi mata yana kiran sunanta, saurin kallonshi ta yi “please Nainarh don't bother your self kinji,kar wani ciwan ya kamaki,na tabbatar in Sha Allah ya Naeem will find out the truth soon, in sha Allah they will regret” gyaɗa mashi kai kawai tayi “ki dage da yi masu Adu'a kinji,in sha Allah everything will be ok” “in sha Allah” ta faɗa, sosai ya shiga kwantar mata da hankali kamar yanda ya Naeem ya ce har su ka iso gida, lokacin da su ka iso su yumnah tuni sun jima da shiga ciki,parking yayi a compound,kallonta yayi “promise me baza ki sa damuwa a ranki ba,zaki saki jikin ki kamar baya??” “in sha Allah,Nagode” “don't mind” harta kama handle ɗin ƙofar sai kuma ta juyo tana kallonshi “sorry banyi maka godiya ba ranar nan,Nagode sosai Allah ya saka da Alkairi” murmushi ya sakar mata “karki damu you deserve more than that for me” “thank you” “ok good night,slept tight” gyaɗa mashi kai tayi tana faɗin “ba kace zaka gaishe da mom ba?” “no sai da safe zan zo” gyaɗa mashi kai kawai tayi ta fice daga motar “take care” ya faɗa, sai da yaga shigewarta tukun yayi ma motar key ya bar gidan. lokacin data shiga gidan bata samu kowa ba duk sun shige ɗakunan su saboda lokacin sallah daya gabato,ɗakin su ta nufa samun yumnah tayi tana ƙoƙarin shiga toilet. Mom bayan da ta kammala sallah magrib part ɗin Abbah ta nufa ganin tunda su ka baro gidan Abbah bai dawo gida ba kuma har kiran shi tayi baiyi picking ba. tayi mamakin ganin har lokacin bai dawo ba,sake kiran shi ta yi amma bai ɗauka ba,tana shirin sake kiranshi sai gashi ya shigo,da kallo ta bishi jikinshi duk a sanyaye kallo ɗaya zaka mashi ka fahimci akwai damuwa a tattare da shi. “barka da dawowa” jin jina mata kai kawai yayi ya nufi part ɗin shi,da har ta juya zata nufi bedroom ɗinta sai kuma ta fasa,bin bayan shi tayi,zaune ta sameshi saman sofa a parlorn shi,duk sai taji wani iri ta san wannan yanayin na shi bai rasa alaƙa da ƙin amincewar da tayi akan Auren Irfan,yayi burin haka ta kasance ba dan komai ba sai dan zumuncin shi da ƴaƴan uwanshi ya ƙara ƙarfi. har gaban sofa da yake zaune ta ƙaraso “yallaɓai lafiya,meke damunka??” ta faɗa tana kallonshi,ɗago da kanshi yayi kallo ɗaya yayi mata ya ɗauke kai “lafiya lau nake” shine kawai abunda yace ya miƙe ya nufi bedroom ɗin shi,da sauri ta bi bayan shi amma sai bata shiga bedroom ɗin ba ganin mamy ta buɗe ƙofar ɗakin alamar tana ciki,ta gefenta dady yabi ya shiga bedroom ɗin,kallo ɗaya mom tayi mata ta juya ta bar part ɗin gaba ɗaya,da harara mamy ta bita har ta fice. Dady ba komai yayi sanadiyyar shigar shi wannan yanayin ba sai tashin ciwan Noor,tunda su ka kaita hospital likitocin ke kanta sai da ƙyar aka samu ta dawo hayyacinta. *ASO VILLA* tunda ta kammala sallah isha take zaune saman sallaya a ɗakin su Ammar wanda yanzu nan ta maida wurin zamanta. kallo ɗaya zaka mata ka gane tana cikin farin ciki wanda rabonta da shiga irin wannan farin ciki tun farkon Auren su lokacin cikin su Ammar. idan tana tuna wancan lokacin sai taga kamar ba ya Zaabith ɗin ta ba,kamar an sauya mata shi ne. A yanzu fatan ta Allah yasa ta samu soyayyar shi kamar wacan lokacin,tana fatan wannan cikin ya zama sanadin da zai sauya halayensa gaba ɗaya. shafa cikinta tayi tana saki murmushi,turo ƙofar su ka yi su ka shigo, da gudu su ka nufo inda take “momy ba ki zo mun yi dinner ba?” Jan cheek ɗin su tayi tana faɗin “dadyn ku nake jira ya zo sai muyi tare” “yau zai dawo ne?” “eh yana hanya,ku tashi kuyi wanka ku zo ku canza kaya” “momy zamu jira ya dawo” “A'a kuyi wanka dai ku kwanta kunga gobe akwai islamiyya” to su ka ce suna miƙewa,da sauri su ka shiga zare kayan dake jikin su kowa so yake ya riga ɗan uwanshi shiga toilet,Fahimtar abunda su ke shirin yi ne yasa tayi saurin cewa “kai Aman ka tafi bedroom ɗina Ammar ya shiga nan” sanin fitina za su mata ne yasa ta rabasu,da sauri Aman ya fice daga ɗakin Ammar kuma ya shiga nan,tana anan zaune har su ka kammala shirin na su “oya ayi Adu'a ka kafin a kwanta” to su ka ce. bata fice daga ɗakin ba sai da ta tabbatar sunyi bacci lokacin sha ɗaya saura,tashi tayi ya linke carpet ɗin da tayi sallah ta maida cikin wardrobe ɗin su kafin ta fice daga ɗakin zuwa bedroom ɗinta bayan ta kashe masu hasken ɗakin. tana shiga bedroom ɗin toilet ta shiga tayi wanka,zama tayi gaban mirror bayan ta tsane jikinta,ɗan light makeup tayi kafin ta tashi ta nufi wardrobe ɗinta,wata irin haɗaɗiyar sexy silk dress red color ta ɗauko, ɗaga rigar tayi tana kallo lokacin ɗaya ta saki murmushi tana shafa flat tummy ɗinta. a jiye rigar tayi saman bed, earrings ta ɗauko haɗe da wasu open toe pump black color. shaf shaf ta shiga shiryawa ganin lokaci yaja kuma zai iya shigowa at any time,kayan ba ƙaramin kyau su ka yi mata ba kamar irin a club ɗin nan, ƙarema kanta kallo ta shiga yi a gaban mirror, perfume ta sake ɗauka ta feshe jikinta kafin ta fice daga bedroom ɗin bayan ta ɗauki envelope ɗin da fawar ya kawo mata, direct part ɗin shi ta nufa. A hankali take tafiya ƙarar sautin shoes ɗinta mai ɗaukar hankali ya cika ko ina na part, a bakin ƙofar ɗakinshi ta tsaya,tura ƙofar tayi ta shiga,daddaɗan ƙamshin rose flower wanda aka ƙawata ɗakin ne ya daki hancinta,ciki ta ƙarasa hasken candles ne ya haska ɗakin,ko ina na ɗakin an ƙawata shi da roses,daga saman bed ɗin anyi zanen heart da flower,takiyar roses ɗin ta ajiye envelope ɗin,food trolley dake gefen mirror ta tura zuwa bakin bed ɗin,kallon ɗakin ta shiga yi sai data tabbatar komai dai dai tukun ta fice zuwa parlor ta zauna zaman jiran shi saman sofa. tana anan zaune har bacci ya soma ɗaukarta bai shigo ba sai around 1 am ya shigo lokacin tuni bacci yayi awan gaba da ita,banko ƙofar parlorn yayi wanda hakan yayi sanadiyar farkawar ta daga bacci,saurin miƙewa tayi tana kallon ƙofar,cikin wani irin yanayi dake nuna yau ma a bige yake ya faɗo parlorn, direct sama ya nufa zuwa ɗakinshi bai ko lura da ita ba,tafiya yake yana layi kamar zai kifa ƙasa,da kallo ta bishi tana jin wani iri a zuciyarta,daurewa kawai tayi ta bi bayan shi,tana shiga bedroom ɗin yana faɗawa toilet,wayarsa da rigar suit ɗin sa da ya yasar saman bed ta kalla sai kuma ta kalli ƙofar toilet ɗin daya bari a buɗe. ƙararar shigowar message taji daga wayarshi sai ga kira kuma,kallon wayar tayi da kamar zata share sai kuma ta ɗauki wayar,abunda bata taɓa ba kenan tsawan zaman su,kallon screen ɗin wayar tayi tana kallon number dake kiranshi wacce akayi serving da Ruth,da mamaki take kallon wayar yanayin da ya shigo ne ya bata ƙwarin gwiwar ɗaga wayar,kai wayar tayi kunnenta,muryar mace taji tana faɗin “Hi beb, I hope you arrived safely?,I sent you your message via WhatsApp, When will you come back, I'm starting missin you,Please come back soon, I won't drunk anything again until you come back” Wani irin faɗuwa gabanta yayi ji abun da mai kiran nashi tace,da sauri ta zame wayar daga kunenta tana rejecting kiran,kallo wayar ta shiga yi sai kuma ta ɗaga ido ta kalli ƙofar toilet ɗin,wani message ɗin ne ya sake shigowa wayar via WhatsApp,saurin shiga message ɗin tayi direct ya kaita WhatsApp ɗin shi,wani irin mummunan faɗuwa gabanta yayi lokacin da taci karo da wasu irin nudes masu muni da aka turo mashi da sauri ta dafe saitin zuciyarta,zama tayi gefen bed ba tare da ta shiryama hakan ba,scrolling chart ɗin tayi zuwa can sama,abun da taga gani ma yafi wanda aka turo mashi yanzu muni,gaba ɗaya abunda su ke yi a chart ɗin kenan, maganganun da su ka yi basa da wani yawa suma gaba ɗaya porn yafi yawa a ciki ,saurin fita tayi daga chart ɗin,ɗaya bayan ɗaya ta shiga buɗe charts ɗin dake WhatsApp ɗin shi,ƴan mata ne yake chart da su iri iri wasu ma ba musulmai ba ne,saurin fita tayi daga WhatsApp ɗin gaba ɗaya tana sake dafe zuciyarta dake neman fasa ƙirjinta ta fito,tuni hawaye sun wanke fuskarta,bata taɓa dana sanin Auren Zaabith a rayuwarta ba sai yau,tayi takaicin haɗa zuri'a dashi,wata irin muguwar tsanar shi ce ta rufeta,gaba ɗaya farin cikin da take ciki ya rikiɗe zuwa tsantsar ɓacin rai,wani irin haushin cikin dake jikinta take ji yanzu,ga ƙyamar jikinta da take ji,miƙewa tayi rai a ɓace ta nufi ƙofar fita da wayarshi a hannunta,harta kama handle taji fitowar shi daga toilet. daga shi sai short ya fito,kallon bayanta yayi,wani irin makirin murmushi ya saki,he is staggering ya nufo inda take,hannunshi ya kai saman bayanta,cike da salon iskanci ya matsa ass ɗinta yana wani sauke ajiyar zuciya, murmushi yayi yana kai hannu ya kama shoulder ɗinta,a wani irin fusace ta juyo baiyi aune ba sai ji yayi ta sauke masa lafiyyun maruka a cheek,saurin dafe cheek ɗinshi yayi yana binta da idanunsa da kallo ɗaya zaka masu gane he is drunk,sun ƙanƙance tsabar jaraba,kallota yake kamar zai faɗo mata, rai a ɓace cike da tsana take kallonshi from head to toe “kar ka ƙara kuskuren taɓani,na tsaneka” ta faɗa cikin ɗaga murya,turo baki yayi yana sa ɗayan hannunshi ya tallabo kumatunshi kamar ƙaramin yaron,cikin ƙunar rai take faɗin “wallahi na tsaneka,bana son ganin ka,banyi tunanin bayan shaye shaye kai mazinaci ba ne,ban san cewa kai fasiƙi ba ne,nayi dana sanin kasancewata matarka na tsawan shekaru,nayi takaicin tara zuri'a da kai,ina baƙin cikin kasancewarka ɗan uwana,fasiƙi,mazinaci kawai, wallahi na tsaneka” with heartbrok take faɗin wannan kalaman hawaye na bin cheek ɗinta,shi kuwa binta kawai yake da ido ba wai dan yana fahimtar abunda take faɗa ba ne. “na tsaneka, I hate yo you,na gama zama da kai,our marriage is over, ka sawwaƙe man,bazan cigaba da zama da kai ba wallahi” ku ka take sosai tana faɗin ya saketa amma kamar ba dashi take magana ba,tunda ya kafe bakinta da ido ko motsi baya yi. Jifa tayi da wayarshi dake hannunta,saurin kallon wayar yayi sai kuma ya kalleta,ɓata fuska yayi kamar zaiyi ku ka,sai kuma ya nufota yana buɗe mata hannayenshi yana faɗi “ohh... noo ... ooo wife ta... ta.. yi fushi,why a... are ... ... y u o an... angry, so so sooooryyy stop cary pleaseeeeee” ya faɗa kamar mai koyan magana yana kai hannunshi da nufin hugging ɗinta. A fusace tasa hannu biyu ta hankaɗeshi har sai da yayi tag taga zai faɗi “stay away from me, I hate you” ta faɗa tana ɗaga mashi murya, fashe mata da ku ka yayi kamar ƙaramin yaro can kuma ya kwashe da dariya. wani irin abu ne ya tsaya mata a maƙoshi,tsaki kawai taja tana faɗin “i hate your attitude” buɗe ƙofar ɗakin tayi zata fita,wani irin fisgota yayi jikinsh,zare ido ta shiga yi a fuskarshi gabanta na wani irin duka dan ba ƙaramin tsorata tayi ba. Lumshe ido yayi kaɗan ya buɗe yana kai hancinshi saman shoulder ɗinta,ƙamshin perfume ɗin dake jikinta ya shaƙa “you smeal damn sexxy,i miss u beb” wani irin baƙin ciki ne ya rufeta jin abin da ya ce. ko kawar kwace kanta ta shiga yi daga rikon da ya yi mata amma ina yaki ya sake ta,ganin ta kasa ne yasa ta shiga kai mashi duka tana kuka “stop beating me wife,I miss you,I need to have...”sai kuma yayi shiru bai karasa ba,cizo ta kai mashi arm ɗinshi da sauri ya saketa “na tsane ka har abada ba ni ba kai” ganin ta na ƙoƙarin fita daga ɗakin ne ya sa ya fizgota a karo na biyu,jifa yayi da ita saman bed kamar ba shi ba. idanunta ne suka sauka a kan short ɗin da ke jikin shi,saurin kauda kai tayi gabanta na wani irin faɗuwa,da sauri ta yunkura zata sauka daga saman bed din, sai dai kafin ta sauka tuni yayo kanta, gaba ɗaya ya faɗa kanta, zare ido ta shiga yi gabanta na wani irin duka, duƙo da fuskarshi yayi zuwa tata da nufin manne bakinshi da nata. saurin kauda fuskarta tayi, kokawa ta shiga yi da shi don ta ƙwace kanta amma ta kasa. duk da he is drunk karfin mace da namiji is not decem,without anything ya afka mata like animal,gaba daya rigar dake jikinta ya maida ta feses ya yi jifa da ita haka short ɗin dake jikin shi. duka,cizo da yakushi babu wanda bata kai mashi tana faɗin I hate you amma duk a banza,kamar zai kashe ta yake faɗin “why are you angry,stop angry” ganin ba sarki sai Allah ne yasa ta fara bashi haƙuri tana haɗa shi da Allah amma ina kwata kwata bai san tana yi ba, baya ma tare da ita, banda kalmar i love you babu abinda ke fita daga bakin shi,tun tana da bakin bashi hakuri har bakinta ya mutu sai hawaye kawai dake bin cheek ɗinta. sai da ta dawo ko numfashi da kyar take fitar da shi tukun ya kyaleta bayan yayi satisfy. Can gefe ya koma yana sauke ajiyar zuciya cikin ƙanƙanin lokaci bacci yayi awan gaba da shi. Ta kai tsawan 30 minutes a kwance ko ɗan yatsanta bata iya ɗagawa,ga wani abu da ya zo saitin mararta ya tsaya mata kamar dutse. gaba ɗaya jin jikinta take kamar an watsa mata ɗanyen barkono tsabar baƙin ciki da takaicin kusantar ta da yayi,da kyar ta yi getting courage ta sauka daga saman bed ɗin. da sauri ta durƙushe ƙasa saboda kulle matan da mararta yayi ga wani irin azabiben ciwo da take ji ƙasa ƙasa, da kyar da jan ƙafa ta fice daga ɗakin. bedroom ɗin ta ta nufa, tana shiga hijab ɗinta da ke cikin wardrobe wacce tayi sallah ta ɗauka, zura hijab ɗin tayi a jikinta, da dafa bango ta fice daga ɗakin,lokacin da ta isa compound ɗai ɗaikun securitys ne ke kai kawo, da gudu ɗaya daga cikin su ya nufota yana tambayar lafiya da ƙyar ta iya furta mishi yayi ma driver magana, da gudu ya juya sai gashi tare da drivers har su uku,mota ta sa suka ɗauko, kyar ta ɗaga kafarta ta shiga mota. cike da tashin hankali securitys ɗin su ke kallon inda ta tsaya,key driver yayi ma motar yana faɗin ina za su gida tace mashi, ɗan juyowa driver yayi ya kalleta, cike da ladabi yace “amma madam a irin wannan yanayin da ki ke hospital ya kamata mu tafi” da ƙyar ta iya karfin halin ce mashi yayi abinda tace,toh kawai yace yana reverse su ka nufi gate motar securitys biyu na gaba biyu na baya su ka fice daga Villa ɗin. *Queen Kainart*💫 Ringing din wayar ta ne ya tashe ta,firgigit ta farka tana faɗin innalillahi wa inna ilaihir raji'un saboda ringing ɗin wayar har cikin kwakwalwarta kasancewar wayar tana ajiye ne a saitin kunnenta. da sauri ta tashi zaune tana kai hannunta ta kunna bedside lamp haske ya ɗan gauraye ɗakin,kallon agogon da ke manne jikin bango tayi wanda ke nuna karfe huɗu da arba'in da biyu na dare,kallon yumnah dake kwance gefen ta tana bacci tayi lokacin har kiran ya katse wani ya sake shigowa. a hankali ta ɗauki wayar tana duba mai kiran nata privet number ta gani alamar mai kiran yayi hiding number ne. Bin screen ɗin wayar da ido tayi tana mamakin waye wannan yake kiranta a irin wannan lokacin kuma da ɓoyayyar number,har kiran ya sake katsewa bata yi picking ba. wani kiran ne ya sake shigowa wayar a karo na uku still da ɓoyayyen Number, shahada kawai tayi ta ɗaga tana ambatar bismillah. shiru tayi tana sauraron me na cikin wayar zai faɗa, amma taji anyi shiru, jin anyi shirun ne yasa tayi ƙarfin halin cewa “Assalamu Alaikum” on the other side taji muryar da koda za tayi shekaru ɗari bata ji ta ba bazata ɓacemata ba ance “Nainarh!” wani irin duka kirjinta yayi har sai da ta dafe saitin zuciyar ta, janye wayar ta yi daga kunnenta tana kallon wayar don ta tabbatar da abunda ta ji gaskiya ne. kallon wuyar take sosai ga alamar time nan yana tafiya na kira,da gaske dai abunda taji gaskiya ne,da sauri ta maida wayar a kunnen ta “Y... ... ya... .. Abid” shi ne sunan da ta ambata cikin rawar murya, kallo ɗaya zaka mata ka hango ruɗani da tsoron da take a ciki “na'am ƙanwata, kin yi mamakin jin murya ta ne?” “ya Abid dama kana raye!?” ta faɗa tana zaro ido kamar wacce tayi ma sarki ƙarya “ƙwarai Nainarh,ina nan a raye” “amma ya Abid aka ce ka mutu,kuma mutane da yawa sun shaida mutuwarka??” “haka ne Nainarh amma ina nan a raye” “don allah ka faɗa man miye ya faru da kai akace ka mutu,kenan daddy na ma yana raye??” “labari ne mai tsayi Nainarh” “dady na fa,shima bai mutu ba kamar kai?” “Allah kaɗai ya san gaskiya Nainarh” yanayin fuskarta ne ya canza lokaci daya, hawaye har sun taru a idanunta fatan ta ace shima dadyn ta bai mutu ba kamar yayanta “ina fata Nainarh duk wani bayani da ya kamata kinyi ma CM baki ɓoye mishi komai ba” “waye cm kuma ya abid?” ta faɗa cikin rashin fahimtar wa yake nufi “Colonel Major naeem nake nufi,ba ya gayyace ki gidansa ba har yayi miki tambayoyi ina fatan biki ɓoye mishi komai ba har flash ɗin da uncle ya baki kin basa??” tunda ya fara magana tayi shock,ko motsi ta kasa yi,mamakin ta duk a ina yasan wannan “ina fatan kin basa Nainarh,hakan da zaki yi shi kaɗai zai taimake momyn ki dani kaina” da kyar ta iya buɗe baki tace “amma ya Abid taya akai ka sani” “ki ajiye wannan tambayar a gefe ba shine mai mahimmanci ba a yanzu, kin basa flash ɗin ko baki ba sa ba??” wani irin faɗuwa gabanta yayi,muryar tana rawa tace “wane flash,bansan akan wane flash kake magana ba??” “Nainarh!” ya kira sunanta da ɗan ƙarfe “flash ɗin da dadyn ki ya baki, ko baki son a gano wanda suka kashe shi ne?” kamar za ta yi kuka tace “wallahi ya Abid babu wani flash da dady ya bani” “ki tuna Nainarh, ko dai kin jefa shi wani wuri kin manta?” “wallahi ya Abid ka ji na rantse babu wani flash da dady ya bani,lokacin ma da suka kashe shi bana hayyacina” “ai ba a wannan lokacin ya baki ba, ki sake tunawa Nainarh, rayuwarmu na cikin haɗari har da ke, bashi wannan flash ɗin shine kawai zai fitar damu daga halin da muke ciki” “rayuwa ta fa kace ya Abid” “kwarai kuwa Nainarh wanda suka kashe dadynki sun jima da sanin flash ɗin da suke nema yana hannunki, ki yi ƙoƙari ki tuna inda ki ka ajiye shi Nainarh, kullum cikin bibiyar rayuwar mu suke Nainarh, ki daure ki tuna in da kika ajiye shi,idan baya tare da ke ne ki sanar da ni in da yake zan je na dauko shi ko a ina ki ka ajiye shi” hawayen da suka taru a idon ta ne suka shiga zubowa “na shiga uku ya Abid wallahi ka tsoratar dani,sau biyu ana turo man message ana man barazana akan flash wallahi babu wani flash a hannu na” “You see! kinga abun da nake faɗa maki ko?, ki daure ki tuna inda kika ajiye shi” “taya zan tuna ya abid bayan ba'a bani ba” “to shikenan na fahimta,ki daure ki sanar da CM an turo maki massege, amma kar ki sanar da shi komai game da dawowa ta kin ji” “in sha Allahu bazan faɗa mashi ba, yanzu kai kana ina?,ina son ganin ka” “gani na a yanzu ba zai yiwu ba Nainarh, kema ina son ki kula,motsinki kaɗan suke jira” “shikenan in sha Allah, nagode amma idan ina son nayi magana da kai taya zan same ka?” “karki damu zan dinga kiranki don naji a wani hali kike ciki,yanzu ki koma ki yi barci, kar ki sa damuwa a ranki kinji ko” gyaɗa kai tayi kamar tana a gaban shi “goodnight take care,bye bye” ya faɗa yana rejecting call ɗin zame wayar tayi daga kunnenta gaba ɗaya a tsorace take, to ita wane flash ake tahumarta bayan dadyn ta bai bata komai ba, kuma a ranar da suka shigo gidan duk wani flash na gidan sai da suka ƙone shi hatta laptop din su. ta shafe tsawon mintuna 40 tana saƙawa da kwancewa kafin dai ta kwanta bayan ta kashe bed-side lamp, addu'a ta sake yi ta shafe jikinta gaba ɗaya, a tsorace take amma deep down tayi matukar farin ciki da dawowar yayanta,sai around 3 am bacci ɓarawo yayi awan gaba da ita. barci bai yi nisa ba taji saukar hannun mutum a jikinta,wani irin bugawa zuciyarta tayi,suman kwance tayi ko motsi bata iya yi, jin hannun ya fara yawo a jikinta ne yasa bugun zuciyar ta ya tsananta, ba zato ban tsammani taji saukar hannun mutum a kirjinta bata san lokacin da ta kware baki zata fasa ƙara ba,saurin toshe mata baki aka yi,kokawar fizge hannun daga bakinta ta shiga yi amma ta kasa,bakin mutum taji saitin kunnen ta in a whisper taji muryar data sake jefata cikin tashin hankali “kada ki tsorata ban zo da nufin cutar dake ba, naga kina cikin damuwa ne yasa nazo dan na ɗebe maki kewa,tun ranar da na fara tozali da ke gaba ɗaya na rasa sukuni na,na shiga halin tunanin zazzafar surar ki mai matukar ɗaukar hankali,ki amince man nayi miki alƙawarin zan mantar dake duk wata damuwarki,zan jiyar dake daɗin da ko ɗa namiji ba zai jiyar dake irin sa ba,ki amince da buƙatata Nainarh, a kullum da tunaninki nake kwana da shi nake tashi,you dominate my mind,I love you Nainarh” A lokaci ɗaya wani irin tsoro da tashin hankali ne su ka mamayeta,tuni hawaye sun fara zarya a kumatunta. kokawar yanda zata ƙwace kanta take amma ta kasa, hankalinta ne ya ƙara tashi lokacin da taji tana neman rabata da PJ dake jikinta. bata sake shiga tashin hankali ba sai da taji saukar bakinta a nata,sosai hankalinta ya sake tashi,kokawa ta shiga yi da ita tana kai mata duka ta ko ina amma kamar tana dukan dutse,ba bu ma alamar ta san tana yi,ganin dai ba sarki sai Allah ne yasa ta shiga laluben yumnah amma taji wayam bata kan bed ɗin,tsoronta ne ya tsananta, gashi har ta so ma rabata da kayan jikinta. Allah ne ya taimaketa ta samu Sa'a ta daddage ta galla mata cizo a tongue,da sauri ta saki bakinta tana fasa ƙarar azaba, da mugun sauri Nainarh ta zabura ta koma can gefe. da sauri ta kai hannunta jikin switch,duk da tsoron da take ciki amma ko ba komai zata so tabbatar da zarginta. ganin abun da Nainarh ke shirin yi ne yasa ta miƙewa,da gudu ta nufi ƙofar fita daga ɗakin,tana kaiwa tsakiyar ɗakin Nainarh na kunna bulbs haske ya gauraye ɗakin, da kallo Nainarh tabi bayanta har ta fice daga ɗakin da gudu. a jikin head board ta takure jikinta sai rawa yake kamar wacce sanyi ya yi ma mugun kamu,kifa kanta tayi saman laps tana fashewa da wani irin ku ka mai ban tausayi. cikin muryar ku ka take faɗin “mi yasa zaki man haka,dama tsawan zaman mu dake sha'awata ki ke yumnah,why, mi yasa,mi yasa yumnah!!” ta faɗa tana sake fashewa da wani ku kan. ku ka take Sosai babu mai lallashinta, yumnah ta karya mata zuciya,tayi data sanin sanin yumnah a rayuwarta, a wannan lokacin tayi fatan ace a hannun dangin mahaifiyarta ta zauna ko na mahaifinta,gara mata azabar su da irin wannan ƙazantar. har aka kira sallar fajr bata sake komawa bacci ba,har lokacin jikinta kyarma yake ga wani ciwan kai da zazzaɓi da ya rufeta lokaci guda. da ƙyar ta samu tayi ƙarfin halin tashi ta nufi toilet ta ɗauro alwala ta fito, dressing room ɗin su ta nufa, carpet da hijab ta ɗauko,bedroom ɗin ta dawo,anan gefen bed ɗin ta shimfiɗa carpet ɗin tayi sallah. ko da ta kammala sallah bata tashi a kan carpet ɗin ba anan bacci ɓarawo yayi awan gaba da ita. *UNITED STATE❤* *Las Vegas (Nevada)* Kamar yanda Mrs Malika ta faɗa washe gari ta tafi, Nailarh har Airport ta rakata,da zata tafi harda kukanta. tun a ranar Aunty Sophia ta fara mata Allurar a bisa tsarin da Dr daniel ya bada, Alluran na tsawan one month ne,after one one day,15 days kenan. Tunda akayi discharging ɗinta daga hospital kullum ne sai C E O ya turo mata da message sau uku a rana morning, evening and night,lokuta da dama shi ke tashinta daga bacci,tun abun nashi na ƙular da ita yanzu har ya koma bata mamaki da baya missing koda rana ɗaya ko lokaci,wasu lokutan kuma kiranta yake,tun bata picking har ta koma tana picking duk da ba wata maganar arziƙi su ke ba,masifa da buge mashi warning sun fi yawa a kalamanta. duk time ɗin data tace zata ɗauki mataki akanshi, murmushi yake mata yace idan zata hukuntashi tayi mashi sassauci kar shima heartAttack ya kamashi,duk lokacin ɗaya furta mata hakan amsa ɗaya take bashi “zanfi jin daɗin haka,domin ka takura man”. Yauma kamar kullum tana kwance a bedroom ɗin ta har 10 pass 11 bata farka daga bacci ba,tun ɗazu wayarta ke haske alamar shigowar message,sau biyu Aunty Sophia na shigowa dubata amma bata tashi ba. kiran daya shigowa wayarta ne yayi sanadiyyar tashinta,a hankali ta buɗe idanunta masu ɗauke da bacci,ɗan tsaki taja tana tashi zaune,ta san babu wanda zaiyi mata wannan kiran at this time bayan shi. jawo wayar tayi tana duba screen ɗin,kamar yanda tayi zargi shi ne,girgiza kai tayi tana jan wani tsakin. picking call ɗin tayi haɗin da kara wayar a kunnenta,zazzaƙar muryarshi mai cike da natsuwace ta daki dodon kunnenta “sleeping baby,Are you still on the bed?” “why are you disturbing me in this morning?” “you start ko,why are you still on the bed,I take my breakfast but still I'm hungry,ashe beb ce ba tayi breakfast...” bai ƙarasa ba yayi shiru dalilin dariyar da yaji Nailarh nayi, kalaman shi ne su ka yi matuƙar bata dariya,shiru yayi yana sauraron dariyarta dama yayi hakan ne dan ya sata farin cikin,sai da tayi mai isarta tukun tayi shiru,ɗan ajiyar zuciya ya sauke “please wake up and take a shower and come have breakfast baby” “I won't do it!” ta faɗa kai tsaye “please cutie pie” ya faɗa cikin kwantar da murya “I Can't” ta faɗa tana ɗan ɗaga murya haɗin da yin rejecting kiran,jefar da wayar tayi gefe tana furzar da iska mai zafi daga bakinta haɗi da zura hannunta cikin sumar kanta tana yamutsata. turo ƙofar ɗakin Aunty Sophia tayi ta shigo tana turo food trolley,ɗago da kai Nailarh tayi tana kallonta,har bakin bed ɗin Aunty Sophia ta ƙaraso “baby kin tashi,hope you slept well?” kallonta Nailarh tayi harta zauna gefen bed ɗin without saying anything her,kallonta Aunty Sophia tayi ganin ta zuba mata ido “baby lafiya?” “he disturbing me” ta faɗa tana ɓata fuska “baby ai duk laifinki ne,kin fasa hukuntashi ne” “no kawai naga yayi regretting ne” “saboda yayi regretting ne yasa ki ka ƙyaleshi yake disturbing ɗinki?” “wani side na zuciyata ne ke cewa na yafe mashi tunda ba yana sane yayi ba” ɗan ajiyar zuciya Aunty Sophia ta sauke “shikenan baby,bazan hana ki yafe mashi ba,dama yana da kyau mutum ya zamo mai yafiya” ɗan ya mutse fuska Nailarh tayi tana matsowa kusa da Aunty Sophia,kwantar da kanta tayi saman shoulder ta,shafa kanta Aunty Sophia tayi “sorry,go and take a shower,ga breakfast nan da sauran injection ɗinki” ɓata fuska Nailarh tayi “wai yaushe ne injection ɗin nan zata ƙare?” “two month ne baby” “gaskiya am tired Aunty Sophie,wai ma ta mecece?” “Dr Daniel zaki tambaya” ɓata fuska Nailarh tayi,hannu ta zura ta jawo wayarta dake ringing, picking call ɗin tayi tana kara wayar a kunnenta, muryar momyn ta ce ta daki dodon kunnenta “baby ke da waye a waya ina kira ba kiyi picking ba?” shiru Nailarh tayi ba tare da tace mata komai ba “magana nake baby?” “momy yaushe za ki dawo?” “next month” Malika ta faɗa “zan kuwa biyo ki ne” Nailarh ta faɗa tana rejecting kiran “baby Please wakeup and take a shower” Aunty Sophia ta faɗa “zaki man ne?” wani kallo Aunty Sophia tayi mata “dama ni nake maki?” “to ai kin hana masu yi man suyi man” “saboda ina so ki zama cikakkiyar budurwa ba yarinya ba,ko kina so CEO ya cigaba da rainaki?” taɓe baki Nailarh tayi without saying anything to her,tashi tayi ta nufi bathroom da kallo kawai Aunty Sophia ta bita tana sakin murmushi,tunda suka dawo daga hospital ta hana su lolarh yi mata wanka,da Nailarh tace wani abu sai ta fake mata da kar CEO ya rainata. tashi tayi daga saman bed ɗin ta gyara mata,har ta kammala Nailarh bata fito ba,wayarta ta ɗauka a dalilin shigowar message da taji. messages ta gani daga Number da yawa wasu Nailarh ta buɗe wasu na unread,ta sama ta shiga karanta message ɗin ba tare da ta shiga ciki ba, murmushi ta saki lokacin data kammala karanta message ɗin “i don't know who are U,ban san mi ka ke so a tare da Nailarh ta ba” saurin ajiye wayar tayi jin alamar Nailarh zata fito,tashi tayi da sauri ta nufi Nailarh tana faɗin “baby have you done?” ta faɗa tana jan hannun Nailarh dake sanye da bathrobe zuwa dressing room ɗinta,da kanta ta shiga shiryata,tunda su ka dawo daga hospital ita ke mata komai. bedroom ɗin su ka dawo bayan ta kammala shiryata,good trolley data shigo da shi ta jawo,sarving ɗinta tayi,da kanta ta shiga bata abincin harta kammala. Injection ta haɗa tayi mata,harda yar ƙwallarta da tayi mata,tattara kayan Aunty Sophia tayi tana faɗin “anjima nake son muje Orphanage, nurse laurah tace man yaranki na ta tambayar kina ina” “Ayyah,shaf na manta da su” “anjima sai muje” “okay Nailarh ta faɗa ficewa Aunty Sophia tayi. *tun ranar da su ka amso kaya a port,kusan kullum ne sai taje ta duba jikin yaran,dawowar Momyn ta yasa ta rage zuwa saboda Momyn tata ta nuna bata son tana zuwa* *ABUJA NIGERIA*💫 har yanzu kwance take saman carpert ɗin da tayi sallah,turo ƙofar ɗakin Ishrat tayi ta shigo,ganin kowa na gidan ya fito Nainarh ce bata fito bane yasa ta zo duba ko lafiya. da mamaki take kallonta kwance a ƙasa,har inda take kwance ta ƙaraso,a hankali ta shiga kiran sunanta,da alama tayi nisa sosai a cikin baccin yasa ba taji kiran da tayi mata ba,hannunta ta kai saman kafaɗarta da nufin tashin ta wata irin zabura tayi haɗi da fasa ƙara,saurin toshe mata baki Ishrat ɗin ltayi tana faɗin “nice Aunty Nainarh” wata irin wawuyar ajiyar zuciya ta sauke jin muryar Ishrat a kusa da ita,gaba ɗaya a tsorace take. kafeta da ido Ishrat tayi “lafiya ki ke Aunty Nainarh?” gyaɗa mata kai Nainarh tayi “lafiya lau nake” gyaɗa kai kawai Ishrat tayi ba dan ta yarda da abunda Nainarh ta faɗa mata ba,tashi tayi daga duƙen da take. bed ɗin su ta fara gyara masu,tashi Nainarh tayi ta nufi bathroom,mirror ta nufa da sauri,kallon lips ɗinta da shoulder ɗinta da su ka yi jawur tayi,wasu irin hawayen baƙin ciki ne su ka wanke fuskarta,tayi data sanin sanin yumnah a rayuwarta,bata taɓa expecting haka daga gareta ba,ta kai tsawan five minutes a gaban mirror kafin ta cire kayan jikinta,ruwa ta tara a bathtub,wanka ta shiga yi,kamar zata fasa fatar jikinta haka take dirzarta da sponge,gaba ɗaya ƙyanƙyamin jikinta take saboda abunda yumnah tayi mata. sai da jikinta ya fara mata zafi tukun ta dakata,fatar tayi jawur kamar wacce aka watsama tafasasshen ruwa, fashewa tayi da wani irin kuka mai ban tausayi “mi yasa ƙaddara ta haɗani dake yumnah,mi na aikata ne wannan abubuwan ke faruwa da ni” ta faɗa cikin ƙunar rai,ta kai tsawan 30 minutes a toilet tana aikin ku ka kafin ta wanke jikinta ta fice,har time ɗin hawaye ne ke zarya a fuskarta. lokacin data fito bata samu Ishrat ba harta kammala gyara masu ɗakin ta fice, dressing room ɗin su ta nufa, idanunta ne su ka sauka akan ƙaton kwalin da su ka yima momynta shopping ita da yumnah,yau su ka yi za su kai mata ziyara amma ta ɓata komai,kauda kai tayi daga kallon kwalin ta nufi wardrobe ɗin su,ɓangaren da kayanta su ke ta nufa,doguwar rigar atamfa ta ɗauko haɗe da hijab,zura kayan tayi a jikinta, shaf shaf ta shirya a cikin kayan, bag hanger su ta nufa, ƙaramar side bag ta ɗauka, wayarta da atm dinta ta saka a cikin jakar. parlor mom ta nufa ta yi mamakin ganin falon tsit babu kowa har ta juya da da nufin zuwa bedroom ɗin mom,Ishrat ce ta fito daga kitchen,kallon Nainarh dake ƙoƙarin shiga bedroom ɗin mom tayi “mom ba ta nan” ishrat ta faɗa,dakatawa tayi tare da sakin handling ɗin kofar,dawowa tayi cikin parlorn tana faɗin “ok bari na shiga na gaishe da daddy” “shima baya nan” Ishrat ɗin ta bata amsa,da mamaki Nainarh ke kallon Ishrat ɗin “to ina suka tafi,Aunty laatifa fa??” “suna hospital gaba ɗayan su har da Aunty yumnah,Aunty Kainart ce bata da lafiya” “Aunty Kainart!?” Nainarh ta faɗa jinjina mata kai Ishrat ɗin tayi alamar Eh gyaɗa kai Nainarh tayi tana faɗin “Allah ya bata lafiya, amma tun yaushe suka tafi?” “gaskiya ban sani ba, amma ina tunanin tun cikin dare su ka tafi,dan da safe Aunty yumnah da Aunty Fa'iza sun zo sun ɗaukar masu breakfast,tace idan kin tashi ki kirata a waya tayi ma driver magana ya kai ki” ok kawai tace mata tana nufar dining room,nufo dinning room ɗin Ishrat tayi da nufin saving ɗinta, dakatar da ita Nainarh tayi tana cewa “barshi kawai zan yi saving kaina” da to Ishrat ɗin ta amsa tana barin wurin, black tea kawai ta haɗa tasha,tashi tayi handbag ɗinta dake kan sofa ta nufa dauka tayi ta fice daga parlorn. da mamaki Ishrat ke kallon warmers ɗin da ke kan dining,ganin Nainarh ba taci komai ba,tunani ta fara anya lafiya,musamman tsoratan da tayi lokacin da ta tashe ta daga bacci. warmers ɗin suka shiga kwashewa ita da munirat suna kaiwa kitchen. Nainarh tana ficewa daga parlorn direct compound ɗin gidan ta nufa ɗaya daga cikin securitys din gidan dake shawagi tayima magana a kan tana son zata fita ne,daya daga cikin drivers ɗin da ke zaune tare da maigadin gidan ya kwalama kira,a hanzarce ya taso ya nufo inda suke, cike da girmamawa ya gaishe da ita,da kulawa ta amsa mashi tana sanar da shi zai kai ta prison ne wurin mahaifiyarta, da ladabi ya amsa mata da to yana nufar parking space ɗin gidan,ɗaya daga cikin motocin dake parking space ɗin ya nufa key yayi ma motar tare da nufar inda take, back seat ta buɗe ta shiga, reverse yayi suka nufi main gate ɗin gidan,suna isowa securitys ɗin dake bakin gate ɗin suka dakatar da su,daya daga cikin security ne ya taso,da sauri driver ya sauke glass ɗin motar,gaisawa su ka yi da security yana tambayar ina za su “prison” ya faɗa, tambayarshi yayi shida wa yana nufar back seat,sauke glass Nainarh tayi da ladabi ta gaishe da shi amsa mata yayi cikin kulawa yana faɗin adawo lafiya haɗi da barin wurin,key driver yayi ma motar su ka fice daga Estate ɗin. direct hanyar central Jail su ka nufa,sai da su ka yi nisa Nainarh tace “please idan ka samu mall a gaba zan ɗanyi shopping” da ok ya amsa mata. a bakin wani haɗaɗɗen Mall na yan gayu yayi parking,fitowa tayi,ciki su ka shiga yana biye da ita a baya within a five minute ta kammala shopping ɗin duk wani abu data san mahaifiyarta zata buƙata,wurin biyan kuɗi su ka nufa driver na tura cart. Atm ɗin ta ta ciro bayan an gama calculating kuɗin kayan,ATM ɗin ta miƙa masu amma sai mutumin ya sanar da ita ai an biya kuɗin kayan,da mamaki take kallon mutumin “ban gane an biya ba” ta faɗa dan jin waye zai biya kuɗin kayan data saya “afuwan ba'a bamu damar faɗa ba,zaku iya tafiya”taɓe baki kawai tayi koma waye matsalarshi damuwar da take ciki ma ta isheta,har parking lot ma'aikatan wurin su ka kai mata kayan,a booth driver yasa kayan, reverse yayi su ka bar mall ɗin. within a time su ka iso Jail ɗin,ɗaya daga cikin securitys ɗin dake gadin Jail ɗin ya nufo motar,sauke glass ɗin motar yayi,gaisawa su ka yi da guard ɗin,daga yanayin gaisuwar ta su zaka fahimci sun san juna,umarni ya bada aka buɗe masu gate,cikin Jail ɗin su ka shiga. A parking lot su ka yi parking,fitowaNainarh tayi,buɗe booth ɗin motar driver yayi, shopping ɗin da tayi ya ɗauko, office ɗin C G C suka nufa,a bakin ƙofar office ɗin su ka tsaya, ɗaya daga cikin securitys ɗin dake bakin ƙofar ne ya shiga dan sanar da zuwan su,fitowa yayi yana sanar da su za su iya shiga. cikin office ɗin su ka shiga bakinta ɗauke da sallama, a zaune C G C yake saman chair ɗin shi,da fara'arsa ya amsa sallama da ta yi,ɗaya daga cikin chairs ɗin dake gaban desk ɗin shi ya nu na mata alamar ta zauna,zama tayi driver na ajiye kayan dake hannunshi. fita drivern yayi,ruwa da lemu CGC ɗin ya ajiye mata, ɗan murmushi tayi tana faɗin “ina wuni uncle” “lafiya lau Nainarh,yau sai ke kaɗai,ina barisster da yumnah?” “tana da patient ne a hospital shiyyasa bata zo ba” “Ayyah Allah sarki, Allah ya sawaƙa” “Ameen,Momy fa uncle?” ta faɗa dan ta ƙagara taga momynta “karki damu nasa ayi magana,yanzu zata zo” jin jina mashi kai tayi wasu chairs dake can ɗan nesa da desk ɗin shi ya nuna mata yana faɗin “you have 30 minutes” godiya tayi mashi tana tashi ta nufi chairs ɗin,tana zama ana buɗe ƙofar office ɗin officers mata ne guda biyu su ka shigo tare da momynta,da gudu ta nufi mahaifiyar tata ta faɗa jikinta haɗi da sakin kuka,wani irin sanyi jikin Hajiya Asma'u yayi lokaci ɗaya wasu zafafan hawaye su ka wanke fuskarta, hugging ɗin ta tayi sosai tana jin wani irin tausayin junansu, sun kai tsawan minti biyar kafin su ka raba jikinsu har time ɗin Nainarh kuka take itama mahaifiyarta hawayen dake fuskantar basu dai zuba ba,ƙarfin hali tayi wurin lallashin Nainarh, chairs ɗin dake wurin su ka nufa su ka zauna tana cigaba da lallashinta,shiru Nainarh tayi tana kwantar da kanta saman shoulder momyn ta ta “ina barisster?” hajiya Asma'un ta faɗa “ba ta zo ba,Momy dan Allah ina so na dawo wurin ki” ta faɗa tana ɗago kanta daga kafaɗar mahaifiyar ta ta C G C na daga zaune saman chair ɗin shi duk wani abu da su ke faɗa yana ji haka ma officers ɗin da su ka shigo da hajiya Asma'un, wani irin kallo mai cike da tausayi hajiya Asma'un tayi mata “mi yasa ki ke son zama nan,wani abun ya faru dake ne,ko dai Zulaihart tayi maki wani abu?” girgiza mata kai tayi “A'a kawai dai ina son zama tare da ke,na gaji da zama babu ke a kusa dani” “Nainarh nima kaina bana jin daɗin rashinki a kusa da ni,amma ya za muyi haka Allah ya ƙaddaro a rayuwar mu,babu yanda muka iya dole mu karbi ƙaddarar mu hannu bibbiyu,kiyi haƙuri kinji,zamanki anan bazai yiwu ba” yanayin fuskar Nainarh ne ya canza har ga Allah abunda zai nisanta da yumnah take so a yanzu,sai dai ya za tayi dole tayi haƙuri tunda hakan ƙaddara ta zaɓar mata, lallashinta sosai momyn ta ta tayi,kamar yanda C G C ya faɗa 30 minutes na cika aka fice da Hajiya Asma'un bayan sunyi sallama da Nainarh ta ɗauki shopping ɗin data kawo mata,harda ku ka Nainarh lokacin da suka fice,sallama tayi ma CGC ɗin ta fice,a bakin ƙofar office ɗin ta samu driver,parking lot su ka nufa inda su ka yi parking motar su. Ficewa su kayi daga prison ɗin har lokacin da ɗan sauran hawaye a fuskar Nainarh,wani irin tausayinta ne ya kama driver,tsit motar tayi har su ka kama hanyar da zata maida su Estate ɗin dama a haka su ka zo. da mamaki yake kallon motar dake bayan su idan ba idanunshi ba ne basa gani sosai ba tun lokacin da su ka fito daga Estate ɗin motar take a bayan su,a lokacin bai kawo komai a ranshi ba amma yanzu abun ya ɗan ɗaure mashi kai,ta mirror ya kalli Nainarh dake back seat idanunta a rufe kamar mai bacci. maida duban shi yayi ga motar har lokacin tana biye da su, street ɗin da zai sada su da Estate ɗin ya shiga still motar na nan biye da su,abun ne ya fara bashi tsoro,bai fita daga wannan tsoron ba sai ga wata mota ta tunkarosu gadan gadan,yayi matuƙar mamakin ta inda motar ta ɓullo, ƙoƙarin kauce mata ya shiga yi yana mamakin ko driver motar ya rasa birkinshi ne. duk yanda ya kai ga ƙoƙarin kauce ma wannan motar abun yaci tura,duk in da ya matsa sai motar ta bishi. wani irin mahaukacin burki ya taka har kanshi na haɗuwa da Steering wheel lokacin da motar ta daki gaban motarshi,bai san time ɗin da ya furta innalillahi wa Innah ilaihi raji'un ba salatin da yayi ne yayi sanadiyar buɗe idon Nainarh,ɗagowar da zaiyi yaga motoci har uku sun zagaye motar su “akwai matsala” shine abun da ya furta. Wani irin tsoro ne ya mamaye zuciyar su shi da Nainarh dake zaro ido kamar wacce tayi ƙarya,ɗaya bayan ɗaya wasu samari masu ƙirar majiya ƙarfi su ka shiga fitowa daga motocin suna tunkaro motar su,da sauri driver yasa ma motar Lock, nocking ƙofar su ka shiga yi lokaci ɗaya Nainarh tabi duk ta ruɗe, da sauri takai hannu da nufin buɗe ƙofar motar,driver ne yayi saurin dakatar da ita “karki buɗe madam,akwai haɗari a tattare da mutanen nan” a ruɗe Nainarh tace “idan su ka yo harbi fa,baka ganin gun ɗin dake hannunsu ne?,mu buɗe muji abunda ya kawo su” “karki damu madam ko sunyi harbi babu abunda zai same mu,buɗe masu yafi haɗari” cikin tashin hankali tace “anya kasan mi ka ke faɗa kuwa!??” tana ɗan ɗaga murya “na sani madam motar tanada kariya daga harsashi,bari na sanar da C M abunda ke faruwa” ya faɗa yana ciro wayar daga front pocket ɗin shi ya shiga neman Number C M ɗin,Nainarh tsabar tsoron da take ciki kamar zuciyarta zata fasa ƙirjinta ta fito,shima kanshi driver a tsorace yake daurewa kawai yake Adu'a shi ya samu C M a waya. wata irin razananniyar ƙara Nainarh ta saki lokacin da su ka fara sakar ma motar harsashi,gaba ɗaya ta kifa under seat,shi ma kanshi driver bai san time ɗin daya saki wayar dake hannunshi ba,ƙarar da Nainarh ta saki ta tsoratar da shi. kamar yaƙi haka su ka shiga sakar ma motar bullet,gashi anguwar ba kowa kamar anyi shara,sauƙin su ɗaya da motar ta kasance bulletproof ce. *POLICE STATION HEADQUTER* Gama dai daita parking motocin su suka yi a parking lot ɗin dake headquarter. ɗaya bayan ɗaya su ka shiga fitowa daga cikin motocin,ɗaya daga cikin securitys ɗin ne su ka buɗe back seat ɗin motar dake tsakiyar su,ya Naeem ne ya fito ɗayan side ɗin A C M Usman ne ya fito,main entrance ɗin shiga P H ɗin su ka nufa, da sauri securitys ɗin su ka mara ma su baya amma sai ya Naeem ya dakatar da su hakan yasa su ka dakata,ciki su ka ƙarasa shida usman. mai adaidaita ne yayi parking a bakin gate ɗin P H ɗin,wani dattijo ne ya fito wanda kallo ɗaya zaka mashi ka fahimci wahala ce ta mayar dashi tsoho sosai ba tare da shekarunshi sun kai ba. ta ɗayan ɓangaren wata dattijuwa ce ta fito tareda wata yarinya da bazata gaza shekaru goma zuwa sha 12 ba a duniya wacce kallo ɗaya zaka mata ka fahimci babu isasshiyar lafiya a tattare da ita bayan halin na tsananin rayuwa da su ke ciki daga ita har iyayen nata wanda daga suturar jikinsu zaka tabbatar da haka. gate ɗin shiga headquarter su ka nufa,da sauri securitys ɗin dake wurin su ka dakatar da su,ɗaya daga cikin securitys ɗin ya nufo su “kai tsoho! wai kai wane irin mai taurin kai ne,sau nawa muke faɗa maka ka daina zuwa nan,ka tafi can divisions dake anguwannin ku ka shigar da ƙararka,nan ba wurin kawo ƙananu ƙananun ƙorafi bane irin naka??” dattijon kamar zai fashe da ku ka yace “yallaɓai can ma sunƙi karɓar ƙorafin mu,wata matace tayi mana kwatancen nan tace nan ana karɓar ko wane irin ƙorafi,dan sanku da Manzon rahama ku tausaya ma yarinyar nan tana buƙatar a ɗaukar mata fansar abunda aka yi mata,an zalunceta, ku taimaka ku tsaya mata” ya faɗa yana haɗe hannayenshi wuri ɗaya alamar roƙo, girgiza kai security yayi “matar data turoka saboda ta san baka da hankali shiyasa ta turo ka nan” “wallahi ba haka bane yallaɓai,tace in nemi inspector hussein”wani daga cikin police din ne yace “kai dattijo babu wani ma'aikaci inspector hussein a nan,kaja jikar ka ku bar nan ko muyi maku korar kare” fashewa da kuka matar shi tayi “don Allah yallaɓai ku taimake mu” ja in ja suka shiga yi da police ɗin, sun ƙi bari su shiga su kuma sun ƙi su tafi, sun kafe akan dole sai sunga inspector hussein suna a haka su naeem suka fito, da sauri securitys ɗinshi suka nufi motocinsu,back seat suka buɗe masu,key su ka yima motocin su ka nufi get ɗin headquarter ta cikin mota ya Naeem ya hangi wannan dattijon sai fama security suke da shi akan ya tafi amma ya ƙi, dakatar da drever shi yayi,hakan yasa gaba ɗaya motocin securitys ɗin suka dakata,umarni ya ba drever da ya je yaji me ke faruwa,direban na fita wani daga cikin police din na fisgar hannun wannan dattijon ya hankaɗar da shi gaba daya tsohon ya nufi ƙasa ya fadi,fashewa da kuka matar shi da yar shi suka yi,da sauri driver nufi tsohon,kamashi yayi ya miƙar da shi ,kaf abunda ya faru akan idon ya Naeem, buɗe side ɗin da yake yayi ya fito hakan yasa securitys ɗin shi da ACM usman su ka fito,kama dattijon da dreve ke riƙe dashi ya Naeem yayi yana mashi sannu,masifa usman ya shiga yi mo polis ɗin suna bashi hakuri Hadi da faɗin “yallabai wannan dattijon da kake ganin shi ya cika taurin kai da naci mun ce mashi banan zai shigar da ƙorafi ba,ya tafi division dake anguwannin su amma yaƙikullum sai ya zo nan” “saboda baku san darajar manyanku ba shiyyasa za ku ture shi,idan kullum yana zuwa baza ku iya mashi uzuri ba,ko ba kuga shekarunshi sun ja ba?” “ayi haƙuri yallaɓai in sha Allah hakan bazata sake faruwa ba” tsaki kawai yaja yana nufar ya Naeem da dattijon “kayi haƙuri baba kamar yanda su ka faɗa maka ba nan zaka shigar da ƙorafi ba, division dake cikin yankin ku za kaje ka shigar da ƙorafinka” “yaro can ma naje basu amshi ƙorfina ba sai ma kallon mahaukaci da su ke man,wata jami'a ce tace na zo nan na nemi inspector hussain zai taimaka man” “duk da haka baba kayi haƙuri zanyi maka kwatancen inda ƙanina ke aiki in sha Allah nayi maka alƙawarin zai taimaka maka” sai a time ɗin ya Naeem yayi magana “A'a Usman,baba wane ƙorafi ne ka ke son shigarwa” ya Naeem ya faɗa yana mai da duba shi ga dattijon,da sauri yayi ma matarshi da yarinyar alama da su zo,in da su ke suka ƙaraso, hannu yasa ya yaye hijab ɗin dake jikin yarinyar,da sauri ya Naeem da Usman su ka rintse ido suna ambatar innalillahi wa Innah ilaihi raji'un lokacin da idanunsu su ka sauka akan cikin yarinyar,da alama operation aka yi mata bata samu kulawar likita ba,wurin ya rure yayi jaga jaga ga wasu irin ruwa masu wari da yake fitarwa “yaro kaga halin da yarinyar nan take ciki amma babu mai son ya taimaka mata,an cutar man da jikata” da ƙyar ya naeem ya buɗe idonshi amma ya kasa kallon yarinyar “baba mi yasa ku ka baro asibiti da ita,wannan babbar matsala ce!?” ɗaya daga cikin police ɗin ne yayi carab wurin faɗin “abunda muke faɗa mashi kenan amma ya kasa fahimtar mu” cikin kwantar da murya ya Naeem yace “baba idan kuɗi ne matsalar ku taimako ya kamata ku nema,kuma ga asibitocin gomnati nan” wasu irin hawaye ne su ka wanke fuskar dattijon “yaro da yawan mutane haka su ke faɗa,wa su ma gani su ke mungudu daga asibiti ne saboda kuɗi,amma ba haka bane yaro,daga tura yarinyar nan aikatau ta dawo mana a haka,ban san waye yayi mata hakan ba,shiya nake son shigar da ƙara ko hukuma zata ƙwatar mata ƴancinta,babu lalura ba bu komai su ka farke cikin jikkata,dan Allah yaro ka taimaka mana da abunda zaka iya dan ganin an ƙwatar mata haƙƙinta” dattijon ya faɗa hawaye na bin cheek ɗin shi,matarshi ma ku ka take tana roƙwan ya Naeem da kusan suman tsaye yayi tsabar shock ɗin daya shiga,babu wanda lamarin bai ɗaure ma kai ba,daga zuwa aiki ayima yarinya operation ba tare da sanin wani nata ba. Ajiyar zuciya ya Naeem ya sauke “baba karka damu in sha Allah zanyi iya iyawata dan ganin na taimaka maku,amma yanzu tana buƙatar ganin likita barinta a haka haɗari ne,kunyi sakaci da baku kaita asibiti ba,yanzu abunda za'ayi zan fara kaita asibiti in sha Allah zata samu sauƙi kuma Allah zai toni asirin wanda su ka mata haka” hawayen farin cikin jin za'a taimaki jikarshi ne su ka shiga zaryar a fuskarshi, godiya su ka shiga zuba ma ya Naeem kamar za su yi mayi sujjada “karka damu baba” ya naeem ya faɗa. a ɗaya daga cikin motocin security suka shiga,daga nan direct S I hospital su ka nufa, a parking lot securitys ɗin su ka tsaya ya Naeem da Usman ne su ka shiga ciki tare da su,kai tsaye office ɗin da fawar su ka nufa. a zaune su ka sameshi kan chair ɗin shi yana duba wasu files na patient. cikin girmamawa fawar ya tarebe su,yarinyar ya Naeem ya nuna mashi yace yana su su gano mike damunta sannan ayi mata treatment ɗin cikinta,kulawa ta musamman ya Naeem ya buƙaci da fawar ɗin yaba yarinyar sannan zata zauna a nan tare da iyayenta har lokacin da zata warke “babu damuwa ya Naeem in sha Allah za ta samu kulawar mu fiye da zatonka” “nagode sosai fawar,baba zaku zauna anan tare da ita har Allah ya bata lafiya,zata samu kulawar Dr in sha Allah zata samu sauƙi,duk wani abu da ku ke buƙata ga Dr nan kuyi mashi magana in sha Allah zai sanar dani” godiya su ka shiga yi mashi da Adu'ar gamawa da duniya lafiya “karka damu baba,zuwa anjima zan dawo in sha Allah” ya faɗa yana kallon wayarshi da tun suna cikin mota take ƙara. sallama su ka yima fawar su ka fice su ka bar dattijon da yarinyar. *G J I hospital* *V I P WARD* Kainart a kwance take saman Electrical bed,hospital blue gown ce a jikinta, fuskarta tayi jazur ga idanunta da su ka kumbura,ƙarin jinine aka sa mata,daga yanayin yanda take fitar da numfashi zaka tabbatar da ba ƙaramin jin jiki take ba har wata muguwar rama tayi iya daren jiya kawai,ba'a da ɗe da fito da ita daga Emergency ward ba,mom na daga zaune gaban bed ɗin hannunta riƙe da hannun kainart ɗin da babu komai a jikinshi,da ka kalli fuskarta zaka fahimci ba ƙaramin ku ka tasha ba, laatifa na daga kana sofa fuskar nan tayi jawur idanunta sun kumbura,time to time take sa hankey ta goge hawayen da tun jiya su ka gagara tsaya mata,wani irin mugun tausayin ƴar uwarta take ji,ba komai ta tunawa zuciyarta ke sake karya ba sai irin farin ciki data shiga ciki lokacin da fawar ya tabbatar mata tana da ciki,data tuna sai hawaye sun wanke fuskarta,dady da Abbah na daga tsaye gefen bed ɗin,dady ya goya hannayensa a baya yayinda Abba ke riƙe da sandarshi babu yanda ba suyi da shi ba akan ya zauna amma yace A'a,kowannan su kallo ɗaya zaka mashi ka hango tsantsar damuwar dake shimfiɗe a fuskarshi. Zaabith na daga can bakin ƙofa ya rakuɓe kamar maraya kallon ɗaya zaka mashi shima ka hango tsantsar tashin hankali da ruɗun da yake ciki hatta rigar jallabiyar dake jikinshi a baibai take,har wata yar rama yayi dare ɗaya kawai,da ka kalli idonshi tsantsar nadamace kwance a cikin su,tunda ya shigo ɗakin ya toge a nan,wani mugun shakkar kowa yake da tsoron matakin da za su ɗauka akan shi. ƙofar ward ɗin ce aka turo gaba ɗaya su ka kai dubansu ga ƙofar dan ganin waye zai shigo,wani faɗuwar gaba ne ya riske su a lokacin da su ka sauke idonsu akan waƴanda ke shigowa, zaabith zuciyarshi kusa tsayawa da aiki tayi,kallon juna Abbah da dady su kayi,da kalli fuskar su kasan suna cikin tsantsar tashin hankali,mom tayi tunani su yumnah ne su ka dawo,ba kowa bane face uncle mustafa,yana daga gaba mom Maryam da su Ammar na bayanshi,da gudu Ammar da Aman su ka nufo bakin bed ɗin suna kuka,mom Maryam ma ku ka take kamar ƙaramar yarinya,tashi mom tayi ta nufeta,kamo hannunta tayi tana lallashinta,bakin bed ɗin ya ƙarasa ba tare da ya kalli kowa dake cikin ɗakin ba,bazaka iya gane actuall halin da yake ciki ba fuskarshi ita ba a ɗaure ba ita ba a sake ba. Inda mom ta tashi ya zo ya zauna,hannun kainart ɗin dake kan bed ya kamo cikin nashi ganin haka ne yasa zaabith lallaɓawa ya fice daga ɗakin a tunaninshi babu wanda ya ganshi, direct parking lot ɗin hospital ɗin ya nufa,motar shi dake wurin ya nufa,buɗe driver seat yayi da nufin zai shiga,ɗaga ƙafar da zaiyi yaji an toshe mashi baki ta baya,kokawa ya shiga yi da wanda rufe mashi baki,baiyi aune ba yaji an shaƙa mashi wani abu,baya yayi zai faɗi,da saurin wasu jibga jibgan ƙatti dake sanye da baƙaƙen kaya, fuskokinsu rufe da mask,sama su ka ɗagashi,booth motar dake kusa da tashi su ka buɗe su ka saka shi,babu wanda ya gansu kasancewar parking lot ɗin a ƙasan ginin hospital ɗin yake kuma haka nan ya fito ba tare da securitys ba,a tamanin su ka fice daga hospital ɗin gaba ɗaya. su Aman na daga ɗayan side ɗin,kuka su ke suna kiran sunan mahaifiyar ta su wallahi dole su baka tausayi. Adu'a ya shiga karantowa yana tofama Kainart ɗin gaba ɗaya ɗakin zuba mashi ido su ka yi suna kallon shi har ya kammala yi mata Adu'a, kissing forehead ɗin ta da hannunta dake cikin nashi yayi kafin ya miƙe ya nufi ƙofar fita ya fice,babu wanda bai sha jinin jikinshi da wannan reaction ɗin na uncle mustafa ba,musamman dady da Abbah da ba su san waye ya sanar da shi ba. wurin daya tashi mom Maryam ta nufa ta zauna, hawaye dake idonta ta goge,forehead ɗin kainart ɗin tayi kissing kafin ta ɗaga idonta ta kalli dady da Abbah gaishe da su tayi girmamawa tana tambayar su ya mai jiki da Alhmdllh su ka amsa mata,maida dubanta tayi akan fuskar kainart ɗin,dady ne ya kama hannun Ammar da Aman haɗa su yayi duka yayi hugging,ɗan bubbuga bayan su ya shiga yi yana lallashin su har su ka yi shiru. ɗan gyaran murya Abbah yayi yana sauke ajiyar zuciya,bakin gadon ya matso,kallon seconds 10 yayi ma kainart ɗin kafin yayi mata Adu'a,kallon mom da mom Maryam yayi “ni zan koma gida, Allah ubangiji ya bata lafiya” da Ameen su ka amsa gaba ɗayan su, laatifa dake zaune kan sofa dady ya nufa,su Ammar yace su zauna kusa da ita “kukan ya isa haka laatifa in sha Allah zata samu sauƙi,ki lallashe su suma kinji” “to dady” ta faɗa tana jansu zuwa jinkinta ta rungume su,a hankali take hitting bayan su,dady tare su ka fice da Abbah domin yayi mashi rakiya,a bakin ƙofar ward ɗin su ka samu securitys ɗin Abbah da drivern shi,cike da girmamawa suke tambaya ya mai jiki da Alhmdllh su ka amsa masu. tun daga corridor da zai sada su da reception su ke jiyo hayaniya haɗe da koke koke,suna ƙarasowa reception ɗin uncle mutallab na shigowa ɗauke da Noor,Kamar bata numfashi bakinta sai fitar da kumfa yake,nureses na biye da shi da stretcher sun yi sun yi ya bari su ɗauki Noor ɗin yaƙi,mom Fatilah na bayan su sai ihu take kamar wacce uwarta ko ubanta su ka rasu gaba ɗaya ta cika reception ɗin da kuka,a hanzarce su ka ƙarasa cikin reception ɗin suna ambatar innalillahi wa Innah ilaihi raji'un... Dr's biyu ne su ka nufo Uncle mutallab ɗin,babu wanda ya kalla a cikin su,Direct Emergency ward ya nufa da ita,mara mashi baya su ka yi harda wasu nurses,a bakin ƙofar dady da Abbah su ka tsaya hankalin su a tashe,ga kukan da mom fatilah ke yi duk wanda ya ganta sai yayi tunanin mutuwa aka mata. lallashinta Abbah da dady su ke amma kamar ƙara tunzurata suke,abun nata kamar mai taɓin hankali. a saman Electrical bed ɗin dake ɗakin ya kwantar da ita,da sauri ɗaya daga cikin nurses ɗin ta miƙa mashi surgical gown dake hannunta,Nurses ɗin da Dr's ɗin da su ka biyo shi suma gown ɗin su ka shiga zurawa a jikin su,ba komai yasa su ka kawo ido su ka zuba ma uncle mutallab ba sai he's being their colleague and bugu da ƙari hospital ɗin na su ne. Emergency treatment su ka shiga ba ma Noor,sun shafe kusan two hours suna abu ɗaya da ƙyar su ka samu tafarfaɗo ta hanyar defibrillator,kwata kwata Bata cikin hayyacinta banda kiran sunan Irfan babu abunda take shima sai ka kai bakinka saitin kunnenta sosai tukun zaka iya ji. allurar bacci uncle mutallab yayi mata saboda wannan motsa baki zai iya haifar mata da matsala,ba ƙaramin raunata tayi ba ta shiga halin rayuwa ko mutuwa,yayi mamakin ma yarda har take iya furta sunan irfan. zama yayi gaban bed ɗin da take kwance,zuba mata ido yayi yana kallonta cike da tausayawa,yayi taikici da baƙin cikin halin data shiga saboda ta rasa abunda take so,wani irin tsanar kanshi yake ji na gaza yi mata abunda take so gashi har tana neman ɗaukar rayuwarta,wasu irin hawaye ne su ka taru a idonshi,wata irin wutar tausayinta ce ke ci a zuciyar shi,duk yanda yake daurewa sai da ya zubar mata da ƙwalla,ƙarasowa Dr's ɗin su ka yi inda yake,ganin yanda ya kama hannun Noor ɗin ya riƙe gashi da alama kuka yake yi, hakan yasa likitocin su ka shiga kwantar mashi da hankali in sha Allah zata samu sauƙin,jinjina masu kai kawai yayi,jinin Noor ɗin da su ka ɗiba ɗaya daga cikin nureses ɗin ta ɗauka ta nufi lab ɗin su,tana fita Abbah da dady su ka nufota suna tambayar lafiya haka ma mom fatilah “Abbah ku kwantar da hankalin ku,in sha Allah zata samu sauƙi” ta faɗa tana nufar lab ɗin,ɗaya daga cikin Dr's ɗin ne ya fito,da sauri ya nufi su Abbah “Lelarh mike damunta ne?” dady ya faɗa “she's poisoning her self” har haɗa baki su ke waurin furta innalillahi wa Innah ilaihi raji'un,wani sabon kuka mom fatilah ta sake fashewa da shi “amma yanzu a wane hali take ciki?” “to da sauƙi zamu ce,dan gaskiya she is on life support” “innalillahi wa Innah ilaihi raji'un,amma wane irin poison ne tasha” “abunda muke bincike kenan,poison ɗin ya mata illa gaskiya,ban san ya akayi ba har aka yi sakacen data aikata ma kanta haka ba” ya faɗa yana kallon mom fatilah dake ta aikin tsiyayar da hawaye “zamu iya shiga ciki mu dubata?” “She is in a critical condition gaskiya,ku yi haƙuri zuwa lokacin da zamu kammala binciken,in sha Allah zata samu sauƙi” “to shikenan ba damuwa,ina mutallab ɗin yake?” “yana ciki” ya basu amsa yana kallo mom fatilah da dole ta baka tausayi “please ma'am ki daina wannan kukan, Adu'a ya kamata kiyi mata” jinjina mashi kai tayi ba tare da ta daina hawayen ba gaba ɗaya gani take laifinta ne da ace ta amince da Aurenta da Irfan da duk hakan bata faru ba,wani irin mugun dana sanin abunda ta aikata take,tayi data sanin abunda taje tayi ma mom har gida,gashi yanzu ta dalili wani dalili nata mara tushe zata kashe ƴarta da kanta. dady ma kwata kwata baiji dadi abun ya zo a haka ba,a ganin shi duk laifin mom ne da bata nuna ma Abbah bata son Auren da duk hakan bata faru da Noor ba. “zan shiga lab ɗin naga halin da ake ciki kan binciken” Dr Lelarh ya faɗa “to shikenan dr” Abbah ya faɗa,anan tsaye ya barsu waiting chair dake kusa da su mom fatilah ta nufa ta zauna. “Abbah ya kamata ka tafi gida ka huta tun asuba ka ke nan” dady ya faɗa yana kallon Abbah “Tahir da dai ka bari sun gama binciken sai na tafi” “A'a Abbah gama binciken su ba yanzu ba,ka tafi kawai in sha Allah duk abunda ake ciki zan sanar da kai” “to shikenan”Abbah ya faɗa,sauka su ka yi zuwa parking lot dake ƙasan ginin hospital ɗin,securitys ɗin shi da drivern shi na biye da su a baya,har gaban motar shi ya raka shi,da kanshi ya buɗema Abbah back seat ya shiga,shiga driver yayi securitys ɗin ma su ka shiga motocin su,key su ka yima motocin su ka nufi gate hospital ɗin,har sai da yaga ficewarsu daga hospital ɗin tukun ya juya da nufin komawa ciki idanunshi ne su ka sauka akan motar zaabith, da mamaki yake kallon motar ganin driver seat a buɗe dama zaabith ɗin bai tafi ba kenan ya faɗa a zuciyarshi,nufar motar yayi,abun ya ɗan ɗaure mashi kai ganin motar a buɗe babu kowa a ciki,waige waige ya shiga yi amma bai ga kowa ba kasancewar parking lot a ƙasan ginin hospital ɗin yake ko compound ɗin asibitin ba'a gani,tunani ya fara ko tashin hankalin abunda ya faru ne yasa ya manta da ƙofar a buɗe,maida mashi marfin yayi ya rufe,yana shirin barin parking lot ɗin wata mota ta shigo, kallon motar yayi har su ka yi parking,buɗe door ɗin motar aka yi,mamy ce ta fito daga driver seat yayin da mom halima ta fito ta ɗayan side ɗin,back seat aka buɗe,hajiya zainab ce ta fito ƙanawar mom fatilah,cikin hospital ɗin su ka nufa kwata kwata ma ba su lura da dady dake tsaye ba, tsantsar tashin hankali ne kwance a saman fuskokin su,gaba ɗaya a kiɗime su ke,shima ciki ya nufa. tun kafin su ƙarasa hajiya zainab ta fashe da ku ka ganin ƴar uwar ta ta ,mamy ma da mom Maryam ƙwalla su ke matsewa “garin yaya haka ta faru Aunty fatilah?” hajiya zainab ta faɗa cikin muryar kuka “zainab nima ban sani ba,mai aiki na ke sanar da ni wai taje ɗakin Noor ta sameta a kwance bakinta sai fitar da kumfa yake,lokacin da zan fito har mahaifinta ya fito da ita” “amma waye zai bata guba,gida da ga ke sai mahaifinta?” mom halimatu ta faɗa “sai mai aikin su ba” a cewar mamy “nima ban sani ba,amma ko waye ya cutar dani,bazan taɓa yafe mashi ba” mom fatilah ta faɗa tana goge hawayen dake zuba daga fuskarta. dady ko da ya shigo bai dawo Emergency ward ɗin ba,VIP ward ya nufa in da aka kwantar da kainart,a bakin ƙofa ya tsaya yana ciro wayarshi daga cikin aljihu, Number uncle Mustafa yayi dialing dan gaba ɗaya hankalin shi bai kwanta da yanayin shi na ɗazu ba. har kiran ya katse baiyi picking ba,nannauyar Ajiyar zuciya ya sauke yana maida wayar cikin aljihun shi,tura ƙofar ward ɗin yayi ya shiga,kamar dai yanda ya barsu ɗazu a haka ya same su, Ammar da Aman tuni bacci ya ɗauke su a jikin Laatifa. tunda ya shiga ya sauke idon shi akan mom dake zaune ɗayan side ɗin bed ɗin ta zabga uban tagumi,da wani irin kallon mai wuyar fassarawa ya ke binta,daga yanayin fuskarshi ta fahimci akwai matsala,dan damuwar data hango a fuskar shi ta wuce ta halin da kainart ke ciki, gaba ɗaya tasha jinin jikinta ganin irin kallon da yake jefa mata,kallon two to three minute yayi mata kafin ya sauke ajiyar zuciya,juyawa yayi ya nufi ƙofa ya fita,da mamaki take kallon shi har ya fice,tashi tayi tabi bayan shi a saman waiting chairs dake bakin ward ɗin ta same shi zaune,ƙarasawa tayi gaban shi tana faɗin “yallaɓai Lafiya?” ɗago da kanshi yayi, kallo ɗaya yayi mata ya ɗauke kai,zama tayi kusa da shi “yallaɓai magana nake,me ke damunka ne?” da buɗar bakin shi sai cewa yayi “mi yasa ki ka sauya Zulaihart,da ba haka ki ke ba?” da mamaki mom ke kallonshi “Janar nayi wani abu ne da yasa kace haka?” ɗan nisawa yayi kafin yace ”a da ke ɗin mai haƙuri ce, a da ke ɗin mai tausayi ce,a da ke ɗin mai tsoron cutar da bayin Allah ce, amma lokaci ɗaya kin sauya,baki ɗaya ɗabi'unki sun sauya” tunda dady ya fara magana mom ke bin shi da ido,idanunta sun kaɗa jawur,mijinta abun alfaharinta kullum ya buɗe baki Alkairinta yake faɗa yau an wayi gari da bakin shi yake faɗin ta sauya,tsintar kanta tayi a wani irin yanayi na karyewar zuciya “dan Allah yallaɓai kayi haƙuri ka faɗa man mi na aikata ka ke ganin na sauya,wa na cutar?” murmushin takaici dady ya saki “a dalilin sauyin da ki ka yi kin cutar da yarinyar da ba taji ba ba ta gani ba Zulaihart” faɗuwa gaban mom yayi jin abun da dady yace,tuni hawayen da su ka taru idonta suka shiga zubowa “ka sani a duhu,dan Allah ka faɗa man mi na aikata?” “saboda dalilinki mara tushe Noor tayi poisoning kanta, she's on life support!” wani irin mummunan faɗuwa gabanta yayi, da sauri ta dafe saitin zuciyarta kalmar life support ta shiga maimaitawa “mi ye laifinta dan ta nuna tana son ɗanki,ai duk maso naka masoyinka ne” mom bata san lokacin data fashe da ku ka ba tana ambatar “innalillahi wa Innah ilaihi raji'un,wayyo Allah nah,Allah na tuba ka yafe man, wallahi ban yi haka da nufin cutar da kowa ba sai dan gudun halin da zan shiga Allah shi ne shaidata,dan Allah kayi haƙuri” ƙalla dady bai ce mata ba sai ma kauda kai da yayi ya kalli gefe,yana jin kukanta amma ya zama dole ya nu na mata baiji daɗin abun da tayi ba “magana nake kayi shiru, wallahi ba dan na cutar da ita naƙi amincewa ba,ban san har haka take son Irfan ba” still dady bai ce mata komaiba,hannuwanshi ta kamo “dan Allah ka yi haƙuri ka daina wannan fushin,in dai Aurensu ne na amince ko yanzu ku ke son ku ɗaura masu bana da wata matsala,dan Allah kayi haƙuri” kallonta yayi yana girgiza mata kai “karki damu Zulaihart ni ba fushi nake dake ba,kawai dai banji daɗin abunda ki ka yi ba,a ranar da ki ka nuna baki amince ba kasa jurar rasa ɗanki tayi har hakan ya haddasa tashin ciwanta,da ƙyar da taimakon likitoci ta dawo hayyacinta,na san ganin da gaske ta rasa shi ne ya sa tayi ƙoƙarin kashe kanta” mom bata san ciwan Noor ya tashi ba sai yanzu da dady yake faɗa mata “tunda har ki ka fahimci yarinyar nan tana son ɗanki kuma shima yana sonta da haƙuri ki ka yi ki ka bisu da Adu'a,ko kin manta wahalar da mu ka sha kafin mu samu peace of mind na zama da juna,ke shaidace akan halin da mutum yake shiga idan yaga za'a rabashi da wanda yake so” “kayi haƙuri in sha Allah bazan sake maimaita kuskure irin haka ba,kayi haƙuri” “ba komai ya wuce,Allah ya yafe mana baki ɗaya” “Ameen,yanzu a wane hali Noor ɗin take ciki” “har yanzu likitoci ne akanta” “Allah ya bata lafiya,amma ina son ganin mutallab idan ka amince man,ina so na bashi haƙurin halin dana jefa ƴarsa” “karki damu,yanzu yana tare da Noor ɗin” “shikenan” ta faɗa tana gyaɗa mashi kai. suna a nan zaune sai ga uncle Ahmad tare da mom salima,suna gaba yayinda securitys ɗin su ke take masu baya,banda tsiyayar da hawaye babu abunda mom salima take,tun lokacin da labarin abunda zaabith ɗin ya aikata ya riske su take kuka,shi kanshi uncle Ahmad ya shiga cikin tashin hankali mara misaltuwa. kallon ɗaya zaka masu ka shaida rashin kwanciyar hankalin da su ke ciki,har in da su dady su ke suka ƙaraso, gaisawa uncle Ahmad su ka yi dady tukun su ka gaisa da mom,mom salima kuwa kukan da take ma ya ƙi bari ta gaishe da shi,burinta kawai taga a wane kainart ɗin take ciki. Ward ɗin su ka nufa su ka bar securitys ɗin a waje,dady ne ya tura ƙofar ɗakin ya shiga uncle Ahmad na bayanshi tare da su mom,bakin su ɗauke da sallama su ka shiga,a hanzarce mom salima ta nufi bed ɗin da kainart ɗin take kwance tana fashewa da wani irin kuka ganin halin da kainart ɗin take ciki,lokaci ɗaya ta dawo abunda tausayi. kallo ɗaya mom Maryam tayi masu ta ɗauke kai,har ya mai jiki uncle Ahmad yayi mata amma ko kallon arziƙi bai samu daga gareta ba,babu wanda yaji daɗin abunda ta yi, girgiza kai kawai uncle Ahmad ɗin yayi dama yasan dole hakan zata faru,tashin hankalin shi ma uncle Mustafa,ya san dole ya ɗauki mummunan mataki akan zaabith wanda bazai so hakan ba. gaishe da shi laatifa tayi,da kulawa ya amsa mata yana kallon Ammar da Aman dake bacci a jikinta. kuka sosai mom salima take hannunta riƙe da hannun kainart ɗin. sun ɗan jima a ɗakin,kafin uncle Ahmad ya matsala gaban gadon yayi ma kainart ɗin Adu'a,kallon mom salima dake zaune gefen ƙafafun kainart ɗin yayi “zaki tsaya nan ko?” ɗaga mashi kai tayi alamar Eh,wani kallo mom Maryam ta watsa masu tana kauda kai,ji take kamar ta sauke baƙin cikin da take ciki a kan su dan a ganinta da sa hannun su a abunda zaabith ɗin ya aikata,sallama uncle Ahmad ɗin yayi masu ya fice shi da dady,sai da su ka fita yake tambayar dady ta yarda akai kainart ɗin ta zo gidanshi dan gaba ɗayansu babu wanda ya san da fitar ta. *Lokacin da motar driver da ya ɗaukota daga aso Villa ta iso Estate ɗin,da zummar zuwa gidan su ta baro gidan sai data tuna halin da iyayen nata za su shiga musamman mahaifinta yasa tace su ajiyeta gidan big dady kawai,ko da su ka ajiyeta sai da su ka ga shigarta gidan tukun su ka juya duk da sun so ta bari su kaita asibiti amma taƙi,abunda ya tada hankalin securitys da driver daya ɗauko ta tun a villa take bleeding,motar data shigo ma duk ta ɓata ta, lokacin data shiga gidan babu kowa gidan yayi tsit,a bakin ƙofar ɗakin mom ta tsaya tana nocking cike da ƙarfin hali,a lokacin laatifa ce ta buɗe mata ƙofa,baƙaramin tsorata laatifa tayi ba ganinta a irin wannan lokacin,ko da taga halin da take ciki ga jinin dake bin ƙasanta bata san lokacin data fasa ƙara wacce tayi sanadiyar farkawar mutane da dama na gidan,ko kafin mutanen gidan su ƙaraso parlorn tuni kainart ɗin ta yanke jiki ta faɗi,babu wanda hankalinshi bai tashi ba da ganin halin da kainart ɗin take ciki musamman laatifa,a cikin daren su ka nufi hospital da ita,suna zuwa babu ɓata lokaci likitoci su ka duƙufa akanta,sun shafe sama da awa uku akanta kafin su ka samu nasarar tsayar da jinin dake zuba daga jikinta,tunda aka shiga da ita Emergency ward laatifa ke kuka kamar ranta zai fita,ko da Dr Lelarh ya sanar da su suna buƙatar jinin da za'a ƙara mata saboda ta zubar da jini sosai cewa laatifa tayi a ɗebi nata amma Dr Lelarh yace A'a saboda halin da laatifa ke ciki,dady ne yace su ɗibi nashi in dai zaiyi dai dai dana kainart ɗin duk da Dr Lelarh ya nuna ƙin amincewa da hakan akan za su ƙara mata wanda su ke dashi saboda Emergency patient,ganin dady ya nace ne yasa su ka amince za su ɗiba,cikin ikwana Allah kuwa suna aunawa jinin na su ya zo dai dai,babu ɓata lokaci su ka ɗibi jinin nashi leda ɗaya duk da ba wai zai ishi kainart ɗin ba,dan sosai ta zubar da jini. hankali su dady baiƙara tashi ba sai da Dr Lelarh ya sanar da su Kainart ɗin tayi miscarriage na cikin dake jikinta har sai da su ka yi mata aiki a mahaifa saboda raunatar da mahaifartata tayi wanda su ke ganin ba lallai ta sake haihuwa ba,hankalin su yayi matuƙar tashi da jin abunda Dr Lelarh yace,duk yanda dady ya kai da durewa sai da ya zubar mata da ƙwalla,yayi matuƙar tausaya mata,bai taɓa jin haushin wani abu ba kamar yanda yaji haushin zaabith a lokacin da Dr Lelarh ya sanar da shi zubewar cikin na da alaƙa da mijinta saboda ya kusanceta taƙarfi da tsiya. tun da asuba dady ya kira Abbah ya sanar da shi abunda ke faruwa dan shi ka ɗai ne zai iya tausar uncle mustafa,dan yasan muddin ya sani zaabith ya shiga uku,sai dai tun kafin Abbah ya sanar da shi su Ammar su ka kirashi da wayar kainart ɗin su ka sanar da shi abunda ke faruwa saboda tashin da su ka yi ba su ga Momyn ta su ba da kuma jinin da su ka gani tun daga ɗakinta har zuwa ɗakin dadyn na su, shiyyasa Abbah da dady su ka yi mamakin ta yarda akai ya sani dan Abbah bai kaida sanar dashi ba,ya bari a sai ya koma gida ya kirashi. “ban san mi ya shiga kan zaabith ba da har ya aikata mata haka” “kayi haƙuri yaya lamarin zaabith sai Adu'a,ya ma zo kuwa?” “ya zo” dady ya bashi amsa “mustafa fa,ya san abunda ke faruwa?” uncle Ahmad ya faɗa “tun da har kaga matarshi ai ka san ya sani,dalilin zuwan shi ma ne yasa zaabith ɗin ya fice har yanzu bai dawo ba” dafe kai Uncle Ahmad yayi “ya Allah,dan Allah yaya ka tayani ba Mustapha haƙuri,ina tsoron matakin da zai ɗauka akan zaabith,ka san yanda yake da ƴaƴanshi bai haɗasu da komai ba” “Ahmad mi zance ma Mustapha,kafi kowa sanin baƙar zuciyar shi, zaabith yayi kuskure da har bai yi tunani ba wajen aikata mata haka ba” “haka ne yaya,amma yana jin maganarka fiye da kowa” “duk da haka ban isa na hanashi ɗaukar mataki akan zaabith ba,ya riga da ya aikata kuskuren da ni da kaina zan iya hukuntashi,naji taikaici da baƙin cikin abunda ya aikata,kuma harda laifinka Ahmad babu yarda za'ayi kace baka san abunda ke faruwa a tsakanin su ba,dan wannan abun da yayi mata ya nuna cewa dama can akwai matsala a tsakanin su,kuma gidan gwamnati ka ke zaune in da yafi ko ina ƴan sa ido, motsinka kaɗan ake jira, ko da baka sani ba dole wani daga cikin ma'aikatan gidan ya sanar da kai” “wallahi yaya kaji na rantse ban sani ba,ko yanzu kiran Ja'afar ( VIP ɗin shi mijin Aunty Safeenah ) da Ubaid ne yasa na san abunda ke faruwa,amma wallahi yaya ban sani ba” “har Ja'afar ya sani amma kai baka sani ba?” dady ya faɗa yana kallonshi “shima a labaran safiya ya gani,nayi mamakin da ma'aikatan gidan su ka zaɓi su sanar ma duniya sama dani ubansa,yaja a gari sai zagina mutane su ke,haka shugaban jam'iyya ya nuna ɓacin ranshi matuƙa akan abun,dan Allah yaya ka tayani shawo kan Mustapha nafi jinshi sama da kowa yaya” “kayi haƙuri Ahmad bazan hana Mustapha hukunta Zaabith ba,Noor na nan kwance itama ba lafiya” dady na faɗan haka yayi gaba,iska mai zafi uncle Ahmad ya fesar,ba komai yasa dady yayi mashi haka ba sai dan ya fahimci zaabith yayi kuskure dan yaga kamar yana son ya shigo da son kai a lamarin,kuma yasan dole yasan abunda ke faruwa,shi kanshi bazai so uncle Mustafa ya hukunta Zaabith ba dan yasan bazai taɓa mashi da kyau ba. babu yanda ya iya,dama dady yake ganin zai iya shawo kan uncle Mustafa saboda girmama maganar dadyn da suke,amma tunda har dady yace bazai sa baki ba ya san akwai gagarumar matsala. bin bayan dady yayi har zuwa Emergency ward ɗin da Noor take kwance,lokacin da su ka isa ba su samu su mamy da mom fatilah ba,ba komai yasa ba su gansu ba sai korar da uncle mutallab yayi ma mom fatilah ba tare da ya bari taga halin da Noor ɗin take ciki ba,Dan a ganin shi duk ita tayi causing komai, shiyyasa ya koreta dan baya son ganinta a kusa da su. lokacin da su ka shiga Emergency ward ɗin wanda Dr Lelarh ne yayi masu jagora,kowannan su sanye yake da surgical gown sun rufe fuskokinsu da mask, Uncle mutallab kawai su ka samu tare da Noor ɗin har yanzu bata san wa ke kanta ba, allurar da yayi mata ko minti biyu bata yiba allurar ta saketa,banda kiran sunan Irfan babu abunda take, bakinta kawai ne ke mosti ba sauti,tun ɗazu yake kiran Irfan Amma baya samun shi, Allurar bacci yake mata amma data fara bacci zata farka hakan yasa ba su fitar da ita daga Emergency ward ɗin ba. bakin bed ɗin su ka ƙarasa,hannu su ka ba uncle mutallab ɗin su ka gaisa,kafin su ka matsa kusa da Noor ɗin,tausayin halin da Noor ɗin take ciki ne ya rufe su, Adu'a dady ya shiga karantowa yana tofa mata suna amsawa da Ameen har ya kammala. Kallon uncle mutallab da ya dawo Abun tausayi dady yayi,gaba ɗaya ya koma wani iri kamar bashi ba,tun ranar juma'a da ciwan Noor ɗin ya tashi hankalin shi yake ba'a kwance ba,dafa kafaɗarshi dady yayi “kayi haƙuri mutallab in sha Allah zata samu lafiya” “yaya jikin nata ne kwata kwata babu sauƙi,gubar ba ƙaramin illa tayi mata ba,yaya bana tunanin Noor zata tashi” ya faɗa hawayen dake kwance cikin idonshi na bin cheek ɗin sa,wani tausayin shi ne ya rufe su,girgiza mashi kai dady yayi “ka daina faɗan haka,ciwo ba mutuwa ba ne in sh Allah zata samu sauƙi, Adu'a ya kamata ka yi mata” gyaɗa kai yayi yana sa hannu ya goge hawayen dake zuba daga idanunshi,kallon Noor ɗin dady yayi “me take faɗa ne bakin ta ke motsi?” “tunda ta farfaɗo take kiran sunan Irfan,na kirashi a waya amma ban sameshi ba” girgiza kai dady yayi,wani mugun tausayin Noor na sake shigar sa,ya rasa wane irin so take ma Irfan haka. “amma ka kira Waseef?” dady ya faɗa “ai da ka kira shi na san dole suna tare” ajiyar zuciya uncle Ahmad ya sauke “ban san wane irin so suke ma junan su ba,shi kanshi Irfan kwata kwata babu kwanciyar hankali a tare dashi tun ranar da mahaifiyar shi tace bata amince ba,hatta abinci sai nayi mashi da gaske yake ci,ya Tahir dan Allah ka shawo kan barrister tayi haƙuri ta janye furincinta,tabar yaran nan suyi Aure,duba kaga halin da su ka jefa kan su” dady duk sai yaji wani iri,dama ya san yanzu kowa laifin mom zai gani “karka damu Ahmad ba tun yau ba ta haƙura ta janye ƙudurinta,fatan mu yanzu Allah ya ba Nurjahan ɗin lafiya,in sha Allah data samu sauƙi za'a ɗaura Auren bama sai lokacin da Abbah yace ba” “A'a yaya a ɗaura yau ko gobe tunda ta amince, lokacin da zata samu sauƙi sai ayi bikin kawai,ko ya kace” ya faɗa yana kallon su “duk yanda ku ka ce haka za'ayi” “in sha Allah daga nan gida zan wuce wurin Abbah zan sanar da shi halin da ake ciki,zuwa gobe a masallaci sai a ɗaura Auren lokacin da zata samu sauƙi sai ayi bikin kawai” “hakan yayi,nima yanzu daga nan gidan zan tafi amma bazan shiga wurin Abbah ba,tuna cikin dare dana fito ban koma ba” “shikenan sai mu tafi tare” uncle mutallab dai na jin su bai sa masu baki ba amma deep down ya fisu farin ciki da wannan hukuncin da uncle Ahmad ya yanke,yana fatan Noor idan taji burinta ya cika hakan ya taimaka ma lafiyarta. sake duba jikin Noor ɗin su ka yi tukun su ka yima uncle mutallab ɗin sallama akan dady zai sake dawowa anjima. A tare su ka fice daga ward ɗin zuwa parking lot,a bakin gate su ka samu ƴan jarida jiran fitowar uncle Ahmad ɗin kawai su ke. Motocin su na fitowa su kayi masu rumfa,uncle Ahmad su ka shiga watsa ma tambayoyi duk da kasancewar motar da tinted,umarni yaba driver da su wuce kawai yana mai mamakin munafukin daya sanar da su yana hospital ɗin,duk dan kar asan da zuwanshi ya sa bai fito da motoci da yawa ba. wani irin farin ciki uncle mutallab ya tsinci kanshi,bakinshi ya kai saitin kunnen Noor ya raɗa mata kaf maganganu da su dady su ka tattauna,wasu siraran hawaye ne su ka shiga fitowa daga idonta,hakan ya tabbatar mashi da tayi farin ciki da hukuncin na su. *ESTATE* Yumnah lokacin da su ka bar hospital su ka koma gidan akan za su koma hospital ɗin zuwa anjima,suna shiga gidan da azamarta ta nufi bedroom ɗin su dan ganin a wane hali take ciki,mi ya hanata zuwa hospital ɗin ga ɗokin zuwa prison da za su yi wanda shine maƙasudin dawowarta gidan. A lokacin da ta shiga bedroom ɗin wani irin mummunan faɗuwa gabanta yayi,da mamakin take kallon ɗakin da ya dawo kamar anyi dambe a cikin shi,gaba ɗaya an sauya mashi kamanni,ga pillows nan da blanket da bedsheet a ƙasa hatta matress ɗin su ba dai dai take ba,teddys ɗin su har bakin ƙofar dressing room ɗin su,tunani yumnah ta fara anya lafiya Nainarh tayi ma ɗakin haka,kai tsaye bata kawo ma ranta bata gidan ba,tunani ta fara ko tana toilet,hakan ya sata rage kayan jikinta, a bakin bed ta zauna zaman jiran fitowarta itama dan ta watsa ruwa tana kuma san taji lafiya take tayi ma ɗakin su haka. yumnah tun tana zaman jiran Nainarh harta fara gajiya,tashi tayi ta nufi bakin ƙofar toilet ɗin,nocking tayi tana kiran sunanta,tayi hakan kusan sau biyar amma shiru babu alamar Nainarh na ciki,a hankali ta tura ƙofar toilet ɗin dan ta fara zargin kamar ba kowa a ciki,kamar yarda tayi zargi toilet ɗin ba kowa babu alamun wani ya shige sa a lokacin. ficewa tayi daga toilet ɗin ba tare da tayi wankan ba ta koma cikin bedroom,wayarta ta ɗauka tana nufar dressing room ɗin su,nan taga abunda ya ɗaure mata kai,nan ma anyi mashi kaca kaca har gara ma bedroom ɗin su,kaf kayan su dake cikin clothset ɗin su an watso su hata trolleys ɗin su dake can saman clothset ɗin an zazzage kayan dake ciki anyi jifa da su,takalman su da jakunkunan su gaba ɗaya su ne a tsakar ɗakin anyi jifa da su, dressing mirror ɗin su ma abun ba kyan gani,hata shopping ɗin da su ka yima momyn Nainarh an zazzage su ƙasa, laptop ɗin su ma ga su nan a ƙasa,lafiya Nainarh take kuwa⁉️ ta faɗa,ficewa tayi daga dressing room ɗin ta koma bedroom,hijab ɗin data cire ta ɗauka ta zura a jikinta,ficewa tayi daga bedroom ɗin tana dialing number Nainarh, ringing wayar ta shiga yi,amma har kiran ya katse bata yi picking ba,wani kiran ta sake tana nufar ɗayan bedroom ɗin dake kusa da nasu,nan ma bata nan kuma har lokacin ba tayi picking call ɗin ba, hankalinta ne ya fara tashi,to ina Nainarh ta tafi, bedroom ɗin mom ta nufa duk da ta san zaiyi wuya ace tan can. babu wani ɗaki yumnah da bata shiga ba neman Nainarh amma bata ganta ba,har garden sai da taje ko tana can amma bata can kuma har time ɗin tana kiranta a waya bata picking. part ɗin masu aikin su ta nufa,bedroom ɗin Ishrat tayi nocking,buɗe mata ƙofa Ishrat ɗin tayi sai wani lumshe ido take alamar daga bacci take “ina Nainarh take?” shine tambayar da yumnah ta jefa mata “ba kuna tare ba Aunty yumnah?” wani kallo yumnah ta watsa mata “idan muna tare zan tambaye ki ne,Ina ta tafi?” “tunda tayi breakfast na sanar da ita kuna hospital kin ce ta kiraki ta fice daga gidan nan,nama yi tunanin hospital ɗin ta nufa” “ta fice daga gidan?” yumnah ta faɗa “eh” Ishrat ɗin ta bata amsa “to kenan waye ya shiga ɗakin mu!?” faɗuwa gaban Ishrat yayi jin abunda yumnah tace “wallahi ban sani ba,mi ya faru?” Ishrat ɗin ta faɗa tana kallon yumnah “nainarh bata gidan babu kowa sai ku,waye ya shiga ɗakin mu ya hargitsa mana shi⁉️” “wallahi ban sani ba tunda na gama aiki na dawo ɗaki,ban san waye ya shiga ba,kuma da hannuna na sake gyara ɗakin bayan Aunty Nainarh ta fita” jinjina kai yumnah tayi ta juya,bin bayanta Ishrat ɗin tayi, a parlor su ka dakata “ki kira su muneerat ku gyara shi yanzu” da to Ishrat ɗin ta amsa mata,ita kuma ficewa tayi daga gidan zuwa compound dan ta tambayi securitys ɗin ko sun san inda Nainarh taje. tana isa compound ɗin motocin ya Naeem na shigowa gidan,dakatawa tayi har su ka gama dai daita parking, securitys ɗin shi ne su ka shiga fitowa ɗaya bayan ɗaya,kafin su ka buɗe back seat ɗin motar ya Naeem ɗin. fitowa ya Naeem ɗin yayi, zagayawa yayi da kanshi ya buɗe ɗayan side ɗin motan,hannunshi ya miƙa mata ta kama ta fito,yumnah na daga can tsaye tana kallon su,da gudu ta nufo parking space ɗin ganin Nainarh tare da ya Naeem wacce kallo ɗaya zaka mata ka fahimci bata hayyacinta,jikita sai wani rawa yake kamar wacce sanyi ke kaɗawa. “second father daga ina ku ke haka,Nainarh lafiya ki ke?” yumnah ta faɗa lokacin data ƙaraso in da su ke “bata jin daɗi ne,matsa” shine kawai abunda ya Naeem ɗin yace mata yana jan hannun Nainarh su ka nufi cikin gidan,bin bayansu yumnah tayi. *Abunda ya faru lokacin da wannan mutanen su ka rufe motar su Nainarh.* kamar yaƙi haka su ka shiga sakar ma motar bullet,anguwar ba kowa kamar anyi shara,sauƙin su ɗaya da motar ta kasance bulletproof ce. tsoro da ƙarar harbi ne yasa Nainarh suma,tunda take bata taɓa tsintar kanta a tashin hankali irin wannan ba,ko lokacin da aka kashe dadynta bata tsorata irin na yau ba. zufa ce ta ko ina ta shiga keto ma driver,tsabar karfin hali yana a duƙe yake ci gaba da dialing number CM,still tana ringing amma baiyi picking ba, bai gajiya ba haka ya cigaba da aika mashi kira,shi kan shi bai san iya adadin kiran da yayi mishi ba. gajiya suka yi da harbin motar ganin dai babu alamun glass din zai fashe,gashi so suke su gama abun da ya kawo su ba tare da wani ya gansu ba,ganin dai idan ba wani abun suka yi ba har wani ya zo ya same su a wurin ne yasa majiya karfin da ke cikinsu suka nufi wani katon dutse da ke bakin hanya,kama kama suka yi suka ɗauko dutsen,gadan gadan suka nufi glass din gaban motar za su buga mishi dutsen,sai dai kash Allah maji roƙwan bawansa kafin su aikata hakan karar motar sojoji haɗe da harbi ya cika kunnensu,ba shiri suka yarda dutsen a 360 suka nufi motocin su dake wurin,ko kafin motocin sojojin su ƙaraso sun shige motocin su,key su ka yi ma motocin a 80 suka bar street ɗin,lokacin da su ya Naeem suka karaso sai dai suka hangi motocin su tuni sunyi nisa,mota biyu ta sojojin ta bi bayan motocin su,parking ɗin motocin su suka yi, da sauri ya Naeem ya fito ya nufi motar,back seat ɗin motar ya buɗe, a kasan motar ya ga Nainarh babu alamun numfashi a tare da ita, jijjiga ta ya shiga yana kiran sunanta, wata irin wawiyar ajiyar zuciya driver ya saki jin muryan ya Naeem da sauri ya buɗe driver seat ya fito,jikinshi sharkaf da zufa,hannu biyu ya Naeem yasa ya ciro Nainarh,back seat ɗin motar shi ya nufa da ita,usman ne ya ɗauko mashi ruwa daga cikin mota ya miƙa mashi. A hannu ya zuba ruwan tukun ya shafa mata a fuska,dogon numfashi taja haɗi da zabura zata fita daga motar,da sauri ya riƙota yana kiran sunanta,saurin kallon fuskarshi tayi “lafiya, mi ya faru,mi yasa ki ka fito daga gida??” da ido kawai ta bishi amma ta kasa amsa mashi tambayoyin da yake mata “ba nace duk inda zaki ki dunga sanar dani ba,mi yasa ki ka fita ba tare da kin faɗa man ba?” ƙalla ba tace mashi ba,banda bin shi da ido ba bu abunda take,ƙyaleta yayi ganin har lokacin bata dawo hayyacinta ba, drivern ya tambaya daga ina suke da kuma abunda ya faru,kaf ya kwashe komai ya faɗa masa. jinjina kai kawai ya Naeem ɗin yayi ya shiga back seat ɗin kusa da ita,ganin haka ne yasa kowa shiga motar shi su ka bar wurin,motar da su ka zo driver ya shiga. ta yarda akai ya Naeem ta san suna wurin,bayan kiran da driver yake mashi dama tun ranar daya kira Nainarh gidan shi yasa mata bididdiƙi a wayarta wanda ke sanar da shi location ɗin da take duk wani motsinta yana sane da shi. Direct bedroom ɗin su ya nufa da ita,tura ƙofar yayi,ganin su Ishrat na gyaran ɗakin ne yasa shi juyawa ya nufi wanda ke kusa da nasu,har bakin bed ɗin ɗakin ya nufa da ita “ki kwanta ki huta kin ji” ya faɗa,ba tayi mashi musu ba ta cire takalman dake ƙafarta ta hau gadon,ita kanta zata so tayi baccin ko kunnuwanta za su dai jiyo mata ƙarar tashin hankali da tashiga,ficewa yayi daga ɗakin yana faɗin “ina zuwa” zama yumnah tayi kusa da ita “sister Nainarh wai mike damunki,daga ina ku ke haka?” ƙala Nainarh ba tace mata ba sai ma rufe idonta da tayi, zuba mata ido yumnah tayi ba tare da ta sake cewa komai ba. Ya Naeem ne ya dawo hannunshi riƙe da magani da robar ruwa,bakin bed ɗin ya ƙaraso kiran sunanta yayi, a hankali ta buɗe idonta “tashi ki sha wannan maganin sai ki kwanta” tashi tayi kamar yanda yace,amsar maganin tayi da ruwan,miƙa mashi robar tayi bayan ta sha “to koma ki kwanta,Auta tashi za ki yi ki bata wuri tana buƙatar hutu” to yumnah tace a tare su ka fice daga ɗakin, kasa haƙuri tayi har sai da ta sake tambayarshi mi ya samu Nainarh daga ina su ke,duk tabi ta damu da halin da Nainarh take ciki “ki kwantar hankalinki babu abunda ya sameta,bata jin daɗi ne amma in sha Allah data farka zata dawo dai dai” “Allah ya sa haka” kawai tace ba wai dan ta yarda da bakomai ɗin da yace ba, bedroom ɗin su ta nufa dan ta watsa ruwa. Nainarh da shan maganinta ko two minutes ba ta yi ba bacci yayi awan gaba da ita. Dady lokacin ɗaya shigo gidan ba ƙaramin tashi hankalinshi yayi ba da yayi arba da motar da su Nainarh su ka fita. A main parlor yaci karo da ya Naeem,hankali a tashe yake tambayarshi lafiya dan yaga yaranshi a kusa da motar,bai ɓoye mashi komai ba ya sanar dashi abunda ya faru “innalillahi wa Innah ilaihi raji'un,amma su waye su,miye haɗin su da ita da za su nemi kasheta⁉️” “shi ne abunda ke ɗaure man kai dady,amma in sha Allah asirinsu zai to nu,nasa a bi bayan su” “Allah ya kyauta gaba,yanzu a wane hali Nainarh take ciki?” “lafiya lau take,kawai dai ta tsorata ne sosai,amma na bata maganin bacci in sha Allah data farka zata dawo dai dai” “Allah ya ki ya ye gaba” da Ameen ya Naeem ɗin ya amsa. sallama su ka yi dady ya nufi cikin gidan shi kuma ya fice. Uncle Ahmad lokacin da yake gidan Abbah,rufe shi da faɗa Abbah yayi sosai kan abunda zaabith ɗin ya aikata dan yana ganin sakacin shi ya fi yawa a ciki,ba komai ya ƙara ɓata ran Abbah ba sai yanda mutanen gari ke faɗan munanan kalamai akan uncle Ahmad ɗin musamman abokan hamayyarsa na siyasa,wa su ma wanda su ke da kusanci da Abbah harda kiran shi su ka yi a waya,dake sharrinshi ne babu in da abun bai zagaya ba lungu da saƙo,mutane sun fi saurin yaɗa sharrin mutum sama da Alkairin shi,da ka shiga social media maganar da ake kenan,wasu harda ƙara ma zancen citta wasu ma maganganun da su ke faɗa ba su da alaƙa da al'amarin wa'iyazubullah ya ƴan uwa mu zamanto masu ƴada Alkairi ba sharri ba. faɗa sosai Abbah yake mashi yama ƙi bashi Accesse ɗin da zai ce komai,ban da haƙuri babu abunda ya ke bashi har ya gama mashi faɗa ya koma yi mashi nasiha,sai da Abban ya sauko tukun uncle Ahmad ɗin ya sake baki haƙuri yana sanar da shi Maganar Auren Noor da Irfan. Sosai Abbah ya yi farin ciki da jin mom ta haƙura “gaskiya naji daɗin jin haka,Allah ya sakama Zulaihart da Alkairi,su kuma Allah yasa ma Auren na su albarka,amma mi yasa ku ke son rabashi da na Waseef?,kamar zaifi ayi shi lokaci ɗaya??” “ba komai Abbah,kawai saboda halin da Nurjahan ɗin take ciki ne,kamar ɗaura Auren na su zai taimaka ma lafiyarta tunda fasa Auren shi ne sanadiyyar ciwan nata zuwa bayan sallah sai ayi shagalin bikin tare da na Waseef ɗin” “hakan ma yayi Allah ya bata lafiya in sha Allah zuwa gobe bayan sallar zuhur sai a ɗaura Auren,zan sanar da Shaikh Ibrahim da duk wani wanda ya kamata ya sani,Allah ya ba su zaman lafiya” “Ameen Abbah,ni zan koma gida” “to shikenan ba damuwa” har parking space Abbah ya rakashi,sai da yaga tashin motocin shi tukun ya koma ciki cike da farin cikin Auren Irfan da Noor da za'ayi, murmushi ya saki yana faɗin “Zulaihart Allah ya faranta maki kamar yanda ki ke farantama bayin sa Ameen. Mom fatilah lokacin da su ka koma gida taruwa su ka yi ita da su mamy su ka yima masu aikinta shegen duka kan dole sai sun faɗa masu ubanda yaba Noor guba,Banda ku ka da faɗin ba su san komai babu abunda masu aikin suke,amma hakan baisa sun ƙyale su ba, ƙarshe da su ka gaji su ka kuma fahimci baza su taɓa faɗa masu gaskiya ba,da securitys ɗin gidan mom fatilah ta haɗa su,ai kuwa ba ƙaramar azaba su ka sha a hannunsu ba,ta in da Allah ya taimake su mai gadin gidan ne ya kira uncle mutallab ya sanar da shi abunda ke faruwa hakan ne yasa ya kira securitys ɗin yace su ƙyale su,hakan ba ƙaramin ɓata ran mom fatilah da su mamy yayi ba. Kainart sosai ƴan uwa da abokan arziƙi ke zuwa gaishe da ita duk da har time ɗin bata farka ba, da yawan su sai sun zo gaishe da ita su ke sanin Noor ma bata da lafiya,wasun su sun samu ganinta wasu kuma sai dai su ka tafi akan za su dawo idan an fito da ita daga emergency ward,mama Ameenah ko da ta zo iyakarta wurin Noor amma bata shiga ta duba halin da kainart take ciki ba, hakan kuwa ba ƙaramin ɓata ran Abbah yayi ba da yake a tare su ka zo amma sai tayi kamar bata fahimci ranshi ya ɓaci da abunda tayi ba,tun ba yau ba basa ga maciji ita da uncle mustapha tun yana ƙaramin sa. Nainarh sai bayan sallar isha ta tashi yumnah har ta gaji da zuwa duba ko ta tashi,gaba ɗaya ta damu da halin da take ciki, Alhmdllh ta tashi taji sauƙin abunda ke damunta ta dalilin baccin da ta yi, bedroom ɗin su ta koma, yumnah tasha ruwan mamaki ganin yanda Nainarh gaba ɗaya ta sauya mata,wata irin tsanarta ta hango a cikin idanun Nainarh,roƙon Nainarh ta shiga yi da bata haƙuri dan duk a tunaninta saboda ta tafi ta barta take wannan fushin sai data ga abun ya wuce tunaninta tukun ta fara zargin kanta. Uncle mutallab tun bayan tafiyar su dady ya kira waseef yaji ko su na tare da irfan,amma sai waseef ɗin ke sanar dashi shima rabonshi da irfan ɗin tun safe da su ka zo office,har office ɗin shi yaje amma baya nan kuma ya kira wayarsa bai same shi ba,mamaki ne ya kama uncle mutallab to ina Irfan ɗin ya shiga da har waseef bai sani ba. sanar dashi halin da Noor ɗin take ciki yayi da kiran sunan Irfan ɗin da take “dan Allah waseef idan ka ganshi kace na ce ya zo,ina son ganinshi” sosai hankalin waseef ya tashi jin halin da Noor ɗin take ciki,wani mugun tausayin su ne daga ita har Irfan ɗin ya rufe shi “in sha Allah uncle zan sanar da shi,Allah ya bata lafiya sai mun shigo” “Ameen waseef,sai na ganku” da to waseef ɗin ya amsa yana mashi sallama.  Number Irfan ɗin ya shiga kira still a kashe take,ficewa yayi daga office ɗin shi direct office ɗin Irfan ɗin ya nufa,a rufe ya samu office alamar bai dawo office ɗin ba,parking lot ya nufa motarshi ya shiga direct estate ɗin su ya nufa ci ke da sa ran zai samu Irfan ɗin a can,sai dai ko da yaje bai same shi ba,babu inda bai duba shi ba har gidajen su da za su zauna idan sunyi Aure dake kusa da gidan uncle Ahmad sai da ya duba amma baya nan rabonshi ma da estate ɗin tun ranar friday. duk yanda ya kai wurin neman Irfan sai dai ya haƙura har dare yayi sosai Irfan bai dawo gidan ba kuma har lokacin wayarshi bata ta fiya dan dole tasa ya haƙura,gida ya koma ya shirya ya nufi asibiti wurin Noor da kainart da itama bai samu zuwa ya dubata ba, uncle mutallab bai ji daɗin rashin samun Irfan da Waseef ɗin baiyi ba,ya jima a hospital ɗin kafin ya tafi,heart of Vegas ya koma neman Irfan ɗin duk da yaje ɗazu,still bai zo ba Muhsin kawai ya samu,bai wani jima ba ya nufi gida,gaba ɗaya tashin hankalin in da Irfan ya shiga ya dameshi duk da ya san Irfan bazai ɓata ba dole wani wurin ya tafi. Irfan bai dawo gida ba sai washe gari around 12 PM,Waseef na bedroom ɗin su yayi shirin fita ya shigo,da mamaki Waseef ɗin ke kallon Irfan ɗin da kallo ɗaya zaka masa ka fahimci baya cikin natsuwar shi. Daga yanayin yanda yake tafiya zai tabbatar maka da he's drunk,ko kallon Waseef dake kallonshi baiyi ba yayi jifa da key ɗin motarshi dake hannunshi ya nufi bathroom,girgiza kai kawai Waseef yayi yana zama gefen bed ɗin su,daga bedroom ɗin yana jin yanda Irfan ɗin ke kakarin amai yana fitar da wani irin nishi,kallon ƙofar toilet ɗin yayi cike da tausayin ɗan uwan nashi. ya shafe tsawan 40 minutes bai fito ba,tashi Waseef yayi ya nufi bakin ƙofar toilet ɗin ganin har lokacin bai fito ba ga wani irin nishin wahala da yake fitarwa,ɗan nocking ɗin ƙofar toilet ɗin yayi yana kiran sunan shi “Irfan lafiya ka ke,mi ke damunka ne??” ya faɗa,tsit yaji Irfan ɗin ya daina nishin da yake sai ƙarar ruwa da yaji,barin bakin ƙofar yayi ya koma cikin ɗakin,a bakin bed ɗin ya sake zama,bai jima da zama ba Irfan ɗin ya turo ƙofar ya fito sanye da bathrobe,bed ɗin ya nufo jiki ba ƙwari ya faɗa saman bed ɗin,dafe cikin shi yayi yana ɗan ya mutse fuska,matsowa Waseef yayi kusa da shi “Irfan lafiya ka ke,ina ka kwana ne,jiya kasan irin neman da nayi maka kuwa??” Irfan ɗin na jin shi amma bai ce mashi ƙala ba shi kanshi bazai iya cewa ga halin da yake ciki ba “magana nake Irfan kayi shiru,wannan rayuwar da ku ka ɗaukar ma kanku ba mai ɓullewa bace,ku musulmai ne dukan Musulmin ƙwarai an san shi da yarda da ƙaddara mai kyau ko mara kyau,a rayuwa ba komai muke so mu ke samu ba,tunda har kaga abun ya zo a haka to Allah ne bai ƙaddara akwai Aure a tsakanin ku ba,ya kamata ace kunyi imani da ƙaddarar data same ku kunyi haƙuri,amma wannan halin daka jefa kanka ba mafita ba ne,idan da mutuwace ta ɗauki ɗaya daga cikin ku fa,ya za kuyi,ko wani zai bi ɗan uwanshi ne tsabar so??” Waseef ɗin ya faɗan yana ɗan yi ƙwafa haɗin da kallon fuskar Irfan ɗin,idanunsa a lumshe su ke amma duk abunda Waseef ɗin yake faɗa yana jin shi “dan Allah Irfan ka dawo cikin hankalinka dubi halin daka ka jefa kanka,kullum cikin ɗurama kanka abunda zai zame maka matsala ka ke,gaba ɗaya nema ka ke ka mayar da kanka mahaukaci,kuma hakan ya sauya ƙaddarar da Allah ya ƙaddaro maku ne?” ya faɗan yana kallon Irfan ɗin da har lokacin bai motsa ba,girgiza kai yayi yana cigaba da faɗin “hakan bai sauya komai ba,Noor na kwance gadon asibiti tayi poisoning kanta duk dan saboda an rabaku still hakan bai sauya ƙaddarar ku ba” tunda ya ambaci Noor tayi poisoning kanta Irfan yai zambur ya miƙe yana kallon Waseef ɗin da yayi magana,kallo ɗaya zaka ma fuskarshi ka san abun ya taɓashi “dan Allah ku dawo cikin hankalin ku kusan cewa duk abunda Allah yayi akan bawansa mai kyau ne,kar kuje ku rabu da imanin ku a banza” girgiza kai kawai Irfan ɗin yayi yana nufar ƙofar fita saurin riƙo hannunshi Waseef yayi yana faɗin “ina zaka a haka?” “hospital”shi ne kawai abunda yace mashi yana zame hannunshi dake cikin nashi,sake riƙo hannunshi Waseef ɗin yayi “a haka za kaje wurin ta?” kallonshi Irfan ɗin yayi “dan Allah Waseef ka ƙyale ni” “gaskiya bazan taɓa bari ka fita a haka ba,ko ba kaga halin da ka ke ciki ba ne?” “please Waseef! dan Allah” Irfan ɗin ya faɗa a hankali daurewa kawai yake amma shi ka ɗai ya san ya yake ji,ga kuma halin da Noor take ciki “ka bari ka fara dawowa normal tuku” “please Waseef” “shikenan naji amma ka wuce ka sa kaya tukun” kallon jikin shi yayi can kuma ya juya ya koma cikin ɗakin, clothset ɗin su ya nufa,Waseef na tsaye har ya kammala shiryawa ya fito,key ɗin motarshi daya jefar ya ɗauka ƙofar fita ya nufa bin bayan shi Waseef ɗin yayi. A parking space su ka haɗu da su dady da alama masallaci za su shi da Alhj Ja'afar da PA ɗin sa,har drivern shi ya buɗe masu mota amma ganin su Irfan ɗin ne yasa su ka dakata,ƙarasowa su ka yi cike da girmamawa su ka shiga gaishe da su,da kulawa su ka amsa masu uncle Ahmad na tsaida idonshi akan Irfan “Irfan Ina ka shiga jiya aketa nema ka?” sadda kai ƙasa Irfan ɗin yayi yana faɗin “ina tare da Amjad ne dady” “amma shi ne ka kashe wayarka aketa kira ba'a samun ka?” shiru Irfan ɗin yayi baice komai ba,gyaɗa kai kawai uncle Ahmad yayi “ina za ku haka?” Waseef ne yayi saurin cewa “masallaci daga can zamu wuce hospital wurin Noor ne,bai san bata da lafiya ba” ɗan kallon Irfan ɗin uncle Ahmad yayi tukun yace “ohk mu ma masallacin zamu tafi daga can zamu wuce hospital ɗin,ku shiga mu tafi” da to su ka amsa suna nufar ɗaya daga cikin motocin su dady,su ma motocin su suka shiga. key driver's ɗin su ka yima motocin su ka fice tare da motocin securitys ɗin su wasu na gaba wasu na baya,direct masallacin da su ke sallah su ka nufa. A can su ka samu Abbah da dady da su uncle Hashim harda su ya Naeem,Irfan tunda ya ga ya Naeem da ya Adnan ya wani haɗe fuska kamar bai taɓa dariya ba,ko in da su ke bai je ba bare su samu arziƙin gaisuwa daga gareshi,hakan kuwa ba ƙaramin kunna ya Naeem yayi ba. gaba ɗaya ahalin Abbah su ka haɗu a masallacin wa su daga cikin su sun san da maganar ɗaurin Auren Irfan da Noor ɗin da za'ayi wa su sun su ne ba su sani ba,har shi kanshi Irfan ɗin bai sani ba sai da aka gama sallar su ka ji sanarwa daga bakin Sheikh Ibrahim,bazan iya misalta maku irin farin cikin da Irfan ya tsinci kanshi a wannan lokacin ba,fashe masu kawai yayi da ku ka kamar ƙaramin yaron Uncle Hashim na lallashin shi,babu wanda bai ji tausayin shi a masallacin ba,sunyi mamakin wane irin so ne wannan su ke ma junansu,Waseef shi kanshi sai da ya matse ƙwalla ta taya ɗan uwan na shi murna,ya san yanzu ɗan uwan shi zai dawo cikin natsuwar shi. 500k Uncle Ahmad ya biya sadakin Noor uncle Mustapha ya amsa. ya Naeem tunda aka fara sanar da ɗaurin Auren mamaki ya cika shi,zargi ya fara anya kuwa mom ta sani,ana kammala ɗaurin Auren ya riga kowa ficewa,a parking space ɗin masallaci ya tsaya dialing number mom ya shiya yi Amma har Kiran ya katse ba tayi picking,bai sake kiranta ba,mota su ka shiga shida ya Adnan su ka bar masallacin suma hospital ɗin su ka nufa. fitowa su dady su ka yi harda Irfan da Waseef sai tsokanarshi Abbah yake banda sakin murmushi ba bu abunda yake,motocin su suka nufa,uncle Ahmad back seat na motar da ya zo driver ya buɗe mashi amma sai bai shiga ba yana faɗin ina zuwa,motar uncle Mustafa ya nufa,yana ƙoƙarin shiga motar ya dakatar da shi,dakatawa yayi har ya ƙaraso,tsaye su ka yi uncle Ahmad ya rasa ta wace hanya zai fara ma uncle Mustafa magana,wani irin shakkar sa yake ji,gajiya uncle Mustafa yayi yace “yaya lafiya dai ko?” ɗan ajiyar zuciya uncle Ahmad ɗin ya sauke “lafiya lau Mustafa,dama nace ban samu munyi magana ba,lokacin da naje hospital har ka tafi” jin jina mashi kai kawai uncle Mustafa yayi “ya jikin kainart ɗin” “Alhmdllh” kawai uncle Mustafa ya ce “dan Allah Mustapha kayi haƙuri akan abunda ya faru,ban san akwai matsala a tsakanin su ba da hakan bata faru ba,dan Allah kayi haƙuri zaabith yayi kuskure amma In sha Allah hakan bazai sake faruwa ba,kayi haƙuri ka ji” jin jina mashi kai uncle Mustapha yayi yana faɗin “ohk ba damuwa” ya faɗa yana buɗe car door ɗin shi ya shiga,duk sai yaji badaɗi da irin amsawar da uncle Mustafa yayi mashi,yana a nan tsaye har motarshi ta fice daga masallacin,ya so ya tambaye shi ko Zaabith na tare da shi dan tun jiya rabonshi da shi ga wayar shi da yake kira baya samu,ganin reaction ɗinshi ne yasa kawai yayi shiru,motocin shi ya nufa,suma barin masallacin su ka yi direct hospital su ka nufa. Irfan tunda su ka shigo mota yayi shiru idanun sa na akan side road,kallo ɗaya zaka mashi ka hango tsantsar farin cikin da yake ciki,jin abun yake kamar mafarki wai yau shi da Noor ɗin shi sun zama mata da miji,mafarkin da su ka daɗe suna yi ya zama gaskiya,kallon shi Waseef yayi ya na sakin murmushi “Ango kasha ƙamshi,tunanin mi ka ke?” ya faɗa yana kallonshi, murmushi kawai Irfan ɗin yayi ba tare da ya ce mashi komai ba “yanzu dai ba sauran tashin hankali da ɓacin rai,finally dai burinku ya cika,Irfan angon Nurjahan,gaskiya nayi farin ciki bro,Allah ya baku zaman lafiya,har na ƙosa Noor ta samu sauƙi musha shagali” murmushi Irfan ya saki yana girgiza kai. A jere motocin su suka shiga cikin hospital ɗin,a compound su ka yi parking,ɗaya bayan ɗaya su ka shiga fitowa daga motocin suna nufar cikin hospital ɗin,ɗakin da aka kwantar da kainart su ka fara zuwa Laatifa da yumnah sai fa'iza kawai su ka samu mom da mom Maryam sunje ward ɗin da aka kai Noor,a jiya aka canza mata ɗaki,tunda aka kawota ba su samu damar zuwa ba sai yanzu da aka fito da ita daga Emergency ward,har yanzu Kainart a kwance take,data farka nurses ke sake mata Allurar bacci a bisa umarnin Dr Lelarh. gaban gadon su ka ƙarasa Adu'a su ka shiga yi mata su yumnah na amsa masu da Ameen sun ɗan jima a ɗakin kafin su ka fice zuwa ward ɗin da aka kai Noor ɗin babu nisa daga nan, Irfan gaba ɗaya ya ƙosa ya yi ido biyu da Amaryar tasa dan zaman da su kayi a ɗakin da kainart take daurewa kawai yake dan ji yake kamar ana tsirarshi,ya so ace wurin Noor ɗin su ka fara zuwa. A bakin ward ɗin su ka tsaya,su mom ne su ka fito,tunda su ka fito idonta ke kan Irfan shima kallonta yake rabon da su sa juna a ido tun ranar Friday. Abbah da su dady ne su ka shiga,sai dai su dunga shiga ɗaya bayan ɗaya saboda sun yi yawa. Ƙara sowa su mom su ka yi wurin,cike da girmamawa su ka shaga gaishe da su suna amsa masu da kulawa,zama su ka yi akan waiting chairs ɗin dake wurin banda Irfan da duk a ƙagare ya ke su Abbah su fito. kamo hannunshi mom tayi tana kiran sunanshi ba ƙaramin kewarshi tayi ba,ta san fushi yake da ita amma yanzu ta san komai ya wuce tunda ya samu abunda yake so,faɗawa yayi jikinta yana hugging ɗinta “am sorry mom,kiyi haƙuri idan na ɓata ranki dan Allah ki yafe man nayi kuskure bazan sake ba” ya faɗa a hankali,murmushi mom ta saki tana shafa bayan shi “karka damu Irfan komai ya wuce,fatan Allah ya ba Noor lafiya” tana jin saukar hawayenshi a bayanta wanda ba na komai ba ne sai na farin ciki “Ameen nagode Sosai mom, Allah ya ƙara girma ya kare gabanki da bayan ki,Allah ya haskaka maki mom,Allah ya bamu ikon faranta maki kamar yanda ki ke faranta mana,kin sani farin ciki mara misaltuwa,nagode sosai mom” jikin su ya Naeem ne yayi sanyi da jin irin Adu'ar da Irfan yake mata kai ka san yana cikin farin ciki,ya Naeem duk sai yaji wani iri lokacin da ya tuna ranar da su ka tasa Irfan ɗin a gaba akan sai ya rabu da Noor,bai san cewa har haka yake sonta ba. ɗan bubbuga bayan shi tayi “godiyar ta isa haka Irfan,nauyi ne a kaina na faranta ma ku,ya isa haka kaji Allah ya sanya Albarka a cikin Auren ku ya ba ku zaman lafiya” da Ameen ya amsa,raba jikin su tayi, murmushi tayi tana kallon fuskarshi yayinda take goge mashi hawayen da ke fuskarshi,su mom Maryam sai sakin murmushi su ke,wurin su ya Naeem ya matsa ɗaya bayan ɗaya ya shiga ba su haƙuri musamman ya Naeem, murmushi kawai su ka mashi suna masu Allah yasa Alkairi da fatan zaman lafiya. wurin Kainart su mom su ka koma,su dady sun ɗan jima tukun su ka fito daga ɗakin,tashi su ya Naeem su ka yi su ka shiga Irfan na bayan su,da sallama su ka shiga,a zaune su ka hango uncle mutallab gaban gadon da Noor ɗin take kwance, sallamar da su ka yi uncle mutallab ya amsa masu yana kallon Irfan,har gaban gadon su ka ƙaraso Banda Irfan da ya toge a bakin ƙofa,tunda ya sauke idonshi akan Noor ɗin da idanunta ke a lumshe ya kasa ko da motsi mai ƙarfi,wani mugun tausayinta da kewarta ne haɗe da ƙaunarta ke shigar shi a lokaci guda. ya mai jiki su ya Naeem su ka shiga yi ma uncle mutallab ɗin bayan sun gaisa,da Alhmdllh ya ke amsa masu,ba su wani jimaba su ka fice,kallo Irfan da har lokacin yana bakin ƙofar tsaye uncle mutallab ɗin yayi “Irfan!”ya kira sunanshi,kallonshi Irfan ɗin yayi “ƙaraso mana” uncle mutallab ɗin ya faɗa,sai a lokacin ya ƙaraso gaban gadon,da ladabi yace “ina wuni uncle,ya mai jiki” da Alhmdllh ya amsa mashi “ina ka shiga jiya nake ta kiran ka Irfan?” sadda kai ƙasa Irfan ɗin yayi ba tare da yace mashi komai ba “ka yi shiru?” “bana tare da wayar ne uncle” jin jina mashi kai yayi “ok,matsa ga Noor ɗin can, kwana tayi tana kiran sunanka,nayita nemanka ne saboda halin da take ciki,banji daɗin hukuncin daka yake ba Irfan,a dalilin guje matan da kayi yasa ta shiga wannan halin?” “kayi haƙuri uncle,nayi hakan ne saboda hukuncin da mom ta yanke a lokacin,amma kayi haƙuri ban san hakan zai sa ta aikatama kanta haka ba” “shikenan ai Irfan,komai yanzu ya wuce,zo ka zauna” ya faɗa yana tashi daga saman chair da yake zaune,matsawa Irfan ɗin yayi ya zauna kan chair,kallon Waseef dake tsaye gefen gadon uncle yayi yana faɗin“waseef tunda kun zo bari naje gida na dawo,ban samu na koma ba tunda jiya” “to shikenan uncle ba komai,nima tafiya zanyi Irfan ɗin ma ya isa ya kula da ita kafin ka dawo” “to shikenan,Irfan sai na dawo” da to Irfan ɗin ya amsa,Waseef ma ce mashi yayi sai ya dawo,ficewa su ka yi daga ward ɗin. ba komai yasa uncle mutallab tafiya ba sai dan ya ba su damar kasancewa da juna ko hakan zai taimaka Noor ɗin,Waseef ma dalilin tafiyarshi kenan dan ya san idan suna wurin Irfan ɗin bazai samu sakewar da zai ba Noor ɗin kulawar data kamata ba. tunda ya zauna ya kafeta da ido yana kallon kyakkyawar fuskarta da duk ta faɗa ga wani irin haske da tayi,ya kai tsawan 5 minutes ƙalla baice ba,ɗan ajiyar zuciya ya sauke yana kamo hannunta cikin nashi,a hankali ya kira sunanta yana kai ɗayan hannunshi saman fuskarta,shafa gefen fuskarta ya shiga yi yana sake kiran sunanta,slowly ta shiga buɗe idanunta da su kayi mata nauyi ta sauke akan fuskarshi,tunda aka kawota hospital ɗin wannan ne karon farko data buɗe idanunta duk zuwan da ake gaishe da ita idonta a rufe yake. sake kiran sunanta yayi yana faɗin“ya jikin na ki?” ɗan lumshe ido tayi tukun ta buɗesu tana sake kallon fuskarshi “da sauƙi?” ya sake jefa mata tambaya,hawaye ne su ka taru a idonta,sake shafa fuskarta yayi da hannunshi dake saman fuskar yana girgiza mata kai alamar kar tayi,gyaɗa mashi kai ta shiga yi tana ƙoƙarin tashi zaune,sakin hannunta dake cikin nashi yayi yana miƙewa tsaye,taimaka mata yayi ta tashi zaune,zama yayi gefen bed ɗin yana sake kamo hannuwanta,a hankali ya fara magana“why Noor,mi yasa za ki yi haka,dubi halin da ki ka jefa kanki,kin kuwa san halin da zan shiga idan na rasaki?” zuba mashi ido kawai tayi “ko dana daina kiranki ba wai hakan na nufin na rabu dake ba ne ko na daina sonki,Noor bazan taɓa iya daina sonki ba,kuma ki sani babu wata mace a rayuwar nan da zata maye man gurbinki,bazan iya rayuwa da wata ba bayan ke,mi yasa ba kiyi tunanin halin da zan shiga ba lokacin da zaki sha poison,ke ɗin wani ɓangare ce ta rayuwata Noor,rasaki abu ne wanda ruhina bazai iya ɗauka ba,karki sake maimaita kuskure irin wannan kinji” kallonshi kawai take yayinda hawaye ke sake taruwa a idanunta “please Noor kiyi man magana,ina so naji muryarki” ya faɗa yana kissing hannunta dake cikin nashi. hawayen da su ka taru a idanunta ne su ka shiga zubowa,lallashinta ya shiga yi yana goge mata hawayen “kiyi haƙuri idan maganganuna ne su ka ɓata ranki,ban maki faɗa dan na saki kuka ba kawai banji daɗin abunda ki ka yi ba ne amma yanzu komai ya wuce” lallashinta ya shiga yi har ya samu ta daina kuka,murza hannunta dake cikin nashi ya shiga yi yana faɗin “ban sani ba ko uncle ya sanar dake mom ta janye furincinta akan Auren mu,komai ya wuce Noor daga ƙarshe dai burinmu ya cika,a yau mu ɗin mallakin juna ne,daga yau na tashi daga matsayin saurayinki na dawo mijinki,Noor yanzu ke matatace ba budurwata ba,ban san mi yasa su ka fasa ɗaura Auren mu bayan sallah kamar yanda Abbah yace ba,amma na san hakan bazai wuce yana da nasaba da halin da ki ke ciki ba,Noor su dady yau sun sani farin ciki mara misaltuwa,jina nake kamar an sauke man wani ƙaton dutse daga saman kaina,ina fatan kema kina jin abun da nake ji” zame hannuwanta dake cikin nashi,motsi ta shiga yi da bakinta tana mashi alama da ya zo gareta,a hankali ya matsa sosai kusa da ita,jawota yayi zuwa jikinshi,tightly yayi hugging ɗinta,saukar hawayenta yaji saman shoulder ɗin shi. hitting bayanta ya shiga yi a hankali yana faɗin “please ki daina kukan nan it's paining me” shiru tayi tana sauke ajiyar zuciya,sun ɗan jima a haka kafin a hankali ta kai bakinta saitin kunnen shi,magana ta shiga yi mashi,da ƙyar take furta kalmomi,baza ka iya jin mi take faɗa mashi ba saboda muryarta da tayi ƙasa sosai,shi kanshi sai yayi da gaske yake gane abunda take furtawa,saurin ɗago da kanta yayi daga jikinshi jin furucin da tayi. Cike da tashin hankalin furucin da tayi ya shiga bin fuskarta da ido,kallo ɗaya zaka mashi ka hango tsantsar damuwar da yake ciki “mi yasa zaki faɗi haka Noor, ciwo ba mutuwa bane, Adu'a ya kamata kiyi kinji” girgiza mashi kai tayi hawaye na bin fuskarta,ƙarfin hali tayi wurin furta “ka yafe man ya Irfan,ni kaɗai na san halin da nake ciki” girgiza mata kai ya shiga yi “tunda har baki mutu lokacin da ki ka sha guba ba yanzu ma ba zaki mutu ba,babu abunda zai sameki Noor,in sha Allah zaki samu sauƙi,think about me mana, idan ki ka tafi ya ki ke so nayi da rayuwata,baki tunanin halin da zan shiga?” ya faɗa yana share mata hawayen dake zarya daga fuskarta “Noor we are husband and wife now,think about our unborn babies kin ji,ki daina faɗan mutuwa in sha Allah we will fulfill all our dreams soon,Allah zai baki lafiya,ko kin manta irin rayuwar da muke fatan muyi bayan Auren mu?” hawayen dake zuba daga idanunta ne su ka ƙarfin gudu,girgiza mashi kai ta shiga yi,ita kaɗai ta san halin da take ciki,duk bayanin da zata ma Irfan ba wai zai fahimceta bane. lallashinta ya shiga yi “ki daina kukan nan dan Allah kina karyaman zuciya,ko nima kina son ganin nawa hawayen ne?” girgiza mashi kai tayi “to dan Allah ki dai na kinji,in sha Allah zaki samu sauƙi” hannunshi dake saman fuskarta ta kama ta kai kan surgical cap ɗin dake kanta,cike da kulawa yace “ya aka yi,ciwo kan yake maki ne??” girgiza mashi kai tayi a hankali ta furta “ka cire man” “hulan?” ya faɗa da sigar tambaya,ɗaga mashi kai tayi alamar eh,ohk ya faɗa yana zame mata hular,kitson zane ne guda huɗu akan ta ɗan tufke ƙarshen kitson,ba laifin Noor akwai yalwar suma Masha Allah,kitson ya ɗan zamo saboda santsin da kanta yake da shi,kallon kitson yake da mamaki dan ya kasa fahimtar abunda take nufi da hakan “me kitson yayi,yana maki ƙaiƙayine?” ya faɗa cike da kulawa, girgiza mashi kai tayi tana kai hannunta saman kitson,a hankali ta shiga cusa fingers ɗinta cikin kitson kamar mai shirin zaro wani abu,saurin riƙe hannunta yayi “mi yasa ki ke son warware kitson,yana damunki ne?” a hankali ta furta “wani abu nake so na baka” da mamaki ya furta “wani abu,a cikin kitson??” “eh” ta bashi amsa “ohk bari na ciro da kaina” ya faɗa yana kai hannunshi saman kitson,lumshe ido tayi tana ɗan kwantar da kan saman chest ɗin shi yanda zaiji daɗin ciro abunda take son bashin. a hankali ya shiga ɗaga tsoran kitson yana mai mamakin miye ta ɓoye a cikin kitson,mamaki ne ya kamashi lokacin da ya ciro ɗan madaidaicin flash daga tsakiyar kitson dake kanta “Noor ma ye wannan ɗin?” ya faɗa yayinda yake ɗago da kanta daga saman chest ɗin shi “flash ne yaya” ta bashi amsa “na san Flash ne,amma na minene?” ya faɗa cike da son jin ƙarin bayani daga gareta “zai taimaka maka a duk lokacin da kaji kewata” “ban gane mi ki ke nufi ba,wai Noor mi yasa ki ke faɗan haka,baki son yin rayuwa da ni ne yanzu?” “ba haka bane ya Irfan,a duniyan nan bana jin akwai wata ƴa mace da zata so yin rayuwa da kai kamar yanda na so,kayi haƙuri ba a san raina nake faɗa maka haka ba amma ya zama dole ne,rayuwata ba mai tsayi bace,Allah bai ƙaddara za mu rayu da juna a matsayin ma'aurata ba,kayi haƙuri da rashina a rayuwarka” tunda ta fara magana ya zuba mata ido yana kallo,ya rasa mai zai faɗa mata ta fahimci ƙunar da kalamanta ke ma zuciyarshi,kamo hannunshi da ya riƙe Flash ɗin tayi tana cigaba da faɗin “nasan ba lallai ka iya jurewa ba,amma karka damu wannan Flash ɗin a cike yake da abunda zai baka ƙwarin gwiwa da juriyar rashina, ka man alƙawari bayan ba raina zaka cika man burina,duk wata alfarma dana nema a gareka zaka yi man ita,na maka zaɓi wanda nake ganin Alkairi a rayuwar ka,kayi haƙuri in sha Allah ina da tabbacin zaka so zaɓina” zuba mata ido kawai yayi “ka yafe man duk wani laifi da na maka,sannan ina neman Alfarma no matter what a rayuwar da za kayi ba tare da ni ba karka manta da ni ya Irfan dan Allah” ta faɗa yayinda wa su zafafan hawaye ke yar tseren fitowa daga idanunta,saurin manneta yayi da jikinshi yana jin wani iri a zuciyarshi,he can't imagine life without her,mi yasa sai da burin su ya cika Noor zata kasa jurewa,wace irin ƙaddarace wannan ke yawo da rayuwar su,mi yasa Noor ba tayi tunanin halin da zata jefa rayuwarshi lokacin da zata sha poison ɗin ba. “please Noor ki daina faɗan haka,kina ƙona man zuciya da kalamanki,in sha Allah baza ki mutu ba,za mu rayu da juna kamar yanda mu ka yi fata,zanyi magana da dady na fitar dake outside of the country,in sha Allah zaki samu lafiya kinji” kwantar mata hankali ya shiga yi duk da shima yana buƙatar mai kwantar mashi da hankalin,dan gaba ɗaya ta gama jefashi a cikin wani hali da kalamanta. Uncle mutallab sai around 6 na yamma ya dawo tare da mom fatilah,ba komai ya sa su ka zo tare ba sai kukan data tasashi gaba tana mashi kan ƙin barinta da yayi taga Noor ɗin,kamar yanda uncle mutallab ɗin ya bar Irfan haka ya same shi Noor ɗin har ta koma bacci,tunda ya samu lallasheta ta daina ku ka yake faɗa mata kalamai masu daɗi da sake kwantar mata da hankali,ya kuma yi mata alƙawarin in sha Allah gobe ko zuwa jibi zai fita da ita waje danta sake samu kulawa daga wasu likitocin duk da nan ma ba wai basa da kayan aiki mai inganci ba ne,kawai yana ganin kamar zata fi samu kulawa dai dai da yanda yake so duk da nan ɗin ma suna iya bakin ƙoƙarin su a kanta. ko da ya sanar da uncle mutallab hukuncin da ya yanke na son fita da ita,sosai uncle mutallab yayi farin ciki da jin hukuncin da Irfan ɗin ya yanke,hakan ya sake tabbatar mashi da Noor zata samu kyakkyawar kulawa daga gare shi,ya kuma sake alfahari da kasancewar shi miji ga Noor ɗin “nima nayi wannan tunanin Irfan,Amma ganin nan ɗinma akwai kayan aiki ma su inganci kuma likitocin mu na da ƙwarewa sosai akan aikin su” “haka ne uncle,Amma halin da take ciki za'a duba,kamar canjin zai taimaka mata,amma duk yanda kace ba bu damuwa uncle” ya kai ƙarshen maganar a hankali alamar dai hankalin shi sai yafi kwanciya idan aka fitar da ita ɗin. “bana da ta cewa Irfan,matarka ce kanada ikon fitar da ita ba tare da ma kayi shawara da kowa a cikin mu ba dama shawarace kawai na bada,amma naga kamar kafi son ka fitar da ita ɗin?” ɗan sadda kai ƙasa Irfan ɗin yayi yana sakin murmushi “ba haka bane uncle” murmushi shima uncle ɗin yayi,mom fatilah dai na jin su ƙala ba tace ba. “karka damu,nayi matuƙar farin ciki da ganin irin kulawar da ka ke bata,na sake tabbatar da cewa zaka kula man da Noor yanda ya kamata,shikenan amma kafin komai ka fara sanar da ya Tahir da barrister tukun” “eh uncle zan sanar da su,amma passport ɗin Noor ɗin?” “karka damu,ka bar komai a hannuna yanzu dai ka fara sanar da su kawai” “to shikenan uncle,muna godiya” murmushi kawai uncle mutallab ɗin ya sakar mashi. Bayan sallar magrib Irfan ɗin yayi ma uncle mutallab sallama ya tafi gidan dan ya sanar da dady hukuncin da ya yanke,mom kuma tunda tana nan sai ya dawo dan yana da tabbacin baza tace komai ba haka ma dady,sallama yayi ma uncle ɗin akan zai sake dawowa zuwa anjima dan anan yake so ya kwana. sai da ya tsaya a masallacin Estate ɗin yayi sallar isha tukun ya ƙarasa gidan,ko da yaje bai samu dady ba yana gidan Abbah,direct part ɗin shi dake gidan ya nufa dan yana buƙatar ya watsa ruwa ya canza kayan jikinshi,bayan nan yana buƙatar abun da zai sakama cikin shi, rabonshi da abinci mai ɗan nauyi tun jiya. yana fitowa wanka ko bathrobe ɗin dake jikinshi bai cire ba ya fice daga part ɗin ya nufi part ɗin mom,tsit gidan yake kamar babu kowa a cikin shi,dining room ɗin part ɗin ya nufa riƙe da wayar shi yana kiran layin Waseef rabonshi da shi tunda ya bar hospital,har kiran ya katse Waseef ɗin baiyi picking ba. fasa nufar dining room ɗin yayi,zama yayi saman sofa yana jawo landline da nufin kiran masu aikin gidan,idanunshi ne su ka sauka akan mutum cikin dining room ɗin, mamaki ya fara waye dan ya san su yumnah na hospital wurin Kainart, tashi yayi daga saman sofa ya nufi dining room ɗin,tun kafin ya ƙarasa ya fara jin shashshekar kuka,a hankali ya ƙarasa ciki,da mamaki yake kallonta ta kwantar da kanta saman dining table,ƙasa ƙasa take fitar da sautin kukan,ya kai tsawan 2 minutes a tsaye yana kallonta ba tare da ya ƙarasa gareta ba,mamakin wacece yake da kuma mi akai mata take wannan kukan. A hankali ya kai hannunshi saman kanta da nufin ɗago da ita,a firgice ta ɗago tana haɗiye kukan da take,zazzare ido ta shiga yi saman fuskar shi,shima kallon fuskarta data ɓaci da ruwan hawaye yake yana mai mamakin ganinta a wurin da abunda ya sata kuka,dama bata bi su yumnah hospital ba? sun ɗauki tsawan 40 seconds a haka kafin a hankali ta janye idanunta daga kallon shi,samun kanshi yayi da faɗin “me aka maki ki ke kuka?” ɗan kallonshi tayi kafin ta kauda fuskarta tana ƙoƙarin tashi ta bar wurin saurin kamo hannunta yayi yana faɗin “ba ki ji ina magana, me aka maki ki ke kuka, wani yayi maki wani abu ne??” da kulawa ya jera mata tambayoyin, a hankalin tasa ɗayan hannunta ta zame hannunshi dake riƙe da na ta,barin wurin tayi ba tare da ta bashi amsar tambayoyin da yayi mata ba, da kallon mamaki ya bita har ta shige corridor da ɗakin su yake, dubanshi yake kan wayarta dake haske na alamar kira, yaji haushi wannan share shin da tayi,ko dan taga ya nuna kulawarshi a gareta yasa zata mashi haka,bata san cewa ba wai matsayinta ne yakai har ya nuna kulawarshi a gareta ba kawai yana da wani abu a rayuwarshi, baya son ganin mutum cikin damuwa saboda sanin halin da zuciyar mutum ke shiga a lokacin da mutum ke cikin ƙunci,duk sai ya ji ba daɗi. kallon wayarta da har lokacin mai kiran nata bai daina ba yayi,hannunshi  ya kai ya ɗauki wayar privet Number ya gani alamar mai kiran nata baya da buƙatar a san kowaye shi. ficewa yayi daga dining room ɗin da nufin zuwa ɗakin su dan ya sake tambayarta abunda ke damunta. yana isa parlorn sallamar su yumnah ta daki dodon kunnenshi, da katawa yayi yana amsa masu sallamar,ɗan zaro ido yumnah tayi tana kallonshi fa'iza kuwa murmushi ta saki tana faɗin “angon patient, kai ne a gidan?” murmushi ya saki yana faɗin “fa'iza ni ki ke ma wannan cin mutuncin ko?” ƴar dariya tayi tana faɗin “miye abun cin mutunci angon hospital” dariya kawai irfan ɗin yayi yan girgiza kai,dariya yumnah tayi haɗi da matsowa ta mashi side hug tana faɗin “congratulations ya Irfan, Allah ya baku zaman lafiya” murmushi ya saki yana jan hancinta “thanks you so much Auta” murmushi itama ta saki tana raba jikinsu,miƙa mashi hannu fa'iza tayi suka yi handshake tana faɗin “congratulations bro,Allah ya kawo zuri'a ɗayyiba” murmushi yayi yana shaking hand ɗinta dake cikin nashi “Ameen ya Rabb sistor,kema Allah ya kawo miji na gari” “Ameen,ya mai jikin?” ta faɗa tana zame hannunta daga nashi “taji sauƙi” “Allah ya ƙara afuwa” da Ameen ya amsa,gaba ɗayan su suka juya jin sallamar dady,cikin parlorn ya ƙara so yana faɗin “Irfan yaushe ka shigo gidan?” “ban jima ba,ina wuni” “lafiya lau,ya jikin Noor ɗin” “taji sauƙi dady” “Allah ya ƙara sauƙi” da Ameen su ka amsa su fa'iza na gaishe da shi,amsa masu yayi yana nufar sama,Irfan wayar nainarh dake hannunshi ya miƙa ma yumnah yana faɗin “wayar waye wannan aka bari a parlor?” hannu yumnah tasa ta amshi wayar,ɗan jujjuya wayar tayi tana faɗin “wayan nainarh ce,amma me yasa ta barta a parlor?” ok kawai Irfan ɗin yace yana faɗin “Auta yunwa nake ji,kima Ishrat magana ta kawo man lunch a part ɗin dady” da to yumnah ta amsa,sama ya nufa zuwa part ɗin dady. da landline ɗin dake parlor yumnah ta kira Ishrat ɗin,bayan ta sanar mata da saƙwan Irfan ɗin ne su ka nufi bedroom ɗin su,a zaune su ka samu nainarh saman bed ta zabga uban tagumi,damuwace kwance ƙarara a fuskarta,ga wata irin rama da tayi,abubuwan ne sun haɗe mata da yawa an kashe mahaifinta ga mahaifiyarta a prison ta sa mu yayanta da ya dawo amma babu halin ta faɗa mashi halin da take ciki ko zata samu sassauci abunda ke damunta,dan har yanzu cikin tsoro da firgicin abunda ya faru da ita take,yumnah ce da man mai lallashinta ta faɗa mata kalaman da za su kwantar mata da hankali  yanzu itama ta sauya tashiga sahun masu tara mata damuwa. har idan take su ka ƙaraso dafa kafaɗarta yumnah tayi tana faɗin “wai ni kam nainarh me ke damunki ne kwana biyu,duk kin bi kin ɗauki damuwa kin sa a ranki,nayi tambayar duniyar nan amma kinƙi faɗa man sai fushi da ki ke da ni wanda na rasa dalili” tunda ta dafata ta ɗago tana kallonta,lamarin yumnah mamaki yake bata sai ta dinga yi kamar bata san abunda tayi mata ba “dan Allah nainarh koma me ke damunki  kiyi haƙuri ki daina sa ma ranki damuwa Allah yana tare da ke” wani kallo ta watsama yumnah tana kaɓar da hannunta dake saman kafaɗarta, girgiza kai kawai yumnah tayi kwana biyun nan kullum a haka su ke,ko magana nainarh bata yi mata,kusan zata iya cewa gaba nainarh ke yi da ita,ɗan ajiyar zuciya yumnah ta sauke “Allah ne shaidata nainarh ban san me na maki ki ke wannan fushin dani ba,amma kiyi haƙuri a bisa laifin da na aikata maki ba tare da na sani ba” kauda kai Nainarh tayi tana ɗan jan tsaki,fa'iza tunda ta shigo tana tsaye tana kallonsu ƙala ba tace ma su ba amma ba taji daɗin halin da su ke ciki ba musamman Nainarh “ga wayarki nan a parlor ki ka barta” yumnah ta faɗan tana ajiye mata wayar haɗi da ficewa daga ɗakin dan zata iya fashewa da kuka a gaban su,ba ƙaramin kunnata Nainarh take da wannan halin da take mata ba. ƙarasawa fa'iza tayi gaban gadon,zama tayi kusa da Nainarh “ban san miye ya shiga tsakanin ki da yumnah ba,amma ina sake baki haƙuri a madadinta,kiyi haƙuri Nainarh na san kuskuren fahimta ne ku ka samu amma yumnah bata da matsala” tunda fa'iza ta fara magana ta kafeta da ido tana kallonta,da ace zata iya faɗa mata abunda yumnah tayi mata da bata zauna tana bata haƙuri ba,sai dai duk yanda take jin tsanarta bazata iya tona mata asiri ba ko ba komai ta taimaketa a lokacin da take buƙatar taimako.  “ki yi haƙuri kin ji” jin jina mata kai tayi tana faɗin “nagode sosai” “karki damu” fa'iza ta faɗa. Irfan ya ɗan jima a part ɗin dady dan har kusan 10 pass 30 yana can duk akan maganar fitar da Noor ɗin waje da yake son yi,ko da ya sanar da dadyn baice komai ba sai ma Adu'ar Allah ya ba Noor ɗin lafiya da yayi,sosai irfan ɗin yayi farin ciki ya kuma godema Allah da ya bashi su a matsayin iyaye,nasiha dady  yayi mashi mai ratsa zuciya ya kuma ce ya kamata ya sanar da uncle Ahmad, da to Irfan ɗin ya amsa dama yana da nufin hakan,a tare da dady su ka yi lunch kafin yayi mashi sallama ya koma part ɗin shi dan ya shirya ya koma hospital ɗin. Shaf shaf ya shirya,key ɗin motar shi ya ɗauka  ya fice daga ɗakin,motar shi dake compound ɗin gidan ya nufa ya shiga, ba ɓata lokaci yayi ma motar key ya fice daga estate ɗin gaba ɗaya. Uncle mutallab sai Around 10 ya bar hospital ɗin tare da mom fatilah bayan ya sake duba jikin Noor ɗin,ya kuma umarci nureses ɗin da su kula da ita kafin Irfan ɗin ya dawo. *NOOR*😢 wani irin mummunan zafi jikinta ya ɗauka bacci take amma azabar data gauraye jikinta ce ta farkar da ita,numfashinta ne ya fara fita sama sama,hannunta take son ɗagawa dan taji ko akwai wani a kusa da ita ya taimaka mata da ruwa amma ta kasa,maƙoshinta ya bushe kamar tayi sati rabonta da ruwa,wasu zafafan hawaye ne su ka shiga fitowa daga idanunta lokacin data fahimci babu wata gaɓa a jikinta dake motsi bayan idanunta,bugun zuciyarta ne ya tsananta wanda ita kanta bata san dalili ba,zufa ce ta shiga keto mata ga wani irin zafi dake fitowa daga ko wace ƙofa ta jikinta,hawayen dake zuba daga idanunta ne su ka ƙara yawa dan ta fahimci wani al'amarin ne ke shirin faruwa  da ita gashi babu kowa a ɗakin,tayi fatan Irfan na kusa da ita wannan al'amarin ke faruwa da ita. Jin motsi a cikin ɗakin ne yasa ta shiga raba idanunta dan ta san bazai wuce Irfan ba ne sai dai lokacin da idanunta su ka sauka akan wanda ke yawo tsakar ɗakin ta fahimci ba shi ba ne. sanye yake da baƙaƙen kaya ya rufe ko ina jikinshi,da alama ta wata ƙofa ya shigo ba ainihin wacce ake shigowa ɗakin ba dan ba taji alamar buɗe ƙofa ba,da ido kawai ta shiga binshi,magana take son yi amma bata iyawa. bakin gadon da take kwance ya ƙarasa, zama yayi kan chair dake gaban gadon,idanunta ne ta sauke akan evil mask ɗin dake fuskarshi,a hankali ya zere mask ɗin daga fuskarshi,zaro ido Noor ɗin tayi ganin ko waye,kamar an kunna tap haka hawaye su ka shiga gudu akan fuskarta. a hankali ya kai hannunshi saman fuskarta yana goge mata hawayen,da raunanniyar murya ya fara magana“Noor ba komai yaja maki ba face taurin kai,ban san mi yasa ki ka zaɓi jefa kanki a cikin matsalar da bata shafeki ba,kinyi kuskure babba na  biye ma zuciyarki,ba wai dan bana sonki ba ne zan kashe ki,ina sonki kamar rayuwata amma ki ka zaɓi mutuwa sama da ni, zanyi takaici da baƙin ciki na rasaki da zanyi a rayuwata amma babu yanda na iya kasheki shi ne mafita a gare ni” ya ƙarashe maganar yana goge hawayen dake gefen idonshi,kuka kawai Noor take bata taɓa data sanin saka kanta a abunda bai shafeta ba sai a wannan gaɓar,tayi takaicin biyema zuciyarta ko dan saboda Irfan,ta san ko kafin ya jure rashinta a tare da shi za'a ɗauki lokaci,amma data tuna bayin Allahn da ba suji ba ba su gani ba ne ta taimaka sai taji sauƙi ta kuma sake yarda da haka Allah ya ƙaddaro rayuwarta ba mai tsayi ba ce, ko tasa kanta a masifar ko kar tasa kanta dama iyakar kwanakinta kenan. hannunshi ya zura cikin trousers pocket ɗin shi ya curo wata ƴar madaidaiciyar allura,binshi da ido kawai take har lokacin hawayen dake idonta ba su daina zuba ba “kamar yanda na maki alƙawari na zan barki ki mutu da Auren Irfan akan ki a yau wannan alƙawari ya cika ina fatan kinyi farin ciki?,zan sake yi maki wannan allurar ne saboda bazan iya jurar ganin halin da zaki shiga ba  a lokacin da ruhinki zai bar gangar jikin ki,kiyi haƙuri Noor haka ƙaddara ta zaɓar mana amma ki sani duk wani bugu da zuciyata za tayi da sonki take yin shi bazan taɓa yafe ma kaina alhakin kasheki da nayi ba,na san zan kasance cikin ƙunci har lokacin da ƙasa zata rufe idanuwana,ina maki fatan samun dacewa” ya faɗa yana kamo hannunta dake sanye da cannula bayan da ya kammala haɗa allurar,tana ji tana gani yayi mata allura wacce take zargin ta guba ce kuma da dukan alamu tana bacci yayi mata wata dan ta fara zargin itace ta kashe duk wata gaɓa ta jikinta. ko 5 seconds ba'ayi ba allurar ta fara aiki a jikinta,gaba ɗaya jijiyoyin jikinta su ka fito waje  idanunta su ka kakkafe  bakinta na fitar da kumfa,miƙewa yayi tsaye,kissing forehead ɗinta yayi a hankali ya furta “am sorry Noor,zanyi kewar ki” yana gama faɗa ya ɗauki mask ɗin shi ya fice ta ƙofar da ya shigo. bayan ten minutes da fitarshi dr lelarh tare da nurses guda biyu su ka faɗo ɗakin a kiɗime kamar sun san abunda ya faru,hankali a tashe dr lelarh ya shiga bata taimakon gaggawa sai dai ina ƙaddara ta riga fata tuni ruhinta ya bar gangar jikinta. Inna lillahi wa Inna Ilaihi Raji'un,waye ya aikata ma Noor haka,wace masiface ta sa kanta a ciki ya Allah.  Irfan kai da su uncle mutallab Allah ya baku haƙurin rashinta😭😭😢😢 Gaba ɗaya ba bu wanda jikinshi baiyi sanyi ba a ɗakin,nurses ɗin dake ciki har sai da su ka matse ƙwalla ta tausayin Noor ɗin,dr lelarh ma daurewa kawai yake amma mutuwar ba ƙaramin taɓashi tayi ba musamman da ya tuna irin son da Irfan da uncle mutallab su ke ma Noor ɗin,ya tausaya masu matuƙa. ɗaya daga cikin nurses ɗin ce ta rufe ma Noor idanunta dake kallon ceiling,a hankali taja mayafin dake jikin Noor ɗin ta rufe mata fuska. jiki a sanyaye dr lelarh ya fice. Yana ficewa daga ɗakin Number dady yayi dialing dan bazai iya sanar da uncle mutallab labarin mutuwar Noor ba. Dady ya shiga tashin hankali matuƙa lokacin da Dr Lelarh ya sanar da shi mutuwar Noor ɗin “yallaɓai ba sai kun zo ba saboda dare mu da kan mu zamu kawo gawar gidan Abbah in sha Allah” Dr Lelarh ya faɗa,dady bai iya ce mashi komai ba kawai yayi rejecting call ɗin,ba ƙaramin taɓashi mutuwar tayi ba babban ma tashi hankalin shi halin da Irfan zai shiga,rabasu kawai aka yi ya shiga wani hali inaga yanzu yaji cewa ta bar duniyar baki ɗaya. Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un dady ya faɗa yana dafe kansa. ya jima yana saƙawa da kwancewa kafin ya iya daurewa ya kira su uncle Ahmad ya sanar da su halin da ake ciki,sai daga ƙarshe ya kira Abbah. babu wanda baiji mutuwar Noor ba a cikin su. Uncle mustapha yana gama waya da dady ya nufi ward ɗin da aka kwantar da Noor ɗin da yake yana cikin hospital ɗin. Dr Lelarh yana nan tsaye a bakin ƙofar ward ɗin nurses maza guda biyu suka nufo ward ɗin da stretcher, ba kowa ne ya sanar da su ba sai shi,ƙofar ward ɗin kawai ya nuna masu. ciki su ka shiga,a tsaye su ka samu nurses ɗin nan mata kamar yan da dr lelarh ya barsu. a saman bed ɗin su ka ɗaura Noor kafin su ka fice da gawarta daga ɗakin. gyara ɗakin nurses ɗin su ka shiga yi su ka haɗa duk wani kaya da su ka danganci Noor ɗin. suna fitowa da gawar uncle mustapha na ƙarasowa,jikinshi ne ya sake yin sanyi lokacin da yaga gawar Noor ɗin. tura stretcher ɗin nurses ɗin su ka yi su ka nufi hanyar ficewa daga hospital ɗin,mara masu baya uncle mustapha da Dr Lelarh su ka yi. Suna isowa reception Irfan na shigowa a hanzarce  hannunsa riƙe da ledar eatery da alama ya tsaya yi ma Noor takeaway ne duk da ya san balallai ta iya cin komai ba. tsabar saurin da yake ne yasa bai lura da nurses ɗin dake tura stretcher ba,nufar uncle mustapha da dr Lelarh,hannu ya miƙa ma su suka gaisa,uncle mustapha ne yace “daga ina kake haka?” ledar dake hannunshi ya nuna ma uncle mustapha “daga gida nake,na tsaya yima Noor takeaway ne,amma lafiya uncle,ina za ku?” ya faɗa yana bin fuskokin su da ido dan kallo ɗaya zaka masu ka hango tashin hankali da su ke ciki “bakomai gida za mu,kaima juyawa za kayi mu tafi” da mamaki ya kalli uncle mustapha “amma uncle babu kowa a tare da Noor ɗin,ni nace uncle ya tafi zan kwana tare da ita” “karka damu Irfan Noor bata buƙatar kowa a tare da ita,mu tafi gidan kawai,akwai dalilin da yasa nace muje” tsintar kanshi yayi a wani irin yanayi jin abunda uncle mustapha ya faɗa,tuni tsoro da fargaba sun mamaye zuciyar shi. wani irin tausayin shi ne ya rufe dr Lelarh hakama uncle mustapha,daurewa kawai yake yana wannan maganar. “to uncle amma dan Allah ka bari na ganta tukun sai mu tafi,kuma ga abinci da na zo mata da shi” “karka damu ba jimawa za kayi ba,bari a ba nurses sai su bata kafin ka dawo” gyaɗa kai kawai irfan ɗin yayi amma ba dan yaji daɗi hanshi ganinta da uncle mustapha yayi ba. amsar ledar takeaway uncle yayi ya miƙama nurses ɗin dake reception ɗin kafin ya kama hannun Irfan ɗin su ka fice,lokacin da zasu iso compound tuni an saka gawar Noor ɗin a Ambulance,motar uncle mustapha su ka nufa,passenger seat dr Lelarh ya buɗe ya shiga Irfan ya shiga back seat yayinda uncle mustapha ya zauna a driver seat. reverse yayi ya nufi gate ɗin hospital ɗin motar securitys ɗinshi na gaba yayinda Ambulance ke bayan su tare da wata motar securitys ɗin. Irfan tunda ya shiga motar ya sadda kai ƙasa ya rasa gane taƙamaimai halin da ya ke ciki,abunda kawai ya sani shine ya san wani babban Al'amari ne yake faruwa koma ya faru wanda yake zargin ya shafeshi dan har lokacin hankalinshi bai kaiga ambulance ɗin dake bayan su ba. a bakin main entrance ɗin shiga part ɗin Abbah su ka samu su uncle Ahmad harda uncle mutallab wanda har gida su ka je su ka ɗauko shi sai dai ba su sanar da shi abunda ya faru ba,a tsaitsaye su ke ko wanne ka kalla tashin hankali ne a fuskar shi. parking motocin su suka yi a compound,ɗaya bayan ɗaya su ka shiga fitowa. A hanzarce su uncle Ahmad ɗin su ka nufi Ambulance ɗin. fito da gawar nurses ɗin su ka shiga yi. wani irin bugawa zuciyar uncle mutallab tayi lokacin idanunshi su ka sauka akan gawar Noor ɗin,gaba ɗaya ya nufi baya zai faɗi da sauri uncle Ahmad da Uncle Ubaid su ka taroshi,da wani irin yanayi yake bin fuskokin su da ido kafin ya sake kallon gawar Noor ɗin kawai ya fashe da kuka kamar ƙaramin yaro gaba ɗaya jikinsu ya sake yin sanyi. Irfan ko da ya fahimci abunda ke faruwa yanke jiki yayi ya faɗi sai dai su ka ji faɗuwarshi,da gudu dady da uncle mustapha su ka yi kanshi,jijjigashi dady ya shiga yi yana kiran sunanshi amma ina. Uncle hashim ne ya ba su ruwa dan a yayyafa mashi amma har ruwan container ya ƙare babu alamun zai farfaɗo. tashin hankali da ba'a sa mashi date tuni hawaye sun shiga zarya a fuskar dady,Abbah ne yace su shiga da gawar,uncle mutallab ma ciki su uncle Ahmad su ka shiga da shi,ɗaukar Irfan uncle mustapha yayi suma su ka shiga ciki duk da dr Lelarh ya so su bari kawai su ko ma hospital da Irfan ɗin dan akwai haɗari a tattare da halin da yake ciki.  parlor Abbah  su ka nufa,anan tsakiyar parlor su ka ajiye gawar,uncle mutallab sai sambatu yake kamar wanda ya samu taɓin ƙwaƙwalwa. sofa uncle mustapha ya nufa da Irfan ɗin ya kwantar dashi. Dr Lelarh ya shiga bashi taimakon gaggawa dan ganin ya farfaɗo,ba ƙaramar wahala ya sha ba kafin ya samu Irfan ɗin ya farfaɗo dan har sun fara cire rai da zai farfaɗo ba tare da sun danganta da hospital ba. kusan a tare su ka shiga sauke ajiyar zuciya da godiya ga Allah dan sun tsorata sosai da irin suman da ya yi,sai dai tunda ya buɗe ido akan gawar Noor ɗin bai sake wani motsi ba baya cewa uhm bare uhm uhm. sallama dr Lelarh yayi masu shi da nurses ɗin akan za su dawo gobe da safe saboda dare yayi dole sai dai a bari gobe akai Noor ɗin. a nan parlorn su ka yi jugum jugum baka jin motsi komai sai sambatu uncle mutallab da ya cika parlorn sunyi lallashin amma ina,kamar suna daɗa tunzurashi ne,sosai ya haukace masu,Adu'a Abbah ya shiga karantowa yana tofa mashi a kai haka Irfan ma Adu'a dady yake mashi dan gaba ɗaya hankalinshi a tashe yake da yanayinshi. ba su sanar da matan halin da ake ciki ba dan ko Innah dake gidan bata san abunda ke faruwa ba sai a washe gari su ke samun labarin mutuwar Noor ɗin. Ni kaina bazan iya misalta maku irin tashin hankalin da su ka tsinci kansu a ciki ba. mom fatilah Lokacin da labarin mutuwar Noor ɗin ya risketa suma tayi wanda daga nan bata sake sanin inda kanta yake ba,da an samu tafarfaɗo zata sake wani suman,dole tasa aka nufi hospital da ita ba tare ma da ta samu ganin Noor ɗin ba. Babu wanda mutuwar Noor ɗin bata girgiza ba a family, Nainarh harda kukanta musamman data tuna ba taje ta gaishe da Noor ɗin ba lokacin da aka kwantar da ita,taji takaici da haushin kanta na ƙin zuwa,Waseef ma yaci kuka na alhinin mutuwar da tausayin halin da ɗan uwanshi yake ciki. Driver Abbah yasa ya ɗauko mom da mom Maryam daga hospital domin yima Noor ɗin wanka. A nan part ɗin Abbah su ka haɗu matan su mamy ne kawai babu suma suna tare da mom fatilah a asibiti,babu ɓata lokaci su ka shiryata cikin likafaninta,anan compound ɗin gidan aka mata sallah,ba laifi mutane da yawa sun halarci sallar jana'izar,gaba ɗaya mazan su ka kwashe zuwa maƙabarta,ko kafin su dawo tuni gidan ya cika da mutane, kan kace me ƴan uwa na nesa da kusa sun zo kamar part ɗin zai tsage ko ina ka ɓulla mutanene. Irfan tunda su ka dawo ya shige ɗakin Abbah,wunin ranar ko ruwa bai gitta ta maƙoshinshi ba gashi har lokacin babu wanda yaji wata kalma ta fito daga bakin shi a washe gari dady yasa Dr Fawar ya dubashi amma babu wani cigaba yana nan ba uhm bare uhm uhm kuma anyi anyi ko da ruwan tea ne yasha amma yaƙi,dole tasa dady kawo ido ya zuba mashi sai dai ya dunga mashi Adu'a dama ya san abun is not easy to him. Matan da dare yayi su ke tafiya gida mazan ne kawai ke kwana nan har akayi Adu'ar kwana uku,aranar Kainart ta farka daga nan Dr Lelarh ya ce a dakata da yi mata allura. Mom maimunatu tunda aka yi rasuwar kullum ne sai ta zo,sai a sannan Abbah ya san bata gidan uncle hashim,saboda taron mutane yasa Abbah baima uncle hashim ɗin magana ba. A daren ranar su dady kowa ya koma gidanshi uncle mutallab kawai su ka bari a part ɗin Abbah,shima Abban ne yace ya bari sai anyi sati tukun ya koma gida tunda ba kowa ga halin da yake ciki,da za su tafi ne bayan su dady sun fita daga part ɗin uncle Ahmad ya kasa haƙuri har sai da ya tambayi uncle Mustafa zaabith da tun ranar da aka kwantar da kainart bai sake ganinshi ba ya kira wayarshi baya samu yayi binciken amma bai gano komai ba da ya shafi inda yake shiyyasa yake zargin uncle Mustafa na da sa hannu a ɓatan shi kuma yaƙi yace komai,shirun ma da yayi game da abunda ya faru da kainart ɗin ne yasa shi ƙara tabbatar da zargin zaabith ɗin na tare da shi,saboda halin da su ke ciki ne yasa bai sanar da kowa ba,amma ganin idan yayi shiru abun zaizama babba ne yasa yayi ma uncle Mustafan magana,amma da yayi mashi magana ko kulashi baiyi ba saima yima Abbah sallama da yayi ya fice daga gidan. ran uncle Ahmad ba ƙaramin ɓaci yayi ba,haƙuri Abbah ya bashi akan shi da kanshi zaiyi magana da uncle Mustafa in dai zaabith ɗin na tare da shi zai sa ya sake shi,sallama yayi ma Abbah ya koma gida. dady tunda su ka koma gida kulawa ta musamman su ke ba Irfan shi da mom uncle Ahmad ya so Irfan ɗin ya koma gida amma dady yace ya bari sai zuwa wani lokaci shima a yanzu yana buƙatarshi a kusa da shi,sanin halin da Irfan ɗin yake ciki ne yasa kawai yace to dan ya san yana buƙatar kulawa ta musamman,shi baya da lokacin da zai bashi kulawar data dace. Mom tun ranar da aka yi rasuwar ta sanar da uncle Jonas,su ma sunyi alhinin mutuwar Noor ɗin musamman data kasance mata ga Irfan dan tun ranar da aka yi Auren su ta kira uncle Jonas ɗin ta sanar da shi. tun a ranar ya kira dady yayi mashi gaisuwa ya kuma buƙaci da ya ba Abbah da su uncle Ahmad,ɗaya bayan ɗaya yayi masu ta'aziyya ya kuma sanar da su suna nan zuwa nan da sati biyu dan suyi masu ta'aziyya,Alyar da James ma tun a ranar su ka kira su ka yi masu ta'aziyya su ka kuma sake tabbatar masu da suna nan zuwa nan da two week,Sam ne kawai babu wanda ya kira,har kiran shi ya Naeem yayi ya rufe shi da faɗa akan idan yana fushi da dady ai bai kamata yace su da su uncles ɗin su bazai masu ta'aziyya ba,ko ba komai Noor ɗin ai ƴar uwar shi ce kuma matar ƙaninshi,duk wannan faɗan da yayi mashi baisa ya kira su uncle Ahmad ba Abbah kawai da uncle Mustafa da mom ya kira sai uncle mutallab ɗin shima Abbah ne ya bashi wayar lokacin da ya kirashi su uncle Ahmad kuwa ko tambayarsu bai yi ba dan ko Irfan ɗin bai kira ba,dama can su ne favorite ɗin shi dan tun ranar da aka kwantar da kainart da laatifa ta sanar da shi ya kira uncle Mustafa ya mashi ya mai jiki kuma dama time to time suna waya da juna ko ya kira uncle Mustafa ko shi ya kira shi. dady yayi matuƙar farin ciki da jin labarin za su zo dan harda Sam ɗin uncle Jonas yace mashi a masu zuwan dan yayi alƙawari wannan karon ko me sam ɗin zaiyi sai ya kawoshi Nigeria. Kwanan mom fatilah biyar a hospital aka sallameta,jikinta da sauƙin sai abun da ba'a rasa ba dan ba ƙaramin taɓata mutuwar tayi ba. A ranar da aka sallameta Abbah yace Uncle mutallab ya koma gidan shi tunda mom fatilah ta dawo ko ba komai ganinshi a kusa da ita zai gare mata raɗaɗin mutuwar Noor ɗin. ko da Abbah yace haka baiyi musu ba ya tattara yanashi yanashi ya koma gidan,mom fatilah tayi matuƙar farin ciki da dawowarshi sai dai wani abu da ya ɗaure mata kai tunda ya dawo gidan ya canza mata gaba ɗaya,ko magana tayi mashi sai ya ga damar amsa mata,wani irin fushi yake da ita duk akan wulaƙancin da tayima mom Dan a ganinshi da ba tayi hakan ba da duk hakan bata faru ba. tsawan kwana huɗu a haka su ke a rana ta biyar ne ƴan uwanta suka zo gidan dan sake dubata da su ka tashi tafiya cewa yayi ta haɗa kayanta ta bisu,da farko tayi tunanin wasa yake sai da taga ya haɗata da takarda ya saketa saki ɗaya ta tabbatar da abun nashi da gaske ne,kuka sosai tasha kamar ranta zai fita tana bashi haƙuri yayinda ƴan uwanta keta zazzaga masifa suna zage zage suna kiranshi da butulu mara tausayi,banza yayi da su bai sauraresu ba sai ma ficewa yayi ya bar masu gidan. haɗa mata kayanta su kayi suna faɗin wallahi baza ta sake dawowa gidan shi ba har abada,a washe garin ranar ya bar ƙasar ba tare da kowa ya sani ba dan ko Abbah bai sanarmawa ba sai da yayi kwana biyu da tafiya tukun Abbah ya sani . Sati ɗaya da kwana biyar da rasuwar Noor aka sallamo Kainart daga hospital,uncle Ahmad so yayi daga hospital ɗin su wuce da ita gida ta ƙarasa jinyar a can amma uncle Mustafa yace sam bai san wannan ba,dan yayi rantsuwa kainart ta gama zama da Zaabith har abada kuwa kusan faɗa abun ya so ya zamar masu,ganin haka ne yasa dady cewa a gidan shi zata zauna harta ƙarasa warkewa,ba hakan su ka so ba musamman uncle Mustafa da a yanzu baya son abunda zaisa tayi nesa da shi,maganar dady ba maganar da za suyi jayayya bace dole tasa suka haƙura, uncle Ahmad da za su tafi ƙin binshi su Ammar su ka yi suma sunfi son zama da kakan nasu. bai hanasu ba ya tafi ya barsu. Kainart tunda ta koma gidan dady take samun kulawa ta musamman daga mom da laatifa yumnah da Fa'iza ma ba'a barsu a baya ba,motsi kaɗan za tayi sai sunji me ke damunta,hakan ba ƙaramin daɗi yake mata ba duk sai ta nemi damuwarta ta rasa sai dai duk lokacin da ta tuna abunda Zaabith ɗin yayi mata sai duk taji damuwa ta mamayeta,fahimtar hakan ne yasa Laatifa kullum take cikin yi mata abunda zai ɗauke mata tunaninshi,Dr fawar har gida ya zo ya gaishe da ita, balqis ma har gidan ta zo wurin yayarta daga nan ta sake duba jikin kainart ɗin,duk bayan ƴan kwanaki tana zuwa wurin yayar tata bayan nan kullun sai sunyi waya,kullum cikin ba Laatifa haƙuri take kan abunda dady yayi mata da roƙwanta akan ta ba Momy haƙuri ta dawo gida. babu irin haƙurin da Laatifa da mom ba su ba mom maimunatu akan tayi haƙuri ta koma gidanta amma tace sam bazata koma ba suma bar ɓata bakinsu, bakomai yasa taƙi haƙura ba sai tun ranar data tafi ko kiranta uncle Hashim bai taɓa yi ba ko yaje gidan su hakan yasa take ganin baya da buƙatarta ne sai dai abunda bata sani ba yana fushi da ita ne saboda nuna halin ko in kula da tayi da balqis a ranar da zata bar gidan da balqis ta suma. Mom tunda ta dawo gida ta fahimce Nainarh na cikin damuwa,janta ta dunga yi a jiki duk dan ta faɗa mata abunda ke damunta amma sai tace mata bakomai,ƙyaleta mom tayi ba dan ta yarda da babu komai ba. *UNITED STATE❤* *Las Vegas (Nevada)* A hankali Aunty Sophia ta turo ƙofar ɗakin ta shigo a zaune Nailarh take saman sofa dake can gaban window ɗakin,wayarta ce a hannunta tana opreting. da mamaki Aunty Sophia ke kallonta harta ƙarasa ciki “baby lafiya ki ke zaune har yanzu,ko dai kin manta da zuwa airport ɗin ne??” Aunty Sophia ta faɗa tana tsareta da ido dan tayi mamakin rashin shirin nata. “ban manta ba,kawai bana jin zan je su Naoh kawai suje su ɗaukota” zama Aunty Sophia tayi kusa da ita “baby wai lafiya ki ke kuwa kwana biyu,me yasa ki ke ma momyn ki haka,ko kiranki tayi a waya baki son picking kuma ke baki kiranta,yanzu ta kira tace zata dawo kince baza kije ɗaukota ba bayan duk tayi tafiya ke ke zuwa ɗaukota??” tunda Aunty Sophia ta fara magana ta ya mutse fuska,gaba ɗaya Nailarh ta sauya ma mahaifiyarta bata san kiranta idan ta kira bata picking,kullum Aunty Sophia cikin nuna mata hakan bai dace ba take amma abun ma nata sai ƙara gaba yake. “idan wani abun tayi maki ba fushi ya kamata kiyi da ita ba,bayan nama san babu abunda tayi maki kawai kin ɗauki wani hali ne wanda bai dace ba,Please Nailarh ki daina hakan ba mai kyau bane ita mahaifiyarki ce” “ni ba fushi nake da ita ba,kawai bana sonta ne a kusa dani” da mugun mamaki Aunty Sophia ke kallon Nailarh jin abunda ta faɗa “anya baby kin san me ki ke faɗa kuwa?” “da gaske nake Aunty Sophia har cikin raina bana son ganinta a kusa da ni,haushi ma nake ji idan na tuna da ita” with a shock take kallonta rasa me ma za tace mata tayi she became speechless,Aunty Sophia bata gama fita daga mamakin da Nailarh tasa ta ba ta su ka ji an turo ƙofar ɗakin,da sauri Nailarh ta miƙe ta nufi toilet da mamaki Aunty Sophia ta bita da ido. Mrs Malika ce ta shigo hannunta riƙe da bag ɗinta ta kasa haƙurin halin da Nailarh take mata ne yasa jirginsu na isowa tayi shatan taxi. a hanzarce ta karaso cikin ɗakin tana kiran sunan Nailarh,murmushi Aunty Sophia tayi tana mata barka da dawowa,a takaice ta amsa mata tana tambayar ina Nailarh take,dan sam bata lura da lokacin da Nailarh ta shiga toilet ba. “ta shiga toilet ne yanzu zata fito” Aunty Sophia ta faɗa,ok Mrs Malika tace tana nufar sofa da Nailarh ta tashi ta zauna,ficewa Aunty Sophia tayi daga ɗakin, Mrs Malika tun tana jiran fitowar Nailarh har ta gaji ta nufi bakin ƙofar toilet, nocking ƙofar ta shiga yi tana kiran sunanta,tsit taji kamar ma babu kowa a ciki,gajiya tayi da nocking ɗin,tura ƙofar tayi ta shiga a zaune ta hango Nailarh gaban bathtub,ciki ta ƙarasa “baby!” ta kira sunanta saurin tashi Nailarh tayi daga wurin,hannu ta kai da nufin taɓa Nailarh tana faɗin “baby baki san na dawo bane” ɗaga mata kai kawai Nailarh tayi alamar eh,mamaki ne gaba ɗaya ya kama Malika “amma shi ne ba kije kin ɗauko ni ba?” ɗan ya mutse fuska Nailarh tayi tana faɗin “ban jin dadi ne” yanayin fuskar Malika ne ya sauya “Ayyah sorry,me ke damunki?” malika ta faɗa tana kai hannunta da nufin taɓa Nailarh dan taji temperature ɗin jikinta,saurin kaucewa Nailarh tayi,abun ya ɗan ɗaurema Malika kai ganin kamar Nailarh bata son ta taɓa jikinta,ƙofar fita Nailarh ta nufa bin bayanta Malika tayi,a tsakiyar ɗakin su ka tsaya,kallon Malika Nailarh tayi tana faɗin. “mom akwai gajiya a tare da ke,You need to have some rest,ki tafi zan zo na sameki” “baby kamar ba kiyi farin ciki da dawowata ba ko?” “am very happy Momy just am not feeling better” “ok,Amma mi yasa nake kiranki baki picking” “please Momy kina buƙatar hutu,ki bari zuwa anjima sai muyi maganar” kallonta Mrs Malika take ba tare da tace komai ba, lamarin ne ke matuƙar bata mamaki,ta kasa gane me Nailar take nufi da wannan halin,ita dai a iya saninta ta san bata mata wani laifi da zaisa ta gujeta ba. “baby ko dai nayi maki wani abun ne ba tare da na sani ba?” “babu abunda ki ka man” “to me yasa nake ganin kamar kina guduna,tsawan fa two month kenan bama tare amma kamar ba kiyi kewata ba” “momy nayi kewarki mana” “idan har da gaske ki ke to ki barni a nan na fi buƙatar kasancewa tare dake sama da komai” ta faɗa fuska a marairaice. bed Nailarh ta nufa ta zauna bata san ya za tayi mata ba ta gane ko ganinta ba ta son yi. bed ɗin Malika ta nufa,zama tayi kusa da Nailarh,hannunta ta kai saman hannun rigar dake jikin Nailarh,saurin ture hannunta Nailarh tayi tana faɗin “please mom,bana so” ran Malika ne ya ɓaci har bata san lokacin data rufe Nailarh da faɗa ba abunda bata taɓa mata ba kenan. kuka Nailarh ta fashe mata da shi,hakan ba ƙaramin ƙara ɓata ran Malika yayi ba,ganin idan ta biyema Nailarh zata iya mata wani abun ne yasa ta fice daga ɗakin rai a ɓace. Tana fita Aunty Sophia na shigowa kusan duk abunda ya faru a kunenta,rufe Nailarh da faɗa itama tayi dan me zatama Malika haka. “Aunty Sophi bana sonta,na tsaneta,bana son taɓa jikina da take” “kar na sake jin bakin ki ya sake furta baki sonta,karki manta Aure za ku yi nan da two weeks” “a iya sanina baki son abunda take man,me yasa zaki sauya yanzu Aunty Sophia” “ke ce ki ka sauya Nailarh,ki sani momynki na sonki,kuma wannan abun ba wani abu ba ne,nima ada ban fahimci son da take maki bane yasa bana so” “ni dai bana sonta kuma bazan taɓa Aurenta ba” “waza ki Aura kenan?” Aunty Sophia ta faɗa da sigar tambaya “CEO ni shi nake so ba ita ba” wani irin kallo Aunty Sophia tayi mata “kin san kuwa abunda ki ke faɗa baby,mutumin da yayi sanadiyar kwanciyarki hospital shi ki ke so?” jinjina mata kai Nailarh “ina matuƙar son shi,ji nake bazan iya rayuwa ba idan babu shi” jin jina kai Aunty Sophia ta shiga yi,lamarin Nailarh ya fara bata tsoro,idan ba neman tashin hankali da momynta take ba taya zata faɗi haka. lallashinta ta shiga yi tana nuna mata hakan ba mai yiwuwa ba ne,amma sam Nailarh ta kasa fahimtar ta. Aunty Sophia ba su sake sanin abun na Nailarh da gaske ba ne sai data fara wasan ɓuya da momynta,duk wata hanya data san zata haɗata da ita tayi blocking,Malika tun tana ɓoye damuwarta harta kasa ga wata muguwar sha'awar Nailarh dake ɗawainiya da ita gashi Nailarh ta ɗauki karan tsana ta ɗora mata. karshe data kasa haƙura mamayar Nailarh tayi cikin dare ai kuwa ranar taga tashin hankali dan sosai Nailarh ta nuna tsanar da tayi mata a fili. hakan kuwa baƙaramin ɓata ran Malika yayi ba har ya kaita da marin Nailarh abunda tunda uwarta ta haifeta wani bai taɓa mata ba,sosai saɓani ya shiga tsakaninsu Nailarh na iƙirarin komai Malika za tayi sai dai tayi amma Aurenta da CEO kamar tayi ta gama kuma sai ta bar mata gidan a yau. murmushin Malika ta saki tana faɗin “yau na sake tabbatar da cewa Nailarh baki san ko wacece Malika ba,amma you will see the other side of me,zan tabbatar maki da ko ni wacece,you will regret” Malika ta faɗa tana gyaɗa kai. wani shegen kallon Nailarh ta mata “i don't care about ko wacece ke,na riga na yanke hukunci bani babu ke,komai za kiyi Malika kin daɗe ba kiyi ba” Nailarh ta faɗa tana nufar dressing room ɗinta Dan ta rantse yau komai zai faru saita bar gidan. A masifance Malika ta figota gaba ɗaya ta kifa ƙasa ƙugunta da kanta su ka bugu da ƙasa,ƙara ta saki ta azabar zafi,Aunty Sophia ce ta faɗo ɗakin hankali a tashe,luna ke sanar da ita abunda ke faruwa da Malika da Nailarh. Malika bata damu da halin da take ciki ba ta fara magana. “ke har kin isa kici Amanata, idanma bacci ki ke to ki farka,ki sani duk wani gata dana baki da ji dake da nake inayi ne dan biyan ɓuƙatata bawai dan kin kai matsayin nayi maki hakan ba,ke ba kowa bace a wurina face abun biyan buƙatata,ki sani akan biyan buƙatata zan iya kawar da duk wanda yace zai kawo man cikas,dan haka ke baki isa lokaci ɗaya ki sauya man ba,Aure tsakani na dake kamar anyi shi an gama,kuma shi wannan mutumin da ki ke magana ki sani daga yau babuke babu shi,idan kuma kin musa ki sani zan iya kawar dashi daga doran duniya?” tashi Nailarh tayi daga ƙasa tana kallon Malika hawaye kwance cikin idanunta “malika ban damu da abunda za kiyi ba amma ki sani muddin ki ka kashe shi nima saina kashe ki❗” dariya Malika ta kwashe da ita “haka ki ka ce ko?” “haka nace Malika,kuma a yau ba sai gobe ba zan bar maki gidan ki” jin jina kai Malika tayi “big mistake Nailarh” harara Nailarh ta watsa mata tana juyawa zata shiga dressing room ɗinta. saurin riƙo hannunta Aunty Sophia tayi “Nailarh kina hauka ne,da mahaifiyar taki ke ke faɗa akan mutumin da baki san ko shi waye ba,ba kuma kisan dalilin da yasa ya shiga rayuwarki ba har ki ke iƙirarin zaki bar gida, kuskurene wannan Nailarh idan kin bar gidan ina zaki,kaf duniya baki da kowa bayan mahaifiyar ki,idan wani abu ke damunki tun wuri ki dawo hayyacinki” “ban damu da dalilinshi na shiga rayuwata ba,ko shi waye iya abunda na sani ina sonshi ko da kuwa da wata manufa ya shiga rayuwata” “baby wannan hauka ne, mahaifiyar ki ba abar da zaki wulaƙanta bace” “Aunty Sophia wannan matar ko zata kashe ni bazan mata abunda take so ba,na tsaneta kima bar ɓata bakinki” tana gama faɗa ta shige dressing room ɗin. kallon Mrs Malika Aunty Sophia tayi harta buɗe baki za ta yi magana Malika tayi saurin ɗaga mata hannu “ba sai kince komai ba Sophia dole na nunama Nailarh kuskurenta,zan tabbatar mata da ƙarfin ikona akanta,sai tayi data sanin sanina a rayuwarta” hankalin Aunty Sophia ne ya tashi jin abunda Malika tace,ta san ko wacece Malika zata iya aikata komai akan biyan buƙatarta. “ma'am Nailarh yarinya ce,idan ki...” bata ƙarasaba Malika tayi saurin ɗaga mata hannun “ko me za kice Sophia bazan saurareki ba,nafi ki sanin Nailarh yarinya ce amma zan nuna mata tsantsar yarinta” tana gama faɗa ta nufi ƙofar fita ta fice,da kallo Aunty Sophia ta bita tana jin wani iri a zuciyarta dama ta san dole hakan ta faru idan har Malika ta san Nailarh ba ita take so ba,tashin hankalinta hukuncin da Malika zatama Nailarh. dressing room ɗin Nailarh ta nufa tana kiran sunanta. samun Nailarh har ta sauya kayan jikinta ta shirya wasu kayan cikin box. lallashinta Aunty Sophia ta shiga yi tana bata haƙuri akan ta zauna,amma bata bi ta kanta ba dan yanzu har ita haushinta take ji,dan gani take kamar tana goyan bayan Malika ne,tana gama ɗaukar duk abunda zata ɗauka taja box ɗinta ta fice ba tare da ta ko kalli Aunty Sophia ba. girgiza kai kawai Aunty Sophia tayi bata san me zatama Nailarh ta gane kuskuren faɗa da Malika da take ba,bin bayanta tayi tana shiga bedroom ɗin wasu jibga jibgan ƙati daga cikin securitys ɗin gidan na shigowa Malika na bayan su,hannunsu ɗauke da ɗan wani madaidaicin box,wani irin faɗuwa gaban Aunty Sophia yayi da sauri ta nufi Malika “please ma'am na roƙe ki karki kiyi haka,Ni da kaina zan shawo maki kanta karki kice zaki hukuntata” ko kallon inda Aunty Sophia take Malika ba tayi ba. box ɗin dake hannunta ta ajiye buɗe box ɗin tayi,kwalaben allura ne ciki sai tururi suke na sanyi “kar kiyi haka Malika Nailarh na sonki kawai yarinta ce ke damunta,amma idan ki ka ce zaki mata allurar nan lafiyarta zata samu matsala, Please karki mata allura” “sophia miye matsalarki da abunda zan yi mata, Nailarh ƴata ce ina da ikon hukuntata yacce na so” tunda su ka fara taƙaddama Nailarh na tsaye tana kallonsu ko a jikinta iya abunda ta sani ko mai zai faru bazata bari suyi mata allurar nan ba. “na sani Madam,amma ki sani idan ki ka kasheta babu abunda zai sauya,Please kiyi tunanin” murmushi Malika ta daki “nafi ki sanin babu abunda zai sauya Sophia,bana buƙatar Nailarh a yanzu,samun wacce zata maye man gurbinta ba abu bane mai wahala a wuri na” Malika ta faɗa tana miƙama ɗaya daga cikin security allura,da kai ta basu umarni da suyi ma Nailarh allura. hawaye ne su ka wanke fuskar Aunty Sophia Bata taɓa tunanin Malika zata iya kawar da Nailarh ba. gadan gadan wanda babu allura ya nufi Nailarh,yana kai hannu zai riƙota ta kai mashi naushi a ido saurin ja da baya yayi yana dafe idonshi,saurin ajiye allurar dake hannunshi ɗayan yayi yana nufarta,da gudu ta juya ta nufi ƙofar toilet ɗinta sai da kafin ta buɗe ƙofar har ya cimmata,damtse hannunta ya kamo ya fisgota baya,gaba ɗaya ta tafi ƙasa,ɗagowar da za tayi ta sakar mashi naushi a gefen ciki,dambe ta shiga yi da su kafin Allah ya bashi sa'a ya sauke mata lafiyyan mari da gaba ɗaya ta faɗin kan floor,rintse ido Aunty Sophia tayi hawaye na bin cheek ɗinta,wata ƴar iskar dariya Mrs Malika tayi tana faɗin “good job,kumata dukan mutuwa idan taƙi tsayawa” wanda ta dakar ma ido ne ya ɗagota,wani wahalallan naushi ya kai mata aciki,jini ne ya shiga fitowa ta hancinta,da gudu Aunty Sophia ta fice daga ɗakin dan bazata iya jurar ganin rashin imanin da Malika tasa su yima Nailarh ba,shiyyasa kullum take bata shawara amma Nailarh ba taji ba,ta san wacece Malika sosai,muguwace ta ƙarshe amma Nailarh ta kasa fahimta. Kamar sun samu jaka haka su ka shiga dukanta sai da su ka ga ta daina motsi tukun su ka ƙyaleta, Malika na daga zaune tana kallonsu,ko a jikinta hakan ma ba ƙaramin daɗi yayi mata ba. da kanta ta ɗauki allura tayi mata,umarni taba security da su ɗauketa,a kafaɗa ɗaya ya saɓata su ka fice daga ɗakin. wayar Nailarh da laptop ɗinta Malika ta ɗauka ta bi bayan su,a bakin ƙofa ta samu Aunty Sophia,kuka kawai take musamman da taga yanda su ka fito da Nailarh. wuce Malika tayi,part ɗinta ta nufa,a tsaye ta samu security a bakin ƙofar wani daki dake part ɗinta. buɗe ƙofar ɗakin tayi suka shiga da ita ciki,cikin ɗakin su ka shiga da Nailarh,ɗakin baya da girma,ɗan ƙaramin bed ne a ciki ko window ɗakin baya da ita kamar ɗakunan prison. a saman bed ɗin ɗakin ya jefar da ita,ficewa su ka yi daga ɗakin,maida ƙofar ɗakin Malika tayi ta rufe haɗi da dannan wasu Numbers jikin ƙofar wanda ba tantama security ne tasama ƙofar.. *ABUJA NIGERIA* yau ta kasance ranar juma'a ranar da uncle Jonas yace za su zo,tun jiya dady yasa yumnah tasa masu aiki su ka gyara part ɗin sam,bai sanar da su harda Sam za'a zo ba sai a yau da safe,zo kaga murna wurin yumnah musamman laatifa,kiran Number wayan shi ta shigayi amma bata samu ba,tunani ta fara ko har sun taho ne. da gudu yumnah ta nufi ɗakin su dan ta sanar da Nainarh zuwan sam ɗin ta san dole tayi farin ciki may be ma haka yasa ta daina fushin da take da ita. tana shiga ɗakin Nainarh na fitowa daga toilet,bathrobe ne a jikinta da alama wanka tayi,da gudu yumnah ta nufeta “sis labari mai daɗi” kallonta Nainarh tayi ba tare da tace komai ba,yar dariya yumnah tayi tana faɗin “kin san cewa harda ya sam a cikin masu zuwa,yanzu dady ke sanar da mu, Nainarh ba kiji daɗin da naji ba Finally dai Allah ya amshi Adu'ar ki ya Sam zai zo Nigeria bayan tsawan shekaru,am very happy to you” ta kai ƙarshen maganar tana sakin murmushi haɗi da kallon Nainarh,ga mamakinta ko a fuska ba taga alamun labarin yayi ma Nainarh daɗi ba,abun ya ɗaure mata kai,duk irin son da Nainarh kema sam amma ta faɗa mata cewa zaizo amma ba tayi farin ciki ba “nainarh wai me ke damunki, ya sam fa nace maki yana hanya?” kauda kai Nainarh tayi tana raɓawa ta gefenta ta nufi dressing room ɗin su, hooking yumnah tayi a nan tsaye lamarin Nainarh ya fara bata tsoro,anya ba aljanune suka shiga jikinta ba,gaba ɗaya ta canza idan wani yace mata Nainarh za tayi action irin wannan idan taji labarin zuwan sam baza ta taɓa yarda ba. bayanta tabi zuwa dressing room ɗin,harta kama handle ɗin ƙofar zata buɗe ta fasa,ta ƴar ƙofar dake jikin ƙofar ta leƙa cikin ɗakin,zaro ido tayi lokacin da idonta ya sauka kan Nainarh da tayi sujjudu shukur a tsakar ɗakin,bata gama fita daga mamakin ba Nainarh ta miƙe ta shiga taka rawa tana faɗin “Allah Alhmdllh, Alhmdllh Allah na gode maka,ya Allah kacika man buri na, Allah kasa na samu soyayyar shi cikin sauƙi, gaskiya nayi farin ciki Alhmdllh” ta faɗa tana sakin dariya kamar zautatta, yumnah bata san lokacin da itama ta saki dariyar ba ko ba komai ta san ƴar uwarta tata lafiyar ta lau kawai fushin da take da ita ne ya hana ta nuna farin cikinta. saurin barin bakin ƙofar tayi dan karma Nainarh ta fahimce tana kallonta,ficewa tayi daga ɗakin. shirye shirye su ka shiga yi na tarbar baƙi,dady kallo ɗaya zaka mashi ka hango tsantsar farin cikin da yake ciki hakama mom,su ya Naeem tun wuraren ƙarfe 10 na safe su ka zo gidan tare da su Aunty Nadeeya,mom Maryam ma ta zo tare da su Ammar,ta zo duba jikin kainart da taji labarin zuwan su sam ɗin ne yasa ta tsaya. Ƙarfe 4 na yamma mazan suka nufi airport Dan tarbosu harda uncle mustapha,ƙarfe 5 jirginsu zai iso amma dady yace su tafi da wuri,ya ƙosa yayi ido biyu da sanyin idaniyarshi, yumnah babu yanda bata yi ba dan a tafi da su amma ya Naeem yace A'a, Laatifa ma ta so tare da su za'a je Airport ɗin amma da ya Naeem ɗin yace A'a sai ta hakura. Ƙarfe biyar daidai aka fara sanar da isowar jirgin daya ta so daga los Angles California,zambur dady ya miƙe daga saman waiting chairs ɗin da su ke zaune,fuskarshi ɗauke da murmushi ji yake kamar ya nufi filin jirgin ya taraso a can,farin cikin shi ya kasa ɓoyiwa,zuba mashi ido su ya Adnan su ka yi ya Naeem na faɗin “gaskiya dady mun fara kishi,irin wannan damuwa haka” murmushi dady yayi mashi “baza ka gane bane Naeem” murmushi ya Naeem ɗin yayi yana girgiza kai. passengers ne su ka fara ɓullowa ta ƙofar da aka rubuta Arrivals. mutane ne suka shiga fitowa ɗauke da boxs ɗin su. tunda passengers su ka fara fitowa su ka baza ido burin su kawai su ga ta inda za su ɓullo. Wani kyakkyawan baturen matashin tsoho ne ya ɓullo daga ƙofar,sanye yake cikin blue black ɗin suit, idanunshi a manne suke da farin glasses,sumar kanshi kamar ba ta dattijo ba sai sheƙe take tana ɗaukar ido,fuskarshi ɗauke da murmushi yayinda wasu zaratan samari masu jini a jika ke biye da shi su biyu,hannunsu riƙe da trolleys ɗin su,ƙananan kaya ne a jikinsu,Allah yayi su da surar jiki mai matuƙar jan hankali,fuskokinsu a rufe su ke da mask,walking majestically su ke nufo cikin filin airport ɗin. su dady ne su ka nufo su fuskokinsu ɗauke da murmushi,hugging juna dady su kayi shida wannan dattijon yana masu barka da zuwa,raba jikinsu suka yi,kallon wannan samarin dady yayi fara'ar fuskarshi na daɗa ninkuwa,ɗaya bayan ɗaya suka shiga hugging ɗin su dady ba tare da sun zame mask ɗin dake fuskokinsu ba,kasa haƙuri dady yayi har sai da yace “wai baza ku ɓuɗe fuskokin ku ba ne” dan ya fara zargin wani abu daga muryoyinsu,zame mask ɗin su ka yi suna sakin murmushi da ya ƙarama fuskokinasu kyau,Masha Allah na furta a yayin da nayi arba da fuskokin kyawawan samarin,kyawawa ne na gaske,komai nasu iri ɗaya hatta gyaran gashin su iri ɗaya ne kamar twins haka su ke,launin fata ne kawai ya banbanta su sai zanen tatto da earring da ɗaya ke dashi wanda ko ba'a faɗa maka waye shi ba tsananin kamar da yake da dattijon nan da yumnah zai tabbatar maka da ɗan sa ne,ɗayan kuwa kallo ɗaya zaka mashi ka hango kamaninshi da mahaifiyar sa Aunty mariya. yanayin fuskar dady ne ya sauya,a hankali ya furta “james,Alyar!” da fa'arsu su ka amsa mashi “ina sam ɗin yake?” ya faɗa yana bin fuskokinsu da ido, kallon juna su ka yi fara'ar dake fuskokinsu na ɗauke,kasa ce mashi komai su ka yi,cikin ƙunar rai ya ce “yanzu ma bai zo ba?” jinjina mashi kai su ka yi “eh dady, uzuri ne na gaggawa ya taso mashi shiyyasa bai zo ba” hawaye ne su ka taru a idonshi dama ya daɗe yana tunanin ta yarda sam zai biyo su cikin sauƙi ba tare da gardama ba. cikin tsantsar ɓacin rai ya shiga faɗin “wai me sam yake nufi da ni ne a rayuwar nan,me na aikata mashi da yake wannan fushin da ni,Ni mahaifinshi ne amma ya ɗauki karan tsana ya ɗaura man,irin tsanar da yayi man ko maƙiyinshi bai kamata yayi ma ita ba,na lura yafi son mutuwa sama da rayuwata,kullum cikin azabtuwa nake da soyayyar shi,amma hakan bai sa yayi man adalci ba,nayi ban haƙurin,nayi lallashin,ban san iya adadin zuwan California dan na ganshi ba,amma duk a banza haka zan ƙaraci zamana na dawo ba tare da na ganshi ba,me sam ya ke so nayi mashi wanda zai sa ya fahimci halin dana shiga saboda rashin shi a tare da ni,me zan mashi wanda zai sa ya fahimci irin son da nake mashi???” ya kai ƙarshen magana hawayen dake kwance cikin idonshi na bin cheek ɗin shi,da sauri uncle Jonas yasa hannu yana goge mashi hawayen,babu wanda jikinshi baiyi sanyi ba a wurin ba “kayi haƙuri Tahir, uzuri ne ya taso mashi kamar yarda Alyar ya faɗa,da badan uzurin mai girma ba ne nima da bazan barshi ba,amma ya tabbatar man da yana nan zuwa kafin mu tafi,kayi haƙuri” uncle Jonas ya faɗa “baya son ganina ne kawai Jonas,har yanzu fushi yake dani” girgiza mashi kai uncle jonas yayi yana sake bashi haƙuri. wani irin ɓacin rai ne ya rufe ya Naeem ganin halin da dady ya shiga,bai taɓa jin haushin sam irin na yau ba,dan me zai dinga wahalar masu da mahaifi dan kawai ya fahimci yana sonshi “dady ka daina zubar da hawayenka akan shi,ni nayi maka alƙawari a yau ba sai gobe ba zamuje har California ni da Adnan,komai zai yi sai mun kawo maka shi har gida” ya Naeem ya faɗa “ba sai kunje ba Naeem,da kaina zanje na sameshi,idan ma kashe ni zaiyi ya kashe ni,amma nagaji,nagaji!!” uncle mustapha ne ya yayi saurin cewa “A'a baza'ayi haka ba yaya,tunda har yace zai zo nan kwana biyu,mu jirashi mu gani idan bai zo ba ni da kaina zanje na zo maka da shi,kayi haƙuri” “baza ka gane ba mustapha,ku barni kawai na tafi,bazan iya jira har tsawan wannan kwana kin ba,ni ka ɗai na san yanda nake ji” “na sani yaya,amma kaga baƙo ka yi bai cancanci ka tafi ka barshi ba” “kayi haƙuri Tahir,idan ma bai zo ɗin ba sai mu tafi tare da kai” a cewar uncle Jonas, ya Naeem ne yace“uncle to ku bari ni da Adnan ɗin mu tafi” “A'a Naeem,babu wanda zai tafi” lallashin dady su ka shiga yi akan ya jira nan da kwana biyu idan sam ɗin bai zoba sai su tafi,da ƙyar su ka samu suka shawo kanshi. babu wanda ranshi bai ɓaci da rashin zuwan sam ɗin ba. haƙuri uncle mustapha ya sake ba dady yana kamo hannunshi,bin bayan su suka yi har inda su ka yi parking motocinsu,motar uncle mustapha dady da uncle Jonas su ka shiga yayinda Alyar da James su ka shiga mota ɗaya da su ya Naeem,reverse su ka yi su ka fice daga Airport ɗin. ya Naeem tunda su ka shiga mota yake dialing number Sam amma kiran baya tafiya tsaki yaja,kallon shi ya Adnan dake driving yayi yana faɗin “lafiya dai ko,waye ka ke kira??” kamar jira yake ya Adnan yayi magana ya shiga surfa masifa ta inda yake shiga ba ta nan yake fita ba,shiru su kayi motar babu wanda yace mashi wani abu har ya gama dan sun fahimci ranshi yayi mugun ɓaci. “ni gaba ɗaya a wannan al'amarin nafi ganin laifin dady,Allah ya bashi mu da yawa amma dan me zai hana kanshi zaman lafiya saboda shi,da ace tuntuni ya watsar da lamarinshi da bai rika ɓata mashi rai irin haka ba kuma shima da bai gujeshi ba,amma dady ko za kayi me kana bashi shawara akan Sam baya ɗauka,ya ɗauki son duniya ya ɗora mashi” ya Adnan ya faɗa rai a ɓace “tun yaushe nake nunama dady haka amma kwata kwata baya ganewa,ya fi son depression ya kamashi saboda sam” “dan Allah second father kuyi haƙuri,uzuri ne ya riƙe shi amma ba da gangan yaƙi zuwaba,dashi mu ka yi shirin zuwa Allah ne bai nufa ba” Alyar ya faɗa,suna matuƙar son ɗan uwansu duk sai su kaji ba daɗi da maganganun su ya Naeem,duk da suma kan su basa jin daɗin halin da ya ke nunama dady,basu da yanda za suyi ne kawai “uhmm kana son kareshi ne kawai Alyar,amma ni na san babu wani uzuri daya riƙesa,kawai yayi ne dan yaga halin da dady zai shiga,sai dai ya sani muddin dady ya faɗi ya mutu da ɓaƙin cikinsa Allah bazai barshi ba” “ya subahanallah,dan Allah ya Naeem ka daina faɗar haka,da badan uzurin daya riƙesa ba da babu abunda zai hanshi zuwa,amma in sha Allah yana nan zuwa soon” “dole na faɗin haka Alyar,sam ya matuƙar ɓata man rai yau,a iya sanina baya da jahilcin addini,ya san cewa iyaye ba abun wulaƙantawa bane,amma ya koma kamar wanda bai taɓa sanin komai a addininsa ba,shi ko tsoron Allah ya kamashi da alhakin mahaifinsa bayayi??” “haka ne second father,in sha Allah komai zai wuce,nan da two days yana nan zuwa” “wallahi kar Allah ya sa ya zo,ai duniya ce wanda bai zo ba ma jiranshi take bare wanda ke cikinta” girgiza kai Alyar yayi baya jin daɗin kalaman da ya Naeem ɗin ke faɗa,haƙuri su ka shiga ba su shi da James, ya za suyi da halin ɗan uwan nasu lamarin nashi ne sai Adu'a. dady tunda su ka shiga mota ƙala baice ba kana kallonsa kasan yana cikin damuwa,haƙuri uncle Jonas ya sake bashi yana sake tabbatar mashi da uzuri ne ya riƙe sam ɗin amma yana nan zuwa kafin su tafi,jinshi kawai dady yake amma ya san babu wani uzuri daya riƙesa kawai baya son ganinsa ne,kullum cikin Adu'a yake Allah ya rage mashi son shi amma ina yanzu ya fara tunanin sonshi ne ajalinshi. har suka iso gida babu wanda ya sake cewa komai. mom tayi matuƙar farin ciki da zuwan kawun nata sai dai ta wani ɓangaren tayi takaicin ƙin biyo su da sam ɗin yayi sai dai ba ta nuna hakan ba ta barshi akan da sun tashi tafiya ƙafarta ƙafarsu,ita za taje da kanta ta dawo da shi. babu wanda baiji haushin rashin zuwan sam ɗin ba musamman laatifa da Nainarh,dan Nainarh ɓoyewa tayi a bedroom ɗin su tasa kuka,taci burin ganinshi amma yaƙi ya zuwa,Abbah ma yaji haushin rashin zuwan sam ɗin,har kiran wayarshi yayi amma bai sameshi ba da yake gidan shi su ka fara zuwa,uncle Jonas baiji daɗin rashin samun uncle mutallab da mom Fatilah da yayi ba,yaso ace yayi masu ta'aziyya ido na ganin ido,sun ɗan jima a gidan Abbah kafin suka nufi gidan dady,acan su ka sa mu uncle Ubaid da uncle Hashim sun zo yi ma uncle Jonas barka da zuwa ba su san sun tafi airport ba da sun je tarbosu. Tarba ta musamman uncle Jonas ya samu daga ahalin Abbah hakan kuwa baƙaramin daɗi yayi mashi ba,ya sake tabbatar da karamcin su,ba wannan bane zuwanshi na farko ba. Alyar basu wani jima a Estate ɗin ba su ka nufi gidan su shi da James duk da dady ya so su zauna part ɗin sam amma Alyar yace zuwa gobe za su dawo. su uncle Ubaid sun jima sosai a gidan,fira sosai su ka sha da uncle Jonas,sai da dare yayi sosai tukun su ka yi mashi sallama su ka koma gida. su uncle ubaid na tafiya dady ya rakashi bedroom ɗin dake kusa da nashi wanda mom ta gyaramashi,zama dady yayi,kwantar mashi da hankali uncle Jonas ya shiga dan ya lura har yanzu da sauran damuwar duk da yana ƙoƙarin dannewa,murmushi kawai dady ya mashi yana faɗin bakomai zai jirashi nan da kwana biyun,mom ce ta shigo ɗakin,tashiga ɗakin dady bata ganshi ba yasa ta zo nan,kusa da kawun nata ta zauna tana sake mashi sannu da zuwa da tambayar lafiyar mahaifiyarta da matarshi,duk suna lafiya yace mata yana tambayar Irfan da tunda ya zo bai sa shi a ido ba. tunda safe ya fice daga gidan zuwa aso Villa,tunda aka yi rasuwar bai fita ba sai yau. sun ɗan jima a ɗakin sosai suna buɗe wani babin firar yaushe gamo,sai da dare ya raba sosai tukun su ka yi mashi sallama su ka fice. bedroom ɗin dady su ka nufa “Naeem ya sanar dani komai daya faru,ni kaina banji daɗin rashin zuwan sam ɗin ba amma dan Allah kayi haƙuri ka cire damuwar sam a zuciyarka,ganin ka damu dashi ne yasa yake wahalar da kai,kuma bai kamata kana nuna tsantsar soyayyar shi a gaban ƴan uwanshi ba” “Zulaihart ni kaina ban san wane irin so nakema sam ba,bana iya ɓoye soyayyar shi a ko ina” “na sani ƴallaɓai amma daurewa za ka yi,ko dan saboda ƴan uwanshi,kullum burin su su faranta maka,Ni na san basa jin daɗin banbancin da kake nunawa tsakanin su da ɗan uwan su kawai suna daurewa ne yasa ba su taɓa nuna maka ba” ta san su ya Naeem kawai baza su faɗa bane amma dole suna jin ba daɗi da irin soyayyar da yake nuna ma sam ɗin “in Allah zan gwada yin hakan” “Allah ya sa” lallashin shi ta shiga yi tana sake kwantar mashi da hankali har bacci yayi awan gaba da su. dady sai da ya tabbatar da mom tayi nisa a cikin baccin tukun ya tashi, toilet ya shiga bai wani jima ba ya fito,jikinshi da damshin ruwa da alama wanka yayi, dressing room ɗin shi ya nufa,mom na nan kwance tana bacci ya fito har ya shirya cikin suit silver color,wayar shi dake ajiye saman nightstand ya ɗauka,matsawa yayi kusa da ita, kissing forhead ɗin ta yayi kafin walking calmly ya fice daga ɗakin. lokacin da zai isa compound har driver shi ya fito da mota da alama ya jima da sanin tafiyar,back seat ya buɗe mashi ya shiga kafin shima ya shiga mazaunin driver,reverse yayi su ka ɗauki hanyar ficewa daga Estate ɗin. tunda ya fito yake laɓe jikin Piller yana kallon su sai da ya daina ganin motar ta su tukun ya fito,baƙaƙen kaya ne complete a jikinshi,ya rufe ko ina a jikin shi,hannu ya zura cikin trouser pocket ɗin ya ciro waya,dialing wata number yayi,wanda ya kira na picking yace “boss yanzu nan ya fita daga gida” bana iya jin me na cikin wayar ke faɗa mashi sai ji nayi yace “ok sir an gama” zame wayar yayi daga kunnenshi,ya nufar bayan gidan. *A ROUND 3 AM* Ƙarar wayarta ne yayi sanadiyar farkawarta,hannunta ta zura tana laluben switch ɗin bed-side lamp ta kunna,hasken ne ya ɗan haska gadon,idanunta ta kai ga dady dake kwance kusa da ita ga mamakinta baya nan, tunanin ta fara ko yana toilet, a hankali ta kai hannunta ta jawo wayar tana duba mai kiran nata,faɗuwa gabanta yayi ganin number dady, saurin kallon agogon dake manne jikin bango tayi wanda ke nuna ƙarfe 3:40 na dare kafin ta kalli wayar tana mamakin to ina yaje a wannan lokacin da har yake kiranta a waya,har kiran ya katse ba tayi picking ba wani ya sake shigowa, picking tayi tana kara wayar kunnenta,on the other side taji wata murya saɓanin ta dady nayi mata sallama,saurin sauka tayi daga saman bed ɗin gabanta na wani irin mummunan faɗuwa,to waye wannan me ya kai wayar mijinta hannunshi,da ƙyar ta samu tayi ƙarfin halin faɗin “bawan Allah waye kai,ina mai wayar yake ⁉️” “dan Allah da katte nake magana” bugun zuciyarta ne ya tsananta jin sunan da na cikin wayar ya ambata,cikin rawar murya tace “Eh itace,waye kai,ina mai wayar yake⁉️” “ya gamu da haɗari ne a...” ai tun kafin ya ƙarasa ta saki wayar hannunta,kamar saukar aradu haka taji zancan nasa,ficewa tayi daga ɗakin kamar zata tashi sama ita kanta bazata iya cewa ga halin da take ciki ba,tana shiga main parlor ya Naeem da ya Adnan na faɗowa,tana ganin su kawai ta yanke jiki ta faɗi..... *INNALILLAHI WA INNAH ILAIHI RAJI'UN,ALLAHUMMA AJIRNI FI MUSIBATI WA'AKLIFLI KHAIRAN MINHA,LAHAULA WALA QUWWATA ILLAH BILLAHIL ALIYUL AZIM* *ina dady zashi,waye ke sanar da fitowarshi,wa yake sanar mawa,ta ya akai wannan haɗarin ya faru da shi⁉️* *Shin bari mu koma baya* *Wacece wannn baturiyar data haihu a ɗakin hotel har tayi sadaka da ƴarta ba tare da ko taji ɗumin jikinta ba,sannan su waye mata da mijin data yima sadaka da ƴarta⁉️* *Su waye ke bibiyar rayuwar Nainarh,taya akai Abid ya rayu bayan an shida ma court mutuwarshi,wane flash ne mahaifin Nainarh ya bata,ina Flash ɗin yake,shin da gaske ne yumnah ce ke bibiyar Nainarh,su waye su ka kashe mahaifin Nainarh⁉️* *Shin da gaske Zaabith na tare da uncle Mustafa ko dai kawai zargi ne⁉️* *Waima waye ya kashe Noor,wace masifa ce tasa kanta a ciki,su waye bayin Allah data taimaka,menene a cikin Flash ɗin data ba Irfan,wane zaɓi ne take cewa tayi mashi⁉️* *Shin kuna ganin hukuncin da uncle mutallab ya ɗauka akan mom Fatilah ya dace❓* *Wacece Carol ne❓* *shin kuna tunanin Nailarh ta rayu bayan duka da Allurar da mahaifiyarta tasa aka mata,waye CEO dake bibiyar Nailarh,wacece Aunty Sophia,Allurar mecece taba Noah ya ba Mrs Malika,waye mijin Mrs Malika,wane yara ne Nailarh ta gani a container lokacin da mahaifiyarta ta turo masu da kaya,Mrs Malika wace irin uwa ce ita dake neman ƴarta,wace irin uwace da zata lalata rayuwar ƴarta,wane irin business ne ma take yi⁉️* *Club ɗin waye su Irfan ke kula da shi,wacece yarinyar da aka yima opretion su waye su ka yi mata opretion ɗin,shin kuna ganin mom maimunatu zata koma gidan uncle Hashim ⁉️* *Wanene SAM,me ye asalin abunda ya haɗashi da dady,shin duk laifin da dady yayi mashi ya cancanci yayi fushi da shi,kuna ganin zai zo kuwa bayan two days ɗin da su Alyar su ka ce⁉️* _Masu karatu tambayoyin fa da yawa,kuma ko wacce na buƙatar amsa,dan jin wannan amsoshin kukasance dani taku Queen Kainart a cikin wannan labari mai taken SHIRYAYYAR ƘADDARA,ku kasance dani a season two dan samun amsoshin tambayoyin ku._ *Alhmdllh Alhmdllh Alhmdllh anan na kawo ƙarshen littafin shiryayyar Ƙaddara season one game buƙatar two 500 ne za'a tura kuɗin ta wannan asusun 9131306012 Hadiza mukhtar opay bank sai a tura shaidar biya ta wannan nambobin 08133650574/09163957890* *Daga Alƙalamin Queen Kainart...✍* *Chat me via WhatsApp* *08133650574/09131306012*