BAƘIN SHAFI oumyasmeen HILUX aguje suke shigowa layin Alhaji Hussain me tangaran da kuma mayan motoci a babban masallacin da ke gidan za a iya daurin auren jikokinsa har guda biyu tuni kusoshin gwamnati sun cika maƙil da kuma attajirai cikin masallaci kuwa wani ne ya matso kusa da mahaifin sabeer kai mahaifin sabeer jin jina kai yayi ya dubi waliyin amarya yace '' a dakatar da daurin auren nan na fasa.., da sauri uncle Yusuf ya ɗago da tsoho me ran ƙarfe Alhaji Hussain me tangaran da kyar ya iya haɗeye yawun baƙin sa wanda yayi mai ɗaci yace '' me ya faru...?, tashi yayi ya dubi sabeer yana cewa tashi mu tafi mun fasa ashe damar yar su bata da uba sannan yar iskace shine soyayya ta rufe maka ido zaka dauko mana abin magana a family din mu tashi yayi haka yan uwansa suka fara zarewa da dadde dadadde gumi ne ya shiga karyowa yan uwan nasreen da kyar daddy yace '' baffa ya zamu yi tun da nake ɓan taɓa ganin tozarci irin na yau ba.., ran baffa ya ɓaci iya ɓaci idanuwansa yayi yaja yace ''komai aka faɗa mata ita ta jawa kan ta bani da ikon hana mutane abin da za su faɗi amma idan har khadijatou bata gyara halinta ba wallahi zan zartar da hukunci da ba zai mata dadi ba karo na biyar a fasa auren ki amma ba zaki hankali ba ..., baffa hakuri za a yi cikin cije leɓe yace ...a daura na ALTAB ba wanda aka sanarwa nan take aka daura auren ALTAB da rufaida akan sadaki dubu dari biyu nan da nan basu shela suka fara Cikin gida kuwa har labari ya isa kunnen nasreen zubewa tayi a ƙasa hawaye na bin fuskarta babban takaicin ta shi ne sai Da komai ya zo ƙarshe yayi mata wannan cin mutuncin ina ma ya bari a daura ko wata ɗaya tayi karo fa na biyar da fasa auren ta ko wanne daga an kawo kuɗi Sai abin ya rushe amma wannan fa ranar daurin aure aka fasa me wannan shegen zai ce tashi tayi ta goge hawayenta gyara fuskarta ta shiga yi adda asma ce ta shigo tace ''nasreen ya na ganki haƙa...?, juyowa tayi tana murmushi wanda ya fi kuka ciwo tace '' adda asma meke nan ban fahimce ki ba..., shigowa ta kara yi tace '' an fasa daurin auren ki amma kina cikin kwanciyar hankali ga su abban Sultan nan duk ransu a ɓace Please nasreen ki canja halinki ke ce kaɗai da muwar wannan family din namu..., ranta ne ya ɓaci ta ɗaga mata hannu tana cewa adda asma ina mutunta ki da ganin darajar ki wallahi idan baki kiyaye kalaman ki ba zan cire duk abin da nake ganin ki dashi nayi miki ba dad'i duk wanda zai damu barin ni ce sau fa biyar to s kuke na mutu anyi na farko na suma har da kwanciya a asibiti na biyu iya suma nayi na uku na rame na fita hayyacina na hudu na damu har hakan ya sakani na dinga cuta na biyar kenan so kuke na mutu to ba ai wannan namjin nan ba wallahi dan haka ga hanya nan kama haɓa tayi ta fita wallahi gwara da kikai musi haka dame zaki ji Please humy ki fita ina buƙatar hutu idan an jima tayi mu haɗu a club sakar baki tayi ta ɗauki jakarta tace ''ni kike kora..., a fusace tace ''ki ɗauka haka ne zo ki fita ƙiiii ta jata kaciɓis sukai da abokanan Altab suna shigowa sun ci babbar riga haɗiye wani yawu tayi me kauri garin irin kallon da ya jefe ta dashi mazaiwa tayi cikin iya barikanci tace ''sannun ku da zuwa ya hidima.., mamakine ya ishe shi be taɓa zaton shedancin yarinyar nan ba ya kai haka yau a fasa auren ki kuma ga tanan normal har tana da kwarin gwuiwar shiga mutane Alhamdullah haka suka ce ido ya mujaheed ya kora mata murmushi ta sakar mai shima martani ya sakar mata ya matsa kusa da ita hannunsa ta kama idanuwanta suka ciko da kwalla ƙasa ta tayi da ido tace '' blood line kaga abin da sabeer yayi min..., kama hannun ta yayi suka matsa duk abin da ke faruwa altab ya na lura da komai be san me khalil zai yi da wannan yar iskar yarinyar ba zama sukai a guarding tace '' ko zaka iya faɗamin dalilin da yasa ka sabeer ya fasa aure na ko dai akan magana ɗaya ce da na sani da..., NASREEN bazan ɓoye miki ba akan dayan ne amma yace wai yar iska ce dafe kanta tayi kallon hannun ta yayi da yaci uban farata har da tattoo bayan kunshiin da tayi innalillahi kinga ko wallahi idan har ba zaki canza dabi'un ki ba to kina tare da kalubale kala kala daga yau sai yau kar na ƙara jin kin tafi club dole ki canza idan har kina neman miji na gari..., ya khalil dame zanji kanaga yau tace zata dawo daga cairo amma me ta dawo a gaban ta na haɗata da Allah akan daurin aurena ka ɗai idan ta halarta ta gama yi min komai amma me tazo ya khalil dame zanji kowa laifina yake gani sannan maganar barin kawayena Please mubar maganar nan idan shawara kake bani to tayani da addu'a fakat ta faɗa tana tashi sakar baki yayi yana fatan Allah ya shirye ta sosai yan biki ake gutsiri tsoma musamman ma ɓangaren amarya rufaida ta taji wannan labari har rawa ta taka basa ga muciji da nasreen saboda a komai tayi mata fintinkau ko ina nasreen hakan ba karamin dad'i yayi mata ba yanzu dole ta ajiye wannan shegen girman kan nata da yammaci kowa ya fara shirye-shiryen tafiya dinner idan dangin mai tangaran da na rufaida kowa zai halarci dinner nan a bangaren nasreen shirin fita take taci uwar doguwar riga fitted gown peach colour da adon stone white colour da blue sosai rigar take kwallil ha wani uban kamshi da take bazawa Kai kace ɓarin turare akai daman ko ɗaya bata dinka lefenta ba tana da shago a zooroad komai order tayi ban da na abbanta da ya bata necklace ta saka irin me tsayawa a makoshin nan tuni tattoo din da tayi a huyanta ya fito daura veils tayi blue Black sannan ta ƙara fashe jikinta da turare kiran sallar magariba da kai ta ɗan dakata ta zauna jakarta ta dauka da wayar ta ta kunna sakon sabeer taci karo da su har guda bakwai ba tare da ta duba ba ta goge su ajiye wayar tayi ta zuba ta gumi wayar ta ce tayi ringing alamun shigowar sako dubawa tayi ta kurawa sakon ido tsaki ta ja kamar ba zata duba ba sai ta duba ga abin da aka ce mata Assalamu alaiki kiyi hakuri aiki yayi min yawa so bani da time din da zan zo kano ina taya ki murnar auren ki tsaki ta ja ta goge ji tayi kamar ta jefar da wayar saboda takaici ganin an idar da salla ta saɓa jakarta ta fito ba kowa a floor a farfajiyar gidan ce ta haɗu da mutane ana ƙoƙarin tafiya dinner kowa sai kallonta yake ko a jikinta gurɗewa tayi da yake hil ta saka ga kallon mutane tsaki tayi ta gyara tafiyar ta danna remote tayi motar ta ta buɗe shiga tayi ta yi mata key a hankali ta fara tafiya horn tayi me gadi ya buɗe mata ai kuwa a guje ta fita har tada kora take tafiya take da gudu har ta isa kan titi sannan ta dena gudun da take ta fara tafiya a hankali zuciyar'ta duk ba dadi idan tace abin nan be taɓata ba tayi karya sai ta nutsuwarta tayi gudun samin matsala wayar ta ce tayi ringing ganin me kiran gabanta ya waɗi parking tayi a bakin titi ta ɗaga kiran tace ''assalamu alaika baffa barka da dare..., Khadijah duk ida kika tafi ki dawo aje gurin dinner din nan da ke gumi ne ya wanke ta tace '' bani da get pass..., kije altab ya baki yana faɗar haka ya kashe wayar sanin shi din magana ɗaya yake jikinta yayi sanyi ta juya zuciyar'ta na mata soya har ta isa gida bata dena mita ba a waje tayi parking ta fito kai tsaye shashin altab ta nufa wanda kaf duniya ta tsane shi bata kaunar ganinsa ba tayi wahalar knocking ba a bude yake tana iya jiyo muryar abokanan sa shiga tayi bakin ta dauke da sallama amsa mata suka wayar ta ce tayu ƙara daidai fitowar altab sanye da ash din shadda tayi bala'in amsar sa ɗagawa tayi ta ƙara a kunne tace '' jazz gani nan zuwa amma bazan dade ba kuyi duk abin da ya dace...,bata jira me zai ce ba ta kashe wayar altab nunawa yayi kamar be ganta ba ya dauke kansa yace '' rufa'i kamar lokaci yayi ko.., eh wallahi amma sai munyi isha ma je mu dauko ta okay gurin ka nazo wani kallo yayi mata ya buɗe baki zai magana ta tari numfashin sa tace ''yanzu ba lokacin sa'insa bace ka adana ta a kwai ranar ta bayin kaina ne ya kawo ni nan ba girgiza kai tayi ta kalli gefen ta ganin yadda suka tsura mata ido kallon su yayi ƙasa ƙasa yana cewa ke yanzu baki ji kunya ba kalli tufar da ke jikin ki ko da yake duk inda dan iska yake bashi da kunya ba abin da ba zai iya aikatawa ba sannan wallahi kijin na rantsai miki ko tuba kikai idan har ba zaki canza halin ki ba ba me auren ki mace me daraja da rufe jikinta ake kai aura ban da ƙaruwar da take banzatar da jikin ta ko wanne dan iska ya zo ya taɓa... 🤔 🤔 BAƘIN SHAFI oum yasmeen EPISODE 2 Mayafinta ne ya zame daga kanta da sauri ya kalli wuyan'ta yaga star ta tattoo jinjina kai yayi ransa duk a ɓace yace '' fice min daga daki tunka fin nayi miki ba dad'i..., da sauri ta ɗago kaf duniya bata da maƙiyi sama da Altab kallo ɗaya zakai wa fuskarta kaga tsagwaran tsana da yayi mata me yayi zafi kuma dada ce wa take tana yarinya ya bauta mata amma yanzu fa ba wanda ya tsana sama da ita wayar ta ce ta ƙara ringing da sauri ta kalli screen ɗin wayar sai neman agaji take ganin sunan humy chairlady ɗagawa tayi tare da barin gurin , zama yayi ya saki gauran numfashi gaskiya abin da kai be dace ba ya zaku haɗa mata biyu dan dai tana da dakakkiyar zuciya ce da tuni wallahi wani zancen ake ba wannan ba.. Rufa'i ya faɗa ransa a ɓace a'zafafe altab ya ɗago yace '' mene abin daga hankali akan yarinyar nan ba ita ta siyawa kanta ba mutum shi yake saiwa kansa da kansa daraja shekaran jiya ba a hotel muka ganta ba munje kamawa baƙin mu da za su zo ita da ƙawayenta nifa wallahi na tsani yar iskar yarinyar nan gani yayi ba zai iya zama da ita ba shi ya saka yace ya fasa..., toshe kunnan ta tayi wayar ta ta waɗi species ko wanne ɓangare yayi nasa guri tuni idonta ya ƙada yayi ja abin ka da farar fata ɗurƙusawa tayi ta ɗauki layinta da sauran species din wayar ta fita tayi ta bugo mai kofar zuciyar ta duk a jagule zama tayi akan fafaren kujerun da ya zuba su a farfajiyar shashin nasa zuba tagumi tayi tun da take bata taɓa ganin cin mutunci irin na yau ba amma ba komai duk iyayenta ne sula zata zama abin da suke zargi sai a faɗa da hujja da wannan tunani ta tashi ta bar gurin dakin ta , ta shiga lokacin ba kowa sun tafi dinner kwanciya tayi ba tare da ta cire komai ba duniyar na juya mata kallon species din wayar ta tayi ta ja tsaki bacci ne ya kwashe ta ba tare da taci re komai ba Wannan kenan sosai guri ya ci ka dam ƙam da abokanan arziki rufaida sai murmushi take baki yaƙi rufewa sosai adda asma ke baza ido ko zata ga nasreen amma ba ita ba alamar ta kardai fa ta jawa kanta daman baffa ciki yake da ita shiru tayi tana tunani ji tayi an taɓa ta da sauri ta juyo dan murmushin karfin hali tayi tace '' zeena har kun zo...?, eh wallahi daman tun ɗazu nake neman ki ya taro zama tayi akan kujera zeena ta ja itama ta zauna adda asma tace '' wallahi alhamdulillah..., haka abu kuma ya zama abin gaskiya be mun dadi ba na tausayawa nasreeen yawa wacce aka saka mata hannu yan iskan nawa ne suke auro wa shiru adda asma tayi tana danna wayar ta ba tare da ta tofa komai ba tasan halin zeena tas ta iya munafurci sannan aminiyar umman yaya ce uhmm nace ba ɗagowa tayi tace '' Please bana son wannan zancen kama yayi muyu addu'a koma mene Allah ya kawo karshen abin idan kuma da wanda ya saka mata hannu insha Allahu dan sa zata aura.., uhmm Allah ya kyauta amin ya Allah Sai ƙarfe ɗaya taro ya watsai kowa ya ɗauki motarsa ya tafi gida lokacin nasreen ta farka jin hayaniyar mutane tashi tayi tana ya tsuna fuska shaf ta manta da zata je club dafa kanta tayi gashi ba waya a hannun ta dole gobe ta je ta siya waya , tashi tayi ta cire kayanta ta saka na bacci ta koma ta kwanta ji tayi an turo kofar ta kunna bedside blam tashi tayi tace '' lafiya kuka shi go min daki...?, aunty nasreen gurin yayi kaɗan har guestrooms sun cika shine dada tace muzo dakin ki wata uwar harara ta zabga mata tace '' to ba guri maza ku fitar min daga daki ina za ku zauna a nan..?, ke yanzu nan dakin har abin alfaharin kine wai yau she zaki hankali ne..?, ya jero mata tambayar ajere tashi zaune tayi ta yaye blanket din da ta rufe jikinta da shi dafe kanta tayi ta cusa hannu wanta cikin gashinta tace '' ku fitar min daga daki saboda tsabar raini a ina zaku kwanta ni bana son matsuwa..., amma kin iya da sauri ta ɗaga mai hannu tace '' kana faɗamin magana iya son ranka narantsai da Allah ka jirayi sakamako zo ku fitar min da ga daki bawai tsoranka nake ji ba altab kaddara ce bata wuce faɗawa kan ka ba idan ba zakai wa mutum fatan shiriya ba be kamata ka dinga jefan shi da mugayen kalamai ba wallahi wata ran sai kai dana sani mara amfani zo ku wuce ku barmin daki kowa da inda ya tashi da shi yake alfahari..., kallon su basma yayi yace '' ku jira ni a waje...., sum sum suka bar gurin suna mamakin nasreen da bata jin tsoransa kowa na gidan tsoransa yake ji musamman ma yaran gidan da yake shi ne babban jika a gidan takowa yayi har ida take tsaye ya zura hannuwansa a aljihu yana jefa mata wanni irin kallo me cike da fassara kala kala danne tsoransa da yake shiga zuciyar ta tayi musamman ma da taga iya kirjinsa ta tsaya dogo ne sosai amma kibar sa ta shanye tsayinsa bawai kiba sosai ba wacce zatai mai muni aa daidai da kirar jikinsa cikin dar dar tace '' malam fuce min daga daki..., shiru yayi mata ba amsa ratsawa tayi zata fita ta bar mai dakin ya riƙo mata hannu fisgewa tayi tana cewa bana bukatar ganin ka nace maka ka fitar min daga daki wannan wacce irin kaddara ce ba za a bar zuciyar mutum ta huta ba daga wannan sai wannan ba ruwan Ubangiji ke kika saka kan ki a ciki zama tayi a ƙafa tayi shiru zuciyar ta na tsananin bugawa daguwa tayi taga ya fita jan tsaki tayi ta rufe kofar ta dakyar ta samu tayi bacci washegari wanka tayi ta shirya cikin riga da wando amma wandon falazo ne Golding colour da riga milk colour stocking dinta gashi wuyan rigar up-shoulder ne ko yaya tayi motsi ana iya hango kirjinta ɗaukan jakarta tayi ta riƙe a hannu ta yafa mayafi a kafaɗa takalmin kafar ta hil ne shafa kanta tayi shaf ta manta da wula kawai sai ta saka mayafin ta a ka tafiya take tana taku dai-dai har ta fito Parlour kallon rashin fahimta dada take mata tace '' Khadijah sai ina kuma...?, kallon a gogon hannun ta tayi tace '' zooroad..., ban gane zaki tafi zooroad ba dafe kanta tayi tace '' ya Allah dada zanje na bude shagona fa.., gutsurar tufa tayi tana ci tace '' Allah ya shirye ki haka kurum kin zamar da kanki na miji in banda zamani ina mace ina buɗe shago ta zauna..., ɗago wa za tayi suka haɗa ido da altab yana cin wainar shinkafa da miyar a gushi kau da kanta tayi daga shi har rufa'i wallahi ba wanda zata gaisar tace '' Dada ba laifi bane mace ta nemi halak ɗin ta kinga Allah ya sakamin albarka na har shagon saloon na bude...tun ina yin online na buɗe shago.., wallahi kuwa da ace miki zaune gari banza gwara ki nemi abin yi cewar rufa'i ya tsuna fuska tayi ɗagowa tayi jin sallamar blood line hugging din sa tayi tana cewa good morning blood line morning beautiful lady cika shi tayi yace '' beauty me ya samu wayar ki ina ta kira a kashe.., ta sami matsala yanzu ma wata zani na siyo kafin na buɗe shagona a'a nasreen ina zuwa haka zuwa fa anjima za a kawo amarya cewar adda asma murmushi tayi me cike da ma'anoni ta samu damar kuntatawa altab tace '' yanzu aunty me ya hadani da kawo amarya na tafi neman arziki ko da yake duk neman da kake baya cire ka daga zargin mutane ba.., hannunta khalil ya kama yace '' muje na siya miki wata special gift happy birthday to you.., zaro ido tayi shaf ta manta da yau birthday din ta tace '' wallahi na manta abubuwan sun min yawa nagode sosai.., idanuwanta duk ya ciko da kwalla karki damu aini ina sani ummi ma tace '' na taya ki murnar zagayowar ranar haihuwar ki..., da sauri ta kallesa cikin mamaki tace '' anya kuwa..., Wallahi da gaske nake kinga sakon da ta turomin ture wayar tayi tace '' basai na gani ba da motar ka za mu tafi ko da tawa...?, farin cikin ki shine nawa murmushi tayi tace '' nima haka.., fita sukai a tare suna hira adda asma ce tace '' Allah sarki khalil komai yana yi domin ya kawar mata da damuwar ta.., taɓe baki dada tayi tana cewa kinga alamun ta damu ne kike faɗar haka dada abin fa zai mata ciwo wallahi kawai dai tana kawar wane dan ma duk tarin kawayenta ba wanda ta gayyata wasu ma basu san za ayi bikin ba... Wannan shine rufin ashirin da Ubangiji yayi mata da fita ma sai ta gagareta dada ta faɗa cikin takaicin abin addu'a nasreen take buƙata Allah ya kawo karshen abin nan cewar adda asma tabe baki altab yayi yana tashi binsa rufa'i yayi yace '' dada sai anjima.., kun gama cinye mata waina ai dole kuce zaku tafi dariya rufa'i yayi yana cewa adda asma kenan kuɗi muka bata tayi mana tambaye ta idan karya muka yi a'a abin harda sharri ni ko ficika ba su bani ba Dada wane be san halin su ba sai addu'a barin kar wannan mutumin yaji labari wallahi ni tausayawa yarinyar nan nake auran soja ba dad'i wallahi daman gashi ga halinsa wallahi kuwa kawai dai Allah ya saɓa hali cewar adda asma Wannan kenan wani shu'umin murmushi take saki tun ɗazu ko banza ta nuna mata ƙarfin ikon ta wace mata barno gabas ce kaɗan ta fara gani wallahi mamy da sauri ta jiyo tace '' basma lafiya kika shigo min ba ko sallama..., wallahi nayi kece dai baki ji ba kina tunani ajiyar zuciya ta sauke tace '' to me kika zo yi...nan ..?, wani ne yazo a baƙar mota yace '' na ƙira ki..., cikin sauri tace '' okay na gane ce ne mai muyi magana ta waya.. har ta juya zata tafi da sauri tace '' mata tsaya kawai tafi na ki guri za mu yi magana ta waya amma mamy wane shi...?, basma bana hana ki irin wa'yannan tambayar ba maza maza zo ki wuce ki bani guri fita basma tayi batare da tace komai ba wayar tace tayi ringing da sauri ta dauka tace '' aminiya ta wallahi ban taɓa zaton wannan shirik namu zai yi ta siri ba sai gashi lokaci ɗaya mun burkita zuri'ar me tangaran..., wata shu'umar dariya kawar tata tayi tace ''ai idan har zaki ci gaba da ɗaukar shawarata to wallahi kowa sai kin gyara masa zama..., limshe ido tayi tace '' ai kuwa dana fi kowa murna wallahi..., sallama sukai sannan ta kashe wayar shaf ta manta da batun me jiranta a waje Wannan kenan Cikin nishaɗi suka fito daga wajen saida waya tsayawa yayi yace '' ni zan koma akwa wanda zamu haɗu dashi anan ga shi can yana jirana..., langwaɓar da kai tayi tana cewa gaskiya naji dadi sosai wallahi Nagode Allah ya bar zuminci amin ya Allah ya faɗa yanayin gaba buɗe motar ta tayi ta shiga a hankali ta fara tafiya har ta isa zooroad fito da mukulli tayi ta buɗe shagonta tana shiga jazz da shi da pretty suka shigo kallon su tayi tace '' Allah ya rufa muku asiri baku daki gurbi ba ban dade da zama ba.., zama sukai jazz tace '' lallai kam jiya nai ta kiran wayar ki switch up me ya faru bayan mu gama tsara guri har 2:49 ina club..., BAƘIN SHAFI oum yasmeen EPISODE 3 Previous to the last page '' lallai kam jiya nai ta kiran wayar ki switch up me ya faru bayan mu gama tsara guri har 2:49 ina club..., Continue ajiyar zuciya ta sauke tace '' wayata ce ta lallace.., fito da syrup pretty tayi ta buɗe tace '' Allah ya kiyaye gaba.., amin ya Allah amma dan Allah kar ki sha ba zai yiwu ba customer's su zo min ba ana kallon ki ki ta tun ɓele.. haba nasreen ya kike mana yawa ne yanzu ni nake tunɓelen yawa wata akuya ko tinkiya Pretty ta faɗa tana kai Syrup bakin ta tunda ta saka shi tas sai da ta shaye shi ta wurlar da kwalbar fashewa tayi da sauri nasreen tace '' wallahi sai kin share min anya kuwa ina cikin nutsuwar ki..?, ina fa take cikin nutsuwar ta sunyi faɗa da bash Jazz ya fada yana dariya tashi nasreeen tayi ta cire mayafinta tace '' ya kake mata dariya..yau dara fa ba dad'i wallahi tama yi kokari da ba faɗi ba an kwashe ta.., Nasreen kenan ya ali yaga ali fa akai ya fito daga dakin hotel ta fito ina abatun damuwa shine fa har da marin budurwar indai takaice miki labari kaca kaca akai har sai da yan sanda suka shiga cikin lamarin yanzu bashi ba ita shine fa ta shiga cikin wani hali to mene abin damuwa tunda ke kin aikata shima ya aikata ga ani na gaskiya ba abin daga hankali ko ki damu baza ki gane ba wai mutumin nan fa yan sanda ya faɗa suyi mana tsakani da shi kin ji fa wani rainin hankali tashi tayi ta zauna kusa da jazz ta kwashe da dariya shima dariyar yake yace '' wallahi ban taɓa ganin original yan iska ba irin bash da pretty yau ya saba kai ta gurin yan sanda nifa gani nake kamar fa ya raina su wallahi.., buɗe fridge tayi ta ɗauko lemoka ta miƙa musu itama ta buɗe tana cewa gaskiya nima ban taɓa ganin haka ba kar kai mamaki dan da wani watan su koma su jone wallahi kin kai da nisa ki basu nan da zuwa sati ki gani duk yadda kike tunanin su to wallahi sun wuce gurin cewar jazz yana shan lemo ita dai pretty tayi shiru domin ba a cikin hayyacinta take ba dan ma dai Allah ya rufa asiri bata surutai beb yau fa naga tsohon dan iskan nan sabeer ke kinga kallon da ya jefe ni da shi...kin fa cool esay ce take faɗamin ya fasa auren ki yanzu maganar ake tayi a media da sauri ta ɗago lemon da ta kurɓa kasa haɗewa tayi ta furzar dauko wayar sa yayi yace '' kalli.., da sauri ta karɓa idan wata futsararriyar yar tiktok sanye da towel ta riƙe brush take cewa Update update jama'a har zan shiga wanka naji wannan labari nace ba zan bari ta wuce ba tare da na faɗa muku ba asirin dai NASREEN MAI TANGARAN ya tonu ana ƙoƙarin daura auren ta miji yace ya fasa saboda yar iska ce akwai video ta duk me so ya je internet yayi searching wannan account din saboda gudun yi min blocking account Dina Zan dora muku anan idanuwanta ne suka ƙada sukai ja sabeer ya gama cutar ta tsakanin ta dashi saidai Allah ya saka mata wayar ta ce tayi ringing da sauri ta dauki jaka ta buɗe ta dauko ganin sunan baffa rado rado gaban ta ne ya waɗi hannun ta na rawa ta dauka muryar ta na rawa tayi sallama a wannan karon ba be amsa ba daga jin muryar sa yana cikin tsananin baƙin ciki yace ''Duk inda kike ki zo parlour ina son ganin ki.., jin sauti kamar ya kashe ta kalle wayar kallon jazz tayi tace '' su mary za su zo yau naga ba su zo da wuri ba zan je gida ana son gani na.., Okay ba damuwa sai kin dawo ɗaukan jakarta tayi da key ta fita cikin sauri ta buɗe motar ta ta shiga gudu ta dinga sharadawa har ta isa gida fitowa tayi ta fara knocking gate din tana maida hannunta za ta ƙara bugawa me gadi ya buɗe shiga tayi yana mata magana ma da yake hankalinta ba akan sa yake ba har ta isa part din baffa tana tunani bata san me ya saka sa kiranta ba shiga tayi bakinta dauke da sallama gabanta ne ya waɗi ganin daddy abbey abban yaya uncle Yusuf jikinta ne ya ƙara sanyi ta ƙarasa zama tayi wani kallo baffa ya watsa mata tare da miƙa mata waya bata san me yake nufi da haka ba hannunta na rawa ta amsa ɗagowa tayi suka hada ido da Altab sai a lokacin ta fahimci wa ya wura wutar kallar wayar tayi gaban tane ya waɗi ganin akan a ke maganar amma duk wanda ya tsaya yayiwa... Video kyakkyawar fahimta ba ita bace ba ɗagowa tayi tace '' yarfen yan media ne wallahi bani bace ko daban ba kunyar mutane ko dan kunyar Ubangiji na bazan so na aikata abin da zan zo nayi dana sani ba wallahi masu editing ne suka haɗa wannan baƙin shafi suka so su yi min amma kai wa vedio kallo na tsanaki bazan so na zubar da mutuncin gidan nan..., Rufe min baki daman ke baƙin ki baya mutuwa to daga yau kune yayana ku sheda shima zan kirawo mahaifinta na sheda mai na cire hannuna akan ta ke Khadijah kema ban yarda ko kwayar shinkafa ki bata ba tun da bin da take kenan ta ci da kanta... tana so ta ƙara maimaita mana abin da ya faru shekarun baya idan shekarun baya na iya ɗaukan tension din abin da ya faru to a wannan karon ba zan iya dauka ba kamar yadda na zare hannu akan ta kuma ku zare rayuwar duniya darasi ce wata ran zata koya mata darasi wanda zai zauna a kanta har abada tunda yanzu darasin da Ubangiji ya nuna mata be mata ba har taje ta ƙara wani abun Baffa kai hakuri idan hankali ya gushe tunani ke dawo da shi be kamata mu zuba mata ido mudai ci gaba da yi da baki da kuma addu'a har Allah ya dawo da ita kan tafarki Cewar dada Wani kallo yayi mata ya ɗauke kai ya Khalil ne yace "Baffa wallahi nasreen baza ta taɓa aikata haka ba kawai dai abin da nasani tana tare da mutane nan banza..ni zan aure ta.., wallahi ban yarda ba ai daman idan ka ga kare na shinshina takalmi ɗauka zai yi to wallahi ban yarda ba wata kila ma yanzu haka ma wata kila tana ɗauke da cutar kanjamau.. Cewar mamy tana wura hanci shaf idanuwanta sun rufe ashe harda man tan gidan aka haɗa taron ƙasa tayi da kai tace '' ko baki faɗi haka ba zan taɓa auran sa ba ya khalil na gode da irin karamcin ka a gare ni..., Cikin baƙin abba yace '' futsararriya ana magana kina mai da wa karya tayi ba ta hanyar ake samun cutar ba wallahi kin zame mana baƙar kadara..., ko ganin gaban ta bata yi fita tayi bata tsaya ko ina ba sai a wajejen motar ta bude wa tayi ta shiga ashe ya khalil ya biyo ta ganin yana ƙoƙarin tsai da ita ta fisgeta yau zata aikata abin da kowa yake fatan aikatawa yau zata sama duk abin da suke cewa tana yi basu da fahimta ne taya zasu ga wannan video suce ita ce a gaban wani joint ta faka ta fito shiga tayi wajensa ta zauna a gaban me sai da wine tana zuwa ya jera mata kwalba biyar ya buɗe wata ya zuba mata a glass cup ɗauka tayi har ta kai baƙin ta sai kuma tunanin ta da ya gushe ya dawo a hankali ta furta Ya ayyuhalladhina amanu innal khamra wal maysira wal ansaba wal azlamu rijsun min 'amali shaytani.., sauke wa tayi ta miƙa mai ATM ya cire kuɗin wacce ya fasa mata ta fito daga gurin jikin'ta na rawa cin karo tayi da ya khalil cikin rawar baki yace '' nasreen daman kina shan giya...? Ina ilimin ki da tunanin ki yake me zata amfanar da ke abin da Ubangiji ya hana shi kike yi wallahi a yanzu kin fara saka min shakku akan ki.., kai ta girgiza tace '' I went because I drank, but one time God brought back my thoughts that I didn't drink.., wani kallon rainin hankali yayi mata sannan ya juya batare da yace komai ba ya shiga motar sa cikin sauri ta ƙarasa amma tuni ya ja ya tafi shiga tayi cikin motar ta ko gabanta bata iya gani a da tayi niyar daukan mataki akan wa'yanda sukai mata wannan abu a yanzu kowa da kowa ya zare hannunsa a kanta komai ta fice mata a rai tana fatan Allah ya ɗauki ranta ta huta daman maganar uwa da uba ba a maganar su suna can wata duniya ma banbanta suna can suna rayuwa successful ba wata damuwa ita dai sun ruga sun cutar da ita sun haifeta ta hanyar da bata kamata ba gashi nan rayuwa sai watan gaririya take da ita.. a hankali ta fara tafiya cikin gushewar hankali ji tayi ta ci karo da wani abu ɗaga nan bata ƙara sanin inda take ba gashi titin nasrawa JRA ne ba mutane sosai mota ma zuwa take fit ta wuce tamkar walkiya raka raka gaban motar yayi kanta ya bugu da glass din taka ya fashe BOMFAI JAR.... Sosai suka shiga harkar idimar abinci saboda masu kawo amarya suna kan hanya adda asma ce ta ajiye flask din hannunta tace ''maman iffa dan Allah kinga dawowar nasreen wallahi tun dazu zuciya ta ƙasa nutsuwa da fitar da tayi bata cikin hayyacin ta be kamata a barta ta fita a wannan lokacin ba duk kuwa irin laifin da ta aikata a wannan karon baffa ya nuna tsani da yawa wallahi ban taɓa zaton zai yi haka ba..., to ke mece damuwar ki ina cewa iyayenta ma sun watsar da ita kina ga dan tashin nuna mahimmancin auren yar su ba wanda ya zo a cikin su gwara shi abban sufwan ma ya turo da kuɗi mahaifiyarta fa wa yasan inda take tunda iyayenta suka kawo ta suka wuce Cameroon sun ƙara waiwayar ta dan haka ba ruwanki da duk wata sabgarta ai daman buri yayi kama da mutum ke kinga uban shagon da ta bude a zooroad ta fake da bashin baki taci ubanta ne ya bata kudin da ta bude idan ba karuwanci take ba innalillahi wa'inna'ilaihir raji'un kinga zato zunubi ne wallahi ta nuna min komai yanzu ma ta kusan biyan su dariya dukkan su sukai maman iffa tace '' lallai ta mai da ke wata bita can yanzu mene ba ayi fake domin ta rufe mutane abokin dan iska Dan iska ne wallahi ga mutanen da take yawo da su baki ga uban birthday din da tayi ba ko ina shi kaɗai wallahi ya ci a zarge ta nifa mamy tayi min dai-dai da tace danta bazai aur ta ba ko nice abin da zanyi kenan yar iska kawai sai aikin girman kai.., Maman arfa tace '' ai wallahi gwara da suka budewa shegiya aiki yau ma naji ance za aje a kwaso kayan da aka jera a gidan da za akaita sun dauki kayan lefen su ma..., kai adda asma ta girgiza ta fita yan kawi amarya ne suka zo da uwar gararsu bayan an Kaita gurin su Dada suka bada amanarta sannan suka kaita gidan ta gaba da su sosai.. sai satin gidan nata suka ahaka taro ya watsai sai rufaida da ƙawayenta sai washe baki take amma ƙasan ranta , ta kasa nutsuwa da kwanciyar hankali zare jikinta tayi daga na cikin kawayenta ta shiga wani daki ta murza key dauko wayar ta tayi bugu ɗaya aka ɗaga ƙasa ƙasa tayi da muryar ta, tace '' wallahi anty tsoro nake karfa ya gane.., saurarwa tayi domin jin me aunty nata zata ce ajiyar zuciya ta sauke tace '' duk abin da kika ce insha Allahu zan kiyaye amma wallahi duk randa ya gane a kwai matsala aunty.., da hallacan rufewa mutane baki ke da kanki kikewa kanki mugun fata kinga sai an jima sauran kuma ki ƙiyin abinda na saka ki wallahi ke ta dama ba ni ba kinsan irin kudin da na ɓatar akan auren nan ita kanta babar tasa, zata shiga uku mudai gama da shi ita duk me sauki ce Insha Allahu aunty zan kiyaye karma ki kiyaye tana gama faɗar haka ta kashe wayar ta mai da wayar ta tayi inda ta ciro ta ta gyara kanta ta fito yauwa tun ɗazu nake neman ki sara ta faɗa tana kunna turaren wuta a bonner dafa kanta tayi tace '' na dan shiga can daƙin..nayi waya hayaniyar ku ba zata bari naji komai..ba, dariya suka saka sara tace '' amarya bakya laifi ko kin kashe dan masu gida kedai faɗi gaskiya ko kin matsu muyi gaba ango ya shigo..?, tura ɗauro gaban goshi tayi tace '' ku kwana mana ni me ce damuwata..., wallahi karya kike kina da damuwa ke ɗin ni wallahi nayi mamaki ma da har aka fara bakin nan cikin sauri rufaida ta tari numfashin Maryam tace '' haba dan Allah ku dinga sanin zancen da zaku yi yanzu me ne abin yin maganar nan anan salon wani yaji kamar baki san komai ba.., dariya sarah tayi tace '' kura da fatar akuya wahainiya me canza siffa an zaton wuta a maƙera sai a ka ganta a masaƙa..., ke yi shiru kamar knocking naji ana yi ko gaskiya kamar shi ake yi koma ɗaki wata kila yan uwansa ne mu zamu tare su da sauri ta koma har tana tuntuɓe buɗe kofa sara tayi aunty lubna da aunty Aisha su suka shigo suna ɗaga kai sama.. kusan halin su ɗaya da umman yaya wato mahaifiyar altab a kwai jin kai da isa da sauri Sara tace '' bayin Allah ku suwa ye kun shigo mana kai tsaye kamar baku ga mutane a parlour ba ba gaisuwa balle sallama...?, wani kallo aunty lubna tayi wa sara na sama da ƙasa sannan ta ja ɗan ƙaramin tsaki tace '' da hallacan matsai ko na bige ki ke kinsan mu suwa ye to Kannan ango ne.., Maryam ce ta, ta tashi tace '' Allah ya saka uwar sa ce taya za ku shigo mana ba sallama ko wayanne irin gidadawa ne..?, chingum ɗin bakin ta , A'isha ta tofar tace '' ke har awa kike wannan maganar to wallahi idan yau muka ga dama sai kun yi kwanan cell kinga ko abin da nake umma ta fahimta ta toshe kunnen ta dangin matsiyata ga kayan ɗakin nata zo mu tafi.., ta ina zata gane aminci ya rufe mata ido cewar aunty lubna jan hannunta A'isha tayi suka fita sai jin karar tashin motar su sukai fitowa rufaida tayi tace '' gwara da kukai musu haka yan iskan karya wallahi sai na gyarawa kowa zaman ta.., dariya suka saka da shewa POV ALTAB.... Dan rainin hankali ko ka gama zumu ɗin ne kamar baka son barin gidan nan tun ɗazu nake ce maka an kawo ta ka haɗa kayan ka zuwa sallar isha sai mu kai ka amma kayi buruss Cewar RUFA'I dan murmushi yayi shi kaɗai yasan me yake ji a jikin sa ba daban biyayyar mahaifiya ba da son kaucewa zaɓen tumin daren da yake neman ya yiwa kansa ba zai iya auren rufaida ba duk da ba abin da ta rasa ilimin addini aiki da shi tsoron Allah ya khalil ne ya shigo a birkice zama yayi ya na sauke gauran numfashi.. Zuciyar ta kasa aminta da abin da idanuwansa suka gani zancen ta yake so ya gaskata amma me ya ga fa takai bakin ta innalillahi wa'inna ilaihir raji'un Allah ya yaye mai wannan baƙin shafin da ya lulluɓe kwakwalwar sa wannan wacce irin ƙaddara ce kallon sa altab yayi ya taɓe baki wani irin haushi sa yake ji tashi yayi yace '' malam lafiya ka shigo min ba ko sallama..?, idanuwansa ne suka ƙada sukai ja haka idanuwan altab akwai abin da yake hangowa a idanuwan altab amma tunanin da hangen nesan sa sun kasa hasaso mai mene wanne abu ne kamar yadda idon altab yayi ja haka na Khalil kallon ido cikin ido sukewa junan su cikin jin zafin abin da altab ya aikata khalil yace '' Wallahi Allah altab ka bani mamaki yan zu da ka nuna musu wacce riba ka samu ni nasan wace ce nasreen na Fika sanin ta.., Cikin ƙaraji altab yace '' wallahi karya kake yarinyar da na raina da hannuna yarinyar da tun tana cikin jini aka danƙa min ita a hannu na.., tashi khalil yayi tamkar zai shiga jikin altab yace '' wannan duk abanza tunda baƙa kokarin sakata farin ciki baka kokarin gushe mata damuwa ni nayi rawar gani akan nasreen dan nayi mata maganin damuwar ta na haɗa wata mata da Allah akan ta zama mahaifiyar nasreen ta nuna mata so tamkar mahaifiyar ta ta jawota a jiki sai dai kash tun kafin a je ko ina matar ta gajiya...nasreen bata cancanci tsana daga gurin ka ba har da zaka tun zura baffa yanzu dan an hanani aurenta sai me idan har nasreen mata ta ce zan aure ta..., Karya kake idan har ina numfashi a doron duniya baza ka taɓa auren ta ba da sauri RUFA'I ya shiga tsakaninsu yace '' haba khalil me kuke yi haka kun tashi tare komai naku tare kuna yara ba kuyi faɗa ba sai yanzu yau fa ranar farin ciki ce a gare ku.., Ni wallahi ba ranar farin ciki bace rana mafi muni a guri na kasan irin halin da ya jefa baiwar Allah nan kasan a halin da na barta shi ya zo yana rayuwa kamar ba shi ya saka ta ba bara kaji RUFA'I idan aka bawa ALTAB bindiga ya harbe nasreen tsab zai iya harɓe ta domin baya kaunar ganin ta a doron duniya A'uzubilla me kake faɗa ne haka..?, Cewar rufa'i yana riƙe altab da yake kokarin kai wa khalil duka Ja da baya khalil yayi yace ''sake shi RUFA'I ce mai akai shi ka dai ne me zuciya..., Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un wai me ya shiga kan ku ne ina raba ku , kuna ƙoƙarin yin faɗa da hankalin ku da tunanin ku me maƙon ku kuyi wa wani faɗa kune yau da kan ku kuke yi kar ku manta fa lokacin muna makaranta mahaifiyata Allah ya jikanta da rahama har kwatance take mun da ku amma yanzu kune kuke neman illata junan ku Rufa'i ya faɗa ya share hawaye jikin su ne yayi sanyi musamman Khalil juyawa yayi zai fita sai kuma wayar sa tayi ringing ashe akan kujera ya ajiye ta komawa yayi ya ɗauka ganin baƙuwar number ya ɗaga tare da akarawa a kunne sallama yayi ba tare da wanda ya bugo ba ya amsa sallamar sa ya zarce da cewa kai ne khalil...?, Cikin sauri yace '' eh nine me ta faru.., zan turo maka address kazo asibiti yar uwarka tayi hatsari ana buƙatar ku ehyi me kace kit ya kashe wayar kallon sa rufa'i yayi yace '' me ya faru..?, nima wallahi na rasa gane wa me ke faruwa wai zai turo min address yar uwata tayi hatsari ko nasreen ce nima haka nake tunani domin na barta a wani hali sai da na tawo nayi dana sanin tawowa amma bara na ƙara kiran shi danna kira yayi message ya shigo wayar sa da sauri ya bude a fili ya shiga karanta wa yace Unique Care Al-Haramain Hospital Plot 297 Jido Layout, Danladi Nasidi Housing Estate Mariri da sauri rufa'i ya karɓi wayar karantawa yayi ka be ƙarasa ba ya karɓi wayarsa ya daka a aljihu ya fita cikin sauri ya ke komai mantawa da yayi mukulli baya jikinsa tsaki ya ja ya koma part dinsa ya dauko key ya fito bude mota yayi ya shiga yayi mata key ya kusan buge me bawa shukoki ruwa sai kaucewa yayi ganin a yadda yake Sahara gudu a cikin gidan ya bawa ma'aikatan gidan tsoro sudai sunsan baya shaye shaye buɗe mai get me gadi yayi dai-dai sako hancin motar su lubna sai dai sune suka kauce mai amma shi kamar ma be gansu ba ko da ya hau titi sharara gudi ya dinga yi har ya isa asbitin parking yayi a waje domin ba zai tsaya jira ba har a ba shi katin shiga da mita ayi checking ta ƙaramar kofa ya shiga wayar sa ya fito da ita daga aljihu kiran mutumin ya shiga yi amma ba ɗauka ƙara kira yayi sai a na biyar sannan ya ɗaga kai tsaye yace mai kana kina gani nan a cikin asibitin...?, Faɗama masa yayi nan da nan ya mai da wayar aljihu ko tsayawa kashe wayar be ba ya shiga reception hannun sa na dama ya shiga akwai hanya miƙe hanyar yayi har emergency room wuru wuru ya fara can ya hango mutumin yana zurga zurga cikin sauri ya ƙarasa yace '' tana wanne daki ne..?, kai hakuri yanzu likitoci na kanta ta bugo ne akai nima wucewa na zo yi na ganta na kaita wasu asiti saboda rashin dan sanda ba a karɓeta ba shi ne na kawo ta nan da ita saboda abin yayi yawa zato suke ba hatsari bane jingina da bango khalil yayi ko me ya faru da nasreen da sa hannun altab shi ne sanadin komai da ya faru da ita kasa cewa yayi sallar magariba aka kirawo dole ta saka ya tafi yayi salla bayan ya idar ya tsaya yayi mata addu'a sannan ya dawo lokacin wani likita ya fito yana share zufa da sauri khalil ya ƙarasa gunsa yace '' yaya take kun shawo kan matsalar...?, dafa shi baturen yayi yace ''don't worry everything will be fine.., kai khalil ya gyaɗa yace ''I can go in and see her.., yanzu za a fito da ita a Kaita wani dakin zaka iya shiga amma kafin nan ina son ganin wanda ya kawo ta sai a lokacin khalil ya lura da mutumin nan baya nan yace '' kawo ta yayi nine dan uwanta shi temaka mata yayi.., Okay biyo ni office binsa yayi har office dinsa zama yayi sannan yace '' a'a ga guri ka zauna mana..., zama yayi zuciyarsa na tsananin bugu buɗe laptop likitan yayi sannan yace '' yar uwar ka ta kamu da cutar ciwon zuciya me tsanani i am sorry to say da sauri khalil ya ɗago yana hango baƙar fuskar altab duk shi ya sakata a cikin wannan hali ci gaba da cewa likitan yayi idan ba ayi taka tsantsan ba ko wanne lokacin zuciyar ta zata iya bugawa sannan ta kamu da cutar mental processing disorder amma wannan ba wata matsala bace hankali ana tafiyar fa ita yadda take so zata war ware idan har kun lura za ku ga akwai abubuwan da take selecting idan kunyi kokarin da raba da shi ciwon zai ci gaba har ya girma ya zame mata matsala Rubutu yayi a takarda ya miƙo amsa yayi yayi mai godiya magani zai siyo sannan ya biya duk wani kuɗi da aka ka she mata wayar sa ce ta fara ringing cirowa yayi sunan mamy ya gani raɗa raɗa akan screen din wayar sa yasan yanzu za su iya samin labari wata kila saboda haka ta kirawo shi ɗan haka be ɗauka ba... A yanzu nasreen bata da wani gata da ya wuce nasa insha Allahu ba zai taɓa barin ta tayi kuka ba fita yayi yaci ka ciɓis da mutumin da kawo ta hannu ya miƙa mai yace '' bawan Allah kai hakuri a dazu bana cikin kwanciyar hankali nagode nagode Allah ya saka da alkairi ya baka abin da kake nema duniya da lahira..., Ba komai ai yiwa kaina wallahu nayi maka wannan uzurin kallo ɗaya za ai maka a san baka cikin kwanciyar hankali ya me jiki aa nine da godiya me jiki alhmdllh komai ya zo da sauki kai masha Allah motar ta tana gurina zo muje na nuna maka inda take... KU HANZARTA PAYMENT DIN KU BAZAN DADE INA FREE PAGE BA DOMIN SHIGA PAID GROUP ZAKU BIYA 500 Amina Muhammad Alhasan opay 8141785374 Ku turo da sheda ta wannan number 09061890481 ƁAƘIN SHAFI EPISODE 4 A'a bara na haɗa ka da bakanike ni a kwai inda zani tunda kacs motar ta samu matsala sai ya tafi da ita ya gyara ta gaskiya ta samu matsala ga ban motar duk ya lotsai ba damuwa kira shi sai na je da shi ya dauki motar waya ya khalil ya ciro a aljihunsa yace '' to sai dai ban san sunan ka ba.., dariya yayi yace '' nima ban san sunan ka ba ni dai sunana HAFIZ JIBRIL MAI DAWA..., ƙara waya yayi a kunne yana cewa '' KHALIL HAMZA HUSSAIN MAI TANGARAN.., to nayi saving number ka kai ma sai kayi tawa insha'Allah zan ƙara kawo muku ziyara na ga jikin ta wallahi na tsorata da ganin halin da ta shiga a lokacin da na kawota jini jiƙa min rigata yayi Okay ba damuwa mun gode sosai wallahi sauke wayar yayi yana cewa kaga be ɗauki kiran ba rana na ƙara yi mai ko Allah zai saka ya ɗaga kaga dare na ƙara yi Haka ne wallahi cikin sa'a ya ɗaga karawa yayi a kunne ya danna matsa gefe ci gaba da danna wayar sa Hafiz ke yi har ya gama wayar ya dawo yace '' ga shinan zuwa ni zan tafi phamarcy na siyo magani.., okay Allah ya kawo shi lafiya sai ka dawo amin ya Allah ya ce yana fita da ga gurin ba ƙaramin bill sukai mai ba haka ya dawo hannun sa riƙe da ledar magani daidai karasowar makanike dan haka juyawa yayi yana cewa ka ganshi ya kirawo ni yana waje zo muje sai ku tafi wayar sa hafiz ya mayar aljihu suka fara tafiya har wajen musabaha sukai da me gyaran mota sannan ya juyo ya barsu tare da man ya riga da ya gama yi mai bayani kai tsaye dakin da aka kwantar da nasreen ya shiga tana kwance ban da na'urar da aka saka mata ke motsi alamar tana da rai ba abin da ke motsi a jikinta kanta an nannade mata shi da bandeji ga oxygen da aka saka mata limshe ido yayi ya jingina da bango a lokacin wayar sa ta ƙara ringing wannan karon adda asma ce ɗagawa yayi cikin tashin hankali tace mai har yanzu fa nasreen bata dawo gida ba ko zaka bincika kaga inda take kallo yabi gadon da take kwance yace '' tayi hatsari yanzu haka ina asibitin da aka kwantar da ita amma da sauƙi..., ajiye Sultan tayi da yake hannunta gaban ta ya yanke ya wadi tace '' innalillahi ya akai haka ta faru...?, adda asma ina zan sanu nima kirawo ni akai aka ce ga halin da take ci wallahi kin ganni nan jikina duk ba dadi ga ta nan ko motsi ba tayi sai na'urar da aka saka mata ita ke motsi amma baya ga haka ba abin da ke motsi a jikin ta innalillahi wainna ilaihir raji'un Allah ya bata lafiya bara na sanar da su cikin sauri ya dakatar da ita ta hanyar cewa adda asma kin manta dazu me ya faru...? Kinga wanda ya damu da ya neme ta ko yasan halin da take ciki wallahi abar tausayi ce NASREEN farin ciki muka kasa bata shi ya saka take tare da mutanen da take tare da su tafi jin dadin zama da su fiye da kowa wallahi tun ba yau ba ma fahimci haka ɗebe mata kewa suke shi ya saka take zama da su amma Allah yaye wannan baƙin shafin da ya lulluɓe zuciyar mu da idanuwan mu Amin ya Allah zan dai sanarwa da daddy Sultan idan zai faɗa musu ya faɗa muku cewar adda asma Okay hakan yayi sai an jima turo min address din gobe zan zo Insha Allah tu zan turo miki ya faɗa yana kashe wayar zama adda asma tayi ta zuba ta gumi kasa motsi tayi har sai da uncle Yusuf ya shigo firgigit ta ɗago kanta, ta kallesa tace '' sannu da zuwa..., zama yayi ya kalleta yace '' tunanin me kike..?, Nasreen tayi hatsari yanzu haka an kwantar da ita a gadon asibiti cikin halin ko in kula yace '' wannan shine abin damuwa..har ya sakaki tunani..?, runtsai idanuwanta tayi tace '' nidai alfarma ɗaya na ke nema gobe insha Allahu zanje gurin ta idan na dubata naga halin da take ciki..., ba a gaban ki baffa yayi magana ba wato ke zaki fara karya mai dokarsa ko ma me ya sameta ba ita ta waja kanta ba to wallahi ba ruwana idan kika je dana nan kiyi gidan ku sai na neme ki da sauri ta ɗago sai dai ƙasa magana tayi ganin har ya fara hawa kan staircase kwantar da kanta tayi a kan kujera rasa wanne tunani za tayi ko wanne ta kamo sai taga be mata ba... ______________⁠❥ ALTAB ya kamata fa mun binciki khalil ka gansa shiru har ƙarfe tara kai kuma baka da alamun tashi mu raka ka wasu daga cikin abokanan mu har sun tafi Za fafe altab yace ''Rufa'i yau kai ko maye ne sai ka kyale ni dan wallahi bazan ciwu ba tun ɗazu nake faɗa maka ba inda zani ana dole ne..., Ƙawayen amarya fa na jiranka suma suna so su tafi gida karma su tafi su kwana anan banu da issue da shi cewar altab yana gyara kwanciya tab abin na altab yau a zemin ne cewar wazir zama rufa'i yayi yace '' baƙara mi ba ni ta taɓa jin wannan abu na rasa gane inda ya dosa ya zame min bai bai wannan wanne irin baƙin shafi ne ya lulluɓe tunanin sa .., wayar sa ce ta ƙara ringing ɗauka yayi ya ja tsaki yayi rejecting din kiran ya saka wayar sa a playmode can kuwa a marya ta gaji da haɗuwa sai zabga kamshi take amma zuwa yanzu ciyar ta ta ci gaba da bugun da take ko wacce sa'ar a gogo da zuciyar ta yake bugawa barin yanzu da taka 10:58 na dare karfa altab so yake ya kunya'ta ta a cikin ƙawayenta baya dauƙin ta kamar ba sabon aure sukai ba.. Sarah ce tace '' rufaida dare fa yana yi ba ango ba dalilinsa..?, daurin kanta ta cire ta ɗora a kan gado tace '' sara gaskiya ina tunanin lafiya ba na kirashi amma ba ai picking.., cije lips din tayi ba tare da tace komai ba maryam ce ta shigo tace '' sweet kinga ba ango ba dalilin sa ni wallahi abba na ke tsoro kinsan halinsa yau mukai da shi zan dawo wannan ma zaman bikin nan fa da nayi ce wa nayi na tafi gidan kaka shi ya saka nake sharafi na..., wallahi Maryam maganar da muke da sara kenan ko zuwa za kuyi ku bincika rufaida ta faɗa idonta na ƙawo ruwa ba ƙaramin ado ta canca ɗaba amma duk fuskarta ta caɓe kamar ba a AC take ba da yake tana da oil face da sauri Sara tace '' haba rufy yawa wata mara gata da galihu taya za ayi mu tafi neman ango ranar daren farkon sa me mene sunan mu ke baki da mahimmancin da zai yi zumuɗi a kan ki komai.., dafe kanta tayi tace '' ko su lubna sun fada mai abin da ya faru ne kinsan shi da son yan uwansa..., ba mamaki amma taya zai tuzarta ki ta wannan hanyar bayan ya san tare kike da kawayen ki gaskiya kune mo wani dalilin ba wannan ba cewar Maryam Maryam nima abin da na gani kenan rufy ta faɗa tana kwanciya a gado yawa wacce kwai ya fashewa a ciki tab tun yanzu kin fara gamuwa da shika shikan rashin mutuncin na miji ina kuma da zama yayi nisa gun gogu da juna Cewar sara ta faɗa tana taɓe baki ai ga irin ta nan sai da nace miki kada kiyi aure kina waje mene bakya samu ina cewa ma sai dai ki kunsawa matan auren takaici amma tunda kika kyalla ido kika ga ALTAB kika ce kefa sai shi tun yana basar dake har ya zo yana yata taki.. maryam ta faɗa tana rayata mayafi jin sallamar sa da sauri ta fito tana cewa ganin yadda ya kalleta ta haɗiye zancen ta kallon gefen ta tayi su maryam ne suka fito ganin ba wata fuskar arziki sukai mata sallama dafa kafaɗar sara tayi da suke gaishe da altab ya amsa kamar ko da yaushe ba annuri a fuskarsa tace '' nagode sosai amma gobe za ku dawo ko.., kai suka ɗaga mata suka fita ko wacce da haushin altab a zuciyar su.. sannu da zuwa mijina yau ranar nan ta musamman ce a gare mu amma naga kamar akwai abin da ke damun ka fuskarka ba farin cikin da nake fatan samu daga gare ka ba kafe ta da idanuwa yayi har ta gama zancen ta jira yake a tashe shi daga nannauyen baccin da ya kama shi har ya tafi mafarki shi wannan wacce mace ya aura ne shi da zai yi ɗaukin ita take daukin sa ba irin kin sa Altab kana jina kai min shiru innalillahi rufaida ta faɗa tana dafe bango. sauran page shidda na gama free page Ku hanzar ta payment domin fara shiga paid group ta wannan hanyar 8141785374 Amina alhasan Muhammad opay Ku turo da shedar biya ta wannan hanyar 09061890481 ƁAƘIN SHAFI OUMYASMEEN EPISODE 5 Idan ta nuna gazawar ta tun yanzu ta bashi wata kofa da zai ci gaba da yi mata abin da ya ga dama idan kuwa ta bi shi a sannu a hankali za ta fahimci wanne sabon taku ya zo mata dashi sai ta dage duk kuwa da ɗacin da zuciyar ta keyi tace '' ya ka tsaya daga nan ka shigo..mana, ƙarasa shigowa yayi ta riƙe mai hannu tace "sannu da zuwa.., murmushi ya sakar mata yace '' kiyi hakuri na barki ke kaɗai..., da sauri ta saka masa yan yatsunta akan lips dinsa tace '' kai shiru miji na har abada baza ka taɓa yi min laifi ba yau rana ce mafi girma a gurin mu..dama duk wani me kaunar farin cikin mu..., amma nagode da kikai min wannan uzurin shafa ajihunsa yayi yara na dauko kaya a cikin mota ina zuwa... kai ta gyaɗa mai da sauri ta shiga bedroom dinta ta ƙara gyara fuskarta cikin sauri bayan ta gama ta ne mi guri ta zauna zuciyar' ta na dukan uku uku ita kaɗai tasan wanne hali take ciki bata taɓa yiwa kanta tanadin wannan rana ba dame zata wanke kanta bayan dinbin laifin da take dashi shin zai mata afuwa kamar yadda tayi tsammani ko kuma zai nuna mata ɓacin ransa har ya shigo bata san ya shigo ba jin da tayi ya dafata firgigit ta dawo daga duniyar tunanin da ta lula tace '' har ka dawo..?, zama yayi kusa da ita yace '' har ne ma ko ɗaya bakya ɗauki nane duk irin dadewar da nayi.., tab kaji wani rainin hankali shi din wanne irin bahagun mutum ne ta faɗi haka zuciyar'ta afili kuwa sai tace mai '' hmm wallahi a'a kowa ya kalle ne yaga ina cikin farin ciki Allah ya dai ya bamu zaman lafiya.., zama yayi kusa ita ya ajiye lida kusa da ita hamdala tayi shikkenan dama ta samu da zata ai watar da aikin ta ƙasa tayi da kanta tana wasa da yan yatsunta yace '' Amin ya Allah..jeki ki dauro alwala.., ina da alwala dazu nayi gab da zaka shigo tashi yayi ya cire agogon sa da wularsa ya zaro wayar sa a aljihu ya ajiye shiga toilet yayi, yana shiga wayarsa tayi ringing da sauri ta leƙa ganin sunan khalil da kamar ta kashe sai ta ɗaga ba tare da tace komai ba cikin tashin hankali ta jiyo Muryar khalil yana cewa ALTAB dan Allah wani temako za kai min kazo asibitin da aka kwantar da nasreen ana buƙatar jini sun gwaɗa nawa ba zai yi ba tab yau take ganin tashin hankali anya kuwa khalil yana da hankali yanzu kenan da ace shi ya ɗaga sai ya tafi ya barta rana mafi mahimmanci a gare su kaf mazan ma gidan yarasa wanda zai ce yazo ya bada jini sai shi kashe wayar tayi tare da sata a playmode ta ajiye ta ganin yana ƙoƙarin fitowa ta koma inda take ta zauna kallon ta yayi kamar wayar sa ce a hannun ta ko da yake me za tayi da wayarsa wani dai abin ta dauka yayi saurin kawar da zargin da zuciyar take kokarin kawo mai shinfiɗa daduma yayi ya kalleta yace '' sako hijabin ki muyi salla.., cije lips dinta tayi ta kallesa ta gefen ido dauko hijabin tayi tare da turare yi tayi kamar zata fesa a hijabinta sai ta fesa mai a jiki atishawa yayi da kautar da kansa buɗe baki yayi zai magana ta haɗe bakin su be komai yana yi ne ba cikin hayyacinsa ba... __________ da sauri khalil ya kalli wayar kashe wa yayi kenan komai yanzu idan ba shi ba wa yake da shi da zai taso cikin daren nan ya bada jini be yi fushi ba ƙara kira yayi amma yaji wayar a kashe kiran mahaifiyar sa ne ya shigo kundun bula yayi ya amsa tare da karawa a kunne sallama yayi mata amma bata tsaya amsa sallamar sa ba ta fara cewa wallahi ka ban mamaki khalil har ni zan kafa maka doka kaƙi bi yanzu kana gurin shegiyar yarinyar nan duk abin da nake kokarin fahimtar da kai ka saba fahimta ko suma da ka gani sun zare hannunsu akanta gajiya sukai shi duk inda shege yake gurin ba albarka yake ba shine kai da yake bakajin maganata ke shishshe mata to wallahi duk inda kake ka dawo gida bana kaunar ganin ka kusa da wannar shegiyar shiru yayi har ta gama faɗanta kamar da dutsai take magana a fusace tace '' yanzu kana jina kai min shiru na taɓa yar gwal anya kuwa Alhaji Abdulrasheed ba asiri yayi maka ba dole naje a duba min wallahi ba zan yarda ba kaine babban ɗana nayi faɗuwar bakar tasa.., mamy kiyi hakuri zuwa safiya zan dawo gida duk wata magana mayi ta amma yanzu wallahi bana fuskantar me kike ce min kuttumar uban can lallai wuyanka ya isa yanka ta faɗa tana kashe wayar limshe idanuwansa yayi zuciyarsa na tsananin harbawa shi yanzu besan ina ya dosa ba wazai nema ya bashi jinin nan daman beyi tsammanin cewa altab zai zo ba a yadda ya tsani ganin nasreen tana shaƙar numfashi a duniya daman rashin madafa ne ya saka ya ne me shi shi da kansa yasan mawuyacin abu ne altab yazo sai dai ma yayi mata addu'ar mutuwa zama yayi yana kallon agogo lokacin 11:34 mai da kallonsa yayi kan gadonta still ba abin da ya sauya tana nan dai yadda take kama hannun yayi, ya riƙe gam yawa za a kwace mai ita hannunta yayi sanyi ƙalau ko uncle Rasheed zai kira amma ya zu kuwa ya kamata ya kira shi , shi da ba a ƙasar yake ba, tunanine kala kala ya rikita mai kwanyar kansa ya kasa aikata wani abu ya kasa action akan komai a hankalin ya furzar da wata iska me wuci yace '' Allah ka fitar dani daga cikin wannan tsaka me wuyar da na shiga a hankali ta buɗe idanuwanta jin kanta tayi yayi nauyi da sauri ya kalleta yace '' nasreen..nasreen.., bin shi tayi da kallo ta limshe idon ta hawaye nabin kuncinta ai ta zata zata ganta tsakanin tukwane ta zata zata farka taji kasa ta rufe mata fuska duk wanda ya temake ta be mata adalci ba wallahi ta gaji da rayuwar ta wanda yake gaskatata shima yazo ya dena. sa hannu yayi ya share mata hawaye yace '' nasreen kiyi hakuri ko wanne bawa akwai irin tashi ƙaddarar idan kikai hakuri da juri sai Ubangiji ya baki ikon cin jarabawar ki yanzu da kin mutu mene matsayin ki kin manta abin da Ubangiji yace duk wanda ya kashe kansa zai tashi kafuri.., girgiza kai tayi cikin rawar murya tace ''nima bansan nayi hatsari ba amma banji dadi ba da Ubangiji be dauki raina ba.., riƙe mata hannu yayi yace '' ba kyau wanda yayi yawa kansa fatan mutuwa Ubangiji shike ɗaukan ran bawansa a lokacin da yaso bawa baya taɓa gujewa lokacin da Ubangiji ya deba mai., ƙoƙarin tashi zaune tayi tace '' kace musu su zo su cire min wannan abun gida nake son tafiya.., da sauri ya kalleta yace '' gida kuma ciwo ne a jikin ki yanzu nake tunanin wanda zan kira ya bada jiini sakamakon hatsarin da kikai kin zubbar da jini sosai jinin ki yayi ƙasa.., cire oxygen din da Ka saka mata tayi tare da dafe kanta dayayi mata wani irin nauyi ga zugin da ke mata tace '' wallahi ba zan zauna anan ba na gaji bana don zaman nan.., wata ƙara na'urar da aka saka mata ta fara da sauri likitoci har uku suka shigo dakin turus sukai ganin ta cire oxygen din da aka saka mata da abubuwan da suka saka mata a kirjinta yace '' ya akai ka barta taci re..?, da sauri wani likita zai kamata cikin ɗaga murya tare da daga mai hannu tace '' don't touch me.., Kujera yaja ya zauna yayi ƙasa da muryarsa yace '' mece damuwar ki mu nan da kika gani ba iya kula da lafiyar mutane muke ba har da damuwar maganin damuwar al'umma..sunana doctor Azez Imran ni Dan ƙasar Pakistan ne.., ɗa sauri ta ɗago kanta ta kallesa bata yi mamaki ba jin yana jin hausa raɗau kamat jakin kano ta kauda kanta tace '' ni ba abin da ke damuna babbar damuwa ta bana son zaman asibitin nan zaka iya treating dina a gida ina da harkoki da yawa inda bani ba zasu tafi daidai ba yadda nake so..., Iska ya furzar me huci yace '' idan baki da lafiya zaki neman kudi ne zaki yi mutuwar tsaye ne lokacin ki be ƙare ba david ina tunanin a buguwar nan da tayi ko ta taɓa mata brain dinta za muyi mata brain scanning wannan abin da take beyi kama da wanda yake cikin hayyacinsa ba..., kuka ta saka ta dafe kanta dake mata tsananin ciwo tace '' lafiya qalau... wallahi blood line kana ji kana gani ake kokarin saka min ciwon hauka ni ba abin da ke damuwana believe me ..., ya kike tunanin zamu amince da ke bayan duk wasu kalamai naki basu yi kama da na me ishashshiyar lafiyar ƙwaƙwalwa ba gashi kuma kin bige hakan na iya faruwa buguwa ba abin da bata sakawa.., cewar David yawa wasu picture haka ta shiga kallon su ɗaya bayan ɗaya ƙarin ruwan da aka saka mata ta cire tare da miƙewa tsaye kallon kurayen kayan da ke jikinta tayi ta dafe bango tace '' ina kayana..., kwalla khalil ya share tausayin ta ya ƙara shigarsa kama hannunta yayi ta fusge tallafar haɓarta yayi yace '' dan Allah ki dena abin da kike ke dawo da nutsuwar ki ki dawo kamar da wallahi idan kika ci gaba da haka nima zaki sakani cikin wani hali bara na kira uncle rasheed na faɗa mai nasreen zuciya ta baza iya ɗaukan wannan sabon halin da kika fito da shi ba..., ji tayi wani abu ya tsiri fatar ta daga nan tayi lu zata waɗi khalil ya taro ta ƙara treatment din sukai sannan suka fita yadda yaga rana haka yaga dare ganin an kira sallar asuba ya fita daga dakin masallaci yaje yayi sallah sannan ya fita inda yayi parking din motar sa budewa yayi ya shiga a hankali ya fara tafiya har ya isa gida yana fitowa sukai four eyes da altab ƙarasowa yayi inda yake ya miƙa mai hannu duk irin zuciya ta altab bashi da riƙo kallon cikin khalil yayi mai yace '' me kake a wajen nan..? kamar ba ango ba.., tuni zuciyarsa da kwakwalwar sa ta tuno mai ada abin da ta faru ransa ne ya ƙara ɓaci ya rasa ina zai saka kansa tunani yayi mai yawa amma ita kanta bayi wani action da zai nuna zarginsa ba bayan shi dai abin da yaji a jikin sa daban action da tayi da ban duk kuwa da a lokacin hankalin sa ya gushe yace '' yanzun nan na fito daga masallaci me ya faru yau bakai sallar asuba ba...?, kallon mamaki yake mai da rainin hankali amma da ya tuna shi ya fake nema a gunsa sai ya danne yace '' a gurin nasreen na kwana muryar sa ce ta sarƙe da ya tuno cikin halin da ya barta yaci gaba da cewa tana abu kamar wanda ya kamu da mental problem saboda jinin da ta zubar na neman jini jiya na kiraka amma ban sani ba ko kana cikin nutsuwar ka ka ɗaga kiran.., tabbas biri yayi kama da mutum rufaida ce ta ɗaga kiran basarwa yayi yace '' ban gane ba shaye shaye tayi ta bugu ko me..?, Innalillahi me isaka kullum baka kyawatawa nasreen zato kamar baka san jiya abin da ya faru ba hatsari tayi ta bugu a kanta motar ta ma duk ta lallotsai Saboda abin da kai mata burin ka ya cika altab dafe kafaɗarsa yayi yana wani murmushi wanda ake kira da yafi kuka ciwo ya ci gaba da cewa ina me farin cikin sanar da kai kata nadi LILƘAFANI burin ka ya kusan cika Sakamakon mugayen kalaman da kake amfani da su sunyi nasarar tsaga mata zuciya sauran kaɗan zuciyar'ta ta tarwatsai Sauran page 5 domin payment zaku iya biyan 500 ta wannan hanyar 8141785374 Amina alhasan Muhammad opay Ku turo da shedar biya ta wannan number 09061890481 ƁAƘIN SHAFI Oumyasmeen *abin da mutane kuka kasa fahimta shi ne zagi na ko kayi tagging ɗina ka faɗa min banzar magana by the way, it doesn't bother me ,The champion that God intended to fight or be bullied is overcome😾littafina na kuɗi ne me so muyi magana ta prevent* EPISODE 6 Khalil Why are you trying to blame me, Ka , ka sa fahimta abin nan a bude yake ko ni na saka sukai video suka yaɗa a duniya tunzura zuciyar khalil tayi ya nuna shi da ɗan yatsa tace '' but you bring them a baffa video, Allah loves those who hidden mischief amma kai lokacin duniyar ka take maka dadi to ka bayyana abin da , ba kowa ne ya sani ba ni na rasa mece rebar ka idan ka saka nasreen cikin damuwa ba dole nace kai ne sanadin komai ba..., cije lips dinsa yayi tace '' yanzu ba lokacin gardama bane muje asibitin.., Majeed ne ya fito da sauri ya ƙara so inda suke tsaye yace '' lafiya nagan ku a tsaye kamar kuna faɗa..?, Majeed komai ya lalace ina ganin karshen dan gantaka ta da ALTAB ya zo kasan duk wata wuta da ake rurawa tsakanin baffa da nasreen shi ne me iza wutar a jiya shi ya nuna musu video kamar be san halin yan media da yaɗa karya ba ko sau ɗaya ban taɓa kallon nasreen da abin da ake faɗa ba wallahi ko a ina take idan lokacin salla yayi sai tayi halayan ta da dabi'un ta sai ka zauna da ita sannan zaka fahimci wace ce ita ba MAJEED yace '' turƙashi yanzu kai kowa be goyi bayan ta ba amma kai kake goyan bayan ta taya zamu yi amfani da baɗini bayan kuma ga zahiri mun gani ka faɗa min mutumin kirki guda ɗaya cikin mutanen da take mu'amalla da su.., kai khalil ya girgiza yace '' wallahi ƁAƘIN SHAFI ne ba halin ta bane kawai tana tare da su ne amma me isaka kuke nufi mata kallon bai bai bayan kuma ga zahiri a sa musali ma aikatawa take me zai hana mu jawo ta jiki a sannu a hankali muna nuna mata dai-dai faɗa kyamatar ta ba shine solution ba..., tafi MAJEED yayi yace '' wallahi Allah wa'azi ya kama ce ka ba ka zama ma'aikacin lafiya ba kaga yadda kuwa kake tsara zance shagon da ta buɗe uban wane ya bata har guda biyu kwanaki naga tayi bikin buɗe wani shagon ta na saloon kai ka bata..?soke auren ta da ake yi duk a cikin kaddara ce ba kamshin gaskiya.., Shiru yayi domin ya fahimci ko me zai faɗa musu ba yarda za su yi bs ALTAB yayi yace '' kaga ko bashi da amsar bayar wa zo mu tafi na bata jinina domin Allah..., kai yanzu karuwar zaka bata jinin ka bayan ta tashi ka saka mata tallafin da zata dinga aikata alfasha da shi cewar MAJEED ko kuwa ya bar KHADIJAH ABDULRASHEED HUSSAIN MAI TANGARAN ni KHALIL HAMZA HUSSAIN MAI TANGARAN zan tsaya mata zan zame mata bango abin jinginar ta jinin ka kuma riƙe ko nan da bayan duniya ne zan je na samo mata ita kanta ba zata yafe min ba idan taji cewa da jinin wanda yake ƙin ta shi aka zuba mata take rayuwa barta wallahi kai yanzu daman duk abin da take aikatawa shi ne zaka bata tab kana ruwa aini MAJEED gwara na bawa mahaukaci jini na wanda ban sani ai sai Ubangiji ya kama ka dariya Khalil yayi yana ja da baya yace '' baku kyauta wa uncle rasheed ba jinin sa guda ɗaya da ya mallaka a duniya shi kuke wulakantawa.., mota ce ta tawo da gudu zata buge shi da sauri suka janyo shi gefe altab yace '' kana da hankali akan wata banza wawuya zaka cutar da kanka..ko kai ma ka kamu da cutar haukan da kake cewa nasreen ta kamu da ita..?, kaga altab zo mu tafi ka bada jinin nan kar muyi a sarar sa ki yayi suka ja shi har mota tun da suka fara tafiya ba wanda yacewa dan uwansa ƙala har suka isa asibitin.. parking sukai suka fito khalil yayi mai jagora har cikin dakin da take handle ya murɗa shiga yayi suka biyo bayansa da sauri ta ɗago ganin altab da majeed bakin tane ya fara rawa tace '' ya khalil me zan gani Please tun kafin na ai watar da haukan da kuke neman maƙala min ya fice ya bani guri.., da sauri ya dafa kansa ashe gizo take mai kallonta yayi tana kwance tamkar gawa yace '' majeed.., Altab kamar ta mutu ko karfa mugun kulle Khalil yake neman ya yayi mana dafa gadon khalil yayi ya riƙe mata hannu jin hannun nata kamar ba ya saki ya ɗaga shi ya saki riƙe hannun ta ya yi gam idanuwansa suka ƙada sukai ja kasa magana yayi, yayin da altab da majeed sukai mai runfa.. sai wata ƙara da injin dake kirjinta yake da sauri su doctor aziz suka zo gurin tare da wasu injina masu kama da dotsan guga suka fara dana mata kirji da shi tari tayi ta ƙara sanan ta buɗe idonta da yayi ja riƙe ƙarfe gadon tayi tana girgiza kanta ja da baya khalil yayi yace '' altab ko kiran uncle zan yi zuciya ta tayi rauni..., haba namijin duniya be kamata zuciyar ka tayi rauni tun yanzu ba majeed ya dafa shi yana fadar haka jikin altab ne yayi sanyi amma da yake zuciyar sa tsayayyiya ce a tsaye take ƙyam sai yace '' kai majeed anya kuwa..?, sai kuma sauran zancen suka maƙale anya me ƙara sa mana ya za kai shiru doctor Aziz ne yace '' kuna damun mu da surutu Dan Allah Ku fita.., fita sukai ba wanda yace kala zama altab yayi a kan waiting chair's bin shi majeed yayi ya zauna yana cewa Khalil yan zu mene abin yi mun zo mun zauna yawa masu zaman makoki ga ango nan ma ka taso shi wallahi Khalil kaji tsoron Allah kar hakkin mutane yayi maka yawa banza Khalil yayi musu ji yake kamar yayi jifa da sy ko ya sami sauki da salama a zuciyar sa zare tagumin da altab yayi ya jiyo ya kalle sa yace '' Khalil ce warka fa muke jira kazo ka tusa mu gaba kana kallo baka ce komai ba.., Altab ina cewa a gaban ku likita yace mu basa guri kai kayi magana shi yayi da wanne zanji Altab kai kake da mata ni kuwa daman zero ne ka tashi kabar gurin nan ni wallahi ban taɓa ganin wannan lamari ba washe garin an kai maka matar ka , ka fito yawan ɓa ɓal cewar majeed Jingina da bango altab yayi yace ''Majeed ya zan yi da wannan tunƙwa din zuciyar sa da kwakwalwar sa sun tushe ya kasa fahimtar gaskiya bayan ga gaskiya nan a bayyane amma yaƙi fahimta.., ina zai fahimta sai lokacin da yaji ta dauko mai abin da yafi karfin sa majee ya faɗa yana yin miƙa da sauri Khalil ya karasa gurin doctor yace '' dr ta dawo dai-dai..?, eh ta dawo abin da nayi shawara shine kamar zaman ta asibitin nan yana takura ta mun gama binciken mu jinin ba sai an ƙara mata ba akwai magunguna da za su yi recovery jikin ta da kanta ma mun duba normal sai dai yanzu a yi taka tsantsan wajen bata mata rai kamar yadda na fada maka farko godiya yayi mai ya shiga lokacin har ta cire rigar da suka saka mata tace '' ya Khalil mu tafi.., okay bara na kwaso kayan nan jingina tayi da bango ya dauka ko ya kalle ta yace '' mu tafi ko.., ba tayi magana ba tayi gaba turus tayi ganin majeed altab kallon mamaki take musu musamman altab da yasan yau kamata yayi ace yana gurin amaryar sa ɗauke kanta tayi tace '' zan hau napep nagode da kulawar ka a gare ni in motata wayata.., Ba komai ga wayar ki me gyaran mota ya bugo min yace tana cikin motar ita ba abin da ya same ta yanzu sai mu biya mu amsa amma me i saka kika ce ba zaki hau motata ba ...? saboda naga bakai kaɗai bane wallahi na gode da temakon ka agare ni amma motar ka in har zaka dibe su to ba zan shiga ba ban san me ya kawo su ba me suka zo su yi min ko zuwa sukai su karasa sani..? nasreen me kike fada haka anya kuwa abin da ya faru da ke ya zame miki izina riko babu kyau ki zamo me yafeya Ubangi yana kaunar bayinsa masu yafi wa'yanda basa kwana da mutum cikin ransu kasan Allah idan wa'yannan mutanen suka bi bazan bi hanyar ba haba ya Khalil kamar baka san komai ba Majeed ne ya tashi tsay yace '' Khalil kai fa muke jira kazo ka ajiye mu a guri ba wani bayani.., altab kusa tashi yayi fuskarnan a haɗe kamar an mai mutuwa ba ɗugon annuri ko ɗaya a kan ta yace '' Khalil na gaji da so zama zan tafi gida.., Khalil kallon nasreen yayi da ta haɗe rai tamkar taga mala'ikan mutuwa da sauri altab ya kalle ta tun daga sama har ƙasa ya ja tsaki yace ''I won't get into your car, if you take this girl, you're a bastard and you're walking around with a woman like that.., da sauri Khalil da nasreen suka ɗago matsar da gashin'ta tayi ya koma baya ta dafe kanta saboda motsa wajen ciwonta da tayi tace ''I will not get into this car if you get into it..The sparrow went on its feet.., dariya yayi yana shafa sajen'sa yace '' shikkenan kin ga kin fito a kamannin ki.., khalil ne yayi ƙasa da murya yace '' Please kiyi hakuri mu tafi kinga baki da lafiya motata ce ba tasa ba dan Allah ku dena raba hali sai kace masu ganin hanjin juna...dan girman Allah kar ki ce min a'a.., ya daure ta da jijiyoyin jikinta Dan haka ba zata iya ce mai a'a ba fara tafiya tayi ya biyota ya riƙe mata hannu har inda yayi parking da sauri altab ya karbi key a hannun Khalil yace '' shiga na yi drive da kai na ban yarda da kai ba.., kallon rashin fahimta Khalil yayi mai sai kuma yayi shiru majeed ya shiga gaba Khalil da nasreen suka zauna a baya goge mirro din motar yayi da tissue nasreen da ta kwantar da kanta akafadar Khalil suka haɗa ido harara ta gallamai be nuna ya san tana yi ba sai ya ƙara karkatar da mirror din domin ya fi ganin ta kautar da kanta tayi tana jan ƙara min tsaki fara tafiya sukai ya sakar musu karatun Alkur'ani.. sakin staring wheel ya juyo yace '' na manta da uwar shedanu a motar nan kai a bude bara na kashe kai Khalil idan ita bata san darajar Alkur'ani ba ai kai ka sani shi ne kai shiru.., runtsai ido tayi baƙaramin cakar mata zuciya maganar tasa tayi ba jan baƙin ta tayi ta tsuke domin ta lura shi ce ce kucen nan yake so to wallahi ba da ita ba ganin ba tayi magana ba haka Khalil ya kashe karatun Alkur'ani mai girma ba wanda ya ƙara cewa dan uwan sa kala dama shi majeed sai danna waya yake ya mai da hankalin sa ga baki daya akan wayar sa.. kamar ance ta ɗago taga yana ƙoƙarin kauce hanyar gida da sauri ta buga kujerar da yake zaune tace '' malam tsaya anan zan fita.., wani kallo ya juyo yayi mata sai da hantar cikin ta ta karta amma sai ta dake tayi wa kanta alƙawari ta dena sawa zuciyar'ta tsoron altab gwara suyi ta buga wa wanda ya gaji ya dena amma duk wani kallo da zai mata ya dena zamar mata baraza na zaro mai dara daran idanuwanta tayi tace '' da kai fa nake naga kana kauce hanya.., cikin I don't care manner yace '' zaki iya zowa ki murɗe ni ki tsayar da motar.., ganin yayi horn me gadin gidan sa ta buɗe da sauri tace '' nace maka ka tsaya zan fita.., dai-dai ta parking dinsa yayi ya buɗe kofa ya fito biyo bayan'sa majeed yayi aka bar Khalil da ita a motar shima Khalil fitowa yayi yana cewa '' nasreen fito kinga sai muje muga gida nasan ma baki taba zuwa ba.., da sauri tace '' from here I have nowhere to walk... Sauran page 4 free ya ƙara ku hanzarta payment domin kar ayi tafiyar nan babu ku 8141785374 Amina alhasan Muhammad opay Ku turo da shedar biya ta wannan number 09061890481 500 VIP 1000 special group 1500 Dan Allah wanda be shirya ba kar kai min magana ƁAƘIN SHAFI OUMYASMEEN EPISODE 7 NASREEN dan girman Allah ki fito haba ya Khalil dole sai an bi abin da zuciyar sa ta ƙitsa masa bakar saƙa idan har ku yana iya lanƙwasa ku ni wallahi nafi ƙarfin'sa bazan fito ba amshi key ɗin motar ka kai ni gida kaga shegiyar matar nan tasa me suffar bururruka na shiga sai na fasa mata kai idanuwan altab ne yayi ja be san lokacin da ya fusgota ba ya dinga jan ta har cikin Parlour sa da sauri rufaida ta ajiye burner din hannunta kallon mamaki take mai tace '' honey lafiya naga kana jan ta..?, Sai a lokacin ya saki nasreen majeed da Khalil suka shigo gaishe su tayi amma hankalin ya na kan nasreen Allah ya na gani bata kaunar ganin nasreen da namijin ta guri ɗaya itama da za a tambaye ta dalili bata sani ba ajiyar zuciya ta sauke tace '' sannun ku da zuwa..., da sauri majeed yace '' yauwa ki dai yi hakuri ranar farko a gidan mijin ki mun ɗauke shi sai yanzu muka dawo da shi.., dan murmushi tayi tace '' wallahi ba komai ga kuri nan bisimillah..., zama sukai ta kawo musu drinks da snacks a cikin ƙaton tray ta ajiye har yanzu nasreen tana tsaye kallon ta tayi taga jini a rigar ta komawa tayi ta zauna kusa da altab tana jifan ta da wani irin kallo sai dai abin bakin ciki har yanzu nasreen bama ta san da zaman ta a parlour ba. ya Khalil kai fa nake jira na gaji wallahi so nake nayi wanka na kwanta tashi khalil yayi yana cewa Amarya sai na ƙara zuwa na kwashi girki da sauri altab ya riko shi yana cewa ya zaka tafi bayan ba abin da kaci da sauri nasreen ta kalle sa tana aika mai da wani mugun kallo wallahi bata san yadda za tayi da altab, ta wuta wannan wanne irin mutum ne duk abin da zai sakata baƙin ciki ya iya shi tace '' ya khalil ni zan tafi.., da sauri ya zare hannunsa daga riko da altab yayi mai yace '' muje ya za ayi na barki, ki tafi ke kadai bayan ba ishashshiyar lafiya gare ki ba.., ni na samu sauki in anjima fita zanyi da sauri khalil ya kalleta yace '' haba nasreen me isaka duk abin da zaki cutar da kanki shi kika fi so.., tashi altab yayi yace ''ka kyaleta mana dole ne duk abin da take aikatawa tasan ba dai-dai bane kawai dan ta zubarwa da halin mu mutunci take yi wallahi tur da me hali irin naki.., juyawa tayi ta kallesa sai kuma ta fasa magana da wani abu zata faɗa mai da zai yi sular tarwatsai war farin cikin sa amma da ta tuna idan ka ruwa wani asiri Allah sai ya rufa maka asiri sai ta juya ta fara tafiya bin bayan ta Khalil yayi ya bude mata mota ta shiga ya zayo wajen driver ya shiga a hankali ya fara tuki har ya fita da ga cikin gidan horn yayi mai gadi ya buɗe mai parking ya daidai ta ya fito ya bude wa nasreen daidai da fitowar mamy da mukullin mota a hannunta da alama wani gurin zata chak ta tsaya tana nuna khalil tace '' wato khalil ban isa na faɗa maka ba ko..?sai abin da kayi niya yanzu mutuncin kane za aka dauko kilaki a motar ka , ka wuce mutane su dinga nunaka da baki.., sosai maganganun mamy sukaiwa nasreen daci a rai giram Khalil ta gani da kimarsa amma yau da ace ita da ita ta faɗawa haka da ta kwashi ruwan mamaki amma ba komai a juri zuwa rafi wata ran tulu zai fashe ratsawa tayi ta gaban ta ta wuce main parlour ta shiga ba kowa a ciki ita haka ba karamin dad'i yayi mata ba hawa sama tayi ta tura kofar dakin ta, yadda ta barsa haka tazo ta same sa cire kayanta tayi ta shiga toilet sakarwa kanta shower tayi ta runtsai idanuwanta hawaye na bin kuncin ta da ba dan tsoron Allah ba , da wallahi abin da mutane suke zargin ta shi zata aikata da ba dan gatan Allah dana ya khalil ba da wani zancen ake ba wannan ba to a haka tayiwa Allah godiya.. gama wankan tayi ta dauro towel ta fito jan dressing mirror tayi ta zauna kurawa kanta ido tayi sai a lokacin ta tuna tayi gyaɗa da ta jiƙa kanta dafe kanta tayi ji tayi an turo kofa da sauri ra jiyo dada ce tace '' yanzu abin da kikai kin kyauta kenan daga yi miki faɗa shine lilkafa ta ci uwar ta da kika tafi har da kwana me kike so jama'a su kiraki bayan sunan da suke kiran ki ada .., idon tane yayi ja ta ɗago da fuskarta da sauri dada ta kalle plaster dake kanta ta buɗe baki za tayi magana kenan khalil ya hauro sama yana cewa nasreen ga maganin ki ganin dada da yayi ya tsuguna har kasa yace ''ina wuni mun tashi lafiya..., Lafiyar qalau alhamdulilah ya miƙa mata ledar maganin nasreen yayi yana cewa yauwa dada dan Allah ki dinga lura da ita tana shan magani na san kinsan ba son sha take ba da sauri ta kalle nasreen din tace '' yimin bayani kun sani a duhu me yake faruwa..?, Dada baki san nasreen bayan ta fita ba hatsari tayi Allah ne ya rufa asiri da tuni yanzu wani zancen ake ba wannan ba yanzun nan aka sallamo ta daga asibiti kallon tausayi tabi jikar ta ta dashi zuciyar'ta ce tayi ba dadi tana fatan Allah ya kawo karshen wannan abin da ke faruwa komai ya daidaita sanadiyar wannan abu yau kimanin shekaru goma sha ɗaya bata ƙara ganin dan ta ba sai dai waya kullum ya dinga ce mata zai zo ga yau nasreen shekararta ashirin cib a duniya da wasu kwanakin tu tana shekara tara ya bar garin ajiyar zuciya ta sauke tace '' Allah ya ƙara sauki amma kam na son magani nasreen take ba.., tashi yayi yana ajiye maganin a kan mirro yana cewa sai an jima kallonsa nasreen tayi tace '' Nagode Allah ya saka da alkairi..., amin ya Allah yace ya fita itama fitar tayi shaf shaf ta gama shirinta busar da kanta tayi sannan ta bude wardrobe wata doguwar riga ta dauko read colour da adon flowers black da white colour ba ƙaramin kawata rigar sukai ba feshe ta tayi da tsadaddun turarurruka Sannan ta saka tare da yin bisimilla bata da hannu hannunta irin siririn nan ne kuma bata durar mata har ƙasa ba iya kaurinta ta tsaya ana gano kyawawan diga diginta farare tas da su ... kunshin da tayi na bikin nan ba ƙaramin kyau yayi a fatar ta ba takalmi ta dauko mara tudu baki ta zura jaka ta dauko ta rike a hannu itama baka ajiyawa tayi da ta tuna bata daka agogo ba daurawa tayi sannan ta dauko mayafi ta yafa buɗe jakar tayi ta saka Atm dinta sannan ta fito tun daga sama take jin hayaniya. ciro bakin glasses dinta tayi a jaka ta saka daga sama tana iya hango mutane da kakin sojoji da alama yan gurin aikin su altab ne ba ƙaramin kyau tayi ba , wanda zai kalleta yayi tunanin bahaushiya ce zakai tunanin balarabiyar kasar Turkiyya ce saukowa ta ƙarasa yi ba tare da ta gaisar da su ba ta fara tafiya kallonta dada tayi tana cewa nasreen ina zaki ke da ba lafiya ce da ke na chak ta tsaya sannan ta juyo kallon agogon hannun ta tayi tace ''bazan jima ba zan dawo.., sakar baki wani a cikin su yayi yana kallon ta ba ƙaramin tafiya da itamanin sa yayi ba daman altab yana da kanwa kamar haka amma be fada mai ba yasan irin matar da yake burin aura amma be taɓa faɗa mai ba khalil ne ya shigo kallon ta yayi yace '' ina zaki bace min kikai ba kin gaji kina so ki wuta.., dan ya tsuna fuska tayi ta langwabar da kai tace '' blood line ina so na je saloon kaina yayi min nauyi sannan zan biya restaurant nayi take away zan je na siya mota tun da waccen ba a san ranar dawowarta ba.., da sauri ya kalleta jin wannan uban lissafi da take yi ko da yake kayan dubu nawa ne a shagonta yace '' amma kya bari ki sami lafiya sannan dan girman Allah ban da zuwa.., da sauri ta saka mai yan yatsunta a bakin sa kasa kasa tace '' ban da zuwa club.., Sannan ta cire hannun ta daga bakin sa dafe kanta tayi tace '' da ace karatu ne wannan maganar da na ruga da na gama cin jarbawa idan aka zo yi min saboda na hadda ce kullum maganar ka ɗaya..., komai da ke nake yi domin kyautatuwar taki rayuwar nake yi nasreen juyawa tayi ta haɗa ido da altab murmushi ta sakar mai wanda ya kusan zumar da Nasir tace '' are any way barana na tafi kar nayi wasting time.., muje na sauke ki girgiza mai kai tayi dan mayafin da ta yafa ya zame daga kanta raba gashin ta gida biyu tayi tayi kitson nan two step tace '' okay muje.., kallon abokanan altab yayi yace '' soja marmari daga nesa sannun ku kun iso lafiya.., dukkan su suka masa da alhamdulilah Nasir yace '' soyayya ta rufe maka ido sai yanzu ka gan mu.., dariya Khalil yayi yace '' wacce soyayya kuma muna tauna babban issue ne ya aiki..?, Alhamdulilah nasreen gaba tayi tana fito da chingum ta saka a bakin ta ganin suna neman cinye ta.., binta Khalil yayi tabe baki sharifa tace '' da wannan kyawun nata take rudar maza kinsan shekaran jiya basma da tazo wucewa ta islamiyyar mu lokaci kina aji ta ga wata ta fito malam sunusi wanke hannu ya dinga yi ranar ba ƙaramar dariya nayi ba .., dariya basma tayi tace '' ai ta can canta wallahi komai nata me kyau ne.., duk da kasa kasa suke hirar su amman altab yana jin su da sauri basma ta tashi tana cewa kai wallahi na manta kinga ban tambaye ta ba nawa take Saida wannan lace din da best tace a shagonta ta siya da sauri sharifa ta riko ta tace '' ga wani zubar da kai ki tambayi besty mana kinga ina rabaki da shiga sabgar nasreen wallahi a kirkine da ita ba..., dariya mubaraka tayi tace '' wallahi ba kusan wace ce ita ba , bata da girman kai tana da saukin kai a haka ne zaku zata kamar zata wulakanta dan adam.., dada ce ta jiyo tace '' kudak tsai gumin ku yayi yawa wallahi.. anya ba kai ku zan yi ai muku irin training din sojojin ba ko kwayo hankali..., dariya dukkan su suka saka ban da altab da ya nuna kamar ba me san be ake ba sai danna waya yake nasreen ce ta shigo da sauri dada ta kalleta tace '' kin fasa fitar ne.., a'a ban fasa ba abu na manta wallahi gaji bana son sake hawa saman nan amma ba yarda zanyi dole na hau Dada tace '' kinyi dai kidan ki kinyi rawar ki ai gwara ki dinga motsa jikin ki in ba haka ba kiba za tayi miki yawa.., adda asma da ta shigo yan zun nan tace '' ai ita nasreeba ƙiba ce da ita ba kawai tana da hibs ne da girji shi yasaka wasu ke mata kallon kiba ce da ita.., Dada ce tace '' eh kuma fa haka ne ., gaishe da ita sojojin nan sukai nasreen ta hau sama bata dade ba sai kata ta sauko da wata leda a hannun ta cikin sauri ta fita tana zuwa wajen da khalil yayi parking ta tarar yana zaune zaman jiranta tace '' ya khalil Dan dai da mutane na kasa yi maka musu dazu baka ji abin da mamy tace ba mahaifiyar ka ce yi mata biyayya ya zama dole nagode sosai da nuna kulawar ka amma ka barshi zan tafi a napep.., haɗe rai yayi yace '' yaushe muka fara ja in ja dake ki shiga mu tafi.., ba yarda ta iya haka ta shiga amma zuciyar ta ba dan ta so ba tafiya suka fara yi ba wanda ya cewa dan uwansa komai wayar ya khalil CE tayi ringing a kusan lokaci ɗaya suka kalli wayar ɗauke kai nasreen tayi tana limshe idanuwanta kallon ta yayi ya ƙara mai da kai ya kalli wayar nasreen kishin sa take ko me abin da ya kasa tantance wa matar da yace zai aure ta , tace bata so ko kuma akwai wani abu a sau uku ana kira ba picking sai me gyaran ya katsai ci gaba yayi da tukin ya sakae musu waka kaɗan ya rage volume din yana bi ɗa gowa tayi tace '' ya khalil waka daman ka iya...? dariya yayi yace '' ai duk wakokin yayin nan na iya nasreen ina zaune a office ba ni da aiki na gaji da bincike sai kawai na shiga na internet naji..amma bana dauko ta , dariya tayi tace '' ya khalil kenan me ne marabar dambe da faɗa daman barta kayi a cikin wayar ka ta rage maka saukin batar da data.., Jan kumatun ta yayi yana yar waka kau cewa tayi tana dariya sosai yanayin na yau ya sata cikin nishadi da walwala tace '' blood line duk ran da kai aure baka da lokacina ko sai na matar ka..?, sakar staring wheel yayi ya juyo ya kalleta yace '' ke ba zaki auren ba ne...?, ba tayi tunanin fitowar wannan magana ba daga bakin sa wasa ta fara da faratan hannunta tace '' I don't feel like getting married ya khalil abubuwa da yawa sun faru I think not getting married is the solution muryar ta ce ta sarke tissue ta yago ta goge hawaye da ya taru a idon ta taci gaba da cewa whoever his parents will tell him ya ji ya ɗauki shawarar su ba zai iya aurena ba saboda The black paint that people gave me ban yi tunanin zan ci gaba da rayuwata normal ba tunani nake gwara na mutu na huta wannan rayuwar cike take da fake love, fake people dakyar ka samu mutum ɗaya like you wanda zai so mutum dan Allah gaskiya sabeer ya cuce ni temakon da Allah yayi min ba a daura ba yace ya fasa..., idanuwanta ne suka kada sukai ja ta kasa ƙarasa maganar sai ta rushe da kuka kyalete yayi, tayi me isarta sannan yace '' nasreen ko wanne bawa akwai irin jarabawar da Ubangiji yake mai idan ya saka hakuri sai kiga ya cinye jarabawar da Ubangiji yayi mai ko bayan aurena zaki ce na faɗa miki insha Allahu komai zai zama tarihi.., da sauri ta ɗago tace '' insha Allah zan bi shawarar ka amma saboda me ya saka kace ko bayan ranka..., dariya yayi yana shan kwana yace '' kullu nafsin za'ikatul maut duk kan me rai mamaci ne wannan ran da aka bamu arone wannan duniyar ba ta gaskiya bace akwai gidan gaskiya..., Please kayi shiru bana son wannan maganar mutuwar gurin me gyaran mota kenan zamu fara zuwa cewar nasreen ta fada tana kallon titi eh nan zamu fara zuwa akwai wani abun ne ...?, kai ta girgiza mai tafiya kadab suka ƙara suka isa yana ganin su ya taso tare da dauko wayar nasreen dewa sukai suka fito Khalil ya miƙa mai hannu suka gaisa yace '' ya gyaran komai yana tafiya dai-dai.., eh komai yana tafiya dai-dai mu ka kusan gamawa ya fada yana miƙowa nasreen wayar ta amsa tayi tana juyawa ba abin da tayi ƙasa kasa tace '' thank.., mai da hankalin sa kan khalil yayi domin wannan yar rainin hankalin besan lokacin da zai duddura mata ta maguzawa ba yar rainin hankali ce yace '' kuɗin gyaran ta dubu dari uku..., kai khalil kawai ya gyaɗa ya dauko wayar sa transfer yayi mai sannan yace '' ka duba nayi maka.., da sauri nasreen ta kallesa za tayi magana saka hannunsa yayi abaki yace '' shiiii.., ƙasa ƙasa me gyaran mota yace '' daman aurenta kayi ka huta kayi yidima da ita me hujja.., da sauri nasreen ta kallesa sai kuma ta fasa maganar ta dauke kanta ba komawa tayi cikin motar bayan su gama ya shigo ya tada motar tana danna waya bata dago ba tace '' kaga yan amana kaf cikin su ba wanda be kirani ba saboda ajiya bar musu shagon nayi na fito...kulawa na dad'i wallahi... yayin da ni kuma narasa kulawar ban gare biyu, parking yayi ya ɗauki wayar sa batare da yace mata komai ba cikin contact dinsa ya shiga ya danna layin uncle rasheed bugu ɗaya ya ɗauka a hands free ya saka ta yace '' Assalamu alaika uncle barka da rana.., amasawa yayi tare da cewa ya mutan gidan kallon nasreen yayi yace '' kowa lafiya..., to masha Allah ka gaishe da kowa ga nasreen zaku gaisa Uncle yace '' ina kan aiki ne idan na dawo ka turo min da number ta za muyi waya daddy kalli wannan kayan zabar min wanne zai fi kyau dani suka jiyo Muryar yarinya ƙarama tana fadar haka kai nasreen ta girgiza kai ta rufe idanuwanta khalil da jikin sa yayi sanyi zuciyar sa tayi ba dad'i me makon gyara ya ƙara jagula komai yace '' tom shikkenan zan turo maka..., atake anan ya tura mai number yace '' zai kiraki na tura mai number ki.., dariya tayi tace '' me kake tsammani zuciyar ka ita kanta bata yarda da zancen da labban ka suka faɗa ba , ni yanzu tunanin da nake ya za a yi rayuwata ta dawo kamar da ..., tada motar yayi yana cewa insha Allahu zata dawo kamar da sun gugare da dama har take away sukai sannan ta bada rabin kuɗin mota gobe zata cika sauran a gajiye suka dawo lokacin ƙarfe 3:40 dafe kansa yayi yace '' namana ta zan je office sannan banyi sallah ba har 3:40.. shagwabe fuska tayi tace '' ayya sorry ni na ja maka wallahi nima ban san lokaci zai tafi haka ba kai hakuri..., Domin yin payment sauran three pages free ya ƙare ₦500 8141785374 Amina alhasan Muhammad opay sai ku turo da shedar biya ta wannan number 09061890481 ƁAƘIN SHAFI EPISODE 8 BOOK 1 Murmushi yayi yace '' ba komai haka Allah ya tsara..., amsar take away din hannun sa tayi ta shiga parlour bakin ta ɗauke da sallama duk suna zaune yawa an kafa ƙusa a inda ta barsu anan tazo ta same su kallon ta adda Asma tayi sultan na cinyar ta tace '' sannu da zuwa ya jikin naki.., dan murmushi tayi sannan tace '' da sauki ..., Allah ya ƙara sauki amin ya Allah tace ta hau sama ajiye kayan hannun ta tayi ta fito da abincin da ta siyo shiga toilet tayi ta wanke hanyenta a hankali ta fara tsakurar abincin bawai dan be mata dadi ba aa kawai turawa take baza ta ita cewa ga daɗin abincin ba wayarta ce tayi ringing da sauri ta ɗauka ganin me kiran tace '' hello humy kwana dubu..., kai nasreen wanne kwana dubu ina kika shiga two days ba ma ganin ki ko an samiki ta kunkumin fita ne dariya tayi tana matsar da take away din da ke gaban ta tace '' wane mutum inji mutuwa aini an bani lasisi yanzu zaman kaina nake so nake abubuwa su lafa na yanki visa nayi gaba karatu zan tafi na ƙaro idan kasuwanci ya juya min baya sai na karkade takarduna na tafi aiki duk da bana fatan haka.., dariya humy tayi tana ɗaukan lemon da ke gaban ta a cikin kofi tace '' kina wuta kawata wallahi kin min daidai su basu san wace ke ba sai nan gaba za su sani.., dan jim tayi sannan tace '' ya maganar kayan nan kin magana da me kayan ko kuma kawai bani number wayarsa.., Oka zan turo miki ta WhatsApp kin san kuwa sabeer yayi aure bara na turo miki picture's din bikin da sauri tace '' bana buƙata barshi yanzu na soke shi a rayuwata kwata kwata babu shi ki ɗauka kamar ma ba mu taɓa sanin juna ba hakika sabeer ya cutar dani tsakani na dashi Allah ya isa ban yafe ba.., kai ka kai amma gaskiya be kamata ki ɗauki wannan mataki ba iyayen sa ne suka ce ba zai aure ki ba , ba shi ba wallahi yau da na saka miki voice dinsa da sai kin tausaya mai wallahi tausayi, tausayi fa kika ce lallai humy kin ga mu bar maganar sai an jima kar ki kashe wayar ki yi min alkalanci mana shi da bakin sa ya faɗa miki haka su basu san wane dan nasu ba basu san irin temakon da kikai musu ba kece sanadiyar sa shi ya dena shaye shaye wallahi nasreen da ace za su wannan irin temako kikai mai Please dan girman Allah mu bar maganar nan sai an jima okay amma yau zaki fito ko a'a ba zan fito ba.., Dariya humy tayi tace '' okay sai mun haɗu.., kashe wayar tayi ta ajiye ta janyo take away dinta ta ci gaba da cin abincin *CAMEROON YAOUNDÉ CITY CENTRE* A gajiye ta dawo daga gun aiki ajiye jakar hannun ta tayi parlour yayi tsit ba kowa ɗaga murya tayi tace '' juhud holi to ngarɗaa suudu, gujjo ari wujji geɗe am, a anndaa .., da sauri juhud ta fito tace '' a wartii e jam...?, zama tayi tana cewa Alhamdulilah ba tare da papa din ku nake ba yau ni kaɗai na dawo mana idan na tafi aiki haka kuke komawa daki yanzu da ace ɓarawo ne da shikkenan sai ya zari abin da yake so yayi gaba.., zama tayu tana cewa '' wallahi mama yasmeen ce bata son zaman parlour nan ga masu gadi ba me shigowa kawai dai sai dai mu kiyaye gaba..., ajiyar zuciya ta sauke tace '' ina Yasmeen din take..?, tana bacci bara na haɗa miki ruwan wanka ga nyaamdu maa dow dining okay Allah yayi albarka Amin mama ya maganar tafiya tawa America papa ya yarda dan jim mama tayi ta cije lips dinta nan da nan yanayin ta ya sauya tace '' ba inda zaki ko shi ya yarda ni ban amince ba me kike nema da anan ƙasar tamu ba zaki samu ba har sai kin tafi can wata uwa duniya karatu.., kwallace ta taru a idon juhud tace '' mama.., da sauri ta tari numfashinta tace '' na gama magana zaki iya tafiya.., hawa sama tayi tana kuka zama mama tayi ta zuba tagumi itama da ta hana juhud karatu zuwa wata ƙasar ranta be so ba ita lokacin ta am barta result din da ta dawo da shi ne shine babbar matsalar da ta gamu dashi a rayuwar'ta sannan ko wanne bawa da irin tashi kaddarar wata kila juhud ta samu kaddara me kyau amma tunda tana tsoro ko bacci baza ta iya ba dama abubuwan sun caɓe mata ballanata yanzu da wayewar da da ta yanzu ba ɗaya ba sannan mutane kiris suke jira shikkenna mutum ya shiga uku zare ta gumi tayi ta hau sama lokacin har juhud ta gama haɗa mata ruwan wanka a bathtub cire kayanta tayi ta saka towel tace '' ki ɗauka ki zuba min a Landry basket ko kuma kawai samin a washing machine.., Kai ta gyada mata da sauri ta juyo tace '' are you okay..?, karo na biyu ta ƙara gyaɗa mata kai mama tace '' dawo zo muyi magana..., dawowa tayi ta zauna a bakin gado itama ta zauna tace '' kina fushi dani dan na hanaki zuwa wata ƙasa karatu.., kai ta girgiza da sauri mama tace '' yi magana mana kurma kika zama..?, kai ta girgiza ta buda baki kenan za tayi magana sai kuka ya kubbuce mata kwantar da kanta tayi a kafadar ta tana kuka bubbuga bayanta mama ta ci gaba dayi tana cewa juhud bawai na hanaki zuwa wata kasar karatu ba haka kurum ina da nawa dalilin a dama tarbiyya tana lalacewa ballantana yanzu akwai hatsarurruka da mutum ke haɗu a idan ya tafi karatu abroad ana din ma ana haduwa dashi amma nacan din yafi risk saboda ba uwa ba uba ba wani dangi abin da mutum yaga dama shi zai yi wani zai tafi lafiya dan ƙaramin abu ya canza mai ƙaddararsa, dan jim tayi muryar ta tayi rauni kamar ta tuno wani abu da ya shude shekara da shekaru ta ci gaba da cewa ke yarinya ce ba zaki gane me nake nufi ba sai nan gaba wasu zugar ƙawaye su yi aiki akansa har ya wada wata hanya ta daban duk tarbiyyar ka wallahi a lokaci ƙalilan aboki yana iya canza maka ita a kullum kina min tambayar nan me ya saka naƙi barin ku , ku dinga kula abokai yau zan amsa miki juhud, aboki yana da mutukar tasiri, iyaye sai su shekara ashirin suna tarbiyya amma rana daya zai rushe wannan tarbiyyar yayin da shedan ke tun zura shi ya akata abin da sai lokacin da mala'ikan mutuwa ya tsaya akan sa sannan zai manta da abin bayan mutuwarsa iyayen da ya bari idan za ayi kwatance ba za a yi da kyawawan halin mutumin ba sai ayi da abin da ya taɓa aikatawa ba ya mace da kike ganin ta yar taka tsantsan ce duk abin da namiji yayi adone , bawai shima ba kyau ba amma na macen yafi illa saboda shi ba me fahimta sai dai dole ayar Ubangi tayi aiki akansa saboda Ubangiji ne ya hanemu da yin zina sannan yace idan kayi da yar wani dole ayi da yarka ko da yar uwarka wanda dai dole sai kafi jin zafi sannan ita bin jini take idan kika duba wannan zamani juhud ba'a mai da zina da kallon fina finan banza ba wani abu ita rayuwar nan me sauki ce idan har mutum ya ɗauke ta da sauki sannan akwai wanda baya aikatawa amma , saboda yana tare da mutanen banza sai halin su ya nashe shi a dinga yi mai kallon yana aikatawa kuma wallahi Allah ba me fitar dashi sai Ubangiji shi yasaka duk wani waje da ake aikata badala juhud kar kuje hali na so yake yau da gobe tun abin baya burge ku har shedan ya ƙawata muku shi a ranku, Wannan abubuwan ne idan na auna na duba sai naga zuciyata ba ta nutsu aka kije wata ƙasar karatu ba shiru juhud tayi tace '' insha Allahu bazan ƙara ce miki zan tafi ba..., shafa kanta mama tayi tace '' yauwa Allah yayi miki albarka.., amin tace ta fita daga dakin shiga wanka tayi bayan ta gama ta fito cikin sauri take shiryawa cikin wata abaya yar Turkiyya milk colour haska farar fatar ta tayi ta ɗauki wayar ta kai ta girgiza sannan ta fito tana cewa yasmeen tashi wannan wanne irin bacci ne haka ya tsuna fuska yasmeen tayi ta tashi tana sakar miƙa zuri ƙafafuwan ta tayi ƙasa ta ɗan dade a zauna kafin ta fito mama tana kan dining table tana bude warmer tace '' yar baka sai yanzu kika damar tashi..?, zun buro baki tayi idanuwanta tab da kwalla tace '' ba papa ya hana ku fadar yar bakar nan ba.., to ban da bakin ki karya akai muku taya za a gane jiya fa da nihila ta kawo min kayan da nayi order a wajen ta ce min tayi wannan amma ba maman muce ta haife ta ba nace wallahi itace amma kowa ce wa ake anya kuwa mama ce ta haifita kuka ta saka tace '' to sai ki nemo min wata uwar wallahi Allah bazan yarda ba.., dariya juhud tayi tace '' to zan nemo miki kinsa adda dodowa ita ce maman ki.., ihu ta saka har da buga ƙafafuwa kallon ta mama tayi tana cewa bana son shashanci zo kije kiyi alwala kiyi salla kin same sake tun da malamin ku yayi tafiya ki ka samu gurin zama kullum bacci gaki nan kullum ƙara ƙiba kike wallahi ki rage hutu ko kya samu kiyi ƙasa kai mama yanzu kema haka zaki ce wallahi yasmeen kiba kike kara yi kullum zan dinga tashin ki kina bin papa training ko a zamu kiyi ƙasa idan kuma baki ba na kai ki gun likita dariya juhud ta saka tace '' mama wai a ina ta gado wannan uwar kibar tata..kaf family din mu ba me wata kiba sosai.., dariya mama tayu daman dan su ƙara kun bura abin ya saka suka fadi haka tace '' maza jeki kiyi salla ki dawo.., zaki kunna min kallo harararta tayi tace ''kar Allah ya saka kiyi sai har papa ya dawo kya yi bayani tun da ni kin raina ni daman juhud ba a magana kin maida ta kamar kanwar ki., tafiya tayi tana kun kuni mama mai da hankalin'ta kan abinci juhud kuma na danna waya da sauri tace '' yauwa mama kalli wannan ita nake faɗa miki yar ƙasar Nigeria yace tana burgeni sunan ta NASREEN.., amsa mama tayi kara zooming din picture din tayi gaban ta na waduwa ta miƙa wa juhud wayar tace '' ungo bana son wannan shashancin.., amsar wayar ta tayi tana dariya walwalar mama ce ta tsaya kasa cin abincin dake gabanta tayi ta tashi tace '' juhud kwashe kayan nan na koshi..., Mama bakyaci abin da fa kika fi so nayi miki idanuwanta ne suka ƙada sukai ja tace '' nace miki bana so na koshi idan papa ya dawo kice mai nace kar a tashe ni kaina na ciwo.., cikin sauri ta hau staircase hawaye na bin kunci ta rasa inda za ta saka kanta tayi duniyar tayi mata zafi kamar sa ta gani a fuskar yarinyar nan da sauri ta tura kofar bedroom dinta ta murza mata key kwanciya tayi hawaye na bin kuncinta.. ________nigeria Dan ladi na sidi quarters*** sosai iska ke kadawa cikin lambon yayi da bishiyoyi sukai koraye shar da su gyara zama tayi ta ɗora kafa ɗaya kan ɗaya ta ci gaba da danna wayarta cikin kwanciyar hankali kai kace bata da wata damuwa jin karar taku tayi da sauri ta juyowa tayi da sauri ta tashi zata bar gurin kafa ya saka mata tayi tangal tangal zata wadi ya taro ta hankade shi tayi idanuwanta suka kada sukai ja tace '' mene darin gamina da kai ina ruwanka da ni.., tamkar da dutsai take fisge hannun ta tayi daga rikon da yayi mata tace '' abu kaɗan kacewa mutum dan iska kai yanzu ai tarbiyya ce ta saka ka riƙe ni.., cire baƙin glasses dinsa yayi yace '' of course me zanji in na riƙe hannun ki dubuna sun rike kashe din da nazo nayi miki ki buɗe kunnuwanki ki jini kar na ƙara ganin nayi baki, kin zo kina wuce su idan kuwa kika ƙi wallahi na lahira sai ya fiki jin dadi ce miki akai abokai na irin halin mazan da suke tare da ke ne ko zaki samu kasuwa Allah ya temaka zuciyar su ba irin wacce kika sani bace.., Ya altab tun ina ƙarama kake jifana da mugayen kalamai to wallahi Allah dan sauran mutuncin da nake ganin ka dashi zan cire me ruwanka da rayuwa wallahi wata ran sai kai takaicin wannan kalmar da ka faɗa lokacin dama ta kure maka dariya yayi yace '' yarinya ke dai zaki dana sani ki bi a hankali wallahi na aure ki na gasa miki aya a hannu ki dawo kan hanya..., dariya tayi ta cire farin glasses da tasaka tace '' au Allah dan girman Allah kai baka ji kunyar wannan kalaman naka na kayi amai ka lashe kenan abin da zan faɗa maka shi ne kaje ka fara gyara gida kafin kazo ka gyara ni.., shafa sajensa yayi yace '' ai kece gidan ke zan fara gyarawa kaf cikin ahalin me tangaran wa kika ji yana aikata makamancin abin da kike aikatawa..., dariya tayi ta wuce shi tace '' ja bincika kaji na wata ma yafi nawa munu sai dai kuma akwai na sarari akwai na boye wani da kuɗin sa ya saka ya auri na boye sai lokacin da bai zata ba asiri zai tonu.., da sauri ya kalleta har ta kulewa ganin sa me kenan take nufi turkashi akwai fa lauje cikin nadi dole ya nemo koma mene juyawa yayi ya bar gurin shashin hajiyar sa ya shiga tana zaune sai girgiza kafa take luban Aisha na gefenta Assalama yayi suka amsa gaishe su sukai ya amsa yana gaishe da Hajiya cikin fara'a ta amsa tace '' barka dai ya gida..., Alhamdulilah yauwa daman ina so na faɗa maka kaja kunnan matar ka akan ya'yana jiya tayi musu diban albarka to wallahi bazan amince ba da sauri ya ɗago abin ya bashi mamaki kwana ɗaya har an fara kawo mai kara kai halin Hajiya da yaran nan sai Allah yace ''insha Allahu zan faɗa mata wallahi ban san haka abin ya faru ba..., owo dai na faɗa maka idan zaka dauki mataki ka dauka dan wallahi bazan lamunta ba kai kaɗai ne babban dana ace ƙananan ka basu da iko da gidan ka ai tama lami din na kirawo ta nace taja kunnen yarya idan ban da na dage yar ta ta zata aure ka wallahi ba zan lamunci yarda take juya uban rufaida ba su juya min kai haka kurum shiru yayi yana bin zanan kasan carpet din dakin da ido yace '' Allah ya wuce zuciyar ki.., amin yauwa ba ruwanka da shiga sabgar wannan shegiyar yarinyar kasan fa duk inda shege yake dan sunna ya rabe shi zai ga ba dai-dai ba nidai na faɗa maka yanzu nace wa yaran nan indai suka ganta to su matsa daga hanyar ina zamab zamana ba za su sani yawan karbo magani ba garin biye biye mutum ya kauce hanya be sani ba tashi yayi yana cewa to hajiya sai anjima to Allah ya tsare ya kare ka yaushe kuma zaka koma gun aikin naka dan jim yayi yace '' sai nan da ƙarshen watan nan ..., okay Allah ya kai mu amin ya Allah ya fada yana futa kai tsaye yana fita be biya ko ina ba ya hau motar sa ya wuce gida parking ya daidaita ya fito kai tsaye hanyar da zata sada shi da shashin rufaida ya nufa sallama yayi da sauri ta amsa batare da ta ɗago ba idanuwanta nakan wayar ta abin mamaki parlour yayi kaca kaca kai kace anyi wata ba a gyara ba kallo ya shiga bin ko ina ga rubar lemo da ruwa yadda kasan kana kasuwar sai da robobi ka kuntun cake da donut ga ledojin biscuit cikin bacin rai yace '' rufaida kinsan ni fa bana son kazanta wannan wanne irin abu ne tun safe da kikai shara baki ƙara yi ba..., ɗagowa tayi tace '' ni wallahi tsiyata da kai kenan ka dinga fadan da ba dalili ina ni ina sharar katon parlour nan ai sai kuguna ya karye Wallahi bazan iya ba a dazun ma turare kawai na saka sai yanzu nake charting da aunty take ce min nayi maka magana ka samomin yar aiki.., da sauri ya kalleta yace '' yar aiki kuma a ina ance miki ina da burin ajiye yar aiki to wallahi tun wuri tunanin nan ya bar zuciyar ki idan har zaki kanzanta wallahi ba xakiji daɗin zama dani ba rufaida tun wuri ki ɗauki tsintsiya ki gyara dakin nan tun kafin ranki ya ɓaci.., da sauri ta ajiye wayar ta tace '' haba altab ka tausaya min ina ni ina share wannan dakin kalli fa kagani ni wallahi a gidan mu ban saba ko tea ban iya dafawa ba idan kuma kaga zaka iya jigilar siya mana take away bisimillah.., tun da yake be taɓa jin rainin hankali irin wannan ba anya kuwa rufaida lafiyar ta qalau lallai zai gyara mata zama soja ba wasa ba dole ta nutsu idan kuwa ta ƙi zata sha wuya..yace '' ki kawo min abinci bedroom dina.., tashi tsaye tayi tana zuba uwar miƙa tun kayan dazu ne da safe da tasaka suke a jikin ta wato kawai kyale dan adam idan ba zama da shi kayi ba baza ka iya fahimtar wane shi ba duk uban barar da turaren da rufaida ke yi yau babu ko kamshi a dakin da take ko jikinta ma banda wari ba abin da take baya jin ko wankan tsarki tayi domin wannan wari da walakin hausa suka ce goro amiya 😂😂 ba ruwan oum yasmeen kowa ya debo da zafi bakin sa Sauran page biyu free ya ƙare domin yin payment zaku biya ta wannan account din 8141785374 Amina alhasan Muhammad opay ku turo da shedar biya ta wannan account din 09061890481 ƁAƘIN SHAFI Oumyasmeen Daga wannan page wannan page din freee ya kare ku daure ku siya ku karanta halalin ku duk wanda ya karanta min littafina ba tare da ya biya ni ba yaje shi da Allah.. masu fitar min da book ku kuma kuje dan kan ku sai ka gama wahala rana tsaya mutum ɗaya ya fitar maka da book.. domin biyan kudi zaku biya ta wannan account ɗin 8141785374 Amina alhasan Muhammad opay ku turo da shedar biya ta wannan hanyar 09061890481 ₦500 yan niger zaku iya turo da katin moov ko sahel fcfa 300 ku ɗauke shi gaba da baya ku turo ta wannan number 09061890481 Cameroon Ghana chadi zaku turo da katin VTU ta wannan number 09061890481 Complete document 1000 yan aljanna ku nuna min one love EPISODE 9-10 Bedroom dinsa ya shiga ransa a ɓace yana shiga ya cire takalminsa ta ajiye zama yayi akan armchair rasa ma me zai yi shi mutum ne da baya son ƙazatan ta amma yarinuar nan ya lura ba ƙaramar ƙazama bace kwana ɗaya har tafara nuna halinta to wallahi ba zai dauki wannan kazantar ba kamar an waɗo ta haka ta shigo tana sosa kai zanin zata a ɓantare tace '' beb Wallahi tun safe nake cin snack na gaji ko za kai mana take away...?, kansa ya ɗago da yake sara mai yayi mata wani irin kallo sannan ya ɗauke ƙansa abin da ya lura idan ya ci gaba da zama a gidan nan rufaida bata gyara halinta ba wallahi a kwai matsala tashi yayi ya shiga bathroom, Cire kayansa yayi ya jefe cikin Landry basket sakarwa kansa shower yayi domin ji yayi kansa har turiri yake saboda tsabar ɓacin rai, cikin daki kuwa ko da ya tafi ya barta ko a jikin ta sai ma taɓe baki da tayi ta fice daga dakin tana cewa bara na samawa kaina mafita yunwa ba kanwar uwarka bace zama ka sauko kan hanya wayar tace tayi ringing da sauri ta ɗaga ta fashe da kuka tace '' aunty ni wallahi bazan iya ba dawowa gida zanyi yanzu naya dawowa ya rufe ni da faɗa ba irin kulawar nan da nuna tarairaya kinga dazu ma da ya fita sallar asuba wallahi be dawowa ba sai wajejen ɗaya Sannan abokanansa suka zo ya kara wanka ya fice bayan ba haka ake ba da suka tafi yawa wani kwaɗo ya kara wanka ya fice shi ko mura baya gudu yanzu ma gashi nan wankan yake ... wai kuma bazai samo min yar aiki ba idan zanyi inyi da kaina wallahi rana ɗaya dan baki ga yadda na firgice ba kuma ji kamar ba zan yi raina amma.., da sauri aunty ta katsaita tace '' ke tsaya bana son shashanci wannan ai zakanin kine da mijin ki bana son jin wannan zance wai yaushe rufaida zaki hankali kwata kwata bakya iya rufawa kanki asiri zancen kuma aikin wannan tabkeken gidan wallahi ba zata saɓu ba tun da nake dake kin taɓa yi min shara ne ai yasan gidan da yaje ya dauki ki dan haka anan ma ko tsintsiya ban yarda ki dauka ba kinga share hawayen ki autata.., share hawaye tayi tace '' to na share..., yauwa abin da ya saka na bugu nayi miki magana a charting baki buɗa ba ya gane ko kuma shirin mu yayi aiki kinsan daman dayan biyu ne idan ya gane a canza wani shirin kallo kofar dakinsa tayi da sauri ta shiga nata dakin tace '' hmmm aunty Allah ya rufa mana asiri be gane ba amma kuwa idan ma ya gane to yana cikin ko kwanto ..., aunty tace '' dan kuka me jawa uwar shi jifa yanzu da ace ban sani ba da shikkenan kin zubar mana da martabar gidab mu ni ban ga abin so a wannan shegen yaron ba Allah yayi miki kafiya duk da ma lokacin da na sani abubuwa su ƙure da wallahi karya yake ya sani sai dai in kuma shima yana yi..., dariya ta saki tace '' shi yasa ka nake alfahari da ke aunty sai an jima ga shi nan..., da sauri ta kashe wayar ta saka akan gado budewa tayi cikin haɗe rai kamar lokacin da ta fara haɗuwa da shi ba annuri ko ɗaya a fuskarsa yace '' wato tun yanzu rufaida ban isa na faɗa miki kiji ba ...? , ba zaki share gidan nan ba kitchen ma gashi nan kaca kaca..dakin duk wari yake wallahi Allah bani na ɓata kitchen ba su Maryam ne da sara suka dafa mana indomi zancen kuma kace daki na wari to ai da sauki tun da bani nake ba dazu da safe na saka turaren wuta Rufaida ta faɗa tana ɗaga hammatar ta tana shin shi nawa.. wata kan idan kana da rai zaka sha kallo bin ta yayi da ido ya ma kasa magana dole ya nema wa kansa mafita yace '' kafin na dawo wallahi Allah ki gyara gun nan idan kuma ba haka ba zaki ga abin da zai faru.., zama tayi a kan gado tana cire daurin ta ashe a jiyan hular gashi ta saka tamanta da yanzu ma bata saka ba ta ture daurin kanta sai gashi yan mutsi mutsin kalba irin wacce ake wa yara da sabulu ta fito kasa tantance me yake gani, kamar fa kan jariri yake gani jar uban can haka ya ambata a zuciyar sa zuciya da hange hange sai ta hango mai dazu lokacin da suke tara da nasreen a lambo da sauri ya kawar da tunanin nan daman ya dade da shafe wannan babun a ransa duk da shi kansa yasan karya yake wa kansa ba zai iya ba.., afusa ce ya fice domin a halin da yake ciki idan yayi magana to kalma mara dadi ce zata fito daga bakin sa da harara ta bi bayansa da ita sai a lokacin ta lura da kanta tsaki ta ja tace '' koma mene ai an riga da an daura kome zai biyu da baya me sauki ne.., kwanciya tayi a binta a nan bacci ya ɗauke ta tayi rashi rashe bakin nan a buɗe miyun bacci na zuba har akai sallar isha tana wannan baccin na asara kamar da ga sama taji an buga mata pillow a gigice ta tashi tana zab ga ihu ganin shi ne ta mustsuka idanuwanta tace '' kai innalillahi ashe daman haka auren sojan yake haba altab abin da kake ba baya kyautawa ka dena cin zali wallahi.., wata uwar harara ya gallamata yace '' idan na rantsai bazan yi kaffara ba akai magariba kina kwance akai isha kina kwance duk baki tashi kin yi ba sannan aikin da nasaka ki baki ba..., wani uban salati ta saki tana tashi tace '' haba sweet na ga addinin nan dan sauki ne dan girman Allah idan kai kake amsar sallar nan idan nayi dawo min da a bata naga tun da kata shi da safe baka irin tarairaye ni ba haka kayi sauri ka tafi kayi sallar asuba sai wani cewa kayi, beb tashi kiyi wanka kiyi sallah tsakani da Allah ya dace ban taɓa shan azaba irin ta yau ba kuma da ace mazan waje ne har toilet suke raka mace da sauri ya kalleta yace '' ke ina kika san ana yin haka.., da sauri ta rufe bakin ta tace '' kar ka ne mi ga zarge ni nima faɗa min ake yadda yake yi shi ya saka na kwanta ina jiran ka dawo to shiru shiru baka dawo ba kuma ga yanayin sanyi na shigowa garin nan gudun mura sai kawai nayi kwaskwarima idan rana ta danyi na yi wanka na haɗa sallar nayi to da rana tayi na duba zan kunna heater switch din yaƙi kunnuwa kawai sai na hakura idan ka dawo ka haɗa min ruwan wankan nayi tamkar wani mata laka haka ya zauna dafe da kai yace '' yanzu dai asuba ahazar la'asar magariba isha duk baki ba..?, cikin da confidence ta ɗaga mai kai domin ita bata ga abin laifi ba addnin nan dan sauki ne kuma Ubangiji yaga zuciyar ta tsawa ya daka mata da sauri ta takure guri ɗaya tana zare idanuwa yace '' wallahi rana ɗaya nasan na gamu da ƙaddara domin ke wallahi kaddara ce da ranki da lafiyar ki har ki dinga haɗa sallar saboda baki da tunani wallahi idan zaki ci gaba da haka wata ran bazan san lokacin da zan karkaryaki ba kin san kuwa mece sallah kinsan kuwa wanne mahimmanci Ubangiji ya bata...itace fa marabar arne da musulmi sannan kuma itace idan mutum ya tsayar da ita zata zo ta dinga tash zaman kabari.., zunburo baki tayi ta tashi tana karka da mai zani ta shiga toilet fita yayi dakinsa ya kwanta wayarsa ya ɗago duk ƙarfin zuciya irin tasa a yanzu zuciyar sa tayi rauni yasan ba zai taɓa samun muradin sa limshe ido yayi ya buɗe a lokaci ɗaya ka ƙurawa screen din wayar sa ido itama kamar shi din take kallo ajiye wayar yayi.. ya kurawa suspender ido yawa me shirin gano wani abu idan ya furta zai zama barazana da farin cikin wasu har da nasa idan ya furta yasan baƙin cikin da mahaifiyar sa zata shiga ba ƙarami bane gwara ya bar shi a ransa idan ya mutu ajalinsa ne wayar sace tayi ringing da sauri ya ɗaga ganin me kiran cikin girmamawa ya yi mai sallama tare da gaishe shi amsawa me kiran yayi yace '' ya kowa da kowa dafatan kowa yana lafiya..?, Altab yace '' lafiya qalau alhamdulilah ya su ni'ima..?, Suna lafiya qalau alhamdulilah kowa lafiya dan Allah ka ƙara riƙe min amanata ina gab da dawowa tashi zaune yayi yace '' Allah ya dawo da kai lafiya...insha Allahu baka da wata matsala., godiya yayi mai sukai sallama ya kashe wayar sa _______________ BOMPAI jazz ka tabbatar wannan zancen gaskiya kake faɗa min cewar nasreen da ta dora kafa ɗaya kan ɗaya acikin mota shi kuma jazz yana tsaye da kan sa yawa abarba saboda tara gashin da ya yi yayi tsaibebe a ka yace '' na taɓa kawo miki rawo tan karya ne..?, da kunnuwana naji suna maganar.., cije lips dinta tayi ta duki staring wheel tace '' kasan me jazz wallahi tara matar nan nake akwai ranar da zan kamata naci ubanta.., Sai wacce rana kenan kawao hajiya ta ki baza yanayin ki kema ɗagowa tayi tace '' ban gane ba nayi mai kaga duk wata harkar haram kai ne a sahun gaba nidai barni a nan rabon bawa da arziki mutuwa baruna yanzu ba wannan ce a gabana ba da sauri ta ɗago jin karar parking din mota baffa ne driver sa ya fito ta buɗe mai idanuwansa ne lokaci ɗaya suka canza launi tun daga sama har ƙasa ya kalli... jazz shi kansa wandon sa yawa an kwato shi daga bakin kura ga wani Ban zan aski sai kace kan abarba kai ya jin jina ya wuce a yau zai zartar da hukunci ko ya yiwa kowa dad'i ko karya yiwa amma dole ya ɗauki mataki akan yarinyar nan tun kafin ta fara ajiye musu shegu a gida.. idan na waje yaƙi zama da ita dole ya tursasa wanda yake ganin ko bayan ransa ba zai iya hufuntar da ita ba wanda zai tsaya tsayin daka gurin tarbiyyar ta ta dawo yadda take a baya kafin ta haɗu da shedanun mutane wayar sa ciro bugu ɗaya aka dauka cikin girmamawa alhaji Usman yake kokarin gaishe shi katsai shi yayi yace '' ka buwa yan uwanka su duk inda suke suzo ina son ganin ku..., yana kaiwa wannan be jira me zai ce ba ya katsai wayar kafin kace mai kowa ya hallara gyara zama yayi sannan ya karato addu'ar buɗe taro yace '' ba komai ne yasa ka na tara ku ba sai akan dalili Babba na lura ina gab da shiga cikin wani yanayi da al'ummar gari zasu fara zagina na gama hukunta masu laifi amma me laifi dake rayuwa a cikin gidana na kasa wani ɗaukan mataki akan abin da ke faruwa bayan dogon nazari da nayi yau kuma idanuwana sun gane min abin da ya kamata tun farko na yiwa tubkar hanci duk masu gadin gidan nan da security din dake cikin gidan nan da raina da lafiya ta a matsayina na babban alkali wanda ya rike mukamai da dama ni za a dinga tara yan iska a cikin gida to yau zan zartar da hukunci duk wanda yaga an mai rashin adalci ba haka naso ba amma ba yarda zanyi da nayi fushi sai kuma na gane hannunka baya taɓa rubewa ka yanke ka yar gyatsuna fuska Hajiya tayi duk wannan kwana kwanar ya fito fili ya fada musu me ke faruwa amma sai zance yake cikin zance kallon ta mamy tayi tayi ƙasa da murya tace '' yaya me kika fahimta a cikin wannan zancen na tsoho..?, kallon ta tayi ta take mata kafa tace '' sai an lura damu koma mene ai zai fada..., dan jim baffa yayi ya kalli altab yace '' jeka ka kirawo min wannan yarinyar Khadijah.., tashi altab yayi da sauri ya fita har yanzu tana inda take kallon ta yayi yace '' baffa yace ki zo..., fitowa tayi daga motar jazz tana cewa hukuma tayi kira muyi magana ta waya okay ni yanzu akwai inda zani komin dare dai ki bar wayar ki a kunne Okay ba damuwa ta faɗa tana bin bayan altab har suka isa parlour cire takalminta tayi ta shiga zama tayi ba tare da ta kalli kowa ba tace '' baffa gani.., wani kallo yayi mata sannan yace '' KHADIJATOU ABDULRASHEED HUSSAIN MAI TANGARAN.. wannan sunan shi kike amsa wa ko..?, kai ta ɗaga mai mayafinta ya cire yar stair din dake huyanta ya gani ta tattoo ya girgiza kai yace '' dabi'un ki da halayyar ki sunyi kama da ta musulmin kwarai.., da sauri ta kallesa baza ta iya ci gaba da kallon cikin idanuwansa ba maida kallon tayi kan hannayen ta da jiya taje ta cire farcen hannunta tattoo ne kawai a jikinta kasa magana tayi, murmushi takaici yayi tace '' ke kanki kinsa gaskiya jibi wuyan ki kamar ba yar musulma ba kai Khalil.., da sauri yace '' na'am baffa.., Na baka nasreen a yau zan daura muku aure ka amince kai khalil ya ɗaga alamar eh da sauri ta ɗago altab ya dago zuciyar sa na tafasa Abba kuwa yace '' gaskiya baffa ban amince ba wata kila ba za a rasa ta da cutar kanjamau ba haka kurum na rasa ɗana altab ne ya ɗago be yi zaton haka daga gurin Abba ba ya buda baki yace..... turƙashi me hakan ke nufi me altab zai ce tab da sauran rina akaba wacce nasreen wane zai aure ta saboda duk mazan da yayi yunkurin aurenta sai a fasa wai shin ina mahaifinta ɓangaren mazan gidan har guda uku ko wannensu akwai kudirin sa akan ta shin idan altab yace shi yaji ya gani rufaida fa ita zata ji ta gani yanzu auren ma kuwa zai yiwu...?, domin jin wannan amsosin wa'yannan tambayar ku biyo ni a littafi na gama book 2,3,4,5 duk akan farashi me sauki 500 Idan na gama ya zama 1000 Alhamdulilah Allah nayi maka godiya da ka bani ikon gaba book 1 lafiya kamar yadda na gama lafiya Allah ka bani ikon gamawa sauran lafiya. ni fatahiyya Muhammad yakasai (oumyasmeen) nake cewa ku huta lafiya kar ku manta masu son a tallata musu hajojin su kofa a buɗe take muyi magana ta wannan number 09061890481