[2/11, 5:10 PM] Hafsaat🧕: *_KWANKWASON JIMINA!!_* _(MAI WUYAR SHAFAWA)_ 🦩🦯🦾 _NA_ _NANA HAFSATU_ _MX_ *_ZAFAFA BIYAR 2024_* *_arewabooks:mssxoxo_* *_Free page :01_* _wannan LITTAFI mai suna a sama kirkirarre ne, wasu sunayen, garuruwa, abinci, al'adu da sauran su duk kirkira ce. Idan hakan yayi dai dai da rayuwar wani ko wata... Toh akasi aka samu👌_ _بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ_ ________ _01_ *YANKIN BUNZA...* Mutanen da suka fara zama a yankin bunza makera ne da suka tashi daga garin GAFA domin neman kasa mai arzikin zinare, wacce za su sarrafa su yi karfe da ita mai ado.. Mutanen sun yi dace da samun kasar mai kunshe da sinadarin zinare, sannan kuma mai albarkar noma da ruwa da dazuzzuka da za a iya yin farauta... Wajen ya kuma kasance mai matukar tsaro kasancewar akwai manyan duwatsu da tsaunuka, da mutane za su iya hawa su fake idan an kai musu hari, Duwatsun su ne dutsen BUNZA da GAFA da FANNAU da SARBO da DENTEKA Akwai kuma koguna daban-daban da suka kewaye yankin, da suka hada da kogin Lawuna, da kuma kogin Nakare. Hakan ya sa mutane da dama suka ringa yin kaura zuwa yankin domin zama... Daga cikin mutanen da suka fi shahara cikin wadanda suka fara zama a yankin akwai wani jarumin makeri da ya iya kera zinare ana cewa dashi BUNZA, kuma sunansa ne aka sanya wa garin na BUNZA.. Dutsen BUNZA wanda girmansa ya kai murabba'in kilo mita 634,209, watau kwatankwacin kashi 52 cikin dari na girman jihar baki daya. Yankin BUNZA ya hada da hamadar GAFA mai cike da tsaunika.. Mafi yawancin jama'ar yankin amce larabawa ne na Lebanon wanda ibtilai ya same su a daruruwan shekaru aka kwaso su zuwa kasar nijeriya. A ka kuma sauke su a yankin na BUNZA...Nan suka hayayyafa suka tara zuri'ah, akwai kuma barebari, Fulani da kuma Hausawa.. Yankuna da dama ne suka taru don shiryawa yadda zaa ci yankin BUNZA da hari. Domin yankin nada tarin arziki na zinare da suke hakowa. Kasashen da dama sun bukaci da yan usulin yankin su sayar musu da sansanin don mallakar wajen. Mutanen BUNZA suka ki amincewa da hakan... Hakan yasanya yankuna dadama suka hada karfi da karfe suka kaiwa garin BUNZA hari. Suka kashe na kashewa suka farfasa duwatsun suka haqe suka kwashe zinaren. Sai babban uslin dutsen yankin na BUNZA shine bai karasa fasuwa ba daga gefe basu lura ba maharan. Suka ci garin da yaki suka kyale su. Harin da aka kaiwa yankin BUNZA ba karamin rasa rayuka da arzikan tattalin yan garin sukai ba. Zuriya dadama sun mummutu. Wasu sun bar yankin sun gudu. Yayinda wasu da aka kwashe wa arzikin su nan take wasu suka futa hayyacin su. Wasu Suka samu tabin kwakwale da sauran su... Bayan tafiyar lokaci mai tsawo....yankin BUNZA a yanzu babbar sana'ar yankin itace cinikin gishiri da dabino, sai dai a shekarun 1970's harkar bude ido ta zama wata babbar sana'ar yankin... Amman duk da hakan al'adar yankin ta na nan 'ya'ya mata basa karatun boko. Mazan ne keyi kawai... Suma da sum dan tasa za'a dakatar dasu sun daina sai su koma noma da sauran aiyukan karfi na gado. Dan karatun da sukayi amfamin sa shine idan masu yawon buda idanu suka zo yankin. Kuma basa jin hausa ko fullanci ko larabci to sai yaran su mazan suyi mu'amala da su ta yaren turanci.. Haka zalika matan da sun dan tasa sun fara girma sai a aurar da su ga mazaje. Suma mazan ba Kuma masu shekaru bane. Dik Yara ne wadanda Suka dara matan da shekaru kadan.. Ba Kuma son ransu ake basu ba. Al'adar itace namiji zai nome gona acikin kwanaki kadan. Ya yinda macen zata dinga zuwa bingi/tekun ruwa don debo ruwa a manyan bokitai ta kai gidan surukai. Har sawu goma duk kwana daya. Kuma tsakanin tekun da inda gidajen yan yankin yake akwai tazara sosai a tsakani... Amman duk wannan uban wahalar da ake sha kowane yaro da yarinyar sai sun cikace hukuncin sannan a daura musu auren dole. Hakan Kuma zaka hakura... Domin KADDARA!! KOWA DA IRIN TAASA (Free book dina)👌 Mai karatu kada na isheka/ki da ratattako takaitaccen bayani game da yankin na jihar BUNZA... Bara mu tsunduma cikin labarin don jin yadda kowane bangare zai kasance... Amman Kafin sannan bari na Kara maimaitawa Mutanen yankin BUNZA. Kyawawan asaline musanman zuri'ar: *HAMIDNIYYA LEBANON* *Zaune* Nawraah take akan yar katifar ta. Hannun ta rike da biro da paper tana rubuta ABCD da manyan baki. Amnah ta shigaa dakin da sauri. Tana karkada mata hannu. Hakan yasa Nawraah daukar littafin da sauri ta cusa shi karkashin katifa biron Kuma ta boye shi acikin hular kanta. Sai zare idanu takeyi. Kalo daya zakai mata kasan batada gaskia. Ta tsiri riko hannun Amnah tana ce mata......... _INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_ _KU MARMATSO KUSA...🔊_ _ZAFAFA BIYAR 2024_ _ZAFAFA BIYAR!!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_ _YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_ _GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_ _________ _1_ *_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_ _2_ *_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_ _3_ *_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_ _4_ *_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ [2/13, 1:49 AM] Hafsaat🧕: *_KWANKWASON JIMINA!!_* _(MAI WUYAR SHAFAWA)_ 🦩🦯🦾 _NA_ _NANA HAFSATU_ _MX_ *_ZAFAFA BIYAR 2024_* *_arewabooks:mssxoxo_* *_Free page :02_* __   "Ba kiji ciwo ba ai ko?... Ki dai na tsalle tsalle Amna.." Ta karasa fada tana mai tambayar ta da hannu alamar menene? Amna ta bude dan karamin bakin ta tana furta sunan yafendo a hankali. Ai kuwa bata karasa rufe bakin nata ba yafendo ta karasa dakin tana dogara yar sandar ta. "Ah yafendo..." Cewar Nawra tana mai danne gefen katitar data zura littafin ta zauna akai. "Amna tace baki da lafiya ko?" Nawra ta kakaro murmushi tana kada kanta. "Da sauki amma.." "Tun dazu nake cewa kina ina ne duk su Layla suna nan.. Bake kwata kwata. Kwanakin nan na rasa gane kan ki. Na tambayi mahaifiyar ta ki tace zata miki magana. Sai Amna ce danasa Adam ya kirawo ki tace ai baki da lafiya " Nawra dai kanta a kasa tana lankwasa yatsunta. Tace, "Uhum... Amman da sauki ai. Nagode sosai" "Sannu kinji?. Allah ya baki lafiya Nawrah. Kwanta ki huta" "Tohm yafendo.. " Nawra ta haye Kan katitar sosai ta kwanta tana mitsitsika idanu.. Yafendo ta mike dakyar tana dafe bango ta fice daga dakin Nawra ta sauke katuwar bahaguwar zuciya ganin yafendo ta fita. Tadaga gefen katitar da saurin gaske ta zaro littafin, ta bankada kasan akwatin ta ta saka. Amna na gefe tana kallon ta. Nawra ta riko hannun kanwar tata tace, "Nagode sosai Amna tah.. Yau da yafendo taga Ina rubutun nan ai sai an kusa yankani. " Ta karasa fada tana kada Kai. Amnah tayi murmushi kawai. Tana Wasa da zaren jikin rigar ta. "Ungo biyar dinnan na baki jeki sayi wani abun" "Nagode" Amna ta karba cike da farin ciki ta fice da sauri. Nawra ta kwanta akan katifar ta ta lumshe idanun ta.... Fuskar ta ta gauraye da murmushi. A zuciya take karantowa. idanuwan ta na hasaso mata rubutun haruffan da zanen su. Ya yinda labbanta ke matsowa ahankali tana karanta su... "Nawra.... Nawra .... Nawra" Layla ta kwada mata kira. Ta shiga dakin nasu. Nawra ta mike da sauri tana duban ta tace, "Kai Kib katse ni wallahi" "Dalla aiken mu akayi..." "Ina aka aike mu ?" "Gidan bappah Auwalu." "Tam. Bari nasaka hijabi" "Dalla muje a haka kaman wasu manya zamu saka hijabi?" Cewar Layla ta fada tana yiwa Nawra nuni da kanta. Nawra ta girgiza kai tache, "Zan saka.. Ammi tace da hakan ake dorewa har girma. " "Shikenan sai ki saka ai" Nawra ta girgiza kai. Ta bude wardrobe din kayan su ta dakko hijabin ta ta zura... tana duban kanta a wani madubin su karami dake jikin dressing mirror dinsu.. Tsaf da ita kamar wata babbar budurwa ta dubi Layla dake nannade kasan zaren hannun rigar ta tace, "Muje" "Yauwa." A tare suka futa daga cikin dakin sukayi hanyar fita daga gidan yafendo na daga can runfarta ta hango su tace, "Nawra kinji sauki me? Layla ba ke kadai aka aika bane sai dakika taso ta?" "Wai ba..." Bata karasa ba Nawra ta saka hannu ta gwabe wa Layla baki. Da Sauri tace, "Na ji sauki yafendo yanzu..." "Mashaa Allahu. To kuyi sauri ku dawo" "Tohm" suka hada baki.. Fita sukayi daga cikin gidan. Layla ta dubi Nawra cike da mamaki tace, "Ina tsoron ranar da su bappah zasu Kama ki..." "Ba zasu Kama nI ba inshaa Allah.. " "Toh Allah yasa... Ni kam Dadi nakeji bama yi, karatun nan ba fa wani Dadi ne dashi ba kinaji yan maza na fada" "Ni dai inaso" "To ai shikenan..." Suna tafe suna hira hadi dawasa a hanya Suka karasa gidan bappan na su. Basu dawani nisa sosai. Don hakan bazasuyi wata tafiya can ba Sika karasa. Bakunan su dauke da sallama suka shigaa cikin gidan. A zaure Suka ci Karo da shi Yana tafe Yana duban goro a hannun sa. "Ahh.." Ya fada Yana kallon su "Bappah Ina kwana?" "Bappah Ina kwana?" Suka shiga gayshe da shi. Ya amsa musu Yana duban su da Karin bayani. "Bappah Wai Kai ake jira.." Layla ta fada tana duban sa. "Ai gabi Nan dama candin zani ai. Muje ko?" Ya nuna kofa.. suka matsa ya shige suka bi bayan sa suka futa . "Zo mu biya dangaki.... (Dangaki shine sunan babbar gonar data mamaye rabin garin BUNZA. Gona ce data fi wani garin girma. Itace ake yankawa samarin garin idan zasuyi sure. Kowanne sai a shata masa wani yanki nadaga ciki ya nome. Shi daya ba dan tayi. Idan ya nome ita kuma amaryar dazaa hadasu sure. zata dinga ebo ruwa sawu goma daga Rafinrau (sunan babban rafi ne da wasu ke Kira da teku. Ance duk shekara ma ya kanci mutane sama da dari. To Nan amaren ke zuwa suna ebo ruwa daga rafin da take can bayan garin zuwa gidajen surukan su wato gidan iyayen mazajen. Su Kai su koma har sawu goma. Shikenan sai a daura musu aure. Gwarzon da gwarzuwa kenan. Amfamin noman da angob yayi shikenan sai suyita ci agidan auren nasu. Ruwan nan kuma haka za aita bawa amarya tana girki ko aikin abinci har adadin data evo Kafin aure. .. wannan wata babbar al'adace da Yan yankin BUNZA ke gudanarwa shekara da shekaru... 'Yau farisu ke nome gonar auren su da fiddau.. zo muje kinji?" Nawra ta girgiza kanta , "Jeki ke kadai " "Kinsan fada zaa mun agidaa idan ba ke. Idan mu biyu ne kuwa fadan kadan ne bama lalle ayi ba." Nawra badan taso ba. Tabi bayan Layla suka nufi dangaki don ganewa idanun su noman karshe da farisu angon fiddau zai yi... Bappah Muhammad sani ya karasa cikin gidan bakin sa dauke da sallama. Yayi hanyar sashen mahaifiyar su Ya durkusa har kasa ya gayshe da ita. Ta amsa kanta a gefe cike da kunyar dan fari. Duk yaran nata sun hallara. Bappah sani, Bappah Auwalu shine na biyu amman yaci sunan Auwalu Lawan, Bappah salisu da bappah Junaid sai kuma mace guda daya yakunbo aminatu. Wadda itace ta biyun karshe. Bappah Junaid ne autan Dadaa (yafendo).. _INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_ _KU MARMATSO KUSA...🔊_ _ZAFAFA BIYAR 2024_ _ZAFAFA BIYAR!!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_ _YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_ _GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_ _________ _1_ *_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_ _2_ *_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_ _3_ *_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_ _4_ *_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ [2/13, 5:49 PM] Hafsaat🧕: *_KWANKWASON JIMINA!!_* _(MAI WUYAR SHAFAWA)_ 🦩🦯🦾 _NA_ _NANA HAFSATU_ _MX_ *_ZAFAFA BIYAR 2024_* *_arewabooks:mssxoxo_* *_Free page :03_* ***Hajiya Fanta... Wato Dadaa mahaifiyar su Bappah Auwalu kuma kaka ga su Nawra dake kiran ta da yafendo... Tana a zaune ne akan babbar kujerar parlorn.. parlor ne matsakaici dauke da saitin kujeru dai dai misali. Yayinda yaran nata ke zazzaune daga kasa kowannen su yana fuskantar ta. Dadaa tayi gyaran murya tace, "Dalilin daya sa na kirawo ku nan gaba daya akan wannan taron abubuwa uku ne zuwa hudu... Kuma dukkanin ku nan babu wani dayasan dalilin hakan sai Allah mahaliccin mu. Sannan bana bukata wani acikin ku ya nemi bijerewa ko ince kawo wata shawara ta daban ga zantukan da zanyi. Ina fatan Kuna saurara?" "Muna sauraron ki Dadaa" suka hada baki wajen amsa ta.. Dadaa ta kada kai ta cigaba da cewa, "Allah ya muku albarka duka...Allah ya hade kawunan ku ya kauda fitnah a tsakani. Allah ya raya muku zuri'ah ya albarkace su.. Aamin" "Aameen Dadaa" "Aaameen" "Yauwa ku saurari abunda Zan fada da kyau. Ku Kuma nazarci zantukana a kwakwalen ku. Kada wani yayiwa maganganu na fahimta a baibai ce. Sannan duk abunda na fada Ina fatan ya kasance mafi alkhairi agare mu baki daya" "Aameen" "Allah ya kara Miki lafiya Dadaa" "Aameen... Maganar fitar da ni waje don gano menene gundarin wannan rashin lafiyar tawa ni Fanta na soke ta... Babu ita" "Amma Dadaa... "Ya isa karkace komai...sai da na ce muku da fari bana bukata wani acikin ku ya nemi bijerewa ko ince kawo wata shawara ta daban ga zantukan da zanyi. Ku ma kuka amince ko baa ayi hakan ba?" "Anyi Dadaa." "Tuba muke" "Yauwa wannan magana ta futa na soketa. Dukkanin abunda Allah ya kadarta wa bawa na rashin lafiyar kai komai ma da sauran su. Allah ne kadai zai magance maka a duk sanda yaso.. sa'annan wannan lalurori nawa sunci kudaden da cikinmu basu ci ba. Garuruwa nesa dana kusa bawanda baa zaga da Ni asibutin sa ba don gano gundarin ciwo. Don hakan na hakura ni. Wannan ciwo bana warkewa bane .. Allah ne kadai zai mun maganin sa." "Dadaa ki dai na cewa hakan" "Me ake jira ne? Dukkanin munan kowa fa tasa yake jira... Mutuwarnan sai ta dauki kowa babba dayaro kowa ba Wanda zata Bari. Don hakan a kyale ni na zauna da ciwo na. Kankarar zunubai ce. Idan Kuma lokacin tafiyar ne yayi Allah yasa mu cika da Imani" "Ki bar fadin hakan Dadaa" "Magana ce ta gaskia... Allah ya sa mucika da Imani" "Aamin Dadaa" "Aamin" Suka amsa mata dukkanin su. Dadaa ta Dan dubi fuskokin su. Bappah Auwalu ita yake kallo, Bappah sani ma itan yake kalla data kalle shi sai ya sadda kansa kasa. Ya yinda bappah salisu kansa ke akan agogon dake daure a wutsiyar hannun sa yana saita lokaci. Bappah Junaid Kuma kansa a kasa.. Sai yakunbo Aminatu dake lankwasa yatsunta tana duban mahaifiyar tasu Dadaa. Dadaa ta sauke katuwar ajiyar zuciya tace, "Allah ya hade kawunan ku...ya kauda fitnah a tsakani. Amin" "Aamin Dadaa" "Aamin" "Sai magana ta gaba akan yaran wajen ku mazan... Wadanda ke makarantar boko yanzu... Tun ba yau ba ahali da yawa na yankin bunza ke aibatar mu kancewa mu muna qafafa muna fatali da al'adar kaka da kakanni. Bama koyi da sauran mutanen gari... Ku dubi ibtila'in daya saukarwa yar wajen ku kalatacciyar al'adar jigilar ruwan Rafinrau zuwa ga gidan surukan ta akan hanyar ta rasu a sawu na bakwai... Wannan munanan al'adu naki jinin su bana kaunar su.. Don hakan tun kafin rasuwar mahaifin ku muka gama magana dashi muka yanke shawara.. Zamu tarkata komai namu mu bar musu yankin nan. Zaman mu acikin sa babban ibtilai ne musanman da zuriyar mu ce kadai ke da kadarorin zinarai ragowa na dutsen bunza..." "Mashaa Allah Dadaa... Wannan zance naki haka" "Hakan shike Dadaa.. Allah ya amince" "Amma Dadaa kina ganin Mutanen Nan zasu kyale mu mu bar yankin nan? Kinsan mugayen alkadarin su akan zuriyar mu" "Babu abunda suka Isa suyi Mana Wanda Allah bai rubuta ba. Mu mayarda komai gare shi sai ya buda Mana kofa masaukakiya. Don hakan Kar ku wani damu da su. Idan aka sauya yanki sai a kyale yarannan maza suci gaba da karatun su. Matan Kuma a kyale su har zuwa sanda zasu tasa a aurar da su... Duk dai yadda ta kasance din..Kar a tsaurara akan matan nan" "Inshaa Allah hakan zaai Dadaa." "Wannan zance naki haka shike Dadaa" "Toh Allah ya Mana muwafaqa" "Aamin Yaa Rabbi "Sai magana ta karshe.... Dukkanin dukiyar data ragemun a duniya na hadeta waje daya na kasata kashi uku. Kashi daya zaa ajiyeta ayiwa Yara aure idan sun tasa... Su Sameer, Khaleed, Ashiir da ashfeef, Ahmad, Kashi daya zaa bawa miskinan yankin nan wajen mararrabar Ballo Mai sardii.. kashi daya na rabata tsakanin sani, salisu , Auwalu da Kuma ke Aminatu..... Duk sukayi shiruu suna sauraron ta. Ta daga Kai ta dora akan autan ta Bappah Junaid da kansa ke a kasa tace, "Kason daya rage na karshe kuma na barwa junaidu shi kadai.... A nan na kawo karshen maganganun da zanyi. Ina fatan Kuma zaku dauki zantuka da nayi kuyi amfani da su. Ko bayan rai na bana fatan wani acikin ku ko zuriyar sa da ya tada wata husuma ta daban. Kudi shirme ne karewa zasuyi su barku. Amman jinin Yan uwantaka na zumunta zumunci ne Mai karfi na har abada. Dan girman Allah kada ku yanke zumuntar dake tsakanin ku. Kada ku yanke alakar da kuka taso tare da ita. Kada ku bari duniya taji kan ku...kada ku bari ayi muku dariya ana zundar ku. Ku hade kawunan ku sai Allah ya shigaa lamuran ku... Hamidniyya Lebanon kada ku bari sunan zuriyar nan ya tagayyara Allah ya muku albarka" "Aaamin suka hada baki wajen amsa ta. Tana karasawa ta mike tana dogara yar sandar ta ta bar wajen ta koma daki. Donma kada wani ya kawo mata wata maganar ta daban data shiga dakin sai ta sakaya kofar ta turo ta. Ganin hakan yasa daya bayan daya suka bar wajen. Kowanne da zancen da yake azuciyarta sa.. musnaman akan jimilar kadarorin ta da tayi... *Hamidniyya Lebanon....* Mai karatu zai so yaji asalin tushen wannan zuri'ah dake cikin yankin bunza mai tarin albarka... Ku biyo ni a next page don jin kanun labaran🏃 _INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_ _KU MARMATSO KUSA...🔊_ _ZAFAFA BIYAR 2024_ _ZAFAFA BIYAR!!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_ _YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_ _GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_ _________ _1_ *_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_ _2_ *_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_ _3_ *_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_ _4_ *_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ [2/13, 5:57 PM] Hafsaat🧕: *_KWANKWASON JIMINA!!_* _(MAI WUYAR SHAFAWA)_ 🦩🦯🦾 _NA_ _NANA HAFSATU_ _MX_ *_ZAFAFA BIYAR 2024_* *_arewabooks:mssxoxo_* *_Free page :04_* ____ *HAMIDNIYYA LEBANON* Hamidniyya Lebanon wata zuri'ah ce mai karfi dake shiyar sansanin yankin bunza. Yankin bunza na dauke da yarika kala kala. Mafi yawa acikin su Fulani ne, Fulani dai kabila ce da tarihi ke turke asalinta tun karni na 15 daga wasu manyan yankuna biyu da ke kasashen Senegal da kuma Guinea Conakry, wato Futa Toro da kuma Futa Jalloh... Sai mafi karfin ciki wato wadanda sukafi tarin dukiya zuri'ar hamidniyya ne wadanda usulin usulin su larabawa ne yan kasar Lebanon.. Daga su sai barebari, Yarabawa, Idoma, Igbira da sauran su. Kusan dukkanin wasu yarirrika dake kunshe cikin kasar akwai su a yankin garin na bunza.. **ASALIN SU** Tarihi yazo da cewa usulin zuriyar hamidniyya yan kasar Lebanon ne, Lebanon kuma kasa ce a Western Asia.. Tarihi ya nuna cewa Marigayi Hamidniyyah Mohannad Lebanon Wanda sunan sa ne zuriyar ta samu asali. Ance sunzo kasar ne yin wani bincike. Jiragen da suka zo da su suna da dan yawa. Dan haka sansanin inda ake ajiyar jirgin sai a ka samu ibtila'in gobara jiragen duk suka kone... Sai jirgin su Marigayi Hamidniyyah Mohannad wanda shi Marigayi da cikin daga cikin manyan kasa alokacin sun fita yawon bude idanu a gajimare da jirgin daga nan suka biya wata kasar.. Labarin gobarar jiragen ya koma kunnuwan can kasar inda sukayi koke koken su. Ance dukkanin jiragen sun kone da Mutanen su dake ciki. Baa banbance gawa da karfen jirgin aka tarkata aka wanke aka sallace su a haka aka birne... Ko da ragowar jirgi daya ya dawo wato nasu Marigayi Hamidniyyah Mohannad. Sai suka samu mummunan labarin abunda ya faru..Gashi babban lefi ne ya koma kasar su shi da sauran wadanda basu rasun ba. Su ce dalilin daya faru sun bar kasar hakan ta faru to akan me zasu tafi yawon bude idanu su bar sauran mutanen su da aiyukan da aka turo su suyi? Wannan dalilin ne yasa suka yanke zama anan kawai. Domin idan suka koma kasar su ma hukuncin kisa ne za'ayi musu. Anan suka kafa sansanin su suka auri junan su.. su da fulanin wajen suka zama mutane daya...Suna daya daga cikin manyan kabilun da suka taimaka wajen sama wa kasar 'yanci daga turawan mulkin mallaka. Baya ga zaratan sojoji na Fulani da suka yi gwagwarmaya, akwai kuma fitattu da suka taimaka wajen sama wa kasar 'yanci. Daga nan ne suka ci gaba da bazuwa cikin kasashen duniya musamman yammaci da kuma tsakiyar nahiyar Afirka domin nema wa dabbobinsu abinci da kuma ingantacciyar rayuwa. Ko da yake babu tsayayyen adadi na yawan Fulani a duniya, amma kiyasi na nuna yawansu ya kai akalla miliyan 45, kuma sun fi yawa ne a kasashen yammacin nahiyar.. Kamar yadda Fulanin ke da masarautu da dama haka ma kuma suke da karin harshe kala-kala wanda masana tarihi suka kasa kashi shida. Wannan ne ma ya sa ba lallai ne wasu Fulanin Najeriya su fahimci fulatancin wasu 'yan uwansu da ke kasashe kamar Senegal da Gambiya ko kuma Burkina Faso ba. Ko da a Najeriya, akwai wani karin harshe da wasu Fulanin ba su fahimtarsa. Akwai aminta sosai tsakanin fulanin yankin bunza da zuriyar Hamidniyya Lebanon.. Tun shekarun baya ya zuwa yanzu. Kuma Allah ya sanya musu wata albarka ta tarin dukiya. Basu da wani yawa. Dan sun rarrasu da yawan su. Sai 'ya'yan 'ya'yayan su da sukayi aure sika hayayyafa suma suka tada tasu zuri'ar amman duk da haka basu da wani tarin yawa sai tarin dukiya . Danma dukiyar ta babu koda kwatan rabin ta yanzu. Hakan ya samo asali ne kuma alokacin da yankuna suka hada karfi da karfe suka ci garin na bunza da yaki. Suka kwashe musu tattalin arzukan su da tarin dabbobin su sai wadanda ba'a rasa ba. Wanda suka fita kiwo hatsarin bai auku akan su ba.. Dan tattalin arzikin zuriyar ta hamidniyya kuma wadda ta ragu ce na daga abunda mahara yaki basu kwashe ba a babban dutse mai suna bunza. Wanda shine duk tarin zinaran cikin sa dama na zuriyar hamidniyya ne. Da mayakan suka raba dutsen biyu suka kwashe abunda zasu kwasa. Sai Allah bai basu ikon ganin sauran zinaren dake gefen dutsen ba daga daya bangaren.. wannan zinare shine zuriyar suka raba aka fitar wa Yafendo (Dadaa) kaso daya mafi yawa acikin . Kasancewar ta itace uwa datayi ragowa. Duk sun rasu sai 'ya'ya'ye da jikoki... Tana dauke da rashin lafiyar hauhawar jini da sukari. Sai ciwon kafafu suma da sukarin ne yayi silar su da Kuma girma na shekaru. Wannan dalilin ne yasa zaa kaita kasar waje afura da ita Domin duba lafiyarta sosai acan din. Ita kuma bayan tayi wasu tunani nata na daban. Ga ganin girma daya zo mata sosai.gashi an talauta zuriyar tasu ba kamar a baya ba. Domin rabin rabin rabin dukiyar tasu ta baya basu da kwatan kwatankwacin ta a yanzu. Hakan yasa ta tara yaran nata take sanar dasu tayiwa dukiyarta rabo gida uku bisa hudu. Kamar yadda na zayyano muku a shafin baya... Inda dadaan ke kasafce dukiyar ta... Gata kamar haka, Sai magana ta karshe.... Dukkanin dukiyar data ragemun a duniya na hadeta waje daya na kasata kashi uku. Kashi daya zaa ajiyeta ayiwa Yara sure idan sun tasa... Su sameer, khaleed,Ashiir da ashfeef, Kashi daya zaa bawa miskinan yankin nan wajen mararrabar Ballo Mai sardii.. kashi daya na rabata tsakanin sani, salisu , Auwalu da Kuma ke Aminatu..... Duk sukayi shiru suna sauraron ta. Ta daga Kai ta dora akan autan ta Bappah Junaid da kansa ke a kasa tace, "Kason daya rage na karshe kuma na barwa junaidu shi kadai.... A Nan na kawo karshen maganganun da zanyi. Ina fatan Kuma zaku dauki zantukan da nayi kuyi amfani da su. Ko bayan rai na bana fatan wani acikin ku ko zuriyar sa ya tada wata husuma ta daban. Kudi shirme ne karewa zasuyi su barku. Amman jinin Yan uwantaka na zumunta zumuncii ne Mai karfi na har abada. Dan girman Allah kada ku yanke zumuntar dake tsakanin ku. Kada ku yanke alakar da kuka taso tare da ita. Kada ku Bari duniya taji kan ku...kada ku bari ayi muku dariya ana zundar ku. Ku hade kawunan ku sai Allah ya shigaa lamuran ku... Hamidniyya Lebanon kada ku bari sunan zuriyar nan ya tagayyara Allah ya muku albarka" "Aaamin suka hada baki wajen amsa ta. Tana karasawa ta mike tana dogara yar sandar ta ta bar wajen ta koma daki. Donma kada wani ya kawo mata wata maganar ta daban data shigaa dakin sai ta sakaya kofar ta turo ta. Ganin hakan yasa daya bayan daya suka bar wajen. Kowanne da zancen da yake azuciyar sa.. musanman akan jimilar kadarorin ta da tayi... Anan mun karkare ASALIN tushen zuriyar hamidniyya Mohannad Lebanon dake a yankin birnin bunza.. Sai kuma SHAFI na gaba zamu dora daga inda aka tsaya... _INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_ _KU MARMATSO KUSA...🔊_ _ZAFAFA BIYAR 2024_ _ZAFAFA BIYAR!!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_ _YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_ _GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_ _________ _1_ *_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_ _2_ *_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_ _3_ *_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_ _4_ *_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ [2/13, 9:22 PM] Hafsaat🧕: *_KWANKWASON JIMINA!!_* _(MAI WUYAR SHAFAWA)_ 🦩🦯🦾 _NA_ _NANA HAFSATU_ _MX_ *_ZAFAFA BIYAR 2024_* *_arewabooks:mssxoxo_* *_LAST FREE PAGE: 5_* _____ *Suna* kan hanyar layin su zasu koma gidah suka hadu da Hammah Ashfeef .. Yana hango su ya yafuto su da hannu da sauri yana dafe kansa saboda yadda rana ke dukan goshin sa.. Karasawa sukayi wajen nasa.. Ashfeef ya dube su duk sunyi futu futu yace, "Tun dazu nake neman ku... Yafendo tace daga aiken data muku ku Kira Bappah ba a sake ganin ku ba. Hankalin ta ya tashi sosai. Saboda tace ke bakida lafiya ashe ko? Wai ko jikin naki ne ya tashi a hanyar dawowa? " Ya karasa fada dan yatsantsa na yin nuni ga Nawra dake kikkifa idanu Nawra ta bude baki zatayi magana Layla tayi saurin cewa, "Eh kanta ne yake ciwo shine muka shiga gidan su Nano umman su tabata magani " Ashfeef ya kada Kai Yana kallon Nawra yace, "Ya jikin naki to?" "Da Sauki naji Sauki ...Amma" Bata karasa fada ba Layla ta saka hannu ta mintsino hannun ta, Hakan yasa tayi shiru tana mai duban Layla ta wutsiyar idanu. Sam batason halin Laila nayin karya akan abunda ba haka ba. "Allah ya sawwake ya kara sauki. Muje gidan. Don yafendo hankalin ta atashe ganin ba kudawo ba an je har gidan bappan ko kuna can bakwa nan." Yayi gaba. Suna biye da shi a baya. "Toh Yayaa.." Nawra ta juya ta dubi Layla cike da takaici kasa kasa yadda Hamma Ashfeef ba zai juyo ba tace, "Me karya fa dan wuta ne...kina ji dai malam Yana fada mana Kuma ma yafendo tana mana tuni akai" Layla ta tabe baki tace, "Fada zamu sha idan ba haka na fada ba" Nawra ta girgiza kai kawai tayi gaba abunta. Layla tabi bayanta tana Kiran sunan ta a haka suka karasa gidah..   Da yafendo suka fara cin karo a zaune ta zabga uban tagumi tana kallon babbar kofar da Zata sadaka da wajen gidan da shigowar sa. "Assalamu alaikum.." suka hada baki wajen yin sallama.. "Waalykm Salam... Ina kukaje ne haka iye? Nawrah Layla tun dazu ake tsumayin ku shiru. Ko jikin ne?" Ta tambaye su cike da kulawa. "Wai kanta ne ashe yake ciwo..." Ashfeef ya amsa yafendo. "Shine mukaje tasha magani ta kwanta agidan su ....... Layla bata karasa fadar abunda Zata karasa ba Nawra ta yi hanzar cewa da yafendo, "Dandagi muka biya ganin noman farisu angon Fiddau.. Bamu ma gama kallon Fiddau dake daukar ruwa daga Rafinrau ba.." Tana karasa fada tayi shiru kanta a kasa tana lankwasa hannuwan ta. Duk da karancin shekarun ta hakan bai sanya ta dinga karya ba... "Kiyi hakuri yafendo..." Ta sake fada kanta a kasa. Layla dake gefenta kirjinta ya cika fal da tsoron abunda zai biyo ba. Dama tun ba yau ba Nawra tasaba kwafsa musu. Don haka itama ta sadda kanta a kasa cike da muryar ban tausayi tace, "Kiyi hakuri yafendo" Ashfeef yayi kansu zai dake su yafendo ta hana shi, "Kyale su....Ai Nawra kamar ko da yaushe ba itace me laifin ba. Ni nasan yau dinma kece Layla.. Allah ya shrya mana ku..." "Kiyi hakuri yafendo bazan sake ba. Allah so nake kawai naga yadda farisu zai noman." Layla ta tsugunna tanata bawa yafendo hakuri Nawra ma ta tsugunna agaban yafendon suka shiga bata hakuri a tare. "Ku tashi kuje.. Allah ya muku albarka ya yafe mana baki daya" "Aamin Aameen" Kowaccen su tayi bangaren su sumi sumi. Nawra cike da madaukakin farin ciki ta shjga sashen su. Don Sam batason ta dinga karya akan abunda ba hakan bane. Gwara kowane lefi ne ta fadeshi awuce wajen. Domin malaman islamiyar su suna koya musu haramcin karya da illolin ta... :::::::::::::: Ranar wata jumuah. Yanayin damuna ne dama. Garin yayi sanyi ya Kuma yi shiru ba hayaniya. Ni'iimar Allah a ko'ina, ciyawa tayi kore gaba daya. bishiyu nata kadawa. Ga kamshin kasa dake tashi.. A ranar ne Kuma ahalin zuri,ar hamidniyya suka tsinci kansu cikin tashin hankalin da suka Dade basu tsammaci kansu aciki ba. Wannan tashin hankalin Kuma shine na babban rashin bango majinginar su ne wato yafendo... Daadaa. Allah ya karbi ran yafendo da asubahin ranar bayan an idar da sallah. Kuma a satin ne sun gama shirya komai tsaf don yin hijra daga garin bunza zuwa yankin gaban sa.. Abunda yasa basu koma din ba ma.. jira suke su karasa sayar da kadarorin su gaba daya sai su bar garin na bunza. Allah cikin ikon sa da kudurar sa da hikimar sa Domin shidin mamallakin kowa da komai ne.. Kuma kowanne rai sai ta dandani zakin mutuwa. Domin Allah daya halicci kowane dan Adam yafu kaunar sa akan komai.. Yafendo ta cika ne alokacin tana zaune akan sallaya ta idar da sallah tana azkhar. Daman jikin ya sake tsananta. Har ya Kai ga sallah ma azaune take yi. Idan zata mike ma sai an taimaka mata. Haka idan zuwa bayi ne nanma haka. Hakika alokacin da rashin lafiyar yafendo ta Kara tsanani. Ahalin sun shiga madaukajin rudani Mai wuyar fassarawa. Domin ko menene sai da yafendo. Itace a tsaye akan kowannen cikin su. Don haka rasuwar yafendo ta taba dukkanin su. Manya da kananan cikin zuriyar. Lungu da sako sai koke koke suke yi.... Hakika yafendo bango ce majinginar bayi.. ita din itace tsintsiya mai daure da zumunci, temako , dattako, tausayi, kyautata wa gaba ki daya na ahalin zuriyar hamidniyya. Ba zuriyar hamidniyya kadai rasuwar yafendo ta taba ba. Ciki harda yarika daban daban na zuri'ah da dangi na mutanen birnin bunza. Sunji mutuwar yafendo sosai. Garin yayi shiru. Anata koke koke. Haka aka wanke yafendo. Alhamdu Lil Laah yafendo tayi cikawa Mai kyau da kalmar shahada. Ta Kuma rasu tana kan sallayar da take ibadah. Da asubah sannan kuma a cikin babbar Rana Mai tarin albarka da alkhairai wato ranar jumuah... Bayan an gama mata wanka. Aka Kira dangi Kashi Kashi na ahalin hamidniyya don yin sallama da yafendon. Kowannen sai da ya zubar da hawayen babban rashin jigo da sukayi na yafendo. Suka yiyyi mata addua. Aka nannade ta aka zura a makara... Aka sallaceta aka tafi kaita gidan ta na gaskiya.. Acan dinma iyalan nata Maza sunsha kuka. Musanman Dan autan ta Bappah Junaid. Wanda banbare shi akai daga kan kabarin yana ta rusa Kuka tamkar karamin yaro.. ------- Hakika rashin yafendo ya haddasa rabuwar kayuwa da dama na daga cikin ahalin zuriyar hamidniyya... Koda wajen gado ma sai da aka samu dan hargitsi Kafin dai daga baya Kuma su sulhunta. Duk kuwa dawasun su ne daga ciki suka kawo husumar. Sai da sukayi kwanaki hamsin da biyu... Sannan suka tashi baki daya kwansu da kwarkwatar su daga yankin na birnin bunza suka koma can babban birnin Naduka......... .... _Anan karshen shafukan free pages suka tsaya...zamu shiga kundun labarin a cigaban paid pages Inshaa'Allah_ _shin wacce iriyar rayuwa ahalin Hamidniyya Lebanon zasuyi a birnin Naduka?_ _Ya labarin zai kasance mai dauke da suna mai tafiyar harshen damo ... KWANKWASON JIMINA!! MAI WUYAR SHAFAWA.... !?_ _#Hamidniyya Lebanon family_ _#Dr. Abubakhr dollars family.._ _#Alhaji Yusuph Family_ _#Twist of fate, Destined lovers#Life-partners#Al-Hub-Hayaat#Rich vs poor...._ ✔️✔️ _INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_ _KU MARMATSO KUSA...🔊_ _ZAFAFA BIYAR 2024_ _ZAFAFA BIYAR!!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_ _YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_ _GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_ _________ _1_ *_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_ _2_ *_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_ _3_ *_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_ _4_ *_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ [2/17, 1:34 AM] Hafsaat🧕: *_KWANKWASON JIMINA!!_* _(MAI WUYAR SHAFAWA)_ 🦩🦯🦾 _✍️: MX_ *_ZAFAFA BIYAR 2024_* _vip pages na arewa👇_ *_arewabooks:mssxoxo_* *_paid page :06_* ______ _BABBAN BIRNIN NADUKA_ _(FEDERAL CAPITAL TERRITORY)_ NADUKA: Karamar Hukuma ce. Area kuma Babban Birnin Jihar NADUKA a Arewacin Najeriya. Naduka tana da nisan 160 miles (260 km) gabas da birnin, BUNZA da 84 miles (135 km) arewa maso yammacin Galko, kusa da kan iyaka da hez Jamhuriyar... Hakika Birnin shi ne cibiyar yankin noma da ke samar da gyada, auduga, fatu, gero da masara ta Guinea, sannan kuma yana da injina na sarrafa man gyada, da karfe, ya kasance cibiyar kiwon shanu, awaki., tumaki da kaji. Mafi yawan al'ummar Birnin musulmi ne musamman daga al'ummar Hausawa da Fulani. Marigayi Shugaban Najeriya Nande 'Yar'kuwatua ya kasance dan asalin birni rike da sarautar gargajiya a Naduka.. Gwamnan jihar Naduka mai ci a yanzu shi ne Mal. Harisu Yusha'u PhD, wanda aka rantsar da shi a matsayin gwamnan jihar a ranar 29 ga Mayu shekara ta alif ...., wanda ya gaji Dantekan.. Birnin kewaye yake da bango mai nisa kilomita 21(mil 13) a tsayi, an yi imanin cewa an kafa Naduka tun kusan shekaru sama da 1100. A zamanin da, idan aka samu Sarkin na Naduka da mulki na rashin sanin yakamata ana yanke masa hukuncin kisa. Daga karni na 17 zuwa na 18, Naduka ta kasance cibiyar kasuwanci a kasar Hausa, kuma ta zama mafi girma a cikin jihohin Hausa Fulani sun mamaye Naduka a lokacin yakin Fulani a shekarar 1807. A shekarar 1903, Sarki Bakri Yarzm ya karbi mulkin Birtaniya, wanda ya ci gaba har zuwa lokacin da Nijeriya ta samu ‘yancin kai daga kasar Ingila a shekarar 19..... A lokacin cinikayyar yankin kudu da hamadar sahara, an san birnin Naduka na daya daga cikin manyan wuraren kasuwanci da karin iko, kuma an yi imani da cewa ita ce mafi karfi daga cikin masarautun kasar Hausa ta fuskar ilmi na addini da kasuwanci da sana'o'i. Bajamushe mai binciken frankis Hon ya isa Naduka, Bature na farko da ya yi haka, a farkon karni na 19.. Tarihin birnin na ilimi irin na yamma ya samo asali ne tun farkon shekarun 1950, lokacin da aka kafa makarantar sakandare ta farko a Arewacin Najeriya ( Kwalejin Malamai ta Naduka ). Yanzu haka akwai manyan makarantu da dama da suka hada da jami’o’i uku: Jami’ar Naduka university, da Jami’ar Gwamnatin Tarayya ta Naduka da kuma shaharariyar Jami'ar Al-Haramein Naduka(mai zaman kanta) Makaranta ce ta kudi da yayan masu hannu da shuni suke zuwa, kasashe da dama na zuwa don samun gurbin karatu a makarantar saboda tsananin kyawun ta komai da komai makarantar ta hada musanman fannin karatu tamkar a kasar waje .sai Makarantar Fasaha ta Hun Naduka Polytechnic da Kwalejin Ilimi ta Tarayya, da Kuma Makarantar koyon jinya(School of nursing) wadda ke cikin babbar asibitin Naduka . Haka nan birnin Naduka yana da wani masallaci da aka gina a karni na 18 wanda ke dauke da Hasumiya,mai tazarar kafa 50 (mita 15 ). Hasumiyar da aka yi daga kasa da rassan dabino.... Hakika birnin Naduka ya hada dukkanin wasu tarin alkhairi na rayuwa da Dan Adam zai bukata. Sai dai birnin ya rabu Kashi biyu Akwai yankin talakawa masu dai dai karfi. Da Kuma yankin masu farcinan Susa Wanda suka tada Kai da kudi... Don haka sai ya zamto masu kudin sun ware wajen su daban...sunyi wa layikan su gate gate suna rufe su da daddare. Kuma akwai yar tazara sosai tsakanin Naduka crescent (Apple island). Da Kuma Naduka zone . Naduka crescent shine matattarar inda masu kudin suke. Kama daga kan masu rawani na sarauta, da Yan siyasa ciki harda bangaren gwamnan birnin da sauran su.. hadadden yanki dai daya tunbatsa da naira ake Kuma gogawa da ita. Wannan Yana bani waje... Kowa da kudin sa wani yafi wani... Sai Kuma bangaren yaku bayi na marasa karfi .... Ana kiran wajen da Naduka zone.. Sai birnin ya zamto tamkar kauye da Kuma cikin babban birni. duk kuwa da unguwa ce kowacce daban.. Amman akwai tarin bambamci Mai matukar yawa a tsakanin su. Duba da yawan gidajen masu tsaunika na benaye, manyan masallatai, wuraren shakatawa, wuraren siyayya na tafka tafkan shagunan more rayuwa na kayan alatu da sauran su... Kuma babbar jami'ar garin ta kudi wadda a kasa akeji da ita Wanda dalibai da yawa na manyan kasashe da garuruwan suna zuwa karatu makarantar. Makarantar kudi ce Bata gwamnati ba sai 'ya'yan wane da wane ne kawai ke zuwa ... Don haka makarantar a babban yankin Naduka take na Naduka crescent da a kewa laqabi da (Apple island) saboda tsabar haduwa da kawatuwar sa. .. birane dadama da wasu kasashen na zuwa hutun yawon bude idanu birnin Naduka.. yanada manyan koramu da suke da ruwa an Kuma gyare su sosai wajen ya zama tourist attractions spot.. ::::::::::::::::::::::::::::: Sai yamma likis zungureriyar motar bus dake tafe da su da kayayyakin su ta sauke su a kofar wani gidah Mai bene da wani a gefen sa shi Kuma na kasa ne ba bene.. Dukkanin su suka firfito daga cikin motar a matukar gajiye saboda sun Sha tafiyar hanya don akwai lokaci /tazara Mai tsawo tsakanin yankin bunza da birnin Naduka.. Nawra ta tsugunna tana bubbuga Yan yatsun kafafunta dake mata ciwo saboda azabar zaman da tayi na tafiyar mota.. "Sannu Nawra..." Cewar abbiey mahaifin su.. Ya fada cikin kulawa... Nawra tayi murmushi tana daga kanta ta gyada shi da sauri tace, "Nagode abbiey........" _INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_ _KU MARMATSO KUSA...🔊_ _ZAFAFA BIYAR 2024_ _ZAFAFA BIYAR!!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_ _YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_ _GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_ _________ _1_ *_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_ _2_ *_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_ _3_ *_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_ _4_ *_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ [2/17, 1:44 AM] Hafsaat🧕: *_KWANKWASON JIMINA!!_* _(MAI WUYAR SHAFAWA)_ 🦩🦯🦾 _✍️: MX_ *_ZAFAFA BIYAR 2024_* _vip pages na arewa👇_ *_arewabooks:mssxoxo_* *_paid page :07_* ______    Ya riko hannun ta suka nufi hanyar shiga gidan na su. Ya yinda mahaifiyar su ke dauke da Amnah a hannun ta tayi baccin gajiya... Sai su Hamma Ashir da Hamma Ashfeef da ke baya... Gidan bene maidaidaici karami sama da kasa shine Wanda yake a matsayin na Bappah junaidu mahaifin su Nawra. Sai dayan Kuma flat shima Mai kyawu maidaidaici bana bene ba shine na Bappah Auwalu da iyalin sa.. Yakumbo Aminatu ita mijin ta bai samu gidah a birnin Naduka ba.. don haka suka samu wani gari daga gabas suka mallaki nasu muhallin.. Bappah salisu Kuma ya samu sauyin wajen aiki... Ma'aikatar da yake aiki sun yi babban kamfanin su mai hade da gidajen maaikatan da zasu zauna aciki har lokacin da zasuyi ritayar aiki ko kamfanin ya sauke su. Don haka shi da iyalan sa suka tattara suka koma can... Bappah sani kuma sun tafi kasar Oman don jinyar Mai dakin sa da ke dauke da lalura.. Don haka a birnin Naduka kawai gidan bappah Junaid ne da bappah Auwalu sai iyalan su.. Cike da maduakakin murmushi marar misaltuwa suka shiga gidan nasu bayan bappah junaidu yasaka mukulli ya bude shi.. ko'ina tsaf tsaf a Kuma gyare mashaa Allahu.. Falo ne maidaidaici daka shiga gidan Mai duake da setin kujeru mashaa Allah. Sai daki guda daya a kasan Wanda yake a matsayin na su Hamma Ashir da Hamma Ashfeef. Sai kitchen maidaidaici da store dinsa aciki. Sai Kuma bandaki a kasan guda daya. Sai matattakalar da Zata sadaka da saman gidan Dakuna ne kawai guda biyu a saman sai bandaki guda daya da wani dan corridor da aka shimfidah Masa sallaya da hijabi a ninke da Kuma charbi. Sai wani dan katako an jera alqur'ani akai da littafin adduoi .. Daki daya daga hagu shine Wanda iyayen nasu zasu zauna aciki. Sai daki Mafi kusa da shi Wanda dama guda biyu me kawai dakunan a sama yayinda kasa keda daya da parlor Baki daya gidan dakuna uku ne.. Biyu a sama da bandaki daya... Dayan dakin su bappah junaidu da maidakin sa mahaifiyar su nawra.sai dakin kusa da shi na su Nawra da Amna. Da bandaki a tsakiyar dakunan... Bandakuna biyu, dakuna uku, sai kitchen da store dinsa.. sai kofar da Zata sadaka da gidan... Daga gefen su kadan Kuma gidan bappah Auwalu ne da matar sa da 'yayan su... Nawra na shiga dakin su ta bude baki tana duban dakin nasu cike da tsantsar kyawu da yayi mata. Dauke dakin yake da katifa babba wadda zata dauki mutane uku.. Sai drawer din su da aka zuba musu kayan sawar su itada Amnah. Tun ta gidah ce Amman aka zamanantar da ita akayi mata fenti... Sai labule me kyawu shima .. Da dan mudubin su da aka kafe musu shi. Gefe daya kuma dakin malale yake da ledar daki sabuwa gadaagal da ita . Nawra ta zauna akan katifar Tasu ta saka hannuwanta biyu akan katifar dake dauke daw filallika har biyu da bargo babba guda daya ya Sha zanin gado . Ta shiga shafawa tana kumshe idanu ba karamin kyau dakin nasu yayi mata ba.. Ta kwantar da kanta ajikin pillow tana duban saman ceiling.. Cikin tunanin data fara lulawa ne ta jiyo muryar mahaifiyar su tana Kiran sunan ta. "Nawra kina ina ne?" "Na'am ammiey... Ga ni nan" Ta amsa da sauri ta fita daga cikin dakin zuwa kasa inda parlon gidan yake. Dukkanin su suna parlorn sun hallara.har Amnah data fara bacci dazu itama ta tashi tana kan cinyar mahaifiyar ta su.. Muje gidan bappan ku a gaysa ko? Sai a huce gajigar gaba daya idan muka gayshe su." "Toh abbiey" Tashi suka yiyyi da ga kan kujerun da suke zaune suka fita daga cikin baki daya suka nufi gidan bappah Auwalu.. Yar tafiya kasan daga cikin bappah Junaid zuwa gidan bappah Auwalu akwai wani karamin daki da yake a matsayin na baki ko da anyi idan sunzo sai su kwan anan.. Amma bisaga rashin Yan uwa a kusa kowanne garin daya ke daban da sauran su. Hakan yasanya bappah Auwalu ya nemi shawarar bappah Junaid kan yadda zasuyi da wajen Inda bappah Junaid ya sheda masa Cewar duk yadda ya yanke yayi. Kuma kasancewa sa babba ya rike dakin kawai don shine babu isassun waje agidan sa. Hakan kuwa akayi. Bayan bappah junaid ya babbawa bappah auwalu baki ya amince ya karba dakin Inda Mai dakin sa ta hora Masa kashin bacin ya bar mata dakin ta zuba kiwon da take. Dakyar ya amince shi ma sai da su bappah Junaid suka saka baki. Ta zuba kaji dakin ya koma akurkin kaji.. kasancewar ba wani shahararren girma ne da shi ba.. ........ Ta a tsaye gaban labule data dage ta hango su a jere suna tahowa gidan su Sun tsaya gaban dakin akurkin kajin Junaid ya saka hannu Yana musu nuni da dakin Yana magana. Alokacin Kuma Amna ce da tambaye tambaye ta ta tsare shi tana jefa Masa tambayoyin shi Kuma Yana Bata amsa dai dai da tambayar da take Masa. Yadda zata Gane kasancewar tana da karancin shekaru.. Tabe baki tayi ta sake labulen tana jan dogon tsaki.,cike da Takaici su . "Menene ummy?" Hanyar daki tayi tana daga mata hannu hade da karkada mata su tace Layla, "Idan sunzo kice bacci nake yi". "To" Daki ta shige zuruf tanata kananun mita. Dai dai lokacin da bappah Auwalu ya futo daga kitchen ya shiga parlorn Yana sallama.. Layla na amsawa sai ga sautin bugun kofar su Nawraah.. "Waye?" "Layla bude, Mu ne"... Da sauri har tana tuntube taje ta bude musu kofar... _INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_ _KU MARMATSO KUSA...🔊_ _ZAFAFA BIYAR 2024_ _ZAFAFA BIYAR!!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_ _YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_ _GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_ _________ _1_ *_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_ _2_ *_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_ _3_ *_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_ _4_ *_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ [2/17, 2:01 AM] Hafsaat🧕: *_KWANKWASON JIMINA!!_* _(MAI WUYAR SHAFAWA)_ 🦩🦯🦾 _✍️: MX_ *_ZAFAFA BIYAR 2024_* _vip pages na arewa👇_ *_arewabooks:mssxoxo_* *_paid page :08_* ______    A tare suka shiga ciki baki dayan su, bakunan su duake da sallama. Kana shiga gidan parlor zaka fara cin karo dashi. Dake dauke da kujeru da karamar tv da kayan kallo. Daga hannun daman ka kuma dakuna ne biyu daya Yana kallon daya. Sai bandaki dake tsakiyar su.. Daga can kofar corridor Kuma kitchen ne da karamin store dinsa aciki. Sai yar farfajiyar tsakar gidan su mai shuke shuke da wasu kujeru guda biyu tsofi ne na gidan da suka taso da wani dan teburi a tsakiyar su. Sai wajen ya hadu ya bada ma'ana sosai. Daki daya daga ciki duake yake da gado da drawer harda mudubi. Nan ne yake a matsayin dakin bappah Auwalu da Mai dakin sa. Sai daki Mai kallon sa Kuma na Ahmad ne yayan layla Wanda tsaran shekarun nasu ba yawa. Kasancewar dukkanin su Yara ne basu mallaki hankalin kansu ba. Hakan yasa bappah Auwalu Cewar dakin ya zama na Ahmad Amma yar katitar Layla na gefe sai ta runga kwana. Mahboub yace yaci girma ya bar mata dakin. Shi zai rika fito da katifar sa parlor Yana kwanciya. Domin shi yafu kaunar parlorn ma acewar sa... "Nawraah" "Uhm.. Layla" Kamo hannun Nawraah Layla tayi suka shiga parlorn suka zauna... Kawu Auwalu yafuto daga kitchen daya shiga Shan ruwa Yana murmushin ganin su. Fuskar sa akan Dan uwan nasa yace, "Junaidu ne? Ku karaso ku zazzauna mana" Bappah junaidu ya durkusa har kasa Yana gayda yayan nasa. Bappah Auwalu ya amsa fuskar a sake "Ka koma kan kujerar ka zauna Dan Allah. " Daya bayan daya su nawrah suka shiga gayshe shi ciki harda mahaifiyar su data durkusa itama sosai cike da ladabi da biyayya ta gayshe da wan mijin nata. Ya amsa musu fuska a sake duka... "Layla Ina umman na ku?" "Tana daki ".. "Je kice mata ga bappan ku nan sunzo da su nawrah kice ta taso su gaysa." "Ah idan ta kwanta a kyale ta . Ma sake dawowa mu gaysa a tsanake inshaa Allah"Cewar malama Hindu. "Aa ataso ta dai... Yanzun ta tashi daga nan anan na barsu dasu Layla.. jeki kirata ke" Layla ta mike tana yamutsa yatsunta ta nufi dakin mahaifiyar tasu. Ta Dan bubbuga kofar Kafin ta saka Kai ta shiga bakinta dauke da sallama, Tana shiga ta tarar da ita akan gado tana zaune tana kallon kofar, "Ummy bappah ne ke Kiran ki yace kizo su bappahn nawrah sunzo.." "Naji ... Kema can daya Mai abun haushi sai kice Mai Kai na na ciwo haka ba sai an taso ni ba" "Yo hakuri" "Je ki" Layla ta fita tana kakaro murmushi tace, "Wai tana zuwa" "Ko a kwance take ne na shiga na dubata?" Malama Hindu ta tambayar, "Aa fa " Fitowa tayi daga daki tana bude baki tamkar gonar auduga tache, "Gajiya ce ta mamaye ne shine na Dan kwanta ko zan ji dama. Bappan su Ina wunin ku? " "Dama nace ko jiki ne? Sannu ya kike ji yanzu?" Malama Hindu ta tambaye ta, "Alhamdulillah naji dama sosai .." "Sannu Allah yakara afuwa" Cewar bappah junaidu "Aamin bappan su " Daya bayan daya su nawrah ma suka gayshe ta cike da ladabi Kai kace wasu sabbin baki ne daga wajen bayan dazu suka rabu amman saboda tsananin tarbiyya tun sanda suna yankin bunza ma haka suke gaisuwar safe da ta rana data dare daban cike da ladabi da dinbin biyayya... Ki nunnuna musu yadda akayi jeren ko nusaiba? Cewar mijinta bappah Auwalu. "To bappansu Mai zasu gani anan gidan. Amma dai muje. Nan din fa iya kasa ne bamu da sama" malama nusaiba ta fada tana mikewa tsaye Basuyi mamakin kalamanta ba don ba ranar ta fara ba. Don haka malama Hindu tace, "Haba bappah ai munsan gidan kamanta duk tare mukai komai? Ai ana tare muma komawa zamuyi mu Dan sake kikkintsa inda ya kamata" "Yo ai dake musanman tunda ku gidan sama ne daku. Ga bene ko'ina fala fala babu matsatsi ba kanara Nan ba da dakuna biyu ne jalllin jal" Malama Hindu batayi magana ba murmushi kawai tayi ta mike tana kamo hannun Amna autar ta. Bappah auwalu kunya ta sake dabaibaye shi tamkar kasa ta tsage ya fada haka yake ji. Cikin kakaro murmushi dayafi kuka ciwo yace, "Junaidu kaga an zuba tumakin da Yan kajin fa mashaa Allah. Allah ya saka maka da alkhairi ya kara arziki. Nusiaba kin sake Masa godiya kuwa?" Malama nusaiba tana soso kasan gashin ta ta cikin dankwali tace, "Sosai ma. Mungode kwarai . Nan gaba ma kawak sai a bige a shigo da shi cikin nan gidan muma ya zama dakuna uku kamar su" Bappah A. ya saka yatsa a baki ya ciza Takaici ya sake gauraye Masa wuya da ilahirin jikin sa baki daya ji yake tamkar ya hau nusaiba Mai dakinsa da bugun tsiya ya bude kofar Yana cewa, "Muje ka gani junaidu... Allah dai ya bar zumunci ya saka maka da alkhairi" "Aamin** suka amsa baki daya Banda nusaiba da ke tabe baki Dan dakin abun kiwon sika nufa. Dauke da tumakin biyu da akuya daya sai kaji zasuyi goma. "Kagani ko ? Wallahi kamar Dan su aka Gina shi komai da komai ya yi mashaa Allah" "Gashi nan kam Allah yasa albarka Amin" "Aamin Aamin" "Laaa ga kwai Ina so..." Amnah ta fada Hadi da shiga cikin dakin ta dakko Kwan kajin har biyu. "Jeki ajiye* "A bar mata Mana ai na uwar ta ne" bappah Auwalu ya fada Yana wa nusiaba murmushi. Ta kakaro murmushin yake tana cewa, "Dauki mana Amnah... A soya Miki Kona dafa Miki kici kinji?" "Nagode" Amnah ta fada da sauri tana gudu "Sannu da miskri Allah ya bar zumunci ya kara arziki su zama garke" malama Hindu ta dubi malama nusaiba tana mata godyar kwai data bajwa Amnah Daga nan kuma suka koma nasu gidan bayan sun musu sai da safe. ... Malama nusaiba tabu bayan su da kallo tana Mai tabe bakin ta ta koma cikin gidan nasu tana jera tsaki.. "Kul kika sake daukar abunda baa baki ba baa ce Miki gashi ba kinaji na ko?" "Eh... Bazan sake ba ammeiy kiyi hakuri" Amnah ta bawa mahaifiyar tasu hakuri "Ya wuce... A dafa Miki ko a soya? " " A soya" "Yauwa... To jeki parlor ki zauna kinji idan aka soya sai a kawo Miki" Amnah ta koma parlor da sauri ta zauna akan kujera tanata murna. Malama Hindu ta nufi wajen kwanuka ta dauki wani Dan karamin mazubi ta fasa Kwan aciki Kallo daya zakai nata kasan ita din mahaifiyar su nawrah ce duba tsananin kamar da suke yi da yaran nata duka. Duk kuwa da sun dauki kamannin mahaifin na su ma ciki harda tsawon sa da gashin hirar sa Zara Zara masha Allah... _INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_ _KU MARMATSO KUSA...🔊_ _ZAFAFA BIYAR 2024_ _ZAFAFA BIYAR!!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_ _YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_ _GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_ _________ _1_ *_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_ _2_ *_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_ _3_ *_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_ _4_ *_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ [2/17, 2:20 AM] Hafsaat🧕: *_KWANKWASON JIMINA!!_* _(MAI WUYAR SHAFAWA)_ 🦩🦯🦾 _✍️: MX_ *_ZAFAFA BIYAR 2024_* _vip pages na arewa👇_ *_arewabooks:mssxoxo_* *_paid page :09_* ______   Muhammad Junaid hamidniyya shine cikakken asalin sunan mahaifin su Nawraah... Kuma shine 'da na karshe ga marigayiya yafendo. Haka zalika karamin kani ga su Bappah Auwalu. Hindu Musa shine sunan mai dakin sa kuma mahaifiya ga su nawrah da sauran yan uwanta. Hindu da Junaid yan uwane wanda ke karkashin inuwa daya ta zumunta. Kuma aka hada auren su auren zumunci wanda yayi dadi. Don shekaru da yawa kenan tunda aka yi hadin auren su gashi har sun Tara iyalin kansu. Baa taba jin fadan su ba ko cacar baki. Auren su ya kasance Mai Dadi Mai tattare da sirri domin ko yaji Hindu Bata taba yi ba. Duk kuwa da kowanne aure ana samun sabani don tsakanin harshe da hakori ma ana sabawa don haka Koda sunyi fadan babu Wanda ke jin kansu ko da kuwa iyayen su. Su kan shirya kansu su sulhunta. Hakan yasa Ko a dangi ake kwatance da su idan zaa kulla auren zumunta ko idan ana jan kunnen sabbin ma'auratan akance da su suyi koyi da iyayen su Yakumbo Hindu da Bappah junaidu... Da mahaifiyar Hindu Marigayiya Yagwalgwal Fatime Domin ita ta Dade da rasuwa tun ana goyan Nawraah, da Kuma  Marigayiya yafendo mahaifiyar junaidu yar wa da yar kani ce.. Don haka iyayen su Kanwa da Yaya ne wadanda iyayen su suka fito tsatso daya... Kasancewar tsatson na su larabawa ne na yankin Lebanon gefe daya kuma suka hada zuri'ah Mai tarin yawa daga fulanin yankin bunza ta hangar auratayya. Hakan yasa zuriyar tasu ficewa gaba saboda tsananin kyawun su da dabi'unsu na nagarta. Masu dinbin tarin arzuka Kafin mahara su Kai wa yankin sumame suka kwakushe masu tattalin arzikin su cikin Kashi uku ba Kashi biyu... Allah ya azurta Hindu Musa da Junaid hamidniyya da Yara Kadan masu tarin albarka, Ashir shine babban Dan su, Sai mabiyin sa Ashfeef , Sai Kuma Nawrah sai autar su Amnah shikenan su hudu. .Maza biyu mata biyu Hakika junaidu da Hindu sunyi wa yaran na su tarbiyya sosai da sanin yakamata Dan ko a yaran dangi ana yabon su saboda tsananin biyayyar su da sanin yakamata.. Suna kiran yan uwan iyayen nasu wasu da Bappah wasun su Abu kaza, idan bangaren mata ne sukan Kira su da yagwalgwal kaza ko yadukko, ko Maamaa tamkar yadda larabawa ke kiran iyayen su. Wani abunda zai Kara kayatar da zuciyar Mai karatu shine akwai biyayya sosai tsakanin Yan uwan. Kowanne Yana bin Mai bi Masa a shekaru. Babban want nasu kuwa wato ashir sun dauke shi tamkar mahaifin su junaidu. Domin duk kuwa da shekarun sa shima Bai wani manyanta can ba. Amman duk da hakan Yana tsaye akan Yan uwan nasa tamkar mahaifin su. Da aljihun sa da karfi sa Yana kokarin killace Yan uwan nasa musanman matan tana basu tsark sosai da kulawa ta musanman dubada mata na da rauni. Ga su Kuma kanana ba masu shekaru ba.. Duk kanin yaran na su sun dauka tsatson iyayen na su. Sunada matukar kyawu mai Sanya a sake kallon suakaro na baadadi. Dogaye ne dubada shekarun su ba su njsa ba duka.amman kowanne yayau tsawon kafa acikin su tubarkallah.. Sirara ne basu cika kiba ba.. Amman ranar batai musu nuni ba ainun ba. Gashin su duka mazan da matan wani irin kanannade ne awaraare juma bakukkirin da shi na larabawa usul. gashin a cike yake a Kuma chure Mai tsananin santsi da laushi ..gaban gashin girayr su a kwance baki sidik da shi a Kuma cike. Domin girar kowannen su tsabar cika ta kusa hadewa ma.. Kyawawa ne sosai Wanda alkalami yayi kadan wajen zayyano irin kalma kyawun yawon da Allah ya halitta akan su. Ba abunda zance sai dai mu bisu da cewar tubarkallah don kwarai matuka Allah yayi halitta.. Dawowar su ba dadewa sosai aka Sanya yaran Maza a makarantar boko da islamiya. Haka ma matan suma an Sanya su a islamiyar kadai ba bokon dubada al'adar yankin bunza inda suka tashi tun taletale mata basa karatun boko saboda wani labari Mai raba zuciya daya taba aukuwa akan wata yarinyar da malamin makarantar yayiwa fyade har ta mutu. Kuma malamin irin masu visiting dinnan ne daya aikata abunda zai aikata sai ya gudu ya bar yankin baa sake sanin inda yake ba. Wannan abune ya dasa tsoro Mai tasiri a zukatan iyaye mata da dattikai na yankin bunza . Inda aka yanke shawara bayan anyi gangami anyi taro aka Sanya dokar Hana Yara mata karatu gabw daya na boko sai dai islamiya wadda makarantar Yan cikin yankin ne kowa ya San su... Duk kuwa da abunda ya farun yayi shekaru da shudewa Amman ko sau daya baa taba cewa yakamata acire dokar ba. Kowa ya hakura Yara mata suka Dena karatu. Tun kafin a haifi Nawraah. Don shekarun bayan ashiir ne kawai sai Ashfeef Sai sauran yan manyan yaran dangi.. Nawraah ta kasance maabociyar son karatun boko. Don haka takan labe a kofar ajin tana sauraron karatun da ake koyarwa su Ashfeef a makarantar. Har ya kasance tana daukar littafin Ashfeef din tana koyin rubutu tana Kuma karantawa. Tun Bai sani ba har ya kamata yayi yayi bai hanata ya kasa saboda yadda taketa rokon sa tana kuka haka ya jyaketa daga baya ma sai ya zamto yakan koya mata a boye kar iyayen su Gani ko ya Bata littafin sa ta koya. Harr dai ya saya mata Dan kirraci take koyan rubutu da karatun acikin sa da dan fensurin da ya bata.. Duk abunnnan babu Wanda ya sani sai Ashfeef da ashir daya sani daga baya sai Kuma autar su Amnah data kana yayar tata nawrah tana karatu inda nawrahn ta zaunar da ita ta gaya mata komai tana rikon ta duk kuwa dakankancin shekarun amnan da basu taka kasa sun karya ba. A boye take koyan karatun da rubutun. . Ba Wanda ya sani daga wajen Yan uwa bayan yayyaun ta da kanwata Amnah Amnah sai Layla yar gidan bappah Auwalu wadda suka taso tare aminan juna. Don wata uku ne tsakanin su kawai Layla tabawa nawrah . Shekaran n su daya gashi komai tare suke yi.. Haka dai nawrah ta rike su bisaga Amana Kar su fadawa iyayen nasu don zaa hanata a Kuma mata babban hukunci. Suka rike mata amanar kuwa basu taba fada ba ita ma Kuma nawrahn ta Ina takunta ba a taba kamata ba sanda take rubutun, take Kuma karahrawar... Haka Sika cigaba da rayuwa a sabon yankin da suka dawo ... Bappah junaidu da iyalan sa su Nawraah da Kuma bappah Auwalu da nasa iyalan.. Nusaiba itace Mai dakin bappah auwalu.. ita ba auren zumunci bane gari daya ne kawai ya hada su na bunza. Amman itama tsaton fulanin bunza ce. Allah ya azurta su da yaran su su biyu jachak, Ahmad shine na fari Wanda saan Ashfeef ne yayan nawrah, sai Kuma Layla din da take tsaran nawrah.. ___ Haka rayuwar ta cigaba da garawa da Dadi ba Dadi ... Bappah junaidu Yana aikin kera karfe zuwa na zamanj a wata masana'anta. Ya zuba dukiyar sa baki daya ya sassayi ahubbun amfani inda ya bawa matar sa jari na tafara awarar sayarwa Nan da Nan kuwa Allah ya sanyawa kasuwar albarka. Burni da kewayen yankin zuwa ake ana saya har layi ake yi Rayuwar sai hamrala kawai, don Ashfeef da Ashir ma sukan je masaaniyar mahaifin nasu su tayashi aikin fenti da sauran su .. da wannan sike rufawa kansu asiri musanman da yanzun babu tarin dukiyar da suke da ita a baya Kafin a yiwa yankin bunza hari...... [12/25/2023, 7:14 PM] Hafsaat🧕: _INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_ _KU MARMATSO KUSA...🔊_ _ZAFAFA BIYAR 2024_ _ZAFAFA BIYAR!!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_ _YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_ _GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_ _________ _1_ *_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_ _2_ *_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_ _3_ *_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_ _4_ *_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ [2/17, 2:17 AM] Hafsaat🧕: *_KWANKWASON JIMINA!!_* _(MAI WUYAR SHAFAWA)_ 🦩🦯🦾 _✍️: MX_ *_ZAFAFA BIYAR 2024_* _vip pages na arewa👇_ *_arewabooks:mssxoxo_* *_paid page :09_* ______   Muhammad Junaid hamidniyya shine cikakken asalin sunan mahaifin su Nawraah... Kuma shine 'da na karshe ga marigayiya yafendo. Haka zalika karamin kani ga su Bappah Auwalu. Hindu Musa shine sunan mai dakin sa kuma mahaifiya ga su nawrah da sauran yan uwanta. Hindu da Junaid yan uwane wanda ke karkashin inuwa daya ta zumunta. Kuma aka hada auren su auren zumunci wanda yayi dadi. Don shekaru da yawa kenan tunda aka yi hadin auren su gashi har sun Tara iyalin kansu. Baa taba jin fadan su ba ko cacar baki. Auren su ya kasance Mai Dadi Mai tattare da sirri domin ko yaji Hindu Bata taba yi ba. Duk kuwa da kowanne aure ana samun sabani don tsakanin harshe da hakori ma ana sabawa don haka Koda sunyi fadan babu Wanda ke jin kansu ko da kuwa iyayen su. Su kan shirya kansu su sulhunta. Hakan yasa Ko a dangi ake kwatance da su idan zaa kulla auren zumunta ko idan ana jan kunnen sabbin ma'auratan akance da su suyi koyi da iyayen su Yakumbo Hindu da Bappah junaidu... Da mahaifiyar Hindu Marigayiya Yagwalgwal Fatime Domin ita ta Dade da rasuwa tun ana goyan Nawraah, da Kuma  Marigayiya yafendo mahaifiyar junaidu yar wa da yar kani ce.. Don haka iyayen su Kanwa da Yaya ne wadanda iyayen su suka fito tsatso daya... Kasancewar tsatson na su larabawa ne na yankin Lebanon gefe daya kuma suka hada zuri'ah Mai tarin yawa daga fulanin yankin bunza ta hangar auratayya. Hakan yasa zuriyar tasu ficewa gaba saboda tsananin kyawun su da dabi'unsu na nagarta. Masu dinbin tarin arzuka Kafin mahara su Kai wa yankin sumame suka kwakushe masu tattalin arzikin su cikin Kashi uku ba Kashi biyu... Allah ya azurta Hindu Musa da Junaid hamidniyya da Yara Kadan masu tarin albarka, Ashir shine babban Dan su, Sai mabiyin sa Ashfeef , Sai Kuma Nawrah sai autar su Amnah shikenan su hudu. .Maza biyu mata biyu Hakika junaidu da Hindu sunyi wa yaran na su tarbiyya sosai da sanin yakamata Dan ko a yaran dangi ana yabon su saboda tsananin biyayyar su da sanin yakamata.. Suna kiran yan uwan iyayen nasu wasu da Bappah wasun su Abu kaza, idan bangaren mata ne sukan Kira su da yagwalgwal kaza ko yadukko, ko Maamaa tamkar yadda larabawa ke kiran iyayen su. Wani abunda zai Kara kayatar da zuciyar Mai karatu shine akwai biyayya sosai tsakanin Yan uwan. Kowanne Yana bin Mai bi Masa a shekaru. Babban want nasu kuwa wato ashir sun dauke shi tamkar mahaifin su junaidu. Domin duk kuwa da shekarun sa shima Bai wani manyanta can ba. Amman duk da hakan Yana tsaye akan Yan uwan nasa tamkar mahaifin su. Da aljihun sa da karfi sa Yana kokarin killace Yan uwan nasa musanman matan tana basu tsark sosai da kulawa ta musanman dubada mata na da rauni. Ga su Kuma kanana ba masu shekaru ba.. Duk kanin yaran na su sun dauka tsatson iyayen na su. Sunada matukar kyawu mai Sanya a sake kallon suakaro na baadadi. Dogaye ne dubada shekarun su ba su njsa ba duka.amman kowanne yayau tsawon kafa acikin su tubarkallah.. Sirara ne basu cika kiba ba.. Amman ranar batai musu nuni ba ainun ba. Gashin su duka mazan da matan wani irin kanannade ne awaraare juma bakukkirin da shi na larabawa usul. gashin a cike yake a Kuma chure Mai tsananin santsi da laushi ..gaban gashin girayr su a kwance baki sidik da shi a Kuma cike. Domin girar kowannen su tsabar cika ta kusa hadewa ma.. Kyawawa ne sosai Wanda alkalami yayi kadan wajen zayyano irin kalma kyawun yawon da Allah ya halitta akan su. Ba abunda zance sai dai mu bisu da cewar tubarkallah don kwarai matuka Allah yayi halitta.. Dawowar su ba dadewa sosai aka Sanya yaran Maza a makarantar boko da islamiya. Haka ma matan suma an Sanya su a islamiyar kadai ba bokon dubada al'adar yankin bunza inda suka tashi tun taletale mata basa karatun boko saboda wani labari Mai raba zuciya daya taba aukuwa akan wata yarinyar da malamin makarantar yayiwa fyade har ta mutu. Kuma malamin irin masu visiting dinnan ne daya aikata abunda zai aikata sai ya gudu ya bar yankin baa sake sanin inda yake ba. Wannan abune ya dasa tsoro Mai tasiri a zukatan iyaye mata da dattikai na yankin bunza . Inda aka yanke shawara bayan anyi gangami anyi taro aka Sanya dokar Hana Yara mata karatu gabw daya na boko sai dai islamiya wadda makarantar Yan cikin yankin ne kowa ya San su... Duk kuwa da abunda ya farun yayi shekaru da shudewa Amman ko sau daya baa taba cewa yakamata acire dokar ba. Kowa ya hakura Yara mata suka Dena karatu. Tun kafin a haifi Nawraah. Don shekarun bayan ashiir ne kawai sai Ashfeef Sai sauran yan manyan yaran dangi.. Nawraah ta kasance maabociyar son karatun boko. Don haka takan labe a kofar ajin tana sauraron karatun da ake koyarwa su Ashfeef a makarantar. Har ya kasance tana daukar littafin Ashfeef din tana koyin rubutu tana Kuma karantawa. Tun Bai sani ba har ya kamata yayi yayi bai hanata ya kasa saboda yadda taketa rokon sa tana kuka haka ya jyaketa daga baya ma sai ya zamto yakan koya mata a boye kar iyayen su Gani ko ya Bata littafin sa ta koya. Harr dai ya saya mata Dan kirraci take koyan rubutu da karatun acikin sa da dan fensurin da ya bata.. Duk abunnnan babu Wanda ya sani sai Ashfeef da ashir daya sani daga baya sai Kuma autar su Amnah data kana yayar tata nawrah tana karatu inda nawrahn ta zaunar da ita ta gaya mata komai tana rikon ta duk kuwa dakankancin shekarun amnan da basu taka kasa sun karya ba. A boye take koyan karatun da rubutun. . Ba Wanda ya sani daga wajen Yan uwa bayan yayyaun ta da kanwata Amnah Amnah sai Layla yar gidan bappah Auwalu wadda suka taso tare aminan juna. Don wata uku ne tsakanin su kawai Layla tabawa nawrah . Shekaran n su daya gashi komai tare suke yi.. Haka dai nawrah ta rike su bisaga Amana Kar su fadawa iyayen nasu don zaa hanata a Kuma mata babban hukunci. Suka rike mata amanar kuwa basu taba fada ba ita ma Kuma nawrahn ta Ina takunta ba a taba kamata ba sanda take rubutun, take Kuma karahrawar... Haka Sika cigaba da rayuwa a sabon yankin da suka dawo ... Bappah junaidu da iyalan sa su Nawraah da Kuma bappah Auwalu da nasa iyalan.. Nusaiba itace Mai dakin bappah auwalu.. ita ba auren zumunci bane gari daya ne kawai ya hada su na bunza. Amman itama tsaton fulanin bunza ce. Allah ya azurta su da yaran su su biyu jachak, Ahmad shine na fari Wanda saan Ashfeef ne yayan nawrah, sai Kuma Layla din da take tsaran nawrah.. ___ Haka rayuwar ta cigaba da garawa da Dadi ba Dadi ... Bappah junaidu Yana aikin kera karfe zuwa na zamanj a wata masana'anta. Ya zuba dukiyar sa baki daya ya sassayi ahubbun amfani inda ya bawa matar sa jari na tafara awarar sayarwa Nan da Nan kuwa Allah ya sanyawa kasuwar albarka. Burni da kewayen yankin zuwa ake ana saya har layi ake yi Rayuwar sai hamrala kawai, don Ashfeef da Ashir ma sukan je masaaniyar mahaifin nasu su tayashi aikin fenti da sauran su .. da wannan sike rufawa kansu asiri musanman da yanzun babu tarin dukiyar da suke da ita a baya Kafin a yiwa yankin bunza hari...... _INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_ _KU MARMATSO KUSA...🔊_ _ZAFAFA BIYAR 2024_ _ZAFAFA BIYAR!!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_ _YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_ _GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_ _________ _1_ *_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_ _2_ *_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_ _3_ *_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_ _4_ *_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ [2/17, 2:44 AM] Hafsaat🧕: *_KWANKWASON JIMINA!!_* _(MAI WUYAR SHAFAWA)_ 🦩🦯🦾 _✍️: MX_ *_ZAFAFA BIYAR 2024_* _vip pages na arewa👇_ *_arewabooks:mssxoxo_* *_paid page :10_* ______ *BABBAN BIRNIN NADUKA* _(FEDERAL CAPITAL TERRITORY)_ _NADUKA ZONE!!_ ______      Kasancewar yanayin damuna ne, babban birnin Naduka sun samu rahamar ruwan sama sosai tamkar da bakin kwarya... Domin ruwan har gyara yayi awasu wajajen.... Wasu daga cikin gidajen Naduka zone da ke na kasa wasu sun zube, Wasu barin su ya rushe. Wasu Kuma ruwan ya mamaye gidan. Alhamdulillahi. Ruwan yayi gyara sosai don kwatoci ma sun cika makil. Sai samari da dattawa mazan ne suka hada karfi wajen gyara unguwannin. Aka furfuto masu shanya nayi masu kwalema nayi . Garin yayi matukar sanyi mashaa Allah abunda zaa iya cewa kenan... Bishiyu sai kadawa suke, Iska Mai Dadi na ratsa ilahirin birnin da kewayen sa. Ciyayi sun Kara zama koraye shar. Alhamdulillah ni'imar Allah ta sauka a ko'ina... 'Ashir ne tsugunne agaban murhu yanata fifitawa da mahuci, Sanadin ruwan da akayi yayi gyara baki daya itatuwan mutuwa sike saboda danshi.. Sai anyita fiffitawa..Haka ya gwaggwafe Yana fifita wutar sosai tamkar wata mace... Sanye yake cikin kananun Kaya na gidah. Mahaifiyar su malama Hindu ta fito daga cikin gidah hannunta dauke da katon tray da awara sai turiri take da alama yanzun ta sauketa a wuta. "Sannu Hamma (dake haka take ce mai kasancewar sa dan fari a gare ta) sannu da kokari.. kawo Nan na tayaka" "Aa Ummy ai tama kama Ina man yake?" "Gashi can bayan Kofa. Laa tabbas ta kama Allah ya shi maka albarka" "Aameen ummy" "Ina Ashfeef ?" "Nace Masa yaje ya huta ummy. Dan Allah karki ce komai" Malama Hindu tayi murmushi, Zancen dai kenan kamar ko da yaushe. Ta dube shi tace,.. "Ba zaka dena jika kannen naka ba ko Hamma?" "Ummy idan ban jika su ba wasuke da shi bayanni?" Yakarasa fada Yana murmushi. Itama murmushin tayi ta gyada kawai tace, "Toh Allah ya muku albarka gaba daya Aameen" "Allahumma Aameen" Nan da nan ya dakko man ya dora akan wuta tuni daman sun rage hanya ta hanyar soyashi da lawashi sai kamshi ke tashi. Yana fara zafi Ashir yaja kujerar tsugunno wajen murhun ya shiga tsoma awarar cikin ruwan kwai daya Sha kayan hadi yanaa saka ta amai. Mahaifiyar ta su na gefe tana shi Masa albarka. Nan da Nan kuwa aka fara yin layin awarar wasu da kulolin su na abinci wasu Kuma a Leda zaa saka musu wasu Kuma a takeway pack zaa sa musu a nade da kyauro. Cikin haka su Nawraah suka dawo daga islamiya itada Layla.. "Sannu da aiki Yakumbo" Layla tace da Malama Hindu "Ummy sannu da aiki... Laa icen ya huru? Sanu ummy sannu Hamma" Nawraah ta fada tana zare hijabin makarantar islamiyar kalar ruwan omo.. "Sannun ku duka Allah yabada ladan karatu .. ungo Layla kuje ku hada da abinci" Layla ta saka hannu ta karbi bakar ledar da malama Hindu ta Mika mata cike da awara sai kamshin yajin tafarnuwa ne ke tashi ga coleslaw shima a gefe da kayan su tumatir. "Angode" Ta nufi gidah da sauri tana murna, Don dama Koda yaushe sai malama Hindu ta aika musu da awara fal ko saya bappah Auwalu ya Aiko ayi hanawa take tace a mayar masa da kudin ta zuba musu kyauta. Kamar ko da yaushe don kusan kullum ita take kaiwa saboda da yamma ake farawa wani lokacin da rana don haka da sun taso islamiya malama Hindu zata bata tace ta Kai gidah.. Ta shjyga cikin gidan nasu da sauri bakinta dauke da sallama, "Umma gashi" Ta mikawa mahaifiyar su nusaiba ledar awarar, bappah Auwalu na daga gefe Yana duban su, "Meye wannan din dalla kina baromin Abu a Ido" "Awara ce inji yakunbo" Mtscew taja tsaki tana hararar ta, "Awarar ce kika tsaya kerere a akai na sai kace wani babban Abu nazo mu gani ko na nama haka? Matsa daga nan Kafin na Kai Miki gula aciki na hanbare ki" ta karasa tana sake dankara mata harara, "Kawo nan Layla. Je ki cire kayan makarantar kinji?" "Toh Bappah" Ta nufi wajensa ta Mika amsa awarar jikinta a sanyaye ta nufi daki. Ya dubi matar tasa ta sauke kanta tana hada yatsunta yace, "Ba Zaki dai na wannan halayen na ki ba ko nusaiba! Awarar ajiya muka basu da kullum sai sun Aiko mana kyauta?" "Yo ai sunada kudin ne. Don sun tsinnana mana da awara da me Allah zai rage su" Tsaki yaja shima Yana karkada mata hannu yace, "Dakin da kike kiwon ki kudi kike biya ko kyauta sukutum junaidu ya dauka ya baki iye? Ko wani abun ki saya ki basu na karamci amman kin ki" "Kyauta ce mana.. yo wancen akurkin dakin ai sai da ya tabbatar Dan Adam ba zai iya kwana aciki ba ko da kuwa Rai daya ne bare yace zai ci moriyar sa shine ya jefe ni da shi. Su kansu kiwon Dakyar suke nunfashi saboda azabar zafi da dubu ba wundo ba a dakin haba haba Dan Allah. " Mikewa bappah Auwalu yayi Yana girgiza kai cike da Takaici Mai tattare da dinbin bacin ran dake fitowa daga bakinta yace, "Tunda hakan be Miki ba kyautar tazo da sakayya Mai cin mutincin to ki tattara ki kwashe kiwon ki ki mayar musu da mukullin dakin su" Dariya ta saki tana tabe haba Hadi da tada hannuwa tana shewa tace, "Lalle Auwalu wallahi ni dariya ma kake bani wai daki . Wancen akurkin ne daki? Wancen Dan ficicin wajen kamar bandakin kaji zaka ce mun daki? Koda yake banga laifin ka ba duk wata Yana sanmaka sadaka fisabilillahi ai shysa idanuwanka sika rufe baka ganin lefin su. Batin na mayar musu da mukullin na kwashe kiwon na Kuma ba zan ba. Nace bazan kwashe din ba. Raba Arne da makami ibada ne. Don sun dau wancen shirme wajen cikin tarin dukiyar su ta Ina Allah zai rage su? " Bappah auwalu yayi kwata Yana cije kasan labban sa yace, "Wadatar zuciyaa ce kawai da junaidu da iyalin sa alhamdulillah. Domin kowa sheda ne junaidu ya sayar da sauran kadarorin sa da sukai ragowa ya fara harkar kasuwancin Nan da ita ya sanwa Mai dakin sa take awara suka taru suke rufawa junan su asiri. Nan danacee maki ga dubu uku ki fara sanaa kema ai kikayi don haka karki sake kawo mun sukar Yan uwan kinji na gaya Miki" Yana gama magana ya saka Kai ya shige kitchen tabi bayansa tana sakee fashewa da dariya tana harara tana mita, "Dubu uku... Allah ya kwashewa dubu ukun Nan albarka. Wallahi Auwalu nafi karfin dubu. Wacce sanaar Zan fara da dubu. Har da wani mun gori wai kar na karar kawo sukar Yan uwan ka. Yo ai ba sai kamin gori ba. Abunda naka gajiya da fada kullum nasan junaidu da Hindu Yan uwanka ne na jini dukkan su. Mtscew aikin kawai" Ta shige daki ta tana bugo kofar garam. Bappah auwalu ya tabe kansa kawai yana juye awarar ababban tray... :::::::: Wata hadaddiyar luntsumemwniyar mota ce ta faka a daidai kofar gidan... Sliding mirror din bayanta tayi na owners corner tana hangar dandazon layin awarar.. "Hajiya kinga layin ko! Yasin Kuma duk Wanda na roka abani basa yadda Yan taurin Kai ne Mutanen dake layin" Agogonta ta sake kalla lokaci na gogawa. Cikin ta sai kugin yunwa yake gashi awarar kawai take son ci. Batace masa komai ba ta bude kofar motar ta futa...Kallo daya zakai mata kasan wannan daga jinsin masu farcinan Susa tafito. Dubata kayan dake jikinta kadai ma abun kallo ne tabbas kudi yayi kuka awajenta. Agogon dake daure awutsiyar hannunta Rolex ne latest design na shekarar. Jakar hannunta samfurin hems. Fara ce sosai tamkar baturiya, fatar ta sai sheki take duk kuwa da katon sunglasses din prada designer dake sakale a idanunta...Kai tsaye ta shige cikin gidan tamkar ta San masu gidan....... [2/21, 6:52 AM] Hafsaat🧕: *_KWANKWASON JIMINA!!_* _(MAI WUYAR SHAFAWA)_ 🦩🦯🦾 _✍️: MX_ *_ZAFAFA BIYAR 2024_* _vip pages na arewa👇_ *_arewabooks:mssxoxo_* *_paid page :11_* ______ ::::::::::::::::   ***Bakinta dauke da sallama a gayance ta shiga cikin gidan har yar rumfar da Malama Hindu da yaran nata ke zauna suna ta tuyar awara har kasake biyu manya. Ga layi mashaa Allah anata shige da fice na sayan daddadar awarar... Saboda awarar na da matukar dadi ga laushi mai tattare da kwai daya lullubeta. Tasha kayan hadi. Ga tumatir da albasa cucumber a yanke a gefe da Kuma yajin tafarnuwa sai kamshin kayan kamshi yake yi... Babban al-muhim Kuma awarar akwai tsafta. Komai a tsaftace idan kaje saya. Harta abun daukar awarar aware yake a gefe da ledar hannu ta dauka itama. Don haka Yan hayu masu kudin birnin Kai har ma da talakawan ma siya sukeyi... Ga faraa da karanci da malama Hindu da yaranta ke nunawa masu sayar awarar ta su.... Wannan yasa da karfin addua da istigfari da shimfidar fuska da Kuma kyautatawa irinta Hindu da ahalin ta yasa baki daya mutane ke kaunar awararta. Don kullum sai ta kare idan anzo saya babu duk yawanta....    Ta lumshe idanun ta ta bude a lokacin data karasa inda suke suyar awarar. Malama Hindu ta daga Kai da sauri duk suka juya suna kallonta hadi da amsa sallamar da tayi Kafin daya bayan daya su shiga gayshe ta. Ta amsa fuskar ta a sake. Malama Hindu ta mike da sauri tana cewa "Hajiya shigo ciki" Murmushi tayi cike da mamakin bata taba zuwa ba, Amman tamkar sun Santa har da cewa ta shiga cikin gidan? Bakinta dauke da sallama ta shiga parlorn malama Hindu ta amsa tana daga tsaye . "Ga wuri ki zauna, mu Kara gaisawa . Barka da yammaci? Iyalin kalau?" "Alhamdulillah." Ta amsa ta tana duba parlorn dan karami madedeci, Amman a killace ko'ina tsaf tsaf a gyare sai kamshin turaren wuta ne ke tashi... Lalle suna da tsafta . Ganin ba wani baki dake ciki ko masaaniyar zuwan ta balle tace shiryawa sukai . "Ma shaa Allah" malam Hindu ta fada... "Kinsan gidan Dr. Abubakhr dollars?" Malama Hindu ta girgiza kai da sauri tana mai him ta da kallon Karin bayani, "bansan shi ba gaskia" "Hakane kam ba lalle ki San shi ba. Dubada bangaren ku daban namu damu. To shi Dr. Abubakhr din miji na ne. Ni Kuma sunana hajiya qibdiyya. Kusan kullum ai Ina aiko a saya mun awara a wajen ki" "Allah sarki. Nagode Allah ya saka da alkhairi. Da ke mutanen da yawa bazan waye wanene ke zuwa ba" "Hakane kam..." Hajiya qibdiyya ta fada tana murmushi hadi da duban agogon da ke daure a wutsiyar hannun ta tace, "Yanzun ma shine mun fito tare da shi tun dazu yacemun layi yayi yawa Dakyar idan zaa samu.." Malama qibdiyyah ta kada Kai Kafin tace, "Eh wallahi.. masha Allah Nan da Nan da anyi take karewa. An goggode muku baki daya masu saya Allah ya saka muku da mafificin alkhairin sa. Aameen" "Aameen".. "Shysa na fito da Kai na .. naji zan iya samun awarar ko kuwa. Wallahi wannan ne shi ya saka " ta yi shiru bata karasa ba. Malama Hindu na nazarce da ita daman tun shigar ta gidan dazu a farko ta hango cikin da ke jikin ta. tayi murmushi tace,. "Allah ya raba lafiya hajiya. Ba matsala wallahi. Zaki ci anan ko a zuba Miki a pack ki tafi da ita?" "Aah mashaa Allah, Nagode kwarai. Gashi" ta Mika mata Yan dari biyar guda biyu. "Ta dubu biyu kenan? Har zaki cinye ta dubu biyu? "Karki damu. Zubamin a plate kawai na ci anan. Kamar guda takwas ta Isa" "To bari a kawo. Amman dan Allah ki rike kudin nan wallahi zan baki kyauta. Uwa uba Kuma kudin sunyi yawa " "Ahh yar uwa banason musu " "To shikenan nagode Allah ya saka da alkhairi Amin" Malama Hindu ta nufi wajen babbar food flask da suke saka awara ta dakko plate ta zuba awarar fal da kayan hadi da yaji aciki.. "Gashi ranki ya dade... Bari a kawo ruwa".. "Kakk takura kanku bari na ce driver din waje ya kawo" "Aa dan Allah . Ki bari nima na sami lada tukun" Hajiya qibdiyya tayi murmushi kawai hadi da kada Kai tace,.. "To shikenan tunda haka kikace. Nagode kwarai " Malama Hindu ta sake fita tana Kiran Nawraah. Nawraah dake zubawa wani coleslaw acikin kwanon abinci ta mike da sauri, "Naam ummy" "Ungo rike. Ki sayo lemo daya karami da ruwa babba shima daya. Kiyi sauri banda wasa akan hanyar" "Tohm ummy" ta fada da sauri harda hadawa da gudu. Malama qibdiyya ta koma wajen su Ashfeef dake tuyar auren Ashfeef ya hanata ta hanyar rcewa, "Ummy kin har bakuwa ita kadai fa. Ki koma zamu karasa Allah" "Hamma kaji abunda yace ko" Ashir yayi murmushi Yana sosa keyar sa yace, "Kije ummy ku cigaba da hirar ku aii sauran kasko daya daya mu karasa" "Tohm sannun ku da kokari. " "Yauwa ummy" Komawa parlorn tayi wajen hajiya qibdiyya. Hajiya qibdiyya dai sai zura lomar awara take. Tamkar zaa kwace mata saboda yadda ta gigice tana wani lumshe idanun Hajiya qibdiyya ta saci kallon malama Hindu. Jikinta a tsaftace ba akanta irin masu sayar da awara ba shadda suke tashi idan kaje kusa da su sai hamamin wari ne ke tashi. Amman malama Hindu daga ita har yaranta tsaf tsaf suke. Uwa uba ko'ina a killace musanman parlorn da take a zaune... Ga plate din da aka zuba mata shima tas a wanke yake...tana cikin ci sai ga nawrah ta dawo rike da lemo da ruwa a hannun ta,.. "Ummy gashi" "Yawwa an gayshe ki. Mikawa anty qibdiyya abincin" "Tohm ummy" Nawraah ta karasa wajen hajiya qibdiyya ta ajiye mata lemon da ruwa. Hajiya qibdiyya ta daga Kai da sauri ta kallo malama Hindu tace "Ruwa kawai fa nace. Don Allah a mayar da shi. Kinji?" "Ki dubi girman Allah ki amince kinji? Hindu ta fada mata. "Ai shikenan ... Bata ta shanye naga wata karama awajen. Dake bana shan Zaki yanzu sosai Ina kan dieting ne" "Allah ya bada sa'a. Shikenan, dauki kije ku shanye" Amnah ta durkusa har kasa ta karba da hannu biyu. Hajiya qibdiyya na kallon ta dakyau kwarai matuka ta birgeta. Yar karamar yarinyar da bata shekara biyar ba amman take ladabi haka! Lalle iyayen ta sun bata kyakkyawar tarbiyya, ta Kuma luraa dukan su yaran nada hankali da biyayya. Ta kasa hakura bayan ta dangwali yaji ta afa a baka tana taunawa tace, "Wannan ma yar kice ko?" "Eh...Amnah ce" "Mashaa Allah su nawa kenan kaman uku ko?" "A'ahh su hudu, Biyu mata, Biyu maza.... Akwai Ashir shine wancen nawaje me tuyar awarar .sai Ashfeef sai sai nawraah wadda ta kawo lemon nan da ruwa. Sai kuma autar mu Amnah..".. "Mashaa Allah Allah ya raya su ya musu albarka".. "Allahumma Aameen".. Ta matso da robar wankin ruwan da aka kawo gabanta ta wanke hannuwan ta.. "Nagode sosai.. Allah ya kara kasuwa mai albarka Amin" "Aameen" , "Bayan awara sai mai kike sayarwa?" "Awarar ce kawai ba wani abu" "Mashaa Allah... Idan ba takura ko zaki dan dinga zuwaa kina tayani wasu aiyukan na gidah ? Mai aiki na ce tatafi. Itace mewa yara girkin abunda suke so. " Malama Hindu tayi shiru Kafin ta daga Kai tace, '"To zanyi shawara da abbiey dinsu. Idan ya amince zaki gani." "Ga number wayata nan. Ki bani taki. Idan har kin amince zaki dinga zuwa to seki Kira a aiko driver ya dauke ki" "Tom shikenan babu damuwa. Nagode sosai hajiya Allah ya raba lafiya" "Ni ce da godiya sosai. Allah yabar zumunci Amin".. Har kofar gidah malama Hindu ta rakata tana mai kambama dattako irin nata. Wajen suyar ta je tuni har sun gama ma an saye tas bata ma kai daren ba ranar. Duk dadi ya mamaye su ganin yadda ake tururuwar zuwa sayen awarar tasu.. Nan ta sheda musu yadda sukayi da hajiya qibdiyya ta karkare musu da, "Idan abbiey dinku yazo zan sanar Masa duk hukuncin da ya yanke sai ayi amfani da shi. Ga katin data bani da number wayarta a baya. Ta saka tawa number a wayarta. " Duk sukai mata fatan alkhairi da kuma hukuncin da abbiey dinsu zai yanke... ___ *DR. ABUBAKHR DOLLARS DWELLING:HOME/RESIDENCE)* _INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_ _KU MARMATSO KUSA...🔊_ _ZAFAFA BIYAR 2024_ _ZAFAFA BIYAR!!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_ _YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_ _GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_ _________ _1_ *_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_ _2_ *_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_ _3_ *_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_ _4_ *_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ [2/21, 5:42 PM] Hafsaat🧕: _KKJ_ _12_ _✍️:MX_ _ADVERT👇👇_ _YERWA INCENSE AND MORE_ _(DUNIYAR KAYAYYAKIN KAMSHI MASU MATUKAR DADI DA KAMA JIKI, GIDAH, KAYA DA SAURAN SU)_ _INA MA'ABOTA TURARE? KADA KU MANTA SHI FA KAMSHI RAHAMA NE, KUMA TSAFTA CE_ _TSAFTA KUMA TANA CIKIN IMANI… TOH KU MAR-MATSO KUSA_ _MUN KUMA ZUWA DA HAJAR KAYAYYAKIN_ _*YERWA INCENSE AND MORE*_ _DOMIN SAMUN ZAFAFAN TURARUKAN WUTA NA GIDA, KAYA, JIKI, TSUGUNNO, GASHI... AKWAI KHUMRAHS MASU DADI YAN BORNU, CHADI, SUDAN DAMA SENEGAL, AKWAI OIL PERFUMES, DA TURARUWAN MOPPING DANA WANKA DANA WANKI DANA GADO DA KUJERU DA BANDAKI DA DRAWER DA MOTOCI.._ _AKWAI MAN GASHI NA FESAWA ME SA KAMSHI DANA KITSO. AKWAI KAYAYYAKIN KAMSHI DANA GYARAN JIKI SOSAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA. •_ _ADIRESHI: KANO.. AMMA SUNA TURA KAYAN SU KO'INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE..._ _INGANCI KYAU RAHUSA DA DADEWA A GIDAH DA KAMSHI SAI KAYAYYAKIN TURAREN YERWA INCENSE AND MORE_ _NAMBAR WAYAR SU: 08095215215, INSTAGRAM/THREADS/TWITTER:yerwaincense_and more_ _YOUR NUMBER ONE STOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS... THEY 'VE GOT YOU AND YOUR HOME COVERED_ :::::::::::: _ _NADUKA CRESCENT( APPLE ISLAND)_ (Dr. ABUBAKHR DOLLARS DWELLING/RESIDENCE) *Ahankali* cike da nutsuwa da kwarewa direban ke tuka babbar motar da hajiya qibdiyya ke ciki a baya mazaunin owners corner.... Kallo daya zaka yiwa motar kasan ba karamin kudi aka sa aka saye ta ba. Mota ce mai nishin kudi. Kyau da kuma tsananin kawatuwa.. Baka ce irin bakin nan mai sheqi a idanu.. babbar mota ce mai kama da land cruiser . Irin Saharan mota dinnan ce wadda ke tafiya ko acikin guguwa ne da tabo. Uwa uba kuma motar bullet proof ce. Ko harbi aka saki akan ta ko gilasan ta babu abunda motar zatayi. Unguwa ce data amsa sunanta ta manyan masu kudin birnin Naduka... Kaama daga masu rawani na sarauta, Manyan siyasa, Manyan yan boko , Ma'aikatan asibiti wato likitoci, Yan kasuwa da sauran masu farcinan susa.. Wani hadadden daular gidah tamkar a kasashen ketare. Nan direban ya nufa da hancin motar ta su. Hadadden gidah ne fari tas kalar sa. Yayinda gate din gidan jijjigagge shi kuma baki wuluk ne... Tafkeken gidah ne yayi wata unguwar a kauye. Kai ka rantse ba a Nigeria bane gidan. Ganin yadda tun awaje ba ma a shiga cikin gidan ba amman gidan ya hadu kwarai matuka .. Ga famfuna nan anyi su awaje. Talakawan Naduka zone sunzo sunata dibar ruwan a manyan bokitai da jarkuna.. Hajiya qibdiyya ta dube su ta window yadda suke jere a layi sunata dibar ruwan . Ta sauke ajiyar zuciya kawai cikin zuciyar ta tana mai nanata, "Allah ka horewa kowa...." Suna karasawa camerar dake jikin gate din tayi zooming tana scanning motar kafin daga bisani gate din ya bude da kansa. Direban ya shiga da motar ciki. Mashaa Allahu.... Mai karatu ai kawatuwar gidan ba daga waje yake ba kadai. Ashe akwai sauran kallo a gaba. Wato cikin farfajiyar gidan ma kadai wata daular duniyar ce. Habawa. Jamaa Allah yayi mana arziki mai amfani wato kudi suna inda suke .. Wajen motocin gidan ya nufa.. kowacce motar an tanadar mata wuri acikin wata katafariyar katuwar rumfar data hadu fiye da yadda kalmomi zasu bayyana... Manyan moticine a jere a Kuma fake. Wannan tana bani wuri. Kowacce mai tsananin tsada ce da Kuma kudi Mai yawa. Direban ya nufi kofa zai bude mata tayi saurin budewa ta futa tana mai daga masa hannu. Murmishi yayi kawai ya koma baya... Domin ko da yaushe idan sun fita hakan ce take faruwa ko da ya bude mata sai ta saka hannu ta rufe ta kara budewa da kanta. Ta kance masa ya kyaleta ta dinga budewa tana rufewa da kanta ai ba aiki bane. Sangartar Kuma sai tayi yawa. Har mamaki da daure Kai lamarin yake bashi musanman idan suna magana da yan uwansa direbobi dake aikin tuki awasu gidajen yadda matan gidan ke sarauta mai cike da izza. Shi kuwa ko sau daya sai dai bacin rana shima ba fada take yi ba. Amman tunda yake arayuwar sa bai taba ganin mai saukin kai da sanin yakamata ba irin hajiya qibdiyya. Sam batada wulakanci duk kuwa da tarin arzikin da take da shi. "Sannu hajiya akwai wani aiken ne?" Ta grigiza masa kai tana mai duba jakar hannun ta. Ta kirgo kudi ta dunkule ta mika masa yasa hannu biyu ya karba, "Na menene hajiya?" "Naka ne.,... Aciki na ci awarar dana shigaa kaga ban fito maka da ita ba ka nemi wata awani wajen idan ka gani ka saya hakki ne." Ya girgiza kai da sauri Yana mika mata kudin yace, "Hajiya wahalar ta Isa wallahi, bugu da Kari ma kuma wallahi a koshe nake nak. Kuma kudin da kika bani da safe ma ban Ida kashe su ba wallahi. " "Rike rabon ka ne. Nagode..." "Ni ne da godiya hajiya Allah ya saka Miki da mafificin alkhairin sa. Ya biya Miki bukatin ki na alkhairi duniya da lahira Amin" "Aamin... Jam'an..." Har tayi gaba zata shiga cikin gidan sai Kuma ta juya, "Malam Liti...." Da sauri ya amsa Yana takawa inda take, "Naam hajiya..." "Wannan matar me awara..." "Eh hajiya Ina sauraron ki" "Yan Ina ne su? Dama can tana awara bamu sani ba?" Malam Liti ya girgiza kai da sauri cike da girmamawa yace, "Gaskia ba Yan nan Naduka bane ance daga baya suka dawo. Amman basuda matsala yadda naji mutane na maganar. Kusan matar da mai gidan nata ma anfi yabon su kwarai matuka. Ance sudin mutanen arziki ne. Wani abun ne hajiya?" Tayi saurin girgzia Kai tana murmushi tace "A'ahh ba komai malam Liti. Tanada kirki ne sosai. Ga yaranta masu tarbiyya sosai wallahi.." "Mashaa Allahu.. haka akace kam" "Tohm dama. Kaga tafiyar Indo me aiki an dau lokaci. Yaran nan basa cin abincin malama Talatu. Basariya Kuma tayi kankanta. So na dai yi kuskuren harshe zance ko ko gandoki ne" "Idan na fahimta kina nufin me awarar ta dinga zuwa tana yiwa su junior abinci?" "Eh" "Kuma har kin gaya mata?" "Eh... Nayi sauri ko?" "Eh to Amman insha Allahu nasan babu matsala zata amince.." "Wallahi na yaba da hankalin ta ne. Ga shi tanada tsafta mashaa Allahu" "Allah yasa adace hajiya" "Aameen Yaa Rabbi. To sai gobe In shaa'Allahu " "To hajiya ahuta lafiya. Allah ya saka da alkhairi " "Aameen " ta amsa kasan makoshi . Ta shige cikin gidan ta cikin wata babbar kofa mai nauyi da ado ajikin ta. Harda madanni na kararrawa da yar camera dake haska fuskar wanda yazo. Bakinta dauke da sallama. Ta shiga ciki tana mai zare mayafin jikin ta, "Wash Allah na..." Ta furta ahankali tana dafe kugunta, "Sannu da zuwa Mami..." Cewar wata yarinyar daga gani maai aiki ce... Ta Sha uniform fari da dankwali baki. "Yauwa sannu basariya. Kina lafiya?" "Alhamdulillah Mami... A kawo ruwa?" "Eh maza kawo mun. Nagode" Yarinyar tatafi dasauri ta dakko ruwa da kofi akan tray ta ajiye agaban Mami. "Amatsa kafafun naki yanzu" "Yauwa yar kirki. Basariya tah. Allah ya miki albarka kinji" Basariya tayi murmushi cike da jin dadi ta kamo kafafun hajiya qibdiyya tana matsa mata kafafun da har sun dan kunbura ma saboda tsananin ciwo. ... "Su Hayfa sun dawo kuwa?" "A'ah ai da sauran lokaci." "Okay eh Allah ya dawo dasu lafiya" ta fada tana kallon agogon hannun ta. Ta tsiyayi ruwan a kofi tana sha.. Yayinda basariya ta cigaba da matsa mata kafafun ahankali tana mata sannu... *NADUKA ZONE* _INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_ _KU MARMATSO KUSA...🔊_ _ZAFAFA BIYAR 2024_ _ZAFAFA BIYAR!!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_ _YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_ _GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_ _________ _1_ *_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_ _2_ *_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_ _3_ *_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_ _4_ *_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ [2/21, 6:58 PM] Hafsaat🧕: _K'K'J_ _(M/W/S)_ _✍️:MX_ _13_ _ADVERT👇👇_ _YERWA INCENSE AND MORE_ _(DUNIYAR KAYAYYAKIN KAMSHI MASU MATUKAR DADI DA KAMA JIKI, GIDAH, KAYA DA SAURAN SU)_ _INA MA'ABOTA TURARE? KADA KU MANTA SHI FA KAMSHI RAHAMA NE, KUMA TSAFTA CE_ _TSAFTA KUMA TANA CIKIN IMANI… TOH KU MAR-MATSO KUSA_ _MUN KUMA ZUWA DA HAJAR KAYAYYAKIN_ _*YERWA INCENSE AND MORE*_ _DOMIN SAMUN ZAFAFAN TURARUKAN WUTA NA GIDA, KAYA, JIKI, TSUGUNNO, GASHI... AKWAI KHUMRAHS MASU DADI YAN BORNU, CHADI, SUDAN DAMA SENEGAL, AKWAI OIL PERFUMES, DA TURARUWAN MOPPING DANA WANKA DANA WANKI DANA GADO DA KUJERU DA BANDAKI DA DRAWER DA MOTOCI.._ _AKWAI MAN GASHI NA FESAWA ME SA KAMSHI DANA KITSO. AKWAI KAYAYYAKIN KAMSHI DANA GYARAN JIKI SOSAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA. •_ _ADIRESHI: KANO.. AMMA SUNA TURA KAYAN SU KO'INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE..._ _INGANCI KYAU RAHUSA DA DADEWA A GIDAH DA KAMSHI SAI KAYAYYAKIN TURAREN YERWA INCENSE AND MORE_ _NAMBAR WAYAR SU: 08095215215, INSTAGRAM/THREADS/TWITTER:yerwaincense_and more_ _YOUR NUMBER ONE STOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS... THEY 'VE GOT YOU AND YOUR HOME COVERED_ :::::: *NADUKA ZONE* **Malama Hindu ta haye sama don watsa ruwa, Ta sauya kaya zuwa doguwar riga marar nauyi... Sauka kasan tayi tana tafe da carbin ta a hannu tana ja.... Ba kowa a kasan sai Amnah da tayi bacci akan doguwar kujera an lullube ta da zanin gadon Ashir... Wajen ta futa. Tas tas ko'ina tamkar baa taba aikin wuta ba wajen. A gyare a kuma tsaftace tamkar ko da yaushe .. Ashfeef na wanke takalman ball dinsa, Yayin da Nawraah ke taje wa yartsanar Amnah gashi tana mata kalba yan kanana, "Sannun ku da aiki...." Malama Hindu tace dasu tana mai cigaba da kallon tsakar gidan. Ranta fes... "Ah ummy..." Ashfeef ya amsa ta yana duban ta. "Ummy nema na kike?" Cewar Nawraah ta mike tsaye. "Aa ba neman ki nake ba Nawraah.. Ina Hamman ku?" "Ya fita ba dadewa. " "Okay" Komawa tayi ciki ta gyarawa Amnah kwanciya ta zauna tana mai cigaba da jan carbin ta. Can ba dadewa Ashfeef ma ya shiga ciki bakinsa dauke da sallama malama Hindu ta amsa. Sai kuma Nawraah itama ta ajiye yartsanar Amnah a gefen Amnan. "Su maman baby anyi bacci." Nawrah ta fada tana dariya. Ta gyara zaman yartsanar Amnan. Ummy da ashfeef sukayi dariya. Can bayan mintoci Kuma sai ga dawowar Ashir rike da jakar abbiey dinsu na wajen aiki Ya shiga ciki bakinsa dauke da sallama. Abbiey din nasu na biye dashi a baya...shima yayi sallamar Duk suka hada baki wajen amsa musu. Amnah ta mike daga baccin da take tana mutstsika idanu Da gudu ta nufi wajen Hamma Ashir ta rungume shi. Ya dagata yana mata Wasa bayan ya ajjye jakar abbiey dinsu akan yar kantar da suke ajiye abubuwa. "Sannu da zuwa abbieyn su. Hamma ashe Kai ma baka nan na fito su Nawraah ke cewa ka futa ba dadewa." "Eh wajen aikin su abbiey naje muka taho tare" Malam junaid yayi murmushi Yana dafa kafadar Hamma Ashir yace "Aiki ya tayamu wallahi. Inata ya barshi ma baya gajiyawa a dole ya nace na hakura na bashi... Allah ya maka albarka. Allah ya muku albarka baki daya Amin" "Aameen suka hada baki wajen amsawa." "Abbiey akai ruwan wanka ko abincin zaka fara ci?" "A koshe nake yanzun dai kan saboda na sai fura na sha. Sai dai wankan" "To shikenan bari a Kai bandakin." Kitchen ta nufa ta janyo bokitin data tafasa ruwan zafi ta rufe ta haye dashi sama ta zuba a bokitin bandaki na wanka. Ta dauki soson sa da sabulu ta sanya masa su kusa da bokitin. Kana ta dakko tiraren ruwa ta dan yayyarfa a rariyar bandaki da lunguna. Ta janyo buta itama ta cikata ta taf da ruwa ta rufe.. Ta sauka kasan ta mayar da bokitin kitchen. "Abbiey an hada suna bandaki" Mikewa yayi Yana nannade hannun rigar sa yace, "Sannu da kokari Ummy .... Allah ya saka miki da alkhairi" "Aameen abbieyn su .. Allah ya saka mana baki daya. " "Aameen.." yaran suka amsa baki daya.. Bandakin ya haye sama ya shiga bakinsa dauke da addu'ar shiga bandaki. Ya shiga yin wanka yana mai sake baje kofofin hancin sa yana shakar ni'imantaccen kamshin tiraren toilet mist na kamfanin yerwa incense and more 08095215215... Sam ba karni ko bashi bashi da wasu bandakunan kanyi. Kamshi dadda'da ne kawai ke tashi tamkar ko da yaushe.. Murmushi ya saki tattausa, cikin zuciyar sa yace, "Hindu kenan.... Sarkin tsafta, Allah ya miki albarka... Aamin" Ya cigaba da yin wankan Yana jin sa cikin wata ni'ima. Domin yayi dacen matar kwarai da zuriah dayyiba. Ya dan jima a bandakin don bayan da yayi wanka sai da ya rage cikin sa sannan ya dauro alwala. Dakin su ya nufa ya sauya kayan zuwa aikin da wata jallabiya da yafendo ta kawo masa tsaraba alokacin dataje makka wata shekara.. Tsayawa yayi Yana duban kansa agaban mudubin... Ya saka hannu Yana shafa aikin jikin jallabiyar. Yafendon sa kawai yake tunowa alokacin data kawo masa jallabiyar ta bashi a boye tace gashinan tsarabar sace tasa ta daban kasancewar sa dan auta. Don duk girman sa. Da iyalin sa dake karkashin sa. Yafendo kallon dan karami take masa. Jika shi take tamkar yadda akewa yan kananan auta.. Samun gefen katifar yayi ya zauna. Ya daga kansa sama Yana Mai tare hawayen dake kokarin zuba daga idanun sa.. ya tuna ana'i jibi zata rasu ta kamo hannun sa lokacin ya shiga da asubah ya gayshe ta tace, "Allah yayi maka albarka junaidu. Allah ya raya maka zuri'ah junaidu. Allah ya bunkasa ahalin ku baki daya ya muku albarka... Junaidu baka taba mun lefi ba. Idan ma kayi akan sani ko rashin sa na yafe maka junaidu. Allah yayi maka albarka. Allah yayi maka albarka Allah yayi maka albarka. " Hankincinsa ya zaro ya goge dan hawayen daya fara diga. Cikin haka malama Hindu ta shiga dakin bakinta dauke da sallama bayan ta kwankwasa kofar, "Oh har ka fito abbieyn su?" Ta tambaye shi tana karasawa inda yake ta zauna... Ta janyo kafafun sa ahankali ta dora akan cinyar ta tana matsa masa har zuwa dunduniyar tasa. "Abbiey yanata hawaye .. meya faru?" Yayi azamar gogewa da sauri Yana girgiza kai yace, "Me kika gani! Hawaye Kuma? Abune ya fada idanu na shine na cire" ya fada Yana kakaro murmushi. Itama murmushin tayi masa kawai. Tabbas ta gani kuka yayi. Amman tasan daman ba zai Fadi kukan menene ba kasancewar inde abun damuwa ne wani lokacin ya kan dannewa baya fada mata... "Sannu da dawowa...." Ta fada tana murmushi, "Nagode Hindu na....." "Ya aikin to?" "Alhamdulillah komai kalau..." "Mashaa Allahu abbiey . Allah ya jara tsarewa ya kareku daga sharrin masu sharri. Allah yakara buda muku yasanya albarka a nema. Allah Kuma ya amince maka a duk kanin abubuwa daka saka a gaba" "Aameen Hindu.. tare da ke. Nagode sosai . To ya yau din? Fatan komai kalau ?" "Alhamdulillah fa. Ta bangaren awara ma an samu ciniki yadda ya kamata fiye da tunanina mashaa Allah." "Alhamdulillah haka ake so. To Allah yakara sanyawa nema albarka Amin" "Aameen... Sai kuma wata bakuwa da mukayi yau din... Duk da dai tache tana aiko direba ya saya ko da yaushe. Nache mata bazan san shi ba saboda mutanen na da yawa masu zuwa a abun hawa .." "Eh... Ina sauraron ki" "Ta sayi awara ta dubu biyu... Tace abata guda takwas kawai ta isheta nayi nayi ta bar kudin ma taki wallahi. Nasa Nawrah ta sayo mata lemo da ruwa. Ta sha ruwan lemon tace Amnah ta dauka suka raba da Nawraah.." "Ina jin ki..." "Yauwa da fari tacemun wai nasan wani dakta wanene?... Oh kaji sunan ya bace mun," "Wanene?" "Wani sananne ne a yankin su na masu kudin nan na tabbatar. Don tayi mamaki nagani danace bansan shi ba. Inaga sananne ne sosai" "Dan uwanta ne mutumin?" "Aa Mai gidan ta ne ... Tace dai an San gidan gaskia... Wani abu dollar daga karshe" "Ah ..gidan Dr. Abubakhr dollars???" Abbiey ya karasa fada cike da tsantsar mamaki daya gauraye ilahirin fuskar sa. Yana bun ummy da kallon Karin bayani don tabbatarwa... Malama Hindu itama cikin son sanin taya ya ya san shi ta kada kai da sauri tace......... _INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_ _KU MARMATSO KUSA...🔊_ _ZAFAFA BIYAR 2024_ _ZAFAFA BIYAR!!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_ _YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_ _GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_ _________ _1_ *_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_ _2_ *_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_ _3_ *_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_ _4_ *_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ [2/22, 2:04 PM] Hafsaat🧕: _K'K'J_ _(M/W/S)_ _✍️:MX_ _14_ _ADVERT👇👇_ _YERWA INCENSE AND MORE_ _(DUNIYAR KAYAYYAKIN KAMSHI MASU MATUKAR DADI DA KAMA JIKI, GIDAH, KAYA DA SAURAN SU)_ _INA MA'ABOTA TURARE? KADA KU MANTA SHI FA KAMSHI RAHAMA NE, KUMA TSAFTA CE_ _TSAFTA KUMA TANA CIKIN IMANI… TOH KU MAR-MATSO KUSA_ _MUN KUMA ZUWA DA HAJAR KAYAYYAKIN_ _*YERWA INCENSE AND MORE*_ _DOMIN SAMUN ZAFAFAN TURARUKAN WUTA NA GIDA, KAYA, JIKI, TSUGUNNO, GASHI... AKWAI KHUMRAHS MASU DADI YAN BORNU, CHADI, SUDAN DAMA SENEGAL, AKWAI OIL PERFUMES, DA TURARUWAN MOPPING DANA WANKA DANA WANKI DANA GADO DA KUJERU DA BANDAKI DA DRAWER DA MOTOCI.._ _AKWAI MAN GASHI NA FESAWA ME SA KAMSHI DANA KITSO. AKWAI KAYAYYAKIN KAMSHI DANA GYARAN JIKI SOSAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA. •_ _ADIRESHI: KANO.. AMMA SUNA TURA KAYAN SU KO'INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE..._ _INGANCI KYAU RAHUSA DA DADEWA A GIDAH DA KAMSHI SAI KAYAYYAKIN TURAREN YERWA INCENSE AND MORE_ _NAMBAR WAYAR SU: 08095215215, INSTAGRAM/THREADS/TWITTER:yerwaincense_and more_ _YOUR NUMBER ONE STOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS... THEY 'VE GOT YOU AND YOUR HOME COVERED_ :::::::;    "Ka san shi ne abbieyn su?" Ta tambaye shi, Fuskar ta dauke da son sanin karin bayani... Malam junaid ya kada mata kansa cikin tabbatarwa yace, "Na san shi..... Amman ba wai sanayya sosai ba. Aminin mai gidan mu ne nan inda muke aiki a maqera. Alhaji Sambaso. Abokai ne kwarai da gaske. Don wadanda suka dade suna aiki a wajen ma suka ce kullu yaumin tare suke. Daya yana wajen daya... Suka ce mutanen kwarai ne sosai. Kuma yanada kyauta ainun shi Dr. Abubakhr din domin nima kwanaki da na aiko Ashir da dubu biyu ya kawo miki wanda nace miki awajen aiki aka bamu kyauta ai shine wanda ya mana kyautar. Dubu biyar biyar... Ko da na tambayi abokanan aiki na awajen sukace mun sunan sa Dr. Abubakhr dollars... Aminin Alhaji Sambaso ne. Don da sukace daloli yake rabawa ma da su yake kyauta. Anan ya gado sunan nasa. Ana ce masa Alhajin dollar." Ya kai karashen zancen yana kada kansa cikin tabbatar da maganganun da yayi. "Mashaa'Allahu..... Lalle mutanen kwarai ne..." "Ba lefi kam... A dai yadda mutane suke fada. Kuma nima da zai babbamu kudin hannu biyu ya karbe ni har yake tambayar shi uban gidan namu yana ce masa ya sunana? Amma ni sabon dauka ne ko dan bai sanni ba. Alhaji Sambaso yace masa eh daga baya na dawo Naduka da iyalina..." "Mashaa Allahu, Allah sarki... To Allah yasaka musu da alkhairi duka damu baki daya" "Allahumma Aameen ... Ina sauraron ki. Meya faru?" "Yauwa to ashe mai dakin sa ce. Tace sunan ta hajiya qibdiyya kuma ita mata ce agare shi. Wai ko da direban yace mata akwai laayi ba lalli su samu ba shine ta kasa hakuri kasancewar batada lafiya tana Kuma son taci awarar sosai. Shine tashi go ciki kanta tsaye tana sallama baiwar Allah..." "Allah sarki. Allah ya bata lafiya yasa kaffarane" "Allah ya sauketa lafiya" "Aameen" "Don daman tana shigowa Ina duban yanayinta kasancewar saitin wajen Kwan lantarkin nan ta tsaya hasken ya haske ta nan na hango mashaa Allah. ..." "Allah sarki.... Ina sauraron ki sai meya faru?" Malama Hindu ta sauke numfashi tana murza yatsunta tace, "Catai idan ba damuwa dan Allah ta yaba da hankali na da tsafta ta idan zan iya girkawa yaranta abinci mai yi musu tatafi... Ta bani wani kati da number wayarta ta karbi tawa.." Bappah junaidu ya kada kansa kana ya numfasa ainun tukun yace, "Sai kika bata amsar me?" "Ina ni Ina yanke hukunci abbieyn su? Ai sai abunda kace. Kaga yaran nan suma haka suka fada sukace duk hukuncin da abbiey ya yanke Allah sa shine mafi alkhairi Amin" Bappah junaidu ya sake numfasawa ya daga kansa tamkar mai tunani sai Kuma ya sauke yace, "Wane irin aiki kenan?" "Abinci.... Na yaran ta, meyi musu tatafi ita kuma tayi nauyi" "Tohm banyi niyyar amincewa ba gaskia dubada ba sanin hallayar ta mukai ba sai dai dan kin ga wasu daga ciki datazo din .. Kuma mai gidan nata ma ance bashida matsala. Babban abunda yasa zan iya amincewa Kuma shine dalilin wannan nauyi da kikace tayi Allah ya sauketa lafiya Amin" "Aamin ..abbiey ka amince kenan?" Bappah junaidu ya kada Kai Kafin yace, "Eh to.... Bazan hanaki ba. Ban Kuma gama amincewa da barin ki kije ba saboda banyi magana da Hamma ba naji hukuncin dashi zai fi dacewa duk kuwa da nasan babu matsala ... Amman zan same shi yanzu inshaa Allah. Duk yadda muka tattauna muka yanke zan gaya miki.", "Toh shikenan abbieyn su. Allah ya zaba abunda yafi alkhairi a rayuwar mu gaba daya Amin" "Allahumma Aameen..." "Azubo abincin yanzu?" "Eh azuba.. Amman akai wajen su Bappahn su zanje muchi da shi daga nan sai mu tattauna abunda zamuyi idan na dawo zakiji komai" "Toh Allah yasa muji alkhairi Amin, bari a zuba." "Aameen... Allah ya miki albarka" "Aameen abbieyn su... Duk hukuncin daka yanke na aminta da shi wallahi. A har kullum amincewar ka nake so a dukkanin lamurana. Kasani har a raina ban yanke hukuncin komai ba sai wanda ka zabar mun. Hasalima bansa zanyin ba. Dubada aikin awara da mukeyi muma anan din." "Nasani Hindu.... Kada ki damu kinji? Mu Mika lamuran mu wajen Allah baki daya. Badan rayuwa ma data sauya mana ba Hindu ai munfu karfin duk aiyukan nan abaya... Sai dai ma mu mu kyautar ba dai abamu ba. To ruwa ne ya daki babban zakara. Allah yasamu dace" "Allahumma Aameen..." Kasan suma sauka a tare. Bappah junaidu ya fice zuwa gidan bappah Auwalu. Ya yinda malama Hindu ta nufi kitchen cikin babban tray ta jera komai na abincin dede cin su ta hada da plates biyu da cokula, "Ashfeef..." "Naam ummy" "Ungo bi abbieyn ku dashi ka Kai musu gidan bappan ku acan zasu ci" "Tohm" Ashfeef ya karbi tray din ya fita ya nufi gidan bappah Auwalu. A barandar kofar gidan ya hango su a zazzaune su biyun akan tabarma. Ya kai musu ya ajjye agaban su bayan yayi sallama ya gayshe da su. "Sannun ka Ashfeef . Allah yayi albarka" Cewar bappah Auwalu "Aameen Bappah..." "Tashi kaje ko? Magana zamuyi" "Tohm abbiey. Bappah a huta lafiya" Mikewa yayi har zai nufi hantar gidah yaci karo da Ahmad tsaransa wato yayan Layla. Abokin sa ne kuma dan uwan sa ne. Wata biyu ne a tsakanin su. Don haka suna aminta sosai. "Waje na kaje ne?" Ahmad ya tambaye shi Yana nuna kofar gidan su Ashfeef ya girgiza kai yana sosa kasan keyar sa yace, "Wajen su Bappah naje na kai abinci" "Okay... Ya za'ai ball fa da Argentina zo muje mu kalla. Ana haskawa a gidan kallon ball dinnan. " "Tohm bari na tambayi ummy tukun. " "Ga bappah nan ka tambaye shi mana" "Abinci zasuci Kuma magana zasuyi shi yasa. " "Okay muje ka tambaye ta" Suka mike suka tafi gidan su Ashfeef din suna tafe suna hira. Suka shiga cikin gidan bakin su dauke da sallama. Ahmad ya gayda su ummy ya zauna a bakin kujera. Ashfeef ya tambayi ummy tace, "Kuje amman karku dade ana tashi ku dawo gidah" "Inshaa Allah ummy" Ashir na zaune yana sauraron labarin da Amnah ke bashi na yara ya saka hannu a aljihun sa ya zaro nera hamsin ya mikawa Ahmad "Ungo ku sayi wani abun" "Mungode Hamma" "Godia muke Hamma" Suka fice sunata murna. ..ummy ta dubeshi tayi murmushi kawai... Kyawawan halayen Ashir sunada wuyar misaltuwa.... ____ Bappah junaidu da bappah Auwalu sun jima sosai suna tattauna sun Kuma yanke shawara maganar aikin ummy na gidan Dr. Abubakhr dollars.. Don haka Kai tsaye ya nufi gidah bayan sun gama maganar. Ya shigaa parlor bakinsa dauke da sallama ba kowa yaran duk sunyi bacci sai malama Hindu data saka radio a kunne tana sauraron wa'azin da akeyi... _INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_ _KU MARMATSO KUSA...🔊_ _ZAFAFA BIYAR 2024_ _ZAFAFA BIYAR!!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_ _YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_ _GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_ _________ _1_ *_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_ _2_ *_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_ _3_ *_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_ _4_ *_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ [2/22, 6:28 PM] Hafsaat🧕: _K'K'J_ _(M/W/S)_ _✍️:MX_ _15_ _ADVERT👇👇_ _YERWA INCENSE AND MORE_ _(DUNIYAR KAYAYYAKIN KAMSHI MASU MATUKAR DADI DA KAMA JIKI, GIDAH, KAYA DA SAURAN SU)_ _INA MA'ABOTA TURARE? KADA KU MANTA SHI FA KAMSHI RAHAMA NE, KUMA TSAFTA CE_ _TSAFTA KUMA TANA CIKIN IMANI… TOH KU MAR-MATSO KUSA_ _MUN KUMA ZUWA DA HAJAR KAYAYYAKIN_ _*YERWA INCENSE AND MORE*_ _DOMIN SAMUN ZAFAFAN TURARUKAN WUTA NA GIDA, KAYA, JIKI, TSUGUNNO, GASHI... AKWAI KHUMRAHS MASU DADI YAN BORNU, CHADI, SUDAN DAMA SENEGAL, AKWAI OIL PERFUMES, DA TURARUWAN MOPPING DANA WANKA DANA WANKI DANA GADO DA KUJERU DA BANDAKI DA DRAWER DA MOTOCI.._ _AKWAI MAN GASHI NA FESAWA ME SA KAMSHI DANA KITSO. AKWAI KAYAYYAKIN KAMSHI DANA GYARAN JIKI SOSAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA. •_ _ADIRESHI: KANO.. AMMA SUNA TURA KAYAN SU KO'INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE..._ _INGANCI KYAU RAHUSA DA DADEWA A GIDAH DA KAMSHI SAI KAYAYYAKIN TURAREN YERWA INCENSE AND MORE_ _NAMBAR WAYAR SU: 08095215215, INSTAGRAM/THREADS/TWITTER:yerwaincense_and more_ _YOUR NUMBER ONE STOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS... THEY 'VE GOT YOU AND YOUR HOME COVERED_ :::::::: Ya sake sakin sallama a karo na biyu yana Mai zare takalman dake kafafun sa... Sai a sannan ummy ta jiyo sautin sa. Ta zare rediyon daga kunnenta tana mikewa tsaye, "Sannu da zuwa abbieyn su" "Sannu kade... Yi hakuri na shagala munata hira ashe dare ya kule haka .. duk sunyi bacci ko?" "Wallahi kuwa... Kowa yayi bacci" "Ayyah... Yi hakuri na shiga hakkin ki. Wallahi sai da Nusaiba ta leko tana cewa ya shigar mata da tabarmar idan mun gama na duba agogo nace kai haka dare ya wuce bamu sani ba? Astagfirullah." Malama Hindu tayi murmushi tana jijjiga kai tace, "Kai Nusaiba.... Halinta sai ita" Bappah junaidu yayi murmushin shima yace, "Allah yasa mu dace" "Aameen..." "Muje ko?... Mayi maganar a sama" "Tohm abbiey." Ta rurrufe ko'ina sannan suka haye sama dakin su .. sai data fara lekawa dakin su Nawrah suna bacci sannan ta shige nasu dakin bakinta dauke da sallama... "Ko kana bukatar wani abun abbiey?" Bappah junaidu ya matsa kusa da ita ya kamo hannuwanta cikin nasa yana murzasu ahankali. Idanuwan sa cikin nata yace, "Bana bukatar komai Hindu.... Ke kadai kin ishe ni... Ke kadai nake bukatar kasancewar ki matata agare ni a Koda yaushe .. kin zarce matsayin duk wani abunda kike tunanin zai kere ki.... " Tayi murmushi kanta na mata girma ta dashare hakora sosai tace, "Godia nake abbieyn su..." "Ki fadi sunana mana daga ni sai ke ne fa... Junaidun naki Kuma?" Hindu ta sake sakin wani tattausan murmushin da ta saka bappah junaidu Kai hannunsa kan kumatun ta yace, "Kinji......?" Yaja ji..... Din sosai ta yadda Hindu sai data kasa danne yanayin daya sakata tace, "Junaid .... Junaidu.... Junaidu na..." Bappah junaidu dadi ua sake mamaye shi. Sunayen datake Kiran sa kenan lokacin suna saurayi da budurwa da aka saka ranar auren su kafin ayi auren idan yaje zance yana ce mata, "Hindu... Hindunah.... Hindatuna tawa ni kadai ..." Ya tuno bayan yana mai sake fada ahankali a kuma rarrabe Ta sake murmushi tana cusa fuskar ta a akan cinyar sa tace, "Kai abbieyn su har kasa na fara kunyar ka.." "Kunya....? Ni Kuma yau?" Ya tambaye ta yana daria sosai. Itama dariyar tayi ...ya saka hannuwan sa biyu ya dago fuskar ta. Ya tallabo fuskar sosai yana duban ta, Ya kai kansa saitin fuskar ta dab da dab suna shakar numfashin juna .. Ya samu kansa da Kai bakinsa kan saitin tsakiyar gashinta ya sakar mata sumba.. "Allahumma barik ....." "Wa iyyakum ...." "Hindu....." "Naam...." "Da farko Kafin na baki amsar hukuncin da muka yanke akan maganar aikin ki zuwa gidan Dr .... Inaso ki bani nutsuwar ki sosai .." "Ina sauraron ka Junaid... Allah yasa muji alkhairi" "Tohm aameen ya rabbi.... Alkhairi nema.. da farko dai kinga a kudaden da yafendo ta babbamu anyiyyi guzuri akazo Kuma kashin kudin nan garin ba irin na bunza bane.nan birni ne sosai kudin komai anan Naduka ya ninka na bunza sau uku... Ko ba haka bane?" "Haka ne abbieyn su.." "Dukkanin ku kunsani ke da Nusaiba da sauran matan su bappah sani. Kudin da yafendo ta bari don ayiwa yarannan kidimar karatu da Wanda zaa musu idan sun tashi aure sun Kare anyi haka?" "Hakane abbiyen su" "Tohm... A dawo kan namu kasafin kudin. Kinga anawa kudin da gado na da Wanda yafendo tabani ta karamun dasu nayi gidan nan na Kuma tattara nake harkar kasuwancin nan da su ciki sune dai na tsakura ba yawa na baki kike awarar nan. yaran nan maza Kuma suke fenti idan an samu dama. Ake biya musu kudin boko da arabi matan ma ake biya musu kudin islamiya ko?" "Wannan haka yake abbiyen su. Ai kowa ya sani Allah dai ya saka maka da alkhairi..." "Aameen dukkan mu .. To kinga a abunda ake samu kema da Wanda kika bayarwa da Wanda yaran nan musamam Ashir ke kawowa duka kokari muke a taru a rufawa juna asiri. Abunda ya rage mun na boye kawai wannan ajiyar ce... Zaki dakko mun ita da safe inshaa Allahu... " "Allah dai ya kara horewa Amin... Amma abbiyen su me zakayi da wannan ajiyar dakace ka tanade ta ne saboda nan gaba idan da rai idan auren Yara ya tashi..." Bappah Junaid ya sauke nannauyar ajiyar zuciya mai turiri ya sake kamo hannuwanta yace, "Babban uzuri neya taso... Kuma ba aro zan bada su ba kyauta zan bayar. Inshaa Allah Allah zai hore mana agaba... Kinji?" Taso tambayar sa menene sai Kuma ta danne kawai ta daga masa kai. Don tasan koma menene tsakanin sa neda dan uwan sa. Don haka batasan shiga lamuran yan uwantakar su inde ba ance mata gashi gashi ba... "Hindu ....." Ya sake kiran sunan ta.. "Naam.." "Tunanin me kike ne?" "Bakomai abbiey..." "Kinga ki kwantar da hankalin ki ba wani abu bane. Gidan bappah Auwalu ne yake yoyo sosai baki daya katangar sai an canza ta .. wasu kofofin suma sun lalace sai ya sauya. To kinsan Nusaiba ta saka shi agaba wallahi. Ransa ba dadi sai dana tilasta masa sannan yake fada. Yace na tayashi neman inda zai samu bashi. Kuma kinga Hindu hannun ka baya rubewa kace zaka yanke ka wullar ko? Dan uwana ne bazan iya zuwa wani wajen na aro masa kudi ba bayan ni inada shi ni ne zan share masa hawaye tunda ni ne dan uwansa dake kusa yanzu... Shi yasa nace zan duba Masa acikin mutane zuwa da safe.. Amman ni ba aro zan bashi ba kyauta zan bashi. Nasan Allah bazai hana mu ba nan gaba. Dama shi ya bamu... Ko kuwa?" "Hakane abbiey ka gama magana. Allah ubangiji ya saka maka da aalkhairi.. Allah yabar zumuncin ku. Ya biya maka dukkanin bukatin ka duniya da lahira. Allah Kuma ya kara arziki ya bude maka kofofin alkhairi Amin... Hakika Kai dan uwane na gari ne mai share hawayen nasa Yan uwan ko da kuwa shi nasa idanun rufe suke da damuwa. Allah ya iya maka abbiey. Amin" "Aamin Hindu ... Tare da ke .. Allah ya Miki albarka. Nayi dacen mata tagari a duk halin dana tsinci Kai na Hindu bazan taba mancewa da alkhairin ki gare ni ba... Allah ya saka Miki da gidan aljanna. " "Aameen abbiey..." "Sai maganar zuwa gidan Dr abubakhr dollars... Shin againiki ke akan kankin kanki babu takura kiyi aiki a karkashin wasu tunda ba taba yi kikai ba? Kada kiga ko sabuwar rayuwar da muka tsinci kanmu aciki a haka zamu dauwama kike tunanin kaskantar da kanki kiyi aikatau a biya ki.. don rufin asirin mu" "Ko kadan abbiyen su... Kuma kasan ni Ina son dukkanin abunda ya danganci fannin girki. Da ba girki bane bama bana tunanin zan karbi aikin gaskia" "Hakane.... Kuma mun yi magana da bappah Auwalu. Shima yace a nemi yarjewar ki tukun dukkanin yadda Kika yanke yayi. Idan kin amince zamuyi to muna murna idan bakyaso nanma muna murna da fatan alkhairi.. me kika zaba? Wanne hukuncin ne yayi miki".. Malama Hindu ta dan nisa can tache, "Na amince abbieyn su ....zanyi aikin" "Toh Allah yasa hakanne nafi alkhairi , Allah ya dafa Miki yasa ki fara a sa'a" "Allahumma Aameen abbiey" Haka sai adaren ranar suka kusa raya rabinsa da hira. Daga nan sukayi alwala sukayi sallar dare kana sukabi lafiyar katifa suka kwanta bacci ya dauke su... Sai da malama Hindu ta dauki kwanaki biyar tukun sannan ta kira hajiya qibdiyya tace mata ta amince. Hajiya qibdiyya tayi murna kwarai matuka tace mata zata aiko a dauketa da safe inshaa Allahu .. ai kuwa haka akayi da safe wata zungureriyar mota hadaddiya tazo ta dauki malama Hindu har kofar gidah zuwa gidan da zata fara aikin abinci na iyalan Dr. Abubakhr dollars..... _INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_ _KU MARMATSO KUSA...🔊_ _ZAFAFA BIYAR 2024_ _ZAFAFA BIYAR!!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_ _YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_ _GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_ _________ _1_ *_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_ _2_ *_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_ _3_ *_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_ _4_ *_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ [2/24, 12:58 AM] Hafsaat🧕: _K'K'J_ _(M/W/S)_ _✍️:MX_ _16_ ::::::::: Dr. ABUBAKHR DOLLARS DWELLING/RESIDENCE:   Malama Hindu na bayan mota, Ya yinda kanta ke kallon window na mota tana duban gidajen layin masu matukar kyawu Ma shaa' Allah .. Malam Liti ya karya kan mota ya shiga gidan, Yayin da malama Hindu taga gate din ya bude da kansa motar ta shiga ciki.... Kasa boye mamakinta tayi har sai da ta waiwaya ta bayan motar ta sake duban gate din ya koma ya rufe da kansa... Ta bude murfin motar ta futa bakinta dauke da addua... Sanye take cikin doguwar riga ta atamfa mai dogon hannu... Ta saka wadataccen hijabi kalar kayan na ta. Hannunta rike da yar karamar jakarta da wayarta me torchlight aciki sai charbi da take ja.. "Yauwa, Bismillah! ga kofar da zaki shiga nan..." malam Liti ya nuna mata kofar da zata shiga ciki "Tohm, Nagode." Ta dan kakkalo harabar gidan cikin ranta tana yaba kyawu da tsaruwar komai na wajen tun ma bata shiga cikin ba. Don a iya motar da aka zo daukar ta kadai tasan ba karamin gidah zata jebah.. "Mashaa Allah ..!" Ta fada ahankali alokacin da ta zare kafafunta daga cikin takalman data saka ta taka wani lallausan welcome carpet da kafafun ta suka lume ciki saboda tsananin laushin sa. Ta sadda kai kasa ta dubi dan karamun carpet din da ke shimfide a bakin kofa an rubuta masa welcome da manyan baki.. Sake doka wata sallamar tayi bayan wadda tayi ta karasa shiga ciki tana mai nanata wa a karo na uku . "Waalykm Salam" wata dattijuwar mata ta amsa mata daga wani daki data leko da fuskar ta. Malama Hindu ta kakaro murmushi tache, "Ina wuni?" "Lafiya kalau... Ina zuwa" Malama Hindu ta nemi jikin bango ta tsaya tana dan kallon cikin babban parlorn da mai karatu zai iya fasalta shi da aljannar duniya. Ya hadu karshen haduwa, Domin babu ce kawai babu a parlorn nan duk inda hadadden parlor ya Kai na manyan attajiran masu kudi parlorn nan ya kai. Don ko acikin manyan masu kudin ma ba kowanne bane zai yi dace da gidan sa ya samu kayan dake cikin parlorn . Wasu irin Royal chairs ne ainihin royal na sarauta. Kirar oman kalar golden da white. Ya yinda curtains din parlorn ma royal ne design din kujerun suma. Kai harta marikin labulayen da tv stand da dinning area da sets dinsa da ke gefe duk royal ne. Komai da komai na parlorn royal design ne. Lamarin sai dai ache tubarkallah kawai. Dattijuwar matar tafito daga cikin dakin da take tana gyara zaman dankwalin data daura akanta. "Baliwar hajiya ce ke" "Eh...Ina kwana ?" "Lafiya kalau Alhamdulillah. Bari a gaya mata" "Tohm shikenan" "Ki zauna ga waje nan bari na kirata" "Tohm godia nake" Malama Hindu ta nemi waje ra zauna a kasan carpet jikin wata kujera, ta hango dattijuwar ta nufi wajen wata waya dake manne a bango 'intercom' ta danna wasu number ta kira waya. "Assalamu alaikum... Eh tazo to shikenan" ta mayar da wayar ta shiga wata kofa dake kallon daya bangaren inda dinning area yake. Wanda zaka tabbatar kitchen ne Tray ta fito dashi ta ajiye agaban malama Hindu. Dauke tray din yake da lemo da ruwa da snacks da kofi na tangaran, "Bismillah tana zuwa" "Nagode... "Malama Hindu ta fada tana gyara zaman tray din Matar ta koma cikin kitchen ta rufo kofar. Malama Hindu na zaune shiru shiru sai dube dube take Cikin haka sai ga sakkowar hajiya qibdiyya daga bene sanye cikin doguwar riga bubu ta material marar nauyi ta daura dankwalin kayan a kanta. Ta dashare hakora a lokacin da suka hada idanu da malama Hindu "A kasa? SubhanAllah... Tashi tashi ki koma kan kujerar dan Allah" "Ah wallahi nanma ya Isa hajia. Ina kwana" "Dan Allah banason musu ki hau ki zauna please. Mama Talatu, mama Talatu" Malama hindu ta haye kan kujerar ta tsakure kanta a kasa. Dattijuwar ta fito daga kitchen da alama itace malama talatun. "Hajiya ga ni.." "Mena ce miki idan bakuwar nan tazo?" "Kikace nache kina zuwa. Na Kuma kawo mata ruwa da lemo da su cake." "Bance ki ce ta zauna ta jira ba" "Na gaya mata hajia" " A kasan carpet saboda Allah? me ze hana kice ta hau kujera haba mama Talatu" "Kiyi hakuri hajiya nayi kuskure" Malama Hindu da sam bata dauka abunda hajia qibdiyya zata ce bane da sauri ta g girgiza kanta tana daga hannu,don sam batason daga zuwanta sanadiyyar ta mutanen da suke zaune da ita su bata Kuma ace ta dalilin ta. Cike da sauri tace "Wallahi ta jatbte ni hannu biyu, Muka gaysa ta kawo mun su lemo. Allah ni ko tace na zauna akan kujerar ma bana zama hajiya. Nafi kaunar zaman kasan . Mama Talatu ba ruwanta wallahi" Mama Talatu kanta a kasa ta ce, "Ayi hakuri hajiya." "Je ki...." Cewar hajia qibdiyya. Jikin malama Hindu yayi sanyi. Gaskia sam batajin yadda hajia qibdiyya ta yiwa mama Talatu ba. Tamkar kuwa ta ga zuciyar ta. Tache da ita, "Karfa ki dauka Ina da faada .... Wannan dinma kamawa tayi. Kinsan lokacin abu ka gyara shi kawai ba daga baya idan bata nan ba nazo inayi da ita ban kyauta ba. Haka nake ni a duk sanda kowane yayi Abu alokacin zan wankeshi awuce wajen . So wallahi wannan abun ma ya wuce. Kakki damu ai muna tare. Mama Talatu yar uwa ce ta zarce yar tayin aiki ba ita kadai bama harda sauran maaikatan.. kinaji na?" "Ina sauran ki hajia" "Ita wanan da tabar nan sunanta Mama Talatu. Babbar Mai aiki ce dake abincin gidan gaba daya idan zaa ma Mai gidan ma ita ke tayani, yanada diabetes so ba komai yake ciki ba" "Allah sarki Allah yabashi lafiya Amin" "Aamin Yaa Rabbi... Ni sunan ki nema ke kwatanin wlh" "Sunana Hindu..." "Mashaa Allah.. sunana hajiya qibdiyya kamar yadda na gaya Miki a baya. Alhaji abubakhr dollars shine mijina, Kuma babban maikacin lafiya ne da kasa keji dashi baki daya. Don har number yabo ta duniya aka bashi watanni uku da suka wuce. Na zangon farko kan mukamin gwarzon dayafi kowane likitan iya tiyatar haihuwa ", "Mashaa Allahu hajiya. Allah yakara hazaka. " "Aamin... Ni yar kasuwa ce. Ina saye da sayarwa na manyan dilolii ke kaiwa manyan yan kasuwa Kaya suna Kuma zuwa su Sara awaje na cargo cargo. inaga foundation na tallafawa marayu da marasa karfi Mai taken, "MARIYATUL QIBDIYYA DOLLARS (Compassion care foundation) " "Mashaa Allah! Allah ya kara tsarewa ya buda Amin" "Aamin tare da ke. Yauwa sannan inada Yara uku, Wanda yaci sunan mahaifin su Dr. Muna kiraan sa da junior shine na fari, sai ta biyu Hayfa. Sai auta na na karshe.... ANEES ABUBAKHR DOLLARS......... _INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_ _KU MARMATSO KUSA...🔊_ _ZAFAFA BIYAR 2024_ _ZAFAFA BIYAR!!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_ _YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_ _GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_ _________ _1_ *_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_ _2_ *_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_ _3_ *_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_ _4_ *_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ [2/24, 1:29 AM] Hafsaat🧕: _K'K'J_ _(M/W/S)_ _✍️:MX_ _17_ _ADVERT👇👇_ _YERWA INCENSE AND MORE_ _(DUNIYAR KAYAYYAKIN KAMSHI MASU MATUKAR DADI DA KAMA JIKI, GIDAH, KAYA DA SAURAN SU)_ _INA MA'ABOTA TURARE? KADA KU MANTA SHI FA KAMSHI RAHAMA NE, KUMA TSAFTA CE_ _TSAFTA KUMA TANA CIKIN IMANI… TOH KU MAR-MATSO KUSA_ _MUN KUMA ZUWA DA HAJAR KAYAYYAKIN_ _*YERWA INCENSE AND MORE*_ _DOMIN SAMUN ZAFAFAN TURARUKAN WUTA NA GIDA, KAYA, JIKI, TSUGUNNO, GASHI... AKWAI KHUMRAHS MASU DADI YAN BORNU, CHADI, SUDAN DAMA SENEGAL, AKWAI OIL PERFUMES, DA TURARUWAN MOPPING DANA WANKA DANA WANKI DANA GADO DA KUJERU DA BANDAKI DA DRAWER DA MOTOCI.._ _AKWAI MAN GASHI NA FESAWA ME SA KAMSHI DANA KITSO. AKWAI KAYAYYAKIN KAMSHI DANA GYARAN JIKI SOSAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA. •_ _ADIRESHI: KANO.. AMMA SUNA TURA KAYAN SU KO'INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE..._ _INGANCI KYAU RAHUSA DA DADEWA A GIDAH DA KAMSHI SAI KAYAYYAKIN TURAREN YERWA INCENSE AND MORE_ _NAMBAR WAYAR SU: 08095215215, INSTAGRAM/THREADS/TWITTER:yerwaincense_and more_ _YOUR NUMBER ONE STOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS... THEY 'VE GOT YOU AND YOUR HOME COVERED_ :::: 17      Malama Hindu ta jinjina Kai tana sauraron hajia qibdiyya har ta karasa maganar da take yi. "Mashaa Allah. Allah ya raya su baki daya ya inganta su ya Kuma tsare musu kuruciyar su har girman Amin " "Aamin Aaameen godia nake .... Hindu, Allah Kuma ya saka da alkhairi da kika amince da rokon da nayi Miki...." "Bakomai hajiya. Ni ceda godiya" "Ni dai x.... Kinga me musu girkin tatafi kauye ne ganin gidah wai. To Kuma sai ta Kirani ma take cemun bazawarin da zai aure ta ya matsa yanaso ayi auren kawai. Nace mata babu komai wallahi ai auren shine gaba da komai. Allah yasa albarka. To yaran Kuma basa cin abincin da ake wa baban su Wanda mama Talatu keyi saboda akwai Abubuwa da yawa da baa saka masa a abinci kasancewar ciwon sukarin da yake da shi.... Wannan wadda tazo nan itace malama Talatu. Itace babbar mai aikin mu. Sai basariya tana Ina ne.? Basariya" hajiya qibdiyya ta kwadawa sunan basariya kiraa da karfi Basariya ta sakko daga sama da sauri, "Naam! Ga ni" "Zo.." Tazo har wajen su. Ta tsugunna ta dubi malama. hindu tace, "Ina kwana?" "Lafiya kalau basariya ." "Itace basariya... Je ki" "Mashaa Allah Allah ya rayata Amin" "Aamin Aameen " direban daya dakko ki sunan shi malam Liti. Direba na ne shi.. Sai emeka direben Alhaji ne. Ana Kiran sa da oga emaka..... Da Ribado direban Yara ne. Ya kai su makaranta da.sauran su. Sai su Mudi, Barau... Masu gadi ne. Sai Samuel gateman, wato security in charge of the inspection da sauran su.. sai Ghali da dahiru masu wanki da guga. Bilal Mai share share. Nuhu gardener ne. Sai latifa ita ba kwana take ba jeka ka dawo take. Tana zuwa ta share ko'ina na cikin gidan nan ta gyara ta wanke da dakuna da sauran su. " "Mashaa Allahu...Allah yakara arziki ya biya ku baki daya" "Allahumma Aameen.... Hindu .. dama already kin gaya mun yaran ki hudu ko da sunayen su" "Eh duk da dai ban buda sosai ba. Sunana Hindu. Mijina sunan sa junaidu. Mu mutanen yankin garin bunza ne zama ne ya dawo da mu Nan Naduka. " "Bunza dai ta gabas?" "Eh ita.." "Allah sarki. Nasan bunza farin Sani. Akwai matar kawu na yar garin ce muna kanana an Sha zuwa da mu sosai ita bafulatanar ce kinsan garin naku ya Tara yarika kala kala" "Allah sarki..eh haka nekam .donmu kan mu zuriyar tamu ta rabu gidah biyu" "Mashaa Allahu. Tabbas kala kala qabilu kam naga harda larabawa lokacin muna kanana" "Eh tsatson zuriyar mu ne. Larabawan. Kuma mun hada fullanci" "Kai mashaa Allahu. Ai ina ganin ki da yaran ki nace Kai tubarkallah mashaa Allahu. Tamkar larabawa ashe ashe akwai jinin su atare daku" Malama Hindu tayi murmushi. Hajia qibdiyya itama murmushin tayi tace, "Ku kadai ne anan garin kenan?" "Aa akwai yayan miji na da iyalin sa anan. Da duk ma anan din zamu zauna to Kuma sai kowanne aiki ya mayar shi wani wajen shi da iyalin sa. Allah vai amince ba sai mu biyu kawai. Mu da iyalan yayan baban yarana" "Mashaa Allahu... " "Tare muke da su... Gidan su na gaba da mu bamu da nisa sosai" "Allah sarki Allah yabar zumuncin ku, Hindu ... Me yaran ki ke Kiran ki saboda yaran nan din su dinga Kiran ki da haka?" "Ummy suke cemin" "Mashaa Allah .. tohm Ummy su Anees zasu dinga Kiran ki da shi inshaa Allahu. Sai wani hanzari ba gudu ba. Naga kina sana'a Kuma banason na tauye Miki Taki sanaar da kike... " "Babu komai hajiya duk ba zai gagara ba inshaa Allahu wannan ma ai sanaa ce" "Duk da haka Hindu... Karfe nawa kike farawa" "Da rana muke farawa. Wani lokacin yamma zuwa dare inshaa Allahu. " "Mashaa Allahu. Tohm dama abinci ne kawai Zaki dinga dafawa Yara. Indo itace meyj musu Kuma aure zatayi. Da niyyar ganin gidah taje Kuma manemin aurannata ya matsa kan lalle shidai ayi auren kawai ta kirani tana neman sharawa nace mata Indo kiyi auren ki kinji? Shi yafi komai." Malama Hindu ta Kada Kai tache, "Hakane kam Allah ya basu zaman lafiya amin. Ni Kuma Allah yasa na iya irin abincin da take yiwa yaran naki" "Weekends sai 12 suke breakfast so kaman 10 haka kinzo Kafin 12 kin gama musu, da rana snacks suke ci already munada frozen ones a freezer sai dare Kuma muna fita dinner da babansu muci abinci awaje." "Kenan idan na fahimce ki ranakun hutu na azabar da lahadi abincin safe kawai akeyi nazo karfe 10 na gama na ranar shikenan darana suna cin snacks da dare kuna ci awaje ko hajiya?" "Eh haka nake nufi Hindu... Sannan ranar litinin zuwa alhamis su zaki dinga zuwa karfe 12 na rana ki gama Kafin 2 haka zuwa uku shikenan. Da safe mostly toasted bread ko sandwich suke ci. Abincin da kika girka da rana Kuma shi zasuci inshaa Allah da daddare yawanci indomie suke dafawa da sausage da kansu." "Mashaa Allah Allah ya raya su ya tsare kuruciyar su har girman su Aamin." "Aameen Yaa Rabbi Hindu..Aameen" "Hajiya ranar jumuaah fa banji kin ambata ba?" "Duk ranar Fridays gidan mu nake zuwa acan muke wuni yawanci da yaran da su mama Talatu idan Kuma yaran sun tsaya lesson toh sai su samenu acan din dai. Ranar jumuaah duka Yan gidan mu muke hallara gidan mu duka acan ake cin abindi a sada zumunci" "Mashaa Allahu lalle kuna sudaa zumunci kam. Allah yabar zumuncin Amin" "Aameen Yaa Rabbi wataran zamuje dake ai inshaa Allahu kiga Gwaggon mu" "Mahaifiyar ki?" "Eh..." "Mashaa Allahu Allah yakara mata lafiya da Nisan kwana Amin" "Aaameen Yaa Hayyu ya qayyum nagode kwarai. Naku iyayen suna can bunza kenan ?" "Aa sai dai Yan uwa da abokan arziki na nesa. Domin duk ahalin duk sun rasu" "SubhanAllah Allah sarki Allah ya jikan su ya rahamshe su yabaku daya Amin" "Aameen Yaa rahbi. Dake gaskia zuriyar tamu ana samun rashe rashe duk dangin yawanci babu sun tafi." "Kowa tasa yake jira. Allah ya kyautata namu zuwan Hindu" "Aaameen hajiya..." "Sai maganar kudin...nawa kike ganin zai isheki?" "Hajia ki bada abunda Allah ya hore kawai" "Ki dai fada Hindu" "Bantaba aikatau ba hajia saboda bansan nawa ake biya ba wallahi " tafada tana lankwasa yatsun hannuwan ta. Hajiya qibdiyya tace, "Dubu hamsin ya miki?" "Hajiya yayi yawa ki rage" "Bai yi ba ai kinada iyali Hindu. Kuma zama dasu Hayfa sai hakuri musanman Anees..." "Dan auta?" "Eh fa kamar kin sani ... Amma ba wai karamin dan auta bane kamar Amnah dinki don ya kai dayan yaron ki dinnan" "Mashaa Allahu wanne daga cik? Babban Ashir ? Ko na biyun sa Ashfeef?" "Yauwa na biyun" "Ah mashaa Allahu kam. Toh Allah ya raya su duka Amin. Nagode hajia Allah ya saka Miki da mafificin alkhairin sa ya kara arziki Amin" "Aameen Yaa Rabbi muje nanuna Miki kitchen dinki?" "Toh hajia...." Hajia qibdiyya ta mike. Ya yinda malama Hindu tabi bayan ta.... _INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_ _KU MARMATSO KUSA...🔊_ _ZAFAFA BIYAR 2024_ _ZAFAFA BIYAR!!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_ _YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_ _GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_ _________ _1_ *_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_ _2_ *_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_ _3_ *_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_ _4_ *_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ [2/24, 1:48 AM] Hafsaat🧕: _K'K'J_ _(M/W/S)_ _✍️:MX_ ._ADVERT👇👇_ _YERWA INCENSE AND MORE_ _(DUNIYAR KAYAYYAKIN KAMSHI MASU MATUKAR DADI DA KAMA JIKI, GIDAH, KAYA DA SAURAN SU)_ _INA MA'ABOTA TURARE? KADA KU MANTA SHI FA KAMSHI RAHAMA NE, KUMA TSAFTA CE_ _TSAFTA KUMA TANA CIKIN IMANI… TOH KU MAR-MATSO KUSA_ _MUN KUMA ZUWA DA HAJAR KAYAYYAKIN_ _*YERWA INCENSE AND MORE*_ _DOMIN SAMUN ZAFAFAN TURARUKAN WUTA NA GIDA, KAYA, JIKI, TSUGUNNO, GASHI... AKWAI KHUMRAHS MASU DADI YAN BORNU, CHADI, SUDAN DAMA SENEGAL, AKWAI OIL PERFUMES, DA TURARUWAN MOPPING DANA WANKA DANA WANKI DANA GADO DA KUJERU DA BANDAKI DA DRAWER DA MOTOCI.._ _AKWAI MAN GASHI NA FESAWA ME SA KAMSHI DANA KITSO. AKWAI KAYAYYAKIN KAMSHI DANA GYARAN JIKI SOSAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA. •_ _ADIRESHI: KANO.. AMMA SUNA TURA KAYAN SU KO'INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE..._ _INGANCI KYAU RAHUSA DA DADEWA A GIDAH DA KAMSHI SAI KAYAYYAKIN TURAREN YERWA INCENSE AND MORE_ _NAMBAR WAYAR SU: 08095215215, INSTAGRAM/THREADS/TWITTER:yerwaincense_and more_ _YOUR NUMBER ONE STOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS... THEY 'VE GOT YOU AND YOUR HOME COVERED_ _18_ 18       *Wani* hadadden kitchen suka shiga... Kana shiga na'urar sanyin ac zata bugo sanyin ta jikin ka... Katoton kitchen ne wanda ke luntsume da hadaddun kitchen cabinets green and yellow... Dukkanin kitchen utensils din dakin girkin nan kalolin sa kenan guda biyu kore da yalo.... Ga wani dankareren fridge mai kofofi biyu da zaa iya bude su. Yayinda kasan sa kuma freezer ce sai water dispenser daga gefe.  Da wasu madannai ajikin sa da remote controller. malama Hindu ta dauki mintinan tana kallon fridge din. Azuciyar ta tana nanata mashaa Allah tubarkallah. Ga wani daki karami shi Kuma dankali da doya da albasa ce kawai acikin sa a zube gaba ki dayan dakin. Da manyan freezers tafka tafka guda uku ajere. Daya kayan Miya, daya snacks, daya kaji da nama fal. Sai wani baskets Mai hawa hawa da yawa cike da plantain da crates na kwai ajiye dasu tafarnuwa da su spices. Da manyan jars na daddawa, kuka, Yajin daddawa na tafarnuwa dana daddawa. Gishi, maggi da sauran su. Sai gallons na farin mai da manja da su olive oils da sauran su... Komai da komai daya danganci kayayyakin abinci na alfarma Kama daga basmati rice da shinkafar tuwo data dafawa, spaghetti, garin tuwo, indomie, noodles da sauran su buhu buhu cartons cartons gasinan jibge a store.. Harda su kayayyakin shayi suma gasinan a kwali da gwangwanaye manya manya nasu mayonnaise, cream salads, waken gwangwani da nasarar sa, su ruwan robar da lemuka birjik kai da sauran su dai komai dai akwai babu ce kawai babu... "Kinga komai na abincin ko Hindu?" "Nagani hajia mashaa Allahu" "Akwai abunda kike bukata da babu?" Malama Hindu tayi hanzarin jinjina kai da sauri tace, "A'ah fa hajia, ai babu abunda babu anan gashinan mashaa Allahu kamar shagon siyayya. Allah yakara arziki" "Aameen Hindu. Amman ba zaa rasa ba. " "Hakane kam. To gaskia dai a iya abunda na sani ko ince wadanda zan iya amfani dashi dai duk gasinan sai dai ko Nan gaba idan an tashi idan babu.. Don naga wasu daga cikin spices dinmu ma kuna da su. " Ta karasa tana nuna wasu spices na labarawa "Mashaa Allah kina amfani dasu? Oh haka fa ku da jinsin ku.. girki da su akwai dadi ga nara dandano mashaa Allah" "Sosai kam" "Tohm bari na barki kiyi musu Abu Mai saiki kawai. " "Su uku kikace ko hajia?" "Eh su uku ne... Ga tukwanen Nan ga oven ga grilling machine, ga gas cooker nan. Da sauran su dai duka" "Mashaa Allahu.... Sai dai wannan sai an koya mun amfani da su. " Ta fada tana nuni da wadanda vlbata gane ba Hajiya qibdiyya ta gyara tsayuwarta ta shiga nuna mata aikin kowanne da yanda aje kunne su da kashe shu. Zaai mana . "Ga waya anan intercom ce idan kina bukatar wani abun sai ki Kira ki danna wadannan madannan. Ga ruwa Nan da lemo ki dauka ki sha duk sanda kike so. Ga rigar girki Nan idan bakyaosn kayan ki suyi kamshin girki sai ki sauya. Ga Kuma daki Nan na hutawa wanna kofar da ke kallon ki idan kin fita akwai sallaya da carbi da hijab da toilet aciki .." "Mashaa Allah sannu da kokari hajiya. Allah yakara arziki" "Aameen Hindu. Allah ya jara mana baki daya " "Aameen Yaa Rabbi" "Toh bari naje na yo wanka Nima. Sai na sakko ko. Dukabunda kike bukata dai ko Karin bayani wannan number jikin takardar Dana baki uta Zaki Kira ta wannan wayar. Idan abunda Kuma ya kulle Miki Kai nema Zaki iya tambayar mama Talatu . Idan dakko Abu ne Kuma ki saka basariya. " "Tohm hajia sannu da kokari. Allah ya saka da alkhairi. Aamin Yaa Rabbi" "Aameen Yaa Rabbi. Allah yasa ki fara a sa'a" "Aameen" Ficewa yayi daga kitchen din. Ya yinda malama Hindu ta sauke katuwar bahaguwar zuciya tana karewa kitchen din kallo. Harda TV tanata yi ga kujerar zama har biyu. "Wannan ba zaka Kona girki ba kana kallo?" Ta tambayi kanta Ashe mama Talatu ta shigo ta jita. Tayi dariya tana dubanta tace "ba zaka Koma ba Hindu indai ka mayar da hankali. Koma kallon na debe kewa sai kiga duk daddawar da zakai a kitchen baka ganin dadewarr" "Mashaa Allahu .. Allah yakara arziki Amin" "Aameen Yaa Rabbi... Sunana na yanka Asma'u amma ana Kirana da Mama Talatu." "Mashaa Allahu sunana Hindu .kema anan garin kike?" "Aa a daga kauyen kusa da Nan din nazo dai. Amman ni anan nake a zaune aikin kwana nake. Na Dade anan gidan" "Mashaa Allahu. . Ni Kuma daga baya muka dawo Nan birnin Naduka. Da a bunza muke" "Mashaa Allah ai kuwa kinyi kama da Mutanen bunza mashaa Allah tubarkallah " Malama Hindu tayi murmushi... A nutse tace, "Nagode .. Allah yasa mu fuskanci juna. Dan Allah duk abunda zanyi ba dai dai ba ki gyara mun nagode" "Inshaa Allahu... Bakida damuwa. Matsalata daya dama reni abundna ke hadamu da indo kenan data tafi. Amman ke naga zubin kima na muminai ne don haka banjda matsala da ke inshaa Allahu." "Inshaa Allahu Zaki sameni me biyayya mama Talatu. Nagode kwarai" "Allah ya bamu sa'a." "Aameen Yaa Rabbi...Mama Talatu idan ba takura zan iya samun abincin da kowannen su yafu so?" "Wia ai tsurfar su Hayfa ce sai su wallahi. Kawai ki dafa abunda Zaki iya. Zasuci a hakan.  Wancen yace kayan fulawa wancen kayan ganye wancen Abu me yaji. Haka suke ki dafa duk abunda zai fi Miki guda daya zasu ci" "Allah sarki bayin Allah... Nagode sosai mama Talatu" "Ba damuwa... Nima bari natafi nawa kitchen din girkin gidah gaba daya na oga zan fara sai namu " "Okay ba anan kike ba akwai wani kitchen din!" "Eh akwai kitchen har uku ne ai. Nan abincin Yara ake ko Mai sauki da daddare haka. Wancen na barandar Kuma shine ake na gidah gaba daya da gayshe gayshe idan da yawa zaai. Sai abincin azumi Dana sallah Dana sadaka Kuma a kitchen din waje wajen gate anan akeyi" "Mashaa Allahu komai dai a tsare to Allah ya jara dafa musu Amin" "Aameen.." Mama Talatu ta nufi nata kitchen din donyin girkin bangarenta. Yayinda malama Hindu ta zare hijabibta ta zura rigar girki da aka bata. Ban da Nan ta shiga sarrafa girkunan da ta saka zatayi. 'Tayi Naan bread da chicken wings sauce, Sai spaghetti mai veggies, da sauce na Hanta sai ta hada fruit salad da madara ta saka flovor ya bada wani hadadden kamshi da gardi. Ta Kai musu kan dinning duka ta ajiye .. Nan da Nan ta gyara dukkanin abubuwa da ta bata. Ta shiga dakin da hajia qibdiyya ta nuna mata dazu. Tafkeken gado da setin sa da kayan sallaya da hijabi da Qur'an da Kuma bandaki aciki tsaftatattce. Watsa ruwa ta yi ta kodauro alwala Dan anata kiraye kirayen sallar azahar dama. Tayi sallah tana zaune akan sallaya hajia qibdiyya ta kwankwasa ta shiga dakin tana sallama. Malama Hindu ta amsa. Hajian ta zauna a bakin gado ,. "Har kin gama? Sannu da kokari" "Na kammala gidah ma zan tafi" "Ah ki tsaha kici abinci " " A mozge nake hajia" "Ai ko ba Zaki ci ba sai kin tafi dashi kwanon ma zan saka maki kullum sau kin tafi abinci Allah. Dama na gayawa mama Talatu ta zuba Miki." "Nagode Allah saka da alkhairi" "Aameen." Har bakin kofa ta rakata ta shiga mota direban ya mayar da ita har gidah tanata yaba karamci da dattako irin na hajia qibdiyya.... Hajiya qibdiyya na shirin komawa sama ta jiyo karar horn din ribadu driver yadakko su hayfa daga school sun dawo. Ta kallii agogo lallek lokaci i har yayi. Komawa tayi kasan ta fasa hawa. Kamshin dake tasowa yasa tayi wajen wajen dinning ta fara bude warmers din... Sukayi knocking ta saka basariya ta bude musu kofar. Hayfa ce ta fara shiga ciki ranta a matukar bace....... [2/25, 2:56 PM] Hafsaat🧕: _K'K'J_ _(M/W/S)_ _✍️:MX_ _19_ _ADVERT👇👇_ _YERWA INCENSE AND MORE_ _(DUNIYAR KAYAYYAKIN KAMSHI MASU MATUKAR DADI DA KAMA JIKI, GIDAH, KAYA DA SAURAN SU)_ _INA MA'ABOTA TURARE? KADA KU MANTA SHI FA KAMSHI RAHAMA NE, KUMA TSAFTA CE_ _TSAFTA KUMA TANA CIKIN IMANI… TOH KU MAR-MATSO KUSA_ _MUN KUMA ZUWA DA HAJAR KAYAYYAKIN_ _*YERWA INCENSE AND MORE*_ _DOMIN SAMUN ZAFAFAN TURARUKAN WUTA NA GIDA, KAYA, JIKI, TSUGUNNO, GASHI... AKWAI KHUMRAHS MASU DADI YAN BORNU, CHADI, SUDAN DAMA SENEGAL, AKWAI OIL PERFUMES, DA TURARUWAN MOPPING DANA WANKA DANA WANKI DANA GADO DA KUJERU DA BANDAKI DA DRAWER DA MOTOCI.._ _AKWAI MAN GASHI NA FESAWA ME SA KAMSHI DANA KITSO. AKWAI KAYAYYAKIN KAMSHI DANA GYARAN JIKI SOSAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA. •_ _ADIRESHI: KANO.. AMMA SUNA TURA KAYAN SU KO'INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE..._ _INGANCI KYAU RAHUSA DA DADEWA A GIDAH DA KAMSHI SAI KAYAYYAKIN TURAREN YERWA INCENSE AND MORE_ _NAMBAR WAYAR SU: 08095215215, INSTAGRAM/THREADS/TWITTER:yerwaincense_and more_ _YOUR NUMBER ONE STOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS... THEY 'VE GOT YOU AND YOUR HOME COVERED_ ::::: 19 *Hajiya Qibdiyya* ta juya tana duban kofar. Ganin yanayin Hayfa yasa ta kira sunanta, "Meye haka kika shigo kina zunburo baki gaba, ba sallama?. koma ki sallama" Komawa tayi baya ta shigo tana sallamar ta zube akan kujera tana mayar da numfarfashi. Junior ma ya shiga bakin sa dauke da sallama ya saqala earpiece a kunnen sa. "Waalykm Salam.... " Hajia qibdiyya ta amsa sallamar ta su tana duban su tache, "Ina Anees?" "Yana baya Mami.... Woahh kamshin meye haka?" "Oh abincin ku ne da aka dafa." "Ai kam nima naji kamshin mai dadi" "Meye kika dawo da fari fuskar ki akumbure ke kuma" "Ko ba Yaya junior bane Mami. Ya kwace lipgloss dina a school na Kylie dinnan" "Ke meye na zuwa da lipgloss school saboda Allah Hayfa?" "Tohm Mami ba ita kadai aka karbewa ba classes da yawa duk an kwace ai ba zanyi favoring nata ita daya ba ko?" Cewar junior. "Eh hakane... Kuje ku zuba abincin. Anees!!" Ta wuce ta nufi wajen tana kiran sunan sa. "Naam Mami...." Ya amsa ta ahankali yana shafa magen sa dake zagaye shi tana kuka. Hajia qibdiyya tayi murmushi. Ashe dashi da magen sa ne. "An bawa Vanessa abinci kuwa?" Ya fada kansa akan magen tasa dake ta zagaye shi tana' meow meow' "An bata dazu basariya ma na saka ta zuba mata an bata ruwa na. Madarar ta kuwa sai zubarwa akai aka wanke kwanon nata." "Okay" ya amsa mahaifiyar ta su yana mai mikewa tsaye daga tsugunnawar dayayi. A tare suka shiga parlorn shi da ita bakin su dauke da sallama.. Hayfa ta zuba nyaan bread da miya. Junior ya debi spaghetti. "Kamshin meye haka?" "Abincin new cook dinmu ne. Mami macace ko namiji?" "Macece sunanta Ummy ...haka zaku dinga kiranta kuma bata dade da tafiya ba." "Mashaa Allah gaskia she's a great cook. " "Wallahi kam dan words aren't enough to express how delicious abincin nan yayi Mami. Kai gaskia she's talented. Duk alokaci daya tayi kaman tasan kowa da abun da yake so?" Cewar Hayfa. "Wallahi kam . Don ni banma gaya mata abubuwan da kuke so ba. Amma bari na tambayi mama Talatu. Mama Talatu! Mama Talatu" Mama Talatu tafito daga daki da sauri tache "Naam hajia " "Ni ke kika gayawa Hindu abincin da zata dafawa yaran nanne ?" "Aa wallahi. Nasan dai ta tambaye ni me yaran ke so? Nace kawai ta dafa abunda zata iya. Don kusan kowannen su da abunda yake so. Ban kuma lissafa mata nace wancen da wane abu kaza suke so ba. Nasan dai nace mata akwai me son taliyah da kayan fulawa da kuma abinci marar nauyi ma akwai me so acikin su. Wani abun ne ya faru?" "Kai amma gaskia an gayshe da Hindu. Wannan kokari haka? Kinga tayi Naan bread da sos din chicken wings tayi spaghetti da veggies shima da sos na hanta ga fruit salad da madara shima bakiji yadda ko'ina ya gauraye da kamshi ba wallahi" "Ga kamshin nan kan da an shigo. Gaskia tayi kokari abubuwa da yawa haka cikin kankanin lokaci. " "Mashaa Allah kam. Kin zubawa su basariya da kowa a kwanon sa?" "Eh na zuzzuba musu na Alhaji ma na kai masa bangaren sa. " "Yauwa sannu da kokari" "Yauwa hajia bari na je idan shikenan" "Eh shikenan mama Talatu." Anees ya ebo fruit salad sosai ya koma gefe yana sha. Sai lumshe idanu yake, "Da dadi shima?" Hajia qibdiyya ta tambaye shi "Beyond words" "Mashaa Allah... Bari dai na zuba naci nima" ta fada tana mikewa tsaye "Mami kar ki cinye mana please" "Da yawa ai tayi gashinan. Ai daga yanzu har ni zata ringa dafawa zan yiwa girkin mama Talatu bankwana" Suka kyalkyale da dariya baki daya banda anees da ya mayar da kansa kan TV dake nuna shirin labarai a tashar larabawa ta aljazeera.... "Auta ya school?" "Alhamdulillah Mami ..." "Mashaa Allah..Allah ya temaka kaji.? Akwai abunda kake so yanzu?" "Banason komai Mami. Thanks a lot" "Allah ya maka albarka" "Aameen Mami... Wa iyyakum" "Mami school Alhamdulillah mu da baki tambaye mu ba" Cewar Hayfa Junior yayi dariya yana girgiza kai kawai. Hajia qibdiyya itama murmushi tayi tace, "Toh Hayfa ya school? Junior ya school?" "Alhamdulillah Mami Amma Ina bukatar abubuwa gaskia" "Kai Hayfa..." Cewar junior "Yaya ai gaskia ne" Mami dai bata ce ya school din ba sai ma dariya da tayi kawai tace, "Idan Baban ku ya dawo ki same shi ki gaya masa.. Allah ya muku albarka Amin" "Aamin Mami" "Aameen duk da dai kinfi kaunar autan ki .." Mami tayi murmushi tana mikewa tsaye ta Isa wajen wanke hannu dake gaban dinning din ta tatsi hand washing mist ta wanke hannun nata. Daya bayan daya kowanne ya tashi. Hayfa dakinta a sama yake . Yayinda dakin anees, daban dakin junior ma daban kowanne da parlorn sa da kayan kallo da saitin kujeru hakama dakunan su da kayan kallo .. ::::::::: :::::::::: Sai da akayi sallar isha'i zungureriyar motar Dr. Abubakhr dollars ta kunno da kan hancin ta mai nishi gate din gidan .. Oga emeka driver dinsa ne ke tuka babbar motar da alkalami yayi kadan wajen bayyana maku adadin kyawun ta da tsadar ta. Ta matukar haduwa fiye da yadda kalamai zasu bayyana muku ita. Kalar ruwan bula ce mai turuwa amma turuwar sheki take bayarwa. Masu gadi da security suka taso kan motar duka suna yi masa sannu da zuwa. Da sauri suka bude masa gidan gaba inda yake zaune ba abaya ba kamar yadda da yawan masu kudi kan zauna a owners corner. Shi din agaba yake zaune tare da direban sa dake tuqawa . "Sannu da dawowa yallabai.... " Cewar Mudi ya karbi brief case din hannun Dr. Yayinda sauran ma suka shiga doka masa sannu da zuwa. "Sannun ku dai.... Nagode kwarai. Ga wannan aje wajen nai tsiren can aci." Ya mika musu kudi a dunkule yace su raba ya shiga ciki bayan ya karbi brief case dinsa Sukayi ta doka masa addua suna masu shi masa albarka. Sashen sa ya wuce... Wanda zaa iya shiga ta bangaren hajia qibdiyya ma. Babban parlor ne mai matukar girma da dinning area. Sai dakuna manya guda biyu. Komai da komai na rayuwar masu kudi an tana deshi abangaren sa kai harda abubuwa da yawa ma da wasu masu kudin basu samu iko ba.. Bandaki ya shige yayi wanka. Ya sauya kayan sa zuwa jallabiya. Yana fitowa ya iske matar sa hajia qibdiyya. Itama taci ado cikin wata atamfa riga doguwa samfurin a shape. Cikinta ya dan tillo kadan ya kara mata kyau sosai. Tayi daurin ture kaga tsiya. Wadataccen gashin kanta yazubo har kafadar ta. Sai kamshin turaren kaya na kamfanin yerwa incense and more ne ke tashi a jikin ta. Ga na gidah data kunna a burner shi ma na kamfanin tiraren yerwa incense and more ko'ina sai tashin kamshi yake uwa uba ga na'urar ac dake sanyaya wajen . Ya sauke idanun sa akanta...suka sakar wa juna wanj tsadaddan murmushi .. ba kadan ba tayi masa kyau kamar ko da yaushe cikin cin kwalliya take. Da yawa wasu matan idan suna da ciki zaka gansu da daurin zani kansu a taje ba kitso da leda ko gwangwani suna zubar da yawu aciki .. Ita kuwa ko da yaushe tana kokarin zama tsaf tsaf cikin cin uban su ado juma. Duk kuwa da rabin zaman mai gidan nata a asibuti yake yi, Amma hakan be hanata gyara kanta ba "Tsarki ya tabbatata ga Allah madaukakin kowa da komai .... An gayshe ki kujerar tsakar gidah uwargidah sarautar mata.....Kinfi kyawu kyau... Yake mabudin zuciyata.... MARIYATUL QIBDIYYA!!!... _INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_ _KU MARMATSO KUSA...🔊_ _ZAFAFA BIYAR 2024_ _ZAFAFA BIYAR!!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_ _YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_ _GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_ _________ _1_ *_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_ _2_ *_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_ _3_ *_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_ _4_ *_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ [2/25, 3:10 PM] Hafsaat🧕: _K'K'J_ _(M/W/S)_ _✍️:MX_ _20_ _ADVERT👇👇_ _YERWA INCENSE AND MORE_ _(DUNIYAR KAYAYYAKIN KAMSHI MASU MATUKAR DADI DA KAMA JIKI, GIDAH, KAYA DA SAURAN SU)_ _INA MA'ABOTA TURARE? KADA KU MANTA SHI FA KAMSHI RAHAMA NE, KUMA TSAFTA CE_ _TSAFTA KUMA TANA CIKIN IMANI… TOH KU MAR-MATSO KUSA_ _MUN KUMA ZUWA DA HAJAR KAYAYYAKIN_ _*YERWA INCENSE AND MORE*_ _DOMIN SAMUN ZAFAFAN TURARUKAN WUTA NA GIDA, KAYA, JIKI, TSUGUNNO, GASHI... AKWAI KHUMRAHS MASU DADI YAN BORNU, CHADI, SUDAN DAMA SENEGAL, AKWAI OIL PERFUMES, DA TURARUWAN MOPPING DANA WANKA DANA WANKI DANA GADO DA KUJERU DA BANDAKI DA DRAWER DA MOTOCI.._ _AKWAI MAN GASHI NA FESAWA ME SA KAMSHI DANA KITSO. AKWAI KAYAYYAKIN KAMSHI DANA GYARAN JIKI SOSAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA. •_ _ADIRESHI: KANO.. AMMA SUNA TURA KAYAN SU KO'INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE..._ _INGANCI KYAU RAHUSA DA DADEWA A GIDAH DA KAMSHI SAI KAYAYYAKIN TURAREN YERWA INCENSE AND MORE_ _NAMBAR WAYAR SU: 08095215215, INSTAGRAM/THREADS/TWITTER:yerwaincense_and more_ _YOUR NUMBER ONE STOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS... THEY 'VE GOT YOU AND YOUR HOME COVERED_ :::::: *Ya* karasa kusa da ita yana mai riko hannuwan ta cikin nasa, Yayinda kofofin hancin sa ke shakar ni'imantaccen khumrar kamfanin yerwa incense and more da ke tashi daga jikin ta... Har ta kai sai da ya kai hancin sa gefen wuyan ta ya sinsina... Cikin kunnenta ya saka bakin sa ya shiga mata magana tamkar mai yi mata rad'a yace, "Kinji kamshin da ke tashi daga jikin ki? Kayan ki? Kai dama baki dayan parlorn... Mariya tahhh kullum kuma da kalar kamshin da kike bayarwa .. wannan kamshin da me da me ye ne? Uhm?" Ya karasa fada yana sunbatar gefen kumatun ta... "Sannun ka da dawowa mijina mai tarin albarka... Kuma dan aljanna inshaa allahu... hakika nasamu babban rabo a wannan rayuwar kasan meyasa?" Dr. Abubakhr dollars ya girgiza mata kansa tamkar karamun yaro yana sake langaba kansa akan kafadarta... "Saboda nasami miji tamkar amini, mai kula dani, mai sani farin ciki, yana kaudar mun da bakin ciki. Hakimin dake tare da ni yafi mun komai a wannan duniyar.... Ina kaunar ka doctor na.. Allah yabar mun kai" "Hakika nayi dacen mata ta gari matar kwarai, Tamkar aminiya,Mai kula da ni, Mai yaye mun bakin ciki, tana sanyani cikin annushuwa, hakimar dake tare da ni tafi mun komai a wannan duniyar. Ina kaunar ki Mariyatah. Allah yabar mun ke.." "Aameen Nawan... Har abada" Ta matse shi sosai a jikinta. Yayinda shima ya riketa gam yana cigaba dashakar niimattacrn kamshin da ke futa daga jelar gashin ta... "Kai Mariyatah sarkin tsafta sarkin ado, Kuma sarkin kamshi. Har gashin ki na kamshi yake kullum kuma kamshin ko'ina na jikin ki ya banbanta da na baya da kike sawa different scents" "Zinare na kenan.... Kawai hadaddun hadin kayan turaren kanfamin yerwa incense and more ne... Kaga na turara jiki na, na saka khumrah na shafa mukammaria na shafa perfume oils dinta again na kuma turara kayan jikina sannan na fesa kabbasine spray na fesawa a kayan kafin a turara su, sannan kuma na fesa man gashin ta na fesawa mai kamshi na gashi dana shafawar sa., and na shafa kulaccam dinta ta oudi " "Kai tubarkallah... Allah ya saka mata da alkhairi da take baki wannan dadadan kayan kamshi haka. Kinsan kullum naje asibuti harda patients na tambayana kamshi da nake? Saboda wannan turaren gadon da kike fesa mana a zanin gado dana labule dana mota dinnan dana drawer da kike sakawa . Wallahi kamshin ya zauna ajiki na. " "Mashaa Allahu.. ai turaren su bana banza wallahi. Ga rike waje".. "Gaskia.. cuz wannan da kika saka kiga sai yi yake yana futar da kamshin har yanzu" ya karasa fada yana nuni da burner ... "Haka kayanta suke .. worth buying wallahi. " "Mashaa Allahu.. she's blessed" "Sosai ma....ga abincin ka a dinning muje kaci" "Tam" Mikewa tayi ta riko hannun sa ya bii bayanta tamkar rakumi da akala. Taja masa kujera ya zauna ta dauki plates tayi serving dinsa komai.. "Bismillah" "Godia nake Mariyatah....", "Haa bude bakin" Murmushi yayi ya bude bakin nasa ta debi abincin ta zura masa a baki ya karba yana taunawa, "Nagode sosai" "Anytime..." Haka ta cigaba da feeding dinsa har ya koshi. Ta kira mana Talatu a intercom da basariya suka kwashe kwanukan bayan sun debi gaisuwa awajen Dr. Abubakhr dollars. "Uhm ni na manta ma ban gaya maka ba. " Ta fada tana janyo tray din data rage Naan bread din dazu tana ci da miyar "Meya faru?" Ya tambaye ta cike da kulawa.. "Matar nan fa tazo ta fara aikin ta. Kaga sauri kuwa? Tayi Naan bread da sauce, spaghetti da veggies da creamy milky fruits salad. Mashaa Allah komai superb" "Mashaa Allah haka akeso... " "Wallahi bakaga ba yara nata santi fa. Kuma ba wanda ya gaya mata ga yadda zatayi. Ita tayi komai da kanta. And it turns out perfect " "Gashi nan kam sai kamshin abincin ne ke tashi. " "Sosai .... So ya aikin asibutin ya patients din naka da komai?" "Alhamdulillah... Komai kalau fa. Sai ma wani abu mara dadi daya taso" "SubhanAllah... Meya faru Kuma?" Ta tambaye shi a gigice "Calm down ba wani abu bane thou. Amma dai ni ne ban aminta da shi ba" "Ka lullube ni a cikin duhu .... Meya faru?" Ta sake tambaya da cike da kulawa. Dai dai lokacin da yaran na su sukayi sallama suka shiga su biyu... Hayfa da junior... Suka amsa musu sallamar. Hajia qibdiyya kanta na kan Dr abubakhr tana son jin menene matsalar, "Kai ku koma magana muke" "No su zauna ai ba wani abu bane ya kamata su sani....Ina Anees?" Hayfa ta juya baya tana duban junior "Dama bai taho ba?" Junior ya girgiza kansa, Yana daga kafadar sa. Wayar sa Dr abubakhr ya janyo ya Kira number Anees bugu uku ya dauka yace yazo bangaren sa yanzu yanzu Ba jimawa kuwa sai gashi ya yi sallama ya shiga sanye cikin riga da wando na bacci ya sakala airpod a kunnen sa . "Babaa barka da dare, Mami barka da dare" "Barka kadai" "Barkan mu.... Wato da ban Kira ka a waya ba anees ba zaka zo ba kenan? " Anees ya saka hannun sa ya sosa keyar sa kansa a kasa yace, "Ina assignment ne. Tuba nake" "Well ya wuce... ALLAH yasa mu dace. Abunda Zan fada ba wani abun tashin hankalin bane awajen ku so Mariyatah please clam down. Ki duba condition dinki baa san damuwa please. Ba wani abu bane masarauta ce take ta bibiyata tun watanni biyu da suka wuce" "SubhanAllah wane lefi kayi musu?" "Dan Allah ki sawa kanki salaama. Ba wani abun tashin hankali bane. Dalilin daya saka naki karbar neman da suke mun ba komai bane fyace rashin son karbar mukamin da suke so su bani . Har ga Allah banaso. Amma yanzu abun yakai har gwamna ma ya nemi gani na naje mun gana yace sako daga mai martaba satin sama ba dagawa lalle na amince abani sarautar Talban Naduka wato hakimin waje" "Mashaa Allah! Mashaa Allah! Wannan ai abune mai kyau labari ne mai madi. Allah yasa albarka" "Congratulations baba" "Allah shi tayaka riko baba" "Mashaa Allah..." Cewar Anees. Dr. Abubakhr dollars ya kada kansa ya dubi hajiya qibdiyya yace, "Kina ganin na amince kema?" "Mu cigaba da addua kuma kayi istikhara, Don neman zabin Allah idan alkhairi ne Allah zai amince a nada ka idan ba alkhairi aciki ba zaai ba inshaa Allah inason ka sakawa ranka haka kawai" Ya sauke gwauron numfashi, Yana sake kada kansa yace, "Toh shikenan Allah ya tabbatar da abunda yafi alkhairi Amin" "Aameen " suka amsa baki daya... Haka dai suka cigaba da tattauna lamarin. Kafin yaran suyi musu sai da safe kowanne ya tafi daki don kwanciya kasancewar dare yaja.. Nan sukabar iyayen na su. Hajia qibdiyya na dada tausasar zuciyar mai gidan nata Dr. Abubakhr dollars.... ::::: NADUKA ZONE _INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_ _KU MARMATSO KUSA...🔊_ _ZAFAFA BIYAR 2024_ _ZAFAFA BIYAR!!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_ _YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_ _GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_ _________ _1_ *_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_ _2_ *_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_ _3_ *_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_ _4_ *_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ [2/26, 4:22 PM] Hafsaat🧕: _K'K'J_ _(M/W/S)_ _✍️:MX_ _21_ ::::: *NADUKA ZONE* *Malam Liti* ya sauke Malama Hindu har kofar gidan su dake unguwar Naduka zone. Ta bude kofar ta sauka tana yi masa godia, "Nagode sosai" "Yauwa sai da safe" Ya amsa ta yana mai juya kan motar... Cikin gidah ta shiga bakin ta dauke da sallama ta zare hijabin ta ninke ta ajiye akan kujera tayi kitchen tanata sauri. Ta ajiye Kwanon akan kanta ta fara kokarin daukar food flask zata wanke taji shi da nauyi. Sai a sannan ta lura kwanukan baki daya an wanke su tas. Ya yinda food flask din data daga taji nauyi ta bude murfin sa... Tururin shinkafa da wake ya daki fuskar sa ta karkade murfin gumin ya tsatstsafe sannan ta rufe Ko a Ido sunyi washar washar. Ko data saka abun diba ta debi kadan ta saka a baki taji lugif kowanne ya dahu. Ta taba bokitin ruwan wanka ma taji shi taf an cika shi da tafashasshen ruwan zafi. Gaba daya dukkanin aiyukan da zatayi anyi. Ga awara nama tanata turiri an yayyanka. Ta fito daga kitchen din tana dokawa Nawraah Kira, "Nawraah.. Nawraah" "Naam ummy.." ta sakko daga bene da sauri, "Kin dawo?" "Na dawo Nawraah. Waye yayi aiyukan nan.?" Ta tambayeta tana nuni da kofar kitchen da yatsa. Dai dai lokacin da Ashfeef ya fito daga dakin su yana rufe bakinsa da tafun hannun sa sakamakon hammar data taho masa, "Sannu da zuwa ummy" "Sannun mu... " "Hamma ne yayi ummy.. shi yayi komai nima nace zan taya shi wanke wanke yace aa yaji Ina mura na barshi" "Yana Ina?" Malama Hindu ta tambaye su tana mayar da hawayen da keson ya tsiyayo daga idanun ta "Yaje baya shanya" "Shanyar me?" "Kayan abbiey ya wanke da naki. Yace muma gobe zai daure nanu ni da Amnah... Ai bata karasa sauraron Nawraah ba ta fice daga cikin gidan tayi baya inda suke wanki suke shanya a igiyar wankin da suka daura a bayan Alokacin har ya kammala shanyar, Yana katse gumin da ke zuba daga goshin sa saboda ranar dake tsananin dukan goshin nasa. "Hamma" ummy ta kira shi tana girgiza kai "Ah ummy har kin dawo?" "Na dawo .... Haba Hamma duk Kai kadai?" Ta fada tana kallon sa cike da tsananin tausayi. A duniya batasan me zata sakawa da babban dan nata ba. Hakika shi din babban jigo ne acikin rayuwar su baki daya. "Wane aiki ummy? Dan dauraye kayan nannayi fa kawai. Sauran aikin bani nayi ba" "Kai kayi mana... Ashfeef yanzu ya tashi daga bacci. Nawrah ta gaya mun duk Kai ne kayi komai kamar ko da yaushe. Aiyukan nan sun maka yawa Hamma ka dinga bawa kanka hutu dan Allah " "Ummy idan banyi ba wa zeyi musu uhm?" "Sai a rarraba aiyukan kowa yayi. Kuma ba zama zan dingayi ba acan inda na samu aikinn Ina gamawa zan dawo inshaa Allah . Kaji ko?" "Tohm ummy" "Allah ya maka albarka. Allah ya maka albarka. Allah ya maka albarka. Ya inganta rayuwar ka Allah ya daga ka ya buda ka ya sanya tarin alkhairi a dukkanin abunda ka saka a gaba kaji?" "Aamin ummy... Jam'an inshaa Allahu" Cikin gidah suka koma. Abincin data taho dashi tace yaci rabi ya bar wa yaran sauran yace aa yayi cokali biyu ya bar musu. Ya tashi ya futa ya hada murhunan awara nan da nan ya hada komai. Ya koma kitchen ya dakko abubuwan da zasu bukata ya Kai wajen. Ummy ta sauya kaya taje ta zauna suka fara tuyar atare. Nan da nan aka fara tururuwar layin awarar. Malam Liti ne a farko farko da food flask din hajia qibdiyya. Ba yadda ummy batai ba ba zata karbu kudin awarar nan ba malam Liti yace hajia qibdiyya tache inde bata karba kudin awarar ba to ya barshi kar ya sayo mata. A dole ummyn ta zuba masa awarar ya tafi.. Bappah Junaid ya dawo daga wajen aiki a matukar gajiye. Ashir ya yi sauri ya karasa ya tare shi ya karbu jakar aikin sa ya shiga da ita cikin gidah yana doka masa sannu. Ya kai masa ruwan wanka mai zafi bandakin sama. Sannan ya koma wajen awarar yana taya ummy . Yayinda ita Kuma ta tashi ta nufi wajen Mai gidan nata Ya karasa wankan ta zuba masa abincin a plate tana bashi ya cinye ras Yana shi mata albarka. Suka shiga hirar Ashir da irin kyautatawar da yake yi musu sosai sun dade suna shi masa albarka da sauran yaran na su baki daya Alokacin ne Kuma bappah Junaid yake gayawa ummy ya kaiwa bappah Auwalu kudin nan daya ce masa shi ya bashi sai bappah Auwalun yaki karba kan shi lalle bashi yake so idan ba zai karbi bashi Wajen wani ba to ya barshi. Dakyar bappah Junaid ya tausashi ran dan uwan nasa yace masa ba kudin sa bane bashi ya karbi masa dama da niyyar shi zai biya nasa idan ya samu kudin. Amman tunda baya so shikenan ya rike bashin sanda ya samu ya bayar.. Ya karkare mata da, "Yanzu dai dama sheda nake nema... Kuma ga ki. Ko bayan rai na kudin nan dana baiwa Hamma Auwalu.. kyauta na bashi ba bashi ba. Dan Allah kada ku manta saboda halin mantuwa" "Abbieyn su ai babu wanda yasan gawar fari. Ka dai na cewa haka ma. Sannan wannan batu tsakanin ka ne da dan uwan ka. Ni nasan nan gaba idan ka gaya masa ai kudin ka ne ka bashi kyauta ka tausashe shi zai amince ya bar batun bashi ne ala dole sai ya biya .. Amman yadda kache hakan zaai abbiey" Bappah Junaid yayi murmushi yayinda ya saka hannun sa kan kumatun ta yana shafawa ahankali yace, "Hindu na kenan .... Kyakkyawa Mai kyakkyawar zuciya, dabiah, nutsuwa, biyayya, hankali, tausayi, Kai komai kin hada hindu. Ubangiji Allah ya shi Miki albarka. Ya raya Miki yaran ki Amin" "Aamin abbiey tare da Kai Allah ya raya mana su baki daya ya musu albarka.." "Aameen...Ni kuwa ya gidan aikin naki?" "Yauwa daman yanzu nake shirin cewa baka tambaye ni ya yau takasance da ni ba...." "Maza.. Maza bani na sha..." Malama Hindu ta gyara zama tana duban mai gidan nata cike da murmushi ta shiga labarta masa dukkanin abunda ya faru tundaga lokacin data shirya tayi wanka direba ya dauketa ya kaita gidan har ya zuwa sanda ya dawo da ita. Komai da komai sai data gaya masa. Kuma bappa Junaid yaji dadi da irin karbar da tace sunyi mata. Ya Kuma sake aminta da aikinta agidan sosai. Yayi musu addua sosai hadi da fatan cigaba da samun nasarar rayuwa marar yankewa.. Sunata hira har awara ta kare yaran suka karasa gyara wajen komai da komai... Sun samu ciniki sosai mashaa Allahu.. :::::::: Farin ciki lullube a fuskar sa, yayinda hannuwan sa ke rike da ledar mai baki da yellow dake dauke da kudaden da kanin sa junaidu ya aro masa ya shiga gidan nasa bakinsa dauke da sallama. Ya yinda daya hannun na sa buredi ne ya saya da ganyen shayi da sukari ya tura kofar gidan nasa bakinsa dauke da sallama........... _INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_ _KU MARMATSO KUSA...🔊_ _ZAFAFA BIYAR 2024_ _ZAFAFA BIYAR!!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_ _YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_ _GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_ _________ _1_ *_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_ _2_ *_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_ _3_ *_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_ _4_ *_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ [2/26, 5:06 PM] Hafsaat🧕: _K'K'J_ _(M/W/S)_ _✍️:MX_ _22_ :::: *Tana* kaame akan kujera ta harde kafafu tana kuma karkada su atare. Kanta a sama. Yayinda hannuwanta ke dunkule daya cikin daya. Kana kallon ta kasan tunani ne takeyi da alama kuma tayi nisa ainun a abunda takewa tunanin.. "Salamu alaikum..." Ya sake yin wata sallamar a karo na uku.. Girgiza kai yayi ya karasa shiga ciki ya daki hannun kujerar da take Kai. Ta girgiza da sauri cike da firgice. Ganin shine yasa ta ja dogon tsaki tana wulkita masa harara, "Meye haka dan Allah?" "Bansani ba. Sau nawa Ina sallama kinyi kunnen uwar shegu? Sai kache ba musulma ba wai ke ba zaki wa kanki fada ba ko Nusaiba?" "Ah menayi? Ko kuwa Kai baka tunani? Akwai dan Adam din da baya tunani ne balle ni dake cikin matsatsi da kuncin rayuwa. A wannan tsurkun gidan mai cike da ban haushi? Har a tambaye ni tunanin me nakeyi? " Dogon tsaki yaja yana girgiza kai ya dubeta cike da takaici yace, "Zakaran ka dai rakumin ka Nusaiba. Ki dai na Kai kan ki inda Allah be Kai ki ba fa.." "To kaji ka. Astagfirullah irinku ne masu janyowa mutum masifa yana zaman zamansa. Yanzun wani abun sab'on nache? Yo ai zama da Kai shine babban tashin hankali idan ba kasani ba yau ka sani" Murmushi yayi Wanda yafi kuka ciwo Yana karkada hannu yace, "Tun safe nake neman Abu daya.. tun safe ko karyawa banyi ba na futa nema. Tun safe ko iyali na bansaka su a Ido ba na futa garari nema, Amman kice mun haka Nusaiba? Wai ni yaushe Zaki hakalii ne? Kullum girma kike amman tamkar kina cin kasa" Mikewa tayi ta saki guda hadi da daga hannu sama ta nana a cinyarta tace, "Auwalu kenan.. inbanda matsalar gida data fara bada matsala idan baa gyaraba damuna zatai gyara shine kake tunanin tun safe ka fita nema? to namiji ai da nema aka san shi ba zama agidaah ba kamar mace. Mace ce akasanta agidah. Dole ne namiji ya fita ya nemo ya bata. Duk mazan kwarai haka suke idan ka tsame kan ka. Har ni zaka cewa yaushe zanyi hankali Auwalu? Ai babu mai hankali da zata zauna da Kai wallahi kaji rantsuwar Allah. Duk nace mai hankali ishasshe data san mutinci da daraja ta ya mace wallahi ba zata zauna dakai a matsayin matar ka ba. Domin kuwa ta gama tabewa. " Mtsceww, Tsceww, Mtw... Ya saki tsaki har Kaso uku a jere. Ya dubeta cike da tsananin bacin rai yace, "Duba kiga ni... Kaf birnn nan kadan ne inda ban zagaya ba Ina neman rance na kudi da zanyi wannan gyaran na rasa. Har sauran yan uwa na Kira a waya kowannen ya bani uzurin sa kan babu. Wanda dai banason gayawa din saboda kowane hali yake zaije ya nemo wallahi kafin nace ya samomin ma don munyi maganar gyaran amman bance inaso ya nemo mun ba wallahi sai gashi yazo da kansa dauke da kudin ya kawo mun fiye da adadin yadda nake bukatar ma. A duniya idan ban godewa junaidu ba wa zan godewa! Kaf Yan uwana babu Wanda keda zuciyar Yan uwantaka da dinbin zumunci irin junaidu.." ya karasa fada yana mai zama akan kujera hadi da dafe kansa da hannuwan sa biyu ya tallabe. Leka ledar tayi idanuwanta suka sauka akan farare kal bugun Abuja .. Ta silale ta zauna a kusa da shi hadi da saka hannu ta janyo ledar sosai ta buda ta hango bandir din dubu dubu mash tarin yawa. Jikinta har rawa yake ta dau bandir daya tana gwalalo idanun . Bappah Auwalu ya wafce kudin ya rike ledar a hannun sa yana kallon ta Nusaiba akwai makirci nan da nan ta kwabe fuska ta rausayar da Kai tana jan kasan jelar gashin ta tace, "Naga ranka ya baci akan maganganun dana fada . Kayi hakuri kuskuren harshe ne... Bazan sake ba" Bappah Auwalu yayi murmushi kawai ya gano ta sarai. Amman saboda tsabar sonta ya rufe masa idanu kawai ya girgiza kai, "Allah yása mu dace Amin" "Aamin..yanzu yaushe zaai gyaran gidan" "Ko gobe ma inshaa Allahu.." "Auwal......" Ta Kira sunan sa irin yadda take Kiran sa tun suna saurayi da budurwa. Yana jin sanda ta kira shi ya sake murmushi kawai, don Sam bata Kiran sa da haka sai idan ya samu kudi tanason ya bata wani abun. Don rabon data kira shi haka tsakani da Allah tun suna saurayi da budurwa da Kuma farkon satinnai na auren su "Auwal magana nake maka" "Auwalu nake Nusaiba " "Nusaiba gatsal? Kai ma kadan saya mana... Nusyn Auwal... Ko ka manta wakar tamu ne da muna saurayi da yammata?" Mikewa yayi zai tashi ta mike itama tana riko hannun sa "Ka tsaya kaci abinci mana Ina zaka?" "Wanka zanyi Nusaiba. Ki kyale ni" "Aa bari adan kashe sanyin ruwan yanzu. Sai kayi kaci abinci kaji. Zauna mana" Komawa yayi ya zauna Yana grigiza Kai. Nusaiba akwai ta da salo kala kala duk yadda yask yaki biye mata hakan yaci tura. Don bayan da ta dafa ruwan yayi wanka. Ta zuba masa abinci yaci. Haka ta dinga jansa da hira har yaran su da ta aika siyo gawayi suka dawo. Su kansu Layla sunyi mamakin ganin iyayen nasu zaune suna hira. Nan suka zauna suma anatayi da su. Yake gaya masu ya samu kudin da zaa gyara musu gidan sunata murna. Har lokacin kwanciya bacci yayi Layla ta nufi daki ta kwanta. Nusaiba ta tasa bappah Auwalu suka tafi daki. Yayinda Ahmad ya dakko katifar sa ya saka a parlor ya makala net ya kwanta... Duk yadda bappah Auwalu yaso zillewa haka ya hakura ya bada kai bori ya hau. Dole sai da Nusaiba tasaka ya saya mata waya da ake latsa ta wato torch screen ta yan gayu. Sai wani yauki take tana rike da wayar duk inda zata.. Yan layin nasu kowa ya sheda tayi wayar masu kudi Har gidan bappah Junaid ta shiga tanata fiili da wayar a hannunta. Lamarin ma daria ya bawa Malama Hindu. Don sarai tasan da kudin da aka bawa bappah Auwalu ne zata tursasa shi tasa ya saya mata wayar adole... ============ Toh haka rayuwar ta cigaba da kasancewa. Kowanne bangare ana samun cigaba musanman gidan bappah Junaid. Su Nawrah sunyi sauka mashaa Allah. A Kuma shekarar ne su Bappah sani zuka ziyar ce su Inda bappah sanin ya Kira meeting duka Yan uwan suka taru. Akayi magana kan matsayar karatun yara matan na boko. Lalle burin Nawraah ya cika duk kuwa da makaranta ce ta gwamnati zaa saka su tayi murna kwarai matuka don har hawayen farin ciki tayi. Dakyar aka shawo kan bappah Junaid daya ki amincewa kan wasiyyar yafendo ce yara mata kar suyi boko. Nan yan uwan nasa suka wayar masa dakan ba haka tace ba. Tace dai ga yaran nan kar dai amatsa Idan Kuma rayuwa ta sauya to sai abita da yadda tazo akuma yi addua... Don a rayuwar da suka samu kansu Idan Yara matan basuyi bokon ba Koda kadanne to akwai natsaloli da zasu fuskanta masu tarin yawa musamman da yanzun sabuwar rayuwa ce suke ginata wadda suka shiga ta zama a birnin Naduka garin yan boko da wayewar kai.... Lamarin ya cigaba da tafiya yadda ya kamata Alhamdulillah lalle Allah qadirun ne ala manyashau. Su Nawraah an fara zama yammata yanzu sosai cikar budirc ta fara bayyana atattar da su. Wani irin musulmin kyau ne ke kara haskakata. Wanda wani lokacin saboda tsabar maza samari dake cewa ana sallama da ita gata da kananun shekaru hakan yàsa ummyn ke cewa ta dinga saka niqab idan zata futa. Unguwa ma sai aka dena zuwa da ita ba kowacce ba. Don hajia qibdiyya ma tayi tayi taga yaran, ummy tace zasu zo mata In shaa Allahu nan da wani lokacin idan komai ya dai dai ta... _INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_ _KU MARMATSO KUSA...🔊_ _ZAFAFA BIYAR 2024_ _ZAFAFA BIYAR!!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_ _YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_ _GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_ _________ _1_ *_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_ _2_ *_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_ _3_ *_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_ _4_ *_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ [2/27, 11:26 AM] Hafsaat🧕: _K'K'J_ _(M/W/S)_ _✍️:MX_ _23_ _DR. ABUBAKHR DOLLARS DWELLING:_ Bakın ta dauke da sallama ta shiga cikin gidan bayan Malam Liti direba ya sauke tah. Ja tayi ta tsaya alokacin da basariya ta bude mata kofar parlorn ta shiga, Sakamakon manyan akwatinan data gani a parlorn an ajiye su. “Hajiyan na sama ne?” Malama Hindu ta tambayi başarıya mai aiki “Tana bangaren baba yanzu zata dawo amma ai tafiya zasu yi ma.” “Ah tafiyar ta tabbata kenan? Mashaa Allah Allah yasa aje a sa’a. Kafin ta dawo bari na rage wani abun” kitchen ta shiga ta zare hijabin ta ta rataye shi a maratayi, ta dauki rigar girki ta zura ajikin ta. Nan da nan ta shiga hada girkin su Hayfa, kasancewar yanzu ta gane kowannen su abincin da yafu so dan haka Kowanne tana dafa masa daga cikin cimar sa iyakar bakin kokarin ta. Kuma yaran suna yabawa sosai suna jin dadin girkin ta.. Tana çıkın aikin ne Hajia qibdiyya ta dawo sashen nata bakin ta dauke da sallama. Malama Hindu ta fito daga kitchen tana goge hannunta da tissue kafin ta jefar acikin dustbin ta tsugunna tana gayshe da ita. “Da Allah tashi Hindu. Nace ki dai na tsugunnawar nan Allah. Yaushe kikazo? Ina wajen baban su ne.” “Ban jima can ainun ba dai. Eh haka başarıya tace mun da nazo ta bude mun kofa. Har na dubi akwatinan ma nace Allah sarki Hajia tafiyar ta tabbata kenan?” “Wallahi kuwa Hindu. Tafiya ta tabbata inshaa Allah. Sai gobe da daddare ne amma jirgin mu zamu tashi yanzun dai nace akai akwatinan booth na mota kar mu wasu abubuwan manta” “Hakane kam gaskia don tafiya tagaji haka. Toh Allah ya tabbatar da alkhairin sa yasa kuje a sa’a yasa ki sauka a sa’a Amin” “Aameen Yaa Hayyu yaa Qayyum. Godia nake kwarai Hindu. Dan Allah Idan kin gama aikin ma zan aike ki gidan wata kawata ko ince yar uwata ma don mun zama yan uwa, matar aminin mijina ce. Malam liti zai kai ki please” “Tohm Hajia bari na kammala. Yanzu” “Yauwa eh zan baki daya wayata ma sai ki tafi da ita ki dakko samfarin kayan hotunan su. Kaya ne ta kawo zamu zuba a store . To wasu sunyi extras haka double shine zaku daddauka da kuma rubuto jerin samples “ “Toh Hajia amman dai daukar hotan ne dai da duk ma abunda za’a iya miki ta wayar wallahi ban iya ba kasancewar bana rike da babbar waya. Amman Idan ba damuwa sai mu biya na dau matar yayan mijina taşan kan waya Idan kuma Nawraah sun dawo daga makaranta ma sai muje da ita” “Toh shikenan duk yadda kukai ba damuwa. Ai kuwa yakamata ace kin fara amfani da babbar waya Hindu. Daman wayar ba wani amfani nake da ita ba sosai saboda inada ipad da ita nake amfani. Inshaa Allah Idan kika dawo na kwashe komai na kai sai na bar miki. Ma dinga vedio call Idan na tafi inshaa Allah” “Nagode Hajia, Nagode Allah ya saka miki da alkhairi Allah ya biya miki dukkanin bukatun ki na duniya da lahira Allah ya saukeki lafiya Allah kuma ya raya miki yaran ki ya iya miki ya daga ki amin.” “Aameen Yaa rabbi Hindu. Jam’an inshaa Allahu” “Bari na karasa girkin sai na zo” “Tohm Hindu. Nima bari na cire rigar nan na saka marar nauyi….” “Tohm Hajia” Hajia qibdiyya ta haye sama dakin ta. Ya yinda Malama Hindu ta koma kitchen ta cigaba da girki. Nan da nan kuwa cikin ikon Allah ta karasa duka girkunan abincinnan data yi na Junior da Hayfa da kuma Anees. Ta jere musu kulolin abincin akan dinning ta dakko plates da serving spoons da fork da komai dai ta jera musu kowanne sannan ta shiga dakin hutawar su tayi wanka hade da dauro alwala ta mayar da kayanta. Sannan ta hau kan sallaya jin ana kiraya kirayen sallar azuhr ta yi sallah hadi da addu’oin ta.. Sannan ta mike ta gyara zaman hijabin ta ta fita... Ta nemi gefen carpet ta zauna tana jiran sakkowar hajia qibdiyya. Bata jima sosai ba da zama hajiya qibdiyya ta sakko daga saman sanye cikin kaya marar nauyi. "Hindu har kin kammala?" "Na gama hajiya. Ya jikin?" "Alhamdulillah Hindu" "Zaa karbi sakon yanzu ne?" "Eh, Amma kinci abinci ne? Kici abinci tukun ko?" "A koshe nake hajia" "Wane irin a koshe. Ki ce dai idan kika dawo zaki ci banason musu Hindu" "Tohm hajia inshaa Allahu... Nagode Allah ya saka da alkhairi " "Ba godia a tsakanin mu Hindu. Yauwa ga wayar na cire password" "Tohm" ta saka hannu biyu ta karbi wayar tana riketa da kyau "Wayar ki ce fa atoh ki kalleta da kyau" Malama Hindu tayi murmushi tana jujjuya wayar a hannun ta. Hadaddiyar waya kallo daya zakai mata kasan me kyau ce da tsada kuma.. Samsung ce latest design. "Nagode sosai hajia. Allah ya biya miki dukkanin bukatin Ki. Yadda kike faranta mana Allah ubangiji ya faranta Miki. Ya sauke ki lafiya Amin" "Aameen Yaa Rabbi Hindu" 'B'it pi'pi' pit B'it' Malam Liti ya nata danna horn ta motar. Malama Hindu ta fita da sauri tana rufe kofar parlorn ta shiga motar da sauri malam Liti yaja suka futa daga gidan, "Mu biya ta gidah zamu dau Nawraah da zata dakko hotunan sakon da hajia ta ce" "Okay tohm" Naduka zone ya nufa da motar tasu. har kofar gidan su malama Hindu ya sauke ta. Ta shiga da sauri tana kiran Nawraah. Nawraah da bata jima da dawowa daga makaranta ba tana zaune a parlorn su tana karanta wani littafi na 'computer science' "Naam ummy" "Ina Amnah?" "Sun fita da Hamma" "Okay! Maza shirya ki mun rakiya zaki dakko wa hajia qibdiyya wasu hotuna. Da wayar nan rike ta ma tace ba password." Nawraah ta karbi wayar tana zura hijabi, "Tohm ummy " A tare suka fito daga cikin gidah sukayi kicibus da Nusaiba tana tafe tana yamutsa da wayarta a hannu. Suka tsaya suna gaysawa tana daga wayar hannun ta ummy dai tayi murmushi kawai... "Fita zakuyi a motar can?" Nusaiba ta tambaye su tana kallo motar da malam Liti ke tukawa hadaddiya sai sheki takeyi. "Eh futa zamuyi " "Ungo Nawraah dan dauke ni anan wajen motar haka ki tabbatar ta fito" Nusaiba ta karasa fada tana gyara tsayuwar ta ajikin motar. Nawraah ta karbi wayar ta yiyyi mata hotunan. Ta mika mata. Nusaiba ta karba tana duba hotunan tana murmushi. Suka bude motar suka shiga ciki ita Kuma ta koma cikin gidah tana sake zooming hotunan tana murmushi musanman da motar ta dache da ita kamar ta ta.. Ta daga Kai ta dubi gidan su ranta ya sosu sam bata kaunar zaman ta agidan dan tafi son gidan nasu kudi inama ace ita mayar mai kudi ce, ta fantama inda take so acikin shiga ta alfarma da hawa manyan luntsuma luntsuman motoci da masu aiki suna take mata gaba da bayan ta... "Nusaiba Ina kokon?" Ta jiyo muryar Auwalu ta doki dodon kunnen ta . Ta yamutsa fuska tamkar yana ganin ta cike da kufulewa tace, "Dan Allah ni kakka ishe ni. Koko! Koko! Koko sai kace a karkara" ta tabe baki ta shiga cikin gidan... ::::: Babu nisa ainun suka karasa unguwar da gidan aminiyar ta hajia qibdiyya. Dankareren sign board ne an rubuta da manyan baki... *ALHAJI SAMBASO AVENUE* _INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_ _KU MARMATSO KUSA...🔊_ _ZAFAFA BIYAR 2024_ _ZAFAFA BIYAR!!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_ _YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_ _GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_ _________ _1_ *_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_ _2_ *_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_ _3_ *_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_ _4_ *_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ [2/28, 2:22 AM] Hafsaat🧕: _K'K'J_ _(M/W/S)_ _✍️:MX_ _24_ ::::::::: *ALHAJI SAMBASO AVENUE* *Wani * tafkeken gidah suka nufi gate din sa.. Manyan masu gadi majiya karfi a mummurde su biyu ne suka taso sukayi kan motar da malam Liti ke tukawa ganin ya tunkari gate din.. Ja yayi ya tsaya da motar. Masu gadin suka leka suka saka ya bude har booth dinsa tukun sannan dayan ya janyo wata aba kamar rediyo baka ya koma gefe Yana magana. Can ya dagawa dayan me gadin hannu ya koma ya zauna "Ku shiga" Ya fadawa malam Liti Yana rufe masa murfin booth. Malam Liti yaja motar Yana zakin siririn tsaki yace, "Na tsami zuwa gidan nan yadda kikasan gidan gwamna wallahi tsare tsaren su yayi yawa. Sun san nafi shekara nawa ko muzo da hajia ko ta aiko ni ni kadai amman masu gadin nan sai sun tsayar dani..." "Kayi hakuri. Inaga yanayin aikin nasu ne yazo da tsauri haka" malama Hindu tace da shi "Allah ya kyauta kawai. Abun nasu ne yayi yawa kam" "Ayyah" Ita dai nawrah na zaune tana raba idanu. Ta saba ganin hadaddun gidaje a dramas da labari idan ana basu. Amman bata taba ganin gidah me kyawun wannan ba.. "Allahumma arzuqniy" ta fada tana sake duban gidan alokacin da suka shiga harabar gidan da mota Malam Liti ya nemi wajen parking ya faka motar. malama . Hindu suka fita da ga ciki ta riko hannun Nawraah dake kalle kallen gidan. Murmushi malama Hindu tayi tace, "Ai gidan hajia qibdiyya yafu wannan kyau fa? Su gate dinsu da kansa ma yake budewa Nawraah" "Mashaa Allahu sunji dadin su" "Mashaa Allah! Kuma Allah ya Kai ku inda zakuje ku huta sa kwanciyar hankali Amin" "Toh Aaameen.. Amma ummy samun irin wannan gidan kan nasan ko a mafarki" "Yi sauri kitchen astagfirullah. Waye me azurtawa?" "Astagfirullah Allah ne" "Waye me talautawa? "Allah ne" "Waye me bayarwa" "Allah ne" "Waye mai rayawa" "Allah ne" "Waye me kashewa? Ya bayar asan da yaso ya hana asanda yaso" "Allah ne" "To ki yi maza ki roki gafarar Allah mumini baya yanke rai ga rahamar ubangijin sa. Allahn daya basu bai manta da mu ba kina ji na?" "Astagfirullah... Eh Ina jin ki ummy " "Shysa a har kullum ake son ka kalki na kasa da Kai kada ka kallo na sama da kai lalle idan ka kalla na kasa da Kai Wanda ka fishi komai tanan zaka Kara godewa Allah da rahamar da yayi maka. Nawraah wasu suna nan basu da matsugunin da zasu zauna Ina nufin gidah.. wasu basu da abincin da zasuci bara suke. Nawraah wasu suna nan kayan da zasu saka ma basu da shi sutura tayi karanci Nawraah. Wasu Kuma suna asibuti ma sai dai a kwantar a tayar basusan Wanda ke kan su ba. Wasu ma hankali ne basu da shi a zare suke suna kwana a bola. Nawraah lafiya kadai ma idan Allah ya barka da ita wallahi babban arziki ne. ... Ki kasance cikin hamdala ga mahaliccin ki shi Kuma zai ninka maki bukatin ki inshaa Allah" "Inshaa Allahu ummy" "Yauwa Nawraah,,, mace ce ke sai kiga Allah ya daga ki ya Kai ki gidan wani hadadde Wanda baki taba zaton samu ba Allah ne kadai yabar wa kansa sanin wayasan gobe. Kuma inshaa Allah khair" "Hakane ummy.. nagode sosai da tunatarwa" Suna tsaye a bakin kofar tun da suka danna door bell dai baa bude musu ba sai da Nawraah ta sake saka hannu ta danna madannin tukun sannan bayan yan mintina wata matashiyar budurwa kamar Nawraah tazo ta bude musu kofar Ta sakala earpiece a kunnenta kana jiyo karar sautin wakar da take ji.. Sanye cikin kananun Kaya riga da wando kanta ba dankwalii ta yi parking gashin nata. Wani hadadden babban parlor ne mai girma sosai yana dauke da saitin kujeru har biyu . Yayi matukar kyau parlorn kudi yayi aiki agidan domin komai Mai tsada ne sosai. Yarinyar data bude musu kofar wadda kallo daya zakai mata kàsan yar gidan ce dubada wani zama da tayi akan doguwar kujera ta cigaba da karkada kafa tana bun wakar da take sauraron ta earpiece. Can sai ga wata mata fara irin fararen ne don yarinyar ma data bude irin farar nance haka. Sunada kyau ba lefi . Irin buzayen nanne yan nijar Matar ta dashare baki tana duban su tace, "Dan Allah ku zauna... Malama Hindu ko?" "Eh ni ce ce. Barka da rana mun same ku kalau?" "Alhamdulillah..." "Ina wuni?" Nawrah ta gayshe ta "Lafiya kalau yammata" "Uhm lily kawo musu ruwa please" "Mommy ni fa ba Mai aiki bace. In kawo musu ruwa Ina Dela take takawo musu mana?" "What nonsense coman get up. Ki dakko harda lemo ki kawo".. "Wallahi a koshe ma muke hajiya" "To kinji sun koshi ma" yarinyar data kira da lily ta fada. Hadi da komawa ta gyara zamanta tana harde kafafun "Bari a kawo kayan. Ah ai dole kusha ruwa malama Hindu...takanas daga gidan kawata ai dole a karramaka . Sunana Dr. Bintu... Ke dama nasan naki hajia qibdiyya ta fada wannan ce bansan sunan taba. Yar ki ce?" "Eh yata ce... Nawraah" "Mashaa Allah... Sunan Mai Dadi Mai kyau kamar jta tubarkallah. Ga yata can Ilham muna ce mata Lily . Sai babban 'dana Marwaan... Lily zo ga kawa na Miki" Lily ta juya ta dube su duka a shekeke ta tabe baki tana girgiza kai, "Not my type.... " Dr. Bintu ta mike ta shiga wani daki tana kwada sunan, "Dela.. Dela" Da alama Mai aikinta ce don da sauri ta futo daga kitchen, "Naam hajia" "Zo ki fito da kayan nan duka please .." "Tohm hajia yanzu kuwa" Suna dai zaune suna kallon sarautar Allah dela ta fito da wasu manyan buhubuna dauke da kaya kaka kala. "Kunzo da wayar ki? Ku fara dauka* "Eh. Nawraah daukar mata" Nawraah ta mike tana daga kayan daya bayan daya tana daukar hotunan su wasu budiyoyin su take yi. Dela aiki ya kachame mata tamkar zatai hauka tazo tana cewa Dr bintu tuwo yayi ruwa gashi ko miyar bata hada komai ba. Malama Hindu dake jin su tace, "Bari na zo na kama Miki ko miyar ce" "Kai harda wahala ayi haka?" "Bakomai hajiya" Malama Hindu ta futa tabu bayan dela suka je kitchen din. Nan da nan dama miyar kuka ce. Malama hindu ta hada komai da zata tanada gata da saurin aiki ta fara hada miyar nan. Baa dau wani lokaci Mai tsawo ba kitchen din ya fara tashin kamshin Miya. Nan da Nan ta gama ta ta zuba a food flask ta dauraye hannun ta ta koma inda Nawraah ke daukar hoto da bidiyo din . Suka kammala daukar Yayinda suka lissafa Hadi da irga kayayyakin da suka haura guda biyu iri daya suka rarraba su Kashi biyu. Kowanne nawrah ta rubuta ta wayar ta ajiye. Suna gamawa sukai mata sallama zasu tafi.. Ta bawa Malama hindu dubu biyar ta Kuma bawa Nawraah riga da skirt na cikin kayan sabbu. Suka mata godia suka tafi. A mota malama hindu ta curo dubu daya tabawa malam Liti Dakyar ya karba yana shi mata albarka. Nawraah ta saka aka sauketa agidan su Kuma suka wuce. Malama Hindu ta kaiwa hajia qibdiyya wayar ta Kuma nuna mata alkhairin kayan da Dr bintu ta baiwa Nawraah. Da ita kanta data Bata dubu biyar ta nuna nata ta Kuma karin tabawa malam Liti dubu daya. Tayita yiwa hajia qibdiyya godia. Dakyar ta tsaya taci abinci aka Kuma zuba mata wani a kwanon ta. Hajia qibdiyya ta dauki wayar bayan ta kwashe komai ta hada da chajar ta mikawa malama Hindu Wanda saboda tsabar farin ciki har kukan dadi ta saki... :::; Washegari malama Hindu dataje yiwa hajia qibdiyya sallama Nan take sheda mata ai Dr bintu ta kira waya tanata yaba mutinci da iya girkin malama Hindu ta kuma roki alfarmar tunda futa qibdiyya zata tafi haihuwa waje yaranta biyu Kuma zasu yi jamia. Zatayi hutu acan sosai Kafin ta dawo tana rokon Dan Allah malama Hindu ta rika zuwa tana mata abinci saboda Mai gidan ta ya yaba kwarai da miyar da tayi yanata santi.. Dakyar malama Hindu ta amince dubada yadda hajia qibdiyya keta rokon ta... Nan sukayi sallama da su har yaran na ta da zaa Kai makaranta, junior da Hayfa. Yayinda anees Kuma zaiyi hutu tare da hajia qibdiyya zasu huta idan ta haihu har zuwa wani dan lokaci Kafin su dawo. Har hawaye malama Hindu da hajia qibdiyya sukayi saboda tsananin sabon da sukai da juna, malama Hindu tana katse hawayen ta tace, "Nagode hajia .. da dukkanin tarin alkhairin ki gare ni Allah ubangiji ya saka Miki da mafificin alkhairin sa ya bude Miki kofofin albarkar sa. Ya raya Miki zuri'ah ya shriya su tundaga kuruciyar su har gidan su. Allah Kuma ya sauke ki lafiya Amin. Dan Allah idan na Miki wani lefi Wanda nasan da Wanda bansani ba dan Allah ki yafe mun.Allah ya KADDARA saduwar mu ya hada fuskokin mu da alkhairi Amin" "Ni ce da godia Hindu Allah ya daga Miki yaran ki duk kuwa da kin mun rowar ganin su Kuma bakimin lefi ko daya ba Hindu. Sai ma ni da nasan tabbas na Miki Dan Allah ki yafe mun" "Ku gafarce ni hajia.abubuwan ne sai ahankali, Amma inshaa Allahu har sai kin gaji da ganin su ma. Ni ke Zaki aurar da su ma. Saboda ki yafemun " "Inshaa Allahu Hindu. Allah ya yafe mana gaba daya" Hajia qibdiyya ta rungume Hindu jikinta sukai sallama suna daga mata hannu suka shiga mota direba oga emaka yaja suka tafi. Yayinda ita Kuma ta shiga motar malam Liti ya sauketa agidah. Satin ta daya agida Kafin daga bisani Dr bintu ta fara Aiko direban ta yana daukar malama Hindu tana zuwa tana abinci Yana dawo da ita... Da wannan suka cigaba da rayuwar su.sabo sosai ya shiga tsakanin malama Hindu da Dr bintu. Itaxe yiwa mijin Dr bintu abinci Kuma ya aminta da abincin sosai yana masa Dadi don har kyautar kudi yake bayarwa ayiwa malama Hindu Wanii lokaci takan tafi da Nawraah don ta tayata wasu aiyukan na gidan aikin nata... Ranar wata asabar da yammaci..... _INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_ _KU MARMATSO KUSA...🔊_ _ZAFAFA BIYAR 2024_ _ZAFAFA BIYAR!!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_ _YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_ _GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_ _________ _1_ *_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_ _2_ *_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_ _3_ *_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_ _4_ *_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ [2/29, 2:02 PM] Hafsaat🧕: _K'K'J_ _(M/W/S)_ _✍️:MX_ _25_ ::::::::: *Ranar* wata asabar da yammaci... Malama Hindu nata sauri kasancewar Dr. Bintu tace mata kada tazo da safe ta bari da yamma tazo tayiwa mai gidan nata girki zai ci da daddare ba zai samu cin na ranar ba saboda wani meeting da yake da shi, Don haka malama Hindu ta karasa aiyukan da zatayi a gaggauce.. Ta zura hijabin ta tanata sauri ta sauka kasa. Duk yaran suna nan har da Layla yar gidan Bappah Auwalu tana zaune a kan kujera mai cin mutum biyu tana yiwa Amnah kalaba kanana a kanta. "Ummy tafiyar za ki yi yanzu ji rani.?" "Eh Nawraah kilama na so na makara." "Bari na saka hijabi na nazo" "Ai Nawrah baki gaji ba? Da kin zauna yau" "Aa zanje" "Tohm.shikenan shiryo da sauri" Malama Hindu ta karasa fada tana zama akan hannun kujera ta dubi Ashir tache, "Hamma dan Allah idan abbiey dinku ya dawo ga abincin cin sa nan a food flask na saka a kasan kantar kitchen. Idan yanason shayi kuma akwai ganyan shayi acikin kwanon nan na kan freezer." "Tohm ummy inshaa Allah." "Allah ya muku albarka baki daya... Ashfeef naga ka wanke takalman ball dinnan dan Allah dai karkayi dare kar ka dinga dare ma dai kaji ko?" "Ummy kwana zaki acan ne?" Ashfeef ya fada Yana kallonta Jin tamkar kwana zatayi tana bashi sallahu "Aa inshaa Allah komai dare da zan Kai a gidah zan kwana... " "Tohm Allah yasa" "Amnah banda wasan ruwa kinji? Kinga mura kike yi" "Tohm ummy" "Zo nan"Ta fada tana duban ta Amnah ta mike daga kalbar da ake mata daman saura daya. Ta karasa wajen ummy . Ummyn ta rungumeta tsam a jikin tana shafa gadon bayan ta "Allah ya miki albarka Amnah. Allah ya raya ku ya tsare kuruciyar ku har girma Aameen" "Aaameen.. "suka amsa ta baki daya "Layla bappah Auwalu Yana nan ne?" "Eh Yana gidah" "Okay. Idan nawrah tafito kuce ta sameni agidan Bappah Auwalu." "Tohm ummy," Fita tayi da sauri ta nufi gidan Bappah Auwalu... Ta kwankwasa kofar nusaiba ta bude tana mita ta dauka Layla ce, "Dan uban ki kinje kin zauna. Marar zuciya kawai. Kullum bini bini kina hanyarr gidan su dan uban ki. Uwar taurin Kai" "Kai Nusaiba.... " Ummy ta fada tana girgiza kai ta Kara da cewa, "Assalamu alaikum ga bakuwar yammaci" "Waalykm Salam Hindu ce Ashe. Na dauka Layla ce" "Uwar Layla ce wannan. Kai Nusaiba kiyi waa kanki fada dan Allah ki dinga shan ragowar ruwan alwala ance Yana saka hakuri ya tausasa zuciya" "Fada mata dai Hindu." "Ah Bappahn su ashe kana ciki,? Barka da yammaci?" "Barkan mu dai. Ina ciki . Duk Ina jiyo ku Ina jin maganganun da take yi ai kinsan mai hali baya fasa halin sa" ya fada yana hararo nusaiba. Ta gatsina fuska tana juya baya tace, "Maganar gaskia ce ai. Layla kaman taci kafar kare saboda yawo,kullum tana gidan su haba ai da gajiya " "Gajiyar me Nusaiba? Kada ki manta da nan da can din duk tsatso daya ne. Ko yau Layla ta tattara kayan ta ta koma can wallahi gidan su ne, Haka zalika idan Nawrah ta dawo nan ma gidan su ne, Nusaiba ke fa uwa ce. Maganar dama da nazo miki kenan nace miki ke uwa ce. Ta iya yiwuwa agaba ke zaki zama mahaifiyar su gaba daya ke zaki aurar da su. Ba wai sai bayan rai na ba ko a yanzu. Yanzu ace idan rai yayi halin sa Nusaiba ke ce mafi kusantakar zama uwa agare su wadda zata share musu hawayen maraicin su Nusaiba." "Haba Hindu maganganun me ne haka kikeyi? Ai babu Wanda yasan gawar fari sai Allah. Kuma 'yayan ki ko taki ko ta so 'yayanta ne. Haka zalika nata 'yayan naki ne" "Kwarai dagaske baooan su. Don ni anawa rashin hankalin wallahi gani nake ko ba rai na ba zasuyi kukan maraici ba saboda Ina da ku".. "Bar ma wannan zancen ta iya yiwuwa ma duk mu mutu mu bari ki. Yaran namu ma ke zaki cigaba da renon su . " "Sai dai idan kai ne zaka mutu ka barta Allah . Inshaa Allah sai na zama mai uban kudi na tara dukiya na zagaye kasashen duniya , na taka nera na bada dollar na lika yan dubu dubu da kyautar motoci sai na zama babbar attajira tukui" Cewar nusaiba tana murmushi da girgiza kafa "Toh Allah ya kyauta..." Bappah Auwalu ya fada Malama Hindu tayi murmushi ta mike tsaya jiyo muryar nawrah tana cewa , "Ummy na gama ki fito mu tafi" "Bari muje bappan su. Dama gidan aiki nazan leka. Allah ya kaddara saduwar mu" "To masha Allah, Allah ya dawo daku lafiya" Sa kayi ta fita. Nusaiba taja dogon tsaki tana bankawa kofar da malama Hindu tabi ta futa da harara. Ta mike tamkar jirgin sama kamar zata tashi sama ta shige dakinta tana rufo kofar da karfi ji kake 'kauuuu' Malama Hindu ta fita suka jera sika nufi titi kasancewar direban da zai dauketa ma ba zai samu damar zuwa ba. Don haka titi suka fita ta saka sika tsaya awajen aikin kai gidan nata wato bappah junaidu. Nawrah na daga can gefe ta basu waje tana wasa da kasan hijabin ta. "Hindu na...." "Naam junaidu na..... Ya aikin naku ?" "Alhamdulillah... Ai na gaya miki mai gidan dakike aikin ogan namu sun shiga meeting dazu ai yace mu taya shi da addua wasu manyan kadarori yake so ya mallaka inde ya samu dama zai mana manyan kyauta sosai . Kinga sai mu sake gyara gidan nan sosai" "Oh shi ya saka mai dakin sa tace ya shiga meeting kar nazo da safe sai dai da yamma kenan. Allah sarki to Allah ya amince. Amma abbiyen su ai gidan mu babu abunda ya same shi kasa ka wani damu kanka Allah " "Shagon awara nake son na bude miki daga gefen baya dinnan zaa tada shago a dingah sayar da awarar da sauran abubuwa." " Allah sarki junaidu. Allah ya saka maka da mafificin alkhairi. Hakika bani da bakin godia agare ka. Ka a sani har kullum ba zan taba dai na godewa Allah da kasancewa mata agare ka ba. Allah yabar mun Kai har gaban abadan abbiyen su. Allah ya hada fuskokin mu da alkhairi yasa ko a aljanna mu kasance atare da juna. Nagode kwarai... " "Wadannan kalaman fa Hindu? Sai kace wadda zatayi tafiya. Toh Allahumma Aminn ai komai na miki ban fadi ba Hindu. Domin duk inda matar kwarai ta Kai kin Kai kin zarce ma" Murmushi tayi ta dan kallo gefen Nawraah taga ta juya baya tana danna wayar ummyn dake hannun ta yayinda ba maaikaci ko daya awajen. Ta rungume da shi da sauri ta sake shi tana goge hawayen dake neman zubo mata, "SubhanAllah kukan meye wannan,?" "Kuma dadi ne.. kukan farin ciki ne, kuka ne mai dauke da tarin ma'anoni. Kasancewa ta mata agare ka. Kasancewar uwa ga yarana. Kasancewar suruka ga su bappah Auwalu. Abubuwa da yawa. Nagodewa Allah da samun zuri'a ta gari wato hamidniyya Lebanon. Allah ya biyaka da aljanna Junaid .. Allah kuma ya cigaba da bude maka kofofin alkhairi ka cigaba da kula da yaran mu. Gasunan amana ne Allah yabamu. Kaga nj dai bana nan yanzu aiki zan tafi. Ka Kula da su don Allah.." "inshaa Allah Hindu... Wannan kalamai haka? Yanzu zan koma karki ji komai Allah. Nasan dama saboda su kiketa maganganun akai kwantar da hankalin ki kinji?" "Inshaa Allah. Abincin ka Yana can na bawa Hamma sallahu. Bari mu tafi kar lokaci ya kure" "Sai kun dawo Allah ya bada sa'a ya miki albarka " "Aameen abbieyn su . Komai dare ai inshaa Allah gidah zamu dawo" "Tohm Allah ya amince Hindu" Daga masa hannu tayi shima yana daga musu suka nufi tasi suka shiga ta Kai su can unguwar ta su Dr bintu Gidan sika shiga bakunan su dauke da sallama suka gayshe da ita tana parlor itada mai gidan nata Kitchen suka zarce nan da nan ummy ta fara hada abubuwan abincin da zata dafa yayinda nawrah ke tayata. A haka har suka kammala komai. Ummy da nawrah suka nufi parlorn suka jera komai akan dinning Dr bintu da Alhaji Sambaso mijinta sunata magana a parlorn dauke da wasu takardu agaban su... Ya yinda tashar talabijin ke nuna wakar Maher Zain ta rahamatun lil alamin Nawrah na son wakar don haka ta danna recording ta ajiye wayar daga can gefe don ta tariyo mata muryar Maher Zain da ke raira baitin Waya Alhaji Sambaso ya daga ya gama amsa kiran ya saki Kara da karfi Yana jijjiga Dr bintu yace, "Alhaji ateeks ya amince.... Plazas dinnan din sun zama mallaki na. Harda estates din mejesa da guzare dana Gpo da na bayan Maduki., shikenan nayiwa Dr abubakhr warwas matsiyaci duk tarin arzikin sa da sannu sai sun zama mallaki na..." "Alhamdulillah.... Dama naki jinin munafukar matar sa sai uban izza da iyayi. Allah yasa su mutu acan duka kowa ya h... Ji kake taratsats malama Hindu dake tafiya tana jinsu zata ajiye tray din jikinta sai rawa yake jin maganganun da suke kafafunta suka fara rawa tray din ya kufce daga hannuwanta ya fadi.. A matukar razane suka jiyo gaba dayan su suna kallon ta. Duk sai suka sha jinin jikin su, "Me kike anan Hindu?" Dr bintu ta fada da karfi "Ba abunda naji Dr.. Dan Allah kuyi hakuri santsi ne ya kwashe ni" "Bangane ba abinda kikaji ba me kike nufi.?" Nawrah na daga kitchen tana jiyo su ta fito da sauri ta janyo wayar ta, "Menene wannan din me kike da waya?" "Wayar ummy ce na ajiye" ta fada tana futa daga wajen recording din" "Hajia sai da safe" malama Hindu ta fada tana kamo hannun nawrah Dr bintu ta juya ta kalli mai gidan nata. Ya saka yatsa a hannu yana ciza shi. "Hindu... Hindu?" "Naam hajia dare yayi tafiya zamuyi" "Ai baki gama ba, dama mana kunu" ta fada tana nuna mata kitchen Jikin malama Hindu ya cigaba da kakkarwa tana yarfe yatsa tace "Dan Allah hajia" "Banason musu jeki dama mana kunu nace" "Toh" Komawa tayi kitchen ta janyo hannun nawrah jikinta na rawa suka futa tsakar gidan ta zaro nera dari ta mika mata, "Maza maza tafi gidah" "Ummy meyasa?" "Ni dai nace miki ki tafi gidah ko? Tafi da wayar tawa ma " "Idan aka kira ki fa" "Baa wanda zai kira ma jeki yi sauri karki juyo ki, tafi gidah ki wuce kar ki dawo. Ki kashe wayar ma me kikayj awayar ne" "Recording wakar Maher Zain nayi" "Lokacin duk suna wadannan maganganun?" "Eh bansani ba ni dai tun dazu na ajiye ta" "SubhanAllah to tafi gidah dai ki kashe wayar idan kinje gidah ki bawa Hamman ku ya ajjye idan na dawo zan karba " "Kai ummy?" "Nawrah nace ki tafi ko?" "Tohm shikenan. Ga tawa ki rike" ta mika naga wayar me torchlight ta ummyn ta da da ta bar mata , Ummyn ta girgiza kai tana kakaro murmushi tace, "Ai dole sai kin saka na karba Kai nawrah dadi na dake KWANKWASON JIMINA ce MAI WUYAR SHAFAWA... Je ki Allah ya miki albarka..." Ummyn ta karba tana cusa ta a jakarta ta hannu ... Tana kambama jarumta irin ta Nawrah tun tana karama. Lalle idan ta girma za'ai mace mai kamar maza.... Nawrah ta futa daga gidan taje titi ta hau mota ta koma gidah. Yayinda malama Hindu ta koma cikin kitchen din duk abunda da suke ashe Dr bintu na hango su... Ba dai ta jiyo maganganun da suke.. Jikin malama Hindu na rawa ta shiga aikin data sakata ta dama kunun tazuba a flask "Hajia na karasa" "Hindu" "Naam" "I don't care da rantse rantsen da kike Amma Allah idan naji magana daya ta fita wallahi sai kinyi mamaki" "Wace magana hajia nace ba abunda naji" "Ni dai na gaya miki" "Inshaa Allah hajia. Ni ba zamma Kara aikatau ba wallahi daga yau da yardar Allah, na tuba dan Allah kiyi hakuri ki gafarce ni" ta durkusa kasa tana hada hannuwan ta "Shikenan jeki sai da safe" Hindu ta mike dasauri jikinta na rawa ta zura takalman ma wari da wari ta saka.. Tana futa Alhaji Sambaso ya mike zai fita shima, "No Alhaji please " "Kin aminta da ita.. ba ita ce mai aikin su ba kafin tafiyar su waje" "Dan Allah ka kyaleta nasan ba zata fada ba" "Okay ni ba wajenta zani ba" "But am... "Nace miki ba wajenta zani ba. Refreshing brain na kawai zanyi zan dan fita yanzu ba nisa zanyi ba ita kuwa ai nasan ta hau mota ta tafi ma" "Shikenan sai ka dawo" Fita yayi wajen gidan ya dau motar sa ya fita daga cikin gidan a hankali yake tafiya yana hango malama Hindu tana tafe tana waiwaye tana tafiya atsorace... Tunani dankare cikin kirjinta, wannan wace iriyar rayuwa ce haka? Dama zaman cin amana suke da su? Lalle duniya abar tsoro ce... Wayar dake gurin ta ce ta fara kara mai gidan ta ne wato bappah junaidu ta dauka muryarta na rawa ta saisaita kanta tace gata nan zata dake yanzu inshaa Allah... Daman titin yayi dubu ba street lights sun mutu..Salati ta fara yi tana karanta la'ilaha illa anta subhanaka jnni kuntu minazzalimin.. Alhaji Sambaso ya kara gudu zuciyar sa na kuna,, wato har ta fara kiran waya tana fada kenan? ya tashi kanta tana komawa gefen bishiya ya hadata da bishiyar ta daga sama can ta fado kasa tim kamar ba mutum ba .. Ya arce dagudu ya hau babban titi. Sai bayan yan mintina tukun sannan mutane sika taru tana numfashi dakyar,..aka lalubo waya ajikinta aka Kira number data amsa Kira karshe ta bappah junaid da nawrah tayi saying da abbiey ban da nan suka kira shi suka gaya masa hankalin da ake ciki. . Suka nufi gidan da ita wani mutumi ya temaka aka kaita kasancewar ummyn tanata magana da kyae kan akaita gidah Ana kaita baki daya yaran sukai kanta sunata ife ife da adduoi. Daga na suma rankaya asibiti Likitoci sukai kanta aka saka mata oxygen kasancewar numfashin ta ya fara sarkewa. Likitocin sunata kokarin bata temako, Bayan wani lokaci, Likita on duty ya fito daga emergency ward yana zare facemask dinsa ya dubesu kansa a kasa . Ashir ya karasa kusa dashi yana girgiza kafadar sa, "Ya jikin ummyn wani abun ake bukata? Jini? Kudi? magani? Me kuke so?" Likitan ya girgiza kansa bayan ya sauke katuwar bahaguwar zuciya yace, "Sai dai muyi hakuri Allah ya mata rasuwa...babban dadin kuma ta cika da kalmar shahada Alhamdulillahi.... _INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_ _KU MARMATSO KUSA...🔊_ _ZAFAFA BIYAR 2024_ _ZAFAFA BIYAR!!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_ _YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_ _GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_ _________ _1_ *_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_ _2_ *_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_ _3_ *_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_ _4_ *_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ [3/1, 1:57 PM] Hafsaat🧕: _K'K'J_ _(M/W/S)_ _✍️:MX_ _26_ :::::::::     *Dukkanin* su a tare ji da ganin su suka dauke na 'yan wasu daki'kai... Ji ka ke timmmmmm... Bappah junaidu ya fadi wanwars a kasa sumamme .. Likitan yayi kansa. Ashir ya shiga bubbuga kansa a bango... Yayinda Amnah ke duban su duka tana hawayen itama duk kuwa da karama ce ainun. Ashfeef ya rike hannun ta shima yana rera kukan sa ahankali Nawraah ta sulale daga jikin bango ta yi zaman dab'as na yan bori...Ta saki marayan kuka mai tsuma zuciyar duk wanda ya saurara.... "Ummy.... Wayyo ALLAH na ummy" Ta shiga maimaitawa tana bubbuga hannuwanta a kasa. Bappah Auwalu yana tsaye daga bakin kofar dakin bawa marasa lafiya na gaggawa temako inda aka shigar da Bappah junaidu da yayi doguwar suma suna bashi temako don ya farfado. Nusaiba na gefe tana girgiza kai... Mutuwar Hindu kwarai matuka ta girgiza ta. Hawaye suka shiga zirarowa daga idanun ta .. Su Layla suka karasa asibitin itada Ahmad... Ganin su suka yi cikin yanayi marar dadi... Jikin su yayi sanyi. Layla ta karasa wajen Nawraah dake kuka sosai kamar ranta zai fita ta zauna a kusa da ita tana kallon ta, "Nawraah..... Meya faru? Meya samu ummy? Operation ake ma ta? Ko ciwon ne ya kara tsamari?" Nawraah ta girgiza mata kai tana zubar da hawaye. Ta saka hannun ta ta share hawayen tace da ita, cikin rawar murya, "Ummy ta rasu" "Inna Lillahi wa inna ilaihi raji'un... Ummyn?" Fashewa tayi da kuka sosai itama ta saka tafukan hannuwan ta akan bakin ta. Ahmad ma ya fara hawayen yana girgiza kansa cikin dimaucewa, Har tsakiyar dare Bappah Auwalu ya futa ya kawo musu burodi dakyar ya tsawatar musu suka sha da ruwa. Wasa wasa har akayi asubah sukaci sauran burodin... Wata nurse ta futo daga ciki tana duban su... Kowanne cikin tashin hankali. Bappah Auwalu ne kawai yake kokartawa yana kukan zuciya, Ta karasa kusa da shi tana masa sallama. Ya amsa ta yana sharce hancin sa da hankici, "Mashaa Allah an samu ya farfado mun masa allura saboda ya samu nutsuwa . Ita kuma marigayiya idan akwai motar da zaa sakata aciki to idan babu munada kurkura mota ta haya sai a sakata aciki, dubu biyar ne kudin kaiwa" Ya kada kai yana sanya hannu acikin aljihu zai zaro kudin Nusaiba dake gefe tana duban su ta karasa da sauri, "Menene ?" "Kudin motar da za'a saka Hindu aciki ne zan biya meya faru?" "Har nawane kudin?" "Menene haka sai? Dubu biyar ne mana " "Yanzu dubu biyar din zaka kwasa ka bayar?" "Bakida hankali Nusaiba wallahi bakida hankali " "To ai gaskia ne. Shi ya bayar mana.... Dubu biyar dinnan idan ka kwasa ka bayar ya zamuyi da sayen taliyar...?" Dogon tsaki yayi ya girgiza kai cike da takaicin maganganun ta yace, "Zaki matsa ko sai na hanbare ki?" "Hanbareni halin naka zaka nuna a bainar jamaa hanbare ni Auwalu" Kudin ya kirga da sauri ya mikawa nurse din ta koma ciki. Ya bar Nusaiba a tsaye tanata banbamin mita. Ya nufi wajen Ashir ya riko shi Ashir din ya fashe da kuka. Bappah Auwalu ya riko shi ya rungume shi tsam a jikinsa Ashir ya shiga rusgar kuka tamkar karamun yaro yana kiran sunan mahaifiyar ta su "Ummy... Ummy" "Dan Allah ku dai na mata kuka, ku dai na zubar mata da hawaye. Addua take bukata yanzu ba zubar hawayen ku ba. Soyayyar kadai da zaku nuna mata yanzu addua ce. Sai tafi bukatar ta. Kuyi hakuri dan Allah. Uhm munyi rashi kam . Allah ya gafartawa Hindu ya kyautata namu zuwan. Bar kuka Ashir dan Allah kaji? Alhamdulillah jikin mahaifin naku ma ya farfado yanzu nurse ta fada. Kuma zamu kai gawar gidah don a sallace ta.," "Wayyo Allah na. Ummy na wayyo Allah " Nawraah ta shiga nanatawa tana cigaba da hawaye. Bappah Auwalu ya shiga wajen da aka rufe gawar malama Hindu da wani yadi shudi baki daya ya rib'e ya koma kalar jini. Saboda tsananin jinin dake futa daga jikinta har yanzu. Tun sanda aka kawo ta. Daman bayan likitocin sun yi gwaje gwajen su angani ta samo karaya takwas. Hudu a kwibi. Biyu kafafun ta daya hannun ta. Yayinda dayan Kuma gefen wuyan ta. Sai internal bleeding shima data samu. Sai Kuma jini daya taru a kwakwalwar ta. Sai ciwo a gefen goshin ta da aka mata dinki har zuwa lebenta. Domin fuskar ta ma ta rabe gidah biyu. Da sauran ciwuka Wanda ba zasu kirgu ba don da tayi rai ma ba lalle ta cigaba da moruwa ba, kasancewar spinal cord dinta ma ya tsinke. Bappah Auwalu ya saka hannu ya toshe bakin sa da tafin hannunsa alokacin daya shiga dakin yaga an lullube Hindu har kanta. Dankwalin data saka a kanta shi aka rufe fuskar ta. Tabbas kayan data saka ne dazu da ta je gayshe su. Kwakwalwar sa ta shiga tariyo masa ashe dama bankwana take musu na tafiya tamkar wasiyya? . . Wani siririn hawaye ya silalo masa ya sharce da bayan hannunsa sa. Tsayawa yayi aka gama cike ciken da zaai na takardu kasancewar irin wannan idan aka kawo marasa lafiya ranga ranga haka magashiyan, To police na shiga cikin case din. Don haka anyi dikkanin abunda ya dache daga karshe maaikatan suka Kai gawar malama Hindu cikin mota yar kurkura aka saka ganye agaba da bayan motar Ballah Auwalu ya tattara kan su baki daya yaje su tafi gidah zaa yiwa malama Hindu wanka a sallace ta... . Bappah junaid da allura ta sake shi ya dubi Karin ruwan da ake masa ya fizge shi da karfi ya mike Yana dafa bango ya fita Likitocin sukai kansa suna kokarin mayar dashi dakin hutun na marasa lafiya atafau yaki yace shi gidah zashi shima a sallaci malama Hindu da shi. Ba yadda sika iya haka suka kyale shi bayan sun bada maganin da aka saya masa. Akayi hayar mota ta debe su baki daya suka koma gidah Ko da suka koma gidan ma sabon shafin alhini sika bude. Masu kuka na yi masu surutai nayi masu dukan kansu nayi. Aka Kira yaran nasu baki daya lokacin da aka gama yiwa marigayiya malama Hindu wanka aka nadeta cikin likkafini fuskar ta kawai aka bari abude saboda yaran su gana da ita na karshe suyi mata addua. Fuskar ta takara kyau tamkar tana murmushi . Ataree suka shiga baki daya har bappah Junaid kowanne da addu'ar da yake suna sake bude babin wani kukan mai kuna "Allah ya jikan ki da rahamar sa Hindu Allah ya yaye Miki dukkanin zunuban ki ya sadaki da ajnabin rahama . Rabbi ya karbi bakuncin ki yasa karshen wahalar kenan. Ba abunda kikai min Hindu idan ma da akwai na yafe miki duniya da lahira Allah ya gafarta miki" bappah Junaid ya karasa fada har yana dora kansa akan gawar bappah auwalu ya fita dashi dakyar. "Ummy ... Ummy Allah ya gafarta miki Allah ya yafe mi ki, Allah ya sa aljanna makoma agare ki ummy. Ummy na rike alkawarin ki dayardar Allah zan cigaba da rike yan uwana har karshen rayuwata ummy" Ashir ya fada shima ya tashi ya mike ya fita kamar yadda bappah Auwalu yace kowanne idan yayi sai yabar dakin "Ummy Allah ya jikan ki Allah ya jikan ki ummy Allah ya jikan ki ya gafarta miki ya shayar da ke ruwan alkausara" Cewar Ashfeef ya mike da kyar ya fita yana boye hawayen sa "Ummy.... Ummy na... Ummy Allah ya jikan Ki da rahama Allah ya gafarta Miki Allah ya kyautata makwancin ki Allah ya sa aljannatul firdaws makomar ki ce, ummy inshaa Allah indai har Ina raye da raina da yardar Allah sai na kwato Miki hakkin ki da dik Wanda yayi Miki wannan mummunan hukuncin . Ubangiji Allah ya dafamun ummy. Inshaa Allah, Allah sai ya tozarta su ya wulakanta su ya d'ai d'aita su. " Mikewa tayi dakyar ta futa tsna sake fashewa dakuka... Nusaiba ta bi bayanta da kallo tana nazari akan kalaman ta na karshe... Suwaye suka kàshe Hindu? Nawrah tasan wani abu kenan? Lalle akwai sauran kallo a gaba idan da rai. Domin Nawraah KWANKWASON JIMINA ce MAI WUYAR SHAFAWA.... "Bappah... Ummy ta mutu yaushe zata dawo eh?" Amnah ta fada tana rike kafar wandon bappah Auwalu .m "Allah ya miki albarka Amnah Allah ya raya ki ya tsare ki kinji?" Ya fada mata yana kokarin mayarda kukan daya tayo masa Waje ya futar da ita bakin kofa. Nusaiba dawasu mata makota suka sake rufe gawar malama Hindu har zuwa fuskar ta suka daure. Aka sanyata a tabarma aka kullubeta da wani zanun aka sanyata a makara. Bappah Auwalu ya kira su Ashir aka sallaceta aka kaita gidan ta na gaskia Kafin a fitar da ita daga gidan sai da akayi dagaske yaran ta gaba daya da bappah Junaid sika birkice suna riko makarar suna hawaye kowanne yana surutai kamar mahaukata. Dakyar aka banbare su aka fita da ita zuwa makabarta aka binne ta Ta samu yabo sosai daga bakunan jama'ar da suka santa. Takuma samu mutane sosai da suka halarci jana'izar ta aka sallaceta suka kaita gidan ta na gaskia. Sannan aka dawo gidah akayi cirko cirko unguwar tayi tsiit. Yayinda zuriyar hamidniyya Lebanon tamkar ruwa ya cinye su saboda alhini . Hakika baa taba musu mutuwa data grigiza su bayan ta yafendo ba sai wannan ta rasuwar malama Hindu, Mai dakin bappah junaidu, Kuma mahaifiyar su Ashir, Ashfeef, Nawraah da kuma auta Amnah... _INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_ _KU MARMATSO KUSA...🔊_ _ZAFAFA BIYAR 2024_ _ZAFAFA BIYAR!!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_ _YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_ _GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_ _________ _1_ *_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_ _2_ *_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_ _3_ *_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_ _4_ *_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ [3/1, 7:15 PM] Hafsaat🧕: _K'K'J_ _(M/W/S)_ _✍️:MX_ _27_ ::::::::: *Haka* rayuwar ta cigaba da garawa.... Bayan kwanaki arba'in da rasuwar malama Hindu. Dangi na kusa dana nesa duk sun Kokkoma inda suka fito. Yayinda kowanne ya cigaba da rayuwar sa idan ka cire ahalin na malama Hindu da mutuwar ta dake su kwarai matuka... A Kwanakin ne Kuma hajia qibdiyya dake kasar waje ta kira wayar malama Hindu dake hannun Ashir. Ya amsa mata bayan sun gaysa ne data tambayi malama Hindu yake sanar mata cewar ai Allah ya mata rasuwa tun kwanaki... Hakika mutuwar ta daki hajia qibdiyya ji tayi tamkar da Wasa ko Kuma waswasi kunnenta yake mata sai data sake tambayar sa har sai uku Yana tabbatar mata sannan ta amince. Kuka ta fashe da shi tun awayar tana sallallamin wallahi batada masaniya. Don kwana biyu itama wayar tata bata hannunta sakamakon ta haihu dan ba rai kuma ciwon ta ya tashi na hauhawar jini sai da mai gidan nata ya sake zuwa yayi ciku ciku ya sake canza date din ranar da zasu dawo zuwa dogon zango mai nisa. Ashir sai ya koma bata hakuri jin tana kuka sosai mutuwar ta dake ta. Dakyar ta iya kashe wayar bayan ta bashi mai gidan ta Dr. Dollars ya musu gaisuwa. Ta Kuma bawa yaranta daya bayan daya sunyi musu gaisuwa ta wayar. Ta kashe wayar jikinta asanyaye Sai datayi kuka ta koshi sosai har sai da zazzabin ya tasar mata ta kira Dr bintu a waya don tasan Kila batada masaniya bata gaya mata ba bayan sunyi waya jiya da su . A handsfree ta saka wayar bayan sun gaysa. Murya a cike da alhini tache, "Baki da labarin rasuwar da akayine Dr bintu ko kuwa mantawa kike baki sanar min?" "Rasuwa kuma? Rasuwa fa kikace? Waye ya rasu? Kinganni a zaune Kinsa na mike a tsaye. Bangane ba waye ya rasu eh?" "Hindu dai mai aikina da ke maki aiki a yanzu" "Innnalillahi wa Inna ilaihi raji'un. Wallahi bansani ba. Yaushe ta rasu? Rannan tazo da yamma kamar yadda nace mata tazo da yamma tayi abinci wlh har take cewa zata dena aikatau. Naceto shikenan. Dama inata cewa kwanaki biyu shiru idan nakira wayar ta ma a kashe nache to inaga hutawar take bari nan da kwanaki kadan sai na kirata ko naje da Kai na na Kai mata kudin sallamar ta wannan watan meya sameta ? Zazzabin nan da akeyi ko Kuma tana da wani ciwon ne! Astagfirullah ko mutuwa ce dai tazo lokacin ta? " "Ashe baki sani ba. Har anyi arbain dinta? Wallahi sai yau dana kira saboda Nima kwanaki biyu dinnan kinsan saboda rasa babyn da nayi Dr yasa na dau hutun komai harda rike waya. Bashine mukai waya dake ba aranar dana fara amfani da waya" "Anyi haka ya jikin naki kuwa?" "Alhamdulillah da sauki." "Kwana arbain har anyi. Allah sarki Hindu Allah ya jikanta wallahi bansani ba. Kai banji Dadi ba wallahi. Don Allah ki gayamun kwatancen gidan ko Kuma driver ya Kai ki ni ai yasani tunda shi ke dakkota ya komar daita." "Wallahi bintu . Bakiji rai na ba Kai Allah ya gafartawaa Hindu. Wallahi bantaba ganin mace irin taba na Dade banga mutum Mai saukin kai da Bai dau rayuwar duniya da komai ba irin wannan matar. Inshaa Allah aljanna makoma ce agareta " "Tabbas tanada hakuri wallahi. Batada lafiya ne?" "Aa yace min accident ne irin hit and run dinnan?" Dr bintu na tsaye sai ta zauna jin kafarta ta fara rawa ta gaza daukar nauyin jikinta. Ta dafe kirjinta idanuwanta suka furfuto waje cikin tashin hankali tace, "Mota ce kenan ta kasheta ta gudu? Innnalillahi wa Inna ilaihi raji'iun " "Wallahi kusan haka yaronta yacemun. Yace police sun shiga case dinma, Amman dai an kasa gano Wanda yayi. Kasancewar dare ne Kuma ba haske awajen da aka kashe ta. Wai yaushe kikace tazo aiki last?" Gaban Dr bintu ya buga fuss. Tsabar tashin hankali sai harbawa yake kamar zai fado daga jikinta tace, "Kwanaki ne can kamar ranar larabaa date din........ Tazo da yammaci ta tafi da dare" "Exactly a ranar ne to daga gidan ki take wlh aka samu wani Wanda yake sauri kamar zai tashi ya bugeta ya gudu saboda rashin Imani. Ai addua nake Allah ya waiwayo damu ayi mai yiwuwa a nemo koma waye da karfin ikon Allah inshaa Allah da dakarun taro. Dole suyi dubada na issue din" Jikin Dr. Bintu asanyaye tache, "Kwarai ma kuwa .... Kai amma banji dadi ba Allah ya jikanta da rahama" "Toh aamen dai. Nima bari na je na kwanta dare yayi anan mu" "Shikenan kawata. Sai da safe agayda yaran" "Zasuji inshaa Allahu. Ki gayda mun da su Lily" "Inshaa Allah." Dr bintu ta zare wayar daga kunnenta ahankali ta daga kai ta dubi makeken hotan mai gidan nata Alhaji Sambaso dake jikin frame tamkar shi take ganu agaske tana girgiza kai tace, "Ko kaffara ba zan ba. Wannan aika aikan nakane Alhaji .. bayan rokon ka da nayi nace ka kyale matar nan, Ashe ashe abunda kayi kenan.. innalillahi wa Inna ilaihi raji'un yanzu ya zamuyi kenan .?" _INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_ _KU MARMATSO KUSA...🔊_ _ZAFAFA BIYAR 2024_ _ZAFAFA BIYAR!!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_ _YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_ _GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_ _________ _1_ *_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_ _2_ *_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_ _3_ *_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_ _4_ *_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ [3/2, 7:41 PM] Hafsaat🧕: _K'K'J_ _(M/W/S)_ _✍️:MX_ _28_ ::::::::: *Zagaye* parlorn ta shiga yi taje ta dawo tanata safa da marwa cikin tsananin tashin hankali. Jikin ta ya fara kakkarwa sosai, Baki daya tsoro ya cikata ya gauraye ta. Tabbas idan hajia qibdiyya da mijinta Dr abubakhr dollars suka dawo suka karbi ragamar case din to lallai sai an gano su, sun kwashi kashin su a hannuwan su. Tamkar zararriya ta shiga magana ita daya tana girgiza kai, "Sai da na roke ka nache dan Allah kada ka mata komai . Amman ka aikaita wannan mummunan hukuncin? Innalillahi wa Inna ilaihi raji'un." Jikinta na rawa tamkar mazari ta dauki wayarta ta kira shi har sau biyu bai dauka ba. Nanma ta masa message tace tanason magana da shi urgently ba reply. Mayafinta ta zura ta fita daga cikin gidan zuwa parking lodge. Wajen mai gadi ta nufa dake rike da makullayen motocin gidan, "Hajia ranki ya dade" "Barkan mu... Bani mukullin Glk" "Tohm gashi hajia. Allah ya dawo dake lafiya" "Amin" Direban ya taso da sauri ya gayshe ta ya karbu mukullin ya bude mata ta shiga sannan ya zagaya shima ya shiga ciki.... Baki daya bata cikin nutsuwa.. "Da gudu zaka tuka yau" "To hajiya.. Ina zamu je?" "Wajen Alhaji" Suna tafe tana dukan bayan kujerar gaba, kasancewar a owners corner take, Idan ta tuno mummunan hukuncin da ya zarce ya aikata musu, Cikin bacin rai da fargaba data gauraye ilahirin jikin ta har suka karasa kanfamin direban ya ajiye motar ta a ma'adanar motoci Ta shiga cikin kamfanin bayan ta gyara facemask din data saka acikin mota. Wasu maaikatan suka gane ta. Duk da facemask din data saka suka shiga gayshe da ita ladabce cike da girmamawa ta amsa tana tambayar daya daga cikin su, "Yana ciki?" Ta nuna kofar ofishin sa dake kallon su "Eh yana ciki hajia" "Okay nagode" Kofar ofishin ta nufa ta tsaya. Ta saka hannu tayi kicking har sau uku. Yana daga zaune akan doguwar kujera makeken ofishin nasa dake dauke da bangaren desk da kujera da computer da mini fridge da kayan kallo Sai kuma daga gefe set din kujeru ne suma da makekiyar tv da dispencer. Sai wani drawer kuma da murfin ta garai garai ana hango komai na ciki. Su plates da cups ne da tissue da sauran su. Shiga tayi ciki bakinta dauke da sallama. Ya daga kwalbar sugar free lemo yana sha Dubanta yayi ta gefen idanu, ya sake karkata kwalbar cikin bakinsa ya shiga zuka ahankali yaki ajiye kwalbar, Zama tayi a kujera mai kallon sa tana masa wani irin kallo tace, " Ko shekara zakai kana shan lemon nan cikin kurbar tafiyar kunkuru da yardar Allah zan jira ka gama sha ka amsa mun tambayoyi na. Ko ince ka mika kanka ga jami'an tsaro bisaga mummunan ta'asaf d akai" Ya shanya lemon ya ajiye kwalbar yana duban ta. Ya dakko wani lemo a gefen sa daya ajiye ya mika mata yana murmushi, "Ungo sha... Haba rabin rai na" "Ba maganar wasa ce ta kawo ni ba" ta hade rai tana amsa shi "To fa menayi? Wait ko dan ban miki sallama ba na futa dazu? Sauri nake zamu shiga meeting. Kiyi mun afuwa" "Kaga Alhaji ka dena wani kwana kwana . So nake ka fito a mutum ka gaya mun dalilin ka na aikata abunda kayi jiya" "Jiya? Menayi jia?" "Kafini sanin abunda kayi ai. Ka kyauta kenan haba Alhaji wane irin roko ne ban maka ba kan ka kyale matar nan wallahi nasan ba zata fada ba. Amman Alhaji kaje ka... "Kinga ni bansan maganganun da kike magana akai ba. Wace mata kikace na kyale? Shin me na aikata?" "Har kanada bakin magana ? To bari na fito maka a mutum tunda Allah yasa kaki magana... Mena ce maka akan mai aikin mu Hindu? " "Me kike nufi ne? Wace mai aiki? "Mai aikin gidan Dr dollars da mu kai magana. " "Oh mai akai! Kudin ta zaa bata kome?" Dr bintu taja dogon tsaki cike da takaici ta mike tsaye ta karasa daf da shi tace, "Ni renin hankali ne wataran banason sa wallahi. Kayi abu ka nuna kai atafau bakai bane. " "Bintu me ya sake samun ki ne wai eh? Idan kudi kike bukata ga atm din kinsan pin ai je ki spoiling kan ki" "Banason kananun maganu wallahi. To tunda kaki amincewa Kanata nuna bakasan me kake nufi ba. Matar da ka buge a mota kana sane akan sani. Ta mutu ... " "Wace mata? Wane buge? Bangane me kike nufi ba" Murmushi tayi tana girgiza kai tace, "Ni ce ba wata ba... Yusuf" ta karashe maganar ta cikin fadar ainihin sunan sa na yanka Ya dubeta yana maze fuska. Domin duk sanda ta kira ainihin sunan sa to lalle babban lamari ne Kuma cikin fushi take fada . Su kanyi haka daman idan yan fadan sun tashi.. "Magana nake maka" "To me kikeson nace bayan tambayar danayi mi ki?" "Yusuf a ajiye maganar raha a gefe. Tunda kaga na tako da Kai na nazo kasan ba karamin abu bane. Kai kanka kàsan akwai abunda kake boyemun. Sau nawa Ina kiran ka kaki dauka? Ga wayoyin ka nan, daya agaban aljihun ka dayar gatanan a kusa da Kai. Amman kaki dauka. Don haka duk wani boye boye da kake banaso ka fito ka gayan gaskia ", "Wai maganganun me kike haka ne? Ba Kai ba ... "Yusuf dan Allah banason jayayya. . Ka futo ka gayamun gaskia boye boye ba naka bane. Case yana nan yana nisa awajen iyalan marigayiyar, Yusuf. Kai kanka kasan sai kanada babban issue ne kake zama a office baka dawo gidah ba. Kaki daukar waya da sauran su. Matar ka ce ni nasan halayen ka bari na fito maka a mutum . Hajia qibdiyya ce take sanar da ni, Rasuwar Hindu case din hit and run exactly ranar datazo mana ta karshe ta taafi da daddare dinnan. Daman Kuma na gaya maka nace wayar ta bata shiga a kashe ko yaushe idan na kirata saboda hakkin ta na kudin aikinta na wannan watan... " "Ni menene hulda ta da rasuwar ta yanzu? Allah ya jikan rai" "Yusuf boye boye ba naka bane. Case hana kokarin komawa hannun su hajia qibdiyya kasan su da hin diddigi da dakarun tsaro na kasa. Ka dena wannan kunbuya kunbuya din ka fito ka sanar mun komai musan yadda zaai maganar nan ta bata" " Ke menene damuwar ki aciki ne? "Yanzu ka amince kenan. Yusuf meyasa zaka kashe ta?" "Kisa fa kaman na chaka mata abu ko na tura an kasheta . No ko daya. Kawai dai na bige ta da mota hoping ta samu karaya da sauran su".. "To ta mutu Yusuf ta rasu. Case din hit and run ne yanzu. . " "Ki kwantar da hankalin ki ba abunda zai faru" "Yaya zan kwantar da hankali na Yusuf! Ya Yaya! Sai da nache maka dan Allah karkayi mata komai matar nan ba zata fada ba na sani. Ka amince kace ba abunda zakayi iska kawai zaka sha haba yusuf" "To nj dai ban kasheta ba na dai bige ta da mota tabbas, wait yanzu me kike so ayi tsoran me kike ne?" "Yusuf itace fa as head of her family. Itake shiltering yaran ta da sauran su" "Kakki damu. Everything is under control. Zan saka a aika musu da kayan abinci. " "Dan Allah kayi kokari kaji? Ko Kuma zanje da Kai na store din na karba komai" 'karki damu" "Zanje na Kai kudin aikinta na".. "okay ba damuwa" Mikewa tayi ta gyara zaman gilashin fuskar ta ta zura takalman ta ta bar kamfanin.... Gidah suka koma tanata sauri ta sauya kayanta cikin wasu kayan da suka sha duwatsu da ado masu matukar kyau da tsada . Ta sake shiga mota suka dau hanya, "Muje kamfanin Alhaji na kayan abinci, daga nan zamuje gidan Hindu mai aikin nan nawa da kake Kai wa da dakkowa, Allah ya mata rasuwa" "Hindu ta rasu? Kai Kai Kai duniya, mace mai kamala da kirki. Allah ya gafarta mata." "Aamin" Suka dauki hanyar babban katafaren kayan masarufi na Alhaji sambaso. Wato, *SAMBASO PRODUCTIONS* _INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_ _KU MARMATSO KUSA...🔊_ _ZAFAFA BIYAR 2024_ _ZAFAFA BIYAR!!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_ _YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_ _GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_ _________ _1_ *_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_ _2_ *_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_ _3_ *_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_ _4_ *_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ [3/2, 8:04 PM] Hafsaat🧕: _K'K'J_ _(M/W/S)_ _✍️:MX_ _29_ ::::::::: ... Motar na fakawa... Ma'aikatan wajen suka tattaso... Dr bintu ta zuge glass tana daga musu hannu. Suka shiga gayshe da ita daya bayan daya kasancewar sun san mai dakin mai gidan su..Wani lokacin yakan zo da motar da tazo da ita ma. "Akwai Kaya ko?" "Akwai hajia" "Mota fa?" "Itama akwai. Aciki za'a kai miki kayayyakin?" "Eh... " "Tohm hajia me da me akeso?" Cewar wani daga cikin su don shine in charge na maaikatan wajen. "Inason buhun shinkafa ta tuwo data dafawa, buhu daya daya kowanne.. Inason taliya cartons uku. Macaroni cartons uku. Indomie cartons uku. Sai garin tuwo buhu biyu. Akwai mai ko sun kare?" "Akwai ranki ya dade." "Okay inason 25 litres na man gyada da manja kowanne jarka daya daya. " "Tohm hajia bari a saka miki a motar. " "Godia nake" Ta fada tana zuge glass din zuwa sama. Maaikatan suka sassaka mata kayyakin a daya daga cikin motocin da ake delivery na kayan abincin idan customers sun saya suna son dispatch. "Hajia gidah zaa kai?" "Aa yabiyo motar mu. Naduka zone zamu shiga" "Tohm shikenan bari ya biyo ku a baya" "Nagode" "Munda fa godia hajia. Allah ya saka da alkhairi ya biya bukatu" "Aaameen" Baki daya a atsora ce take. Gabanta ya shigaa bugawa fat fat alokacin da direban ya gangara da motar zuwa kofar gidan marigayiya Hindu. "Hajia min karaso" "Ta jiyo muryar sa ta daki dodon kunnenta" "Okay..." Fita tayi ahankali tana gyara zaman mayafin jikin ta Yayinda motar data dakko kayan abincin itama tayi parking a bayan tasu, "Hajia ya za'ai da su?" Direban motar kayan ya tambaya "Ku shiga dasu nan gidan" "Okay tohm" Ya fita daga cikin motar shi da direban motar tata suka fara kama kama da buhunhuna na shinkafar da kayan abincin cikin gidan na Bappah junaidu. Alokacin duk suna parlor a zaune. Bappah Auwalu, Bappah junaidu, Nusaiba, Ashir, Ashfeef, Nawraah, Layla, Ahmad da kuma Amnah. Suka jiyo bakuwar sallamar su direbobin, "Waalykm Salam. Suwaye?" "Aiko mu akai aina zamu saka kayan nan?" Cewar daya daga cikin direban Ashfeef daya amsa musu ya juya yana kallon mahaifin sa yace da su, "Anya ba batan kai kukai ba.? Ba nan gidan bane" "Ba manne gidan marigayiya Hindu ba?" "Eh nanne. " Ashfeef ya amsa su "Kai suwaye ne?" "Bappah wasu ne suka kawo kayan abinci nace ba gidan nan bane shine suka ce bananne gidan marigayiya ummy ba?" Bappah Auwalu ya mike Kafin ya taka ya tafi tuni nusaiba ta wuce da sauri ta isa wajen su tana kikkifta idanu sai hucin iskar tafiyar ta yaji ta kunnen sa😂 "Nan ne ku shigo da su" ta amsa su tana bin kayan da kallo Suka sauke suka sake komawa. "Nusaiba menene hakan wai! Ya haka kawai bamu san mutane ba zaki ce musu eh nanne su ajiye ke meyasa ne har yanzu ... Ya kasa karasawa kawai ya girgiza kai hadi da sakin tsaki. .." "Kayan abincin zasu mayar da su muna nema?" Tsabar bakin cikin kalamanta wai"suna nema" tamkar kayan abincin su aka kawowa ba gidan na Bappah junaidu ba. Bappah Auwalu baki daya halayen Nusaiba sun dai na bashi mamaki.. Suka shigaa kawo kayayyakin suna ajiyewa har suka kammala suka koma suna gayawa Dr bintu sun Kai musu kayan . Nusaiba sai leken su take tana sake daga kafafunta don hango su sosai. Tun daga tafukan kafafun ta ta shiga kallon ta cikin kayan ta masu matukar tsada ya zuwa fuskar ta data sanya facemask . Takawa tafara yi har ya zuwa kofar gidan da zaka shiga ta rangada sallama, "Shigo ciki yar uwata"😂 cewar nusaiba tana dashare baki taga kalar masu kudi da suke burgeta. Dr bintu ta dan kalleta tana kakaro murmushi itama ta facemask ta zare takalman ta ta shiga parlorn Sallama ta sakeyi. Suka amsa baki daya aka nuna mata wajen zama ta zauna, "Uwar dakinta ce ko? Hajian Naduka crescent ?" Nusaiba ta tanbayeta tana kallon fatar dr bintu dake shekin masu kudi. "Eh yar uwar ta ce ni, Amma ba ita bace. Hajia qibdiyya kike nufi ita suna kasar waje basu dawo ba. Ta haihu dan ba rai sai Kuma ta hadu da rashin lafiya. Shine suka sake daga dawowar tasu zuwa wani lokacin a gaba " "Okay ko kece wadda takewa abinci ta biyu bayan tafiyar h.. "Nusaiba haba. Ki dakata mana tayi magana da kanta" bappah Auwalu ya tsawatar mata. Dr bintu da dama nusaiba ta isheta da magana tayi hamdala kasan zuciyar ta. Ta gayshe da su suka amsa kananan Kuma suka gayshe da ita ta amsa musu, "Ya Karin hakurin mu? Ashe Hindu lokaci yayi? Toh Allah ya jikanta da rahama ya gafarta mata." "Aamin... Aamin" suka amsa baki daya. "Wallahi bamu sani ba. Mai gidah nama Yana muku taaziya yace zai zo inshaa Allah abubuwa ne suka rike shi. Yace ga kayan abinci nan ba yawa dan Allah adafawa iyali su ci. " "Allah sarki angode kwarai" "A ranar da muka zo ni da ummyn mu.... Lokacin data ce na taho gidah ta koma ciki bansan meya faru ba. A tsorace take dai. Kikace lalle ta dama muku kunu Kafin ta taho.. A ranar aka bige ummy a mota ta rasu a hanyar ta dawowa daga gidan ku" Kofofin kunnuwan Dr bintu suka jiyo mata kalaman muryar Nawraah data karashe zancen tana sake nanatawa da, "Ba kece Dr bintu ba inda ummy ke miiki aikin abinci da rana. A ranar kikace taje da yammaci?" Nusaiba ta juya ta dubeta tana kallonta da Karin bayani. Bappah Auwalu ya dan zunguri kafar bappah Junaid dake kusa da Nawraah, daya kishingida kansa Yana kallon sama. Baki daya tunda ummyn ta rasu ya dawo tamkar ba shi ba ya zama shiru shiru baya magana gaba daya sai ta kama. . "Nawraah... Menene haka?" Bappah junaid yace da ita yana kallon ta Dr. Bintu gabanta ya tsananta bugawa tayi hanzarin seseta kanta. Bappah Auwalu yace, "Nawrah ya Isa. Ai da yardar Allah Hindu yar aljanna ce. Lokacinta ne yayi. Kuma wannan koma wanene kowacece da sukayi aika aiken nan sai dai muce ubangiji Allah ya saka mana ya biya mana hakkin mu a madakata. Allah Kuma ya bayyana mana su tin a duniya. Hajiya kiyi hakuri kinsan yarinta. Nawraah, Tunda akace a titin nan haka ta rasu kinsan tare ranar suka fita. To abun ya tabata sosai ne wallahi" bappah Auwalu ya ce da dr bintu cikin tabbatarwa Tayi murmushi tana kallon Nawraah tace, "Nawraah Allah ya gafartawa mahaifiyar ku kinji? Wallahi banida masaaniyar mutuwar ta ma sai da yar uwata kawata hajia qibdiyya uwar dakinta ta farko ta kirani take gayamun dazu. Wallahi sai na kasa zaune na wuce ofishin mai gidan nake sanar masa. Abubuwa sun masa yawa shi Kuma. Shine fa yace na kawo kayan abincin Kafin yazo. Kuma wallahi nima inata Kiran wayar ta a kashe don nayi mamaki ma da hajia qibdiyya tacemun ta samu wayar Hindu nan take sanar mun ai Hindu ta rasu Kuma accident nema muka kiyasata ranar da tazo gidah na ne ai . Wallahi na shiga dimuwa fiyeda yadda baki zai furta. Don kudin aikinta na wannan watan ma wallahi bata karba ba. Yana waje na, Gasu ma nace bari na kawo . Allah ya jikan Hindu ya gafarta mata" "Ah kin kyauta. Allah ya saka muku da mafificin alkhairin sa .. Amin" "Allahumma Aameen. Ni zan tafi sai mai gidan na wa yazo inshaa Allahu, Nima zan sake waiwayowa. Allah ya baku hakurin rashin ta" "Ko ruwa baa kawo miki ba" nusaiba ta fada tana mikewa tsaye itama Dr bintu tace da ita, "A koshe nake karki damu. Nagode. To sai anjiman ku" "Sai anjima, Allah yabada ladan " Ficewa tayi da sauri nusaiba tabi bayanta tana cewa da ita, "Angode sosai... Sai da safe." Dr bintu ta daga mata hannu kawai alamar bye bye, ta shiga bayan mota da sauri driver yaja suka tafi. Ta saka hannunta akan kirjinta saboda yadda yake mata duka. Tiryan tiryan maganganun Nawraah suka shiga mata yawo a kwakwalwa, Wannan wace iriyar yarinyar ce ne? Bata mantuwa? To me take tunani kenan! ? Lalle wannan yarinyar sai anyi dagaske akanta kar ta ballo musu ruwa Duk kuwa da yadda ac din motar ke turarawa hakan bai hana tashin hankalin da Dr bintu ke ciki ba jikewa jagab da ruwan gumi tamkar tayi wanka da kayanta a jike.. Har suka koma gidah bata daina nazari akan maganar da Nawraah tayi ba... Tirk'ashi! _INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_ _KU MARMATSO KUSA...🔊_ _ZAFAFA BIYAR 2024_ _ZAFAFA BIYAR!!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_ _YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_ _GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_ _________ _1_ *_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_ _2_ *_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_ _3_ *_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_ _4_ *_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ _K'K'J_ _(M/W/S)_ _✍️:MX_ _30_ :::::::::    Tana zaune akan sallaya tun sallar asubah data tashi bata koma bacci ba, Bacci ya kauracewa idanun ta .. Kamar ko da yaushe tana karanta wasu surori na daga cikin alqur'ani ta ciki harda su suratul Kauthar da Mulk ta roki Allah ladan ya kai wa mahaifiyar su ummy da sauran musulmai baki daya da suka rigamu da gidan gaskia .. Mikewa tayi bayan ta karasa sauraron addu'oin ta tayi azkhar. Bandaki ta shiga ta dauraye shi kasancewar akwai wuta. Kuma da ruwa ko'ina a cike... Ta dubi autar su Amnah dake baccin ta ahankali tana sauke numfashi. Ta rankwafa tana duban fuskar ta sosai. Daman kanwar tasu duk cikin su tafi su debo kama da mahaifiyar ta su marigayiya Hindu . Kallon ta take tana hasaso fuskar ummyn ta su. Da tana raye da tuni yanzu tana kasa ta fara hada karin kumallo da kintsa gidah da sauran su .. Hawaye sirara suka shiga zirara daga idanun ta ta saka kasan dankwalin ta ta goge.. Mikewa tayi ta sauka kasa don sharewa, ko'ina tas an share har da dorin kamshin turaren wuta na tsinke dake ci daga gefen wata huda.. Motsin karar kwanuka data ji ne daga kitchen yasa ta nufi kitchen din tana kiran sunayen, "Hamma ne ko Hamma Ashfeef?" Ta karasa shiga cikin kitchen din bakinta dauke da sallama. Ashir ne a tsaye, Yana gyara zaman kwanuka acikin kwando. "Hamma" Ta kira sunan sa Ya juya jin kamar an kira sunan sa. Yana hangota yayi murmushi yana goge hannuwan sa ajikin tsumma, "Nawraah" "Naam Hamma... Ai nayi sallama na kira sunan ka baka ji ba" "Banji ba Nawraah. An tashi lafiya?" "Alhamdulillah Hamma. Ina kwana?" "Alhamdulillah Nawraah..." "Hamma ai nace ka barshi zan dinga yi Allah. Naga har shara kayi ka gyara ko'ina" Murmushi Ashir yayi, Yana shanya tsumma akan wani karfe yace "Kaki damu babu komai ai.... Duk yiwa kai ne, Na gaya miki ai nace ki dinga wanke bandakin sama kawai kina gyara dakin ku dana abbiey. Kasa zan gyara inshaa Allah. Namu bandakin Kuma Ashfeef zai dinga wanke shi. Kije ki koma ki kwanta oh ba da makaranta ba yau kuna da exams?" "Hamma Allah ya saka maka da mafificin alkhairin sa. Ai bana jin bacci tun Kiran sallar fari. Zan dai yi wanka sai nazo naga abunda zaa dafa" "Kakki damu ai na dafa shayi tun jiya Kuma an sayo biredi." Hawaye ne ya cika idanun ta taf. Ashir ya dubeta yana girgiza mata kai, "Mayar da wannan kukan na meye?" "Hamma dukkanin abubuwa da kake ko ummy na nan sai haka. Gaba daya baka hutawa" "Idan banyi muku ba wanene zai muku Nawraah? Bakisan cike nake da farin ciki ba idan Ina taya wasu abubuwan na aiyukan gidah? Banda wani babban burin daya wuce naga farin ciki shimfide akan fuskokin ku. Nawraah ummy da kanta ta bani amanar ku tun da ranta... Don haka duk abunda kikaga nayi muku wallahi ban fadi ba. Fatan Allah ya buda mana duka ya yalwata mana kofofin arzuka Amin. Allah Kuma ya jikan mahaifiyar mu da dukkanin musulmai baki daya Aameen" "Allahumma Aameen Hamma.. Tohm shikenan. Allah ubangiji ya dafa maka ya shi maka albarka ya baka mata tagari Amin" Murmushi yayi jin ta ambaci maganar auren sa. Ta kalle shi tana murmushin itama tace, "Hamma ko budurwa ma baka da ita fa ko meyasa oho" "Nawraah ai yanzu ba lokacin kule kule yammata bane, Ta gidah ake yanzu bana waje ba. Idan komai yayi normal agidah sai mu duba mugani." "Amma Hamma lokaci na kurewa ai" "Aa fa... Komai da nasa lokacin ballantana ni bana son kule kulen yammatan nan haka. Fatana kawai Wanda zan nema ma ta kasance ita zan aura kingane? Banason yaudara. " "Hakane kam Hamma Allah ya dafa maka adukkanin abunda ka cinma buri." "Allahumma Aaamin Nawraah" "Ga ruwan zafi nan a bokiti ki juye kiyi wanka zan Kara wannan da zai tafasa akai Wanda ya riga tashi bayan ke sai yayi wankan" "Tohm Hamma yanzu kuwa. Bari naje nayi" Ta dakko bokiti ta debi ruwan ta haye bandakin su na sama tayi wanka. Tanata sauri tana shiryawa kasancewar a yau ne zasu zana jarabawar su ta karshe ta gama sakandire. Tana cikin shiryawa Amnah ta tashi lokacin garin har yayi haske. Tayi mata wanka ta saka mata kaya suka sauka kasan a tare Abincin karin kumallo suka ci. Suna cikin ci Ashfeef ya tashi shima yayi wanka ya shirya zuwa kayan aiki zasuyi fenti ra fenti don sun samu aiki na fente wani site da ake ginawa... Daga baya ba jimawa bappah junaid ya sakko sika gayshe da shi baki daya. Dakyar yaci abinci kadan ya tashi ya koma sama yayo wanka bayan Ashfeef ya Kai masa ruwan zafi sama. Nawraah taje tayiwa bappan su sallama sai ta dawo, zata tafi zana jarabawar ta ta karshe ta kammala sakandire, Yayi musu addu'ar temako da samun nasarar jarabawar.. ya dakko kudin break ya bata, tayi masa addua ta futa rike da hannun nawrah kasancewar zata kaita gidan bappah Auwalu Kafin su dawo tunda Hamma ma dashi zaai aikin fentin... Ta kai Nawraah gidan bappah Auwalu wajen Nusaiba. Daga nan ta jira Layla ta karasa shiryawa suka nufi makaranta don zana jarabawar.. Da misalin karfe hudu na yamma sika kammala zana jarabawar karshe ta sakandire... Sai fatan samun nasara da dinbin fatan alkhairi ga sabbabin kofofin rayuwa da zasu bude..... _INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_ _KU MARMATSO KUSA...🔊_ _ZAFAFA BIYAR 2024_ _ZAFAFA BIYAR!!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_ _YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_ _GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_ _________ _1_ *_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_ _2_ *_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_ _3_ *_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_ _4_ *_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ [3/5, 7:07 PM] Hafsaat🧕: _K'K'J_ _(M/W/S)_ _✍️:MX_ _33_ ::::::::: Amnah yau lafiya gobe babu. Sunata zuryar asibiti duk kudaden hannuwan su suka kare. An mata tasa tasai an gani tanada ciwon tonsils shi ke sakata amai da yunkurin aman. Sannan typhoid ta mata illa.. Bappah junaidu bayasan bin mutane ko yan uwan sa yana cewa su temaka masa. Don haka ya saka gidan su jingina bada masaniyar kowa ba ya karbu kudin aka yiwa Amnah aiki da shi aka kwantar da su a asibiti sukayi jinya sosai. Sai bayan da aka sallamo su ne bappah junaidu ya shirya ya tafi ofishin da Alhaji sambaso ya bashi katin. Ya nufi unguwar har kamfanin akace ya shiga. Ya nufi ofishin zai shiga ya ja ya tsaya jin da akwai mutane aciki suna magana. Har zai juya yaji an ambaci sunan sa da na matar sa. Sai kuma ya jiyo suna maganar tarin dukiyar dr Abubakar dollars dayake so ta zama mallakin sa har ya saka hannu. Can kuma yake gayawa mutumin, Tsautsayin daya same shi na niyyar illata Malama Hindu sai kuma ya kasheta har lahira. Kafafun Bappah junaid suka gaza daukar sa. Ya sanya hannu a baki ya toshe saboda wani abu daya taho masa. Kafafun sa suka gaza daukar sa. Ya nemi jikin kofar ya jingina saboda wani yanayi na tashin hankali daya samu kansa aciki. Alhaji sambaso suka gama magana da mutumin na ciki sukayi sallama. Mutumin ya tashi ya nufi kofa zai tafi. Laptop din Alhaji sambaso ta fara karan shigowar waya ta app ya dauka yana murmushi kasancewar video call ne… Alhaji ateeks na daga masa hannu yana bude kofar sai ga Bappah junaidu fuskar sa shabe shabe da hawaye. Alhaji ateeks ya dube shi ya wuce dan baisan waye ba ma. Alhaji sambaso ya ja hannun sa ciki yana rufe ofishin. Ga video call din nata tafiya. Na ciki yanata 'hello hello' yana duban sa. “Meyasa ka kashe mana Hindu? Me ta maka?” Alhaji sambaso ya bude baki yana shafo keyar sa yana hura iskar bakin sa mai zafi yace... "Bangane me kake nufi akai ba. Hankalin ka daya kuwa kasan me kake cewa?" "Na sani mana, da hankali na duk na ji dukkanin abubuwan da kuke fada, Kai da abokin ka. Kun hada kai kun kwato duniyar Dr abubakhr dollars ta karfin dole. Kun kashe Hindu meta muku? Shin akan wani dalili kuka kashe mana hindu? Ashe kai ka bigeta a mota ka kasheta Alhaji? Yanzu duk wadannan kayan abinci da kake aika mana da sauran su dama duk toshiyar baki ne? To Allah ya tona asiirin ku wallahi Allah kuwa daga yau zaka kwashe kashin ka a hannu" Ya saka hannu akan mabudin kofa da niyyar murzawa ya fita Alhaji Sambaso yayi hanzarin riko hannun nasa yana duban sa sosai, "Ka tsaya muyi magana ta hankali ba abunda kake tunani bane" "Babu abunda zanji. Kuka samu kanku gaban hukuma zakuyi bayani, yanzu a yau zan bankada dukkanin kofofin sharrin ku. Mugaye kawai. Allah ya yi wadai da halayen ka" Ya sake kai hannu zai fita Alhaji Sambaso ya tare hanyar ya riko shi yana duban cikin idanun sa yace, "Kasan wanane ni kuwa! ? Na ga alamar ba hankalin ka kake ba, wannan zantukan, Idan kudi kuke bukata zan baka ishasshe yanzu. Dan naga alamar rashin su ya fara taba maka kwakwalwa kake ta surutun magana da sambatu acikn ta" "Wai ka dauka kudi na sayan mutane? Ka dauka dukiya itace kwanciyar hankali? Ka dauka dukiya itace maganin damuwa? To ka bude kunne ka kaji. Daga yau kwanan ka a doren duniya cikin gidan ka babu kai babu kwanciyar hankali. Inshaa Allahkashin ka ya bushe. Police station zan tafi wallahi wallahi " ya fada yana duban sa cikin tsantsar tsana. Alhaji Sambaso yayi hanzarin riko kafadunsa. Bappah junaidu ya fuzge. Alhaji ya sake riko shi. Suka shiga kici kici har zuwa wajen wata baranda. Bappah junaidu ya jinga a jikin bango yana magana cikin fushi Jiyuwar nan da Bappah Junaid yayi Alhaji Sambaso ya hada shi da karfen baranda yana dukan cikin sa. Ya daga hannu cikin tsantsar tashin hankali da tsana ya shararawa masa mari Alhaji Sambaso ya rike kuncinsa, Yana duban bappah Junaid daya sake daga hannu zai kauda masa wani , Alhaji Sambaso ya jinginar da shi a jikin baranda, bappah junaid ma ya tattake ya buga shi da kofar. Alhaji Sambaso cikin hazalar fushi ya cakumi wuyan bappah junaid ya hankada shi da karfunan barandar. "Kashe ni zakai? Nima ka mar yadda ka kashe matata?" Alhaji Sambaso ya saka hannu, Yana rufe bakin bappah Junaid dayaki ya sake cakumar sa. Alhaji Sambaso ma ya riko tasa yana sake cakomar rigar sa yace, "Shashasha" "Kai ne shashasha, Mugu, Azzalumi...." Garin riko shi zai naushe shi ya hankada shi. Bappah junaidu ya fada kasa ji kake 'Timmmmm Kamar kara ya fada, Take kansa ya fashe bai shura ba ya mutu awajen alokacin.... _INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_ _KU MARMATSO KUSA...🔊_ _ZAFAFA BIYAR 2024_ _ZAFAFA BIYAR!!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_ _YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_ _GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_ _________ _1_ *_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_ _2_ *_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_ _3_ *_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_ _4_ *_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ [3/5, 7:07 PM] Hafsaat🧕: _K'K'J_ _(M/W/S)_ _✍️:MX_ _34_ ::::::::: Rufe bakinsa yayi da sauri, yana zare idanuwa jin muryoyi suna kururuwa daga waje lalle da alama mutumin ya mutu.... Tun sanda mutumin ya shigo dama yayi hanzarin danna recording kiran na video call da sukeyi.... Alhaji Sambaso ya saka hannunsa ya shafo kasan keyar sa, Yana rufe bakinsa da tafin hannun sa.... "Naga kaman labarai kake kalla ko? Bari na kashe na sake kira yanzu nima zanyi abune?" Ya jiyo murya daga cikin laptop. Dama bai katse video call din ba? Ai baki daya ya manta. Ya dafa teburin yana kallon sa ta cikin system din yace "Dama baka kashe ba? Me kake nufi da labarai? Ka saurari maganganun da nake fada ne?" Alhaji Sambaso ya tambaye shi cikin tsananin tashin hankali Ya girgiza kansa yana bashi amsa da "No da naga Jana kallon labarai ne kome. Magana sama sama sai na tashi na shiga bandaki fitowata kenan kuma naga kaman da kanta ma muna waya" "Ka tabbatar abunda ka sani kenan?" "Eh mana... "Ya kakaro daria ya sake cewa, "Futsari na tashi nayo ma sai na tsaya na karba parcel dina da aka kawo yanzu" "Oh okay. To shikenan zamuyi magana, yanzu zamu shiga meeting ne " ya katse kiran yana rufe laptop din baki daya.. Zagayawa yayi ta kofar baya emergency exit dinsa wanda ba kowa bane ya sani a kamfanin ya fita ta ciki ya koma kasa... Nan da nan maaikatan wajen suka fara taruwa akan gawar bappah junaidu.... Da sauri wasu maaikatan suka nufi ofishin nasa suka bude baya ciki. Aka dudduba bayan ko'ina Nan suka shiga fara kiraye kirayen wayar sa. ... Ya fito daga cikin wani guri a kasan kanfanin da suke kira da lodge . Daki ne da parlor da bandaki inda manyan maaikatan suke shiga su huta. Nan ya futo daga ciki yana mitssika idanu, "Ah ranka ya dade ashe baka cikin ofishin na ka?" Cewar wani leburan kamfanin daya nufe shi yan yana tambayar sa. Duk sauran maaikatan suka yayyabe su. Alhaji Sambaso ya saka hannu yana rufe bakinsa alaman hamma ce tataho, "Alhaji ayi hakuri amaana afuwa, Ashe hutawa ma kake" "Wallahi kuwa bansamu bacci bane gaba daya nache bari na dan huta. Bayan tafiyar Alhaji ateeks" "Ranka ya dade wani mummunan labarin ne ya faru" "SubhanAllah Allah yasa muji alkhairi meya faru kuma?" "Wani ne ya fadi daga barandar ofishin ka... Kafin su karasa maganar da suke. Alhaji Sambaso ya katse su cikin buda baki yace, "Ba dai junaidu ba da yazo duba gyaran da zaa mun a barandar" "Allahu Akbar kabiran. To shine... Bawan Allahn nan yazo dazo yake tambayar mu wajen ka muka nuna masa ofishin ka . Dama bakuwar fuska ne kam. Amman daya nuna katin ka dinnan nasan babban bako ne shysa ma muka kyale shi ya shiga. Ashe ashe ajalinsa ne ke kiran sa. Kuma akwai tsani fa a bayan kofar bai duba ba kenan ya taka karfen dama karfen ai girgidi yake" Alhaji Sambaso farin ciki ya taho masa ya danne don kar su gane. Ba kadan ba yaji dadi da daya ji daya a cikin maaikatan yace dama karfunan barandar suna girgidi.. Wucewa yayi gaba tamkar Wanda yake cikin tsananin tashin hankali .mutanen suka rufu akansa sam ba dadin ganin gawar ma ta bappah junaid. Aka dakko kyalle aka rufe shi. Alhaji Sambaso ya sanya aka kirawo ambulance nan da tazo aka fara wucewa aasibiti aka gyara shi sannan aka kira gidah da number Ashir dake cikin wayar ta bappah junaidu. Nan ake sanar dashi zaa kawo gawar mahaifin su ya fado daga benen barandar me tsananin tsayi ya rasa rayuwar sa yanzu ma gasunan akan hanyar motar kwana kwana sun biya ta asibuti an gwada gwaje likitoci sun tabbatar ya rasa ransa.. Ashir baki daya dama suna zazzaune a parlor ne. Ya na tsaye wayar ta fadi daga kunnen sa yana salati "Menene Ashir? Menene ?" "Hamma menene?" "Ashir Ashir menene?" Bappah Auwalu ya shiga girgiza kafadun Ashir. Ashir yana zubar da hawaye duk tsananin dauriyar sa jikin sa na rawa yace, "Abbiey ne..." "Abbieey din. Meya same shi meya samu junaidun?" "Bappah.... Abbiey ya ra su... Abbiey ya rasu bappah " "Innalillahi wa Inna ilaihi raji'un....... Bappah junaidu ya ambatada da karfi gwiwoyin sa sun gaza daukar sa ya zube awajen ya fara kuka sosai tamkar karamun yaro ... _INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_ _KU MARMATSO KUSA...🔊_ _ZAFAFA BIYAR 2024_ _ZAFAFA BIYAR!!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_ _YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_ _GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_ _________ _1_ *_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_ _2_ *_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_ _3_ *_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_ _4_ *_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ [3/5, 7:07 PM] Hafsaat🧕: _K'K'J_ _(M/W/S)_ _✍️:MX_ _35_ ::::::::: Nawraah na sama ta sakko rike da bokiti a hannun ta da kaya aciki. Tana murmushi tana taka kafafun benen tana sakkowa tace, "Hamma! Yau ni ma na rigaka Ina son na samu lada.... Na wanke kayan abbiey daya cire jiya. Yana dawowa zan gaya masa" Tana sakkowa ta tsaya tana duban su. Yadda sukai cirko cirko masu kuka nayi masu salati nayi. "Menene?" Ta tambaye su jikinta a sanyaye .. Duk sukayi shiru suna kuka sosai. Ta karasa kusada da Layla ta dafa kafadarta, "Meya faru ? Eh? Menene? Wane ne ba lafiya ko wani abun ne na daban?" Layla ta daga fuskarta sharkaf da hawaye ta saukar ta akan Nawraah tace, "Bappah ne?" "Bappah sani Bappah salisu ko bappah Auwalu? Meya same su bappahn?" Layla ta sake girgiza mata kai tache, "Bappah junaidu?" "Bashida lafiya? Wani abun ne ko? Daman yadda kwana biyu abbiey yake yi nasan bashida lafiya. Me akace ya same shi?" "Nawraah. Abbieyn ku Allah ya masa rasuwa" "Innalillahi wa Inna ilaihi raji'un..." Ta fada da karfi ta zube awajen a sume. Sukai kanta da sauri. Bappah Auwalu ya saka aka kawo ruwa aka yayyafa mata. Ta farfado da kyar tana wani irin sauke numfashi mai nauyi tamkar zata shide.. "Innalillahi wa Inna ilaihi raji'un... Bappah Auwalu ku tasheni daga baccin da nake.. wai abbiey ya rasu? Abbiey fa kukace? Abbiey ya rasu fa kukace? Innalillahi wa Inna ilaihi raji'un. Wannan wane irin wasa ne? Layla meyasa zaki ce abbiey ya rasu akan wane dalilin abbiey zai rasu eh?" Ya karasa fada tana sakin dariya harda tafa hannuwa tamkar sabuwar marar hankali, can kuma ta saki kara mai razana ta fashe da wani irin kuka tana birgima. "Wayyo Allah na. Abbiey. Wayyo Allah na! Wayyo Allah na Ummy. Wai abbiey shima shikenan ya rasu ya bar mu? Abbiey ya tafi shima? Ummy ma tarasu fa? Innalillahi wa Inna ilaihi raji'un. Waya kashe mana abbiey? Kashe abbiey sukai. " "Kiyi hakuri Nawraah babu Wanda ya kashe junaidu kinji. Lokacin sa ne yayi. Kinaji daga wajen aiki ne wai a karfen baranfa ya taka shine ya fado rai yayi halinsa sun akai shi asibiti ma ance ya cika. Yanzu sun taho kawo shi gidah. " Ya karasa fada mata shima yana sake barkewa da wani kukan Baki daya sai suka bude shafukan kuka. Nusaiba daga can gefe tayi shiru itama kanta a kasa. Hakika mutuwar kanin mijin nata junaidu ta razananta kwarai matuka. Agubi agubi anyi musu mutuwa biyu kenan ajere ba daukar lokaci. "Shikenan Hamma bamuda iyaye? Abbiey da ummy sun rasu? Shikenan bamuda sauran gata ko Hamma? " Ashfeef ya fada yana girgiza kai. Ashir ya katse hancinsa Yana goge hawayen fuskar sa yace, "Ga mota can inaga sune..." Dunguma sukai suka fita wajen ...ambulance ce ta kawo shi har kofar gidan suka shigar dashi gidan bisa jagorancin maaikatan.. Daya daga cikin leburan dake kamfanin na Alhaji Sambaso yace, "Ina wunin ku? Kuyi hakuri fa. Allah ubangiji ya gafarta masa.ya kyautata namu zuwan Allah Kuma ya baku hakurin rashinsa...wallahi Yana gyaran wani bangare ne dake babbar barandar ofishin mai gidan mu. Ashe bai hau tsaani ba sai yahau karafunan barandar a haka ya taka. Su Kuma dama rawa sukeyi shine ya fado Allah yayi masa rasuwa. Domin kwanyar kansa ma afashe take... Inshaa Allahu aljanna makoma ce agareta shi. Yanzu zamu jira a gama wanke shi sai mu sallah shi mu Kai shi gidan gaskia baki daya daku iyalan sa..." Bappah Auwalu ya fara kiraye kirayen dangi na kusa dana nesa Yana sanar musu rasuwar junaidu. Auta daga iyalan yafendo. Dangin Hamidniyya Lebanon.. Hakika kowannen su mutuwar ta dake shi . Alkalani yayi kadan wajen bayyana adadin alhini da dangin suka shiga baki dayan su. Musanman iyalan sa na cikin sa sun shiga cikin dimuwa marar misaltuwa. Haka aka yi masa wanka. Anayi jini na fita daga jikinsa har da guda guda. Haka aka nannade shi duk da hakan jinin yaki tsayawa. Aka Kira iyalan sa daya bayan daya suka yi masa sallama. Kowanne da koke koke aka futar da shi. Aka dauke gawar junaidu aka sanya a makara aka sallace shi aka kai shi gidan sa na gaskiyar wato makabarta. Allahu Akbar wata bishiya ce ta raba tsakanin kabarin marigayi Bappah junaidu da mai dakin sa marigayiya malama Hindu. Allah ya jikan su ya gafarta musu ya musu rahama.. Hakika junaidu ya samu sheda daga bakunan iyalan sa na cikin sa, dangin sa su bappah Auwalu bappah sani da matayen su baki daya dai dangin hamidniyya Lebanon. Sannan mutanen wajen aikin sa dama yan unguwar baki daya sun yabe shi. Ya Kuma samu mutane sosai da suka sallace shi suka kai shi makabarta. A farfajiyar gidan aka shinfida tabarma aka fara makoki dukkuwa da ahalin Hamidniyya Lebanon basa zaman makoki, Amma mutane na zuwa yi musu ta'azyiya wasu tundaga birnin bunza na kusa dana nesa... Suma yan yankin bunza sosai sun yi alhini da jimamin rashin junaidu. Domin yanada halaye na kwarai bai taba fada da wani ba .. kowa nasa ne ga temako . _Yanzu zamu sake tsunduma cikin labarin:_ _KWANKWASON JIMINA MAI WUYAR SHAFAWA... Ayi hakuri da yadda rubutun yake zuwa... Labarin na gaba In shaa'Allah_ _INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_ _KU MARMATSO KUSA...🔊_ _ZAFAFA BIYAR 2024_ _ZAFAFA BIYAR!!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_ _YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_ _GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_ _________ _1_ *_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_ _2_ *_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_ _3_ *_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_ _4_ *_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ [3/6, 1:52 PM] Hafsaat🧕: _K'K'J_ _(M/W/S)_ _✍️:MX_ _36_ ::::::::: Anyi shela anyi cikiyar wadanda ke bin junaidu kudi ko wani na ajiya suyi magana a basu. Yawanci ma anfi samun wadanda shi yake binsu bashin basu biya shi ba.. duk wadanda suke binshi bashin da yawan su wasu sun yay'yaafe. Wasu kuma sun karbi wani kaso na cikin kudin sunce sun bar sauran.. Sai wani mutumi daya tashi ya taba kafadar na gefen sa suka mike. Suka ce hakika ana bin Junaidu zunzurutun kudade masu matukar yawa. Hakan ta faru ne kuma alokacin da daya daga cikin yaran sa babu lafiya. Aka tambaye su adadin kudin sukace ai wannan magana ba tasu bace. Domin suma shedu ne na mutumin da junaidu ya karbi bashin agaban su. Kamar jingina yayi ya karbi tarin kudi... Aka nemi ganin mutumin don sanin waye shi da yadda zaa biya da sanin ma shin nawa ne adadjn kudin daya karba? akace daya mutumin yayi tafiya sai ya waiwayo gidah nigeria tukunna. Daya daga cikin su ya karkare magana da "Abunda ya saka muka fada ma saboda hali ne irin rayuwa kada abar mamaci da tarin bashi akan sa. Duk kuwa da kadarar sa ya jinginar ya karbu kudin. Amman dai mun ga yakamata fadar shi yafi alkhairi Allah yasa mu dace" "Ko zamu iya sanin kadarar daya bayar ya karbu kudin a hannun sa?" Bappah salisu ya tambayi mutumin Mutumin ya girgiza kai sannan yace, "Wannan batu baki daya sai an kawo takardar da faifan bidiyo da sukai yarjejeniyar ya sanya hannu tukunna shi mamacin. Kafin shima Alhajin ya rattaba nasa hannun" "Toh Allah ya rufa asiri. Allah ya dawo dashi lafiya. Shi Kuma wannan Dan uwan namu Allah ya jikan sa ya gafarta masa Allahumma Aameen" Suka amsa da aameen baki daya. Aka shiga yiwa bappah junaidu addu'oin samun rahamar Allah da nasarar amsa tambayoyin kabari. ::::::::;;;;;; Sannu ahankali haka mutane suka fara darewa, kowanne yanzo daa irin kyawun halayen da yake fada game da manacin. Hakika bappah junaidu ya samu yabo sosai daga bakunan abokanan sa, Yan unguwa, Yan wajen aikin su, makotan su, Yan unguwar baki daya dama dangi na kusa dana nesa. An kakkawo musu kayayyakin abinci na tallafawa marayun. Saboda kallo daya zakai musu su baka matukar tausayi marar misaltuwa. Dubada duk ba wani kawo girma sukai sosai ba har shi Ashir din. Be Kai shekarun da zaa ce zai hade kawunan Yan uwan na sa ba. Amman dake yanada zuciyar tashi ya nemi na kansa don kare daraja da martabar yan uwan nasa. Hakan bai hanashi kutsawa nan da can ba don ganin ya rufa musu asiri...wannan kenan Haka aka nannade makoki. Akabi mamacin da addua. Hadi da dangana da hakuri da iyalan sa zasuyi. Kowa ya watse na kusa dana nesa Idan ka tsame dangi mafi kusantana marigayin ba. Wato su Bappah Auwalu da su Bappah sani... A parlorn Bappah Auwalu suka hallara baki daya iya yan dakin su. Sai nusaiba da tayi kanai kanai taki tashi suna magana tana tsoma baki.. Ba wanu abu ya bari da yaran zasu mori ba illa dubu biyu da dari uku dake aljihun sa Kafin rasuwar sa, sai Kuma wayar torchlight dinsa . Da wasu dari takwas dake drawer dinsa. Toh su aka harhada dai aka gangada dai da sauran abubuwan sa aka raba gado aka baiwa yaran sa. Wasu daga cikin kayan sawar sa bayan yaran sa maza sun dauka suna so. Sai Yan uwansa wasu ma suka dauki wasu. ragowar Kuma aka kyautar sadaka duk Wanda yazo karba sai ache masa yayiwa mamaci addua.. Baki daya a zazzaune suke suna kallon kuna. Suna magana,nusaiba na daga saman kujera tana jin abubuwan da suke fada. Wani ta saka baki baki wani tayi shiru.. Ashir ya taho daga gidan su zuwa gidan bappah Auwalu zai gayshe da bappanin na su kamar ko da yaushe yanata sauri ya karasa kofar gidan. Ya saka hannu zai murza kofar ya jiyo su suna magana haka sama sama tamkar masu rigima ko fada, Bappah Auwalu na cewa.... ... _Assalamu alaikum... HGL CHARITY FOUNDATION. Na neman temako me hamsin me dari ko sama da haka ko da kayan abinci ne zaa dafa a tallafawa abawa mabukata da sukayi azumi a wannan wata Mai abarka..._ _idan kudi zaa bayar ga asusun banki na opay 9044191709. Haka zalika idan kayan abinci zaa kawo zaa zo tarauni dake unguwar Kano sai akira number opay dincan dake sama_ _zaayi abincin azumi, kosai da Kuma kunu. Wani lokacin harda kankara ta ruwan sanyi ma da za rabawa mabukata masu buda baki.._ _kofa a bude take da dik Wanda zai taimaka. Allah yabada saa ya hadamu a ladan duka amin_ [3/6, 2:03 PM] Hafsaat🧕: _K'K'J_ _(M/W/S)_ _✍️:MX_ _37_ _Assalamu alaikum... HGL CHARITY FOUNDATION. Na neman temako me hamsin me dari ko sama da haka ko da kayan abinci ne zaa dafa a tallafawa abawa mabukata da sukayi azumi a wannan wata Mai abarka..._ _idan kudi zaa bayar ga asusun banki na opay 9044191709. Haka zalika idan kayan abinci zaa kawo zaa zo tarauni dake unguwar Kano sai akira number opay dincan dake sama_ _zaayi abincin azumi, kosai da Kuma kunu. Wani lokacin harda kankara ta ruwan sanyi ma da za rabawa mabukata masu buda baki.._ _kofa a bude take da dik Wanda zai taimaka. Allah yabada saa ya hadamu a ladan duka amin_ °°°°°° "Dukkanin mu nan uwar mu daya uban mu daya... Ba bare acikin mu idan kuka tsame Nusaiba..." "Nima ba bare bace Auwalu . Auro ni fa kayi ka cire ni daga cikin dangi na ka dawo da ni naku. Kana da bakin cewar wani ni ce bare?" Nusaiba ta fada tana gatsine. Yakumbo Aminatu ta tabo ta tana girgiza kai tace, "Kash ba da wani abun ya fada ba Nusaiba. Dan Allah tashi ki koma daki. Idan muka gama kyaji duk yadda mukayi. " Mikewa tayi tana zunburar baki hadi da kananun mita ta shige cikin daki. Ko da ta shiga ma d'age labule tayi ta kasa kunnuwanta tana jiyo abunda suke fada... "Bappah sani, bappah Auwalu, Bappah salisu, Yakumbo Aminatu ... Kamar yadda yaran nan ke fada dukkanin su baki daya ciki harda yaran mu. Basuda wasu da suka fi mu ko suka kamo kafar mu. Mune uwar su mune uban su yanzu. Wallahi Allah sai ya tambaye mu idan bamu kula da yaran nan ba ... Bari na sake nanatawa. Acikin mu da muka rage mu hudu dinnan. Kowanne zai iya daukar yaran nan baki daya ya rike su ba wani abun bane. Zumunci ne. Naka shine naka. Ido biyun duk sun tsiyaye musu, sun rasa uwa da uba cikin kankanin lokaci baki daya ba jimawa. Zan sake nanatawa, Salisu, Sani, Ameenatou. Dukkanin ku kunfini karfi Kuma kowannen ku zai iya rike fiye da yawan yaran nan ma akarkashin sa. Allah ya hore muku. Yaran nan suna bukatar danshin iyaye atare da su. Ku temaka yanzu acikin ku wanene zai dauki yaran nan baki daya? Kuna ganin abunda mutanen nan sukazo sukace ma akan junaidu yayi jingina ya karbi kudi. Bayaga haka nace muku junaidu nima ya rantomun kudade nayi gyaran gidah har yacemun kyauta da fari nace masa wallahi bazan karba ba bashi nake so... Kunsan dai halin dan uwan mu da rufawa nasa asiri? Sam bayasan wani na waje yaji barakar mu. Zai iya salwantar da komai nasa don ganin ya sanya mu acikin farin ciki. Dan Allah kada mu bari yaran nan suyi maraicin iyayen su. Kada mu bari yaran nan su Gane Cewar bamuda hadin Kai a tsakanin mu ba zamu iya rufawa dan uwan mu asiri ba. Wanda dukkanin mu nan kowannen mu junaidu yayi masa da aljihun sa, da jikin sa da gumin sa. Bai taba gajiyawa ba..... Shin wa zai karbi rikon yaran nan su dawo hannun sa? Su hudu ne kawai, Ashir, Ashfeef, Nawraah sai Kuma auta Amnah... Wallahi summa tallahi da inada halin da zan rike yaran nan wallahi zan rike su, Amman banda shi. Junaidun dai ke rike damu duka har ni ya rasu. Dan kuwa komai na rayuwa wallahi shi yake mun ya dauke mun komai . Ba abunda zance da shi sai fatan Allah ya masa rahama yasa ya cika da kyau da imani amin " "Aameen " suka amsa baki daya "Sani zaka rike su?" Bappah sani ya grigiza Kai Yana duban agogon hannun sa yace, "Kasan halin da nake ciki yanzu. Wallahi Idan na ce zan rike yaran nan zan takura bazan iya ba wallahi." Bappah Auwalu ya kada Kai ya dubu Bappah salisu yace dashi, "Salisu kaifa! Nasan dai ba zaka ki ba. Kusan a bunza junaidu yafi shakuwa da Kai ma" Bappah salisu yayi hanzarin girgiza kai yace, "Bazan iya rike su ba gaskia. Abubuwan sai ahankali yaran gaba na kadai ma sun ishemu. Bazan iya hadawa da yaran nan ba saboda banida karfin hakan" Bappaah Auwalu ya kada Kai cike da takaici . Ya dubu gwaggo Ameenatu yace, "Ke fa? Aminatu ke fa? Zaki rike su ko? Nasan ke bazaki ki amincewa ba ba zaki ki tallafar ahalin junaidu ba. Ni na sani" Gwaggo ameenatou ta sauke katuwar bahaguwar zuciya tace, "Ba wai naki bane. Amman Auwalu a situation din da ake ciki Allah mai gidan ma baze bari na dauke su duka ba. Kaga expenses din sunyi yawa. Amma dai ni Ina son abani Amnah zan riketa. A shirye nake na tafi da Amnah. Idan yaso su Ashir, Ashfeef da Nawraah sai asan yadda zaa kula da su. Ko a rarraba su. Ni na dau Amnah, Kai salisu ka dau Ashfeef da Nawraah, sani Kai Kuma ka rike Ashir dakin nan na wajen gidan ka ku bashi ya zauna aciki ya muku tsaro ma tunda namiji ne Kuma babba, Ko duk wata wata zamu dinga harhadawa yan kudi ana kula dasu. Kowannen acikin mu sai a bashi ya kula da dan dake gaban sa yana ragewa. " Ashir ya girgiza kai din takaici har hawayen bakin ciki yayi. Wato da iyayen su na raye bappanin nasu kamar su cinye su suna nuna suna kaunar su. Amman yau dan ba ran bappah junaidu da su ke uwa daya uba daya shine autan su Kuma 'yayan sa na cikin sa. Amma kowanne yaki amincewa ya karbe su. Cikin zafin nama ya bude kofar ya shiga yana goge hawayen sa yana kallon su yace, "Yakumbo ba zaki dau Amnah ba, ba Wanda zai dau kowa... Ku barshi kuje ku zauna da iyalan ku na cikin ku. Ni zan rike kanne na. Zan kula da cin su, Shan su, tufatar da su da yi musu komai Wanda mahaifi da mahaifiyar su zasuyi musu. Zan share musu kukan su. Da yardar Allah ba zasuyi na damar kukan rashin iyayen su ba a kusa. Barkan mu da rana dama gayshe mu nazo yi. Ku huta lafiya..." Ya juya ya fice cikin zafi nama. Ransa na matukar Susa. Ya rakube a jikin wani gini Yana kuka sosai. Dama haka Yan uwantakar take? Wato idan kana raye ne akeyi da Kai da iyalan ka idan ka rasu baya ake juya musu ana kyamatar su haka? Lalle sunyi rashin bango majingina. "Yaa Allah.... Ka dubi maraicin mu ka kawo mana dauki Aaameen." Ya fada Yana goge hawayen sa yayi hanyar gidan su jiri nata dibar sa. Jijiyar kansa ta tashi radau ransa amatukar javula haka ya seseta kansa ya shiga gidan na su. Kai tsaye ya wuce dakin su. Ashfeef baya nan. Ya nemi katifar su ya kwanta Yana rufe fuskar sa da tafin hannun sa.. Hawaye masu matukar dumi suka shiga kwarara daga idanun sa... ::::::::: _Assalamu alaikum... HGL CHARITY FOUNDATION. Na neman temako me hamsin me dari ko sama da haka ko da kayan abinci ne zaa dafa a tallafawa abawa mabukata da sukayi azumi a wannan wata Mai abarka..._ _idan kudi zaa bayar ga asusun banki na opay 9044191709. Haka zalika idan kayan abinci zaa kawo zaa zo tarauni dake unguwar Kano sai akira number opay dincan dake sama_ _zaayi abincin azumi, kosai da Kuma kunu. Wani lokacin harda kankara ta ruwan sanyi ma da za rabawa mabukata masu buda baki.._ _kofa a bude take da dik Wanda zai taimaka. Allah yabada saa ya hadamu a ladan duka amin_ [3/6, 2:22 PM] Hafsaat🧕: _K'K'J_ _(M/W/S)_ _✍️:MX_ _38_ ::::::::: Bappah Auwalu ya mike tsaye yana nuni da kofar da Ashir ya futa hawaye na gangara a fuskar sa yace, "Kun gani ko? Tun ba'aje ko'ina ba. Kun fito kun nunawa iyalan sa na cikin sa ba kaunar su kuke ba. Haba haba haba wallahil azim kunban kunya. Wallahi summa tallahi da inada halin da zan rike yaran nan wallahi zan rike su.. Amman tir da halayen ku, kun yanke amanar zumuncta Allah kyauta" "Ni dai na gaya maka uzuri na. Ai wata kusan tafi wata kusa. Har ga Allah banga ma abunda akayi anan ba. Yaran dai dama yanada tinkaho ne kawai amman me akayi anan ko salisu?" "Gaskia nima sani banga abunda akayi ba. Magana ce fa aketa gaskia domin Allah. Magana ce ta dindinin abunda zaka dore. Ai bakyau mutum ya dau a abinda ba zai iya cigaba da shi ba. Mun fito mun fadi uzurin mu shin menene matsalar anan? Me mukayi ni gaskia banga wani aibu da akai anan ba kai ma Auwalu da son kakaro mana lefi. " "Hmm bare ni dana amince zan rike daya daga cikin su. Ni menene aibuna? Na amince zan karbeta na riketa. Ba shikenan ba? Amman yaci ace yaron nan yazo tsakiyar mu manyan sa, da uban sa yace zai gasa mana maganganu har haka? " Yakunbo Aminatu ta karasa fada tana jan dogon tsaki... Bappah Auwalu ya ja tsaki akaro na uku yana karkada hannu Yana nuni da ceiling dinsa yace, "Wannan ceiling din da sabun kofofin nan/kyaurukan nan. Marigayi ne ya kawo mun kudin wallahi kyauta ma yace ya bani shi zai biya su. Nace aa wallahi bazan amince ba nafi kaunar ni na biya da Kai na idan na samu. Domin junaidu adadin bashikan da yaron nan ya biyamun Allah ba zasu fadi ba. Cin mu , suturar mu, komai namu wallahi Allah shine shahidi. Junaidu yana matukar kokari ganin ya mana dai dai gwargwadon ikon sa. Haka ma matar sa wallahi batada bakin hali kwata kwata. Hakama yaran nasu baki dayan su wallah kowanne sai sam barka. Amman tin da ga kowanne acikin ku uzurin daya kawo bazan takura muku ba. Allah ya kyauta. Ni naji na amince zan rike su" Nusaiba ta fito daga cikin dakin da take labe. Ta daga hannu tayi guda ta nana a cinyarta tace, "Katarar ubancan. Lalle ma Auwalu, mu sai yan hakora. Da jiki duk qashi muna tafiya da kwana acikin talauci. Kache zaka rakito mana wasu rayikan har hudu su tare awurin mu. ? Shin Ina zamu saka su acikin wannan gidan naka mai ukubar rayuwa eh? To ahir dinka. Wallahi ahir dinka. Narantse da uban da ya haifeni ban amince ba" "Gaskia babu babbar butulu a duniya irin kiba nusaiba. Babu Allah. Menene a duniya Wanda mamatannan basu Miki ba su da yaran su.? Junaidu daki sukutum ya dauka ya baki kika saka kiwon da kike. Banda tarin alkhairin da yake mana mu da yaran mu kullum. Marigayiya Hindu baiwar Allah nan ba abunda ta rage Miki ta dauke ki tamkar kanwarta bata Miki kallon faccala dede da second daya. Duk sanda tayi awarar data fara ta sayarwa har Allah ya karbu ranta kullum yaumin sai ta aiko mana, karewarta ma ranar da zata rasu sai data shigo muka gaysa tace daman wajen ki tazo ma tamiki fada . Yaran nan wataran wajen ki zasu dawo ki rike su ma ke zaki aurar da su. Wai Amman duk wasiyyar da take bar miki din kuwa wasiyya ce dai dai da kwayar zarra baki taba ajiyar ta ba a... "Ya Isa dakata da wannan wa'azin kurman da kake don ba saurara nake ba. Da fari kana magana yo wancen akurkin dakin ai sai da ya tabbatar dan Adam ba zai iya kwana aciki ba ko da kuwa rai daya ne bare yace zai moriyar sa shine ya jefe ni da shi. Su kansu kiwon dakyar suke nunfashi saboda azabar zafi da duhu ba ai wundo ba a dakin haba haba dan Allah... Kana maganar awara awarar banza awarar wofi Allah ya kwashewa waken soya ma albarka Auwalu, . Kana maganar suna kyautata mana to ba dole su kyautata ba kudin yafendo ne data bayar ya handame don kuwa sata yayi yasa tayi masa kyautar dole. Dake Kai zakara ne sai da tsaba ya saye ka da kananun kashin kudin da yake maka ya rufe maka baki baka iya ganin lefin sa . Wannan kai ya dama. Na fada na sake fada ba yaran da zai zauna mun agidah wallahi. Muna karime Karime to abincin da zamu ci kullum na rai hudu dakyar zaka karo mana wasu hudun? Tukun nama aina zasu kwana? Wannan gidan Mai kama da turken agwagwi. Muma bai ishe mu ba bare Karin wasu mutanen Na gama magana Allah . Ba dan da yar da zasu zauna mun " tana karasa maganar ta shiga daki ta bugo kofar. Bappah Auwalu yayi shiru ya kasa cewa komai. Babban abunda yafi daure masa kai da Yan uwan sa uwa daya uba daya ke wajen basu tanka sun tsawatar mata ba, Amman ba wani abun mamaki bane tunda sun ki amincewa su rike yayan kanin su uwa daya uba daya . "Allah ya kiyaye hanya idan kun tafi. Na bar ku lafiya Allah yabada ladan taaziyya mungode" Ya saka kansa ya fuce ya bar su zaune... Suka gama maganar da zasu yiyyi suka hada Yan kudin hannun su suka zura a takardar envelope suka saka masa a bayan kujerar da ya tashi . Daya bayan daya suka dare suma batare da sunji kunyar abunda suka aikata ba na kin daukar 'ya'yan kanin su uwa daya uba daya... Ashir yana kallon kowannen su ya shiga motar sa ya tafi, ta cikin windon dakin sa.. yakumbo aminatu ma direban ta yazo daukar ta ta shiga mota tatafi. Rayuwa kenan dama wasu dangin basayi da iyalin ka sai kana raye idan ka rasu kabar iyalan kama juya musu baya suke.. Lalle bango majingina ya fadi. Allah ya jikan Bappah junaidu da malama Hindu. Ya Kuma raya musu yaran da suka bari, Ashir, Ashfeef , Nawraah da auta Amnah. Sabon shafin rayuwa suka bude mai ban tausayi da ban tu'ajjabi.... _Assalamu alaikum... HGL CHARITY FOUNDATION. Na neman temako me hamsin me dari ko sama da haka ko da kayan abinci ne zaa dafa a tallafawa abawa mabukata da sukayi azumi a wannan wata Mai abarka..._ _idan kudi zaa bayar ga asusun banki na opay 9044191709. Haka zalika idan kayan abinci zaa kawo zaa zo tarauni dake unguwar Kano sai akira number opay dincan dake sama_ _zaayi abincin azumi, kosai da Kuma kunu. Wani lokacin harda kankara ta ruwan sanyi ma da za rabawa mabukata masu buda baki.._ _kofa a bude take da dik Wanda zai taimaka. Allah yabada saa ya hadamu a ladan duka amin_ [3/7, 2:50 AM] Hafsaat🧕: _K'K'J_ _(M/W/S)_ _✍️:MX_ _39_ ::::::::: _ADVERT👇👇_ _YERWA INCENSE AND MORE_ _(DUNIYAR KAYAYYAKIN KAMSHI MASU MATUKAR DADI DA KAMA JIKI, GIDAH, KAYA DA SAURAN SU)_ _INA MA'ABOTA TURARE? KADA KU MANTA SHI FA KAMSHI RAHAMA NE, KUMA TSAFTA CE_ _TSAFTA KUMA TANA CIKIN IMANI… TOH KU MAR-MATSO KUSA_ _MUN KUMA ZUWA DA HAJAR KAYAYYAKIN_ _*YERWA INCENSE AND MORE*_ _DOMIN SAMUN ZAFAFAN TURARUKAN WUTA NA GIDA, KAYA, JIKI, TSUGUNNO, GASHI... AKWAI KHUMRAHS MASU DADI YAN BORNU, CHADI, SUDAN DAMA SENEGAL, AKWAI OIL PERFUMES, DA TURARUWAN MOPPING DANA WANKA DANA WANKI DANA GADO DA KUJERU DA BANDAKI DA DRAWER DA MOTOCI.._ _AKWAI MAN GASHI NA FESAWA ME SA KAMSHI DANA KITSO. AKWAI KAYAYYAKIN KAMSHI DANA GYARAN JIKI SOSAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA. •_ _ADIRESHI: KANO.. AMMA SUNA TURA KAYAN SU KO'INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE..._ _INGANCI KYAU RAHUSA DA DADEWA A GIDAH DA KAMSHI SAI KAYAYYAKIN TURAREN YERWA INCENSE AND MORE_ _NAMBAR WAYAR SU: 08095215215, INSTAGRAM/THREADS/TWITTER:yerwaincense_and more_ _YOUR NUMBER ONE STOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS... THEY 'VE GOT YOU AND YOUR HOME COVERED_ ::: **Dawowar sa kenan daga bakin tashar motar unguwar su ta Naduka zone. Ya shiga gidah bakin sa dauke da sallama. A matukar gajiye yake baki daya jikin sa ciwo yake tamkar ana kwankwatsar kashin sa. Ya bude parlorn ya shiga yana doka sallama. Amnah ce zaune akan kujera dauke da kofi a hannun ta. Ta amsa sallamar tana murmushi. Kasancewar akwai shakuwa sosai tsakanin ta dashi. Kusan shi ya reneta tun tana zanin goyo har girman ta. "Amnah nah" "Hamma" Ta kira sunan sa tana murmushi. "Sai ke kadai? Suna Ina?" "Adda Nawraah ta na kitchen hamma Ashfeef kuma baya nan" "Me kike sha ne baki rage mun ba?" 'kunu ne Hamma. Gashi na rage maka" ta mika masa kofin Ya girgiza kai yana komawa kusa da ita ya zauna yana kai hannun sa kan goshin ta, "Ya jikin naki?" "Da sauki hamma" "Toh sannu kinji? Allah yabaki lafiya mai dorewa Amnah" "Aamin Hamma" Bakar ledar dake aljihun gefen rigar sa ya janyo ya sunceta. Yana dubanta yace, "Kinci abinci?" "Na koshi Hamma" "Ah ai bazeyiwu ba. Jeki ce Adda nawrah tabaki plate. To zakici biredi?" Nanma ta grigiza kai tana mikewa tsaye tace, 'ga kunu nasha. Na koshi" "Toh jeki kice ta baki plate" Tayi hanyar kitchen zata kira Nawraah sai ga fitowar nawraahn " "Ah hamma yaushe ka dawo?" "Ba dadewa kenan na shigo. " "Sannu da dawowa hamma. A kawo abinci?" "Aa barbabincin nan cikina ya cushe ban dai ruwa kawai, ki taho da plate" "Tohm Hamma" Kitchen ta koma tana yan zikirinta labbannata na motsawa ahankali . Ta dakko plate da ruwa ta kawo masa ta durkusa ta mika masa ya karba, "Allah ya shi miki albarka" "Aamin Hamma. Wa iyyakum" Ya karasa shan ruwan kenan sai ga shigar Ashfeef parlorn ya dawo daga filin ball. Ya tsaya suka gaysa da Hamman na su sai Kuma ya wuce bandaki. Wanka yayi ya sauya kayan sa zuwa na gidah ya koma parlor ya zauna shima Ashir ya nannade takardar naman ya zazzage naman akan tray. Ba wani mai yawa can bane. Amman yankan su nada girma ya debi manyan tsoka da yawa ya mikawa Amnah 'kin dora akan abinci. A Zuba Miki ko da biredi zakici uhm?" "Zanxi da bread" "Yauwa Ashfeef Miko mata bread idan da akwai" "Suaran sa kenan dazu na cinye Kafin na gama abinci wallahi." Nawraah ta amsa shi tana langabar da Kai 'okau ba damuwa Ashfeef huta ka karno bread anan shagon naga Yan majalisa fal dawowata dana aika Nawraah, "Ah zan karbo Hamma. Ai ban gaji sosai ba" "Rike ungo ban naka ne. Nawraah kema ungo naki." Ya daddanka musu nasu kasan naman yana karkade hannun sa "Hamma Kai fa?" Nawraah ta tambaye shi cike da tausayin sa Ya girgiza kai yana kauda shi yace, "Yana yankawa Ina ci. Kaki damu" ya bata amsa da haka Sarai tasan bawani naman dayaci sanda ana yankawa. Wannan dabiar tasa ba zai taba sauyawaba. Kusan kullum hakane ke faruwa. Ko abinci ne bai Isa ba zai ce su cinye shi a koshe yake.. Ganin irin kallon da suke masa su ukun yasa ya kakaro murmushi don tabbatar da su yace, "Gyaran wata mota mukai babba. Ta gyaru sosai shine mutumin da aka gyarawa dayazo karba yaji dadin gyaran sai yayi mana alkhairi" "Allah sarki Hamma. Allah ya kara daga ku ya inganta ku" "Aameen. Jam'an" Ashfeef ya fita ya sayo biredi. Haka suka gaggand'a da abinci suka ci. Dare yaja suka kwanta.. Ashir na tsaye tsayin daka akan su. Kwata kwata baya samun hutu ko na minti. Kullum Yana aikin da zai rufawa kansa dana Yan uwan sa asiri. Idan yaga ana gini zai cire kayan sa. Yaje ya musu lebura ya debo musu ruwa su biya shi ko bulo, Idan yaga gidan Mai yayi datti ya shiga ya share a biya shi. Yaje gareji nanma yayi gyaran mota ya Kuma wanke ta a biya shi. Ahakan Kuma duk da haka idan fenti aikinsa ya taso yana zuwa yayi shi da Ashfeef Ya yinda Nawraah ke kula da gidan tana dawainiya da kanwar ta su marar cikakkiyar lafiya wato Amnah... Nawraah tana yin kitso akan mutane daya daya haka. Da haka suke hada yan kudaden su rufawa junan su asiri mashaa Allah... _Assalamu alaikum... HGL CHARITY FOUNDATION. Na neman temako me naira hamsin me naira dari ko sama da haka ko da kayan abinci ne zaa dafa a tallafa abawa mabukata da sukayi azumi a wannan wata mai albarka..._ _idan kudi zaa bayar ga asusun banki na opay 9044191709. Haka zalika idan kayan abinci zaa kawo zaa zo unguwar tarauni dake garin Kano sai akira number opay dincan dake sama_ _zaayi abincin azumi, kosai da Kuma kunu. Wani lokacin harda kankara ta ruwan sanyi ma da za rabawa mabukata masu buda baki.._ _kofa a bude take ga duk Wanda zai taimaka. Allah yabada saa ya hadamu a ladan duka amin_.. [3/7, 2:50 AM] Hafsaat🧕: _K'K'J_ _(M/W/S)_ _✍️:MX_ _40_ _Assalamu alaikum... HGL CHARITY FOUNDATION. Na neman temako me naira hamsin me naira dari ko sama da haka ko da kayan abinci ne zaa dafa a tallafa abawa mabukata da sukayi azumi a wannan wata mai albarka..._ _idan kudi zaa bayar ga asusun banki na opay 9044191709. Haka zalika idan kayan abinci zaa kawo zaa zo unguwar tarauni dake garin Kano sai akira number opay dincan dake sama_ _zaayi abincin azumi, kosai da Kuma kunu. Wani lokacin harda kankara ta ruwan sanyi ma da za rabawa mabukata masu buda baki.._ _kofa a bude take ga duk Wanda zai taimaka. Allah yabada saa ya hadamu a ladan duka amin_.. ::::::::: .... Suna zazzaune baki dayan su a parlorn su. Nawraah na koyawa Amnah karatun alqur'ani tana kara mata ayoyi biyu kamar ko da yaushe na daga surar da suke... Domin Amnan kasancewar batada cikakkiyar lafiya. Kullum a kwance take. Hakan yasanya baa sata a makarantar ba tun da ran mahaifan su... Ashir na zura yan ashirin ashirin da goma goma na dari takwas din daya samu awajen wankin mota. Yana ta cusa su acikin asusu yace taru zasuyi sosai da azumi sai afasa inshaa Allah ayiwa yaran kayan sallah da abincin sallah. Ashfeef Kuma Yana gefe da yar wayar sa rakani Kashi a hannu Yana latsawa. Bubbuga kofar gidan na su aka fara yi da karfi kamar zaa ballo kofar baki daya. Ashfeef ya mike ya fita . mutane ne guda biyu suka zo acikin wata zungureriyar mota. Sun fakata a daidai kofar gidan tamkar zasu shigar da ita aciki saboda yadda tayi dab da dab motar da kofar shiga gidan. Sallama yayi musu suka amsa masaa gayshe su yayi Yana bin su da kallon Karin bayani. Manyan mutane ne Wanda kallo daya zakai musu kasan masu kudi ne.. dubada motar da suka zo da ita da kayan dake jikin su ma na manyan attajirai ne. "Kai dan gidan marigayi junaidu me ko?" "Eh Dan sa ne" "Eh ga kamar Nan" daya daga ciki ya fada "Kai ne babban Dan sa?" "Aa akwai Hamma Yana ciki" "Kira mana shi yanzu " "Tohm. Amma su waye zaa ce?" "Kache magana zaai da shi" "Tohm" ya fada Yana komawa cikin gidan ya shiga Yana sallama suka amsa Ashir ya daga Kai Yana kallon sa yace "Su waye?" "Wasu ne gasunan da motar su. Suke tanbayan ni dan abbiey ne? Ni ne babban nace aa akwai Hamman mu shine sukace na Kira ka wai magana zasuyi da Kai" "Toh Allah yasa lafiya" ya mike Yana gyara zaman rigar jikin sa Fita yayi ya basu hannu sukayi musabaha ya gayshe da su bayan hannun da yabasu cike da girmamawa, "Kai ne babban da ga marigayi junaidu ko?" "Eh ni ne..." "Mashaa Allah. To ya Karin hakurin mu?" "Alhamdulillah da godia" "Toh Allah ya gafarta masa" "Allahumma Aameen" "Sunana Alhaji Garbosai . Kuma ni munyi zaman mutinci da mahaifin ku. Ba sa'a na bane na kere shi a shekaru. Amman saboda ganin daraja da kimar sa ta mutane da mutanta kowa yasa aka zama tamkar Yan uwa. Wato abunda ya faru shine duk kuwa dai da anyi zancen ai lokacin rasuwar ko kan wani Yana binsa kudi akwai shedu ma da sheda ko?" "Eh anyi haka" "Toh mashaa Allah .. Ni ne Wanda ya bawa Marigayi junaidu kudade. Ya bada jinginar kadarar sa. Ya karbi kudi masu tarin yawa alokacin yazo mun da maganar rashin lafiyar yarinyar karama na daga cikin iyalin sa. Yazo cikin wani yanayi na tashin hankali da ban tausayi. Na debo kudin na bashi yace ba zasu Isa ba Amman ya gode. Na temaka dai na ranta masa kudi masu tarin yawa kimanin naira miliyan d..... Yace ga jinginar kadarar sa kaza ana kammala aikin asibutin yarinyar zai kawo kudin ya karbi takardun kadarar tasa... Lokacin daya diba har ya shude ma. Don magana ta Allah kudin Dana bashi ma yafi jinginar daya bayar tsada bama zaa taba hadawa ba. Amman dai na bashi saboda tausayi. Lokacin daua diba da mukai rubuce rubuce sheda ga sanda zai dawo dasu ya karbi takardun sa, ni Kuma daga baya na tafi Johannesburg wani uzuri ya taso mun..... To Kuma sai ake sanar mun da rasuwar sa. Shedu nama sun zo nan din sunyi magna. " "Kwarai anyi haka sun zo. Kuma abbiey din tabbas ya dau dawainiyar kanwar mu da batada lafiya aka yiyyi mata aiki sosai..." "Allahs sarki ya jikin nata?" "Da sauki Alhamdulillahi... " "To Allah yakara sauki Amin... Ga shedar faifan bidiyo da Wanda akayi a rubuce ma. Bari a dakko komai" "Okay bari nasa a Kira bappan mu yayan mahaifin mu ne. Nan gaba kadanne gidan sa a compound daya muke" "To shikenan ba matsala" "Ashfeef" "Naam Hamma" "Dan kira Bappah Auwalu kace ana iso da shi muna tsaye da su" "To shikenan" Ashfeef ya zagaya ta kofar baya ya nufi gidan bappah ya gaya masa atare suka taho Bappah Auwalu yasa aka dakko tabarma suka zazzauna sannan suka gaysa sosai. Alhaji Garbosai ya dakko file da takardar shedar take. Ya Kuma budd wayar sa Yana kunna musu faifan bidiyo tar tar tar. Suka karasa kalla. Ya bude paper nanma ga rubutun bappah junaidu nan ya saka hannu ya karbi kudi ya bada jinginar gidan sa da suke ciki kan idan ya samu kudin zai mayar karshen watan ya karbi kadarar sa ta gidan sa daya bda papers din ginin da komai da komai na court ..... _INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_ _KU MARMATSO KUSA...🔊_ _ZAFAFA BIYAR 2024_ _ZAFAFA BIYAR!!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_ _YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_ _GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_ _________ _1_ *_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_ _2_ *_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_ _3_ *_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_ _4_ *_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ [3/7, 2:50 AM] Hafsaat🧕: _K'K'J_ _(M/W/S)_ _✍️:MX_ _41_ :::::::::.. _Assalamu alaikum... HGL CHARITY FOUNDATION. Na neman temako me naira hamsin me naira dari ko sama da haka ko da kayan abinci ne zaa dafa a tallafa abawa mabukata da sukayi azumi a wannan wata mai albarka..._ _idan kudi zaa bayar ga asusun banki na opay 9044191709. Haka zalika idan kayan abinci zaa kawo zaa zo unguwar tarauni dake garin Kano sai akira number opay dincan dake sama_ _zaayi abincin azumi, kosai da Kuma kunu. Wani lokacin harda kankara ta ruwan sanyi ma da za rabawa mabukata masu buda baki.._ _kofa a bude take ga duk Wanda zai taimaka. Allah yabada saa ya hadamu a ladan duka amin_.. ::: ... Suka kammala ganin komai. Jikin Ashir da Bappah Auwalu sukayi sanyi. Baki daya sun shiga cikin dimuwa. Alhaji Garbosai ya ce da su, "To kunga yadda komai ya kasance. Bayan lokacin daya diba ma bai kawo dinnan ba kasancewar halayen sa na kwarai yasa nayi tafiyata ma waje nasan ba damuwa ko da aka sanar mun rasuwar sa nace to shaidun suzo su Fadi akwai nauyi ko ince alkawarin a kansa dake bukatar saukewa. Amman abari na dawo ba damuwa kar a dimauta iyalan sa suna cikin alhini. Hakann kuwa akayi bayan na dawo na Kara bada lokaci Mai tsawo sosai sannan nazo yanzu. " "Mashaa Allahu. To yanzu Alhaji akan me kazo kenan. Don yanzu sai abunda kace. Tunda Wanda kukayi maganar nan da Kai Allah ya karbu abunsa. Kuma bamuda masaaniyar komai akai" "Hakane kam Allah ya gafarta masa. Magana daya ce zuwa biyu. Na farko dai idan da akwai kudaden abiyasu kawai acire dubu dari biyar din Kai na yafe wallahi. Akarbu takardun gidan nan. Idan Kuma babu to gaskia zai yi wuya a idan baa karbu gidan ba baki daya Ina nufin kadarar zata maye gurbin kudin da ya karba duk kuwa ma da sai yayi ciko amman na yafe" "Mashaa Allahu Allah ya saka maka da alkhairi Amin. To yanzu Alhaji ba wata hanya ta daban da zaka bayar. Allah bamuda dalilin biyan ka kudaden daka ambata, Kuma bansan gidan nan nasu ya tafi don shi kadai suka mallaka gaba daya wallahi Alhaji" "Sai dai muyi hakuri don wallahi a halin da ake ciki nima banida rufin asirin da zan iya hakura da kudaden nan Allah shine sheda" "To Alhaji yanzu kamar shekara nawa zaa bayar don mu samu mu maido da kudin?" "Ai bawan Allah baa cewa kawai. Dan wallahi kudaden nan kaga Dan uwana Nan. Rabi nasa ne rabi nawa. Daga baya na bukaci kudin ya ranta mun rabin. Don haka wallahi dama da an biya kudaden Nan to shi zan basa don nasa ne. Haka zalika idan kudin bai samu ba. To lalle wannan gidan zai zama mallakin sa. Sai dai kuyi hakuri. Batun Kara baku lokaci wallahi an baku Kuma Kun sani" "Munsani ranka ya dade Dan Allah kayi hakuri ni yayan mahaifin su ne. Da Marigayi junaidu da ni uwar mu daya uban mu daya ranka ya dade. Bamu da kadarar da zamu maye gurbin kudaden da kake bi. Kuma wallahi bamaso gidan nan ya salwanta agrare mu. " "Kuyi hakuri don wallah an Kara muku lokaci an rage kudin ma. shima Kuma Yana bukatar gidan wallahi. Kuyi hakuri" "To Alhaji kamar yaushe zasu bar gidan kenan? Don nagaya maka shine rufin ashirin su damu baki daya" "Gaskia gaskia karshen gaskia daga wannan satin da zamu shiga shine karshen kuyi hakuri" Ashir ya mike da sauri Yana dafe bango Bai jira Mai zasu sake cewa ba ya bi bango Yana dafe dashi ya koma cikin gidah bandaki ya shige cikin sa ya kada saboda tsabar tashin hankali Nan da Nan kuya yafara zawo kamad ruwa.. Daga karshe bappah ne yaji musu sallama suka ja motar suka tafi shi kuma ya shiga cikin gidan inda ya tarar Ashir din a kwance akan kujera ya rufe fuskar sa da littafi. Jikin yaran duk a sanyaye suna jiyo komai tun dazu da fari har aka kammala. da kawu Auwalu ya rakazu, kowanne fuskar sa duake da damuwa. Ya dan kwantar musu da hankali ya musu sallama shima ya koma gidan sa dauke da damuwa. Dik kowane danuwan su ya kira su ko zasu temaka kowanne yace bashi da hali. Don bakin ciki har kuka yayi bappah Auwalu. Haka Kwanakin sukayi ta ja. Mutanen Alhaji Garbosai sai zuwa suke suna bin notice, Ashir yaje gwangwan ya Kira masu saye suka sayi kayan kallon su da firjin su da katifar dakin mahaifan su da suka rasu da drawer su nawrah da kujeru Banda babba daya 3 sitter baki daya ya sayar da komai harda labulaye sai biyu ya rage. Komai da komai ya sayar , Amman kudin da suka samu kwantan kwatan kwantan kwatankwacin rabin rabin rabin rabin abunda ake bi basu hada ba. Haka ya hakura ya sanya kudin a asusu kawai gab daya. Ranar wata talata da safe kanin Alhaji Garbosai yazo yace lalls su tashi su zubar masa gidah na zuwa da yamma. Suka karasa komai nasu tun da safe Ashir ya zuciya suka fita daga gidan Bappah Auwalu ya ce suje gidan su. Su koma gidan sa baki daya da zama shi bai wulakanta yayan Yan uwan sa ba. ...... Ya kwankwasa. [3/8, 5:26 PM] Hafsaat🧕: _K'K'J_ _(M/W/S)_ _✍️:MX_ _42_ ::::::::: _Assalamu alaikum... HGL CHARITY FOUNDATION. Na neman temako me naira hamsin me naira dari ko sama da haka ko da kayan abinci ne zaa dafa a tallafa abawa mabukata da sukayi azumi a wannan wata mai albarka..._ _idan kudi zaa bayar ga asusun banki na opay 9044191709. Haka zalika idan kayan abinci zaa kawo zaa zo unguwar tarauni dake garin Kano sai akira number opay dincan dake sama_ _zaayi abincin azumi, kosai da Kuma kunu. Wani lokacin harda kankara ta ruwan sanyi ma da za rabawa mabukata masu buda baki.._ _kofa a bude take ga duk Wanda zai taimaka. Allah yabada saa ya hadamu a ladan duka amin_.. ::::: °°°°° Ya sake kai hannun sa ya kwankwasa a karo na biyu. Yana riko hannun Amnah acikin nasa. Nusaiba dake zaune a kujera taja tsaki ta mike tana mita, "Auwalu kenan. Kawai saboda kasan yanzu Ina hutawa ne. Zaka dinga wani bugo kofa don na tashi lalle na bude? To gaskia ba komai agidan gwara ka shigo mana da biredi ka koma Layla ta kwanta Kuma na san yunwa ce. " Ta fada tana bubbuga kofar itama Bappah Auwalu yaja tsaki cike da takaici yace, "Bude mana. Ba ni kadai bane" Nusaiba ta gyara zaman dankwalin ta. Ta dauka bako yayi ko zai basu dan kudi su samu suyi abinci. Ta gudu ta shiga dakin Layla ta tasota, "Tashi dan uban ki. Inaga mutumin rannan abokin baban ku ne yazo. Je parlor ki zauna idan kin gayshe shima karki tashi nasan idan suka gama hirar su kamar rannan. Zai baki ko yar dubu biyu ce" Layla ta tashi tana murza idanu saboda baccin dake kanta tashiga bandaki ta dauraye bakin ta, "Ba Zaki sauri ba. Wane irin wulakanci ne?" "Umma yanzu zan tafi ai" Nusaiba ta zauna a kujera. Alokacin bappah Auwalu ya cika yayi fam. Layla ta saka hannu ta bude kofar tana cewa, "Ina wuni?" "Lafiya. Ke Kuma wa kika dauka? Akace kinyi bacci. ? Nusaiba wane irin wulakanci ne wannan tun dazu saboda Allah nake cewa ki bude mana Amman shine kika ki sai da kika taso ta tazo ta bude. Wato ban Isa kizo ki bude mana kofar ba kenan ba ko?" Bappah Auwalu ya karasa fada yana jan tsaki." Nusaiba ta mike har tana ball da kofin ruwa agabanta tana mai nuni da su Ashfeef da kowanne ke rike da akwatin sa a hannu tace, "Bangane ba. Wadannan nan Ina zasu? Wanne bappanin ne ya amince ya rike su? Bappah salisu ko sani ko kuwa Gwaggo Aminatu ce? Ko gidan aikatau dinne suka ce zasu karbe su?" Tsaki yaja dogo yana nuni da yan kujerun parlorn na su yace "Ku zauna Nawrah" "Ka wayar mun da Kai mana Auwalu. Ga ka ga yara rabe rabe kowanne da kayan akwatin sa dashi. Shin wani gidan suka sauya da yafi wannan? Hmm to Auwalu ai gwara Kai ma kasan abunda ke maka ciwo kullum jiya iya yau. Sai dai kache wanin ka. Ba zaka tashi ka nemi na kanka ba." Bappah Auwalu ya grigiza Kai Yana yatsina fuska yace, "Dan Allah ya isheki haka. Yi shiru. Haba sai magana kiketa ratattakawa. Meye haka eh? Haba banason irin wadannan abubuwan wallahi ,yara dan kin gansu acikin gidan nan ai yaya nane suma ko kin ki ko kin so inda kara kema ai baki ne. Bayaga haka. Tun ba yau na gaya miki. Ba Kuma wai amincewar ki ko kin amincewar ki zan bi ba. Wadannan Yara da uban su da ni uwar mu daya uban mu daya. Don haka na dawo dasu gidah na da zama baki daya har zuwa sanda Allah zai warware mana matsalolin mu." Nusaiba ta saka hannu a baki taja guda tana watsa hannu sama cike da bakar masifa tace "Ah lalle. Nace mekace a karshen zancen ka! Ka san ba kasafai maganganun ka suke ratsa kunne na ba" "Nace Yara sun dawo gidan nan. Ba na neman amincewar ki ko kin amincewar ki" "Kan babban balastin. A wannan kungun gidan Mai kama da ramin cinnaka zaka ce zamu zauna da yara zagada zagada har hudu? Wallahi summa tallahi bazan yarda ba. Bazan amince ba. Wallahi kaji rantsuwar musulmai kenan." "Gidan ki ko nawa? Ni Kuma nace yara sun dawo nan gidan da zama kiyi abunda Zaki. Ku zauna Ashir bari a kawo muku ruwa" Kitchen ya nufa. Nusaiba tabi bayan sa tana ife ife tamkar zata rusa gidan hannunta daya akan kofar kitchen tana kwaso rantsuwa tana bubbuga hannunta cike da tsantsar masifa tace... _INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_ _KU MARMATSO KUSA...🔊_ _ZAFAFA BIYAR 2024_ _ZAFAFA BIYAR!!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_ _YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_ _GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_ _________ _1_ *_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_ _2_ *_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_ _3_ *_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_ _4_ *_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ [3/8, 7:22 PM] Hafsaat🧕: _K'K'J_ _(M/W/S)_ _✍️:MX_ _43_ ::::::::: "Wallahi summa tallahi yaran nan bazasu dawo mun gidah da zama ba. Aina zasu zauna rai hudu? Zagada zagada, dakuna biyu ne kawai jallin jal. Daya muna ciki. Daya Layla . Ahmad kuwa a parlor yake kwana saboda babu wajen kwana. To akan mu kakeson wannan rai hudun sun kwana ko meye? Sannan munada halin ciyar dasu ne eh? Muma da Yaya muke samun abincin da zamu saka acikin mu hudu ballantana ka karo rai hudu? Kanzo zaa jika a basu ko menene? Duk acikin Yan uwan ka Kai ne koma baya. Kowanne yafi ka hali nesa ba kusa ba. Amman sika kekashe idanun su. Suka bada musu kasa kowanne yace shi ba zai iya daukar su ba da dawainiyar su saboda halin rayuwa. Amman sai Kai uban dan sarkin son birgewa ba kada ko sisi kana tafe tamkar iska zata hure ka saboda yunwa har Kaine zaka je ka jajibi mana rayuka uku saboda San asani da nuna birgewa aljihu ba ko sisi. To narantse da Allah bazan rike yaro ko daya ba. Kuma babu yaron da zai zauna mun agidah. Wallahi" nusaiba ta fada tana kururuwa tamkar zata hau kansa da duka. Bappah Auwalu da maganganunta duk sun cika shi ga kunya daya dabaibaye shi yadda take gasa masa magana agaban yayan sa na cikin sa. Duk da sun saba ji su da su nawrah din Amman dai da kunya. Don haukanta na ranar yafi na ko yaushe... Hannunta Yaja ya shigar da ita ciki ya rufe da mukulli. Suka shiga fadan kache nache tamkar zasu cinye juna don masifa musanman nusaiba dake masa tsiwa tamkar zata rufe shi da duka "Hamma daman su bappah ca sukai suma na zasu rike mu ba kenan?" Ashfeef ya tambaye Hamma Ashir da kansa ke a sunkuye idanun sa sun kada sunyi jazir "Hamma wai hakane? Su bappah fa da Gwaggo Aminatu ko ba ka sani ba Hamma?" Ashir ya saka hannu ya goge hawayen dake zuba a Idon sa Yana Jan majina. Sam bai gayawa Yan uwan nasa bappanin su sinki daukar su ba saboda bayasan suji haushin su saboda zumunci. Amman tunda sun rigada sunji da kunnen su yanzu. Bashida wani dabarar da zai ce baai haka ba. Don idan ya karyata ma yayi kuskure don haka ya kada yai Yana sharce idanun nasa yace "Abune ya fadamun a idanu na. Anyi haka. Amma ba da wani abu suka fada ba. Kunsan rayuwar yanzu tayi tsada ne gashi muna da yawa. Ku tashi mu tafi. Yan kudaden nan da aka sayarwa gwangwan kayan mu ya Isa mu kama ko da dakine da parlor awani wajen mu koma. " Mikewa yayi Yana goya jakar Amnah a bayan sa. Suna shirin buda kofa su fita sai jin muryar bappah Auwalu ya kira sunayen su daya bayan daya, "Ashir Ashfeef, Nawraah, Amnah Ina zuwa ? Ku dawo ku zauna mana ga ruwan" "Ai bappah daka basshi wallahi. Zamu je inda zamu samu wajen kwana ne Kafin mu nemi wuri sosai akwai kudin awaje na" "Ah karmuyi haka da ku ahsir Dan Allah. Kada ku bari maganganun wannan sakaryar suyi muku tasiri a kwakwalen ku gidah dai nawane don haka nike da iko da gadara akan sa. " "Ita nusaiba da Layla su kwanta akatifa daya. A dakko babbar katifar can dakin a sakata aciki Nawraah da Amnah su kwana tare da su. Dakin Layla Kuma sai Kai da Ashfeef da Ahmad kub dinga kwana aciki. Ni kaga kujerar nan ta bayan ka ta ishenuli daman wani lokacin ma akanta nake kwanciya har safe iska parlorn ga dadin bacci". Ashir yayi murmushi yana grigiza Kai yace, "Dan Allah kayi hakuri bappah Amman wallahi bazan iya dawowa gidan nan da zama ba tabbas gaskiyar Aunty yayi mana kadan" "Yauwa Ashir kaji yace gaskiyar ta. Yo mu kanmu Ina gidan nan zai dauke mu bakidayan mu" "Zan mugun saba miki nusaiba Allah kuwa. Ashir.... Kafin bappah Auwalu ya karasa maganar dazai Ashir ya katse shi ta hanyar zube gwaiwoyin sa akassa yace, "Dan Allah kayi hakuri bappah. Ka dubi girman Allah ka saurari abunda Zan fada. Kuma dan Allah ka amince da abunda Zan fada din. " "Inasauraron ka Ashir" "Bappsh gidan nan wallahi ba zai dauke mu ba yayi kadan wallahi Anty tayi gaskia. Na biyu dama wallahi bada niyyar zaman agidan nan muka biyo ka ba yau din. Dama akwai tsare tsare. Da nake akai na.kayi hakuri yau din na amince akan dare yaja zamu kwana anan, Amman daga gobe inshaa Allah ba zamu sake kwana ba. Zamu samu waje kusaa da nan din. Idan Allah ya amince na mun samu kudaden da zamu biya wancen mutumin shikenan sai mu karbi gidan bappah mu biya shi. Dan Allah karma ka ki amincewa bappah. Idan kaki amincewa akwai matsala. Dan Allah Kai ne mahaifin mu albarkar ka muke nema" ya rike kafafun bappah Auwalu ya faraa hawaye dumin su na diga a kafar bappah Auwalu. Sunkuyawa bappa Auwalun yayi ya riko hannuwan Ashir yace dashi, "Shikenan na amince Ashir. Amman sai idan inda aka samu din anan zagayen layin yake ko nan yankin idan baa samu ba to gaskia ban amince ba. Haka zaku dawo nan mu cigaba da rayuwa tare watarana ma duk mutuwa zamuyi ashir. Dan Allah Nima Ina rokon wannan alfarmar kaji?" "Shikenan bappah. Na amince" "Yauwa ko kaifa Allah yayi muku albarka kaji? " "Aaameen bappah wa iyyakum" Nusaiba sai Harare hararare take bappah Auwalu yasa ta dakko zannuwan gado Ashir da su Ahmad sukayi shimfida a parlor suka kwanta. Nawrah da Amnah da Layla Kuma suka kwanta a adakin layla. A haka sukayi bacci kowanne da abunda zuciyar sa ke saka masa.... Ashir da asubah ya futa tunda akayi sallah Bai dawo gidah ba. Ya sayi biredi wajen takwas na safe da madara da sukari ya Kai musu duka gidan suka ci Nan ya shiga neman gidan haya kain dana in anan yankin.. Amma Allah cikin ikon sa baa dace ba. Gashi Ashir bayason ketare maganar manya don haka ya cewa bappah baa samu ba . Ya Kuma nemi gafarar sa daya barsu su nema a unguwar kusa da su. Bappah Auwalu yace sai nan gaba amman ba yanzu ba. Tunda nusaiba ta jiyo su ta fara hauka kamar sabuwar tabi. Har da fashe fashe na kofuna tana nanawa kanta wuka zata kashe kanta kan lalle Auwalu ya zabi daya ko ita ko su. Ganin haka yasa Ashir yace da kannen nasa su tashi su dakko kayan su duka suka fito. Bappah Auwalu ya biyo su Yana hawaye, "Dan Allah Ashir karku yanke mana zumuntar mu ku nake kalla naga kamar junaidu don Allah . Kayi hakuri ka janye maganar ka ni ku na zaba ba ita ba. Ita tamkar riga ce da zan cire na sako wata haka take awaje na. Aurota nayi ,Dan haka iya rabuwa da ita na auro wata ku kuwa Yaya na ne bazan iya taba yanke zumuntar mu ba har gaban abadan. Jini ya wuce gaban komai" Ashir Ya goge hawayen sa Yana rasa Mai zace Duk suna tsaye cirko cirko da akwatinan su a hannu... _ADVERT👇👇_ _YERWA INCENSE AND MORE_ _(DUNIYAR KAYAYYAKIN KAMSHI MASU MATUKAR DADI DA KAMA JIKI, GIDAH, KAYA DA SAURAN SU)_ _INA MA'ABOTA TURARE? KADA KU MANTA SHI FA KAMSHI RAHAMA NE, KUMA TSAFTA CE_ _TSAFTA KUMA TANA CIKIN IMANI… TOH KU MAR-MATSO KUSA_ _MUN KUMA ZUWA DA HAJAR KAYAYYAKIN_ _*YERWA INCENSE AND MORE*_ _DOMIN SAMUN ZAFAFAN TURARUKAN WUTA NA GIDA, KAYA, JIKI, TSUGUNNO, GASHI... AKWAI KHUMRAHS MASU DADI YAN BORNU, CHADI, SUDAN DAMA SENEGAL, AKWAI OIL PERFUMES, DA TURARUWAN MOPPING DANA WANKA DANA WANKI DANA GADO DA KUJERU DA BANDAKI DA DRAWER DA MOTOCI.._ _AKWAI MAN GASHI NA FESAWA ME SA KAMSHI DANA KITSO. AKWAI KAYAYYAKIN KAMSHI DANA GYARAN JIKI SOSAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA. •_ _ADIRESHI: KANO.. AMMA SUNA TURA KAYAN SU KO'INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE..._ _INGANCI KYAU RAHUSA DA DADEWA A GIDAH DA KAMSHI SAI KAYAYYAKIN TURAREN YERWA INCENSE AND MORE_ _NAMBAR WAYAR SU: 08095215215, INSTAGRAM/THREADS/TWITTER:yerwaincense_and more_ _YOUR NUMBER ONE STOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS... THEY 'VE GOT YOU AND YOUR HOME COVERED_ [3/8, 8:20 PM] Hafsaat🧕: _K'K'J_ _(M/W/S)_ _✍️:MX_ _44_ ::::::::: "Zamu iya kwana nan Bappah..." Ashir ya fada yana nuni da dan dakin da Bappan su ya bawa nusaiba take zuba kiwon ta . Tamkar akurkin kaji. 'ah haba ahsir. Ya za'ai rai na dan Adam ya iya zama nan? Ai ba zeyiwu ba" "Allah Bappah zai yiwu. Zamu zauna har ya zuwa sanda zaa samu dan waje na kamawa anan yankin. Idan har zuwa nan da yan lokacin dana bari ya cika bamu samu ba. To kayi hakuri ko da awani unguwar ne zamu kana waje mu koma. Kuma zumuncin mu har aljanna inshaa Allah. Haka na dai yanke bappah .. Daurewa zai ayi" "Ashir ka kalli dakin nan kuwa." Nusaiba dake binsu dadi fam ranta ta nufesu tana murmushi, "Kalau daki yake. Tumakan kawai zaa janye. Kajin Kuma a mayar da kejin su gefen can haka daga ciki ai yayi" Bappah Auwalu ji yake tamkar ya Kai mata gula aciki ya hanbare ta baki daya. Cike da takaici yace, "Bar nan nusaiba" "Naje Ina? Ko ka manta mallaki na ne nan din? Ai na wa ne" "Mahaifin su ne dai ya baki kada ki manta. Ke butuluce wallahi Allah" "To daya banu yanzun ai nawa ne ko na baka ta rabaka da kayan ka. Allah na tuba nan din dan ya bani har wani abun birgewa ne... "Da kata anty.ya isa hakaa. Kada ki tabo abbiey ko ummy. Maganar ta tsaya akan mu please." Ashir ya katseta Yana kada Kai. Bappah Auwalu ya juya ya dankara mata harara, "Ai ga irin ta Nmnan" ya fada Yana Jan dogon tsaki ya dubi Ashir yace, "Amma da sharadin zaayi gyara sosai acikin sa da sauran su. Don daii ka hadamu da babban bango ne kace Allah bazan iya musu ba. Amman kasani har cikin raina banji dadin kasancewar ku anan dakin ba wallahi Allah ne sheda. Dakinda ake saka kiwon tumaki da kaji daa harda zomaye ma ace dan Adam ne zasu kwana acikin sa?" "Bakomai bappah Allah. Mungode hakan ma ta mana kokarin" "Kokarin me bayan mahaifin ku nema ya bata ba wai kudi ta saka ta saya ba" "Kuma dai ai ba roka nayi ba da zaka ce haka. Allah na tuba dakin da kiwon da duk mutuwa suka dinga y kamar an canfa shi. Ni dai ga daki nan nace su zauna aciki ba Kuma kyauta na bayar ba ban amince Kuma ayi wani fàshe fashe ko gine gine acikin sa ba batare da izini na ba gaskia. " Tana gama magana ta koma ciki kamar Zata tashi garin, "Kifi ruwa gudu ma nusaiba. Aikin kawai" bappah Auwalu ya fada Yana hararo bayanta data tafi Ashir yayi gaba Yan uwan na biye da shi abaya aka bude dakin. Ba lefi Yana da Dan girman sa. Sai dai kofa ce kawai babu window a dakin. Sai kashin tumaki Dana kaji da kazanta dai sosai. Ashir ya kade hannunsa yana duban nawrah yace, "Muje keda Amnah . Idan muka gama zamu kira ku. Sai anyi gyara sosai" "Hamma zan tayaku".. "Aa jeki zauna da amnah" "Toh shikenan Hamma Allah ya bada sa'a" "Aamin" Tafiya tayi ... Ashir da Ashfeef da Ahmad da b. Auwalun suka fara kaude kauden kayan wajen zasu gyara nusaiba ta leko tana kiran Ahmad. Tunda ta kiraa shi bappah Auwalu ya girgiza kai kawai don ya tabbatar Kiran sa tayi ta hana shi aikin. Ai kuwa suna fita ta rufe shi da fada, "Dan uban ka a wannan kurar,wannan shekararren akurkin dakin da ba bil adama ke kwana aciki ba kaje ka baje hanci kana tayasu aiki. Wuce muje gidah. Kuma wallahi ka sake ka fito sai na ci haka kaza ta uban ka" "Kai umma" "Zakaa wuce ko sai na sharara maka Mari" Ciki ya nufa,Yana kananun mita. Ta shiga ta rufe kofar harda mukulli ganin haka yasa nawrah rike hannun Amnah suka koma can gefen famfo suka zauna. Sannu ahankali suka fara gyara dakin suka wanke shi. Ya bushe suka saka katifun da suka rage akayan da basu sayar ba. Suka raba dakin biyu da labule. Rabi daya na Ashir da Ashfeef. Dayan Kuma Nawrah da Amnah sai yama tamkar ciki da parlor don sai ka daga labulen zaka Isa wajen su Amnan. Suka jajjera Yan abubuwan su da suka taho dasu. Suka jinginar da akwatunan su a gefe . Ashir ya kunna karatun alqur'ani awayar ummyn su dake wajen sa tun da suka fara aikin har safiya sai da wayar ta kare karaf sannan ya kashe... Haka rayuwar tasu ta cigaba da garawa. Da safe zai sayo biredi ya Kai gidan bappah auwalu suci gaba daya. Da Rana ma Dan kudin da suka samu da Ashfeef zasu auno taliya yar aune ko shinkafa su bawa nusaiba ta dafa... Dare ya zama safjya, safiya ta zama rana, Rana ta zama yammaci yammaci ya koma dare lalle Allah buwayi ne gagara misali. ------- Zaune suke baki daya a parlorn su bappah Auwalu wasu a akasan kujera wasu Kuma akan kujerar. Tun ba su yarda suna zuwa ba. Har dai suka saba saboda takurawar da bappan nasu yake musu kan lalle su je su zauna ayi hira. Duk abunda ake cewa nusaiba sai dai ta yamutsa fuska. Tana jinsu. Sai data mula ta sha iska tace... _ADVERT👇👇_ _YERWA INCENSE AND MORE_ _(DUNIYAR KAYAYYAKIN KAMSHI MASU MATUKAR DADI DA KAMA JIKI, GIDAH, KAYA DA SAURAN SU)_ _INA MA'ABOTA TURARE? KADA KU MANTA SHI FA KAMSHI RAHAMA NE, KUMA TSAFTA CE_ _TSAFTA KUMA TANA CIKIN IMANI… TOH KU MAR-MATSO KUSA_ _MUN KUMA ZUWA DA HAJAR KAYAYYAKIN_ _*YERWA INCENSE AND MORE*_ _DOMIN SAMUN ZAFAFAN TURARUKAN WUTA NA GIDA, KAYA, JIKI, TSUGUNNO, GASHI... AKWAI KHUMRAHS MASU DADI YAN BORNU, CHADI, SUDAN DAMA SENEGAL, AKWAI OIL PERFUMES, DA TURARUWAN MOPPING DANA WANKA DANA WANKI DANA GADO DA KUJERU DA BANDAKI DA DRAWER DA MOTOCI.._ _AKWAI MAN GASHI NA FESAWA ME SA KAMSHI DANA KITSO. AKWAI KAYAYYAKIN KAMSHI DANA GYARAN JIKI SOSAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA. •_ _ADIRESHI: KANO.. AMMA SUNA TURA KAYAN SU KO'INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE..._ _INGANCI KYAU RAHUSA DA DADEWA A GIDAH DA KAMSHI SAI KAYAYYAKIN TURAREN YERWA INCENSE AND MORE_ _NAMBAR WAYAR SU: 08095215215, INSTAGRAM/THREADS/TWITTER:yerwaincense_and more_ _YOUR NUMBER ONE STOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS... THEY 'VE GOT YOU AND YOUR HOME COVERED_ [3/9, 4:40 PM] Hafsaat🧕: _K'K'J_ _(M/W/S)_ _✍️:MX_ _45_ _ADVERT👇👇_ _YERWA INCENSE AND MORE_ _(DUNIYAR KAYAYYAKIN KAMSHI MASU MATUKAR DADI DA KAMA JIKI, GIDAH, KAYA DA SAURAN SU)_ _INA MA'ABOTA TURARE? KADA KU MANTA SHI FA KAMSHI RAHAMA NE, KUMA TSAFTA CE_ _TSAFTA KUMA TANA CIKIN IMANI… TOH KU MAR-MATSO KUSA_ _MUN KUMA ZUWA DA HAJAR KAYAYYAKIN_ _*YERWA INCENSE AND MORE*_ _DOMIN SAMUN ZAFAFAN TURARUKAN WUTA NA GIDA, KAYA, JIKI, TSUGUNNO, GASHI... AKWAI KHUMRAHS MASU DADI YAN BORNU, CHADI, SUDAN DAMA SENEGAL, AKWAI OIL PERFUMES, DA TURARUWAN MOPPING DANA WANKA DANA WANKI DANA GADO DA KUJERU DA BANDAKI DA DRAWER DA MOTOCI.._ _AKWAI MAN GASHI NA FESAWA ME SA KAMSHI DANA KITSO. AKWAI KAYAYYAKIN KAMSHI DANA GYARAN JIKI SOSAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA. •_ _ADIRESHI: KANO.. AMMA SUNA TURA KAYAN SU KO'INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE..._ _INGANCI KYAU RAHUSA DA DADEWA A GIDAH DA KAMSHI SAI KAYAYYAKIN TURAREN YERWA INCENSE AND MORE_ _NAMBAR WAYAR SU: 08095215215, INSTAGRAM/THREADS/TWITTER:yerwaincense_and more_ _YOUR NUMBER ONE STOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS... THEY 'VE GOT YOU AND YOUR HOME COVERED_ ::::::::: :::: "Rayuwar nan da muke gaskia ba zata yiwu ba ... Haka zamu cigaba da tafiya kwan gaba Kwan baya shi kenan mu kowa Yana ci gaba amman mu rayuwar mu na sake tabarbarewa. Haba ga nauyi ya sake hawa kan mu. Wutar nepa ma yau da yan nepa suka zo baku ga rokon dana dinga musu ba kar su yanke" Ta karasa fada tana hararo Ashir dake gefe yana jan carbin dake hannun sa. Bappah Auwalu na hankalce da ita sai da ya bari ta Kai karshe sannan yace, "Me kike nufi kenan? Duk kokarin nan da yaran nan suke bakya gani kenan? Allah ya jikan Hindu da rahama ba futa take tana aikatau ba tana nemowa iyalin ta? Ke meya hana ki tashi ki nemo Kya dinga biyan nepar ai dake akeshan wutan kusan kinfi kowa amfana da wutar ma. Kullu yaumin wayar ki na makale a socket" "Lalle ma Auwalu. Ku ba kune mazan ba. Itama Hindu ai junaidu Allah ya jikan rai ba zaman banza yake ba ya tashi tsaya yana nemowa iyalin sa abinci. Kai bakaji kunyar amsar da ka bani ba saboda Allah ? Ai ko a musulunce ca akai uba ya nemo ya kawo. Kuma kaine mijin ba ni ce mijin ba. Don haka kai zaka nemo bani ba. " "Ni ma ai ba a zaune nake ba haka kawai. Ina tashi Ina nemowa iyakacin karfi na. Wutar ai ba dole bace a yanke ta" "To ai kuwa ba zai yiwuwa ba ne. Da maza zagada zagada kamar Ashir ace zaa yanke mana wuta. " "Kinata famfamin magana shin acikin gidan nan suke a zaune? Yaran da duk kwanan Allah sai ya kawo biredi da safe da kayan shayi baya gajiyawa da rana kuma shi da Ashfeef su hada kudi su kawo taliya ko shinkafa ko garin tuwo ayi ajiya kika basu? Ko sassaka su kikayi? Haba dan Allah ki dinga magana kina aunawa a mizanin hankali da tunani mana. Yaran nan dakin da suke ma babu wuta baa jawa dakin wuta ba haka sike kwana sike tashi chajin waya sai dai su kai wajen chaji saboda masifa irin taki. Kai Kai Kai Nusaiba Allah ya kyauta " "To ai gaskia ne. Tunda dai da su ake girkawa aci ai dole su kawo nasu tagomashin. Maganar wuta ma kuwa ai sukan kawo nan din a saka musu. To bayaga haka ma ai arziki suke ci s... "Ya Isa haka dakata nan. Ke wataran dama idan kika fara magana wallahi ko Amnah ba zatayi ban sam ba Kai. Arzikin me suke ci? Yadda Ahmad yake anan gidan haka suma suke. Wadannan yaran arzikin su muke ce, Domin mahaifin su abubuwan da yayi mun har na koma ga Allah ba zan dai na godiya da neman rahamar Allah agare shi ba. Badan junaidu ba da yanzu kwanon gidan nan ya rufta. Ba dan junaidu ba da yanzu kofofin gidan nan sai dai ajingine su. Badan junaidu ba da kowacce damanina sai mun fitar da kayan gidan nan saboda ruwa sai ya cinye komai. Ke ba dan junaidu ba wallahi da ni Auwalu ba zan samu matsugunin zama a Naduka ba bari kiji Ina gaya miki tunda naga ke manta alkhairi ne da ke. Alkhairan da marigayin nan ya mun wallahi ko iyayena sai haka. Don haka arzikin mahaifin su muke ci don kuwa fata nake Allah ya hore. Mun na biya kudin da ya ranto mun nayi gyaran gidan nan da shi. Nayi tambayar nayi cikiyar nayi nayi nayi tun da rasuwar tasa har bayan rasuwar sa dik wanda na tambaya sai yace junaidu bai ranci kudi kimanin haka wajen sa ba. Na gama tabbatarwa na sa ne ya bani kamar yadda da fari yace ba rance yabaniba naki. Don haka sai ya ce mun to ranto mun yayi din amman na bayar a duk sanda na samu babu takura .... Saboda haka dana samu kudi Allah kudin junaidu zan bawa iyalin sa gasunan arzikin su muke ci wallahi. Har gobe " Nusaiba taja tsaki tana karkada kafa tace, "Ni dai na gama magana ai, dole kowanne ya sake zage dantse ya nemo abincin da zaa ci da kudi. Nawraah ki duba acikin gidajen aikin da marigayiya Hindu tayi aikatu kema ki samu inda zakuyi mu rage wasu abun" "Wace nawrahn Anty? Nawraah karatu zata cigaba.... Gaskia ba zatayi aikatau ba" Ashir ya fada yana kada Kai cikin tabbatarwa. Bappah Auwalu ya dubeta ya zabga mata harara cike da takaici da yaki kololuwar mizani yace.... _INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_ _KU MARMATSO KUSA...🔊_ _ZAFAFA BIYAR 2024_ _ZAFAFA BIYAR!!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_ _YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_ _GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_ _________ _1_ *_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_ _2_ *_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_ _3_ *_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_ _4_ *_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ [3/9, 4:47 PM] Hafsaat🧕: _K'K'J_ _(M/W/S)_ _✍️:MX_ _46_ _Assalamu alaikum... HGL CHARITY FOUNDATION. Na neman temako me naira hamsin me naira dari ko sama da haka ko da kayan abinci ne zaa dafa a tallafa abawa mabukata da sukayi azumi a wannan wata mai albarka..._ _idan kudi zaa bayar ga asusun banki na opay 9044191709. Haka zalika idan kayan abinci zaa kawo zaa zo unguwar tarauni dake garin Kano sai akira number opay dincan dake sama_ _zaayi abincin azumi, kosai da Kuma kunu. Wani lokacin harda kankara ta ruwan sanyi ma da za rabawa mabukata masu buda baki.._ _kofa a bude take ga duk Wanda zai taimaka. Allah yabada saa ya hadamu a ladan duka amin_.. ::::::::: ::::: "Nusaiba dan Allah tashi ki bar nan wajen. Don wallahi yadda zuciyata ke tafarfasa ta ke kuna akan maganganun ki da girman Allah zan iya hanbare ki na sumar da Ke yanzu..." "Ni dai na gama magana.... Idan Kuma baa daiku mataki ba zan dauka da Kai na". Mtsceww..." Allah wadaran hali irin na ki nusaiba" bappah Auwalu ya fada Yana grigiza Kai "Aa karka sake tanka ni wallahi. Magana ce ta gaskia nayi. " Ta shiga daki ta dakko pillow ta dora akan kujera, "Ka kwana a parlor banason hayaniya yau" Ta shige daki ta bugo kofa tana murza mata mukulli. Yaran duk suna saukar da idanun su kasa. Kunya ta dabaibaye shi. Nusaiba ta gama renashi yarasa yadda zai yi da ita. Ashir ya mike yana kara waya a kunnen sa ya fice. Ashfeef ma yabu bayan sa. Can daga baya Nawraah ta ja hannun Amnah sukayiwa bappan sai da safe suka fita. Dakin su suka koma. Ashir yasa suka dakko katifar su shida Ashfeef suka shimfida awaje saboda zafi sika nada net. Sai aka yaye labulen su Nawraah su kuma saboda iska ta dinga shigar musu. .. Haka suka cigaba da rayuwar su gwanin ban tausayi. Lalle iyaye bango ne kuma fukafukai ne dake lullube yaran su Wai yau yayan bappah junaidu ne da malama Hindu suke kwana a dakin ajiyar tumaki da kaji. Ba wuta a dakin ba bandaki. Ba wajen girki da ga su sai yan kayan su gwanin ban tausayi. Ko window babu a dakin, Wata iriyar rayuwa sukeyi, Mai ban tu'ajjabi Wanda dole Mai Imani sai ya tausaya musu da hawayen tausayi . Amman duk da haka basu karaya ba. Ashir zai fita tasha da safe yayi lodi yana saka matafiya a mota. Kuma Yana zuwa wajen wanke mota dake tsallaken tashar nanma yana taya maaikatan wajen wanke mota suna bashi dan wani abun... Sannan duk inda ake gini zai shiga ya musu leburanci ya daukar musu bulo ya ebo musu ruwa idan suka bukata ya kwashe baraguzai na gini... Sannan idan sun samu aikin yin fenti na wani gidan ko wata ma'aikatar suna zuwa suyi shi da Ashfeef. Ta haka suke samu su rufawa junan su asiri. Ashir na tsaye tsayin daka akan yan uwan nasa. Duk dai burin sa bai wuce ya wayi gari yaga farin ciki lullube a fuskokin yan uwan nasa ba shakikai da suke uwa daya uba daya .. Ahakan Kuma kullum sai Ashir ya sayo biredi da kudin daya samu ya Kai wa nusaiba sunyi karyawar safe dashi kullum ba gajiyawa wata rana harda madara ma Yana hadawa idan ya samu faraaga... Idan Bai samu ba Kuma Yana sayo biredi da sukari da lipton daya, su sha ruwan bunu. Amman duk da wannan wahalhalin buga bugar da suke suna kawo cefane ana abinci. Nusaiba Bata gani idan Bata ga dama bama sai tace abincin ya kare ko tace ya kone ta zubar ta hanasu abinci ta bawa yaranta kadai.. °°°°° Ashir da Ashfeef a yanzu sun dawo kwanan waje gaba daya sun barwa su Nawraah dakin. Net suke kafawa su saka katifa su kwanta. Da rana kuma su dan zauna suyi hira ko suyi karatu Ashir Yana kara musu duk asubah. Da safe Kuma Nawraah ta koyawa Amnah dai dai hizb din da take. Ashir ya kurbi ruwan dake cikin kofi Yana duban Nawraah dake kalabewa Amnah Kai yace, "Ina takardar makarantar da kika samu? Dakko mun muga" "Hamma kakka damu wallahi ni baki daya karatu yabar Kai na. Allah kuwa" "Banason musu dakko mun. Akwai lissafin da nake acikin Kai na" "Tohm Hamma Yi hakuri" mikewa tayi ta nufi akwatinta ta daga kayanta daga can kasa ta zaro paper ta Mika masa da hannu biyu ya karba yana karantawa... _INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_ _KU MARMATSO KUSA...🔊_ _ZAFAFA BIYAR 2024_ _ZAFAFA BIYAR!!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_ _YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_ _GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_ _________ _1_ *_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_ _2_ *_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_ _3_ *_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_ _4_ *_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ [3/9, 4:58 PM] Hafsaat🧕: _K'K'J_ _(M/W/S)_ _✍️:MX_ _47_ _Assalamu alaikum... HGL CHARITY FOUNDATION. Na neman temako me naira hamsin me naira dari ko sama da haka ko da kayan abinci ne zaa dafa a tallafa abawa mabukata da sukayi azumi a wannan wata mai albarka..._ _idan kudi zaa bayar ga asusun banki na opay 9044191709. Haka zalika idan kayan abinci zaa kawo zaa zo unguwar tarauni dake garin Kano sai akira number opay dincan dake sama_ _zaayi abincin azumi, kosai da Kuma kunu. Wani lokacin harda kankara ta ruwan sanyi ma da za rabawa mabukata masu buda baki.._ _kofa a bude take ga duk Wanda zai taimaka. Allah yabada saa ya hadamu a ladan duka amin_.. ::::::::: ::: "First choice Jami'ar Al-Haramein Naduka mai zaman kanta da ke Naduka crescent (apple island) dinnan? Second choice jami'ar gwamnatim tarayya ta Naduka dake baya, Third choice Kuma makarantar polytechnic ta koyan jinya ta cikin babban asibitin na Naduka.. mashaa Allah. Allahumma barik" "Nagode sosai Hamma. Amma dagaske ni banason zuwa wata jamiaa Allah kuwa" "Kede kita addua Nawraah. Da yardar Allah Zaki karatu a jami'ar nan ta farko kamar yayan kowa. Inshaa Allah Zaki karatu Nawraah. Burin ki da kokarin ki ba zasu salwanta ba inshaa Allah. Fatana dai Allah ya shige mana gaba ya zama gatan mu a dukkanin lamuran mu Allahumma Aameen" "Aameen Aameen Hamma." "Aameen Hamma. Allah ya amince" Ashfeef ma ya amsa. "Eh abunda nake so dake kawai ki cigaba da addua kuma inshaa Allah muna tayaku . Kowane tsanani Yana tare da sauki Nawraah komai daren dadewa. Rayuwar biyu shi akwai gidan duniya da lahira. Allah ba zai bar mu haka ba. Inshaa Allah wannan kaddarar tamu sai ta zama tarihi agaba Nawraah. Ki rubuta ki ajiye. Ko da rai yayi halin sa Nawraah ba zaku wulakan ta ba ni na sani. Ina Kuma da hope akan ki kinji ko?" "Ina sauraron ka Hamma. Amma ka dena fadan haka don Allah Ina jin wani iri Hamma. Inshaa Allah dukkanin mu zamu rayu har ya zuwa lokacin da zamu samu sauki acikin wannan matsatsi da muke ciki. Zakayi aure ka hayayyafa ka tara iyalin da yawa Kai ma Hamma" Murmushi yayi Yana kada Kai yace, "Ba Wanda yasan gobe sai Allah Nawraah. Kuma dan ku ai ba zaa barni ba. Hakama dan ni ai ba zaa bar ku ba. Kawai dai Ina magana ta ne. Zance ne ya shigo cikin zance. Kita addua kede kada ki karaya. Inshaa Allah sai kin zama cikakkiyar babbar maaikaciyar a fadin kasarar nan sai an dinga kwatance dake ana yaban kyawawan halayen ki da temakawa mabukata da Zaki dingayi masu karamin karfi. Hakama Ashfeef Kai ma Allah zai cika maka naka burin ka zama babban dan ball Wanda kasa da ketare zasu yi alfahari da kasancewar sa gwarzo jajirtacce. Sai kayi fice ana nuna ka sai kere su messi su Ronaldo inshaa Allahu. " "Hamma ni fa?" Amnah ta tambaye shi tana mitstsika idanu zatai kuka. Duk ta sake ramewa gwanin ban tausayi daman ba cikakkiyar lafiya ce da ita ba kullum a kwance. Itama har biscuits da cheese balls Ashir ya saya mata ya ajiye ake bata kullum . Ashfeef Kuma ya saya mata bobo guda goma shima tana sha sosai. Ashir ya riko hannunta ya taso da ita ya zaunar da ita akan cinyar sa. Ya saka hannunsa yana tallabo habarta yace, "Ke?.... Amnah ta ai ke babbar maaikaciyar lafiya zaai. Babbar likita Zaki zama inshaa Allah ki dinga temakwa marasa lafiya kina basu kulawa ta musanman cike da tausayin su da kyautata musu kinji.? Allah ya muku albarka gaba daya Allah ya tsare gaban ku da bayan ku Allah ya shiga lamuran ku ya iya muku a dukkanin komai. Allah Kuma ya kare ku daga sharrin masu sharri. Allah ya muku katangar karfe da azzalumai. Allah ya daga darajar ku duniya tasan muhimmanci ku, Ta Kuma yi alfahari da kasancewar ku acikin, Al'ummar ta. " "Aameen Hamma, Amma dan Allah ka dena irin wannan maganganun" Nawraah tace dashi tana hawaye sosai. Bude baki yayi Yana murmushi ya dubi Ashfeef yace, "Kaga? Jaruma ce fa ke Nawraah bansan ki da laushi ba. Banason wannan emotional yanayin naki Allah. Ki jajirce ki tsaya tsayin daka wajen ganin komai ya tafi yadda ya kamata. I count all my hopes n you Nawraah. Ke din KWANKWASON JIMINA ce MAI WUYAR SHAFAWA...." "Ai kuwa dai Hamma gaya mata. Wannan idan ta fara kuka samari da alama kowanne sai ya sakata kuka Allah kuwa. " Ashfeef ya fada Yana Kai mata rankwashi ta goce tana dariya. Suka saka dariya baki daya ciki harda Amnah dake kyakyatawa. Ashir ya dube su daya bayan daya Yana goge hawayen fuskar sa dake tsiyaya yace, 'haka nake son ku kasance ko da yaushe cikin farin ciki . Da dariya dauke a fuskokin ku. Allah ya dawwamar daku cikin farin ciki ya yaye muku dukkanin damuwa ya nisanta ku da damuwar dake cin ku ya lullube ku da rahamar sa allahumma Aameen" "Aameen Hamma tare da Kai." "Eh mana hamma ka dena cire kanka dan Allah" Murmushi yayi Yana gyara Kai yace, "Ai idan kuka kasance cikin farin ciki ku kadai ma ya wadatar. Ni kune nawa farin cikin. Farin cikin ku shine nawa, ganin ku cikin farin ciki shi ke faranta rai na da zuciyata da gangar jiki na. Yan uwana, Ashfeef , Nawraah da Amnah kune farin cikina,. Da ke sanyaya ya Kuma lullube zuciya da ran Hamman ku Ashir a Koda yaushe. Allah ya jikan iyayen mu da rahama Allah ya gafarta musu Allah yasa aljanna makoma ce agare su" "Allahumma Aameen Hamma" "Inshaa Allah Hamma" "Aameen" Yauwa Amnah ta. Ya ce da Amnah Yana lakutar kumatun ta. "Zaki Sha alawa?" "Eh" ta fada tana tafa hannuwan ta. "Nawraah jeku sayo alawa please. Ungo ki taho da omo da sabulu zan mana wanki sun taru. Kowa ya curo nasa" "Tohm Amma dan Allah Hamma ka bari muyi kowa yayi nasa" "Aa ban amince ba. Illa dai Ashfeef zakayi dauraya ka shanya. Ke Kuma ku zauna da amnah idan Kun dawo daga sayo alawar ki koya mata karatu" "Tohm Hamma inshaa Allah. Allah ya saka muku da mafificin alkhairin sa" "Aameen Yaa Rabbi jam'an..." Mikewa yayi ya shiga hada kayan su da sukai datti Yana kaiwa wajen rariya zai wanke. Ashfeef ma ya dakko bokitai ya fara ebo ruwa Yana tarawa a babban baho Wanda zasuyi wankin dashii.... _INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_ _KU MARMATSO KUSA...🔊_ _ZAFAFA BIYAR 2024_ _ZAFAFA BIYAR!!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_ _YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_ _GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_ _________ _1_ *_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_ _2_ *_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_ _3_ *_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_ _4_ *_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ [3/9, 6:10 PM] Hafsaat🧕: _K'K'J_ _(M/W/S)_ _✍️:MX_ _48_ _ADVERT👇👇_ _YERWA INCENSE AND MORE_ _(DUNIYAR KAYAYYAKIN KAMSHI MASU MATUKAR DADI DA KAMA JIKI, GIDAH, KAYA DA SAURAN SU)_ _INA MA'ABOTA TURARE? KADA KU MANTA SHI FA KAMSHI RAHAMA NE, KUMA TSAFTA CE_ _TSAFTA KUMA TANA CIKIN IMANI… TOH KU MAR-MATSO KUSA_ _MUN KUMA ZUWA DA HAJAR KAYAYYAKIN_ _*YERWA INCENSE AND MORE*_ _DOMIN SAMUN ZAFAFAN TURARUKAN WUTA NA GIDA, KAYA, JIKI, TSUGUNNO, GASHI... AKWAI KHUMRAHS MASU DADI YAN BORNU, CHADI, SUDAN DAMA SENEGAL, AKWAI OIL PERFUMES, DA TURARUWAN MOPPING DANA WANKA DANA WANKI DANA GADO DA KUJERU DA BANDAKI DA DRAWER DA MOTOCI.._ _AKWAI MAN GASHI NA FESAWA ME SA KAMSHI DANA KITSO. AKWAI KAYAYYAKIN KAMSHI DANA GYARAN JIKI SOSAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA. •_ _ADIRESHI: KANO.. AMMA SUNA TURA KAYAN SU KO'INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE..._ _INGANCI KYAU RAHUSA DA DADEWA A GIDAH DA KAMSHI SAI KAYAYYAKIN TURAREN YERWA INCENSE AND MORE_ _NAMBAR WAYAR SU: 08095215215, INSTAGRAM/THREADS/TWITTER:yerwaincense_and more_ _YOUR NUMBER ONE STOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS... THEY 'VE GOT YOU AND YOUR HOME COVERED_ ::::::::: :::: Rufe kofar gidan tayi ahankali, Ta shirya tsaf cikin riga da zani na atamfa ta yafa mayafin ta ta rike yar jaka. Ta sauka daga yar matattakalar da ake haurawa ahau gidan nasu Da sauri ta wuce har tana tuntube ta rankwafa kasa dataje wajen dakin su Amnah ta durkusa ta wuce da sauri tana saye fuska. Dan adaidaita ta tare ta shiga ciki . Bata mance da kwatancen gidan data karba ba awajen direban daya kawo wa su Ashir kayan abinci kwanakin bayan tun da ran bappah junaidu. Har kofar gidan ya kaita ta sauka ta lalubo kudin sa a jaka tana kallon darin biyun ta dan adaidaita, ya wafce da karfi ganin taki bashi, ta tsirawa wa kudin idanu. Alokacin Kuma Nusaiba tunani take dama bata zo ba da ta kafa ta daba don tanason ta saka data ta hau duniyar online. Baki ta wangame alokacin data Isa kofar gidan tana yaba tsaruwa irin tasa tamkar a gidajen da ake nunawa a talabijin na masu kudi. Ta nufi gate din tanata sauri masu gadin suka tareta. "Ya ke Ina Zaki?" "Wajen hajiya nazo." "Wacace? Bantaba ganin ki ba anan gidan" "Tabbas bakuwar fuska ce kam, Bana kasar ne" Nusaiba ta dashare baki tana sosa kasan keyarta ta sake cewa, "Kawatace matar gidan" daya daga cikin masu gadin ya bushe da daria har yana rike ciki ya kalleta tun daga kasan kafarta zuwa fuskar ta . Gaba daya ko alamar daukar kalar ire iren kawayen hajiyar tasu batai ba. Don haka ya grigiza Kai hana tabe baki yace, "Ba nan gidan bane Ina tunanin kinyi batan Kai" "Banyi ba fa. Gidan Dr bintu mana. Zan maka karya ne" "Kirata awaya " ya fada yana rera fito. Nusaiba ta zaro idanu tana janyo wayarta ta fara latse latsen karya ta danna wajen kira ta kara a kunnenta, "Eh nazo bintu. Okay bari na shigo. Ai masu gadin nan naki ki canza su basuda kirki. Na gidah na kin manta korarsu nayi alokacin da suka hana hadiza shiga? Okay gani nan" Ta nufi kofar kantar kantar zata shiga Mai gadin ya tare kofar da hannun sa yana hura hanci yace, "Aa... Duk munsan ire iren ku. Ba wata hajia da kika kirawo dan Allah malama ki kama kafa ki koma inda kika fito" Nusaiba ta saka hannu tana mai nuni da shi tace, "Ka bude mun na shiga... Ya sunan ka ne?" "Sunana Naziru gidah Kuma nace ba Zaki shiga ba don bansanki ba bakuwar fuska ce, na biyu Kuma ba wata hajia da kikai waya da ita. Yadda kika zo baki a abude tamkar Zaki handame mu ma kina kallon gidan kowa yasan bakuwa ce ke kuma marar karfi iri na. Don haka ki koma inda kika fito kada kisa na saka miki shocking wallahi" ya karasa fada Yana daga shocking din hannunsa. Wata waya Mai karafuna ajiki tanata hartsatsi "Naziru ko? Ka kyauta ko? Zan nuna maka wacece ni a kasar nan" "Mtsc" Yaja tsaki yana komawa kan kujerar sa Yana rera baitin wata waka, Cikin ikon Allah sai ga fitowar motar direban rannan data gani. Ta dashare baki tana daga masa hannu. Ya yi murmushi shima yace, "Ina wuni? Hajia ta...?" "Kwarai ta Naduka.... " "Tasan Zaki zo ne?" "Munyi waya ai tana ciki" "Eh tana nan. Ya haka nazman ka barta a tsaye ko wani abun kake?" Naziru ya dube shi yana kallon nusaiba yace, "Ka Santa ne?" "Na kakkai su hajia gidan ........... Ta katse shi da sauri tana murmushi tace, "Bai sanni ba ne na masa uzuri. Bari na shiga" Ta kutsa Kai ta gaban Naziru Mai gadi ta shiga ciki. Ba yadda ya iya ya koma wajen zaman sa ya zauna. Shi Kuma direban ya wuce tsalallaken titi wajen masu kankana... Ko data shiga bata San kan gidan ba sai da sata Mai aiki ta nuna nata kofar da zata shiga. Ta shiga ciki bakinta dauke da sallama. Kai tsaye ta shiga parlorn ta hakimce ta zauna ba kowa aciki Sai daga baya Dr bintu ta sakko tana gyara dankwalin ta. Ta dubeta tana kallonta sama sama, "Wacece wannan din?" "Ah hajia ni ce fa. Matar bappan su nawrah " "Oh" ta fada tana dubanta shekeke. Dake Itama Dr bintu akwai jin Kai "Baki iya gaisuwa bane? " Ta sake tambayar ta tana mata kallon tara saura kwata ganin yadda ta babbake akan kujera ta harde kafafu.. "Oh Ina kwana?" "Lafiya. Meke tafe dake?" "Dama zuwa nayi akan kayan abincin da kuke bayarwa kwana biyu shiru. " "Ajiya kuka bamu ne? Na dauka niyyace da temakon musulunci mukayi iyayinmu ko dolen ku akan mu take?" "Hajia kwantar da hankalin ki ni bada wani abun na ce haka ba. Kuma ni a bayan ki nake wallahi" "Bangane me kike nufi ba malama" "Ina nufin rannan ba Nawraah na fadin wasu maganganu ba da kukazo? nufina ki kwantar da hankalin ki nasan komai Kuma bazan bar wani abu ya taso ba muddin kika bani bukatin da nake nema" Dr bintu tayi shiru gabanta na bugawa tasan komai? Kenan tasan Alhaji Sambaso mijinta shi yake kashe malama Hindu 'kjnsan komai fa kikace .?" "Kwarai na sani harda wani abun da ke bakida masaniya ma akansa" Nusaiba ta kara da qarya tana karya Kai bayan ba abunda ta sani Dr bintu ta gyada kai tana gyara zamanta tace, "Me kike bukata?" "Kudi... Kayan abinci.., sutura irin ta ku ta manya. Kuma ba su Nawraah zaa kaiwa ba gidana zaa kawo. Sannan suma su Nawraah ki kawo kudi a basu. Idan kika dore akan haka to shikenan Ina Mai tabbatar Miki komai ya wuce. " Dr bintu ta gyada Kai. Ta mike ta dakko jakarta hannunta na rawa. Ta ciro check dinta ta dakko biro ta rubuta kudi masu yawa ta mikawa nusaiba. "Ki dauki rabi ki basu rabi su nawrahn." "Bakida damuwa ai awajena ma suke agidana ni nake dawainiya dasu ta komai daga abinci zuwa sutura" "Allah sarki. " "Kayan abincin fa?" "Zan aiko a kawo miki inshaa Allah. Zaki iya tafiya yanzu Ina da abubuwa ne agabana" Nusaiba ta gyara zaman ta ta dakko wayarta ta rike tana gyara mayafi tace. "Dan daukeni da wayar ki a haka sai ki tura mun dan Allah"😂 Ba abun Dr bintu tayi, Ba musu ta dauki wayarta ta dau hotunan nusaiba ta tura mata a lokacin Sannan nusaiba ta mike ta futa sukayi sallama. Ta tsaya a gate ta gaggasawa Mai gadin magana yayi banza da ita yana Jin rediyo harda Mai dakuwa ta Zagi. Tana tafe tana addu'ar Allah yasa kar Dr bintu ta gane batasan komai ba. Wani bangaren na zuciyar ta Kuma na mamaki hadi da tabbacin lallai akwai wani boyayyen lamari da suke boyewa. Kuma koma menene Nawraah tasan wani kaso daga ciki... Gidah ta koma ranta fes. Ta boye kudin har nasu Nawraah ta hanasu taki basu. Taki Kuma gayawa kowa kudin data samu da inda taje. Tace wai neman aiki taje a Naduka crescent. Matar ta bata dubu goma tace tayi cefane. Ranar dai abinci har da nama akai kowa yanata mamaki. Dr bintu na lekan nusaiba ta taafi. Jikinta na rawa ta nufi parlorn Mai gidan nata Yana zaune yana karanta jarida ta zauna akusa da shi tana yarfe hannu tace, "Nusaiba dinnan tazo komai tac har abunda bansani ba ta sani... A firgice ya juya ya dubeta bai San sanda ya furta Cewar, "Tasan ni na tunkuda junaidu Mai gidan Hindu ta baranda ya mutu ma kenan." Dr bintu ta mike tana zaro idanu tana girgiza kai tace, "Alhaji.... Kana nufin kace shima kashe shi kayi? Kacemun ya fado bai taka tsani ba ya rasu. Ashe ashe Alhaji Kai ka kashe shi?. Ka kashe matar sa shima din kaje ka kashe shi. Alhaji wace iriyar rayuwa ce. Kisa fa? Kamai da rai tamkar kiyashi Alhaji? Innalillahi wa Inna ilaihi raji'un. Wallahi tallahi nagaji. Yanzu kenan tunda itama ta sani zaka bita ka kasheta kenan?" Alhaji Sambaso ya girgiza kai yana harde hannuwa ban roko yace, "Wallahi bada sani na kashe shi ba. Fada muke na turashi ya Fadi ya mutu. Ki yarda Dani bintu. Zancen gaskia kenan. Ita kuma bansan a inda taji ba Allah" "To magana ta gaskia Alhaji na tsame hannuwanaa akan ka. Maganar Hindu na rufa maka asiri kace kuskure ne na bar maganar. Amman ka sake kashe musu mahaifiy saboda Allah. Wato kenan itama wannan kasheta zakai ko? Daman tazo tana bukatar kudi da kayan abinci da sutura idan baa bataba ba zaa samu matsala. Saboda tana cewa ita kadai ce tasan yadda zatai da Nawraah komai ya wuce " "Karki damu duk abunda takeso zaa mata. Allah zaa yi. Kome tameso. Ni ki yafemun kinji?" "Wace bintu ce zata yafe maka? Ka nemi yafiyar Allah dai ka Kuma roki gafarar iyalin su. Ba ruwana acikin Allah kuwa." "Trust me baa abunda zanwa matar nan Allah shima shi ya takalo ni Yana gayamun maganganu Yana marina kinga abunda ya faru kenan" "Alhaji koma meyake maka sai kayi enduring ka kashe masa mata,shi tunda acikin bacin rai yake. Idan ya huce sai ka gyara amma ka kashe shi?" "Tasu ta kare ne su. Ya za'ai da wannan matar. " "Yanzu dai inada aiki asibiti idan na gama cikin week dinnan zanyi tunani" "Yauwa bintu na Allah ya miki albarka." Mikewa tayi ta fice ta nufi asibutin tah dake bayan unguwar, gabanta nata faduwa . Ko da direba ya sauketa ma ta dade Bata futa daga mota ba saboda tunanin data tafi :;;; Kwanaki suka shude. Alokacin Ashir har ya fara hada kudade sosai na Sanya Nawraah a jamia. Ranar wata laraba da yammaci Dr bintu taje gidan na nusaiba ta Sha mamaki dataga gidan dama aciki suke rayuwa Ta zauna tana kyamatar ko'ina. Aka kawo mata ruwa ma taki Sha. Suka gaysa da nusaiban ta tambayi nusaiban abinda take so. Nusaiban tace yaran su sun samu gurbi a jami'ar Al-Haramein. Amman ba kudin da zasu shiga. Kuma an dena daukar daliban tallafi. Dr bintu tace ba damuwa. Satin sama zaa biga musu admission letter. Makarantar harda share din mai gidan ta Dana hajja qibdiyya. Don haka zaa basu scholarship khauta su nawa ne. Nusaiba tace su hudu ne . Layla, Nawraah, Ashfeef da Kuma Ahmad. Dr bintu tace ba damuwa zaa basu gurbin karatu. Itama yayanta biyu daya zata fara daga kevel one . Dayan Kuma a babban gurbi yake zai karaa karatu ne . .. Hakan kuwa akayi ana shiga satin aka bugo admission letters aka Aiko dasu akace nanda sati biyu suzo su fara daukar darasi a jami'ar Al-Haramein dake Naduka crescent. Hakika su Nawraah sunyi murna. Musamman Ashir daya kasa boye farin cikin sa. Ashfeef da Nawraah ma harda su a gurbin karatun. Wani bangare na zuciyar Nawraah Kuma na kokonto akan amincin Dr bintu da Nusaiba. Don haka ta zuba musu Ido kawai tana nazartar su.... :;; Ashir na zaune akan kujera... Ya sayo second fairly used din waya dake hannun sa.. Ya ciccire komai na wayar ya mayar kan second din daya saya. Ya kuma bar su akan ta ainhin. Recordings din wakokin Nawraah data yiyyi ya ajiye mata su ya Kuma tura wasu a wadda ya sayo .. Daya bayan daya ya shiga danna wakokin larabawa yana saurara duk Wanda batai masa ba ya goge akan wayar daya sayo yayinda dayar Kuma ya ajiye don Nawraah yake son ya barwa duka tunda yanzu ta shiga jamia tana bukatar browsing assignment da sauran su. Tasa Kuma sai Ashfeef ya dinga amfani da ita. Yaje kan wani recording na wakar Maher Zain. Har zai goge sai Kuma ya cigaba da saurara jin tanada dadi. Maganganu ya fara ju suna fitowa daga wayar yayinda recording din wayar baa jinsa sai can daga kasa. Kamar zai goge sai Kuma ya cigaba da saurara Yana ji....jikinsa ya dau rawa jin maganar da macen da mijin keyi. Da sanda ummy take basu hakuri tana bataji komai ba. Mikewa yayi a tsaye . Whatsapp dinsa ne yayi kara. Ya duba wayar dake hannun sa. Ganin fefen bidiyo ne aka tura Masa da wata number ta waje. Yana budewa hankalin sa ya tashi na daga abunda ya gani Jikinsa na bari ya tura budiyon daya wayar daya barwa Nawraah . Ya sake dubawa zai kira number data turo yaga ta bace bat bata kan WhatsApp gaba daya idan ya kirama sai ace batakan network Fita yayi ransa na zugi. Har zai fuce baki daya sai Kuma ya kwaso shanyar da Nawraah tayi ya Kai mata dakin ya koma ya gyara ko'ina ya shigar musu da takalman su da kayan wasan Amnah daki ganin garin da hadari. Ya koma ciki ya dakko Dan balangun daya sayo musu basanan ya dora akan katifar su ya fita Yana rufo kofar sai ga Nawraah ta dawo rike da hannun Amnah "Hamma Ina zaka?" "Ba nisa zanyi ba yanzu zan dawo inshaa Allah. Ungo rike wayar nan taki ce. Ki dinga browsing na assignment da itaa idan kin fara jamia..duk rintsi duk wuya kada ki bari wayar nan fa subule daga hannun ki. Kar ki bawa kowa, Na roke ki da girman Allah kuma recordings din wayar nan kada ki jisu har sai kin shig aji na biyu zaki shiga na uku, sai na hudun kammala jamia kinji ko? . Allah yabada saa" "Hamma meye haka kamar Wanda zaiyi tafiya ba dawowa? Nagode Allah ya saka da alkhairi Amin" "Aameen ya Hayyu waayum. Sai na dawo. " Ficewa yayi dasauri bayan ya yiwa Amnah wasa Yana lakuce mata kumatu Kai tsaye ya nufi ofishin Alhaji Sambaso ya ci sa'a kuwa yana nan. Akayi masa iso ya shiga Yana shiga dama Alhaji Sambaso shi kadai ne. Ashir cikin zafin nama ya cikumi wuyan sa yana kunna masa recording din wayar nan. 'kai ka kashe ummy.... Kuma ka kashe abbiey..." Ya karasa fada Yana daga wayar sa. "Kaga komai nan evidence ne cikin nan. Inshaa Allah rayuwar ka sai ta tagayyara sai ka zama abun tausayi. Zakasha mamaki" "Ka tsaya muyi magana yaro" "Magana? Hahaha zakayi magana aagaban hukuma da gaban Allah ranar gobe kiyama" Ficewa yayi. Alhaji Sambaso ya saka hannu ya shafo habar sa Yana furzar da iskar bakinsa Mai zafi . Wayar sa ya dauka ya rubuta sako ya koma ya zauna Yana shafe kansa. Ba jimawa can wayar sa tayi haske ...ya dauka yana dubawa hamdala yayi ya kwantar da kansa akan kujera Yana sauke ajiyar zuciya.. °°°°° Zaune suke baki daya sai ga waya akan kira number Ashfeef ance suje asibitin Naduka na gwamnati bangaren yan accident da quna. Suna zuwa suka tarar da wata leda an nannade da kyalle. Tamkar an Kona takarda ta yayyanke dinnan tayi baki tayi toka. "Menene wannan din?" Ashfeef ya tanbayan bakinsa bude .. Sauran kuwa suka kasa magana. Daya daga cikin maaikatan wajen yace, " sunyi hatsari ne da wata tankar mai sun kone baki daya. Su bama a gane komai nasu. Kai ma dakyar aka samu wani dan area ku ya bada number ka .... " "Bangane ba 'da na. Me yake faruwa? Konuwar me? . Motar mai kuma?" bappah Auwalu ya tambaya baki daya kamar mahaukaci yama rasa mai zai ce. Gaban Nawraah ya tsananta bugawa tammar zai zullo ya fado, Maaikacin yace. "Bayan dogon binciike da mukai.Sunan sa Ashir junaidu. Ko daga Naduka zone.. Allah ya masa rasuwa" Diiiiim komai ya dauke. Tamkar duniyar ta tsaya chak.baki daya haka suka zama tamkar mutum mutumi dukkanin su aka rasa mai cewa komai. Idanuwa na zubar da hawaye. Hanci na tsiyayar majina ta tashin hankali. Yayinda fitsari ya cika marar su. Kafafuwa sun gaza daukar nauyin su. Hannuwan su na lankwasar tashin hankali, Ya yinda sassan jikin su baki daya suka yi laushi.. "Allah ya jikan ka da rahama... Hamma Ashir." Suka jiyo muryar Amnah daga gefe ta kwanta akan ledar da aka sanya shi namansa sun kone kurmus kamar babbakakken kan rago gaba daya shine sanye acikin ledar sai gutsattarin naman jikin sa kamar an soya su sun babbake sun kone. Yayinda sauran rassan jikin nasa kuwa ma babu sun nike a titi sun kone da mai. Wasu kuma bazasu ganu ba. Kasancewar direban motar. Da shi Ashir din da yaran motar tirelan man duk sun mutu... 🥴🤐Acigaba da bin littafin KWANKWASON JIMINA MAI WUYAR SHAFAWA...... A kuma yi hakuri, bana labarin haka yazo 🙏🤭 #RICH VS POOR #ANEES #MARWAAN #NAWRAH..... #LIFEPARTNERS #AL HUB HAYAT _INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_ _KU MARMATSO KUSA...🔊_ _ZAFAFA BIYAR 2024_ _ZAFAFA BIYAR!!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_ _YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_ _GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_ _________ _1_ *_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_ _2_ *_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_ _3_ *_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_ _4_ *_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ [3/10, 12:23 PM] Hafsaat🧕: _K'K'J_ _(M/W/S)_ _✍️:MX_ _49_ _Koda kuɗinka sai da rabonka. Ka gani su birgeka, ka saya ka birge mai kallonka. Albishirin ku ƴan kasuwa da masoya. Kuna ina? Ina kuka shiga? Maza ku garzayo kantin sauƙi da rahusar ingantattun kaya na kasarku dama ketarenta. Bari na kaiku, *BILYN ABDULL ONLINE SHOPPING* ke muku sallama irin ta addinin musulunci da babban albishirin shiryawa tsaff domin kawo muku kayayyakin buƙatunku na yau da kullum. Tun daga kan irinsu, atamfa, lasses, shaddoji, materials, abayas, takalma, handbags na zamani, vails ƴan yayi. Hijjabai. Sarkoki da dangoginsu. Kayan shafe-shafen dana kwalliye fuska. Agoguna harma dasu eyeglasses na manyan mata. Kai kai Karfa na cikaku da zance, dan zaku iya ganin komai a *BILYN ABDULL ONLINE SHOPPING* domin farin cikinku. Kayan yara harma dana maza ba mata kawai ba. Ba'a sayen ɗai-ɗai zamu tsaya ba harda sari ga mai buƙata zamu bada in sha ALLAHU kuma akan RAHUSA mai sauƙi da kaima zaka samu naka rabon. Zakuma mukai maka kaya a duk inda kake a *NIGERIA* in sha ALLAHU. Ƴan kasuwa masu sari da masu sayen ɗai-ɗai ku garzayo nan domin gani da ido in sha ALLAHU. Ka gani su birgeka, ka saya ka birge masu kallonka sai a *BILYN ABDULL ONLINE SHOPPING*👇_ https://chat.whatsapp.com/Cce1etNkvVKCBlgSqXa4Ek ::::::::: Allahu Akbar! Lalle Allah buwayi ne gagara misali, Ya azurta wanda ya so a sanda ya so. Ya talauta wanda yaso a sanda ya so. Ya raya wanda yaso a sanda yayi iko. Haka zalika ya kashe wanda yaso a sanda ya so. Kuma dukkanin abubuwan nan kaunar da Allah ke wa bawan sa yafi karfin alkalami da bakin da zai furta ..... Hakika ahalin Hamidniyya sun shiga dimuwa wadda ta kere duk yadda alkalami zai fasalta. A gub'i a gub'i sun rasa rayuka hudu ... Daga kan kaka, Uwa, Uba zuwa 'Da wato marigayi Ashir ... Marigayiya yafendo, Marigayiya Hindu, Marigayi Junaidu, da kuma marigayi Ashir. Kuma dukkanin su ba wasu lokaci mai tsawo aka dauka na tazara tsakanin rasuwar ta kowanne ba.... Lalle bawa ya kamata ya koma ya tuba ga ubangijin da ya halicce shi. Domin shi din buwayi ne gagara misali. Mamallakin kowa da komai ... Dakyar likitoci da maaikatan asibitin bangaren sashen suka tausashe su duka tun daga kan Bappah Auwalu zuwa Amnah .suka saka su a mota suka mayar da su gidah dauke da ledar da ragowar naman gawar marigayi Ashir ke ciki... Aka wanke shi aka nannade shi a likafani. Haka dan tsakuren sauran naman nasa sai ya zama kamar jariri ne ya rasu aka nade shi... Akayi masa sallah aka kai shi gidan sa na gaskia wato makabarta gidan kowa... Ba tazarar kaburarruka tsakanin kabarin marigayi Ashir dana iyayen sa marigayi junaidu da marigayiya Hindu... Ashir ya samu mutane, Mutane sosai da sai ka dauka wani babban maaikacin gwamnati ne ya rasu, ko wani babban dan siyasa ko kuwa mashahurin dan kasuwa ne.. Ba ahalin Hamidniyya Lebanon ko ince ahalin marigayi junaidu su Nawraah ne kadai suke alhini ba. Baki daya mutanen Naduka zone suke alhinin rasuwar Ashir. Ya samu yabo sosai daga bakunan mazauna yankin Naduka zone, Dana unguwar da sike da ma yan layin su, da wajen aiyukan sa. Bangaren lodin tasha, Da na gangaren wajen wankin mota, Da inda yake leburanci idan ana gini... Magina sun shiga dimuwa wanda suka san shi. Da ma masu fenti Wanda suke harka daya... Banda tarin mutane da suka zo daga yankin bunza da rasuwar tasa ta riski kunnuwan su. Sun shiga dimuwa sosai. Haka zalika Ashir ya samu jamaa da suka dinga biyan duk wasu bashikan da ake binsa... Suka koma harhada yan kudade suka ce a bawa yan uwan mai rasuwar Allah ya gafarta masa ya kai masa ladan Amin. Haka aka dinga zuwa ana taaziyya. Saboda kowa yayiwa marigayi Ashir shaida ta kirki, Babu ruwan sa da shiga harkar da ba tasa ba, Yana mutinta kowa ga ladabi da biyayya, Bai taba fada da kowa, Kuma kowa nasane, komai kankantar aiki inde halal ne zaiyi a biya shi. Don haka kowa yake shedar sa ana masa addu'oin halayen sa nagari su bishi Allah ya haskaka makwancinsa. Haka aka share makoki... Duk wannan Kwanakin da akai ana makoki. Hankukan kannen marigayin sun tabu sosai tamkar zararru wadanda basa hauka. Don kuwa magana ma sai an tsawatar musu da fada da magig sannan sike yi Sun koma haka haka gwara Ashfeef da Amnah ma. Amman Nawraah mutuwar ta daketa sosai. Don har karin ruwa ma sai da akayi mata na leda biyar . Sun Sha zazzabin na rashin lafiya sun kwanta ciwo dukkan su. Abun ya tayarwa da mutane hankali musanman bappah Auwalu da ya Dan sayi alawa ya Kai islamiyar kusa da su yace arabawa Yara akuma yi addua dan Allah Allah ya sanyawa Yan uwan Ashir su Nawraah hakuri da dangana Ameen.. Sannan ya sake sawa aka musu saukar karatu na alqur'ani. Shi ma Kuma ko da yaushe a sallah da bayan yayi karatu, Yana yi musu adduoi Yana gayawa Allah kan ya farfado da zukatan Yan uwan marigayi Ashir Sai da suka dau dogon zango sosai Kafin su farfado. Amman duk da haka ba wata magana suka cika yi ba daga uhm sai uhm uhm kawai. Kullum cikin Nawraah take. Bappah Auwalu yayi yayi amma Ina ta kasa hakuri kullum sai tayi Kuka sosai idan ta tuno da shi kadai ne dama ya rage musu tamkar shine mahaifi da uwa agare su. To gashi shima an wayi gari Allah daya fi su kaunar sa ya dauke abun sa. Maganganun Ashir su nata dawo mata Kai. Daman wasiyya yake musu duk maganganun da yake fada a baya.tamkar yasan mutuwa zaiyi kullum cikin yi musu nasihar rayuwa yake Yana kara Dora su akan hanya madaidaiciya. :: Toh haka rayuwar ta cigaba da tafiya ta kowanne bangare na cikin sashen littafin. Ko'ina ana samun sauyi na rayuwa wani na dadi wani akasin haka. A yanzu dai babu wadanda duniya ta sauyawa ta kuma juyawa baya fyace su nawrah da suka sake zama abun tausayi. Sun rame baki daya sun jeme. Gashi makarantar tamkar da aka basu gurbi gini har an fara karatu basu taba zuwa ba saboda alunin rashin Dan uwan na su. Layla ma taki yadda taje ita kadai sai da Nawraah. Nusaiba ta daketa ta kyareta amma kmadagas layla tace ita gaskia sai da Nawraah zata fara zuwa jami'ar. Hakan kuwa akayi sai bayan kwanaki hamsin da uku da rasuwar Ashir tukunna sannan Nawraah ta hakura zata fara zuwa jami'ar. Kasancewar bappah Auwalu ya zauna ya sake mata nasiha Mai ratsa jiki da jikinta yayi sanyi ya karkare yace, "Dukkanin wadandan abubuwan agaba zasu wuce inshaa Allah. Haka rayuwar take wucewa yake kamar baayi ba nawrah. Kuma akace wai mutanen kirki Allah ya ke saukewa. Bayaga haka sanin kanki mahaifan ki da dan uwan ki mutanen kirki ne na kwarai. Duk inda mutanen kirki suke masu Kuma su junaidu sun zarce. Kuma wallahi Allah ba zai barku haka ba. Akwai jin dadi agaba da yardar Allah. Domin Allah shi kadai ya barwa kansa sani Nawraah. Tabbas munyi rashi. Amman Allah dayafi mu son su ya karbe su Nawraah. Sai mu fawwala lamuran mu gareshi. Da yardar Allah Nan gaba sai kinyi dariya . Zakiga komai ya wuce. Addu'ar mu kawai sike bukata musanman taku da kuke Yaya agsre su haka zalika Ashir yake Yaya agare ku..Allah ya gafarta musu kinji? Ki shirya goben Dan Allah kuje kinji? Ki dau hakan a ranki ki saka daga gobe kin shiga wata sabuwar rayuwa wadda acikinta ne komai zai yi sauki na matsatsi kinji? Allah ya muku albarka" "Allahumma Aameen Bappah. Inshaa Allahu zanje" "Yauwa haka nake son ji. Mashaa Allah. Bari naje nan layin baya na dawo" "To bappah sai ka dawo" Fita yayi daga dakin nasu. Ta juyar da Kai tana duban Amnah dake. Bacci ta sake ramewa itama baiwar Allah duk sai Kashi baki daya sun mokade. Mikewa tayi ta nufi baya tayi futsari kasancewar akwai rariya da famfo awajen ta dauro alwala ta dakko sallaya ta shimfidah tana sallah. Kan Allah ya shiga lamuran sun ya musu zabi nagari adukkanin abubuwan da suka saka agaba na rayuwar su Allah Kuma ya jikan iyayen su da yayan su. Ya gafarta musu. Jamia Kuma da zasu fara Allah yasa suje a sa'a Amin" Haka ta daga hannuwa sama bayan ta idar tanata kwarara adduan daga nan juna ta dakko alqur'ani ta zauna tana karantawa. Hawaye ya shiga diga daga idanun ta rayuwar su ta baya kawai take tunowa lokacin da dukkanin su suna raye yadda rayuwar tasu ke tafiya ahankali cike da farin ciki. Amman yanzu duk sun rasu, rayuwar tasu ta jima cikin dinbin bakin ciki da ya mamaye farin cikin su na baya ... _INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_ _KU MARMATSO KUSA...🔊_ _ZAFAFA BIYAR 2024_ _ZAFAFA BIYAR!!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_ _YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_ _GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_ _________ _1_ *_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_ _2_ *_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_ _3_ *_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_ _4_ *_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ [3/10, 12:23 PM] Hafsaat🧕: *_KWANKWASON JIMINA!!_* _(MAI WUYAR SHAFAWA)_ 🦩🦯🦾 _✍️: MX_ *_ZAFAFA BIYAR 2024_* _vip pages na arewa👇_ *_arewabooks:mssxoxo_* _*BOOK ONE*_ _paid page :50_ _(FINALE/KARSHE)_ ____ *Zafi* ake yi sosai astagfirullah. Gashi babu window a dakin nasu. Dan Amnah ma da wando take kwanciya kawai. Kusan kwana Nawraah take a zaune tana mata fiffita. Gashi ciwon ta kwana biyu ya motsa ya lafa ya dawo yakeyi. Duk yan kudaden da aka raba musu na ragowar gadon su baki daya har na wajen marigayi Ashir duk akan rashin lafiyar Amnah yake tafiya. Saboda lalurorin ta masu cin kudi ne... Bappah Auwalu yayi yar buga bugar da zai yi ba wani kudi da yake samu. Wanda ya dan samu din Nusaiba sai ta kwace tace yara ba lafiya su Ahmad zata saya musu magani.... Ko da yake maganar zaa fasa wundo a dakin dasu Nawraah suke. Haka nusaiba a ranar tun safe ta dinga tijara har dare tana dire tsallan albarkar wallahi babu mahalukin da ya Isa ya fasa mata wundo . Ai dakin mallakin ta ne halaliyar ta ne din haka Bata amince ba. A ranar tsabar bakin ciki sai da Bappah Auwalu ya jera mata marika har biyu a kuncinanta ta dafe kuncinta tana duban sa, "Ka mareni Auwalu?" "Na mareki nusaiba. Kiyi abunda Zaki. Haba mace sai kace zazzauciya ? Aradun Allah wani mai tabin kwakwalar ma yafi ki sanin abunda ya Kamata. Ace ke kwata kwata ba digon tausayi a ranki? Ke fa uwa ce. Kin haifa gasunan agaban ki. Baki tsoron ayiwa naki haka?" "Okay baki zaka mana kenan ni da yaran? To ni na haife su da Kai na kenan? Kai ma ai jinin ka ne. Ko ka ki, ko ka so su, su din da baka son su dai sune 'yayan ka na cikin ka wadancen yayan dan uwan ka ne" "Duk daya suke awaje na, 'yaya na ne. Wai tsaya na tanbaye ki. Baki tunanin mutuwa ne? Bakya tunanin idan kika mutu kika bar naki yaran wa zai rike mike su? Ko gani kike ba mutuwa Zaki ba jiran duniyar zaa bar Miki eh? Idan baki sani ba duk abunda kayiwa Dan wani ko kaiwa wani na badai dai ba Allah sai anyi akan naka. Musanman maraya wallahi maraya yayi kuka akan zalun tar da kake masa na rantse da Allah Allah dai ba zai barka a haka ba. Na Miki karatun nan nayi nayi amman saboda kwakwalwar kifi ce dake Sam kinki dauka to bari kiji wallahi kin Kai ni karshe. Kinsan Allah sai anyi window a dakin nan sai dai ki hadiye zuciya ki mutum ai dan uwana ne yabaki wajen Kuma mahaifi ne agare su. " "Sai Kuma kayi. Duk wadannan zubar maganar da kake kamar rubabbiyar bishiyar kanya ba damuna take ba kaji na gaya maka. Abunda na sani wallahi summa tallahi idan akayi window a dakin nan sai kasha mamakin abunda Zan aikata narantse da Allah sai kayi dana sanin sani na" "Ko? Yo zan nuna Miki ni ne mijin ni ke auren ki ba kece ke aure na ba. A karkashina kike. Kina wani tunkaho kina chatting da matan manya kina hada kanki da su. To bari na tuna Miki Naduka mu zuwa mukai, Baki ne ba anan aka haife mu ba. Kuma mu ba kowan kowa bane bamuda ko sisi. A baya munyi dukiya a bunza a zuriyar mu ta hamidniyya lebanon Wanda ke bakya ciki ma. " "Yanzu ka fito da abunda yake ranka Auwalu. Gorine Allah na tuba ba yau ka saba ba. Naji bani acikin zuriyar ku ta hamidniyya Lebanon Amman Nima nawa jinin ba matsiyata bane. Allah na tuba kuda kuka Tara dukiyar yanzu Ina fake eh? Mutum ya dinga sanin maganar da zai fada ba' "Ke dalla can sakarya. Wadda ke bude baki waaaa tana zuba agaban yaran data haifa. Allah ya jikn Hindu a ranar da zata rasu ma sai data Miki nasiha ki kula da yaranta Amma baki daya kinyi fatali da zacen ta" "Haba nagaji ya ishe ka haka. Hindu Hindu Hindu Hindu kullum dai ba gajiyawa" "Hmm. Faccalanci dai ba hauka bane. Wannan rashin hankalin naki tun kina amarya na daukar faccala kamar kishiya ba Zaki sauke shi ba. Ace mace ta mutu ma Amman baki dai na kishin faccala da ita ba. Bayan ita bata zauna dake a faccala bama sai yar uwa.. Allah ya wadaran halayar kishin ki ta faccaloli datafi ta kishiya wannan hauka ne. Duk wannan tsanar da kike wa halainta daga nan ta farko. Saboda ta fiki da komai ko. Ta futo a tsatson manya tsatson mu daya sannan anmata kaya na yar manya lokacin bikin su. Sannan tanada kashin samu da yalwar arziki a komai ta kere ki shine dai kike wannan abubuwan to Allah ya kyauta. Ace ta rasu ma Amman kin cigaba da bakin kishin faccalar ki akan yaranta. Suma abin Yana bi su. Allah ya kyauta." Nawraah da fadan su ya isheta ta jima daki ta dauki hijabi ta zura ta rike hannun Amnah zasu fita nusaiba tace, "Kagani ko? Yanzu wannan ita zataje haka? Ni fa ban yadda da wannan yawon naki ba kina wani rike hannun Amnah." Layla ta mike zatabi bayan Nawraah. Nusaiba ta janyo ta ta bayan rigarta , "Ina zakije? Ba bu inda Zaki bita. Koma ki zauna ba Zaki koyo wannan halayyar tata ba ta fita gaba gadi kullum a titi ", Bappah junaidu daya kasa magana saboda tsananin bakin ciki kawai ya durkusa ya gyara zaman takalman sa ya shige cikin gidah Nusaiba tabi bayan Nawraah da harara tana yatsina fuska tana gatsine gatsine . Ko da Nawraah suka futa tsayawa tayi ajikin bango tana kife kanta hawaye ne masu dimi suka shiga zirara daga idanun ta na bakin cikin kalaman nusaiba. "Kenan zargina take? Zargina take Ina aikata wani abun awaje kenan na haramci! Yaushe nake fita nida kullum Ina gidah? Yaa Allah kana gani Allah ka mun sakayya. Allah ka dubemu ka saka mana. " Ta share hawayen ta ta cigaba da tafiya tana rike da hannun Amnah. Baki daya ta gama tsorota da halayen nusaiba. Ta Kuma gama yanke kundurinta kawai "Ko guduwa zamuyi mu bar garin? To muje Ina? Ko mu rama abunda take mana mu fasa window ta karfi? Kai Yaa Allah Yaa Allah" ta karasa fada tana dafe kanta dake mata tsananin ciwo Suna ta tafiya har zuwa Naduka crescent. Suka tsaya awani shago ta dakko nera hamsin din wajenta ta sayawa Amnah biscuit da alawa kamar Koda yaushe. Ta kan Dan fitar da ita haka su sha iska saboda dakin da suke babu window. Gidan su nusaiba Kuma da sunje shan fanka take fara hararae su. Shysa Nawraah take dan zagawa da Amnah su sha iskar Allah ta waje. Ko Amnah taji dadin jikin ta. suka cigaba da tafiya.. Tana daga Kai ta sauke akan dankareriyar jami'ar nan da akace sun samu gurbin karatu ta Al-Haramein Naduka. Tsayawa tayi sosai tana yaba kyawu da tsaruwar ginin na makarantae. Sai kache a turai. Manya manyan gidaje ne na masu kudi a layin harda gate dinsa layin . Ya hadu kwarai matuka layin dan Bata taba zuwa nan haka ba ta shagala tanata kallon ko'ina lungu da sako. Kallon ta ya sauka akan tankamemen wani katon gidah an rubuta masa NADUKA GRAND ORPHANAGE PALACE a kasan Kuma an rubuta (Gidan Marayu) gidan marayun na kallon wani sugnoard da taketa tunanin a inda tasan sunan wato DR. ABUBAKHR DOLLARS DWELLING.... Zuciyarta da gangar jikinta nata ingizata ta shiga cikin katafaren gidan marayun janye da hannun Amnah. Ga mata nan Yara da manya harda Wanda ake rikewa a hannu Kuma duk marayun ne. Ga Kuma wani bangare daga hagu can an saka wasu manyan wayoyi na karfe anyi Katanga an rufe wajen maza ne can kuma bangaren su Da sauri ta shiga cikin reception/waiting area. Sukaga matar in charge of wajen Nawraah ta karasa ta gayshe da ita hakama Amnah "Meke tafe daku Yan kanne na?" Matar ta tanbaye su. Nawraah ta dan sunkuar da kai tana lankwasa Yan yatsunta tace "Marayu ne iyayen mu sun rasu da babban wan mu. Daga ni da kanwata sai dayan yayan mu muka rage. Bamuda wani sauran gata da yarage mana. Shine Allah yasa na biyo nan yankin haka naga nan gidan marayun. Bansani ba ko kuna daukar marayu ko Yaya a abun yake?" "Allah sarki Allah ya jikan su da ra rahama. Daga wace ungeua kukazo kenan?" "Aameen Yaa rabbi. Daga Naduka zone muke" "Okay to .. bakuda wasu Yan uwa ne haka da sauran su?" Nawraah tayi shiru tana tunani. Wane yan uwan Zata ce bayan yan uwan nasu sun juya musu baya. Da su da babu su duk daya ne. Bappa Auwalu ne Kuma yayi iya yinsa, matar sa tafi karfin sa. Shi ma Kuma bashida halin da zai iya rike su, da sauri tace, "Ba muda kowa. Duk sun rasu dama daga birnin bunza mu kazo da iyayen mu Kuma daya bayan daya cikin kankanin lokaci duk suka rasu kowanne ba rata da daya sosai " "Allah ya rahama musu" "Aameen yaa rabbi" "Abunda za ai shine. Kuje kuzo da yayan naku da kayan ku kawai. Din yanzu ma ba paper da form da sauran su.." "Toh inshaa Allah" "Nagode sosai. , bari muje" Nawraah ta mata sallama suka fita. Sunzo zasu wuce ta kofar signboard din gidan dazu taga wata zungureriyar mota da alama kaya ne aciki, sai wasu biyu masu matukar tsada da fara da blue hadaddun motoci, sun bi bayan babbar motar suka nufi gidan dataga signboard din DR. ABUBAKHR DOLLARS DWELLING. Motocin suka tunkari gate din da alama mutanen gidan ne sukayi tafiya suka dawo alokacin. Tayar dayar motar bayan ta sache alokacin direban ya kasa jarasa shiga da motar gidan. Gashi sauran motocin ba dama su shiga. Motar ta tokare... Wata kyakkyawa mata tafito daga cikin bayan motar owners corner tana gyara mayafin ta.. Bayan tafito ne wani matashin saurayi shima ya futa daga bayan moyar Yana latsa wayar hannun sa. "Anees...." Matar takira shi da alama mahaifiyar sa ce saboda tsananin kamar da suke. "Naam Mami" "Yi sauri mu shiga mana. Ka tsaya. " "To mami" Yana biye da ita a baya suma yan sauran dayar motar suka fito daga ciki. Harda babban mutumi. Kana gani kasan mahaifin su ne. Yana tafe da waya a kunnen sa yana amsawa. Can kuma sai ga mace da namiji suma da Nawraah take kyauta zaton Yan gidah daya ne. Saboda suna kama. "Anees, junior meye haka kuzo mu shiga gidah mana. Ke Hayfa duba bayan mota na manta USB cord na ki dakkomin " 'Anees, Junior, Hayfa...." Nawraah ta shiga nanata sunayen su tana waywayawa baya har suka shige cikin gidan su. Itada Nawraah suka dauki hanyar gidah a filin ball taga Ashfef Yana buga karasa ta sanar da shi duk abubuwan da akayi tundaga gidahn Bappah Auwalu da nusaiba ya zuwa gidan marayun data gani. Kan zasu koma da zama nan Ashfeef bayi musu ba. Yayi addu'ar Allah ya zaba musu abunda yafi alkhairi idan zaman dakin tumakin ne alkhairi Allah ya zaunar da su idan kuma tashin su ne Mafi alkhairi Allah ya hada su da Mutanen kwarai Suka koma gidah Nawraah ta fara hada musu kayan su ta gama tsaf. Asubar fari suka bar gidan suka nufi gidan marayun... *ALHAJI SAMBASO AVENUE* Shirye shiryen dawowar yaran Dr bintu takeyi. Kowanne da irin abincin da yake so.. Karfe hudu na yamma jirgin su ya sauka..direba yaje ya dakko su Matashin saurayi ne mai jini a jika. Wanda mahaifiyar su Dr bintu ta nufe sy tana musu lale marhaban.. Marwan ya rungume mahaifiyar tasu Yana murmushi. Harda kunan Dadi. Lily kuwa ko ajikinta ta yi murmushi kawai tana yrigzia Kai. :;; ..... Bappah Auwalu ya nemo su Nawraah Yana rokon su dawo kusa da shi Nawraah tace gaskia zaman su ya kare agidan nan. Yana rokon sa suna rokon sa ya kyale su Domin dakuna ne da gado hudu a dakin gidan marayun... Kowanne daki Itada Amnah kowacce da gadonta sai Kuma wasu yammata suma guda biyu suma da gadajen su. . Da tv dinsu harda fridge mashaa Allah ga fanka da ac, ac din kunnawa ake a kashe idan tayi awa biyu. .. A dole bappah Auwalu ya hakura ya barsu Amman sai da yayi hawayen nadama musanman kasancewar matar sa Nusaiba itace silar komai, komai ya baci da 'yayan dan uwan nasa shakikan sa... Haka ya hakura ya koma gidah zuciyar sa na kuna... Ranar lahadi su Nawraah da Layla suka sukaje kasuwa suka dan sassayo kayan gwanjo.saboda zuwa school . Suka shirya tsaf. Layla ta bugawa Nawraah suka nufi makaranta ranar washegari.. *Al-Haramein university* Baki daya kusan rabin daliban tsayawa sukai suna kallon su Nawraah suna musu dariya. Ganin Shigar su daa kallo daya zakai musu kasan talakawa ne. Cikin haka suna shiga ba dadewa sai ga motocin biyu sun shigo ta ciki suna yar tsere. Dalibai aka taru akan su. Motocin ma kadai abun kallo ne. Saura kadan ya Nawraah data tsaya tana duba jakarta . Ya fito a harzuke Ya daddanna mata horn taki matsawa, ashe bataji ba hankalin ta ya tafi kan Jakarta, Yan kudin ta naira dari da Ashfeef ya bata taci abinci ne bata gani ba. Futa yayi da niyyar mata magana a tsawace. Marwan ya futo da sauri daga tasa motar Yana rike hannun anees daya yiwa Nawraah nuni da yatsa Yana dubanta. Yasan shi da zuciya. "Ke daga fuskar ki, How dare you? Ba ki gani ne ko ke bebiya ce. ?" Nawraah ta daga Kai jin an mata magana kanta a kasa sa, don Sam bata ji ko gansu ba sai alokacin, hankalin ta baya jikin ta. Cikinta nata kugin yunwa.. Tana dagowa suka zuba mata idanu atare. Anees ya nemi abunda zai fada mata a abakin sa ya rasa. Haka Marwaan daya kasa hakuri ya lankwasa kansa Yana dubanta. Tayi musu matukar kyau fiye yadda alkalami zai rubut. Rakabewa tayi ta gefen su ta wuce, ganin sun mata shiru... "Senior man na nayi new catch ta. Ina Kai nayi mata ma ni wannan yarinyar kallo daya tatafi Dani, zan auretaa" Marwaan ya fada Yana shafa keyar sa Anees Yana so yace shima ya fara jin wani ahu akanta sai Kuma yayi shiru jin abunda Marwan ya fada. Don dama ba iya magana zai yi ba haka halin sa yake. Kuma bayason wani ya hadasu da abokin sa, kasancewar iyayen su aminai ne suma Kuma aminan juna ne. Har ta kule musu gano basu dai na kallon ta ba musanman Anees da idanunsa suke sexy eyes kamar Mai bacci yadda yake kallon ta da idanunsa daya narjse akanta Kai kanka sai Kaji wani irin idan kai ake ma. Zamu iya Kiran kallon da love at first sight. A hausan ce kallo daya yayi mata zuciyar sa sai ta kamu. Tana yin nisa dai dai wasu kujeru ta zauna tana mayarda numfashi. Layla ta karasa wajen tana dafa kafadar ta, 'kai kiban tsoro wallahi ..." "Dalla dan abun tsoron baya Miki yaw?. Na tambayi sunan su. Kinga wancen dogon me haske kamar balarabe sunan sa ANEES ABUBAKHR DOLLARS.... wancen dayan abokin nasa shima kyakkyawa wayyo har na fola shi Kuma sunan sa MARWAN SAMBASO, ance iyayen su nada share a makarantar nan. Iyayen su multi billionaires ne. Amma baban ANEES din yafi baban MARWAN kudi. Alhaji Sambaso... Shine sunan mahaifin MARWAN! Shi kuma baban ANEES din sunan sa Dr. Abubakhr dollars" Nawraah tayi shiru tana tunani aina tasan sunan ma? Tamkar tasan su ko sunayen su take ji? To amma a Ina? Sam ta kasa ganewa ta yamutsa fuska kawai ta riko hannun Layla suka tafi. Layla nata tsokanar ta tace, "Wannan ace su biyu su so ki, lalle zaa sha gwagwarmaya.. Kinga kallon da kowannen su yake miki kuwa? Tab akwai kallo agaba Nawruhs........" Nawraah tayi murmushi kawai tana girgiza kai tache, "Rufamin asiri Laylus..." Kai tsaye suka nufi department dinsu na course din da zasu karanta. Wato department of CRIMINOLOGY... TIRKASHI!!! Akwai sauran ruguntsumi agaba.... ::: #RICH VS POOR #CRIMINOLOGY/CRIME/CONVICT #ROMANCE #LOVE/AL-HUB HAYAT #LIFE-PARTNERS #KAUNA MARAR GAURAYE _Alhamdu Lil Laahi! Duka duka anan ni Nana hafsatu zan dire alqalami na... Wannan shine shafin karshe na kashi daya na wannan littafi mai suna a sama. Wato mun kammala shafukan *BOOK ONE...* sai kuma bayan mun kammala Ibadah ta watan ramadhan inshaa Allahu. Anyi bikin sallah. Da yardar Allah sai mu dora daga inda muka tsaya. Wato zamu dora da sabbin shafukan *BOOK TWO* kenan..._ _Ina fatan masoya wannan littafi zasu cigaba da karantawa idan muka fara posting *BOOK TWO* Bayan bikin sallah Inshaa Allahu .. ayi hakuri da yadda littafin wannan karon yazo. Fata dai Allah yasa mu amfana da darussan ciki, Ya hadamu a ladan duka. kurakuren dake ciki rabbana ya yafe mun da ku baki daya .. Aaameen_ _Kowane dan adam tara yake bai cika goma ba. Ina neman afuwar dukkanin wanda na batawa rai farawar littafin nan zuwa inda na tsaya . Allah yasa muyi Ibadah karbabbiya Allahumma Aameen_ _Aje a saya turaruwa masu matukar kyau da kamsasawa. A kamfanin YERWA INCENSE AND MORE. Idan kunje kuce a hada muku da mukammaria da set din zafafa biyar... Idan anje ache daga zafafa biyar ne akwai ragi....08095215215_ _Ina masu son samun gwaggwabar lada ta ciyarwa da azumi?HGL CHARITY FOUNDATION ta kawo muku komai cikin sauki, Masu nera ashirin , hamsin, dari da sama da haka. Ko kayan abinci ma zaku iya bayarwa don talafawa mubakata. Tarauni Kano... 9044191709 OPAY... zaa yi kunu, kosai, abinci, ruwan sanyi, da duk yadda hali ya kama a dafa abawa mabukata masu azumi, Dan Allah a saka ko nawane a sami lada idan kayan abincin nema sai a Kira number opay din akai musu gidah Allah ya hadamu a ladan duka Aaameen_ _Tohm masoya makaranta zafafa. Yankin KWANKWASON JIMINA.... MAI WUYAR SHAFAWA.. Anan zan dasa aya. Sai cigaban a littafi na biyu (BOOK TWO) idan Allah ya kai mu bayan sallah da yardar Allah_ _Allahumma Ballighna Ramadhan! Allah yasa muyi Ibadah karbabbiya. Allah kuma yasa ayi sallah lafiya Allahumma Aameen..._ _INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_ _KU MARMATSO KUSA...🔊_ _ZAFAFA BIYAR 2024_ _ZAFAFA BIYAR!!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _ZAFAFA BIYAR!!_ _SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_ _YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_ _GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_ _________ _1_ *_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_ _2_ *_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_ _3_ *_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_ _4_ *_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_